Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 68

COPY N COMPILED BY

ESHAAT SMILER HOM OF


HAUSA NOVLS DOCUMNTS
WASAPP 08066360176 FOR MORE
AISHATUL MUBEENA 1-20
[12:12AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
[1]-[5]
Na Miss hafcy
©ONLINE HAUSA WRITTERS
A fusace ya shigo gidan yana mita "Haba!!
Mutum dame zeji? Da zafin talaucin dake damuna
ko kuwa da Rashin haihuwa,,Nagaji da wannan
rayuwar! "" Da sauri ta fito daga daki" Haba
malam ai talauci ba hauka bane kuma haihuwa aiy
ta Allah ce,,ka shigo gida bako salama kana
fadan wannan maganganun ai komai yayi zafi
maganinsa Allah"" Ya dago a fusace ya kalleta
"ma'u kinga kimin shiru ki barni naji da abinda
nake ji ace yau duk wahalar dana sha a kasuwa
amma ba wani cinkin kirki dame zanji haba!
Haba!!"" Ma'u tace "Amma ai be kamata wannn
maganar ta dinga fitowa daga bakin kaba,,Kasani
fa Allah yana cewa,, Acikin suratul baqarah Aya
ta 153 "" innalla ha ma^as -
sa biri n .""Ma'ana: Allah yana tareda masu
haquri"",, Ya juyo ya kalleta toh sarkin wa'azi,,
naji shikenan yanzu da abinda zan samu naci??
Tayi murmushi,,Dazu na sami 200 wankin
danayiwa talatu shine na yi mana danwake har
tumatir ma na bada aka siyo min"" Ya washe baki
yauwa mata ta gari nagode an gaishe ki,,Suka
shiga cikin dakin
Bayan ta zuba mai danwaken a plate ya fara ci se
santi yake yi can ya kalleta yace "Duk sanda nake
cikin matsala in na tuna muna tare zan dawo na
ganki se naji wani dadi a raina,,saboda nasan
dole zaki faranta min rai" Tayi murmushi sannan
tace "malam kenan nima ai duk hakan take" Yace
"madalah ni yanzu matsala dayace take damuna
wanan rashin haihuwar dan na tabbata daga
gareni take mata nawa na aura bayanki amma har
yanzu ba wada ta taba ko bari"" Ta nisa "Malam
ba lallai bane hakan ne kawai dai mucigaba da
addua,,,Se kaga cikin yardar Allah mun samu"
Yayi murmushi yace toh mata ta gari na gode
Allah ya amsa adduar mu tace "Amin malam"
Bako sallama ta banko dakin,,ma'u da sauri ta
tashi tana "Ahh iya ce? Sannu da zuwa,, iya ta
balla mata harara "Dallah yimin shiru se shegen
kinibibin tsiya ba wajen ki nazo ba wajen dana
nazo" Ma'u ta sunkuyar da kai bata qara magana
ba....Iya ta kalli Mal,, "Kai kuma mara zuciya
kawai kaqi rabuwa da wannan matar me baqar
kafa ta tsiya na gaji ace har yau banda jika,,nasa
ka auri mata bata ko shekara ka saketa,, se
wannan mayar matar taka,Naga alama so kake na
mutu van sami jika ba "" Ta fashe da kuka,,Mal ya
kalleta "Haba inna,,Ya kikeso nayi? Da sauri ta
katse shi KA SAKI MATAR KA MAU SAKI 3! A
firgice ya juyo ya kalleta "Haba iya,,ki tuna fa a
duk matan da nake aura ita ce kadai me rupa min
asiri take zaune dani a wannan quncin,Ga rashin
haihuwa amma kuma kice na saketa haba iya!,,
Iya ta juyo da mamaki "Auho lallai sule ka girma
ka isa har ina ma magana kana maida min,,ta
fashe da kuka ace dan dana haifa shi muke
musayar yawu dashi na shiga uku ni tani!""Ya nisa
sannan yace "iya ba haka bane ba wlhy abinda
kika bukata ne bazab iya ba,"" Iya ta fusata "to
kaje wlhy matar nan ta qara wata3 bata sami ciki
ba se an raba auren nan,,,Tunda ban isa nasaka
abu ka yi ba,,"" Ta fice cike da fushi Ma'u datake
ta kuka ta juyo ta kalleshi "Bansan me nayiwa iya
ta tsane ni haka ba,,Har yau ta kasa gane cewa
haihuwa ta Allah ce"" Mal ya juyo ya kalleta "Kiyi
haquri ma'u na Insha Allah matsalarmu ta kusa
zuwa qarshe! Ma'u ta share hawayenta "Allah
yasa ameen" Ta dauke kwanukan dake dakin ta
fita dan wankesu shikuwa kishingida yayi akan yar
katifar dakin ina jinjina maganar iya
Share
Recent Posts
[12:13AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
©ONLINE HAUSA WRITERS
NA MSS HAFCY
[6]-[10]
***ASALINSU****
Malam Sulaiman Abubakar me rariya Dan kasuwa
ne sana'arsa bata huce Ta saida rariya ba, yana
yin rariya ya kuma siyar a kasuwa sana'ar kuwa a
wajen babansa ya gada,Alhaji abubakar me rariya
marigayi,,,,
Alhaji Abubakar me rariya yanada mata biyu da
yaya guda 4 guda daya ta rasu,, Balki itace
matarsa ta farko wadda ta haifa masa yaya
biyu,,,Bashir da hauwa,Wanda dukansu sunyi aure
cikin rupin asiri, Se kuma matarsa ta biyu Amina
(Tani) Masifafiyar mata ce ta gaske ga rashin
haquri Ta haifa masa yaya biyu Mal sule shine na
farko se kuma habiba wadda ta rasu tun tana
qarama,,,,,,,,,
Mal Sule matarsa daya wanda suke zaune a halin
yanzu, asmau ma'u wacce sukayi auren soyayya
amma shiru kusan shekara 10 kenan suna tare
Amma ko batan wata bata taba yi ba,,,Hakan
yasa tani wadda suke cewa Iya ta takura masa
akan se ya qara aure,, mata aqala sunkai 5 ta
kawo masa in ya auri wanan ta fita se ta kuma
samo wata yan mata da zawarori amma kuma
sam basa zama Kuma a cikinsu ba wadda ta taba
ko batan wata balle bari,,In suka gaji se su
tafii,Ga talauci ga rashin haihuwa da kansu su
suke neman saki, Wasu kuma in ya gaji da
halayarsu se ya sake su Iya tayi masifar ta
gaji,,,Tayi neman malaman akan nemawa tilon
danta sule haihuwa amma har yanzu shiru
Ma'u matace me haqurin gaske da tawakali
tanada ilimin addini sosaii hakan yasa rashin
haihuwar sam be dame ta ba Duk da talauci irin
na mal sule amma Haka take haquri ta zauna
dashi wataran ma da en dabarunta take ciyar
dasu,Dan itama gidansu ba wasu masu arziki
bane,Ga miji shima ba wani me arziki ba dan da
sana'ar rariya kawai ya dogara ko noma ba yayi
saida gonar gadonsa yayi,,Suna zaune yau da ci
gobe babu.
********CIGABAN LABARI******** Ma'u da
gudu ta fito daga daki tana kwarara amai a
rariyar tsakar gida,,daidai shigowar iya kenan,,iya
da sauri ta isa wajen ta "yar nan meya faru haka
me kika ci" Ma'u Tana huci tace " Wlhy tun da
safe nake jina wani iri ga zazzabi dazu kuma
zuciyata ta fara tashi shine fa na fara jin amai
har nazo nayi" Iya ta dago kanta" Yaushe rabon
da kiga aladar ki? Ma'u tace "Watan daya huce
dai bangani ba""
Iya ta duba idonta sosai aikuwa se ta saketa ta
rangada guda ""Ayiriyiri" Yarinya ki godewa Allah
ai alama ta tabbatar da cewa ciki gareki kai yau
ni nafi kowa murna ayiriririiriiiii"" Ma'u ta zaro
ido maganar iya se tazo mata kamar a mafarki ta
dago cikin dashashiyar murya tace "Iya ciki fa
kika ce?" Iya ta washe baki "Tabbas yar nan kiyi
murna fa"
Daidai lokacin mal sule ya shigo gidn dauke da
rariya a hannunsa ya tsaya turus ganin iya tasa
ma'u a gaba tana rangada guda ya matso yace
"Iya me ya faru ne" Iya ta kuma washe baki "Yaro
albishirin ka?"Da sauri yace goro iya" Iya tace "to
matarka ciki gareta alama ta nuna!"
Mal sule ya yarda rariyar dake hannusa se ganni
Inna tai ya daga hannu sama yana godiya se
kuma hawaye,,Ma'u da take tsugune kuka ta fara
a hankali kukan murna! Yau dai Allah ya amshi
addu'arsu! Mal sule a fili yace "Allah nagode
maka,ya allah daka amshi addu'a ta, Ya Allah
kasa dan dake cikin matata ya zamo namiji! Allah
yasa namiji zata haifaa na samu magaji ameen!!
Ma"u da sauri ta share hawayenta ta kalleshi
"Haba malam Ai ba'a yiwa Allah haka kai dai
kawai kayi fatan allah ya bamu nagari, inma
namiji ne inma mace !"
Ya juyo ya kalleta "A'a fa Ma'u ki banni na roqi
Allah ya ban namiji dan ni banida wani buri daya
huce na haifi da na miji ba mace ba!" Iya se a
lokacin tace " fadi ka kara dana,me za'ayi da wata
mace? Ina laifin da na biyu ta haifo mace amma
wannan cikin Inshaa Allahu namiji ne ehe!"
Ma'u ta tashi ta girgiza kai alamar kalaman basu
mata dadi ba ta shige daki cike da farin ciki A
zuciyarta kuma mamakin furucin su Mal
take,tabar Mal da iya a tsakar gida suna ta Farin
ciki da anashuwar abinda ya faru! Iya tace "ka
dinga kula da ita bari naje na sanarwa da en uwa
da abokan arziqi wannan abin alherin,Ai banga ta
zama ba" Ta fice tana guda shima kuwa cewa
yayi "nima banga ta zama ba kuwa nima bari naje
na siyo mata kayan makulashe!
Share
Recent Posts
WA GARI YA WAYA? 2
WA GARI YA WAYA? 1
WA GARI YA WAYA?? 3
Comments
No comments yet. Why not make the first
one!
New Comment
[]
Name:
Comment:
(Some BBCode tags are allowed)
Post Comment
options
Home
Guestbook
About Me
Feedback
Blogroll
Feed: RSS / Atom
Comment Feed: RSS / Atom
Get a
October 2016
October
13
Thursday
11:12 PM
Go to top
Visitor Counter : total-0060690
© 2016 Hafsat's Mobile Blog .
fmb_Powered by
Copyright 2016 mrs hafcy design by
muhammad abba gana (09039016969)
[12:14AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS
[15]-[20]
Ma'u tana zaune tana cin tuwo mirar kuka da
yajin dadawar da mamanta ta aiko mata, gefe
guda kuma farfesu ne Goggo(k'anwar
babansu,wadda tazo mata zaman wanka) ta kawo
mata,suna zaune ita da goggon suna hira,Babyn
na hannun goggo,, Salamar Mal sukaji,ya shigo
fuska ba yabo ba falasa suka gaisa da goggo tace
"Ahh angon k'arni ne ke tafe ashe" be amsa mata
ba,tamai barka, ciki-ciki ya amsa sannan ta basu
waje
Ma'u da murmushi ta juyo ta kalleshi "Mal
kenan,inata cigiyarka kazo kaga kyauta da Allah
ya bamu,Yau dai Allah ya amshi addu'ar mu,se
mu gode masa"a fusace ya kalleta "ke dallah
sauraramin! Kin tashi kin haifo wata mace,
zakimin dadin baki,bari kiji zuwan nan danayi abu
biyu ne ya kawo ni, ki saurara da kyau kiji""
Ma'u tace "Ikon Allah mal meya yayi zafi haka?
kuma ai bani ce ke bada haihuwa ba,Allah ne ke
bayarwa" Ya katse ta"Abu na farko shine: kinga
wannan(ya fito da dari biyar 5) ita kadai zan bada
ayi hidimar suna da sauran abubuwa,Kaya kuwa
kinsan na gama siya dan haka kyasan yadda
kikayi,,Ragon dana siya ma,zuwa zanyi a cazamin
aban tunkiya dan banga amfanin yankawa mace
rago ba! Abu na biyu, nazo muyi salama domin
tafiya zanyi bayan suna na dawo,Dafatan kin
gane?, Ma'u bata san sanda ta fashe da kuka ba,,
"Mal yanzu abinda kayi ya dace mal? Kayi mana
aladalci nida yarka? ,, Ya katse ta "kinga ni bance
kimin surutun banza ba,in kina da magana ki fada
da sauri, dan tafiya zanyi gidan iya yanzu,,Ma'u
ta cigaba da kuka bata bashi amsa ba
Yana k'ok'arin fita ne cikin dashashiyar murya
tace " Mal dan Allah ina neman alfarma a
wajenka" ba tare da ya juyo ba yace "tame?" Ta
cigaba"Inaso kayi ma yarinyar nan huduba kamar
yadda Kowanne uba ya kamata yayiwa Dansa ko
yarsa,Sannan kuma inaso ka dauketa ta ji dimin
jinkin ka koda na minti 5 ne,,Ta fashe da kuka
Ya danyi jim sannan ya gyada kai,ya koma ya
zauna,Ya turbune fuska, ta dauko babyn, ta mik'a
masa ya karba yana gun-guni,, "Ai se ki fadi
sunan da zan samata," Ma'u ta juyo tace "Da
nazata ai kaine zaka zaba" a fusace yace "ke
bansan bata lokaci" cikin sanyin murya tace
"AISHATUL MUBEENA"" Tsaki yayi ,toh shikenan,,
Ya mata hudubar,ta dan dade a hannunsa sannan
ya mik'a wa ma'u ta karba tana murmushin
yak'e,tace "nagode mal Allah ya kiyaye hanya"
yace ameen, yasa kai ya fita" Ma'u ta k'urawa
AISHATUL MUBEENA ido kawai se jin sabon
hawaye tayi na zuba,Tausayin Yarinyar duk ya
cika mata zuciya,,,Goggo ta shigo ta tadda ta
tana kuka,da sauri ta iso wajenta"Ma'u meya faru
kike kuka?" Ma'u ta share hawayenta "bakomai
goggo" Goggo tace "ban yadda ba,ki fada min
abinda ke damunki,ko wani wajen ke miki ciwo?"
ma'u tace "A'ah goggo kaina ne ke ciwo" goggo
tace "kuma shine kike kuka,bari na dauko miki
magani" ta tashi dan dauko mata maganin
Iya tashigo kamar yadda tasaba yau ma ba
sallama" ke ma'u dama nazo fada miki sak'o ne,
mijinki yaban kudin,Shinkapa da kayan miya na
taron suna,Dan haka bazan baki kudin ba kuje ke
da daginki ku kashe a banza,dan haka ana gobe
suna kome ake buk'ata se kiyi magana,,""Ma'u ta
girgiza kai"A'ah iya ki barshi kawai,Ni bazanyi
taron suna bama,Na hak'ura kawai Allah ya
rayata,Tunda bezo a al'k'urani ba dole se anyi
taron suna ba" Iya ta zaro ido ta dafe k'irji "Lallai
yar nan kin rik'a wato ni kike fadawa magana a
fakaice koh?" Se a lokacin goggo tasa baki " A'a
a'a Tani karki soma,Yarinyar nan a kalamata ba
wanda yayi kama dana zagi ko kuma na bak'ar
magana, iya tace kwaji dashi dai dangin tsiya ta
fita tana masifa",Ma'u ta fashe da kuka "oh ni
asma'u ya zanyi? Da bak'in cikin mijina ko dana
uwarsa?
® OHW
AISHATUL MUBEENA 20-30
[12:15AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS
[20]-[25]
Goggo da sauri ta katse ta"karki soma fadan
wadanan maganganun Ma'u kinji,Kiyi hak'uri
komai lokaci ne" Ma'u tace toh goggo insha Allah
bazan kuma damuwa ba,Zanta addu'a Allah ya
ganar da mal gaskia,,Goggo tace yauwa yar
albarka..
Yan uwa da abokan arzik'i sunata zuwa
barka,Yarinya tana ta samun kaya masu
kyau,,rannar suna kuwa duk da Ma'u tace bazata
yi taron suna ba mutane anzo dayawa...wata
mak'ociyarta wadda suke mutunci sosai khadija
shinkafa dafa duka ta yimata me dadi da
zobo,dayake mijinta nada hali,Ma'u tayi farin ciki
sosai da abinda khadija ta mata tayi ta
godiya,,,dangi aka zo anata kwashar girki ana
santi,hada su Iya,don ita har diba tayi ta kai gida
kowa yaji sunan yarinyar AISHATUL MUBEENA Se
ya yaba sunan ,,,Liman ne ya yanka tunkiyar
suna, Iya kuwa ta tsaya tsayin daka akan naman
k'iri-k'iri ta hana dangin Ma'u da sauran mutane
taba naman,Daga ita se yan'uwanta ne suka
sarafa naman,Wai kada su Ma'u su handame, ita
ma'u ma ko a jikinta...yarinya ta samu kaya kuwa
masha Allah daga ita har Ma'u itama tana samu
kudi da atamfofi,tayi mamaki sosai dan bata taba
zata zata samu abin alherin data samu ba
Bayan suna mal ya dawo,Ba yabo ba
falasa,Amma kuma sam yaqi yadda ya dauki
yarinyar koda wasa,Tun Ma'u tana damuwa har ta
dena,Ta cigaba da kula da yarta da ita kanta
bayan tayi arba'in ta zagaya dangi yawon arbain
shima da kyar ya barta,,Iya kuwa kullum cikin
tsangwamar AISHATUL MUBEENA take,Har yanzu
kuwa bata dauke ta ba,se dai ta kalleta daga nesa
BAYAN SHEKARA BIYU
Mal naezaune a kofar gida suna tadi shida wani
abokinsa sanda,Wasu mata suka nufo gidan su
3,A tare suka gaida Mal ya amsa yana washe baki
daya daga cikinsu tace" Mune masu yak'i akan
cutar poliomyelitis wato cutar polio,Mun samu
labarin kana da ya shine zamuyi mata
rigakafi,"Mal ya kalleta "ke ni banda yaro a
gidana ku fice min daga nan shashasahai kawai"
Dayar tace "kaga malam dan munzo mu taimake
ka kaida iyalinka,baka isa ka zage mu ba,ko
dayake naga alama kai jahili ne!" Ya juyo ya
kalleta" ke wallahi se na kwada miki mari,wa kike
cewa jahili?" Tsaki tayi "kai mana" Taja sauran
suka yi tafiyarsu ...yayin da suka bar mal da
sanda suna ta balbalin masifa Ma'u duk taji
abinda ya faru,AISHATUL MUBEENA tana tsakar
gida abinta tana wasa, Ma'u kuma tana wanki a
tsakar gida, mamakin halin Mal kawai take...
Ya shigo yana balbalin masifa ko salama beyi ba,
ta kalle shi "Mal wannan yar muce fa, tana da
hakki akan mu,Ka tuna fa tunda muka haifi yar
nan bamu taba kaita asibiti ba,ko cuta tai se dai
inyi yan dubaru na,nice zuwa neman maganin
gargajiya,Amma kai ko da wasa baka taba nuna
damuwar ka ba,,,Sun biyo mu har gida don su
mata rigakafin wannan muguwar cutar, sannin
kan kane wannan cuta nakasar da yayan mutane
take,akan me bazamu basu damaba? Basu nemi
ko biyar daga gare mu ba fa,Mal nagaji da wanna
halin naka nagaji!!! " ta fashe da kuka... Ya galla
mata harar sannan yayi tsaki " Ma'u ki shiga
taitayin ki fa,Ya isheki abinda kike yi,rigakafin ne
nace baza'ayi ba!,Ai yata ce nina haife ta kuma
na isa da ita har dake!
Sh
[12:18AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS
[25]-[30]
Ma'u da sauri tadago kai ta kalleshi "au yarka?, se
yau kasan cewa yarkace,Kai yanzu baka ji kunyar
fada bama? Wallahi mal in baka canza halin ka ba
Allah se ya tambayeka,Allah wadaran wannan
mumunan halin naka!" Mal a fusace ya dago ya
wankawa mata mari ji kake Tas!! Aishatul
mubeena se data tsorata ta fara rusa kuka itama,
Mal ya kalli ma'u ya cigaba"Naga alama kin fara
raina ni a gidan nan,Wato yanzu har ina fada kina
fada zan fara maganinki ne mara kunya kawai
wadda batada tarbiya"" Ya sa kai ya fita daga
cikin gidan a fusace......Ma'u ta share hawayenta
tace "Allah ga baiwar ka,Allah ka raya wanna
yarinyar ya Allah"" ta dauki aishatul mubeena ta
fara rarrashinta tana hawaye ahaka har aishatul
mubeena tayi bacci
To rayuwa dai haka ta cigaba yau da dadi gobe
babu dadi,Ma'u kullum cikin hak'uri take da
mijinta da kuma uwar mijinta wanda suka zamo
mata matsala a rayuwarta
Yanzu dai shekarun AISHATUL MUBEENA 3 ta
taso yarinya kyakyawa san kowa k'in wanda ya
rasa,ga farin jini masha Allah,yara har fada ake
akan daukanta saboda kullum tsaf da ita,Har ta
fara magana sosai,abin mamaki kuwa itama
tsoron babanta ma take dan tun tana k'arama
tasaba tana zuwa wajenshi ze hantare ta hakan
yasa ko kusa da shi bata san zuwa..
Yau AISHATUL MUBEENA ta tashi da zazzabi me
zafin gaske ga ciwon kai se kuka takeyi,dagabaya
kuma tace kafarta na mata ciwo ta kasa tafiya
sam kafar ta rik'e ,,Ma'u ta rikice sosai ta rasa
yadda zatayu ga yarinya tana ta rusar kuka, Data
ga abin yayi yawa gashi tasan mal ko me zatai
mai baze kulata ba se ta saba ta a baya ta shiga
gidan khadija bayan sun gaisa ta mata
bayyani,Khadija itama duk ta rude,Can tace
"Inaga gwara mukai ta asibiti,Dan shine kadai
mafita" ma'u tace "Toh shikenan ba matsala"
khadija tasa aka hayo musu mota dan kai su
asibitin garin dayake akwai wanta yana aiki a
asibitin,,,Basu dade ba se ga mota ...nan nan da
nan taja sukai asibitin
Emergency aka shiga da ita aka shiga bata kulawa
ta gaugawa,,Ma'u se kuka takeayi dan ita ganni
take kamar mutuwa zatayi,,Khadija ce ke
rarrashinta
Bayan dan lokaci likita ya fito yana share
gumi,Ma'u tana kuka tace "likita ya take? Ya jikin
nata?" Likita ya ce a gskiya yanzu bamu gano
komai ba,amma dai yanzu zamuyi mata test na
aika lab,Se kujira kan result din ya fito" Ma'u tana
kuka tace "toh likita Allah yasa muga alheri,,"
Yace ameen ya fice,Ma'u kukan nata ya k'aru
sosaii; khadija itama se ta fara kuka dan suna
bata tausayi sosaii, Tace "kiyi hak'uri maman
mubeena komai yayi zafi maganinsa Allah,Inshaa
Allah zata tashi cuta ba mutuwa bace !" Ma'u ta
share hawayenta sannan tace "Toh khadija Allah
yasa amma se nake ganni kamar bazata tashi ba!"
Khadija tce"A'ah insha Allah zata tashi,Bari naje
can gida sena na sanar dasu iya su san abinda
ake ciki"
Tana isa kai tsaye gidan iya ta shiga bayan sun
gaisa ta sanar da iya,Abun mamaki iya se ta nuna
damuwarta ba laifi ta sakko hijabi tace suje
asibitin,sannan tabar sako da a nemo mal sule a
fada mai halin da'ake ciki A kuma fada mai ya
samesu a asibiti!
Har suko isa ma'u kuka take se rarrashinta suke
yi, a dan lokaci nan duk ta fita hayyacinta
idanunwanta duk sun k'ank'ance saboda kukan
datakeyi,
Suna zaune se ga likita ya fito a razane ya kallesu
yace............................
Share
AISHATUL MUBEENA 30-40
[12:19AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS
[30]-[35]
Likitan ya kallesu yace "ku biyoni office!" Ma'u ko
takalmi bata sa ba ta bishi da sauri suma su
khadija suka biyota
Bayan sun zaune likita yaja numfashi sannan yace
"ki nutsu ki fada min al'momin da ta fara kan
ciwon yayi tsanani, Ma'u ta share hawayenta
sannan tace "Ta fara da ciwon kai da dadewa
amma jefi jefi in na bata magani takanji
dadi,sannan takance kafarta na ciwo,to shine yau
tun safe abin yayi yawa tana ta kuka,Ga zazzabi
ga ciwon kafa" Likita ya share guminsa yana
jinjina kai
Likita ya maida numfashi sannan yace "Ana wa
yarinyar rigakafin Cutar poliomyelitis (polio)
kuwa?" (Gaban ma'u ya fadi)"A'ah ba'a taba yi
mata ba" Likitan a fusace yace ' u see,kun ganni
(ya daga murya) Duk k'ok'arin da gwamnati
takeyi akan yak'i da cutar polio tana turo mutane
su bi gida-gida dan yin rigakafin cutar,Kuna
ina????Meyasa baku basu damu su mata ba,Dan
nasan tabbas suna zuwa amma kuk'i basu
dama,,,meyasa???!!!"" Ma'u ta fashe da kuka
"Wlhy likita BA LAIFI NA BANE laifin babanta ne
ba yadda ban yi dashi ba amma sam yak'i,," likita
yace "Toh shikenan yanzu kun janyowa yarku,A
iya gwajjin da mukayi.....Am sorry to say,,
kwayar cutar polio ya riga ya gama bin
jikinta,kuma kafarta ya taba "A YANZU HAKA
YARKU TA RASA KAFARTA TA HAGU,ZEYI WUYA
TA SAKE TAKAWA DA KAFAR !!DOMIN KWAYAR
CUTA TA FI K'ARFI A KAFARTA!!!
Innalahi waina ilaihi raju'n Khadija ta shiga
maimaitawa iya kuwa kasa magana tayi,,Ma'u
kuwa sulalewa k'asa tayi sumamiya!! Da sauri
sukayo kanta nurses suka zo da gado aka dora ta
Likitoci sun dade akanta,,Anci sa'a kuwa mal yazo
shima yadan damu ba laifi ,Se wani kumbure-
kumbure yake Likita ya fito yace," ku biyoni
office",a gigice suka bishi ya kallesu cike da fushi
yace "wai ku dan Allah meyake damun kune,?
Matar nan tana da hawan jini amma baku taba
kawo ta asibiti an gwada taba,Yanzu jinin ta ya
hau over,,Allah ne yayi kiyaye da wlhy zata iya
samun mutuwar barin jiki stroke! Suka zaro ido
gaba daya banda mal,khadija tace "likita wallahi
bamu sani ba,bata taba fada mana ba "likita ya
nuna mal" kaine mijinta,, Ya galla masa harar
sannan yace "Eh nine ya akai yi ne?" Likita a
fusace yace "Amma wlhy baka da tausayi
sam,wacca irin zuciya ce dakai?? Ka yi sanadin
nakasa yarka sannnaan kana nema ka nakasa
matarka ko ka hallaka ta har lahira,Kai wani irin
mutum ne?
Mal ya kalleshi kallo na rainin hankali sannan yace
"Kaine bakada hankali,Ni nasan abinda
nakeyi,kuma ba ruwanka da harkar
gidana,mutumin banza kawai'' likita yayi
murmushi "Ni bazan tsaya cacar baki da kai ba
saboda ni bana cacar baki da jahilai irinku!
[12:19AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [1:33PM, 12/02/2016] Miss Hafcy:
◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS
[35]-[40]
Mal yana nema ya cakumi wuyan rigar likita da
sauri iya ta tare shi" Wlhy ka sake kayi fada dashi
sena maka baki mara hankali kawai' Ya kalleta
yayi tsaki sannan ya fice daga asibitin,likita
girgiza kai yayoi cike da takaici ya cigaba da yi
musu bayani
An sanar da yan gidansu ma'u mamanta da
goggo ne sukazo se kuka sukeyi da kyar aka
lallasheshu,,,Ma'u kuwa bata dan fara dawowa
daidai ba se datayi kwana2 a kwance Aishatul
mubeena kuwa tana can an ware mata gadon ta
daban likitoci ne kawai ke zuwa dubata
Ma'u ta dan murmure,Tana shan magugunata
sosai sannan likita ya mata nisiha sosai aka ta
kwantar da hankalin ta,Addu'a ce ya kamata ta
dinga yi,,Yawan damuwar datakeyi ne yasa ta
hawan jini!
Bayan ta dan warware hankalinta na kan
yarta,,Hakan yasa tace suce wajen likita ya musu
bayani,,bayan sun shiga,Ma'u cikin sanyi murya
tace "Likita yanzu ba wani magani Da za'ayi mata
ta sami sauk'i kafarta ta dawo daidai tunda naji
kace kafarta Ta riga ta shanye"
Likita ya nisa sannan yace "Malama ma'u kiyi
hak'uri,Hanya daya da za'a iya maganin cutar
shine....... RIGAKAFI! wanda ku kuma bakuyi wa
yarku ba! Amma cutar polio in har ta riga ta
kama mutum BATA DA MAGANI!!,Amma yanzu
muna bata painkillers wanda zasu maganin
wannan ciwon kai da zazzabi,da kuma ciwon
kafar,,Kuma Alhamdulilah yanzu ta fara samun
sauk'i,,,,Sannan batun kafarta na fada muku cewa
bazata iya tafiya ba due to weakness na
kafar,Yanzu zamu bata WHEEL CHAIR in ta k'ara
girma kuma se ta fara amfami da FOREARM
CRUTCH,lokacin kafarta ta dama ta k'ara
kwari,Dan kunsan itace me lafiyar kuma yarinya
ce,Kafar ba wani kwarin kirki tayi ba" Ma'u ta
fashe da kuka yayin da mamanta,iya,Goggo,Da
khadija suka Jin jina kai cike da tausauyi,,(Dan
yanzu iya ta saduda ta gane laifinta,Har kuka tayi
da tana bawa ma'u hakurin abinda tamata a
baya)
,Likita ya cigaba "Ba kuka zakiyi addu'a zaki ki
kuma godewa Allah dayasa nata yazo da
sauk'i,Dan akwai wanda take ja musu
paralys,Amma ita ai kafarta ta hagu kawai ta
taba kuma zata iya komai dinta nrml,Nan da sati1
zakiga ta dawo daidai se dai kawai kafarta ta
hagu da ta tabu ne!" Ma'u da murya kuka tace
"shikenan likita,Allah ya raya ta,ya kuma sa
k'arshen wahala kenan! Gaba ki daya sukace
ameen,,
Mama(maman ma'u tace) " Ma'u kiyi hak'uri ki
fawala Allah komai,Yana tare dake kinji kiyi
hak'uri duk da nasan kinayi ki dora akan wanda
kike yi"Ma'u ta rungume mama "toh mama insha
Allahu" khadija ta runtse idonta se hawaye
tausayinsu duk ya cika mata ciki...
BAYAN SATI 1
A yau aka salame su,Gwamnati ce dama ta dau
nauyin duk wata dawainiyar sh,,Da zasu tafi aka
basu wheel chair da kuma forearm crutch,kyauta
shima,se godiya suke yi,,AISHATUL MUBEENA
kuwa ta warware har dariyar ta takeyi,,Amma
rannar data koma normal se data kalli ma'u tace
"Umma,kinga kafata yadda ta dawo,A haka zatai
ta zama?" Ma'u ta fashe da kuka a hankali duk da
tana k'ok'arin kada ta gane ta dage tace "a'ah
aishatul mubeena zata warke yi hak'uri,," Tayi
murmushi tace "toh umma"
A rannar da suka koma yan'uwa da abokan arziki
suka dinga zuwa dubiya,kowa ya zo se yaji
tausayin aishatul mubeena,ita kuwa dayake da
yarinta haka take dariyarta tana harkar ta ba
ruwanta,ita a wayonta ta zata kafar tata zata
warke ne kamar yadda mamanta ta fada mata,,,
Mal ne ya shigo gidan yana masifa 'Bazan iya
bafa,baze yiwuba,Ayi ta zagina a gari anacewa
inada ya gurguwa! Ma'u a fusace tace "Mal ya
isheka fa,Waye ya ja mata? Ba kaine ba,Azzalumi
kawai,Me bak'ar zuciya! Ya juyo da mamaki "lallai
ma'u kin rik'a,Amma saurara kiji,Yau din nan
zanyi maganinki!" Ma'u wani murmushin tak'aici
tayi ta tana kallansa,,Ina sauraronka,,
Yayi wata dariyar mugunta sannan yace............
Comment as:
Publish Preview
No comments:
AISHATUL MUBEENA 45-60
[12:22AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [45]-[50] Likita ta
ganni tsaya a jikin mota yana murmushi,,kasa
magana tayi ta tsaya kawai tana kallansa cike da
mamaki,,Dayaga shirun yayi yawa se yace
'Malama ma'u ya kika tsaya anan k'araso mana"
jiki ba kwari ta karaso ya durk'usa ta gaishe shi
ya amasa tare da murmushi sannan yace "nasan
zakiyi mamakin ganina" Ta gyda kai alamar eh Ya
cigaba"Hak'ik'anin gaskiya tunda na ganki ke da
yarki nake tausayin ku,inason taimakon ku kuma
Cikin ikon Allah Se akamin transfer na koma
Asibitin aminu kano,Shine kwanaki na kawo ziyara
garin nan se nake tambayarku se ake cemin ai kun
rabu da mijiniki,,To gskia bazan boye miki ba tun
daga nan nake jin sonki a zuciyata daga baya
shine na yanke hukunci nazo na nemi amincewarki
dan Da aure nake sanki ba da wani abu ba! Ma'u
tayi murmushi "Toh likita zanyi shawara insha
Allahu nagode kwarai,Se dai kuma bansan sunan
ka ba", Likita yayi murmushi sannan yace "
Sunana DR MUHAMMAD AMEEN" Ma' u tace
"Toh Dr nagode,' yayi murmushi sannan yacr
"Inason zanyi magana da magabatanki in har kin
amince dan na dinga zuwa wajen ki" tace
"Bakomai Insha Allahu ba matsala" yace "Masha
Allahu amma nagode da wannan tarba me kyau
da kika min,, ma'u tace bakomai ai,,,Yace "ina
yartawa take? Ma'u tace tana ciki bari na fito
maka da ita" yace toh ya bude motarsa ya dauke
wata leda sannan ya kulle motar Ma'u bata dade
ba se gata da aishatul mubeena tana turota,Ita
kuwa tana murmushi tace "Ina wuni" yace lafiya
lau my daughter, Ya jikin naki? Tace da sauki,, Ya
mik'a mata ledar da kyar ta karba ma'u tai ta
godiya Sun dan yi hira Kadan yana bata shawara
akan yadda zata dinga kula da aishatul mubeena
dagabaya sukai salama Bayan ta koma gida tayi
wa mama bayanin komai mama ta ji dadi ta kuma
ce zata fada wa kawaunan ta da kuma yaya basiru
Abu kamar wasa zancen har ya mik'a yau Dr yazo
da magabatansa bayan sun Gaisa kawu na katsina
(Kawun su ma'u) yace,"Zamu iya sanin ka sosai"
dr yayi murmushi yace "Nidai sunana DR
MUHAMMAD AMEEN inada mata daya da yaya
guda hudu : Ameen(Abba) ,Abdulhafeez,Se
Husna da Aisha,,Ni baban likita ne yanzu a aminu
kano ina zaune a kano da iyalaina unguwar
lamido cresent,,Wayan nan kuma (ya nuna
kawunansa) daya k'anin babana ne dayan kuma
k'anin mamana ne wannan kenan Kawun katsina
yayi murmushi "Masha Allahu"Yanzu zamu kirawo
ita ma'u muji daga gareta kaga tunda bazawarace
in ka amince yau se a daura auren,Amma se munji
daga bakinta "dr ya gyda kai "toh bakomai" Yaya
basiru ne yaje ya kirawota kanta na k'asa ta
gaida su cikin girmamawa suka amsa ,,Kawun
katsina yayi mata bayanin komai sannan yace
"Yanzu yardar ki muke neman in kin amince se a
daura aure!" Gaban ma'u ya fadi ashe dai da
gaske ne ita bata zata abun ya kai ga haka ba har
ana cewa za'a daura auren yanzu,,Ta sunkuyar da
kanta tace..................
Like · 4 · Repl
Share
[12:22AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HASA WRITERS [50]-[55] Tace "To
shikenan Allah ya zaba mafi alheri"Dr wani dadi
yaji a ranshi,Tana gama fadan hakan ta fita daga
falon,,kawun katsina yace "To Masha allahu tunda
ta amince yanzu se muje masalaci tun dan naga
ana kiran sallar la'asar bayan an idar se a daura
auren,ince dai a shirye kuke(Ya kallesu)? Dr yace
eh mal muje" Cikin K'ank'anin lokaci aka daura
auren Muhammad ameen da Asma'u (ma'u) akan
sadaki dubu10,Ango yayi alkwarin wani satin ze
aiko da Kayan lefe se ta tare.. Tuni dama ya
sanar da matarsa Hajiya Hadiza,Dayake tana da
mutunci sosai kuma ba ruwanta addu'ar fatan
alheri tayi masa,Ta kuma ce inshaAllahu zasu
zauna lafiya,Indai ta bangarenta ne baza'a samu
matsala ba Yau ne tariyar ma'u,Bayan tayi yar
walima a gidansu,,Ita kadai aka kai gidan mijinta
banda Aishatul mubeena a cewar mama insunyi
sati 1 se akawota,Dan dr da kanshi yace ze dauke
ta ya dau nauyin komai dinta kamar yarsa ta
cikinsa Gida Masha Allah me kyau da shi bene ne
sama da k'asa,Hajiya hadiza tana sama yayinda
ma'u ke k'asa falo ne dan madaidaici da kuma
dakuna biyu se kitchen da bandaki da dan tsakar
gida ,,Dan yaya basiru da su kawun katsina sunyi
mata kayan daki ba laifi,,,Kowa se yi mata murna
akeyi mama ta mata nasiha sosai akan ta zauna
lafiya da uwargida ta kuwa dauka dan ita ba
ruwanta bata san hayaniya ma Dr ya tarasu yayi
musu nasiha baki daya kuma sun nuna mai sun
dauka suka mai alkwarin zasu zauna lafiya,, Bayan
sati Dr da kansa yaje ya dauko aishatul mubeena
da kayanta tana ta murna za'a kaita wajen
ummanta,Rannar da'aka kaita suka fara sabawa
da husna ;Sa'arta kuma akwai san mutane tafi
aisha san mutane sosaii nan da nan suka saba
kamar dama sun San juna,Husna tana shekara 4
ita kuma Aisha shekara 6 Suna zaune a falo dasu
husna YA ABDUL ya shigo fuska ba yabo ba
falasa, masha Allah kyakyawa ne sosai,Ga shi
akwai tsayi,duk da befi shekara 15,Ya gaida
Umma(ma'u)ta amsa da fara'arta tana mai sannu
da zuwa dan boardn skul yake yi yau ya
dawo,,Husna da Aisha da sauri suka taso zasu
mai oyoyo cak! Suka tsaya sakamakon muguwar
hararar da ya wurga musu,,"ku meyasa ba kuda
hankali ne ni zaku zo kuna wa oyoyo ?banzaye
kawae" ya fada cike da fushi daidai shigowa haj
hadiza(ummi haka suke cemata) tace "kadai abdul
Allah ya shirye ka ,kai da yan -uwanka Kana
hantararsu kaji kunya wlhy" Yace "To ummi akan
meye zasu zo suna min oyoyo se kace yaro
sa'ansu!" Umma datake dariya se a lokacin tayi
magana " Anty na ,ai da gskiyar sa ya girma fa"
ummi tayi dariya "halinsa ne kenan fa,ni rasa
gane irinsa,Haka yake,hira ma basa yi ,Suna mai
magana ya hantaresu wai shi baya san raini,dadai,
YA AMEEN,,kikace shine ba ruwanshi,yaranan
kamar k'awayensa haka ya daukesu,,suyita hira
suna raha abinsu abin sha'awa" umma tace "
shima ai yanason su,Da alama magana ce bata
dameshi ba ,(ta kalleshi)Rabu da ita Dana bari na
kawo maka abinci kaci,, Yayi murmushi "Toh
nagode" be sake magana ba ,umma ta tashi ta
nufi kitchen dan zubo masa abincin,,,yayin da ya
zauna a kujera yana jiranta,, se a lokacin ya lura
da Aishatul mubeena dake kan wheelchair tayi
tsuru-tsuru,dan har ta fara tsoronsa,, Ya kalli
ummi da mamaki "Ummi wannan waccece??
L
Share
[12:23AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [55]-[60] Ummi tayi
murmushi "k'anwarka ce,Yar antynka ce" yace
"Allah sarki,But yana ganta a wheelchair ciwo taji
ne? Ummi ta kada kai "A'ah polio victim ce! Ya
zaro ido ya maimaita "polio victim kuma??!,garin
yaya? Ya akai ta samu? Ummi tace "Kai kaga
bansan tambaya nima bansani ba, Allah ne ya
dora mata,ya isheka haka, yace toh ummi,, Kallo
daya ya mata ya kauda kai a fili yace "Sannu kinji
ya sunanki? A tsorace tace "Aisha..tul..mubeena"
ya gyda kai "nice name" Daidai lokacin umma ta
shigo da tray na abinci a hannunta ta dire mai a
gabanshi yayi godiya ya kai loma daya kenan
daga waje suka jiyo murya "Salamu alaikum
Ummina my lovely sisters kuna ina?? Hakan ya
tabbatr musu da cewa YA AMEEN ne,, Da gudu
aisha da husna suka tashi suka nufi wajen sa, ya
ware hannunsa suka taho da sauri suka rungume
shi Yayi murmushi "Nayi missing dinku Deariz"
suka amsa muma munyi missing dinka bros Ya
rik'e hannunsu suka k'araso wajen su ummi ,
ummi tayi murmushi ta kalli umma "kingani ko
dama na fada miki wuyata ya dawo,shi ba
ruwansu ba kamar wannan sakaran ba!" Umma
tayi murmushi ya k'araso wajen ummi ya
rungumeta, Da sauri ta kwace "kaga ni bansan
wannan shashashacin" yayi dariya " ummi nayi
missing dinki dayawa" tace "nima haka dana"
Yace "Finally dai mun gama secoundry skul Nan
da yan shekaru zan zama PILOT,, Ummi tace
"Insha Allahu munan muna ma addu'a yace "Dats
my ummi" Ya juyo ya kalli umma ya gaisheta da
girmamawa ta amsa,,Tare da yi masa sannu da
zuwa da kuma murna kamala sakandire,,Yayi ta
godiya,,Se a lokacin ya lura da Aishatul mubeena
Ya kalle ta yace "Fine girl bakida lafiya ne? Ya na
ganta a wheel chair? (Ya kalli su ummi)Umma tayi
murmushi ta sunkuyar da kanta,, Da mamaki se
sukaji tace "Ni polio victim ce!" A tare ummi da
ya abdul suka zaro ido,,Lallai yarinyar nan daga
fadan abu har ta gane ta haddace,, Haka Ya
abdul yace a zuciyarsa"Ya ameen yace 'Eyyah
Subhanalahi " ya kalli ummi " Ummi da gaske
take? Umma da sauri tace"Da gaske take Ameen,
kawai se ta fashe da kuka,, Ummi ta shiga
rarashinta shikuwa ya ameen be san sanda
hawaye suka fara zubo masa ba nan da nan
tausayinta ya cika mai zuciya,, yaji kuma wani
santa a zuciyarshi,,jinta yake tamkar k'anwarsa
uwa daya uba daya ! ya matso kusa da ita yayi
murnushi "Ya sunanki" ta wangale baki "Sunana
Aishatul mubeena! Yace wow nice name " zaki sha
sweet?" Tace ' eh" yace " toh zomuje na siya
miki, umma da sauri tace" aah ameen ka bari ka
huta mana, daga dawowarka? Yace bakomai
umma yanzu zamu dawo Ai nan kofar gida ne,,
Ya ja wheel chair din suka fita Jin haka husna da
aisha suka ce zasu je suma,ba musu yace su taho
yaja wheel chair din yana mata murmushi "Muje
na siya miki sweet koh? Tace "Ehh tana wangale
baki" suka fice Abdul kuwa tabe baki yayi, ya
cigaba da cin abincinsa ,Umma kuma dadi taji a
ranta sosai Basu dade ba se gasu sun dawo Kowa
da sweet a hannunshi se wangale baki
suke,,Aishatul mubeena ta kalli Ya ameen kainu
wajen umma,,Yace toh yaja wheel chair din wajen
umma ta wangale baki "Ummana kinga ya siyamin
sweet" Umma tace"nagani angode" Ya ameen
yace "Niwa? Ya sunana? Tace "Bansan sunan kaba
ni" umma tace "Auu baki san sunan shi ba?" Tace
"Eh ya sunanka" Yayi wani murmushi sannan
yace...
AISHATUL MUBEENA 60-80
[12:23AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [60]-[65] Sunana Ya
ameen amma kin san me zaki dinga cemin? Ta
gyada kai "A'ah" Yace toh ki dinga cemin "Bros"
ya abdul dayakr k'ok'arin tashi ya fashe da
dariya,"Wayaga bros! Su bros manya" ya tsuke
fuska kamar ba shi yayi maganar ba sannan ya
tashi ya fita,, Ya ameen yace "Ka dai ji dashi dan
rainin hankali" Aishatul mubeena kuwa maimaita
sunan ta shiga yi "Bro...s Yau ma kamar kullum
bayan sallar magariba suna zaune gabadayansu a
falon Abba suna hira ,,Ya ameen yace "Abba
nikuwa inada shawara" abba yace inaji "Abba me
ze hana aishatul mubeena ta dinga gwada tafiya
duk da dai tafiyar bazata zama daidai ba? In ba
haka wlhy tafiya da Forearm crutch din nan ze
mata wahala sosai" Abba ya numafasa sannan
yace "To ka dinga koyawa mata takawar
muga,Indan tana takawa shikenan ba matsala
idan kuma ta kasa kaga dole sai dai tayi amfani
da forearm crutch din" yace to insha Allah za
dinga gwada mata,, Umma tace "Angode fa Allah
saka da alheri" yace "Bakomai umma" Yau da
yama ya ameen Ya sauko da ita daga wheel chair
din yana koya mata tafiyar,Ba laifi ta na dan
k'ok'artawa yaji dadin Haka kullum addu'arshi
Allah ya taimake ta,Ta fara cangala kafar tata
dan a ganin shi hakan yafi da yawo da sanda"
YAU DA GOBE SAI ALLAH yanzu dai Aishatul
mubeena tana ss2,tana iya takawa amma saidai
tafiyarta ba irin ta masu lafiyar kafa bace cikin
ikon Allah tana iya cila kafarta tayi tafiya,,,, Ta
k'ara girma ta zama yan mata,,Tana da shekaru
16 Duk da ba lallai ka gane hakan ba saboda yar
k'arama ce kuma gata Ba k'iba saboda cutar
polio ta k'ara motse ta,,Amma duk da hakan
kyanta yana nan akwai kyau Masha Allah,,, Ya
abdul yana final year dinshi a university inda yake
karantar Engineering danshi dama burin sa kenan
ya zama engineer yayin da Ya ameen Ya zama
cikaken pilot har ya fara aiki ma Allah mai baiwa
duk da nakasa irinta Aishatul mubeena,,Amma
Kuma Allah ya bata kwakwala Tanada masifar
k'ok'ari mussaman ma a fanni Ilimin addini harda
na bokon ma,,,sannan kuma cikin ikon Allah,Allah
se ya bata fasahar yin ZANE yanzun zata kalli abu
ta zana shi tsaf kuma ya zanu sosai tayi fice A
makarantarsu a harkar zane sosai,,Kuma cikin
ikon Allah Ya ameen ne ya fara gano haka kuma
ya bata kwarin gwiwa sosai,,Duk wani abu datake
buk'ata a harkar zane da kudinshi yake siyowa ya
bata! AISHATUL MUBEENA ce t zaune akan Farar
kujera a compound din gidan,Kur'ani ne a
hannuta tana karantawa a hankali,,, YA ABDUL ya
shigo da motarsa ya faka ta a wajen fakin din
motoci,,Sanye yake da Bakin wando da riga sky
blue yayi bala'in kyau,,Ya k'ara girma ya kuma
k'ara kyau A hankali ya tako wajen datake karatun
yana sauraron k'ira'arta me masifar dadi,, Taji
kamar alamar mutum da sauri tajuyo suka hada
ido,,Bashiri ya kauda kai,,ya tsuke fuska yace "
Ke me kike yi anan? Murya na rawa tace "Daman
karatu nake yi," yace "Toh shi karatun ba'ayinshi
a ciki ne? A sanyaye tace "Saboda naga suna
kallo ne banason na dame su" yayi dan k'aramin
tsaki sannan ya bar wurin,,Ita kuwa ajiyar zuciya
tayi ta cigaba da karatunta Ba'a dade ba sai ga
Ya AMEEN nan ya taho daga dakinsa yana ta
mata murmushi(Dan bashida aiki week din) Tana
ganinshi tayi wani yalwatatacen murmushi ya
k'araso yana mata murmushi "SIS karatu ake ne?
Tayi murmushi "ina wuni bros" yace "Lafiya lau
sis karatu ake ne? Tace "Eh suratul khaf nake
karantawa kasan yau juma'a kuma sannan jibi
insha Allahu zamu yi musabak'a ! Ya wangale
yabaki "Masha Allah my l sister am very very
proud of you,,Allah ya bada sa'a insha Allahu ke
zaki ci,, Tace "ameen nagode bros" Yace "Ga
wani albishir din kuma;, tace inaji bros" yayi
murmushi " Yanzu uncle hashim(teachern su
aishatul mubeena) yace min aiy an zabe ki a gasar
zanen da za'ayi a Schools din dake kano wanda
kuma idan kinci shi ze bada damar ki wakilci kano
gabadaya a gasar da za'ayi da states din dake
nigeria.... Ta zaro ido da gaske bros? Yace
"kwarai kuwa! Tace anya zan iya kuwa? " yace see
you! Zaki iya mana insha Allahu se kin cinye
mudai kawai mu cigaba da addu"a,, Tace
"Nagode bros" Ya harareta "To meye na godiyar
kinsan dai banaso
Like · 3 ·
[12:24AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: by Hafsat
◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [65]-[70] Ta sa hannu
ta rufe bakinta toh shikenan na dena, yace
"Yauwa ko kefa" Bayan sallar isha,Aishatul
mubeena na zaune akan sallaya tana
muraji'a,Husna ta shigo da kur'ani a hannunta,Ta
zauna kusa da ita tace " Sis pls biya min nan,Ko
sau daya ne" Aishatul mubeena na k'ok'arin
dauka sai ga ummi nan ta shigo,Ta kalli husna"
Ke husna me yasa zaki dinga damunta kinsan dai
Musaba'ka garesu gobe ki barta tayi tilawa mana"
Husna tace "Kai ummi kawai fa cewa nayi ta biya
min shafi nan sau daya" Ummi tace "eh duk da
haka,Kije umma ta biya miki mana" Aishatul
mubeena tace 'Ummi dakin bari ma na k'ara
mata" ummi tace "Aah dai gwanda ta barki kiyi
karatunki" Husna na zumbure zumbure ta bar
wajen......... To Yaune dai zasu tafi musabak'ar
tun safe ta shirya tsaf cikin hijab har k'asa
uniform din makarantarsu Tayi kyau sosaii,,Ya
ameen ne da kanshi ze kaisu,, ita da su husna da
kuma k'aninta Amir( Yaron da Umma ta haifa a
gidan) dayake duk makarantarsu daya.... ,,(Da
harda su umma za'a amma zasuje Gaisuwa zaria
wani dan uwan abba ya rasu) A lokacin da suka
isa Mutane an taru sosaii,Makarntar dazasu yi
gasar da ita har daliban sun iso da kuma wanda
zasu kara da Aisha....Bayan an bude taro da
addu'a,Aka fara.... Cikin ikon Allah kuwa Aishatul
mubeena tayi kok'ari sosai,,Gyra da aka mata
basu da yawa,,bayan an kamala aka Aka kirawo
malam salisu(Babban malami ne shi) dan yazo
yayi jawabi sannan ya fadi sakamako,,,,,Sai da
malam ya fara jawabi ya kuma ja hankalin dalibai
da su dinga maida hankali wajen karatu sannan ya
fara karanto sakamakon kamar a haka: "A
musbak'ar Alkur'ani mai girma da muka gabatar
tsakanin makarantar,khalid ibn walid islamiya da
kuma Nana khadija Islamiya,, Makarantar nana
khadija islamiya wadda ta samu wakilcin Aliyu
sani tana da maki sha biyar (15) a cikin maki
talatin( 30)A mata kabara,,(Dalibai suka dauka
Allahu akbar) Sannan makarantar Khalid ibn walid
islamiya wadda ta samu wakilcin AISHATUL
MUBEENA MUHAMMAD AMEEN tana da maki.....
ashirin da biyar(25) a cikin maki talatin(30)! ku
musu kabara(Dalibai suka wage baki Allahu akbar)
Aishatul mubeena dake gefe wata ajiyar zuciya
tayi tare da Hamdala bata san sanda ta fara
hawayen murna ba,, Mal ya cigaba ' Wannan ne
ya tabbatar mana da cewa makarantar khalid ibn
walid itace ta cinye wannan gasar karatun
Alkur'ani me girma,, ku sake rangada musu
kabara(Dalibai aka dau kabara da karfi,nima
danake gefe wage baki nai nace Allahu akbar)
Dan haka an shirya kyautuka masu tsoka ga
wandanda suka yi Musabak'ar domin mu k'ara
k'arfafa musu gwiwa dama sauran dalibai,, Dan
Haka yanzu zan fara da Aliyu sani,, Alhaji Abdu
mai nerori ya bada kyautar Dubu Da kuma
Alk'urani me girma izu sittin ya kuma ce a bawa
wanda ya zo ta biyu a wannan gasar karatun
Alk'urani me girma,, Aliyu sani sai ka fito ka
amshi kyautar ka,, Ba dadewa aliyu sani yazo ya
karbi kyautarsa ana ta masa kabara Malam ya
cigaba sannan Zamu kira AISHATUL MUBEENA
MUHAMMAD AMEEN domin ta amshi
kyaututukanta,,Ba'a dade ba sai gata ta taho
tana cangala kafarta malam ya cigaba " Alhaji
Audu mai nerori ya bada kyautar Naira dubu dari
(100),Ga duk wanda yazo na daya Sannan
Shugaban kamfanin jirgin **** ya bada kyauta
kujerar umara shima ga wanda yazo na daya,Sai
kuma haj asabe ta bada kyautar atamfa guda uku
(3) itama ga wanda ya lashe gasar karatun
alkur'ani Dan Haka Malama Aisha se kizo ki karbi
kyautarki ta matso ta karba ana ta daukan
hotonta mussaman ma da'aka lura da nakasar
dake jikinta,, Ita kuwa se hawayen murna takeyi
hannu na rawa ta karba aka dinga kabara,, Malam
daga k'arshe yace,Dan haka sai muyi wa bayin
Allah nan addu'ar Allah ya saka musu da alheri ya
kuma k'ara budi.... Yayi addu'a sannan ya koma
ya zauna.... Tana dawowa daga wajen Karbar
kyautar kai tsaye wajen Ya ameen ta nufa ta
mik'a masa kyautar sannan ta koma ta zauna ta
kifa kai a gwiwa tana kuka,Ya ameen kuwa
rarashinta ya fara "Haba sis ki dena wannan
kukan mana Godewa Allah ya kamata kiyi ba kuka
ba! Ta dago idonta ta share hawayen sannan tace
" Toh bros insha Allahu na daina " yace "Toh
yimin murmushi mana" Batasan sanda murmushi
ya kubce mata ba,,Shima murmushi yayi yace
"Yauwa ko kefa" mutane se zuwa yimata Allah
sanya alheri suke mussaman ma dalibai da kuma
malaman makarantarsu kai hadda baki.... Bayan
an rufe taron Har zasu tafi gida tace a tsaya ta
zata je ta dawo,Suka ce toh......Kai tsaye wajen
shugaban makarantarsu ta nufa ta tsuguna har
k'asa ta gaishe shi ,Ya amsa da murmushi "Tashi
mana Aisha,Gaskiya kin burge mu sosaii muna
alfahari dake Allah ya saka miki da alheri ya k'ara
buda miki kwakwalki ,,kin k'ara fito da
makarnatar mu ba abinda zamu ce miki sai
godiya da fatan alheri"" Tayi murmushi "Malam
aiy nice da godiya,Nice ya kamata nayi muku
godiya ma,,Nagode nagode Allah ya saka muku
da mafificin alheri Ameen" Malam yace "Ameen
Aisha,Allah ya sa sauran dalibai suma suyi koyi
dake" Tace "Ameen" sannan ta bude jakarta ta
zaro envelop din nan da aka bata na Naira dubu
dari(100)....
Like · 2 · Reply · Ed
[12:25AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [70]-[75] Ta mik'awa
Malam Iro (Sunan shugaban makarantar tasu)
murya a sanyaye tace "Malam ga wannan kai da
sauran malamai ku kasa sauran abinda yayi
ragowa kuma a siyo butoci da tabarmu akai
massalacin makaranta " Malam ya zaro ido "Haba
a'eesha(Dayake haka yake ce mata) Ai kudinki ne
ba namu ba,Ki rik'e kudinki kinji Allah ya samu su
albarka mukam mun gode bama karbi kudinki ba
gaskiya" ta ja numfashi sannan tace "A'ah malam
dan Allah ka k'arba,Ba a maida hannun kyauta
baya!" Malam yayi murmushi " To sai da mu dauki
dubu ashirin(20) ta ishe mu" tace "A'ah malam
dan Allah ka karba duka" Yace "Toh shikenan
raba a biyu ki bamu rabi Allah ya sa albarka" ta
wangale baki " Yauwa malam gashi(Ta mik'a masa
kudin duka) ya ciri dubu hamsin (50) kamar yadda
Yace sannan ya mik'a mata yace "Gashi nan
a'eesha mun gode sosaii Allah ya saka miki da
alheri ba abinda zamu ce miki sai godiya" tayi
murmushi "Godiya nake malam Allah ya biyaku"
Sannan ta koma wajen motar tasu suka nufi gida
Suna isa gida a harabar gidan ummi da sauri tazo
ta rungume ta,Tana ta murna "yata kin burgeni
gaskiya,Am soo proud of you My daughter,Ina
alfahari dake Yata, aishatul mubeena tayi dariya
"Nagode ummina" Umma itama ta zo wajen cike
da murna Ta rungume yarta ta,Batasan sanda taji
hawaye na zuba ba duk iya kok'arin datayi na
ganni hawayen basu zuba ba amma sai da suka
zuba,,A firgice ta kalli umman tata "Umma kukan
me kike yi?" Da sauri ta share hawayen nata
"Kukan murna ne mubeena kukan murna
nakeyi,,Dama na dade ina jiran irin wannan
rannar Sai yau Allah ya nuna min,, ina ma
zanga........Da sauri ta canza zancen nata ,,muna
alfahari dake Allah ya k'ara buda miki
kwakwakarki,,Dake da sauran yan uwanki!" Su
Husna dake tsaye suka ce Ameen..... Ya abdul ya
fito daga dakinshi,Ya tsaya turus Yana kalonsu
"Meya faru ne? Ummi da sauri tace "Abin arzik'i
ne ya faru,,k'anwarka ce taci Gasar karatun
Alkur'ani me girma " Yace "Masha Allah wacce a
ciki?" Ummi tayi murmushi "yo waka sani banda
mubeena,Kasan wadanan sakarkarun(Ta nuna su
husna) Ba abinda suke tsinanawa" ya tabe baki
"Okay" ummi tace Sai kayi mata murna ai,Ya juyo
ya kalleta ya k'irk'iro murmushi yace "Congrats"
yana rufe bakinsa da sauri ya koma dakinsa,,Ya
ameen har a zuciyarsa beji dadi ba dan haka ya
yanke hukuncin yaje ya sameshi ya mai
magana,,Ya bishi dakinsu yayin dasu ummi suka
shiga ciki (Abinda yasa suka san itace ta lashe
gasar shine, Ya ameen ne ya kirasu ya sanar
dasu,,jim kadan bayan an gama fadan
sakamakon) Ya murda kofar ya shiga a zaune ya
ganshi yana kallon system dinshi dake kan
Bedside drower,,Ya shigo da salama sannan ya
zauna a kusa dashi, Yace "Ahki(My brother
dayake haka yake cemai) Gaskiya abinda kayi yau
baka kyauta ba"" Ba tare da ya kalleshi ba yace
"Me nayi" Ya ameen yayi murmushi,, "okay
bakasan me kayi bama? Ya kallesa "Yes
eh,Bansani ba" Ya ameen yace "To abinda kayi
yanzu a harabar Gida nasan nasan cewa umma
bataji dadi,Dan Allah ka dena yiwa yarinyar nan
haka kodan nakasar ta ai ka sota,,Kamar
k'anwarka fa take,,Dan Allah ki dinga janta a jiki
ka dena hantararta dan Allah na rok'e ka" Ya
abdul ya nisa sannan yace "To bakomai,Amma ni i
dont knw why(Bansan meyasa ba) kwatakwata
bata burgeni,Inaga jinin mu ne be hadu ba!!
Kuma dama kasan halina ai,,ni ban cika san
shigewa mutane ba and kar ka dauka wai ko dan
ba blood sister dinmu bace,No ko su husna ma
kasan ba wani sakar musu fuska nake ba Ya
ameen yace "To shikenan amma ya kamata ka
rage wannan halayar,Wani in ya fahimce ka wani
baze bayi ba,Dats why(shiyasa) mutane ke maka
Kallon me girman kai " ya abdul yace "Wannan ya
rage nasu ni ban damu cuz nasan ba halina bane"
lets keep this aside (mu aje wannan gefe) Wai ni
ina maganar FATY ne naga yanzu baka
maganarta,, Ya ameen ya bata fuska "kai ni daina
min maganarta mu b'ata" ya abdul ya kalleshi da
mamaki "Why meyasa" ya ameen ya nisa sannan
yace "Waifa daga taga pics dinmu da Mubeena
shikenan ta dau zafi, Wai budurwa tace,,inata
k'ok'arin na mata bayani amma tak'i yanzu bata
daga wayana ma" ya abdul yace "Tayiwa
kanta,Amma i bet you dakanta zata dawo tace ku
shirya" Ya ameen yace "oho mata" Ya kalli ya
abdul "Kai dama wayo kake min ko da wasa baka
min maganar budurwarka" ya abdul yayi
dariya"Wayaga me budurwa,, Hhh ni banda
budurwa ai" ya ameen yace "Ban yadda ba,Duk
yan mata dake binka kace bakada budurwa
wannan shayi ne kake mun" Ya abdul ya k'ara
dariya sannan yace ................ Kuyi hak'uri kunji
ni kwana2 biyu shiru
Like · 1 · Reply · E
[12:27AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [75]-[80] Yayi dariya
sannan yace "Kasan Allah? Ni har yanzu ban ga
wadda tayi min bane,Ni kaga ba kula mata ma
nake ba,In banda yan-uwa sai kuma classmates,"
ya ameen yace "Kuji shi kamar gaske" ya abdul
yace "Wallahi da gaske,," ya ameen yace " To
shikenan Allah ya zaba mana mafi alheri, nidai
kaga a shekarar insha Allahu zan yi aure na barka
(yayi masa gwalo)" Ya abdul yayi dariya,,wayar sa
ce tayi ruri da sauri ya dauka" Yace salamu
alaykum" dayan bangaren akace "wslm abdul ka
fito ina kofar gida" ya kashe wayar ya kalli ya
Ameen "Hafeez ne frnd dina bari naje ltr zamuyi
magana" Ya ameen yana k'ok'arin tashi yace
"okay nima bari na tafi". Kai tsaye falon umma ya
nufa inda ya tarada Nana(Aysha) Na chatn a
waya,Husna na kitchen,Aishatul mubeena Na
zaune Tana koyawa amir assignment,, Ya shigo
yana murmushi hade da kallan Mubeena' Hafizar
mu" tayi dariya "Kai bros" yace "Ko nayi k'arya?"
Da sauri Nana tace "a'ah bakayi k'arya ba ya
ameen, gaskiya ce" Yanzu kaga yan islamiyar mu
sai cemin suke nace suna taya ta murna da fatan
alheri, hadda masu sa pic dinta lokacin suna
musabaqar a display Picture(Dp)kaga(Ta mik'a
mai wayarta) ya karba "Masha Allah,Ai yau
kwanan farin ciki za'ayi a gidan nan" Nana tace
"Aikwa dai" Ya zauna akan kujera yana dana waya,
Nana ta kalleshi "yauwa na tuna,Ya ameen kasan
wata faty? " da mamaki yace "Yes nasanta" Nana
tace " A layin nan take?" Da sauri yace "A'ah a
unguwar nan dai suma suke,,me ya faru wai?"
Tace "Amma ni bansanta ba,Wani ta aiko da
sak'o dazu wai abaka,Am sorry mantawa nayi,,
da sauri yace "sak'on me? Fada min" tace "bari
na dauko maka" yace "yauwa" ala-ala yake ta
kawo masa yaga ko mene ne Bata dade ba kuwa
sai gata da yar k'aramar jaka a hannunta ta mik'a
masa, cike da zumud'i ya karba yana washe baki,
,Mubeena kuwa bata ce musu komai ba shiru tayi
kamar ma bata san abinda suke ba ,, Yana karba
ya fice abinshi ya nufi dakinshi. Kan gadonshi ya
baje da sauri ya dauko jakar yana bud'ewa wani
kati ya gani ya sha kwalliya cikin hanzari ya bude
ya fara karantawa kamar haka "" Remember the
good times we had spent together,And the
beautiful future we had dream of,,Darling i never
wanted to create a distance between us...please
let us bridges the gaps,,. Wani tsale murna yayi
ya rungume kati a fili yace "Bakomai my faty na
hak'ura!" Wayarsa ya dauko yayi dailing number
ta,akace a kashe take,,Yayi tagumi yana sake
kalan katin shi abin mamaki yake basa ma ashe
dai abdul da gaske yake da yace da kanta zata
dawo su shirya!,, Wayarsa yagani tana ruri da
sauri ya dauka,, Ashe faty ce cike da murna Yake
tambayarta ta canza number ne tace masa eh,,
bayan sun gaisa tace "Kayi hak'uri ya ameen
rashin fahimta ne ya kawo hakan, amma yanzu na
gane komai,ina neman yafiyarka" yayi murmushi
"Bakomai faty darling Allah ya barmu tare
sweetheart" tace ameen dear suka cigaba da
hirarsu ta soyayya. Aishatul mubeena bayan ta
gama yiwa Amir assignment din ya tafi wajen su
umma,,ta juyo ta kalli nana, "Ya nana wacce
FATY wai" Nana tayi murmushi "inaga fa
budurwasa ce !Dan dama rannar na labe naji suna
hirarta shi da ya abdul ""Mubeena bata san dalili
ba sai kawai taji gabanta ya fadi a sanyaye tace
"Amma nikuwa bai taba fada min ba" Nana ta
harareta da wasa "Ko ni dana girme ki be fada
min ba saike yarinya" mubeena tayi murmushi "To
yaya baba" nana tace "Kinsan mu akwai san
girma" Mubeena tayi dariya ...Ta tashi ta shiga
cikin daki ta zauna jikin gado tayi tagumi Tana
tunane-tunane kala-kala a zuciyarta.. Umma ce
ta shigo dakin,,kusa da ita ta zauna a hankali ta
dube ta tace "me yafaru naga kin yi shiru kina
tunani? Meke damunki?" Mubeena da sauri tace "
bakomai ummana kaina ne ke ciwo kawai" umma
tace "toh kuma ai se ki sha panadol,bari na
dauko miki magani kisha" Ta tashi ta dauko
mata,, ta k'arba da kyar ta sha maganin duk jinta
take wani iri,, Ta d'an yi jim,Can ta tuno wani
abu da sauri ta kalli umma tace "umma dan Allah
wata tambaya zan miki amma dan Allah umma
kimin alkwarin zaki bani cikakiyar amsar"" umma
ta danyi jim sannan tace "inajinki indai inada
amsar insha Allahu zan baki ita" Mubeena tayi
murmushi "yauwa ummana" sannan tace.. "Umma
DAN ALLAH WAYE MAHAIFINA? Gaban umma ya
fadi sosaii cikin dauriya tace "Wai ke mubeena
me ke damunki ne? Sau nawa kike tambayata
nace miki Abba ne babanki,Abba shine babanki
kar ki sake yi min wannan tambayar tunda kinsan
amsar"" mubeena ta runtse idonta se
hawaye,cikin murya kuka tace "Umma Abba
bashine mahaifina ba, Na dade da sanin haka,"
Ummi cikin muryar masifa tace "to sai ki fada
min waye Mahaifin naki,tunda ni baki yadda dani
ba Mubeena ta fashe da kuka "Umma ba haka
bane,Umma Dan Allah ki fada min,Kar kisa na
fara tunanin ko ni yar shege ce,,Ba ta hanyar
Aure aka haife ni ba!! Umma da sauri ta juyo
idanunta fal da hawaye tace "Auzubillahi" "ke ba
yar shege bace! Ke yar halak ce! Idan bakyason
bacin raina to ko da wasa kar na kuma jin
maganar nan,,tana gama fadan hakan ta fice
daga dakin tana share hawayenta!
Comment as:
Subscribe to: Post Comments (Atom)
Saturday, 15 October 2016
Posted by MissHafcy at 08:00
AISHATUL MUBEENA 85-105
[12:29AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ ©NA MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [80]-[85] Mubeena
kuwa kukan ta ta cigaba dayi daga baya barci
b'arawo ya sace ta. Da asuba ta tashi tayi
sallolinta da kuma nafila,,Tana zauna tana karatun
Alkur'ani har gari ya washe.. Bayan ta idar da
karatun ta tashi ta nufi dakin Umma,,zaune ta
tadda ita akan sallaya Tana addu'a,A bakin gado
ta zauna tana jiran Umman ta kamalla addu'oin
ta,, bayan Umma ta idar ta juyo ta kalli
mMubeena,da sauri Mubeena ta k'ara duk'awa
k'asa ta gaishe ta cikin sanyin murya "Umma ina
kwana,kin tashi lafiya?" Umma tayi murmushi
"Lafiya lau Mubeena" Mubeena tace "Umma dama
ina neman yafiyarki naga jiya kamar na b'ata miki
rai,insha Allahu baza ki sake jin maganar daga
bakina ba" Umma tace "Ban yi fushi ba
Mubeena,bakomai komai ya wuce" Mubeena ta
washe baki "yauwa Ummana nagode sosaii"
Umma tace "muje muyi karin kumalo(breakfast)"
Mubeena tace "Toh" Bayan sun gama cin
abincin,suna zaune ya Ameen ya shigo sanye da
kayansa na pilot ya rik'e hular a hannunsa sai
murmushi yake yi, Har k'asa ya duk'a ya gaida
umma ta amsa da fara'arta,Mubeena ma ta
gaishe shi ya amsa. Bayan sun gama gaisawa ya
kalli Mubeena"Sis ni kinga yau zan koma aiki" ta
canza fuska "Da gaske bro? ai nazata sai next
week" yayi dariya "Yauwa dan Allah inaso ki
maida hankali akan gasar zanen nan da za kuyi
kinsan Ran monday zaku fara,Ku goma(10 )Aka
zaba kuma a cikinku ne za'a zab'i ta d'aya( 1)
Please inaso ya zamana kece ta dayar nan! Zaki
iya, ga wannan(ya mik'a mata leda) duk wani
items da zaki buk'ata a harkar zane yana ciki
inaso ki fara practice tun yau,,Please ki dage "
tayi murmushi "Toh bros nagode sosaii insha
Allahu zan fara daga yau mu dage addu'a,insha
Allahu bazan baka kunya ba." Yayi murmushi
"Dats my sis,ki kuma sa a ranki zaki iya,indai kin
yadda da hakan to baza ki samu matsala ba insha
Allahu". Sai a lokacin umma tace "Gaskiyane Allah
ya bada sa'a" Dukansu suka ce "Amin."
Gabad'aynsu hadda Abba suka rako shi harabar
gida,Mubeena kuwa daurewa kawai tayi dan ji
take kamar tayi kuka idanunta sun yi rau-rau
alamar me shirin yin kuka, shikuwa sai k'ara
jadada mata yake akan ta dage sosai, itakuwa
tana cemasa "insha Allahu zata dage sosai" su
Abba suka mai fatan alheri suka kuma mai
addu'ar Allah ya kiyaye hanya,sannan suka shige
ciki,suka barshi daga shi sai Mubeena datake jikin
motar tayi jim ta kasa magana ,daga baya ta
kalleshi tace "Yanzu bros sai yaushe? " yace
"Gaskiya for now bansani ba" tace "Okay Allah ya
taimaka ya tsare ka Ameen,A dawo lafiya" yace
"Amin sis nagode" har ta tafi sai ta dawo da
sauri ta kalleshi "Ka gaida FATY in kunyi waya"
bata ko jira amsar shi ba ta shige ciki, shikuwa
mamaki yayi ,ko taya tasan faty budurwasa ce ?
oho. Mota taja suka tafi.. Yau monday da sassafe
suka shirya itada Amir suka tafi skul,Dayake dama
can Husna da ya Nana sun fita aji a makaranta,su
sunyi candy last year kuma Abba yace sam be
yadda su fara unibasiti ba sai sunyi aure,Da kyar
da taimakon su umma ma ya barsu suka fara
zuwa Computer school. Tana zaune a kan bencin
ta ita da k'awarta Asiya suna hira,dayake lokacin
break ne,inda Mubeena ke bata labarin gasar
zanen da za'ayi,, Uncle hashim ya shigo nan take
ajin yayi tsit,suka tashi suka gaishe shi ya amsa
sannan yace duk wanda ya kira sunansu su same
su a Principals office, Ya fara kiran sunan kamar
haka: "Nafisa Jameel, Auwal Isah, AISHATUL
MUBEENA MUHAMMAD AMEEN,, Sai ku
biyoni,"Yana gama fadan haka ya fita,yayin da
yan ajin kowa ya shiga fadan albarkacin
bakinsa,daga masu cewa laifi sukayi sai masu
cewa suspension za'a basu, duk dai, Ita kuwa
Mubeena sam bata damu ba dan tasan dalilin
kiran,Suka jera ita da Nafisa sai yatsine take ita
tana tak'ama an zo har aji an kira suna hada suna
ta. A office suka tadda malamai da sauran
Dalibai guda bakwai(7) suna jiransu,bayan sun
gaida sauran malaman uncle hashim ya fara
magana cikin harshen turanci kamar haka: "Mun
tara kune anan ba dan komai ba dan wata
gagarumar gasa da gwamnatin taraya ta shirya
akan ZANE-ZANE,wato ART, ana neman kuma
mutum d'aya mace ko namiji wanda ze wakilci
kano baki daya,dan haka mukayi registar wannan
makaranta, da farko dai a cikinku ku goma nan
damuka zab'a, gobe zamu fara gasar mu a iya
makarantar mu kuma duk wanda ya cinye shine ze
wakilci makarantar mu a gasar da za'a yi da
sauran makarantu guda biyar(5) da gwamnati ta
tantance, idan Allah yasa wakilin makarantar mu
ya samu ya lashe gasar to shine ze wakilci kano
baki d'aya a gasar da za'ayi da sauran state
(jihohi) dake k'asar nan tamu Nigeria,,da fatan
kun gane?. Gaba ki d'aya suka ce "mun gane".
Principal ya kuma musu wani k'arin bayani tare
da yi musu fatan alheri daga baya aka salame su
kowa ya koma ajinsu Nafisa sai wani iyayi take a
zuciyarta kuwa cewa take aiy tasan ita zata lashe
gasar. Suna shiga aji yan class suka fara
tambayarsu abinda ya faru Nafisa ta k'arfi ta
fada musu ,aikuwa suka d'au ihu "Se kinyi
wallahi!!,se kin cinye nafisa!, ita kuwa sai busa
hanci take yi, cikin murya isa ta fara magana"
hmm ai ni dama sun ban mamaki,ai da basu b'ata
lokacinsu ba wajen cewa sai anyi gasa sun zab'i
gwani,suna b'ata lokacinsu ne amma kowa yasan
nice zan cinye,ko ya kuka ce friends?" Suka kuma
ihu "hakane Artist nafeesa, sai kinje abuja kin
karbo mana award dinan!
Share
[12:30AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:53AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [95]-[100] Uncle
Hashim murmushi yayi yace "To kunyi gueesin
right" Nafisa kuwa iya kulawa ta kulu batasan
sanda taji hawaye ba,dataga abin ya fara isarta
sai ta fara zage-zage "wallahi bazan yadda ba!
Wannan ma aiy sankai ne, aikin banza
kawai,kuma...bata k'arasa maganar ba taji saukar
mari a fuskarta ji kake tas! Kallo ya dawo kan
Nafisa dake rik'e da kuncinta tana hawaye, sai a
lokacin suka gane ashe anty sa'adah (english
teacher dinsu) ce ta wanka mata mari,,wasu suka
hau yi mta dariya yayin dana kusa da ita sukai tsit
dan suna tsoranta. Anty sa'a taci gaba "ke waye
sa'anki a cikinmu saboda tsabar rashin kunya mu
sa'aninki ne?" Uncle Hashim ya k'araso wajen
"bari ni da ita zanyi maganinta" ya kalli Nafisa
dake ta sheshekar kuka yace "shige muje" ba shiri
ta bishi Zuwa staff room...Dama lokacin tashi
yayi dan haka aka sallami dalibai. Mubeena ce
zaune ita da Asiya a bus stop din skul din,
Mubeena da Amir na jiran drivernsu yayin da
Asiya ke jiran skul bus din unguwarsu Asiya ta
kalli Mubeena "gaskiya Mubeena kin burgeni, ni
dama nasan ke zaki cinye,dama nice ke!"
Mubeena tayi dariya "hmm Asiya kenan kema fa
kinada taki baiwar fa" Asiya tace "tame fa?"
Mubeena ta cigaba" na rubuta labarai mana
novels ni kome zaki min bazan iya rubuta
k'agaggen labari ba wallahi,ke kuwa fa kina iya
k'irkira ki rubatasu kala-kala" Asiya tayi dariya
"kema dai Mubeena nan abinda ni kadai nake
rawa ta nake kida na, in na rubuta da sisters dina
kawai nake bawa su karanta sai kuma ke"
Mubeena tayu murmushi "duk da haka' Asiya tace
"kodayake inmunyi candy inason na fara
publishing din wanda wasu danake rubutawa
wasu kuma na fara typing dinsu a whatsapp ko
facebook wato online writeups" Mubeena tayi
murmushi," lallai ashe kema kin kusa zama su'
Benaxir,Lubbatu,Chuchu,Ybk,Jabo,Faty
axland,etc danaji su Ya Nana na fadan su suna
rubuta online hausa novels ,,kinsan su Ya Nana
sun dage da karatun hausa novels,kullum zaki
gansu mak'ale da waya suna karatun littafi" Asiya
tayi dariya "lah ashe kema haka,wallahi nima
sisters dina haka kullum cikin karatu a whatsapp
har group garesu kala-kala na hausa novels"
Mubeena tace "aiy suna k'ok'ari". Drivern su yazo
suka wuce gida. Suna shiga gida Amir da gudu
yayi falo yana kiransu umma,suka firfito a tsorace
dan a zantonsu wani abun ne ya faru marar
dadi...Yayi wani tsalle ya kalli umma "Yaya
Mubeena ce tazo ta d'aya(ya nuna yatsan sa guda
d'aya) Ummi ta wangale baki "Ai daman nasan a
rina! ina 'yar tawa take? Mubeena ta k'araso tana
murmushi "gani Ummina!" Ummi ta rungumeta
tana murna "Allah ya sanya Alheri" Mubeena ta
amsa, Ameen ummina! Amma kinsan meye?
Ummi ta girgiza kai" next week zamu kuma yin
wata gasar da Nafisa Jameel wanna wadda nake
baku labarinta" Ummi tace "ai insha Allahu zaki
samu nasar 'yata zamu dage da addu'a" Umma
tace "kar kisa tsoro a ranki insha Allahu sai kin
cinye gasar nan" Mubeena tace "Ameen my
mother's" Umma ta cigaba "bari na kira Ameen
na sanar dashi wannan abun arzik'in" ta shiga
d'aki dan dauko wayarta. Murna wajen ya Ameen
ba'a magana sun dad'e suna waya yana bata
kwarin gwiwa akan ta dage zatayi nasara insha
Allahu ta kuma dage da addu'ar daga k'arshe
sukai sallama ta mik'awa Umma wayarta.
Mubeena ce zaune akan carpet din falon Umma
abinci ne a gabanta amma ta kasa ci tayi tagumi
da alama akwai abunda take tunani, Umma ta
k'araso wajen ta tace "Mubeena me ke damunki?
Kinsa abinci a gaba tun dazu kink'i ci? Mubeena
ta d'ago idonta sharkaf da hawaye tace "Umma
wallahi wani labari aka ban yau in na tuno duk sai
naji ba dadi" Umma ta kara matsowa kusa da ita
"na mene?" Mubeena ta share hawayen nata
sannan taba umma labarin da Asiya ta bata na
yarinyar nan me cutar polio data ja mata
paralysed,, Umma itama sai ta fashe da kuka ta
tuno irin gwagwamayar data sha itama lokacin da
Mubeena na k'arama,, Mubeena ta katse mata
tunanin da cewa "Umma wannan dubu hamsin
d'in dana samu a wajen musabak'ar nan nakeso
kiban muje dake muyi mata siyayya kayan abinci
da kayan sawa da kuma daiper size dinta,Atamfar
nan kuma abani guda biyu na kaiwa mamanta
d'aya sannan kuma aba Safi tella ta dinkawa
yarnyar, mu kai gidansu" Umma tayi murmushi
"Kaji d'iya ta kwarai Mubeena ke daban ce!
Kinada zuciya me kyau Mubeena a kullum godewa
Allah nake daya bani 'ya kamar ki, Mubeena Allah
ya shi miki albarka ya kuma albarkaci rayuwarki,"
Mubeena ta ce "Amin Ummana nima ina alfahari
dake, Allah ya saka miki da alheri ya biya miki
duk bukatan ki duniya da lahira" Umma tace
"Amin nagode AISHATUL MUBEENA" amma sai ki
bari Abbanku ya dawo sai a sanar dashi koh?
Mubeena tace "gaskiya kam Allah ya dawo dashi
lafiya"
[11:55AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [90]-[95] Mubeena
tayi shiru can sai hawaye suka fara zirarowa,Asiya
a rude ta fara share mata hawayen "yi hak'uri
Aisha wallahi ba dan na saki kuka nayi wannan
tambayar ba kawai dai..." Mubeena ta katse ta
"bake kika sani kuka ba Asiya... bari na fad'a
miki" Asiya tace "toh inaji" Mubeena ta
cigaba"cutar poliomyelitis (polio) ce ta maida ni
haka! Asiya ta zaro ido "polio??,da kina k'arama
ba'a miki rigakafi ba? Mubeena ta share
hawayenta "eh,nidai kawai watarana na wayi gari
naga kafana ta dawo haka,ba zan iya tuna abinda
suka faru da ba,kuma banasan na tambayi Umma
tunda naga itama basan zancen take ba" Asiya
cikin sanyin murya tace "Allah sarki,Allah ya
kiyaye gaba,ya kuma sauwak'e. Mubeena tace
"Amin". Asiya ta girgiza kai cike da takaici tace
"akwai wata yarinya a unguwar su cousins d'inmu
itama polio ne, itafa ya ja mata paralysed,ga
iyayenta talakawa ne,ko wheel chair ba tada, a
k'asa zakiga sun shanya ta,tayi fitsari etc duk
anan sai dai su gyra,yarinyar 12years amma ta
k'ank'ance sai ki rantse bata fi 4-5years ba abun
tausayi,rannar danaje gidan dubu d'aya(1000) ne
a hannuna wallahi duka na basu naji tausayinsu
ita da iyayenta,har takai ta kawo daga karshe
maman bara takeyi saboda sukansu wani sa'in
abincin da zasu ci gagararsu yakeyi,sun ban
tausayi sosaii" ta k'arasa maganar tana kuka...
Mubeena itama sai ta fashe da kukan, zancen ya
matuk'ar bata tausayi,, ta dage tace "Allah
sarki,shi yasa nake godewa Allah kullum dakuma
iyayena,amma zaki gane gidan? Asiya tace "eh
zangane kusa da gidan su cousins d'inmu ne"
Mubeena tace "insha Allahu gobe zan zo ki
rakani" Asiya tace "to bakomai Allah ubangiji ya
kaimu" Mubeena tace "Amin." Akazo aka
kirasu,Nafisa sai wani iyayi akeyi,bayan an musu
bayanin komai aka raraba musu kayan da zasuyi
zanen akace kowa ya zana abu mai kyau amma
banda abu me rai,an basu minti talatin(30mint)
nan da nan suka fara. Mubeena kuwa exactly
abunda ta zana jiya (har ya Abdul yace yayi kyau
daga k'arshe yace yanso tace ya dauka),ta zana
,tunda taji yace yayi kyau to tasan kuwa tabbas
yayi din da gaske,, dan haka ta k'ara zana irinshi
har yafi na jiya ma kyau... Lokaci ya cika,uncle
Hashim ne ya k'arbi zanen aka bawa masana
zanen da hukumar makarantar ta gayyato takanas
don su duba su kuma fad'i sakamakon tun daga
zanen daya zo na d'aya har zuwa na
k'arshe....Bayan sun dade suna duba suka fadawa
hukumar makarantar result din sannan suka tafi..
Uncle Hashim ne yazo yace musu su koma aji za'a
had'a assambili na mussaman wanda anan ne za'a
fad'i sakamakon. Nafisa tana shiga aji yan aji suka
hau tafi suna mata kirari ita kuma sai busa hanci
takeyi can tace "Sai ku shirya anjima za'ayi
assambili anan ne zaku tabbatar dacewa nice na
lashe gasar" Asiya ta tab'e baki "ba giringirin ba
dai tai mai!" Nafisa tsaki tayi ta juya ta mata
wani kallon raini sannan tace "ni bansan shishigi a
rayuwata ita gurguwar da kike shigewa ai itama a
bayana take wallahi,dukanku nan sai da ku zama
'yan amshin shata dan nice gaba da ku akomai"
Mubeena murmushin takaici tayi ta sunkuyar da
kanta. Asiya a fusace ta tashi "keee!! Ba'a aibata
halitar Allah,ke in banda jahila/jahili ma wa yake
yabon kansa? ,kuma da kike cewa gurguwa ai
Allah ne ya haliceta haka,, a haka yaso ya
ganta,kuma kema baki fi k'arfin Allah ya maida
ke haka ba,wai ke da me kike tak'ama ne? eh?
Nafisa a fusace tace "kut! Ke har kin isa ki zage
ni,"tayi wani kukan kura zata wankawa Asiya
mari,da sauri Asiya ta rik'e hannunta cak! Tace
"karki kuskura ki taba min fuska,niba karya bace
irinki bana dambe,"tana gama fadan haka ta
zauna tabar Nafisa nata kumfar baki,,daidai nan
teachern su ya shigo ,yana shigowa a fusace ya
kalli Nafisa "get out!!" Simi simi tabar ajin tana
gunguni. Malami suka dinga shiga aji-aji suna
cewa dalibai sufito za'ayi asambili na musaman
ba'a dad'e dalibai suka cika wajen assembly din
Nafisa kuwa sai wani tak'ama takeyi. Uncle
Hashim dayake shine me kula da harkar gasar ya
fito ya fara jawabi kamar haka "Gud afternoon
students,,abinda yasa muka tara ku nan ba dan
komai ba dam mu fad'a muku sakamakon gasar
zanen iya makarantarmu da muka gabatar yau,, a
cikin mutane goma da suka yi participating a
gasar mutum biyu zamu dauka wa'enda su kuma
zasu yi tasu gasar next week,a cikinsu kuma mu
dau wadda tazo ta d'aya dan ta wakilci
makarantarmu,, wanda yazo ta goma(10) shine:
Auwal Isah na tara(9 ) Jamila Muhd na 8 Iro
Faisal................,,.wadda tazo ta biyu....Nafisa
Jameel sai kuma zakaran wato wanda/wadda ta
lashe gasar ......(ya k'ara daga muryarsa)
AISHATUL....kan kace meye dalibai suka d'au ihu
suka k'arsawa masa "Mubeena Muhd Ameen.
[12:32AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:53AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [100]-[105] Umma
tace "Amin, wannan satin insha Allahu inason
muje k'auye wajen mama bata ji dadi ba ashe sai
jiya yaya Basiru yake fad'amin a waya" Mubeena
tace "eyyah Allah sarki Mamana Allah ya bata
lafiya" Umma tace "Amin" . Abba ya dawo suka
fad'a masa niyyarsu ta ziyarta iyayen yarinyar
Abba yaji dadi kwarai ya k'ara musu dubu ashirin
(20) akai,, ya dau waya ya kira Ya Abdul "Abdul
Hafeez kana ina ne?" Ya Abdul yace "ina dakina"
Abba yace "toh ka shirya yanzu zaka kai su
Ummanku unguwa kasan driver yayi bulaguro"
Yace "toh gashi nan". Ba dad'e ba kuwa sai gashi
bayan ya gaishesu gaba d'aya,Mubeena ma ta
gaishe shi ya amsa ba yabo ba falasa...Su Ya
Nana ma sukace zasu bisu aikuwa suka shirya
abinsu, Mubeena kuwa hijab dinta ta d'auko ash
colour har k'asa tasa abinta hoda kawai ta shafa
sai farin man leb'e ..ta fito suka shiga mota, se
da suka fara zuwa wani babban mall suka siyo su
kayan abincine,kayan makulashe, kayan sawa,
daiper etc sun kashe kud'i dayawa ... dama
already Mubeena ta taho da wheel chair dinta da
take amfani da ita kan ta fara tafiya don ta bawa
yarinyar. Sai da suka fara zuwa gida su Asiya
suka dauko ta dan ta rakasu gidan,basu dad'e ba
kuwa sai gasu a gidan, k'aramin gida ne na k'asa
wasu wuraren na gidan ma duk ya rushe kana
ganin gida kasan na talakawa ne futuk.. Da
sallama suka shiga gidan a lokacin, wata
matashiyar mata ta amsa musu da fara'a,yayin
data aje tsintsiyar datake shara da ita,,
"Sannunku da zuwa" ta fad'a tana fara'a, Umma,
Mubeena, Ya Nana, Husna da kuma Asiya, Ya
Abdul da Amir suna cikin mota su basu fito ba.
Matar ta shimfid'a musu tabarma suka zauzauna,
ta tashi ta nufi randar ruwa ta d'ebo musu ruwa
a kwanon sha ta aje a gabansu, Sannan ta zauna
suka gaigaisa, matar tace "sai dai kuma ban gane
kuba, waccan kawai na gane(ta nuna Asiya) ko
yan gidansu ne?" Umma tayi murmushi sannan ta
fad'a mata dalilin zuwansu, matar sai hawaye
kawai tace "Nagode kwarai Allah ya biyaku dama
in Allah ya kawo makashinka sai ya kawo me
ceton ka" Umma tace "gskiya ne, ina yarinyar"
Matar tace " YUSRA tana cikin d'aki ku shigo"
suka shiga dakin. A kwance suka tadda ita sai
kallonsu takeyi ta kalli Mamanta "Mama suwaye?"
Maman tayi murnushi "bak'i ne suka zo duba ki"
A tare su Mubeena suka had'a baki "ya jikinki?"
Tace "da sauk'i" Mubeena ta kura mata ido sai
hawaye sharr ta sunkuyar da kanta tana kuka a
hankali... ita kuwa Umma godewa Allah tayi da
banda taimakon Allah ba da tuni itama suna cikin
wannan halin... Umma ta dage ta ce "Ina
mahaifinta?" Maman tayi murmushi takaici "Aiy
bama tare yanzu nan gidan iyayen mune da suka
mutu suka bar mana nida k'anina anan muke
zaune, tunda muka rabu da mahaifinta be kuma
waiwayar mu ba" ta fashe da kuka,, Umma ta
runtse ido sai hawaye, a zuciyarta tace "ashe
akwai masu hali irin nan Mal Sule a duniya? Allah
wadaran wannan mumuman hali tur dashi! Itama
da tuni fa tana cikin wannan hali kai dole ta
godewa Allah daya musan yamata da mafi alheri"
Umma ta share hawayenta tace " nima kinga 'yata
nan itama polio ne amma ita kafarta ce kawai"
Maman tace "Allah sarki ita yazo mata da sauk'i
ma". Nan da nan wasu maza suka fara shigowa da
kayayyakin da su Mubeena suka siyo,, Maman
tsayawa tayi tana kallon ikon Allah ta kasa
magana ma saboda tsabar murna,, Umma ce ta
katse dacewa "gashi wannan kyautace daga
AISHATUL MUBEENA ga wannan daiper sai ku
dinga saka mata kinga kin huta da wanki kashi da
fitsari sai dai kawai ki cire a tsaftace, ga kayan
makulashe nan ana bata, ga Wheel chair nan
shima a dinga dora ta ana zagayawa da ita itama
ta zaga gari,, duk dai gasu duk naku ne
malakinku ne ga wannan(ta mik'a mata dubu
ashirin(20) da Abba ya bada) sak'o ne daga
Abbansu kwayi wani abun dasu, Allah ya k'ara
sauk'i" . Maman ta fashe da kukan murna "duk
mukadai? Allahu akbar ashe akwai mutane irinku
AISHATUL MUBEENA mun gode kwarai Allah ya
biyaki ya daukaki bansan dame zan gode muku
ba, bansan da wata kalma zanyi amfani na gode
muku da ita ba, Allah ya biyaku, ya kare ku ya
biya muku buk'atunku duniya da lahira, Mubeena
da za'a sami mutane irinku da yan uwanku masu
wannan masifafiyar cuta ta polio basu wahala
ba,da basuyi bara akan titi ba, da kuma wasun su
basu rasa ransu ba saboda wannan cuta,," ta
k'ara fashewa da kuka. Mubeena ta k'araso
wajenta ta rungume ta tana kuka "Maman ki dena
kuka,a kullum raina yakan baci inda naga yan
uwana masu irin wannan cuta suna wahala ,
inason in taimakawa yan uwa masu irin wannan
cutar mussaman ma wa'enda basu da bud'i
irinku,, kar ki gode min ki gode dan Allah"
Maman tace "Allah sarki Allah me baiwa" Yusra
dake kwance tace "mun gode Anty Mubeena".
*** ina gayyatar ku zuwa sabon group din dana
bude yau a facebook, masu yin facebook sai kuyi
searching "MISS HAFCY NOVELS" Nagode
Like · 2 ·
[11:53AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [95]-[100] Uncle
Hashim murmushi yayi yace "To kunyi gueesin
right" Nafisa kuwa iya kulawa ta kulu batasan
sanda taji hawaye ba,dataga abin ya fara isarta
sai ta fara zage-zage "wallahi bazan yadda ba!
Wannan ma aiy sankai ne, aikin banza
kawai,kuma...bata k'arasa maganar ba taji saukar
mari a fuskarta ji kake tas! Kallo ya dawo kan
Nafisa dake rik'e da kuncinta tana hawaye, sai a
lokacin suka gane ashe anty sa'adah (english
teacher dinsu) ce ta wanka mata mari,,wasu suka
hau yi mta dariya yayin dana kusa da ita sukai tsit
dan suna tsoranta. Anty sa'a taci gaba "ke waye
sa'anki a cikinmu saboda tsabar rashin kunya mu
sa'aninki ne?" Uncle Hashim ya k'araso wajen
"bari ni da ita zanyi maganinta" ya kalli Nafisa
dake ta sheshekar kuka yace "shige muje" ba shiri
ta bishi Zuwa staff room...Dama lokacin tashi
yayi dan haka aka sallami dalibai. Mubeena ce
zaune ita da Asiya a bus stop din skul din,
Mubeena da Amir na jiran drivernsu yayin da
Asiya ke jiran skul bus din unguwarsu Asiya ta
kalli Mubeena "gaskiya Mubeena kin burgeni, ni
dama nasan ke zaki cinye,dama nice ke!"
Mubeena tayi dariya "hmm Asiya kenan kema fa
kinada taki baiwar fa" Asiya tace "tame fa?"
Mubeena ta cigaba" na rubuta labarai mana
novels ni kome zaki min bazan iya rubuta
k'agaggen labari ba wallahi,ke kuwa fa kina iya
k'irkira ki rubatasu kala-kala" Asiya tayi dariya
"kema dai Mubeena nan abinda ni kadai nake
rawa ta nake kida na, in na rubuta da sisters dina
kawai nake bawa su karanta sai kuma ke"
Mubeena tayu murmushi "duk da haka' Asiya tace
"kodayake inmunyi candy inason na fara
publishing din wanda wasu danake rubutawa
wasu kuma na fara typing dinsu a whatsapp ko
facebook wato online writeups" Mubeena tayi
murmushi," lallai ashe kema kin kusa zama su'
Benaxir,Lubbatu,Chuchu,Ybk,Jabo,Faty
axland,etc danaji su Ya Nana na fadan su suna
rubuta online hausa novels ,,kinsan su Ya Nana
sun dage da karatun hausa novels,kullum zaki
gansu mak'ale da waya suna karatun littafi" Asiya
tayi dariya "lah ashe kema haka,wallahi nima
sisters dina haka kullum cikin karatu a whatsapp
har group garesu kala-kala na hausa novels"
Mubeena tace "aiy suna k'ok'ari". Drivern su yazo
suka wuce gida. Suna shiga gida Amir da gudu
yayi falo yana kiransu umma,suka firfito a tsorace
dan a zantonsu wani abun ne ya faru marar
dadi...Yayi wani tsalle ya kalli umma "Yaya
Mubeena ce tazo ta d'aya(ya nuna yatsan sa guda
d'aya) Ummi ta wangale baki "Ai daman nasan a
rina! ina 'yar tawa take? Mubeena ta k'araso tana
murmushi "gani Ummina!" Ummi ta rungumeta
tana murna "Allah ya sanya Alheri" Mubeena ta
amsa, Ameen ummina! Amma kinsan meye?
Ummi ta girgiza kai" next week zamu kuma yin
wata gasar da Nafisa Jameel wanna wadda nake
baku labarinta" Ummi tace "ai insha Allahu zaki
samu nasar 'yata zamu dage da addu'a" Umma
tace "kar kisa tsoro a ranki insha Allahu sai kin
cinye gasar nan" Mubeena tace "Ameen my
mother's" Umma ta cigaba "bari na kira Ameen
na sanar dashi wannan abun arzik'in" ta shiga
d'aki dan dauko wayarta. Murna wajen ya Ameen
ba'a magana sun dad'e suna waya yana bata
kwarin gwiwa akan ta dage zatayi nasara insha
Allahu ta kuma dage da addu'ar daga k'arshe
sukai sallama ta mik'awa Umma wayarta.
Mubeena ce zaune akan carpet din falon Umma
abinci ne a gabanta amma ta kasa ci tayi tagumi
da alama akwai abunda take tunani, Umma ta
k'araso wajen ta tace "Mubeena me ke damunki?
Kinsa abinci a gaba tun dazu kink'i ci? Mubeena
ta d'ago idonta sharkaf da hawaye tace "Umma
wallahi wani labari aka ban yau in na tuno duk sai
naji ba dadi" Umma ta kara matsowa kusa da ita
"na mene?" Mubeena ta share hawayen nata
sannan taba umma labarin da Asiya ta bata na
yarinyar nan me cutar polio data ja mata
paralysed,, Umma itama sai ta fashe da kuka ta
tuno irin gwagwamayar data sha itama lokacin da
Mubeena na k'arama,, Mubeena ta katse mata
tunanin da cewa "Umma wannan dubu hamsin
d'in dana samu a wajen musabak'ar nan nakeso
kiban muje dake muyi mata siyayya kayan abinci
da kayan sawa da kuma daiper size dinta,Atamfar
nan kuma abani guda biyu na kaiwa mamanta
d'aya sannan kuma aba Safi tella ta dinkawa
yarnyar, mu kai gidansu" Umma tayi murmushi
"Kaji d'iya ta kwarai Mubeena ke daban ce!
Kinada zuciya me kyau Mubeena a kullum godewa
Allah nake daya bani 'ya kamar ki, Mubeena Allah
ya shi miki albarka ya kuma albarkaci rayuwarki,"
Mubeena ta ce "Amin Ummana nima ina alfahari
dake, Allah ya saka miki da alheri ya biya miki
duk bukatan ki duniya da lahira" Umma tace
"Amin nagode AISHATUL MUBEENA" amma sai ki
bari Abbanku ya dawo sai a sanar dashi koh?
Mubeena tace "gaskiya kam Allah ya dawo dashi
lafiya"
Comment as:
Publish Preview
No comments:
Post a Comment
MissHafcy
View my complete profile
About Me
► 2017 (16)
▼ 2016 (34)
► November (1)
▼ October (33)
WELCOME
ASMAUL HUSNA 6
ASMA'UL~HUSNA
ASMAUL~HUSNA 4
ASMAUL~HUSNA 3
ASMAUL HUSNA 2
ASMAUL HUSNA
AISHATUL MUBEENA 155-160
AISHATUL MUBEENA 145-155
AISHATUL MUBEENA 110-140
AISHATUL MUBEENA 85-105
AISHATUL MUBEENA 60-80
AISHATUL MUBEENA 45-60
AISHATUL MUBEENA 30-40
AISHATUL MUBEENA 20-30
AISHATUL MUBEENA 1-20
WANI HANIN END!
WANI HANIN 26-27
WANI HANIN 24-25
WANI HANIN 22-23
WANI HANIN 20-21
WANI HANIN 19-20
WANI HANIN 15,16,17&18
WANIN HANIN 12,13,&14
WANI HANIN 11
WANI HANIN 9&10
WANI HANIN 7&8
WANI HANIN 5&6
WANI HANIN 3&4
WANI HANIN 2
WANI HANIN 1
....
WANI HANIN
Blog Archive
Miss_Hafcy. Watermark theme. Powered by Blogger .
More
AISHATUL MUBEENA 110-140
[12:33AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:51AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS A tak'aice dai ansa
rannar Ya Ameen da Faty, da kuma Aisha( Ya
Nana) da Saifulah nan da wata biyu(2) ,, Su
Umma kuwa sai shirye shiryen biki sukeyi.. Ya
Abdul kuwa har ya gama karatunshi Abba ya
samar masa aiki har ya fara yi dan haka ma ba
kullum yake zama a gida ba. Baiwar Allah
Mubeena kuwa tacan duk ta damu dan ta dad'e
da gane cewa tana son ya Abdul ! amma sai take
ganin abun da kamar wuya, na farko dai Umma
tace mata Abba ne babanta to indai har kuwa
Abba ne babanta to ba aure a tsakaninsu saboda
wanta ne uba d'aya kuma ba aure a tsakaninsu
k'anwa da wa.!.na biyu kuwa, tasan halin ya
Abdul shida ko magana bata shiga tsakaninsu sai
ta k'ure,, in ba kwanan nan dayake d'an sakar
mata fuska,,kuma tasan ma baze rasa budurwa
wadda yake so ba,,,,yadda yake d'in nan
tubarkalah gashi kuma d'an gayu,, doleh 'yan
mata suyi rububinsa... dan haka sai ta dinga
addu'ar Allah ya cire mata sanshi a zuciyarta,, a
kullum kuma tana k'ok'arin cire sanshi daga
zuciyarta,, dan a iya tunaninta ko da da aure a
tsakanin su, in ba wani ikon Allan ba,to ko a
mafarki baza ta tab'a zama matarsa ba,, Ita dai
kullum addu'arta shine Allah ya bata miji na gari
ya kuma zab'a mata mafi alheri Yau saura befi
kwana biyar (5) suyi gasar ba,kuma dama sun
gama exams an basu hutu, dan haka lokacin hutu
za'ayi gasar.. Mubeena na zaune a falo tana kallan
musab'akar alkur'ani da akasa a sunnah Tv,,
Umma ta fito daga d'aki cikin shirin fita unguwa,
Mubeena ta d'ago ta kalleta "Umma fita zaki yi
ne?" Umma tace "eh k'auye zani wajen Mama"
Mubeena da sauri ta tashi "Umma dan Allah nazo
muje? Na dad'e banga Mama ba" Umma tace to
maza shirya muje,kafin rigimaman nan yazo(Amir)
dama neman dalilin k'in zuwa islamiya yake yi"
Mubeena tayi dariya sannan ta shiga dakinsu ta
dauko hijab dinta ta bi bayan umma ,, suka yiwa
su Ummi sallama sannan suka nufi k'auye. Bayan
sun isa Mama tayi murna sosaii da ganin su,
bayan sun gaisa sun sha ruwa , Mubeena nakan
cinyar Mama suna wasan su na jika da kaka,
Mama ta kalli Umma," Ma'u kinsan IYA ta samu
mutuwar b'arin jiki kuwa? Gaban Umma ya fad'i ,
"subhanalahi,wacca iyan??" ta fad'a had'e da
dafe k'irji, Mama tace " Iya dai surikarki, wallahi
abun tausayi kuje ki duba ta dan Allah kullum
fad'i take a kirawo mata ke da yarki ta nemi
gafarar ku . Umma tace "Allah sarki Iya, a ina
take zaune? Mama tace "inda dai kika santa tana
nan' Mubeena dake kwance akan cinyar Mama da
sauri ta taso ta tsutsura musu ido ,, ta kalli
Mama tace"Mama wacce ce Iya?" Mama na
k'ok'arin magana Umma ta dakawa Mubeena
tsawa "bansani ba,dake muke magana,ban hanaki
sa min baki in ina magana ba?" Mubeena ta
sunkuyar da kanta , yayin da Mama tace "ke Ma'u
wai meyasa kike haka ne? Daga tambaya saiki
hayayak'o mata?" Umma tace "Mama haushi
taban ai manya na magana ta dinga sako baki,
bari na tashi naje na dubo ta"" ta tashi ta dauki
jakarta tana k'ok'arin saka takalminta, Mama ta
kalleta," Ma'u indai nina haifeki to ki tafi da
Mubeena" Umma ta juyo jiki ba kwari tace "to se
ki taso muje" bata jira amsar Mubeena ba ta sakai
ta fita, Mubeena da sauri tasa hijab dinta tabi
bayanta. Har suka iso gidan Umma bata yiwa
Mubeena magana ba, da sallama suka shiga gidan
amma suka ji shiru,, sai da sukayi sallama yakai
guda hudu(4) sannan suka jiyo wata dashashiyar
murya nacewa "Wa..alai..kum..us..salam...,k
u..shigo..mana,, Umma ta kad'a kai sannan ta
shiga dakin data juyo murya, Mubeena tabi
bayanta. Umma ta zaro ido saboda abinda ta
gani ya masifar tsorata ta, duniya kenan! ... IYA
ce kwance akan wata yagalaliyar tabarma duk tayi
fitsari akai, dakin in banda zarni ba abinda yake
yi. Umma a firgice ta k'arasa wajen Mubeena ta
bi bayanta, Iya ta k'are musu kallo sannan tace
"Wannan kamar Ma'u nake gani kodai mafarki
nakeyi? Umma ta runtse idonta sai hawaye 'Nice
Iya!" Iya ta fashe da kuka "kece Ma'u ! ashe rai
kanga rai? Ina jikar tawa take?" Umma ta nuna
Mubeena "gata nan, tare muke ma" Iya ta k'ara
fashewa da kuka "zo nan 'yar jikalle ta, ni bansan
ma da wani ido zan kalle ki ba, randa aka haife ki
nida mahai....." Umma ta da sauri ta katse ta "Iya
komai ya wuce dan Allah a bar zancen nan baki
yimin komai ba ni kuma koda kin min ma na yafe
miki, garin yaya kika sami wannan ciwon?". Iya
tana kuka tace "rannar ina zaune ni kad'ai a daki
naji mage a gefena, kinsan dama ina tsoron mage
,to tun daga nan na tsorata sosai bakina ya juye
magana ma na kasa yi, hannuna ma na kasa
d'agawa balle na d'aga kafata,, Haka na kwana
ina kuka bame ceto na,, washe gari makota da
suka ji shiru suka zo suka bud'e kofar aka fito
dani aka kaini asibiti anan akace mutuwar b'arin
jiki nasamu,,shine nake kwance anan masa'udu
(dan k'anwar iya) shine kawai yake kula dani,,, ta
sake fashewa da kuka,, Umma ta fashe da kuka
hakama Mubeena dama ga Mubeena da tausayi.
Iya ce ta katse musu kukan da cewa "Ma'u baki
fad'a wa jikartawa ni kakar ta bace ba? Dan daga
ganin alama bata san nice na....Umma ta katse ta
" Iya dan Allah ya isa haka, zancen nan ya wuce
banse tasan komai ba ai" Mubeena duk ta rikice
ta kasa gane maganar tasu, sun caja mata
kwakwalwa....Iya cikin dashashiyar murya tace
"Ma'u RANNAR WANKA BA'A BOYEN CIBI!
Like · 2 · Reply · Edit · 3 February
Khadija Muhamed
[11:52AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [105]-[110] Mubeena
ta shafa fuskarta" bakomai yusra Allah ya baki
lafiya" yusra ta rik'e hannunta "Amin",, sukai
musu sallama suka juya suka bar Maman nata
kukan murna k'aninta mu'az yazo shima murna
kamar me, ya dinga shiwa su Mubeena
albarka,,dama kudin reg din makaranta yake
nema ya cika dubu biyar(5000)amma ta gagara
sai gashi Allah ya share musu kukunsu. A mota ne
Umma ke ba ya Abdul labarin yarinya jaji
tausayinta sosaii shima ya kuma ji dad'i da'aka
musu wannnan taimakon..Suka aje Asiya a gida
suka mata godiya sannan suka koma gida. Kwanci
tashi ,gobe ne Mubeena da Nafisa zasuyi gasar
su, Mubeena tayi practice sosai, a rannar raba
dare tayi tana addu"ar Allah ya bata sa'a su
Umma ma haka duk 'yan gidan ma, Ya Abdul ma
yazo yayi mata fatan alheri,dan yanzu ba laifi
yana sakar mata fuska. Da sassafe ta tashi ta yi
sallolinta sannan tayi zikirorinta ta shirya suka
huce makaranta...bayan an fito break 'yan class
sun zagaye Nafisa dake wa mickey mouse din
data zana musu fenti wai zasu sa a wall bangon
class din ,bayan ta gama ta d'aga zanen "ya kuka
gani friends?" Suka hada baki "Woww..yayi kyau
sosaii amma da Mubeena ce ta zana munsan se
yafi haka kyau" Nafisa ta juyo a fusace "lallai ma,
in sha wahala in muku abu amma kuce da wata
banza ce tayi sai yafi kyau?" D'aya daga cikinsu
tace "a'ah kinga kar ki sake ce mata banza "
Nafisa tace "an fad'a mata d'in, bari ku gani" nan
da nana ta warce zanen ta yayaga shi, sannan ta
fita daga ajin tana zage-zage,sukuwa dariya
sukayi sukace "kanki kika cuta ai,wahalaliya kawai.
Mubeena ce da Nafisa zaune suna jiran akawo
musu abubuwan zanen, Uncle Hashim ya shigo ya
raraba musu sannan yace mutum d'aya ta biyo
shi saboda za'a raba musu aji gudun kar wani ya
kwafi na wani, caraf Nafisa tace zata bishi ,hakan
kuwa akaiyi yabar Mubeena da anty Sa'a sannan
shi kuma suka tafi wani staff room d'in shi da
Nafisa. Cikin minti talatin suka kamala zanen
kowa yayi submitn,, suka koma aji ... aka bawa
wanda suka duba zanen kwanaki dan su duba
wannan d'in shima. Suna zaune a aji suna class
work din maths Uncle Hashim yazo ya kira
Mubeena anan ya tabbatar mata da cewa itace ta
lashe gasar!! Wohoho murna wajen Mubeena
kamar me ta rasa ma me zatai dan murna.
Assamibili aka k'ara hadawa anan aka kirawo
Mubeena gaban assambili aka sanar da sauran
dalibai itace ta cinye gasar kuma ita zata wakilci
makarantarsu a gasar da za'ayi nan da sati biyu2
dalibai aka d'au ihu ana Up Up Up Mubeena!!
Mubeena kuwa sai murmushi take tana godewa
Allah daya bata nasara... Nafisa dajin haka ihu ta
saki ,tana wani fizge fizge daga k'arshe ta tada
aljanun k'arya malamin islamic studies yasa
prefect mata suka d'auke ta zuwa staff room dan
yayi mata ruk'iya nan kuwa be san na k'arya ne
ba. Mubeena kuwa se murna ake mata malamai
kuwa sai wani nan-nan suke da ita kodayake
dama can malamai suna santa saboda
kwazonta...Nafisa kuwa da Ustaz(malamin
islamic) ya gane cewa na k'arya ne,dorina ya
dauko zabgegiya ya shiga lafta mata, bashiri ta
tashi tana kuka sharaf sharaf tana bashi
hak'uri,dariya yayi sanan yace ta koma aji, aka
dinga mata ihu ana cewa me aljanun k'arya a
rannar tayi alkwarin baza ta sake dawowa
makarantar ba, dan abin kunya data aikita baza
su barta ta zauna a makarnatar lafiya ba. Yau Ya
Ameen ya ze dawo murna a wajen 'yan gidan
kamar me,kowa ka gani yana cikin walwala hatta
Ya Abdul... Mubeena kuwa cewa tayi a bar mata
zata mai girki me dadi, dayake yanason abincin
gargajiya fankaso da tuwo ta yi masa da miyar
taushe dan ya fad'a mata a waya ya dad'e be
cisu ba,, su ya Nana kuma suka yi masa kunun
aya da zob'o. Bayan yayi parking din motar shi
ya shigo gida Amir da gudu yazo ya rungume shi
yana masa oyoyo , su Mubeena suka fifito suna
masa sannu da zuwa shikuwa yana amsawa fuska
d'auke da murmushi..ya k'araso cikin gida Umma
da Ummi kuma na falo suna jiranshi suka yi masa
sannu da zuwa sa kuma ya hanya. Ya amsa da
"lafiya lau nagode,,kuma nayi missing dinku
sooooooo much" a tare suka ce "muma munyi
missing dinka". Bayan yayi wanka yayi sallah ya
dawo ya zauna Mubeena tace abincinsa na kan
dinning table( teburin cin abinci) yaje ya zauna
yana budewa ya fara "wow nasan wannan aikin
kine Mubeena", Ummi tace 'ai kuwa kamar
kasani,kayan shan ne su Nana sukayi yimaka" yayi
murmushi "amma kuwa nagode lovely sisters"
Bayan ya gama cin abincin su Ummi ke sanar
dashi Mubeena ce zata wakilci skul dinsu ba
k'aramin murna yayi ba,a rannar ta faranta masa
rai. Washe gari ya sami Umma yake fad'a mata
cewa iyayen Faty sun takura masa daya turo dan
nan da wata hudu (4) za'ayi bikin yarta kuma
sunaso a had'a da na Faty...shikuma yana kunyar
fad'awa Ummi da Abba,, Umma tayi murna dajin
haka, ta kuma yimasa alkwarin zata fad'awa
Abban sannan kuma indai ya shirya to ba
matsala. yayi mata godiya ya tafi. Umma ta sami
Abba ta fada masa yaji dadin haka dama yana
shirin yi masa maganar auren dan a ganinsa
lokaci yayi daya kamata ya zama cikaken mutum
wato yayi aure...yace ta fad'awa ya Ameen d'in
ya kwantar da hankalinsa zasuje shida yan-
uwansa su nema masa auren insha Allahu..
[12:34AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:48AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [125]-[130] Wakilin
shugabanin da suka shirya gasa wanda yazo daga
birnin taraya Abuja wato MR MIKE da shugaban
k'ungiyar masu zanen dake kano ALHAJI AL-
AMIN BAWA sune suka fito dan fad'an result din
bayan manyan-manyan kwararru a harkar zane
sun duba sun fitar da sakamako, Alhaji Bawa shi
zai dinga kiran suna yayinda Mr Mike ze dinga
d'aga zanen dan kowa ya gani. Bayan sun yi d'an
jawabansu, Alhaji Bawa ya fara magana kamar
haka:" zamu fara da na sha biyar (15)" nan ya
fara kiran sunaye yayin da Mr mike ke d'aga
zanen, sai kuma wanda aka kira ya fito bainar
jama'a. Sai mutane su tafa masa/mata . A haka
dai yana fad'a har yazo ta biyu. Wanda ya kira
dalibi Ahmad Huzaifa, aka d'aga zanen shi nan
mutane suka fara ihu sosaii dan zanen nashi yayi
bala'in kyau. Bayan nan yace yanzu za'a d'aga
zanen wanda/wadda ta yazo ta d'aya, mutane
kowa ya baza ido yana jiran ganin wani zane ne
wanda ya zarce had'ad'un zanen da'aka nuna, da
kuma wani tauraron ne ko kuma wata tauraruwar
ce ta samu nasarar lashe gasar? Mr Mike wani
had'ad'en ko nace gaba da had'ad'e zanen ya
d'aga sama, zane ne wanda aka yishi akan al'adar
bahaushe wato , da farko dai , bukka aka zana
yar k'arama me bala'in kyau a gefen ta kuma
tabarmar kaba ce wanda aka zana akushi da
kwanon sha da kuma kwaryar akai, ga butar
alwala a gefe, a d'ayan bangaren kuma atamfa ce
aka zana da kuma dan kwali irin na da, sannan ga
murajani da dai sauran kayan hausawa na mata.
Zanen yayi bala'in kyau mutum in ya kalla sai ya
rantse hoto ne aka d'auka a camera saboda
tsabar tsaruwar da yayi. Nan da nan wajen ya
gauraye da ihu kowa sai washe baki yake yi daga
masu cewa "wow!" Sai masu cewa 'masha Allah"
duk dai, Kowa burinsa be huce yaga wanda/
wadda yayi zanen ba. Yan jarida kuwa da sauran
mutane sai d'auka hoton zanen suke. Mubeena
kuwa suna hira da su Husna taga an d'aga zanen
ta wani farin ciki taji wanda bata tab'a jinsa a
rayuwarta ba,, ta runtse idonta sai hawayen
murna, ta kuma k'i fadawa su Ya Abdul cewa
zanen tane, sukuwa suna gefe sai fama zuzuta
zanen suke,amma kowa a zuciyarshi, ji yake
kamar zanen Mubeena ne. Alhaji Bawa ne ya
dakatar da mutane daga hayaniyae da suke
dakuma ihu, yayi gyran murya yace , "yanzu zan
kira wanda yayi wannan zane, ina me farin ciki
kirin AISHATUL MUBEENA Muhammad Ameen!".
Murna a wajen su Husna kamar me ,sai kallon
Mubeena suke suna k'ara kallonta, fuskarsu
d'auke da farin ciki, Mubeena kasa tashi tayi da
kyar suka lalab'eta ta tashi jiki ba kwari ta nufi
inda aka kirata. Mutane dake ta jiran fitowar ta,
sai hango ta sukai tana cangala kafarta dan
zuwan wajen, mamaki duk ya cika su, amma
wannan ta ciri tuta ashe dama da nakasasu masu
irin talent irinta? Ihun mutane ya k'aru gaba
d'aya suka tashi suna kallonta yayin da 'yan jarida
suka cika wajen suna d'aukar ta hoto, da kuma
hoto mai motsi(video). Isarta keda wuya , Mr
Mike abinka da arne cak ya d'agata sama! Duk
k'ok'arin datake dan ta kwace amma ya rik'e ta
gam, cikin d'aga murya da hausar sa da wadda
bata fita sosai yace " wannan itace ta lashe
gasar, itace tazo ta d'aya!"
Like · 2 · Reply · Edit · 6 February
[11:50AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [115]-[120] Umma
tace "hakane Iya amma..." Iya ta katse ta
"dakata" ta janyo hannun Mubeena ta rik'e gam
sannan tace "Aihatul mubeena nice kakar ki, nice
na haifi mahaifinki SULAIMAN, nida mahaifinki
mun kasance masu wata irin zuciya,masu butulci
kuma wa'enda basu da godiyar Allah,, nan da nan
ta fada mata komai tun daga auren Umma da
Mal Sule har rannar da suka rabu" Mubeena ta
fashe da kuka,kuka take sosaii haka ma Umma.
Mubeena tana kuka tace "Umma dama na fad'a
miki, na fad'a miki cewa Abba ba shine mahaifina
ba!" Umma cikin tsawa tace " shine mahaifinki !
Abba shine mahaifinki! , shine yaso ki a lokacin
da Mal sule ya k'i ki har yake ik'irarin cewa ke ba
'yarsa bace, shine ya ciyyar dake, ya tufatar
dake, ya baki ilimi, daidai da rana d'aya bai tab'a
nuna bambanci a tsakaninku ke da 'yan'yansa ba,,
sabanin Mal Sule da ya firta da bakinsa kar na
sake ko da wasa nace ke d'iyarsa ce , wanda
shine sillar gurguncewa k'afarki, wanda besan cin
kiba, besan shan kiba, besan wahala kiba, besan
komai naki ba! Abu d'aya ne ya miki a rayuwa,
shine sillar zuwan ki duniya , amma bayan haka
ba abinda ya tsinana miki a rayuwa, wallahi kome
Mal sule ze miki yanzu in aka d'auke Silan zuwanki
duniya dayayi baze ko kusa yi miki abinda Dr
Muhammad ya miki ba,, Mal Sule ya amsa sunan
sa na cewa shine ubanki wanda ya haife ki kawai,
amma ko kusa baze amsa sunan , wanda yayi
wahala dake tun kina yar gwililuwa har yanzu,
wanda ya ci dake, ya sha dake,ya tufatar dake,ya
baki ilimi ya kuma baki tarbiya, Shine ya cika
sharud'an zama uba wanda uban naki wanda ya
haife ki ya kasa cikawa!(Ta sassauta murya ta)
amma Mubeena kar abinda nida Iya muka fad'a
miki ya sa ki tsani mahaifinki, ko kusa kar ki fara
domin in badan shiba baza kizo duniya ba!....ta
k'arasa maganar cikin sheshek'ar kuka. Kukan
Mubeena ya k'aru sosai, tama kasa magana, sai
sheshek'ar kukan data keyi,,, Umma ta kalli Iya
dake ta faman sharbar kuka tace "Iya kiyi hak'uri
ban fad"i maganar ba dan ta b'ata miki rai,
gaskiya ce kawai na fad'a, Iya tace" baki b'ata
min rai ba Ma'u, gaskiya ke kike fad'i, nayi dana
sanin abinda na aikata a baya"" Ma'u tace "Iya
bakiyi mana komai ba Iya wannan maganar ta
huce saboda ni tun d'ad'ewa da kika nemi
gafarata na yafe miki, dama ko baki nemi na yafe
miki zan yafe miki dan wallahi ni tamkar Uwa na
d'auke ki!" Ga wannnan ta aje mata bandir din
yan dubu d'aya(1) sannan tace "gobe insha Allah
zan aiko miki da sauran abinda kike buk'ata,
kuma insha Allahu za mu dinga ziyartar ki akai-
akai. Iya ta rik'e hannunta " Ma'u tsaya na fad'a
miki wani abu,, yau tsawon shekaru goma(10)
kenan ban sa Sule a idona ba, tunda yazo yace
min ya tafi birni cirani na nuna ban amince ba
amma sam ya k' jin maganata ya tafi ya barni, be
kuma waiwayata ba, ko yana da rai? Ko ya rasu?
Allahu a'alam,, amma dan Allah in Allah ya had'a
ku dan Allah ma'u ku yafe masa ke da Aiha
(Aisha), ki kuma ce nima na yafe masa, dan ina ji
ajikina kwanan ya kusa k'are da k'yar na k'ara
kwana a duniya ,nima ku yafe min Allah ya had'a
fuskokin mu a aljana..." ta fashe da kuka,,,,jikin
Umma da Mubeena yayi sanyi sosaii Mubeena tayi
dauriyar cewa "ni na yafe miki Iya, kuma ki dena
ambaton mutuwa insha Allahu zaki tashi, cuta ba
mutuwa bace! " Iya ta girgiza kai "kayya! Suka
mata sallama suna kuka tana kuka suka rabu. A
gidan Mama ne, Mama ta kwantar da murya
tayiwa Mubeena bayanin komai, Mubeena wani
sabon kukan ta sake Mama na rarashinta, taji
tausayin Ummanta sosaii sosaii ga wani sonta
dake k'aruwa a zuciyarta,, sannan kuma taji
tsanar Mal Sule a zuciyarta, ji take ba wanda ta
tsana sama dashi..godewa Allah tayi daya bata
uwa ta gari kamar Umma dan ita gani take tafi
kowa dacen uwa a duniya! Haka suka koma gida
dukkansu ba farin ciki da walwala.. ◆◆◆◆◆◆◆
Washe garin rana Allah yayi wa Iya cikawa,, su
Umma sunji mutuwarta sosaii a wannan dak'in
Allah yayi mata cikawa cikin dare. Da sassafe su
Umma suka tafi suna ta kuka abun tausayi
mussaman ma Mubeena, da 'yan gidan suka tafi
gabad'aya har da Abba, dan shima yaji mutuwar
dan ya santa, lokacin da 'aka kwantar da
Mubeena a asibiti da cutar polio ta sameta,,sai
da suka fara sauka a gidan Mama sannan sukaje
gidan marigayiya Iya,, a lokacin ma ko wanka
ba'a yiwa gawar ba, Umma da taimakon Mubeena
su suka wanke gawar tas aka samata likafani aka
fita da ita ,maza suka sallaci gawar aka kaita
kuhewarta , Allahu akbar Allah kasa mu cika da
imani, ka bamu kyakyawan K'arshe Ameen ya
Allah.. Ba wani zaman makoki akayi ba tunda wa
za'ayiwa gaisuwar? Dama Mal Sule ne kawai d'an
data haifa kuma baya nan bai san ta rasu bama,
'yayan mijnata kuwa Bashir da Hauwa sun dad'e
da dena kulata bama sa k'asar gabadaya. A 'yan-
uwanta kuwa ita kad'ai tayi ragowa duk sun
rasu,, sai dai sauran dangi da ba'a rasa
ba..Masa'udu dama shi ake yiwa gaisuwar dan
shine ya kula da ita tun data sami rashin lafiyar
har ta warke, shima kuwa a rannar data rasu
admission dinsa ya fito yaci Ahmadu Bello
unibasiti zaria(ABU zaria) dan haka ya had'a
kayansa ya tafi Umma kuwa kud'i me yawa ta
bashi tace yayi harkar makaranta dashi ya yafi
yana ta godiya.
[12:35AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:46AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [135]-[140] Bayan an
dawo hutun tak'aitacen lokaci. Aysha Amatulah:
to barkan mu da dawowa. Hajiya Mubeena shin
wai ta yaya kika tsunduma cikin harkar zane-
zane? Mubeena: To agaskiya nidai na taso ne
kawai na gani inayi, a lokacin inga abu ya min
kyau sai na zana shi, cikin ikon Allah kuma sai
kiga zanen ya fita sosaii...lokacin da ina primary
kuma in kika duba littafai na na arts zaki ga inaci
sosaii, koda merit za'a bada ma a Art ni ake
bawa. Kuma akwai Yayana Ya Ameen shine ya
cigaba da ban kwarin gwiwa har nazo matakin
danake yanzu. Aysha Amatullah: madalah, to
kafin ki fara wanan zane-zanen mene burinki a
rayuwa? Mubeena: Burin na da shine na zama
likita dan nima na bada gudunmawa ta wajen
yak'i da wannan cutar sai kuma Allah beyi ba.
Aysha Amatullah: to Allah zaba mafi alheri, meye
ya fi b'ata miki rai da kuma abinda yafi faranta
miki rai? Mubeena: Abinda ya fi b'ata min rai
guda biyu ne na d'aya ya shafi personal life dina,
na biyun kuwa shine, idan naga yan'uwana masu
wannan cuta ta polio suna bara ko kuma suna
cikin wani hali na rashin gata a gaskiya raina na
sosuwa kuma ina iya k'ok'ari na dan ganin na
taimake su. Sannan abinda yafi faranta min rai
shine, ina tuno irin nasororin dana samu a
rayuwa, sannan kuma ina ga masu irin cuta ta
wato polio basa fuskantar wani k'alubale a
rayuwa ,suna jin dadin rayuwarsu sannan suna
samin gata daga wajen iyayensu dama al'uma
baki d'aya, to nakan ji raina yayi fari . Aysha
Amatullah: Allah sarki, yanzu zamu d'auki waya
guda biyu(2) duba da yanayin lokaci, zaku turo
sak'o ne ta wannan lambar 064**** sannan zaku
kira mu ta 064****. Mutane an kira an mata
fatan alheri, an kuma turo sak'oni ba adadi.
Aysha Amatulah:wani kira zaki yi ga iyaye da
kuma masu cutar polio? Mubeena: kiran da zanyi
shine dan Allah iyaye su dinga bada yayansu a
dinga musu d'igon rigakafi, sannan iyaye su dage
su dinga gano talent din da suke dashi su
k'arfafa musu gwiwa, bawai su dinga barinsu
suna bara ba, da sauransu. Sannan irina masu
wannan cuta ta polio, ganin suna da nakasa kar
hakan yasa su fidda rai da rayuwa , su d'age suyi
karatu suma su zama wasu a dinga damawa
dasu, in hakan ya faru zan fi kowa farin ciki.
Aysha Amatullah: to duba da yanayin lokaci mene
sak'on ki na k'arshe? Mubeena: to Alhamdulilah
ba abinda zance sai in godewa Allah da kuma
iyayena nakan ji farin ciki sosaii in na tuno da
iyayena,yayena da k'anina, da sauran dangi.
Aysha Amatulah: to masu sauraron mu lokaci
yayi halinsa , anan zamu k'ark'are wannan shirin,
Hajiya Mubeena muna godiya da kika amsa
gayyatar mu, da fatan duk sanda muka sake
neman ki zaki amsa kiranmu. Mubeena: to nima
nagode masu saurarona da kallona ina muku
fatan Alheri,(tayi murmushi) sai anjima. Ahaka aka
gama shirin, ta fito driver yaja suka tafi.
*********** A yau ne aka d'aura auren Ameen
Muhammad Ameen da Fatima Adam, Aisha
Muhammad Ameen(Nana) da kuma Saifulahi
Abdalah. Ansha biki sosaii an kuma kashe kudi
dai-dai misali, Mubeena kuwa lemukan nan da'aka
bata kyauta su ta bada akayi hidimar biki da su,
sannan katuwar jaka da calanda me sunayen Allah
ta musu a matsayin gudunmawa sun sha murna
tare da yi mata addu'ar Allah ya saka mata da
alheri. Bayan biki aka kai amarya Nana gidanta
dake Hotoro, Sannan amaryar Ya Ameen Faty aka
kaita gidan ta dake Janbulo. A yau su Mubeena
sukayi final exam dinsu, sunsha kukan rabuwa da
dalibai, Mubeena da Asiya ma ansha kuka,
malamai sunyi bak'in cikin rabuwa da Mubeena
sosai , hadda masu kwala, bayan sunyi sharing
contacts driver yazo ya d'auki Mubeena suka
koma gida, Mubeena cike da kewayar dalibai,
malamai dama makarantar baki d'aya. Yau ta
kama rannar lahadi kuma dama duk Lahadin
k'arshen wata sukan je shopping... Suna cikin
mota dan zuwa shopping d'in Abba ne ke driving
dan yau yace sha'awar driving yake saboda ya
d'ad'e beyi ba, Umma na gaba, yayin da Husna,
Amir da Mubeena ke bayan mota Ummi kuwa taje
bikin 'yar aminiyata. Suna tafe cikin raha da
anashuwa. Can wata mota ta taho da gudun
gaske, dai-dai lokacin da wani datijjon mutum
yazo tsalaka titi, ai kuwa fuu motar ta bige shi,
bata ko tsaya ba drivern mota ya k'ara falawa da
gudu, cikin 'yan sakani aka dena hango motar sai
k'ura da motar ta tayar... shikuwa dattijon
mutumin nan yana baje a titi jini sai zuba yake.
Abba da sauri ya fito daga motar yana salati
suma su Umma suka fito dan ganewa idonsu, a
firgice suka k'araso wajen da mutumin ke kwance
cikin jini, Umma da ta k'araso wajen da sauri,
dora idonta akan mutumin keda wuya ta kwala
wani k'ara anan ta fad'i k'asa sumamiya!
Lik
[11:47AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [130]-[135] Nan take
wajen ya d'auka sai ihu akeyi su Husna dake gefe
sai dariya suke yi dan sunsan Mubeena yau ta
shak'i haushi itada ko hannunta bata san wani
namiji ya tab'a, sai gashi yau k'aton arne ya
d'aga ta, shikuwa Ya Abdul ji yake kamar yaje ya
wankawa Mr Mike mari dan haushi. Da kyar ta
samu ya sauke ta k'asa, ai kuwa sai tabar
wajenshi ta koma d'ayan banganren, sai
d'aukanta hoto ake. Certificate aka bata ta,
sannan aka buk'aci ta sa hannu taje ta saka kuwa,
sannan aka mik'a mata shi, bayan nan aka shiga
raba kyautuka ga wanda suka yi participating
kyauta kuwa ta samu kala-kala, kamfaanin wani
shahararen lemu ya bata da kuma sauran
participant's d'in kud'i da kuma lemuka, kyauta
dai iri-iri ta sha su wai kuma aka samun tab'i ne
dan ba'a bata babbar kyautar tata ba. Check na
miliyan d'aya(1) aka bata daga hukumar da suka
shirya gasar sannan kuma k'ungiya masu zane
dake kano suka bata kudi naira dubu d'ari(100).
Mr Mike ne ya d'auko wasu sarkok'in medal's
guda uku(3) 'yan k'anana d'aya na gold d'aya na
silver na ukun kuma na bronze. Ta uku ya rataya
wa bronze medal aka fara tafi ana d'aukan
hotuna, sannan ya kira Ahmad Huzaifa ya rataya
masa na silver, shima aka d'au tafi. Bayan nan
kuma wakilin gwamnati ya tabbatar mata da
cewa bayan ta kammala karatun sakandire
gwamntani zata d'auki nauyin ta taje tayi course
din zane a wata makatantar zane-zane(art school)
dake amurka(America) Na gold din kuwa
Mubeena ya ratayawa nan waje ya k'ara d'aukan
ihu 'yan jarida nata d'aukan hoto da kuma hoto
mai motsi(video) domin a yawancin kafafen yad'a
labarai ta talabijin abin live ake nunawa. Su Abba
dake zaune suna kallo LIVE murna a wajensu
kamar me, sun ma rasa me zasuyi saboda murna,
hak'k'ika wannan rana tana cikin rana mafi farin
ciki a rayuwarsu, mussaman ma Umma da
alk'warin da tayiwa Mal Sule ya cika yau, a
zuciyarta cewa take dama Mal Sule ya ji ko ya ga
wannan abin alherin. Bayan an kammala taro aka
rufe taro da add'ua, nan aka fara d'aukan hotuna
dasu Uncle Hashim da bakinsa ya kasa rufuwa
saboda farin ciki, su Ya Abdul ma haka, kana
ganinsu zaka gane irin halin da suke ciki. Zanen
kuwa tafiya Mr Mike zeyi dashi, inda za'a kai shi
wannan babban ART GALLERY dake Abuja. Su
Alhaji Bawa basu so hakan ba dan su sunfi san a
barshi a Art gallery din dake kano amma ba
yadda suka iya. Fitowar su Mubeena ke da wuya
wakilan 'yan jarida da gidajen radio sukawo mata
caa akanta, sai tambayoyi suke mata tama rasa
wadda zata amsa, can dai tace "Alhamdulilah ba
abinda zance sai godiya ga Allah da ya bani
nasara a wannan gasar, sannan ina godewa
iyayena da suka bani k'warin gwiwa har nazo
matakin dana ke yanzu! Nagode.". Tana gama
fad'an hakan tayi hanyar motarsu. Zwan ta keda
wuya ta tadda wakilan wani shahararen gidan TV
suna jiranta, numfasawa tayi tace "wannan shine
anyi gudun gara an tadda zago". Nan suka shiga
yi mata magiya akan suna so su tautana da ita
gobe, saboda gobe ne ta kama rannar masu
cutar polio da duniya wato (WORLD POLIO DAY)
wato ashirin da hud'u ga watan oktoba(24th
october) bata musu musu ba kuwa ta amsa sunyi
farin cika sosaii inda suka bata wani kati na
gayyata. Farin ciki ya dawo sabo sanda suka
koma gida su Umma hadda kukan murna, Ya
Ameen dake can k'asar holland ya sami labari
daya duba news ya kira su aka sha murna,
makarantarsu kuwa dayake tana final year suka ce
sun d'auki nauyin ta har ta gama su waec da
neco duk zasu biya mata, saboda ta fito da
sunan makarantarsu, bayan k'ananun kyaututuka
da suka bata. Yau ta kama 24th october(World
polio day), tun da safe ta ta shirya driver ya
kaita dan Ya Abdul ya tafi wajen aiki. Tana zuwa
dama ita suka jira, aka shirya komai tazo ta zauna
akan kujerar da za'a tautauna da ita.(wasu
gidajen radio suma sun juno dan masu saurarun
radiyo suma suji) Me gabatarwa ta fara:
Assalamu alaikum warahamatul lahi ta'ala wa
barkatuhu masu kallo da sauraranmu. Barkan mu
da sake saduwa a wannan shiri na mussaman da
muke gabatarwa duk a rannar polio ta duniya
duk shekara. A yau shirin namu yayi babban
kamu, domin yau zamu tautauna da AISHATUL
MUBEENA Muhammad Ameen, wadda itama ta
zamo polio victim ta farko tada fara lashe gasar
zane-zane dake gabatarwa duk bayan shekara
hud'u a jihohi dama k'asa baki d'aya... Sunana
Aysha Amatullah wadda zan gabatar da shirin,
Hajiya Mubeena ko nace Artist Mubeena barka da
zuwa. Mubeena: Barka kadai. Aysha Amatullah:
shin zamu iya jin tak'aitacen tarihin ki? Mubeena:
To Alhamdulilah, nidai sunana Aishatul Mubeena
Muhammad Ameen an haifeni a garin Kano na
taso a Kano, kuma a yanzu haka inada shekara
sha bakwai next year zan shiga sha takwas(18),
saboda ban fara makaranta da wuri ba yanzu dai
ina ss3 a sakandire. Aysha Amatullah: Masha
Allahu, shin kina shekara nawa wannan cuta ta
sameki? Kuma mene ne dalili? Mubeena: A
gaskiya wannan cuta ta same ni ina 3-4 years,
dan dama kinsan a yara masu shekara d'aya zuwa
biyar(1-5) tafi kamawa..kuma a gaskiya zan iya
cewa wannan cuta kaddara ce daga Allah, dama
can Allah ya riga ya rubuta cewa a haka zan
tashi, cutar zata same ni. Aysha
Miss Hafcy
Newer Post Older Post Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)
Saturday, 15 October 2016
Posted by MissHafcy at 08:01
AISHATUL MUBEENA 110-140
[12:33AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:51AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS A tak'aice dai ansa
rannar Ya Ameen da Faty, da kuma Aisha( Ya
Nana) da Saifulah nan da wata biyu(2) ,, Su
Umma kuwa sai shirye shiryen biki sukeyi.. Ya
Abdul kuwa har ya gama karatunshi Abba ya
samar masa aiki har ya fara yi dan haka ma ba
kullum yake zama a gida ba. Baiwar Allah
Mubeena kuwa tacan duk ta damu dan ta dad'e
da gane cewa tana son ya Abdul ! amma sai take
ganin abun da kamar wuya, na farko dai Umma
tace mata Abba ne babanta to indai har kuwa
Abba ne babanta to ba aure a tsakaninsu saboda
wanta ne uba d'aya kuma ba aure a tsakaninsu
k'anwa da wa.!.na biyu kuwa, tasan halin ya
Abdul shida ko magana bata shiga tsakaninsu sai
ta k'ure,, in ba kwanan nan dayake d'an sakar
mata fuska,,kuma tasan ma baze rasa budurwa
wadda yake so ba,,,,yadda yake d'in nan
tubarkalah gashi kuma d'an gayu,, doleh 'yan
mata suyi rububinsa... dan haka sai ta dinga
addu'ar Allah ya cire mata sanshi a zuciyarta,, a
kullum kuma tana k'ok'arin cire sanshi daga
zuciyarta,, dan a iya tunaninta ko da da aure a
tsakanin su, in ba wani ikon Allan ba,to ko a
mafarki baza ta tab'a zama matarsa ba,, Ita dai
kullum addu'arta shine Allah ya bata miji na gari
ya kuma zab'a mata mafi alheri Yau saura befi
kwana biyar (5) suyi gasar ba,kuma dama sun
gama exams an basu hutu, dan haka lokacin hutu
za'ayi gasar.. Mubeena na zaune a falo tana kallan
musab'akar alkur'ani da akasa a sunnah Tv,,
Umma ta fito daga d'aki cikin shirin fita unguwa,
Mubeena ta d'ago ta kalleta "Umma fita zaki yi
ne?" Umma tace "eh k'auye zani wajen Mama"
Mubeena da sauri ta tashi "Umma dan Allah nazo
muje? Na dad'e banga Mama ba" Umma tace to
maza shirya muje,kafin rigimaman nan yazo(Amir)
dama neman dalilin k'in zuwa islamiya yake yi"
Mubeena tayi dariya sannan ta shiga dakinsu ta
dauko hijab dinta ta bi bayan umma ,, suka yiwa
su Ummi sallama sannan suka nufi k'auye. Bayan
sun isa Mama tayi murna sosaii da ganin su,
bayan sun gaisa sun sha ruwa , Mubeena nakan
cinyar Mama suna wasan su na jika da kaka,
Mama ta kalli Umma," Ma'u kinsan IYA ta samu
mutuwar b'arin jiki kuwa? Gaban Umma ya fad'i ,
"subhanalahi,wacca iyan??" ta fad'a had'e da
dafe k'irji, Mama tace " Iya dai surikarki, wallahi
abun tausayi kuje ki duba ta dan Allah kullum
fad'i take a kirawo mata ke da yarki ta nemi
gafarar ku . Umma tace "Allah sarki Iya, a ina
take zaune? Mama tace "inda dai kika santa tana
nan' Mubeena dake kwance akan cinyar Mama da
sauri ta taso ta tsutsura musu ido ,, ta kalli
Mama tace"Mama wacce ce Iya?" Mama na
k'ok'arin magana Umma ta dakawa Mubeena
tsawa "bansani ba,dake muke magana,ban hanaki
sa min baki in ina magana ba?" Mubeena ta
sunkuyar da kanta , yayin da Mama tace "ke Ma'u
wai meyasa kike haka ne? Daga tambaya saiki
hayayak'o mata?" Umma tace "Mama haushi
taban ai manya na magana ta dinga sako baki,
bari na tashi naje na dubo ta"" ta tashi ta dauki
jakarta tana k'ok'arin saka takalminta, Mama ta
kalleta," Ma'u indai nina haifeki to ki tafi da
Mubeena" Umma ta juyo jiki ba kwari tace "to se
ki taso muje" bata jira amsar Mubeena ba ta sakai
ta fita, Mubeena da sauri tasa hijab dinta tabi
bayanta. Har suka iso gidan Umma bata yiwa
Mubeena magana ba, da sallama suka shiga gidan
amma suka ji shiru,, sai da sukayi sallama yakai
guda hudu(4) sannan suka jiyo wata dashashiyar
murya nacewa "Wa..alai..kum..us..salam...,k
u..shigo..mana,, Umma ta kad'a kai sannan ta
shiga dakin data juyo murya, Mubeena tabi
bayanta. Umma ta zaro ido saboda abinda ta
gani ya masifar tsorata ta, duniya kenan! ... IYA
ce kwance akan wata yagalaliyar tabarma duk tayi
fitsari akai, dakin in banda zarni ba abinda yake
yi. Umma a firgice ta k'arasa wajen Mubeena ta
bi bayanta, Iya ta k'are musu kallo sannan tace
"Wannan kamar Ma'u nake gani kodai mafarki
nakeyi? Umma ta runtse idonta sai hawaye 'Nice
Iya!" Iya ta fashe da kuka "kece Ma'u ! ashe rai
kanga rai? Ina jikar tawa take?" Umma ta nuna
Mubeena "gata nan, tare muke ma" Iya ta k'ara
fashewa da kuka "zo nan 'yar jikalle ta, ni bansan
ma da wani ido zan kalle ki ba, randa aka haife ki
nida mahai....." Umma ta da sauri ta katse ta "Iya
komai ya wuce dan Allah a bar zancen nan baki
yimin komai ba ni kuma koda kin min ma na yafe
miki, garin yaya kika sami wannan ciwon?". Iya
tana kuka tace "rannar ina zaune ni kad'ai a daki
naji mage a gefena, kinsan dama ina tsoron mage
,to tun daga nan na tsorata sosai bakina ya juye
magana ma na kasa yi, hannuna ma na kasa
d'agawa balle na d'aga kafata,, Haka na kwana
ina kuka bame ceto na,, washe gari makota da
suka ji shiru suka zo suka bud'e kofar aka fito
dani aka kaini asibiti anan akace mutuwar b'arin
jiki nasamu,,shine nake kwance anan masa'udu
(dan k'anwar iya) shine kawai yake kula dani,,, ta
sake fashewa da kuka,, Umma ta fashe da kuka
hakama Mubeena dama ga Mubeena da tausayi.
Iya ce ta katse musu kukan da cewa "Ma'u baki
fad'a wa jikartawa ni kakar ta bace ba? Dan daga
ganin alama bata san nice na....Umma ta katse ta
" Iya dan Allah ya isa haka, zancen nan ya wuce
banse tasan komai ba ai" Mubeena duk ta rikice
ta kasa gane maganar tasu, sun caja mata
kwakwalwa....Iya cikin dashashiyar murya tace
"Ma'u RANNAR WANKA BA'A BOYEN CIBI!
Like · 2 · Reply · Edit · 3 February
Khadija Muhamed
[11:52AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [105]-[110] Mubeena
ta shafa fuskarta" bakomai yusra Allah ya baki
lafiya" yusra ta rik'e hannunta "Amin",, sukai
musu sallama suka juya suka bar Maman nata
kukan murna k'aninta mu'az yazo shima murna
kamar me, ya dinga shiwa su Mubeena
albarka,,dama kudin reg din makaranta yake
nema ya cika dubu biyar(5000)amma ta gagara
sai gashi Allah ya share musu kukunsu. A mota ne
Umma ke ba ya Abdul labarin yarinya jaji
tausayinta sosaii shima ya kuma ji dad'i da'aka
musu wannnan taimakon..Suka aje Asiya a gida
suka mata godiya sannan suka koma gida. Kwanci
tashi ,gobe ne Mubeena da Nafisa zasuyi gasar
su, Mubeena tayi practice sosai, a rannar raba
dare tayi tana addu"ar Allah ya bata sa'a su
Umma ma haka duk 'yan gidan ma, Ya Abdul ma
yazo yayi mata fatan alheri,dan yanzu ba laifi
yana sakar mata fuska. Da sassafe ta tashi ta yi
sallolinta sannan tayi zikirorinta ta shirya suka
huce makaranta...bayan an fito break 'yan class
sun zagaye Nafisa dake wa mickey mouse din
data zana musu fenti wai zasu sa a wall bangon
class din ,bayan ta gama ta d'aga zanen "ya kuka
gani friends?" Suka hada baki "Woww..yayi kyau
sosaii amma da Mubeena ce ta zana munsan se
yafi haka kyau" Nafisa ta juyo a fusace "lallai ma,
in sha wahala in muku abu amma kuce da wata
banza ce tayi sai yafi kyau?" D'aya daga cikinsu
tace "a'ah kinga kar ki sake ce mata banza "
Nafisa tace "an fad'a mata d'in, bari ku gani" nan
da nana ta warce zanen ta yayaga shi, sannan ta
fita daga ajin tana zage-zage,sukuwa dariya
sukayi sukace "kanki kika cuta ai,wahalaliya kawai.
Mubeena ce da Nafisa zaune suna jiran akawo
musu abubuwan zanen, Uncle Hashim ya shigo ya
raraba musu sannan yace mutum d'aya ta biyo
shi saboda za'a raba musu aji gudun kar wani ya
kwafi na wani, caraf Nafisa tace zata bishi ,hakan
kuwa akaiyi yabar Mubeena da anty Sa'a sannan
shi kuma suka tafi wani staff room d'in shi da
Nafisa. Cikin minti talatin suka kamala zanen
kowa yayi submitn,, suka koma aji ... aka bawa
wanda suka duba zanen kwanaki dan su duba
wannan d'in shima. Suna zaune a aji suna class
work din maths Uncle Hashim yazo ya kira
Mubeena anan ya tabbatar mata da cewa itace ta
lashe gasar!! Wohoho murna wajen Mubeena
kamar me ta rasa ma me zatai dan murna.
Assamibili aka k'ara hadawa anan aka kirawo
Mubeena gaban assambili aka sanar da sauran
dalibai itace ta cinye gasar kuma ita zata wakilci
makarantarsu a gasar da za'ayi nan da sati biyu2
dalibai aka d'au ihu ana Up Up Up Mubeena!!
Mubeena kuwa sai murmushi take tana godewa
Allah daya bata nasara... Nafisa dajin haka ihu ta
saki ,tana wani fizge fizge daga k'arshe ta tada
aljanun k'arya malamin islamic studies yasa
prefect mata suka d'auke ta zuwa staff room dan
yayi mata ruk'iya nan kuwa be san na k'arya ne
ba. Mubeena kuwa se murna ake mata malamai
kuwa sai wani nan-nan suke da ita kodayake
dama can malamai suna santa saboda
kwazonta...Nafisa kuwa da Ustaz(malamin
islamic) ya gane cewa na k'arya ne,dorina ya
dauko zabgegiya ya shiga lafta mata, bashiri ta
tashi tana kuka sharaf sharaf tana bashi
hak'uri,dariya yayi sanan yace ta koma aji, aka
dinga mata ihu ana cewa me aljanun k'arya a
rannar tayi alkwarin baza ta sake dawowa
makarantar ba, dan abin kunya data aikita baza
su barta ta zauna a makarnatar lafiya ba. Yau Ya
Ameen ya ze dawo murna a wajen 'yan gidan
kamar me,kowa ka gani yana cikin walwala hatta
Ya Abdul... Mubeena kuwa cewa tayi a bar mata
zata mai girki me dadi, dayake yanason abincin
gargajiya fankaso da tuwo ta yi masa da miyar
taushe dan ya fad'a mata a waya ya dad'e be
cisu ba,, su ya Nana kuma suka yi masa kunun
aya da zob'o. Bayan yayi parking din motar shi
ya shigo gida Amir da gudu yazo ya rungume shi
yana masa oyoyo , su Mubeena suka fifito suna
masa sannu da zuwa shikuwa yana amsawa fuska
d'auke da murmushi..ya k'araso cikin gida Umma
da Ummi kuma na falo suna jiranshi suka yi masa
sannu da zuwa sa kuma ya hanya. Ya amsa da
"lafiya lau nagode,,kuma nayi missing dinku
sooooooo much" a tare suka ce "muma munyi
missing dinka". Bayan yayi wanka yayi sallah ya
dawo ya zauna Mubeena tace abincinsa na kan
dinning table( teburin cin abinci) yaje ya zauna
yana budewa ya fara "wow nasan wannan aikin
kine Mubeena", Ummi tace 'ai kuwa kamar
kasani,kayan shan ne su Nana sukayi yimaka" yayi
murmushi "amma kuwa nagode lovely sisters"
Bayan ya gama cin abincin su Ummi ke sanar
dashi Mubeena ce zata wakilci skul dinsu ba
k'aramin murna yayi ba,a rannar ta faranta masa
rai. Washe gari ya sami Umma yake fad'a mata
cewa iyayen Faty sun takura masa daya turo dan
nan da wata hudu (4) za'ayi bikin yarta kuma
sunaso a had'a da na Faty...shikuma yana kunyar
fad'awa Ummi da Abba,, Umma tayi murna dajin
haka, ta kuma yimasa alkwarin zata fad'awa
Abban sannan kuma indai ya shirya to ba
matsala. yayi mata godiya ya tafi. Umma ta sami
Abba ta fada masa yaji dadin haka dama yana
shirin yi masa maganar auren dan a ganinsa
lokaci yayi daya kamata ya zama cikaken mutum
wato yayi aure...yace ta fad'awa ya Ameen d'in
ya kwantar da hankalinsa zasuje shida yan-
uwansa su nema masa auren insha Allahu..
[12:34AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:48AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [125]-[130] Wakilin
shugabanin da suka shirya gasa wanda yazo daga
birnin taraya Abuja wato MR MIKE da shugaban
k'ungiyar masu zanen dake kano ALHAJI AL-
AMIN BAWA sune suka fito dan fad'an result din
bayan manyan-manyan kwararru a harkar zane
sun duba sun fitar da sakamako, Alhaji Bawa shi
zai dinga kiran suna yayinda Mr Mike ze dinga
d'aga zanen dan kowa ya gani. Bayan sun yi d'an
jawabansu, Alhaji Bawa ya fara magana kamar
haka:" zamu fara da na sha biyar (15)" nan ya
fara kiran sunaye yayin da Mr mike ke d'aga
zanen, sai kuma wanda aka kira ya fito bainar
jama'a. Sai mutane su tafa masa/mata . A haka
dai yana fad'a har yazo ta biyu. Wanda ya kira
dalibi Ahmad Huzaifa, aka d'aga zanen shi nan
mutane suka fara ihu sosaii dan zanen nashi yayi
bala'in kyau. Bayan nan yace yanzu za'a d'aga
zanen wanda/wadda ta yazo ta d'aya, mutane
kowa ya baza ido yana jiran ganin wani zane ne
wanda ya zarce had'ad'un zanen da'aka nuna, da
kuma wani tauraron ne ko kuma wata tauraruwar
ce ta samu nasarar lashe gasar? Mr Mike wani
had'ad'en ko nace gaba da had'ad'e zanen ya
d'aga sama, zane ne wanda aka yishi akan al'adar
bahaushe wato , da farko dai , bukka aka zana
yar k'arama me bala'in kyau a gefen ta kuma
tabarmar kaba ce wanda aka zana akushi da
kwanon sha da kuma kwaryar akai, ga butar
alwala a gefe, a d'ayan bangaren kuma atamfa ce
aka zana da kuma dan kwali irin na da, sannan ga
murajani da dai sauran kayan hausawa na mata.
Zanen yayi bala'in kyau mutum in ya kalla sai ya
rantse hoto ne aka d'auka a camera saboda
tsabar tsaruwar da yayi. Nan da nan wajen ya
gauraye da ihu kowa sai washe baki yake yi daga
masu cewa "wow!" Sai masu cewa 'masha Allah"
duk dai, Kowa burinsa be huce yaga wanda/
wadda yayi zanen ba. Yan jarida kuwa da sauran
mutane sai d'auka hoton zanen suke. Mubeena
kuwa suna hira da su Husna taga an d'aga zanen
ta wani farin ciki taji wanda bata tab'a jinsa a
rayuwarta ba,, ta runtse idonta sai hawayen
murna, ta kuma k'i fadawa su Ya Abdul cewa
zanen tane, sukuwa suna gefe sai fama zuzuta
zanen suke,amma kowa a zuciyarshi, ji yake
kamar zanen Mubeena ne. Alhaji Bawa ne ya
dakatar da mutane daga hayaniyae da suke
dakuma ihu, yayi gyran murya yace , "yanzu zan
kira wanda yayi wannan zane, ina me farin ciki
kirin AISHATUL MUBEENA Muhammad Ameen!".
Murna a wajen su Husna kamar me ,sai kallon
Mubeena suke suna k'ara kallonta, fuskarsu
d'auke da farin ciki, Mubeena kasa tashi tayi da
kyar suka lalab'eta ta tashi jiki ba kwari ta nufi
inda aka kirata. Mutane dake ta jiran fitowar ta,
sai hango ta sukai tana cangala kafarta dan
zuwan wajen, mamaki duk ya cika su, amma
wannan ta ciri tuta ashe dama da nakasasu masu
irin talent irinta? Ihun mutane ya k'aru gaba
d'aya suka tashi suna kallonta yayin da 'yan jarida
suka cika wajen suna d'aukar ta hoto, da kuma
hoto mai motsi(video). Isarta keda wuya , Mr
Mike abinka da arne cak ya d'agata sama! Duk
k'ok'arin datake dan ta kwace amma ya rik'e ta
gam, cikin d'aga murya da hausar sa da wadda
bata fita sosai yace " wannan itace ta lashe
gasar, itace tazo ta d'aya!"
Like · 2 · Reply · Edit · 6 February
[11:50AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [115]-[120] Umma
tace "hakane Iya amma..." Iya ta katse ta
"dakata" ta janyo hannun Mubeena ta rik'e gam
sannan tace "Aihatul mubeena nice kakar ki, nice
na haifi mahaifinki SULAIMAN, nida mahaifinki
mun kasance masu wata irin zuciya,masu butulci
kuma wa'enda basu da godiyar Allah,, nan da nan
ta fada mata komai tun daga auren Umma da
Mal Sule har rannar da suka rabu" Mubeena ta
fashe da kuka,kuka take sosaii haka ma Umma.
Mubeena tana kuka tace "Umma dama na fad'a
miki, na fad'a miki cewa Abba ba shine mahaifina
ba!" Umma cikin tsawa tace " shine mahaifinki !
Abba shine mahaifinki! , shine yaso ki a lokacin
da Mal sule ya k'i ki har yake ik'irarin cewa ke ba
'yarsa bace, shine ya ciyyar dake, ya tufatar
dake, ya baki ilimi, daidai da rana d'aya bai tab'a
nuna bambanci a tsakaninku ke da 'yan'yansa ba,,
sabanin Mal Sule da ya firta da bakinsa kar na
sake ko da wasa nace ke d'iyarsa ce , wanda
shine sillar gurguncewa k'afarki, wanda besan cin
kiba, besan shan kiba, besan wahala kiba, besan
komai naki ba! Abu d'aya ne ya miki a rayuwa,
shine sillar zuwan ki duniya , amma bayan haka
ba abinda ya tsinana miki a rayuwa, wallahi kome
Mal sule ze miki yanzu in aka d'auke Silan zuwanki
duniya dayayi baze ko kusa yi miki abinda Dr
Muhammad ya miki ba,, Mal Sule ya amsa sunan
sa na cewa shine ubanki wanda ya haife ki kawai,
amma ko kusa baze amsa sunan , wanda yayi
wahala dake tun kina yar gwililuwa har yanzu,
wanda ya ci dake, ya sha dake,ya tufatar dake,ya
baki ilimi ya kuma baki tarbiya, Shine ya cika
sharud'an zama uba wanda uban naki wanda ya
haife ki ya kasa cikawa!(Ta sassauta murya ta)
amma Mubeena kar abinda nida Iya muka fad'a
miki ya sa ki tsani mahaifinki, ko kusa kar ki fara
domin in badan shiba baza kizo duniya ba!....ta
k'arasa maganar cikin sheshek'ar kuka. Kukan
Mubeena ya k'aru sosai, tama kasa magana, sai
sheshek'ar kukan data keyi,,, Umma ta kalli Iya
dake ta faman sharbar kuka tace "Iya kiyi hak'uri
ban fad"i maganar ba dan ta b'ata miki rai,
gaskiya ce kawai na fad'a, Iya tace" baki b'ata
min rai ba Ma'u, gaskiya ke kike fad'i, nayi dana
sanin abinda na aikata a baya"" Ma'u tace "Iya
bakiyi mana komai ba Iya wannan maganar ta
huce saboda ni tun d'ad'ewa da kika nemi
gafarata na yafe miki, dama ko baki nemi na yafe
miki zan yafe miki dan wallahi ni tamkar Uwa na
d'auke ki!" Ga wannnan ta aje mata bandir din
yan dubu d'aya(1) sannan tace "gobe insha Allah
zan aiko miki da sauran abinda kike buk'ata,
kuma insha Allahu za mu dinga ziyartar ki akai-
akai. Iya ta rik'e hannunta " Ma'u tsaya na fad'a
miki wani abu,, yau tsawon shekaru goma(10)
kenan ban sa Sule a idona ba, tunda yazo yace
min ya tafi birni cirani na nuna ban amince ba
amma sam ya k' jin maganata ya tafi ya barni, be
kuma waiwayata ba, ko yana da rai? Ko ya rasu?
Allahu a'alam,, amma dan Allah in Allah ya had'a
ku dan Allah ma'u ku yafe masa ke da Aiha
(Aisha), ki kuma ce nima na yafe masa, dan ina ji
ajikina kwanan ya kusa k'are da k'yar na k'ara
kwana a duniya ,nima ku yafe min Allah ya had'a
fuskokin mu a aljana..." ta fashe da kuka,,,,jikin
Umma da Mubeena yayi sanyi sosaii Mubeena tayi
dauriyar cewa "ni na yafe miki Iya, kuma ki dena
ambaton mutuwa insha Allahu zaki tashi, cuta ba
mutuwa bace! " Iya ta girgiza kai "kayya! Suka
mata sallama suna kuka tana kuka suka rabu. A
gidan Mama ne, Mama ta kwantar da murya
tayiwa Mubeena bayanin komai, Mubeena wani
sabon kukan ta sake Mama na rarashinta, taji
tausayin Ummanta sosaii sosaii ga wani sonta
dake k'aruwa a zuciyarta,, sannan kuma taji
tsanar Mal Sule a zuciyarta, ji take ba wanda ta
tsana sama dashi..godewa Allah tayi daya bata
uwa ta gari kamar Umma dan ita gani take tafi
kowa dacen uwa a duniya! Haka suka koma gida
dukkansu ba farin ciki da walwala.. ◆◆◆◆◆◆◆
Washe garin rana Allah yayi wa Iya cikawa,, su
Umma sunji mutuwarta sosaii a wannan dak'in
Allah yayi mata cikawa cikin dare. Da sassafe su
Umma suka tafi suna ta kuka abun tausayi
mussaman ma Mubeena, da 'yan gidan suka tafi
gabad'aya har da Abba, dan shima yaji mutuwar
dan ya santa, lokacin da 'aka kwantar da
Mubeena a asibiti da cutar polio ta sameta,,sai
da suka fara sauka a gidan Mama sannan sukaje
gidan marigayiya Iya,, a lokacin ma ko wanka
ba'a yiwa gawar ba, Umma da taimakon Mubeena
su suka wanke gawar tas aka samata likafani aka
fita da ita ,maza suka sallaci gawar aka kaita
kuhewarta , Allahu akbar Allah kasa mu cika da
imani, ka bamu kyakyawan K'arshe Ameen ya
Allah.. Ba wani zaman makoki akayi ba tunda wa
za'ayiwa gaisuwar? Dama Mal Sule ne kawai d'an
data haifa kuma baya nan bai san ta rasu bama,
'yayan mijnata kuwa Bashir da Hauwa sun dad'e
da dena kulata bama sa k'asar gabadaya. A 'yan-
uwanta kuwa ita kad'ai tayi ragowa duk sun
rasu,, sai dai sauran dangi da ba'a rasa
ba..Masa'udu dama shi ake yiwa gaisuwar dan
shine ya kula da ita tun data sami rashin lafiyar
har ta warke, shima kuwa a rannar data rasu
admission dinsa ya fito yaci Ahmadu Bello
unibasiti zaria(ABU zaria) dan haka ya had'a
kayansa ya tafi Umma kuwa kud'i me yawa ta
bashi tace yayi harkar makaranta dashi ya yafi
yana ta godiya.
[12:35AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: [11:46AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [135]-[140] Bayan an
dawo hutun tak'aitacen lokaci. Aysha Amatulah:
to barkan mu da dawowa. Hajiya Mubeena shin
wai ta yaya kika tsunduma cikin harkar zane-
zane? Mubeena: To agaskiya nidai na taso ne
kawai na gani inayi, a lokacin inga abu ya min
kyau sai na zana shi, cikin ikon Allah kuma sai
kiga zanen ya fita sosaii...lokacin da ina primary
kuma in kika duba littafai na na arts zaki ga inaci
sosaii, koda merit za'a bada ma a Art ni ake
bawa. Kuma akwai Yayana Ya Ameen shine ya
cigaba da ban kwarin gwiwa har nazo matakin
danake yanzu. Aysha Amatullah: madalah, to
kafin ki fara wanan zane-zanen mene burinki a
rayuwa? Mubeena: Burin na da shine na zama
likita dan nima na bada gudunmawa ta wajen
yak'i da wannan cutar sai kuma Allah beyi ba.
Aysha Amatullah: to Allah zaba mafi alheri, meye
ya fi b'ata miki rai da kuma abinda yafi faranta
miki rai? Mubeena: Abinda ya fi b'ata min rai
guda biyu ne na d'aya ya shafi personal life dina,
na biyun kuwa shine, idan naga yan'uwana masu
wannan cuta ta polio suna bara ko kuma suna
cikin wani hali na rashin gata a gaskiya raina na
sosuwa kuma ina iya k'ok'ari na dan ganin na
taimake su. Sannan abinda yafi faranta min rai
shine, ina tuno irin nasororin dana samu a
rayuwa, sannan kuma ina ga masu irin cuta ta
wato polio basa fuskantar wani k'alubale a
rayuwa ,suna jin dadin rayuwarsu sannan suna
samin gata daga wajen iyayensu dama al'uma
baki d'aya, to nakan ji raina yayi fari . Aysha
Amatullah: Allah sarki, yanzu zamu d'auki waya
guda biyu(2) duba da yanayin lokaci, zaku turo
sak'o ne ta wannan lambar 064**** sannan zaku
kira mu ta 064****. Mutane an kira an mata
fatan alheri, an kuma turo sak'oni ba adadi.
Aysha Amatulah:wani kira zaki yi ga iyaye da
kuma masu cutar polio? Mubeena: kiran da zanyi
shine dan Allah iyaye su dinga bada yayansu a
dinga musu d'igon rigakafi, sannan iyaye su dage
su dinga gano talent din da suke dashi su
k'arfafa musu gwiwa, bawai su dinga barinsu
suna bara ba, da sauransu. Sannan irina masu
wannan cuta ta polio, ganin suna da nakasa kar
hakan yasa su fidda rai da rayuwa , su d'age suyi
karatu suma su zama wasu a dinga damawa
dasu, in hakan ya faru zan fi kowa farin ciki.
Aysha Amatullah: to duba da yanayin lokaci mene
sak'on ki na k'arshe? Mubeena: to Alhamdulilah
ba abinda zance sai in godewa Allah da kuma
iyayena nakan ji farin ciki sosaii in na tuno da
iyayena,yayena da k'anina, da sauran dangi.
Aysha Amatulah: to masu sauraron mu lokaci
yayi halinsa , anan zamu k'ark'are wannan shirin,
Hajiya Mubeena muna godiya da kika amsa
gayyatar mu, da fatan duk sanda muka sake
neman ki zaki amsa kiranmu. Mubeena: to nima
nagode masu saurarona da kallona ina muku
fatan Alheri,(tayi murmushi) sai anjima. Ahaka aka
gama shirin, ta fito driver yaja suka tafi.
*********** A yau ne aka d'aura auren Ameen
Muhammad Ameen da Fatima Adam, Aisha
Muhammad Ameen(Nana) da kuma Saifulahi
Abdalah. Ansha biki sosaii an kuma kashe kudi
dai-dai misali, Mubeena kuwa lemukan nan da'aka
bata kyauta su ta bada akayi hidimar biki da su,
sannan katuwar jaka da calanda me sunayen Allah
ta musu a matsayin gudunmawa sun sha murna
tare da yi mata addu'ar Allah ya saka mata da
alheri. Bayan biki aka kai amarya Nana gidanta
dake Hotoro, Sannan amaryar Ya Ameen Faty aka
kaita gidan ta dake Janbulo. A yau su Mubeena
sukayi final exam dinsu, sunsha kukan rabuwa da
dalibai, Mubeena da Asiya ma ansha kuka,
malamai sunyi bak'in cikin rabuwa da Mubeena
sosai , hadda masu kwala, bayan sunyi sharing
contacts driver yazo ya d'auki Mubeena suka
koma gida, Mubeena cike da kewayar dalibai,
malamai dama makarantar baki d'aya. Yau ta
kama rannar lahadi kuma dama duk Lahadin
k'arshen wata sukan je shopping... Suna cikin
mota dan zuwa shopping d'in Abba ne ke driving
dan yau yace sha'awar driving yake saboda ya
d'ad'e beyi ba, Umma na gaba, yayin da Husna,
Amir da Mubeena ke bayan mota Ummi kuwa taje
bikin 'yar aminiyata. Suna tafe cikin raha da
anashuwa. Can wata mota ta taho da gudun
gaske, dai-dai lokacin da wani datijjon mutum
yazo tsalaka titi, ai kuwa fuu motar ta bige shi,
bata ko tsaya ba drivern mota ya k'ara falawa da
gudu, cikin 'yan sakani aka dena hango motar sai
k'ura da motar ta tayar... shikuwa dattijon
mutumin nan yana baje a titi jini sai zuba yake.
Abba da sauri ya fito daga motar yana salati
suma su Umma suka fito dan ganewa idonsu, a
firgice suka k'araso wajen da mutumin ke kwance
cikin jini, Umma da ta k'araso wajen da sauri,
dora idonta akan mutumin keda wuya ta kwala
wani k'ara anan ta fad'i k'asa sumamiya!
Lik
[11:47AM, 18/03/2016] Hapsat: ◆◆◆AISHATUL
MUBEENA◆◆◆ ©MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [130]-[135] Nan take
wajen ya d'auka sai ihu akeyi su Husna dake gefe
sai dariya suke yi dan sunsan Mubeena yau ta
shak'i haushi itada ko hannunta bata san wani
namiji ya tab'a, sai gashi yau k'aton arne ya
d'aga ta, shikuwa Ya Abdul ji yake kamar yaje ya
wankawa Mr Mike mari dan haushi. Da kyar ta
samu ya sauke ta k'asa, ai kuwa sai tabar
wajenshi ta koma d'ayan banganren, sai
d'aukanta hoto ake. Certificate aka bata ta,
sannan aka buk'aci ta sa hannu taje ta saka kuwa,
sannan aka mik'a mata shi, bayan nan aka shiga
raba kyautuka ga wanda suka yi participating
kyauta kuwa ta samu kala-kala, kamfaanin wani
shahararen lemu ya bata da kuma sauran
participant's d'in kud'i da kuma lemuka, kyauta
dai iri-iri ta sha su wai kuma aka samun tab'i ne
dan ba'a bata babbar kyautar tata ba. Check na
miliyan d'aya(1) aka bata daga hukumar da suka
shirya gasar sannan kuma k'ungiya masu zane
dake kano suka bata kudi naira dubu d'ari(100).
Mr Mike ne ya d'auko wasu sarkok'in medal's
guda uku(3) 'yan k'anana d'aya na gold d'aya na
silver na ukun kuma na bronze. Ta uku ya rataya
wa bronze medal aka fara tafi ana d'aukan
hotuna, sannan ya kira Ahmad Huzaifa ya rataya
masa na silver, shima aka d'au tafi. Bayan nan
kuma wakilin gwamnati ya tabbatar mata da
cewa bayan ta kammala karatun sakandire
gwamntani zata d'auki nauyin ta taje tayi course
din zane a wata makatantar zane-zane(art school)
dake amurka(America) Na gold din kuwa
Mubeena ya ratayawa nan waje ya k'ara d'aukan
ihu 'yan jarida nata d'aukan hoto da kuma hoto
mai motsi(video) domin a yawancin kafafen yad'a
labarai ta talabijin abin live ake nunawa. Su Abba
dake zaune suna kallo LIVE murna a wajensu
kamar me, sun ma rasa me zasuyi saboda murna,
hak'k'ika wannan rana tana cikin rana mafi farin
ciki a rayuwarsu, mussaman ma Umma da
alk'warin da tayiwa Mal Sule ya cika yau, a
zuciyarta cewa take dama Mal Sule ya ji ko ya ga
wannan abin alherin. Bayan an kammala taro aka
rufe taro da add'ua, nan aka fara d'aukan hotuna
dasu Uncle Hashim da bakinsa ya kasa rufuwa
saboda farin ciki, su Ya Abdul ma haka, kana
ganinsu zaka gane irin halin da suke ciki. Zanen
kuwa tafiya Mr Mike zeyi dashi, inda za'a kai shi
wannan babban ART GALLERY dake Abuja. Su
Alhaji Bawa basu so hakan ba dan su sunfi san a
barshi a Art gallery din dake kano amma ba
yadda suka iya. Fitowar su Mubeena ke da wuya
wakilan 'yan jarida da gidajen radio sukawo mata
caa akanta, sai tambayoyi suke mata tama rasa
wadda zata amsa, can dai tace "Alhamdulilah ba
abinda zance sai godiya ga Allah da ya bani
nasara a wannan gasar, sannan ina godewa
iyayena da suka bani k'warin gwiwa har nazo
matakin dana ke yanzu! Nagode.". Tana gama
fad'an hakan tayi hanyar motarsu. Zwan ta keda
wuya ta tadda wakilan wani shahararen gidan TV
suna jiranta, numfasawa tayi tace "wannan shine
anyi gudun gara an tadda zago". Nan suka shiga
yi mata magiya akan suna so su tautana da ita
gobe, saboda gobe ne ta kama rannar masu
cutar polio da duniya wato (WORLD POLIO DAY)
wato ashirin da hud'u ga watan oktoba(24th
october) bata musu musu ba kuwa ta amsa sunyi
farin cika sosaii inda suka bata wani kati na
gayyata. Farin ciki ya dawo sabo sanda suka
koma gida su Umma hadda kukan murna, Ya
Ameen dake can k'asar holland ya sami labari
daya duba news ya kira su aka sha murna,
makarantarsu kuwa dayake tana final year suka ce
sun d'auki nauyin ta har ta gama su waec da
neco duk zasu biya mata, saboda ta fito da
sunan makarantarsu, bayan k'ananun kyaututuka
da suka bata. Yau ta kama 24th october(World
polio day), tun da safe ta ta shirya driver ya
kaita dan Ya Abdul ya tafi wajen aiki. Tana zuwa
dama ita suka jira, aka shirya komai tazo ta zauna
akan kujerar da za'a tautauna da ita.(wasu
gidajen radio suma sun juno dan masu saurarun
radiyo suma suji) Me gabatarwa ta fara:
Assalamu alaikum warahamatul lahi ta'ala wa
barkatuhu masu kallo da sauraranmu. Barkan mu
da sake saduwa a wannan shiri na mussaman da
muke gabatarwa duk a rannar polio ta duniya
duk shekara. A yau shirin namu yayi babban
kamu, domin yau zamu tautauna da AISHATUL
MUBEENA Muhammad Ameen, wadda itama ta
zamo polio victim ta farko tada fara lashe gasar
zane-zane dake gabatarwa duk bayan shekara
hud'u a jihohi dama k'asa baki d'aya... Sunana
Aysha Amatullah wadda zan gabatar da shirin,
Hajiya Mubeena ko nace Artist Mubeena barka da
zuwa. Mubeena: Barka kadai. Aysha Amatullah:
shin zamu iya jin tak'aitacen tarihin ki? Mubeena:
To Alhamdulilah, nidai sunana Aishatul Mubeena
Muhammad Ameen an haifeni a garin Kano na
taso a Kano, kuma a yanzu haka inada shekara
sha bakwai next year zan shiga sha takwas(18),
saboda ban fara makaranta da wuri ba yanzu dai
ina ss3 a sakandire. Aysha Amatullah: Masha
Allahu, shin kina shekara nawa wannan cuta ta
sameki? Kuma mene ne dalili? Mubeena: A
gaskiya wannan cuta ta same ni ina 3-4 years,
dan dama kinsan a yara masu shekara d'aya zuwa
biyar(1-5) tafi kamawa..kuma a gaskiya zan iya
cewa wannan cuta kaddara ce daga Allah, dama
can Allah ya riga ya rubuta cewa a haka zan
tashi, cutar zata same ni. Aysha Amatullah: to
madalah, wani kalubale kika ko kike fuskanta?
Mubeena: Alhamdulilah a gaskiya nidai k'alubalen
dana fuskanta be huce lokacin da ina k'arama ba,
lokacin danake koyan tafiya, amma bayan haka
ban fuskanci wani k'alubale ba gaskiya. Aysha
Amatullah: to masu kallo da sauraranmu, kunji
yadda hirar mu ke kasancewa, yanzu zamu je
hutun tak'aitacen lokaci
Share
Comment as:
Publish Preview
No comments:
Post a Comment
MissHafcy
View my complete profile
About Me
► 2017 (16)
▼ 2016 (34)
► November (1)
▼ October (33)
WELCOME
ASMAUL HUSNA 6
ASMA'UL~HUSNA
ASMAUL~HUSNA 4
ASMAUL~HUSNA 3
ASMAUL HUSNA 2
ASMAUL HUSNA
AISHATUL MUBEENA 155-160
AISHATUL MUBEENA 145-155
AISHATUL MUBEENA 110-140
AISHATUL MUBEENA 85-105
AISHATUL MUBEENA 60-80
AISHATUL MUBEENA 45-60
AISHATUL MUBEENA 30-40
AISHATUL MUBEENA 20-30
AISHATUL MUBEENA 1-20
WANI HANIN END!
WANI HANIN 26-27
WANI HANIN 24-25
WANI HANIN 22-23
WANI HANIN 20-21
WANI HANIN 19-20
WANI HANIN 15,16,17&18
WANIN HANIN 12,13,&14
WANI HANIN 11
WANI HANIN 9&10
WANI HANIN 7&8
WANI HANIN 5&6
WANI HANIN 3&4
WANI HANIN 2
WANI HANIN 1
....
WANI HANIN
Blog Archive
Miss_Hafcy. Watermark
AISHATUL MUBEENA 145-155
[12:37AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ ©MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [140]-[145] Abba
cikin rud'ewa ya d'auko wayarsa yayi dailing
numbern drivern asibitin shi, ya mai kwatacen
inda accident d'in ya faru, yayinda ya d'auki
Umma ya sata a motar su, su Mubeena kuwa duk
sun rud'e. Sai da suka jira Motar asibiti tazo, da
taimakon mutanen wajen aka sa mutumin a Mota
suka bi bayan su Abba dan zuwa asibiti.
Emergency aka shige dasu, Umma kuwa bata
dad'e ba ta farfado dan haka aka kaita resting
room, shikuwa mutumin likitoci suka duk'ufa
akansa ana duba shi. Bayan Umma ta farfad'o ta
dawo dai-dai sai kuma kuka, kuka take sosaii
tama kasa magana, Abba dake gefenta sai
lalashinta yake, su Mubeena kuwa suna reception
suna jira. Abba cikin sanyin murya yace "Asma'u
wai meya faru ne? Kinada alak'a da mutumin nan
ne ko kuwa me? Daga ganin mutum sai ki yanke
jiki ki suma, ke da kike da hawan jini, Allah ya
taimaka ma jininki be hau sosaii ba.....Asma'u
magana fa nake miki kin min shiru, kukan nan ba
abinda ze amfana miki dashi fa". Umma kasa
magana tayi kawai sai runtse idonta tayi tana
kuka a hankali, wata Nurse ta shigo sanye da
kayan Nurses ta kalli Abba " Doctor, Dr.Faruk ya
gama dubashi mun samai bandage da komai,
yanzu ma mun canza masa daki, kuma da alama
ya dawo hayyacinsa ma, Abba ya kalleta "okay
nurse Sadik'a, muje d'akin naga jikin nashi"
zumbur Umma ta mik'e tana k'ok'arin binshi,
Abba ya juyo da mamaki " Asma'u ina zaki?", ta
kalleshi "inda zaka je" murmushin tak'aici yayi,
sannan yace" to muje", yana gaba, tana binshi a
baya har suka isa zuwa d'akin mutumin. Yana
kwance idonshi na kan celling sai zubar da
hawaye yake yi, Umma ta k'araso wajen sa a
nutse, tace "ya jiki?" yana had'a ido da ita ya
kauda kansa cikin muryar sa da bata fita yace "
Ma'u yau gizon naki da kike min hadda magana?
Kodai mafarki nakeyi? Ina ne nan?. Ma'u tayi wani
murmushin tak'aici sannan tace "ba mafarki kake
ba, kuma ba gizo nake maka ba, kalle ni da kyau
kagani, nice dai Ma'u mahaifiyar nakashashiya,
nice dai Ma'u wadda ka tsana kake hantara
saboda kawai ta haifa maka d'iya mace kuma nice
dai Ma'u wadda ka wulak'anta daga k'arshe ka
sake ta, nice dai Ma'u tsohuwar Matar azzalumi
MALLAM SULE, ta fashe da kuka.. Abba ya dafa
kafad'arta yace "ya isa haka Asma'u muje gidan ki
d'an huta, anjima ma dawo muyi maganar (ya
kalli Mal Sule, Allah ya k'ara sauk'i) suna k'ok'arin
fita ya kalleta yace, "and inaso ki share
hawayenki", ta kalleshi "toh" sannan ta share
hawayen, Abba yace to muje ta shige suka tafi.
Bayan sun shiga gida Umma kai tsaye dakin ta ta
shige ta kwanta, zuciyarta fal da tunane-tunane
kala-kala, Mubeena ta turo kofar d'akin ta shigo,
a kan gado ta tadda ta tayi tagumi, Mubeena ta
zauna a bakin gadon tace " Ummana wai meya ke
damun ki ? Waye wannan mutumin? Meya miki?
Har ganinsa ya sa ki suma? Umma ta juyo ta kali
Mubeena sannan ta dafa kafad'arta tace "
Mubeena wannan mutumin bakowa bane illa
MAHAIFINKI Mal Sule! , Mubeena ta zaro ido
"mahaifina kuma?" Umma tace " tabbas"
Mubeena ta d'an yi jim sannan ta tashi da sauri
ta nufi d'akinta, tana zuwa ta haye kan gado ta
fashe da kuka, a daren rannar kuwa gabad'ayan
daga ita har Umma kasa runtsawa sukayi.
Washegari........ Da sassafe suka tashi suka shirya
gabad'aya 'yan gidan suka d'unguma suka tafi
asibitin Abba, Mubeena cike da d'okin taje taga
wannan babanta da baya santa. A kwance suka
tadda shi, yau ma kansa na kan celling sai
hawaye yake, daga ganin bayan damuwar dake
tatare dashi akwai zafin ciwo ma, yana kallonsu
ya kauda kai , Mubeena ta k'araso wajenshi da
sauri dan ya bata tausayi sosai, bakin gadon shi
taje ta zauna cikin sanyin murya tace "Baba ya
jiki??? *****ku yi hak'uri na rashin jina da kukayi
kwana biyu, wayata ce ta sami matsala shiyasa,
Nagode.***
[12:38AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
[145]-[150]
©MISS HAFCY
®NWA
Ya juyo cike da mamaki, cikin muryarsa da bata
fita yace "Allahu Akbar, Alhamdulilah ashe akwai
rannar da nima zanji d'an ko 'yar dana haifa ta
kirani da Baba?" Mubeena tace " ai dama can
kane bakso kaji ba da'ace kaso kaji da baka
wulak'antani nida mahaifiyata ba" ya kauda kansa
"hak'ika nayi kuskure babba na kasance mutum
mara godiyar Allah, dan Adam butulu, ku yafe
min dan Allah" ya fashe da kuka.
Mubeena ta runtse ido sai hawaye ta kalleshi "ai
saika fara nemin gafarar Allah domin Allah
gafurur rahim ne" Abba yace "Mal ya jiki?" Mal
Sule yace "jiki da sauk'i".
Mal Sule yace " ni naga rayuwa, naga sakayata,
Allah yaban 'ya mace amma fir nak'i gode masa
sai ma sab'o dana dinga yi kala-kala, ya kalli
Umma datayi shiru tana sauraransa, Bayan
rabuwar mu dake, a k'auye duk inda na nemi
aura ba'a bani, saboda abinda na aikata ya baza
gari sosaii mutane sai suke kyamar hadda jini
dani,,, rannar sai na yanke shawarar komawa
birni wajen yayana Bashir, anan ya bani kudi da
d'an dama yace naje na ja jari, naje na sami d'an
k'aramin gida me d'aki biyu da bandaki na bud'e
shagon kayan masarufi na sami mata na aura,
amma shiru ba haihuwa data gaji tayi tafiyar ta, a
tak'aice dai wallahi sai dana auri mata sunkai
biyar(5) ciki harda masu ciki guda biyu2, wai dan
duk su haifi d'an a gidana na rene shi ya zama
d'ana, amma abin mamaki a cikinsu ba wadda ta
tab'a haifar cikin a raye a mace suke haifosu.
Daga baya auren ya gagara jari na ya cinye na
zamonto banda komai,na koma gidan yayan nawa
shima na tadda basa k'asar ma gabadaya,,,
rayuwa tamin zafi abincin da zanci gagara ta
yake, tun daga nan na fara nadamar abinda na
aikata, nakuma tabbatar da cewa hak'in ku ne ku
da Iya yake bina, na taho neman ku shine mota
ta kad'e ni kuka taimakeni" ya fashe da kuka.
Gabad'ayansu jikinsu yayi sanyi, kowa yayi shiru
Mubeena cema ke kuka a hankali, ya kalli
Mubeena 'yata ki yafeni, ki yafeni dan Allah kar
na mutu da hakk'in ki akaina na cuce ki, na cutar
da rayuwarki,(ya juya wajen Unma) Ma'u kema ki
yafeni dan Allah, a lokacin da kike ce akwai
rannar da zanyi nadama bazata min amfani ba
ban yadda ba, sai gashi yau ga rannar nan tazo,
ki yafeni, kuma dan Allah ki kaini wajen Iyata
itama na rok'i gafararta, kar na mutu da hak'inta
akaina"
Umma tana hawaye tace "bakomai na yafe maka ,
Allah ya yafe mana baki d'aya, Amma Iya babu,
Allah yai mata rasuwa, sai dai kan ta rasu tace ta
yafe maka" ya fashe da kuka " wayyo Allah na iya
ta rasu? Innalalhi waina ilaihi raju'un KAICONA!
Na cuci kaina,, Umma tace "ga dai 'yarka kamar
yadda na fad"a maka zata zamanto abar
kwatance kuma duniya ta santa akan abin alheri
to Allah yayi, yanzu duk shafukan jaridar daka
duba zaka labarinta, gidan rediyo dana talabijin
dama..." Abba ya katse ta "ya isa haka ! Me ya
kawo wannan zancen kuma, komai ya wuce
mubar maida hannun agogo baya".
Ya kwantar da murya yace "kuyi hak'uri kai kuma
tunda sun yafe maka har Iyan ma ta yafe maka,
ka gode Allah,k a kuma cigaba da nemi gafarar a
wajen Allah domin kamar yadda 'yarka ta fad'a
ma Allah gafurur rahim ne"" Allah ya sawwak'e,
mu bari mu tafi,(ya kallesu)"kuzo mu tafi"
Mubeena ta share hawayenta tace "ni ku barni
anan zanyi jinyarsa" da mamaki suka juyo "me?"
Tace "cewa nayi zanyi jinyarsa" Mal Sule yayi tari
"a'ah zan zauna nan ma nagode d'iyar kirki, Allah
ya shi miki albarka, tace "amin, amma zan zauna
d'in anan,,da kyar ya rok'e ta ta hak'ura tace
zata bisu. Da kuma alk'warin kullum zasu dinga
zuwa suna duba shi.
Yau kimanin kwana biyar5 kenan da ganin Mal
Sule, a ranna ta biyar d'in kuwa Allah yamai
cikawa sun sha kuka sosaii da sosaii mussaman
ma Mubeena data rasa Uba, haka dai suka sha
kukansu su gaji suka daina. Tare dayi masa
addu'oi kala-kala.
**********
Admission d'in Mubeena ya fito nan da wata
d'aya zata tafi America.
Abba ne zaune a falonsa gefensa Ummi ce tana
karanta jarida,,ya d'an yi jim sannan yace "nikuwa
Hadiza wata shawara na yanke, amma bansani ba
ko ke zata miki,, Ummi tace "tame fa?" Abba
yayi gyran murya sannan yace
"Akan yarinyar nan ne Mubeena kinsan admission
d'inta ya fito nan da wata d'aya1 zata tafi
America gashi shekara biyu 2 ne sai nake ganin
kamar be dace mu barta ta tafi ba muharami
ba,kuma kinsan ta isa aure shekara sha takwas da
d'ori ai ba kad'an bane, dan haka na yanke wata
shawara......
Ummi ta gyra zama tace "gaskiya ne wannan,
amma shawarar me ka yanke?" Abba yayi
murmushi " ina so zan had'a ta aure da Abdul-
Hafeez ne!, kinga dama already an sa rannar
Husna sai a had'a a d'aura auren tare! Ummi da
mamaki tace "gaskiya ne, amma a gaskiya sai a
kira su yaran aji ta bakinsu in sun amince falilahil
hamd in basu amice ba kuma shikenan sai asan
abin yi"
Abba yace " dad'i na dake garaje baki tsaya kinji
me zance ba kin tari numfashina, dama ya za'a yi
na d"aura musu aure ba amincewarsu? Kuma
bazan musu auren dole ba, yanzu dai je ki kira
min 'yar uwarki Asma'u itama muji ta bakinta,
Ummi a sanyaye ta nufi part d'in Umma ta kira
ta suka nufo wajen Abba a jere.
Abba yayi mata(Umma) bayanin abin itama tayi
mamaki sosaii dan a ganinta Abdul ya wuce ajin
Mubeena amma dai sai tacewa Abba Allah zab'a
mafi alheri yaji dad'i sosaii.
Abba dakansa ya d'au waya ya kira Ya Abdul ya
kuma ce masa yazo yana son ganinsa, yace gashi
nan, sannan ya sa Umma ta kira Mubeena suka
zauna suna jiran Ya Abdul. Mubeena cike da
fargabar ko wani laifin ta aikata..
Be dad'e ba ya shigo sanye da shadar light bleu,
Abba ya kalleshi " kai dai Abdul Hafeez har yanzu
baka girma ba?, kasa shadda manyan kayanmu
na hausawa, kuma kana yawo kai a haka ba hula,
ina hularka? Ya sosa k'eya "tana daki wallahi ina
sauri ne dats y kaga na barta, yi hak'uri", Abba
yace bakomai zauna nan muyi magana.
Ya zauna, sai a lokacin ya lura da Mubeena dake
kan kujera kanta a sunkuye kallo d'aya yayi mata
ya kauda kai.
Abba ya fad'a musu hukuncin da ya yanke,dum!
Gabansu ya fad'i gabad'aya, Mubeena kuwa
murza idonta anya ba mafarki nake ba? Ta fad'a
a zuciyarta, shikuwa Ya Abdul suman zaune yayi
yama kasa magana, Abba dayaji shirun yayi yawa
yace "ya dai? Ya kukayi shiru?" Ya Abdul ya dage
yace " Allah ya zab'a mafi alheri" Abba yace
"Amin Alhamdulilah" kefa? Mubeena tace "Allah
zab'a mafi alheri na amince, Abba yaji dad'i
sosaii ya kuma cewa su Umma su fara shirya
shiryen biki.
Abba ne ya sanar da Ya Ameen shima yaji dad'i
sosaii dan dama ya dad'e yana wannan tunanin,
ya fad'a wa Faty matarsa dake d'auke da ciki
itama tayi murna sosaii, ta kuma musu fatan
alheri.
Umma ta sanar da daginta, suma sukayi fatan
alheri, dagin marigayi kuwa dama basan nan,
kuma dama bama su wani saba ba dan in ta
gansu yanzu ma bazata gane su ba.
Shirye shiryen biki akeyi sosaii, amare kuwa suna
ta shan gyra kala-kala Ya Nana da itama ke dauke
da ciki itama ta taimaka musu da shawarari da
magunguna da sauransu.
Abin mamaki kuwa Mubeena da Ya Abdul har hira
sukeyi sun fahimci junasu ba laifi.
◆◆RANNA BATA K'ARYA SAI DAI UWAR D"IYA
TA JI KUNYA◆◆
A yau ne aka d'aura auren ABDUL HAFIZ
MUHAMMAD AMEEN DA AISHATUL MUBEENA
M. AMEEN akan sadaki dubu hamsin (50) da kuma
na Husna Muhammad Amin da angonta Al'amin
Jafaru akan sadaki dubu arba'in(40) .mutane
dayawa sun hallaci d'aurin auren.
Bayan d'aurin aure ba ai wata bidi'a ba yini kawai
akayi sai kuma kamu kan d'aurin auren , dagin su
Al'amin ne ma suka shirya dinner suka gayyaci
amaryarsu Husna taci kwaliyarta taje kuwa.
Mubeena kuwa kallo d'aya zaka mata kasan tana
farin ciki, dan ta godewa Allah ba adadi saboda
cika mata burinta da yayi. Ta kuma yiwa babanta
da kuma kakarta addu'a sosaii. Sannan a kullum
addu'ar tashine Allah ya basu zaman lafiya mai
d'orewa..
An kai amarya Husna gidan mijinta sun sha kuka
rabuwa da gida, Mubeena kuwa dama tana gida
sai nan da kwana biyar (5) zasu lula k'asar
America shima Ya Abdul cikin ikon Allah kamfanin
dayake aiki suka tura shi wani course can America
hakan yazo daidai, abinsu dagwas!
Yau zasu tafi k'asar America kukan wajen
Mubeena kuwa kamar me, dan a daren rannar
kasa bacci tayi tana tunanin rabuwa da iyayen
nata, amma ba yadda ta iya, idanuwanta kuwa
duk sun kumbura saboda kuka..
Mr& Mrs Ameen, Abba, Umma, Ummi, Amir da
Ya Nana sune suka musu rakiya zuwa airport,, da
kyar aka banbareta daga jikin Umma, Umma na
kuka itama tanayi haka suka rabu, Ya Abdul ya
kama hannunta suka shige jirgi abinsu, nikuwa ina
binsu a baya har muka shiga jirgi, jirgi ya lula
damu sai k'asar America.....
[12:39AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
©MISS HAFCY
®NWA
[150]-[155]
Bayan sun sauka ne motar kamfanin su Ya Abdul
tazo ta d'auke su ta kaisu masaukinsu, inda zasu
zauna , gida ne d'an k'arami falo sai d'akuna gida
biyu d'aya babba d'aya k'arami sai kuma tiolet da
kitchen da dinning,,,Mubeena ce ta kai kayan
d'akin
dan gida baya bukatar gyra saboda ko ina tsaf
dashi. Yayin da shi kuma Ya Abdul ya fita nearby
restaurant dan yayo musu take'away ya dawo , a
lokacin har ta fito daga wanka ma tana kan kafet
tana sallah , gannin haka yasa ya aje abincin akan
dinning shima ya shiga band'akin d'ayan dakin
dan
yin wanka da sallah.
Ya d'an jima sannan ya fito sanyen da wando 3
quater iya gwiwa da riga armless, ya tadda ta
tana
kan kujera tana dana laptop din dake kan centre
table,, ya zauna kusa da ita, ta juyo tace "sannu
da
fitowa Yaya" yayi d'an murmushi "yauwa
Mubeena
ya gajiyarmu?" Tayi murmushi "aiy ta tafi" yace "i
see, me kike yi a system ne? Naga alama dai baki
gaji ba" Tayi murmushi "A'ah Yaya kawai dai naga
ba abinda zanyi ne shine nake duba school din da
yanayinta, ashe ma next week ne za'a fara
registration" yace "Gud Allah ya kaimu" tayi
murmushi "Amin".
Ya dauko musu abincin suka ci, sannan Mubeena
ta
shige d'aki dan shirya kayanta a wadirop
(wardrob
e) ta barshi nan yana kallo a Talabijin(TV).
Da daddare ma fita yayi yaje ya siyo su pizza,
shawarma, da roasted chicken, sannan da su ice
cream, lemuka da yagut(yaghurt) ya shiga d'akin
nata.
Tana zaune akan dressing mirrow, tana taje
yalwatacen gashinta, rigar bacci ce a jikinta iya
gwiwa pink, tana da d'an kauri ba sharara ba, ya
tsaya kawai yana kallonta, ita bata san ma yanayi
ba, sai data duba mirrow din da kyau ta ganshi
tsaye kunya ta kama ta sosaii tayi saurin d'auko
hijab d'inta dake kan gado tasa, dariya abin ya
bashi ma, yayi murmushinsa me ban shawa'a
sannan
a zauna kan carpet din d'akin had'e da aje ledojin
hannunsa.
Cikin sanyin murya yace "Mubeena" da sauri tace
na'am, yace "sakko muci" ta k'araso wajen sannan
ta duba ledodin, murmushi tayi "nidai shawarman
nan zanci kawai na sha ice cream ya isheni, cuz
dazu
na ci abinci" yace "okay Gud." Ya d'an yi jim
kamar zece wani abu can dai ya fasa ya aje mata
ice cream d'in da shawarma d"aya sannan ya
kwashi sauran ledodin ya tafi d'aya d'akin ya
zauna
ya cika cikinsa sannan ya koma falo ya d"an yi
kallo
dagabaya ya koma d'aki ya kwanta abinshi, itama
kuwa rufe k'ofar ta tayi tayi kwanciyarta. Sai
daya dad'e akan gado yanata tunane-tunane
kala-
kala sannan daga baya bacci b'arawo ya d'auke
shi,,, Asuba ta gari ango mijin amarya
Washegari da safe ta fito sanyen doguwar riga
red
da adon golden tayi bala'in kyau, da niyyar gyra
gidan , da mamakin ta sai ta tadda wata mata
tana
shara da alama dai mai aiki ce, suka gaisa anan
take fad'a mana cewa ita mai aiki ce sunanta Kim
dayake matar nada faran faran nan da nan suka
saba suna hira kamar dama can sun san juna.
Tana gama gyran sukayi salama ta tafi, ita kuwa
Mubeena wayarta ta d'auko ta sa number Husna
ta
kira ta, bugu uku ta d'auka, Mubeena tayi dariya
"
'yar rainin hankali bakya neman mutane koh?"
Husna tayi dariya " ke waketa ta neman mutane
inata mijina, ai in gaya miki aure da d'adi wallahi"
Mubeena ta bud'e baki "lallai Husna ko kunya
bakyaji kike fad'an haka,ko kin manta ni surukar
kice? Ta fad'a da zolaya,, Husna ta tuntsure da
dariya " yo wayake ta surika a wannan harkar?
Yauwa ban labari nasan Yayl Abdul daga gani
baze
yi sanya ba, wai shin ya kuka k'are ne?" Mubeena
tayi tsaki 'ke ni banda lokacin ki, ki gaida mijin
naki sai anjima" Husna tace "zeji yanzu ma jira na
yake a d'aki" Mubeena ta kashe wayar tana dariya
tayi mamaki sosaii yadda aure ya canza Husna
matar da ko irin maganar akayi sai ta nuna bata
san komai ba bataso ashe dai ashe dai.
Yau kimanin sati d'aya kenan da zuwansu amma
kuma har yanzu ba abunda ya shiga tsakinunsu
sai
dai su ci abinci wani sa'in tare suyi kallo amma
dare nayi kowa ze tafi d'aki ya kwanta abinshi.
Yau Mubeena ta fara zuwa makarantarsu tunda
suka ganta nakashashiya suke ji da ita, dan su
basa
wulak'anta irinsu sai ka sonsu dasuke yi, hakan ba
k'aramin dad'i ya mata dan ganin yadda mutane
ke
nan-nan da ita kamar wata 'yar sarki ko shugaban
k'asa,, tayi k'awaye sosaii mata malamansu ma
suna shiri sosaii da su.
Ya Abdul shima ya fara zuwa wajen aikinsu, tare
suke fita wani sa'in ma tare suke dawowa,
wataran
inda time itace ke musu abinci wani lokacin kuma
sai dai su siyo ko kuma suje can wajen cin abincin
su
siyo.
Yau ma kamar kullum bayan sallar isha, Ya Abdul
yana zaune a falo yana kallon wani series film,
Mubeena ta shigo falon sanyen da wata doguwar
riga wadda ta kama ta ta kuma bayyanar da surar
jikinta riga ta k'arbi jikinta sosaii, tunda ta shigo
yake kallonta har ta lura ta sunkuyar da kanta
cike
da kunya, a haka ta k'araso har kujera mai facing
dinshi ta zauna ta fara kallo abinta, shikuwa dena
kallon yayi ya tsura mata ido cike da sha'awa
data
lura kallon yayi yawa sai kawai ta tashi ta nufi
d'aki tayi kwanciyarta dan bazata iya jura kallon
dayake mata ba,, shikuwa be ji dad'in tafiyar data
yi ba, ya tashi ya kashe TV din ya nufi d'akinta
har
ze shiga sai wata zuciyar tace masa "aa" jiki ba
kwari ya koma d'akinsa ya kwanta.
Yau Friday, a gajiye ta dawo daga school wajen
k'arfe biyar da rabi 5:30 gashi ba laifi an d'an yi
zafin rana kad'an tana zuwa ta shige d'aki a kan
gado ta cire kayanta, ta janyo towel ta shige
band'aki dan ta watsa ruwa, bayan tayi wanka ta
fito sanye da towel iya gwiwa ta tsaye a bakin
gado tana taje gashinta, dai-dai shigowar Ya
Abdul
kenan ya tsura mata ido yana kallonta nan take
yaji sha'awarta ta mamayeshi,ita kuwa sunkuyawa
tayi zata d'auki ko mayafi ne ta rufa ai kuwa
towel
ya sauko k'asa ta zaro ido ganinta tsurara
haihiwar
uwarta a gaban Ya Abdul, da sauri ta sunkuya
zata
d'auka da sauri shima ya sa hannun ya janye da
towel d'in, rungume tayi nan ya fara kissing dinta
ta koina ita kuwa sai turjewa take tana bashi
hak'uri, nan dai labari ya canza nidai rufe musu
d'akin nayi na fito abina.
A rannar dai ta sha wahala sosaii dan a rannar
suka
zama cikakun ma'aurata, sai shimata albarka yake
yana kuma jin wani sabon santa a zuciyarsa itama
kuma haka.
Kwanci tashi sunkai shekara d'aya 1 a America
suna
zauna zama cike da so da kuma kyautatawa juna,
sai dai 'yan abun da ba'a rasa ba, dan hausawa
sunce zo mu zauna tamkar zo mu sab'a ne...
Yau Mubeena ta tashi da wani zazzab'i me zafin
gaske ga amai datake ta kwararawa tun safe Ya
Abdul kuwa duk ya rud'e ganin ta a wannan hali,,
d'aukanta yayi sukutum ya kirawo drivern motar
kamfaninsu ya sata a ciki suka nufi asibiti bayan
an
duba ta anan ne aka tabbatar da cewa ciki gareta
har na wata biyu 2 zokaga murna wajensu a
rannar
sunyi kwanan farin ciki. Dan dama sun daidai
suna
tsumaye da har sun fara damuwa ma ganin
Mubeena shekara d'aya amma har yanzu shiru ba
ciki, dan ita Husna ma har ta haifi d'anta
santalele
namiji yaci sunan baban mijinta. Basu je gida ba
kuwa har yanzu Ummi ce tace subari sai ta haihu
sai su dawo.
Kullum tana samun kulawa wajen mijinta tana
motsawa zece"meya faru?" Ita kuwa saitayi
murmushi tace bakomai
Yau Mubeena ta tashi da ciwon nak'uda cikin
dare a
rude ya kira drivern kamfaninsu yazo ya kaisu
asibitin da take awo,, aka shige da ita d'akin
haihuwa ba ta dad'e ba kuwa cikin ikon Allah ya
sulub'o 'yayanta guda biyu maza.
Aka sanar da uban 'yaya murna a wajensa kamar
me, sai sumbatun murna yake yana kuma
mamakin
wai yau shine da 'yaya har guda biyu,, nan da nan
aka sanar dasu Umma suma murna ba'a
magana...Ya Abdul ya shirya musu tafiya kwana
biyu da haihuwarsu suka dawo nan gida Naija.
Yara tubarkalah masha Allah masu kamada Ya
Abdul sak, kullum suda Mum d'insu suna samun
kula
sosaii sai bulbul suke abinsu.
Ran suna yara suka ci suna Sulaiman da
Muhammad
anace musu SAHAL DA SUHAIL,, ansha shagali
sosaii
anci ansha don rannar murna ce, anyi rabo
kayayaki
ba'a magana,, kowa ya watse ciki da murna da
kuma fatan Allah ya raya mana 'yayan mu Suhail
da Sahal.
Share
Comment as:
Publish Preview
No comments:
Post a Comment
MissHafcy
View my complete profile
About Me
► 2017 (16)
▼ 2016 (34)
► November (1)
▼ October (33)
WELCOME
ASMAUL HUSNA 6
ASMA'UL~HUSNA
ASMAUL~HUSNA 4
ASMAUL~HUSNA 3
ASMAUL HUSNA 2
ASMAUL HUSNA
AISHATUL MUBEENA 155-160
AISHATUL MUBEENA 145-155
AISHATUL MUBEENA 110-140
AISHATUL MUBEENA 85-105
AISHATUL MUBEENA 60-80
AISHATUL MUBEENA 45-60
AISHATUL MUBEENA 30-40
AISHATUL MUBEENA 20-30
AISHATUL MUBEENA 1-20
WANI HANIN END!
WANI HANIN 26-27
WANI HANIN 24-25
WANI HANIN 22-23
WANI HANIN 20-21
WANI HANIN 19-20
WANI HANIN 15,16,17&18
WANIN HANIN 12,13,&14
WANI HANIN 11
WANI HANIN 9&10
WANI HANIN 7&8
WANI HANIN 5&6
WANI HANIN 3&4
WANI HANIN 2
WANI HANIN 1
....
WANI HANIN
Blog Archive
Miss_Hafcy. Watermark theme. Powered by Blogger .
More
AISHATUL MUBEENA 155-160
◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆
©MISS HAFCY
®NWA
[155]-[160].
◆◆ BAYAN SHEKARA BIYU◆◆
Wani hadad'en falo na shigo falon babba ne
sannan an k'awata shi da zane-zane kuwa kala-
kala na paintings sai kamshi falon yake.
A zaune na tadda Mubeena ta k'ara kyau ta k'ara
k'iba ta k'ara fari,ta zama cikakiyar hajiya, tana
zaune Sahal na hannunta shima ya k'ara girma
kamaninsa da mahiafinsa sun k'ara fitowa, tana
bashi abincin yara( Cereal), yayin da shi kuma
Suhail na gefe akan wani mashin na wasan yara
yana ta gwarancinsa, wata yarinya ta fito daga
d'aki yarinyar tana bala'in kama da Ya Ameen,
ganinta yasa Sahal da Suhali suka fara murna
suna wangale baki, ta k'arso wajen Suhail dake
kan keke, ta fara masa wasa, sannan ta kalli
Mubeena " Anty Mubeena kawo na had"a masa
cereal din na bashi " Mubeena tayi murmushi "
zaki iya kuwa Namesy(dayake sunan Mubeena Ya
Ameen ya samata) tace zan iya mana ina bawa
Maama(k'anwarta) Mubeena tace "To wataran kya
bashi shi na fara bawa kan na bawa Sahal anjima
in yaji yunwa kya bashi" taui murmushi "yauwa
anty Mubeena".
Ya Abdul ya shigo shima ya k'ara zama babban
mutum ya k'ara kyau sosaii kana ganinshi kaga
wanda naira ta zauna masa,,, sanye da shadda
golden yayi kyau sosaii, ya kalli Mubeena "Oya
Momin twins time ya kusa yi fa mu kad'ai ake jira
" tayi murmushi "sorry Dadyn twins kaga ni a
shirye nake, Baby Sahal naga yana kuka da alama
yunwa yake ji shine na had'a masa cereal na
bashi, (ta mik'a masa shi) karbe shi na sa mayafi
na, ya k'arbe shi yana masa wasa shikuma yana
dariya, sannan yaja hannun Little Mubeena sukayi
wajen mota ita kuma Mubeena ta d'auko mayafi
da jakarta sannan ta d'auki Baby Sahal suka nufi
wajen mota.
Basu zame ko ina ba sai wata katafariyar
makaranata koyon zane-zane wadda Aishatul
Mubeena ta gina kuma a yau ne za'ayi taron
bud'e makarantar.
Isarsu keda wuya suka yi parking motarsu a filin
parking sannan suka iso wajan da'aka tanada dan
bak'i, mutane ancika kowa jiransu yake family din
su gabad'aya suna can suna jiransu, sukai ta
gasawa da mutane anata Allah sanya alheri.
A kofar makarantar aka sanya wata igiya me
bala'in kyau tasha ado aka zagaye gate din data
ita, Mubeena rik'e da Suhail da Ya Abdul rik'e da
Sahal suka k'araso bakin gate din yayin da Ya
Ameen da Little Mubeena suka mik'a musu wani
dan faranti d'auke da almakashi me shegen kyau,
suka k'arba suna murmushi yayin da yan jarida
suka kara matsowa dan daukan hotuna da
rahoto, Mubeena ta karb'i almakashin Ya Abdul
ya dafa hannunta suka kamo hannun 'yayan nasu
suka dora akai mutanen dake gurin suka k'irga
d'aya har zuwa uku sannan suka yanka igiyar, nan
aka d'au tafi suka shiga cikin makarantar Su
Abba suka bi bayansu sauran mutanen ma haka,
dan ganin makarantar.
Makarantar kuwa Masha Allah tayi kyau gashi
komai da'ake bukata akwae, bayan mutane sun
zagaya makarantar sukaita sa albarka anan ne
kuma Mubeena tayi jawabi akan makarantar a
karshe tace duk wani polio victim wato mai cutar
shan inna dayake sha'awar harkar zane to ze
shigo kyauta ne! Bata bukatar ko sisi daga wajen
masu cutar polio nan mutane suka dinga tafawa
suna shi mata albarka, daga baya aka koma akaci
akasha sannan aka watse. Little Mubeena tabi
iyayenta suka koma gida dan gobe Monday akwai
school.
Suna cikin mota kan hanyar dawowarsu gida,
Mubeena ta kalli Ya Abdul dake tuka motar tace "
Baban twins nikuwa zaka gane gidan su Yusran
nan kuwa daka tab'a kai mu da d'adewa?" Ya
d'an yi jim sannan yace "eh toh bari mu gwada"
ya juya kan motarsa sannan yayi hanyar gida, sun
sha wahala kam kan sun gane gidan sai da
taimakon kwatance, abin mamaki kuma suka
tadda gidan ya canza ya k'ara kyau an canza
fasalin gidan ma, Mubeena na rik'e da Sahal Ya
Abdul kuma na rik'e da Suhail, Mubeena ta fara
shiga gidan shikuma Ya Abdul ya tsaya a kofar.
Da sallama Mubeena ta shiga gidan, sai datayi
salama kusan biyu sannan aka amsa, Maman ta
fito sanye da doguwar riga tana ganin Mubeena
ta fad'ad'a fara'arta da sauri ta k'araso ta
rungume Mubeena da murnarta, sannan ta k'arbi
Sahal " mashaAllah, shigo mana Mubeena sannnu
da zuwa", Mubeena tace yauwa sannan suka shiga
wadatacen falon gidan, Maman ta karbi Sahal
tana tamai wasa shikuma yana dariya, Maman
tace "sannu ke kad'ai ke tafe?" Mubeena tace
"a'ah da mai gidana suna kofar gida" Maman tace
"yo kuma kya barshi nan tsaye ya shigo mana,
bari na lek'a nace ya shigo" Mubeena tayi
murmushi toh, Maman ta lak'e suka gaisa sannan
tace ya shigo, ta kawo musu ruwa da lemo
sannan ta dawo ta zauna itama, tana rik'e dasu
Suhail sai wasa take musu " ikon Allah Mubeena
ashe har kinyi aure hadda 'yaya bamu sani ba"
Mubeena tayi murmushi " eh wallahi kinsan
sha'anin ne kuma ma kinga bayan biki mukaje can
America mu yi shekaru kana muka dawo bamu
dad'e da dawo bama" Mamn tace " Allah sarki
Allah ya taimaka, naji dadin zuwan ku wallahi," ,
Mubeena tace "mungode, nikuwa ina Yusrah
tunda muka shigo ban ganta ba" Maman tayi
murmushi " tana can cafe d'insu itada k'anina
Bello" Mubeena da mamaki tace "cafe?" Maman
ta cigaba "aiy bayan zuwan ku d'inan kun mana
abin alheri k'anina yayi amfani da kudin wajen yin
harkar makarantarsa to dama Computer science
yake karanta kuma yana shekarar k'arshe lokacin,
to cikin ikon Allah sai ya gano cewa itama Yusrah
akwai basira a fagen computer abu kamar wasa
in ya dauko ze koya mata cikin ikon Allah sai
yaga ma wani wajen ma tafi shi kwarewa ,to
shine ya bada shawarar yana so ya bud'e cafe
mukai cikwi cikwi da d'an abinda ya rage mana
muka siyar akasai komai da'ake buk'ata ya bude
shagon yanzu cikin ikon Allah shagon yana nan ya
bunkasa, kuma sannan k'anin nawa ya samu aiki a
wani babban kamfani,, har yayi aure ma, yana
nan da matarsa hada d'a, ya gyra mana wannan
gida nima yaban jari yanzu ina harkar bussiness
na kaya ina sa ran ma a wannan shekarar zanje
Dubai dan na saro kayan da kaina na kuma bud'e
shagon, kunji ikon Allah koh?
Mubeena tayi Murmushi" Alhamdulilah, amma
gaskiya naji d'adi sosaii, Allah shine abin godiya,
dama ance mahakurci mawadaci, kinga da bakuje
kun k'ask'antar da kanku kunyi bara ba, Allah ya
hore muku ya bud'a muku har kuma nasan kuna
taimakon wasu, a gaskiya naji dadi Allah ya sanya
alheri yasa albarka a ciki, dukansu suka ce "Amin"
Ya abdul shima yayi murna kwarai da jin hakan,
Mubeena tace "ina cafe d'in yake ?muje inga
kawartawa" Maman tace "to muje in raka ku" suka
fito a tare dan zuwa cafe din. A kan hanya ne
Mubeena ta bata labari makarantar ta data bud"e
yau, ba k'aramin dadi Maman taji ba ta kuma yi
alkwarin zata ziyarci makaranta gobe.
Sun d"an yi 'yar tafiya sannan suka isa wajen
Katafaren shago ne babba shaguna uku ne aka
had'e suka zama guda d'aya, asaman shagon an
rubuta " YUSBELL INTERNET CAFE" suka shiga
wajen ma'aikatan se aiki suke wajen fal da mutane
customer's can ciki wani ya nuna musu yace
Hajiyar tana can, suka k'arasa wajen.
A kan wheel chair d'inta suka tadda ta tana dan
system din dake gaban ta, ta k'ara cikowa ba
laifi, ta zama 'yan mata, tana juyowa suka had'a
ido da Mubeena ta saki murmushi, farin ciki ya
bayyana a fuskarta k'arara, da mamaki tace
"kamar Aunty Mubeena nake gani ko me kama da
itace?" Mubeena tayi murmushi had'e da dafa ta
"itace Yusra" Yusra tayi murmushi "sannu da
zuwa Anty, nayi murna kwarai dana had'u da
dake, ya bayan saduwa, nan suka fara hira
Sun dad'e suna hira kana Mubeena ta bata
shawarari sannan sukayi exchanging contacts, da
kuma alkwarin zasu dinga ziyarta juna jefi-jefi,
sukayi salama su Mubeena suka koma gida.
◆◆◆◆◆◆◆
Wasa-wasa dai makarnata tana ta samun budi
makaranta ta sharara sosaii mussaman ma
saboda k'wararun malaman da Mubeena da samo
take kuma biyansu albashi me tsoka, itama kanta
tana koyarwa in ta samu lokaci. Wani abin
sha'awa shine yadda polio victims wato masu
cutar shan Inna suke makaranta kusan kaso biyu 2
a cikin biyar 5 sune, wannan ba k'aramin dad"i
yake sa Mubeena ba , saboda ita dama mussaman
dan su ta bud'e makarantar.
Ya Abdul shima yana ta samun cigaba da
d'aukaka uwa uba ga mata ta gari daya samu,
yanzu shima ya bud'e kamfaninsa na kansa, kudi
suna ta shigo mai ya zama babban alhaji haddda
su tumbi irin na manyan masu kud'i yayi(Lol).
Mubeena ce zaune a d'akinsu Suhail bayan ta
gama saka musu kayan bacci kowanensu ta
kwantar dashi a gadonshi, ta tofe su da add'ua
sannan ta musu good nyt ta kashe musu fitila ta
kulo d'akin.
Kai tsaye d'akinta ta shige ta watsa ruwa ta shafe
jikinta da mai da turaruruka masu kamshi, ta taje
kanta ta raba shi gida biyu ta d"auko wata
arniyar rigar bacci da ita gwanda babu ta saka
tayi brush ta kuskure bakinta da mouthwash
sannan ta d'auko wani cewing gum me k'amshi
pineapple ta wurga a bakinta tana taunawa a
hankali, ta k'ara feshe jikinta da turare sannan ta
kulo d'akin ta nufi d'akin Ya Abdul.
A kwance ta taddda shi a kan gado ganin ta
shigo d'akin yayi murmushi yayi ta karaso tana
rangwada sannan ta kwanta gefensa ya jayota
jikinsa "ya akai ne Hun?" Tayi murmushi
"bakomai" ya kad'a kai sannan yace " i Luvv you
soo much my dear wife, ur my everything," ta
cakule shi a kumatu sannan tace "Me too my
man,my husby, my heart desire, i soo much love
you yaya nah, Allah ya barmu tare" yace "amin"
had'e kashe musu wutar d'akin hakan yasa nima
na fito nace:
ALHAMDULILAH!!!
Godiya ta tabbata ga Allah me kowa me komai
da yabani ikon kamala wannan littafi nawa me
suna AISHATUL MUBEENA, tsira da amincin Allah
su tabbata ga shugabmu Annabi muhammad
(swa) da sahabansa da alayensa baki d'aya.
SADAUKAWA: na sadaukar da wannan littafi ga
d'aukancin masu Cutar Shan Inna(POLIO) dake
fad'in duniyar nan musulmai....sannan ina kira da
babbar Murya ga iyaye da su dinga bada 'yayansu
ana musu d'igon rigakafi domin ance prevention
is better dan cure, sannan ina kira ga gwamnati
(Duk da suna iya bakin k'ok'arinu) da sauran masu
hannu da shuni dake wannn k'asa tamu da su
dinga taimakwa talakawa wad'anda wannan cuta
ta riga ta lahanta,
Alhamdulilah tunda yanzu an cire kasar mu
Nigeria daga sahun k'asashen dasuke fama da
wannan cuta amma duk da haka akwai mutanen
da already wannan cuta ta riga ta musu illa a
jikinsu, kuma basu da gata talakawane, ga kuma
rashin sana'a sune a k'arshe suke k'arewa da
bara-barece akan hanya saboda basu da hali basu
da yadda zasuyi su ciyar da kansu balle har su
samu suyi ilimi, ba sana'a sannan kuma ba kudi,
kuma a cikinsu ana samun dayawa masu baiwa
daban-daban(talent) amma saboda kulawa dasu
da ba'a ayi ba'a gano hakan, Allah ya bamu
yadda zamu iya ya k'arawa gawamnati dama
sauran masu hannu da shuni damar taimaka musu
Amin. Sannan wanda wannan cuta ta riga ta
lahanta ina me jajanta musu da iyayensu Allah ya
basu hak'uri jurewa kuma su sani bawai dan Allah
baya san su bane ya dora musu wannan cuta A'A
kawai dai kowanne d'an adam da abinda Allah
yake jarabtarshi dan ya gwada imaninsa, to su
jarabtar tasu kenan,, Allah ya bamu ikon cin
jarabawar daya d'ora mana Amin...
Ina godiya ga duk wandada suka bi wannan littafi
tun daga farkonsa har zuwa k'arashe duk da
tashon lokacin dana dauka kan na gama shi, ba
abinda zance sai Allah yabar so da kauna da
kuma d'akon zumunci.Amin
Domin tsokaci ko kuma gyra kawai- 09097136605
Anan Ni Miss Hafcy nakece muku BISSALAM......s
e mu had'u a sabon littafina nan gaba
Nagode da kulawarku, LOVE YOU ALL
Sh
Comment as:
Publish Preview
No comments:

You might also like