DAREN GOMA SHA HUD'U Complt

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 100

9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

This is historical adventure story which occurred during the era of slave trade in
one of the biggest and prestigious kingdom in middle east........

K'atoton jirgin ruwa ne irin gari gudan nan yana tafe a saman tekun atlantic ocean
cikin tsakiyar daren goma sha hud'u,duniyar tamu gauraye take da hasken farin wata
yana hasken ruwan teku,idan mai hange ya qure dubansa gabas da yamma, kudu da
arewa babu abunda zaka hango sai ruwan tekun bahar maliya wanda baida iyaka,tamkar
gbdy duniyar tamu ruwa ne sbd girman ruwan teku,jirgin ya fito ne daga nahiyarmu ta
africa zuwa qasashen sahara.....

A cikin wannan jirgi kowa yana sabgogin gabansa tamkar ba a saman teku suke ba,
yawancin fasinjojin wannan jirgi larabawa ne da turawa wanda suke zuwa qasashenmu
na baqar fata kwasar al'umma su kaisu qasarsu su maishesu bayi, yanzun ma hknne don
kuwa kusan dukkanin baqar fatar daka gani cikin wannan jirgi toh yana daya daga
cikin kamammun bayin da suka kamo a qasashenmu na africa,wasu y'an mata na gano
cure wuri guda daka gani dukkaninsu sun fito ne daga mabambamtan qasashe don
kowacce cikinsu yanayin shigar jikinta ya bayyana hkn, wasu yan fillo na gano sanye
cikin shigarsu ta saqi daga ganinsu fulanin ruga su biyar ne kowacce ba baya bace a
fagen kyan halitta saida daga qarshen duk na rauna kyawun halittarsu lkcin da idanu
na suka sauka bisa kan d'ayan cikinsu dake takure wuri guda ta sanya fuskarta
tsakanin cinyoyinta nayi nasarar tozali da kyakykyawar fuskarta wannan yar fillo ne
lkcin da wani bature dake gefensu yasa hannu ya dago dakanta ya busa mata hayaqin
sigarin dayake busawa,lalle tsarki ya tabbata ga ubangijin daya qagi wannan
kyakykyawar halitta, tana da dara dara idanu farare tas tamkar madara, bakinta dan
mitsitsi ga le6enta pink tamkar ta sanya jan baki, hancinta dodar yake, kanta babu
dankwali hkn ya bani daman ganin tsawon gashin kanta, gashin ra6e yake gida biyu
rayi kalba, tsawon kalbar ta sauka har duwawunta ga gashin sai kyalli yake don
baqine qirin irinna fulanin usul,billah Allah yyi ruwan tsallar madarar kyau a
wurin, tsantsar kyau ne kawai daga rabbil izzati babu alqus.....

Jikinta rawa yake,haqoranta na had'uwa da juna ta qara qudundune jikinta a cikin


wani kwali dake gefenta don dukkaninsu a yashe suke a qasan jirgin, babbar cikunsu
ta matso kusa da ita tana ta6a jikinta tace" bimbii zazza6i kk,jikinki da zafi
sosai" tana mata mgn ne da harshen fillanci,shiru ta mata batace komai ba, baturen
dake kula dasu ne yazo wurin yana kallonsu sai kuma ya d'ora hannunsa a jikin
bimbii yaji da zafi sosai yace"noo" watsa musu harara yyi yana huci don shi abunda
ya tsana ya samu mara cikakken lfy a cikin bayinsa,gani yake tamkar asara zeyi
kafin ya isa dasu wurin da saidawa,kuma ma ba kowa ne yake siyan bawa mara
isashshiyar lfy ba, dafe kansa yyi ya koma ya zauna ya cigaba da busar sigarinsa,
wani balarabe dake gefe guda shima tafe yake da nasa bayin ya kalli baturen yace"
ita wannan bata da lfy ne" mgn yake masa cikin British English irinna na qasar
birtaniyya, d'ago da kansa yyi ya kalli balaraben yace" ehh" tasowa balaraben yyi
yazo wurin yana kallonsu sai yyi murmushi ya kalli baturen yace" idan kana so sai
muyi musanye na baka bawa mai lfy ka bani ita" tuni baturen ya miqe ya kalli
balaraben yana dariya yace" nunamin bayinka sai na za6a dakaina" murmushi balaraben
yyi ya nuna masa tawagar bayinsa wadanda kusan dukkaninsu zaratan samari ne majiya
qarfi saidai mafi yawancinsu qabilu ne" kallonsu ya dingayi har idanunsa suka sauka
kan wani murd'add'en basamuden mutum mai ji da qarfi ya dafashi yace" muyi musanyan
da wannan" hk balaraben yasa d'aya daga cikin masu kula masa da bayin ya kunce
wannan mutumi ya damqawa wannan bature shi kuma ya taso qeyar bimbii ya kawo masa
cikin jerin bayinsa, tana kuka sauran yan'uwanta suna kuka hk don dole suka rabu
ita ta koma cikin jerin tawagar bayin wannan balarabe......

A jerin bayin nasa su biyar ne kawai mata kuma kowacce yarenta daban ba wanda yake
jin yaren wani, sauran duk maza, tunda ta koma wannan tawagar ta koma tamkar kurma,
basa iya mgn da junansu don basu jin yaren juna, zazza6in dake jikinta ya soma
tsananta sai rawar d'ari take gashi babu abun rufa hk dai ta takure wuri d'aya,
wani saurayi ne d'an qabilar igbo fari sol dashi ya matso kusa da ita ya cire rigar
sanyin dake jikinsa ya rufa mata, jin a rufe ne yasa d'ago dakanta tayi tana
kallonsa sai kuma ta komar da kanta kan guiwowinta, mgn yyiwa daya daga cikin masu
kula dasu ya miqo masa ruwan sha a wata kwarya ya ta6ata ta d'ago da sauri ta matsa
daga kusa dashi don su babban zunubi ne a rugansu namiji ya ta6a mace shiyasa tayi
saurin matsawa,miqa mata kwaryan ruwan yyi ta miqa hannunta ta amsa ta soma sha
sannan ta miqa masa cikin harshen fillanci tace ta gode.........................

*Wannan novel na siyarwa ne karki soma karanta free pages idan kinsan baki da halin
siyan sauran pages wannan shawara ce........Ga wacce ta shirya siye zaki tura #300
ta wannan detail din

acct no: 0100790419

Bank:Union bank

Name: Alhaji shahida Nasir

Idan kin tura saiki turomin da screensht na payment naki ta wannan layin

07041195806

Alk'alamin Bintuu ne👌�


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

2
Kwanaki sun shud'e anyi dare dayawa duk sun shud'e amma sukam suna doron ruwan teku
suna tfy rabonsu da doron qasa sun jima, duk cikin wad'annan bayi babu wanda yasan
qasar da suka nufa abunda suka sani kawai an kamosu daga qasashensu an sakosu cikin
jirgi a matsayin kamammun bayi,tunda bimbii ta soma zazza6i wannan saurayin d'an
kabilar igbo shike kula da ita yana tausayin bimbii sosai sbd gsky tana da qarancin
shekaru, sanyi na ratsa dukkanin sassan jikinsu amma saidai su takure wuri d'aya
don babu abun rufa, shi kuwa wannan saurayin daga shi sai wata yar qaramar riga don
ya cire rigan dake da kauri a jikinsa ya rufawa bimbii, jirgin nasu ne ya soma
tangal tangal tamkar ze kifa kowa cikin wannan jirginsa cikinsa ya d'uri ruwa sbd
tsoro, riqe hannun bimbii yyi qam don yaga gbdy ta rikice cikin ikon Allah jirgin
ya koma yadda yake normal, kowa ya soma ajiyar zuciya, bimbii a hnkli ta janye
hannunta, kallonsa tayi taga alamun shima dai yana jin sanyi amma ya gwammace ya
rufa mata jacket dinsa, hannu tasa ta cire rigan daya rufa mata ta rufa masa,
kallonta yyi yana qoqarin cire rigan tayi saurin dakatar dashi da hannunta cikin
harshen fillanci tace" bana jin sanyi ka sanya kawai" be fahimci mai take fad'I ba
amma ya fuskanci abunda takeson yyi, murmushi yyi mata yace"nagode" saurin dago da
kanta tayi tana qare masa kallo don tabbas idan har ba kunnenta ne ya jiye mata ba
daidai ba kamar hausa taji yyi,tana jin hausa itama 2kad'an don tana fita kasuwa
tallan nono, tace" kana jin hausa ne" murmushi ya kuma mata a karo na biyu yace"
ehh,amma ni igbo ne daga Abia nk" tace" me sunanka" yace" obinnah" yace"ke me
sunanki" tace" bimbii" ya qara nanata sunan nata yace" daga ina kk" tace" ruganmu
tana kudu da qauyen lamirde cikin garin gombe" kad'a mata kai yyi alamun ya gamsu,
daga shi har ita babu wanda hausar tasa ke fita daidai duk tata suke a hausar amma
hk suke dan mgn, bimbii bata da yawan zance amma saita samu kanta da sakewa dashi,
cikin tsakiyar daren goma sha hudu jirginsu ya samu isa matattarar tsayawar jiragen
ruwa wato Brandford port dake Amsterdam,tunda suka fito daga jirgin nan suke 2kalle
kana ganinsu kaga k'auyawa, dole kam suyi k'auyanci don kaf nahiyarmu ta africa ba
irin wannan port din, turawan dake kai kawo a wannan port kuwa kallonsu suke tamkar
kashi sbd tsabar racism, dukkaninsu babu wanda ze iya fad'ar sunan qasar da suke
amma yanayin kalar fatar mutanen qasar ya tabbatar musu qasa masu jan kunne ce wato
lardin turawa suke, falmata d'aya da cikin yan'uwan bimbii da aka rabasu tun a
jirgi ta saci jiki daga cikin tasu tawagar ta shigo cikin tawagar su bimbii, riqo
hannun bimbii tayi tana kuka tace" bimbii zamu rabu gbdy kin ga zasu kuma shigar
damu wani jirgin bamu san inda zasu kaimu ba, mudai tamu qaddarar kenan sun rabamu
da danginmu sun shigo damu duniya,bimbii ki kula da kanki sannan ki saukar da kanki
kiyi duk abunda suka sanyaki don basu da imani zasu iya kashe mutum" kuka suke
sosai suna qanqame da juna har lkcin da baturan dake jagorantar tawagarsu ya ankara
babu mace daya cikin yan matan nan, suna rumgume da juna suna kuka suka ji an
finciko falmata batare da 6ata lkci ba ya sauke mata tagwayen mari a fuska sannan
ya jata ya koma da ita cikin tawagarsu, had'esu turawan sukayi suka zargesu da
igiya sannan suka tasa qeyarsu suka shige wani jirgin dasu,suna tfy suna waiwayen
yar'uwarsu itako bimbii kuka take sosai tana kallonsu har suka shige jirgin,obinnah
dake kusa da ita ne ya soma rarrashinta, itama tana cikin alhinin rabuwa da
yan'uwanta wani daga cikin masu kula dasu yazo yace ta biyoshi, batasan meze mata
ba ita dai kawai batare da gardama ba ta miqe tabi bayansa, obinnah dake gefenta
yyi saurin miqewa ze rakata mutumin ya daka masa tsawa dole ya koma ya zauna ita
kuwa tabi bayansa suka qarasa wurin wani tsohon jirgin ruwa dake gefen port din,
nuna mata kofar jirgin yyi yace ta shiga, shiga tayi shima yabi bayanta, suna
shiga gabanta ya yanke ya fad'I don lura tayi jirgin abandon one ne ba kowa cikinsa
sai tarin shirgi, bata qarasa rikicewa ba saida taga ya soma zame wandon dake
jikinsa, take jikinta ya soma rawa tamkar mazari ta soma ja da baya cike da
tsantsar rudewa, murmushi yyi lkcin daya gama zame dukkanin tufafin dake jikinsa ya
kalleta yaga yadda ta rufe idanunta ruf sai makyarkyata jikinta yake ta durqushe a
wurin tare da daga hannayenta dukka ta soma masa mgn da harshen fillanci tace" ka
yiwa Allah ka yiwa annabinsa ka kyaleni karka ketamin haddi niba kafira bace" cikin
kuka take roqonsa duk fuskarta tayi 2sha6e da hawaye, shi kuwa tumuqin arne besan
ma abunda take fad'I ba don ba jin yarenta yake ba, shima baqar fata ne amma yyi
kala da irin mutanen kenya din nan baqine qirin tamkar gawayi asalin african man,
matsowa kusa da ita tana ja da baya har takai qarshen jirgin yana biye da ita da
murmushin qeta a fuskarsa, hannu yasa yana shirin kamota aka doko kofar jirgin,
wannan asalin balaraben ne daya amsheta daga wurin baturen nan, kallon mutumin yyi
ransa a mugun 6ace ya soma zaqinsa cikin harshen turanci yace" kai wawa ne so kk
kamin asara, kasan dalilin dayasa na amsheta sbd daka ganinta kasan danyar budurwa
ce kuma kudin virgins ko wurin saidawa daban yake, shine dan kai dan iskane kk
neman mini asara daman all those africans are bunch of animals,bauta ita tafi
dacewa daku" hk balaraben nan ya din ga masifa, shi kuwa sai qoqarin sanya wandonsa
yake,bimbii kuwa na daga gefe sai ajiyar zuciya take, qeyarta dan balaraben ya tasa
ya komar da ita cikin tawagar sauran bayin, obinnah na ganinta ya soma tmbyrta ko
sun mata wani abunne ta kada masa kai alamar basu mata komai ba,suna nan yashe a
gefen ruwa tamkar ba mutane ba sanyi sai busasu yake sai wurin asuba suka ga
tsayawar wani jirgi, yana sauke fasinjojin cikinsa ya soma deban wasu fasinjojin,
hk akazo aka tasa qeyarsu suka shige wannan jirgi,kwanansu biyu suna tfy kafin suka
soma shiga lardin larabawa, jirginsu ya tsaya ne qasar KUWAIT..... Abdullah bin
faisal International port, tun saukarsu daga jirgi wasu zungura zunguran motoci
suka soma dibansu kai tsaye kasuwar cinikin bayi aka wuce dasu, yadda ake cin
kasuwa saida tumakai ko dawakai hk ake cin kasuwar saida bayi, manya manya keji
akeyi ake zuba bayin ciki, suma hk aka zubasu cikin keji, farashin bayin hawan hawa
ne wani kudinsa yafi na wani, manya masu kudi da jinin sarauta da masu mulki sukan
siye bayin dayawa sukaisu muhallinsu suna musu kowacce kalar bauta amma yawanci
jinin sarauta basu daukan baqar fata sai larabawa kalar fatarsu, masu ma'aikatu da
gonaki suke siyen baqar fata sukaisu suna musu aiki amma masu daukar boyi boyin gd
ma sunyi son larabawa kalar fatarsu suna mugun kyamar baqar fata musumman na
africa,bimbii an hadata keji daya ne da wasu yan'mata amma dukkaninsu larabawa ne
sukansu kallonta suke suna mamakin wai daman a qasashen baqar fata ma akwai mata
masu kyau kamar bimbii, gani sukayi gashin kanta yafi nasu tsawo gata duk cikinsu
ta fisu kyau da cikakken diri irinna mata saidai kawai su nuna mata hasken fata,
mutanen sai 2zirga suke suna siyen bayin da suka musu,kowanne bawa so yake a siyesa
ko Allah zesa yyi dace da mutanen kwarai su masa riqon arziqi,wata balarabiya itama
tazo duba bayi kallon daya zaka mata kasan ba daga gdn talauci take ba, balaraben
dake dasu bimbii ne yyi saurin tararta ya kawota wurin kejin dasu bimbii suke wai
ta duba koda wacce tayi mata, kallonsu take daya bayan daya tana duddubasu tamkar
wacce zata siyi akuya, idanunta ne ya tsaya kan bimbii ta nuna bimbii da hannu
tace" wannan baqar fata ce koh" balaraben yace" ehh,amma tana da cikakken lfy ba
zaki samu mtsl da ita ba" sake kallon bimbii tayi tace masa ya fito da bimbii
aikuwa ya bude kejin ya fito da bimbii, batare da bata lokaci ba tayi cinikinta ta
biya suka bata certificates of ownership na bimbii har wurin motarta balaraben ya
rakata ya budewa bimbii boot din mota ta shiga aka rufeta sannan matar ta shige gdn
baya drivernta yaja motar suka wuce, bimbii na bayan boot din motar tamkar akuya
tana rakube har suka iso gdnsu sannan aka budeta ta fito, gdn qaramin bungalor ne
mai kyau da tsari ga furanni ta ko'ina kunsan larabawa da son hutawa, tsagaya
matar ta somayi da bimbii tana nuna mata ayyukan da yake nata ciki har da baiwa
wadannan furannin ruwa da kula dasu, duk aikin nata na wajene be danganci cikin
bedroms,kitchen ko cikin parlourn ba don wannan aiki daya shafi cimmarsu ko kula da
wurin kwanansu basu amincewa da baqi yyi musu ba suna da kyankyamin baqin mutum
sosai duk wannan ayyukan na cikin gd balarabiya yar'uwarsu suke dauka, wani qaramin
daki aka baiwa bimbii, kullum bimbii tunkan kowa ya tashi take tashi tayi dukkanin
aikin da matar nan ta yanka mata, batasan sunan wannan balarabiya ba amma taji
ma'aikatan gdn na kiranta ennah, tana da tsauri sosai batason wasa ko sakaci da
aiki, tana yara biyu dukkaninsu maza ne amma kowanne da gdnsa basu zaune tare da
ita, bawai iyali ne dasu ba amma kowa yana zaune shi kadai a gdnsa saidai duk
weekend suzo su gaishe su yini sai dare suke tfy, ennah tana son wadannan yaran
nata sosai da zayeed da maheer, maheer shine qarami atleast bazai gaza shekaru
ashirin da uku ba sai zayeed mai shekaru ashirin da shida, yau weekend tun sanyin
safiya bimbii ta gama aikinta, zuwan bimbii gdn yasa furanni dake gdn suka soma
kyau da fitar da kyawawan furanni masu kala sannan tana yankesu tana saitasu tana
cire ciyayin dake fitowa qasansu suna hanasu girma, kullum ennah na kallon yadda
bimbii ke gyaran furannin ta windown dakinta, ita kanta ta yaba da aikin bimbii,
kullum tana aikinta tana waqarta cikin harshen fillanci,tun tazo gdn bata taba
shiga cikin wannan bungalor na masu gdn ba, ranar wata asabar maheer ya shigo gdn,
tsayawa yyi yana kallon yadda bimbii ke gyaran furanni fuskarsa sam babu annuri don
shi be ta6a tsammani ennah zata kawo musu baqar fata gd ba, qarasa yyi inda bimbii
ke aikinta yasa hannu ya janyo mayafin dake rufe
da gashin kanta ya janyo dogon gashin kanta, cike da tsoro ta dago a idanunta tana
kallonshi tace" malam lfy me na mk" cikin harshen fillanci take masa mgn aikuwa ya
watsa mata mari saida shatar hannunsa suka fito a fuskarta ya bala'i cikin harshen
larabci wai uban waye ya kawo musu baqar fata gdnsu, muryarsa ennah taji tayi
saurin fitowa ta qaraso wurin,kamashi tayi suka shige bungalor ita kuwa bimbii
hawayene ya cika mata idanu kawai ganin yadda ake wulaqanta bil'adama toh shi baqar
fata ba Allah ne ya halicceshi ba, itama bimbii indai a kalar fata ne tana da haske
idan anan africa ne zamu iya kiranta da fara amma su kallo daya suke mata suke gane
ba balarabiya bace duk da tsantsar kyawun halittarta.....

Washegari ennah ta kirata tace ta shirya zata koma gdn danta don ta bar mashi ita
ta din ga masa hidima, gaban bimbii ne ya fad'i tayi shiru kawai don babu yadda ta
iya a qasar da bata da kowa bata da komai sai Allah,ranar da yamma maheer yaxo ya
tafi da ita gdnsa, gani tayi ai shi kadai yake zama a gdn nasa dake Najb ushakhair
steet, gdn nasa qaramin flat ne mai kyau, kallonta yyi cike da tsana ya nuna mata
rumfa da aka kewaye don shaqatawa yace"na miki alfarma ki din ga kwana anan idan
kin tashi ki gyara furanni ki share duk gdnnan sannan ki din ga bawa kifi abinci ya
nuna mata wani qarami fond dayake kiwon kifi,iya aikin daya nuna mata kaf ba wanda
ze shigar da ita cikin flat dinsa, shigewa yyi ciki abinsa yabarta a wurin tare
tabbatar mata da cewa daga yau aikinta xe fara, wata jemammiyar doguwar riga ce a
jikinta da wani tattararren mayafi da take rufe kanta dashi, hk ta tsuguna ta soma
cire matattun ciyayin dake qasan furannin tana tarawa a gefe, cike da kuzari da
himma take aiwatar da aikinta babu kasala don ta qaddara she only want to survive
amma tasan ita gd ko sake haduwa da danginta har abada don ta bar gd kuma nahiyarta
da nisa bata ta6a sanya ran wataran zata tsinci kanta a qasarta ba hk dai take
rayuwa cikin qangin bauta..........

*This book is seriously for sale dnt ever start reading the free pages if you know
u can't afford the remaining pages,for those who want to purchase the continuation
of the story these are the details for transaction*...... #300 naira for this
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank.....send the screenshrt of ur
payment through whatsapp....07041195806...for more information call....08080611486

Alkalamin bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

Ta gama nome busassun ciyayin dake farfajiyar gdn sannan sauyawa kifin dayake kiwo
ruwa ta basu abinci sai gumi take ga yunwa dake neman kayar da ita, wannan rumfar
gezevo din daya nuna mata a matsayin wurin kwananta ta nufa ta zauna tana ajiyar
numfashi, gyangyadi ne ya soma daukarta ta batare data ankara ba taji saukar ruwa a
tsakiyar kanta, bud'e idanunta tayi da sauri ta saukesu akan maheer yana tsaye
akanta riqe da tiyon da ake baiwa furanni ruwa yana mata wanka da ruwan, kallon
tsana yyi mata yace" daman bawa har yana da sukunin baccin yamma koh kin manta
matsayinki ne" bata fahimtar larabcin dayake amma tana fahimtar tsantsar
wulaqancinsa, miqewa tayi ya nuna mata wani karensa dake keji yace" ta fito dashi
ta masa wanka" yanayin yadda yake mata alama da hannunsa yasa ta fahimci abunda
yake nufi, miqa mata makullin kejin da karen yake yyi ta amsa ta nufi kejin da
karen yake tana qoqarin bud'e kejin shi kuwa karen sai haushi yake kamar zeci babu
tunkan ta bud'eshi aikuwa tana bud'eshi ya rarumota yana qoqarin cizonta ita kuwa
sai ihu take tana neman taimako tana tureshi da iyakar k'arfinta, tun abunda ke
faruwa maheer na tsaye daga gefe yana kallonsu yana murmushin mugunta, turmusheta
karen yyi a qasa duk yaji mata ciwo da faratansa ita kuwa kuka take sosai tana ture
karen ta matsawa duk ta cire takalman k'afarta tana jifan karen dashi,kamo rigarta
yyi da haqoransa ya shirin cizonta maheer yyi masa mgn da harshen larabci sakinta
yyi ya koma gefe yana haushi 2kad'an yana kallonta ita kuwa duk ta jigata hk ta
miqe a razane ta soma qoqarin ficewa daga farfajiyar gdn da gudu ta fice waje don
ta mugun tsorata da karen, kallonta maheer yyi sannan yyiwa karen nasa alama da
idanu,wani irin tsalle karen yyi yasha gabanta ya gurnanin haushi, juyowa tayi da
gudu ta koma ciki ta shige wannan rumfar gezevon, karen be biyota ba ya kyaleta ya
tsaya wuri guda, maheer matsawa yyi wurin karen ya tsuguna yana shafashi don ya
gama birgeshi yau din nan, kallon bimbii yyi dake raku6e tana kuka yace" matsa
tashi ki fito kiyi masa wanka" bata ma ji abunda yake fad'i saida ya daka mata
tsawa amma duk da hk taqi fitowa daga inda take kawai kallon karen nan take, nuna
karen yyi inda take ba shiri ta fito jikinta sai rawa yake, kallonta yyi ya kalli
karen sai ya bushe da dariyar mugunta ya nuna mata karen da hannu wai taje ta masa
wanka, gaban mugun fad'uwa yake taje ta ciko ruwa a wani kwarmi tazo ta kama karen
don taga maheer dab dasu, abun mamaki karen be kuma mata komai ba har ta gama masa
wankan, tunda maheer ya shige building d'insa be kuma fitowa ba bare tasa ran ze
bata abinci, yunwa takeji sosai ga dare yyi ba wurin kwanciya tana dai raku6e a
wannan rumfar gezevon, tsirawa sararin samaniyya idanu tayi hawaye na zarya akan
kumatunta, garin da hasken farin wata gashi kuma da yalwar taurari a sararin
samaniyya tana takure wuri d'aya cikinta sai qugin yunwa yake,bata ta6a tsammanin a
cikin larabawa akwai marasa imani da tausayi irin maheer ba, hk tayi kwanan zaune
washegari babu k'arfi a jikinta sbd yunwa amma hk take ta faman 2aikace don tasan
dole ne ma tayi ko kuma yana fitowa yaga ba tayi aikinta ba ya had'ata da karensa,
maheer tashinsa kenan daga bacci ya kunna sigarinsa yana sha ya fito ya tsaya a
barandar gaban building d'insa yana hangawa yaga abunda ba tayi ba ko wanda ya
kamata ya qara mata, gani yyi tayi komai tunkan ya tashi ta gyara furanni ta basu
ruwa sannan ta baiwa kifi abinci ta share farfajiyar wurin ta wanke masa qaramar
motar hawansa tayi fes, komawa yyi ciki ya fito da wani farantin silver ya ajiye a
wani wuri ya juye ragowar abincin dayaci ya rage jiya da dare sannan ya kirata ta
taso tazo wurin dayake, nuna mata wannan abincin yyi yace ta dauka taje taci ta
dawo da farantin wurin ta ajiye, tsugunawa tayi ta dauki farantin abincin ta wuce
ta tafi ta soma ci duk da bata saba da cin irin cimmarsu ba amma hk take taci sbd
yunwa, tana gamawa ta komar da farantin ta ajiye a wurin, toh tun daga wannan lkcin
a wannan farantin yake zuba mata ragowar abincin idan yaci yage ya ajiye mata a
wurin tamkar yadda ake zubawa kare ko sauran dabbobi abinci idan sun gani suzo suci
hk itama idan taga ya zuba saita zo ta dauka ta tafi taci ta dawo da farantin ta
ajiye a wurin wataran ma har abincin ya soma bushewa batasan ya zuba ba sai idan
tazo ta duba ta gani ta dauka hkma kuma zataci ko yunwa ta kasheta a banza baida
damuwa, yau hadari ne ya had'u sosai a garin ana sanya ran samun ruwan sama a
kowanne lkci ita kuwa fargabar sakkowar ruwan take don tasan kwanan tsaye zatayi a
wannan rumfar, cikin dare kuwa aka soma sheqa ruwa kamar da bakin kwarya tun ruwan
yana feso mata har ya jiqa cikin rumfar gbdy, miqewa tayi ta tsaya a tsaye ta
qanqame jikinta don sanyi ne ke shigarta sosai ga kuma ruwan dake fesowa cikin
rumfar duk ya jiqa mata jiki,kayan dake jikinta duk ya jiqe shakaf kuma gashi su
kadai gareta idan ma jiqewa sukayi hk zasu bushe a jikinta, wani lkcin idan sukayi
datti sosai sai ta bari idan dare yyi dare saita tashi ta ciresu ta daura mayafinsu
a jikinta ta wankesu ta shanya kafin asuba ta kwashesu ta maida jikinta, hk aketa
sharara ruwa har da qanqara bimbii na tsaye qanqame da jikinta tana rawar sanyi sai
gab da wayewar gari ruwan ya d'auke, ita kuwa bimbii ruwan daya jiqata ya sanya
mata zazza6i sosai, tashi d'aya tana miqewa jiri ze d'ebeta ga tsananin ciwon kai,
kuka take tana roqon Allah kar yasa zazza6in nan ya kayar da ita tana fargabar kar
maheer ya fito ya tarar bata aiwatar da aikinta ba, jan jikinta ta somayi ta soma
bawa furanni ruwa duk da ruwan saman da aka kwana ana sheqawa, jiri ne ya d'ebeta
ta fad'i a wurin kanta yana wani irin sarawa, rarrabawa tayi ta koma gefe ta zauna
tana maida numfashi tana son taji dama dama kafin ta kuma yunqurin miqewa, maheer
ranar be fito da wuri ba sai yana building d'insa yana playing wani game, wanka ya
shiga sannan ya shirya ya fito da niyya zuwa gaida mahaifiyarsa, abunda ya bashi
mamaki shine yana fitowa ya tarar bimbii batayi ko d'aya daga cikin ayyukanta ba,
makwancinta ya nufa ransa a mugun 6ace ya tarar ruwa ya cika wurin bata ciki,
fitowa yyi ya duddubawa ya hangota jingine da wata qaramar bishiyar guiba dake
qarshen gdn tana yashe a zaune tayi zaman dirshan, qarasowa yyi wurin batare da
la'akari da yanayin da take ciki ba yasa hannunsa ya kamo gashin kanta ya
watstsaketa da wasu lafiyayyun mari har uku sannan ya jefar da ita kanta ya bugu da
bishiyar guiban sannan ya soma zazzage mata ruwan bala'i batare da digon tausayawa
ga yanayinta daya ganta ciki ba ya umarceta data tashi ta kama aikinta, shiru ta
masa taqi motsawa daga inda take bare yasa ran zatayi abunda ya umatceta, ranta yyi
mugun 6aci take taji zuciyarta ta kangare koda kasheta zeyi ta sadaqar bata yin
abunda yace, shi kuwa kallonta yake kawai da mugun mamaki don ya saba duk abunda
yasata ba musu bare gardama zatayi amma yau dubi taurin kan da take gwada masa,
hannu yasa ya cire belt din dake d'aure a k'ugunsa ya soma dukanta dashi tamkar
Allah yyi masa wahayi, duk ya farfasa mata jiki amma be fasa dukanta ba ita kuma
bata motsa daga inda take ba kuma ba tsillin hawaye ko qiris a idanunta, yana cikin
dukan nata yayansa zayeed ya shigo gdn, wurin ya qarasa da sauri don shi kansa
yasan zuciyar maheer idan har ransa ya 6aci zai iya aikata komai, jansa ya somayi
yana qoqarin fizge belt d'in hannunsa shi kuma yana tirjewa, dakyar ya iya
lalla6ashi ya shigar dashi cikin building d'insa yana cika yana batsewa yana kuma
huci don ransa ya 6aci sosai gani yake bimbii bata chanchanci ta masa wannan taurin
kan ba a matsayinta na qasqatacciyar baiwa kuma baqar fata shiyasa cikin zaqin
dayake mata har yana ce mata gorilla family wai duk baqar fata dake africa daga
family na gwagwggon biri suke she never deserve to behave like this cox she is
nothing but gorilla family......zagi na uwa na uba hk ya dinga sauke mata kwando
kwando yyi da larabci yyi da turanci, tun shigarsu ciki tana wurin bata motsa ba
don batajin idan ta miqe tsaye k'afafunta zasu iya d'aukar gangar jikinta, sai
lkcin taji saukar wasu hawaye masu d'umi a saman quncinta, kallon jikinta tayi taga
yadda ya farfashe da duka sai kuma tayi murmushi wanda yafi kuka ciwo,zayeed ne ya
fito ya kalleta shima cike yake da fushi amma yana kallonta ya fahimci bata da
lafiya shima dai ba wani daraja bayi baqar fata ke dashi a idanunsa ba amma dai
yaji tausayinta kad'an, samo mata magani yyi ya bata ta amsa da godiya shiko batare
daya saurari abunda take fad'i ba ya fice daga gdn yyi tafiyarsa, maheer kuwa ranar
bak'in ciki kamar ya kasheshi hk ya kwana cike da qunci, washegari kuwa ya fito da
sanyin safiya yaga ko batayi aikin nata ba don qiris yake jira da ita ya mata dukan
da zata kusa ziyartar lahira sai kuma yyi rashi sa'a don ta gama kowanne da cikin
aikin nata duk da rashi jin dad'in jikinta da take amma ba kamar jiya ba don
maganin da tasha yyi mata amfani yau taji dama dama ba kamar jiya shiyasa tun safe
ta lalla6a ta gama komai ta koma gindin bishiyar guiwa ta zauna, cike da haushi ya
koma ciki ya kwanta akan doguwar kujerar dake qaramin parlourn nasa yana fitar da
hayaqin sigarin dayake busawa,hoton bimbii ne ke dawo masa lkcin dayake dukanta,
idanunta qamas suke babu alamun kuka, zumbur yyi ya miqe ya kuma fita ya tsaya a
barandar dake gaban building d'insa yana hangota zaune a gindin bishiyar guiba tana
tsefe kalbar dake kanta tana sake kitsa wata,ita kuwa batasan ma ya fito ba tana
tsifanta tana rera waqar da take idan ta fita kiwo cikin harshenta na
fillanci,juyawa yyi ya koma ciki ya shiga kitchen d'insa ya soma preparing
breakfast a cikin kowanne tunaninsa bimbii ce ke fad'o masa ya ayyana mugunta daya
dace ya mata,yana gama girkinsa ya zuba a wani plate ya fito wajen inda yake ajiye
mata abinci ya juye mata, ita kuwa bimbii daman tun jiya babu abunda taci kuma
yanzun ma bakinta babu dandano ko kadan bama ta sha'awar cin komai sai koko da
qosai wannan kuwa tasan samunsa wurinta saidai ko a mafarki amma ba'a gaske ba,
bata ta6a sanya ran ze zuba mata abinci ganin yadda suka kwashe dashi jiya kawai
tana biyowa ta wurin taga ya zuba mata abinci, wucewa tayi bata d'auki abinci ba,
shi kuwa duk bayan sakan guda sai ya leqo yaga ko ta dauki abincin daya zuba mata,
hk kawai ya samu kansa da son yaga taci abincin amma har dare ya fito yadda ya zuba
abinci hk ze gansa, shiru yyi yana tunanin ko fushi tayi sbd abunda ya mata jiya
don ya fahimci kamar tana da zucciya, ita kuwa bimbii ta mance ma da batun abinci
kawai lalla6a jikinta take don batason ta kuma kwantawa rashin lfy sbd gudun
wulaqancin maheer, qunci da tsantsar bauta duk sun sauya bimbii ta koma wata irin
miskila bata da fara'a kullum fuskarta a tsuke babu annuri ko kad'an, duk sanda
maheer ya fito ze tarar tayi aikinta ta koma gindin bishiya, yauma yana fitowa ya
tarar ta gama aikinta, kiranta yyi ta taso tazo juyawa yyi ya shiga cikin building
d'insa ita kuwa ta tsaya a inda take don tasan bata da damar shiga wurin, juyowa
yyi yaga tana tsaye bata biyoshi ba, saida ya kuma kiranta sannan ta biyo bayansa
ta shigo ciki gabanta yana tsananta fad'uwa don batasan me ze mata ba ya kirata
cikin wurinsa, parlourn nasa qarami ne amma yana da kyau sosai kuma ya wadatu da
kayan more rayuwa, kitchen d'insa babu abunda babu na kayan amfani, kallonta yyi ya
soma nuna mata wasu ayyuka da zata din ga masa cikin building din nasa ciki har da
girki, itako bimbii binsa kawai take da kallo cike da mamaki toh yaushe ya sauya
ra'ayi har ya amince mata ta din ga ta6a abunda zeci har ma da yarje mata ta din ga
shigowa bangarensa tana masa 2aikace,tsawan daya mata ne yasa ta dawo cikin
hnklinta, saidai itakam bata iya girki irin nasu ba toh me yakeson ta dafa masa ko
irin abincinmu na gargajiyar baqar fata, dayake yanzu tana jin larabci sama sama
don Allah ya mata kwakwalwa mai kyau da kaifin basirah,cikin harshen nasa ta masa
mgn tace"nikam ban iya girki irin naku ba sai irin namu na baqar fata idan kana so
kuma sai na mk" harararta yyi ya wuce yabarta a wurin tare da kora mata warning
cewa duk aikin daya yanka mata ta tabbatar bata gocewa kowanne ba, washegari tana
gama aikin furanni da baiwa kifi abinci ta nufi wurin building nasa, danna masa
alarm tayi saida aka dan jima yazo ya bud'e kofar sanye yake cikin kayan bacci da
alamu alarm din data danna ne ya tashe shi daga bacci, bece mata komai ba ya matsa
gefe ya bata hanya ta shiga, komar da k'ofar yyi ya rufe ya koma bedroom d'insa ya
kwanta, ita kuwa ta shiga kitchen d'in nasa ta soma wanke masa kwanuka,gani tayi
wasu abubuwan ma dake kitchen din duk sunyi qura, hk ta wanke komai ta fitar da
abubuwan da suka lalace a fridge ta gyara komai ta goge floor din yyi tas, tuni
wuri yadau haske da annuri, fitowa parlourn tayi ta goge electronics d'in dake
parlourn ta kad'e kujeru ta gyarasu sannan ta share ko'ina ta goge, ba tayi gigin
girka masa komai ba don itakam bata iya irin girkinsu, har ta gama aikin nata
maheer yana baccinsa baida niyyar tashi, bud'e kofa tayi ta fice tunda ta gama aiki
nata ta koma gindin bishiyar guiba inda ta saba zama, tunda ta shigo gdn maheer
bata ta6a leqa koda k'ofar waje ba kullum tana ciki tana aikatuwa, tana wurin a
zaune taga shigowar wata mota qirar mercedez ta shigo farfajiyar gdn, wasu samari
ne su wajen biyar dukkaninsu larabawa ne amma suna sanye ne cikin qananan kaya,
wurin building maheer suka nufa, shi kuwa tashinsa kenan ya fito parlourn nasa,
tsayawa yyi kawai yana bin ko'ina da kallo tamkar ba parlourn nasa ba ganin yadda
floor din ke kyalli da d'aukar idanu ga komai a shirye tsaf, shelves na
littattafansa a gyare tsaf duk ta kad'e qurar wurin, yana shiga kitchen ya kuma yin
turus sbd komai na kitchen tamkar an maidashi sabo hattar oven d'in dake manne da
gas d'in girkinsa cikinsa sai sheqi yake, tunda yake masu aikin dake kula da
building d'insa be ta6a samun wanda yyi masa wannan aiki mai kyau hk ba, murmushi
yyi kawai be damu ba duk da yaga dinning din dake kitchen babu komai wato bata
girka masa komai ba amma shi aikin nata kawai ya birgeshi don shi a rayuwarsa yana
son tsafta, alarm din dayaji ana danna masa ne yasa ya fito daga kitchen ya nufi
wurin k'ofa ya bud'e, friends dinsa ya gani, dariya yyi ya basu hanya suka shigo,
duk suka kame akan kujerun dake parlourn shi kuwa ya shiga kitchen ya soma qoqarin
had'a musu tea, su kuwa suna parlourn sun kunna waqar Ali bin wasid suna chashewa
da ita abinsu,fitowa yyi ya fita, tsayawa yyi a baranda ya kira bimbii dake gindin
bishiya, tahowa tayi tazo wurin tana kallonsa, juyawa yyi tabi bayansa, tana
shigowa duk suka bita da kallo suna kallon maheer, daya daga cikinsu yace" mah a
ina ka samo mai aiki baqar fata kana nufin ita take maka abinci,God forbid"
bimbii tana tsaye daga gefensa, murmushi yyi ya kalle friends din nasa yyi yace" oh
guys calm down, she is just my cleaner" d'ayan kuwa yana hakimce a kujera tunda
suka fara mgn be furta komai ba kawai bin bimbii yake da kallo tun daga sama har
qasa,tsayar da idanunsa yyi kan k'ugunta wanda sai mutum ya mugun qura mata idanu
ze gano girmansa don doguwar zumbulin rigar dake sanye jikinta ta taimaka wurin
asirtashi, sake dire idanunsa yyi kan na shanunta dake tsaye dodar sukam tsinin
tsayuwarsu ya fito ta rigar kuma data taka kad'an suke girgixa don ba bra a
jikinta, masu yanci suke da arziqin sanya bra,murmushi yyi kawai tare da lumshe
idanu ya komar da kansa ya kwantar jikin kujera yasa hannu yana shafa kwantaccen
sajen dake gefen fuskarsa,maheer kuwa kallon bimbii yyi yace ta biyoshi kitchen,
bin bayansa tayi tana shiga ta tsaya a gefe shi kuma ya soma had'a breafast, duk
abunda yake tana kallonsa.......

Littafin nan na siyarwa ne ki siya kiyi karatunki cikin yanci,idan kin shirya siye
saiki tura naira#300 ta wannan acct no.0100790419,Alhaji shahida nasir,union bank,
saiki turomin da screenshrt na payment dinki ta whatsapp 07041195806, idan kina
buqatar wani bayanin kuma saiki kira wannan layin 08080611486

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

Bayan ya gama komai akan idonta yace ta tafi, fitowa tayi daga kitchen d'in ta fito
parlourn da niyyar fita, daya daga cikin friends nasa dake parlourn mai suna farid
yasa hannu ya damqo hannunta yana murmushin qetai, qoqarin fixgewa take ta kasa
maheer ya fito da cups na green tea a hannunsa, tsayawa yyi yana kallon farid da
mamaki yace" ta maka wani abun ne koh" yace" No, but u said she is ur cleaner so i
want her to clean my body" gbdy sauran abokan nasa suka bushe da dariya, shi kuwa
farid murmushi kawai yyi, wani cikinsu mai suna jalil ya kalli farid yace" clean ur
body as how,just make it clear" dariya yyi ya miqe ya soma 6alle ma6allan rigarsa
ya cireta daga jikinsa ya kalli maheer yace" kace mata ina son tayimin wanka"
maheer jin abun yyi wani banbarakwai ya kalleshi yace"wanka?" yace"yes,ko ba baiwa
bace?" murmushi maheer yyi ya kalli 6angaren da bimbii ke tsaye don farid yyi
blocking hanyar fitar, duk sauran abokan nasa suna daga zaune suna jiran maheer ya
bawa bimbii umarnin yiwa farid wanka, shi kuma gashi baya son abokan nasa suyi
zaton ko yana siding din bimbii ne don hk ya kalleta fuska a tamke yace" kije ki
yiwa abokina wanka" kwalalo idanu waje tayi ta soma ja da baya tace" wanka zan yiwa
wannan qatoton billah ban iya yiwa babba wanka ba" mgnr duk tana yine cikin
harshenta na fillanci don bata gama kwarewa da larabcin ba, basu jin yaren nata
amma yanayin yadda tayi ya tabbatar musu da gardama take baza tayi masa wankan ba,
miqewa maheer yyi ya nufo inda take yace" yauma gardama zakiyimin" su kuwa sauran
duk suna daga zaune suna dariyar qeta tare da qara zuga maheer wai lalle yyi sake
baiwarsa bata bin umarninsa, kafin su ankara bimbii ta bud'e k'ofa ta fice da gudu,
binta yyi da niyyar sakar mata kare ita kuwa Allah ya bata sa'a ta fice daga gdn
gbdy, yana ganinta ta fita ya bita da gudu, ita kuwa tana fita ta miqe hanya tana
ta gudu don wlh tsoro taji sosai gani take idan ta tsaya zasu iya keta mata rigar
mutunci tunda har abun yakai ga hk, shi kuwa maheer gani yyi har ta masa nisa,
komawa yyi gd ya kira masu tsaron hanyar data nufa kansu dakatar da ita baiwa ce
take neman gudu, su kuwa sukace mata basu ganta ba, rikicewa yyi sosai lkcin da
suka sanar dashi basu ganta ba, fita yyi da kansa yana ta zagayen neman bimbii amma
ko mai kama da ita be gani ba, ita kuwa bimbii ba sanin gari tayi ba,tana cikin
gudun tayi wata hanya data nufi outcast wato wajen gari,tsayawa tayi tana kalle
kalle taga tabbas wurin da take wajen gari ne don ba mutane sosai, tana cikin waige
waige ta jiyo qarar takun dawakai tana juyawa taga wasu mahaya dokuna ne su shida
suna gwada tseren sukuwa sun nufo inda take gadan gadan tamkar basu ganin komai a
gabansu, mugun firgita tayi ta soma qoqarin juyawa da gudu aikuwa tuni sun cimma
inda take kafin kace kwabo daya daga cikinsu ya gwabjeta da gefen dokinsa, duk
sukayi wucewarsu batare da sun tsaya ganin halin da take ciki ba don faduwa tayi a
wurin, daga bayansu ashe akwai wasu dakarun mahaya dawakan dake take musu baya,
shugaban wannan dakarun ne ya tsaya ya bada umarni a dauki bimbii dake kwance
tamkar bata numfashi,su kuwa wadannan shidan da suka soma wucewa ya'yan sarakuna ne
dake taqama da izzar jinin sarauta don kowannesu ya fito ne daga sananniyar
masarauta me fada aji cikin daular larabawa, wannan wuri kuma filin tseren sukuwar
dokunansu ne da suke fitowa duk qarshen mako don nishad'intar da kansu, hadimansu
kuma na take musu baya tare da al'qalan dake fitar da gwanin daya cinye tseren
cikinsu, suna isa madakata suka ja tunkan dawakansu suka tsaya, PRINCE
AKBAR....shine ya samu nasarar cinye wasan tseren sukuwar dokin, sakkowa yyi da
fuskarsa da babu yabo babu fallasa daga kan dokinsa, hadiminsa na hannun damansa
ubaid ya kama masa dokinsa, sanye yake da wasu fararen kaya tamkar pakistan kansa
sanye da rawani baki da fari, fari ne sol kallo daya zaka masa kasan cikakken
balarabe, sajen daya zagaye fuskarsa baki ne ya taimaka wurin tona asirin kyan d'an
sarkin,yanayin tafiyarsa da kallonsa kawai zai haska cikakkakiyar izzarsa,
haqoransa a jere suke farare tas dasu duk wata halitta dake jikinsa fara ce idan ka
cire gashin dake jikinsa da kuma kansa,gashin kansa dogo ne tamkar na mata har rawa
yake idan ba rawani akansa,PRINCE AKBAR shi ya buge bimbii ta bashi haushi sosai
daya ganta a hanyar sukuwar tseransu, ubaid ne ya matso kusa dashi yace" Your
highness wannan alamunta ya nuna baiwa ce dake neman gudu" kallo d'aya yyiwa keken
dokin da suka dauko bimbii yace" ku kaita cikin yan'uwanta bayi" abunda yace kenan
ya wuce abinsa ya sake hawa dokinsa suka dau hanyar komawa gdn sarautar burham dake
tsakiyar babban birnin kuwait........

*Masarautar Burham*🔱🔱

Ginin gdn sarautar burham shi kansa abun kallo ne don gini ne da kwararrun magina
suka tsarashi cike da basira, gdn gari guda ne dauke da 6angarori daban daban tare
da lambuka na shaqatawa da qoramai wanda ruwansu ke kwaranya, masarautar burham
tsohuwar masarauta ce a qasar kuwait mai kafaffen tarihi, akwai arziki da tarin
izzah ga jinin sarautar burham, sarki abdallah bin jabal shine mahaifi ga PRINCE
AKBAR kuma shine riqe da sarautar wannan daular masarautar burham, sarki abdallah
bin jabar mutum ne mai tsatstsauran ra'ayi irinna larabawan farko ga taurin kan
bala'i shiyasa har yau suke kan tsoffi al'adunsu a wannan masarauta, suna da tarin
bayi da hadimai,rukunin bayin dake wannan gdn sarauta ya kasu kashi uku kuma
dukkaninsu da alamominsu, bayin farko sune na qasa qasa masu kula da share share da
gyare gyare da yiwa dawakai wanka, sai na biyu masu kula da bangarorin iyalan
wannan gd, kaso na uku kuma sune masu kula da lfy da kuma abincin iyalan wannan gd
tare da tsaftace komai nasu, prince akbar shine daya d'a ga sarki abdallah bin
jabal sai kuma ya'yan wasu sarakunan dake qasan masarautarsu da suka taso cikin
wannan gdn sarauta kuma kowanne cikinsu da 6angarensa da hadimansa tare da gayyar
bayi, 6angaren prince akbar yafi kowanne 6angare girma da fad'i, akwai bayi na
musamman dake hidimtawa 6angaren nasa sai hadiminsa na hannun damansa ubaid, ubaid
yafi kowa sanin halin prince akbar kuma yana mutuqar masa biyayya baya sa6awa
umarninsa, gdn sarautar burham sun dau bayi tamkar ba rayuka ba don laifi qanqani
bawa ze aikata sarki abdallah ya zartar da hukuncin kisa akansa shiyasa bayin gdn
kowa yake taka tsantsan da kaffa kaffa, idan har baka daya daga cikin bayin dake
hidimtawa 6angaren sarki ko sarauniyya ko ya'yan sarki to kuwa baka isa ka shiga
6angarensu ba, kowanne rukuni na bayi akwai wanda ke shugabantarsu, idan aka kawo
sabbin bayi akwai wacce ke nuna musu ayyukansu suna kiranta ummul shukri, bata da
wasa ko kadan gashi ta iya horar da bayi yadda ya kamata a hannunta ubaid ya damqa
bimbii,akwai doka sosai a wannan gdn sarauta, kafin a za6i bayi su hidimtawa
sarauniyya ko sarki ko ya'yan sarki sai an tabbar da asalin bayin da kuma himmarsu,
bayi marasa asali yawancinsu basu aiki a bangaren iyalan gdn suna aiki ne kawai a
cikin gdn sarautar,fadar sarki abdallah bin jabal an ginata ne da danyen gwal
kowacce kusurwa a fadar daukar ido yake, tsarin wannan gd shine bawa ya tsaya
iyakar matsayinsa idan kuwa ya nemi ya qetare kai tsaye hukunci mai tsauri ze hau
kansa, kafin su dauki bawa ya soma aiki a wannan masarauta sai ummul shukri ta
gwadasu ta kowacce siga shiyasa suke kiranta uwar bayi.........
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

*Love is the unsoluble equation to a great mathematician and also a heavy weapon to
hold for a great legends and heroes*......🔱🔱

Tana farfad'owa ta ganta kwance bisa busassun ciyayi a yashe tsakiya wani d'aki mai
yalwar teburan katako da tsoffin kwabobi, gefenta wasu y'an mata ne su uku kyawawa
dasu jinsin larabawa saidai alamu sun nuna tamkar suma suna da tambarin bauta
tattare dasu, suna ganin ta farfado suka matso kusa da ita suna mata sannu cikin
harshensu na larabci, dayake tana d'an fuskantar larabcin 2kadan sai ta d'aga musu
kai kawai ita dai sai qarewa d'akin kallo take tana tunanin yau kuma ina Allah ya
jefota, hannun suwa kuma ta fado, d'ayar da taji suna kira da khulood ta miqe ta
fita da sauri ba jimawa sai gata sun shigo da wata tsohuwar balarabiyya, tana tafe
tana dogara sandarta, doguwar riga ce ruwa k'wai a jikinta ta yane kanta da mayafi
amma hkn be hana gashin kanta dayake fari fat da furfura leqowa ba,wuyanta da wata
katuwar sarqa,kunnuwanta kuma da wasu manya yan kunne sai yatsun hannunta kusan
dukka da manya zobuna na azurfa, fuskarta a tamke ba alamun fara'a tana shigowa
sauran y'an matan bayin nan suka rissinar da dakansu qasa alamar girmamawa ga uwar
bayi ummul shukri, bimbii kuwa kallon tsohuwar kawai take,itako uwar bayi ummul
shukri sandarta ta sanya ta d'ago da ha6ar bimbii tana qarewa fuskarta kallo
musamman cikin idanunta don mafi yawan larabawa suna karantar sirri zucciyar mutum
ne ta cikin k'wayar idaniyansa shiyasa uwar bayi ummul shukri ta qure bimbii da
idanu tana karantar sirrin zucciyarta ta k'wayar idanunta, bimbii kuwa sai tayi
sauri yin qasa da idanunta kamar yadda taga sauran yan matan bayin sun mata, tana
ganin bimbii ta rissinar da idanunta qasa sai tayi wani d'an murmushi na gefen baki
ta d'auke sandarta daga ha6arta ta kalli khulood tace" ki bata abinci" tana fadar
hk ta dogara sandarta ta fice daga dakin bayin,khulood ta tashi da sauri ta fita
don kawowa bimbii abinci itama israt ta tashi ta kawo mata ruwan sha cikin wani
kofin tasa daidai lkcin khulood itama ta shigo da wani qaramin kwanon tasa da
abinci a ciki,duk suka sanya mata a gaba, bimbii kuwa daman da yunwa ta tashi don
hk batare da wani kunya ba ta wanke hannunta da ruwan da suka kawo mata, ta soma
cin abincin duk da a ido ta raina yawan abinci suna kallonta ta gama cin abinci
tasha ruwa tayi hamdala,khulood ta kalleta da murmushi tace ta tashi su fita ummul
shukri na son ganinsu, ba musu ta miqe tabi bayansu suka dinga wuce kusurwowi har
suka shiga kusurwar da ummul shukri take, zaune take bisa kujera tana riqe da
sandarta suka durqusar da guiwowinsu dukka a gabanta tare da rissinar da kawunansu
qasa suna jiran umarninta, itama yadda taga sunyi hk tayi, ummul shukri ta kalle
bimbii ta soma mata mgn cikin harshen larabci tace" kin san inda kk yanzu?" girgixa
kai bimbii tayi alamar aa, tace" kina gdn sarautar burham,kina cikin jerin
maqasqatan bayin masarautar burham"nuna mata su khulood tayi da hannu tace"rukunin
aiki iri d'aya zasu nuna miki naki aiki ciki" rissinar dakanta tayi alamar ta amsa
yadda dai taga sunayi, sallamarsu tayi suka miqe suka fice, bimbii sai bin wannan
gdn sarauta take da kallo don tsarin ginin masarautar ya birgeta sosai, gani tayi
bayin gdn sai kai kawo suke,matan kusan dukkaninsu da mayafi a saman kansu,mazan
kuma yawancinsu da rawani a kansu,ko'ina na gdn zagaye yake da furanni masu kwantar
da zucciya, gdn kusurwa kusurwa ne, kowacce kusurwa an mata yanayi kamar kofar
masallaci sanda sanda, israt da khulood na gaba, laila da bimbii na biye dasu,fita
sukayi daga wannan 6angaren suka wuce wani wuri suka dauki kwanduna, lailah ta
dauki kwando daya ta bawa bimbii ta amsa ta riqe suka sake ficewa daga wannan
6angaren sai tfy suke har suka fara fita daga inda gine gine suke suka soma shiga
jeji jeji kuma fa duk a cikin gdn suke, bimbii dai sai binsu take, wani lambu mai
cike da bishiyoyi na kayan marmari suka shiga, khulood ta hau bishiyar zaitun,
israt tahau bishiyar tuffa suna tsinkowa suna jefo musu su kuma suna tattarawa suna
zubawa a kwandunansu, saida suka cika kowanne kwando sannan su khulood da israt
suka sakko kowacce ta dauki kwandonta ta dora a saman kanta suka fice daga lambun
suka nufi cikin gd, suna cikin tfy wasu samari suma bayi ne suka tare musu
hanya,abunda ya baiwa bimbii mamaki shine ashe kowacce cikinsu tana tafe da qaramar
wuqarta a cikin jikinta sai gani tayi duk sun sauke kwandunansu sun sanya hannu
cikin fatarinsu sun fito da qananan wuqaqensu sun tsatstsaya suna sauraron su ga me
zasuyi musu su soma yankarsu, bimbii kuwa ta qame a tsaye da kwandonta a saman
kanta cike da mamaki, su kuwa suna ganin yan matan sun fito da wuqa sai suka wuce
abinsu saida suka ga sunyi nisa suka maida wuqaqensu cikin jikinsu suka sunkuya
suka dau kwandunansu suka cigaba da tfy,su mazan larabawan wannan yankin Allah ya
zuba musu son jikin mace ba wuya suke yiwa yan mata fyade shiyasa yan matansu ke
yawo da wuqa sbd tsaro, bimbii dai tana ganin abun mamaki cikin wannan gd sbd ita
daman tunda ta shigo qasar kuwait tana qunshe ne a wuri daya batasan al'adunsu ba
sai yanzu da Allah ya jefota gdn sarautar burham, wani qaton kitchen suka shiga,
kitchen bayi ne ciki keta hidima, shugabar bayin dake wannan babban kitchen din mai
suna jahan ita ta amshi kwandunan nasu ta jujjuye kayan marmarin a cikin wasu
manyan kwanduna dake kitchen din ta basu kwandunansu, duk bayin dake hidima cikin
kitchen din sai bin bimbii suke da kallo tamkar sun ga wata sabuwar halitta,lallah
ce taja hannun bimbii suka fice daga kitchen din,maida kwandunan sukayi suka koma
wani 6angaren suka fito da wasu manyan barguna suka nufi wata qatuwar qorama dake
dake tsakiyar gdn suka dauko wasu manyan abubuwan wanki da akayisu da katako suka
soma dirzar wankin wannan manyar barguna sai yamma liqis suka kammala ayyukansu
suka koma 6angarensu,su hud'u ne a dakin nasu,khulood,lailah, israt sai yanzu da
aka kawo musu bimbii, dukkaninsu akan wannan busassun ciyayin suke kwana tamkar
shine suka maida katifarsu saidai su shimfida mayafansu akan ciyayin su kwanta, ita
bimbii ranar kam bacci tayi mai dadi don kuwa gani take ta samu cigaba tunda har ta
samu damar kwanciya cikin daki ba'a rumfa ba kuma har ta samu albarkar kwanciya a
ciyawa ba'a dandamalin k'asa ba wannan kadai cigaba ne a wurinta bata damu da tiqar
aikin da suke ba don daman tasan ta ita baiwa ce kuma tana cikin qangin
bauta,kwanan farin ciki tayi ga qawaye ta samu da basu nuna mata zangwama ko kadan
sun dau kansu tamkar yan'uwa hk suke rayuwarsu tamkar jini daya kuma kusan
dukkaninsu sun fito ne daga qasashe mabambanta saidai su duk daga qasashen larabawa
suke masu makwabtaka da qasar kuwait ita kadai ce baqar fata daga africa, washegari
da sanyin safiya duk suka tashi, tunkan su fita ummul shukri ta shigo ta kama
tsintsiyar qafar bimbii ta sanya mata wata qaramar sarka irin wacce wasu matan ke
sanyawa a qafa sbd ado su kuma wannan sarqar qafan itace alamar dake nuni da
rukunin bayin da suke shiyasa taga suma su khulood kowacce da wannan sarqar a
qafarta ita da ta dauka sbd ado suka sanya ashe shine tambarin rukunin bayin da
suke,kallon qafar tayi taga sarqar ta mata kyau, miqewa tayi suka fice, ranar
kwaryoyi suka dauka suka tafi tatsar nonon raqumi,kowacce saida ta cika kwaryarta
da nonon sannan suka dauko suka taho kai tsaye wannan babban kitchen suka kai nonon
aka juye a charkoki, daga nan suka wuce kowacce ta dauki tulunta suka tafi babbar
qorama don debo ruwa, saida suka ciccika duk wasu abubuwan tara ruwa na 6angarori
2daban sai yamma liqis ranar ma suka koma 6angarensu, bayan sun gama cin abinci
suna shirin kwanciya lailah ta fito da wata sabuwar wuqa yar qarama ta miqawa
bimbii tace" ki riqe wannan kema sbd akwai hadari ki din ga yawo babu abun kare kai
kin ga kema budurwa ce saiki sanya budurcinki cikin hadari" amsar wuqar bimbii tayi
mata gdy sannan ta sanya wuqar qasan wurin kwananta......

***

6angaren maheer kuwa tunda bimbii ta gudu ya rasa kansa,shi kansa ya rasa abunda ke
damunsa tun yana qoqarin 6oye damuwarsa har mutane suka soma fahimta, yau tun safe
yana tsaye a barandar dake gaban building dinsa ya qurawa gindin bishiyar guiban da
bimbii ke zama lkcin tana gdn,gani yake tamkar ze ganta zaune, har yayansa zayeed
ya shigo gdn be sani yyi nisa cikin tunani saida ya dafashi tukun ya ankara da
shigowarshi, zayeed kallo daya yyi masa yasan akwai abunda ke damunsa,ya lura da
maheer tun sa'adda baiwarsa ta 6ace ya shiga damuwa ya kasa dawowa daidai har
yanzu, dafa kafadarsa yyi ya soma masa mgn cikin taushin murya yace" maheer are you
in love with that african lady" saurin dago dakai maheer yyi yana kallon yayan nasa
da mamaki a shimfide a fuskarsa yace" what are you saying?" murmushi zayeed yyi
yace" if not,why are worrying about her disappeared" kallonsa maheer yyi yace" cox
she my slave" dariya zayeed yyi sai kuma yace" ok, i will bring another slave for
you" haushi mgnr ta bashi ya tashi daga wurin ya shige cikin building nasa ransa a
6ace, zayeed kuwa bai bishi don yasanshi da shegiyar zuciyar tsiya ya cigaba da
wasa da kare,maheer kuwa yana shiga ya kwanta a couch din dake parlourn nasa ya
rufe idanunsa yana hango lkcin da bimbii ta 6acewa ganinsa bai ta6a zaton be zata
dawo ba don shi la'akari yake ai bata da inda zataje dole ma ta dawo wurinsa saida
yaga yau kusan kwana uku kenan ba bimbii ba alamun dawowarta, zuciyarsa tana
tsananta bugawa idan yana tunani bimbii,gashi shi ko sunanta ma be sani ba, idan ya
tashi baida aiki sai tunanin bimbii,tunda bimbii ta gudu bacci yake gagarar
idanunsa,yauma dare yyi sosai ya fito ya tafi cikin rumfar gezevon da bimbii ke
kwana ciki ya zauna ciki ya qurawa sama idanu yana kallon hasken farin wata tare da
taurarin dake sararin samaniyya,a hnkli ya furta 'I lost my star,pls my black
african lady come back to me" sai ga maheer uban marasa mutunci yana kuka da
hawayensa,be ta6a sanin ashe son bimbii ya illata masa zuciya ba saida ta gudu
tabarshi, dora kansa yyi akan cinyoyinsa yana kuka har sauti, ruwa aka soma kamar
da bakin k'warya amma maheer na cikin wannan rumfar yana kuka da hawayensa, ji yake
ya tsani friends din nan nasa da suka zama silar gudun bimbii shi kansa ji yake ya
tsani kansa idan ya tuno rashin mutuncin daya din ga shukawa bimbii,sai yanzu ya
fahimci lalle kowanne mutum yana da baiwa, wani baiwarsa a 6oye take Allah kadai
shi yasan irin baiwar daya axirta kowanne bawa nashi dashi, duk irin yanayin da
muka ga mutum karmu rainashi wataqila warakarmu tana tattare dashi,maheer ranar a
rumfar ya kwana yadda ruwa ke jiqa bimbii hk ruwan saman ya jiqash amma shi duk ba
wannan ne damuwarshi,zaman wurin kadai ya sanya masa nutsuwa don gani yake kamar
zega bimbii, washegari ya nufi wurin dayake sanya mata abinci yyi zaman dirshan
gaban plate din yana cin abinci daya zuba mata don dukda yasan bata nan amma kullum
ranar duniya baya fashin zuba abinci a wannan plate gani yake kamar ze dawo yaga
anci abincin, cikin mako guda maheer ya gama zaucewa da soyayyar bimbii,wata irin
zafaffiyar soyayya yake yiwa bimbii wacce ke wahalar da ruhi da gangar jikinsa,
soyayyar dake sanyashi kuka duk dare duniya,hmm, alhaki ai kamar dan kwuikuyo yake,
bibiya yake.....

Masha'Allah, anan na kawo qarshen free pages na wannan littafi duk mai buqatar
cigaban wannan qasaitaccen labari sai ya biya naira #300 kacal ta wannan acct
no.0100790419,Alhaji shahida nasir,union bank, sai turon da screenshrt ta wannan
layi through whatsapp....07041195806 ga mai buqatar qarin bayani saiki nemi wannan
layi....08080611486...

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HU'DU*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

*One Goodbye is enough to melt a heart* he missed her like crazy...💕

Washegeri da sanyi safiya suka tashi kamar yadda suka saba saidai yau ayyukansu
yana dayawa sbd yau itace ranar zagayowar haihuwar PRINCE AKBAR... Princess hindu
ita ta shirya qasaitaccen birthday partyn wanda ze gudana a lambun sarauniyya
mar'atussaliha, bayi da barorin wannan gd na sarauta sai kai komo suke wajen
shirya inda taron ze gudana, su bimbii kuwa su aikinsu a wannan wuri shine su
rissina d'iyan saraki suna bi takansu tamkar sun sami gada sbd tsa6ar izzah da
daukar bawa ba a bakin koman komai ba, dukkanin wadannan ya'yan sarakuna sun
hallara shima kansa prince akbar ya iso cikin wata alkyabba golden da rawaninsa
ruwan k'wai sai irqa baqi daya dora a saman kansa, princess hindu ita ta iso a
qarshe cikin wani keken doki yasha ado, bayinta na biye da ita, dage keken dokin
sukayi ta sakko, takan bayi itama ta wuce har ta isa wurin zamanta dake kusa da
prince akbar, bimbii kawai baiwa idanunta abinci take tana 2kalle don taga wata
al'ada ce ta daban, princess hindu idan mgnr tsantsar kyawu ake toh tabbas zata iya
cin gasar sarauniyyar kyau don bayan izzar da take taqama dashi na jinin sarauta ga
kuma na kyawu da cikar asali, tasha ado na kwala kwalai,wata doguwar rigace a
jikinta irinta d'iyan saraki kalar sararin samaniyya, 2ciye suka soma da 2shaye
suna raha da barkwanci a tsakaninsu jinin sarauta, prince akbar yana daga zaune
fuskar nan tashi dai ba yabo ba fallasa, wata baiwa na hango tsaye a bayansa amma
ita sanye take da kaya masu kyau tamkar ba baiwa ba, kallon israt bimbii tayi tace"
waccar ta dake bayan prince wacce ita?" tace"itace lenah babbar baiwa a 6angaren
prince akbar, ita ke kula da duk wani ci da shanshi da kula da wurin kwanciyarsa
kai har ma ta tayashi kwana ta raya masa dare idan yana da buqatar hkn" jinjina kai
bimbii tayi tana cin tuffan dake hannunta tana qara kallon lenah, tana da kyau
itama ko hassadun iza hassada ze furta hkn, bimbii ta kuma kallon israt tace"
kince har da tayashi kwana idan da buqatar hkn toh kuma ai ba matarsa bace" dariya
lailah tayi don tana bayansu tana jin hirar tasu tace" su al'adarsu shine d'an
sarki da sarkin shi kansa idan sun ga baiwa ta musu sukam maidata ta zama
kwarkwararsu amma da kyakykyawan sharad'i kar baiwar ta yadda ta fad'a soyayyarsu
bare har ki nuna feeling dinki garesu sannan kuma ba haihuwa tsakaninku dasu don
basu hada jini da bayi, hukuncin kisa shi yake tabbata ga duk baiwar data qetare
wannan sharad'i ko kuma daurin rai da rai har qarshen rayuwarta, mafi yawan bayi
suna son su kasance a wannan matsayi sbd tamkar an y'antasu ne kuma duk abunda suke
so zasu samu,zakici maikyau ki saka mai kyau ki fita ki tafi duk inda kkso sbd
kina da y'anci, zakiji dadin rayuwa idan kk samu kanki a wannan matsayi saidai
karki sake ki karya sharadin nan" jinjina kai bimbii tayi tace" yoo idan bakai kai
ba meye hadin zomo da kura ai ramin kura sai y'ayanta,bawa ai sai ya tsaya iyakar
matsayinsa" murmushi israt tayi tace" kin ga ni kuma wlh kullum addu'ata Allah yasa
shekara mai zuwa idan na shiga gasa na samu" harararta khulood tayi tace" waye ya
fada miki rukunin bayin da muke ciki suna samun damar shiga gasar, rukunin bayi na
biyu dana uku suke da damar shiga wannan gasa" bimbii tace" au kafin ma ka samu
matsayin kasance baiwar prince din sai anyi gasa" sukace mata" ehh mn, sai an
gwadaku kafin a fitar, duk shekara yake sauya baiwa" bimbii tace"tirqashi!" fitowar
wasu jerin yan matan bayi ne ya janye hnklinsu daga hirar da suke,yan matan su sha
biyu ne suka fito don nishadintar da wurin da waqoqi, sanye suke da skirt mai baza
ta qasa da wata qaramar riga iyaka cibiya,rawa suka fara tare da girgixa jikinsu
sannan zabiyar cikinsu ta soma rera wak'a mai dadi, wurin yyi shiru kowa na
sauraron baitocin dake fita cikin wannan wak'e nata, baitoci ne da suka shafi
rabuwar masoya, baitocin nata sun samu ta6a zuciyar masoya dayawa dake wannan wuri,
bimbii sunkuyar dakanta tayi tana murza wani zobe dake yatsanta na tsakiya tana
kuka da hawaye don ta tuna ranar da lamid'o ya bata wannan zobe da kuma rabuwarsu
dashi ta qarshe itace ranar da wad'annan turawa suka kamasu lkcin sun dawo daga
tallan nono suna sauri su koma gd don magriba ta kawo jiki Allah ya hadasu da
wadannan turawan akan hanyarsu ta komawa rugarsu suka kamesu suka sanyasu cikin
mota, kullum tunaninta shine wanne halin innanta yadikko zata shiga silar
6acewarta,wanne hali baffi da lamid'o zasu shiga silar 6acewa, tabbas tasan rayuka
dayawa suna cikin wani hali dalilin 6acewarta, kuka take sosai saida su khulood
suka rumgumota suna bata hkr, idanun gimbiya hindu ne ya tsaya akansu lkcin suna
rumgume da bimbii suna bata hkr, nunawa babbar baiwarta su tayi da idanunta
tace"wadan can bayin dake bayan bishiya me suke" kallon wurin zulham tayi
tace"ranki ya jima suna rarrashin yar uwarsu ne" tace"aikin da suka zo yi wurin nan
kenan, basu san murnar zagayowar babban prince muke ba shine suka ware kansu daga
cikin yan'uwansu bayi suka koma gefe, toh kije ki tahomin dasu nan gabana naji me
suke tattaunawa" cikin sauri zulham ta nufo wurinsu tace" gimbiya na son ganinsu
gabanta" dukkaninsu gaban ya fadi suna tunanin ko laifi sukayi, itako bimbii ko
d'ar bataji ba tunda dai tasan babu abunda tayi, hk ta sakosu a gaba ta kawosu
gaban gimbiya hindu duk suka durqusar da guiwowinsu gabanta tare da rissinar
dakansu qasa, lkcin ne idanun kowa dake wurin yazo kansu har shima prince akbar ya
kallesu sau daya ya dauke kansa ya cigaba da shan ruwan inibin dake gabansa, daya
bayan daya gimbiya hindu ke binsu da kallo ta tsaida idanunta kan bimbii tana qare
mata kallo, tace" kece kk janye hnklinsu daga kan aikinsu koh" shiru bimbii tayi su
kuwa su khulood sai suka sake rissinar dakansu suka hada baki sukace" mun tuba
ranki ya dade" kallonsu tayi ta yatsine fuska tace" su tashi su bata wuri amma
bimbii kuwa ta tsaya saita musu rawa da wak'a na abunda yasata kuka" kallon zulham
tayi tace" ta sanar da mai gabatarwa ya gabatar da bimbii a matsayin mai rawa ta
gaba" aikuwa hk akayi, duk wurin bimbii suke kallo itako gabanta sai faduwa yake,
bata iya waqar larabci ko guda ba sai na harshenta na fillaci, kama hannunta zulham
tayi ta fice da ita suka shiga wani wuri ta sauya mata kaya ta saka mata rigar nan
iya ci6i da skirt mai baza ta qasa ta taje mata gashin kanta ya sakko mata har
duwawu gashi da cikowa kuma baqin qirin dashi, bimbii kallon kanta tayi ta kalli
zulham tace" hk zan fita gaban mutane kuma ni ban iya wak'a cikin harshen larabci
ba" tamkar tana mgn da dutse don zulham aikinta kawai take ba sauraronta ba, tana
shiryata ta kamo hannunta suka fito lkcin yan matan dake wak'e sun bar wurin bimbii
ake jira, idanun kowa nakan bimbii sbd yadda kayan nan dake jikinta ya fito da
asirin dirin dake tattare da ita sannan suna mamakin tsawo da cikar gashinta
kasancewarta baqar fata amma ta zarta dayansu tsawon gashi da tsantsar diri irinna
mata, itako bimbii tsayawa tayi a wurin ta kasa komai sai kallonta suke suna jiran
suji ta fara rero baitoci, a hnkli ta soma juya qugunta tana girgixa tamkar
macijiya wata irin rawa take wacce take sabuwa a wurinsu, basu ta6a ganin salon
rawan ba, cikin zazzaqar muryarta me amsa amo ta soma rero baitocinta cikin
harshenta na fillanci tana juya qugu cikin wani salo rawa irin nasu na d'iyan
fillo,rawar ce ta dauko hnklin kowa kanta, prince akbar dago da kansa yyi yana
kallonta tashi daya yaji rawar da take da kuma wak'en da take cikin harshen nata ya
sanyashi nishadi sosai har wani lumshe idanu yake, hk suma sauran yaran sarakunan
dake wurin musamman prince nasaar daya qurawa bimbii idanu yana kallon zubin tsarin
halittarta, kunsan dai san larabawa da mugun qulaficin jikin mace, gimbiya hindu
kuwa gbdy haushin kanta tayi na kuskuren sanya bimbii rawa, kishi sosai taji tanayi
data ga yadda rawar da bimbii take ta dauke hnklin ya'yan sarakunan dake wurin,
miqewa tayi zumbur ta buga teburin dake gabanta cike da tsantsar masifa ta dakawa
bimbii tsawa kan tabar wurin, duk ya'yan sarakunan suka jiyo suna kallonta prince
nasaar yace" no, ta cigaba rawan nata ya birgemu" tace" wlh idan bimbii ta cigaba
ita zata bar wurin" dage kafa bimbii tayi alamar ta gama rawan ta taho kanta a qasa
ta soma qetarawa ta gaban prince akbar ta wuce shi kuma yana satar kallonta ta
gefen ido sai wanda ya lura sosai ne ze fahimci ita yake kallo,ita kuwa bimbii
shigewa tayi taje ta sauya kayan dake jikinta ta mayar da nata na asali, har aka
gama taron gimbiya hindu tacewa baiwarta zulham kar ta sake tabar bimbii ta kuma
dawo wurin taron, bimbii ta gama sauya kaya zulham tace" ki wuce ki koma 6angarenku
karki kuma dawowa wurin taron nan" bimbii kuwa dadi taji don daman kunya takeji ta
koma wurin,kai tsaye 6angarensu ta koma tana jiran dawowar su lailah, sai dab da
magriba su lailah suka dawo suna shigowa duk suka taho da gudu suka rumgumeta,
israt tace" gsky kin iya rawa zaki koyami nima" murmushi bimbii tayi kawai,ranar
basu yi bacci da wuri ba sai faman jarraba yadda bimbii ke rawa suke ita kuma sai
dariya take musu, israt tafi kowa zaqewa don ita a rayuwa tana son rawa da
wak'a,bimbii na koya musu irin rawarta suma suna koya mata irin nasu hk suka 6ata
darensu sun qi kwantawa da wuri duk da kasancewar gobe ayyukansu yana dayawa,
aikuwa suna kwanciya bacci mai nauyi yyi gaba dasu, washegari ummul shukri taga
dukkaninsu babu wacce ta fito kan aikinta, dogaro sandarta tayi ta shigo dakin nasu
ta tarar dasu sai sharar bacci suke ba wacce ta tashi a cikinsu, juyawa tayi ta
fice ba tashesu ba, suna tsaka da sharar baccinsu sukaji saukar ruwan sanyi a
jikinsu gbdy an musu wanka dashi kafin su gama sanin abun yi sun soma jin saukar
dorina a jikinsu, miqewa sukayi da mugun gudu suka fita, ita kuwa ummul shukri tana
tsaye da dorina a hannunta ranta yyi mugun 6ace don batason sakaci da aiki.....

Littafin nan na kudi ne ki biya ki karanta cikin yanci ba satar faga ba, idan kin
shirya siye ga transaction details nan, #300 ta wannan acct..0100790419,alhaji
shahida nasir,union bank, saiki turomin da screenshrt na payment dinki ta whatsapp
through wannan layin 07041195806, idan kuma da buqatar bayani ga layin kira nan
08080611486....

Alkalamin Bintuu ne...


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

7
*We are far apart from the thousand miles of journey only the destiny links us
together*.......never,never leave me my luvv💕

Raba musu aiki ummul shukri tayi ranar kowacce tayi 6angaren da aikin nata
yake,bimbii tsinko kayan marmari ne nata takai babban kitchen,israt da lailah kuma
wanki ne nasu, khulood kuma tatso nonon raqumi, kowanne cikinsu yyi hanyarsa,
bimbii zuwa tayi ta dauki kwando ta tafi lambu, tana shiga ta haye bishiya tana
tsinko tuffa tana jefowa qasa tana yar waqarta cike da nishad'i, tana cillo na
qarshe sai kawai gani tayi mutum ya chafe, prince nasaar ne fuskarsa dauke da
murmushi yana kallonta, ita kuwa bimbii tsa6ar mamaki ne ya hanata sakkowa daga
bishiyar saida ya mata alamar ta sakko da hannu sannan ta sakko,dole bimbii tayi
mamakin ganinsa don ta karanci akwai izzah da cikakkiyar qasaita irinta sarauta ga
jinin sarautar burham, tayi duba da yadda suka dauki bayi ba a bakin komai ba, idan
har sunanka bawa kana dauke da tambarin bauta toh suna maka kallon qasqanci ne tare
da nuna izzarsu akanka toh mamakinta shine me ya kawo wannan d'an sarki gareta,
tashi guda tsoro da fargaba suka mata qawanya sai kallonshi take tamkar taga wani
baqon mutum, tunawa tayi bata gaishe shi ba, saurin duqawa tayi akan guiwowinta
tare da rissinar dakanta qasa yadda taga bayin wannan gida nayi, murmushinsa ya
fad'ad'a ya tsuguna kusa da ita yana qarewa kyakykyawar fuskarta kallo, ita kuwa
jikinta har rawa yake ta qosa tabar wurin, shima kansa ya fahimci hkn shiyasa ya
miqe yace" me sunanki" cikin hard'ewar baki tace" bim...bii" yace" daga ina kk
fito" tace" gombe" shikan besan ina ne gombe ba dama cewa tayi nigeria wataqila ya
fahimci sunan qasa take nufi daga qasashen africa,murmushi yyi yace" koh na tayaki
kwashe tuffan ne" saurin girgiza masa kai tayi jikinta na rawa ta soma tattara
tuffan data tsinko tana zubawa cikin kwando tana gama ta soma qoqarin daukan
kwandonta ta tafi, daukan kwandon yyi ya dora mata akanta yace" bimbii sai anjima"
saurin kallonsa tayi tana mamakin jin yadda ya furta sunanta, sauri sauri take ta
fice daga lambun shi kuwa yyi folding hannunsa a tsakiyar qirjinsa yana kallonta
har ta fice daga lambu, sauri take tamkar zata kife tanayi tana waiwayen bayanta
burinta kawai tabar wuraren lambun, ita batason ta shiga idanun wadannan y'an
sarautan tana zaman zamanta lfy, kitchen ta wuce takai musu suka juye kayan
marmarin suka bata kwandon ta mayar dashi ma'ajiyarsa sannan ta dauki tulu ta nufi
qorama de6o ruwa, ranar hk ta yini da fargaba fal cikin ranta tana mamakin dogon
zancen da wannan d'an sarki yyi mata, hk ta gama aikinta ta koma 6angarensu na
bayi, tana shiga taga su israt ranar sun rigata dawowa, hannunta khulood ta kamo
suka zauna dukkaninsu a qasa suka sanya abincinsu a tsakiya suna ci, bimbii gani
tayi su uku ne kawai ba lailah ta kallesu tace" ina lailah take" khulood ta nuna ta
masa wurin da lailah ke kwance tace" batajin dadi ne" saurin cire hannu bimbii tayi
daga abincin ta nufi wurin da lailah ke kwance bisa busassun ciyayin da suka saba
kwanciya ta dafata tace" lailah sannu koh" dagowa lailah tayi da kanta tana mata
murmushin qarfin hali,hannunta tasa ta ta6a jikin laila tajishi zafi zau, miqewa
tayi ta fita ta samu qaramin bowl ta ciko ruwan sanyi a ciki ta shigo dashi,
mayafin kanta ta cire ta sakashi cikin ruwan tana matsewa tana sanya mata a jiki
sbd jikin nata ya rage zafi, khulood da israt suma duk suka matso inda laila ke
kwance, zazza6i ne sosai a jikin lailah, tashi d'aya kuma saita soma yunqurin amai
ta fita ta dinga kwarara amai, khulood da israt suka fita da sauri don amsowa laila
magani a dakin amsar magani, suna zuwa suka tarar k'ofar wurin a rufe sbd gsky dare
yyi sosai, buga k'ofar suka dinga yi amma jahan yaqi bud'ewa don shine babban bawan
dake kula da wurin maganin, hk suka gaji suka koma, bimbii na ganinsu ta taso da
sauri tana tmbyrsu ko sun amso maganin, duk sukayi shiru tana ganin hk tasan basu
amso ba, tace" sun kulle k'ofarsu koh" suka daga mata kai alamar ehh,duk sun zagaye
lailah sunyi shiru suna kallonta tana numfashi a hnkli gumi sai keto mata
yake,bimbii ta kallesu tace"toh yanzu meye abun yi" khulood tace" kawai muje mu
haura katangar wurin mu sato maganin tunda na tabbata jahan na jinmu ya mana banxa
sbd rashin imani" israt tace" hkma zamuyi" bimbii tace" toh kuma kar muje su kama
mu" khulood tace" insha'Allah ba zasu kama mu ba, ta baya zamu duqa basa rufe kofar
ciki a bud'e suke barinta" hk suka fito cikin wannan tsakiyar daren su uku suka
soma la6a6awa cikin sand'a har suka qarasa gdn maganin,dayake sun saba da haura
bishiya take suka haura katangar gdn magani suka soma tfy cikin sand'a, israt ce ta
bud'e kofar a hnkli ta soma shiga bimbii na biye dasu, bincike suka somayi a wurin
da magunguna ke jera har suka samo maganin zazza6i suka juya zasu fita, sai kawai
jin muryar jahan sukayi yace" duk wanda ke cikin wurin nan ya tsaya karya fita" duk
suka kalli juna cike da tsantsar tsoro, bimbii tayi saurin turasu waje tace" su
suyi gaba zata biyo bayansu don tasan tabbas idan ya shigo be ga kowa ba kasancewar
yaji motsin mutum a wurin ze ankarar da bayin dake tsaron wurin ne shiyasa ita ta
tsaya tace su tafi, suna tfy suna waiwayen k'ofar suka sake haure katangar suka
fice amma sai suka qi tfy suka tsaya jiran fitowar bimbii, bimbii kuwa tana ciki
jahan ya bud'e kofar ya shigo, kallonta yake cike da mamaki yace" me ya kawoki nan
wurin" tace" magani nazo amsarwa yar uwata tana fama da zafin zazza6i kuma nayi
bugu ba'a bude ba" murmushin mugunta yace" shine kk shigo satar maganin, alamu sun
nuna bakisan hukuncin sata a wannan masarautar bane koh" bimbii tace" toh kaimin
aikin gafara" dariya yyi sosai yana qare mata kallo, yace" zan miki aikin gafara
amma da kyakykyawan sharadi,kin amince" tace"fadi sharadin naka naji" dariya yyi a
karo na biyu ya soma kusanto inda take ita kuma tana matsawa har ya cimma mata
yace" sharadin nawa shine ki aminta dani wannan daren ki de6emin kewa" hannunsa
yakai saman qirjinta, saurin buge masa hannu tayi tace" idan wannan ne sharadin
naka toh bana buqatar gafararka gareni" dariyar mugunta yyi yana tauna asuwakin
dake hannunsa, kallon qafarta yyi yaga sarqar kafan nan ya gane rukunin bayin da
take, nuna mata kofar fita yyi yace" ga hanya nan zaki iya tafiya" a hnkli ta soma
takawa tana kallonsa shi kuma yana mata dariyar qeta har ta fice ta haura ta
katangar da suka hawo ta dire, ga mamakin sai ganin su khulood tayi a raku6e suna
jiran fitowarta suna ganinta suka rumgumeta suna tmbyrta abunda ya faru, tace" babu
komai,muyi saurin barin wurin nan kar wasu su ganmu" hk suka din ga la6a6awa suka
koma 6angarensu, suka tarar da lailah sai murqususu take sbd zafin ciwo, cikin
sauri suka hada maganin suka bata tasha, gumi sai keto mata yake a hk ta samu
bacci, kallon bimbii khulood tayi tace"ki fada mn abunda ya faru a gdn magani,
jahan ya ganki ne" daga mata kai tayi tana neman basar da zancen amma suka matsa
dole ta sanar dasu yadda suka qare da jahan din, shiru taga sunyi tace" qalau dinku
kuwa" israt tace" bimbii jahan mugun mutum ne besan arxiki ba cikin rayuwarsa tunda
kkyi hk dashi toh wlh da abunda ze biyo baya gobe sbd basu daukan irin hk da sauqi
cikin wannan masarautar" bimbii tayi murmushi tace" karku damu da wannan kudai ko
mene ma ya biyo baya karku sake ku sanya kanku ciki" khulood tace" abunda bazai
yuwu ba kenan, tunda har tare muka shiga toh koma meye ya biyo baya tare zamu
tareshi" girgixa musu kai bimbii tayi tace" idan mukayi hk toh zamu 6ata biyu ne
daya be kyaru ba, kun ga muna da mara lfy wa kk tsammanin ze kula da ita idan
dukkaninmu muka tafi amsar hukunci, karku damu kudai kuyi yadda nace abun zezo mana
da sauqi" shiru sukayi basu furta komai ba har suka kwanta bacci zuciyoyinsu cike
da tunanin qarfin hali da tsantsar jarumta irinna bimbii, washegari da sanyi
safiyya suka tashi, laila ma tadan ji dadin jikin nata, suna shirin fita kenan
ummul shukri ta shigo 6angaren nasu ranta a mutuqar 6ace tana zuwa ta kalli bimbii
tace" ke ki fita farfajiya ki amshi hukuncinki na shiga sata gdn magani" bimbii ta
miqe ta fita batare data furta komai ba, wasu manya manya bayi ta gani su biyar
riqe da wasu zabga zabgan bulalai, suna ganinta suka nuna mata kan wani itace dogo
wai tahau ta kwanta ta juya bayanta, bata musu gardama ba tahau ta juya musu baya
suka soma zabga mata wadannan manyan bulalan na hannun, lkcin ummul shukri ta fito
riqe da sandarta tana kallon yadda suke hukunta bimbii, israt da khulood kuwa gani
sukayi sam basu iya kyale bimbii ta amshi hukunci ita kadai ba suka dawo da gudu
duk suka zo wurin suka durqushe da kafafunsu, ummul shukri ta tmbyeshi mene ya
kawosu wurin sukace" muma mun zo amsar hukunci ne don tare muka shiga gdn maganin
da ita" wata uwar tsawa uwar bayi ummul shukri ta daka musu tsawa tace" su 6ace su
bata wuri,dole suna ji suna gani bimbii ta amshi hukuncinsu, bulala tamanin suka
mata"duk jikinta ya farfashe jini ne kawai ke fita ya 6ata rigar dake jikinta amma
abun mamaki ko digon hawaye basu gani ba a idanun bimbii, hk suka tasa qeyarta tana
tangadi suka tafi da ita kurkun da ake kulle bayin da sukayi sata wai sai tayi sati
biyu kafin ta fito, suna shiga da ita suka watsata cikin kurkun suka fito abinsu"
tunda suka watsata bata dago da kanta ba sbd radadi da ciwo da jikin yake mata,
tana kwance saman busassun ciyayin dake qasan wurin sai lkcin wasu hawaye masu
d'umi suka soma sakko saman kuncinta, tabbas rashin yanci beyi ba, kafin dare
ko'ina na jikinta ya suntume ya kumbura gashinta duk ya rufe mata fuska babu
dankwali a kanta, idanunta sunyi jajir sun kumbura sbd tsa6ar kuka data tayi wannan
dare,ga ciwo na cinta amma babu magani, Allah shi kadai shine gatanta don bata da
wani gata kasancewarta qasqantacciyar baiwa mara galihu, 6angaren su israt da
khulood kuwa ranar ko abinci kasa cinsa sukayi suna tunanin yar'uwarsu bimbii ga
lailah kuma a kwance jiki ya kuma rikicewa, daren ranar ummul shukri ta shigo
6angaren nasu ta taddasu 2jugum, kallon yanayin lailah kawai tayi tasa hannu ta
dago
da ita tana qare mata kallo take ta hade fuska ta kalli tsakiyar idanun lailah
tace" kina da juna biyu lailah, waye yyi miki ciki lailah" wannan kalma da uwar
bayi ummul shukri ke furta ita ta razanar dasu israt dake gefe suka soma kuka,
lailah kuwa duk da zafin zazza6in da take fama dashi kalaman ummul shukri sunyi
masifar fadar mata da gaba, ta kalli uwar bayi ummul shukri tace" ciki? ciki ne
dani" kafin ta rufe baki ummul shukri ta zabga mata mari har uku a fuska tace"
kinsan hukuncin wannan abun kunya da kk aikata kuwa?" lailah kuwa kuka take sosai
har da sheshsheqa tana roqon uwar bayi ummul shukri ta rufa mata asiri ta mata
aikin gafara,ummul shukri bata kuma cewa komai ba ta miqe ta fita, tana fita su
israt da khulood suka taho wurinta da gudu suna tmbyrta abunda ke faruwa da ita,
lailah kuwa kuka kawai take tana tausayin kanta da rayuwarta,israt ta riqo hannunta
tace" lailah me kk 6oye mn baki daukemu yan'uwa ba kenan" kuka take sosai ta kasa
furta komai,khulood tayi shiru tana tunanin wani abu,a hnkli ta dago kanta cike da
rudani da tsantsar fargaba hadi da tsoro ta kalli lailah suka hada idanu tace"
lailah,lailah meyesa kkyi hk,lailah abunda nk tunani shine,kicemin aa lailah" sai
kawai ta fashe da kuka ta soma jijjiga laila tana cewa tace mata aa, kallon khulood
israt tayi cike da mamaki tace" akwai abunda kk 6oyemin,akwai abunda ya faru ban
sani bane" miqewa tayi ta soma turesu tana kuka tana cewa baku yarda dani bane
kuke 6oye min abu.......

Littafin nan na kudi ne ki biya kiyi karatu na yanci bana satar fage ba,naira dari
uku kacal ta siya miki qarashen labarin DAREN GOMA SHA HUDU....zaki tura #300 ta
wannan acct..0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, sai turomin da screeshrt
na payment naki ta whatsapp...07041195806, idan da buqata wani qarin bayani ga
layin kira nan..08080611486

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

*My luv to you is beyond words but looks into my eyes you will believe the real
magic of your pure luv in it*........I give you my heart dear...💕

Janyo hannunta lailah tayi duk ta hadasu ta rumgume, kuka suke sosai sai can
khulood tace" bazan ta6a gafartawa kaina ba lailah idan har wani mugun abu ya faru
dake" rufe mata baki lailah tayi tace" ki daina fadar hk a rayuwa kowa da
qaddararsa kuma babu wanda ya isa ya goce mata, qaddararmu shine mun zo lkcin da
masu mulki da sarauta suke da qarfin izzah tare da murqushe wanda baida y'anci,
dole mubi rayuwar yadda tazo mn" khulood tace" meye amfanin abunda kkyi lailah da
kin bari mun amshi hukuncinmu a lkcin da duk hk bata faru dake ba" shiru lailah
tayi tana tunanin abubuwan da suka faru kwanakin baya wanda shine silar shigarta
wannan hali yanzu, khulood da lailah sun ta6a yunqurin guduwa kwanakin baya Allah
bai basu sa'a ba aka kamasu don basu da shaidar fita,yawanci yantattun bayi suke da
damar fita ko'ina su kuma bayi na qasa qasa saidai idan suna da shaida fita tare
dasa hannun wani sananne cikin masarautan, bawan daya kamasu shine raqas babban
bawa dake kula da babbar kofar fita daga masarautar,hukuncin bawan da aka kama da
yunqurin gudu shine kisa ko kuma akaisa baqin kurkun qasa,kurkun qasa kurku ne da
suka tanada a qarqashin qasa suke ajiye masu babban laifi tare da azabtar dasu,
lkcin da raqas yaga su lailah da khulood na yunqurin gudu ya kamasu, ba kalar roqon
da basu masa ba yyi kunnen uwar shegu dasu yace" wlh sai ya kaisu gaban hukuma sun
amshi hukunci daidai da laifinsu amma daga qarshe sai ya nemi lailah ta amince ta
kwana tare dashi shi kuma sai ya rufa musu asiri, lailah tayi qememe taqi amincewa
da hkn, yace toh su tafi gobe su tsumayi sammaci, hk suka dawo 6angarensu cike da
tsoron abunda ze biyo baya, lailah ba kanta take tausayawa ba khulood dake jin
tausayi gani take idan bata amince da buqatar raqas ba toh fa daga ita har khulood
basu tsira, lkcin da suka dawo israt ta tmbysu ina sukaje sai suka 6oye mata basu
fada mata abunda sukayi ba, lailah koh saida ta bari bacci ya kwashe ta tashi ta
fice ta tafi wurin raqas, shi kuwa yana ganinta yyi murmushi yace" kinyi tunani
maikyau da kk dawo don kuwa da rayuwarku ta shiga garari" lailah bata ta6a tunanin
samun shigar ciki ba akan wannan dare kawai, sai wurin asuba ta sato jiki ta dawo
lkcin khulood na zaune don ta tashi bata ga lailah ba kuma tabbas zuciyarta ta bata
lailah komawa tayi wurin raqas, tana zaune lailah ta shigo idanunta jajir ga dukkan
kuka tasha, ganin khulood zaune ne yasa ta soma goge fuskarta, khulood ta zuba mata
idanu tace" lailah ina kkje" shiru lailah ta mata itako khulood qara kallon lailah
take sosai taga tfyrta ta sauya, miqewa tayi zumbur ta nufo inda lailah take tace"
lailah komaqa kkyi wurinsa kk miqa masa budurcin naki" rufe mata baki lailah tayi
tace" kiyi shiru kar israt taji hnklinta ya tashi, khulood bamu da wata mafita sai
wannan tunda ya bamu za6i" khulood kasa mgn tayi sai durqushewa da tayi a wurin
tana kuka sosai, wannan shine abunda ya faru dasu kwanakin baya, hk khulood sanar
da israt abunda ya faru, dukkaninsu kuka suke sosai suna tausayawa lailah don ba
makawa hukuncin jefewa ne ya rataya akanta,washegari dukkaninsu ba wacce hnklinta
yake a kwance kowacce cikin fargaba da tashin hnkli take amma duk da hk saida suka
tafi kurku don ganin halin da bimbii take ciki har da lailah, 2qiri bayin dake
tsaron wurin suka hanasu ganinta hk suka koma bakin ayyukansu, bimbii kuwa yunwa
qishin ruwa ga radadin ciwo duk sun galaibartar da ita, kwanan bimbii biyu prince
nasaar yaga baya ganinta sbd yasan duk wurin zuwanta, sanya wani hadiminsa yyi
bincike akanta, batare da wani 6ata lkci ba ya binciko masa inda bimbii
take,dakansa yaje kurkun yasa a fito da ita, jiki na rawa suka fito da bimbii bata
ma gane abunda ke faruwa, wata baiwarsa yasa mai suna salma ta tafi da bimbii ta
kula da raunin dake jikinta, hk kuwa akayi salma ta tafi da bimbii wani 6angare na
daban ta bata ruwa tayi wanka taci abinci ta bata wurin kwana,tunda bimbii tazo
qasar sai ranar ta ta6a kwana a abu mai laushi, salma mace ce mai kirki hk ta din
ga kula da bimbii tana shafa mata magani a raunin dake jikinta sbd kar ya bar mata
ta6o ita mace ce,6angaren su khulood kuwa basu da masaniya kan sakin bimbii da
akayi gashi kullum suna cikin tashin hnkli da tsammani don har yanzu uwar bayi
ummul shukri bata kuma furta komai ba kan mgnr lailah, satin bimbii biyu ta murmure
sosai don bata aikin fari bare na baqi kawai kula take samu saidai kewar qawayenta
da take wato su lailah dukda kasancewar suna cikin gdn sarautan amma da akwai ta
tazara sosai tsakanin 6angare zuwa 6angare, bimbii har yanzu batasan waye silar
fitowarta daga kurku ba ita dai kawai ta samu kanta a hannun salma kuma itama
salman bata fada mata wanda yasanya a fito da ita daga kurku ba, sati biyun na cika
salma ta rakata zuwa 6angaresu, su israt kuwa tun safe suka tafi kurku suna zaton
ranar za'a saketa amma har suka gama tsayuwarsu basu ga an bude kofar kurkun ba hk
suka dawo jikinsu a sanyaye saidai mezai faru? suna dawowa daga ayyukansu ummul
shukri ta shigo ta sanar da laila ta fito, duk suka biyo bayan laila suka fito,
gabansu ne ya fadi lkcin da suka ga bayin dake aiki a kurkun qasa sun gane sune sbd
kalar kayan dake jikinsu, suna ganin fitowarsu suka tmbyi ummul shukri wacce daga
cikinsu ta nuna musu lailah,basu wani 6ata lkci ba suka tasa qeyar lailah suka
tafi da ita,khulood da israt kuka suke sosai suna riqe lailah amma hk suka
hankad'asu gefe suka wuce da ita,suna ji suna gani aka tafi da laila babu suka iya,
toh suna cikin wannan jimamin ne suka ga shigowar bimbii, salma bata biyo bimbii ba
tana kawota bakin 6angaren nasu ta juya, cike da mamaki duk suka miqe suna kallonta
don kyau ma ta qara musu da gudu suka taho suka rumgumeta suna kuka, murmushi tayi
musu ta duba bata ga lailah ba tace"ina lailah take, jikin nata da sauqi koh" gani
tayi duk sun mata shiru, gabanta ne ya fadi don idan har ta tmbyi su lailah abu
taga sunyi shiru sun sunkuyar da kawunansu toh amsar ce babu dadi, tace"wani abu ya
faru ne" khulood tace" sun tafi da ita" tace" su waye" jan hannunta israt tayi suka
koma suka zauna sannan suka zayyane mata abubuwan da suka faru, bimbii tayi shiru
hawaye na fita daga idanunta,juya musu baya tayi ta kwanta bata kuma furta komai ba
sbd zuciyarta quna take da tafasa, suna son tmbyrta abunda ya faru da ita amma sun
fahimci sam bata mood nason mgn, bimbii kuwa wata irin tsanar wannan masarauta ce
ta darsu cikin ranta,gani tayi abun yyi yawa su gbdy basu dauki rayuka a bakin
komai ba,alwashi taci koda zata rasa ranta sai ta kubutar da lailah daga wannan
hukunci na zalinci da suke son aiwatarwa akanta, washegari sunyi mamaki sosai da
suka ga bimbii ta saki ranta ita kuma tayi hkne don ta sanyasu suma su saki ransu
suyi ayyukansu yadda ya kamata kar suje suyi kuskure suma hukunci yahau kansu, yau
bimbii ita daya ta dauki tulu ta tafi babbar qorama debo ruwa,tana zuwa ta tsuguna
zata fara deban ruwanta ta hango wata tsuntsuwa mai kyau da daukar hnkli a jikin
wata bishiya aikuwa sai ta ajiye tulunta ta soma lalla6awa da niyyar kama
tsuntsuwar,tashi tsuntsuwar tayi ta sauya wuri, ita kuwa bimbii sai binta take wai
ita zata kamata suna cikin hk har sukayi nisa da wurin qoramar data tabar tulun
ruwanta, tsuntsuwar har bakin wani lambu takaita sannan ta tashi firrrrr ta6ar
wurin,bimbii kallon tsuntsuwar take har ta qurewa ganinta, tsak tayi ta juya zata
koma inda ta baro tulunta, hango yalwar bishiyoyi tayi a cikin wannan lambu kuma
alamu sun nuna lambu yana cike da yalwar kayan marmari, kofar shiga lambu ta gani a
bude, batare da wani tunani ba ta shiga lambun ta haye wata bishiyar tuffa tana
tsinka tana ci, kishingida tayi abinta akan bishiyar tana cin tuffanta hnklinta
kwance...
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

*Your love become my oxygen I can't live without you*......I'm infected with a
serious virus on earth and you are the only doctor that can cure it......

Wani qasaitaccen k'amshi taji yana tashi ya had'e da ni'imatacciyar iskar dake
kad'awa cikin wannan lambu, tashi tayi zaune ta leqa qasan bishiyar don ganin
abunda ya haddasa wannan qamshi, abunda ta gani ne yyi mugun kad'a y'ay'an
hancinta, PRINCE AKBAK!!.ne shida hadiminsa na hannun dama wato ubaid, tun
shigowarsu suka ganta bisa bishiya abun yyi mugun basu mamaki, baiwa cikin lambu
babban prince, ita kuwa bimbii tsabar tsorata kasa had'iye tuffan dake bakinta tayi
ta sake baki tana kallonsu tamkar wata doluwa, prince akbar kuwa ko kallon bishiyar
da take be sakeyi ba yyi gaba abinsa cikin qasaitaccen takunsa da yake bayyana
tsantsar izzarsa da kuma isar matsayinsa, ubaid ya gama sanin halin babban prince,
idan yana son bashi umarni da ido kawai idan ya kalleshi yana sanin me yake nufi
take ze aiwatar, shi prince mgnr ce take masa mutuk'ar wahala tamkar d'an kurma hk
yake sai tayi masifar kamawa yake bud'e bakinsa yyi mgn, wata irin tsawa ubaid ya
doka mata wanda sauran qiris ya rage ta saki fitsari a wando ba shiri ta diro daga
saman bishiya ta kife akan guiwowinta, kallonta ubaid yyi cike da qasqanci yace"
wace ce ke? yanayinki kawai ya tabbatar min kedin qasqantacciyar baiwa ce amma ki
rasa ina ya dace ki sauke raininki sai a lambun babban prince" kuka bimbii ta soma
masa tace" don Allah kuyi hkr wallah ni bansan lambunsa bane" ubaid tsayawa yyi
kawai yana kallonta don tabbas shi kansa ya yaba da k'arfin halinta, fuskarsa a
murtuke yace" kije ki jira a waje" miqewa tayi sum sum tana d'an waiwayen baya
musamman qaramar k'ofa dake cikin lambu da taga prince akbar ya shiga ya barsu a
wurin,ubaid kuwa yana ganin ta fice yabi bayan prince cikin k'ofar shima sai gashi
ya fito wani babban fili, prince ya hango yana gwada saitin harbin mashi, sauri yyi
ya qarasa gefensa ya tsaya yana miqa masa masun dake hannunsa shi kuma yana amsa
yana harbawa daidai saitin wata bishiya, bimbii kuwa tana wajen lambun tana jiran
fitowar ubaid amma shiru shiru babu shi babu alamarsa har gari ya soma
lumshewa,rana na dab da faduwa suka fito daga lambun tasha jira har ta gaji bacci
ya dauketa a wurin, sai lkcin prince ya kalleta sosai tana baccinta a wurin, tsayar
da idanunsa yyi sosai akanta abun har ya bawa ubaid mamaki don be ta6a ganin prince
ya qurawa abu idanu hk ba, bud'e idanunta tayi a hnkli taga inuwar mutum tsaye
akanta, k'afarsa kawai ta kalla tun kafin ta dago da kanta tasan mutum ne da hutu
ya gama ratsashi,k'afarsa sanye take cikin wani farin takalmi half cover shoe,
tunda take bata ta6a ganin mutum mai kyawun k'afa irin prince akbar ba, kafar nan
tasa luwui luwui tamkar tumatir gata jajir da ita kamar ka matsa jini ya fito,
jallabiya ce fara sol a jikinsa sai rawanin daya rufa a kafadarsa dayake ja da
fari, gashin kansa baqin qirin ya sauka har kafadarsa yana rawa tamkar na
mata,idanunsa tamkar yasa tozali gasu a lumshe kamar yanzu ya tashi daga
bacci,sassayan k'amshinsa ne ya cika hancinta,dago da fuskarta tayi suka hada idanu
take taji gabanta ya tsananta bugawa, yana ganin ta dago da idanunta yyi saurin
dauke kansa akanta ya haye dokinsa shima dokin nasa fari, alamu sun nuna prince din
yana qaunar farin abu, kallon ubaid kawai yyi shima ya haye dokinsa suka barta a
wurin batare da sun ce mata komai ba, bin sawun dawakansu tayi da kallo har suka
qurewa ganinta, tashi tayi tana karkad'e qasar dake jikinta ta soma tfy har ta isa
inda ta ajiye tulunta yana nan inda tabarshi ta cika ruwanta ta dora aka ta nufi
cikin gd,tunkan ta qarasa ta hango uwar bayi ummul shukri da tsumangiyanta a hannu,
tana sauke ruwan ta rufeta da duka tace" tun safe ko aiki guda bakiyi cikin
ayyukanki ba sai yanzu kk kawo sawun ruwa daya" shiru tayi batare data kawo wani
uziri ba,ummul shukri bata amsar uxiri ko qaqa,fito mata tayi da wasu manyan
barguna tace ta kwasa taje ta wankesu gashi dare ya soma shiga sosai don ma garin
da hasken farin wata hk ta kwashi barguna ta nufi babbar qorama dasu ta soma tiqar
wanki, tana cikin shanyawa ta gano inuwar mutum a bayanta, juyawa tayi da sauri
idanunta ya gane mata prince nasaar, murmushi yyi mata da fararen haqoransa yace"
wankin dare kuma baki tsoron mura" wani irin murmushi tayi tamkar kuka iyakarsa
le6enta tare da rissinar da guiwowinta tana gaishe shi, tsugunawa yyi kusa da ita
yace" ina buqatar kwarkwara kuma ke nkso" kalmar taji tayi mugun bugarta ta zaro
manyan idanunta waje tare da dafe kirjinta tace" na shiga uku, wlh ni ban iya komai
ba" dariya ta bashi yyi har jerarrun haqoransa suka bayyana yace" zaki koya ai,
zaki zama baiwar dake kula dani kwanan nan" gabanta ke faduwa sosai tana
kallonshi, babban abunda bimbii ke karewa a wannan yanayin data tsinci kanta aciki
na bauta shine budurcinta bata qaunar abunda ze iya rabata da budurcinta, zama
kwarkwara a gdn sarauta ai dole sai ka rabu da budurci kuma ga hadari na daukar
ciki, itakam tafi qaunar ta cigaba da kasancewa a baiwa mara gata idan har budurcin
bazai ta6u ba, sanya hannunsa yyi da niyyar riqo hannunta ta daka wani uban tsalle
tayi gefe, abunda tayi yyi masifar daure masa kai,tunda yake ba baiwar data ta6a
masa hk sai bimbii shi gani yake kamar taimakonta zeyi amma har ta gwada masa
wannan cin fuskar a matsayinsa na jinin sarauta yace"bimbii wannan abunda kkyi
kuskure ne babba kar ki kuma gwada hkn ga duk wani jinin sarauta" yyi mgnr fuskarsa
a sake tamkar beji haushin abunda ta masa, shiru tayi ta sunkuyar dakanta qasa,
wani dutse ya nuna mata yace" ta zauna ta tayashi hira" ji tayi kamar ta kurma ihu
amma ba yadda ta iya hk ta zauna daga can gefe ta dosana duwawunta akan dutsen,
Allah ya sota ta gama wankinta, murmushi yyi don yana lura da rashin sakewarta
yace" bani labarin qasashenku na baqar fata tare da al'adunku" shiru tayi ba tace
komai ba, shan kunu sannan ta sauka daga kan dutsen ta sauke guiwowinta a qasa tana
roqonsa tace" don girman Allah ka rufamin asiri kabarni na koma bakin aiki
na"murmushi yyi yace" wannan ce kawai buqatarki?" ta daga masa kai alamar ehh,
yace" shikenan jeki saida safe" miqewa tayi da sauri tabar wurin tana qara dubawa
don tabbatar da cewa babu wanda ya ganta tare da prince nasaar, shi kuwa yana daga
zaune yana kallonta harta 6acewa hangensa, tana shiga 6angarensu taga su israt da
khulood sai zaman jiranta suke suci abinci, suna ganinta kuwa suka tarota da murna
suka tmbyta abunda ya sanya ta jima bata fada musu komai ba game da abunda ya faru
da ita, suna gama cin abinci israt ta kalli bimbii da murmushi a fuskarta
tace"albishirinki!" bimbii ta kalleta tace"goro" israt tace" babban prince ya
fitar da ranar za6en sabuwar baiwa dake kula da 6angarensa, nida khulood muna son
shiga gasar saidai bamu da chanchata sbd rukunin bayin da muke ciki basu shiga
za6en" murmushi bimbii tayi tace" tab, amma kuna da karfin hali waye ya aikeni
nikam bani so" khulood tace" wlh nima bawai don ina da sha'awar hkn nakeson shiga
ba saidai hkn shine nake ganin ze taimakamin wurin jeton lailah daga wannan hukunci
kinsan har an kaita kurkun qasa fa" bimbii tace" kamar ya kenan" khulood tace"
idan kina wannan matsayi zaki samu dama sosai wurin neman alfarma wurin babban
prince don shine na biyun sarki a wannan masarauta" shiru bimbii tayi sai kuma ta
dago da kanta tace" kuna ganin hkn bazai ta6a budurcinku ba" dariya sukayi gbdynsu,
israt tace" tab, ai nikam idan prince akbar ya buqaceni da gudu zan miqa wuya don
burina ya cika" bimbii sakin baki tayi kurum tana kallon israt da mamaki shimfide
kan fuskarta, khulood tace" kaf cikin bayin da suka ta6a kula da 6angaren prince
babu wacce ya ta6a nema duk kuwa wacce yau babban prince ya amshi budurcinta dole
ta burge kuma dole tayi alfahari dakanta don ta isa mace" bimbii kallon khulood
take da tsantsar mamakin kalamanta,gyara zama tayi tana fuskantarsu tace" toh ya
akayi kksan baya nemansu" murmushi sukayi israt tace"ai al'adar wannan masarauta
shine babban prince dakansa yake za6en baiwar da zata kula dashi duk wacce ta samu
nasara za'a sanar a wurin za6en amma matakin qarshe na za6en idan har prince ya
samu baiwar a matsayin disvirgin wato ba danyar budurwa ba toh hukunci mai tsauri
ze hau kan baiwar shiyasa duk wadanda suke shiga gasar sai sun yarda da kansu, abu
na gaba kuma idan ya sameki a cikakkiyar budurwa toh washegarin ranar baiwar zata
fito da zanin gadon daya 6aci zuwa babbar qorama ta wankesu dakanta cike da
alfahari, hkn shine shaidar dake nuni prince shine ya fara saninta diya mace kuma
zata cigaba da kasancewa a matsayin baiwarsa koda ya sake sabuwa kuma sarauniyya
zata mata kyautar girma sbd ta faranta ran d'anta ta bashi babbar kyauta,toh shi
prince akbar har yau duk bayin da yake za6e babu wacce ta taba fitowa da wannan
shaida balle sarauniyya tayi mata kyauta sannan ba'a ta6a samun wacce hukuncin
rashin budurci yahau kanta ba hkn na nuni da cewa prince akbar be ta6a kusantar ko
daya daga cikin bayinsa ba, kinji dalilinmu" ajiyar zuciya bimbii tayi tana
al'ajabin wannan al'ada tasu tamkar ta larabawan farko, khulood tace"idan kk
kasance baiwar prince kin tsira kenan don babu dan iskan dazai nemi keta miki haddi
kina matsayin baiwa ga prince akbar" shiru bimbii tayi tana tunani, tabbas idan
hkne gwara ta shiga gasar don tana tunanin abunda prince nasaar yace da ita yau,
wai zata zama kwarkwararsa, kallon khulood bimbii tayi tace" toh su kuma sauran
princes din fa suna kwatar budurcin bayin nasu" khulood tace" sukam kowacce baiwa
suka za6e washegari take fitowa wankin zanin gadon daya 6aci" shiru tayi sai kuma
ta dago da kanta tace"tabbas nima idan zan samu dama zan shiga gasar prince akbar
kodan lailah" rumgumeta sukayi suna dariya, saidai tunaninsu yanzu shine rashin
cancanta musamman bimbii da take ba balarabiyar usul ba shikansa wannan naqasu ne
gareta...........
No editing pls.

WANNAN PAGE SHINE QARSHEN FREE PAGE NA WANNAN LITTAFI MAI BUKATAR KASANCE DANI
CIKIN CIGABAN SAIKI TURO DA DARI UKUNKI#300 TA WANNAN ACCT..0100790419,ALHAJI
SHAHIDA NASIR,UNION BANK,SAIKI TURO DA SCREENSHRT NA PAYMENT DINKI TA WANNAN
LAYI...07041195806.....IDAN DA BUKATAR QARIN BAYANI GA LAYIN KIRA
NAN...08080611486....

Alkalamin Bintuu ne...


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

10

*Zinariyar mace mai ado da tagullah,jinjinar ban girma nk miki uwargida sarautar
mata, kece uwar gd kuma kece amarya a gdn Dr. usman bukar*......a jima anayi sai
uwar kissa mai ado da k'amshi dake nk......Hjy Hafsatu Usman Bukar��ina yinki irin
totally din nan, wannan page naki ne kiyi yadda kkso dashi🌺

*When I feel boring staring at you comfort me,when I feel hopeless your words give
hope,when I feel weak your smile give me strength*.......My luv to you is pure,pls
accept me dear💕

Washegari suka tashi kamar yadda suka saba kullum kowacce tayi 6angaren da aikinta
yake,6angaren lailah kuwa kai tsaye gdn hukunci aka wuce da ita inda alkali ya
zartas da hukuncin kisa akanta amma sai ta haife cikin dake cikinta tukun, kurkun
qasa suka kaita ta raini cikin nata a wurin, bimbii kullum tana cikin tunanin
lailah ta rasa hanyar da zata iyabi ta taimaketa daga wannan hukuncin na zalinci
amma kuma kalaman su khulood har yanzu suna yawo akanta wato idan ta kasance babbar
baiwa ga prince akbar zata iya samu alfarmar ku6utar da lailah kenan daga wannan
danyen hukunci, zama tayi bisa wani farin dutse tana tunanin hanyar daya dace tabi
wurin samun cancantar shiga wannan gasa kuma gashi ranar gabatar da za6en yana
kusantowa, miqewa tayi a hnkli ta dauki kwaryar data cika da nonon raqumi ta dora
akanta ta wuce dashi babban kitchen,ranar dukkaninsu sun kammala aikin nasu da wuri
suka dawo 6angarensu,israt ta zaunar da bimbii tana koya mata wasu baitoci cikin
wata waqar larabci, tace" tunda kince baki iya ko baiti daya daga cikin waqoqinmu
na larabci ba toh ki gwada wannan ko zata shiga da kalar rawarki" miqewa bimbii
tayi ta soma rera baitocin waqar tana yar rawa sai dariya suke gbdynsu, israt ta
miqe tace" ku tsaya ku ga yadda zanyi a gaban prince idan na samu shiga za6en nan"
sexy dance ta soma irin nasu na larabawa tana kada cikinta da kirjinta ita suke
kira raqas sharqi, dariya sosai suke mata bimbii tace" baki da dama israt kuma zaki
iya irin wannan rawar a gabansa baza kiji kunya ba" tace" wacce kunya idan har xe
za6en" khulood tace" amma fa bana bayin da suka shirya shiga wannan za6en suna
dayawa" tsaki israt tayi tace" haushi suke bani ai" khulood tace"kayy israt a
gaisheki da qoqari kice muma muna baki haushi kenan" dariya tayi tace" ku idan kune
ai kamar nice na samu amma sauran bayin suna samu suna matsawa zasu soma sha mn
qamshi dubi fa lenah yadda take yiwa su zainah kamar ba rukuni daya suke ba da"
murmushi bimbii tayi kawai tace" toh yanxu meye abunyi kunsan dai banda rukunin a
tsarin gasar" israt tace" satar jiki zamuyi kawai mu shiga" khulood tace" wacce
irin shawara ce wannan kina tunanin bazasu gane rukuninmu bane" israt tace" nidai
ranar tsinke wannan sarqar kafan zanyi na tafi wurin za6en" shiru bimbii tayi sai
tace" gsky dole su gane mu" khulood tace"kawai mu gwada yin hkn" bimbii tace" toh
Allah ya kaimu ranar" da wannan shawarar a zuciyoyinsu suka kwanta bacci kowacce
tana mafarkin ta samu nasara a wannan za6e........

Yau itace ranar wannan za6e, kyawawan yan matan bayin sun jeru sahu sahu kowacce
cikin sutura mai kyau a farfajiyar 6angaren prince akbar suna sauraron fitowarshi,
bayin dake kula da wannan gasa kuwa sai kai kawo suke a wurin, y'ay'an sarakunan
nan duk suna wurin sun hakimce, gimbiya hindu itama tayi ado sai walwali take da
daukar idanu tana daga gefe a zaune itama,kofar fitowa prince kawai suke kallo suna
tsammanin fitowarsa, ba jimawa kofar 6angaren nasa ta bud'e ya bayyana, sanye yake
cikin wata doguwar farar jallabiya da farin rawani ya dora irqa baqi a saman
rawanin sai baqar alkyabba, sajensa sai daukar ido yake sbd sheqi, gefensa ubaid ne
yake take masa baya sai kuma babbar baiwarsa wacce ze musanya wato lenah,fuskarta
babu annuri ko kadan sai hararar jerin yan matan take don ita tafi son kullum ta
kasance da babban prince tana masa hidima,tsayawa yyi yana qarewa jerin y'an matan
nan kallo, caraf idanunsa suka sauka kan bimbii dake ta faman rissinar dakanta
qasa,duk cikin yan mata ita kadai ce mara hasken fata sosai,dauke idanunsa yyi
akanta ya kalli ubaid yace" ku fara jarrabasu" batare da 6ata lkci ba aka soma
jarrabasu,farko baiwa kowacce abun girki akayi ta canki abinci da prince yafi so ta
girka ta kawo masa ya dandana, bimbii tana can baya don batason prince nasaar ya
ganta shiyasa take ta sunkuyar dakanta, bimbii bata iya irin girkinsu ba tayi tsuru
tsuru, kowacce sai aikinta take don ana tfy ne da lkci, ganin idanu yana zuwa kanta
ne yasa ta soma aikin nata cike da tunanin abunda ya kamata tayi, tashi tayi taje
ta tatso nonon raqumi ta dawa ta soma aiwatar da abunda ya kamata,chugui tayi na
nonon ragumin sannan tayi green tea irin wanda ta koya a wurin maheer, daya bayan
daya kowacce take miqewa taje gaban prince ta sunkuya ta riqe abunda ta girka shi
kuma ya dandana yaji, bimbii itace ta qarshe cikin sanyin jiki ta qaraso don ita
gani take kamar za'a mata dariya abunda ta girka, sunkuya tayi a gabansa ta riqe
dan qaramin plate din data saka chuguin da small mug na green tea, sai da yadan
dakata sbd ganinta da yyi mai duhun fata yana kyankyamin dandana abun nata sai kuma
jan dai ya dauki small spoon din dake faranta ya debi green tea din nata ya dandana
sau biyu yana dandanawa sannan ya dauki chugui kadan ya dora a saman le6ensa cike
da shakku, kallon ubaid yyi tuni ya fahimci abunda yake nufi, ubaid ya kalli bimbii
yace" prince yana son sanin da mene kk had'a wannan abun"ya nuna mata chugui din
dake saman plate din hannunta, dago da idanunta tayi tace" da nonon raqumi na hada"
komar da ita wurin nata akayi ta kuma hada chuguin yadda ta hada na farko, hk dai
aka cigaba da jarrabawar har akazo fagen rawa shima bimbii ta birge kowa don komai
nata fita yake daban,komai irin na al'adarta take hkn shine ya dauki hnkli kowa da
prince shi kansa, prince nasaar dake gefe kuwa wani irin bala'in haushi yakeji, be
ta6a tunanin zata iya shiga gasan nan ba, sauran yan matan dake wurin suma mugun
haushin bimbii suka soma ji tun kafin a bayyana sakamako, gani sukayi komai nata ya
dauki hnklin prince akbar saidai kafin a fadi sakamako rahoto ya shigo musu cewa
bimbii tana cikin rukunin bayi ne na farko kuma suna da shakkun asalinta, prince
yace" duk da hk su saki sakamakon a gaban kowa" batare da 6ata lkci ba aka bayyana
bimbii a matsayin wacce ta lashe wannan za6e don prince ya yaba da salon dandanon
abunda ta hada da kuma yanayin rawarta,israt wani irin tsalle tayi ta qanqame
bimbii cike da farin ciki don sukam riqima ce kawai ta kawo su basu ta6a zato daya
daga cikinsu zata samu nasara ba, musamman ma bimbii da take jinsin baqar
fata,bimbii kuwa ta kasa dago idanunta sbd fuskoki daya aika mata da harara suke
cike da hassada wasu kuma zallar qiyayyace kawai irinsu gimbiya hindu da ba shiri
tabar wurin cike da mamaki babban prince fal ranta tayaya ze karye dokar gdn nan ya
za6i baiwa mara cikakken asali kuma wani abun takaicin ma gata baqar fata a tarihin
masarautar babu dan sarkin daya ta6a za6en baqar fata a matsayin babbar baiwa don
yawancinsu basu da asali don ba jinin larabawa bane, bimbii kuwa saida aka gama
za6en kafin aka gane rukuninsu amma tunda prince ya riga ya za6eta a matsayin
babbar baiwa ta wuce wurin, 6angaren ummul shukri kuwa abun ya bata mata rai sosai
na wannan za6en da prince yyi taya ze za6i babbar baiwarsa daga qasqantattun bayi
rukunin farko wannan ai tamkar zub da qimar gdn ne, za6en bimbii a matsayin babbar
baiwa ya kawo gutsiri tsoma sosai a wannan masarauta wanda hkn yakai kunne
sarauniyya mar'atuusaliha ta kira ummul shukri don jin yadda akayi rukunin bayi na
farko suka shiga za6en shiru ummul shukri tayi don tabbas tasan laifin kowa ze gani
don su bimbii a qarqashin kulawarta suke itace tun farko tayi sake, ranar ummul
shukri tasha fada a wurin sarauniya mar'atussaliha har takai da an dakatar da ita
daga matsayinta na wasu kwanaki, hargitsi aka samu sosai cikin wannan gdn don mafi
yawan jama'ar gdn na ganin rashin cancantar bimbii a wannan matsayi, 6angaren
prince kuwa ko a jiknsa don halinsa kusan daya da mahaifinsa sarki Abdallah bin
jabal akwai taurin kai da kafiya musamman akan abunda suka aminta akansa, babu
wanda ya isa ya sanyashi sauyawa baiwa tunda har ya riga ya za6a, ummu sumayya ita
ta wuce da bimbii wurin gyara aka gyarata kamar yadda ake yiwa duk baiwar data samu
nasarar samun wannan matsayi, wani tamkamemen daki aka kaita a matsayin dakin
kwananta sannan ummu sumayya ta soma sanar da bimbii abunda prince yakeso da kuma
wanda baya so don mugunta sai tace mata prince baya son qamshi kuma yana son mace
ta din ga yawan sanya baqaqen kaya, Allah sarki bimbii duk ta dauka hkne tace"toh"
daren ranar bimbii zata soma ziyartar fadar prince,bimbii cike take da tsantsar
fargaba da faduwar gaba sosai harta soma dana sanin shiga wannan gasar, maqiya da
mahassada kuwa kawai jiran wayewar gari suke su ga ko bimbii zata fito wankin
budurci bakin qorama.....

Littafin na kudi ne ki siya ki karanta cikin yanci ba satar fage ba, idan kin
shirya siya ga trasaction detail nan, zaki tura #300 ta wannan
acct..0100790419,alhaji shahida nasir,union bank,saiki turomin da screesht na
payment ta whatsapp through wannan layi...07041195806, idan da neman qarin bayani
ga layin kira nan..08080611486......

Alkalamin Bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

11

*In the middle of the night when the stars scattered at the sky the moon become
shiny I keep thinking at you*.......Your voice are the sweetest thing I ever.......
Dare yyi sosai amma gdn akwai yalwar fitilu ta ko'ina suna haske kowacce kusurwa ko
allura ce ta radio take za'a ganota sbd wadataccen haske daidai lkcin bimbii ta
fito sanye da wata doguwar riga bak'a qirin hkm mayafin rigar tfy take a wani dogon
corridor hannunta dauke da wani faranti na azurfa da qananan kofina da kuma wani
jug mai kyan gaske a tsakiya, green tea ne aciki kuma wannan dogon corridorn shine
zai sadata da babbar k'ofar inda prince akbar yake wato sashinsa,jikinta rawa yake
sosai don duk a tsorace take sbd batasan meze faru ba, tana qarasowa bayin dake
tsaron kofar suka bata hanya,kofar ta bude da kanta ita kuma ta danna kanta ciki
kanta a sunkuye tamkar wata munafika, tana sanya kafafunta ciki wani sassayan
qamshi tare da sanyi yyi mata maraba, qasan wurin tamkar glass yake sai daukar
idanu yake da kyalli, dakin qaton gaske ne kuma kusurwa kusurwa yake,kowacce
kusurwa tana da kofa kamar ta masallaci an kame wurin da curtains na alfarma ga
kuma shimfida na manyan royal center carpets masu ado, curtains din da aka kame
kowacce kusurwa zaka gansu sharara,komai na cikin wurin abun kallo ne, 6angare guda
kuma wasu kujeru ne irin royal chairs din nan kalar golden, kusurwar tsakiya
idanunta suka kalla inda ta gano kusurwar tafi kowacce girma an kameta da wani
qasaitaccen curtains shara shara milk colour, wani gado ta gano a cikinta tafkeke
yasha bedshit na wawayen kudade shima bedshit din milk colour, bimbii tsayawa tayi
kalle kalle tamkar yar qauye cikin ranta tana mamaki wai nan duk wurin kwanan mutum
guda ne, tunda ta shigo yana zaune a wata kujera yana karanta wani littafi na
tarihi ko dago da kansa beyi ba sai yanzu, ita kuma sai lkcin idanunta suka sauka a
6angaren da yake take taji wata faduwar gaba ta tsaya qam a inda take batare data
qaraso ciki ba, miqewa yyi ya soma takowa a hnkli har ya qaraso inda take fuskarsa
babu yabo babu fallasa kamar dai yadda yake kullum, tsayawa yyi yana qarewa
shigarta kallo ya tsayar da kwayar idanunta akan fuskarta ita kuwa sai tayi saurin
yin qasa da guiwowinta a gabansa, bata ta6a tsammanin zeyi magana ba taji muryarsa
cikin tsadadden larabcinsa yace" kije ki sauya wannan kayan dake jikinki" abunda ya
fada mata kenan ya juya cike da takun qasaita ya koma inda yake zaune ya cigaba da
abunda yake, ita kuwa bimbii miqewa tayi da sauri ta juya da niyyar ficewa daga
dakin har tana hard'ewa ta rasa dalilinsa nacewa taje ta sauya kayan jikinta sai ta
soma wani tunani nata na daba take hnklinta ya qara tashi cikin ya duri ruwa hk ta
koma dakin da take, tana ta cika da mamakin ganin su israt da suka sato jiki suka
zo wurinta suka tarar bata nan suka bararraje a saman gadonta suna baccinsu, motsin
shigowarta ne da farkar dasu suka tashi suna binta da kallon mamaki, khulood tace"
bimbii daga ina kk badai daga 6angaren prince kk ba cikin wannan kayan" kallon
kanta tayi ta dago ta kallesu tace" me kayan yyi" israt ta sakko daga saman gado ta
iso gabanta tace" waye ya fada miki prince yana son baqin abu komai nashi fari ne
shiyasa bayinsa basu sanya duk abunda ya danganci baqi" shiru bimbii tayi sai lkcin
ta gano manufarsa ta kuma fahimci mugunta ummu sumayya taso mata tace ta sanya
baqin kaya, zama tayi a bakin gado ta zabga tagumi, israt ta sanya hannu ta cire
mata tagumin da tayi tace" mene ya faru yar uwa" murmushi tayi tace" wlh nikam
tsoro nk gbdy nayi dana sanin shiga wannan za6en" israt tace" me kkce? sake fada
naji, yanzu bimbii baqin ciki kk mana don gashi dai silar cin za6en nan da kkyi har
muma mun samu arzikin shigowa wannan wuri har da kwana akan gado mai taushi shine
kk cewa kina dana sani, toh meye abun dana sani anan" kwantar dakanta tayi ta
kafadar israt, khulood ta matso ta zauna kusa dasu ta dafa bimbii tace" tashi ki
cire wannan kayan dake jikinki ki shirya cikin masu jan hnkli" harararta bimbii
tayi suka bushe mata da dariya, hk suka sake shirya cikin wata milk colour din
doguwar riga mai cike da kwalliya sannan israt ta mata 6arin turare har sai da
tace" israt wlh ya isa hk" sannan suka qara taje mata gashi suka tufkeshi da wani
band shima milk colour, suka sanya mata wani mai kyalli a le6en bakinta, le6en ya
soma shiny, suna cikin shiryata lenah ita da wasu bayi su hudu suka bankado kofar
dakin suka shigo ta soma binsu da wani matsiyacin kallo sai ta bushe da dariya suma
sauran dake biye da ita suka bushe da dariya, tace" idan kun sauya mata baqin kaya
ai baku isa ku sauya mata kalar fatar jikinta ba koh" israt tana shirin maida musu
da martani bimbii ta riqeta, matsowa lenah tayi kusa da bimbii tana mata wani
kallon wulaqanci tace" basu sanar dake babban prince bashi son baqin abu bane toh
bawai baqin kaya ne kawai baya so ba har ma da baqar fata" khulood tazo iya wuya ta
kallesu itama a wulaqance tace" dadin abun dai shiya za6eta kuma cikin gayyar
fararen fatan yace ita ta dace ta hidimta masa wannan kadai abun alfahari ne" israt
tace" idan ma ba naci da neman fada na wasu matan ba yace ya dena yayinki toh meye
kuma na farkar jeji hk" kalaman nasu sun fusata lenah sosai amma sai ta dake tayi
wani murmushin yaqe tace" toh muna nan muna jira muga ko iskar tusa zata hure wuta"
dariya sauran bayin dake biye da ita sukayi suka juya suka fice abinsu,bimbii tayi
tsuru tsuru da ita saida su khulood suka din ga binta da kalamai na qara qarfin
guiwa,khulood tace" karki mance lailah tana nan tana jiran gudummawar mu gareta
komai rintsi kiyi mn alqawarin ba zaki gjy ba" tashi tayi ta rumgumesu gbdy sannan
suka mata rakiya har kofa ta fice ta doshi komawar 6angaren babban prince, tana
shiga ta tarar dashi sanye da wasu kayan bacci farare qal, gashi kansa ya sauko
masa har kafada yana zaune a wata kujera ta alfarma yana hada wasu takardu,
shigowar ta ne yasa shi dago dakansa yana kallonta sannan ya dauke kansa ya cigaba
da abunda yake, rasa abunyi tayi sai ta koma gefe ta sunkuya akan guiwowinta tana
jiran umarninsa, kallonta yyi yace" wannan abun da kk kawo ni kkson na zuba
dakaina" mgn yake yana abunda yake batare daya kalleta ba, tashi tayi da sauri ta
matso wurin ta dauki qaramin jug din ta tsiyaya masa green tea din data kawo a daya
daga cikin qananan cups din dake saman farantin ta rissinar dakanta tare da sanya
hannu biyu ta miqa masa cup din, kallonta yyi sannan ya miqa hannunsa fari tas
dashi ga yalwar gashi zarara ya amshi cup din daga hannunta ya komar dakansa ya
kwantar jikin kujerar dayake yana sipping green tea din a hnkli tamkar bayason ya
qare ita kanta na sunkuye cike da kunya irinta ta fulanin usul sbd ita tunda take
bata ta6a ke6ewa da wani namiji irin hk ba, shiko prince akbar dayake mutum ne
ma'abocin karantar yanayin jama'a yana biye da duk wani action dinta, sai jin
muryarsa tayi yace"kinsan a tsari na hidimta mini zaki iya kwana dani da biyamin
buqata koh, to meyesa kk shiga za6en duk da kinsan da hk ko kuma kin shiryawa
hknne" tayi mutuk'ar mamakin jin wadannan kalmomi daga bakinsa, wani qasaitaccen
murmushi yyi hkn ya kuma dulmiyata cikin tsagwaron ruwan mamakin wannan dan sarki
da ta6a zaton yana mgn mai tsawo hk ba kuma kalmomin nasa sun sanya zuciyarta
tsananin bugawa tana tsoron kar fa mai afkuwa ta afku akanta idan kuwa hk ta faru
lamido bazai ta6a yafe mata ba har abada koda ta samu damar komawa gd, sai juyawa
tayi bata ganshi a wurin ba dayake tana waiwaya ta gano shi saman royal bed nasa ya
kwance ya saki curtains dinshi, alama ya mata data zo, wayyo Allah abunda ta furta
kenan cikin zuciyarta dake tseren sukuwa sbd tsantsar bugawar da take, jiki a
sanyaye ta nufi kusurwar da gadon nasa yake ta same shi kwance ya juya mata baya
wannan alama ce dake nuni da prince din yana buqatar tausa, hk tahau gadon nasa
cike da tsoro ta miqa hannunta dake rawa sosai ta dora a jikinsa dake fitar da wani
tsadadden qamshi na musamman ta soma masa tausan cikin sanyin jiki, shi kuwa
idanunsa a rufe suke tamkar besan me take ba hk ta cigaba da tausa a wannan jikin
dan sarkin mai mutukar taushi da silbi tamkar jikin aljanu, tunda yaji bacci ya
soma ziyartarsa yyi mata nuni data fice yana son bacci, take wani dadi ya ziyarci
zuciyarta ta saukar da kafafunta qasa a hnkli ta fice da wurin ta sake masa
curtainsa ta rage masa haske kamar yadda aka sanar da ita ta fice a millions tayi
hanyar 6angaren da dakinta yake, tana shiga ta tarar dasu israt da khulood har
sunyi nisa a bacci itama, rage kayan jikinta tayi ta nemi gefensu itama ta kwanta
abinta take itama bacci yyi gaba da ita, khulood ce ta fara farkawa da asuba ta
ganta kwance, israt ma ta tashi duk suna kallonta, baqin ciki ne ya cika
zuciyoyinsu sbd ba hk suka so ba wato itama bimbii prince be amshi budurcinta ba
kenan, kawai abunda suka qara yarda dashi a lkcin shine prince akbar yana tinqaho
cikakkiyar izza mai k'arfi da take hanashi kusantar kowacce baiwa wato yana
kyankyamin hada kyakykyawan jikinsa da bayi hkn suka aminta dashi, bimbii kuwa da
farin ciki ta tashi tana musu albishir da Allah itama ya tsallakar da ita ta fito
da budurcinta, harararta israt tayi tace" ke har wani murna kkyi sbd kin fito da
budurcinki toh mu ba hk muka so ba" bimbii ta kalli israt tace" so kk daya keta min
haddin budurci" khulood tace" tabbas da hk ta faru da mahassada da maqiya sun ji
kunya saidai baqin ciki ya kashesu" dariya bimbii tayi ta miqe tace" wlh gwara da
hkn bata faru ba don kuwa daga da hk ya faru lkcin ni kuma wata baqin ciki na zai
soma" gbdy kalaman bimbii sun basu mamaki kawai kallonta suke cike da al'ajabi amma
sai sukayi shiru, khulood ta kalli israt tace" ki tashi mu koma 6angarenmu kafin
ummul shukri ta fahimci ba anan muka kwana ba" saurin miqewa sukayi bimbii ta
rakasu har kofar shiga 6angaren nasu sannan ta dawo, baiwar gimbiya hindu zulham
kuwa daman a 6angaren ta kwana don daukar rahoto aikuwa tun fitowar bimbii cikin
dare daga 6angaren prince akan idanunta har fitowar da sukayi yanzu,murmushi tayi
kawai wuce sum sum don isar da saqonnin ga gimbiya hindu, gari na wayewa kuwa bayi
suka
soma rige rigen fitowa bakin qorama suna jiran ganin bimbii ta fito wankin
budurci, ita kuwa bimbii da wannan safiya ta shiga kitchen din da ake shiryawa
prince abinci, bayin dake aiki a kitchen duk suka bita da kallon raini don
haushinta sukeji, gaishe tayi fuskarta a sake amma cikinsu babu wacce ta amsa sai
aikinsu suke, itama bata kuma tanka musu ba ta wuce cikin kitchen ta hada ruwan
inibi ta sanya zuma ta dauko wani jug tamkar na zinare ta zuba ciki ta sanya
qananan kofuna, duk suna kallon abunda take, bushewa sukayi da dariya, dayan da ake
kira zulja ta kalli bimbii tace" yadda kk da duhun fata hk tunaninki yake mai kk
dauki babban prince da zaki hada masa wannan shirmen ki kai masa hala baki iya
girki bane" bimbii batace musu komai ba ta dauki faratin da jug da kofunan yake ta
fice ta nufi 6angaren prince akbar, bata ganshi a ciki ba don hk ta qara gyara
komai na 6angaren ta kuma sanya qamshi ta ko'ina ta gyara gadon nasa ta goge ko'ina
don ummu sumayya ta fada mata aikin babbar baiwa mai hidima ga prince tana shirin
fita ya shigo tare da hadiminsa ubaid, sunkuya tayi ta rissinar dakanta alamar
gaisuwa, batare daya kalleta ba ya zauna abinshi ubaid na tsaye a bayansa, tana nan
kan guiwowinta bata miqe shi kuwa yama mance da ita a wurin yana nunawa ubaid wasu
maps, daga qarshe ya bawa ubaid maps din da batasan ko na meye ya fice dashi, sai
lkcin ya kalli 6angaren da take durqushe ya kalli kuma abunda ta ajiye masa, itama
sai lkcin ta tuna aikinta ta miqe da hanzari ta qarasa wurin nashi ta soma tsiyaya
masa ruwan inibin a kofi, kallon ya kumayi ya kalli abunda take zuba masa yace"
meye wannan?" ya nuna mata ruwan inibin da take tsiyaya masa cike da girmamawa ta
sanar dashi ruwan inibi ne, yace" abunda kk iya kenan da safe" bata gane nufinsa ba
tace" yana qara lfyr zuciya da faranta safiya ranka ya dade" shiru yyi be kuma mgn
ba ta miqa masa ruwan inibin ya sanya hannu ya amsa ya ajiye a saman farantin, nuna
mata yyi ta dauka ta fita dashi, shiru tayi kamar zatayi kuma hk ta dauka ta fita
dashi ta koma kitchen, bayin dake kitchen din kuwa dariya suka soma mata har da
tafa hannu,zulja tace" yanzu dai kinsan waye prince koh" fita tayi daga kitchen din
don batasan me zata girka masa ba idan dai ba irin cimmarta ta rugarsu,idan kuwa
tayi wannan ganganci tasan ba abune mai dadi ze biyo baya ba,kafin komai zancen
rashin fitowarta wankin budurci ya karade ko'ina, wannan abu yasa sunan bimbii ya
kuma fitowa cikin bayi kowa yasanta, dayawa abu yyi musu dadi musamman nasaar da
shima ya sanya yar leqen asiri kuma ta kawo masa kyakykyawan labari daya sanya shi
farin ciki,itama gimbiya hindu tayi dariya sosai ranta qal don hk prince akbar yake
birgeta, sarauniya kuwa murmushi kawai tayi don tafi kowa sanin halin danta,ita
kuwa bimbii sai yanzu take fahimtar yadda suka dauki za6en nata bada wasa ba sbd
rashin qaunarsu ga baqar fata.......

Littafin nan na kudi ne idan kin shirya siye ga yadda zaki nan, zaki tura dari uku
#300 ta wannan acct..0100790419,alhaji shahida nasir,union bank,saiki turomin da
screesht na paymenta naki ta wannan layi kamar hk,07041195806, idan da buqatar
qarin bayani ga layin kira..08080611486...
Alkalamin Bintuu ne....
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

12

*I'm waiting for you*.....

Da yamma ummu sumayya ta same bimbii ta qara karanta mata tsarin hidimarta ga
babban prince, yau da dare ta fito sanye cikin wata doguwar riga kalar sararin
samaniyya ta hada masa ginger tea ta sanya cikin qayatattun mazubi ta dauka ta nufi
6angaren nasa,zaune yake bisa wata kujera ya kwantar dakansa a jikin kujerar
idanunsa a lumshe motsin shigowarta ne yasa ya bud'e idanunsa yana kallonta har ta
qaraso wurin dayake ta ajiya abunda ke hannunta, sunkuyawa tayi ta soma tsiyaya
masa ginger tea din sannan ta dago da kanta dauke da qaramin cup din tana miqa masa
cike da alamun girmamawa, amsar cup din yyi ya ajiye sannan ya kalleta yace" ki
koma ki qara sanin abunda nkso a wannan lkci" shiru tayi tana tunanin abunda ummu
sumyya ta sanar da ita prince yake daidai wannan lkcin, kallon wata k'ofa tayi da
sauri ta nufi kofar ta shiga, bece mata uffan ba ya cigaba duba wani littafi,ita
kuwa bimbii tana shiga kofar taga qaton bathroom ne, cikin bathroom din ma akwai
wata kusurwa da aka kame gefe gefenta da wasu shara sharan curtains farare sol,
tsakiya kusurwar wani qaton kwarmin wanka ne, turarukan wanka ta gani ta ko'ina an
jerasu ga fararen towels din wanka 2kala duk an ratayesu, kwarmin wankan ta cika
dam da ruwan wanka sai turiri yake ta sanya turarukan wanka a ruwan da sauran
sinadaran wanka don duk an koyar da ita yadda ake amfani dasu,tana gama hada komai
ta fito ta tarar dashi sanye da wata rigar wanka fara sol yana jiran fitowarta,
bude masa kofar bathroom din tayi ya shiga ciki ta rufe kofar ta koma ta tsaya tana
jira, ba'a jima ba taji qarar qararrawa alamar dake sanar da ita prince yana
buqatarta cikin bathroom, bud'e kofar bathroom din tayi ta shiga, yana cikin
kwarmin wankan amma saman ruwan wankan duk kumfa ne iyakar kafadarsa kawai ake gani
ya kwantar dakansa a wani qaramin matashi idanunsa a lumshe,qarasawa tayi wurin ta
tsaya daidai saman kansa ta sanya hannu ta soma masa tausa a kafadunsa tana daddana
masa jikinsa shi kuma idanunsa a lumshe yake yana jin dadin tausan, san can ya daga
mata hannu alamar tausan ya isa, wucewa tayi ta nufi wani wuri ta dauko wasu
sinadarai ta dawo wurin ta sunkuya ta soma wanke masa gashin kansa tana taje masa a
hnkli sannan ta janyo wani qarami towel tana tsane masa gashin dashi shi kuwa yana
riqe da qaramin cup na ginger tea dinsa yana sipping a hnkli, tana gamawa ya miqa
mata qaramin cup din dake hannunsa ta juya ta fice daga dakin wanka ta koma kofa
tana jiran fitowarsa, ta dade tsaye a wurin sannan taji qarar alarm tayi saurin
bude dakin wankan ta shiga ta ganosa har ya gama wankan yana zaune a wata kujera
dake kallon wani qaton madubi, wurin itama taje ta dauki comb ta soma taje masa
gashin kan nasa sannan ta shafe gashin da mayuka gashin ya soma kyalli da sheqi, a
hnkli kuma ta fara murza masa body cream a fatar jikinsa dake da yalwar gashi
zarara ta ko'ina, shi kuwa yana kallonta ta jikin madubin, itakam ba madubin take
kallo ba aikinta kawai take,tana kammalawa ta rissinar da kanta sannan ta juya ta
fice tana sauraren fitowarsa, ba jimawa ya fito sanye da wasu kayan bacci farare
masu taushi har da takalminsu sai qamshi yake mai jan hnkli, wajen wani qaramin
stool ya nufa ya zauna a kujerar dake gaban stool din, matsawa tayi kusa dashi
itama tana jiran umarninsa, ranar prince ya jima be kwanta ba yana karatunsa ita
kuma tana zaune a gefensa, itako bimbii bacci ne fal idanunta batasan lkcin data
soma gyangyadi ba, juyowa yyi yana kallonta kawai shidai tunda yake ganin bayi be
ta6a ganin irin bimbii ba, motsinsa ne ya farkar da ita tayi zumbur ta miqe ta
mutstsike idanunta tana satar kallonsa, tashi yyi ya tafi ya kwanta bisa royal bed
nasa ya rufe idanunsa, bimbii kallonsa tayi ta turo baki gaba cikin zuciyarta tace
hmm, Allah dai ya kyauta, bimbii tun tana tsammanin ze bata umarnin tfy har ta
saduda don taga kamar bacci ma yake, can dai ta miqe a hnkli ta nufi kofar fita da
niyyar ficewa taje ta kwanta, kofar taqi budewa, dawowa tayi wurin da take ta zauna
cike da haushi, prince kuwa duk abunda take yana jinta amma idanunsa a rufe suke,
ranar kwanan zaune tayi, washegari tun kafin ya tashi ta tashi nan ma bata isa ta
fita ba har sai ta jira farkawarsa, tun kafin ya tashi ta soma goge goge ta qara
qamshin dakin ta gyagygyara curtains din kowacce kusurwa, tunkan ya tashi saidai
yana kwance be miqe ba kuma idanunsa suna rufe ita kuma sai tayi tsammanin be tashi
bane, tana gama gyara wani curtains ta juyo sai kawai ganinsa tayi a zaune a bakin
gadonsa ya dafe kansa da hannunsa, tahowa tayi ta sunkuya kusa dashi, dago da
lumsassun idanunsa yyi ya kallonta ya qureta da idanu da idanu har saida ta tsargu
tayi qasa dakanta, kasa dago dakanta tayi amma jikinta yana bata har yanzu ita yake
kallo,nuna mata dakin wanka yyi yace" kije kiyi wanka" hk kawai yace da ita a
taqaice yyi mgnr, bimbii miqewa tayi ta shige dakin wankan ranta a dagule don ba hk
taso ba, tana shiga ta cire mayafin dake kanta ta soma taje dogon suman kanta
sannan ta tayi wankan a gurguje, tsane jikinta tayi da wani towel sannan ta dauko
kayan data cire ta maida jikinta ta fito ta sameshi a inda tabarshi, kallon daya ya
mata yace"kije ki cire wannan kayan dake jikinki" wucewa tayi sum sum ta nufi kofar
fita da niyyar ta fita taje dakinta ta sauya kayan, kofar taqi budewa, dawowa tayi
ta sunkuya a gabansa tace" kofar taqi budewa" bece mata uffan ba bare tasa ran ze
bata amsa ya miqe yabarta a wurin, abubuwan dake gabansa ya cigaba dayi batare daya
kuma kallon 6angaren da take ba saida ya gama sannan ya juyo ya kalleta ya nuna
mata wata kusurwa da hannu sannan ya juya ya shige wani wuri, kusurwar daya nuna
mata ta shiga ta tarar da gbdy dakin kayan mata ne 2kala masu tsada da kyawun
gaske, wata ash colour ta dauka ta sanya ta mata kyau sosa ita kanta sai qarewa
kanta kallo take a jikin madubi, cikin ranta tace oh bimbii ashe zaki ganu hk, yana
zaune ta fito sanye da wannan rigar kallonta yyi na wasu daqiqai sannan ya kawar
dakansa, ranar yini tayi a 6angaren prince tana masa hidima batare da gjy ba, sai
yamma ta fito da wasu barguna ta tafi bakin qorama wankesu, tana zuwa wurin ta hadu
dasu khulood suka taho da gudu suka rumgumeta tana qarema suturar dake jikinta
kallo, tana gama nata wankin ta shanya ta tayasu nasu don yana dayawa suka shanya,
kamar ance ta waiga ta hango prince nasaar jikin bishiyar daya saba tsayawa ya zuba
mata idanu hannunsa dukka a kirjinsa, sauri tayi ta dauke kanta tayi kamar bata
ganshi ba, sun hada idanu kuma yasan sarai ta ganshi, saurin miqewa tayi zata
tafi,israt ta riqo hannunta tace" ki jiramu" bimbii kuwa sauri take tabar wurin
batasan su fahimci alaqar dake tsakaninta da prince nasaar amma hk ta fasa ta koma
ta zauna bata kuma kallon inda yake ba, takowa yyi a hnkli ya qaraso inda suke, sai
lkcin su israt suka ganshi sukayi saurin duqawa kan guiwowinsu tare da rissinar
dakansu, shikam idanunsa nakan bimbii data tsuke fuska tamau,sukansu su israt
mamakinta sukayi, murmushi prince nasaar yyi yace" nazo ne ina son kiyimin rakiya
wani wuri" kallonshi tayi tace"wani aiki nake yanzu" yace" ki ajiye ki biyoni" be
kuma cewa komai ba yyi gaba yabarsu a wurin, khulood ta kalli bimbii yace" daman
prince nasaar ya sanki ne" israt tayi zagal tace" ba dole yasanta ba tana matsayin
babbar baiwar prince akbar" khulood tace" hkne kuma fa" kallonsu tayi tace"ku
jirani ina zuwa" bayan prince nasaar tabi suka nufi wani wuri nesa da farfajiyar
gdn sarautan kusa da lambun prince akbar, kallonta yyi yace" don nace zaki zama
kwarkwarata shine kk shiga za6en babbar baiwa ga prince akbar" shiru tayi kawai ya
soma janta da zance har lkci yaja sosai ta kalli rana taga ta kusa faduwa ta
kalleshi tace" kayi hkr lkcin aikina yyi" shiru yyi amma cikin zuciyarsa fal da
kishi, yace" zaki iya tfy" juyawa tayi kamar zataji tuntu6e ta wuce cikin gdn,
dakinta ta shige ta shirya tsaf ta wuce kitchen ta gyara kayan marmari ta sanya
cikin qayatattun mazubi ta dauka ta wuce 6angaren prince dashi, bata same shi a
ciki ba ta ajiya ta juya zata fita ya fito sanye da fararen kaya tas, binta yyi da
kallo ita kuma tayi saurin yin qasa dakanta, qarasowa wurin nata yyi sosai ya
kusanto ta ita dai tsaye take qam tana kallonsa,muryarsa taji yace" daga ina kk
fito" tace" daga dakin da nk" tsakiyar idanunta yake kallo, ita bimbii ta rasa
dalilin wannan kallo na babban prince, wuceta yyi ya koma ya zauna a wata kujera ta
gabatar masa da kayan marmarin kadan yaci ya daga mata hannu,nuna mata kan bed nasa
yyi yace taje ta jira a wurin, bimbii bata kawo komai ba taje tahau kan gadon tana
jiransa, saida ya gama duk wani abunda zeyi shima ya nufi gadon ya hau yayi matashi
da cinyarta yace" ki sanyani bacci" gaban bimbii ya soma bugawa kawai kallon prince
akbar take daya dora kansa a jikinta, jikin rawa yake sosai ta kasa aiwatar da
komai, shi kuma idanunsa na rufe yana sauraron ta sanyashi bacci...........

Littafin nan na kudi ne idan kina da buqatar siye ga yadda zakiyi, zaki tura #300
kacal ta wannan acct..0100790419,alhaji shahida nasir,saiki turon da screesht ta
wannan layin na whatsapp.....07041195806.....idan da buqatar kira ga layin kira
nan...08080611486

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

13

*You black cutie skin is the glowing skin I ever seen dear*.........soft and
shiny......💕

Hannunta takai zata d'ora akan sumarsa sai kuma ta janye hannun da sauri,shiru tayi
tana tunani wata zuciyar ta qara jaddada mata matsayinta ba kowa ita face baiwa mai
hidima ga wannan d'an sarki bata da y'anci masa gardama, cikin dokokin da ummu
sumayya ta sanar da ita shine komai prince yakeso dole ta masa a matsayinta na
baiwarsa, ba shiri ta komar da hannunta saman sumarsa ta cusa hannunta ciki tana
barbaza masa gashin cikin yanayi na kwantar da hnkli, shidai prince idanunsa na
rufe ya amsar saqonninta, cikin sanyin murya ta soma bashi labari na qasashen
africa tare da yanayin al'adunmu, abunda yasa ta za6i hk sbd tana yawan ganinshi
yana karanta littattafan tarihi wato mutum ne ma'abocin son tarihi, tana ta bashi
labari yana jinta duk da idanunsa a rufe suke, gani tayi kamar yyi bacci ta gyara
zaman lumtsatstsen pillownsa ta sauke kansa a hnkli daga jikinta ta mayar dashi kan
pillown sannan ta fara yunqurin sauka daga kan gadon, caraff, taji ya riqo hannunta
batare daya bude idanun nasa ba yace" ina zakije,ki taho ki cigaba da bani labari"
dawowa tayi ta kuma zama tana ta bashi labarin bata kuma yunqurin guduwa ba, shi
mamakin bimbii yake cikin ransa sbd duk bayin da yake yayi kowacce saita sanya duk
wata hikima da dabararta na ganin ta jawo hnklinsa kanta ya kusanceta, itako bimbii
yana karantarta bata ta6a gwada wannan hikimar ba kuma ba wata alama dake nuna
bimbii tana da feeling akansa, dalilin dayasa duk ahekara yake sauya baiwa shine
yawancin bayin nasa basa iyawa dole sai sun afka soyayyarsa har su fara nuna masa
feeling dinsu a bayyane batare da sukansu sun ankara ba, shi kuma yana ganin hk
yake sauyasu sbd yana guje musu fadawa tarkon mahaifinsa sarki abdallah bin jabal
don baya daukan irin hk da wasa, idan har abu ya bayyana baiwa ta fara soyayya da
jinin sarauta a wannan masarauta toh fa tsatstsauran hukunci ne yake hawa kanta
batare ko digon tausayi ba, duk bayin da prince akbar yake sauyawa toh soyayyarsu
suka fara nuna masa a bayyane shi kuma yake jiye musu wannan hukunci sai ya sauyasu
kafin su zurfafa har abu ya fito fili, duk cikin masarautan babu wanda yasan wannan
dalili nasa, bimbii kuwa be ta6a ganin alamun hk daga gareta ba duk da hk dai yana
ganin kamar zuwa gaba itama zata bi sawun afkawa kogin sonshi,bimbii kam sai labaru
take bashi amma yyi shiru bece ya isa ba, tun tana daure bacci dayake kawo mata
farmaki har ta soma gyangyadi, shikam beyi bacci ba idanunsa ne kawai a lumshe, jin
tayi shiru ne ya bude idanunsa sai ganinta yyi ta jingina bayanta da jikin gadon
nasa sai baccinta take, fuskarta ya qurawa idanu sai lkcin ya gano tsantsar kyawun
halitta irin na bimbii, tashi yyi zaune ya cire mata mayafin data rufe kanta dashi
sbd taji dadin bacci, abunda ta tufke tulin gashin kanta ya cire gashin ya sauka
mata a gadon baya, gyara mata kwanciya yyi ya kwanta da ita a gefensa sannan yaja
musu bargo, bimbii kuwa duk wannan abu batasan ya faru ba kawai baccinta take hnkli
kwance, haba ku kuwa ba dole bimbii ta lula duniyar bacci ba yadda ta samu kwanciya
a wannan gadon na alfarma mai shegen taushi ga bargo duniyar kule gashi duk ta inda
ta juya qasautaccen qamshi take shaqa mai cire damuwa da kwantar da hnkli,shikam
yana kwance ne wuri guda yana kallon sama ya dora hannayensa akan cikinsa ita kuwa
bimbii sai wani birgima take da gyara kwanciya har ta matsa kusa dashi sosai bata
sani ba, kallonta kawai yyi ya dauke kansa, bimbii tana farkawa ta tsinci kanta a
cikin bargo kuma alamu sun nuna kamar ba ita kadai bace a ciki, hannunta saka tana
lalibe ba zato ta shafa fuskarsa da hannun nata, wani uban ihu ta saka tare da yaye
bargon sai ganinta tayi a gadon prince akbar ashe tare ma suka kwana dashi, salati
tayi ta soma shafa jikinta tamkar wata mahaukaciya shi kuwa yana jinta shiru kawai
yyi amma abunda take ne yasanya shi yin murmushi, tashi yyi zaune aikuwa tana ganin
ya tashi tayi wani irin tsalle ta dire qasa ta kife akan guiwowinta tace" don Allah
kayi hkr wlh ban san lkcin da bacci ya daukeni bane na kwana mk a gado" kallonta
yyi yace" hkn ya nuna baki san aikinki bane shiyasa kk bari bacci ya dauke ki"
fashe masa tayi da kuka tace" don Allah kayi hkr wlh bazan sake ba" be sake mgn ba
ya sakko daga gadon, miqewa tayi da sauri gudun kar ta kuma aikata wani laifin
2kwata ta mance babu mayafi akanta ta shige dakin wanka ta soma shirya masa ruwan
wanka sannan ta fito shi kuma ya taso yazo ze shiga dakin wankan, tsayawa yyi ya
dora mata mayafinta sannan ya shige abinsa, saurin gyara mayafin tayi, ba jimawa
taji qarar qararrawa, saurin tura kofar bathroom din tayi ta tarar dashi cikin
kwarmin wankan ruwan sai fitar da tururi yake ga kumfa ta rufe saman ruwan,tausa ta
soma masa da hannunta da yake jin taushinsu sosai sannan ta wanke masa sumar kansa,
tana gamawa ta fita saida ya kuma danna wannan alamar tukun ta kuma shigowa ta
qarasa gyara masa gashi ta shafe gashin da mayuka, har da gyaran fuska ta masa
ranar ta qara fito masa da sajen daya zagaye fuskarshi, shima kansa cikin ransa ya
yaba da gyaran nata sannan ta fara murza masa cream kamar kar ta dena hk yakeji har
ta gama, rissinar dakanta tayi sannan ta juya ta bude kofa ta fita tana jiran
fitowarsa, ya jima kafin ya fito sanye da wasu pakistan kalar sararin samaniyya yyi
kyau sosai sai fitar da qamshi yake sumarsa ko sai daukar idanu yake, zama yyi a
wata kujera ya kalleta ya daga mata hannu alamar ta tafi, rissinar dakai tayi
sannan ta juya ta nufi hanyar fita daga 6angaren shi kuma yabita da kallo har kofa
ta bude ta fice, dakinta ta wuce tayi wanka ta shirya cikin wata jar doguwar riga
tare da mayafinta, tayi kyau sosai don fatarta ta fara murjewa sbd yanayin cimmar
da take samu tana ci ga kuma makwanci mai kyau, kitchen ta tafi tana shiga taji
bayin kitchen din na qus qus ita dai bata tasu take ba ta, honey tea ta masa ta
sanya ginger kadan ta dora a faranti na alfarma ta nufi 6angaren nasa, tana shiga
ta tarar dashi yana rubutu batasan rubutun me yake ba dai ta ajiye masa honey tea
din a gabansa, ajiye abun rubutun yyi ya dago da idanunsa yana kallonta saurin
dauke kai tayi tare da rissinar da fuskarta sannan ta soma tsiyaya masa honey tea
din a qaramin cup ta dago da fuskarta tana miqa masa cup din, abunda ya bata mamaki
shine ba cup din da take miqa masa yake kallo ba ita yake kallo kuma wani irin
kallo yake mata wanda ta kasa tantance ma'anarsa don bata saba ganin irin kallon
cikin kwayar idanun jama'a ba, riqe cup din tayi ta sunkuyar dakanta qasa, hannunsa
yasa ya amshi cup din ya soma sipping a hnkli tare da lumshe idanunsa, ajiye cp din
yyi ya tashi ya tafi gaban manya manyan windows dake rufe da wasu kofofin glass ya
tsaya tare da kalmashe hannayensa ta baya ya qurawa glasses din windown idanu,
bimbii kallonsa tayi kawai ta fahimci kamar akwai abunda ke damunsa, cikin qarfin
hali ya taho wurin dayake tsaye cikin sanyin murya tace" koh akwai abunda yarima
yake buqata ne" bece mata komai ba kuma juyo ya kalleta ba, ganin hkne yasa ta koma
ta dauki farantin ta fita dashi, tana fita ya juyo yana kallon kofar, komawa yyi ya
zauna ya lumshe idanunsa yana fitar da wata zafaffiyar ajiyar zuciya, hk abu ya
cigaba da tfy tun bimbii tana tsarguwa idan prince akbar ya qureta da idanu har ta
saba da kallon nasa ta dau hkn ko shima duk yana daga cikin al'adarsu wato kallon
qurilla, prince nasaar shima ya takurawa bimbii har ta soma shakkar zuwa qorama don
baya gjy da zuwa wurin musamman sbd ita, bimbii yanzu wannan shegen tsoron nata ya
soma raguwa ta soma zama jarumar mata, prince nasaar baya ta6a samun sakin fuska a
wurin bimbii shi kuwa baya zuciya don har ga Allah son bimbii yake irin sosai din
nan, sai ya shafe kusan awanni yana jiran fitowar bimbii bakin qorama wanki, israt
da khulood kuwa saida bimbii ta samar musu da alfarma suka dawo 6angaren prince da
bauta suka shiga jerin bayin dake aiki a kitchen, musamman bimbii tace su dawo
dakinta da kwana hk suke kwana su uku kamar yadda suka saba,khulood ita ta din ga
koyar da bimbii girke girke irin nasu na larabawa daban daban yanzu ta kware sosai
a fagen girki, israt kuma ita take koya mata waqoqi iri daban daban, suna taimaka
mata sosai, yau suka tashi cikin tsantsar rudani sbd samun labari da sukayi za'a
jefe yan matan bayin da sukayi ciki, hanyar 6angaren prince bimbii tayi da gudu
bayin dake tsaron kofar suka qi bude mata kofa suka sanar da ita prince baya
buqatar ganin kowa, shi kuwa yana tare ne da hadiminsa ubaid suna tattaunawar
sirri, bimbii kuwa hk ta din ga jira amma shiru babu alamun zasu bude mata kofar,
juyawa tayi ta koma ta nufi bakin qorama, bata jima da zuwa wurin ba prince nasaar
ya bayyana shima, tana ganinsa ta miqe kamar zataci tuntu6e ta nufi wurinsa shima
abun ya bashi mamaki ya bita da kallo, kallonsa tayi ta sunkuya bisa guiwowinta a
gabansa tace" don Allah ka taimakamin ka cetomin yar uwa tana cikin yan matan da
za'a jefe yau" shiru yyi sai kuma ya kalleta da murmushi yace" wannan alfarma tana
da wahalar gaske sbd sarki abdallah dakansa ne yasa hannu a jefesu babu wanda ya
isa ya dakatar da hk duk cikin masarautan nan amma...." sai kuma yyi shiru tace"
amma me?" yace" zan iya sanyawa a saceta akaita masarautarmu saidai wannan tamkar
qunar bakin wake ne da tarar aradu da fadin kai don idan har aka samu mtsl toh gsky
nikaina ina cikin mtsl amma karki damu zan iya yin komai sbd ke sbd na yarda da
ingancin soyayyar da nk miki" kallonsa tayi da mugun mamaki ta nuna kanta tace" so
kuma?" daga mata kai yyi alamar ehh, tace"don Allah ka dena fadar hk bani so" yace"
baki sona kenan" tace" Aa, amma tsakanimu akwai bambanci mai karfi wanda yyi mn
iyaka kayi hkr" murmushi yyi yace"bana mgn biyu kuma duk abunda nakeso babu makawa
sai na same shi komai wuya ki fahimci hkn" bimbii sake baki tayi tana kallonshi
tana waiwaye kar wani ya ganta tare da dan sarkin, takawa yyi ya wuce ya haye
dokinsa yabarta a wurin,ranar ta makara sosai na zuwa 6angaren prince shi kuwa yana
kallon kofa yaga shigowarta amma shiru sai yanzu taxo ta tarar ya bada umarni kar
bayin dake tsaron kofarsa su barta ta shigo,qememe suka hanata shiga hk ta juya ta
koma dakinsu ta tarar dasu israt sunyi jugum jugum ita ta zauna gefensu tayi shiru,
tmbyrta israt tayi koda wani kyakykyawan labari, shiru tayi sannan ta zayyana musu
yadda sukayi da prince nasaar, shiru sukayi don tabbas sun san wannan matakin yana
da girma, kallon bimbii khulood tayi tace"kuma shi da kansa ya sanar dake ze miki
wannan alfarma, gsky yaudararki yake don kuwa wannan abu mataki ne mai tsauri mai
cike da kasada" duk abunda suke zantawa lenah na la6e tana jinsu, cikin sauri ta
nufi 6angaren prince akbar jikinta har rawa yake, bata samu ganin prince ba sai
ubaid ta samu ta zayyane masa abunda taji su bimbii na zantawa,batare da wani 6ata
lkci ba ubaid ya shiga 6angaren prince ya tarar dashi a zaune, sunkuyawa yyi daidai
kunnensa ya rada masa abunda lenah ta sanar dashi, shiru yyi sannan ya miqe dakansa
ranar ya nufi 6angaren prince nasaar, cike da mamaki prince nasaar ya kalli babban
prince don yasn ba qaramar mgn bace ta kawo shida kansa har 6angarensa, baiwarsa ce
ta kawo musu green tea duk suka zauna a wasu kujeru suna fuskantar juna, prince
akbar ya kalli prince nasaar yace" ina son ka janye kudirinka da kk dashi na shirin
sace daya daga cikin bayin da aka zartas musu da hukuncin jefawa don ba zaka samu
nasara ba kuma yin hkn tamkar hada masarautu biyu fada ne" cike da mamaki prince
nasaar ya dago dakai yana kallon prince akbar, mamaki yake a ina yaji wannan sirrin
dayasan duk duniya bimbii ce kawai ta sani toh ko ita ta sanar da babban prince
wannan zancen, murmushi prince akbar yyi masa yace"ina baka shawara kar ka sake
kayi wannan kuskuren don ba riba cikinsa kuma zaka sanya rayuka dayawa cikin qunci"
har prince akbar ya gama jawabinsa be furta komai sai daga qarshe kawai yyi
murmushin yaqe yace" zan so naji a ina prince yaji wannan labari na qanxon kurege
duk da nasan cewa kai mutum mai taka tsantsan" murmushi prince akbar yyi tare da
miqewa yace" ni zan wuce fata dai kayi aiki da hange don qaramar mgn kan iya zama
babba" hk prince akbar yabar prince nasaar cike da tunani, washegari bimbii ta
shiga kitchen ta shirya abun sha ta nufi 6angaren prince tana zuwa kofa ta bude
mata ta shige, yana ganinta yyi saurin dauke kansa ya cigaba da abunda yake batare
daya ba shigowar nata wani muhimmaci ba......

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki turon da screesht na
payment naki ta whatsapp da wannan layi..07041195806....idan kuma da buqatar kira
ga layin kira nan..08080611486

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

14

*You break my heart*.......

Ita kanta jikinta yyi sanyi yanayin yadda taga yyi mata, qarasa tayi ta ajiye
farantin dake hannunta tare da rissinar dakanta qasa, saida ya gama duk abunda yake
sannan ya dago idanunsa yana kallonta ba zato taji muryarsa yace" jiya ina kkje"
shiru tayi sai kuma tace" na tafi wanki qorama" tsayar da kwayar idonsa yyi akan
fuskarta yace" sai kuma kk tsaya a ina" tsoro ne ya soma shigarta muryarta har rawa
take tace" ba....bu...k..o.ina" tayi mgnr ne a daburce kuma cikin qinqina,
murmushi yyi yana qare mata kallo ita kuma kanta na qasa, miqewa yyi ya nufi wurin
windows din daya soma tsayawa hannayensa dukka yyi folding nasa a baya, batare daya
juyo ba yace"me ya hadaki da prince nasaar" innalillahi wa'inna ilaihir
rajuna.....abunda ta furta kenan kuma a bayyane sbd razana da tayi ta marairaice
fuska kamar zatayi kuka gashi dai ba damar musawa sai ta sunkuya bisa guiwowinta
tare da rissinar dakanta qasa alamar dake nuni data amsa laifinta, juyawa yyi ya
koma ya zauna ta taso da sauri ta soma tsiyaya masa herbal tea din data hada masa,
yace" kar ki sake sanya kanki cikin abunda be shafe ki ba" rissinar dakanta tayi
tare da miqa masa cup na tea din sannan ta koma bayansa ta tsaya ta sanya hannunta
a kafadarsa ta soma daddana masa jiki tana masa tausa, murmushi yyi sbd yasan
abunda yasa tayi hkn sbd tasan tayi laifi ne, bece mata uffan ba ya cigaba da
sipping tea nasa, daga mata hannu yyi alamar ya isa hk ta tafi, sum sum ta wuce ya
bita da kallon wutsiyar ido, komawa tayi dakinta ta zauna tayi shiru gashi su
khulood basu nan, tunanin abunda prince ya fada mata yanzu, gani tayi kamar yana da
masaniya game da plan dinsu da prince nasaar shiyasa yake mata mgn cikin shagu6e,
dafe kanta tayi kawai cike da tsantsar fargaba, shigowar wata baiwa ce ta sanyata
dago da kanta, kallon bimbii baiwar tayi tace" prince nasaar yana da buqatar
ganinki, kallon baiwar baiwar tayi sosai sannan ta miqe tabi bayanta, tfy sukayi
mai tazara sannan suka shiga 6angaren prince nasaar, lambunsa ta wuce da bimbii
sannan ta juya ta koma bakin aikinta, bimbii koh ta qarasa ciki, ganinsa tayi zauna
akan wani farin dutse fuskarsa babu yabo ba fallasa, rissinar dakanta tayi alamar
girmamawa ga prince din,yace" kece kk fadawa prince akbar plan din dana shirya na
sace wannan baiwar" shiru bimbii tayi cike da mamaki sai kuma tace" Aa,bani bace"
yace" amma kin sanar da wani koh" tace" ehh,munyi mgnr da yan'uwana amma tabbas
nasan sukam basu sanar da kowa" yace"meyesa kk fadawa wani bayan na fada miki
wannan mataki yana da tsauri kuma rashin nasara babban barazana ne" tace" an samu
mtsl koh" shiru yyi yana nazarinta sai kuma yace" prince akbar yazo ya same ni akan
wannan mgn kuma yace na dakata idan kuma ba hk ba za'a samu matsl" shiru bimbii
tayi kamar zatayi kuka tace" babu komai" yace" zaki iya tfy" a hnkli kamar kazar da
qwai ya fashewa a ciki ta juya ta soma tfy har ta fice daga lambun ta nufi
sashinsu, tana shiga ta tarar su israt sun dawo, zama kusa dasu tace" bansan ya
zamuyi ba an samu mtsl" dukkaninsu suka dago kai a razane don sunyi tunanin koh
wurin aiwatar da plan din ne aka samu mtsl, bimbii ta kallesu sosai ta sanar dasu
abunda ya faru, duk aukayi shiru suna tunanin waye kuwa ya sanar da prince wannan
mgn, bimbii tace" ba abun mamaki bane don prince ya samu labari don yana da
tsatstsauran tsaro da kuma tsananin taka tsantsan" israt tace" amma duk da hk alamu
sun nuna akwai wadanda suke mn la6e" bimbii tayi shiru tana nazari kan mgnr israt,
tace" toh yanzu meye mafita" duk sukayi shiru, suna cikin mgn sukaji sanarwa kowa
ya fito wurin jifan bayi, dukka suka miqe a zabure suka fita, wani shararren fili
ne me dauke da rairayi sosai nan aka fito da yan matan su ashirin da biyu wasu daga
cikinsu sun haife cikin dake jikinsu wasu kuma basu haife ba, sai lkcin bimbii ta
ta6a tozali da sarkin abdallah bin jabal dake zaune a wata kujera ta alfarma a can
saman wata matattakala cikin wani tanti, farin balarabe ne tas yana da yalwar dogon
farin gemu ga hancinsa dogo dodar amma ya manyanta sosai hannunsa riqe da sandar
sarauta, sanye yake cikin wata alkyabba dark brown da jan rawani mai adon fari da
ja, gefen hannunsa na dama prince akbar ne sanye yake shima cikin farar jallabiya
da rawaninsa baqi da fari dayan 6angaren hagunsa kuma ragowar ya'yan sarakuna ne
sai ministocinsa da y'an majalissar zartarwa, bayi kuma na tsaye cirko cirko daga
qasa suna jiran ganin abunda za'a aiwatar kan wadannan yan matan, wasu manya manyan
bayi majiya qarfi suka kukkunce yan mata suka soma haurawa dasu saman wani gini
suka kuma daddaure a jikin wani qarfe, bimbii idanunta ne ya saukan akan lailah
wacce hawaye ya gama 6atawa fuska tana daure ita jikin qarfen, fashewa bimbiii tayi
da kuka suma su khulood duk kukan suke, sai yanzu bimbii ta tabbatar da zalinci a
wannan masarauta tayi Allah tirrr da wannan al'ada tasu, prince akbar ne ya miqe
dakansa ya nufi inda aka daure yan matan ya kallesu daya bayan daya sannan ya bada
dama a soma jifansu, murmushi sarki abdallah bin jabal yyi lkcin da aka soma aikawa
yan mata da saqonnin duwatsu, jifansu ake ta ko'ina, bimbii rufe idonta tayi qam
tare da qanqame jikinta tamkar ita ake jifa, bayan an gama jefesu ne aka sakko da
gawarwakinsu qasa abun gwanin tausayi, batare da bata lkci ba sarkin abdallah bin
jabal ya tashi yyi jawabin gargadi ga duk wanda ya kuma aikata wannan abu sannan
suka soma sakkowa daga matattakalan sai darewa ake ana basu hanya suka wuce zuwa
fada, bimbii kafafunta kasa daukarta tayi ta zube bisa rairayin tana kukan zucci
don tayi na filin har ta qoshi, rashin amfaninta kawai take gani tunda gashi ta
kasa ceto rayuwar lailah, dakyar su khulood suka jata suka koma 6angarensu, bimbii
tunda ta shiga dakin bata fito ba har dare sai da daren ta fito takaiwa prince
dinner, tunda ta shiga ta ganshi zaune yana ta rubuce rubucensa ta ajiye masa
dinner din wata kusurwa mai yalwar shimfidadden centre carpet da ado, kunsan mafi
yawan larabawa sun fi son cin abinci a zaune bisa shimfida,tunda ta shigo ya lura
sam babu annuri a fuskarta tayi mugun tsare gd, be kuma kallonta ba ya cigaba da
gudanar da abunda yake, bayan ya gama ne tayi abunda ya kamata na al'adar wankansa
ya fito cikin shigar bacci sannan ta tsaya har yaci abinci sannan ya bata umarnin
tfy, tana komawa 6angaren nasu taga su khulood na jiranta don ta sanar dasu cikin
dare zasu ruwan da aka watsa gawarwakin su lailah su mata kallon qarshe,dare nayi
sosai suka saci jiki suka nufi wannan ruwa dayake nesa sosai daga wannan gd na
sarauta amma duk cikin masarautan ne, gawarwakin na nan basu gama wucewa ba,
tattare rigunansu sukayi suka soma shiga cikin ruwan suna lali6e ko Allah ze basu
sa'ar gano gawar layla, khulood ce ta soma ganin gawar ta kirasu suka zo wurin da
sauri, bimbii ta ta6a gawar, dago fuskarta tayi da sauri tace" kamar tana da sauran
numfashi" israt ta dora kanta taji kamar alamun zuciyarta na buga a hnkli, kallonsu
tayi tace" tabbas akwai alamun numfashi tattare da ita yanzu meye abunyi, shiru
sukayi suna tunanin ina ya dace su dosa da gawar laylan tunda sunji kamar tana
numfashi,jan gawar suka somayi suka kaita bakin wata bishiya, dukkaninsu sunayi
suna 2kalle gudun kar wani ya gansu,bimbii tace" tana buqatar taimakonmu ina ya
dace mu kaita inda ba za'a kamamu ba" suna kan shawara sukaji sawun dawakai sun
nufo wurin da suke,take gabansu ya fara dokawa tara tara.......

Littafin na kudi ne gamai buqata za'a tura #300 kacal ta wannan


acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, sai a tura screesht ta whatsapp
ta wannan layin...07041195806.......

Alkalamin Bintuu ne...


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

15

*I never care about the difference betwee us*....my only concern is you to accept
me as your companion💕

Wasu ne daga cikin dakarun dake tsaron gdn sarautar, suna kewayawa ne ta ko'ina
cikin wannan masarauta don tabbatar da tsaro, tun kan su qaraso wurin da suke,
khulood ta kallesu tace" muna cikin rikici fa idan suka ganmu"neman wurin 6uya suka
somayi amma duk wurin babu wurin da zasu iya 6uya,israt ta kallesu a rikice tace"
mu haye bishiya kawai" aikuwa kafin ta rufe baki sai ganinsu tayi sun rigata hayewa
bishiyar dayake bishiyar tana da yalwar ganye kuma ga duhu, hkn yyi daidai da
qarasowar dakarun wurin, ganin gawar layla da sukayi ne a gindin wannan bishiya
yasa duk suka ja limzamin dawakansu suka tsaya, babban cikinsu ne ya fara sakkowa
daga saman dokinsa sannan sauran ma duk suka sakko, duba gawar sukayi cike da
mamaki don tabbas sun gane gawar na daga cikin gawarwakin yan matan da aka jefe
yau, abunda ya basu mamaki shine wanda ya jawo gawar daga cikin kogi ya kawota
wurin bishiyar nan, 2waige suka soma ko zasu gano wata alama dake nuna da wani a
yankin wurin amma basu ga komai ba kuma basu ji motsin komai ba, babban cikin nasu
ne ya gano alamar sawun kafar su bimbii dayake wurin rairayi ne, bin sawun ya
somayi har ya gano daidai wurin da sawun kafar tasu ya tsaya, su bimbii kuwa dake
maqale akan bishiya tuni cikinsu ya duri ruwa,israt kan rufe idanunta tayi kawai
tana addu'ar Allah ya fisshesu ya rufa musu asiri kar su gano su,babban cikin nasu
ya kalli sauran yace" su duba kan bishiya" israt tana jin hk ta saki fitsari a
wando, bimbii da khulood kuwa sun sadaqar kawai mutuwarsu tazo,duk sunyi 2tsuro a
maqale akan bishiya suka ga dakarun nan sun soma qoqarin hawowa bishiyar, daidai
lkcin wani mahayin doki ya bayyana, takun sawun dokin nasa ne ya janye hnklinsu
daga hawa bishiya duk suka juya suna kallonsa sanye yake da baqin kyalle ya rufe
rabin fuskarsa, wucesu yyi da gudu bisa dokin nasa,hkn da suka gani ne ya janye
hnklinsu suka haye dawakansu suka rufa masa baya,hknne yaba su bimbii damar sakkowa
daga kan bishiya duk da hk zuciyarsu tana tsananta bugawa, sake ta6a gawar layla
sukayi suka ji 2kwata ta dena numfashi alamar rai yyi halinsa, dukkaninsu kuka suke
suna tfy suna waiwayen gawar layla babu halin su mata suttura hk suka bar wurin
cike da taka tsantsan kar a gane takun sawunsu har Allah ya basu sa'ar komawa
6angarensu, suna shiga daki suka rufe da sakata suka hau gadonsu da gudu suka ja
bargo suka rufa dashi zuciyarsu na cigaba da bugawa 2tara don gani suke kamar basu
tsira ba, aikuwa basu jima ba sukaji ana buga musu kofa kamar za'a 6alla, bimbii ta
rada musu kar ku sake koma waye ku bari a gane alamun tsoro ko rashin gsky a
fuskokinku ku aro jarumta idan har kuna son tsira,raggo baya zama gwani damu mutu
ragwaye gwara mun mutu jarumai, wadannan kalmomi su suka sanya wata sabuwar jarumta
ta shigesu tashi guda, bude kofar sukayi fuskarsu da alamun nuna bacci, masu tsaron
farfajiyar gdn ne suke bi daki daki na bayi don tabbatar da kowa yana cikin dakinsa
a kwance, suna ganinsu suka wuce zuwa daki na gaba hk suka din ga zagaye cikin
wannan dare, su bimbii kuwa rufe kofarsu suka sakeyi suna sauke ajiyar zuciya don
da bayin sun zo kafin su dawo suka ga basu nan toh asirinsu ya gama tonuwa kenan
sbd sai sun bincika su ga inda sukaje da wannan dare, komawa sukayi suka kwanta
amma cikinsu babu wanda ya iya rintsawa don zuciyar har yanzu tana cike da fargabar
abunda ze faru gobe,6angaren dakarun da suka bi bayan wannan mahayin dokin kuwa
basu samu damar qarasawa wurinsa ba ma bare su iya kintata siffarsa sbd kwarewarsa
wurin iya gudu da doki tashi daya ya 6ace musu suka rasa inda yyi babu irin duban
da basu masa ba, dole suka koma wurin bishiyar nan suka ga ba gawar da suka bari a
gindin bishiya, hkn ya basu mugun mamaki, kogin da aka watsa gawarwakin nan suka
nufa suka tarar ruwa yyi gaba da kusan dukkan gawarwakin yan matan sai kadan kuma
cikin kadan din da sukayi saura babu mai kama ma da wannan gawa da suka gani a
bakin bishiya, so suke su gano asalin gawar sbd su bincika makusantan ta amma basu
ga gawar ba, hk suka juya suka bar wurin amma sun sanar da dukkanin sauran dakaru
masu tsaron masarautar su sanya idanu sosai kan kowanne lungu da saqo na
masarautar, washegari su bimbii suka tashi suka shirya kowacce ta nufi wurin
aikinta, sun 6oye duk wani tsoro nasu, bimbii sanye take cikin wata farar doguwar
riga mai ado da kyalkyali, gashin kanta kuwa yasha gyara na musamman, kunnuwanta
sanye da wasu manyan yan kunne masu kyau,hannunta kuma da wasu awarwaro, kitchen ta
shiga ta hada abinci kala, bayin dake aiki a kitchen sai kallonta suke a yatsine,
bimbii tana aiki ne cike da tsantsar takan tsan tsan, bata matsawa konan da can
saita gama shirya komai sbd tsaro da kuma gudun kaidi da makirci na gdn sarauta,
wani qaton basket ta dauka mai kyau ta soma sanya mazuban dake dauke da abincin a
ciki ta dauka ta nufi 6angaren prince dashi, tana zuwa kofa ta bude ta danna kai
ciki, yana zaune a wata royal chair yana rubuta wata wasiqa yana gama rubutun
wasiqar ya dauki hatimin gdn sarautar burham ya danna a jikin wasiqar sannan ya
rufe takardar ya sanyata cikin wani qaramin akwati, dago da kyakyawan idanunsa yyi
yana qare mata kallo, ita kuwa tayi saurin yin qasa da kanta alamar girmamawa
gareshi sannan ta wuce inda yake cin abinci ta soma jera masa abincin data shigo
dashi shi kuwa rakata yyi da kallo kawai, bayam ta gama ne ta dawo wurin dayake
tace"komai ya kammala" bece mata uffan ba ya tashi daga inda yake ya nufi wurin
shimfidar alfarmar da abincin ke jera ya zauna, wurin itama taje ta soma zuzzuba
masa abinci a qananan plate yana bin kowanne yana ci 2kadan, bayan ta gama bashi
abinci ya koma ya kwanta akan gadonsa yace"tazo ta masa tausa" kwanciya yyi ruf da
ciki ita kuma tana tausa masa baya, cikinsu babu mai mgn sai qarar awarwaron
hannunta, muryarshi taji yace" ina sake ja miki kunne da ki guji sanya kanki a
fitina idan kuma ba hk ba wataran zakiyi nadama mara amfani" saurin kallon fuskarsa
tayi taga idanunsa a rufe suke yake wannan mgn, cike da jarumta ta 6oye tsoronta
tace" zan cigaba da kiyayewa ranka ya dade" shiru yyi be kuma cewa komai ba ita
kuma zuciyarta cike take da tunanin wannan mgnr ta prince, shi baya furta mgn kai
tsaye saidai yyi shagu6e yabarka cikin tunani, tayi nisa cikin tunanin mgnrsa har
ta dakata da tausan da take masa batare data ankara ba, shi kuwa yana ji ta dakata
da tausan da take masa yasan tunanin abunda ya fada mata yanzu take, hannunsa yasa
ta baya ya riqo hannayenta ya murzasu da karfi,saurin kallonsa tayi taga idanunsa a
lumshe suke kuma yaqi sakin hannun nata, qoqarin janye hannun nata take a hnkli
cikin dabara da hikima ya bude idanunsa ya saukesu akan fuskarta, yanayin yadda
taga idanun nasa yasa tasha jinin jikinta tayi saurin sunkuyar dakanta qasa,ya jima
yana mata wannan kallon qurullan da har yanzu ita ta kasa gane ma'anar kallon sai
ta dauki hkn a matsayin al'adar prince akbar,yace" ki shirya zaki rakani wani wuri"
rissinar dakanta tayi alamar amsa umarnin nasa,sakin hannunta yyi ya mata alama
data tafi, sauka tayi daga kan tafkeken gadon nasa ta sake masa shara shara curtain
din dake kame ta koma can wani gefe ta durqusa kan guiwowinta tana jiran fitowarsa,
ya jima a kwance kuma ba bacci yake ba idanunsa biyu,babban hadiminsa ubaid ne ya
shigo ta sanar dashi bazai samu ganin prince yanzu ba yana kwance,komawa yyi bakin
kofa ya tsay yana jiran lkcin tashinsa, yana jinsu amma akwai abunda ke damunsa ne
kuma yake tunani akai shiyasa yakeson kadaici, saida ya dade a kwance sannnan ya
tashi ya shirya cikin wasu fararen kaya hatta rawanin kan nasa shims fari ne sol,
ubaid ne ya shigo ya tsaya a wurin kujerar da prince yake ya rissinar dakansa
sannan ya dago yace" komai ya tafi yadda ya kamata" ita tana tsaye daga gefe abunda
taji ubaid ya fada kenan, prince ya daga masa hannun alamar shikenan, sake rissinar
dakansa yyi sannan ya juya ya fita ya tsaya a bakin kofa yana jiran fitowar prince,
daukar wani qaramin box yyi mai kalar ja ya miqa mata, sunkuyawa tayi ta amsa box
din, bece mata komai ba ya miqe yyi hanyar waje shima tabi bayansa da sauri, a
keken doki aka daukesu suka tafi wurin taron, sarki abdullah bin jabal ne dakansa
ya shirya wannan qasaitaccen taro wadanda ya samu halarta wasu daga cikin manyan
sarakuna na wannan nahiya, taro ne na cikarsa shekaru hamsin da tara akan mulki,
masarautar burham kuma tana da shekaru dari uku da sittin da uku da kafuwa, wurin
taron ya qayatu da shiri na alfarma ga kuma jini na sarauta masu ji da kansu da
taqama da cikakkiyar izzah ta sarauta duk suna hakimce bisa kujeru na alfarma,
ko'ina ka hanga hasken farar fata kk gani suna mgn da yaren alfarma wato harshen
larabci, bimbii dai tana bayan prince akbar dayake wani babban jigo a taron, ubaid
kuma yana daga gefensa na dama hk suka rakasa mazauninsa ya zauna, wurin bimbii
taga bayi dayawa wadanda suke baqar fata maza da mata amma yawancinsu qasqantattun
bayi ne, gimbiya hindu na daga gefe tare take itama da wasu ya'yan sarakuna,ganin
bimbii a bayan prince yasa abun ya bata haushi ta kuma shirya yadda zata toxarta
bimbii a taron kowa ya shaida, kade kade ne ya soma tashi a wurin irin nasu na
larabawa, prince akbar kuwa duk sakan daya sai ya waiga yaga ko bimbii na nan,
ubaid yana lura dashi yyi mamaki sosai na ganin yadda babban prince ya damu da
lamarin bimbii, yana lura da yadda yake yawan kallon bimbii hkn tamkar wanin baqon
hali ne cikin halayyar prince din don yadda ya sani prince akbar yana da
cikakkiyar izzar da baya yiwa abu kallo biyu musamman mace, macen ma baiwarsa,
baiwar ma wacce suke kira mara asali jinsin baqar fata, taro yyi taro sai shagali
ake da kuma shan shayi irin nasu na al'adar larabawa, gimbiya hindu ce ta tashi ta
nufi wurin sarki abdallah bin jabal tadan rissinar dakanta kusa dashi tace" Allah
yaja zamaninka sarkin masu adalci baqinmu na da buqatar babbawar baiwa ga prince
akbar ta fito ta nishadintar dasu da waqoqi masu dadi don kwararriya ce a
wannan fannin" murmushi sarki abdallah yyi ya juya ya kalli badakaren dake bayansa
yace" ya sanar ana buqatar babbar baiwar ga prince akbar ta fito ta nishadintar da
taron da salonta" batare da 6ata lkci ba wannan badakaren ma'abocin babbar murya ya
soma shela cikin muryarsa data karade wurin,prince akbar yana jin wannan sanarwa
ransa yyi masifar 6aci sbd bimbii babbar baiwarsa ce dole saida izininshi zata
aiwatar da wani abu amma ganin daya yyi babban bawan mahaifinsa ne yake wannan
sanarwa yasan umarni ne daga wurin sarki abdallah dakansa,shiru yyi don ba yadda ya
iya, bimbii ko gabanta ne ya yanke ya fadi tana tsoron fita gaban wadannan
bunqasassu masu fama da izzar mulki, wasu bayi ne suka xo suka mata jagora ta tafi
dakin sauya kaya, kayan da suka bata ta sanya wasu shara shara duk qaurun kafafunta
a bude suke ga cikin nata shima a wangale dakyar suka janyota ta fito don dagewa
tayi bata fita hk, prince akbar na daga idanu ya hango wannan shiga dake jikin
bimbii take ransa ya qara 6aci ya daure fuskarsa tamau,prince nasaar na gefe yana
karantar yanayin prince din har lkcin da bimbii ta hau stage, tsayawa tayi sai
kalle kalle take kafin zaqaqqiyar muryarta ta soma rero wasu baitoci.....

Littafin nan na siyarwa ne, kan naira #300 kacal, zaki tura ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki turo da screesht na
payment ta whatsapp ta wannan layi....07041195806....

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

16

*The more I see you, my heart beat faster than I Imagine*.....so,you are my heart
beat....💕

Idanun kowa a wurin yana kanta, lkcin ta soma rero baitocin dake cikin waqenta
cikin karyayyen harshenta na diyan fillo dake fitar da luqqa na larabci mai dadin
mutuqar dadin sauraro, waqa daya ta dauka cikin waqoqin larabcin da israt ta koya
mata har da irin salon rawar waqar, rawan da ciki ake ana karkad'a k'ugu, toh
abunku da masu ma'adanan kadawa gaba da baya tuni ta janye hnklin kowa na wurin da
salon rawarta, k'ugunta take k'adawa cike da tsantsar k'warewa tana rero baitocinta
da muryarta data gama kared'e wurin sbd zaqi, dayawa a wurin sun koma tamkar mutum
mutumi sun zuba mata na mujiya, gimbiya hindu ranar ma hk ta din ga cika tana
batsewa don ba hk taso ba, ita tunaninta bimbii waqar fillanci zatayi sbd ta
toxarta ta a wurin a aibata harshenta tare da kalar fatarta, sai ga bimbii ta bata
mamaki tayi waqenta cikin harshen larabci, juyi take sosai skirt din data saka mai
batsa ne ta kasa yana hurawa, duk inda ake neman cika na mace toh bimbii ta qetare
wurin, tana zuwa qarshen waqar ta sunkuya da qafa daya tare rissinar dakanta qasa
ta musu hk da hannu�wurin ya dauki tafi sosai, shikanshi sarki abdallah murmushi
yyi irin nasu na manya, prince akbar kuwa gbdy ransa a dagule yake ji yyi zaman
wurin duk ya gundureshi, bimbii koh dawowa tayi bayansa ta tsaya bayan taje ta
sauya kayan dake jikinta, prince nasaar shima takaicine ya ishe shi yadda yaga
bimbii ta koma bayan prince akbar ta tsaya, wata baiwa ce wacce ke cikin bayin dake
rarraba abun sha a wurin ta kawo ruwan inibi ta sunkuya tare da ajiyewa a gaban
prince akbar sannan ta dauka ta tsiyaya masa a qaramin cup ta rissinar dakanta qasa
tare da miqa masa cup din da hannu biyu, bimbii tayi sauri ta zagayo wurin ta zata
amshi cup daga hannun baiwan nan, gani tayi baiwar taqi bata cup din sai miqawa
prince take dakanta, kallon baiwar prince akbar yyi yace" ki bata itace keda haqqin
bani abu naci" jiki a sanyaye baiwar ta miqawa bimbii cup din dake hannunta bimbii
ta dan diga ruwan inibin a farcen dake babban yatsanta, duk suka tsaya suna mata
kallon mamaki,yatsan nata ne yyi duhu sosai, juyawa tayi ta miqawa baiwar ruwan
inibin data kawo tace" babban prince baya shan ruwa inibi" kallonta prince akbar
yyi sannan ya kalli wannan baiwa dake tsaye sai kawai ya miqa mata hannu ta miqo
masa cup din data tsiyaya ruwan inibi yakai bakinsa da niyyar sha, bimbii kuwa sai
kallonshi take taga tabbas sha zeyi sai tayi saurin sanya hannunta ta amshi cup din
daga hannunsa takai bakinta,gimbiya hindu dake kallonsu miqe tayi da sauri cike da
tsan tsar mamaki, baiwa ta amshi abu daga hannu prince takai bakinta, hknne ya
dauko hnklin mutane, prince akbar kuwa tsayawa yyi kawai yana kallon bimbii data
shanye ruwan inibin dake cup din tas, kafin ta sauke cup din, ubaid ya dauketa da
wasu kyawawan mari lafiyayyu guda uku,tana matsayin baiwa har ta samu yancin da
zata amshi cup a hannun prince takai bakinta, wata irin fizga ubaid yakai mata ya
durqusar da ita a qasa bisa guiwowinta, shi kuwa prince bece uffan ba kawai kallon
bimbii yake, ita kuwa bimbii abunda yasa tayi hk shine tun tana rawa bisa stage
idanunta yakai kan dan sarkin dulham wanda ake kira da prince amir shima ya bayyana
a wannan taron, lkcin da baiwar takai masa nasa ta ajiye ta nufo wurin prince da
dayan na hannunta ashe ita kanta baiwar bata ankara ba sa'adda prince amir ya
musanya mata farantin da jug din da ruwan inibin da zata kaiwa prince akbar yake ya
tura mata nashi wanda ta fara ajiyewa, ita kuma bimbii ganin hkn yasa tasan tabbas
babu qamshin gsky kan lamarin, diga ruwan inibin da tayi a saman farcenta har yyi
duhu shine ya tabbatar mata da akwai guba mai qarfi a cikin wannan abu don tun tana
yarinya Allah yyi mata wannan baiwar, idan har akwai abu na cutarwa a abunda zataci
idan ta sanya bisa farcenta tana ganewa, idan farcen nata yyi duhu toh abincin da
akwai abun cutarwa a cikinsa,wannan dalili ne yasa ta hana prince shan ruwan inibi
data ga kuma ya amsa ze sha shine ta amsa ta shanye ita,aikuwa tana wurin a
durqushe kan guiwowinta idanunta suka soma gani dishi dishi, tsintsiyar hannunta
tashi daya ta soma sauya launi zuwa kalar ja, basu ankara ba sai ganinta sukayi ta
zube a wurin, zumbur prince ya miqe daga inda yake zauna ya nufo wurin da bimbii ke
kwance ya tsuguna yakai hannunsa ze riqo tsintsiyar hannunta daya ga tayi jajir
yana son tantance qarfin gubar dake jikinta, ubaid yyi saurin riqe masa hannu yace"
ranka ya dade kar ka ta6a, guba ce mai qarfu zata iya shiga jikinka"sarki abdallah
bin jabal kuwa dayake suna da dan tazara tsakaninsa da wurin da ya'yan sarakunan ke
jera besan abunda ke faruwa ba saida hadiminsa ya matso kusa dashi ya rada masa
abunda ke faruwa, saurin tashi yyi ransa a mutuqar 6ace, baiwar kuwa data kawo
wannan ruwan inibi tashi daya jikinta ya soma rawa, ita dai har ga Allah tasan bata
zuba komai a ruwan inibin ba toh waye ya mata hk, sarki abdallah bin jabal dakansa
ya taso ya iso wurin yana kallon bimbii dake kwance ya kalli hannunta daya suntume
tashi daya hkma wurin maqogwaronta, kallon hadimin dake bayansa kawai yyi shi kuma
ya sunkuya da hanzari ze dauki bimbii ya fice da ita, prince yyi saurin dakatar
dashi shi ya sunkuya da niyyar daukanta, tsawar da mahaifinsa sarki abdallah ya
daka masa ne yasa shi janye hannunsa, akan idanunsa wannan hadimi ya sunkuya ya
dauki bimbii ya fita da ita, ita kuwa wannan baiwa sarki abdallah ya bada umarnin
tfy da ita dakin azabtarwa har saita bayyana wanda ya sanyata aikata wannan
gangacin kan magajin masarautar burham, bimbii wani dogon daki aka kaita suna
binciken irin gubar don bata magani, 6angaren wurin taro kuwa cigaba sukayi da
taronsu batare da nuna kulawa ga abunda ya faru da bimbii ba sbd ita din baiwa ce,
sarki abdallah yana da mugun ra'ayin riqau babu wanda ya isa yasa shi janye abunda
yyi niyya shiyasa suka cigaba da gudanar da wannan taro tamkar babu abunda ya faru,
prince kuwa kasa zama a wurin yyi ya sulale shi da hadiminsa ubaid suka bar wurin
taron,suna fita ya kalli ubaid yace" kaje ka bincika inda suka kaita" rissinar
dakai ubaid yyi alamar ya amsa umarni sannan yyiwa prince rakiya har 6angarensa
sannan ya koma don binciko wurin da akai kai bimbii,prince kuwa ya kasa zaune ya
kasa tsaye saikai komo yake da hannayensa a baya yana tunanin halin da bimbii ke
ciki, zama yyi a wata kujera ya bude wani akwati ya fito da wata qaramar kwalba ta
antidote na irin gubar dake jikin bimbii ya dora saman table din dake gabansa,
bimbii kuwa gubar dake jikinta ba'a son ta jima a jikinta idan ta jima a jikin
mutum tana illata dukkanin garkuwar jiki ne,sun bata magani amma har yanzu jikin
nata beyi respond ga maganin ba, 6angaren prince kuwa ubaid ya kawo masa labaran
dukkanin abunda ke faruwa da bimbii, cikin dare ya fice shima ya nufi sashin da
bimbii, masu tsaron wurin suna ganin prince suka rissinar dakai tare da bashi hanya
ya shige ciki, bimbii ya gani kwance bisa wani dogon gadon katako an lullu6a mata
wani mayafi, hannun nata ya kalla da wuyanta yaga wurin ya qara yin jajir, batare
daya sanya wata safar hannu ba ya kamo hannun nata yana kallo, kallon bayin dake
kula da ita yyi yace su fita su bashi wuri, cikin sauri suka juya suka fice,
handkchief dinsa fari sol yasa ya daure mata hannunta sannan ya fito da wannan
qaramar kwalba ta antidote na wannan gubar ya bude bakinta ya tsiyaya mata ya
jijjigata sosai har antidote din ya wuce zuwa maqogwaronta, qara riqo hannun nata
yyi yana kallon wurin yaga ko mgnin zeyi respond har be ga wata alama data nuna
jinkinta ya amshi mgnin ba, qura mata idanu yyi cike da sanyin ciki yasa hannunsa
ya cire dukkanin awarwaron dake hannunta yasa a aljihunsa, gumi duk ya jiqa masa
fuska sai qare mata kallo yake yana dana sanin gardaman daya mata da hkn be afku
ba, 6angaren su israt da khulood kuwa sun sami labarin abunda ya faru da bimbii
ranar dukkaninsu kasa bacci sukayi, sunyi kuka sunyi kuka har sun gaji, israt ta
kalli khulood tace" shikenan mu kuma hk rayuwarmu zata cigaba da kasance kenan
,dubi abunda ya faru da layla yanzu kuma ga wata masifar ta kuma faruwa da bimbii
duk a silar bauta" khulood ta kalleta tace" muma idan har muka cigaba da wanzuwa a
wannan masarauta wlh qarshenmu bazai kyau ba, gwara mu cire tsoro kawai mu nemarwa
kanmu hanyar gudu" kallonta israt tayi tace" abunda ya kamata kenan amma gwara
musan halin da bimbii ke ciki tukun" khulood tace" hknne" prince akbar kuwa be bar
dakin da bimbii take ba sai gab da asuba, saidai ya gargadi bayin dake tsaron wurin
da wadanda suke aikin cikin wurin kar yaji kar ya gani, wato baya son wani ya
fahimci a wurin ya kwana tare da bimbii, sukam mamaki ne ya cikasu na ganin duk
girma da cikar izza na prince akbar yazo ya kwana tare da baiwarsa sannan ya nuna
damuwa sosai kan halin da take ciki amma duk cikinsu babu wanda yasan ya bata
antidote din nan, basu kawo komai ba saidai suna ganin yana nuna kulawar ne gareta
don nuna halaccinsa ga sadaukarwar da tayi dominsa, sarki abdallah bin jabal kuwa
baida masaniyya cewa prince yaje ganin wannan baiwa dakansa, wannan baiwa kuwa data
kawo ruwan inibi tana nan ta azabtuwa amma har yanzu bata furta komai game da gubar
da suke zargin ta zubawa prince a ruwan inibi............

Pls don Allah kuyimin afuwa kuyi hkr da wannan ba yawa...

Littafin nan na kudi ne kan naira dari uku kacal zaki samu damar karantashi, #300
ta wannan acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki turon screenshrt
na payment naki ta wannan layin...07041195806.....

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

17

*Every second my heart beat just cox of you*........I really care about you💕
Washegarin ranar an tashi ne da ruwan sama sosai kamar da bakin k'warya shi kuwa
yana tsaye a dogon corridorn dake gaban 6angarensa sanye da wata farar rigar iyaka
guiwa da wando shima fari, takalmin qafarsa irin mai laushin nan ne half cover,
kansa babu rawani hknne ya bawa gashin kansa damar sakko masa har kafarsa, iskar
daminan dake kad'awa sai hura gashin nasa take yana rawa, hannunsa dukka suna
hard'e a bayansa yana kallon iskar dake kad'a ganye bishiyu da furanni da kuma
ruwan dake sauka, yanayin tsayuwarsa kawai ze tabbatar mk da yana tunanin wani abu
ne, ubaid ne yazo ya tsaya a gefensa tare da rissinar dakansa qasa sannan
yace"binciken ya nuna gubar an hadata ne da dafin wasu kunamai da bamu da irinsu a
wannan yanki namu yawanci an fi samu irin kunaman a yankin masarautar dulham suna
amfani da dafin kunaman wurin hada abuwawa dayawa ciki har da irin wannan
gubar"shiru prince yyi batare daya juyo ya kalli ubaid ba sai can yace" na bata
maganin kashe qarfin gubar" yana fadar hk ya juya ya soma takunsa cike da izza ya
koma cikin 6angarensa, zama yyi akan wata kujera ya bud'e wani babban littafi mai
dauke da tsohuwar kimiyya ta larabawa game da ilimin sanin 2kala dafin kunama da
maciji yana wani nazari, lenah ce tsohuwar baiwarsa ta shigo hannunta riqe da wani
faranti azurfa sai daukar idanu yake da qananan cups a saman faranti, tfy take
tamkar zata karye sbd da rangwada na salon jan hnkli, le6enta jajir da jan baki ga
gashin girarta tayi sama zara zara a gyare, wuyan qafarta da wata sarqa mai
kwalliya, hancinta ma da dan kunne dan mitsitsi, ajiye masa farantin tayi ta
risssinar dakanta qasa sannan ta sunkuya ta soma tsiyaya masa black ginger tea din
data kawo masa, shi kuwa tamkar besan ta shigo ba ya cigaba da karatunsa, qara
rissinar dakanta tayi ta miqa masa cup din dake hannunta tana murmushi, sai lkcin
ya dago dakansa ya kalleta fuskarsa babu yabo babu fallasa ya sanya hannu ya amshi
cup din ya ajiye a saman table din, daga mata hannun yyi alamar dake nuni da baya
buqatar komai wannan lkci ya maida kansa ya cigaba da abunda yake, ubaid ne ya
shiga kai tsaye ya wuce inda prince ke zaune tare da rissinar dakansa qasa ya ajiye
masa wata farar takarda akan table din dake gabansa, a hknli yasa hannu ya dauki
takarda ya soma karantawa, takardar tana dauke da sanya hannun mahaifinsa sarki
abdallah yana umartarsa yyi shirin raka sarki najash bin akhir wato sarkin dake
mulkin masarautar dulham tare da dansa prince amir da sauran tawagarsu da suka zo
taya masarautar murnar cika shekaru dari uku da sittin da kafuwa,zasu rakasu bakin
bodar da zata fitar dasu daga yankin masarautar burham don tabbatarwa sun fita
daga yankin burham lfy, qara kallon takardar yyi sosai sannan ya ajiye ya kalli
ubaid yace" kun bincika sosai babu wata alama dake nuni da sanya hannunsu a sanya
guban nan" ubaid yace" babu alamar data nuna hkn" shiru prince akbar yyi sannan ya
fito da hatiminsa yasa hannu a takardar sannan ya miqawa ubaid ya rissinar dakansa
sannan ya amshi takardar ya fita, miqewa tsaye prince akbar yyi ya nufi wurin
2sharan curtains din dake sake sun rufe window ya tsaya yana kallon farfajiya waje
hannunsa dukka a baya, 6angaren bimbii kuwa cikin izinin Allah sai gashi ta bud'e
idanunta, le6enta ya bushe sai bin ko'ina na dakin take da kallo, lkcin herbalists
din dake kula da ita ta shigo ta tarar ta bude idanu, matsowa tayi kusa da ita tana
mata sannu, daga mata kai kawai tayi sannan ta mayar da idanunta ta rufe, sunyi
mamakin bude idon nata sbd daren jiya maganin da suka bata sam be nuna ya dauki
jikin nata, su basu san cewa prince ne ya bata antidote nasa ba kuma shine ya mata
aiki don ya kashe qarfin gubar kaso sittin cikin dari,prince akbar kam beso wannan
rakiya da mahaifin nasa yasashi yyi ba, yana cike da tausayin bimbii yana ganin
idan ya tafi yabarta hk kwance cikin ciwo tamkar be kyautawa sadaukarwar da tayi.
dominsa bane amma babu yadda ya iya hk ya soma shiri, daren ranar yaso yaje duba
bimbii amma hkn be samu ba don tfyr dare zasuyi, cikin daren suka dauki hanya
dukkaninsu bisa dawakansu tare da rakiyar manyan dakarin tsaro,kwanansu daya da
yini guda suka isa boda dasu sarki najash, prince amir kuwa babu abunda daya
hadashi da prince akbar ko a hanya, dalili kuwa shine sarki abdallah shine
sanadiyyar mutuwar mahaifiyarsa, shekaru ashirin da suka gabata sarki abdallah
yakai harin bazata yankin dulham inda ta qarfin tsiya yacisu a yaqi ya kwashe
matansu ya maishesu bayi sannan ya kama mahaifiyar prince amir ya kawota
masarautarsa ya maidata kwarkwararsa, qarshen ita kuma baqin cikin hkn yyi
ajalinta, wannan shine yasanya har ranar yau gabar dake tsakanin masarautun tana
nan saidai kowa cikinsu ta bayan fage yake neman durqusar da daya musamman ma
masarautar dulham, sarki najash da dansa prince amir sun shirya zuwa wannan taron
ne kawai don cimma manufarsu,prince amir ya rantse sai ya qunsawa sarki abdallah
irin baqin cikin daya qunsa musu suma hknne yasa ya shirya poisoning din prince
akbar dayake magajin masarautar burham sbd yasan mutuwar prince akbar itace hanya
mafi sauqi ta ganin bayan sarki abdallah don duk wani buri nashi yana kan babban
prince,rashin samun nasarar hknne yake cin ransa har yanzu, bimbii kuwa cikin
hukuncin Allah sun samu sun zuqe ragowar guban dake jikinta, tana soma dawowa cikin
hayyacinta suka ce ta koma bakin aikinta, hk ta dawo dakinta bata tarar dasu israt
ba ta hau gado ta kwanta, khulood da israt kuwa suna bakin qorama suna shan wanki
har kusan yamma sannan suka nufo dawowa, suna shiga tamkar gixo suka ga bimbii
kwance bisa gado, cikin saurin suka qarasa bakin gadon suna kallonta tana bacci,
zama sukayi kusa da ita israt na mata fifita ita kuma tana bacci, sai wurin yamma
ta farka ta gansu zagaye da ita, murmushi tayi musu tare da hadasu ta rumgumesu
suma suka qara rumgumeta suna jajanta mata abunda ya faru, cikin dauriyya ta sauka
tayi wanka ta shirya ta nufi babban kitchen su khulood na biye da ita, tana shiga
duk bayin dake cikin kitchen din suka bita da kallon mamaki don basu da masaniyyar
samun sauqinta tunda ance gubar mutuwa tasha, ta6e baki sukayi, dayar cikinsu ta
kalli bimbii tace"daman baki mutu ba don mun ji ance gubar mutuwa kk sha" israt
tayi zagal tace" gata nan bata mutu ba don mutuwar ba yar aiken uban wani bace
balle ya turata ta kashe" kallon israt sukayi gbdynsu sannan suka sheqe da dariya,
dayar cikinsu tace"toh kema kawai ki maida fatarki kalar nata mn saiku saje" khuood
tayi dariya tace" wasu idan ana mgnr siffa maikyau su daina sanya baki wlh don
farar fatar ce kawai gadararsu amma ba qira da zubin zati irin na mata ba" shiru
sukayi basu sake mgn ba suka cigaba da aikinsu, israt da khulood na daga gefen
bimbii ta gama jera kayan marmari a farantai masu mutuqar kyawu ta nufi 6angaren
prince batasan cewa yyi tfy ba, kan hanyarta ta hadu da lenah ta fito daga 6angaren
prince, shigewa zatayi ta wuce abinta, lenah ta bita da kallon mamaki sai tayi
saurin shan gabanta tana huce don haushi taji na ganin bimbii ta samu lfy sbd ita
aka bawa aikin bimbii ta cigaba da hidimtawa prince kafin bimbii ta samu lfy,
kallon rainin ta yiwa bimbii tace"uban me ya tashi kafadunki baki mutu ba" kai
tsaye batare da wani shakku ba bimbii ta bata amsa tace" ubanki mn" wata irin
zabura tayi ta nufo kan bimbii da niyyar bata mari taji an riqe hannunta, juyawa
tayi a fusace sai tayi toxali da ummu sumayya tace" haba lenah meyesa kk hk ko kin
mance dokar wannan 6angaren ne, kina son a sauya miki 6angaren aiki ne" shiru tayi
sai huci take tana kallon bimbii sannan tayi gaba da sauri tabar wurin, ummu
sumayya ta kalli bimbii tace"idan 6angaren prince kk nufa toh baya nan yyi tfy"
turus bimbii tayi ta kasa gaba ta kasa baya, ita kuwa ummu sumayya ta wuce tabarta
a wurin, babban abunda ya bawa bimbii mamaki shine wato su wadannan mutane basu
dauki bawa mutum ba shiyasa dukka da abunda ya faru da ita tayi ne don kare prince
matsayinta na baiwar dake kula da hidimarsa amma yaci ace ko sau daya yaje ya duba
halin da take ciki, amma sbd kasancewarta baiwa be damu kota mutu kota rayu ba tfy
ma yyi abinsa yabarta cikin mugun yanayi, neman wani tudu tayi ta zauna tana
tunanin gd, mahaifinta da innanta yadda suke nuna mata gata tamkar zasu maidata
ciki, idan kuwa bata da lfy sun shiga damuwa kenan amma nan kuwa wasu ma ftn mutuwa
suke mata, shiru tayi tare da zabga tagumi, tunowa da tayi dasu khulood shine yasa
ta murmushi, tabbas tasan a wannan qasa data samu kanta babu dangin iya bare na
baba su khulood sun nuna mata so tsakani da Allah kuma sun fi kowa damuwa da ita da
halin da take ciki, tabbas su khulood sun fi kowa sonta cikin wannan
qasa..............

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar siya zaki tura #300 ta
wannan.acct...0100790419, Alhaji shahida nasir,union bank, saiki turomin da
screesht na payment ta wannan layin 07041195806.......
Alkalamin Bintuu ne.......
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

18

*I deeply fall in love*......the forbidden love In burham kingdom.....

Ta jima a wurin tana zaune sannan ta tashi ta qarasa 6angaren nasa, tana zuwa bayin
dake tsaron kofar suka bata hanya ta shige, tana shiga ta saki wata ajiyar zuciya
sbd qamshin sassayan qamshin daya ratsata hk kullum 6angaren nasa yake, mutum ne
shi ma'abocin son qamshi, gani tayi komai a gyare yake babu buqatar ta gyara, bude
dakin wankan tayi shima ta gansa a shirye komai a jere tsaf tun daga kan sinadaran
wanka da 2towels duk anyi hanging nasu neat, fitowa tayi ta sassauke curtains din
da suke a kame sannan ta juya ta fice, komawa tayi dakinsu sbd har yanzu lalla6a
jikinta kawai take tana aiki mai tsayi zata soma hakki da fitar da numfashi 2sama,
kwanciya tayi don qara bawa jikin nata hutu,tunawa tayi da wannan dan akwatin da
prince ya bata, sauka tayi a hnkli daga gadon taje ta bude wata drawer ta fito da
qaramin akwatin sai daukar idanu yake ta koma bakin gado ta zauna sannan ta fara
qoqarin bude dan akwatin, tana budewa taci karo da wasu kyawawan awarwaro masu
mutuqar kyau ko ba'a fada mata ba tasan gold ne, qurawa awarwaron idanu tayi tana
kallonsu batasan lkcin da murmushi ya su6uce mata ba zira awarwaron a hannunta,
tamkar an gwadata don chas suka mata daidai hannunta, sai kallon hannun nata take
tamkar wata y'ar qauye, gani tayi kamar awarwaron sun fi qarfin matsayinta amma
prince ya bata kyauta, sanya awarwaron gold ai sai jinin sarauta amma ba ita da
take baiwa ba,shiko prince awarwaron data sanya ranar a hannunta ne suka birgeshi
shiyasa yyi mata wannan kyautar,motsi ta jiyo alamun dake nuni da wani tunkaro
dakin nata, saurin zame awarwaron tayi daga hannunta ta maidasu cikin akwatin tayi
saurin tashi ta komar dashi cikin drawer din dayake ta dawo ta haye gado ta kwanta,
israt da khulood ne suka shigo, zama sukayi kusa da ita suna sake mata sannu,
murmushi ta musu kawai, wajejen yamma suka soma jin hayaniyar bayi a farfajiyan
6angaren prince akbar,bude kofa sukayi suma suka fita suka ga ashe prince ne ya
dawo, gbdy bayin dake aiki a 6angaren nasa sun jeru sunyi 2sahu suna masa barka da
dawowa lfy shi kuma yana daga tsaye a saman dogon corridorn 6angaren nasa,gefensa
daman hadiminsa ubaid ne, kallon bayin yake daya bayan daya sannan ya juya ya soma
takawa a hnkli da niyyar ya shige 6angarensa hkn yyi daidai da fitorwa su bimbii
daga dakin nasu suka shiga sahun bayin, idanunsa ne suka sauka akanta amma sai yyi
saurin shigewa 6angaren nasa duk da idanun nasa yana son qare mata kallo, ubaid ne
yyiwa bayin mgn sannan ya sallamesu kowa ya koma bakin aikinsa, bimbii wucewa tayi
babban kitchen ta hada masa abun sha na zaitun ta dauka ta nufi 6angaren nasa, tana
zuwa kofar ta bude ta shiga, samunsa tayi kishingid'e a jikin wata kujera yana duba
wasu maps, ganin shigowarta ne yasa yabar abunda yake ya dago dakansa ya zuba mata
lumsassun idanunsa yana kallonta, kallon da prince din ke mata ne yasa ta tsarguwa
sosai amma dai ta daure ta tako a hnkli ta rissinar dakanta sannan ta ajiye
farantin dake hannunta, sunkuyawa tayi ta soma tsiyaya masa ruwan zaitun din a
qaramin cup ta dauke tare da sunkuyar dakanta qasa tasa hannunta dukka ta miqa masa
cup din, saida ya jima be amsa ba kawai ya qura mata idanu yana kallonta, dago da
kanta tayi ta kalleshi idanunsu suka sarqe da juna, hannunsa ya miqa ya amshi cup
din dake hannunta ya qara kwantar dakansa a jikin kujerar yana sipping ruwan zaitun
din yana cigaba da kallonta, itace taji kunya ta sunkuyar dakanta qasa tana kallon
floor, murmushi yyi yace" ya jikin naki" dago da kanta tayi suka sake hada idanu
dashi sai kuma duk ta duburbuce sbd idanunsa dake neman kayar da ita, tace"
d...a..sauqi" be kuma cewa komai ba ya miqe yabar wurin hkn ya ankarar da ita
lkcin wankansa yyi, wucewa tayi saurin yi cikin dakin wankan ta soma hada ruwan
wanka yadda ta saba sannan ta fito, ganinsa tayi sanye da wata rigar wanka fara qal
yana zaune, tana fitowa ta rissinar dakanta a gabansa, bece mata komai ba ya miqe
ya shige, ita kuma ta tsaya daga bakin kofa, tana nan tsaye taji alarm alamar dan
sarkin na buqatarta cikin dakin wankan, shiga tayi da sauri ta tarar dashi a cikin
kwarmin wanka cikin ruwan dake turiri, saman ruwan duk kumfa, hannunta tasa a
kafadunsa ta soma masa tausa a hnkli, shi kuwa idanunsa a lumshe suke yana amsar
saqon dake shiga jikinsa ta wata siga daban dashi kadai yabarwa kansa sani,daga
mata hannu yyi tabar tausan ta soma masa wankin gashi tana gamawa ta fice ta
kyaleshi yyi wankan, tadan jima sannan ta kuma jin alarm ta koma ciki, ruwa ta debo
a wani qaramin bahun tazo gabansa ta ajiye ta kuma miqewa taje ta dauko sinadaran
wankin qafa ta zuba a ruwan qaramin bahun, sannan ta riqo kafafunsa da suke sanye
cikin takalmin wanka ta cire takalmin wankan ta sanya kafafun nasa cikin ruwa,
kallon kafafun nasa take da suke jajir dasu tamkar tumatir ga laushi da santsi
tamkar ta jarirai sai ka rantse baya taka qasa dasu, itakam bata ga abun wankewa a
wadannan kafafu ba idan badai kawai izzah da hutu ba, riqo kafar tasa tayi tamkar
wacce ta riqo gold cike da taka tsantsan ta soma wanke masa, duk abunda shi kuwa
idanunsa a rufe ma suke tamkar mai bacci har ta gama masa wankin kafar, fita tayi
tana jiran fitowarsa, ta jima da fita kafin ya fito sanye da wasu kaya masu kalar
ruwan kwai, jikinsu tamkar na mage, gashin kansa kuwa walwali kawai yake da sheqi,
takalmin kafarsa ma mai jikin mage, kai tsaye royal bed nasa ya haye ya kwanta,
ita kuwa dayake ba wata cikakkiyar lafiyar jiki ne da ita ba tuni ta soma dan jin
jiri sbd dan aikin da tayi, so kawai take ya bata izinin tfy taga yyi mata shiru
hkn ya tabbatar mata bata gama aikinta ba so yake ta sanyashi yyi bacci, a hnkli ta
qarasa kusurwar da royal bed nasa yake itama tahau gadon, yana jin ta hawo gadon ya
dago da kansa ya daga mata hannu, alamar baya buqatar tausa, dadi taji har hkn ya
bayyana a fuskarta ta soma qoqarin sauka da sauri, saurin riqo hannunta yyi ya
kalli tsakiyar idanunta yace"kimin rawa ita nakeso" kallonsa tayi tamkar kuka,
sakinta hannunta yyi ya tashi ya sauka daga kan gadon ya koma kan wata kujera,ita
kuwa bimbii bata da karfin jiki tayaya zatayi rawa, tsayawa tayi sai kuma ta fara
rawar 2kadan, shi kuma yabita da kallo tana cikin rawar kawai jiri ya debeta ta
tafi luuuu, sai ganinsa tayi kawai ya tareta da hannu guda ta fada jikinsa, kallon
fuskarsa take 2dishi shima yana kallonta, dagata yyi chak ya kwantar da ita kan
royal bed dinsa shima ya kwanta daga gefenta,kunsan kowanne qabila suna da
techniques nasu a gargajiyance, idanunta ya kalla kawai yasan jiri ne ya kwasheta,
ba zato bimbii taji kyakykyawan bakin dan sarkin bisa nata, duk da halin da take
ciki amma zuciyarta ta soma dokawa 2uku ta qwalalo manyan idanunta waje cike da
razana..........kundai son halin bimbii taku😉....

Littafin nan na siyarwa ne, idan kina da buqata ki tura #300 ta wannan
acct....0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki turomin da screesht na
payment ta whasapp through wannan layin....07041195806......

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔
Written By Bintuu Seer

19

*Forbidden love*.....the beginnig of my story.....

Bakinsa na bisa nata ga dogon hancinsa daya dora saman nata ya qureta da idanun
nasa masu sirrika 2kala yana kallon yadda duk ta gama rud'ewa, rufe idanunta tayi
qam taqi budewa saidai bata fasa jin saukar numfashinsa ba kuma be dauke bakinsa
daga kan nata ba, sun jima a hk sannan ya janye jiknsa a hnkli ya koma gefenta ya
kwanta ya rufe idanunsa shima, bimbii na jin hk ta bude idanunta ta soma qoqarin
sauka daga kan gadon, charaff, taji ya damqe hannun nata, kallon fusksrsa tayi taga
idanunsa a lumshe suke tamkar mai bacci, maida idanunta tayi kan hannunta daya
damqe da nasa, maido da qafafunta tayi ta sake hawa gadon duk da a tsorace take
amma sai ta sanya qarfin hali, hannunta ta chusa cikin sumar kansa tana hargitsawa,
bude idanunsa yyi ya sauke kan fuskarta, take gabanta ya yanke ya fad'I sbd
kallonta yake cike da wani salo mai wuyar fassaruwa kuma gashi ya qura mata idanu,
sauke numfashi yyi a hnkli sannan ya daga mata hannu alamar ta tafi, saurin sauka
tayi daga gadon tamkar zataci tuntu6e ta nufi kofa, binta yyi da kallo har ta fice
sannan ya mayar da idanunsa yyi ya rufe, bimbii kuwa har ta fice tana waiwayen
6angaren tamkar wacce tayi gamo da abun tsoro, bata wuce dakinsu ba sai ta tafi
wani wuri mara hayaniyya ta zauna sai maida numfashi take, tuno moment nasu take da
babban prince tamkar a mafarki ba gaske ba, shafa bakinta ta somayi, tace" anya
kuwa prince yana cikin hayyacinsa yau" abunda ta furta kenan a bayyane, 2kwata ita
bata kawo wai prince ya fara sonta bane don ita tana ganin hkn bamai yiwu bane ita
a suwa kuma? idan har bimbii tasan meye so toh kallon da prince ke mata kawai ya
isa ta fahimci dan sarkin ya afka finanniyar soyayyarta wanda shi kansa besan lkcin
daya fara son bimbii ba har ya zurfafa hk,prince be iya furta kalmar so ba shiyasa
yake qure bimbii da idanu, prince shi kansa da yaqi aminta cewa ya fara son baiwar
tasa sai yanzu da soyayyar qasqantacciyar baiwar tasa ke neman hanasa sukuni ba
dare ba rana, baya son kowa ya fahimci hkn sbd yasan wannan soyayyar dayake yiwa
bimbii tamkar haramtacciyar soyayya ce a wannan masarautar ta burham, baya son
sanya bimbii cikin fitina shiyasa yake iyakar qoqarinsa wurin ganin ya yakice
wannan soyayyar daga zucciyarsa saidai abu ya gagara tamkar kullum qara masa wutar
qaunar bimbii ake, miqewa tayi ta fara tfy, prince kuwa fitowa yyi wajen farfajiyar
6angaren nasa ya tsaya a saman corridor yana kallon haske farin wata, daidai lkcin
ya hango tahowa bimbii tana tafe tamkar wata mara lfy, ita sam batasan yana
hangenta ba, har ta shige dakinsu, hira ta tarar dasu khulood nayi ita ta shiga
anayi da ita amma ana hirar tana skipping, israt ta kalleta tace" bimbii ko jikin
ne" murmushi ta musu tace" aa" khulood tace" ki kwanta ki huta" ba musu ta tashi ta
hau gadon ta kwanta, prince ko har ta shige yana kallonta sannan ya juya ya shige
ciki abinsa, washegari,hk bimbii ta tashi sukuku komai cikin sanyin ciki take,
shakkar zuwa 6angaren prince take amma dolenta ta hada masa herbal tea ta dauka ta
nufi 6angaren nasa, tana shiga ta same shi a kwance ko tashi beyi ba, hkn ya bata
mamaki sosai don prince akbar mutum ne mai tsari da kuma qa'ida, baya gota lkcin
tashinsa hkma lkcin wanka da cin abincinsa duk a tsare suke, tunda ta soma masa
hidima bata ta6a shigowa da safe ta same shi a kwance ba don ba'a shiga 6angaren
nasa mutuqar be tashi daga bacci ba amma yau tayi mamaki da kofar shiga bangaren
nasa ta bude mata, ajiye farantin hannunta tayi a saman table, juyawa tayi kamar
zata fita sai kuma ta dawo ciki ta qarasa wurin royal bed din dayake kwance don
qara tabbatarwa,yanayin yadda taga kwanciyarsa ne ya haska mata kamar baya jin dadi
ne, a hnkli kamar wata mara gsky takai hannunta zata ta6a jikinsa taji koda zafi,
bude idon daya yine ya sanya taja da baya a tsorace, miqewa yyi zaune a hnkli
sannan ya miqa mata hannunsa, tsayawa tayi don bata gane nufinsa ba, saida taji
yace" ba ta6ani kkson kiyi ba" a dan razane ta dafe qirji tace'wlh Allah so nk naji
ko jikin naka da zafi don naga yanayin kwanciyar taka ne tamkar baka jin dadi kuma
na lkcin tashinka ya wuce"har ta gama magana be dauke kansa daga kanta yana
kallonta, murmushi yyi kawai sannan yace" eh, bani da lfy ko kina da maganin da
zaki iya bani ne" shiru tayi ta kasa bashi amsa shima be jira jin komai daga gareta
ba ya sauka daga gadon ya koma kan wata kujera, ranar dai kasa fahimtar prince tayi
2kwata, bata gama tsinkeyawa da lamarinsa ba sai da dare yyi, tausa yasanyata yaqi
barinta taje ko'ina har bacci ya saceta tana daga saman gadon nasa, duvet dinsa ya
rufa mata ya gyara mata kwanciya sannan shima yaja duvet din ya shiga, bimbii
baccinta take shara kawai shi kuwa kasa baccin yyi sai juye juye yake har jikinsu
ya hade, toh fa tun yana daurewa har ya bada kai, daga nan zance ya soma sauyawa,
bimbii na cikin bacci ta soma tsintar kanta a wani irin yanayi da tunda uwata ta
haifeta bata ta6a sanin makamancinsa ba, iyakar rudewa da tsantsar rikicewa hadi
da tsoro suna suka soma walatoyi da ita, kuka ta soma sosai tana roqonsa da iyakar
muryar da Allah ya hore mata amma prince yyi nisa baya jin kira zuciyarsa tayi
rinkaye, duk wani abu na kwatar kai ranar tayi cixo ne, yakushi ne, babu abunda
take kira sai don Allah kar ka yimin hk kaji qaina, banda kowa banda gata karka
rabani da martaba ta, wlh na tuba nabi Allah na bika, innalillahi wa'inna ilairrir
rajun.......wannan itace kalmar bimbii ta qarshe dana iya jiyowa, take nima
alqalamin nawa ya su6uce daga hannuna don tabbas nasan mai afkuwa ta afku
kenan..........

Manage this page pls.


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bituu Seer

20

*You have a thousand reasons to blame me*....I'm sorry dear...💕💕

Prince sam ya kasa control kanshi saida ya samu isa babbar headquarter yyi 6arna
sannan ya soma dawowa cikin hayyacinsa, fuskar bimbii ya kalla yaga tasha kuka har
ta qoshi ta koma kukan zucci, duniyar juya mata take kawai ga wani radadi da zugi
dake damunta, gefe yyi ya kwanta ya juya mata baya yana fitar da numfashi a hnkli
sannan ya lumshe idanunsa, zuciyarsa a wannan yanayin cike take da tsantsar nadama
da dana sanin abunda ya aikata, wani 6angaren na zuciyarsa ya soma tuna masa
matsayin bimbii ba kowa bace face qasqantacciyar baiwarsa, kusantar ta da yyi
alfarmar ce gareta da qarin daraja, duk bayinsa babban burinsu kenan su janye
hnklinsa ya kusancesu amma basu ta6a birgeshi ba, ita bimbii kuwa hk kawai yaji
Allah ya jarabceshi da qaunarta, bimbii ko tana daga gefe ita kuma ji take babu
wanda ta tsana a duniya sama da prince akbar, miqewa tayi zaune a hnkli taja duvet
ya rufe mata kirji sannan ta janyo doguwar rigarta ta saka ta saukar da qafafunta
qasa, tashi take son tayi abu ya gagara sai cixe le6e take, sauka tayi dakyar ta
koma qasan floor ta durqushe tare da sanya fuskarta a tsakanin cinyoyinta tana kuka
mara sauti, tashi shima yyi ya sauka ya wuce dakin wanka ya jima kafin ya fito
sanye da wasu fararen riga da wando, alamu sun nuna wanka yyi, kallon 6angaren da
take durqushe yyi ya matsa kusa da ita sosai ya tsuguna gefenta, hannunsa yasa ya
janye dogon gashinta daya zuba mata gaba ya maidashi baya, dago da kumburarrun
idanunta tayi ta ture masa hannun, murmushi yyi yace" ki tashi ki shiga ki wanke
jikinki" harararsa tayi tace" akwai alfarmar da nk nema a wurinka, don Allah ka
sanya a maidani inda kk tsinto ni" kallonta yyi tamkar beji abunda take fada ba,
tace" idan baka sanya an komai dani inda kk tsinto ni ba toh wataqila nice ajalinka
don wlh saina dauki fansar abunda kayimin sbd bani da maqiyi sama dakai" kalamanta
sun bashi mutuqar mamaki wanda suka sanya ya qura mata idanu,batare data ankara ba
kawai taji ya rumgumota ta baya tayi tayi ta tureshi ta gagara,kwantar dakansa yyi
a dokin wuyanta ya sanya bakinsa daidai kunnenta yace" kinsan me? ko yanzu kk bani
guba da hannunki zan sha,ingarman namiji kamar akbar gwara ya mutu a hannun mace
kamar ki" maganar cikin rada yake mata a kunnenta,yana gama mgnr ya sake ya koma ya
zauna akan wata kujera ta alfarma mai ruwan zinare ya qureta da idanu, yace" ko ki
shiga wanka ko na taso" bimbii na jin hkn tayi saurin afkawa dakin wankan,sama sama
tayi wankan batare data wani gasa jikinta ba ta fito, kai tsaye wurin kofa tayi da
niyyar ficewa, kofar taqi budewa,durqusa tayi a bakin taqi dawo ciki,shikam be kuma
ce mata uffan ba ya dauki wani littafi yana dubawa,washegari da sanyin safiya
bimbii ta janye zanin gadon ta fice dashi,cikin sanda ta soma satar hanyar zuwa
qorama, tana zuwa ta soma wanke zanin gadon da sauri sauri don batason kowa ya
ganta, hk ta gama ta shanya babu wanda ya ganta ta koma 6angarensu, tana shiga ta
tarar har sun fice, dadi taji sosai don daman bata son su fuskanci komai game da
abunda ya shiga tsakaninta da prince, shiga tayi ta gasa jikinta sosai da ruwan
dumi sannan ta dawo ta kwanta, wannan abu daya faru da ita yasa walwalarta da
annurinta sunyi hijira,abu kamar wasa prince ya dena ganin digon rahma a fuskar
bimbii, yau tana gama hada masa abun sha ta sanya a mazubi mai kyau ta dauka ta
nufi 6angaren nasa, baya nan yana lambunsa sai yamma ya dawo, tana shiga ta ganshi
yana rubutu jan gefe tayi bashi wuri saida ya gama sannan ya dago da kanshi yana
kallonta, qara tamke fuska tayi ta soma tsiyaya masa abun sha din, cup din ya amsa
ya soma sha batare da wata shakka ba,gani yyi tana kallonsa, yace" da matsala
ne" ...shiru tayi kawai ta juya ta fice abinta, dare na shiga ta fito a sace ta
soma sanda ta nufi wurin wannan qaton kogin da aka yada gawarsu bimbii batare da
wani tsoro ba ta afka cikin kogin kuma gashi bata iya ruwa ba.......
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

21

*If words were sufficient enough to ease out your sorrow and pain*.....I will keep
talking never ever stop it even beyond after.....💕

Prince tunda ta kawo masa wannan abun sha yaga yanayin sai yaji gabansa na fad'uwa
bayan fitar yasa ubaid ya bibiyar masa lamarin bimbii duk abunda ya gani baqo
tattare da ita ya hanzarta sanar dashi, duk 2tsirgarta akan idanun ubaid take,
lkcin daya ga fitowa da dare tana sand'a ta fice yyi saurin bin bayanta inda yaga
ta nufa ne yasa ya juya da baya ya koma yaje mugun gudu ya sanar da prince akbar,ko
rufe baki be bari yyi ba ya miqe da sauri ya fice ya haye dokinsa ya zabure shi da
mugun gudu, ubaid ko tsaye yyi yana kallon prince da mutuqar mamaki yadda yaga ya
dauki wannan baiwar tashi da muhimmanci hk,tashi guda kuma tsoro ya cikashi ya soma
tunani kar abunda ya faru shekaru dari da talatin da suka gabata ya maimata kansa
cikin masarautar burham, suma ji sukayi wurin iyaye da kakanni cewa shekaru dari da
talatin da suka gabata lkcin zamanin sarki na biyar cikin wannan masarauta ta
burham,d'ansa prince ansar ya ta6a fadawa soyayyar wata baiwa mai suna surayya yar
qasar lebanon,tunda hkn ya bayyana sarki ashraf ya zartas da hukuncin kisa ga
wannan baiwa batare da digon tausayi ba,baqin cikin mutuwar surayya shine yyi
ajalin prince ansar sbd a lkcin ya fada mugun tarko na qaunar wannan baiwa
tasa,ajiyar zuciya ubaid yyi yana fatan kar wannan tarihi ya maimata kansa cikin
masarautarsu,prince akbar kuwa dayake yana bisa doki ne tuni ya kusa cimmata amma
kafin ya qarasa har ta yarjewa kanta kawai ta afka cikin ruwan gwara ta mutu kawai
da wannan tsautsariyar rayuwar da take a duniyar da bata da kowa, fad'awarta yyi
daidai da qarasowar prince akbar wurin, sakkowa yyi daga dokin nasa ya qarasa bakin
kogin da sauri batare da wani jira ba shima ya fad'a cikin ruwan, dayake gwani ne a
ruwa da gudu yake suuuu cikin ruwan kogin yana lalibe kozai jiyota, miqa hannunsa
kawai yake,gani yyi ruwan na janta sosai dayake ruwan mai tfy ne, tana daf da
shigewa wani kwari ta qasan wata gada yyi saurin riqo hannunta ya janyota jikinsa,
matseta yyi sosai a jikinsa ya soma suuuu da ita da mugun gudu suka soma tasowa
saman ruwan kogin har suka kawo ga6a, daukanta yyi chak ya fito da ita bakin kogin
ya kwantar da ita a qasa ya soma danna cikinta da hannunsa ta soma fitar da ruwan
data sha, tari ta somayi sosai a hnkli ta soma bud'e idanunta, mamaki ne ya cikata
lkcin da tayi tozali da kyakykyawar fuskarsa ya qura mata idanun nan nasa, binsa
tayi da kallo kawai,yace" meyesa baki sanyamin guba a abun shan da kk bani ba kafin
kizo kice zaki kashe kanki" batace masa uffan ba ta dauke kanta yace" ashe kina
sona dayawa hk, kin gwammace ni kibarmin duniyar ke ki kashe kanki,toh idan kin
tafi kin barni meye amfanin tawa rayuwar kenan" quresa tayi da idanu ko zata iya
fahimta kalmomin dake fitowa daga bakinsa, qoqarin miqewa take ta kasa yasa
hannunsa ya miqar da ita, tana zama ta ture hannunsa daga jikinta ya kuma dora
hannunsa a cinyarta ta kuma sanya hannunta ta ture hannun nasa,murmushi yyi ya
kwanta a wurin dayake rairayi ya janyo cinyar tata ya dora kansa, idanunsa suna
sama yana kallon fuskarta, hannunta tasa tana qoqarin tureshi kansa daga saman
cinyarta,hannayen nata ya riqe qam cikin nasa, tayi tayi ta kwace ta kasa,ganin hk
ne yasa ta dauke kanta gefe guda,murmushi yyi ya miqe zaune ya matso da fuskarsa
saitin nata kamar ze goga dogon hancinsa da nata ya fara mata mgn da rad'a yana
fada wasu kalmomi da nikaina ban san me yake fada mata ba sbd mgn yake wanda ita
kadai take iya jin abunda yake cewa, gani nayi ta kwalalo idanu waje tana kallonsa
cike da mamaki, matsar da fuskarsa yyi tare da jan hancinta ya mayar dakansa saman
cinyarta ya kwantar tare da folding hannayensa dukka a saman qirjinsa ya rufe
idanunsa, kallonsa tayi tace" wani ze iya ganinka hk fa ka tashi" shiru ya mata
yyi kamar beji me take fadi ba,saida ta kuma maimatawa ya bude idonsa yana kallon
fuskarta yace" idan kina son na tashi ki gyaramin gashin kaina ya hargitse" kallon
gashin nasa tayi taga sai digar ruwa yake dayake kuma gashin nasa dogo ne, tace"
toh ka tashi zaune saina gyara mk" miqewa yyi zaune yayi folding kafafunsa ita kuma
ta miqe tsaye kafin ya ankara ta arce da gudu tana daga masa hannu alamar bye bye,
murmushi kawai yyi ya taho a hnkli yahau dokinsa yabi bayanta, hk suka qarasa
6angaren nasu saida ya tabbatar ta shige dakinsu sannan yasa ubaid ganin wurin,shi
kuma ya wuce 6angarensa yyi saurin cire wannan kayan, israt da khulood kuwa har
sunyi bacci don su da suka ga basu ganta ba sun dauko tana 6angaren prince ne,
washegari, tun prince na jiran bimbii har ya hkr taqi zuwa 6angaren nasa ta wuce
tabi su israt debo kayan marmari,tasan lkcin wankansa yyi amma ta share ta cigaba
da huldar gabanta, shi kuwa prince sanye yake da wata rigar wanka fara sol, ya
zauna yana jiran bimbii,lkci ya qure sosai amma bimbii bata zo ba, kwantar dakansa
kawai yyi a jikin kujerar dayake zaune ya lumshe idanu, ita kuwa dawowarsu kenan ta
kalli 6angaren prince, kamar zata shige abinta sai kuma ta dawo da baya ta wuce
ciki, tana isa masu tsaron wurin suka bata hanya ta shige,tana shiga ta duba ko'ina
bata ganshi ba tana shirin fice ta hangoshi tsaye wurin windows din nan ya harde
hannunsa dukka a bayansa ya qurawa waje idanu tun dawowarsu dasu israt yake
hangenta, yanzun ma yaji motsin shigowarta kawai juyowa ne beyi ba, matsawa tayi
kusa dashi ta rissinar dakai,juyowa yyi yana kallonta fuskarsa babu yabo babu
fallasa sannan ya qetarata ya wuce ya zauna ya dora kafarsa daya kan daya yana
kallonta yace" na miki afuwan gocewa aikinki da kkyi yau amma idan kk sake maimata
hkn toh zan dauki akan wadanda suke janyeki daga bakin aikin ki" gabanta ne ya fadi
don ba qaramin tausayin su khulood takeyi baza ta6a yarda wani abu mara kyau ya
same su silarta ba,durqusawa tayi akan guiwowinta gabansa tace" kayi hkr bazan sake
ba amma kar ka cutar da yan uwana" kallonta yyi sai kuma ya dauke kanshi gefe guda
yace" idan na dauki mataki akansu daman ai shine daidai tunda suke saki rashin jin
mgn, sune silar dayasa kk tura kanki cikin rikici har da zuwa sace gawa a kogi" a
mutuqar razane ta dago kanta tana kallonshi cike da mamakin yadda akayi babban
prince yasan wannan sirrin nasu, harararta yadanyi daidai lkcin kuma ubaid ya
shigo, rissinar dakansa yyi ya ajiyewa prince wani dogon akwati a gabansa, kallonta
yyi yace" baki san aikinki bane koh kuma saina krt miki" wata irin zabura tayi da
sauri ta miqe ta nufi cikin dakin wankan nan ta soma hada masa ruwan wanka cikin
kwarmin wanka, shi kuwa prince da gangan ya mata hk yasan tana son su khulood sosai
shiyass yake mata wannan barazanar, ita har yau batasan shine dakansa ya cecesu
lkcin da suka tafi kogi ganin gawar layla ba,shine dakansa ya dauke hnklin bayin da
suke shirin kamasu ya basu damar gudu shiyasa ya rufe fuskarsa da baqin kyalle,
gani yyi taurin kan bimbii yyi yawa gata da kafiya kamar shi,dawowa da kallonsa yyi
kan ubaid suka soma tattaunawa game da sabuwar takobin da mahaifinsa ya aiko masa
dashi, bude masa akwatin ubaid yyi shi kuma ya fito da takobin sai sheqi take da
walwali,murmushi yyi sosai sannan ya mayar da ita cikin akwatin,dagawa ubaid hannu
yyi shi kuma ya sunkuyar dakanshi qasa sannan ya fice,komar da kallonsa yyi wurin
dakin wankan yana jiran fitowarta, fitows tazo gabansa ta rissinar dakanta qasa
alamar komai ya kammala, batayi saurin dagowa dakanta ba don tasan tunda bataji
motsin miiqewarsa ba toh tabbas ita yake kallo,a zucci tace" haba mutum sai kallon
tsiya kamar wani maye" tashi yyi yaxo ya wuceta ya shige dakin wankan, ranar dai
kam ta jima tana masa tausa cikin dakin wankan kafin ya kammala wanka ya fito,
kwanciya yyi kan gadonsa ya lumshe idanu,tasan sarai tausa yakeso kafin yyi bacci
don shi baya iya bacci hk sai an masa dabara, bimbii kam ita yanzu kam tana tsayuwa
ne tare da bata da yalwatacciyar tazara tsakaninta da royal bed na prince, tana
mugun shakkar hawa gadon nan yanxu, jin taqi hayowa sai abun ya bashi dariya har ya
murmusa sbd ya fahimci abunda take tsoro, daga mata hannu yyi tayi saurin sake masa
curtains din data rufe kusurwar da gadonsa ke ciki ta wuce ta fice,shi kuma yabita
da kallo yasan abunda tafi so kenan shiyasa ya bata umarnin tfy, washegari bimbii
tayi masa rakiya wani taro da sarauniiya dakanta ta shirya a 6angarenta na yanta
wasu bayi, prince baya taba sake bimbii ta 6acewa ganinsa duk inda tayi yana binta
da kallo a sace, sarauniyya mar'atussaliha kuwa uwace wacce tasan halayyar dan nata
ciki da waje, ta lura da kallon dayake bin bimbii dashi a sace, kiran bimbii tayi
tazo gabanta ta rissinar dakai sannan ta maida dubanta kan kwayar idanun prince
dake kallon bimbii nan take ta warware kanta komai tace" bimbii ta tafi, bimbii ta
dawo inda take ta tsaya,sarauniyya mar'atussaliha ta kalli prince da murmushi a
fuskarta sosai tace" idan na nemi alfarma a wurinka zakamin kai tsaye" kallonta
mahaifiyar tasa yyi cike da mamaki yace" umarninki kawai nk jira na aiwatar" fadada
murmushinta tayi tace" toh ina son ka bani wannan baiwar taka" saurin dago da
idanunsa yyi yana kallonta, murmushi tayi masa sannan tace" kar damu saika maida
tsohuwar baiwarka lenah ko ka sake za6en wata cikin bayi na" qaqalo murmushi yyi ya
kalleta yace" meyesa kkson wannan baiwar kawai" itama murmushi tayi tace"kallonta
kawai nayi naji ta kwantamin daka ganin tana da zuciya mai kyau" shiru yyi ssnnan
ya dago dakansa yace" shikenan ranki ya dade na baki ita saidai......." sai kuma
yyi shiru tace" kayi magana dana, fadi abunda kkson fada" murmushi yyi yace" aa,
babu komai"ranar dai bimbii ta tattara ta koma 6angaren sarauniyya tabar 6angaren
babban prince, wannan abu yyiwa mutane da dama dadi ban dasu israt da basu ji dadin
hkn ba,itako bimbii abu yyi mata dadi sosai don hkn yafi nono fari a wurinta, wasu
bayin har mamaki suke da suka ga bimbii na nuna farin ciki, lenah itama 6angaren
abu yyi mata haske ta koma hidimtawa prince akbar, 6angaren prince kuwa abun babu
kyau..........
Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, zaki turomin da screenshrt na
payment dinki a whatsapp ta wannan layi...07041195806..

Alkalamin Bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

22

*Miss each movement spend with you* you are my medicine.......💕💕

Bangaren sarauniyya mar'atussaliha yana da girma sosai kuma suma bayin dake
6angaren nata wajensu yana da yalwa sosai,bimbii bata samu daki ita kadai ba yadda
take a 6angaren prince,hadata akayi da wasu bayi su hudu ita ta zama ta biyar,
neman wuri tayi daga can gefen dakin ta ajiye kayanta, yanayin bayin data hadu dasu
anan ba kamar su khulood bane ta fahimci akwai tsugumi da baqin ciki a lamarinsu
sbd tunda ta aka kawota dakin ba wacce ta mata kallon arziki,ummu nana ta sanar da
ita aikinta shine baiwa furannin dake 6angaren gbdy ruwa safe da yamma sannan da
tatso nonon raqumi, washegari da sanyin safiya bimbii ta tashi ta bawa furanni ruwa
sannan ta dauki kwarya ta tafi tatso nonon raqumi anan suka hadu dasu khulood suna
ganinta suka taho da gudu suka rumgumeta, israt tace" bimbii daman arzikinki muke
ci jiya kina tfy lenah ta dawo dakin tayi mana korar wulaqanci muka koma dakin
hadaka yanzu mu takwas ne a dakin da muke" murmushi bimbii tayi ta janyo hannun
israt tace" karki damu komai na duniya dan hkr ne wani lkcin baka cimma kyakykyawar
qaddararka kai tsaye har saika qetare'''' manyan qalubale na rayuwa" murmushi
sukayi gbdy, khulood tace" wannan hk yake" sunkuyawa sukayi suka soma tsatsar
nonon raqumi duk suka cika kwaryoyinsu sannan suka dora bisa kawunansu suna tafe
suna hira har suka iso hanyar da zasu rabu su khulood suka wuce 6angarensu itama ta
wuce nata 6angaren, prince akbar kuwa ranar kasa runtsawa yyi sai tunani yake
dalilin dayasa sarauniyya ta nemi ya bata bimbii har yanzu ya kasa fahimtar
manufarta saidai yana da tabbaci tana da manufa nayin hkn don mace ce mai mutuqar
hange da fahimtar lamura kuma gata da tarin hikima, kiran ubaid yyi ya shigo ya
rissinar dakai a gabansa cike da ladabi,dago dakansa yyi dake jingine bisa wata
tattausan kujera ta alfarma ya kalli ubaid dakansa ke sunkuye, yace" kana da wata
fahimta kan manufar sarauniyya na amsar wannan baiwa" shiru ubaid yyi na y'an
daqiqai yana tunani sannan ya dago dakansa ya kalli babban prince yace" ranka ya
dade bani da wata fahimta kan hkn saidai abunda ya bani mamaki shine me yasa
sarauniyya ta kira bimbii har gabanta sannan tace ta tafi batare data furta komai
ba sannan ta maida dubanta kan idaniyarka, abunda na fahima anan shine akwai wani
sirri data gani cikin kwayar idanunka bisa al'muran wannan baiwa taka, ka gafarceni
ranka ya dade da wannan hasashe nawa" shiru prince yyi domin amsar ubaid kadai ta
haska masa manufar sarauniyya mar'atussaliha,wato ta fahimci sirrin zuciyar prince
game da bimbii da take qasqantacciyar baiwarsa, kallon da prince ke yiwa bimbii
kawai ya ankarar da sarauniyya cewa d'an nata yana da wani feeling kan wannan
baiwa, abunda yasata aikata hkn shine tana gudun faruwar wani babban al'amari zuwa
gaba mutuqar bimbii ta cigaba da kasancewa da prince, hkn da tayi na amshe bimbii
daga wurinsa tana tunanin shine mafita, cikin kwana biyu kacal prince ya gama
jigatuwa da kewar bimbii, hknne yasa ya buqaci ubaid ya kawo masa su israt yana son
ganinsu, ubaid yaje ya taho dasu israt da jikinsu har rawa yake sbd tsorota da
sukayi na jin wai babban prince nason ganinsu sai sukayi zaton ko wani laifin
sukayi, suna shiga bangaren prince suka same shi a zaune kan wata kujerar mai ruwan
zinare yana rubuta wata wasiqa,zubewa sukayi bisa guiwowinsu duk suka rissinar da
kawunansu, saida ya dauki dogon lkci sannan ya dago da kansa ya kallesu, miqawa
khulood wannan takarda yyi yace" gashi ina son ku miqa wannan takardar ga
yar'uwarku, idan har kk bari wani yaji ko yaga wannan takarda toh hukunci mai
tsauri na tanadar muku" qara sunkuyar dakai sukayi, khulood tasa hannu biyu ta
amshi takardar da take nannad'e cikin wani siririn abu tamkar alqalami, yana miqa
ya daga musu hannu suka miqe da sauri suka fice, ranar basu hadu da bimbii ba don
hk da dare suka fita suka nufi bangaren sarauniyya, masu tsaron 6angaren sarauniyya
ba kowanne bawa suke bari ya shiga 6angaren ba saidai idan a wurin kk aiki ko kuma
kana hidimtawa daya daga cikin iyalan sarki,hk suka hana su khulood shiga 6angaren,
qin tfy sukayi suka koma gefe suna ta tsaye ko zasu gano fitowar bimbii amma shiru,
wani wuri suka samu suka tona rami suka binne takardar sbd basu son su koma
6angarensu da ita tsautsayi yasa wani ya gani, su kansu basu san meke rubuce cikin
wasiqar ba, washegari da sanyin sfy suka fito suka nufi wurin da suka binne wasiqar
suka tono wurin suka dauki wasiqar suka nufi 6angaren sarauniyya suka tsaya bakin
kofa suna jiran fitowar bimbii, ita kuwa bimbii tana ciki ta bawa furanni ruwa
tana gamawa ta dauki kwaryarta ta fito don tatso nonon raqumi, tana fitowa ta miqe
hanya sai kawai ganinsu khulood tayi sun sha gabanta dukkaninsu a dan rikice,
kallonsu tayi da mamaki tace"lfy kk kuwa" basu bata amsa ba sai 2waige suke kamar
wasu marasa gsky saida suka tabbatar babu kowa wurin sannan israt ta sanya hannu
cikin rigarta ta ciro saqon babban prince ta bawa bimbii, sannan suka sanar da ita
gargadin daya musu,shiru bimbii tayi tana kallon wasiqar, khulood ta sake waigawa
taga ba kowa ta matso kusa da bimbii tace" kiyi sauri ki 6oye ki tabbatar babu
wanda yaga wannan saqo wurinki" sauri bimbii tayi ta chusa wasiqar cikin rigarta
sannan ta rabu dasu khulood don su ranar qorama suka nufa, ranar bata samu lkcin
kanta ba bare ta bud'a wasiqar taga abunda ta qunsa sai da dare data koma dakinsu
ta saci jiki ta fito farfajiyar 6angaren ta nemi wurin da babu yalwar kilmawar bayi
ta zauna gindin wata bishiyar dabino ta ciro wannan wasiqa ta bud'e, yyi rubutun ne
da haruffan larabci, dayake itama tasan baqi hk ta soma karanta wasiqa, gabanta ne
ya soma dokawa 2gudu lkcin data soma ganin kalmomin da prince yyi amfani dasu wurin
rubutun wasiqar, ba wasu kalmomi bane sai tsantsar yabo da kuma mutunta darensu na
farko, yyi mata gdy da kyautar budurcin da tayi masa sannan qarshen wasiqar kalmomi
ne dake bayyana kewarta daya yyi cikin wadannan kwanaki sai kuma wasu zafafa
kalmomi na soyayya daya soma furta mata karo na farko,bata qarashe karanta wasiqar
ba tayi saurin rufe takardar jikinta na rawa ta dafe qirjinta dayake bugawa tamkar
ze fashe sbd tsananin tsoro da razana da tayi, kallon takardar take tana tantaman
anya prince ne dakansa ya rubuta wannan wasiqa, addu'a ta somayi cikin ranta Allah
yasa su israt basu bud'a wannan wasiqar ba, duqunqune takardar tayi ta
kutsirtsirata mitsi mitsi ta din ga tfy da nisa tana cillar da kowanne 6angare na
takarda wuri daban daban sbd tsantsar tsaro, jiki a sanyaye ta koma dakin nasu ta
tarar da abokan zaman dakin nata suna hirarsu ko kallonta ba wacce tayi itama bata
sanya musu baki ba sbd akwai abu mafi girma dake dawainiyya da ruhi hade da gangar
jikinta don hk bata da lkcinsu, samun wuri tayi ta kwanta, tana rufe idanunta
kyakykyawar fuskar prince akbar zata soma mata gizo, miqewa tayi da sauri ta soma
mutsitstsike idanunta,kunnuwanta taji tamkar muryarsa yana furta mata wadannan
zafafan kalmomi da suka rudata suka gigita tunaninta baki daya,hannu tasa ta soma
toshe kunnuwanta, duk bayin dake dakin suka soma kallonta suna tunanin ko ta samu
matsalar kwakwalwa ne,6angaren prince kuwa ya rasa kansa sosai, be ta6a tunanin
tarkon son wata diya mace zeyi masa irin wannan kamun ba amma sai gashi dare daya
ya fada soyayyar qasqantacciya baiwa baqar fata da sun bambamta a komai, tun daga
kan nahiya, asali,tushe har ma da kalar fata,riqe kansa yyi kawai ya rasa meke
faruwa dashi, jin zuciyarsa yake tamkar zata zage sbd wani irin bugawa da take da
qarfi, ga kewar bimbii dake azabtar da gangar jikinsa har ma da ruhinsa,miqewa yyi
da sauri ya kira ubaid, kallon ubaid yyi yace" ina son ganin bimbii a wannan dare
kasan duk yadda kayi ka kawo min ita" kallonsa ubaid yyi a nutse cike da girmamawa
yace"an gama ranka ya dade" fita yyi da sauri, israt ya samu cikin sirri ya buqaci
taje 6angaren sarauniyya ta fito da bimbii, sanar dashi tayi bata da damar shiga
yankin sarauniya matsayinta na qasqantacciyar baiwa, wani qaramin gate pass ya ciro
daga aljihunsa ya bata yace"ki nunawa bayin dake tsaron kofar wannan zasu bude miki
kofa ki shiga" amsar gate pass din israt tayi ta tafi da sauri ta nufi yankin
sarauniya tana zuwa ta nunawa masu tsaron kofa wannan gate pass suka bata hanya ta
shige, bata sha wahala ba ta gane dakin da bimbii take, tana shiga dakin taga kusan
dukkanin bayin dake dakin sunyi bacci sai bimbii kawai dake zaune ita kadai kamar
wata mara gata, bimbii kamar ance ta kalli kofa taga israt tsaye tana
kallonta,tasowa tayi da sauri tazo wurin israt, jan hannunta israt tayi suka fice
daga dakin, israt ta kalleta tace" meke damunki hk bimbii yanayinki ya nuna kina
tattare da damuwa" bimbii tayi shiru sai kuma ta kalli israt tace" babu komai"
kallonta israt tayi kadan sannan ta kawar da waccar mgnr tace" babban hadimin
babban prince ubaid shike son ganinki yanzu" dafe kirji bimbii tayi ta kalli israt
tace" israt me kk zaton zemin" israt tace" gsky ban da sani kan hkn amma ga
dukkanin alamu prince ne dakansa ke buqatar ganinki" take gaban bimbii ya yanke ya
fadi, ta soma ja da baya, israt tsayawa tayi tana kallonta cike da mamaki,hannunta
tasa ta riqo hannunta tace" akwai abunda ke faruwa ne tsakaninki da prince" girgixa
kai tayi da sauri alamar aa, jan hannunta israt tayi suka soma tfy har suka fice
daga yankin sarauniyya suka din ga wuce kusurwa kusurwa har suka qarasa inda ubaid
ke jiransu, yana ganinsu yyi murmushi yace israt ta tafi sannan ya kalli bimbii
yace" babban prince nada buqatar ganinki" juyawa yyi ita kuma ta soma bin bayansa
cike da sanyin ciki kamar kaxar da kwai ya fashewa a ciki, gabanta kuma sai cigaba
da faduwa yake har suka qarasa 6angaren prince, suna shiga suka tarar dashi zaune
lenah na tsiyaya masa green tea, shigowarsu ne yasa shi dago da lumsassun idanunsa
ya saukesu kan bimbii,lenah kuwa tana gama zuba masa tea din ta sunkuyar dakanta
qasa sannan taja baya tana jira umarninsa,daga mata hannu yyi alamar ta
tafi,rissinar dakanta ta sakeyi sannan ta juya da niyyar fita, mamki. tayi sosai
na ganin bimbii tsaye a gefe,wata uwar harara ta aika mata sannan ta fita ranta a
mugun 6ace, ubaid yana shigo da bimbii shima ya rissinar dakai,prince ya daga masa
hannu ya fice, suna fita dukka ya rage sai bimbii kawai, yana daga zaune idanunsa
na kanta ya kasa dauke kai,ita kuma ta kasa gaba ta kasa baya tana tsaye kawai wuri
daya, sun dade a hk kanta na qasa ya taso a hnkli ya tako har inda take, matsowa
yyi sosai tamkar zasu manne, ita kuwa take zuciyarta ta tsananta dokawa ta soma
neman matsawa amma sai yyi saurin take mata kafa, zafi taji sosai ta dago dakanta
tana kallonshi, dage mata gira daya yyi, cikin tsantsar dabara da hikima yyi mata
jan bazata ta afko kirjinsa ya hannunsa duka ya mata daurin kazar kuku ta yadda
bata da damar raba jikinta da nashi, kallonsa take cike da tsoro saita fara masa
kuka, murmushi yyi ya dora fuskarsa saman nata ya rufe idanu itama ta rufe idanu
suna sauraron bugawar zuciyoyinsu dake bugawa a tare kuma da qarfi, hannunsa ya
dora kan kirjinta sannan ya kamo hannunta ya dora kan nashi qirjin, yace" wannan
kawai ya tabbatar miki prince bazai iya rayuwa babu ke kusa dashi hkma kema bazaki
rayuwa babu ni ba sbd bugawar zuciyarmu daya" shiru tayi tana jinsa amma taqi bude
idanu gashi jikinta ya mutu murus bata da qarfin aiwatar da komai, sunkuyawa yyi
yasa hannu ya cire mata wannan tsohon zoben dake yatsan hannunta na dama ya sanya
mata wani na danyar azurfa daidai hannunta, jin jikinsa yake wani iri ya tabbatar
idan har ya cigaba da kasance da bimbii toh ze sake tabargaza, janye jikinsa yyi a
hnkli ya juya mata baya, daga mata hannu yyi ya bata izinin tfy batare daya juyo ya
kalleta ba don baya son ta fahimci halin dayake ciki, juyawa tayi ta soma tafiya
zata fita sai kuma ta jiyo ta dawo da baya, muryarta kawai yaji tace" idan za'a
fara soyayya dole sai zuciyoyi biyu sun aminta da juna don cikin soyayya babu izzah
bare nuna fin qarfi, idan daka shawarceni ko ka nemi amincewa ta zan fada mk cewa
akwai wanda nkso, na bashi zuciyata tunkan yanzu kuma har gobe shi nk so, ka huta
lfy" jin maganganunta yyi tamkar saukar ruwan dalma don prince mutum ne mai
tsananin kishi musamman ga abunda yakeso, juyawa tayi zata tafi kawai taji ya damqo
hannunta, idanunsa jajir dasu yace" soyayyata tana da tsada sosai nikaina na rasa
yadda akayi qasqantacciyar baiwa kamarki ta samu zuciyata a araha da rahusa dare
daya, toh ki sani duk wanda zaki so a baya na yake ko kin manta nina amshi
budurcinki ba wani ba, ki sani soyayyarki itace babban kuskuren dana aikata ga
dukkanin wani jini na sarautar burham, wannan irin soyayya ita ake kira
haramtacciya a ilahirin wannan masarauta......ki amshi soyayyata ko karki amsa
wannan za6in ya rage naki amma ina qara tuna miki ki kwana kullum cikin tuna
matsayinki gareni ba kowa bace illah qasqantacciya baiwa mai mini hidima, ina da
cikakken iko akanki" kallonsa bimbii tayi sannan tayi murmushi tace" idan da zaka
zare kalmar so kabarni matsayin qasqantacciyar baiwa hkn shine farin ciki na" tana
gama fadar hk ta juya ta fice daga sashin nasa tabarshi zaune ya dafe kansa dake
juya masa, gani yake idan har bimbii taqi aminta da soyayyarshi zuciyarshi zata iya
tarwatsewa........babbar baiwa ga sarauniya mar'atussaliha kuwa ummu nana tuni ta
miqa zancen zuwan bimbii ga babban prince wurin sarauniya, shiru sauraniya tayi
sannan ta dago dakanta ta kalli ummu nana dakanta ke sunkuye tace" ina son ganin
azeez" jikin ummu nana har rawa yake ta fita don kiran azeez....azeez shine sarkin
hukuncin dauri...............

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan
acct....0100790419,alhaji shahida nasir,union bank....saiki tura screesht ta
whatsapp a wannan layin 07041195806......

Alkalamin Bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

23

*Believe the power of love which make a king to be a servant and a servant to be
the king*............I miss you like crazy......💕💕

Tana hakimce a wata kujerar ta alfarma cikin fadarta, ummu nana suka shigo tare da
azeez sanye yake da baqaqen kaya,fuskar nan tasa babu yalwar fara'a duk suka
rissinar dakansu a gabanta suna jiran umarninta, kallon fuskar azeez tayi yyi
saurin dago da kansa,tace" ina son ka sace babbar baiwar prince dake hidima a
6angaren nan ka miqata babban kurku, bani son kowa yasan tana wannan kurku,sai a
yad'a cewa tsohuwar baiwa ga prince ta gudu, wannan sirri ne tsakani na daku kawai
bani son kowa ya samu wannan labari cikin wannan masarauta sbd wannan itace hanyar
dazan ita ku6utar da prince daga fadawa fushin mahaifinsa sannan na dakatar da
faruwar wani al'amari mai girma cikin wannan masarauta" gbdy suka sake rissinar da
kawunansu alamar yin biyayyar ga umarnin sarauniya, daga musu hannu tayi suka juya
suka fice daga fadar nata,dare nayi bimbii ta fito shan iskarta, batason zaman
wannan daki sbd duk bayin dake suke zaune daki daya da ita basu kulata shiyssa duk
dare take fita shan iska,tayi nesa sosai da farfajiyar 6angaren nasu ta nemi wani
qaramin tudu ta zauna ta tsirawa wannan zobe da prince akbar ya bata idanu, motsi
taji a bayanta tamkar motsin mutum, miqewa tayi da sauri cike da tsoro sbd wurin
babu yalwar jama'a tana waigawa taji an toshe mata baki, tuni ta fadi a wurin suka
dauketa suka sanyata cikin wani keken doki, hk suka din ga tfy har suka isa babban
kurku, masu tsaron kofar basu san wacce bimbii sudai suna ganin azeez suka bude
musu katuwar kofar kurkun suka shige da bimbii, sun samar mata da daki na qarshe a
jerin dakunan dake kurkun, dakin tsagaye yake da manya qarafa masu kauri yadda babu
wani mahalukin dazai iya 6allasu, kasan kurkun busassun ciyayi ne aka zuba,hk suka
shigar da ita ciki suka watsata tamkar wata shara, har lkcin bimbii bata dawo cikin
hayyacinta batasan abunda ke faruwa da rayuwarta ba saida sanyin asubahi ya soma
ratsata ta bude idanunta a hnkli tana qarewa inda ta samu kanta kallo,wasu hawaye
ne masu dumi suka soma ambaliya a fuskarta ta tashi zaune a hnkli tana cigaba da
kallon inda ta kuma tsintar kanta, wahegari, bayin dake kwana tare da ita suka ga
basu tashi da ita, basu kawo komai sai sukayi zaton tashi wuri tayi ta fice bakin
aikiinta, jita jita ne ya soma yawo cikin wannan masarauta cewa daya daga cikin
bayi dake hidima a 6angaren sarauniya ta samu nasarar gudu,su israt kuwa basu ta6a
kawowa cewa bimbii ce ta tsere ba, ranar dai basu ganta, yamma nayi suka gama
2aikacensu suka koma dakin da suke suna shirin kwanciya suka ji ragowar bayin dake
dakin suna hirar, israt ce ta juya da sauri ta kalli daya daga cikin bayin dake
hira tace" don Allah wacce baiwa ce ta gudu" kallonta dayar tayi tace" tsohuwar
babbar baiwar da prince yabarma sarauniya mn" daya daga cikinsu tace" ai kamar ma
ina yawan ganinku tare da ita a bakin qorama" israt da khulood duk suka kalli juna
a rikice, miqewa israt tayi da sauri tayi hanyar waje cike da rudani, khulood ma ta
miqe da sauri tabi bayanta, saurin riqo hannu israt tayi da taga ta nufi 6angaren
prince sbd ta lura bata cikin hnklinta, juyowa israt tayi a fusace ta fizge hannun
daga riqon da khulood tayi mata sai kuma ta tsaya chak ta juyo ta kalli khulood
tace" khulood wannan abu baki tunanin akwai sarqaqiya cikinsa sbd nasan bimbii ba
zata ta6a tunanin gudu ba, anya babban prince baida hannu a wannan abu kuwa sbd na
lura kamar ya takura mata dayawa" khuloo ta jata suka samu wani wuri suka zauna,
kallonta israt tayi tace" nikam a yadda nk gani kamar akwai wani 6oyayyen al'amari
tsakanin babban prince da kuma bimbii kamar hkn shine ze sata tayi yunqurin gudu"
israt tayi ajiyar zuciya sannan tace" tabbas wannan hasashe naki hkne duk da bani
da masaniya amma akwai abunda ke tsakanin prince da bimbii sbd ina yawan ganin
damuwa tattare da ita, bani son matsa mata da tmby ne kawai" khulood tace" mu
tayata da addu'a kawai kar su samu damar kamata" jinjina kai israt tayi alamun nuna
gamsuwa da abunda khulood ta fada, 6angaren prince kuwa fitowarsa daga wanka kenan
yana sanye da wasu kaya masu mutuqar taushi, zama yyi a wata kujera lenah ta matso
ta soma tsiyaya mata ginger tea, daukan cup din tayi ta miqa masa da hannu biyu
tare da rissinar dakanta qasa, amsar cup din yyi ya soma sipping a hnkli yana
tunanin bimbii, zagayawa tayi ta bayanahi ta soma masa tausa a hnkli, ubaid ne ya
shigo da sauri ya tsaye gaban prince tare da rissinar dakansa qasa, kallon ubaid
yyi yasan yana tafe da wani labari mai muhimmanci sbd fuskarsa ta nuna hkn, dagawa
lenah hannu yyi ta dakata da masa tausan ta sunkuyar dakanta qasa sannan sum sum
ta wuce ta fice, ubaid ne ya matso da fuskarsa daidai kunnen prince ya rada masa
wani abu, wata irin zabura prince yyi ya miqe tsaye tare da dire qaramin cup din
dake hannunsa saman small table din dake gabansa, shi kansa ubaid cika yyi da
mamakin yanayin da prince ya nuna,batare daya sake kallon inda ubaid yake ba yyi
hanyar waje da sauri ya fice, ubaid ya rufa masa baya, hk suka isa 6angaren
sarauniya mar'atussali, saida suka din qetare kusurwa kusurwa suka samu shiga cikin
fadarta, ubaid yaja ya tsaya a kofa shi kuwa ko neman iso beyi ba ya afka ciki,
bayi ne jere ta 6angaren dama da hagunta wasu cikinsu na mata fifita, ita kuma tayi
ado na manya gwalagwalai tunda daga wuyanta har kunnuwanta da kuma hannayenta,
batayi mamakin ganinsa ba don daman abunda take jira kenan guduwar bimbii yakai
kunnensa, qarewa suturar dake jikinsa kallo take sbd gani tayi kayan bacci ne ma
sanye jikinsa hkn ya kuma tabbatar mata da gskyr abunda ta gani cikin kwayar
idanunsa, dagawa bayin dake tsatstsaye tayi hannu suka soma ficewa,zuba masa idanu
tayi tana sauraron abunda ya kawoshi gareta,neman wurin yyi kan kyakykyawan turkish
center carpet din dake malale ta cikin wata kusurwa ya harde kafafunsa, tasowa tayi
itama a hnkli ta soma sakkowa daga tudun da kujerar alfarma da take zaune akai ta
shiga wannan kusurwa ta zauna bisa wata lumshashshiya kujera mara tudu tana kallon
prince, kallon shima yyi sannan ya soma mgn yace" ranki ya dade wani labari nakeji
na guduwar baiwar dana bar miki shin wannan zance gskya ne" murmushi tayi sannan
tace" tabbas hk abun yake saidai dakaran tsaro na nan suna bincike kan guduwar nata
sbd an jima ba'a samu wani bawa da laifin gudu ba" shiru yyi batare daya kuma furta
komai ba, tunani kawai yake abunda yasanya bimbii gudu tabarshi da dakon so,
nutsawa cikin tunani yyi sai yake zaton ko furta mata kalmo so da yyine ya tsorata
ta yasa ta gudu daga masarautar,dafashi sarauniyya tayi fuskarta dauke da murmushi
tace" yakai wannan prince ka sanar da mahaifiyarka ma'anar wannan damuwa data
bayyana qarara a fuskarka dalilin guduwar wannan qasqantacciyar baiwa" dago da
idanunsa yyi da bbu komai cikinsu sai tsananin tashin hnkli ya qure mahaifiyar tasa
da idanu, ita kanta ta tsorata dashi batayi tunanin soyayyar baiwar ta masa wannan
illar ba, kunsan tsakanin uwa da d'a take wani tausayinsa ya shigeta, bece mata
uffan ba ya miqe ta dago idanunta tana kallonsa har ya fice, ubaid na ganin fitowar
tasa ya rufa masa baya don shi ko kallon inda ubaid ke tsaye beyi ba ya wuce
abinsa, yana komawa 6angaren nasa ya janyo farin dokinsa ya haye ya zabureshi da
mugun gudu shima ubaid yahau nasa ya rufa masa baya, ba ko'ina suka tosa ba sai
filin sukuwar dokin da suka tsinci bimbii, tsayawa yyi yana kallon hanyoyin da suka
rabu gida biyu, kallon hanyar da tayi damansa yyi batare da wata shakka ba ya
dunfari hanyar bisa dokinsa mai tsalelen gudu,hk yyita zabga gudu bisa kan namijin
dokinsa babban hadiminsa na take masa baya har suka soma shiga cikin gari, hknne
yasa yaja linzamin dokinsa ya tsaya yana qarewa ko'ina kallo, juwaya kawai yyi
dakan dokinsa ya koma baya, suna zuwa daidai inda ya ta6a bangaje bimbii da doki ya
tsayar dakan dokin nasa sannan ya diro yana qarewa wurin kallo, ranar sai tsakar
dare suka koma masarauta ya shige 6angarensa yace" kar abar kowa ya shigo masa
baida buqatar ganin kowa" take masu tsaron kofar suka rufe kofar shiga 6angaren
nasa, yana shiga ya nemi kan wata kujera ya zauna tare da jinginar dakansa cike da
tsantsar damuwa da rudani, wata qaramar locker dake manne da table din dake
gabansa yaja ya sanya hannu ya fito da wani qaramin akwati mai kyan gaske ya bude
akwatin ya fito da wadannan awarwarayen daya ta6a ciresu daga hannun bimbii yana
qare musu kallo tare da jujjuyasu a hannunsa, ranar dai prince kwanan zaune yyi don
be bawa bacci lasisin saceshi......
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *A bitter sweet love affair with so much
struggling and challenges* I'm waiting for you like crazy,pls come back to me my
life.....💕💕

Sati biyu kenan da 6acewar bimbii daga masarautar burham dayawa sun mance da
batunta idan aka dauke prince akbar da duk wayewar garin duniya sai ya fita neman
bimbii ya gama zaga gari ya dawo babu labari, daga qarshe kawai ya soma bin duk
wata kasuwa ta saida bayi, duk kasuwar daya shiga hk zaka ga masu cinikin bayi na
binsa da gudu suna masa tallan bayi ko za'a samu irin wadanda yakeso, idan ya
qarewa bayin kallo be ga wacce yake nema ba sai yyi gaba abinshi, babban hadiminsa
ubaid na take masa baya domin idan zeyi irin wannan fitar ta sirri baya fitowa da
sauran masu tsaron lfyrshi, ubaid shine na hannun damansa ya bashi daman sanin
dukkanin sirrinshi sbd ya yarda dashi dari bisa dari dashi kadai yake fitowa, ubaid
yana mutuqar tausayin prince yadda yaga ya zurfafa kan soyayyar wannan baiwa wanda
tabbas yasan hkn na iya kawo fitina ba qarama ba cikin gdn sarautar burham, ranar
ma hk suka koma gd babu wani kyakykyawan labari, bayan yyi wanka ya zauna ya
zurfafa tunani kan wannan abu daya faru, nasarar gudu ga bawan dake masarautar
burham ba abu ne mai sauqi ba sbd tsatstsauran matakan tsaro ta kowacce kofa,idan
kuwa hkne taya bimbii har ta samu nasarar tserewa batare da kowa daga cikin dakarin
dake tsaron kofa sun ankara ba,sunkuyar dakansa yyi yana tunani sosai don gani yake
kamar da akwai lauje ciki nad'I cikin wannan abu, kiran ubaid yyi dake bakin kofa a
dogare, shigowa yyi da sauri ya iso gabansa tare da rissinar dakansa qasa, dago
idanunsa yyi da suke jaji dasu tamkar yyi kuka ya kalli ubaid yace" kaje kayimin
bincike na musamman kan yadda abun ya faru" ko be nemi qarin haske ba yasan me
prince ke nufi, rissinar dakansa yyi alamar amsar umarni, daga masa hannu prince
yyi sannan ya fice don aiwatar da abunda aka umarce shi, yana ganin ya fita ya
maida kansa ya kwantar jikin kujera dayake zaune,lenah ce ta shigo hannunta riqe da
qaramin basket na kayan marmari taje kan table dake gabansa ta ajiye, ta fito da
yar qaramar wuqa ta dauki tuffa daya tayi slicing dinta gida hudu tana daukan slice
daya daga cikin yankan tana miqa masa idan yaci saita qara masa wani,slices biyu
kawai yaci ya daga mata hannu alamar ya isa hk, daukan basket din tayi ta fita
dashi sannan ta dawo taci uwar kwalliya tamkar wacce zata gasar sarauniyar kyau,
sanye take cikin wata abaya fara sol ta rufe ko'ina na cikinta amma bakinta yadau
jan janbaki sai daukar idanu yake abunku da farar fata, gashi ta tsayar da eye
lashes na idanunta hkn yasa gashin idanun nata yyi duhu, kafarta bbu takalmi don
daman ba'a shiga 6angaren nasa da takalmi, tunda ta shiga yake kallonta amma a
zahiri gixo take masa sai yake mata kallo da bimbii, ita kuma ganin yana kallonta
sai tayi zaton ta yaudaro hnklinsa kanta ne, murmushi tayi ta wuce kan royal bed
nasa ta hau ta zauna tana jiran ya gama abunda yake ya hawo ita kuma ta soma mishi
tausa daga nan ta qure basira da hikimarta ko Allah ze bata sa'a prince ya amshi
budurcinta daren yau, prince kuwa ya jima yana 2karancensa sannan ya taso ya nufo
gadon yahau, yanayin kwanciyar da yyi kawai ya nuna mata baya buqatar komai daga
gareta, duk bayin dake masa hidima sun san alamomin mgnrsa koda be furta komai ba
idan yyi wata alamar suna gane abunda yake nufi, idan yana son tausa ze kwanta ya
juyo bayansa idan kuma ba hk ba toh tsakanin biyu za'ayi daya ko ki tafi ko kuma
dai yana buqatar wani abun daban, itama yanzu tana ganin ya kwanta fuskarsa na
kallon sama taja gefe sai kuma taga ya daga mata hannu, jikinta a mugun sanyaye ta
sakko daga gadon ta sake masa curtains din dake kame gefe gefen kusurwar sannan ta
juya a hnkli ta soma tfy har ta fice, 6angaren bimbii kuwa Izuwa yanzu ta gama
jigatuwa, abinci sau guda kawai ake basu ga ciwo dake cinta a hnkli amma cikin masu
tsaron wannan kurku babu wanda ya kalleta bare tasa ran zasu bata magani, qishirwa
kawai ze iya kar mutum cikin wannan wuri don kusan kullum ma sai an fitar da
fursunonin da suka mace a dakunansu, su kuwa masu tsaron wannan kurku zuciyarsu a
bushe da rashin imani, hk zasu fito da gawarwakin mutanen da wahala ta kashesu su
zubasu cikin keken doki aje a watsasu a babban kogi ruwa ya tafi dasu, dayake
zuciyar tasu babu ko digon imani basu dauki ran mutum bakin komai ba, bimbii
zazza6ine sosai yake wujijjigata kwana biyu amma babu yasan tanayi iyakarsu da
furnoni shine duk safiyya su miqa musu abinci a wani qaramin akushi sai ruwa a wani
cup na katako, hk zasu dauka suna ci tamkar mayu, bimbii tayi duhu ta lalace sai
dogon hanci da manyan idanu da kuma dogon suman kanta daya hargitse ya sake fallasa
tsantsar wahalar da take fuskanta, ruwan hawaye ya qare mata kawai kukan zucci take
fama dashi da tafasar ruhi, burinta a yanzu shine mutuwa ta kawo mata ziyarar
gaggawa, Allah kuma yasa qarshen wahalarta kenan, cikin dare ciwo ya tsananta mata
sai murqususu take tana kakari sbd azaba ga gumi dake fama keto mata ta ko'ina,
jan jikinta ta somayi har ta qarasa bakin kofa ta miqe zaune a hnkli tana buga
kofar da hannunta ko zasu jiyota amma babu wanda ya jiyota har dan qarfin da yyi
saura jikinta yyi qasa ta koma ta kwanta kawai, sai safiyya suka bude don ajiye
mata abinci suka tarar da ita cikin wani irin yanayi na tsananin ciwo, fito da ita
sukayi suka kaita wani babban daki da suka jibge masara lfy, daya daga cikin masu
kula da marasa lfyn ana shigo da bimbii ta kalleta sannan ta koma tsaya bisa kanta,
wasu yan 2kalle tayi kawai a jikin bimbii ta dago dakanta ta kalli wadanda suka
shigo da ita tace" wannan sabuwa ce koh?" daga mata kai sukayi alamar ehh,
tace"tana da aure ne?" duk suka kalli bimbii dake kwance a qasa gefe guda tana fama
da ciwon dake dawainiyya da ita,dayan yace" gsky bamu sani ba ko tana da aure ko
bata dashi" wani yace" ni ban san lkcin ma da aka kawota bare laifin data aikata"
kallonta matar tayi tace" kina da shigar ciki shine ke wahal dake" bimbii na daga
kwance a qasa ba lfy amma tana ji matar ta ambaci kalmar ciki tayi wani irin zabura
ta miqe zaune ta kalleta tace" ciki?ciki kkce ina dashi?toh cikin uban wa?" tsabar
rudewa yasata jero wadannan tmbyoyi tamkar wata zautacciya, matar bata kuma kallon
inda take ba ta kalli wadanda suka shigo da ita cikin wurin tace" gsky bana jin
tana da aure" cikin sauri suka juya suka fita, bimbii kuwa tana daga zaune ta dawo
kamar wata mutum mutumi tunaninta ya tsaya chak, gbdy kwakwalwarta ta dakata da
duty sbd tsabar dimaucewa da tayi, su kuwa wadanda da suka fita kai tsaye 6angaren
azeez sukayi suka sanar dashi cewa an samu wata mai dauke da ciki cikin fursunoni
mata amma basu tabbatar ko tana da aure ko bata da aure ba tinda su basu san lkcin
da aka kawota ba ma,miqewa azeez yyi da hanzarinsa suka nufi wannan dakin da ake
ajiye fursunoni marasa lfy, nuna masa inda bimbii ke zaune sukayi, qare bimbii
kallo yyi tuni ya ganeta, mamaki ne sosai ya kamashi dalili kuwa yasan dai bimbii
babbar baiwa ce ga prince akbar kuma kowa shaida ne prince akbar be ta6a kusantar
kowacce daga cikin bayinsa sbd babu wacce har aka samu ta fito wankin budurci, idan
kuwa hkne toh daga ina babbar baiwa guda ga dan sarki kuma jinin masarautar burham
ta samo ciki,wannan lalle al'amari ne mai girman gaske don kowa tabbas kowanne
cikakkiyar budurwa yake za6e kuma bayanshi babu mahalukin daya isa ya ratsa
gonarshi ko ya kusanci baiwa ko karya kusanceta ita dai ta haramta ga kowa mutuqar
ta taka wannan matsayi,yana gama wannan tunani ya juya ya fice batare daya furta
uffan ba sbd duk wurin babu wanda yasan wacce bimbii ko kuma daga inda ta fito sbd
abun sirri ne, shiyasa yana fita be tsaya ko'ina ba sai fadar sarauniya
mar'atussaliha don sanar mata da wannan al'amari mai girman gaske, ummu nana ce
tayi masa iso ya shiga yana shiga ya rissinar dakai gabanta yyi shiru yana shirin
ta bashi umarnin yin mgn,ita kanta tayi mamakin ganin batare data nemi ganinshi ba
hkn yasa ta soma tunanin ko wani ya fidda sirrinta ne, ummu nana ce ta sanar dashi
sarauniyya ta bashi damar mgn, sai lkcin ya dago dakansa ya kalleta yace" ran
wannan sarauniya ya dade nazo miki da wani babbar al'amari" kada masa kai tayi
alamar tana sauraronsa, sake rissinar dakansa yyi yace" wannan baiwa da hukuncin
daurinta yake kai tsaye daga fadarki an sameta da zaunannen ciki tare da ita"
zumbur sarauniyya ta miqe tsaye tana nuna shi da yatsa a mutuqar fusace tace"
wannan kuma qarya kk mutumin banza kawai, babbar baiwa ga babban prince a ina zata
samu ciki, kowa ya shaida tun aka za6eta bata fito wankin budurci bare ace ya
kusanceta koda ya kusanceta tayi ciki tabbas tana hukunci mai girma bare bai ma
kusanceta toh idan kuwa a wani wurin ta samo ciki nayi rantsuwar da girman Allah
saita gwammace mutuwarta da azabar da zata dandana don wannan tozarci ne ga jinin
sarautar burham"...........

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank,saiki turon da screenshrt ta
wannan layi ...07041195806......

Alkalamin Bintuu ne...


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer


25

*My days of deepest sorrow and pain*........heart full of fear💕💕

Dukkaninsu kowa yyi shiru ya sunkuyar dakansa qasa, sarauniyya ta kuma kallon azeez
cike da tsantsar 6acin rai tace" ka koma ka sanyata cikin dakin ukuba har sai ta
bayyana wannan ciki dake jikinta na waye? amma kar kuyi sake wannan sirrin ya fita
har wani yaji" rissinar dakai azeez yyi da sauri sannan yaja da baya ya fita,
miqewa tayi ta soma zarya ta kasa zaune ta kasa tsaya tana mutuqar shakkar wannan
zance yakai ga kunnen sarki abdallah bin jabal, ummu nana dake tsaye gefenta ta
dago dakanta tace" ranki ya dade ki bani dama na dauki yarinyar nan kawai na
damqata ga masu cinikin bayin dake tfy habasha su maisheta nahiyarta" saurin
kallonta sarauniyya tayi sannan tayi shiru sai can ta dago dakanta tace" wannan
shawarar ba mai amsuwa bace yanzu sai na gama binciken mamallakin cikin dake
cikinta bana fatan ta kasance da wani abu mai kama da jininmu a tare da ita"kada
kai ummu nana tayi alamar gamsuwa da mgnr sarauniya mar'atussaliha, azeez yana
komawa yasa aka dauki bimbii batare da sun duba halin da take ciki ba yyi umarni a
shigar da ita dakin azaba, batare da 6ata lkci ba suka shigar da ita wannan baqin
daki suka dorata kan wata kujera aka daddaure mata hannuwa da kafafu, wata
shafadediyar bulala suka soma tsula mata, saukar bulalar sau daya kawai ya dauke
ganinta na wasu daqiqai kafin ta dawo hayyacinta sun sake zabga mata wata, azeez na
gefe yana kallonta sannan yace" ki fadamin cikin dake jikinki na waye" kallonsa
tayi da idanunta da suka kumbura sannan ta dauke kanta, kunsan bimbii idan ta sanya
taurin kai ko za'a kasheta bata mgn, hk tayi musu shiru su kuwa basu fasa tsala
mata wannan mugur bulala mai tfy da fatar jikin mutum ba, kallonta azeez yyi yace"
wannan itace tmby ta qarshe dazan kuma miki wannan cikin dake jikinki na waye daga
ina kk samo shi, idan baki bani amsa ba toh sai mu gwada miki azabarmu ta gaba"
wuta taga sun kunna a wasu dindinan ginin qasa suka sanya wasu qarafa su jajir,
kallonta yyi ya nuna mata wadannan qarafa yace" yanzu zaki ji saukar su a jikinki
hkn yasa ki bude baki kiyi mgn"sunkuyar dakanta tayi qasa tana jiran su soma
aiwatarwa ta rantse ko zasu kasheta basu sanin waye mamallakin cikin dake jikinta,
6angaren ubaid kuwa tunda prince akbar ya bashi umarnin bincike kan guduwar bimbii
be dire binciken nasa ko'ina ba sai 6angaren sarauniya sbd hk kawai jikinsa yake
bashi kamar dasa hannun sarauniya kan wannan lamarin qila hkne ma yasa ta amshi
bimbii a matsayin baiwarta, duk yadda yyi saida yyi yasa israt da khulood suka koma
6angaren sarauniya da hidima sbd yana da alfarma shima a matsayinsa na babban
hadimi ga babban prince be samu mtsl ba ummu nana ta karbesu ta hannun ummul shukri
sam ita batasan dangantakarsu da bimbii ba, ubaid ya umarcesu su sanya idanu sosai
kan dukkanin shige da ficen dake wakana a fadar sarauniyya mar'atussaliha, fitowar
israt kenan daga babban kitchen taga shigowar azeez ummu nana tayi masa iso ya
shiga don ganawa da sarauniyya, saurin ajiye kwandon tayi ta waiga hagu da damanta
taga babu wanda ke ganinta ta lalla6a ta nufi wurin kofar shiga fadar sarauniyya ta
tsaya da can nesa ta hango kuyangin bayin dake tsaye bakin kofar shiga fada, dakewa
tayi ta qarasa wurin ta shiga cikin jerinsu tare da sunkuyar dakanta qasa, dayan
dake qarshe ta wurin kofa tana ganin israt sai tayi zaton tana cikin masu zuwan
rana waton bayin dake amsar dutynsu da rana, fita tayi daga jeri ta tafi sbd tana
da uxiri mai qarfi, hkn yyiwa israt dadi sosai, wayancewa tayi ta mannu da kofa
sosai tayi qasa kamar tana gyara doguwar rigar dake jikinta, karaff, ta jiyo sautin
sarauniyya tana fadar wasu zantuttuka masu kama da al'mara,umarnin da saurauniya ta
bawa azeez shine kalmar qarshe data iya jiyowa tayi saurin miqewa ta tsaya qam tare
da sunkuyar dakanta qasa yadda taga bayin dake kofar sunyi, daidai lkcin taga
fitowar azeez, tana tsaye duk ta qagu ta rasa yadda zata fice daga cikin jerin
bayin don daman su uku ne kuma idan suka ga ta fita hk zasu zargi wani abu tattare
da ita, tana nan tsaye har ummu nana ta fito kallonsu tayi tace" toh kuje yanzu
wasu zasu zo" ita sam bata gane israt ba sbd daman su uku ne kuma ukun ta gansu,
sauran suka kalli israt amma ganin da sukayi ummu nana batayi mgn game da israt din
ba sai suka juya suka soma tfy daya bayan daya kamar yadda al'adar aikin ta nuna
musu,israt kuwa qasa tayi da kanta har suka wuce sauran ita kadai saida ta tabbatar
sun wuce kuma ummu nana ta koma ciki itama ta janye jiki ta wuce bata tsaya ko'ina
ba sai 6angaren prince, hango ubaid tayi dogare a kofar shiga 6angaren prince, tun
shigowarta ya ganota be bari ta qaraso ba ya janye jiki yabi ta wata kofa suka
hadu, cikin saurin ta damqa masa takardar dake hannunta bata tsaya wata mgn dashi
ba sbd tsaro ta juya ta koma bakin aikinta, shima sanya takardar yyi cikin
aljihunsa yyi tfyrsa, saida ya samu wuri mafi sirri ya ciro takardar ya duba,
abunda ya gani cikin takardar ne yasa shi sake kallon takardar batare da wani 6ata
lkci ba ya nufi komawa 6angaren prince, yana shiga lenah ya gani ta sanar dashi
prince bazai samu ganinshi ba yana kwance, kallonta yyi yace" kije dai ki fada masa
mgnr tana da muhimmaci" kallonsa tayi tare da murmushi tace" ya kk mgn kamar wani
baqo ga dokar wannan 6angare, ni kaina bani da daman iya masa ida baida buqatar
hkn" shiru ubaid yyi yana sake duba yanayi yaga lkci na neman kwacewa yasan su waye
hadiman babban kurku basu da tausayi bare imani tsaf zasu soma gana mata azaba
kamar yadda sarauniya ta bada umarni, qara kallon lenah yyi yace" don Allah ki
taimaka ki sanar dashi" haushin ya bata ta harareshi tayi juyawarta ta kyaleshi
wurin,juyawa yyi da hanxari don yasan komai nacinsa be isa yaga prince yanzu ba,
wurin wata bishiyar magarya ya tsaya ya ciro wani uzir ya hura da qarfi, sai ga
wata kyakykyawar tsuntsuwa ta taso da gudu daga gabas ta nufo inda yake ta sauka a
kafadarsa, saman wannan bishiyar magarya anan shekar wannan tsuntsuwa yake, sautin
wannan uzir ne ke kiranta idan har ba tayi nisa ba,wannan tsuntsuwa ta prince akbar
ce tana da tarin baiwa da fiqira daya banbanta ta da sauran tsuntsaye ba inda bata
shiga a 6angaren prince akbar sannan duk inda ya aikata bata kuskuren isar da saqo,
tasan ubaid sosai don shine kawai da prince ke kiranta da qarar uzir, daukanta
ubaid yyi ya qulla mata saqon wata qaramar takarda a kafafunta sannan ya dagata
sama ya kalli kudu da ita saitin 6angaren prince akbar ya saketa ta tashi firrrrrr,
wannan tsuntsuwa bata tsaya ko'ina ba sai 6angaren prince akbar tasauka har
tsakiyar gadon kwanansa daga gefensa, idanunsa na rufe hannunsa dafe da saitin
zuciyarshi numfashinsa na sauka a hnkli, kansa ne ke tsananta ciwo,kukan wannan
tsuntsuwa tasa yaji kusa dashi, bude idanunsa yyi a hnkli ya kalli gefen nasa ya
hangota tana kada masa fika fikanta, tashi yyi zaune yana murmushi yasa hannunsa ya
dauketa yana shafata, kafarta ya kalla yaga wata qaramar takarda a daure,hannunsa
yasa ya cire takarda yana cirewa ta tashi firrrrr ta fice abinta don ta isar da
saqonta, warware takardar yyi ya soma karantawa,be qarasa gama karanta abunda ke
takardar ba ya sakko daga gadonsa da mugun sauri ya fice, ubaid kuwa na tsaye daga
kofa yana ganin fitowarsa ya rufa masa baya, dokinsa ya hau ransa baqinqirin tamkar
garwashin wuta, a wani irin sukawane ya dauki hanyar wannan babban kurku ubaid
shima yana yana take masa baya, hk suka din ga qetawa ta cikin duwatsu da shuri har
suka fara hango ganuwar kurkun, a cikin kurku kuwa azeez jira yake qarafan nan suyi
jajir ya soma manna mata a jiki har saita magantu, ita kuwa fuskar nan nata tayi
jajir saboda kwanciyar jini, idanunta sun kumbura har sun soma hadewa kamar zasu
rufe, jikinta kuwa duk ya farfashe ko a hk suka kyaleta sai tayi jinya maikyan
gaske, azeez tsugunawa yyi gabanta ya ciro daya daga cikin qarafan dake wutan yyi
jajir tamkar zuga zugi yasa hannunsa yaye mata doguwar rigar dake jikinta yana
shirin yin sama da ita ya manna mata qarfe a tsakanin cinyoyinta, tana ganin hk ta
rufe idanunta rufe tana shirin taji saukar qarfe amma sai taji akasin hk don
kunnenta ne ya jiyo mata sautim muryar da har yau bata mancewa, hancinta kuma ya
jiyo mata qamshinsa,wata irin tsawa mai tsananin rikitarwa ya kwasawa azeez dake
shirin sauke wannan jan qarfen wutan a tsakanin cinyoyin bimbii, hkn ne ya dakatar
da azeez ya jiyo yyi ido hudu da prince, mamakine ya cikashi ya tsaya kawai yana
kallon prince akbar, takowa yyi har tsakiyar dakin yasa hannu daya daya shaqo wuyan
azeez take rawanin dake kime a kansa ya fadi qasa, duk da tsantsar jarimtar azeez
amma kasa kwacewa yyi a hannun prince akbar, dagashi yyi sama da hannu daya,
hannunshi daya harde a bayansa fuskar nan tasa tamau ya cillar dashi gefe guda take
ya fadi kan wannan qarfen wutan dake yashe gefe yyi wata qara sbd zafin wannan
qarfe daya janye fatar jikinsa sauran hadiman kurkun dake wannan daki kuwa duk
sunyi 2tsuru suna kallon prince daya dawo musu tamkar wani namijin zaki, ita kanta
bimbii duk da halin da take ciki be hanata mamakin yanayi na tsantsar fushi data ga
prince ciki ba, qarasawa yyi inda take ya tsuguna 2kwata be dago da kansa ya
kalleta ba sbd bayason ganin halin da fuskarta ke ciki, kunce mata hannayenta yyi
da qafafunta ya dauketa chak ya juya ya fice da ita hk suka din ga bi ta wadannan
dogayen corridorn sbd shi kanshi wannan kurku a jikin dutse aka ginashi, hk suka
din ga ratsawa har suka fito wajen kurkun wurin da dawakansu ke daure ya fara
dorata saman dokin sannan shima yahau suka zabiri dawakan nasu suka bar wurin da
gudu, sosai suke gudu bisa dawakansa cikin jeji ubaid na biye da dokinsu har suka
iso wani kyakykyawan kauye, kai tsaye kofar wani gida suka tsaya,prince ya rufe
kusan rabin fuskarsa da rawanin dake kansa sbd baya son wani ya shaida shi don
wannnan qauye shima mai suna jandun yana cikin yankin masarautarsu ne, wani tsoho
ne ya fito sanye da wata akyabba da qaton rawani yana dogara sandarsa a rankwafe
yake tfy sbd da tsufa, gemunsa fari ne gashi dogo sosai, dakatawa yyi yana
kallonsu, prince dauke yake da bimbii a hannunsa, murmushi yyi wannan tsoho don sai
yanzu ya gane prince daya kalli idanunsa sosai sbd fuskarsa rabi rufe take,nuna
musu hanya yyi suka shige cikin gdn,ginin gdn dai gini ne irin nasu na larabawa na
zamanin baya, ginin jajir irin na jar qasa, cikin wani daki suka shiga mai yalwa
sosai ya nunawa princewa wata shimfida ya kwantar da bimbii data jima da shiga
coma, wata dattijuwa ta shigo riqe da faranti da qananan cups ta ajiye gaban
prince, itace naiha matar wannan tsoho, shi wannan tsoho ya fito ne daga yankin
dilham, Allah yyi masa baiwa ta sanin magani sosai, prince akbar shine ya taba ceto
rayuwar wannan dattijo mai suna abbas daga tarkon sarkin yankin dilham sarki najash
ya bashi mafaka shi da matarsa cikin wannnan dan qauye.....

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki sanya #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank sai turomin da screesht na
payment ta wannan layi..07041195806 da ita nk whatsapp...

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

26

*I'm here to hold you tight dear,if you feel like cry do it on my
shoulder*.......I' m here for you my love💕💕

Tunkan su mishi bayanin komai, matarshi naiha ta sake shigowa dakin dauke da wani
qaramin bowl mai dan fadi da ruwa a ciki ta wuce inda bimbii ke kwance, sunkuyawa
tayi kusa da bimbii ta soma sanya wasu ganye cikin ruwan bowl din nan tana fito da
ganyen ta matse tana daddanna mata a jiki musamman wuraren dake da rauni, saida ta
gama sannan ta fito da wani garin magani tana shafe mata dukkanin jikinta dashi, su
kuwa su prince akbar basu iya hangen abunda take mata har ta gama, ubaid tuni daman
ya fice yana farfajiyar tsakar gdn yana jiran fitowar princce akbar, dattijo abbas
shima miqewa yyi shi da prince suka nufi wurin da bimbii ke kwance, kallonta kawai
abbas yyi yace" amma tana da ciki sbd alamun hkn ya bayyana tattare da ita" shi
kansa prince gabansa yyi mugun faduwa na jin wannan zance, dago idanunsa yyi ya
qura mata idanu, kallonsa abbas yyi yace" dole tana buqatar hutu da cikakken
kulawa" murmushi prince yyi kawai, dattijo abbas ya juya ya fita shi kuma ya nemi
gefenta ya zauna tare da riqo hannunta dukka yana kallon zoben azurfan daya sanya
mata har yanzu yana nan bata cireshi ba, ganin hawaye yyi na fita daga idanunta
dukda kasancewar idanun nata a rufe suke tana bacci, qura mata idanu yyi sosai sai
kuma ya kwantar dakansa gefenta ya dauki hannun nata ya cusa cikin gashin kansa
yadda take masa kenan idan tana son sanya shi bacci, ji yyi duk duniya babu wacce
yake tsananin tausayi irin bimbii sai ya soma ganin laifinsa na rashi bawa abunda
yafi so fiye da komai cikakken kulawan daya dace, shigowar naiha ne yasa ya dago
dakansa da sauri yaja gefe amma still hannunsa na riqe da nata, murmushi naiha tayi
tace" ina son gyarata ne" kallonta prince yyi sai ya maida kansa ya kalli bimbii
daidai lkcin bimbii ta bude idanunta a hnkli ta saukesu bisa fuskarsa, hannunta ta
kalla ta gansa cikin nasa sai ta dago idanunta ta zuba ma fuskarshi idanu shima ita
yake kallo duk sun qure juna da idanu, naiha dake tsaye gefe binsu kawai take da
kallo tana karantar saqon idaniyansu, murmushi tayi kawai don tabbas yanayin kallon
dake kwayar idon kowanne cikinsu ya bata tabbacin dukkaninsu sunyi nitso cikin
kogin soyayya hade da kewar junansu, juyawa tayi ta fice ta basu wuri, bimbii rufe
idanunta tayi tana kuka, matsawa yyi kusa da inda take kwance yasa hannu yana share
mata hawayen dake fita daga idanunta, cikin sanyin murya yace" kiyi hkr ki yafe min
kinji" shiru tayi amma still idanunta na rufe yace" don Allah ki bude idanunki ki
kalleni qila ki yadda da abunda zan fada miki" qin bude idanunta tayi yyi, hannunsa
yasa ya soma tattaro dogon gashin kanta dake baje yasa wani dogon kyalle ya daure
mata wuri daya, duk da hk bata bude idanunta ba, hannunsa yakai kan kirjinta tana
jin saukar hannunsa wurin tayi saurin bude idanunta tana son ture hannunsa daga
wurin amma jikinta ba qarfi tana cikin zafin ciwo, shima da gangan yyi hkn sbd ta
bude idanu ta kalleshi aikuwa yyi nasarar sarqe idanunsa da nata, ta jima tana
kallonsa sannan ta juyar dakanta, naiha ce ta shigo prince ya miqe ya fice, a
farfajiyar tsakar gdn ya tarar da dattijo abbas yana hada wasu magunguna suna hira
da ubaid,suna ganin fitowarsa ubaid yyi saurin tashi daga inda yake ya tsaya qam,
dattijo abbas ya fito da wata qaramar kwalbar magani ya miqawa babban prince yace"
ranka ya dade gashi ka riqe wannan yana maganin duk wani zugin ciwo" hannu yasa ya
amshi mgnin ya daga masa hannu alamar ya gode, rakasu yyi suka fita waje suka haye
dawakansu suka zaburesu suka dauki hanyar barin wannan qauye, 6angaren sarainiyya
kuwa wannan mummunan labari yakai kunnenta, kwatanta rudewar da tayi ba'a mgn,
tasan tabbas tunda hk ta faru dole sarki abdallah bin jabal ya samu labari, sarki
abdallah bin jabal kuwa ya samu labarin zuwan prince akbar babban kurku abunda ya
daure masa kai shine wai prince ya fitar da wata baiwa da aka sameta da ciki, toh
meye hadin babban prince da baiwa kuma? miqewa yyi tsaye ya bada umarnin ayi masa
bincike kan wacce wannan baiwa kuma wanne laifi tayi aka kaita wannan wuri,batare
wani 6ata lkci ba bincike ya kammala, cikin binciken sun tabbatar masa wannan baiwa
dai tsohuwar babbar baiwar prince akbar ce kuma hadima a 6angaren sarauniyya amma
basu gano laifin da tayi aka kaita wannan wuri ba saidai ta tafi wurin ne bisa
umarnin sarauniyya mar'atussaliha, sarki abdallah bin jabal ya dago fuskarsa da
tayi ja sbd tsantsar 6acin rai yace" babbar baiwa ga prince kuma take dauke da
ciki?toh cikin waye?" miqewa yyi kawai ya shige cikin gd, sarauniya kuwa tana
6angarenta sai faman zirya take don tabbas ta rasa mafita, saqon kiran sarki ne ya
tarar da ita, sanye take daman da wata doguwar riga da mayafi ta fito ummu nana ta
mata rakiya har kofar shiga 6angaren sarki tana shiga ta tarar dashi zaune a wata
kujera, neman qasan carpet tayi ta zauna tare da sunkuyar dakanta qasa, be mata mgn
ba sai ya dauki lkci sannan yace" meye laifin baiwar da kk bada umarnin a kaita
babban kurku?" dago dakanta tayi ta kalleshi tace" ranka ya dade wannan baiwa a
6angare na take kuma an sameta da laifin ciki" yace" kurkun qasa shine kurkun da
ake miqa duk baiwar da aka samu da ciki amma ita wannan meyesa aka kaita babban
kurku?" shiru sarauniyya tayi saida ya daka mata tsawa tukunna yace" ina mgn kin
min shiru, cikin waye a jikin wannan baiwa?" sarauniyya jikinta har rawa yake ta
daga idanunta ta kalli sarki abdallah da idanunsa kawai sun tabbatar mata da rashin
wargi, tace" nima binciken da nk kenan" girgixa kansa yyi ya daga mata hannu ta
miqe jiki a mugun sanyaye ta fita, tuni sarki abdallah ya bada umarni cikin wannan
daren yake son su nemo duk inda prince akbar yakai wannan baiwa su kaita kurkun
qasa kafin washegari, isowar prince akbar kenan shi da ubaid labarin abunda ke
faruwa ya taddasu, wannan zance na cikin jikin bimbii gbdy ya zama wani zance dake
masifar tashe cikin wannan gdn sarauta, duk inda taron bayi suka hadu toh wannan
zance suke gutsurawa junansu cikin hk har zancen yakai kunnen su israt, wannan abun
sun jishi tamkar al'amara, mafi yawan mutane cewa suke bimbii a wani wurin tayo
cikinta don tabbas ba wanda ya shaida ta fito wankin budurci, gimbiya hindu har ma
da prince nasaar dukkaninsu sun aminta cewa cikin jikin bimbii bana prince akbar
bane,prince yasan sarai halin mahaifin nasa bazai tanka masa ba har sai ya samo
inda bimbii inda take, kiran ubaid yyi yace" komawa zamuyi qauye jandu don tabbas
yankin burham ne kuma zasu iya gano inda bimbii take" ubaid yace" ranka ya dade
yanzu duk wani motsinka dama duk wanda ke wannan 6angare yana kan idanun masarauta,
yanzu hk gbdy saman 6angaren nan zagaye yake da dakarin sama masu masu" shiru
prince yyi amma hnklinshi ba'a kwance yake ba, 6angaren bimbii kuwa tana samun duk
wata kulawa daga wurin wadannan dattijai sun dauketa kamar wata diyarsu don daman
basu ta6a samun magaji ba, bimbii ta samu ingantattun magunguna bacci mai dadi yyi
gaba da ita, wadanda aka sanya binciko inda bimbii take kuwa tuni suka yiwa kauyen
jandu tsinke cikin shigar bad da kama ta yadda babu wanda ze ganesu suka soma
kewaye cikin qauyen bawai sun tabbatar wannan qauyen bimbii take ba, sun shiga
qauyuka da dama bincike suke sbd ance prince yyi gabas ne lkcin daya dauki wannan
baiwa kuma bisa doki yake, prince baya shiga cikin gari bisa doki kuma idan har
gabas yyi toh tabbas wani qauyen ya kaita dake maqobtaka da masarautar burham,cikin
masu farautar bimbii har da mutanen prince nasaar, suma burinsu su riga dakarun
sarki abdallah bin jabal samo inda bimbii take ya basu umarni mutuqar sun ganta su
dauketa su miqata qasar spain ta jirgin ruwa,cikin izinin ubangiji mutanen prince
nasaar suka riga isa inda bimbii take suka dauketa suka qarasa da ita port suka
sanyata cikin jirgin ruwa saidai kafin wannan jirgi ya tashi har dakarin sarki
abdallah bin jabbal sun bayyana a wurin,bayin prince nasaar kuwa suna ganin hk suka
sulale suka bar port din don basu so wadancan dakaru su shaida fuskokinsu, su kuwa
dakarin babban burinsu su chafke bimbii kuma cikin ikon Allah sukayi nasarar
kamata, 6angaren masarautar burham kuwa sarki abdallah bin jabal ya sanya taro na
musamman wanda ze gudana a filin kofar fadarsa, washegari filin wurin ya cika maqil
da jama'a, sarki abdallah bin jabal yana can saman matattakala bisa kujera ta
alfarma gefensa kuma prince akbar ne sai sauran princes din da ragowar masu fada
aji cikin wannan masarauta ta burham, ta can daya gefe kuma sarauniya
mar'atussaliha ce tasha kaya na alfarma ita da yan fadanta duk suna zazzaune a
kujerun girma idan suka hanga qasa matattakar al'umma ne birjik kowa na sauraro,
wurin tsaro ne ta ko'ina,sarki abdallah bin jabal dakansa ya miqe ya soma jawabi,
jawabinsa na farko shine yace" yau ranar farin ciki ce hade da baqin ciki dukka,yau
itace ranar da masarautar burham zata qulla yarjejeniyar aure tsakaninta da
masarautar abu ansar, wannan yarjejeniya ta aure zan qulla tane tsakanin da prince
akbar da princess mariyatul qifdiya" prince akbar dake gefe sunkuyar dakansa yyi,
zuciyarsa cike da mamakin wannan abu, prince nasaar kuwa sai wani murmushi yake,
fuskokin kowa wurin dauke take da annuri musamman sarauniya mar'atussaliha, sarki
abdallah ya tsuke fuska sannan ya koma ya zauna prince andal ya miqe ya dora bisa
jawabin sarki abdallah yace" sannan yau din kuma wannan masarauta ta zartas da
hukuncin kisa kan wata tsohuwar baiwa dan sarki da aka samu da ciki wanda kowa
yasan girman wannan laifi cikin wannan masarauta ta burham" sai lkcin prince akbar
yyi hanxarin dago da fuskarsa inda ya hango manyan dakaru majiya qarfin sun fara
hawo da bimbii kan matattakalar, tsayar da ita akayi gbdy duk sun daddaureta, sarki
abdallah ya bada umarni sarkin kisa ya sare kan bimbii...........
Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir, union bank, saiki turomin da screesht ta
whatsapp ta wannan layi....07041195806.....

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

27

*My heart is paining*....I can't stop the tears💕💕

Sarkin kisa ra'iz wani gabjejen qaton mutum ne mai yalwar girman jiki da fad'I ga
wani jibgegen rawani akansa, hannunsa rige da wata takobi tsirararta ya soma
haurawa matattakalar inda bimbii ke daure, bimbii gbdy ta jigatu bakinta sai fitar
da jini yake ga gashin kanta daya hargitse ya rufe mata fuska, jira kawai take su
gaggauta fille mata kai ko zata huta da wannan mawuyacin halin da take ciki, ra'iz
ya qarasa hawa wurin ya daga takobinsa sama da niyyar fille kan bimbii yaji an daka
masa wata razananniyar tsawa, dakatawa yyi ya waiga sai ganin prince akbar yyi
tsaye a bayansa, sauke takobin yyi qasa, hkn yyi daidai da miqewar sarauniya daga
kujerarta ta dakawa prince tsawa akan ya hanzarta barin wurin, sarki abdallah kuwa
yana daga zaune yana kallon abunda ke faruwa,murmushi sarki abdallah yyi ya kalli
prince nasaar dake gefensa yace" ka sanar da sarkin kisa yana bisa umarni ne kar ya
tsaya 6ata lkci" miqewa prince nasaar yyi shima jikinsa a mutuqar sanyaye ya daga
murya sosai yace" sarkin kisa ya harzarta aiwatar da umarni batare da 6ata lkci ba"
wannan zance na shiga kunnen sarkin kisa ra'iz ya kuma daga takobinsa da niyyar
cika umarnin sarki abdallah bin jabal, cikin tsananin zafin nama prince akbar ya
chafe takobin nasa yyi wulli da ita gefen daman bimbii tuni takobin ta tsinke
daurin da akayi mata ta 6angaren dama, qara chafe takobin yyi ya kuma cillata gefen
hagunta tuni daurin ya warware dukka ya riqeta yyi gefe da ita, wurin yyi tsit sbd
kowa ya cika tsantsar mamakin wannan abu da prince keyi bisa umarnin mahaifinsa,
sarki abdallah bin jabal miqewa yyi cike da mamaki shima amma sai ya 6oye hkn a
fuskarshi ya kalli shugaban dakarin dake tsaye a wurinl yace" su kama prince maxa
su miqashi kurku tare da azabtar dashi pita kuma wannan baiwa su kawo masa kanta
yanzu gabanshi"wannan umarni da sarki abdallah bin jabal ya bayar yyi masifar
gigita sarauniya mar'atussaliha saidai ko kusa bata da damar mgn musamman a wannan
yanayi da ran sarki abdallah ke tafasa,batare da wani 6ata lkci ba dakarun dake
wurin duk suka zare makamansu sukayi kan prince akbar, shi kuwa yana tsaye yana
ganin hk kawai yaja bimbii zuwa bayansa, kallo daya zaka masa kasan ya shirya
tararsu, suna qarasowa suka afkan kansa da hannu guda kawai yake 6arar dasu dayan
hannun nashi riqe da bimbii, cike da azama da mugun zafin nama yake uwar watsi dasu
tamkar wani gawurtaccen zaki ta tsakiyarsu yake bi idan ya watsar dasu sun zube
qasa, wuri gbdy ya hautsine da artabu tsakanin dakarin sarki abdallah bin jabal da
prince akbar shi daya kawai ya gagaresu, ba kashesu yakeyi ba kawai raunata su
yakeyi ya wuce burinsa kawai ya samu doki ya haye su bar wurin amma ina abu ya
gagare sbd dakarin nan kamar qaruwa suke, gumurxu sosai ake bugawa a wannan wuri,
bimbii bata ta6a sanin prince namijin gaske bane a filin fama sai yau ta tabbatar
da hkn, gwaninta kawai yake nuna ta tsantsar jarumta duk yawansu ko kwarzane babu
wanda yyi masa kuma a hkn yake kare bimbii daga harinsu, fararen kayan dake jikinsa
gbdy sun 6aci da jini, fada yake cikin tsananin zafin nama da gocciya tamkar wani
hatsabibi, yadda prince akbar ke fada da nuna bajinta be kasance ya basu mamaki ba
don duk wanda ya kwana ya hantse a masarautar burham yasan wane ne prince akbar a
filin fama shiyasa shi kansa sarki abdallah bin jabal ke mugun alfahari dashi,
ganin hk ne yasa sarki abdallah bin jabal miqawa hadiminsa uxair hannu ya miqa masa
wani mashi mai tsinin gaske, daga mashin yyi dakansa yyi saitin prince akbar, shi
kuwa yana cikin fada da wadannan dakaru batare daya ankara ba kawai yaji harbin
mashi a bayansa, mashin yana dauke da guba sosai, daga kansa yyi ya hango
mahaifinsa riqe da wani mashin yana saitinsa, batare daya zare mashin dake jikinshi
ba yyi kukan kura yyi watsi da dakarin dake gabansa yaja hannun bimbii da gudu suka
hau kan wani doki, dakyar yahau dokin cike da dauriya sbd wannan harbin mashin,
suna bisa dokin wani harbin ya kuma samunsa, hk ya cije yaja dokin da mugun gudu
suka bar wurin a guje, sarki abdallah ya bada umarnin su bisu, yana kan dokin amma
qarfinsa ya soma qarewa sbd harbin mashin dake jikinsa, zuciyarsa ce kawai ke tfy
dasu bisa dokin, hannu yasa ya cire mashin dake tsire a bayansa, bimbii juyowa tayi
tana kallonshi taga halin dayake ciki amma duk da hk yana qara daurewa yana jan
dokin, gudu suke amma dakarin sarki abdallah na biye dasu, wata hanya suka miqa
cikin jeji suna gudu saida suka je qarshen hanyar suka tarar ba hanya sai wani
qatoton rami mai zurfi da fadi, qasan ramin qananan bishiyoyi ne tare ruwa dake
kwaranya tamkar qorama, dokin nasu yaja ya tsaya gaban wannan qaton rami mai tsayin
gaske, sauka sukayi daga kan dokin duk suka tsaya sukayi cirko cirko, gashi tabbas
wadannan dakaru sun kusa cimmusu, bimbii a wannan lkci ta dena tausayin kanta
prince take tausayawa yanayin yadda ta ganshi, matsowa kusa dashi tayi ta riqeshi
ya durgusa a wurin yasa hannu ya zare dayan mashin dake cake a gefen cikinsa,
tabbas shi kansa lkcin yasan abu ne mawuyaci ya rayu domin wannan mashi na
mahaifinsa yana da gubar gaske, saidai babban burinsa shine ya tsirar da bimbii ita
da abunda ke cikinta, sautin sawun dawakai suka jiyo hkn ya tabbatar musu dakarin
dake biye dasu ne, dago dakansa yyi ya kalli bimbii yace" ki gafarce ni don Allah
ki yafemin" riqo hannunta yyi yace" ina son ki rayu komai wuya sannan kar ki mance
dani cikin rayuwarki, kin ji, ina sonki dayawa na sadaukar miki da rayuwata
gbdynta" kuka bimbii take sosai tana rufe masa baki da hannunta tace" bani son ka
sadaukarmin da rayuwarka na fison mu rayu tare ko mu mutu tare, bazan rayu babu kai
ba, wlh bazan iya ba" kuka sosai take ta kwantar dakansa a kirjinta, daidai lkcin
dakarin sarki abdallah bin jabal suka qaraso wurin, batare da 6ata lkci ba suka
sakko daga kan dawakansu suka nufo wurin, prince yana ganin hk yasan tabbas wlh
kashe bimbii zasuyi, miqewa yyi duk da jirin dake dibansa. yana ja da baya, bimbii
kuwa tana bayansa tana kuka, gani yyi wasu daga cikinsu na bisa dawakai sun saita
bimbii da mashi, ita kanta bimbii bata ankara ba sai ji tayi kawai prince yasa
hannu cikin azama ya hankadata cikin wannan dogon rami, su kansu dakarin dake wurin
basuyi zaton hk ba, ihu take har ta fada qasan wannan rami cikin ruwan dake
kwaranya,shi kuwa prince tsayawa yyi yana kallonsu sai kuma kawai ya sunkuya ya
dauki takobinsa ya afka musu tamkar ba rauni a jikinsa, prince nasaar daya biyo
bayansu yana qarasowa yaga wannan artabu tsakanin dakarin nan da prince, murmushi
yyi yasa hannu ya ciro kibiyoyi ya soma masa dashi, burin daman kawai ya kashe shi,
aikuwa kibiyoyin suka same shi dukka a gadon baya, sakin takobin dake hannunsa yyi
kawai ya durqushe a wurin yyi zaman ruku'u, daga wata kibiyar yyi da niyyar qara
masa yaji an riqe ta baya, juyawa yyi a fusace yaci karo da gimbiya hindu bisa doki
ta rufe rabin fuskarta da baqin kyalle, tace" waye yace ka kashe shi" sauke
hannunsa yyi ya maida kibiyoyin, shi kuwa prince hannunsa kawai yake miqawa saitin
ramin da bimbii ta fada har numfashin shi ya tsaya chak, gimbiya hindu ta sakko
daga kan dokinta ta nufo inda yake ta soma jijjigashi tana hawaye sosai, kamar daga
sama suka soma suka ganin wani irin hayaqi yana gauraye ko'ina cikin dajin, zumbur
gimbiya hindu ta miqe tana waiwaye hkma sauran dakarun dake wurin, prince nasaar
shima 2kalle ya somayi basu ga kowa ba, wasa wasa wannan hayaqin ya cika wurin
sosai ko tafin hannunsu basu iya gani, a hnkli kuma hayaqin ya soma washewa suka
kai dubansu wurin da prince yake kwance suka ga wayam, abun yyi mugun daure musu
kai da basu mamaki basu ji motsin komai ba kuma basu ga kowa ba amma sun nemi
gangar jikin prince akbar sama ko qasa sun rasa, ba kowa ne da wannan aikin ba sai
ubaid babban hadimi ga prince,shine ya sanya wannan hayaqin sannan kuma ya lalla6a
ya dauke prince batare da sun ankara ba, nesa da wurin sosai ya ajiye dokinsa, hk
ya dauki prince ya haye dokinsa yabar wurin, prince nasaar yasa dakarun duk su
bazama cikin wannan jeji don nemo gawar prince akbar don miqata ga sarki abdallah
bin jabal, batare da 6ata lkci ba suka watsu cikin wannan jeji suna neman prince
akbar, shi kuwa ubaid be tsaya ba saida ya tabbatar ya fice daga yankin masarautar
burham, wani kogon dutse ya shige da prince anan ya tarar da dattijo abbas, ajiye
prince yyi dattijo abbas ya matso kusa da inda prince akbar ke kwance yakai
hannunsa ya dora saitin zuciyarshi yaji babu alamun numfashi tattare dashi, kansa
ya dora wurin sai lkcin ya jiyo bugawar zuciyar tasa a hnkli, dago da kansa
yyi,ubaid yace"meke faruwa dashi ya mutu ne" girgixa kansa yyi yace" da sauran
numfashi a tare dashi" ajiyar zuciya ubaid yyi yana kallon fuskar prince da kwance,
dattijo abbas ya fito da wasu magunguna daga jakar dake rataye a kafadarsa, wuraren
harbin mashin ya soma zubawa garin maganin, 6angaren sarki abdallah kuwa jira kawai
su dawo masa da kan bimbii da kuma dansa prince akbar,shi yana son ya hukunta
prince dakansa bisa laifin daya yyi, sai dare suka koma ga sarki abdallah ba bimbii
ba prince akbar, hkn ba qaramin 6ata masa rai yyi ba yasa a rufe dukkanin dakarin,
sarauniya mar'atussaliha kuwa kuka sosai take ta kasa cin abinci ba yadda ummu nana
batayi da ita ba kawai ita danta take son gani, gimbiya hindu ita ta labarta masa
abunda ya faru, miqewa tayi tsaye da sauri ta fice ta nufi 6angaren sarki abdallah
bin jabal, tana shiga ta zube a gabansa tana kuka sosai tana roqonsa don girman
Allah yasa a nemo mata danta, kallonta kawai yyi ya tashi yabarta a wurin,
durgushewa tayi tana kuka kamar ranta ze fita, prince akbar shi kadai ne dansu
yanzu gashi silar wannan baiwa ta rasa danta gudan jininta.........

Littafin nan na kudi ne, idan kin idan kina da buqatar karantawa zaki tura #300 ta
wannan acct.....0100790419,alhaji shahida nasir,union bank,saiki turomin da
screesht ta whatsapp da wannan layin 07041195806......

Alkalamin Bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

28

*You are the only one I can hear*.....You are the only one I can feel cox you are
are the reason of my living💕💕

Bimbii kuwa tunda ta fada wannan dogon rami bata kuma sanin inda kanta yake,
dulmiyewa tayi cikin wannan ruwan dake kwaranya tamkar na 6ul6ula, ruwan zuba yake
shaaaa daga jikin wani dutse gashi fari tas dashi, karfin ruwan ne ya janyeta ta
fada wani qaton ruwa wanda yyi iyakar yankin burham da yankin dilham, wannan ruwa
shi ya raba tsakanin yankunan guda biyu,qananan jiragen ruwa da manyan kwale kwale
masu safarar bayin zuwa yankunan qasashen larabawa 2daban suna ratsawa ta wannan
dogon kogi, igiyar ruwa ce tayi tfy mai nisan gaske da ita takaita ga6ar wannan
kogi cikin izinin ubangiji wani mutuqin kwale kwale mai suna abeed ya hangi gangar
jikinta a yashe gefen wannan kogi igiyar ruwa ta watso ta ga6a, cikin sauri ya nufi
wurin don tabbatarwa kansa yana zuwa kuwa ya ganta kwance babu alamun ruhi tattare
da gangar jikinta, sunkuyawa yyi yakai hannunsa daidai wurin bugawar numfashinta
yaji shiru, duk da hk be hkr ba yasa hannu ya dinga dannan cikinta ruwa ya soma
fita mata ta hanci ta baki har saidai ruwan data sha ya fita, jikinta yyi sanyi
tamkar qanqara hkn ya tabbatar masa cewa ta jima a cikin ruwa, yatsunsa biyu ya
kuma pointing kan qahon zuccinta sai lkcin yaji dif dif alamun akwai sauran ruhi
tattare da gangar jikin nata, daukanta yyi yasata cikin kwale kwalensa ya shige ya
soma tuqa kwale kwalen nasa har suka fita asalin ga6ar da yake da 2hadar jama'a,
duk wanda ya gansa sai yyi zaton baiwarsa ce ta kasa har jaje ake masa hk ya samu
ya wuce da bimbii, abeed mutumin dilham ne kuma masunci ne yana zaune shi da
iyalinsa a wani qaramin gdn katako kusa da wannan kogi, matar shi daya da d'ansa
daya dan kimanin shekaru ashirin sunan shi farhan, matar shi saudat ta tausaya
mutuqa da taga halin da bimbii ke ciki, hk suka din ga bata taimakon daya dace
kasancewarsu masunta, saudat ta dumamawa bimbii jikinta sosai yadda jikin nata ya
dauki dumi sosai, kallon daya ta yiwa bimbii ta fahimci tana dauke da juna biyu, hk
suka cigaba da bata duk wani taimako kusan sati guda kenan amma bimbii bata ta6a
koda motsi ba bare su sanya mata ran samun lfy, dansu farham a lkcin yana high schl
ne ajin qarshe, ba wasu mawadata bane talakawa ne saidai sun fi qarfin cikinsu,
bimbii saida tayi sati uku chur tana kwance tamkar mutum mutumi amma basu gjy da
kula da ita ba, yau da dare saudat tana kasa mata jiki kawai taga yatsun qafarta
sun motsa, murza idanunta tayi ta kuma kallon kafarta taga tabbas motsi take da
yatsun qafarta, kwalawa danta farhan kira tayi suka shigo cikin dakin da gudu shi
da abeed, nuna musu yatsun kafar bimbii tayi su ga tana motsasu, murna sosai suka
somayi tamkar wata jininsu,washegari, da sanyin safiyya saudat ta shigo dakin da
bimbii ke kwance sai ganinta tayi idanunta bude tana 2kalle dasu, matsowa tayi da
gudu ta zauna kusa da ita ta riqo hannayenta tana mata sannu, ita kuwa kawai binta
take da idanu tamkar wata kurma,6angaren prince akbar kuwa shikam be dauki wani
tsawon lkci ba, kwanan shi biyar kwance abbas yana bashi magungunan da suka tsuge
dafin mashin daya soke shi, a kwana na biyar ya bude idanunsa, ubaid da abbas ba
qaramin dadi sukaji ba na ganin prince ya farka, suna dai cikin wannan kogon
dutsen dashi sbd sarki abdallah bin jabal har yau be hkr da nemansu ba, prince
akbar ya zamto wanted ga masarautar burham,mtslr shine har yanzu suna cikin yankin
masarautar burham basu da hnyr da zasu iya ficewa daga yankin masarautar burham sbd
nemansu ake ruwa a jallo, prince akbar ya farfado kuma yana cigaba da amsar magani
wurin dattijo abbas saidai tunda ya farfado har yau be tankawa kowa ba, da tunanin
bimbii ya farka ita kawai yakeson gani a halin da yake ciki, d'an sarki mai
cikakken izzah wanda ya saba kwana bisa tattausa yau shine ya samu kansa cikin
wannan kogon dutse amma shi duk ba wannan ne ya dame shi ba,babbar damuwarsa shine
shin bimbii tana raye ko tana mace, idan har bimbii bata raye toh shikam be ga
amfanin tasa rayuwar ba sbd itace mahadin ruhinsa itace bugawar numfashinsa,
wadannan irin tunani su suka zame masa sana'a, ubaid ya fara damuwa da yanayin da
yake ganin prince ciki sai yake ganin kodai ya samu wata mtslr ne, dattijo abbas
yace ya kyale prince ya kadaice da zuciyarshi, prince akbar ko gama samun sauqi
beyi ba ya fito daga wannan kogo, ubaid ya kalleshi ya rissinar dakansa qasa yace"
ranka ya dade dakarin masarauta sun bazu ko'ina nemanka kawai suke idan kayi wani
wuri yanzu zasu iya ganinka" kallon prince yyi sannan ya dauke kansa ya juya sai
can yace" gudu yana ga raggo ne amma namiji baya gudu a fagen fama koda hkn na
nufin ajalinsa" yana gama fadar hk ya kama dokin dake daure yahau ya sakar masa
linzami yabar wurin, kai tsaye wurin ramin daya tura bimbii ya nufa, yana qarasawa
wurin ya sauka daga kan dokin ya nufi wurin ramin ya leqa qasan ramin ya tabbatar
da tsayinsa batare da wani shakka ba ya soma shirin afkawa cikin dogon ramin shima
ya isa duniyar da bimbii take, murya da yaji bayansa ne yasa shi juyawa, ubaid ne
yace" ranka ya dade kafin ka aikata hkn ya kamata kasan halin da sarauniya take
ciki tun ranar daka bar masarauta ta kwanta babu lfy kuma jikinta ya tsananta tana
da burin sake ganinka kar ka kashe kanka batare daka gana da mahaifiyarka ba"
kalaman ubaid sunyi tasiri mutuqa sun sanya ya soma begen ganin mahaifiyarsa duk da
laifinta gare shi amma uwa ai uwa ce" jiki a sanyaye ya koma ya haye dokinsa kawai
bisa mamakin ubaid sai kawai gani yyi babban prince ya dauki hanyar masarautar
burham, tun daga nesa dakarin dake tsaron kofa suka hango shi batare da wani 6ata
lkci ba suka bude masa kofar wannan gdn sarauta ya shige da dokinsa, duk wanda yaga
prince sai ya cika da mamaki, tuni wannan albishir yakai kunnen sarauniya sannan
yakai ga sarki abdallah bin jabal, umarni ya bayar a rufe kowacce kofa ta wannan
masarauta sannan ya sake bada umarni a kama prince a miqashi kurkun qasa, prince
yana sauka daga dokinsa yaga dakarin tsaron wannan gd sun tsagayeshi ta ko'ina
dukkaninsu riqe da makamai, sarauniya bata da masaniyyar wannan umarni da sarki
abdallah ya bayar saida ummu nana ta shigo ta shaida mata, prince kuwa fuskar nan
tashi tamkar hadari ya kalli wadannan dakaru yace" duk wanda yakeson uwarsa ta
haifi wani ya cigaba da tsayuwa anan" dukda sun san jarimtarshi amma basu kauce ba
don suna mtuqar shakkar mahaifinsa sarki abdallah bin jabal, prince wata qaramar
wuqa ya ciro daga jikin dokin dake gabansa ya nufi shiga cikinsu, kai tsaye yaji
muryar mahaifiyarsa daga bayanshi tace" idan har nina haifeka kar ka kuma aikata
wannan abu,bani son ka kuma zare takobinka bisa umarnin mahaifinka kabi umarnin
shi" juyawa yyi a hnkli ya hango an turota a wheel chair, sauke wuqar dake
hannunsa yyi ya qarasa inda take a hnkli ya tsuguna gabanta ya dora kansa bisa
cinyarta ya rufe idanunsa, hawaye take sosai tasa hannunta tana shafa kansa, daidai
lkcin sarki abdallah bin jabal shi da tawagarsa suka qaraso wurin, fuskarshi babu
digon afuwa, dago dakai prince akbar yyi ya juya sukayi ido hudu da mahaifin nasa,
dauke kai sarki abdallah yyi ya kalli dakarun dake wurin yace" ku miqashi kurku"
kafin ya rufe baki sun matso wurin da prince yake suka kama shi, saurin cire musu
hannu yyi daga jikinshi ya kalli mahaifin nasa yace" zan tafi dakai na" wucewa yyi
gaba suka bishi a baya, sarauniya ta fashe da kuka ta kalli sarki abdallah tace"
don Allah kayi masa aikin gafara" be kalleta ba bare ta sanya ran ze bata amsa ya
juya abunshi yan fadansa suka take masa baya, ummu nana ta tura wheel chair din da
sarauniya ke kai ta koma da ita 6angarenta tana kuka, ita kanta tasan sarki
abdallah ba qaramin kafiya ne dashi da taurin kai ba shima kuma dan nasa hk yake ai
gado ba karambani bane, bude masa kofar kurku sukayi ya shige ya zauna abinsa suka
maida kofa suka rufe, bimbii kuwa tana samun kulawa yadda ya kamata daga wurin
saudat da danta farhan saidai babban tashin hnklin shine bimbii tayi losing memory
nata, 2kwata bata iya tuna komai ta manta duk abunda ya faru da ita ta mance ita
wace ce,komai koya mata ake hatta mgn da yadda ake cin abinci dama komai, farhan
yana mutuqar qoqari wurin kula da bimbii da koya mata abubuwa, shidai abu guda ne
ya tsole masa idanu game da bimbii shine wannan jikin dake jikinta ya tsani yaji
ance bimbii tana da ciki, sudai sun tsinci bimbii basu san ko tana da aure bane ko
bata da aure sudai kawai sun ganta da ciki kuma gashi tayi losing memory nata bata
iya tuna komai bare su nemi ta sanar dasu wace ce ita, yau da gobe jikinta ya
warware saidai komai nata cikin sanyi take yinsa, bata son mgn shiru shiru, farhan
shi kullum mamaki yake wai bimbii yar qarama da ita amma tana da ciki don shi gani
yake ya girmi bimbii, tun bimbii bata mgn har ya dage ya soma sanyata mgn, hk yake
shiriricewa kullum gabanta yana bata labarai na ban dariya, ya maida bimbii tamkar
wata qawarshi itama saita dauke shi aboki kuma dan'uwanta don ita duk zatonta
saudat itace ta haifeta, farhan kuma qaninta ne saidai ita mamakinta meyesa ita
bata kaisu hasken fata ba, tana yawan yiwa farhan wannan tmbya shi kuma sai ya
shashatar da zancen, a kwana a tashi cikin bimbii kullum qara girma yake, tmbyr
saudat tayi wai meyesa cikinta ke girma hk, murmushi kawai saudat tayi tace" kar ki
damu wataran zaki haifa mn baby ne" shiru tayi bata kuma cewa komai ba,hk rayuwa ta
cigaba da tfy, shaquwa sosai ta shiga tsakanin bimbii da farhan sun zama tamkar
abokai,wata rana sun je bakin teku kallon ruwa, farhan ya kalli bimbii yace" ki
bani wannan zoben na hannunki yana min kyau" kallon zoben bimbii tayi wanda ita
bata ce ga yadda akayi zoben ya shiga hannunta ba tace" zoben nan yana min kyau a
hannu bani cireshi don ma kaji" dariya yyi yace" toh shikenan ai" prince akbar kuwa
tunda sarki abdallah ya sanya shi cikin kurku ya dauke masa kai, kuma yace ayi
treating nasa equal da sauran prisoners, babban damuwa prince bimbii ce, shi kansa
yana mamakin irin son da yake yiwa bimbii, duk daren duniya sai yyi mafarkinta,
hali yake ciki na quncin zuciya da damuwa, tun yana daurewa har abu ya soma cin
qarfinsa sai wayar gari akayi prince na aman jini, sarauniya kam kullum tana hanyar
wannan kurku kuma kusan duk ranar duniya saita neman wa prince gafara wurin
mahaifinsa amma ya kafe kai da fata sai prince ya gane kurensa kafin ya fito dashi
kuma sai ya fito duniya ya qaryata soyayyarsa ga wannan baiwa sannan ya nesanta
kansa da cikin dake jikinta idan yyi hk kawai shine ze iya yafe masa, wannan abu
kuwa shine abu mafi tsauri ga prince akbar, bazai ta6a qaryata soyayyar bimbii ba
hkma cikin dake jikinta duk kuwa da cewa besan ko tana raye ko bata raye ba........

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar karantawa zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki turomin da screesht na
payment ta whatsapp ta wannan layi...07041195806....

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

29

*Only one person fill my heart*.....You are the reason of my breathing,I love you
so much dear💕💕

Yau bimbii na kwance ita kadai a daki sbd tun safe take jin jikinta wani iri babu
dadi amma tana ta daurewa batason ummu farhan ta gane halin da take ciki, ummu
farhan ce ta shigo dakin hannunsa riqe da wani qaramin cup da zuma a ciki, bimbii
na ganinta tayi saurin miqewa zaune, murmushi ummu farhan tayi ta miqa mata qaramin
cup din dake hannunta tace" ki shanye zuma ce tana cike da sirrika na magunguna
2kala musamman wurin mace mai juna biyu" murmushi bimbii tayi tasa hannu ta amshi
cup din ta soma shan zumar har ta shanye, da dare lkcin cin abincin dare duk suna
zazzaune kan wata qatuwar darduma duk sun harde kafafunsu suna cin abinci, farhan
ya kalli mahaifinsa abeed yace" abu itama andal akaita mkrt mn" dago dakai abeed
yyi ya kalli 6angaren da bimbii ke zaune yace" andal wai kina son mkrt" murmushi
bimbii tayi tace" ehh abu ina so" kallonta farhan yyi ya kalli cikinta daya dan
turo sosai ya ta6e baki ya cigaba da cin abincinsa, ummu farhan ta kalli abeed
tace" amma dai ba yanzu ba saita haihu tukunna" farhan ya dago ya kalli bimbii
yace" nikam ban ta6a ganin yarinya qarama kamar ki da ciki ba" iyayen nasa ne
sukayi saurin kallonshi tare da harararsa sai yyi saurin sunkuyar dakansa qasa,
shima kawai zancen ne ya kubce masa sbd ya tsani ganin wannan ciki a jikin bimbii
da suke kira da andal, bimbii kuwa tsuru tayi tana son tuna wani abu amma
kwakwalwarta ta toshe duk wata kafa ta tuna mata abunda ya faru da ita a baya, ummu
farhan ce ta dafata da murmushi a saman fuskarta tace" andal ko bacci kkji ne" daga
mata kai tayi alamar ehh, kamo hannunta tayi suka miqe suka nufi dakin kwanan
bimbii, gyara mata wurin kwanciya tayi tace" ki kwanta saida safe" kallonta bimbii
tayi tace" Allah ya bamu alheri" murmushi tayi ta sunkuya ta shafa kan bimbii tace"
ameen summa ameen"bimbii cikin dare ta tashi zaune, bayanta taji ya riqe qam ga
wani irin ciwo da mararta take mata duk ta hada gumi, hk ta din ga fama har asuba
tayi ta soma jin motsin abeed da farhan zasu fita masallaci, tana cikin wannan hali
ummu farhan ta shigo dakin, cikin sauri ta qarasa wurin da bimbii ke durqushe riqe
da mararta, tace" andal mene ke damunki,kiyimin mgn" bimbii ba bakin mgn sai idanu
kawai take bin ummu farhan dashi, ummu farhan kam tasan ba haihuwa bane sbd cikin
nata bekai mizanin haihuwa ba saidai idan wani ciwon ne daban, ruwan zaitun da zuma
ta bata ta sha, suna cikin hk su abeed suka dawo, farhan ne ya shigo dakin ya tarar
da abunda ke faruwa, shigowa yyi cikin dakin a rude yana kiran suna bimbii, tana
jinsa amma ba bakin amsawa, juyawa yyi ya fita da sauri ya sanarwa mahaifinsa,
abeed ya shigo shima cikin dakin, farhan ya kalli mahaifinsa yace" ina ganin kawai
mu wuce da ita asibiti" kada kai abeed yyi alamar hk za'ayi, cikin wannan safiyya
farhan da abeed suka fita, suna fita suka tarar da wani tsoho yana jan keken
dokinsa, alfarma abeed ya roqeshi kan ya amince ya fitar dasu bakin babban hanya ko
zasu samu abun hawa zuwa asibiti,wannan majanyin keken doki kuwa ya amince suka
fito da bimbii suka sanyata ciki tare ummu farhan mai keken dokin yaja suka tafi,
sunyi tfy mai nisan gaske kafin suka isa bakin hanyar motoci ke wucewa, dakatawa
sukayi har su abeed suka qaraso sannan suka tsayar da wata mota suka shige, daidai
king faisal specialist hospital motar tasu ta tsaya suka fito dukkaninsu har da
bimbii, suna shiga hospital din wadanda ke yawo da gadon daukar marasa lfy suka
dauki bimbii suka shige da ita,wata nurse ta wuce da gudu zuwa office din doctorn
dake kula da wannan 6angare ta sanar masa an kawo wata patient mai juna biyu dake
buqatar taimakon gaggawa, doctorn be dago kai ya kalleta ba saida ya gama danne
dannensa a laptop din dake gabansa sannan ya dago dakansa yace" kije gani nan zuwa"
juyawa tayi ta fita sbd idan da sabo duk sun saba da halin DR.MAHEER mugun dan I
dnt care akan patients, hknlinsa kwance ya miqe ya fita daga office din nasa,
farhan da abeed na ganin fitowarsa suka nufo shi da sauri, be sauraresu ba yyi
wucewarsa cikin dakin da bimbii ke kwance,qarasawa yyi bakin gadon da take yana
kallon ruwan drift din dake shiga jikinta sannan ya maida dubansa ga saman
fuskarta......wani irin bugawa gabansa yyi da karfi ya qurawa fuskar bimbii idanu,
tabbas shidai yasan bazai ta6a mance wannan fuskar ba cikin rayuwarsa, fuskar da
kullum take masa gixo ba dare babu rana, mamaki yyi mutuqa na ganin ciki a jikinta,
juyawa yyi ya kalli nurse din dake gefensa ya nuna cikin dake jikin bimbii yace"
meye wannan a jikinta" nurse din kallonsa tayi cike da mamaki sai kuma ta kalli
cikin bimbii dayake nunawa da hannu tace" tana da ciki ne doctorn" cikin tsantsar
rudewa yace" what!" nurse din sai abun ya soma bata tsoro ta soma kallon Dr.maheer
da tarin mamakin wannan action din nasa, yace" waye ya kawota" tace" wadanda suka
kawota suna waje" juyawa yyi da sauri ya fita yana fita farhan yyi saurin shan
gabansa yace" yy jikin nata" tsayawa yyi yana qarewa farhan kallo tun daga sama har
qasa sannan yace" kaine ka kawota?" cikin sauri yace" ehh, nine" Dr.maheer yace"
kai waye nata?" kai tsaye yace" mata ta ce" wani irin kallo maheer ya masa sai kuma
ya juyar dakai yana wani irin murmushi mai ciwo, cike da axama ya juya ya chakumi
kwalar rigar farhan da idanunsa da suka kala sukayi jazir, ummu farhan da abeed
dake gefensu sukayi saurin qarasowa wurin suna mamakin abunda ya hada Dr.maheer da
farhan, maheer da idanunsa suka juye sbd tsantsar bala'en kishi ya kalli kwayar
idanun farhan yace" kasan wacce ita a wuri na kk fadamin wannan iskancin nk" farhan
da idanunsa suka firfito sbd tsaurin shaqar da maheer ya masa yace" kaima kasan
wacce ita a wuri na" hknne yasa maheer yyi jifa dashi gefe daya, yace" wlh,wlh
bazan kyaleka ba saika fuskanci hukunci" wucewa yyi a mugun fusace ya wuce office
dinsa yasa key, nurses din dake tsatstsaye da sauran ma'aikatan asibitin kowa ya
cika da mamakin wannan abu, Dr.maheer kuwa kifa kansa yyi kawai a saman table din
dake gabansa ya fashe da kuka tamkar wani qaramin yaro, meyesa bimbii tayi masa hk,
meyesa bimbii ta bawa waninsa dama har ya ratsa gonar da ba tashi ba, shikam ko a
ido ya raina shekarun farhan amma wai wannan danyen yaron bimbii ta baiwa kanta yyi
mata wannan danyen aiki, tsananin so tare da tsantsar qiyayyar bimbii su sukayi
tarayya cikin zuciyarsa, shi kansa ya rasa wanne ne yafi rinjaye, miqewa yyi a
hnkli ya dauki handkerchief dinsa ya goge hawayen fuskarsa sannan ya dauki farar
rigarsa ta likitoci yasa ya bude office dinsa ya fita, dakin da bimbii take ya
shiga ya tarar da nurses sun zagayeta don bleeding take sosai, suna ganin
shigowarsa suka bashi wuri, kai tsaye ya soma gudanar da aikinsa akanta batare daya
kuma kallon fuskarta ba, cikin izinin Allah ya samu nasarar tsaida jinin dake zuba
sannan ya mata allurar bacci mai nauyi, yana gama aikinsa ya fito daga dakin ko
kallon inda su farhan suke beyi ba saida abeed ya miqe da sauri yasha gabansa yace"
kayi hkr abunda yaro na ya mk don Allah ka dubamin diyata dakyau" kallon mamaki
maheer ya masa sai kuma yyi murmushi yace" ka ta6a ganin inda mutum yyi wasa da
rayuwarshi?" dukkaninsu kallonsa sukayi don basu fuskanci me yake nufi da hk ba, be
sake kallonsu ba ya koma office dinsa, farhan dogarewa yyi daidai bakin dakin da
bimbii take har lkcin da nurse ta basu damar shiga su ganta, cikin sauri duk suka
miqe suka shige dakin, samunta sukayi tana bacci, farhan ya zauna gefenta yana
kallon fuskarta yana hararar cikin dake jikinta don gani yake duk wannan cikin ne
ke wahal da ita,ummu farhan riqo hannun bimbii tayi tana mata addu'ar samun lfy,
ranar Dr.maheer a asibiti ya kwana ya kasa tfy gida, bini bini ze leqa dakin da
bimbii ke kwance, idanunsa kuwa sunyi jajir sbd kukan daya sha, kishi ne kawai ke
wahal dashi mutuqar ya bude idanu yaga bimbii dauke da jikin waninsa sai zuciyarsa
tayi daci,6angaren masarautar burham kuwa har yanzu sarki abdallah bin jabal na nan
kan bakansa, wannan abu dake faruwa shine ya bawa prince nasaar damar samun shiga
sosai wurin sarki abdallah, prince nasaar ya samu cikakken iko da fada aji cikin
wannan masarauta ta burham, hkn shine ya bashi damar fito da abunda ya jima a qasan
ruhinsa wato daukar fansa kan sarki abdallah bin jabal, prince nasaar da ne ga
sarki hamxa mai sarautar birnin al' bait, sarki abdallah bin jabal shine silar rusa
wannan kyakykawan birni ya dawo dashi qarqashin mulkinsa, qarfi da shahara da
masarautar burham ke dashi idanun duniya yasa batare da wani jayayya ba sarki hamxa
ya miqa wuya ga sarki abdallah bin jabal inda birninsa ya dawo qarqashin inuwar
masarautar burham, sarki abdallah dakansa ya nemi sarki hamxa ya bashi riqon prince
nasaar tun yana qarami sbd yana son masarautarsa ta qulla zumunta ta musamman da
masarautar al'bait, wannan shahara da daukaka da masarautar burham ta samu ya mugun
tsolewa masarautu da dama idanu burinsu su durqusar da wannan izzah ta sarki
abdallah bin jabal, prince nasaar babban burinsa shine masarautar burham ta dawo
qarqashin izzah da sarautar birnin mahaifinsa, wannan kudiri nasa yasa shi cigaba
son cigaba da kasancewa cikin wannan masarauta yana aikawa da sirrin wannan
masarauta birnin al'bait saidai har wayau masarautarsu batayi tsayin da zata iya
hada kafada da masarautar burham ba, prince akbar ya kasance babbar garkuwa ga
wannan masarauta ta burham sbd tsantsar jarimtarsa hadi da sharp intelligency nasa,
rufe prince akbar da sarki abdallah yyi ya baiwa tarin maqiyansa na ruguza
masarautar burham ne batare daya fahimci hkn ba,prince nasaar ya samu yarda da
amincewar sarki abdallah sosai, prince akbar yasa bimbii cikin qalbinsa, zuciya da
gangar jikinsa bimbii suke buqata, yau tsawon watanni hudu kenan yana rufe amma
bimbii bata ta6a 6acewa cikin tunaninsa ba,yau da dare yana zaune ya kalmashe
kafafunsa ya jingina da jikin qarfen kurkun, idanunsa a lumshe suke yana tuna duk
wani kyakykyawan memory nasa da bimbii,muryar mahaifiyarsa yaji tana masa mgn
tace" ina son kayi yadda mahaifinka keso ka mance da wannan baiwar, cikin jikinta
ba nk bane daman ai, ka furta hkn gaban kowa, mahaifinka yana yin hkne duk don ya
kare muhibba da daraja na wannan masarauta, ina son ka bashi hadin kai" shiru
prince akbar yyi sai kuma ya bude idanunsa ya kalli mahaifiyarsa dake hawaye tana
kallonsa yace" ranki ya dade idan har na furta hkn nayi qarya, cikin dake jikin
wannan baiwa nawa ne bana wani bane sbd me zan qaryata hkn,kar ki damu dani ko
halin da nk ciki a yanzu koda na fita daga nan ba lalle rayuwa tayi tsawo ba nima,
nafi son nima na tafi na bar wannan duniya mai cike da rudani" kuka sosai sarauniya
take tace" kafi fifita soyayyar mace fiye da soyayyar mahaifiyarka yarima" kallonta
yyi sosai yace" soyayyarki ta daban ce cikin ruhina baki da mahadi nan duniya ranki
ya dade" murmushi tayi hade da kuka a hade ta zauna dakanta take bashi abinci a
baki cike da qauna,hmmm,uwa uwace Allah kabarmu da iyayenmu ka bamu ikon faranta
musu, soyayyar uwa soyayya ce da babu alqus so ne na haqiqatan, idan mutanen duniya
dukka sun gujeka uwarka tana nan tare dakai.............

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar karantawa zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir, saiki turon da screesht ta wannan layi a
whatsapp...07041195806......

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

30

*Without you in my life there is no happiness*.....how long can I wait for you my
love💕💕

Cikin dare ta farka ta bude idanu ta ganta kwance bisa gadon asibiti, dakin babu
kowa sai ita kadai, qoqarin miqewa take zaune taji duk jikinta yyi tsami tamkar
wacce ta shekara tana jinya, ciza le6enta tayi ta miqe zaune dakyar, kofar dakin
taga an turo ta waiga da sauri ta gano ummu farhan, tana ganinta zaune ta qaraso da
yalwar fara'a a fuskarta tana mata sannu da jiki,daga kai kawai bimbii tayi,kamar
yadda ta saba mata cup ta dauka ta zuba mata zuma a ciki ta bata ta shanye,
shigowar Dr.maheer cikin dakin ne yasa su kallon kofa, tsayawa yyi chak yana qarewa
bimbii kallo da take zaune riqe da cup a hannunta sannan ya soma takowa a hnkli ya
qaraso wurin gadon da take, kallon dayake mata ne yasa ta dago da kanta ta kalleshi
suka hada idanu, sam ita bata gane shi ba amma mamakinta shine meye yasa hk kawai
shi wannan mutum ze tsareta da idanu hk, Dr.maheer kuwa tsabar mamakin bimbii ne ya
qamar dashi a wurin ganin yadda ta nuna 2kwata bata ma gane shi ba, kallonta yyi
sosai ya nuna mata cikin dake jikinta yace" wannan meye a jikinki" ummu farhan
kallon maheer tayi galala sai kuma ta mayar da dubanta kan bimbii data sunkuyar
dakanta tana kallon cikin dake jikinta, yace" daman hk kk ban sani ba, sai yanzu na
fahimci abunda yasa ki gudu wato sbd baki samun abunda kk buqata koh" dukkaninsu
kallon maheer suke da tarin mamaki musamman bimbii da ko kusa bata fuskanci inda
zancen Dr.maheer yasa gaba ba, kallon ummu farhan bimbii tayi ta nuna maheer da
hannu tace" ummu wannan waye shi" murmushi ummu farhan tayi tace" shine likitan
daya duba ki" murmushi bimbii tayi tace" toh meye yake fada hk" dafata ummu farhan
tayi tace" ki bar wannan mgn zamuyi anjima" wannan abu ba qaramin fusata Dr.maheer
yyi ba yace" kin manta dani koh sbd kin samu tsinannen daya la'anta
rayuwarki,uhumm" miqewa ummu farhan tayi cike da fushi tace" ya isheka hk mn, baka
ganin halin da yarinya ke ciki ne kk takura mata da wasu zantuttuka nk" bimbii ta
kalleta tace" ummu wai meye ke faruwa ne dani" daidai lkcin abeed da maheer suka
shigo suka tarar da abunda ke faruwa, farhan ya kalli Dr.maheer yace" wai kai waye
ne kk takura mn" murmushi Dr.maheer yyi ya fizgo hannu bimbii ya cire mata drift
din dake hannunta tunda ya riga ya qare sannan ya dago dakansa ya kalli farhan
yace" nine mamallakinta gbdy" abeed ya kalli Dr.maheer yana son mgn kuma sai yyi
shiru can dai ya dago dakansa yace" doctor ita wannan da kk gani tana da matslr
lose of memory bazata gane abunda kk fada ba yanzu" saurin kallon bimbii maheer yyi
cike da mamaki, farhan kuwa haushi ne ya cika shi, ita kuwa bimbii kallon kowa take
a wurin galalau tamkar wata sakarya sbd bata fuskanci abunda yake faruwa ba, juyawa
abeed yyi ya fice daga dakin Dr.maheer yabi bayansa, office din Dr.maheer suka
shiga ya nuna masa wurin zama ya zauna, 2tiryan abeed ya labartawa Dr.maheer
yanayin daya tsinci bimbii, shiru yyi ya kasa mgn, dago dakansa yyi yace" kaima
bakasan waye da cikin jikinta ba kenan" kada kai abeed yyi alamar ehh, gbdy kansa
ya kulle ya rasa abunda ke masa dadi, miqewa yyi ya fice daga office din shima
abeed ya miqe yabi bayansa, batare da wani 6ata lkci ba Dr.maheer ya nufi
neurologists dept ya samu Dr.waaz suka tattauna, washegari aka sanya bimbii cikin
wani na'urar don't bincika mtslr dake faruwa da kwakwalwarta, abunda suka gani
kawai shine ta samu temporary lose of memory amma with time insha'Allah all past
events ze din ga dawo mata cikin brain nata, cikinta dake jikinta kuma yana da
watanni shida da kwanaki, lkcin daya ga result din shiru yyi sbd shi sai yanzu ne
yarda tayi losing memory, kwananta uku sukayi discharge nata amma 2qiri Dr.maheer
ya nunawa abeed wlh bimbii wurinshi zata koma tunda ita din property dinsa ce yana
da certificate na mallakarta, farhan da umminsa suka doge kan basu san wannan zance
ba, Dr.maheer yace" idan kunki bani ita da arziki toh hukuma zata bani ita" abeed
mutum ne mara son hargitsi tashi daya ya damqawa Dr.maheer bimbii, farhan baqin
ciki kamar ze kashe shi, ranar qin yiwa kowa mgn yyi, bimbii kam bata san abunda ke
faruwa ba sai wayar gari tayi ta nemi wannan iyali ta rasa sun tafi sun barta a
asibitin ko sallama abeed be bari sun mata ba sbd kar hnklinta ya tashi ko kuma
taqi amincewa, Dr.maheer ya shigo dakin dakansa ya sanar mata tfyrsu sannan ya
shaida mata duk abunda ya faru, yace" yanzu gida na zaki koma da zama" wani irin
kallo ta masa mai kama da harara sai kuma ta fashe da kuka tace" kai wanne irin
mutum ne hk kawai zaka rabani da dan'uwana da iyayena" murmushi yyi yace" su waye
iyayen nk? uhum, ko ban furta miki ba kina kallon launin fatarki da nasu kinsan
basu ne iyayenki ba ai suma tsintarki sukayi da cikin da basu san daga inda kk samo
shi ba,kona arziqi kona tsiya nafi gani ma dai na tsiyan ne" qura masa idanu tayi
kawai tana sauraron baqaqen maganganun dake fita daga bakinsa kan cikin dake
jikinta da ita kanta batasan a ina ta same shi ba, murmushin rainin hnkli ya mata
daya ga tana kallonshi ya noqe kafadarsa tare da ta6e baki, badan ta so ba hk ta
tashi tabi bayan Dr.maheer suka fita daga dakin suka fice compound na hospital din
sai 2waige take ko zata gano ummu farhan ko farhan amma bata ga ko masu kama dasu
ba, bude mata mota Dr.maheer yyi ta doge taqi shiga saida ya matso da niyyar
daukanta ya cusata ciki tayi saurin shiga motar,farhan kuwa yana la6e daidai gate
din fita daga hospital din yana kallon fitowarsu, hawayen dayake 6oyewa suka soma
sauka kan quncinsa yana kallo har suka fice daga hospital din, tana ta 2kalle ta
jikin glass din motars, har suka qaraso wani wurin inda ta hango tarin mahaya
dawakai suna wucewa, wannan abun yaso tuna mata da wani abu amma ta kasa tunawa
dole ta hkr, suna shiga farfajiyar gdn yyi parking yar motar shi gefe sannan ya
fita ya bude mata ta fito, sai kallon gdn take har suka shiga building din
maheer,two bedroom flat ne don hk ya bata daki daya, zama tayi a dan qaramin
parlourn nasa sai qarewa ko'ina kallo take, shi kuwa ya shige bedroom nasa sai can
ya fito sanye da three quater baqi da wata shirt ya shiga kitchen dakansa ya hada
mata black tea da honey meast ya kawo gabanta ya ajiye, sannan ya tafi ya gyara
mata bedroom din nata, ni kuwa nace lalle yaushe maheer ya zama bawan baqar
fata,dakyar bimbii ta yarda tasha black tea, nuna mata dakinta yyi ta tashi ta
shiga, dakin madaidaci mai kyau, ita gabanta har yanzu be bar faduwa ba sbd ta lura
tunda ta shigo wannan gd bata ga matar gdn ba, tashi tayi da sauri ta sanya key ta
rufe kofar sannan ta koma ta kwanta, maheer kuwa yazo ya buga ya buga taqi budewa
so yake ta fito tayi dinner amma qirmishishi taqi bude kofar kuma tana jinsa sarai
hk ya hkr ya koma yyi dinner dinsa shi kadai, bimbii kuwa kwanciya tayi ta
matsantawa kanta da tunani don tana son tuna abubuwa amma kwakwalwarta tamkar ta
toshe hk har kanta ya soma sara mata, hk bimbii ta cigaba da rayuwa a gdn maheer
shi kuwa yana qoqari wurin bata kulawa yana ture damuwarsa kan cikin dake jikinta,
ennah mahaifiyar maheer har yanzu batasan maheer ya gano baiwarsa ba don be sanar
da ita ba hkma yayansa, masarautar burham kuwa tsantsar makirci ne yake kai kawo a
cikinta, sarki abdallah yaqi sakin prince akbar duk kuwa da iyakar qoqarin neman
afuwa da sarauniya keyi a madadinsa kullum ba dare ba rana amma sarki abdallah bin
jabal shegen taurin kai ne dashi tamkar na kafiran farko, sarki abdallah yana zaune
a dakin ganawar sirri shi da prince nasaar suna tattauna kan yadda zasu buda harkar
kasuwanci tsakanin masarautar burham da manyan qasashe na turai, sarki abdallah bin
jabal yana daya daga cikin manyan merchants na duniya dake fita da danyen gold a
kasuwar duniya, shiyasa ya tara arxiki na ban mamaki, prince nasaar ya fito da wani
qaramin akwati ya ajiye a gabansa yace" takardar yarjejrniyar kasuwanci ne tsakanin
wannan masarauta da qasar japan" saurin daukan qaramin akwatin sarki abdallah bin
jabal yyi ya bude, wata farar takarda ya gani a ciki kai tsaya yasa hannunsa ya
fito da takardar ya soma warwarewa, prince nasaar yana kallonsa har ya gama warware
farar takardar, hannunsa ne daya riqe takarda ya soma rawa sosai sbd qarfin gubar
dake tattare da wannan takardar, dago idanunsa yyi yana kallon yana son yin mgn
amma ya kasa,shi kuwa prince nasaar sai zabga murmushin qeta yake yana kallon sarki
abdallah dake jan jiki,abunda ya shirya ya tafi daidai, mirqinewa sarki abdallah
yyi daga kujerar dayake yana qoqarin nuna prince nasaar da hannu, prince nassar
ficewa yyi daga 6angaren yana fita ya tura babbar hadimar sarki abdallah ciki kan
sarki na buqatar ganinta tana shiga ta tarar da sarki abdallah cikin wannan
yanayin, da gudu ta fito tana sanar da masu tsaron lfyrsa, arresting dinta sukayi
kan itace tayi poisoning dinsa, wannan lbri tuni yakai kunnen sarauniyya
mar'atussaliha, a gigice ta iso 6angaren ta tarar da gubar ta soma shiga jikinsa
sosai,prince nasaar kuwa batare da wani bincike ba yasa takobinsa ya cire kan
wannan hadima kan ita tayi poisoning din sarki, sarki abdallah kuwa ba bakin mgn
balle ya furta abunda ke bakinsa yana son yin mgn amma ya kasa sai kallon nasaar
yake, miqewa sarauniya tayi ta umarci kowa ya fita aka barta daga ita sai uxair sai
kuma sarki, prince nasaar yaso ya tsaya amma sarauniya ta nuna shima ya fita dole
ya juya ya fice,kallon uxair sarauniya tayi tace" ina son ka haxarta kai tsaye kaje
a fito da prince mahaifinsa na son ganinsa" rissinar dakai uxair yyi alamar ya amsa
umarninta sannan ya fita, kallon qaramin akwatin dake gefen sarki abdallah tayi ta
qurawa akwatin idanu, prince nasaar kuwa tuni ya sanar da prince amir cewa aiki ya
kammala, zaki ya kwanta dama wato sarki abdallah kenan, zaki ya kwanta dama shi
kuwa dan zaki yana rufe, wannan itace kyakykywan dama da zasu iya amfani da ita
wurin murqushe wannan masarauta ta burham, dayake a shirye suke tsaf tuni suka
zagaye wannan masarauta da dakarunsu masu qarfin kayan yaqi, prince nasaar dakansa
yasa a cinnawa
wannan gdn kurku da prince akbar ke ciki wuta sbd so yake ya 6atar da tarihin
sarki abdallah bin jabal da dukkanin ahlinsa, sarki najash wato mahaifin prince
amir ya riga ya alqawarta ma sarki hamxa idan har ya taimaka musu suka ga bayan
masarautar burham toh zasu samu cikakken dama wurin gauraya da manyan qasashen
duniya musamman qasashen jar fata wurin kasuwanci, suna ganin kamar masarauta
burham ita ta babbanke komai sbd tana da qarfi, su" 2kwata ba'a damawa dasu a
kasuwar duniya........
Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar karatun littafin zaki tura #300 ta
wannan acct...0100790419, alhaji shahida nasir,union bank,saiki turon da screenshrt
na payment dinki a whatsapp ta wannan layin...07041195806......

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

31

*I miss you like crazy*....I will keep up waiting until the end of my last breath
💕💕

Idanunsa na lumshe ya jingina da jikin qarfen kurkun yaji ana bude wurin dayake,
dago idanunsa yyi sukayi idanu hudu da uxair babban hadimin mahaifinsa, kallon
prince yyi ya rissinar dakai sannan ya qara bude masa kofar fita yace" yakai wannan
dan sarki mahaifinka na son ganawa dakai" shiru prince akbar yyi sannan ya miqe
suka fito, fitarsu kenan suka ga wuta ta kama wannan gdn kurku sai kururuwar mutane
ake jiyo daga cikin wannan kurku, cike da mamaki prince ya kalli uxair yace" wannan
ne dalilin dayasa kk fito dani sbd ku kashe bayin Allah marasa gata" girgixa masa
kai uxair yyi yace" yakai wannan dan sarki wannan sharrin abokan gaba ne yanzu hk
sun sanyawa mahaifinka guba yana cikin wani hali sannan gbdy masarauta a zagaye
take da dakarunsu kowanne lkci zasu iya cimmu a yaqi" kallon prince yyi yace" yakai
wannan hadimi ma'abocin kwarjini ina son ka dakata anan ka bada taimako wurin kashe
wannan wuta" batare daya jira amsar uxair ba yyi wani irin tsalle ya haye dokin
daya gani gabansa ya sakar masa linzami yyi hanyar da zata sadashi da masarautar
burham, tun tahowarsa bisa doki kwararrun maharba mashi suke saitinsa, suna la6e ne
bisa kan manyan tsaunika saitinsa kawai suke da mashi, abunku da jarimin gaske
jikinsa ne kawai ya bashi tamkar akwai masu harinsa, cikin tsantsar hikima da zafin
nama ya juya kan dokin dayake kai suka bar kan miqaqqiyar hanya suka fada cikin
jeji, su kuwa maharan suna ganin hk suka tabbatar ya fahimci ana harinsa ne yasa
yyi musu hk, dayake jejin na da duhu da sarqaqiya tuni ya soma shiga wannan
sarqaqiya har ya samu damar 6ace masu ya fice daga wannan jeji, saidai tun daga
nesa ya hango qatuwar kofar masarautar burham a rufe, wasu manya dakaru sun zagaye
kofar ta waje suna son fasa kofar su afka ciki, qara gudun dokin yyi ya tunkari
wannan rundunar mayaqan, ba jira kawai ya janyo wani bisa doki yyi wulli dashi ya
amshe takobin hannunsa ya daga takobin sama tsirararta kafi kace kwabo kawai ya
soma shayar da wannan takobi dake hannunsa jinin abokan gaba, wata irin bajinta
yake nunawa tamkar wani ifiritin aljani hk yake fada ba gjywa, dakarin masarautar
burham dake saman qanuwar masarautar suna hangen artabun dake wakana tsakanin
wadannan dakaru da babban prince, fada yake cike da sadaukarwa batare da shakkar
mutuwa ba domin zuciyarsa ta bushe qamas baya tsoron mutuwa ko kadan, daga idon da
zeyi ne ya hango prince amir dakansa ya saitinshi da mashi, yana harbo mashin ya
damqo wani daga cikin mutanensu ya tare mashin dashi,gbdy jikinsa ya 6aci da jini
sai lkcin masu tsaron babbar kofar shiga masarautar burham suka wangale kofar
dakarin sarki abdallah suka soma fitowa sanye da shigar yaqi saidai lkcin prince
akbar shi kadai kawai ya riga yaci qarfin yaqin, abun mamaki prince nasaar na cikin
dakarin masarautar burham domin har yanzu babu wanda ya fahimci fuska biyu ne
dashi, tsayawa yyi yana kallon yadda prince yyi musu 6arna, tsoronshi daya kar suyi
failing plan dinsu sbd idan har aka samu mtsl tabbas daga shi har mahaifinsa suna
cikin mtsl don sun san masarautar burham saita dauki fansa akansu, shiga cikin
wannan filin artabu ya somayi sai yyi kamar yana yaqar dayan 6angaren, prince akbar
kuwa yana tsaka da fatattakar wannan dakaru ya hango fitowar dakarin mahaifinsa
sanye da shigar yaqi, juyawa yyi ya cigaba da 6arar da maxa abinsa, prince nasaar
cikin hk ya samu qarasowa kusa da prince akbar, prince ya ganshi amma ya dauka a
6angarensu yake don hk ya juya ya cigaba da fadansa, ba zato kawai yaji saukar
takobin prince nasaar a qirjinsa, juyawa yyi yana kallon prince nasaar da mamaki
yaga ya sake daga takobinsa da niyyar yanke kansa cikin zafin nama ya bige dokin da
prince nasaar yake kai ya fadi qasa yasa sawun dokinsa ya takeshi ya wuce abinsa,
takobin daya sara masa bata samu damar ratsa shi sosai ba don hk ya cigaba da wasa
da jinin abokan gaba, cikin qanqanin lkci suka musu kyakykywar 6arna, tsirarun
dakarinsu sarki najash suka soma ja da baya suna neman gudu, prince amir kuwa ya
dade da arcewa tunda yaga 6arnar da ake musu daman shi ba wani jarimi bane a filin
fama barshi dai da iya hada tuggu, lkcin da prince yaga abokan gaba sun soma arcewa
sai yaja gefe ya sauke takobinsa qasa sai digar da jini take ya nufi wurin da
abokan gaban suka kafe tutarsu ya tugeta ya jefar, salute kawai dakarin masarautar
burham suke masa cike da girmawa, hk suka soma shiga cikin babbar kofar masarautar
burham cike da murnar samun nasara akan abokan gaba, tun daga kofa yan mata ne jere
sunyi ado suna rera waqar yabo da jinjina ga jarimai mazan fama wadanda suka
sadaukar da rayuwarsu sbd kare mutunci masarautarsu, suna rera waqar ne cikin
harshen larabci hannunsu dauke da furanni suna watsa musu suna daga musu hannu
alamar barkansu da dawowa lfy, prince kuwa fuskar nan tashi tamkar hadari sai bin
dokinshi suke suna zuba masa fure suna masa baitoci da jinjinar ban girma bisa
namijin jarumtarsa, cikin waqar tasu suna danganta shi da zaki dan zaki, jarimtar
gadonsa ce ba haure ba, hk dai suka din ga binsa da baitocin yabo har ya isa cikin
gdn sarautar burham, nan ma ya samu tarar girma ga dukkanin bayi da masu tsaron
wannan gida hk suka raka shi da baitoci, sarauniya na 6angaren sarki abdallah
wannan lbr na isowar danta ya taddata, ummu nana ta sanar da ita prince akbar shine
yyi uwar watsi da maqiya ya kuma cire musu tuta, wannan kyakykywan labari yasanya
xuciyar sarauniya tayi haske duk da alhinin da take ciki na ganin sarki abdallah
bin jabal kwance rai a hannun Allah, tana zaune gefen sarki abdallah prince ya nemi
iso take ta bashi damar shigowa, cikin sauri ta tashi ta rumgume shi tana kuka sai
kuma ta soma duba jikinsa ko ya samu rauni, murmushi yyi ya riqe mata hannunta suka
qarasa inda sarki abdallah bin jabal ke kwance, kallon mahaifin nasa yyi sosai yana
nazarin symptoms na poison din dake jikinshi, hannu yasa cikin aljihunsa ya fito da
wata qaramar kwalba ta antidote din daya ta6a baiwa bimbii ya bude bakin mahaifin
nasa ya tsiyaya masa, wannan antidote shima dattijo abbas ne ya ta6a bashi lkcin
daya ceto rayuwarsa a hannun sarki najash, antidote din yana kashe qarfin kowanne
irin guba, sarauniya ta kalleshi tace"ka gafarci mahaifinka bisa kuskurensa gare ka
yakai wannan jarimin dan sarki" riqo hannayenta yyi yace" komai laifinsa gare ni
mahaifina ne shi dole ranki ya dade" murmushi tayi kawai,prince ya jima a 6angaren
mahaifinsa suna tattaunawa da sarauniya kafin ya dawo 6angarensa, komai na 6angaren
nasa yana nan yadda yake sannan bayin dake hidimtawa 6angaren kowa yana kan
aikinsa,lenah itace daman mai kula da makwancin prince 6ata wasa da aikinta, ubaid
yana shima yana kan aikinsa, prince yana shiga ya bada izini baya buqatar ganawa da
kowa, lenah ce kawai ta samu damar shiga ciki, batare da 6ata lkci ba tayi masa
gyaran fuska ta wanke masa qafa, ta rage masa tsawon suman kansa data sauko masa
har baya tamkar gashin mata ta maida shi ya dawo kafadarsa,tuni sumar tasa ta soma
walwali da sheqi tana daukar idanu, duk abunda take gani yake kamar bimbii ce take
masa hidima,6angaren gidan maheer kuwa bimbii bata masa aikin fari bare na baqi
komai shine yakeyi dakansa, idan ya dafa abinci tunkan yaci ze kawo mata nata ya
zauna ya sata gaba har sai taci sannan zeci nashi, wani lkci idan ya zauna yana
kallonta sai ya qurawa cikin jikinta idanu ya tunanin uban waye da wannan ciki, ji
yake tamkar idan ya hadu da wanda yyi cikin nan ze iya kashe shi sbd baqin kishin
dayake ji idan ya kalli cikin amma a hk dole yake daurewa yake hidimta mata sbd
qarfin so daya rinjayi qarfin qiyayya, kullum idan ya shirya fita aiki sai ya ajiye
mata komai kusa da ita tamkar wacce bata iya motsi sannan baya fita sai ya tabbatar
ya rufe duk wata kofar fita ta gdn, gani yake kamar idan yabar kofa bude bimbii
zata sake guduwa ta fice daga rayuwarsa ta barshi da dawainiyya da dakon
soyayyarta, idan ya dawo sai ya dubata ya tabbatar ita da abunda ke cikinta suna
cikin qoshin lfy, fatar jikinta tuni ta murje tayi kyau da santsi sbd cima da take
samu mai kyau da gina jiki,duk bala'I bata bari maheer ya matso kusa da ita tuni
zata matsa nesa dashi, wannan abu yana masa ciwo amma Allah ya dorata akansa yadda
komai takeso shi yake tamkar wani bawanta,ranar wata laraba ennah mahaifiyarsa ta
kawo masa ziyarar bazata, lkcin data ga bimbii abun ya mugun bata mamaki da daure
mata kai musamman data ganta da ciki, kallon Dr.maheer tayi tace" a ina ka samota"
sosa qeya ya somayi yace" a asibitinmu mn" wata uwar harara ta doka masa tace"
shine baka fadamin ba yaushe ka soma 6oyemin abu" murmushi yyi yace" sorrryy" cikin
wasa ya furta hkn ya soma riqe mata hannu, fizgewa tayi cikin fushi ta kalleshi
tace" wannan cikin dake jikinta na uban waye?! ko kana nufin kacemin a hk ga gano
ka kuma amince ta dawo gdnka sbd kai daqiqi ne" kalaman mahaifiyar tashi sun masa
tsauri sosai tuni ya tamke fuska, sam shi be saba ganin ennah na masa fada ba ta
shagwa6a shi dayawa, batare data kula da hade ran daya yyi ba ta dokawa bimbii
tsawa tace" ke cikin uban waye a jikinki" bimbii kuwa jikinta rawa yake ta tsorata
da matar kawai kallonta take ta kasa mgn, ennah ta nunawa bimbii hanyar fita tace"
ina son ki fita ki kama gabanki ko waiwaye wannan gdn kar ki kuma yi" saurin
kallonta maheer yyi yace" what are talking, did you mean ta tafi ta barni kenan"
murmushi yyi yace" idan ta tafi nima zan bita mu tafi tare cox she is my life"
galala ennah tayi tana kallon abun mamaki..............

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar karantawa zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419, alhaji shahida nasir,union bank, saiki turon da screenshrt ta
whatsapp through wannan layin....07041195806.......

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer


32

*Come back to me my love*......I can't hold back my tears, I can't forget your
beautiful face,I'm missing everything about you my sweetheart💕💕

Ennah ta daka masa wata rikitacciyar tsawa tace" are you in your right sense? kai
makaho ne baka ga abunda ke tare da ita bane, maheer mai ke faruwa dakai ne, just
cox of this stupid slave you are exchanging word with your mother" bimbii kuwa
jikinta na rawa sbd tsorata da tayi ta soma qoqarin fita ta gudu, charaff, maheer
ya riqe mata hannu, kallon ennah yyi yace" I just want to marry her" wata irin
zabura ennah tayi tana masa wani irin kallo irin wanda ake yiwa masu ta6in
kwakwalwa, tunani ta somayi anya maheer be samu matsl a brain nasa ba kuwa,
murmushi tayi kawai ta juya ta fice daga gdn gbdy ta shige mota driver nata yaja
suka nufi gd, tun a mota zuciyarta ke kai kawo da tunani barkatai game da
bimbii,tana isa gd ta kira faisal tayi masa bayanin kan abunda ya faru, shiru yyi
sai can yace" kinsan rigimar maheer amma ina ganin kawai abunda yafi ki dauki
yarinyar ki mayar da ita kasuwar saida bayi inda kk siyota ki musanyo da wata amma
kar ki kuma kawo mn baqar fata" murmushi tayi tace" hkn ya kamata nayi kam" maheer
kuwa dakyar ya rarrashi bimbii yyi ta bata hkr kan kar ta damu babu inda zata
mutuqar yana raye, washegari, ya shiga kitchen ya hada breakfast ya kawo mata har
dakinta, tana daga kwance tana faman tunani taga ya bude kofa ya shigo, saurin
miqewa zaune tayi tana kallonsa, wani qaramin stool ya jawo ya ajiye mata honey tea
din daya kawo mata da wani abu kamar samosa a small plate, yace" ga breakfast ki
tashi kici sai kiyi wanka ki kwanta ni zan tafi hospital" daga masa kai kawai tayi
ya juya ya fita daga dakin, qaramin briefcase dinsa ya dauka ya fice wajen building
din ya hau qaramar motarsa ya nufi hospital, bimbii kuwa a hnkli ta sanya hannu ta
dauki cup na tea din tana sipping cike da sanyin ciki ga cikinta sai motsi yake
mata, hannunta ta dora kan cikin nata tana shafawa, hawaye ya soma sauka saman
kumatunta ba komai ne yasata kuka ba sai rashin sanin waye da wannan cikin dake
cikinta wanda akanshi kowa sai tsangwamarta yake, gani take kawai ita tamkar rayuwa
take mara alqibla don batasan komai game da rayuwarta ba, sautin qarar bude kofan
da taji ne yasata kallon kofar shigowa dakinta, shiru bata ga kowa ya shigo ba,
tashi tayi da sauri ta nufi kofar ta dan bude don leqawa aikuwa idanunta ya nuna
mata ennah, faisal ne yasa wani key ya bude kofofin shigowa building din gbdy don
maheer ya rufe ko'ina, qoqarin rufe kofarta take ta sanya key faisal yyi saurin
turowa, kallonta suka tsaya yi cike da mamaki wato har ma daki ne da ita na
musamman cikin building din maheer,ennah tace" ki fito mu tafi" kallonsu ta tsaya
yi saida faisal yyi mata tsawa sannan ta fito, hk suka tasata a gaba har bakin
motarsu, cikin sauri driver ya bude mata butt ba musu ta shiga ya rufe butt din,
ennah da faisal suka shige bayan mota suka zauna drivern yaja suka fice daga gdn,
kai tsaye kasuwar saida bayi suka wuce da ita, yawanci masu cinikin bayin sun qi
siyenta sbd basu son mai ciki sun fi son suna siyen bawa su siyar dashi amma ita
idan sun siyeta saidai suyita wahala da ita masu siye basu son mai ciki, ennah da
taga kowa yaqi siyen bimbii sai kawai ta kalli wani daga cikin masu saida bayin
tace" toh gata na baka ita kyauta" washe baki balaraben mutumin ya somayi yana
dariya cike da jin dadi ya mata gdy sosai, ennah ta siya wani bawan suka shige
motarsu suka tafi, bimbii kuwa balaraben ya sanya gefe cikin bayin da basu da
kasuwa don be sanya cikin kejin siyar da bayi ba kar masu siye su qi qarasowa
wurinsa idan suka hangi mai ciki cikin bayinsa, wasu manyan hadimai ne daga
masarautar abu ansar suka shigo wannan kasuwa don siyen bayi, masu cinikin bayi
kuwa suna ganinsu suka soma zuwa wurinsu da gudu suna nuna musu bayinsu don tun
daga ganinsu sun san daga gdn sarauta suke kuma sun san sarakai bayi dayawa suke
siye basu siyen dai dai, su kuwa wadanda manyan hadiman gdn sarauta sai wani shan
qamshi suke suna tfy suna kalle kallen kejin da bayi ke ciki, tsayawa sukayi wurin
kejin wannan balarabe da bimbii ke wurinsa, kallonsa sukayi suka ce suna son siyen
dukka bayin dake wurinsa, jikinsa na rawa ya shiga rumfarsa ya soma rubuta musu
certificate na mallakar bayin da suka siya ya fito ya miqa musu, har zasu wuce
dayan ya kalli bayin dake gefe yace" wadannan bana saidawa bane" da gudu balaraben
yace" suma na saidawa ne ranka ya dade" yace" toh meyesa baka hada dasu ba" shafa
dogon gemunsa yyi yace" su wadannan suna da yar matsala ne shiyasa" nuna bimbii yyi
da yatsa yace" waccer ita ciki gare ta sauran kuma basu da cikakken lfy" murmushi
daya daga cikin hadiman yyi yace" bamu son marasa lfy amma ita mai cikin tana da
cikakken lfy ne?" cikin sauri balaraben yace" ita tana da cikakken lfy kawai cikin
ne mtslrta" yace" ka hada mn da ita" da gudu ya shiga cikin rumfarsa ya rubuta musu
certificate na mallakar bimbii ya kawo musu, hk suka din ga bi keji keji suna siyen
bayi suka hada bayi dayawa suka kwashesu cikin wata doguwar mota suka nufi
masarautar abu ansar, sarki abu ansar aminin sarki abdallah bin jabal ne sosai
kuma shima masarautarsa tana da qarfi sosai, yana da ya'ya mata guda biyu, gimbiya
khamriyya da gimbiya mariyatul kifdiyya wacce itace akayi yarjejeniyyar aure
tsakaninta da prince akbar, dukkanin wadannan gimbiyoyi kyawawa ne na gaban
kwatance, gimbiya mariyatul qifdiya itace qarama, sarki abu ansar ya dora buri
sosai kan wadannan yara nasa yana mutuqar son su baya son 6acin ransu ko kadan,
lkcin da manyan hadiman wannan masarauta ta abu ansar suka iso da bayi, tuni uwar
bayi ramlatul asuwat tayi jawabi ga wadannan sabbi bayi ta sanar dasu duk wasu
dokoki na wannan gd, tana gamawa ta rarrabasu 6angarori daban daban na wannan gdn
sarauta tare da basu ayyuka daya dace da kowanne, kallon bimbii tayi ta ganta da
ciki tace" ke zan kai ki turakar jira sbd anan baki da aiki amma can qila wani ya
buqaci mai yaron ciki" kallonta bimbii kawai take don ita bata fuskanci ina ne
turakar jira ba, turakar jira wuri ne da ake ajiye mata masu kyawun jiki da siffa
mai kyau dake iya daukar hnklin maza sbd da tarar manyan baqi, idan aka kai mace
wannan wuri bata da aiki saidai gyaran jikinta da kula dakanta da kwalliya da
sutura mai kyau, toh idan akayi wasu manyan baqi a wannan masarauta akan zo turakar
jira a za6i mata a kai musu don su debe musu kewa, suyi musu tausa su kwana dasu
idan suna buqata, duk macen dake turakar jira toh amfaninta kenan a wannan
masarauta, batare da wani 6ata lkci ba ramlatul aswat ta miqa bimbii hannun suwaiba
wacce itace mai kula da matan dake turakar jira, suwaibah kallon bimbii tayi da
murmushi a fuskarta tace" tabbas zaki samu wurin zama a wannan turaka sbd kina da
siffa mai kyawun gaske duk da kasancewarki baqar fata" ita dai bimbii bata fahimci
kwata kwata me suwaiba take nufi har ta kira wata baiwa tace" kije ki gyara wannan
sabuwa ce tana buqatar a koya mata dabarun jan hnkli da kula da jiki,amma yanxu ki
shiga da ita ki soma gyarata tukunna" kama hannun bimbii tayi suka shige ciki,
dogon gashin bimbii ta soma wankewa tayi masa tas sannan ta hada sinadaran wanka ta
kalli bimbii dake tsaye tamkar wawuya tace" ki shiga kiyi wanka da wadannan
sinadarai" ba musu bimbii ta shige dakin wanka, tana wanka tana ganin datti sosai
na fita sbd wadannan sinadaran wanka basu barin datti a fata, tana fitowa wannan
baiwa mai suna rabi'at ta zaunar da ita ta soma shafeta da kayan gyara, tuni
fatarta ta soma sheqi da daukar idanu tamkar ba baiwa ba, gashin kanta shima ya
kwanta har tsakiyar gadon bayanta, sai kyalli yake,ita dai bimbii sai kallon ikon
Allah take gani tayi sai gyarata ake tamkar wata amarya, kayan mai kyau rabi'at ta
bata ta sanya ta nannade mata gashnta yyi tudu tamkar a cuci sannan ta yafeta da
wani mayafi mai shara shara, turare kuwa an mata 6arinshi, maida ita tayi dakin da
suwaiba take, tana ganinta tayi murmushi tace"masha'Allah" basu sanya bimbii cikin
jerin masu tarar baqi ba sai ta kware sosai wurin iya hillata da kissa da sauran
dabaru na janye hnklin maza kafin su sanyata cikin jerin matan dake tarar manyan
baqi, daki na musamman aka kaita inda ta ga dukkanin mata dake dakin sunyi ado na
kece raini suna zazzaune, wata hamshaqiyar mace zaune tana koyar dasu salon tfy da
rausaya da iya juya jiki har ma da yadda zasuyi taku a gaban namiji, tashin kowacce
take cikinsu daya bayan daya suna gwada yadda zasuyi taku da karkada jikinsu don su
janye hnkli, bimbii sakwato tayi tana ganin abubuwan mamaki, lalle kuwa cikin akwai
salon rayuwa 2kala sai wanda idanunka suka iya gani da wanda kunnuwanka ya ta6a ji,
ita dai bimbii gata ta shigo duniya tana diban darasi 2iri mai amfani da mara
amfani, yau dai ga bimbii Allah ya jefota masarautar abu ansar kuma a turakar
jira,6angaren masarautar burham kuwa jikin sarki abdallah bin jabal dai toh har
yanzu dai cigaban kadan aka samu da taimakon wannan antidote da prince akbar ya
bashi yanxu yana iya motsa jikinsa, prince tunda yake be ta6a tsintar kansa cikin
halin rayuwa irin wannan ba, ga mahaifinsa babu lfy ga bimbii besan tana raye ko a
mace ba, yau shi kadai yana tsaye bakin wannan glass window din dayake tsayuwa
hannunsa dukka a bayansa, sanye yake da wasu fararen pakistan, gashin kansa yyi luf
luf don yana shan gyara, fuskarsa ta dan fada hkn ya baiwa dogon hancinsa damar
fitowa dodar tamkar biro,sajensa kwance gefen fuskarsa, kallon waje yake tamkar mai
tuna wani abu hannunsa na dama riqe da wadannan awarwarayen na bimbii, lenah ce ta
shigo hannunta riqe da wani qaramin faranti mai kyan gaske ta ajiye saman wani
table, takowa tayi a hnkli wurin dayake tsaye ta tsaya a bayansa tare da rissinar
dakanta qasa tace" ranka ya dade ka kwantar da hnklinka insha'Allah jikin sarki mai
daraja zeyi sauqi bada jimawa ba" shiru ya mata kuma be jiyo ya kalleta ba,
idanunta ne yakai kan hannunsa na dama inda ta ga yana riqe da wasu awarwaraye,
mamaki sosai ya cikata take tunanin ko wannan awarwaron wacce prince yake riqe
dashi, cigaba tayi da tsayuwa har ya juyo
ya wuceta ya koma kan wata kujera ya zauna ya janyo alqalami da farar takarda yana
rubutu, tahowa tayi wurin ta soma tsiyaya masa herbal tea din data kawo masa,
hannun biyu tasa tare da rissinar dakanta qasa tana miqa masa cup din, dago da
kansa yyi ya kalleta sannab yasa hannu ya amshi cup din ya ajiye ya daga mata
hannu, hkn yasa ta dauki farantin data kawo ta juya ta nufi hanyar fita jikinta a
sanyaye, ubaid ne ya shigo ciki da sauri ya tsaya tare da rissinar dakansa qasa
yace" ranka ya dade muna da baqi daga masarautar abu ansar" .....

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan
acct..0100790419,alhaji shahida nasir,union bank,idan kin tura saiki turomin da
screenshrt na payment dinki ta whatsapp a wannan layin...07041195806....

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

33

*I still love you, I still miss you*.........I just want to see you back,pls come
back I'm still waiting for you💕💕

Baqi ne daga masarautar abu ansar sun iso ne bisa wakilcin ammar bin jabir don duba
jikin sarki abdallah bin jabal,sun samu tarar girma sosai cikin masarautar burham,
sarki abdallah kam yanzu jikin nasa babu laifi tunda yana iya miqewa zaune saidai
baya iya furta komai,masarautu da dama sun ji dadin wannan cuta da sarki abdallah
bin jabal ya kwanta, 6angaren da sarki abdallah ke jinya kuwa ko quda be isa ya
ratsa ta wurin ba sbd tsatstsauran matakan tsaro, iyalanshi kawai keda damar shiga
su duba shi shiyasa har yanzu babu wanda ze iya bada tabbacin ya jikin sarki
abdallah yake ana samun cigaba ko ba'a samu game da lalurar data tadda shi, yau da
dare sarki abdallah bin jabal ya daga idanu ya kalli prince akbar dake zaune
gefensa yana son furta masa wata kalma amma babu bakin mgn, miqa hannunsa yyi yana
buqatar a bashi takarda da alqalamin rubutu, prince ne ya dauki alqalamin da
takarda ya miqa masa don ya fahimci abunda yake nufi, amsar takardar yyi ya soma
rubutu a hnkli,yana gamawa ya ajiye alqalamin ya miqawa prince akbar farar takarda,
amsar takardar yyi yana duba abunda ta qunsa, umartar prince akbar yyi kan yabi
wadannan baqi da suka zo daga masarautar abu ansar don ganawa da sarki abu ansar da
kuma yarsa gimbiya mariyatul qifdiya, saurin dago idanunsa yyi yana kallon mahaifin
nasa cike da mamaki, sarauniya dake zaune gefe ta amshi wannan takarda dake hannun
prince akbar ta duba, saurin dago idanunta tayi ta kalli sarki abdallah bin jabal
tace" ranka ya dade, yanzu lfyrka itace mafarin farko a gare mu ba batun aure ba
don Allah ka kyale wannan mgn har Allah ya tashi kafadunka,tayaya prince ze tafi
nesa hk alhalin kaima da kanka kana buqatarshi kusa dakai" kau da kansa yyi gefe
alamar hkn dai yakeson ayi, kun dai san taurin kai irin na sarki abdallah sam a
tsarinshi baya zance biyu, washegari prince akbar tare da rakiyar babban hadiminsa
ubaid da kuma wadannan manya baqi da suka zo suka dugumxuma suka nufi masarautar
abu ansar, tun kan su isa sarki abu ansar yasan da zuwan prince akbar don hk ya
shirya liyafar girma don tarar wannan dan sarki ma'abocin daraja da qarfin
izzah,sun qawata wannan masarauta da kayan ado, jan carpet aka shimfida dogo inda
takan wannan carpet prince ya taka har ya samu isa cikin fadar sarki abu ansar,
yana zaune bisa kujerar mulkinsa fuskarsa da yalwataccen murmushi dakansa ya miqe
ya riqo hannayen prince akbar ya zaunar dashi a kujerar da aka tanada domin
shi,sarki abu ansar yyiwa prince akbar dayake tamkar surikinsa barka da ziyartar
wannnan masarauta, bayan wannan jawabi na sarki abu ansar sai liyafar da aka
shiryawa prince akbar ta soma gudana, gimbiya mariyatul qifdiya kuwa tunda ta samu
lbrin zuwan prince take ta murna har farin cikin nata ya kasa 6oyuwa, gimbiya
khamriyya tayi ruwa tayi maqarbiya wurin kimtsa tilon qanwarta tata sbd ta fahimci
mariyatul qifdiya bata da masoyin data mallakawa ruhinta kamar prince akbar,
gimbiya mariyatul qifdiya tayi kwalliya na ruwan zinare hannu,wuya har ma da qafa,
sanye take cikin wata lafiyayyen jar doguwar riga da mayafinta data yane kanta
dashi,riga ce irin wacce yaran sarakai da manyan attajirai ke iya sakawa,gbdy ta
zaqu ta gana da masoyinta prince akbar, shi kuwa babban prince ana qare wannan
liyafa sarki abu ansar yasa aka kaisa royal louge na wannan masarautar,6angare ne
na musamman suka tanada sbd baqi jinin sarauta, wurin yyi kyau sosai don an qawata
wurin tun daga farfajiyar 6angaren idanun mutum zasu soma lumewa kan kyakyawan
furanni masu mutuqar daukar hnkli tare da kukan tsuntsaye ta ko'ina,babban hadimin
sarki abu ansar jamal tare da wasu hadiman suka yiwa prince akbar rakiya zuwa
wannan royal louge, ubaid na biye da prince akbar har ya shiga cikin wurin shi kuma
ubaid da sauran wadannan hadimai suka tsatstsaya a bakin kofa don tsaronsa, prince
na shiga ya samu komai tsaftsaf, zama yyi bakin wani gado na alfarma yyi shiru,
6angaren turakar jira kuwa inda bimbii take lbrin isowar wannan dan sarki ya iso ga
suwaibah don hk ta tashi ta shiga inda yan mata suke don za6o mai cikakken dirin
halitta da kaifin basirah ta kasance da wannan dan sarki don hidimta masa, yan
matan duk suna zazzaune kowacce tayi ado na a kalleta, kallonsu take daya bayan
daya, idanunta ne ya sauka kan bimbii, tace" ke tashi na ganki" miqewa bimbii tayi
a hnkli ta tsaya suwaibah na qare mata kallo tun daga sama har qasa, kallon
buqasassun hips dinta tayi daya fito sosai ga albarkatun fulaninta tsaye qam tamkar
danyar budurwa duk da cikin dake cikinta, kowacce a cikin yan matan burinta a
za6eta don tarar wannan dan sarki amma sai suwaiba ta nuna bimbii tace" maxa ki
biyo baya na" mamaki ne ya cika kowa wurin sbd kowa yasan ba'a tarar jinin sarauta
da baiwar da ba virgin ba wato danyar budurwa toh don me shugaba zata za6i bimbii
wacce take da yaron ciki,suwaiba kuwa sam bata duba hk ba abunda kawai tayi
la'akari dashi shine bimbii tafi dukkaninsu cikar dirin halitta ta cikakkun matan
girma burin kowanne da namiji duk da kasancewarta baqar fata kuma mai yaron ciki,
kai tsaye dakin gyara ta wuce da ita ta shiryata dakanta cikin wasu sexy dress masu
mutuqar janye hnkli ta taje mata gashin kanta ya saukar mata har tsakiyar gadon
bayanta sannan ta dauko wata abaya fara sol ta sanya mata ya rufe wannan shiga dake
jikinta,gashin idanunta kuwa shima yasha gyara yyi baqi qirin hasken kwayar
idanunta kawai ake iya gani ga lips nata yasha pink lipatick sai glowing yake,
murmushi suwaiba tayi yadda taga bimbii tayi masifar kyau na gasken gaske,
hamshaqiya ramlatu ce ta shigo ta kalli bimbii sai kuma ta kalli suwaibah tace"
shugaba wannan wa zata tara hk" murmushi suwaiba tayi tace" zata tari dan sarki
prince akbar na gimbiya mariyatul qifdiya ma'abocin cikakkiyar izzah" hamshaqiya
ramlatu tayi saurin kallon suwaiba cike da mamaki tace" amma baki gani wannan ba
budurwa bace sannan cikin darasin jan hnkli da ake koyar dasu sam bata da fahimta
gashi tana dauke da yaron ciki shugaba karki saba doka kinsan cikakkiyar izzah irin
ta jinin masarautar burham tayaya zaki tari wannan dan sarkinsu da baiwar daba
budurwa ba qarewa ma tana dauke da juna biyu wannan tamkar gangaci ne kk shirin
aikatawa" dafata suwaibah tayi tace" sam babu gangaci cikin wannan hikima tawa baki
da sani cewa prince akbar shine masoyi kuma miji ga gimbiya mariyatul qifdiya,itace
ta umarceni kar na sake na tura virgin din baiwa ga masoyinta" shiru hamshaqiya
ramlatu tayi tana tunani, tabbas ba komai ne yasa gimbiya mariyatu tayi hk ba sai
tsantsar kishi irin nata bata son suwaiba ta tura danyar budurwa ga prince akbar
don tasan idan ma yana da tunanin mace ta debe masa kewa yaga an tura masa baiwa
mai yaron ciki tasan babu ta yadda za'ayi ya sauke buqatarsa kan wannan baiwa sbd
yana da cikakkiyar izzah bazai ta6a kusantar macen da take a bude ba, kuma dakyar
ne be koreta ba, ita kuma gimbiya mariyatu hk take so sbd tana da kishi akansa
sosai, lkcin da gimbiya mariyatul qifdiya ta nemi ganin suwaiba ta sanar da ita
buqatarta, murmushi suwaibah tayi tace" ranki ya dade kar damu don yanzu hkma ina
da wata baiwa cikin yan matana dake dauke da yaron ciki kuma gata bata da wata
dabara na janye hnklin namiji ita zan tura masa"wannan batu na suwaibah ba qaramin
sanya gimbiya mariyatu qifdiya farin ciki yyi ba har saida ta yiwa suwaiba kyautar
zoben gwal,bayan an gama shirya bimbii suka fito suwaiba ta kama hannun bimbii ta
sanyata cikin keken doki wasu hadimai hudu suka soma jan keken dokin suka wuce da
ita royal louge don tarar wannan dan sarki, suna isa ta sakko daga keken dokin
fuskarta rufe da mayafi, babbar baiwar dake kula da wannan 6angare mai suna
aslamiyya ita ta miqawa bimbii wani kyakykyawan kwando dan qarami mai dauke da
kayan marmari ta nufi hnyr shiga cikin wannan 6angare, masu tsaron dake kula da
wurin suka bata hanya cikinsu har da ubaid, sam be ganeta ba domin fuskarta a rufe
take da mayafi ya bata hanya ta shige,tfy take a hnkli bawai da niyyar yanga ba ko
jan hnkli ba saidai kawai ita daman hk Allah ya mata wannan baiwa, idan tana tfy
tamkar tarwada duk wasu ma'adanai na jikinta juyawa suke suna tsole idon masu
budadden ido suna musu kwalele,cikin wannan irin salon tfy ta samu shiga wannan
louge, tsarin wurin yyi mata kyau sosai, bata bude mayafin data rufe fuskarta dashi
ba amma tana ganin komai a hk, prince kuwa yana zaune bisa wata kujera fitowarsa
kenan daga wanka don be aminta wata baiwa ta taimaka masa wurin wanka ba koh a gida
babbar baiwar kadai keda wannan yancin bare a masarautar daba tashi ba, aslamiyya
ita ta fara shiga wurinsa kafin bimbii ta iso ta hada masa ruwan wanka a kwarmin
wanka ta sanya sinadaran wanka tana gama wannan aiki ya daga mata hannu alamar ta
tafi baya buqatar komai bayan hk, yana daga zaune yaji motsin shigowa amma be waiga
ba har ta tako inda yake zaune ta tsaya a bayansa,ta bude fuskarta ta dora kyawawan
hannayenta wanda ke sanye da awarwaraye masu kyan gaske ta dora bisa kafadarsa ta
soma masa tausa...........

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw saiki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, idan kin tura saiki turo da
screenhrt na payment dinki ta whatsapp a wannan layin...07041195806........
Alkalamin Bintuu ne.......
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

34

*My heart is bursting,my heart is beating more and more*......the time I set eyes
on you I was totally confused💕💕

A hnkli take masa tausan tamkar tana tausayin jikinsa, yanayin yadda take masa
tausan yasa shi lumshe idanunsa yana tuna wacce take masa irin wannan tausan wato
bimbii, ji yake tamkar itace ke masa tausan sbd exactly yadda take masa hk wannan
baiwar take masa, so yake ya dago da kansa yaga wannan baiwa saidai izzah irin tasu
ta jinin sarauta na yawo a jikinsa, daga mata hannu yyi alamar tausan ya isa hk,
gabansa ta dawo ta tsaya tare da rissinar dakanta qasa sannan ta dago dakanta ta
dauki tuffa daga cikin qaramin kwandon data shiga dashi na kayan marmari ta sanya
wata kyakykyawar qaramar wuqa ta yanka tuffan ta sake rissinar dakanta tana miqa
masa slice na tuffan,shi kuwa babbar prince yana tozali da fuskarta numfashinsa ya
dauke na wasu sakanni kafin ya dawo hnklinsa, zuciyarsa bugawa ta somayi da qarfi
tamkar zata fasa kirjinsa ta fito ya qureta da idanu ko qiftawa baya yi cike da
tsantsar mamaki, ita kuwa bimbii kanta na sunkuye tana riqe da tuffan da take miqa
masa jin shirun yyi yawa ne yasa ta dago dakanta tana kallonshi, kallon daya qureta
dashi ne yasa taji gabanta ya fadi, miqewa yyi a hnkli yasa hannunsa ya dago da
ha6arta yana kallon cikin qwayar idonta cike da tarin rudani, gani yake tamkar gixo
take masa ko kuma mafarki yake, ita kuwa bimbii rawa jikinta ya soma tamkar mazari
sbd daman taji tattaunawar shugaba suwaiba da hamshaqiya ramlatu kan zuwanta tarar
wannan dan sarki matsayinta na mai yaron ciki sai take gani kamar ganin cikin dake
jikinta ne yasa wannan dan sarki yi mata hk, sauke hannunsa yyi yana cigaba da
kallonta, gani yyi a tsorace take dashi hkn ya nuna tamkar bata gane shi
bane,gabansa ne yaji ya yanke ya fadi, maida kallonsa yyi kan qaramin cikinta daya
turo sosai ya jima yana kallon cikin sannab ya dago da jajayen idanunsa da tashi
daya suka sauya launi, idanunsa ne suka sake bata tsoro tayi saurin ja da baya, a
hnkli ya soma takawa har ya isa inda take tsaye ya matsa jikinta sosai tamkar ze
hade jikinsu, ita kuwa bimbii ji take tamkar ta saki fitsari a wando sbd tsabar
tsorata da tayi dashi, cikin wata irin murya mai cike da rudani yace" me kk nufi?
baki gane ni ba?" mgn ta soma cike da qinqina tamkar me koyon mgn tace"
ni...baiwa..c..e, shu..ga..ba ce ta turon gareka" be kuma furta komai ba saida
kallonta dayake tun daga sama har qasa, ja yyi da baya ya koma kujerar dayake ya
zauna ya kwantar dakansa jikin kujerar ya rufe idanunsa sbd dokawa da zuciyarshi
take 2akai,ita kuma tayi saurin qarasowa gabansa ta durqushe qasa bisa guiwowinta,
batare daya bude idanunsa ya kalleta ba yace" me sunanki?" cikin sauri ta amsa masa
tace" suna na andal" bude idanunsa yyi ya kalleta sosai sai kuma ya rufe saida ya
jima sannan ya sake mgn yace" waye da cikin jikinki?" cikin tsantsar rudu ta dago
da fuskarta tana kallonshi taga idanunsa na rufe sai ta sunkuya ta kalli cikin dake
tare da ita, cikin sanyin murya tace" nima ban sani ba kawai ganin cikin nayi a
jikina" cikin sauri ya bude idanunsa yana kallonta yace" me kkce?" shiru tayi bata
sake mgn ba don yanayin yadda yyi yasa taji tsoron sake maimaita abunda ta fada,
tashi yyi zaune sosai ya zuba mata idanu sai kuma ya miqe abinsa ya qarasa hadadden
gadon dake can gefe ya kwanta sannan ya dago ya kalleta yaga tana inda yabarta bata
da niyyar tashi yace" hk shugabar ta koyar dake aikinki" saurin tashi tayi ta
qaraso wurin gadon ta tsaya batare data hau kan gadon ba, murmushin yaqe yyi wanda
a zahiri ji yake tamkar ya rushe da kuka, ga zuciyarsa ta gaza dena bugawa da qarfi
kawai dauriyya yake yace" ina buqatar ki sanya ni bacci" shiru tayi sai kuma ta hau
gadon cikin sanyin jiki yana ganin tahau yyi matashi da cinyarta ji yake tamkar ya
rumgumeta a jikinsa ko bugawar da zuciyarsa keyi ze ragu, saidai kawai ya daure,
ita kuwa sakoko tayi tana kallon gashi kansa,ba zato taji.muryarsa yace" idan ina
jin bacci sai an bani labarai masu dadi nk bacci,ki bani labarinki sai nayi bacci
sbd kin min kama da wata wacce na sani" kallonshi take da mamaki sai kuma ta kalli
gyararren sumar kansa dake kwance a saman kafadarsa, ji tayi gbdy ya birgeta, cikin
sanyin murya ta soma bashi lbrinta iyakar wanda ta sani har da lbrin gidansu farhan
da zaman a gdn maheer har kawo wannan lkci, kwance yake a saman cinyarta idanunsa a
sama yana kallonta ya harde hannayensa saman qirjinsa ya qura mata idanu a hnkli
yace" kuma baki da buqatar sanin me wannan cikin na jikinki" yasa hannu saman cikin
nata yana dannawa a hnkli, shiru tayi sai kuma tace" in Allah yaso wataran zan tuna
lbr na" murmushi yyi yace" kiyi qoqarin tunawa sbd qila mai cikin yana jiran
abinshi" shiru tayi tana mamakin wannan dan sarki daya sake yake mgn da ita hk kuma
ya bada interest nasa yana sauraren lbrinta, cikinsu babu wanda ya sake mgn, shi
babban prince duk cikin lbrin data bashi babu wanda ya 6ata masa rai yaji bala'in
kishinsa irin maheer, be sanshi ba amma yaji tsanarsa sosai cikin ranshi, lumshe
idanusa yyi yana jinsa tamkar wani sabon mutum yau gashi ga rayuwarsa suna numfashi
a muhalli guda abu kamar cikin mafarki, ita kuwa bimbii hannunta na cikin sumar
kansa tana son sanyashi bacci, tunda ya rufe idanunsa be kuma budewa ba, idanun
nasa na rufe ya daga mata hannu alamar ta tafi, ji tayi sam batasan sauka sbd
qamshin dake fita daga jikinsa yana mata dadi sosai amma dole ta sauka ta nufi
hanyar fita, tana fita yyi saurin tashi zaune yana kallon hanyar data bi, zumbur
yyi ya miqe ya soma zirya, bimbii kuwa tana fita ubaid ya bita da kallo,saidai be
samu nasarar ganin fuskarta ba amma ya hangi cikin dake jikinta, hknne ya bashi
tabbaci dalilin dayasa babban prince ya koreta kenan, wani hadimi ne ya sanar dashi
prince na son ganinshi ya shiga da sauri,batare da bata lkci ba prince ya bashi
umarnin abunda ze aikata.....

**

6angaren maheer kuwa hauka tuburan ya gwada musu lkcin daya dawo gida ya tarar ba
bimbii ba alamunta cikin gdn, a guje ya fito tamkar mahaukaci yahau motarsa yyi gdn
ennah, tana zaune tana krt wata jarida taji shigowarsa ya afko ciki kamar an jefo
shi kallonta yyi yace" ina kk kaita ina kk kaimin ita?" kallonshi tayi cike da
rashin fahimta tace" me kk fada" kallonta yyi a tsorace yace" ban ganta ba ina kk
kaita nasa kece kk dauke min ita" miqewa tayi tana kallonsa tace" au taji gargadin
da na mata kenan ta nemi hanyarta hkn yyi kyau" kallonta ya tsaya yi yace" ina
take?" tace" wannan kai zan tmby" kallonshi tayi kawai sai taga yana hawaye yace"
do you want me to live?" kallonshi ta tsaya tanayi cike da mamaki don batayi zaton
abun nashi yyi tsananin hk ba tace" what do you mean maheer" wani murmushi yyi ya
kuma kallonta batare data ankara ba yyi saurin daukar qaramar wuqar yanka lemo dake
gefenta ya soma ja da baya yace" I told you my life is useless without her, do you
know how much I suffered when I lost her? a rikice take kallon wuqar dake hannunsa
tace" no, maheer dnt do this u are a muslim" murmushi yyi be sake cewa komai ba ya
chaka wuqar a qirjinsa, wani irin ihu ta kurma a guje tayi kansa tana kiran sunan
shi, shi kuwa sulalewa yyi qasa cikin jini...........

pls manage it pls....


Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir, union bank saiki turo da screenshrt na
payment naki a whatsapp ta wannan layi...07041195806....

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

35

*To me you are the princess*........you are my queen,you build a perfect kingdom in
my heart.....so, you are the star💕💕

Bimbii na komawa turakar jira kuwa yan mata wannan turaka suka soma tuntsira mata
dariya don su tunaninsu babban prince ya koreta ne, wata daga cikinsu mai suna
veesha tayi saurin miqewa tayi wani irin juyi da rausaya tana karkada jikinta cike
da salo, sauran yan mata suka dauki tafi da shewa, murmushi veesha tayi tace" ku
duba fa ku gani da mata irinmu wadanda suka kware wurin iya sarrafa jiki da kissar
dauke hnkli kowanne taurarren namiji amma wai duk a wuce mu dauki wannan mai
tutsetsen cikin,hhhh" zeena tace" kedai yi shiru kawai ai daman sanya idanu nayi
naga yadda abun ze kaya, ke kin ga haduwar wannan dan sarkin kuwa, tayaya ne ma ze
sauke buqatarsa kan ragowar wani ga danyun yan mata irinmu masu cikakken budurci ga
kuma salon hillata" tafawa sukayi suna sheqa dariya ita kuwa bimbii tana zaune gefe
tayi tsuru tana kallonsu, ganin suna watsa mata baqar mgn yasa ta miqe ta wuce
dakin kwananta,2kwata kasa rintsawa tayi burinta kawai ta sake shaqar qamshin jikin
babban prince,miqewa tayi ta soma shinshina jikin kayanta ko ya kama qamshin nasa,
hk ta din yi tamkar wacce ta samu aiki, shigowa wasu yan mata biyu da suke kwana
daki daya ne yasa tayi saurin komawa ta kwanta amma a zahiri hoton fuskarsa ne yake
mata gixo, hannu tasa ta daki kanta dashi tace" na shiga uku me nake yi hk"
zuciyarta ta gargadeta kan ita fa qanqantacciyar baiwa ta tsaya matsayinta kar ta
sake takai kanta inda Allah be kaita ba, hk dai ta din ga fama tana qoqarin manta
fuskarshi dake mata yawo har ta samu bacci ya soma daukarta,washegari, suwaiba taje
ta sanar da gimbiya mariyatul qifdiya wannan kyakykyawan lbri hkn yyi mutuqar
sanyayawa gimbiya mariyatu zuciya, musamman aka shiryata cikin wasu kayan na
alfarma don ganawa da masoyinta rabin rayuwarta, babban prince yana tare da sarki
abu ansar a dakin ganawar sirrinsa, sarki abu ansar ya kalli prince akbar yace"
tabbas maqiya sunyi amfani da baquwar guba ne wacce take sabuwa qirqira da har yau
masana basu gano laqonta wurin cutar da mahaifinka sai zan tura ka ga wani bawan
Allah tsohon masani ne kuma bayahude daya jima yana qirqirar gubobi masu tsananin
cutarwa ga lfyr bil'adam, yasan sirrin kowacce irin guba, wannan bayahude yana
rayuwa ne a wani tsibiri can arewacin spain da ake kira oldest Inland na tabbata
wannan bayahude bazai rasa sani game da abunda ze daqusar da wannan guba dake jikin
mahaifinka ba" shiru prince akbar yyi sai kuma ya dago ya kalli sarki abu ansar
yace" yakai wannan sarki ma'abocin sani tabbas da yarda wannan raina ke hannunsa
bazan koma ga mahaifina ba har sai da mgnin matsalarsa" murmushi sarki abu ansar
yyi yace" madallah da d'a nagari kuma kyakykyawan jarimi a fagen fama" rissinar
dakai prince yyi alamar girmamawa ga sarki abu ansar" hannun prince akbar sarki abu
ansar ya riqe suka fito, babbar hadima ga sarauniya ita ta yiwa babban prince
jagora har wani babban lambu mai cike da kyawawan furanni da tsuntsaye masu dadin
kuka, wata kyawawan kujeru aka tana don zaman shi, bayan fitar ta bada jimawa ya
soma jiyo wani sassayyan qamshi mai kwantar da hnkli, daga kansa yyi yana kallon
6angaren da qamshin ke tahowa, gimbiya mariyatul qifdiya ce sanye da wata doguwar
riga mai ruwan kwai, tayi ado na awarwaron zinare ga sarqa ga abun wuya, tasha kyau
na ban mamaki, kallo daya za'a mata a fahimci diyar girma ce kuma jinin sarauta,
tfy take dai dai cike da qasaita da kuma izzah har ta qaraso wurin dayake daya daga
cikin hadiman dake take mata baya ta gyara mata zaman kujerar dake gefensa ta
zauna, juyawa hadiman sukayi suka fice daga lambun ya rage daga ita sai babban
prince, duk sunyi shiru don kowanne cikinsu yana taqama da izzah da kuma qasaita
gdn sarautar daya fito, gimbiya khamriyya da kanta ta jaddadawa gimbiya mariyatu
akanta 6oye soyayyarta ga prince akbar ta martaba izzar gdn sarautar abu ansar, ta
bari shi ya soma sauke izzarsa gareta ya fallasa mata sirrin zuciyarshi, prince sau
daya ya kalleta duk da kuwa tsantsar kyawunta irin na larabawan usul,sun jima a hk
babu mai niyyar mgn cikinsu, gimbiya mariyatu kam taji ana ambatar cikakken izzah
irin na wannan dan sarki amma bata ta6a zaton yakai hk ba, miqewa taga yyi ya soma
takunsa mai cike da qasaita ya fice daga wannan lambu yabarta zaune tamkar an
dasata, kuka ta fashe dashi tana dana sanin daukar shawarar yayarta kan ta nuna
masa cikar izzarta gashi nan ya fita ya barta da izzar nata, shi kuwa prince akbar
duk duniya mace daya ce zata iya gwada masa izza tasha kuma ita din ba kowan kowa
bace face qasqantacciyar baiwa amma ita Allah ya dora bisa kansa ko durqusawa
gabanta ze iya yi sbd ta gama da qarfin izzarsa, hadimansa na ganin fitowarsa suka
take masa baya, ubaid na daga hannun damansa, bimbii ta tashi da kasala ranar sai
bin jiki take babu abunda takeson ji sai qamshin jikin prince, fitowa tayi tana
kwashe shanya tana zubawa cikin wani kwandon saqi, tana shiga 6angarensu ta hango
dukkanin yan matan dake turakar jira sun fito farfajiya wurin sunyi jeri tana
shigowa duk suka bita da kallo,ramlatul aswat ta gani tare da suwaiba sai kuma wasu
qattan bayi, kallonta ramlatul aswat tayi a wulaqance cikin fada tace" ke daman
gudandiyar baiwa ce daga gdn yasser bin walid amma har kk shigo wannan masarauta ta
abu ansar" wani hadimi dayake cikin hadiman da suka siyo bimbii yace" tabbas bamu
san gudaddiyar baiwa bace daga gdn yasser da bamu siyenta" ramlatul aswat ta galla
masa harara sannan ta kalli bimbii take sauraronsu don bata gane abunda suke fada
ba, turata cikin hadiman gdn yasseer bin walid ramlatul aswat tayi tace" ka
baiwarku nan amma ku bawa nana hkr kar wannan zance yakai kunnen sarauniyya"
hadiman gdn yasser suka ja bimbii suka fita da ita har suka fice daga masarautar
abu ansar da ita, yasser bin walid shararren attajiri ne mai qarfin arziqi da
yalwar bayi, sarakuna suna ganin darajarsa sosai sbd qarfin arziqinsa, yasser bin
walid abokin kasuwancin prince akbar ne kuma shine ya tura ubaid wurinsa kan ya
masa wannan alfarmar batare da bata lkci ba ya aika hadimansa gdn sarautar burham
don aiwatar da wannan aiki, yasser ya damqa bimbii ga ubaid sai lkcin ubaid yaga
bimbii shi kansa ya cika da mamakin ganinta, kamar yadda prince ya umarci ubaid hk
ya aiwatar yasa bimbii cikin wani babban jirgin ruwa mai zuwa spain tare da wata
amintacciyar hadima mai suna sumayya da yasser ya hadasu da ita don kula da lfyr
bimbii har su isa qasar spain, sumayya mace ce mai mutuqar jarimta tamkar na maxa
gata da hikima hk ta din ga kula da bimbii har jirginsu ya isa qasar spain suka
wuce masaukinsu, ubaid ya isa ya sanar da babban prince jirginsu bimbii ya tashi
zuwa spain, suma da yamma tawaga guda sarki abu ansar yasa suka yi masa rakiya har
ya shiga jirgin ruwa tare da ubaid, sauran hadimansa kuwa suka koma ga masarautar
burham suka sanar da tfyr babban prince spain don ganawa da tsohon bayahude abram
dake oldest Inland, bimbii tunda jirginsu ya tsaya a port na tsayawa jiragen ruwa
dake qasar spain ta fito sai kalle kalle take, gani tayi ta dena ganin masu rawani
sai turawa nasarar asarar duniya, qasar spain ta mata kyau ko'ina hasken fitilu
dayake da dare suka qarasa, sun sauka ne a wani orchard house mai kyau, qaramin
gini ne irin na turawa amma ya tsaru sosai, ko'ina ta gefe bishiyoyin fruit ne da
shuke shuke, tsarin wurin kawai akwai kwanciyar hnkli, bimbii ranar bacci tayi mai
rai da lfy sbd peaceful environment din data samu kanta ciki, cikin kwana uku ubaid
da babban prince suka iso qasar spain, suma a wannan orchard house suka sauka sbd
tsarin wurin yana yiwa prince dadi idan ya shiga spain a wannan wuri yake
rayuwarsa, nesa kadan da wannan orchard house teku ne,bimbii dai kam batasan
dalilin zuwanta wannan waje ba ita dai kawai gata nan ne batasan ina rayuwarta ta
dosa ba,da dare sumayya ta sanar da ita wanda ya siyeta ya iso yana buqatar takai
masa abun sha, ba musu bimbii ta tashi ta hada lemon zaitun da zuma ta zuba a
kyakykawan mazubi ta din ga qetare corridor har ta isa bakin dakin da prince
yake,ta6a kofar tayi taji ta a bude tayi sallama ta shiga, bedroom ne mai girman
gaske, komai na wannan bedroom fari ne da dark blue, everything is so cool, qamshin
da take maita ta soma shaqa, prince kuwa yana kwance a tafkeken gadon dake dakin
yana duba wani littafi yaji ta turo kofa, ita bata lura dashi ba kawai kallon dakin
take sai data waiga wurin da wannan tafkeken gadon yake ta hango shi kwance ya
tsareta da idanu,gabanta ne ya yanke ya fadi ta tsira masa idanu cike da tarin
mamaki da al'ajabin ganinsa a wannan wuri, shafa idanunta ta somayi tana son
tabbatarwa wannan dan sarkin ne kuwa.....

***

6angaren maheer kuwa tuni ennah ta kira faisal suka nufi hospital dashi, hnklinta
duk a tashe sbd tana da masifar son yaranta,maheer yyiwa kansa rauni sosai, bayan
hk likitoci sun tabbatar musu jininsa yahau dayawa a kowanne irin lkci zuciyarsa
zata iya bugawa, ennah kuka take sosai sai lkcin take nadamar dauke masa bimbii da
tayi har kasuwar saida bayin data kai bimbii ta koma amma wannan balaraba ya fada
mata shi wlh ya saida ita dole hk ta dawo hospital din da maheer ke kwance cike da
tarin dana sani, zama tayi ta tsura masa idanu, shi kuwa yana kwance duk an sanya
masa oxygen a hanci da bakinsa, numfashinsa na fita a hnkli, tunani take wai wanne
irin so kuwa maheer yake yiwa wannan baiwa hk, she can't imagine this kind of
sacrifices until she witnessed it on her son......

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw saiki tura #300 ta wannan
acct..0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki turo da screenshrt na
payment nk ta whatsapp ta wannan layi..07041195806.....

Alkalamin Bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer


36

*I LOVE YOU*💕💕I MISS YOU💕💕

Duk abunda take idonsa na kanta yana qare mata kallo, dauke kansa yyi daga kallonta
ya cigaba da karanta littafin dake hannunsa, hknne itama ya bata damar takawa a
hnkli ta qarasa wurin qaramin stool din dake gefen gadon dayake kwance ta ajiye
farantin hannunta ta dauki cup ta soma tsiyaya masa drink, daukan cup din tayi ta
matsa daidai wurin dayake kwance ta rissinar dakanta qasa tare da miqa masa cup din
dake hannunta, daga idanunsa yyi kawai yana kallonta, tashi yyi zaune ya ajiye
littafin dake hannunsa ya amshi cup din dake hannunta ya soma sipping drink na
zaitun din, miqa mata cup din yyi ta mayar dashi kan faranti ta ajiye sai kuma ta
dauki farantin da niyyar ficewa dashi don ta soma gjy da wannan kallon qurallah da
wannan dan sarki ke binta dashi, rissinar dakanta tayi alamun girmamawa sannan ta
juya da niyyar fita saidai taku daya zuwa biyu tayi taji charaff an damqe mata
hannu, kafin ta dawo cikin tunaninta ya rumgumeta ta baya hannunsa nakan qugunta ya
dora kansa akan dokin wuyanta yana sauke numfashi a hnkli, ita kuwa bimbii mutuwar
tsaye tayi zuciyarta na wani irin tsere da mugun speed, saukar numfashinsa kawai
take iya ji, jikinta sai rawa yake kamar mazari, shi kansa yaji rawar da jikinta
yake yi, murmushi yyi ya janye hannunsa daga qugunta ya juyo da ita suna fuskantar
juna, tsirawa juna ido sukayi, bece mata uffan ba amma tana iya karantar saqonsa da
cikin kwayar idonsa, zallar madarar sonta kawai take hange cikin kwayar idonsa shi
kuwa babu abunda yake gani cikin idonta sai tarin tsoro da rudu, hannunsa yakai
wurin idanunta yyi kamar ze tsole mata idanu tayi saurin blinking eyes nata, janye
jikinta ta soma qoqarin yi amma ta kasa don namijin gaske ne yake riqe da ita,
raurau tayi da idanunta da niyyar fashe masa da kuka, rufe idanunsa yyi don baya
son ganin hawayenta kuma baida niyyar fasa abunda yyi niyya, matsar da fuskarsa yyi
sosai ya hade da nata ya dora dogon hancinsa kan nata, bimbii kuwa qirjinta kamar
ze faso sbd tsoro, bata gama sallamawa da lamarinsa ba saida taji ya hade bakinsu
wuri guda,numfashinta ne ya soma fizga shi kuwa gently yake kissing nata dukkaninsu
idanunsa a lumshe kowanne cikinsu zuciyarsa na bugawa da qarfi, a hnkli ya tsare
bakinsa daga cikin nata amma be dauke fuskarsa dake manne da nata ba kuma be bude
idanunsa ba, itama idanunta na rufe, saida suka jima a hk sannan ya janyota ta fada
qirjinsa yasa hannunsa around her, kuka take masa, idanunsa shima sunyi jajir he
wish to be with her this night but he can't until she gain her memory back, bimbii
tana kuka tana qara manna fuskarta a qirjinsa tana shaqar qamshinsa sbd abunda take
so kenan, ya jima yana rumgume da ita yana shinshinar qamshin da gashinta ke
fitarwa yana tunanin abunda ze iya raba shi da ita, mahaifinsa ne ya shigo cikin
tunaninsa take yaji gabansa ya yake ya fadi, idan har ya rasa bimbii baya jin
rayuwarsa zata dore sbd kowanne sashi na jikinsa qaunarta ne hatta jinin dake
circulating a cikin jikinsa, sonta shine bugawar zuciyarsa, hannunsa yasa ya dago
da fuskarta data jiqe da ruwan hawaye ya tsura mata idanu, qasa tayi da kanta don
kallon nasa na sanya mata mutuwar jiki, hannu yasa a aljihu ya fito da wani farin
handkchiep nasa yasa hannu ya dago da ha6arta ya soma goge mata hawayen da yyi
spoiling beautiful face dinta, gani tayi ya durgusa a gabanta ya dora kansa kan
cikin dake jikinta yana jin motsin abunda dake cikin, hannu tasa ta tureshi yyi
saurin miqewa yyi yana murmushi ya kanne mata ido daya tare da dage mata kafada
kamar wani qaramin yaro, komawa yyi ya kwanta abinsa ya daga mata hannu alamar ya
sallameta, kamar jira take tayi hanyar kofa da sauri kamar zata ci tuntu6e ta murda
handle na kofar ta fice, murmushi yyi kawai daya ga ta fita ya lumshe idanunsa, ita
kuwa bimbii tana fita tasa gudu ta qarasa dakin da take tana sauke numfashi tare da
kallon kofa tamkar wacce tayi gamo, sumayya dake bayanta riqe da cup na black tea
tace" mene ya tsorataki hk na ganki duk a rikice" inda inda ta somayi kamar wata
munafika don gani take kamar sumayya tasan abunda ya faru da ita, sumayya na ganin
hk ta wuce tare da basar da tmbyr data mata, zuma ta sanya a black tea din dake
cikin cup din hannunta ta miqa mata, amsar cup din tayi tana shan tea din a hnkli
har ta shanye, bathroom ta shiga tayi wanka da warm water sannan ta fito ta sanya
wasu kayan bacci masu taushi tabi lfyr gado, mood nasu na dazu kawai take tunawa ya
kasa 6ace mata a cikin brain nata, hannunta tasa ta shafa lips dinta daya sha
kissing, yanayinsa take tunawa da cool love nasa mai tsayawa a rai, mafi yawan
soyayyarsa a kwayar idonsa take be cika yawan mgn ba, murmushi ne ya su6uce mata ta
rufe fuskarta da small pillow din dake gefenta, da wannan tunanin bacci 6arawo yyi
gaba da ita, washegari, bata samu ganin prince ba sbd da sassafe suka fice shi da
ubaid suka nufi oldest Inland, cikin nasara suka gane inda wannan tsohon bayahude
yake, abram yana rayuwa ne shi daya a wani gdn katako, suna tsayawa da mota ubaid
yyi saurin budewa babban prince kofar mota ya fito, hk suka taka suka qarasa wannan
gdn katakon, ubaid yasa hannu ya buga kofar katakon a hnkli, saida aka dauki time
abram ya bude kofar ya tsaya yana kallonsu, tsoho ne sosai, gashin gemunsa dogo
kuma fari sol, sanye yake da wata hula iyakarta tsakiyar kansa irin wacce jews ke
sanyawa, kansa duk saiqo, kallonsu yake da mamaki kuma yaqi basu hanya su shiga
ciki yace" arab men to my house, what's are you up to...?" ubaid yace" this is not
abram house" they are speaking with pure british english, yana ji sun ambaci sunan
shi ya basu hanya suka shiga ciki, ko'ina cikin gdn kwalabe ne dauke da chemical
samples, ta gefe guda kuma shelter ne na manya tsoffi littattafan manya scientists
da suka shude, yanayin tsarin gdn kawai ya tabbatar musu gd ne na masana kimiyya da
binciken qurulla, coffee ya kawo musu yana turiri suka soma sipping sannan prince
ya soma masa bayanin abunda ya kawosu gare shi, shiru yyi na wasu daqiqai sai kuma
yace" ina son ganin mahaifin nk don na duba yanayin gubar dake circulating a
jikinsa" gdy sosai babban prince yyi masa bai ta6a tsammanin wannan bayahude zeyi
saurin amincewa dasu ba cox most of jews basu da trust ga larabawa.......

Pls don Allah kuyi manage da wannan page din, bani jin dadi ne naso yau nayi muku
dogo typing amma jiki da jini sai gdyr Allah.....
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

37

*Your love is a special chemistry and also the most concentrated pure love to my
heart*.......I love everything about you💕💕

Sun shirya komawa masarautar burham da abram don ya duba sarki abdallah bin jabal
dakansa ya fahimci irin gubar dake jikinsa,6angaren bimbii kuwa tana zaune ita da
sumayya suna hira taji mararta tayi wani irin murdewa, skipping tayi ta runtse
idanunta tare da riqe mararta, cikin sauri sumayya ta matso kusa da ita ta riqeta
tana mata sannu, abu kamar wasa ciwo ya soma cigaba, fita sumayya tayi da hanzari
ta nufi wurin ubaid ta sanar dashi abunda yake faruwa, shiga yyi ya sanar da
prince, cikin hanzari ya fito suka nufi dakin da bimbii take, ubaid ya tsaya a
bakin kofa,prince da sumayya suka shiga ciki, saurin qarasawa yyi inda take
durqushe riqe da mararta ya tsuguna ya riqo hannunta, sumayya na gefenta itama,
kallon prince tayi tace" kamar haihuwa ce ta matso mata" saurin dago da kansa yyi
yana kallon sumayya bece komai ba yyi saurin miqewa tsaye ya fita, ubaid yyiwa mgn
sannan ya dawo ciki, gbdy gumi sai tsatstsafo masa yake tamkar shine yake labour
din, a telephone ubaid ya kira gdn sarautan even kan suna buqatar royal doctor,
bada jimawa ba even house suka turo musu da wata likita, baturiya ce ta shigo itama
atleast bazata gaza shekaru hamsin ba, shigowa tayi da gudu da qaramin briefcase a
hannunta, ubaid na ganin shigowarta yyi mata jagora har dakin da bimbii take ta
shiga, prince na ganinta yyi saurin miqewa ya bata wuri, bude briefcase dinta tayi
ta fito da handgloves ta saka cikin azama take gudanar da abubuwa, sumayya na
taimaka mata prince kuwa, kasa cigaba yyi da kallon yadda bimbii ke shan azabar
naquda yyi saurin ficewa daga dakin,ita kuwa bimbii wani irin ninshi take sbd ciwon
da takeji bata ta6a jin irinsa ba tunda uwata ta haife sai yau, bayan ciwon naquda
ga kuma wani azababben ciwon kai tamkar kanta ze rabe biyu,ita dai gbdy ta sadaqar
da rayuwa sbd ta soma jiyo qamshin lahira,Dr.Margaret pushing nata take sosai,
itama tana numfasawa da qarfi, prince yana bakin kofa ya harde hannayensa dukka a
baya yana jiyo sautin ninshinta, idanunsa ya kada yyi ja shi kadai yasan me yakeji
but still he looks very smart, cikin izinin Allah sai ga kan jariri ya fito, hannun
doctorn tasa ta ciro jaririn ta miqawa sumayya dake gefe, jaririn kuwa ya charke
musu da kuka, prince da ubaid kukan jaririn kawai suka jiyo,murmushi ubaid shi kuwa
prince kawai so yake yaji yaya lfyr uwar jaririn, yana son shiga dakin amma yana
daurewa, bimbii kuwa tasha wuya ba kadan ba gashi kanta be dena ciwo ba, hknne yasa
doctorn tayi mata allurar bacci sbd ta huta, sumayya ce ta fita cike da farin ciki
ta yiwa babban prince albishir bimbii ta sauka ta samu yaro namiji, sai lkcin ya
shiga dakin wurin gadon da take kwance ya nufa yana kallonta tana bacci, kallo daya
ya yiwa fuskarta yasan ta jigata ba kadan ba, doctorn da kanta ta dauki jaririn ta
miqa masa tana murmushi, hannu yasa ya amshi jaririn ya tsira masa idanu, yaron
fari ne qal gashi dogo masha'Allah, yanayin ga6o6in jaririn ya kalla yasan komai
nasa ne, murmushi yyi sosai har fararen haqoransa suka bayyana, bimbii baccinta yyi
tsayi sosai har kusan yamma bata farka ba, hkn ne ya tashi hnklin prince ita kuma
doctorn sai kwantar masa da hnkli take sai dare ta tashi a razane, tana kallon inda
take, fuskar da bazata ta6a mancewa da ita bane ta gani kusa da ita, kallonshi take
sosai shima ya qura mata idanu, fashewa tayi da kuka ta dora kanta saman kafadan
shi, kallonta yake cike da mamaki, ita kuwa all that past events da suka faru take
tunawa ta sake dago da fuskarta tasa hannunta tana shafa face dinshi sannan ta
sakko da hannunta daidai wurin da mahaifinsa ya harbe shi da mashi, hannunta ya
riqe dukka ya janyota jikinsa ya kwantar da ita tana kuka a hnkli, yace" ki dena
kuka baki ganin yanzu kin zama ummi" ya nuna mata babyn dake kwance a gefenta,
saurin janye jikinta tayi ta komar dakanta ta kwanta ta rufe idanunta tana son tuna
komai da komai ne, prince matsawa yyi kusa da ita yaja duvet ya rufeta, sunkuyawa
yyi ya mata peck a kumatu, shiru tayi bata bude idanunta har saida taga ya fita
daga dakin ta bude idanunta tana kallon babyn data haifa tana qura masa idanu,kuka
take sosai tana tausayawa rayuwarta, tunani take yanzu idan qaddara ta kuma
daukarta ta mayar da ita nahiyarta me zata fadawa su baffa da innah, tayi ciki har
ta haife kenan bada igiyar aure ba, sosai ta kuma fashewa da kuka, sumayya ce ta
shigo dakin ta ganta tana kuka tayi saurin qarasawa wurinta ta zauna kusa da ita
tana rarrashinta da kalmomi masu kwantar da zuciya, prince komawa yyi side dinsa ya
zauna ya dafe kansa, babban tashin hnklinsa mahaifinsa ne ya rasa ina ze dosa da
wannan rayuwar, zuciyarsa fal take da tsantsar tausayin bimbii da babynsa dake tare
da ita, har gobe yasan shine silar faruwar komai, tashi yyi da sauri ya koma dakin
da bimbii take ya tarar da ita zaune fuskar nan nata babu alamar annuri, hannunsa
yasa da niyyar kama mata hannu tayi saurin matsawa gefe ta dago da fuskarta tana
kallonshi tace" kaga na haife muku jininku dake tare dani don Allah ku mai dani
nahiyata na koma wurin iyayena na gaji da wannan rayuwar mara madafa" durqusawa
tayi a gabansa ta daga hannunta alamar roqo tana kuka tace" don Allah ku maida ni
nahiyata kar ka komar dani wannan masarautar na mahaifinka" shiru yyi komai ya
daqule masa ya kalleta da jajayen idanunsa yace" kina son ki tafi ki barni kenan
baki da damuwa, duk tsawon wannan lkcin dana dauka ina jiranki ki dawo gare ni kk
dawo batare da kin iya shaida fuskata ba hk na kuma hkr har memory nk ya dawo kk
gane ni amma abunda zaki iya fadamin kenan sbd baki dauki soyayyar da nk miki da
daraja ba" kallonshi tayi tace" ranka ya dade ba wannan zaka duba ba, wannan son da
kk fada tun farko na fada mk ze haifar da mtsl gashi silarta ne har rayuwarka ta
shiga garari, mahaifinka dakansa ya harbeka da mashi duk silar wannan soyayya da kk
fada don Allah kayi hkr ka taimake ni na koma qasata" wata uwar tsawa ya daka mata
wacce ta sanyata shiga taitayinta, ubaid da sumayya dake waje su kansu sun razana
da wannan tsawar da prince yyiwa bimbii, yace" kiyi yadda kkso" juyawa yyi ya fice
ransa a 6ace sosai, bimbii fashewa tayi da kuka ita dai ta gaji da wannan rayuwar
qasarta take son komawa don muguntar larabawan nan ya tsorata ta dayawa, basu dauki
kisa a bakin komai ba, laifi qanqani sai su kashe rai batare da shakku ba, fushi
sosai prince yyi da ita kusan kwana uku be sake shigowa inda take ba saidai sumayya
ta dauki babyn takai masa duk safiyya da maraici, idan ya tuna abunda take fada wai
ya maidata qasarta sai gabansa ya yanke ya fadi, tunani yake kar fa ya wayi gari ya
rasa bimbii ta gudu tabar shi da dakon sonta, shi gani yake kamar bimbii ba sonshi
take ba shine kawai Allah ya jarabta da soyayyarta, qanqame babyn dake hannunsa
yyi yana kallonshi, idanunsa yyi ja tausayin kansa yake sosai, rana zafi inuwa
quna, ta 6angaren mahaifinsa babu sassauci gata itama tana son ta gudu tabar shi,
bimbii kam sai duk taji babu dadi fushin dayake da ita, tana zaune sumayya ta shigo
ta sameta, kallonta tayi tace" kije ki bawa prince hkr sbd ranshi ya 6aci sosai
dake tana mugun kafiya da zuciya bazai ta6a kallonki ba kar ki bari ya juya miki
baya kece kadai macen da Allah ya dora akanshi" shiru tayi kawai tana sauraron
sumayya, sai kuma tace"tohm" sumayya tace" ki same shi da dare a bakin teku nan
yake zuwa duk dare" kallonta bimbii tayi tace" shikenan"da dare ubaid dakansa yyi
mata rakiya har wajen teku, garin da hasken farin wata sosai, tunkan ta qarasa ta
hango inuwarsa yana tsaye hannunsa dukka a baya ya qurawa ruwan teku ido, alamu sun
nuna tunani yake mai zurfi, a hnkli ta qarasa inda yake ta tsaya a bayansa, shima
ya hangi inuwarta kawai juyowa ne beyi ya kalleta ba, ita kuwa shiru tayi ta rasa
abun fada, ta jima tana tsaye a wurin, juyowa yyi ya wuce ta da niyyar komawa gd,
tana ganin hk tayi saurin qarasa kusa dashi ta sanya hannunta cikin nashi, tsayawa
yyi chak ya juyo yana kallonta, cire hannunsa yyi daga cikin nata yyi gaba abinsa,
da gudu ta kuma binsa ta rumgumesa ta baya ta qanqamesa da dukka hannayensa tana
masa kuka tana bashi hkr, shiru yyi sannan ya juyo ya riqeta sosai a jikinsa duk
sukayi shiru,hannunsu ta sarqe dana juna suka soma tfy a hnkli kanta na kafadarsa
hannunsu na sarqe har suka qarasa bakin teku suka nemi rairayin suka zauna suna
kallon ruwan teku, shiru sukayi saidai zuciyoyinsu na amsar saqonnin juna, muryarsa
a hnkli cike da sanyi yace" har yanzu kina son ki tafi ki barni koh?" yanayin yadda
yyi mgnr ta fahimci akwai rauni tattare da muryar nasa, dago da idanunta tayi tana
kallonshi, daga hannunta tayi ta cusa a gashin kansa tana wargaza masa sumar
kanshi, shikam binta kawai yake da kallo, cikin sanyin murya tace" bazan barka ba
komai wuya zan kasance tare dakai" tsayar da idanunsa yyi kan fuskarta sai kuma yyi
murmushi, nuna mata bakinsa yyi yace" kimin abunda zan so anan" sosai ta gane
abunda yake nufi tayi saurin rufe ido ta 6oye fuskarta a saman shoulder dinsa cike
da kunya irin nasu na fulani, shi kuwa dariya ta bashi yadan murmusa yace" kina son
akbar?" sosai tmbyr tasa ta qara bata kunya, ta6e baki yyi kafin ta ankara sai ji
tayi ta kwantar da ita a wurin rairayin shima ya kwanta ya dora kansa a saman
qirjinta, dukka kansu na sama suna kallon hasken farin wata da taurarin dake watse
a sararin samaniyya,hannunta ya kamo ya hade da nashi, ita kuma tana wasa da sajen
fuskarsa da dayan hannunta, wannan yanayin da suke ciki ya kore musu duk wata
damuwa ji suke tamkar su kadai ne a duniyar, tmbyrsa take abubuwan da suka faru
dashi duk ya fada mata amma sai ya 6oye mata sanya shi a kurku da mahaifinsa yyi
gudun kar ya qara mata karayar zucci, har dare ya shiga sosai basu sani ba suna nan
kwance wurin, hadarin da suka gani ne yasa suka miqe suka soma tfy suna manne da
juna suka nufi orchard house din da suke, kafin su isa ruwa ya tsuge sosai, hnklin
prince ya tashi sosai sbd gani yyi bimbii ba wani kwarin jiki ne da ita ba ga
danyen jego kar
ruwan saman ya sanya mata zazza6i, itama dan qaramin hannunta ta daga wai zata
kare masa ruwa amma tsayinta ya gaza kaiwa saman kansa sai dage take, dariya yyi,
kallonsu tayi don ita wallah bata saba ganinsa yana dariya ba saidai
murmushi,rawanin dake kafadarsa ya cire ya rufa mata amma duk da hk saida ruwa ya
jiqasu, tfy suke kamar masu tausayin qasa a hk suka qarasa, dakyar ta iya kwace
hannunta a cikin nashi ta shige dakin da take shima ya nufi dakin dayake,
washegari, sun tashi ne da shirin komawa gd, bimbii dai gabanta faduwa yake idan
taji an ambaci sunan masarautar burham, dukkaninsu suka shiga cikin jirgin ruwa
tare da abram, bimbii fuskarta a rufe take kuma batare suke da prince ba tamkar ba
tfyrsu daya ba sbd tsaro, sumayya tana rumgume da baby dayake cikin yalwatattun
kayan sanyi, abram yana zaune kusa da ubaid, tmbyrshi yyi alaqarsu dasu bimbii,
batare shakku ba ubaid ya soma bawa abram lbrin soyayyar dake tsakanin bimbii da
prince mai cike da sarqaqiya da tarin qalubale, sosai wannan tsohon bayahude ya
tausaya don lbrin nasu ya ta6a masa zuciya,hk har suka qarasa yankin masarautar
burham, tunkan jirginsu ya iso dakarun masarautar burham suka iso don tararshi,
lkcin da jirginsu ya iso fasinjojin jirgin suka soma fitowa, kamar yadda prince ya
shirya tuni sumayya ta wuce da bimbii ta wani 6angare daban babu wanda zeyi tunanin
tare suke da prince, bimbii fuskarta na rufe cikin niqab, sumayya tana da wayo
shiyasa yaseer ya hadosu da ita, yadda prince ya umarceta ta wuce da bimbii
qasarban wani asirtaccen gd ne da babban prince ke zuwa shan iska yana nesa ne
sosai da masarautar burham,bimbii cike take da tunani kar wannan sarki mara imani
ya ganota cikin yankinsa ya turo a kasheta ita da jaririnta,tuni tsoro da fargaba
suka mata dirar mikiya...

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw zaki tura #300 ta wannan
acct..0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, saiki tura screenshrt na payment
ta whatsapp a wannan layin..07041195806...

Alkalamin Bintuu ne.....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

38

*I want to be with you even beyond for ever*......you are my destiny💕💕

Sun isa masarautar burham inda kai tsaye wasu hadimai suka wuce da abram inda akayi
masa masauki,prince kuwa wucewa yyi 6angaren mahaifinsa ya same shi yadda dai yabar
shi, sarauniyya na zaune gefensa, sarki abdallah yana daga kwance idanunsa na
kallon prince akbar, tabbas prince yana cike da tausayin mahaifinsa bisa halin
dayake ciki, baya iya mgn har yanzu kawai saidai yana bin komai da idanu tamkar ba
sarki abdallah bin jabal ma'abocin cikar izzah da qarfin mulki ba, prince ya
labarta masa yadda abubuwa suka kasance tsakaninsa da sarki abu ansar da kuma
haduwarsa da abram, batare daya iya cewa komai ba sai kawai murmushi daya bayyana a
saman fuskarsa, hkn ya nuna yaji dadin bayanin da prince yyi masa, sarauniya ta
kalli prince tace" tashi kaje ka huta don kana buqatar hutu" miqewa yyi ya rissinar
dakansa alamar girmamawa sannan ya juya ya fice daga turakar mahaifin nasa,
6angarensa ya wuce ubaid na take masa baya, suna shiga suka tadda bayin dake
6angaren sun jeru sunyi layi don tarbar babban prince, suna ganin shigowarsu duk
suka rissinar dakansu har ya shigesu ya wuce 6angarensa, ubaid ne ya dawo ya tsaya
a saman corridorn dake 6angaren ya sanar dasu babban prince ya dawo lfy kuma yana
kowa fatan alheri sannan ya umarcesu kowa ya koma bakin aikinsa,yana zaune sanye da
wata farar riga ta shiga wanka lenah ta shigo, sanye take da wata doguwar jar riga,
hannunta yasha tsiraran awarwaro ya cika mata hannu,bisa al'adarta qafarta daure da
sarqar qafa, qarasowa tayi inda yake ta tsaye tare da rissinar dakanta qasa alamar
girmamawa sannan ta dago dakanta ta wuce da sauri ta shige dakin wanka ta hada masa
ruwan wanka mai dumi a cikin kwarmin wanka tasa sinadaran wanka sannan ta fito ta
sake rissinar dakanta qasa tayi gefe ta tsaya, wuce ta yyi ya shige dakin wankan,
washegari, tun safe abram da prince suka bayyana a turakar sarki abdallah bin
jabal, abram kallon sarki abdallah kawai yyi yaga yanayin yadda jikin nasa yyi,
dago idanu yyi ya kalli sarauniya mar'atussaliha dake tsaye gefe yace" ina buqatar
ku bani lkcin nan da kwana uku nayi bincike akan gubar" tace" an baka amma ka
tabbata kayi bincike maikyau don mu nan bamu son kuskure" sunkuyar dakansa yyi
alamar girmamawa ga wannan sarauniya sannan ya fita, sarauniya ta kalli babban
prince tace" kana ganin akwai alamun nasara tattare da wannan bayahude, kasan fa
mutane abun tsoro ne bani yarda da kowa ya duba mahaifinka sai cikakken amitacce
sbd muna da maqiya dayawa masu neman ganin bayan wannan masarauta" murmushi babban
prince yyi yace" ranka ya dade wannan bayahude baida wani niyya mara kyau ki duba
kwayar idanunsa zaki tabbatar da hkn" murmushi tayi ta shafa kansa cike da qauna
tace" madallah da wannan jarumin d'a nawa mai tsananin kaifin basira tabbas ina
alfahari dakai" murmushi shima yyi ya miqe tare da rissinar dakansa ya fice, komawa
yyi 6angarensa yana son ziyartar qasarban don duba lfyr bimbii da gudan jininsa
saidai yana shakkar hkn don ko qaqa baya son wani ya gano bimbii na raye har ta
haife cikin dake jikinta sbd tsaro, ubaid ya buqaci gani ya shigo da sauri ya iso
wurinsa tare da rissinar dakansa qasa yana sauraron umarni,kallonsa babban prince
yyi yace" meye tunaninka da ziyarar da nkson kaiwa qasarban" shiru ubaid yyi yana
tunani sannan ya dago dakansa yace" yakai ma'abocin hikima tabbas har yanzu duk
wani motsinmu akan idanun masarauta yake kuma ko yaya ka fita ziyartar wani wuri a
yanzu zasu iya tunanin wani abu wanda hkn zesa su sanya masu binciken sirri su soma
gudanar da bincike" jinjina kai yyi alamar gamsuwa, ubaid yace" duk wani kulawa
tana samu ita da gudan jinin burham dake tare da ita, kuma nasa cikakken tsaro daya
dace" kallonsa prince yyi yace" madallah da wannan amintaccen hadimi" rissinar
dakai ubaid yyi saida prince ya daga masa hannu ya ja da baya sannan ya juya ya
fice, jinginar dakansa yyi a kujerar dayake zaune yana tunanin qalubalen dazai
fuskanta zuwa gaba kan wannan batu don masarautar burham na da tsauri sosai bisa
jagoranci mahaifinsa sarki abdallah bin jabal, yana daga cikin tsaurin wannan
masarauta basu amfani da maganin bature komai a gargajiyance suke yinsa suna kan
al'adun iyaye da kakanni wato larabawan farko, bimbii tana qarqashin kulawar
sumayya tana bata cikakken kulawar data dace, gudan jinin burham kuwa yana cike da
kuzari sam be dauko bimbii a komai ba yyi gadon larabawa ne, yau suna kwance cikin
dare yaro ya soma kuka sosai yaqi yin shiru, daukansa bimbii tayi tana ta
jijjigashi ko zeyi shiru amma yaqi yin shiru kuma yaqi karbar nono yasha, kukan shi
sumayya taji tayi hanzarin shigowa dakin a rikice tana tmbyr bimbii abunda ya same
shi, bimbii tace" nima gani nayi ya fara kuka yaqi yin shiru" hannu tasa ta amshi
jaririn tana kallonshi, jikinsa taji yyi zafi alamun sun nuna zazzafi ne a jikinsa,
ruwan dumi ta hada ta sanya shi ciki sannan ta bashi mgnin zazzafi, saida ta jima
dashi cikin ruwan dumi sannan ta fito dashi ta goge shi ta sanya masa kaya masu
taushi,hkn data masa yasa ya tsagaita da kukan har bacci yyi gaba dashi, washegari,
kwana ukun da abram ya diba ya cika, sai yamma abram ya iso akayi masa iso ga
sarauniya ita kuma ta wuce dashi turakar da sarki abdallah ke kwance, anan suka
tarar da babban prince yana tare da mahaifinsa suna sauraron qarasowar abram,
batare da 6ata lkci ba abram ya fito da wasu tsinkaye masu kaifin gske ya ajiye
gefe, tare da wani farin ruwa, dago dakan sarki abdallah yyi ya bashi wannan ruwan
dake cikin wani gora yasha sosai sannan ya sanya wannan tsinken daya a bakinsa ya
fito masa da wani abu kamar dan wuya ya ajiye a cikin wani qoqo hk ya cigaba dayi
har ya gama, wata qaramar kwalbar ya fito da ita da wani ruwan magani a ciki ya
sake bashi yasha sannan ya goga masa wani mai mai kyalli a dukka sasssan jikinsa,
prince da sarauniya kuwa suna daga gefe suna kallon abunda wannan bayahude yake,
miqewa yyi ya kalli sarauniya tare da rissinar dakansa qasa yace" ranki ya dade na
gama sai mu saurara mu ga yadda jikin nasa ze amshi mgnin, gubar dake jikinsa
baquwar guba ce wacce ta fito daga nahiya mai nisa wato nahiyar baqar fata, nayi
nasarar gano antidote dinta ne sbd na ta6a krt yanayin wannan guba, idan har jikin
nasa yyi maraba da wannan antidote toh daga gobe alamar hkn ze soma bayyana"
murmushi sarauniya tayi tace" idan har nasara ta tabbata lfyrsa ta dawo kana da
kyakykyawar kyauta ta musamman idan kuma muka ga akasin nasarar tabbas fushi na ze
tabbata akan ka" murmushi abram yyi ya sake rissinar dakai sannan yaja da baya ya
fice,dukkanin wanda ke wannan masarauta kawai tsumaye yake yaji ya lfyr sarki
abdallah bin jabal har tsawon kwana daya da yini jikin sarki abdallah be nuna wata
alamar na sauyi ba, cikin izinin ubangiji a washegari sai gashi ya soma miqewa
zaune dakansa, wannan cigaban da aka samu a lfyr sarki ba qaramin farin ciki
yasanya sarauniyya ba, saidai sarki abdallah da batun auren babban prince da
gimbiya qifdiya ya bude baki,hkn yasa prince yyi shiru, cikin kwanaki uku jikin
sarki abdallah ya warware ya dawo yadda yake tun farko, sarki abdallah bin jabal
yyi farin ciki da wannan lfy daya samu tuni yasa aka kira masa wannan bayahude wato
abram har fadarsa, abram na shiga wannan fada ta sarki abdallah bin jabal da aka
ginata da danyen gwal ya zube gaban sarki yyi gaisuwa, murmushi sarki abdallah yyi
yace" yakai wannan masani ma'abocin kimiyya da tarin sani tabbas nayi farin ciki da
wannan ingantaccen magani nk don hk ka fadamin buqatarka gareni kowacce iri ce nayi
maka alqawarin cika maka ita batare da wani 6ata lkci ba,zan faranta ranka kamar
yadda ka faranta min" fadar sarki abdallah tayi shiru kowa na sauraron jawabin dake
fita daga bakin sarki kuma suna sauraron suji buqatar wannan bayahude ga sarki
abdallah, prince na tsaye gefen mahaifinsa shima yana sauraro, abram dago dakansa
yyi ya kalli sarki abdallah sosai yace" yakai wannan sarki ma'abocin qarfin mulki
da magana daya ina da buqata mai qarfi a gareka duk da ina da cikakken sani kan
halayyarka ta cika alqawari da tsayawa kan mgn daya amma duk da hkn ina da shakka
bansan ko zaka iya cikamin wannan buqata tawa ba don tana da qarfi" wannan zance na
abram ya sanyawa kowa tunani shin wanne bayahude kuwa wacce buqata ce dashi hk
dayake wannan batu, jikin sarki abdallah yyi sanyi da jin wannan batu na abram don
shi tunaninsa wannan bayahude buqatarsa bata wuce dukiya, shi kuwa dukiya kowacce
iri yakeso ze iya mallaka mishi batare da yasan yyi wani abu ba don yana da qarfin
arziqi, prince shima a nashi 6angare mamakin abram yake yana tmbyr kansa shin wanne
bayahude wacce buqata yake da ita a wannan masarauta tasu da har yake fadin tana da
qarfi, kallonsa sarki abdallah yyi yace" ka fadi buqatar taka naji kai tsaye" shiru
abram yyi yana shakkar fadin wannan buqata tashi kar wannan sarki yasa a masa kisan
gilla, daka masa tsawa uxair yyi yace" yakai wannan bayahude ba'a yiwa sarki shiru
ka hanxarta fadar buqatarka don sarkinmu ma'abocin alqawari ne da mgn daya kowa ya
shaida" ajiyar zuciya abram yyi ya numfasa sosai sannan ya dago dakansa ya kalli
sarki abdallah bin jabal dake hakimce a wata kujera ta alfarma mai ruwan zinare
yasha alkyabba baqa da rawani mai baqi da fari, duk da sarki abdallah ya cika masa
idanu amma hkn ya bude yace" yakai wannan sarki buqatar da nk nema gare ka itace ka
yarje auren prince akbar da tsohuwar baiwarsa daka yankewa hukunci kisa sannan kayi
aikin gafara a garesu tare da sanya musu albarka su da gudan jininka da yanzu hk
wannan baiwa ta zama silar zuwansa duniya".....fadar yanayin rudani da daya bayyana
a fuskokin al'ummar dake wannan fada yafi gaban kwatance, prince akbar kuwa mutuwar
tsaye yyi, sarki abdallah bin jabal kuwa qurawa abram idanu yyi da fuskarsa da babu
alamun annuri, jin zciyarsa yake kamar zata tsago ta fito sbd tsananin 6acin rai,
fadar tayi tsit tamkar mutuwa ta gifta, prince gabansa mugun faduwa yake duk da
tarin jarumtarsa yana masifar shakkar mahaifinsa, wannan
yanayi da abram ya gani ne yasa tsoro da tarin rudani hade da firgici ya bayyana a
fuskarsa,jikinsa rawa ya somayi sosai, miqewa sarki abdallah yyi yayi ya soma
takawa a hnkli masu tsarinsa suka take masa baya yabar cikin wannan fada batare
daya furta komai ba,sarkin hukunci yaba dakarun dake fadar umarni su kama abram su
wuce dashi dakin horo don koyar dashi darasin harshe.......
Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw zaki tura #300 a wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,saiki tura screenahrt na payment naki ta
whatsapp ta wannan layi......07041195806..........

Alkalamin Bintuu ne......


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

39

*I feel a lot about you darling*........My blood circulate in your blood,yeah, our
love has an identity, I adore you💕💕

Qaramin kurku suka kai shi kafin sarki ya yanke masa hukunci dakansa, prince kuwa
zuciyarsa a hargitse ya koma 6angarensa, ubaid ya kira yace" ka samu amintacciyar
baiwa ka tura ta qasarban don isar da wannan saqo ga sumayya" miqa masa wata farar
takarda yyi, rissinar dakansa yyi ya amshi takardar sannan yaja da baya ya juya ya
fita, wurin qorama ya wuce ya tsaya can nesa ya hango su israt da khulood suna
wanki, kamar ance israt ta juya ta hango shi tsaye ga dukkan alamu su yake son
gani, shikam ubaid yana ganin sun ganshi a wayance ya soke musu wata takarda a
jikin wata bishiya yyi saurin barin wurin, khulood na ganin hk tayi saurin tashi da
niyyar zuwa wurin israt ta dakatar da ita suka cigaba da wankinsu suka basar sai
bayin dake wanki wurin suka watse sannan israt cikin dabara taje wurin bishiyar ta
zare takarda suka wuce abinsu, wurin da babu koma suka samu suka warware takardar,
dayan takardar itace wacce zasu kai ga sumayya dayan kuma takardar shaidar fita ce
da sanya hannun ummu nana don basu basu mai sanya hannun babban prince ba kar a
zargi wani abu sai ubaid ya samu ummu nana ta sanya hannu itama kanta bata fahimci
komai ba don ubaid kamar qani yake a wurinta shiyasa ta bashi sa hannunta batare da
wani tunani ba, israt ta kalli khulood tace"kece zakije koh sbd shaidar fitan mutum
guda ne wannan" murmushi khulood tayi tace" kece zaki iya wannan aiki sbd kin fini
qarfin hali da dabara" wucewa sukayi babban kitchen suka dauki kwandunan debo kayan
marmari suka nufi lambu basu jima ba suka dawo kawunansu dauke da kwanduna cike da
tuffa suka kai musu babban kitchen, cikin dabara israt ta saci jiki ta nufi babban
kofar fita daga masarauta, ganin bayi tayi jere masu shaidar fita suna nunawa ana
basu hanyar su fita, layin yyi tsawo dayawa haka take ta Allah Allah a iso kanta
har masu tsaron kofa suka iso kanta ta nuna musu shaidar fita suka bata hanya ta
wuce, cikin izinin Allah tana fita saqon sarki abdallah ya iso ga masu tsaron
dukkan kofofin masarauta su rufe kofar shiga da fita, batare da sun sake barin kowa
ya fita ba suka hade kofa suka rufe ruf,israt kuwa qarar rufe kofan da taji ne yasa
ta juyawa, farin ciki tayi da Allah ya bata damar fitowa lfy, tfy take sosai tana
qetarawa ta siraran hanyoyi da suka ratsa ta gefen gidajen jama'a kunsan yanayin
ginin larabawa yadda yake hk har ta qarasa qasarban, rufe kanta tayi sosai har da
gefen fuskarta, tsayawa tayi tana hangen kofar shiga wurin ta ganta da qaton kwado,
kofar shiga wurin be nuna mata akwai wani mahaluki sake rayuwa a cikin wurin ba,
hkn ya ankarar da ita lalle karta qarasa kofar shiga wurin ta shiga wurin ta wani
wurin, 2kalle take ta babu kowa don wurin bayan gari ne sosai,tsalle tayi ta haye
katangar shiga wurin ta dire ciki, ko'ina yyi qura har ta soma jin tsoro anya kuwa
da wani abu mai numfashi a cikin wannan gd,shiga dai take tana danna kai cikin gdn
dayake da zurfi, tuntu6e tayi da wani dutse ta fadi ta riqe kafarta, sumayya kuwa
tana nesa kadan da wurin ta jiyo motsin mutum, miqewa tayi da hanzari ta isa inda
israt take ta bayanta sai ji tayi an saka mata wuqa a wuya, bude idanu israt tayi
tana kallon sumayya tace" kiyi hkr ki sake ne don nidin isar da saqo nazo yi" sauke
wuqan sumayya tayi, israt ta kalli sumayya sosai ta ganta yadda ubaid ya kwatanta
kamanninta cikin takarda, ciro takardar tayi daga jikinta ta miqa mata,saurin
warware takardar sumayya ta ga sanya hannun babban prince sannan ta soma krt abunda
ke ciki, tana gama krtw tayi ciki da sauri, israt tabi bayanta don tana son sake
ganin bimbii, kai tsaye suka shiga inda bimbii take, bimbii na dago dakanta taga
israt tsaye da gudu ta taho suka rumgume juna cike da farin ciki, sumayya kuwa
saurin kama hannun bimbii tayi, jaririn na hannunta shiga dasu wani wuri, wata
kusurwa suka shiga ta janye center carpet din dake shimfide wurin sai ga kofa ta
bayyana ta bude kofar tayi da hannunta suka hangi matattakala data shiga qasan
wurin, takawa suke a hnkli sumayya na haska musu hanya da wata qatuwar fitila har
suka qarasa qasan wurin, cikin qasan wurin yana da fadi sosai, rumbii tara dukiya
ne sbd ta kowanne gefe diamond ne a jere sai kyalli yake da daukar idanu,
dukkaninsu sake baki sukayi suna kallon wannan tarin arziqi tamkar ba za'a mutu
ba,zaunar da bimbii sumayya tayi israt ta zauna kusa da ita, fita sumayya ta sakeyi
taje tayi clearing komai wanda ze nuna akwai mutane a gdn sannan ta dawo ta shiga
ta maida kofar wurin ta rufe kamar yadda yake a baya, befi awanni uku da faruwar
hkn ba, dakarun sarki abdallah suka shigo wannan gd don bincike, sumayya kasa kunne
tayi ta jinsu suna bincika kowanne lungu da saqo na wannan gd don suna tunanin nan
prince ya kawo bimbii, har suka gama bincikensu ba bimbii babu alamarta, har zasu
juya su tafi wani daga cikinsu ya hangi mayafin mace a saman gado, nuna ma sauran
yyi suka dawo, daukan mayafin sukayi suna qara kallon ko'ina, binciken qurulla suka
cigaba dayin cikin gdn har kusurwar da dakin qasan nan yake suka shiga suka gama
bincikensu basu ga komai ba hk suka koma suka sanar da masarauta,sarauniya
mar'atussaliha kuwa lkcin data ji wannan abu daya faru ba qaramin tashi hnklinta
yyi ba bata ta6a tsammanin wannan baiwa na raye ba har kuma wai ta haife cikin
jikinta, tsoron da take yanzu kar sarki abdallah bin jabal ya kuma fishi da prince
sam bata fatan hk, tashi tayi cikin sauri ta nufi turakar sarki ta nemi iso, uxair
ya shiga ya fito ya sanar da ita sarki bazai ganta ba, dole ta hkr ta koma
6angarenta cike da rudani,sarki abdallah bin jabal be sake fitowa ba sai washegari
ya nufi fadarsa, umarni yyi kan a kawo masa abram, batare da 6ata lkci dakarun
tsaron fadar suka gabatar da abram gaban sarki abdallah bin jabal, prince shima
yana fadar beyi shakkar zuwa ba, yana tsaye daga gefe kansa a sunkuye har lkcin da
aka gabatar da abram gaban sarki, abram kallo daya zaka masa kasan ya jigatu abunka
da jar fata tuni jigatuwa da wahala ta bayyana a tare dashi, fada tayi tsit kowa na
jiran yaji hukuncin da sarki abdallah ze yankewa wannan bayahude tare dansa, daga
kai sarki abdallah yyi ya kalli abram yace" kamar yadda na mk alqawari na amshi
buqatarka zan cika mk sbd bana alqawari na saba wannan itace nasarar da kayi saidai
da kyakykyawan sharadi, shine na amince zan aurawa d'ana baiwa mara asali dalilin
alqawarin dana dauka saidai aure ne dazai wakana batare da masarautarmu ta gayyaci
kowa ba kuma ba za'ayi wani sha'ani ba"prince dake gefe yyi saurin dago dakansa
cike da mamaki yana kallon mahaifin nasa, don be ta6a zaton mahaifin nasa ze amshi
wannan buqata ta abram ba, shiru yyi yana tunani anya sarki abdallah be shirya wani
tuggu ba kuwa shi yasa yyi hkn,kallon prince sarkin yyi yace" ina son daren yau ka
gabatar da wannan baiwa da kk 6oye da ita ga ahlinka" rissinar dakai prince yyi
alamar biyayya da amsar umarni,sarki yyi umarni da dakarin nan su saki abram, daga
nan zaman fada ya watse, prince ya qarasa 6angarensa cike da tunani kan manufar
sarki abdallah kan wannan batu gani yake kamar da wata a qasa kar fa sarki ya
shirya masa shigo shigo ne ya samu damar damqe bimbii da dansa dake tare da ita ya
aikasu lahira, zuciyarsa ta kasa nutsuwa har yanxu, lbrin wannan hukunci da sarki
abdallah ya yanke tuni ya isa ga sarauniya itama dai mamaki abun ya bata, gimbiya
hindu kuwa da bata jima da dawowa daga habasha ba baqin ciki da takaici ne ya
cikata itama batayi zaton har yanzu bimbii na raye ba don akan idon kowa bimbii ta
afka wannan dogon rami........

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419, alhaji shahida nasir,union bank, saiki tura screensht na payment
dinki a whatsapp ta wannan layi...07041195806....

Alkalamin Bintuu ne....


9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔

Written By Bintuu Seer

40

*I give you my heart,I give you my blood,I give you my soul*............I sacrifice
everything to you my beloved💕💕

Prince dakansa ya nufi qasarban ya taho da bimbii, ranar duk inda ka zauna cikin
bayi tsegumin wannan zancen suke wai tsohuwar baiwar babban prince ta dawo tare da
sabon jariri, mafi yawan masu tsegumin basu aminta cewa wannan d'an na babban
prince bane, sarauniyya mar'atussaliha dakanta ta bada umarnin a shiga da bimbii
6angarenta, bimbii kam zuciyar cike take da tsoro musamman yadda taga fuskar
wadanda suka tare ta, ummu nana da wasu kuyangi biyu suka kama hannun bimbii suka
shige da ita,ummu nana ta amshi jarrin dake hannun sumayya ta wuce dashi ciki,
wanka aka yiwa jarrin aka sanya masa kaya na alfarma sannan ta fito dashi ta wuce
dashi ga sarauniyya, tana shiga ta sunkuya ta miqa mata jaririn, miqa hannu tayi ta
amshi jaririn, qurawa jaririn idanu tayi tana kallon ikon Allah don wannan jariri
babu ta inda ya baro kakansa sarki abdallah hatta idanunsa na kakansa ne, kasa dena
kallon jaririn tayi tana qara jaddada mulkin ubangiji wato dai zakaran da Allah ya
nufa da chara ko ana muzu ana shaho sai yyi, yaro dai kakansa ya dauko, miqewa tayi
dakanta hannunta biyu riqe da jaririn ta nufi 6angaren sarki abdallah ummu nana da
sauran kuyaginta na take mata baya, uxair ne ya shiga ya nema mata iso sarki
abdallah ya bata damar shigowa ta shigo, yana zaune a wata kujera ta sarauta tunda
ta shigo yake kallonta, rissinar dakanta tayi a gabansa sannan ta miqa masa jaririn
dake hannunta, qin miqa hannunsa yyi ya amshi jaririn ya daga mata hannu alamar ya
sallameta, shiru tayi tana kallonsa sanin halin taurin kai da kafiya irin nasa yasa
taja da baya jikinta a sanyaye ta juya ta fita, komawa tayi sashinta ta tarar itama
bimbii ta shirya tsaf, itakam sarauniya ta zubar da makaman yaqinta tunda ta dora
idanunta kan jaririn nan, bayin gdn gbdy sun saka idanu har sun gaji amma basu samu
damar ganin bimbii ba bare jaririn dake tare da ita,shi kansa prince ganin bimbii
ya gagare shi,kamar yadda sarki abdallah ya alqawarta hkne ya faru, safiyar alhamis
al'ummar fadar masarautar burham suka shaida daurin auren bimbii da prince akbar,
wurin wannan daurin aure tamkar wurin makoki babu mai annuri ko walwala, a dai
daura, sarki abdallah ya tabbarwa al'ummar duniya shi sarki ne mai mgn guda da
tsayawa kan alqawari, wannan rana baqa take qirin ga sarki abdallah da dukkanin
wani jini na sarautar burham idan muka dauke babban prince da ranar take fara qal a
wurinsa, a tarihin masarautar burham yarima akbar shine d'an sarki na farko daya
karya tsaurarriyar dokar wannan masarauta ya auri baiwarsa, wannan aure ya zamto
tamkar faruwar mugun abu ga jinin sarautar burham, dayake abun duniya baya 6uya
kafin giftawar ido wannan aure tsakanin d'an sarki da baiwa ya karad'a sauran
masarautun larabawa, sarakai dayawa idan suka ji wai duk qarfin mulki da izzah irin
ta sarautar burham magajin masarautar ya bige da auren qasqantacciyar baiwa kuma
baqar fata, hkn yasa sarki abdallah ya dena halartar taron sarakuna na nahiyar
larabawa sbd wannan abun kunya da d'ansa ya janyo masarautarsa,bimbii har yanzu
tana 6angaren sarauniyya daren yau za'a miqata 6angaren prince akbar, sun shirya
sosai albarkacin hada jini dasu da tayi, prince yasa matakan tsaron sirri masu
sanya idanu kan duk wani motsi na masarautar burham kan iyalinsa,keken doki na
musamman aka kawo don daukar bimbii zuwa 6angaren babban prince, dakarun tsaro da
yan matan bayi kewaye suke da wannan keken dokin, fuskarta rufe take da jan mayafin
kayan dake jikinta, ta wata siririyar dake saman gada suka bi,hanya ce da dawakai
ke ratsawa zuwa 6angarori daban daban na gdn, tfy suke zabiyoyi dake biye da keken
dokin na rero waqoqi na masoya masu dadi har suka kai tsakiyar hanyar, suna
tsakiyar wannan siririyar hanya sai gani sukayi kawai an tsagayesu, wasu mutane ne
sanye da baqaqen kaya, fuskokinsu ma a rufe suke batare da wani 6ata lkci ba suka
soma fada da dakarun dake janye da keken dokin da amarya ke ciki, sunyi masifar iya
fada kafi kwabo sun soma kwantar da dakarun, burinsu kawai su qarasa wurin wannan
keken doki su dauke amarya da jaririn dake tare da ita, ihu kawai kkji, jini duk ya
6ata keken dokin, yan matan bayin nan qoqarin fito da amarya suke su gudu da ita
kafin wadannan mutane su qaraso, tuni suka gane nufin kafin suyi wani yunquri wani
cikin mutanen ya yarfa musu wani sai ga wasu kananan allurai masu guba sun fita sun
sossoki jikinsu suka zube a wurin, sai da suka gama da kowa suka bude keken dokin
suka janyota waje wani daga cikinsu yasa hannu ya wafce jarrin dake hannunta, jin
jikin jaririn yyi wani iri, saurin bud'e kyakykyawan farin towel din da jaririn
yake ciki yyi,tirrqashi! kunsan me ya gani qatuwar teddie, kallon juna sukayi cike
da tsantsar mamaki, aikuwa tamkar hadin baki su duka suka sanya hannu suka yaye
mayafin da armarya ke rufe dashi sukaci karo da wata baiwa itama duk a tsorace
take, batare da wata wata ba babban cikinsu ya daga takobi ze fille kan wannan
baiwa a fusace,wani mahayi fuskarsa rufe da baqin kyalle ya bayyana bisa farin doki
tunkan ya qaraso yake harbinsu da kwari da baka har ya qaraso wurin, hkn yasa
hnklinsu gbdy ya tafi ga wannan mahayin doki suka gyara riqon takubban dake
hannunsu hkn ya bawa wannan baiwa daman barin wajen don tsira da rayuwarta, wani
irin fada suke gwabzawa tsakaninsu da wannan mahayin dokin burinsu kawai suyi masa
illah saidai salon fadansa yyi masifar basu mamaki sbd fada yake irin na cikakkun
jarumai masana sirrin takobi, gashi da zafin nama da iya gociya, suna ganin hk
sukayi wani irin alkafira suka fada qasan gada su dukka, sauka yyi a hnkli daga
saman dokinsa yana kallon irin 6arnar rayukan da sukayi sbd kawai son zuciya,
shikam taurun kai wannan sarki na bashi mamaki besan sai yaushe ne ze ajiya wannan
kiyayyar da taurin kai ba, qara jinjina kaifin basira na prince yyi daman yasan hkn
na iya faruwa shiyasa ya bawa sumayya kayan da bayi ke sanyawa yace ta bawa bimbii
ta saka ta fito da ita a sace ya tura mata wannan baiwa ta zama a madadin bimbii,
saida sumayya ta bari an gama shirya bimbii daga ita sai ita tayi saurin sanyata ta
cire wannan kayan dake jikinta sannan ta shigo da wannan baiwa ta cire kayan
jikinta sukayi musaye, ita baiwa ta zauna a madadin bimbii ta rufe fuskarta da
mayafi, sumayya sanya jaririn cikin kwando bimbii ta fita dashi batare da kowa ya
ankara ba ta nufa inda sumayya ta fada mata don daman tasan ko'ina cikin gdn, sai
qasa take da fuskarta kar wani ya ganeta hk har ta samu ta fice daga 6angaren
sarauniya ta nufi daidai gdn magani wurin da sumayya ta fada mata ta hangi inuwar
mutum tana waigawa ta hangi ubaid ta qarasa, batare da wata doguwar mgn ba ya samu
ya qarasa da ita 6angaren prince akbar ta shige, wannan shine zahirin abunda ya
faru a 6angaren sarauniyya, lkcin da bimbii ta shiga ta tarar da prince tsaye yana
sauraron qarasowarta don ya aminta da hikimar hadiman dayasa wannan aiki yasan
dakyar ne a samu kuskure, yana ganin bimbii ta shigo yyi murmushi tare da bude mata
hannayensa, tsayawa tayi don kunyarsa take ji, murmushi yyi ya qaraso ya amshi
yaron dake hannunta ya rumgume shi a qirjinsa itama ya janyota ya rumgumeta suka
qarasa bakin gado suka zauna hannunsa yasa ya dago da fuskarsa data 6oye a saman
kafadarsa yace" kin zama sarauniyata nafi kowa farin ciki da hkn kefa?" shiru tayi
masa ta qara 6oye fuskarta a kafadarsa, juyawa yyi ya kwantar da babyn dake
hannunsa a saman gadon ya dawo ya zauna ya sake janyota jikinta suna fuskantar
juna, numfashinsu na haduwa, bakinsa ya matso dashi daidai da dan mitsitsin bakinta
ya dora saman nata a hnkli kuma ya soma kissing nata cikin wani salo mai saurin
rikita lissafi, bimbii kam idanunta na lumshe, sun yi nisa cikin wannan yanayi suka
ji qarar kukan babynsu yana wani irin kakari, a rude suka saki juna suka juya don
ganin me ya same shi................

Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqatar krtw zaki tura #300 ta wannan
acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank,saiki tura screenshrt na payment
ta whatsapp ta wannan layi...07041195806.....

Alkalamin Bintuu ne......

You might also like