Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 432

Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira)

‘YAR GATA CE!


BY MIEMIEBEE Page 01

_Gidan Alhaji ISMA’IL YUSOUF Unguwar Dutsen Tanshi, Bauchi, Bauchi


State._

Matsakaicin gida ne ba yabo ba fallasa, na d’an kasuwa meh arziki dai-dai ba


irin na hauka d’innan ba, arzikin sa beyi yawa ba be kuma kasa ba. Kalan arzikin
Alhj Isma’il Yusouf ake kira da middle class earners. Gidan nasa wanda ya k’unshi
sashi biyu, k’arami na bayan ya kasance BQ. Daga babban sashin wata ‘yar yarinya
chocolate skinned meh k’imanin shekaru goma sha d’aya (11) ce tafito a gurguje ta
nufa kitchen inda ta d’au wani k’warya da magani ciki tafito a hanzarce, tsabagen
saurin da take har tafashashshen maganin na zube mata a hannu amman hakan be hana
mahaifinta k’olla mata kira a fusace daga ciki ba “MARIAM! MARIAM! Wai d’auko
maganin ne har yanzu?! Mschww!” kamar wacce zatayi kuka takaici kwance fal a
fuskarta tace, “gani nan zuwa fa Baba” chan k’asa k’asa tace, “haihuwa sekace hauka
Ya Allah karkasa Mama ta haifi na mac-” bata k’are maganan ba tayi kacib’us da
Baban nata a bakin k’ofa, wani kallo ya galla mata tare da wabje k’waryan maganin
ya nufa ciki da hanzari a yayinda Mariam ta juya tayi d’akinsu da k’anwarta YASMIN.

“Gashi HAFSAH sha kinji? sannu, sannu ko?” Baba wanda ya kasance dark skinned
amman kyakkyawa ajin farko yanada ball eyes da long eyelashes with thick brows,
sajen fuskarsa ya had’e da moderate gemun dayake ajiyewa, ya kasance cikakken na
miji me tsayi dakuma kauri kad’an, sede ba wani babban mutum bane dududu shekarunsa
talatin da takwas (38) ne. Maganar yayi ma fara kyakkyawar matar dake kwance kan
turkey bed dake d’akin. Mace ce me shekaru talatin da d’aya, (31.) A very young and
beautiful woman. Miqe akan gado take tana juyi da tsohon ciki tattare da ita se
nishin nak’uda take duk tabi tayi zufa sede sam yanayinta be hana kyawunta wanda
yasamo asali daga tushen Fulani fitowa ba. Gefenta wata ungozoma ce zaune tana mata
sannu. A sannu a sannu ungozomar tasamu ta d’ura wa Hafsah maganin har a yanzu Baba
na a tsaye kan matarsa hankali tashe yana me addu’a a ransa Allah sa Hafsah ta
sauqa lafiya ta haifo masa santaleliyar ‘ya mace. Yake ga ba me kaisa murna in
matarsa ta haifi ‘ya mace, ‘ya macen da ze samu yayi wa margayiya beloved sis nasa
ZAINAB takwara. Zainab takasance best sibling na Alhaji ISMA’IL cikin yayyun sa
mace da miji d’aid’ai dakuma k’annensa mata biyu ciki harda Zainab d’in wacce take
binsa dab daga shi se ita. Duk cikinsu ba wacce yafiso suka kuma fi shiri da
shaquwa kamar marigayiya Zainab ba, shekaranta d’aya (1) da aure mutuwa yayi
halinsa, shekaru biyar (5) da suka wuce kenan yanzu amman Alhaji se gani yake kamar
jiya ne rasuwan nata, tun rasuwan ta Alhaji Isma’il yad’au alk’awarin da zaran
Hafsah ta sake samun ciki ta haihu muddin mace ce takwaran Zainab sistersa zeyi
kodan zena tunawa da alkhairun data masa wanda kad’an daga cikinsu ya kasance na
basa jarin fara kasuwancin da yakeyi har a yanzu wanda Allah ya mugun sa masa
albarka ciki se bunk’asa yake.

Sede kash! tundaga kan Yasmin meh shekaru shida (6) yanzu wacce takasance ‘yar
auta cikin yaransa hud’u wanda biyu daga ciki maza ne biyu kuma mata, tun daga nan
haihuwa yayi rana wa matarsa mafi so fiye da komai a rayuwansa, yau shekaru hud’u
(4) kenan rabuwanta da haihuwa se a shekara na biyar (5) Allah ya azurta ta da wani
cikin wanda Alhaji Isma’il yad’au buri da gatan duniya ya aza wa cikin, burinsa a
kullum bayyafin Allah yabasa santaleliyar macen da zema margayiya Zainab takwara. 2
months back yaje aikin hajj inda ya riga d’awafi yana rok’an Allah cika mai
burinsa.

Babban d’ansa IBRAHEEM wanda ya kasance fari ne tas wane mahaifiyarsa Hafsah,
kyawunsa kuwa sak na mahaifinsa yanada 13years ayanzu yana matakin JSS 3 a karatu a
Havardth School wanda ke kusa da unguwansu da k’afa ma suke tahowa se kaisu ne
mahaifin keyi a motansa k’iran Corolla S baqa, dan gudun kada suyi latti. Daga
Ibraheem se k’anwarsa MARIAM shekaru biyu (2) ne a tsakaninsu. Mariam wacce
takasance 11years kyakkyawa ce itama kamanninta irin na Baba kaman Ibraheem sede
ita ba fara kamar mahaifiyarsu bace bakuma baqa kaman mahaifin nasu ba chocolate
skinned take tana JSS1 a matakin karatu itama a Havardth. Daga Mariam se OMAR
shekara d’aya da rabi (1½) ne a tsakaninsu, Omar is 9½ years yana Primary 5 a
karatu shima a Havardth, skin colour nasu d’aya da Mariam sede kaman yad’an fita
haske. Daga Omar se Yasmeen auta. Shekara uku (3) ne tsakaninsa da Yasmeen she is 6
years tana matakin Primary 2 a karatu itama a Havardth, tanada haske sosai sede
bara a kirata da fara ba.

Cike da tashin hankali da tsatsan tausayin Hafsah data kasa haihuwa tin tin
d’azu, a kaita asibiti kuma taqi, bana wai haihuwan gida takeson yi. Alhaji ya
d’ago kai yana kallon Omar daya sasa yima Mamansu fifita kafin Ibraheem ya siyo
petir da za’a sa a engine a tayar.
“Wai a bangon duniya Ibraheem yaje siyo petir d’inne?!” Yayi maganar cikin
kakkausar muryan dayasa Omar b’ari ko amsa mahaifin nasu yakasa se fifita Maman su
yake da sauri da sauri. “Omar dakai fa nake magana! Ina Ibraheem?”
“Bbb... Bbaba ban sani ba kaifa ka aikesa siyo petir yana han-” be k’arisa
maganan ba Ibraheem yashigo da galon na petir a hannunsa tare da yin Sallama “Baba
gash-” tunkud’esa Baba yayi tare da wabje galon d’in “se yanzu kaga daman dawowa
kabar mahaifiyarka tana jiqewa anan dan zufa ko?!”
“A’a fa Baba yau gidan man da layi ne-”
“Rufa min baki ka wuce kaje kasa ka tayar yanzun nan” ya danqala masa galon d’in
a sanyaye yaje ya aiwatar da abinda mahaifinsa ya buqacesa.

_30 minutes later..._


A’ee (Ungozoma) ce tafito da jariri nannad’e cikin shawul pink a hannunta
batai ko inaba se d’akin Baba inda tayi Sallama, rashin amsawansa yasa kawai tasa
kai ta shige, zaune kan Sallaya hannayensa biyu d’age a sama yana addu’a ta tarar
dashi. Bayan Sallaman da tayi tanemi gu ta zauna har anan Baba be juyo ya kalleta
ba sakamakon kukan jariri dayaji yasa yabar dukkanin abinda yake ya juyo da hanzari
“A’ee bade Hafsah ta sauqa ba?”
“Ga santaleliyar ‘yarku nan anan.”
“ ‘Ya mace?!” Yayi maganar cike da k’in yarda tsantsan murna da farin ciki “kina
nufin mace ta haifa?!” yayi maganan a lokacinda yake amshe jaririyar daga hannunta,
yarinyace kyakkyawa ajin farko hanci tun tana k’arama a miqe ba abinda ya rabata da
mahaifiyarta Hafsah illa fari da Hafsah tafita, jaririyar ta kasance tana da haske
sosai erin masu golden skin d’innan amman da alama harda hasken jarinta tattare da
ita nan gaba barata kai hakan haske ba, kyau de kam masha Allah ga gashi kota ina a
fuskarta.

“Alhamdulillah! Alhamdulillah! Allah mai iko kai Allah abin godiya azumin
bakancen dana yi alk’awarinyi a gobe zan fara in shaa Allah ya Hafsah da jiki?”
“Alhamdulillah ta sauqa lafiya tana wanka ne.”
“Masha Allah! Wannan kyauta haka daga Allah, Hafsah taci kyauta!” nan yayi
hud’uba wa jaririyar a b’oye sannan a fili yace, “Allah ya raya ZAINAB, Allah raya
Mana ZEEZEE a tafarkin addinin muslinci ya albarkaci rayuwarta AMEEN” shida A’ee
suka fad’i a lokaci d’aya. “Toh masha Allah Alhaji Allah ya cika maka burin ka
sekaje kaga Hafsah kai mata godiya nikuma barin je in sanar da yaran kyautan da
Allah yayi mana gabad’aya” ganin tanada niyyan amshen Zeezee Baba yayi saurin
dakatar da ita, “barta kije ki fad’a musu a baki ban gaji da riqe Zeezee ba.”
“Oh! Oh! Oh! Alhaji anya zakazo kayi adalci tsakanin yaran nan kuwa?”
“Ke ina ruwanki?! Matsa min anan” yana kaiwa nan ya miqe yabar mata d’akin zuwa
d’akin Hafsah har alokacin Hafsah bata fito daga bayin ba dan haka yayi zaman
jirarta a bisa gado se k’are wa Zeezee kallo yake yana taking nata pictures a
yayinda take ta mummutsika jiki da hannu which is damn adorable.
***
“Assalamu Alaikum gwamnoni da matan shugabannin k’asa” A’ee tayi maganan
alokacin da take sa kanta cikin d’akinsu Mariam inda dukansu dasu Ibraheem suka
taru sukayi jugum tare da had’a tagumi kowannen su na addu’a a ransa Allah kar yasa
mahaifiyarsu ta haifi ‘ya mace, Allah yabata na miji inda hali ma maza biyu su basu
damu ba amman de kam banda na mace dan kuwa tun baby’n na ciki basu samu sakat ba
ina ace an haifosa yau?
“Samari da ‘yan matan nawa barasu amsa bane?” Tayi maganan tana k’ok’arin zama
gefen Yasmeen dake kusa da Ibraheem, se ayanzu hankalinsu ya buga duk suka dawo da
kallonsu kan A’ee dake binsu da kallo fuskan kowannensu d’auke da tambaya da
tsantsan tashin hankali. Kusan atare sukace “Baaba A’ee meh Mama ta samu?” Dariya
ta saki kad’an sannan tace, “meye haka? Sekace dugjal aka haifo maku?” Nanma almost
a tare sukace, “dan Allah mana Baaba A’ee meh Mama tasamu?” Kowannensu na me kasa
kunne dan jin amsarta. Ibraheem yayi k’wafa yace, “Allah sa ba mace ba” qannensa
suka amsa da “ameen” a takaice ciki harda ‘yar Yasmeen, ita yanzu shikenan baby’n
da aka haifa zata k’wace mata autanci.

“Toh ku kwantar da hankalinku d’a na miji Mama ta samu” ta musu k’arya don
ganin reaction nasu, zan so kuga yadda ake sakin hamdala a d’akinga daga meh
“yes!!” Se meh “alhamdulillah” semeh “thank god” se me sujjada seda ta barsu suka
gama haukansu sannan tace, “lallai kuwa yaran nan! Toh ‘ya mace mesuna Zainab
Mamanku tasamu”
Ibraheem ya had’e gira kai “Baaba A’ee banda wasa please.”
Mariam tace, “ai ma wasa take bawani macen da Mama ta haifa na miji ne born boy!”
tad’an murmusa.
Omar ya bud’e baki zeyi magana kenan Baba ya k’olla ma Ibraheem kira.
“Ibraheem! kazo nan kai da k’annenka” anan duk suka tabbatar da maganan A’ee
gaskiya ne, “shikenan mace ce, wallahi mace Mama ta haifo mana” Mariam tayi maganan
tare da dafe kanta. Omar yaja ‘yar tsuka “mace ko jaraba Adda Mariam?” Yasmeen
wacce takaici yabi ya ratsa ta tace, “Adda Mariam yanzu banice auta ba??” Ita
abinda ke damunta kenan sau dayawa friends nata a school sukan ce mata da zaran an
mata k’anwa ko k’ani shikenan nata ya k’are, Mama da Baba zasu bar sonta se new
baby. Ganin Mariam batada niyyan amsata yasa Yasmeen karkato da kallonta gareda
A’ee cikin sauti cike shakwab’a tace, “Baaba wai Baba da Mama zasu bar sona yanzu
se baby?” Dogon sumanta A’ee ta shafa a hankali tana mata murmushi “inji wa?
Yasmeen d’in Baba? Har a kullum Baba ze cigaba da sonki keda sabuwar k’anwarki
Zeezee kinji?” Badan ta yarda ba ta gyad’a mata kai.
Omar ya miqe tare da fad’in “yanzu duk sallolin daren da muka tayi a iska
kenan?” A’ee ta dafe baki in suprise _wato yaran nan har Sallan dare suke kar
Mamansu ta haifi ‘ ‘ya mace? Lallai ga dukkan alamu Alhj bareyi adalci tsakanin
yaran nan ba._ Tayi tunanin haka a ranta.
“Wai ina kuke neh?” Baba yayi maganar wannan karan a fusace. Firgit duk suka
miqe Ibraheem ne a sahun gaba k’annensa na a bayansa suka fice zuwa d’akin Mama
inda suka hango Baba ciki suka shige ciki A’ee na mara musu baya. Akan kujerar 3
seater dake d’akin sukayi lining suka zauna according to girmansu suna me kallon
Baba dayayi banza da shigowansu se wasa wa ‘yar jaririyan da bata ma san yana yi ba
yake.

Ganin sunci fiye da minti biyu Baba baida niyyan kulasu Ibraheem yace, “gamu
Baba” daidai nan Hafsah (maman su) tafito daga bayi da zani d’aure a k’irjinta,
murmushi ta sakar wa ‘ya‘yan nata one by one suka gaisheta da jiki suna faking
murnan k’aruwan da suka samu banda Yasmeen data turo baki taqi koda magana da Mama
ta gano hakan seta murmusa, dankuwa Yasmeen akwai kishi. “Yasmeen d’ita” cewar
Mama. “Zo mamana kinji? Zo auta taa” a sanyaye Yasmeen ta nufa wajen Mama suka
k’arisa kan gado inda Baba ke zaune da Zeezee se kallonta yake yana mata wasa suka
zauna. Daga d’an nesa Mama ta zauna da Yasmeen a gefenta Baba yayi saurin d’ago kai
“haba Hafsah na matso nan mana ko bakisan yau k’ima da darajar ki ya k’aru bane?
Matso please.” D’an murmushi ta saki tana wasa da gashin Yasmeen “kai Baban Yasmeen
barade kabar halinkan nan bako?”
Gira ya had’e “waye Baban Yasmeen? Na kashe sunan nan daga yau Baban Zeezee
nakeso” cike da mamaki kowa ke kallonsa a d’akin harta Mama, a hankali ‘yar Yasmeen
tafara kuka Mama ta rungumota tana jijjiqa ta.

“Yi shiru kinji Auta ta? Baban Yasmeen wace erin magana kuma kake haka? Yanzu
dan an samu Zeezee se a k’i Yasmeen kuma?”
“Toh meh? Yayinta ya wuce ke Yasmeen banason shakwab’a meh haka? Tashi ki zauna!
Ke bakisan ke yaya babba ce yanzu ba? Kukuma Ibraheem da Mariam haka ake yi a
garinku ko? Harda kai Omar, ba wanda yayi yunk’urin amshe Zeezee yaganta cikinku,
an samu k’aruwa amman ko ajikinku kuzo kuga lafiyar abinda aka samu dana Mamanku
koh? Ku kiyaye nifah!”
Ibraheem ne yasoma yunk’urin magana Baba yadaka mai tsawa “rufa mani baki!
tarbiyyan dana baku kenan koh?”
“A’a Baba kayi hakuri” suka fad’i a tare. Ibraheem ya miqe tare da nufowa gun
Baba haka Mariam ma hannu ya miqa ze amshi Zeezee Baba ya bige hannun “seda na
tambaya toh banaso barin bada taba matsa min anan!” A sanyaye suka koma kan kujeran
suka zauna.

“Hafsah ya jiki? Ba inda ke maki ciwo koh?” Baki ta tab’e sannan ta amsa “a’a
babu alhamdulillah.”
“Masha Allah, sannu Hafsah ta sannu kin chanchanci a baki tukuici Hafsah.” Cike
da mamaki su Ibraheem ke kallon Baba a hihuwar Yasmeen Baba be bada tukuici wa Mama
ba se ana wannan Zeezeen?
“Tukuici kuma Baban Yas... Aww Baban Zeezee” ta gyara kanta ganin yadda Baba ke
hararta. “Tukuicin meh kuma?”
“Sekin tambaya ne? Na wannan kyautan mana, kap yaran nan bame kyan Zeezee gashi
ita kad’ai ke kama dake, kin chanchanchi kyautan dubu hamsin.”
“Baban Zeezee dubu hamsin?” ta zaro manyan idanunta, “In ban manta bafa kace
kwana biyun nan bakada kud’i yanzu ga harkan suna ga na dubu hamsin kuma?”
“Kinga erin halinki da banaso kenan inde akan Zeezee ne toh ba abinda barinyi ba
in barakiyi godiya bane fine.”
“A’a Alhaji na meyayi zafi? Godiya nake Allah dad’a bud’i.”
“Ameen” yace daidai nan Zeezee tasoma ‘yar kuka. A’ee tanufo gaban Baba dan
amshe crying Zainab Baba ya hanata, baki ta tab’e “Alhj anya kuwa zakayi adalaci
tsakanin yaran nan?”
“Ke A’ee ina ruwanki? Yaran nan de kowa yasha gata yanzu kuma lokacin Zeezee ne
itama a barta taci gatan ta saboda wannan *_YAR GATA CE!_”* Su Mariam de har yanzu
sun kasa cewa komai se kallon abinda Babansu ke suke harda wai tukuici wa Mama
saboda ta haifi ‘ya mace suna cikin wannan nazari a zuqatansu Baba ya daka masu
tsawa “ku kuma yayyun banza kuna jin kukan k’anwarku ko a kolan rigunan ku koh?
Banason mugunta fah!” Da wuri Mariam ta doso gun ta miqa hannu zata amshe Zeezee
Baba ya bige hannun nata itama “matsa min sekace dagaske Hafsah yi sauri ki
karb’eta ki shayar da ita.”

Mama dake shafa mai tace, “toh Baban Zeeze yanzu zan gama shafa man ina zuwa.”
“Har sekin gama? Itakuma abarta tana kuka? A dalilin meh?”
“Yo! Alhj barin shafa man zanyi?” tayi maganan baki asake.
“Eh Hafsah bari zakiyi ki amsheta” zata sake magana Baba yayi tsawa “kibari
nace!” kowa ya tsaya kallonshi haka Mama ta yanke shafa man ta amshe Zeezee tasoma
shayar da ita se anan hankalin Baba yasoma kwanciya ganin yadda Zainab ke tsotsan
abincinta a hankali Baba besan lokacinda yasoma sama Hafsah albarka ba.
Kusan minti biyar Mama tad’au ta na shayar da Zeezee, a hankali ta zare Mamanta
daga bakin Zeezee take Baba yayi magana “ya haka Hafsah? Har ta k’oshi ne?”
Mama batai magana ba Zeezee tasa kuka “miyar mata, miyar mata nace!”
“Baban Zeezee nima fa inada abinyi zan miqa ta wa A’ee tad’an jijjiqata nan
danan zatayi bacci.”
“Akan yinwan? Akan yinwan zatayi bacci nace?”
“Wani erin yunwa kuma Alhj bayan na shayar da ita” har anan Zeezee bata bar kuka
ba.
“Hafsah ki miyar mata nace karna sake nanata kai na.”

“Oh Allah!” Daga fad’in haka ta miyar wa Zainab mama karap ta chafke tacigaba
da tsotsa da zaran Mama tace zata cire se Baba ya hanata haka seda Zeezee tayi
bacci Baba ya yarda aka kwantar da Zeezee kan gado anan su Ibraheem suka miqe zasu
fice suma.
“Ina kuma zakuje?” Baba ya dakatar dasu.
“D’akinmu Baba” Omar yabada amsa.
“Ita kuma Zeezeen fah? Ita kad’ai zaku bari anan?”
“Baba ga Mama da Baaba A’ee.” Cewar Ibraheem.
“Uwarka nan! Uwarka nace! Dawo kaida Omar ku tsaya akanta kuyi mani gadinta.”
Baki wangalau Ibraheem ya bud’e, bashi kad’ai ba harta su Mama.
“Baban Zeezee gadi kuma bayan gani da A’ee a d’akin?”
“Bansani ba yimin shiru kicigaba da abinda ke gabanki.” Ganin Ibraheem be motsa
ba har yanzu Baba ya buga musu tsawa “daku fa nake magana!” k’iris yarage Zeezee
bata farka ba, a sanyaye suka juyo sukayi kan gadon Ibraheem na k’are wa d’an abar
da za’a sasu yima gadi kallo.

*ACIGABA...???*

*©MIEMIEBEE*

beeenovels.blogspot.co.ke

Page 02
And this page goes to *ANEELURV* thanks for everything dear #OneLove

“Yauwa Hafsah ta barinje in siyo miki gashin koh?”


“Alhaji ni banga amfanin gashin nan ba kawai madara da milo nake buqatan k’ari
sabida insamu k’arin ruwan nono ma Zeezee.”
“Toh angama Hafsah ta ina dawowa.”
“Toh Allah ya kare Baban Zeezee.” Dad’i sosai yaji ya miqe kan gadon tare da
kissing Zeezee a hanci sannan ya d’ago kai ya galla ma Ibraheem da bakinsa kan ya
tab’a bango dan turi harara “sauran kuma in na fita kai da qaninka kufita kujira
kuga abinda zan muku” yana kaiwa nan ya fice zuwa garrage achan yasamu Yasmeen tana
wasa “Baba ina zakaje?”
“Zanje siyowa Mamanku da sabon baby kayan tea ne.” Tanajin sabon baby ta had’e
rai har Baba ya gano kishi take “zo nan” ya kirata bayan ta iso yace, “baraki bar
wannan banzan kishin naki da bansan daga ina yasamo asali bako? Yanzu da k’anwar
nakin kike gaba? Iyyeh? Kicigaba.”
“Baba kacewa Mama wai karta sake cemaka Baban Yasmeen se Baban Zeezee ni banason
Zeezee.” ta turo baki.
“Karki sotan maras kunya kawai, zamuga me siya miki chocolate a gidan nan ai.”
Da gudu ta ruga ciki tana kuka taje ta samu Mama.

*~ * ~ *~
Daidai nan Baba yadawo daga d’an siyayyan dayayi ma Hafsah bayan yayi parking
mota yaciro tsire da kazan daya siya mata a hannu sannan ya danna wa Mariam kira.
“Na’am Baba” ta amsa.
“Zo nan kicire kayakin daga mota kikai d’akin Mamanku.” Daga kitchen tafito tayi
mai sannu dazuwa kafin ya amsa yaji wani erin kukan jaririya wane ana cire mata rai
cike da tashin hankali ya kalli Mariam “meke faruwa? Kukan waye wancan bade na
Zeezee ba?”
“Nata ne” ta fad’a wane tana enjoying kukan Zeezeen.
“Me akeyi mata?”
“Wankan gargajiya Baaba A’ee ke mata tana miqar mata da joints.”
“Meneh?” Daga nan yayi d’akin Hafsah a 360, Mariam tace, “daidai kenan” sannan
taje ta soma ciro manyan gongonin madara da ovaltine number 1 da Baba ya siyo wanda
barata iya tuna when last ya siya musu kalan suba.

Yana shiga ciki yaci karo da A’ee zaune kan kujera da bahon wanka gabanta ta
juya hannun Zeezee a baya tana matsawa ayayinda Zeezee keta ihu kan ba gobe
“Subhanallahi! Ya haka me kike mata A’ee?” yayi maganan yana k’ok’arin ajiye ledan
tsiran kan kujera a yayinda Mama ke zaune kan kujerar, kafin Baaba ta amsa Mama
tace, “sannu dazuwa Alhj, wankan gargajiya A’ee ke mata.”
“Wanka ko azabar da yarinya?” Be jira me zasuce both ba ya k’wace Zeezee daga
hannun A’ee.
“Alhj ya da haka?” Mama tayi maganan baki bud’e haka ma A’ee.
“Banason wankan in baza kuyi mata asalin wanka ba se abar wankan gabad’ai haba
me haka?” Ya kwantar da Zeezee a jikinsa yana bubbugata ko zatayi shiru amman ina
se kuka take. “Daga yau kada a sake yimata wannan wankan, ke Hafsah kinada matsala
wallahi d’iyarki na kuka amman ko a jikinki wad’ancan sakararru biyun kuma” ya dawo
da kallonsa kan su Ibraheem da suke da shirin dariya. “Kaman ma kukan nata dad’i
yake masu.”
“Amman Alhj fa kasani wankan nan dole ne shi ze miqar mata da kasusuwa ya hana
kasala ko Yasmeen ma anyi mata kuma da chan bakayi magana ba.” A’ee ta gwada masa
bayani.
“Naga ai wannan Zeezee ce ba Yasmeen ba, bana so nide na fad’a muku aka sakeyi
ko a bayan ido na ban yafe ba.”
“Toh munji kawota a gama mata wankan.” Mama ta miqa hannu tana jiran ya dire mata
Zeezee.
“Eh kafin nan kibata mama tasha tayi shiru.”
“Toh ai naga seda ruwan nonon zan iya shayar da ita kokuwa? Kuma babu.”
“Wannan ba matsala bane ina Mariam kawo madaran nan” dai-dai nan Mariam ke
shigowa da gongonayen madara da ovaltine, baki Mama ta bud’e in suprise “Alhj
wannan fah?”
“Madaran ki saboda Zeezee tasamu ruwan nono itama.” Hannu ta tafe, “lallai Baban
Zeezee dagaske kake!”
“Niba wannan ba yanzu had’a kisha kibata mama tasha.”
“Kawota bara’a rasa na bata ba.” Nan da nan Mama ta amsheta ta shayar da ita
sannan aka gama yima Zeezee wanka aka shafa mata mai anzo sa kaya tasoma kuka.
“Kekuwa A’ee kiyi mata a hankali mana bafa Yasmeen bace kina wani sa mata kaya
da k’arfi da kuma hanzari haka seki b’alla mata hannu ai. K’asusuwanta ba k’wari
garesu ba.” cewar Baba.
Mama kanma kasa cewa komi tayi dan mamakin sabon halin Baba da take. A’ee ne ta
tab’e baki tace, “yanzu Alhj sa kayan ma koya min za kayi? Ko ka manta ungozoma
ceni?”
“Chan miki nide kimata a hankali in kuwa bara kiyi ba zan mata da kaina.”
“Yi hak’uri zan mata.” Nan tabi Zeezee a hankali ta gama shiryata tsaf cikin
baby pink rigan sanyi da shawul, amsheta yayi daga hannun ta ya nufi bakin k’ofa da
niyyan fita, yana kaiwa bakin k’ofar Mama ta dakatar dashi ta hanyan kiran sunansa.

“Baban Zeezee ya haka? Ina zaka kaita?”


“Ina kuwa? D’aki na mu zauna.”
“Toh Alhj in ‘yan barka suka zo ganin baby fah, se in ce masu meh?”
“Se kice masu babyn na gun Babanta meson ganinta yazo d’akina, kuma ki tabbata
kinsha tea da kyau kar Zeezee tasoma jin yunwa kice ba ruwan nono.” Yana kaiwa nan
ya fice cike da mamaki Mama ta kalli A’ee dake kallonta itama sannan ta tab’e baki
tajawo cup ta had’a tea tana kurb’a a hankali. Koda ‘yan barka suka fara zuwa Mama
taje d’aki ta samu Baba kan yabata Zeezee haka yaqi ya sake nanata abinda ya gaya
mata akan duk meson ganin *_‘YAR GATA_* yazo d’akinsa.

*~ *~ *~
Bayan Sallan Isha Baba na a zaune a d’akinsa da Zeezee kwance kan cinyarsa se
buga budget na bikin suna yake, Zeezee ta soma ‘yar kuka take yayi gefe da abinda
yake ya nufa d’akin Hafsah inda ya tarar da ita tana bayi tana wanka. K’ofan ya
k’wank’wasa daga ciki tace, “waye?”
“Baban Zeezee ne me kike kifito.”
“Alhj wanka nake.”
“Nasani ai shine nace kifito.”
“Inbar wankan kenan?”
“Eh kibari.”
“Toh Alhj kumfan dake jikina kuma fah?” Nan Zeezee ta dad’a kuka. “Kifito nace
Hafsah karki bari na sake nanata kaina tam!” Haka nan dan dole ta watsa ruwa ta
goge jikinta da sauri tafito tana tura mai baki. Hannunta yaja izuwa gado ya ajiye
mata Zeezee kan cinya “gashi yi ki shayar da ita yunwa takeji.”
“Wai Alhj kana magana se kace kasan meke damunta halan kukan bacci ko k’ishin
ruwa fa take ba na abinci ba, kuma na cigaba da shayar da ita minti minti haka ai
seta ramar dani.”
“Karki damu za kina cin abinci bata mana da sauri ba kijin kukanta ne?” Seda ta
k’are masa kallo sannan ta shayar da Zeezee har seda tayi bacci, duk anan albarka
Baba keta sa mata.
“Yanzu da tayi bacci ka yarda in zare abuna?”
“Abinta de ba naki ba Hafsah zare ai tayi bacci.” A hankali Hafsah ta zare
mamanta daga bakin Zeezee ta kwantar da ita. “Yanzu kuma se a barni inyi wanka
aiko?”
“Sosai ma Hafsah kiyi kifito akwai tsaraban dana tanadar miki.”
“Again akan dubu hamsin d’in?”
“Sosai ma kuwa jeki, kika gama kizo ki sameni a d’akina.” Cike da jin dad’i ta
miqe tare da fad’in “toh” ta fad’a bayi.

D’akinsu Ibraheem Baba yayi inda ya sami duka yaran zaune suna assignments nasu,
yana shiga suka yi masa ‘sannu’ banda Yasmeen datak’i koda kallonsa, ‘yar murmushi
ya saki yasa hannu a aljihu yaciro chocolate na bounty guda biyu ya miqa mata “zo
ki karb’a Mamana na kaina” ba yabo ba fallasa taje ta amsa tare da yin godiya
“Yauwa Ibraheem wuce kaida Omar kuje ku tsaya kan Zeezee tana bacci.” Cike da
mamaki Ibraheem ya d’ago kai yana kallon Baba totally speechless, wai shin Baba
bega yana assignment bane da zesa sa yima Zeezee gadi? Tambayan dayayi ma kansa
kenan.
“Da kaifa nake magana d’an fari ka kuma jini koh?” Baba ya sake magana. “Kai
Omar miqe! Kabar abinda kakeyi ka dawo seka cigaba.”
“Ayyii Baba assignment fa nakeyi” cewar Ibraheem.
“Ai nagani ba makaho ne ba ni, kuje kuyi gadinta in nagama abinda nake zan
karb’e ku.” Ibraheem ze sake magana Baba ya daka mai tsawa “wuce nace!” A sanyaye
shida Omar suka bi gefensa suka fice se gunguni suke.

*~ *~ Bayan Mama tagama kimtsa kanta ta kalli su Ibraheem da suke tsaye kan
Zeezee se harararta suke ayayinda take bacci peacefully. D’an murmushi ta saki
tace, “dade kunbar wanan kumbure kumburen koni mahaifiyar ku ban tsira ba inde akan
Zeezee ne kuma ku hak’ura kawai wataran se labari.”
“Toh shikenan Mama wai in wannan abar zatayi bacci se an tsaya a na gadinta
mschw!”
“Katayi kaji? Bari yazo ya jika ni ba ruwana, Omar d’ina karka kulasa kaji ko?
Yanzu zanje in dawo seku tafi.” Daga nan ta wuce d’akin Baba dake chan babban
parlour, Sallama tayi sannan ta shiga, zaune ta tarar dashi kan gado da paper akan
cinyansa se budget list yake bugawa. Bayan ta zauna gefensa tace, “Alhj gani” tayi
maganan tana leqa abinda yakeyi nan taga budget yake had’awa kona meh oho?

“Yauwa ina zuwa, Hafsah” yana kai wani point ya ajiye biron ya miqe ya nufa
wardrobe nasa tare da ciro wasu manya-manyan shopping bags guda biyu ya dire mata a
gaba “wannan nakine, wannan kuma na Zeezee.” ya nuna mata da yatsa. Baki ta sake in
shock.
_Bade kayaki bane cike ciki?_ tambayar data iya tama kanta kenan aiko tana
bud’ewa ta tabbatar da zaton datake, d’ayan cike yake da zannuwa manya dakuma laces
sekuma d’ayan kayan babies had’ad’d’u qualitative ones.
“Alhaji duka wad’annan?!” Abinda bakinta ya iya furtawa kenan.
“Ai ba yawa Hafsah, farin cikinki yafiye mani komai a duniya, kalamu barasu iya
kwatanta irin farin cikin da kika sanya ni ciki ba yau kinga ko dole insan taya
zanyi in kwatanta miki, komi anan naki ne dana Zeezee.”
“Wayyo! Baban Zeezee you are too much duka wad’annan?!” Ta zazzago kayakin k’asa
tana bi da kallo kap ciki ba k’arami zani. “Nagode sosai Baban Zeezee Allah ya qara
bud’i yabarmin kai.”
“Ameen Hafsah ta ai ni naki ne ke kad’an ki.”
“Ba kishiya koh?” Ta gwada jin bakinsa.
“Haba! Ai alk’awarin nan dana d’au miki tun kafin muyi aure yana nan har yau kuma
har gobe.”
_“Kafin ke ba kowa Hafsah, haka zalika bayan ke ma ba kowa, kece first and last
I’m all yours”_ Hafsah ta nanata alk’warain da Baba yayi mata tun kafin suyi aure.
“Exactly! Kinga ko ba zancen kishiya duk abinda nake so nake buk’ata kina dashi
kina yimin dan meh zan miki kishiya?”
“Gaskia ne Alhj Allah yabar soyayya I love you.”
“I love you too” ya yi maganan tare da zama a gefenta.

“Alhj na kayakin nan sunyi yawa! Karka biye min da Zeezee ka tsiyaye kana mana
siyayya wallahi koba kayakin nan ma ni am satisfied and happy...”Ta nisanta “amman
fa kace bakada kud’i kwana biyun nan ina kasamu kud’in wannan siyayya?”
“Ai na gaya miki inde akanki da Zeezee ne toh inada millions.” Baki ta tab’e ba
tare da tace komai ba se bin kayakin take da kallo chan ya miqo mata dubu hamsin
“as promised, wannan kuma sekiyi d’inki dashi koh?”
“Alhj!! Karkasa in kasa bacci mana yau.”
“Aikuwa dana ji dad'i kinga sekita gadin Zeezee.”
“Toh nikam ba abinda zance banda Allah ya qara bud’i barin je in samu Zeezee su
Ibraheem su samu su gama homework nasu.”
“Toh toh ba abinda kike buqata again koh? In akwai speak up.”
“Ba komai Baban Zeezee... Yauwa nace me kakeyi shigowa na? Naga kaman budget
kake had’awa kona meh?” ‘yar murmushi ya saki “karki damu you’ll find out soon My
Dear.” Bayan d’an nazarin datayi ta juyo tana kallon sa kamar yadda shima ke
kallonta “Alhj bade taron suna kake planning yiba koh?”

“Me kike fad’i wai? Jeki samu Zeezee kibar suaratan banza” daidai ze miqe ta
riqe hannunsa “Alhj gayamun gaskia taron suna kake shirin yi?”
“Toh haramun neh? Kuma naga yaran nan duk kowa anyi taro a sunansa se ana *_YAR
GATA_* ne zakice bara ayi ba?”
“Alhj ni bafa abinda nake nufi ba kenan, kaifa kace min kwana biyun nan baka
samu sosai kuma ni banga amfanin kashe kud’i ba dalili ba, taron sunan nan de ba
dole bane ‘yar ragon suna aka yanka walillahil hamdh.”
“Maki kenan amman nikam senayi taron sunan nan aci asha a tayani murnan samun
Zainab.”
“Yanzu Alhj murnan da mukayi nan du be isheka ba?”
“Be isheni ba Hafsah se kap ‘yan unguwa, ‘yan uwa da mutan arziki sun min
congratulations zanji dad’i so tun wuri ki fara tura gayyan suna.” Baki ta tab’e
tace, “toh duk abinda kace amman wallahi kasani in kazo daga baya kana min
complaining cewa bakada kud’i barin saurareka ba.”
“Karki sauraran” nan ta miqe tare da ledojin a hannunta “seda safe toh.”
“A huta gajiya Hafsah ta, Allah yabamu alkhairi.”
“Ameen” har ta kai bakin k’ofa Baba ya dakatar da ita, “Hafsah please kar kiyi
ignoring kukan Zeezee koda da daddare ta tashi buk’atan nono kibata.”
“Toh Baban Zeezee naji” daga nan ta fice su Ibraheem suka samu daman k’arisa
assignment nasu suka yi kwanciya kasancewar da akwai school gobe.

*~ *~ ~RANAR SUNA* ~* ~*

Gidan Alhj Isma’il Yusouf cike yake da ‘yan uwa da abokan arziki se hidima ake
ana ci ana sha ana d’aukan hoto, wato yadda Alhj ya tsara bikin sunan Zainab ya
wuce tunanin kowa daga kan iyalansa har ‘yan unguwa. Bikin suna amman sekace na
aure, komai is in abundant supply, Mama data d’au ko zob’o za’ayi serving guest
dashi ta mugun shan mamaki ganin ana sauk’e canned and bottled drinks ga snacks, ba
abinda babu, uwa uba ga kaji nan barkace. Babu kaman su Ibraheem da suka ringa
satan drinks suna kaiwa fridge na d’akinsu, tunda yake be tab’a ganin anyi suna
akayi bushasha haka kamar na Zeezee ba, ba shakka Zeezee *_‘YAR GATA CE!_*

Bikin suna de ba abinda za’a ce banda Allah shi raya Zainab dan kuwa abin se
wanda yagani!

_6:50PM_
Yawancin mutane sun watse kad’an daga ciki ne suka rage wanda yawancin su ma
dangi ne, Hafsah da Zeezee sunci kyauta sosai na sosai zannuwa da kayan baby har
neman wajen sasu ake, kan gado cike yake dam da kayaki. Kwance Zeezee take bisa kan
gado agefe guda tana ta zuba bacci ita kad’ai a d’akin. Daga bisani tasoma kuka
alokacin Mama na bayi tana watsa ruwa se sauri sauri take tafito ta d’auketa, ai
kaman alarm Baba keda yajiyo kukan Zeezee ya shigo da hanzari ya tarar da ita se
kuka take. Da hanzari ya d’agata yashiga danna wa Hafsah kira.
“Na’am Alhj gani fitowa ” nan da nan tafito.
“Kinajin Zeezee na kuka bara ki bar duk abinda kike ba ki d’auketa? Ina yaran
suke?”
“Sun shiga nan mak’ota, Alhj da Allah riqe min ita in samu in sa kaya.”
“Har kisa kaya tana jirar ki kenan? Amsheta ki shayar da ita.”
“Wai-” katseta yayi, “bana son jin wani zance amsheta nace” haka ba yadda Mama ta
iya ta karb’eta ta shayar da ita har seda ta koma bacci Baba ya yarda ta zare
maman.

Da misalin k’arfe 9:34PM Mariam dake taya Mama kwana tun haihuwan Zeezee tashigo
cikin shirin baccinta ta dire bargonta gefen Zeezee tare da k’are mata kallo.
Lallai kuwa gaskian jama’ah kap cikinmu ba me kyan wannan ‘yar jaraban tayi maganan
a zuci tare da sakar da tsaki a fili ba tare da tasan tayi hakan ba, tas taji an
buga mata k’eya har ribbon nata na neman fad’i a hanzarce cike da rikicewa ta juya
tana kallon direction dataji sauk’an marin, Baba taga tsaye akanta.
“Baba nikuma menayi?” Ta tambayesa tana shafa k’eyar tata.
“Zeezeen kike kalla haka harda jan tsaki?” Daidai nan Mama tafito daga bayi
itama da shirin kwanciya.
“Baban Zeezee ya haka? Baka kwanta ba?”
“Ina kuwa zan kwanta bayan jikina na bani keda wannan muguwan” ya nuna Mariam da
yatsa “kuna ignoring Zeezee da daddare saboda haka anan zan kwana yau. ”
“Anan kuma?” ta tambayesa fuskarta d’auke da neman k’arin bayani.
“Eh anan Hafsah ai na gaya miki jiki na na bani da daddare kuna barin yarinyan
nan tai ta kuka da wannan muguwan yartan” ya galla wa Mariam harara yanzu kuma.

“Yo Alhj ba sena gama arba’in ba tukunah?”


“Ke kika sani, nide anan zan kwana Mariam fice kije ki d’ago Yasmeen daga d’akina
ki kaita d’akinku achan zata kwana yau.”
“Toh” ta fad’i tana jin dad’i dama harga Allah ta gaji da tashi kullum da
daddare tana yawo da Zeezee a hannu har seta koma bacci, “seda safe Mama, seda safe
Baba” tace dasu tare da ficewa.

Bayan Mama taja comforter ta kwanta ta kalli Baba dake zaune gefen gadon yana ma
Zeezee addu’a tana turo baki tace, “ni wallahi Alhj nasan yau hanani bacci zakayi
in kasa wannan Zeezee agaba.”
“Ai dama nasani ignoring nata kike da daddare kuma daga yau hakan bare sake
faruwa ba” nan ya miqe ya kashe masu wuta suka kwanta da Zeezee rigingine a
jikinsa.

_2:47AM_
Cikin bacci Baba ya soma jin kukan Zeezee, take ya tashi tare da kunna wutan
d’akin ya d’agata yana jijjiqata ganin tak’i yin shiru ya maido da kallonsa kan
Mama da tayi kamar bataji kukan Zeezee ba tana ta bacci.
“Hafsah!” yayi whispering sunanta, shiru bata amsa ba.
“Hafsah tashi nasan kina jina tashi nace ko ba kijin kukan Zeezee ne?”
“Alhj dan girman Allah ka barni in huta, ka fa san irin hidiman da na sha jiya.”
“Meaning baraki bata mama ba kenan komeh? Tashi nace!” yasa hannu yana jijjiqata
da k’yar ta miqe ta zauna tana galla mai harara har a nan Zeezee bata bar kuka ba.
Chan ta miqa hannu ta d’ago feeder’n Zainab ta mik’a mai, “gashi bata ruwan tasha
k’ishi takeji” kallonta kawai Baba ya tsaya yi totally speechless mah.

*© MIEMIEBEE*

PAGE 03

*December, 2016*

“Amshi mana Alhj bacci fa nake ji.” Ganin baida niyyan karb’a ta ajiye mai
akan gadon ta juya zata kwanta, sede wani hanzari ba gudu ba kafin kanta ya dire
kan pillown Baba yasa d’ayan hannunsa yaja “hab-” take ya katse ta;
“Bana son dogon surutu karb’eta nace ki karb’eta mana!” haka tana gunguni ta
amshe Zeezee ta shiga bata mama da zaran tace zata cire Baba ya hanata, yau kam
koda Zeezee tayi bacci Mama ta gwada zare maman daga bakin Zeezee seta sa kuka haka
Baba ya sata gaba ta kwanta mamanta maqale bakin Zeezee, da zaran tace zata cire
Zeezee tasa kuka Baba yahau mata surutu a takaice de a tak’ure Mama tayi bacci
ranan.

*~ *~
Mu kwana mu tashi be ragar komi ba, a yanzu haka Zeezee nada 4 months a
duniya, yarinya tana girma tana dad’a kyau ko kad’an hasken ta be gushe ba, ga
gashi masha Allah. Gatan da Baba ke bata yasa har ita Mama kanta abin na bata
haushi atimes, banda yayyun ta da suka d’au karan tsana suka aza mata dan duk wani
abinda Baba yasamu Zeezee kad’ai ya sani komai Zeezee, Mama tayi tayi dashi a fara
baiwa Zeezee madara amman yaqi haka har ta rame dan irin shan nono na Zeezee bata
qi a yini ana shayar da ita ba. ‘Yan unguwa kuwa kowa yasan Baba da Zeezeen sa duk
da 'Baban Zeezee' suke kiransa akoda yaushe da yamma ze zauna a harabar bakin gate
na gidanshi da Zeezee ajikinsa suna shan iska, kap cikin yaransa ba wanda yake
jinta a jikinsa kaman Zeezee kodan tanada sunan margayiya ne oho?

****
Zeezee ce kwance bisa kan gado da abin wasanta a hannu se wasan miyau take
ayayinda Mariam ke k’ok’arin canza mata diaper (pampers) se wani tuttura baki take
daidai ta cire ma Zeezee used diaper d’in tana k’ok’arin sa mata sabo kenan Zeezee
ta tsula mata fitsari siiirrrr! a fuska. Ihu ta saki wanda yasa su Ibraheem shigowa
da sauri ganin meke faruwa. Dariya sosai suka saki ganin fuskan Mariam na yoyon
fitsari, Zeezee kuwa ganin yayyun ta na dariya itama ta kama dariyar, ba kaman
Ibraheem da har yana dafe ciki, kusan a tare Mama da Baba suka shigo suna tambayan
meke faruwa a zatonsu ba lafiya ba.

Kamar wacce zatayi kuka Mariam tace, “Baba wai dariya sukemin saboda Zeezee
tamin fitsari a fuska.”
“Amman Mariam kema seda na fad’a miki kibar b’ata lokaci a duk lokacin da zaki
canza ma Zeezee diaper saboda incasities haka ai ga irinshi nan.” Mama ta yi
scolding nata. Baba daya k’arisa kan gadon ya d’aga Zeezee yana mata wasa yace,
“shine zakiyi kuka dan Zeezee ta miki fitsari? Mschw! Banason sakarci fah Mariam.”
“Ayyi Baba kalli dariyan da Ibraheem kemin fah.” Idanun Baba da na Ibraheem na
had’ewa Ibraheem yayi tsit tare da calming kansa. “Dariya ko? Nasan maganinka,
Hafsah amsheta kisa mata pant tasha iska” nan da nan yaran sukayi waje se neman
tsokanan Mariam suke.
Chan bayan Azahar su Ibraheem suna zaune a tsakar gida suna chin abinci Baba
ya k’wala mai kira, ba tare da b’ata lokaci ba ya miqe ya je kiran “na’am Baba
gani.”
“Yauwa zo ka amshi Zeezee kayi mata tsarki ka kuma wanke pant d’in tayi kashi
aciki.”
“What?!” Yayi exclaiming batare da yasan yayi hakan ba.
“Meh kace?”
“Bb.. Babu banji me kace ba Baba”
“Cewa nayi kazo ka ma Zeezee tsarki ka kuma wanke pant d’in tayi kashi ciki.”
Fuska Ibraheem ya maraice “Baba kayi min rai dan Allah, taya zan wanke wa Zeezee
kashi? Ni wallahi ban iya ba.”
“Baka iya wanke kashi ba?”
“Eh wallahi ban iya ba Baba.”
“Tohhhh... In kayi naka wake wanke ma? Ni ko Mamanku? Will you come and carry
her my friend!” Ya daka mai tsawa.
“Baba dan Allah kayi hak’uri.”
“Ba ka iya ma Mariam dariya ba? Nan gaba zakayi hankali.”
“Baba kayi hak’uri wallahi na tuba.”
“Ibraheem kaji na rantse kasake barina na nanata abinda na fad’i maka ranka ze
b’aci” haka kan wanda zeyi kuka ya k’ariso ciki ya amshi Zeezee daidai nan Mama ke
fitowa daga wanka idanunta basu sauqa ko ina ba se kan pant na Zeezee dake a cike
dam “laaa bade pupu tayi ba Alhj? Shi yasa ban son barinta ba pampers kawota
Ibraheem in wanke mata in mata wanka gabad’ai.” Dad’i sosai Ibraheem yaji wanda ya
kasa b’oyewa bekaiga miqa wa Mama Zeezee ba Baba yace, “ka wuce nace!”

“Ayya Baba mana, Mama tace zata wanke mata.”


“Meke faruwa neh?” Mama ta tambaya, nan Baba ya labarta mata komai ta tab’e baki
tace, “Alhj dade ka barsa zan wanke mata kai kuma nan gaba se kayi hankali.” Har
b’ari bakinsa ke yace, “wwa...walla..wallahi nayi, nayi hankali Mama.”
“Hafsah ki basa waje ya wanke ma yarinyan nan jiki bakyau fa barin kashi jikin
yaro akwai harmful acids ciki.”
“Jeka wanke mata Babana yi hak’uri.” Mama tace dashi a hankali.
“D’an banza kawai!” Baba ya fad’i yana hararansa, haka yasa kai cikin bayin yana
galla wa Zeezeen dake ta faman masa dariya harara har yasamu ya wanke mata jikinta
tsaf sannan ya riqo pant d’in a d’ayan hannunsa ya fito daga bayin akan gado ya
direta ya fice nan qannensa da suke ta faman leqansu tin d’azu suka hau masa dariya
banda kaman Mariam da har take sauqa k’asa tana hawaye, bece dasu komi ba ya nufa
bakin famfo tare da neman kara haka yana yamutsa fuska ya samu ya wanke pant d’in
ya shanya. Akan yayi wajen abincinsa seya hau yin d’akinsu.

“Ya Ibraheem abincin naka fah? Ka k’oshi ne ko Yasmeen ta kai ma d’aki?” Mariam
ta tambayesa full of sarcasm.
“Wallahil azimu Mariam kika sake min magana me hanani dukan ki agidan nan se
Allah hegiya kawai.”
“Oho dai! Allah ya rama min, daidan ka kenan nan gaba zaka sake min dariya.”
Har ya kama tafiya yaga bare iya hak’ura ba da gudu ya nufo inda take ganin haka
ta miqe itama tasa gudu tanayi yana binta har suka isa d’akin su Baba. Bayan Mama
Mariam ta k’arisa tana b’uya “ya haka? Meke damunku ne wai? Shin baku iya sallama
bane?” Baba yayi scolding d’insu a yayinda Mama ke k’ok’arin k’wace kanta daga
rik’on da Mariam ta mata.
A fusace Ibraheem ya soma magana, “Baba wallahi ka ja mata kunne ta dena shiga
harkana in ba haka ba b’ab’b’allata zanyi into pieces.”
“Ehhh sannu fah, sanu ubanta” cewar Baba cike da mamaki yana mamakin k’arfin
hali irin na Ibraheem. “Kai d’in ba dariyar ka mata d’azu ba? ” Shiru Ibraheem yayi
bece komai as se harara n Mariam yake. “Da kai fa nake?!”

“Alhaji ya isa please, Ibraheem Baba na kayi hak’uri” Mama tace cikin sanyin
murya sannan ta dawo da kallonta kan Marian “ke kuma ki shiga taitayinki kidena
yima wan ki rashin kunya kina ji ko?” Baki Mariam ta turo “toh Mama ni d’azun bemin
dariya bane?”
“Oya find your way out!” Baba yayi masu nuni da hannu. Ganin Ibraheem yak’i
motsawa Mariam ma tak’i fita.
“Daku fa nake” this time a tsawace.
“K’el” cewar Ibraheem yana nodding kai yana kallon Mariam nufin ‘inya kamata
d’innan’ daga nan ya fice ya b’oye bakin k’ofa Mariam na fitowa ya cafko hannunta
tare da danna mata nank’washi me uban zafi akai, k’ara ta saki sosai idanunta auka
ciko dm da hawaye, “Allah ya isa mugu kawai” ta murgud’a mai baki beyi ta kanta be
ya wuce BQ ko a babu ya kusa sata kuka.

Bayan Sallan La’asr Baba ya shirya tsaf ze fita kasuwa, ganin haka Mariam tabi
sahunsa Mama dake a kitchen tana had’a dinner tayi tsaye tana kallonsu ta window.
“Baba!” Cewar Mariam, chak Baba ya tsaya tare da kewayowa.
“Wani abu ne Miryaamu?” Ya tambayeta.
“A’a Baba” tace tana wasa da yatsun ta, “uhm Baba nace ko akwai kud’i zaka siya
min jakar makaranta nawa ya tsufa.”
“Yaushe ne na siya miki jakan Mariam?”
“Baba tun last last year fa, tun primary 5.”
“Toh naji Mariam, Allah ya kawo kud’i.” Shiru tayi bata ce komai ba as tana
nazarin wani irin kud’i Baba yake magana baida shi. “Ba kiji me nace bane? Allah ya
kawo kud’i.”
“Amman fa Bab-” da sauri ya katse ta “in baki iya fad’in amin ba seki jira in
Maman ku ta kwashe adashe ta sai miki.”
“Ameen” ta fad’a a hankali sannan ta juya ta basa waje. Seda Mama taga ficewar
Baba daga gidan takira Mariam take mata magana.

~* ~* Da goshin Maghrib Baba ya dawo daga fitan da yayi, wasu manya manyan
shopping bags ne k’waya biyu hannunsa wanda ya shige dasu d’akinsa nan da nan ya
d’auro alwala ya fice masallaci. Ashe kam tun shigowansa su Mariam suke leqensa
yana fita suka shiga d’akinsa ita da Omar suka soma neman inda ya dire ledojin daya
shigo dasun, cikin wardrobe nasa suka samu suka zaro tare da bud’ewa kayaki ne bil
adadi masu kyan gaske wanda ko ba’a gaya ba ansan masu tsada ne duk na Zeezee ba ko
na Yasmin d’ai ciki, dam ledojin duka kayakin Zeezee ne ciki bayan ko wanda aka
mata suna dasu ma bata gama sawa ba amman ya sake yimata siyayya, Mariam da tace a
sai mata jaka ance mata ba a da kud’i.
Omar ya nisanta yace, “ai dama na sani when it comes to Baba and Zeezee expect
more.”
“Amman Omar yanzu Baba ya kyauta? Wallahi su Bilqees, Khadija, Sadiya dasu
Halima a class namu har dariya suke min akan jaka ta.”
“Hak’uri zakiyi Adda Mariam tunda aka haifo jarababbiyar Zeezeen nan kam ai namu
ya qare” ahaka ya taimaka mata suka miyar da kayakin ledan. Bayan Mariam ta idda
Sallan Maghrib taje tasamu Mama ta mata bayani, cike da mamaki Mama tace, “lallai
Babanku! ina Zeezee zata zo ta kai kayakin? Karki damu Mama na zan mai magana za’a
siya miki sabon jakar kinji?” Kai Mariam ta gyad’a “nagode Mama” nan ta nufa
d’akinsu suka hau kallo.

Bayan dawowan Baba ya kinkimi ledoji yayi d’akin Mama dasu, zaune ya tarar da
Zeezee cikin gadonta se wasa take, tana ganinsa ta soma tsalle nufin ya d’auke ta,
bayan ya gama yimata wasa ya cire mata kayan jikinta ya hau gwada mata sabin daya
siyo wanda duk suka mugun amsheta. Ana cikin haka Mama ta shigo da sallamarta ta
zauna a gefensa tana kallonshi daga bisani tace, “sannu da k’ok’ari kaya sunyi
kyau.”
“Sekin fad’a ma? Ai nan da kike gani duk kayan dubu hud’u da d’ari biyar
(N4,500) yayi sama ne, a shagon Yusha’u na siyo su.” Baki Mama ta dafe da hannunta
d’aya tace, “yanzu Alhj kayi adalci kenan?” Cike da k’in nuna damuwa yace, “name
fah?” Yana me sake gwada wa Zeezee wani kayan.
Mama bata b’oye komi ba ta basa labarin dukkanin abinda tasani, shiru Baba yayi
chan yace, “ni wallahi banason suratai yanzu me kikeson implying? Bana adalci
tsakanin yaran nan ko meh? Jaka de baze kawo fad’a ba.” Hannu ya cusa a aljihu ya
fito da dubu d’ai-d’ai ya irga biyar ya watsa wa Mama “seku siya mata jakan, da an
sai wa yarinya kaya shikenan kowa idonsa na kai toh Allah kyauta.”

“Ameen koma me de ka bada kud’in jakan.” Cewar Mama tana k’ok’arin barin d’akin.
Ko uffan Baba bece da ita ba ya cigaba da abinda yakeyi.

★★★

Gata mara misaltuwa Zeezee ke samu gun Baba a yayin da hakan ke tusa tsanar ta
gun ‘yan uwanta. Sosai take girma wane kazan agric sam Baba bai barin Mama tabar ta
da yunwa, aduk lokacin da Zeezee ta soma jinyan hak’ori kuwa Baba ji yake kamar shi
ke rashin lafiyar duk yabi ya tada wa kowa hankali a gidan barin ma Mama da take
yini tana shayar da Zeezee 24/7.

Zazzab’in sati biyu Zeezee tayi ta mulmule ta sake komawa old self nata. Da
yamma bayan yaran sun tafi islamiyya Baba kuwa tun fitarsa safe be dawo ba Mama
tafito rik’e da Zeezee a hannu, d’ayan hannunta kuwa ribbons ne da comb da kifiya
da alama so take ta kamawa Zeezee gashin ta bayan ta nemi kujera ta zauna ta shafa
mai akan sannan ta soma tajewa a hankali, comb d’in na tab’a gashin, Zeezee tasa
ihu a rayuwa in akwai abinda ta tsana shine a tab’a mata kai dai-dai nan neighbours
nata su Maman Sudeis, Ummu HH, Maman Sultan da Maman Samha suka shigo dan duba
jikin Zeezee dan ko basu da labarin ta warke. Sannu da zuwa Mama tayi musu a
yayinda suka k’ariso kan daddumar dake a kusa da Mama suka zauna bayan gaisuwa suka
tambayi ya jikin Zeezee Mama take cemasu jiki da sauk’i, anan suka soma hira. Da
zaran Mama ta tab’a kan Zeezee seta sa ihu.

Maman Sudeis ce ta bada shawara kan asa ma Zeezee mama a baki zatayi shiru,
hakan kuwa Mama tayi, kum Zeezee tayi tsit wane bata gidan sede Mama na sake tab’a
gashin ta saki maman tasa ihu, dariya Maman Samha da Sultan sukayi suna mamakin
wayo irin na Zeezee “wato ita de kar a tab’a mata kai.” cewar Ummu HH. Maman Samha
ta tab’e baki tace, “ai kuwa de ga gashi har gashi amman bayason kulawa, ina ma ace
Samha ta keda wannan gashin? Yanzu ya zakiyi toh Maman Zeezee?”

Mama ta kalli Zeezee da tayi lamo a jikinta sannan tace, “danne ta zanyi
wallahi ai Baban nasu bai gida, ‘ya‘yan kowa ana masu kitso ni bance zan mata kitso
bama, d’an kamawa da ribbon da zan mata tace baza ayi ba!” Nan tasa comb tana taje
sumar, Zeezee na dad’a ihu kaman ana cire mata rai tasha mama ma tak’i se ihu take
amman haka be hana Mama fara sa mata ribbon d’in aka ba. Daga sama kawai ta jiyo
sallaman Baba, ko kad’an bataji k’aran honk na motansa ba kodan kukan Zeezee ne
oho? Cike da tashin hankali ya nufo inda matan suke zaune. Ko ta kan gaisuwan da su
Maman Sudeis suke mai beyi ba ya soma masifa.
“Ya haka? Meke faruwa Hafsah?!”
“Sannu da zuwa Alhj.” cewar Mama.
“Ba abinda na tambaya ba kenan” yayi maganar tare da d’ago crying Zeezee daga
cinyan Mama yana lalashinta har ta samu tayi shiru, se anan ya amsa gaisuwan su
Maman Samha.

“Ina jinki Hafsah me kike ma Zeezee kukanta ya cika unguwa haka?”


“Alhj me zan mata? Gashin nata na keson kama mata naga yayi tsawo dayawa ana
barin sa haka.”
“Da kuma bata so fah?”
“Al-” yayi saurin katse ta;
“Nace da kuma bataso fa? Me ya kamata kiyi?”
“In bari” ta fad’a sounding humiliated a gaban k’awayenta yana scolding nata
haka. Ido ta d’an mai ko zeyi shiru ya bari se bak’in nata sun tafi yaso se yayi
scolding natan amman ina se kaman cewa ma tayi ya cigaba.
“Toh meyasa baki barin ba? Kama kan banza da wofi!” ya miqa hannu kan cinyarta
yayi watsi da ribbons d’in, “kinsa yarinya kuka ba gaira ba dalili dududu yaushe
yarinyan ta samu sauk’i neh? Wallahi Hafsah ki kiyaye ni.” Ran ta ne ya b’aci bata
san a lokacin da tace, “shikenan kai Alhj ba’a isa a tab’a yarinyan nan ba ka hau
ma mutum surutu? Kalli kan Samha nan ba kitso neba akai? Amman kai kace wai bara’a
tab’a ba se a aske gashin ai kowa ya huta.”
“Bara a aske ba bara kuma ayi mata kitson ba haka za’a bar gashin ku kuma Maman
Sudeis da saura ina ganin ku da hankali amman kuna ganin Hafsah na rashin hankali
baraku mata magana ba?”
“Kayi hak’uri Baban Zeezee hakan bare sake faruwa ba” cewar Ummu HH.
“Allah kyauta” ya fad’i tare da nufan ciki, binsa Mama tayi da harara tana meh
mamakin hali irin na Baba, kap cikin yaranta ba wanda Baba ya tab’ayi mai abu haka
banda Zeezee. A time na Yasmeen ma kam sata yake a mota ya kaisu gidan kitso yace
ayi ma Yasmeen amman na Zeezee yace bara’a tab’a kanta ba? Toh Allah kyauta!

Hira kad’an suka tab’a da friends nata tayi masu rakiya sannan ta dawo ciki.
Ita a zaton ta ma Baba d’akinsa yake ashe a nata yake ya zauna kan gado yana wasa
wa Zeezee, tana shiga ta gansa kafin ta juya ya kira sunanta chak ta tsaya tare da
kewayo wa. “Gani” ta fad’i rai a b’ace sam ba annuri a fuskarta, daya gano hakan
seya saki murmushi ya gyara zamansa kan gadon.

“Haba! Hajiya Hafsah ta ya da haka kuma?” Banza dashi tayi. “Maman Zeezee dake
fa nake.”
“Alhj kaga zan d’aura girki in wani abun kake buk’ata ka fad’amin inada abinyi.”
tayi maganan in an I don’t care manner.
“Zo ki zauna anan” yayi mata nuni da space dake gefensa nan ma tayi banza dashi
“yi hak’uri mana Maman Zeezee nayi kuskure toh amman kiyi hak’uri.” Sexy long eyes
nata wanda Zeezee tayi gadonsu ta d’ago tana kallonsa a yayinda ya kashe mata ido
d’aya “yi hak’uri my wonderful Wife.” Batasan a lokacinda ta saki murmushi ba taje
ta zauna gefensan kamar yadda ya buk’ata. Dad’i sosai yaji “yauwa ko kefa tawan?”
“Uhm” tayi murmuring.
“Nace kafin ki shiga kitchen kid’an bawa Zeezee mama inason mud’an fita
strolling da ita.”
“Wai Alhj ni shikenan kullum cikin bawa Zeezee mama, banida aikin da yafi
wannan! Ni gaskiya wallahi na gaji a had’a mata da madara, barin iya ba”
“Kin gaji? Ke bakisan farillah neba shayar da yaro?”
“Eh nasani amman ai ba’ace koda yaushe ba, abanza ta zubar min da nono ta mai min
dasu slippers, ni gaskiya banaso ina maintaining jiki na.”
“Ahh lallai fa Hafsah sannu! Sekace bana biyanki albashi k’arshen wata kamar
yadda muslinci ya tanadar as kyautatawa? Ko badan haka bama baraki shayar da ‘yarki
ba?” Zata sake magana ya dakatar da ita “yimin shiru ki bata muyi mu fita kema kiyi
abinda ke gabanki.” Harararsa tayi ta gefen ido sannan ta amshe Zeezee ta shiga
bata mama seda ya tabbata Zeezee tayi nak ya yarda Mama ta zare abinta sannan suka
fice da Zeezee.

Haka nan rayuwa ta cigaba da kasancewa, family’n Alhj Isma’il Yosouf komi
Zeezee, ba’a tashi kama wa Zeezee kai se in an tabbata Baba ya fita dan kuwa in
yana gida bayi bari. Ahaka yarinya take girma da kuma tashi cikin gata da tsantsan
so gun mahaifinta tun tana yarinya ya saba mata da samun duk wani abinda takeso.
There was a time a gidan biki Mama taje da Zeezee, Zeezee taga kayan wasa gun
wani yaro ta ringa kuka tana shure k’afafu itama tanaso, Baba najin haka ya ari
sample na kayan wasan yaje ya siyo mata exactly irinsa har guda biyu, itade Mama
tayi magana har ta gaji, ya zamanto ta zuba mai ido kawai yanzu. Shi da kansa
wataran zeyi nadaman abinda yake ma Zeezee.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com
PAGE 04

★★★
A kwana a tashi babu wuya game rai, Zeezee nada shekara d’aya (1 year) tal a
duniya yanzu! Yarinya son kowa k’in wanda ya rasa, sede Mama bata fita da ita
unguwa ko gidan biki ba idon kowa na akanta, ga kaya masha Allah tun tana Baby se
to-match ake sa mata kasancewar Mama ‘yar gayu ce ajin farko amma wani abu Zeezee
se tashi take da uban k’uiya, banda ‘yan gidansu bata san kowa ba again, a cikin
‘yan gidan nasu ma wani sa’in zab’a take, atimes in tana hannun Baba ko hannun Mama
batason zuwa.
Tunda Baba yake be tab’a celebrating birthday’n yaransa ba se akan na Zeezee.
Grand birthday party had’ad’d’e ya tsara wa Zeezee lokacinda ta cika 1 year.
D’imemen cake ya sai mata akayi celebrating, families ne da ‘yan unguwan da basu fi
a k’irga ba se friends nasu Mariam suka ziyarci party’n. Su Mariam se palli ake
anje an gayyato friends gabad’ai ana ta rawan kai. Se a ranan suke marmarin Zeezee
kan ba gobe saboda ganin yadda tayi kyau. Har dan haka suka so yin fad’a ita da
Omar. Sosai Zeezee tayi kyau ranan, an gyara mata gashinta cikin colourful ribbons,
bugu da k’ari kuma ga yadda glassy green princess ball gown nata ya mata kyau da
silver crown nata. Pictures suka sha sosai, suka ci suka sha suka kuma chashe!

_Wannan ke nan!_
Tun da Zeezee ta cika shekara d’aya da watanni biyar a duniya Mama ta soma
zancen yayeta amman inaaa Baba ya hana wai sam se Zeezee ta k’ara watanni uku ko
hud’u kamar yadda muslinci ya tanadar sannan ze yarda a yayeta.

“Haba Alhj dan Allah! Yarinyan nan de tayi wayo ko a yanzu aka yayeta ba’ayi
depriving nata komi ba, aiko a muslincen ma cewa akayi 18-20 months ba’a ce lallai
se yaro ya cika 20 months d’inba tukuna kuma yarinyan nan is 17 months now me
marabar 17 da 18?” Baba da yayi shiru yana sauraronta tun da ta fara wannan zuba
yace;
“Ki fad’i koma meh Hafsah, kin ga dama kita bayani daga nan har gobe but
believe me wallahi se yarinyan nan ta cika watanni ashirin (20) d’innan ki yayeta.”
Yayi maganan tare da miqewa da Zeezee a hannunsa.
“Ai sede in kai zaka cigaba da shayar da ita, yarinya gata doguwa ina ma ace
wacce bata girma ne! Ni wallahi har kunyan cireta nake cikin jama’a zan shayar da
ita, mutane se gani suke kamar ma tayi girma a shayar da ita saboda tsawonta.”
“Awww! Yanzu Hafsah sabida bakin jama’a kikeson tauye wa Zeezee hak’k’inta? Da
kyau ban yarda ki sake fita gidan suna ko biki ba har se in kin yaye Zeezee kuma ki
shirya nan da anjima zan kawo ta ki bata mama seta k’oshi sannan kiyi wani harkan
gabanki.” Be jira me Mama zata sake cewa ba yayi tafiyarsa.

Anyi haka da kwana uku tafiya ya tasowa Baba zasa Lagos saro laces da zannuwa da
sauran abubuwa, ranar Asabar tafiyar ta kama. Duk iyalan nasa suna a garriage suna
jiran ya shiga mota su mai ‘Allah kare’ amman ina seya kama hanyan zuwa mota ya
dawo ya karb’e Zeezee, itama data gane tafiya zeyi se kuka take tana ‘Baba’ duk
jikin sa yabi ya mutu seji yake kan ya fasa tafiya if only an yaye ta da yayi
tafiyan da ita. Da k’yar ya iya ya shiga mota yayi wining glass k’asa yana kallon
yadda Zeezee keta kuka hannun Mama.
“Toh ki lalasheta mana Hafsah!”
“Alhj wani irin lalashi ne ban ma yarinyan nan ba? Ai inba wai tafiya kayi ba
barata bar kukan ba.”
“Zeezee na yi hak’uri kinji barin dad’e ba zan dawo.” Cikin kuka take ta fad’in
“Baba... Baba... Baba.”
“Toh wallahi Hafsah sauran bayan tafiya na ki yaye Zeezee ki jira kiga abinda
zan miki.” Shiru tayi batace koami ba, “dake fa nake magana!”

“Yanzu Alhj nace wani abu ne? Allah dawo da kai lafiya.”
“Ameen, kuma kar ki barta da yunwa, Ibraheem, Mariam nabar Zeezee a kulawanku in
wani abu ya sameta ban yafe ba.”
“Toh Baba Allah ya kare hanya ya dawo da kai lafiya” yaran suka fad’i a tare.
D’ari biyar-biyar ya bisu dashi sannan ya tada mota nan fa Zeezee ta fara sabon
kuka ahaka Mama tayi ciki da ita. Yau Baba ya tafi washegari Mama ta yaye Zeezee,
yarinya data saba kowani minti shan nono kam seji take duniyar ma gabad’ai ba dad’i
tata kukan ‘mama... mama’ ina sede Mama ta d’au abinci ta bata haka zata k’i chi da
yamma Mama ta aika Ibraheem kasuwa ya siyo cerealac aka fara bawa Zeezee sam tak’i
sha ita wai se mama seda yunwa yaci k’aniyanta ta amince tasha cerealac d’in. Na
yini biyu Zeezee ta saba dashi sede still atimes zata ta kukan mama ko tata sa
hannunta cikin kayan Mama amman hakan bai sa Mama ta cire ta bata.

Baba kuwa tun tafiyarsa kullum se yayi video call yasa a had’a sa da Zeezee ya
tai mata wasa tana dariya. Sati d’aya cus Baba yayi kamar yadda Mama tayi addu’a
dan kuwa inhar ace before a week ya dawo tsab zece beji abinsa haka ba se an mayar
wa Zeezee nono amman yanzu da ya kai sati Zeezeen kanta ta manta da nonon. Pounded
yam and eghusi soup me rai da lafiya Mama ta shirya wa Baba sannan duk sukayi wanka
suka shirya tsaf bayan kintsa gidan da sukayi sannan suka fara zaman jiran shigowan
Baba.
Da misalin k’arfe 5:14PM Baba ya shigo Bauchi seda ya tsaya a Bauchi club ya
siyo masu gashi sannan ya k’arasa gida duk sun yi murnan dawowan sa tare da mai
sannu da zuwa sannan suka soma shiga da kayakin ciki, shide Baba Zeezee ya amshe
yana ta mata wasa sosai itama taji dad’in dawowan Babanta.

*~ *~ Zaune suke duka a parlour se cin tsire suke suna sipping cool Maltinan su
hankalin kowa na ayi a gama ci abud’e kaya. Baba dake tauna naman yana bawa Zeezee
yaga alaman kamar yunwa takeji dan yadda take taci har in be sa mata a baki da wuri
ba ta soma kuka. “Hafsah anya kuwa yarinyan nan ba yunwa takeji ba?”
“Yaushe ne ta sha cerealac natan?” Tayi maganan ba tare da tasan how and when
ba.
“Dawo baya meh kikace?” Baba yayi maganan cike da k’in gaskata abinda kunnensa
suka jiye mai. Nan fa Mama ta shiga kame-kame tayi tsit ta kasa cewa komai. “Dake
fa nake Hafsah, meh kikace?”
“Alhj...” Ta kasa k’arisa maganan.
“Yayeta kikayi koh?” Shiru... “Nace yayeta kikayi ko?!” Yayi maganar cikin
sautin tsawan da yasa Zeezee cusa kanta jikinsa. “Wai mesa bara’a tab’a gaya miki
magana kiji bane iyyeh? Mena gaya miki kafin nayi tafiyar? Kinsan ko gun Allah
kinada laifi koh?”
“Alhj kayi hak’uri” be sake cewa komai ba ya miqe ya bar musu wajen nan su
Mariam duka suka dawo da kallonsu kan Mama. Ibraheem yace, “Mama wallahi da baki
yaye wannan Zeezee ba a banza yanzu ran Baba ya b’aci d’an tsaraban da ya kawo
manan ma seya fasa badawa.”
“D’an banza abinda ke daminka kenan koh? Mschw!” Nan itama Mama ta miqe tabi
sahun Baba, d’akinta ta fara dubawa bata gansa ba hakan yasa ta nufa d’akinsa
direct, k’ofar tasamu a rufe tayi knocking shiru Baban dake zaune bakin gado yana
bawa Zeezee bobo yayi be amsa knock natan ba.

“Baban Zeezee na shigo?” Bata jira amsar sa ba ta bud’e k’ofar ta shige, ko


d’ago kai ya kalleta beyi ba se feeding Zeezee yake. A hankali tazo ta zauna
gefensa a bakin gadon tana kallon yadda Zeezee keta shan bobon sekuma ta bata
tausayi taji dama bata yaye tan ban. “Baban Zeezee kayi hak’uri nayi laifi.” Kamar
wanda bareyi magana ba yace;
“Ita ya kamata ki baiwa hak’uri bani ba” yayi maganar ba tare da ya d’aga kai ya
kalle ta ba. Daga nan Mama bata sake fad’in komi ba seda Zeezee ta shanyen bobon
sannan ta miqa hannu ta d’agota daga cinyan Baba ta aza ta kan nata. Hannu tasa ta
ciro mamanta ta gwada kaiwa Zeezee duk Baba na kallonta bece ko uffan ba sede abin
mamaki ko kallon nonon Zeezee bata son yi hasali kuka ma ta soma kai Baba ya kad’a
yace, “tsami kika ringa shafawa bakin nonon seda kika kori hankalin ta daga kai ko
ba haka ba?” Shiru Mama tayi duk kunya yabi ya kamata, “ko ba haka ba?” Ya sake
tambayar ta. A hankali ta gyad’a kai.
“Kin kyauta sosai bani ‘yata” ya miqa hannu ya amshe Zeezee.
“Alhj nafa baka hak’uri we are humans we all make mistakes wallahi da zata kama
maman yanzu na yarda zan cigaba da shayar da ita se lokacin da ka yarda a yayeta,
kayi hak’uri kaji?”
“Yaushe kika yayetan?” Chan k’asa k’asa tace, “washe garin tafiyar ka.”
“Hmm! kin kyauta Hafsah.” Hak’uri Mama tata bashi da k’yar ta samu ta shawo kansa
ya hak’ura. Bayan Sallan Maghrib duk ya tara yaran a parlour ya ciro wa kowa
tsarabansa Ibraheem da Omar English wears qualitative jeans da T-shirts set biyar-
biyar, Mariam laces uku masu tsadan gaske da atamfofi super biyu, se Yasmeen laces
biyu da ‘yar kanti masu kyau guda uku. Mama kuma laces biyar da atamfofi super
biyu, se Yasmeen laces biyu da ‘yar kanti masu kyau guda uku. Mama kuma laces biyar
da atamfofi super biyu sena uwa uba Zeezee wanda suke nan fiye a k’irga.

★★★
Life couldn’t be better for Zeezee! Wato duk wani abinda take so shi ake mata
a gidan sede in Baba bai gida, yarinya tana girma tana dad’a kyau da kuma dad’a
kama da mahaifiyarta. Cikin rumfa da rayen Allah Zeezee ta kai har shekaru biyu da
watanni goma a duniya (2 years 10 months) baki ya nuna ras se aukin surutu da kuma
rashin ji da b’arna. Sede duk laifin da tayi komin girman sa Baba bai bari ko tsawa
ayi mata bale wai amata duka koda wasa ba wanda ya tab’a d’aga hannu ya daki Zeezee
harta Mama da kanta.

*~ *~
Yau ranar ta kasance Sunday as usual tin k’arfe 7:00AM Zeezee ta tashi ta
d’ago babban teddy bear nata sannan ta sauk’o daga kan gadonta fuskan Mama da Baba
ta leqa taga du bacci suke sannan a hankali ta fice daga d’akin ta sake ja musu
k’ofar. D’akin su Mariam ta nufa ta bud’e ta tarar da su suma suna ta bacci kan
gadon nasu ta d’ale ta fara tsalle-tsalle a kai, badan komi ba dan kawai ta tadasu.
Cikin bacci Mariam ta soma magana tun bata bud’e ido ba tasan waye da d’anyen aiki
haka.

“Zeezee dan Allah kiyi wa Allah kiyi hak’uri ki koma d’akin ku Baba na
kiranki.”
“K’ayyan kine Baba na basshi.”
“Toh muma ki bar mu mana muyi baccin.”
“O’o ce kun tashi dan sha tea.”
“Fisabilillahi Zeezee sau nawa kike shan tea a rana? Kibari se anjima.”
“O’o ni yanzu nake sho” ta cigaba da tsalle kan gadon. A fusace Mariam ta miqe
ta galla mata wani mugun harara aiko Zeezee dan munafirci tasa kuka sekace dukanta
akayi. Yasmeen da k’aran kukan Zeezee ya tada ta tace, “Adda Mariam kin shiga uku
me kika mata?”
“Kibar munafuka ko tab’ata banyi ba.”
“Zeezee dawo” cewar Yasmeen. Kafad’a Zeezeen dake bakin k’ofa tana k’okarin
bud’ewa ta buga da nufin o’o. “Wayyayi chena fad’a ki da Baba.”
“A’a Zeezee ta yi hak’uri kar kije zo abinki kinji?” Cewar Yasmeen trying to
sooth her.
“Ki barta tajen in ta fasa ai in taga ana tsoron takai k’aran mutum ne take jin
dad’i yake kuma sake bata garab’asan cigaba da yin hakan, kije ba wanda ya rik’e
miki k’afa.” Mariam na kaiwa nan ta juya masu baya tare da rufe fuskarta da bargo
ta cigaba da kwanciya. Zeezee na barin d’akin tasa sabon kuka ahaka har ta isa
d’akinsu Mama ta hau jijjiqa Baba. Jin kukanta take ya tashi ya zauna, “ya haka
Zeezee keda waye?” Ya azata kan cinyansa. Cike da shakwab’a kan yadda ta saba tace,
“Adda Mayyam.”
“Ai kaman na sani muje mu sameta.”

**
Banging k’ofar d’akin su Mariam yayi firgit suka miqe zaune dukansu. “Me kika
mata?” yayi tambayar wa Mariam yana me hararta.
“Nifa ba abinda na mata tazo muna bacci tana mana tsalle-tsalle kan gado shine
nace ta bari take wannan kukan.”
“Laaa! Baba wayyayi kayyan tane, mari na tayi a zuciya na.”
“A zuciyanki Zeezee? Ni?!” Mariam ta nuna kanta. “Yaushe ma naga zuciyan naki
bale in mara?”
“Eh a zuciya na.” Zeezee ta kuma jaddada mata.
“Sannu ko k’anwata” Baba ya shafa kan Zeezee “yi hak’uri” sannan ya dawo da
kallonsa kan Mariam “Allah Mariam ki kiyaye ni in sake jin kin tab’a yarinyan nan
kiga! Ke shikenan kullum kina cikin bin gindin yarinya kina sata kuka sekace ba
babba ba, this should be the last time I’ll warn you again.”
“Allah sark-”
“Rufa min baki!” yayi saurin katse ta.

“Shikenan Zeezee?” Kai ta gyad’a a shagwab’ance sannan tace, “zan sha tea.”
“Tea? Ko a dafa miki Indomie kina jin yunwa ne?” Ya matse cikinta yana mata
cakul-kuli, nan ta hau dariya.
“Eh” ta basa amsa.
“Oya Mariam miqe ki je ki dafa mata Indomie da k’wanta guda biyu akai kafin nan
Yasmeen kije ki had’a mata tea sauran ki d’ibar mata madara kisha kuma.”
Kamar wacce zatayi kuka Mariam tace, “wallahi Baba ko an dafa mata Indomie’n ba
ci take ba haka jiya ma k’arshenta zubar wa akayi kawai dan tasa nutum aiki ne.”
“Toh ina ruwanki ai bake kike siya ba, shegen rashin son aiki maza tashi yaso
kuka gama seku koma baccin, ku tashi mana!” A sanyaye suka miqe suka nufa bayi dan
washing up se gunguni suke.

~* ~* Tea’n ta me kauri Yasmeen ta kawo mata tana zaune kan dining table nata da
chair ta shanye tas, a rayuwa Zeezee akwai son tea bayan 25 minutes Mariam dake ta
kumbure kumbure har yanzu ta kawo wa Zeezee abincin. As expected Zeezee ta
jagualgwala taci kad’an ta k’ara mai abinta.

_09:34AM_
Su Mama na a kitchen suna had’a breakfast, bayan Yasmeen tayi wa Zeezee wanka
ta saci jiki tayi d’akinsu Mariam daidai gaban dressing mirror ta tsaya ta fara bi
ta kan cosmetics d’in tana applying ita a dole tana kwalya, kaca-kaca tayi da
kayakin kwalyan, data kama sharpening eye pencil seda taga k’arshen shi, data waina
jan baki seda ya karye, liquid eyeliner ta bud’e ta zana a saman girarta saura ta
zagar a k’asa. Komi seda ta b’ata sannan ta masu wanka da turare, daidai tazo
fitowa kenan tayi kacib’us da Mariam dake shigowa. Hannu bibbiyu Mariam ta aza kan
bakinta da taga fuskan Zeezee.
“Ki masha min in wuce” cewar Zeezee tana k’ok’arin kare fuskanta.
“Da kayan kwalyan wa kika-” bata k’are maganan ba idanunta suka sauqa kan
ta’addancin da Zeezee ta masu da kayan kwalya. Fincikota tayi da hannu takai ta
gaban mirron.

“Meh amfanin haka? Ban hanaki tab’a min kayan kwalya ba?” Ganin haka Zeezee tasa
ihu wane ana cire mata rai, Baba da Mama ne suka shigo a tare a cewansu ma ko
Zeezee ta fad’i ne. Zeezee na ganin Baba ta ruga aguje wajensa ya d’agata sama
“Baba kaga Adda Mariam koh?”
“Me haka a fuskan ki Zeezee?” Mama ta tambaya.
“Mama dubi fa, kalli abinda ta min da kayan kwalya komai seda ta b’ata kuma da
gangan take.”
“Taya zaki ce da gangan?” Cewar Baba, “bakiga yarinya ce ba? A jinki in tasan
whats right and wrong zata yi abinda tayin neh?”
“Amman fa Baba this is not her first time kwanaki da tayi seda na mata magana”
tayi maganan idanunta na cikowa da hawaye.
“Toh Mariam kema seda na fad’a miki ki riga sa kayan kwalyan naki cikin wardrobe
kina rufewa achan Zeezee barata iya tab’awa ba.”

“Shikenan Zeezee?” Kai ta gyad’a a shagwab’ance sannan tace, “zan sha tea.”
“Tea? Ko a dafa miki Indomie kina jin yunwa ne?” Ya matse cikinta yana mata
cakul-kuli, nan ta hau dariya.
“Eh” ta basa amsa.
“Oya Mariam miqe ki je ki dafa mata Indomie da k’wanta guda biyu akai kafin nan
Yasmeen kije ki had’a mata tea sauran ki d’ibar mata madara kisha kuma.”
Kamar wacce zatayi kuka Mariam tace, “wallahi Baba ko an dafa mata Indomie’n ba
ci take ba haka jiya ma k’arshenta zubar wa akayi kawai dan tasa nutum aiki ne.”
“Toh ina ruwanki ai bake kike siya ba, shegen rashin son aiki maza tashi yaso
kuka gama seku koma baccin, ku tashi mana!” A sanyaye suka miqe suka nufa bayi dan
washing up se gunguni suke.

~* ~* Tea’n ta me kauri Yasmeen ta kawo mata tana zaune kan dining table nata da
chair ta shanye tas, a rayuwa Zeezee akwai son tea bayan 25 minutes Mariam dake ta
kumbure kumbure har yanzu ta kawo wa Zeezee abincin. As expected Zeezee ta
jagualgwala taci kad’an ta k’ara mai abinta.

_09:34AM_
Su Mama na a kitchen suna had’a breakfast, bayan Yasmeen tayi wa Zeezee wanka
ta saci jiki tayi d’akinsu Mariam daidai gaban dressing mirror ta tsaya ta fara bi
ta kan cosmetics d’in tana applying ita a dole tana kwalya, kaca-kaca tayi da
kayakin kwalyan, data kama sharpening eye pencil seda taga k’arshen shi, data waina
jan baki seda ya karye, liquid eyeliner ta bud’e ta zana a saman girarta saura ta
zagar a k’asa. Komi seda ta b’ata sannan ta masu wanka da turare, daidai tazo
fitowa kenan tayi kacib’us da Mariam dake shigowa. Hannu bibbiyu Mariam ta aza kan
bakinta da taga fuskan Zeezee.
“Ki masha min in wuce” cewar Zeezee tana k’ok’arin kare fuskanta.
“Da kayan kwalyan wa kika-” bata k’are maganan ba idanunta suka sauqa kan
ta’addancin da Zeezee ta masu da kayan kwalya. Fincikota tayi da hannu takai ta
gaban mirron.

“Meh amfanin haka? Ban hanaki tab’a min kayan kwalya ba?” Ganin haka Zeezee tasa
ihu wane ana cire mata rai, Baba da Mama ne suka shigo a tare a cewansu ma ko
Zeezee ta fad’i ne. Zeezee na ganin Baba ta ruga aguje wajensa ya d’agata sama
“Baba kaga Adda Mariam koh?”
“Me haka a fuskan ki Zeezee?” Mama ta tambaya.
“Mama dubi fa, kalli abinda ta min da kayan kwalya komai seda ta b’ata kuma da
gangan take.”
“Taya zaki ce da gangan?” Cewar Baba, “bakiga yarinya ce ba? A jinki in tasan
whats right and wrong zata yi abinda tayin neh?”
“Amman fa Baba this is not her first time kwanaki da tayi seda na mata magana”
tayi maganan idanunta na cikowa da hawaye.
“Toh Mariam kema seda na fad’a miki ki riga sa kayan kwalyan naki cikin wardrobe
kina rufewa achan Zeezee barata iya tab’awa ba.”

“Ahtoh! In har dagaske kike, kuma me kika ma Zeezee take ihu?”


“Duka na tayi a zuciya na.”
“A zuciyanki koh? Yi hak’uri, wallahi Mariam ki kiyaye ni sau biyu nake miki
magana kenan yau na uku duka ne.”
“Alhj amman Zeezee’n ma kai mata magana ta rage b’arna ko jiya a islamiyya seda
ta yage wa Mrs. Bee littafi.”
“Lokacin ta ne ba maganan da zan mata ke Allah kad’ai yasan kalan b’arnan da
kikayi kema” yana kaiwa nan ya fice k’arisawa Mama tayi kusa da Mariam da har ta
fara kuka tana bata hak’uri haka seda Mama ta bata dubu biyu tayi shiru.

Su Baba suna zaune a tsakar gida da Zeezee’nsa se hayewa jikinsa take tana wasa
wane d’an biri, Ibraheem ne ya dawo daga yawonsa, da wayansa riqe hannunsa ya bashi
full attention nasa a haka har ya k’arasa d’aki Zeezee na ganin shigewan sa ta taso
daga jikin Baba tabi bayansa. Zaune ta tarar dashi kan couch dake d’akinsu a
hankali taje ta zauna gefensa ko uffan bece mata ba se chatting nasa yake yana
murmusawa time-to-time, da Zeezee ta d’anyi observing nasa seta gane chatting yake
a whatsapp. “Ya Ibyaheem da whashapp.” tace da shi.
“Ya akayi Zeezee?”
“Ya Ibyaheem zanyi game.”
“A’a Zeezee ni gaskiya bara ki kashe min battery ba duk games d’in ma gogewa
zanyi” ba tare da tace mai komai ba ta miqe ta kama tafiya “k’ara na zaki kai gun
Baba koh? Zo in sa miki toh.” Ko ta kansa batayi ba taje ta samu Baba ta fara kuka
“wa ya tab’a min k’anwa?”
“Ya Ibyaheem ne.”
“Meh ya miki shi kuma?”
“Yak’i bani wayanshi nayi game.”
“Ibraheem! Ibraheem!”
“Na’am Baba!” ya amsa tare da goge dukka games na wayan nasa sannan ya fito.
“Gani Baba” ya durqusa gefe guda.
“Ina wayan naka? Bata tayi game d’in.”
“Baba nifa ba game a waya na.”
“Ka goge kenan?” Kafin Ibraheem ya amsa Zeezee tace, “eh Baba yace min zeyi
deleting.”
“Ni? Yaushe nace miki haka Zeezee?”
“A’a barshi Zeezee jeki amso wayan nasa.”
“Baba me zaka min da waya?”
“Downloading mata zanyi ba ka iya gogewa ba? In na sake installing seka sake
gogewa kaine da asaran data dan ba shi ze hanani next in ka goge na kuma
downloading ba, amso min wayan Zeezee.”

“Baba in na fita anjima zan tura a wayan friend d’ina wallahi ba nida data nima
managing nakeyi.”
“Wannan kuma damuwan ka amso min Zeezee” haka Ibraheem naji yana gani Baba ya
shiga playstore “wani game kikeso K’anwa ta?”
“Shubway churfers da plincess salon.”
“Zeezee har biyu Baba wallahi data na ze k’are.” Banza dashi Baba yayi yama
Zeezee downloading duka sannan ta fara playing. “Kaje in ta gama zata kawo maka
wayar.” Kamar wanda zeyi kuka Ibraheem ya kalli Baba sannan Zeezeen dake ta game
nata ya miqe ya bar gidan ma gabad’aya.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
beeenovels.blogspot.co.ke

PAGE 05

*December, 2016*

_This page is in honour of *Fathooma Ali* a great fan I never knew I had. I
have recieved your message, thank you so much for the love stay blessed Habibti
#OneLove💕_

Game Zeezee tai tayi kamar ba gobe, dan kanta ta gaji da bugawa ta shiga
photos tata kallon pictures saura kuma ta rik’a gogesu a takaice seda tayi mai
battery low wayar ta mutu gabad’ai sannan ta kai mai wayan alokacin yana zaune a
parlour a side nasu yana assignment nasa na Technical Drawing “Ya Ibyaheem ga wayan
ka” ta fad’i tare da ajiye mai a gefensa ko kallonta beyi ba ya cigaba da abinda
yake chan tace, “Ya Ibyaheem zane kake yi?” Nanma ko uffan be ce mata ba feeding
bottle nata da ke rataye a wuyanta wanda tea ne had’e ciki ta d’aga zata bud’e dan
sha. A garin haka tean da yake ciki ya zube kan zanen Ibraheem, “shikenan ai kin
huta yanzu! Tashi ki ficemin daga kallo!” ya daka mata tsawa.
Lamo tayi tana kallonsa a yayinda hawaye ke ciko mata a ido, “baraki fita bane?!
Ace mutum kullum se bad luck fice min! Yaso in Baban naki ya dawo ki fad’a mai, get
out!” kuka ta soma ba makawa amman ko a jikinsa, kamar kyaftawan ido ya fisgota da
hannu ya direta bakin k’ofar tare da rufewa harda kwad’o. Kuka Zeezee ta ringa yi
wajen haka dan kanta tayi shiru sabida Baba yafita bai gida Mama kuwa nacan
d’akinta tana kwance. Mariam dake tsakar gida ko a kwalan rigarta ta lalasheta
daman acike take da ita for what she did to her makeup items earlier.

Chan da ta gama kukan ta k’arisa wajen garriage inda takejin hayaniyan su


Omar. Zaune ta tarar dasu yana ma Yasmeen homework nata na ‘paper mache.’ Waje ta
nema ta zauna kusa dasu itama sannan tace, “Ya Omal meh kukeyi?” Kamar wanda bare
amsa taba yace, “homework.”
“Ya Omal paper ne kuka dafa?”
“Eh da Allah shegen tambayoyi sekace ‘yar jarida kinga baraki iya yin shiru ba
find your exit” daga nan Zeezee bata sake cewa komai ba sede duk abinda suke tana
observing nasu.
K’arfe uku suka gama shiri suka wuce islamiyya nan Zeezee ta samu kanta, da full
confidence nata taje tana k’ok’arin bud’e k’ofa only to find it locked kamar Mama
tasan b’arna data saba zatayi any moment yayyun nata suka barta ita kad’ai a gida,
dalilin rufe k’ofan d’akin datayi kenan don restraining nata.

“Mama ki bud’emin k’ofa.” Banza da ita Mama dake shirin bacci tayi.
“Mama ki bud’e.” tayi maganan tana jijjik’a k’ofan.
“Saboda kije kiyi b’arna ba taho mu kwanta in bara ki kwanta ba ga kayakin wasan
ki can se kiyi wasa.”
“O’o ni ki bud’e min.”
“Barin bud’en ba mab’arnaciya kawai.” Kuka Zeezee ta soma rusawa wajen tun Mama
tana ignoring nata har ya soma daminta haka seda ta bud’e mata k’ofar bayan jan
kunnen data mata na karta tab’a kayan yayyun ta. Like a good girl tace ita wasan ta
zatayi. Mama na maida k’ofanta Zeezee ta zarce d’akinsu Mariam luckily yau sun
mance basu rufe k’ofan su ba nan ta samu ta shiga. Bata nufi ko ina ba cikin d’akin
se inda suke jera school bags nasu, na Yasmeen taja ta bud’e ta ciro notebook d’aya
sannan ta fice izuwa kitchen inda ta nemo tukunya ta loda ruwa ciki sannan ta bud’e
littafin Yasmeen wanda ya kasance Mathematics ta soma yagewa tana kacancanawa tana
sawa cikin kwanon in aka tambayeta wai haka taga su Omar sunyi d’azu. Hakan ta
cigaba da yi seda taci rabin littafin sannan ta ajiye ta d’au tukunyar ta aza akan
charcoal stove, ashana ta shiga nema wanda bata samu ba saboda chan saman cupboard
Mama ke ajiyewa. Dan kanta ta hak’ura bayan ‘yan mintuna ta sauk’e tukunyan sannan
ta d’ibo cups da plates da saucers duk bibbiyu ta zauna tsakar gidan itama a dole
zatayi paper mache.

Moulding jikin cups d’in ta shiga yi tana manna papers d’in jiki amman ina se
sumb’ilewa suke, haka ba fashi ta tayi sannan data gama taje ta jerasu layi d’aya
da inda Omar ya ajiye wa Yasmeen nata.

_5:30PM_
Anan yaran suka dawo daga islamiyya se Allah Allah Yasmeen ke ta ajiye jakarta
ta duba home work nata ko yayi dan gobe Monday zasuyi submitting. Dad’i sosai taji
ganin Zeezee bata tab’a mata abinta ba sede ganin wasu cups datayi a gefe bayan
data gama duba nata seta d’au na Zeezee tana dariya “wai! Ji shirme itama wai a
dole tayi pap-” maganan da Yasmeen bata k’arisa ba kenan ganin handwriting nata
jikin paper’n data lura da kyau kuwa taga Mathematics note nata ne. Salati ta saki
sannan tasa gudu zuwa d’akinsu ta shiga neman Maths note nata sede its nowhere to
be found. Dam idanta ya cike da hawaye ta kama hanyan d’akin Mama dan kai k’ara,
tana fitowa taga rabin Maths note nata a k’asa gabad’ai ya canza kamanni tunanin
irin dukan da Mr. Chika (Maths teacher’nsu) ze mata kawai take. D’akin Mama ta nufa
tana kuka, Zeezee da tasan this was comig tuni taje ta lab’e jikin Mama.
“Ya haka Yasmeen waya tab’aki?” Cikin sautin kuka tace, “Mama kalli fah, kalli
abinda Zeezee tamin da Maths notebook d’ina” se kuma ta fashe da kuka. Amsan
littafin Mama tayi ta k’are mai kallo sannan ta mai da kallonta kan Zeezee datayi
tsit, daga bisani tace;
“Mama bani bane.”
“In ba keba ai nice, mesa bakiya ji ne iyye? Meh amfanin hakan? Wallahi ga ta
Yasmeen kimata duk abinda zaki mata nan gaba ko cewa akai ta tab’a jakarki barata
tab’a ba” da hannu Yasmeen ta finciko Zeezee ta nad’a mata na jaki, Mama na
kallonsu batace komai ba se anan Yasmeen taji tad’an huce. Kuka Zeezee take wane
dan shi aka kawota duniya. Chan ta wuce wajen garriage ta cigaba da kukan har tazo
tayi shiru, tana jin k’aran motan Baba ta soma sabon kukan aiko parking na arziki
Baba beyi ba yafito yana tambayarta ita da waye. Nishinta har wani sama sama yake
tace, “Mam.. Mama ne tasa Yasmeen tamin duka.”

“Duka?! A dalilin meh? Muje ina Maman naku?” tun daga gun ya shiga k’wala wa
Mama kira.
“Alhj lafiya haka?” Tayi maganan tana k’ok’arin fitowa daga kitchen.
“Me kika sa Yasmeen ta mata? Yasmeen! Yasmeen! Kema fito nan.” Nan da nan ta fito
rik’e da Maths note nata.
“Ehen ina jinki kibani k’wararren dalilin da zaisa kice Yasmeen ta daka min
k’anwa.”
“Yasmeen mik’a mishi littafin naki” cewar Mama, nan Yasmeen ta miqa wa Baba
bayan daya k’are wa littafin kallo yace, “wa yayi maki haka da littafin?”
“Zeezee ce.”
“Taya kika san itan ce? A idonki tayi ne?”
“Alhj wani irin magana kake haka? Mu biyu da ita aka bari a gidan nan ko ni
kakeson kace nayi wannan b’arna?”
“Ba abinda nake nufi ba kenan abinda nake nufi shine ku dena zato tunda ba
kamata kukayi in the process ba, ko ke kikayi Zeezee?” Kai ta girgiza alaman a’a.
“Toh baga erin saba kun kama kun d’au alhak’in yarinya a banza.”

“Baba wallahi Zeezee ce, ita tamin kuma Maths teacher’n mu duka na zeyi
wallahi.”
“Naji gobe zamu je makarantar naku na masa bayani amman koda wasa karki kuskura
ki sake d’aga hannu ki tab’a Zeezee ever!”
“Meh kake nufi da hakan Alhj? Baka yarda Zeezee ce tayi wannan tabargaza ba
kenan ko meh?”
“Taya zan yarda bayan ban kamata red-handed ba?”
“Lallai kam!” Mama ta had’e hannunta biyu ta dafe a ciki “baka yarda bama bale
ace ka ja mata kunne koh?”
“A dalilin me zan ja mata kunne, ba abinda zan mata.”
“Toh wallahi Alhj ka cigaba kai da kanka wataran zakayi nadaman abinda kakeyi,
yarinya ace bata jin maganan kowa se naka Allah kyauta!”

~* ~*
Da daddare bayan Sallan Isha’i Baba da Mama suna d’akinsu yaran suma haka a
d’akinsu. Zeezee ne zaune a parlour ta baje kayakin wasanta se wasa take chan da
taji ta gaji ta miqe ta nufa d’akinsu Mariam inda duk yayyun nata suke mik’e suna
kallo a laptop na Ibraheem ba tare da tace dasu komai ba ta jawo k’ofan tayi d’akin
Mama taje ta samu Baba.
“Baba zan kayyi fyozen (Frozen.)”
“Toh je kice wa Ibraheem ya sa miki.”
“Toh” tace sannan taje ta samu Ibraheem. “Ya Ibyaheem Baba yace kasha min
fyozen.”
“Bara asa ba ke baki tashi kallo se kinga mutane sunayi toh bara’a sa ba, se mun
gama za’a sa maki.” Ibraheem yayi maganar ba tare da ya kalli direction nata ba.
“Dai-dai kenan” cewar Mariam “wai ita a rayuwa dan iskanci seta ga mutane suna
kallo take fad’in zatayi toh bara a saba tunda ba laptop naki bane.”
“Muguwa ba, naji ba nata bane amman naga ai ni na saya koh? Ni ke da iko dashi”
atare suka d’aga kai suka ga Baba tsaye gabansu da alama tun d’azu yake tsaye gun.
“Baba!” Cewar Mariam.
“Eh ni, ai kaman nasan this was coming, ke bara ki tab’a barin halinki na
muguntan nan bako Mariam? Oya sa mata frozen d’in.”
“Allah sarki Baba sauran episodes biyu mu k’are season d’in fah.” Ibraheem said
trying to explain calmly.
“Se ku jira in Zeezee tagama ku k’arisa, sa mata ka kuma kai mata laptop d’in
chan d’akina tayi kallonta ba tak’ura.”

Se kumburi da gunguni suke Ibraheem ya sa mata frozen d’in yakai d’akin Baba ya
ajiye. Bayan dawowansa d’akin ya d’au wayansa kamar ance ya shiga gallery yana
shiga yaci karo da tabargazan da Zeezee ta mai almost half of his pictures are gone
kuka ne kawai beyi ba.

Washegari Monday duk yaran sun shirya school kafin nan seda suka kukkule
d’akunansu suka bawa Mama key gudun kar uwar b’arna ta musu tabargaza. Aikuwa bayan
Mama ta mata wanka ta karya ta nufa d’akinsu Ibraheem taji a rufe tayita jijjigawa
ganin yak’i bud’uwa kawai ta je ta samu Mama tayita mata k’ananun b’arna a kitchen
tana sata surutu. Da Azahar Baba ya dawo gida as always Zeezee taje ta mai oyoyo a
parlour ya direta ya d’ago d’aya daga cikin ledojin daya shigo dasun ya bud’e
sabuwar ipad ce pil ciki. Cike da murna Zeezee tace, “Baba ipad na waye?”
“Naki ne k’anwata” daidai nan Mama ta shigo d’akin. Tsaye tayi in akinbo style
tace, “Alhj menaji kace?”
“Me ruwanki? Ipad na siyo mata.”
“Ipad fa kace Alhj?” Kasa gaskata kunnenta tayi ta k’ariso ciki taga ipad d’inne
dagaske hannun Baba.
“Lallai Baban Zeezee ina jinka da Yasmeen last week take ce maka ka sai mata
waya duk kusan kowa a ajinsu nada waya k’ememe kace wa yarinyan nan ba kada kud’i
but here you are ka saya wa ‘yar Zeezee ipad bama tab ba ipad gabad’aya ko me
zatayi dashi ban sani ba.”

“Kinsan meh Hafsah in bakinki bare fad’i alkhairi ba seki fice min daga d’aki
daman bani na gayyato kiba.”
“Ai gaskia ne wallahi baka kyautawa, Yasmeen ya kamata ka sai ma waya ba Zeezee
ba kaima kasani.”
“Mschw! Ke dama kika kama surutu baki gajiya” hannu yasa a aljihunsa ya zaro
dimbun kud’ad’e sannan ya irga dubu goma ya danka mata “sekiyi mata ciko ki siya
mata.”
“Ta rage hanya dai” tace tare da ficewa.
“K’anwata karki kula Mama kinji? Kishi suke saboda basu da ipad” yace da Zeezee
dake zaune kan cinyarsa. “Mu had’a miki a charging koh?”
“Eh Baba akwai games a ciki?”
“Sosai ma K’anwa ta kuma zan sake miki downloading sabi.”
“Yauwa Baba nima barin bawa Ya Ibyaheem da Ya Omal ba tunda suna min rowan
wayansu.”
“Ai kuwa naki ne ke kad’an ki daga yau ba ruwanki da wayoyinsu tunda ga naki nan
babba”
“Yeyy Baba” nan ya had’a mata a charging, an hour later ya zaro yayi mata
downloading games turum yarinya kam dama ta riga tasan kan amfani da torch screen.
A waje ta zauna kan sallayanta tayi cross-legging legs nata ta hau buga game.

2:30PM yaran suka dawo daga school. Da an gansu anga wanda suka kwaso gajiya from
school Yasmeen ce ta soma shigowa harta wuce Zeezee seta kuma dawowa dan gaskata
abinda idanunta suke gane mata. “Ipad!” Tayi maganan tare da k’wararo idanunta waje
disbelievingly. “Ya Omar kuzo kuga abin al’ajabi.”
Daga nesa Ibraheem yace, “wai me neh kike wani tafe hannu?”
“Kude kuzo mana!” A sanyaye suka k’ariso wajen duk baki suka wangale ganin ipad
hannun Zeezee, itako yi tayi kaman batasan suna tsaye a kanta ba se game nata take
tayi.
“Zeezee” Ibraheem ya kira sunanta seda ta b’ata lokaci sannan ta amsa “meh?”
cike da rashin kunya.
“Kalleni” ya buk’ace ta. Nan ma seda ta b’ata lokaci sannan tasa pause ta d’ago
sexy long eyes nata tana kallon sa, “meh?”
“Ipad na waye a hannunki? Uncle Abdallah yazo ne?”
“Nawa ne” ta basa amsa confidently. Dariyan rainin hankali suka hau yi dukansu
especially ma Mariam da tanan tafi kauri dama. “Ipad naki?” Omar yayi maganan in
between laughter.
“Is good to dream big my sister” cewar Mariam harda hawaye dan dariya.
“Uban wa ya siya miki?” cewar Ibraheem.
“Ubanku ya siya mata” cewar Mama dake tsaye akansu tana kallonsu tun d’azu. Nan
duk suka dawo da kallon su a gareta.

“Mama jokes apart please ipad na waye?”


“Gashi kuwa ta fad’a muku, nata ne Babanku neya siya mata.”
“Buro uba!!” Cewar Ibraheem “yanzu ipad Baba ya siya ma yarinyan nan?”
“Eh cewa yayi kuna mata rowan waya and he can’t stand it kuna ma k’anwarsa rowa
ya siya mata uwa uba gabad’aya.”
“Amman shine last week nace Baba ya siya min waya yace min baida kud’i?” Yasmeen
ta tab’e baki.
“Karki damu nasa sa gaba seda ya bada dubu goma zan cika miki mu sai miki
wayar.”
“Yeyy!!” Ta hau tsalle. Dogon tsuka Omar yaja, “Banza mena murna? An siya wa
k’anwarki ipad ke za’a had’aki da wayan da befi na 20k ba kuma kina murna.”
“Yo naga kai ma Zeezeen k’anwarka ce kuma bakada ipad d’in.” tayi retaliating.
“Wallahi barata saku ba wai bindiga a ruwa, nima se an canza min waya.” Mariam
tayi k’wafa ta fice daga wajen. Ibraheem sarkin wayo ya k’arisa wajen Zeezee yana
shafa dogon sumanta “My Zeezee taho muje d’akinmu yau na siya miki big bomb.”
“Dagaske Ya Ibyaheem?”
“Sosai ma taho muje” ba gardama ta bisa d’akinsu bayan ya canza kaya ya d’au
mata sweet d’in as promised ya bata seda ya bari hankalinta yagama bin kan sweet
d’in yace, “Zeezee zaki ara min ipad naki?”
“O’o ba nima kana min rowan wayan kaba.”
“Ai na dena yanzu, bakiga na baki sweet ba, so zaki ara min na ‘yan minutes ne
kawai friends d’ina zasu so inason in nuna musu inada ipad da laptop ne kinji?”
“Ni banasho su b’atamin ipad d’ina” tayi maganan tana lasan sweet nata.
“Ai barin ma basu ba bale su b’ata miki so zaki bani?” Ta gyad’a mai kai. “Yauwa
My Princess and one more thing please koda sunzo kada ki shigo nan side d’in
kinji?” Like a good girl ta gyad’a mai kai.

Bayan sallan La’asr friends na Ibraheem suka iso ina irin shi big boy d’innan
gabansa mac book ne da ipad se palli yake musu yana wani feeling achan d’akin Mama
Zeezee ce zaune se shan sweet da Ibraheem ya had’ata dashi take chan fa taga barata
iya hak’ura da ipad nata ba ta miqe ta nufa BQ kaman yasan da haka yasa lock.
Knocking ta shiga yi seda ya taso ya bud’e, ganinta da yayi ba k’aramin razana sa
yayi ba murya chan k’asa k’asa yace, “Zeezee ya mukai dake?” Yana maganan yana
leqan friends nasa da suke danne-danne cikin ipad d’in. “Kije ki jirani d’akin Mama
kinji?”
“Ina ipad d’ina?” da sauri yasa hannu ya toshe mata baki ai ta shiga shuresa, a
garin haka taga ipad nata rik’e da friends nasa fisge kanta tayi da k’yar ta sa ihu
“ku bani ipad d’ina!” ta fad’i da k’arfi. Ibraheem da ji yake kaman ya tone k’asa
ya shige dan kunya ya gama yima friends nasa k’arya ipad nasa ne Zeezee tazo ta
fasa mai tyre.

Atare friends nasan suka juyo suna kallon Zeezee fuskokinsu d’auke da tambaya.
“Wayyayi sena gaya wa Baba ka basu ipad d’ina.” Fuska yaci “wani erin ipad naki? Ke
shikenan duk abinda aka saiwa mutum seki ringa fad’in naki? Mschw! In game kikeso
ai seki fad’a a sa maki Auwal miqo min ipad d’in da Allah” yayi maganan a fusace
erin baya son bullshit d’innan “gashi!” ya miqa mata “sauran kije ki b’ata min abu
na” daga nan ya turata waje kafin ta sake sakar masa da wani bomb.
“Phew!” Yayi sighing sannan yaje ya zauna ganin friends nasan basu bar binsa da
kallo ba ya tuno da wata dabara “dudes kun kalli empire season 3 kuwa?”
“A’a please kana dashi?”
“Sosai ma!” yaja laptop nasa ya sa musu da haka ya samu ya gusar masu da tunanin
incident daya farun daga brain nasu.

_9:12PM_
Mariam ce tsaye bakin k’ofan d’akin Baba tun d’azu ta kasa gathering courage da
zata shiga seta bud’e baki zatayi sallama se ta kasa ana ckin haka Zeezee tazo
shigewa ko ganin Mariam ma batai ba dan yadda hankalinta yabi kan game da take.
Dabara ce ta fad’o wa Mariam ta kira sunanta cikin wani irin salo, “Zeezee
kyakkyawar gidan mu” se anan Zeezee ta d’ago kai tana kallonta “meh?” Tayi snarling
at her
“Haba *_YAR GATAN BABA_* meh nayi kuma kike b’atamin rai haka?” Tayi maganan
tare da tsugunawa tana gyara mata ribbons na kanta. “Ipad naki yayi kyau sosai.”
“Na sani ai.” ta fad’a mata gatsau da alama ‘yan rashin kunya suna kusa yau.
“Allah baki hak’uri beauty meh kama da Mama, Zeezee nace zaki tayani yima Baba
magana nima a canza min waya?”
“O’o zaki ce a shiya miki irin nawa bana sho.”
“Wane ni? Ai wannan naki ne ke kad’ai ni d’an k’arami za’a siya min kinji My
Darling Sister?” Shiru Zeezee tayi tana nazari da k’yar Mariam tasamu tayi
convincing Zeezee ta yarda zata yima Baba maganan.

Bayan shiganta Mariam ta kasa kunne jin abinda Zeezee za tace. Gado ta haye ta
samu Baba.
“K’anwata zaki kwanta ne?”
“A’a Baba a canza wa Adda Mayyam waya.”
“Ita ta turoki ko?” Nan zuciyan Mariam ya buga Allah sa kar Zeezee ta tone ta.
“A’a ba ita bace naga wayan ta ya shufa ne Baba.”
“Are you sure K’anwata? Ba turoki muguwan chan tayi ba?”
“Eh Baba zaka canza mata?”
“Anything for you My Sister zan canza mata.”
“Toh Baba zanje in kwanta gu’ night.”
“Yauwa Zeezeen Baba sena shigo nima” ya bata peck a forehead ahaka suka rabu tana
fitowa Mariam ta d’aga ta sama tana showering kisses all over her face. “Thank you,
thank you, thank you, very very much.” Hannu Zeezee tasa tana goge kisses d’in “ni
banasho Baba ne kawai yake kishing d’ina.”
“Toh ‘yar autan mu yi hak’uri nagode kinji? Zaki sha tea ko in dafa miki
Indomie?”
“Eh Indomie.”
“Taho muje toh Beauty.”

Sab’anin kullum yau Mariam ce da kanta tayi feeding Zeezee tayi mata wanka
sannan ta karance mata good night story ta nufa d’akinsu Ibraheem alokacin har sun
fara shirin bacci. Bayan ta zauna kan couch tace, “chab Ya Ibrahem ashe de Zeezee
nada advantage” nan ta labarta masa komai bayan dogon nazarin da yayi yace,
“excellent! nima kod’ata zan gobe wallahi se an sai min machine.”
“Ai kuwa de tanan za muna getting on Baba tunda yace komai shi Zeezee.” Hannu
suka tafe da Ibraheem suna masu jin dad’in wannan cigaba da suka samu!

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄

www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 06
Yau Tuesday ya kasance ‘public holiday’ ba school don haka yaran duk ba
wanda ya tafi school ko wannen su na a d’akinsu yana bacci. 7:00AM Zeezee ta tashi
kamar meh alarm as usual ta fita tabar d’akinsu tayi d’akin su Ibraheem yau kuma, a
kulle ta samu k’ofar don haka tayita knocking dan dolen Ibraheem yasa Omar ya bud’e
mata.
“Me kuma ya kawo ki nan?” Ya tambayeta in between hamma. “In kinsan fitina kika
zo yi maza ki juya ki koma.”
“Ya Omal zan kwanta ne.”
“D’akin ku ba wajen kwanciya aiko?” Ibraheem yayi maganar fuskarsa rufe da
pillow. Ganin zata soma masu kuka suka shigo da ita, a tsakiyar su ta kwanta tare
da shigewa bargon Ibraheem. Tun tana shiru taga barata iya ba ta soma kiran sunan
su, shiru suka mata wane basu jinta chan ta miqe ta nufa toilet tayi pupu.
“Naaa gamaaa!!” Ta fad’a da k’arfi. Banza su kayi da ita se a karo na biyu
Ibraheem yaja dogon tsaki. “Nifa shiyasa banason ta shigo nan, shegen k’azanta
sekace farillah kullum se mutum yayi pupu da safe mschw! Omar jeka wanketa ka kuma
tura ta waje ga teddyn ta.”

“Ni wallahi-”
“Kai wallahi meh?” Ibraheem yayi saurin katse sa “da ni kakeso in wanke mata?
Lallai yaro will you stand up my friend!” A sanyaye Omar ya miqe se kumbure kumbure
yake ya shiga bayin yana wani mata mugun kallo. Se da ta bari ya k’ariso ciki ta
kallesa tace, “ni banashon ka, ba kai zaka wanke min ba.”
“Mumu daman ni d’in nace maki ina sonki ne? Tsaya nikam na wanke miki bacci
nakeji.”
“O’o banashon ka tab’ani banasho!” Tasa kuka. Fitowa Omar yayi yaje ya samu
Ibraheem yace, “Ya kaji wai bata son na wanke mata har kuka take.”
“Toh da waze wanke mata? Ke Zeezee ki miyar da hankalinki kinajina koh?”
“Ni kai zaka wanke min.”
“Lallai yarinya zaki mutu da kashi a jikinki inde ni zan wanke miki”
“Ya Ibyaheem na gama” tasa kukan shakwab’a.
“Barta gun hau gado ka kwanta” yace da Omar haka suka barta zaune kan toilet sit
da abin ya isheta tasa wani irin d’an iskan ihun da har su Baba seda suka jiyo ta.
Ba tare da b’ata lokaci ba Baba ya tashi miqe, a zaton shi ma wai ko ita da Mariam
ne ganin ba haka bane ya nufa b’angaren su Ibraheem, tsaye a d’akin ya iskesu suna
raba ido. Kai kawai yayi nodding ya kira sunan “Zeezee.”
“Baba! Baba!” Toilet d’in ya nufa ya sameta. “Ya haka K’anwata pupun yak’i fita
ne?’
“Ya Ibyaheem ne nace yamin tsarki yak’i.”
“Yak’i tun yaushe?”
“Tun d’azu.”
“La ila! Ibraheem!” Ya kira sunansa a fusace, “Zo nan d’an banzan yaro kawai.” A
sanyaye Ibraheem ya k’ariso cikin bayin. “Na’am.”
“Nanata abinda ka gaya mata.”
“Nifa bance mata komai ba.” Masifa sosai Baba ya masa harda make sa a k’eya
sannan yasa sa ya wanke Zeezee tas harda yi mata wanka ya shirya ta tsaf sannan ya
d’au K’anwarsa suka bar musu d’akin. Omar da dariya keson fin k’arfinsa se kare
fuskarsa yake amman inaa seda dariyan yayi finding way nasa out.

“Ma wa kake yiwa dariya?” Ibraheem yayi maganan in a serious tone.


“Bb... Babu.” Yayi stammering.
“Da yafi ma kam.”

****
_Later during the day, 1:30PM_
Zaune yaran da Maman su suke duk a tsakar gida kowa na harkan gaban sa. Gefe
guda Zeezee ce rik’e da ipad nata se game takeyi a yayinda Yasmeen ke zaune gefenta
itama duk ta zuba mata ido tana me kwad’ayin son buga game d’in itama.
“Zeezee na baraki sammin ipad naki inyi game ba koh?”
“Eh ba kin ce min Mumu ba d’azu.”
“Toh ai kuma na baki hak’uri kuma kinga nima in Mama ta sai min nawa zan baki.”
“Bana shon naki kowa ya riqe nasa.”
“Zeezee yi hak’uri mana fad’uwa d’aya zanyi in baki.”
“Sekin ce min Aunty Zeezee.”
“Aunty kuma? Ni dake waye babba?”
“Toh cikenan balin baki ba.”
“Toh Aunty Zeezee bani toh.”
“Toh ki tsaya mana in yi nima tukunah.” Duk maganan nan da suke Mama na kallonsu
daga bisani tace, “amma ke Yasmeen Sokuwa ce wallahi, yanzu k’anwarki kike kira da
Aunty akan banzan game?”
“Ai kuwa sede Sokuwan kam” Omar ya mara wa Mama baya. Ibraheem da keson sa baki
amman baison ruining plan nasa yaja baki yayi tsit.
“Ai duk laifin Babanku ne, bari kema zuwa next week na kwashe adashe na in siya
miki naki, ke kuma Zeezee kar kibar wannan banzan rowan kinji ba? Ki cigaba muga
ina ze kaiki.” Harara mai rai da lafiya Zeezee ta galla wa Mama da dala-dalan
idanunta kan zasu zubo a k’asa.

“La’ila! Ni kike harara?” Mama tayi maganan tana k’ok’arin miqewa kenan Baba
dake lab’e jikin k’ofa tin dawowan sa daga Masjid ya k’ariso ciki a hanzarce tare
da dakatar da Mama. “Koma ki zauna” ya nuna mata gun zamanta da yatsa “da dukanta
zakiyi sabida ban gida komeh?”
“Baban Zeezee harara na fa tayi.”
“Eh toh ai ke kika jawo da kikace mata marowaciya, yayyun nata ba duk haka suke
ba suma?”
“Lallai Alhj ka goyi bayan harara na da tayi kenan.”
“Why not? Nide karki tab’a min K’anwa.” Kai Mama ta gyad’a continiously cike da
mamaki “toh wallahi Alhj ka cigaba da b’ata yarinyan nan.”
“Kanki akeji, kuma bayan nan meh naki dan Yasmeen ta cewa Zeezee Aunty? Ba
sisters bane su? Ni na lura bakison Zeezee a gidan nan komi Yasmeen komi Yasmeen to
kema ki cigaba.”

“Me kake implying wai Alhj?”


“I mean baki adalci mana, kinfi son Yasmeen kan Zeezee ko ke bakisan Zeezee ce
auta ba?” Hannu Mama ta tafe sannan ta d’aura a waist nata “lallai har kura kece wa
kare maye? Baban Zeezee kai baka ganin abinda kake ma Zeezee a gidan nan ne? Ai in
akwai wanda ke partiality tsakanin yaran nan toh kai ne” ta nuna sa da yatsa “mena
siyawa Zeezee ipad kabar Yasmeen ba waya? Waye babba cikin su?”
“Hafsah kinji na rantse duk abinda ya samu ipad na Zeezeen nan kece, dan bakin
ki kad’ai ya isa yayi destroying ipad d’in kuma believe me idan hakan ya faru cikin
kud’in adashen ki za’a sai mata sabo.”
“Hmm Allah kyauta Yasmeen Mama na karki damu Tablet me kyau zan sai miki in shaa
Allahu.” Da gudu Zeezee tayi wajen Baba ya d’agata “Baba kaji Mama koh?” tayi
maganan a shagwabance.
“Share ta K’anwata nasu tablet ne naki kuma ipad duk girman tab na Yasmeen bare
kai naki ba ko kema kinaso a sai miki tab d’in?”
“Eh” tayi nodding kanta.
“Toh angama.”
“Gaskia nima in ta haka a sai min tab d’in na had’a da waya na” cewar Omar.
“Kai asuwa? Wai daddawa acikin kunu in kaga na siya maka tab agidan nan to kabar
mugun halin kan nan ne.”

“Shikenan Baba komi Zeezee komi Zeezee sekace ita kad’ai aka haifa a gidan.”
“Kai! Ni kake gayawa magana?”
“Bar shi ai gaskia ya fad’a” Mama tasa baki. “Kai nan da Zeezee ta harare ni ba
cewa kayi batayi laifi ba don haka bar sa shima.”
“Haka kikace koh? Yayi kyau muje d’aki Zeezee akwai dambun naman dana saya
miki.” Mariam glutton jin an ambaci dambun nama ta lasa lips nata.
“Yauwa Baba zaka siya wa Ya Ibyaheem machine?”
“Machine kuma Zeezee? Me zeyi da machine?”
“D’azu fyends nashi sukazo dukan su suna machine illa shi.”
“Shi ya turoki koh?”
“A’a Baba” ta kad’a mai kai. Juyowa Baba yayi yana kallon Ibraheem.
“Kai ka turota ko?”
“A’a fa Baba ka tambayeta kaji.”
“So kake a siya maka machine kafara yawo a gari anyhow ko?”
“Wallahi a’a Baba.”
“Se a sai mishi ai tunda nasan da akwai kud’i a k’asa” cewar Mama.
“Eh dake kina biya na salary ai dole kice da akwai kud’i a k’asa” ya watsa mata
harara.
“Baba dan Allah ka siya min wallahi barin na yawo a gari ba.”
“Zeezee a siya mishi?”
“Eh Baba” ta basa amsa.
“Toh K’anwata anything for you” ya dawo da kallonsa kan Ibraheem “seka bari in na
samu kud’i tukunah.”
“Toh Baba nagode Allah ya dad’a bud’i.”
“Ameen” ya amsa sannan ya fice.

_Few minutes later..._


Mariam ce tsaye bakin k’ofan d’akin Baba tun ji da tayi an ambaci dambun nama
ta kasa samun sukuni, gabad’ai kwad’ayinta ya shiga cikin dambun naman. Dabara ce
ta fad’o mata tad’an yi baya da k’ofan kad’an ta shiga k’wala wa Zeezee kira ina
irin tana nemanta ta bata abu d’innan.
“Zeezee! Zeezee na!”
Daga cikin d’aki Zeezee dake cin dambunta akan cinyan Baba hankali kwance tace,
“Baba wancan ba mulyan Adda Mayyam bane?”
“Nata ne shareta kici abinki nasan yanzu haka wayo take son miki.”
“Zeezee!” Mariam ta cigaba da kiran ta.
“Baba zanje” ta gwada yunk’urin sauk’owa daga cinyansa.
“Tsaya tukuna. Ke Mariam!” Ya k’wala mata kira. Dum! Zuciyarta ya buga sannan ta
amsa “na’am Baba.”
“Me zaki bata kike wani kiranta haka?”
“Baba na siya mata Awara ne.” Zeezee najin an ambaci awara miyan ta ya tsinke
arayuwa tana son Awara.
“Baba zanje, Adda Mayyam kar ki cinye ina zuwa.”
“Toh kiyi sauri Zeezee ta.”
“Toh Zeezee da dambun naki zaki tafi? Baraki ajiye anan ba sekin dawo?” Baba
yayi maganar yana kakkab’e mata kayanta.

“O’o zan je dashi.”


“Toh karki ba wa kwad’ayayyun nan fa kinji ba?”
“Toh Baba” ahaka ta fice ta tarar da Mariam tsaye bakin k’ofa, d’agota tayi kaman
dagaske, “muje d’akinmu in baki ko?” with a nod takai Zeezee d’akinsu ta direta kan
gado sannan ta shiga neman Awaran da bashi a d’akin, tafi minti uku tana nema har
Zezee ta gaji da jiranta, “Adda Mayyam ina Awaran? Ni nagaji”
“Na nan Zeezee ina nema ne” ganin Zeezee ta kusa cinye dambun nata dabara ta
fad’o wa Mariam tace, “laaa Zeezee ashe Yasmeen da kwad’ayintan nan ta cinye d’azu
amman kinsan meh? Muka fita Islamiyya I promise zan siya miki kinji beautiful Sis?”
Kai Zeezee ta gyad’a mata tare da miqewa dan ficewa daga d’akin, ganin haka Mariam
tayi saurin tare ta “toh Zeezee bara’a sanmin Dambun bane?” Kafad’a ta make “o’o.”

“Aww ni in baki Awara ke ki hana ni Dambun ki? Nima inta haka na fasa.”
“Toh ai baki bani ba.”
“Zan baki ai Zeezee I promise.” Da k’yar ta sha kan marowaciyan ta bata.

~* ~* *~
Bayan tafiyan yaran Islamiyya Mama ta fiddo da duka kayakin ta daga wardrobe da
nufin gyarawa, Zeezee na a zaune kan gado tana kallon kowani move nata kasancewar
Ipad nata yayi running outta charge. Sallaman Aunty Sis da Mama taji yasa ta bar
duk abinda take ta fice da sauri dan taro wannan babbar bak’uwa. Nan fa uwar b’arna
ta samu kanta, a nitse ta sauk’o daga kan gadon, ninkakkun kayakin Mama Zeezee ta
shiga wargazawa tana warwarewa tana sa saura kusan minti ishirin Mama sukayi da
Aunty Sis, koda ta tambayi ina Zeezee Mama tace tana ciki bari ta kirata. Haka
Zeezee naji Mama na kirarta tak’i fitowa da k’yar ta fito daga baya. Aunty Sis wane
ta cinye Zeezee haka kawai yarinyan ta shiga mata rai kamar yadda ta saba shiga wa
mutane rai. Aunty Sis da son kyauta koda tazo tafiya seda ta d’au dubu biyu ta bawa
Zeezee. Bayan tafiyan ta Mama ta dawo d’akin only to see the biggest suprise of her
life.

“Zeezee! Meh haka? Bakida hankali neh? Kayakin nawa kika ma wannan tabargaza?!
Iyyeh!”
“Mama bani bane.”
“Ni ce ai tunda ba keba wallahi me hana ni dukan ki a gidan nan yau se Allah”
kafin Zeezee tasa gudu Mama ta yi kanta ta shiga mammaketa, kuka sosai Zeezee tasa
ganin ba mahalicci se Allah tayi shiru don kanta sannan ta kama hanyan bakin k’ofa
seda taci ready sannan ta kira sunan Mama. Mama na juyowa Zeezee ta d’aga hannu ta
seta ta tayi mata alaman ‘Uwaki’
“Ke! Ni kika zaga? Zaki raina wa kanki wayo yau” Da gudu tabi Zeezee nan itama
tasa gudu har sunkai bakin k’ofa kenan sega Baba shigowa, chak ya d’aga Zeezeen da
tuni tasa kukan munafirci.
“Ya haka Hafsah? Me kika ma Zeezee? Karki gaya min bin yarinyan nan kike.” Nan
Mama ta labarta masa dukkanin abinda ya faru to her suprise Baba yace shi sam be
yarda Zeezee ta zageta ba wai sharri take mata har maqora yakai Mama tace, “wallahi
Baban Zeezee ka cigaba da goye ma yarinyan nan gindi wataran kaima barata barka ba,
mu zuba da kai.”
“Ba ruwanki nide karki kuskura kitab’a min k’anwa. Inba sharri ba wai har Zeezee
zakice ta d’aga hannu ta zageki” A fusace Mama ta juya zata koma ciki Zeezee tace
da Baba, “kuma Aunty Sis tazo tabani kud’i Mama ta k’wace wai zata siya wa Yasmeen
tab dashi.”
“Haba ita da Sultan suka zo?”
“A’a tace ya tafi islamiyya.”
“Hafsah!” Baba ya kira Mama data kusan shiga d’aki. “Ina kud’in da aka bawa
yarinyan nan? Maza ki bata abinta ba naki bane.”
Da tafin ta tajuyo tana kallonsu sannan tace, “LOL ni kuma me zan da dubu biyun
K’anwar ka? Zoki amshi abinki.”

★★★
Haka Zeezee ta cigaba da girma cikin *_GATA_* maras misaltuwa. Ko kad’an Baba
bayi ganin flaws nata duk abinda tayi da dai-dai da ba dai-dai ba shi dai-dai ne a
idonshi. Kuma duk abinda tace ayi shi akeyi machine da sabon wayan da tace asai wa
Mariam da Ibraheem seda aka sai musu. Da yaran suka gano haka kuwa duk wani abinda
suke buk’ata Zeezee suke samu suyi ta mata zak’in baki daga baya har Mama itama in
tanason abata kud’in anko kokuwa na d’inki muddin bata son tab’a kud’in adashen ta
Zeezee take turawa wajen Baba. Sede kafin Zeezee taje musu se sun sha wulak’anci
harta Mama tace se Mama tace mata Aunty Zeezee tukun taje.
Ahaka har yarinya takai 3 years sosai ta k’ara wayo ga kyau har na k’in k’ari in
aka barni ma se ince tafi Mama kyau. Sede uban rashin kunya kan ba gobe, bata ganin
kowa da gashin ido se Baba shi kad’ai ne in yace mata bari zata bari in bahaka ba
sauran duk bata jin maganansu ciki harda na Mama.
Mama kam dad’i kashe ta za’a sa Zeezee a school this year, ko a babu bakinta ze
huta da surutu.

CIKIN GARI.
Kasancewar yaran sunyi hutun 3rd term a School, in aka koma yanzu new section
zasu shiga ga kuma siyar da admission da ake yanzu a school nasun yasa Mama tsayawa
dan sai wa Zeezee form a cika mata itama. Bayan isarta gida ta tarar da family’n ta
zaune a babban parlour’n Baba kowa na harkan gabansa bayan duk sun bita da sannu da
zuwa Yasmeen taje ta d’au mata ruwan sanyi. Tana shanye ruwan tasa hannu a jakarta
ta ziro form data siyon “gashi Alhj form na siyo wa Zeezee se a cika mata gashi
Yasmeen miqa wa Babanku.”
“Form na wani school?” Baba yayi tambayan lokacin da Yasmeen ke miqa masa form
d’in.
“Ji Alhj da wata magana da na wani school zan sai mata? Na Havardth mana ba duk
can yaran suke ba.”
“Se kuma akace miki can za’a sa Zeezee? Nifa banason shishshigi wallahi, waya
rok’eki? Waya saki siyo matan?” Attention na kowa ne ya dawo kan Baba fuskokin su
duk d’auke da neman k’arin bayani.
“Ban fahimce kaba Alhj.”
“Ai baraki tab’a fahimta taba daman, toh I mean kinyi asaran kud’in siyan form
d’in dan ba’a Havardth zan sa Zeezee ba.”
“Ikon Allah wani school zaka sata?”
“Wai ina ruwan ki? Tambayoyi sekace ‘yar jarida? When the right time comes you’ll
know.”

“Hmm! ba gaskia kam ai dole kak’i fad’a anyways tayi tsami ma ji.”
“Wai ma tsoronki akeji ne? A LYS zan sata.”
”L meneh?” Mama ta kwararo manyan idanunta waje disbelievingly, ba ita kad’ai ba
haka siblings na Zeezee mah.
“LYS!” Yaran sukayi exclaiming in shock a tare.
“Eh shi ‘yan bak’in ciki kawai, shi za’a sata.”
“Alhj kasan me kake shirin yi kuwa? Kasan ko nawa ne fees na school d’in kuwa
kake wannan magana?”
“About N70k (dubu saba’in) fah” cewar Ibraheem still in shock.
“Ina sane, shi yamin shi zan sa ta ba ruwan ku tunda bada kud’in ku bane.”
“Lallai Alhj! Makarantan dubu saba’in sekace bamusan me zamuyi da kud’i ba? Ni
wallahi ban goyi bayan shawaran nan ba. Yaran nan naga duk a Havardth suka fara
karatu kuma shi zasu gama in shaa Allah, d’an dubu ishirin zuwa talatin gashi yanzu
SS 3 Ibraheem ze shiga kuma naga ana karatu bawai ba’ayi ba amman kace Zeezee se
makarantar dubu saba’in?!” ta k’are maganan still not believing whats happening.
“Toh ni yanzu na ce miki dama ba’a karatu ne ciki? Kawai achan d’in nafi son
insa Zeezee. Makarantan ‘yan gayu, makarantan masu kud’i ba kalan nasu Ibraheem da
kowani d’an unguwa ke ciki ba. Harta ‘ya‘yan Sarkin Bauchi a LYS Academy suke.”
Kafin Mama tayi magana Yasmeen tayi saurin fad’in “Baba nima asani.”
“Ja chan tsohuwa dake kawai! Kamar yadda sauran ‘yan uwanki suke Havardth kema
chan zaki cigaba.”
“Oh ni Hafsatuu! Partiality a filin Allah haka! Nide kar a zo ana cemin ba’ada
kud’i aga ko I will care dan makarantan 70K kam ba abin wasa bane.”
“Kanki dana yaranki akeji K’anwata de LYS zata shiga ko kuna so ko baku so ‘yan
bak’in ciki kawai instead kuyi rejoicing za’a k’anwarku a School mekyau se uban
kishi da hassada koda shike ba laifin ku bane halin Mamanku ne.”

****
Washegari bayan sun gama breakfast Baba yasa Mariam tayi ma Zeezee wanka tsaf
ita de Mama nata ido ne. Bayan an gama shirya ta cikin leggings and armless top
nata suka fita chan akayi mata passport sannan ya wuce dasu New GRA, LYS Academy
inda ya siya mata form. Washegari suka koma inda akayi mata interview, yarinya da
uban baki duk abinda aka tambayeta ta sani Baba se dad’i yakeji ana yaba K’anwarsa
ana ce mata zatayi ilimi.

_One Week Later..._


CIKIN KASUWAN CENTRAL, BAUCHI.
Zaune family’n Alhj Isma’il Yosouf suke cikin wani babban shagon da ya kasance
mafi girma cikin kasuwan. A gobe zasu koma makaranta shine sukazo yin shopping.
Kowa an sai mai jaka d’aya takalmi d’aya seda dozen na socks banda Zeezee da aka
sai mata school bags uku had’ad’d’u, takalma ma uku da dozen na socks masu uban
kyau guda uku suma. Itade Mama ba abinda take banda kallon Baba dan kuwa yafi
k’arfinta yanzu. Bayan nan suka wuce shagon provisons juice carton-carton kala uku
ya d’au wa Zeezee ba a maganan chocolates da sauran snacks, shopping de kaman ba
gobe yayi wa Zeezee bayan isansu gida duk suka fiddo da kayakin kowa ya shiga gwada
nasa yana jin dad’i sede any moment suka tuna komi na Zeezee yayi tripling nasu se
sujiyo tokari a zuciya amman ya suka iya? Zeezee *_‘YAR GATA CE!_*

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 07
*December, 2016*

Lunch Mama da Mariam suka shiga had’awa nan da nan suka gama aka d’iba ma kowa
nasa da nama d’ai-d’ai akai. Ihu Zeezee ta k’urma “ya haka Zeezee wani abu ne?”
Mama tayi saurin tambayarta.
“Ni banashon nama d’aya, banasho!”
“Jimin ‘ya da guda nawa kikeso? Bakiga plates na yayyun naki bane?”
“Baba! Baba!” Tashiga k’wala mai kira a gigice ya fito “K’anwata meya faru haka?”
“Mama ne!” Tasa kukan da anayin sane amman ba hawaye.
“Wai Hafsah shin yaushe ne zaki koyi son yarinyan nan? Kullum ace bakida aikin da
yafi sata kuka?”
“Seka gayamin mena mata ai, daga sa mata abinci seta hau min kukan banza Mariam
mik’on plate d’ina in d’iba in bar musu kitchen d’in.”
“Meya faru K’anwata?”
“Nama d’aya Mama ta shamin.”
“D’aya kacal? Adalilin meh?” Wabje serving spoon d’in yayi ya kwashi ragowar
naman tas ya zuba wa Zeezee a plate nata ido kawai Mama ke binsa da “ni kuma me zan
samu inci?”
“Inba keda abinki bama me zakiyi da cholesterol a jiki? Jekici abincin ki
K’anwata.” Kafin su Ibraheem su soma cin namansu Zeezee har ta cinye 15 meats dake
kan plate natan ko tab’a tuwon batai ba, ahakan tana neman k’ari wajen Ibraheem ta
nufa ta zauna “Ya Ibyaheem nama.”
“Naman uwaki, ki gama cinye na miyan duka ki wani ce in baki nawa, bazan bada
ba.” Su Mariam najin haka suka b’oye nasu cikin tuwonsu ihu ta k’urma daga ciki
Baba yace, “wa kuma ya tab’ata yanzu?”

“Ya Ibyaheem ne yaban nama wai o’o.”


“Kai Ibraheem kaci girma ka bata mana.”
“Baba ni shikenan kullum sede ban d’ibi abinci ba seta riga cinye min nama.”
“Ka bata nace karka bari in fito.” Dogon tsuka yaja sannan ya d’au naman ya cusa
mata a baki cike da mugunta “seki cinyen ai Mumu kawai.”
“Kaima Mumu” ta murgud’a mai baki.
Fitan su Baba sallan Azahar Zeezee ta fito da had’ad’d’un throw and doghnurt
shaped pillows na Mama wanda take jerasu kan gadon d’akinta waje ta baza kan
varenda tana wasa dasu. Mama na idar da Sallah tafito ta hau ta da masifa, “maza
tashi ki mayar min su d’aki, iskancin naki har ya kaiga fito min da pillows waje
mayar dasu nace!”
“O’o balin mayal inba.”
“Bazaki mayar ba?”
“Eh ni ki banni” mari Mama ta sakar mata a baya nan tasa ihu “Allah ya ishana!”
ana cikin haka su Baba suka dawo “ya haka tun daga waje nake jin hayaniya.”
“Sekazo kayi mata magana, kace ta miyar min da pillows na d’aki tunda bata jin
maganan kowa se naka.”
“Yanzu Hafsah meye aciki dan yarinya tafito da pillows tana wasa dasu.”
“Alhj kalli a k’asa fa take gurzasu.”
“Yi wasan ki k’anwata kinji?” Yayi maganan yana shiga ciki binsa Mama tayi tana
k’orafi “wallahi ka cigaba da goye wa k’arya gindi ace yarinya duk abinda tayi dai-
dai ne a idonka wataran da kanka zakayi kuka wallahi mu zuba mu gani.”
“Kanki akeji” yace da ita lokacinda ya mik’e kan gado “muddin ina gidan nan kam
keda yaranki bazaku tak’ura wa K’anwata ba.”

Futu-futu Zeezee tayi da pillows na Mama sannan ta barsu gun ta zarce tsakar
gida ta hau wasan banza da ganganci, koda Mama tafito ta ganta tanayi bata ce mata
komi ba saboda there is no point doing so, koda tace mata ta bari ba barin zatayi
ba. Kan turmi ta d’alle tana wasa daga bisani kawai ya juye da ita ta fad’i nak! A
k’asa se ihu malam!
“Ai ga erinta nan kita wasan banza sekace na miji kad’an kika gani ai.”
“Eh kad’an tagani muguwa kawai ‘yarki ta fad’i amman ko kiyi yunk’urin d’agata”
Baba wanda sanadiyan ihun Zeezee yafito dashi yayi maganar yana d’ago crying Zeezee
daga k’asa. “Sannu koh? Sannu K’anwata” d’an hannu da gwiwa ta gurje amman se kuka
take wane kanta ne ya fashem
“Sosai ne taji ciwon?”
“Ban sani ba kina zaune achan kaman kayan wanki shiga ciki kid’au min first aid
sannu ko K’anwata yi shiru.”
A sannu a sannu ya samu ya shafa mata dettol wajen sede har yanzu bata bar kukan
ba ita zafi “toh K’anwata me kikeso ayi miki?”
“A kila Ya Ibyaheem ya hula min.”
“Shi kikeso?”
“Eh da Ya Omal.”
“Ibraheem! Ibraheem!”
“Na’am Baba.”
“Kazo kai da Omar” bayan isowan su sukayi tsaye gun not minding halin da Zeezee ke
ciki, “bakuga k’anwarku taji ciwo bane? Can’t you tell her sorry? Banason sakarci
fah.”
“Sannu” sukayi murmuring in unison.
“Oya Ibraheem zo ka mata blowing air a wajen yana mata zafi.”
“Ni kuma Baba?” Yayi maganan yana pointing kansa.
“A’a ni dan k’aniyanka zo ka mata blowing air nace” haka yana kumbure-kumbure ya
iso ya tsuguna gaban Zeezee k’afan nata ta mik’ar ta aza kan cinyansa take ya
tunkud’e k’afar “meh haka zaki wani samin k’afanki me dottin nan kan kaya, bakiga
farin kayane a jikina ba.”
“Bata gani ba sa k’afan naki Zeezee” nan ta miyar “ayyi Baba kayan fa zeyi
dotti.”
“Ungo naka nan kai da farin kayan naka maza! hura mata iskan kaima Omar turn
naka na zuwa in wan naka ya gaji.”

By 3:00PM as always yaran suka hau shirin islamiyya Mama dake neman hutu in
any way possible ta kalli Zeezee dake mak’ale jikin Baba tana game nata hankali
kwance tace, “Zeezee shin ke se yaushe ne zaki fara zuwa islamiyya wai kam? Mates
naki duk sun soma zuwa” Kai Zeezee ta d’ago ta galla wa Mama harara sannan tace,
“ban shani ba.”
“Ya miki kyau, ina Alhj kana ganin irin abinda nake yi maka magana akai ba? Yanzu
ina zan iya shiga cikin jama’a da maras kunyan yarinya haka.”
“Ke shikenan bakida aikin yi a gidan nan se yiwa Zeezee baki?” Baba yayi maganar
a fusace. “Gaskiya banaso, baki tashi zagi a gidan nan se akan Zeezee, islamiyya ne
barata shiga ba seta k’ara girma haka kawai barin kai ‘yata islamiyya a jibgeta a
banza ba.” Hannu Mama ta tafe tare da sakin salati.

“Su Yasmeen da suke zuwa ai ba haifan su akayi ba.”


“Yasmeen daban Zeezee daban.”
“Kuma bokon da zaka satan shi ai ba’a duka koh?”
“A LYS? Kin tab’ajin inda akace miki an daki d’alibi a LYS? Ai rashin dukansu is
the number one reason da yasa zan sa Zeezee school d’in.”
“Lallai kanada aiki toh ko su basu dake taba ni nan zan dake ta sede bata sake
zagina ko min rashin kunya ba.” Ba tare da ta jira me Baba ze sake fad’i ba ta fice
masu daga parlourn.
“Shareta kinji K’anwata? Karki kula Mama and anytime ta tab’a ki tell me kinji?
Zan rama maki da kaina.”
“Yeyy! Baba ni duk nan gidan nafi shonka.”
“Ai nima na fi sonki Zeezee ba a gidan nan kad’ai ba a duniya gabad’aya.” Ya
shafa dogon sumanta.

***
Da fitan yaran bada jimawa ba Baba ya yi alwala ya fice Masjid shima. Bayan
Mama ta idar da Sallah tajiyo sallama daga waje, ba tare da b’ata lokaci ba ta
fita, Sultan yaron Aunty Sis ta tarar da ‘yar basket a hannunsa bayan ya gaishe da
Mama ya mik’a mata basket d’in tare da fad’in “Mama nane tace in kawo miki.”
“Allah sarki Aunty Zainab, toh Sultan d’an albarka kace mata na gode sosai kaji?”
tayi maganan tana bud’e flask d’in. Miyan ganye had’ad’d’e taga ciki (her
favorite.) “Maman Zeezee zan tafi ina Zeezee?” Kaman ance Zeezee leqo tafito daga
d’akin tana kallonsa wane yau ta soma sasa a ido. “Baraka jira kuyi wasa da Zeezee
ba zaka tafi Sultan?”

“Zeezee!” yace da ita yana mata murmushi.


“Kazo gidan mu dan ka d’auke min ipad k-” bata idda maganar ba Mama ta bige
bakinta “ce maki akayi yana d’auke-d’auke? Toh in baki sani ba shima Sultan nada
ipad nasa d’an gatan Baban sane shima.”
“Allah ya isha” tace tana kuka.
“Ni kike jawa Allah ya isa?” Mama ta sake bige mata baki, volume na kukan nata ta
k’ara “kuma wallahi shena fad’awa Baba” data ga Mama bata kallonta ta d’aga hannu
ta zageta se anan taji ta huce.
“Zeezee bar kuka kinji?” Cewar Sultan warmly ko ta kansa batai ba ta nemi gu ta
zauna tana ciccire ribbons da suke kanta tasan sarai Mama ta washi ta ganta tana
yin hakan.

Kai kawai Mama ta kad’a da taga abinda Zeezee ke tasan sarai on purpose takeyi.
“Maman Zeezee zan tafi tunda yau Zeezee tak’i kula ni.”
“Share ta Baba na tsaya in d’an d’auko maka koda juice ne.” Nan tayi ciki,
Zeezee na jin an ambaci juice hankalin ta ya tashi, sahun Mama tabi taga Mama na
k’ok’arin bud’e mata sabon carton na juice nata. Wani irin shegen ihu tasa sannan
tayi gudu ta cafko hannun Mama. “Ni wayyayi ki aje min jush d’ina ai nawa ne ba
naki ba ki ajiye!” Ta rushe da kuka.
“Sake min hannu marowaciya kawai, da Uwarsa tazo ta baki dubu biyu kin iya
karb’a ke kice baza a bashi juice ba? Wallahi kinyi k’arya sake min hannu!” Sake
dandameta Zeezee tayi tana ihu kaman ana cire ranta, ko ta kanta Mama batai ba ta
d’iba juice uku wa Sultan da sauran chocolates and snacks komi uku-uku sannan ta sa
mai a leda. Uwar rowa tayi kuka har nishinta na wani sama-sama dan kanta tayi shiru
ta fice varenda taje ta kwanta flat wajen tana birgima only if ace gun da k’ura da
tayi putu-putu da kayan jikinta ko k’ala Mama bata ce mata ba ta juyo abincinta a
plate ta samu waje ta zauna tana ci. Sarkin rowa ga kwad’ayi tuni kwad’ayinta ya
shiga abincin, ba kunya bale tsoron Allah taje ta samu Mama “nima zanci.”
“Ba abinda zaki ci.”
“Wayyayi sena ci” ta miqa hannunta zata sa cikin plate d’in.
Bige hannun Mama tayi, “da hannu du dottin zaki sama min a plate? Bud’e bakin
marowaciya kawai” haka suka yita drama har suka k'are abincin.

Bayan da suka gama cin abinci Zeezee ta nemi wayan Mama qirar Samsung galaxy S4
ta nufa chan ta side nasu Ibraheem inda ake ajiye manya manyan roba cike da ruwa ta
jefa wayar ciki, se da ya kusan minti biyu sannan ta cire ta basa few seconds ta
sake miyarwa tana murmushin jin dad’in abinda takeyi tace, “nan gaba jaki shake
d’auka min jush kibawa Sul-” sunan da bata gama k’arisawa ba kenan due to
lafiyayyen marin da Mama ta sakar mata a baya. Ihu ta saki Mama ta fisgota zuwa
main tsakar gidan “bakida hankali ne iyye? Da wayonki da komai zaki d’au min waya
ki jefa a ruwa?” Hannunta taja zuwa kitchen sannan ta zari tsintsiyan kwa-kwa guda
biyu ta tattara kayan Zeezee sama ta shiga shwad’eta. Zeezeen da tunda tasan kanta
ba’a tab’a mata duka ba se yau ta ringa kuka kaman ba gobe ana cikin haka Baba ya
dawo gida. Tun daga bakin k’ofa yake jin kukan K’anwarsa a hanzarce ya k’ariso only
to see the biggest suprise of his life.

“HAFSAHHH!!!” Ya kira sunanta da wani irin kakkausar murya amman hakan be hana Mama
cigaba da aiwatar da abinda take ba, seda ta sake shwad’e Zeezee sau biyu again
sannan ta barta alokacin har Baba ya iso inda suke yasa hannu ya d’aga Zeezeen da
ko kukan arziki ma ta kasa yi don azaba. “Meh haka? Kashe ta kikeson yi komeh? Wani
erin sakarci ne haka? Amman Hafsah da hankalin ki kuwa?” duk wannan tambayoyi
jerosu yayi da numfashi d’ai. Hannu yasa ya fisge tsintsiyan dake hannun nata, har
ayanzu Mama bata ce komai ba hannu yasa ya kwantar da crying Zeezee a jikinsa yana
bubbuga bayanta.
“Kinsan baki fi k’arfin in d’au belt in zaneki ba kema koh?”
“Ka fad’i koma meh, kekuma kad’an kika gani ki sake d’aukar min waya kisa a ruwa
kigani,” tayi maganan tana huci.
“La’ila!! Yanzu Hafsah akan waya kika daki yarinyan nan haka se kace zaki kaita
lahira? Ina wayar?”
“Gashi nan” ta miqa mai. Abinda ya aikata ne ya mugun bata mamaki, to her suprise
taga ya nufi wani daron dake cike da ruwa wajen wanke-wanke ya sake tsunduma wayar
ciki baki Mama ta sake in disbelieve.
“Ansa a ruwan an kuma sawa, akan banzan wayan da be kai ya kawo ba zaki kashe
min K’anwa? Nace ansa a ruwan maganan banza kawai!” ya watsa mata harara sannan ya
wuce da Zeezee d’aki. Binsa tayi da kallo tace, “wallahi se ka sai sabo.”

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 08

*December, 2016*

_9:46PM_
Kowa na a zaune a babban parlour yana harkan gabansa Mama ta shigo bata nufi ko
ina ba se kan Baba dake riqe da Zeezee yana kallon NEWS. Gabansa ta sha “ya haka?”
Yayi saurin tambaya.
“Kud’in wayata zaka bani.”
“In nak’i fa?”
“Nikuma inja Allah ya isa.”
“Toh Hafsah kija kinji? Kija please.”
“Ni gaskiya ka bani kud’in waya na ai ‘yarka ce ta b’ata.” Maido da kallon sa
yayi kan Zeezee yace;
“Zeezee abawa Mama kudin waya ta sai sabo?”
“O’o” tace tare da make kafad’a “ba ta bawa Sultan jush d’ina ba ta kuma min
duka.”
“Toh kinji?” ya d’ago kai yana kallon Mama “tace kar a baki kud’in, maganan
K’anwata kuma ya zauna baza’a baida kud’in ba.”
“Allah ko? Wallahi Alhj kar ka bani kud’in wayana kaga aiki da cikawa gobe, ai
nasan shagunan ka da suke Wunti zuwa zan in d’ibi duk abinda yamin.”
“Allah baki sa’a toh ni matsa min kallon NEWS nake” yace da ita. Rai a dak’ule ta
koma gefe ta zauna ta hau taya Yasmeen tsefe kitson ta kasancewar jibi Monday zasu
bud’e school.
Ana cikin haka k’ishin ruwa ya addabi Mama ganin Zeezee ce k’arama cikinsu kuma
ita ke zaune ba abinda take tace, “keh Zeezee wuce ki d’auko min ruwa.”
“O’o” tace gatsau cike da rashin kunya.
“In aike ki kice min o’o? Tashi nace!”
“O’o bayin jeba.” Kallon Baba Mama tayi taga ko a jikinsa ma Zeezee na mata
rashin kunya, “dole kayi pretending kaman baka ji ai dake bakada gaskiya” tace
dashi. Se anan ya juyo ya kalleta sannan yace, “ai da gaskiyar ta ko wani aike kice
se Zeezee, kika tashi kuma ba wanda kike duka kaman ta ba inda zataje, Yasmeen dake
gabanki ba mutum ce ba? Ki aiketa ko ki tashi ki d’auko da kanki cigaba da game
naki Zeezee na.” Kai kawai Mama ta girgiza “ka cigaba wallahi, Yasmeen Mama na jeki
d’auko min ruwa.”

****
Washegari su Mariam sukayi wanka tsaf harda Zeezee suka shirya wai zasu gidan
kitso for the first time Zeezee za’a gidan kitso. Baba da kansa yayi dropping nasu
by tunda harda Zeezeen sa yau. Kitso me kyau sukayi kasancewar za’a koma school.
Banda ma kiston Zeezee dayasha beads da ribbons kamar a sace kan a gudu. Da Azahar
aka gama musu Baba yaje ya d’aukosu nan ma. Dawowan su gida suka tarar da kayaki
sabi zube kan tabarma ta bakin k’ofa wajen duk suka nufa suka shiga duddubawa.
Kayaki suka gani duk sizes nasu masu kyan gaske, suna cikin duddubawa Mama ta fito
daga ciki tare da masu sannu da zuwa. “Iyye kitson autan nawa yayi kyau” ta shafa
kan Zeezee.
“Batai kuka ba Mariam?”
“Batayi ba kasancewar game tayi ta bugawa a ipad nata.” ta amsata a takaice.
“Toh ko kefa? Kin ganki kuwa?” best smiles nata ta sakar wa Mama sannan tace,
“Mama kayan waye wannan?” Zeezee a rayuwa akwai son sabon kaya.
“Naku ne” nan ta rarraba masu se godiya suke shide Baba bece ko k’ala ba. Bayan
da yaran suka wuce d’akinsu Mama ta matso kusa da shi tace, “kayi shiru tun d’azu
baka ga kayakin bane ko basu ma kyau bane?”
“Tsakanin ki da yaranki meya kaini sa baki.”
“Hmm haka ne? Seka kawo kud’i dan duk a bashi na d’auka.”
“Bashi?!” Yayi exclaiming yana nodding head.
“Eh bashi Alhj da aiki nake da zan iya biyan wannan uban kayaki.”

“Shin wa kika tambaya ma kafin kikayi wannan karambani?”


“Karambani? Yanzu Alhj saiwa wa yaran nan kaya shine karambani?”
“Eh mana tunda bakida kud’in biya, nima banda kud’i seki jira in kika kwashe
adashenki ki biya.” Dai-dai ze miqe kenan Mama tasa hannu ta zaunar dashi. “Wallahi
Alhj baka isa ba sekace ni kad’ai na haifi yaran da zaka wani ce ni zan biya duka?”
“Da ni nace ki siya musu? Kaya de yara sunada tunda ba tsirara suke yawo ba
sabida haka sake min hannu.” Sake dandame hannun nasa tayi, “ba kai kace ba amman
ai ya kamata ne shiyasa kai bakasan rufin asirin ka bane ana ganin yaran ka da
kayaki masu kyau ba?”
“Aww! duk wanda suke dashi be ishesu ba kenan? Sake ni nikam nikam ko ki biya
koki miyar wa Maman Fadeel kayakin ta.”
“Ka d’au wai barin iya miyarwan bane? Wallahi miyarwa zan.”
“Yauwa sakeni toh.” Fuska ta maraice sarai Baba yasan barata iya miyarwan ba da
biyu ya fad’a hakan shima “Baban Zeezee dan Allah karka min haka, baka ma ji kud’in
bafa kake wannan magana.”
“Nawa ne?”
“Dukan su ukun fa 35k ne kacal.”
“35k?” Ya zaro ido waje. “Shine kacal? Gaskia banida wannan kud’in yanzu sede in
zamu biya rabi da rabi in biya 20k kibiya 15k.”
“In nayi hakan kuma da me zanyi ciko na sai sabon waya tunda kak’i bani kud’in
duka.”
“In kinsan zance zakiyi ta tadawa toh kije kiyi duk abinda ya miki 20k d’inma na
fasa baiwa.”
“Alhj mana dan Allah karka min haka.”
“Tsaya ma tukun d’an set uku-ukun ne har 35k nifa na lura kayan matan nan tsada
ne garesu.”
“Alhj ai kasan kayan yara da tsada, Zeezee nan kad’ai taci 17K.” Hannu yasa a
aljihu ya zaro kud’ad’d’e masu dimbin yawa sannan ya irga dubu sha bakwai (17) ya
miqa wa Mama. “Ga na Zeezee nan, na sauran ki biya ko kuma ki jira in k’arshen wata
yayi an bibbiya ni bashuka na se in gama biya.” Cike da mamaki Mama ta d’ago kai
tana kallon Baba sannan tace;
“Lallai ma Alhj! wato in na Zeezee ne ka iya biya amman na sauran dake ba
‘ya‘yan ka bane baraka biya ba.”
“Wai ce miki akai barin biya ba? Nace maki banida kud’i” da hanzari ya miqe tare
da adjusting hulan shi without giving ber a chance to speak yace, “zan wuce
kasuwa.” Zeezee ya hau kira.
“Eh Baba!” Ta amsa daga ciki tana k’ok’arin fitowa. Daga k’asa-k’asa Mama
tace, “wai ace yarinya in an kirata sede tace eh bata iya fad’in na’am ba, Allah ya
kyauta deh.”
“Ina ruwan ki? Mschw! Zeezee na zan fita kasuwa kina son in saya miki wani abu?”
“Eh Baba ice cream da dambun nama.”
“Toh K’anwata sena dawo koh?”
Ba-bye ta mishi tare da komawa ciki.
“Ni matar gidan ba’a tambayeni ko me nakeso ba saboda banice a gabanka ba aiko?”
“Oh! Hafsah! Yanzu kishin Zeezee kike?”
“Ban sani ba nide a sai min gashi na kwana biyu ban motsa baki ba.”
“Seki kawo kud’i don ni banida.”
“Kaje tunda se na kawo kud’i na fasa cin” ba tare da yace k’ala ba ya fice.

_2:27PM_
Dai-dai nan Baba ya dawo gida bayan yayi parking ya kira Ibraheem yazo ya ciro
wani babban kwalin da Allah kad’ai yasan meh a ciki faga motar. A varenda ya sauk’e
se anan sunan dake jikin kwalin ya fito. “Washing machine?!” Ibraheem yayi
excaliming da d’an k’arfi, jin haka Mama da yaranta suka leqo suma. Zeezee na
fitowa ta d’ale jikin Baba.
“Baba ina aish clim d’ina?”
“Gashi anan K’anwata, Yasmeen ungo kai fridge na d’akina ki sa mata.” Baba yayi
maganan tare da cire ma Zeezee ice cream d’aya daga cikin ledar. A sanyaye Yasmeen
ta amsa sannan tace, “Baba nima zan sha”
“Wai ke wace irin kwad’ayayya ce?”
“Nima zan sha Baba” cewar Mariam.
“Kwad’ayayyun banza kawai! ku d’au d’ai-d’ai Yasmeen ki kai sauran d’aki.”

“Wannan kuma fah?” Cewar Mama tana me bin washing machine d’in da kallo.
“Bakida ido ne? Washing machine ne.”
“Ina da shi kuma nagani tambayata itace, washing machine na waye neighbours suka
kawo a ajiye masu ko kuwah?”
“What do you mean? Ban kai in sai washing machine ba kenan ko meh?”
“Ni ba abinda nake nufi ba kenan naga d’azu ka gama cewa bakada kud’i.”
“Toh ba ruwanki bane, Zeezee K’anwata kinga wannan?” yayi pointing machine d’in
da yatsa. Kai ta gyad’a as an answer. “Good, naki ne kinji? Ke kad’ai za ana yi
maki wanki ciki.” Zeezee kanta seda tasha mamaki talkless of her siblings.
“Nawa Baba? Duka wannan?”
“Sosai ma K’anwata naki ne.”
“Yeyy!” Ta rungume shi tare da sauk’a daga hannunsa tana shafa jikin kwalin. Har
a yanzu cikin Mama da yaranta ba wanda ya iya fad’in ko qala. Mama ta nisanta tace,
“amman wallahi abin naka ya soma yin yawa Alhj, washing machine fa? Kuma kace na
Zeezee kad’ai sauran ba yara bane? That aside d’azu anan nace ka bada kud’in kayan
yaran nan kak’i kace ba kada kud’i, ka sai min gashi nan ma duk bakada kud’i amman
ka iya d’auko washing machine da ke...” tayi pausing tana neman price tag na
machine d’in. Kafin Baba yasa hannu ya tare ta karance “75k ka siya kuma wai ma
Zeezee kad’ai.” Sosai Baba yaji a jikinsa ba dad’i amman ya dake yace, “toh se meh?
Da tsofi dasu ne zan siya masu washing machine? Sabi’u na masu wanki me kyau shi
kuma ze cigaba da musu amman de kam wannan na wanke kayan Zeezee ne kawai.”

“Ka kyauta toh Ibraheem zo muje ka siyo mana gashi.”


“Tsaya Ibraheem” Baba ya dakatar dashi da wuri, hannu ya sa a aljihu ya irga 3k
ya miqa mai “gashi saya muku shikenan?”
“Nifa bana buk’atan kud’in ka” cewar Mama “miyar masa da kud’insa Ibraheem.”
“In ke bakiso yaran suna so wuce kaje ka siya muku sauran kuma kayita yawo a
gari.” A sanyaye Ibraheem ya wuce.

*** _9:23PM_
Mik’e Mama ke kan gado da shirin baccinta a yayinda Baba ke other bedside d’in
shida Zeezeen sa suna game, daga bisani Baba yace “K’anwata mu kwanta koh? Kinga
akwai school gobe.”
“Baba gobe ne zanje school d’in?”
“Eh K’anwata.” Shiru tayi na ‘yan seconds sannan tace, “toh Baba banida uniform.”
”Karki damu zuwa next week zasu baki yanzu mu kwanta tashi in saki cikin gadon
ki.”
“O’o ni yau anan zan kwana.” Kafin Baba ya amsa Mama tace, “kamar ya anan? Gadon
kin kuma fah? Tashi da Allah.”
“Ke wai Hafsah meh matsalaraki ne? Anan d’in zata kwana.”
“Haba Alhj yarinyan nan ai tayi girman kwana tsakiyan mu.”
“Kanki akeji” ya miyar mata, d’aga Zeezee yayi tare da kwantar da ita tsakiyansu.
Mama de bata ce komai ba, wuta Baba ya kashe yabar dim light zalla sede sam Zeezee
takasa bacci ta juya nan ta juya chan da abin ya isheta ta miqe zaune “Baba!” ta
kirasa yadda ta saba always.
“Na’am” ya amsa cikin bacci.
“Baba ni acile min beads d’in suna hanani basshi.” Nan Mama da batayi bacci ba
tace, “kamar ya acire Zeezee? Ko kin manta yau aka miki kitson kuma kinada school
gobe?”
“Ni acile min.” tayi maganan almost crying.
“Baza a ciren ba mschw!” Duk nan Baba besan me suke ba sautin kukan Zeezee yayi
shooking nasa awake.

“Ya haka? Meke faruwa Hafsah?”


“Seka tambayi K’anwar taka ai.” Tayi maganan tare da juya masu baya.
“Meya faru Zeezee?”
“Baba ni acile min beads d’in suna hana ni basshi.”
“Acire kuma K’anwata? Kinsan gobe fa zakije school yara dayawa za’ayi musu kitso
da beads.”
“Ni bana sho.”
“Toh an gama K’anwata, Hafsah!” Yasa hannu ya jijjiqata. Shiru Mama tai bata amsa
ba. “Hafsah!!” Zeezee ta kira Mama da unanta da k’arfi.
“Lallai kam!” Mama tace tare da juyowa. “Rashin kunyar kin har ya kaiga kirana
da suna na?”
“Toh ba kiran ki nake tun d’azu kika manna min hauka ba, karki tak’ura wa
K’anwata please.” Baba ya kare Zeezee. Ba tare da Mama ta sake cewa abu ba ta koma
ta kwanta.
“Hafsah! Magana fa nake miki.”
“Dan Allah kubarni inyi bacci ko na fice guest room.”
“Tashi ki cire mata beads d’in in kin gama yaso seki koma baccin.” Zama Mama tayi
ba tare da tasan tayi hakan ba duk dan yadda kalamun Baba suka bata mamaki wato
shima ya goyi bayan wannan rashin hankali. Ganin bata soma cirewa Zeezee beads
d’inba se kallonsa take yace, “kefa muke jira ko a kunna maku wuta neh?”

Mik’ewa yayi ya kunna wutan d’akin sannan ya dawo ya zauna, ganin har yanzu Mama
bata soma cirewa Zeezee beads d’in ba ita kuma bata bar fitinan acire ba, Baba ya
d’aga ta ya azata kan cinyan Mama “oya ciccire mata su duka.” Kai kawai Mama ta
girgiza ta hau cire beads d’in, na gaban tace Zeezee tayi hak’uri abar mata su
amman ina sam Zeezee tace se an cire duka hakan ko akayi.

*** Washegari.
_Monday, 6:00AM_
On the dot Mariam tayi knocking bisa k’ofan d’akinsu Baba, yin haka sau biyu Baba
yace, “come in.” A hankali ta bud’e tare da shiga, sanye take da wandon uniform
nasu seda vest a jikinta bayan ta gaishe shi ya amsa tace, “nazo d’aukan Zeezee
inyi mata wanka.”
“K’arfe nawa ne yanzun? 6 yayi neh?”
Eh Baba.”
“Toh ina zuwa” dawo da kallonsa yayi kan Zeezee tare d tapping nata. “K’anwata!
K’anwata tashi kinji? Today is your first day at school.” Zeezeen da tayi nisa a
bacci ko jinsa ba tayi ba, sake jijjigata yayi “tashi kinji yau zaki fara zuwa
school tashi amiki wanka.” Cikin baccin tace, “yau ne Monday?”
“Eh K’anwata yau ne Monday tashi toh.”
“O’o ni abanni inyi basshi se anjima inje.” Haka da k’yar Baba ya iya ya tada
Zeezee, Mariam na ganin kanta ba beads ta dafe k’irji, “Zeezee ina beads naki?”
Kafin Baba ya amsa Mama ta juyo tana fuskantan su tare da fad’in “ba ga tanan ba
fitinanniyar yarinya, haka ta sani gaba jiya seda na ciccire mata su.”

“Kuma se kika biye mata Mama?”


“Ke ina ruwanki? Mschw! d’auke ta kiyi mata wanka da Allah” Baba yasa baki.
“O’o ni ba Adda Mayyam bane zatayi min wanka.”
“Se waye kuma Zeezee?”
“Nishe Ya Ibyaheem.”
“Shi kikeso?”
“Eh” ta gyad’a kai.
“Toh angama, Mariam fice kije ki kiramin Ibraheem kice yazo yayi wa K’anwata
wanka.”
“Toh” tace tare da ficewa.***

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 09

*December, 2016*

D’akinsu Ibraheem ta nufa direct, kwance ta tarar da shi bisa gado da laptop
nasa zaune kan cikinsa ya had’a da earpieace da alama kallo yake. “Ya Ibraheem wai
kaje kayi wa Zeezee wanka” tayi informing nasa. Earpieace d’in yacire tare da
miqewa zaune “what?!” Yayi exclaiming. “Inyi ma waye meh?”
“Kayi wa Zeezee wanka.”
“Buro-uba zan mata ba wanka ba, in ba iskanci ba I have three siblings kizo kina
wani cemin ni zan ma wancan Zeezeen wanka toh barin yi ba kije kice barin yi ba,
aikin banza kawai! Mschw!”
“Oho bani zaka gaya wa hakan ba se kaje kasamu Baban daya saka yimatan ka fad’a
mai anan ne zan san eh ka cika saurayin Eesha White.” yi yayi kan beji last
statement nata ba;
“Baba ne yace in mata wanka?” Yayi maganan a bit shocked.
“Eh naje Zeezee tace se kai.”
“Wallahi se naci uwar yarinyan nan kap gidan nan ba wanda ta raina se ni” Mariam
de bata sake cewa komi ba ta fice kitchen dan had’a musu breakfast.

_10 Minutes Later..._


“Wai kam ina Ibraheem ne? Yazo yayi ma yarinyan nan wanka ne yake b’atan lokaci
haka?” Baba dake riqe da Zeezee a hannu yayi maganar a fusace. “Wai Hafsah ni
kad’ai ne a d’akin?”
“A’a kaida K’anwarka ne a d’akin” ta miyar masa da amsa tare da juya mai baya.
“Oya kema tashi yau ‘yarki zata fara zuwa school kin kama kin wani baje kan gado ga
ke baki damu ba koh? Tashi da Allah kije ki had’a mata lunch pack nata, ki sa mata
komi bibbiyu sannan ki soya mata k’wai biyu ki dafa mata biyu up you go.”
“Alhj!” Mama ta zaro ido waje, “k’wai hud’u ita kad’ai?”
“Ina ruwanki da kud’in ki ake siya?”
“Allah kawo ranan da zaka ce min bakada kud’i.”
“Kan ki akeji, ke wai bakisan ana hakan bane don asa mata son makarantar a ranta?
Kinada matsala wallahi.”
“Allah kyauta” tace tare da miqewa, dai-dai nan Ibraheem shima dake sanye da
singlet da ¾ trouser yayi sallama ya shigo d’akin.
“Se yanzu kaga daman zuwa?” Shiru... “Magana nake ma da wani d’an banzan farin
fuskan ka kamar k’osai a wajen.”
“A’a” ya sadda kansa k’ansa.
“Zoka d’auketa da Allah.” Kai ya d’ago in disbelief yana kallon Baba shin Zeezee
batada k’afa ne da za’a ce masa yazo ya d’auketa? Halan k’afafun nata na kwalya ne.
“Me kake jira wai?” Da wuri yayi kan Baba yasa hannu ze amshe Zeezee dake bacci
abinta, hannunsa na tab’a jikinta ta hau shure sa “ni banasho.”
“Zeezee Ibraheem nefah tashi ya miki wankan” a hankali ta bud’e idanunta tana
kallon Ibraheem sannan ta yarda ya d’auketa. Maimakon yayi hanyan bathroom dake
d’akin, se ya hau hanyan barin d’akin, ya kai dab ga fita Baba yace, “d’an fari ina
kuma zaka kaita? Ko ka manta hanyan bayin neh?”
“Zanje na mata a bathroom namu ne.”
“Brush nata da sponge nata kuma fah?”
“Bari in d’auk-”
“Wuce da Allah kayi mata anan kaima kayi wayo wai ko? So kake kaje can ka mata
mugunta mugu kawai wuce ina ganin ka.” Haka Ibraheem kaman yayi kuka ya shiga bayin
da Zeezee ya cire mata kaya ya mata brushing sannan ya hau mata wanka yana tab’a
mata fuska tasa wani d’ankaren ihu, take Baba ya shigo “ya haka? Me kake mata?”
“Meh kuwa Baba? Wanka nake mata.”
“Kayyanshi ne Baba ya matse min fuska.”
“Ai nasani mugu kawai” Baba yakai masa bugi a baya “yimata a hankali nace!” kuka
ne kawai Ibraheem beyi ba da zaran yad’an tab’a mata fuska seta sa ihu Baba ya
mauje sa shikuma, a haka har suka samu suka gama wankan yafito da ita nannad’e
cikin towel. Man shafawanta ya d’auko da niyan shafa mata ta shiga turesa.
“Meh haka? Da Allah nikam ki tsaya in shafa miki.”
“O’o nishe jikina ya bushe.”
“Yaushe ne jikin naki ze bushe? Ki tsaya in goge jikin naki da towel.”
“O’o ni banasho.”
“Baba kace mata ta tsaya.”
“Zeezee tsaya ya shafa miki kinji?”
“O’o ni banashon Ibyaheem (yau ba Yayan ma) ni Yashmeen nake sho.”
“Tafi nono fari” cewar Ibraheem tare da galla mata harara. “Oya Ibraheem jeka
kira Yasmen kace tazo ta shafa wa Zeezee mai.”

*** A kitchen...
Dawowan Mama kitchen Mariam dake riqe da stirring spoon a hannunta tana kula da
indomie’n su tace, “wai Mama kam ina zaki kai wannan eggs haka?”
“Sekin tambaya ne? Na Zeezee mana.”
“4 eggs ita kad’ai?”
“Iyi kuwa.”
“Wallahi baramu yarda ba muma, ai muma haifan mu akayi mu ace mu d’au k’wai dai-
dai ita hud’u? Hud’u? Nima bibbiyu zan d’aukan mana yau.”
“Na yaushe kuma bayan an riga an aza k’wan kan wuta.”
“Soya mana zan” nan ta nufi fridge ta ciro musu k’wai ta hau soyawa.
“Kins-” shigowan Baba kitchen d’in ya sa Mama katse maganarta.
“Wai ina breakfast na yarinyan nan ne? Ko sekun sata latti tukuna?”
“Gashi nan fa Alhj mu fita nikam.”
“K’wan can fa nawaye?”
“Na Zeezee.” cewar Mama.
“Kamar ya na Zeezee? Ba biyu nace ki soya mata ba?”
“Kai ni Alhj ka cika bin diddigin abu wallahi ga breakfast na K’anwarka nan ba
seka fice ba, ina ruwanka da abinda ke gudana cikin kitchen d’in kuma?”
“Ke Mariam k’wai nawa kika d’aukar muku yau?” Shiru... “Dake fa nake!”
“Bibbiyu.” tayi maganan a tsorace.
“Bibbiyu? Ban hana ba?”
“Ka hana amma naga Zeezee fa har guda hud’u ita kad’ai.”
“Uwaki nan da kike had’a kanki da Zeezee toh wallahi daga yau in sake ganin me
d’aukan k’wai biyu a gidan nan ya soya yaga abinda zan mai” yana kaiwa nan ya wabje
plate daga hannun Mama yayi ficewarsa.

~* ~* ~*
7:07AM aka gama shirya Zeezee, kowa a gidan seda yayi contributing to shirinta
as Baba yayi ta tada musu hankali. Pink leggings da vest meh crossed arms fari me
kwalyan pink aka sanya mata sannan aka d’aura mata k’aramar blazer pink akai. Shoes
nata kuwa pink ne seda farin socks sosai tayi kyau wane ‘yar turawa wai ahaka ma
tasa an cire mata beads nata jiya. Bayan Baba ya gama yi mata wanka da designer
turarukansa ya saqala mata pink disney bag princesses nata a baya sannan ya riqe
mata had’ad’d’en lunch pack nata me heart shape suka hau tafiya, ganin sun iso har
bakin k’ofar barin d’akin Mama batace komi ba, bata kuma da niyan cewa komin Baba
yace, “ke wai haka akeyi neh? Yau ranar farkon zuwan ‘yarki school bako Allah
yabada sa’a? A wani wajen ma ke da kanki zaki kaita.”
“Toh Alhj naji nayi laifi, Zeezee Allah ya bada sa’a kinji Mamana?”
“Niba Mamanki bane niba shohuwa bane.” Ta k’are maganan tana bubbuga k’afa,
dariya ne yaso kub’uce wa Mama amman batason yi kada Baba yad’au wai ta huce seta
maze.
“Toh Auta na Allah yabada sa’a ayi karatu sosai fah.”
“Toh ba-bye” se anan suka fice da Baba har sun iso tsakar gidan amman cikin
sauran yaran kap ba wanda ya fito duk suna ciki suna kan shiri Yasmeen kamma ko
uniform bata sa ba.

“Ibraheem! Ina kuke? Zaku fito ne ko sekun sa min K’anwa latti tukuna?”
“Baba gamu nan” Ibraheem yayi ihu daga ciki yana k’ok’arin sa oil a hannunsa dan
shafawa a kai.

_2 more minutes..._
“Baku san ni bane wallahi tafiya zan in barku, taho mu tafi Zeezee” dai-dai nan
Ibraheem da Omar suka fito. “Su Mariam fah?”
“Bansani ba nima” cewar Omar yana adjusting collar rigarsa.
“Da kyau mutafi, Mariam! Ke da Yasmeen seku biya ta keke napep kokuma ku taka da
k’afa mu mun tafi.”
“Allah sarki Baba gamu nan zuwa fah” cewar Mariam da ihu tana sa kajol a idonta,
Yasmeen dake gefen gado tana pulling socks tace, “ba duk shi yasamu lattin ba aka
fara shirya Zeezee kaman tashin duniya.”
“Kede bari ina lip gloss yake?”
“Na cikin chess of drawer’n farkon nan ki duba.” Har seda Baba ya kunna mota
ready to leave them behind sannan su Mariam suka samu suka fito nan ma Mariam bata
sa socks ba wai se a cikin mota.
As always Ibraheem ya nufa k’ofan gaba ze shiga da wuri Zeezee ta sha gabansa ta
rik’e handle d’in restarining him. “Ke ya haka?”
“Ni jan jauna a gaba.” Tayi stating confidently cike da rashin kunya.
“Ke asuwa? K’aramar kwaro dake matsa min da Allah!” ya tunkud’e ta. D’ankaren
ihu ta saki wanda ya dawo da attention na Baba kansu.
“Ya haka meke faruwa?”
“Ya... Nama fasa ce maka Ya d’in” ta harare sa sannan ta cigaba, “Ibyaheem ne ya
mareni a kaina.”
“Mari?!” Exclaimed Baba, “ba kada hankali ne? Yarinya zata school ka sata kuka?
Ka kiyaye nifa.” Baba yayi scolding nasa.
“Baba ni yaushe na mareta? Ta matsamin na shiga gaba wai a’a.”
“Eh ni jan jauna kaje baya.”
“Oya koma baya toh Ibraheem.”
“In koma baya?”
“Kaji ni deh” ze saki magana Baba ya katse sa “ka shiga ko kuwa ka tafi da
kanka.”
“Ai wallahi gwara na tafi da kainan” ya juya kenan Baba ya kirasa “maras kunyan
yaro kawai dawo! Dawo nan dan Ubanka seka zauna a bayan wuce ina ganinka!” Ya
tsawata masa haka yana kumbure kumbure yayi joining k’annensa a baya, suka matsu su
had’u a yayinda Zeezee ke gaba ita kad’ai tana shanawa abinta. Su aka soma dropping
sannan Zeezee, a inda aka tanadar dan parking motoci wato parking space Baba yayi
parking motarsa sannan ya zagayo ya ciro Zeezee a hannu ya riqeta suka k’arisa
class nasu Nursery 1.

Form teacher’n su Zeezee Mrs. Anderson na hango Baba tayi sauri taje ta taresa
wato tun ranan da akayi interview Zeezee ta shige wa Aunty’n su rai, ba yadda
Aunty’n batai ba amman Zeezee tak’i zuwa wajenta. Bayan sun gaisa da Baba ta nuna
masa seat na Zeezee wanda yake nan close to her table, ajiye Zeezee Baba yayi
yamata adjusting kayanta sannan yace, “se kiyi karatu ko K’anwata in kun tashi by
12:30PM zanzo in d’auke ki okay?” Cike da rashin fahimta tace, “Baba tafiya zakayi
ka banni?”
“Eh Zeezee bakiga sauran ‘yan class naku suma iyayensu sun ajiye su sun koma
gida ba?” Mai da kallonta tayi kan ‘yan class d’in tana binsu da kallo taga duk ba
parent bayan nan gashi duk yara matan an musu kitso da beads gwanin sha’awa, ita
yanzu bama wannan ba wai tafiya Baba zeyi ya barta ta d’au yadda suka zo tare haka
zasu koma kamar a kyaftawan ido ta sauk’o daga kan seat d’in ta shige jikin Baba
“ni o’o tare zamu tafi mu koma gida na fasa makalantan.”
“Zeezee kin tab’a ganin inda aka fasa karatu? Yi hak’uri ki zauna kinji? Anjima
kad’an zan zo in d’auke ki.”
“Ni o’o” ta b’arke da kuka tabar Mrs. Anderson ta tab’a tama tak’i duk ‘yan ajin
se kallonta suke.

Ana cikin haka wani mutum wanda a shekaru ze girmi Baba koda irin 5 years haka
ya shigo, babban mutum ne da an gansa, hannunsa riqe yake da wata little angel
wanda ga dukkan alamu ‘yarsa ce saboda tsantsan kaman da suke. Mrs. Anderson na
ganinsu tayi excusing kanga gun Baba ta nufa wajen mutumin.
“Lubabatu right?” Tayi maganan tana kallon ‘yar mutumin data sha ado sosai wane
Zeezee ga beads kota ina akanta, “follow me please Mr. Maitafseer” tace da mutumin.
Seat na Zeezee ta ajiyewa Lubabatu jakarta tace da Zeezee, “look here, I’ve made
you a friend her name is Lubabatu Maitafseer so stop crying okay?” Zeezeen da tunda
Aunty ta fara magana ba gane abinda take fad’i tayi ba banda Lubabatu dataji ta
ambata ta sake sa kuka bayan data k’are wa Lubabatu kallo, sosai Baba ya shiga
lalashinta “shikenan toh ya isa Lubabatu koh? Ta tab’a min ke? Sorry toh” Kukan
take har yanzu ba makawa, Lubabatu da dad nata suka tsaya kallon ta chan Zeezee
tace, “an yima Lubabatu kitson beads ni ba’a min ba” ta kuma fashewa da kuka.
Dariya sosai dukansu wajen suka hau yi Alhj. Matafseer ya nisanta yace, “da alama
wannan itace auta koh?”
“Itace” Baba ya amsa mai yana murmushi, miqewa yayi da Zeezee a hannunsa suka
gaisa da Alhj. Maitafseer tare da yin formal introduction. “Zeezee sauk’a kije ki
zauna kinji K’anwata?”
“O’o se ammin ilin kishon Lubabatu.” Baba ya kalli Dad na Lubiee dake murmushi
yace, “karka manta fa an mata kitso da beads me kyau tasa mahaifiyarta a gaba sam
se an cire mata take wanan fitina yanzu.”
“Ahab! Ko Lubiee nan jiya seda tace a cire mata na hana uwar, ba duk abinda yara
suke so zamuna musu ba.”
“Hakane...” cewar Baba kamar dagaske.
“Zeezee mama na sauk’o kinji? Ga k’awa nan na miki kinji sunan ta Lubiee.”
“O’o ni ba maman ka bane niba shohuwa bane.” tasa kuka. Dariya duk suka tsaya yi
at her comment, “ya isa, sauk’a toh K’anwata” da k’yar ya samu ya sauk’e ta, ta
tsaya tana kallon kitson Lubiee “ni se ammin ilin wannan.”
“Karki damu, muka koma gida za’a miki” Baba yayi assuring nata. “Sunan ki
Lubiee?” Zeezee ta tambayi Lubiee.
Kai Lubiee ta d’aga in response “ke kuma Zeezee?” Itama ta gyad’a mata kan.
“Yauwa jeku zauna toh se kuyi karatu fah” hannunta Lubiee taja suka zauna ko ba’a
tambaya ba za’a san Lubiee ta girmi Zeezee danko ta fita wayo, shiru Zeezee tayi
bata sake cewa komi ba seda taga Baba ya d’au hanyan barin ajin ta sake sa ihu
shima se yaji bare iya barinta ba, da k’yar Dad na Lubiee yajasa sukayi waje. Kuka
kenan! Kuka Zeezee ke wane ana cire mata rai Lubiee ce ke lalashinta har ta samu
tayi shiru ko da aka fita break Aunty da Nanny suka bubbud’ewa kowa lunch pack nasa
seda suka sha mamaki ganin yadda aka cika wa Zeezee nata.

Sede wani abin mamaki sekace ba Zeezee me rowan da muka sani ba, ganin nata
chocolates d’in sunfi na Lubiee yawa ta d’ibi guda biyu ta bata cikin d’an
k’ank’anin lokaci wasa da shak’uwa ya shiga tsakanin Zeezee da Lubiee.

~* ~* ~*
Ko minti d’aya Baba be k’ara kan 12:30PM (lokacin tashin su Zeezee) ba, ana
ringing bell ya shiga school yayi class nasu Zeezee alokacin suna ta wasa ita da
Lubiee da sauran ‘yan class nasu, tana ganin sa taje tayi hugging nasa, sosai Aunty
ta sake yabawa k’ok’ari irin na Zeezee dai-dai Baba yazo fitowa suka had’u da Baban
Lubiee gaisuwa kad’an sukayi kowa yabi path nasa.

~* ~* ~*
Dawowan su Baba gida Zeezee tayi ciki da gudu, Mama ta tarar tsaye a tsakar gida
da gudu taje tayi mata oyoyo Mama ta d’agata sama “yaya school d’in?”
“Mama nayi k’awa sunanta Lubiee ko Baba?”
“Sannu da zuwa Alhj.”
“Yauwa sannu”
“Zeezee tayi kuka da ka ajiye ta?”
“Sosai ma se a hankali zata saba ai.”
“Toh Auta na me aka koya muku?”
“Littin (written) form of A and sound ‘ahh’, and litten form of B and sound bhh.”
“Ahh gaskiya autan nawa na ja.”

****
Da yamma bayan tafiyan yaran islamiyya Baba kuma masallaci Zeezee ta samu kanta,
k’usa ta samu ta nufa garriage inda Baba ke parking motarsa da yake mugun ji dashi
fiye da duk wani abinda ya mallaka. Dai-dai driver’s door ta zana babban letter A
sannan da small one a gefensa haka tabi other side d’in ma tayi thesame thing with
letter B, jiki ta sata wane batai komai ba taje tasamu Mama dake zaune tsakar gida
tana tsifa, “Mama zan tayaki.”
“Inba kaud’i ba ina ke ina tsifa?”
“Ni shena miki.”
“Nace baza kiyi ba kuma ki yasar da k’usan” ihu tasa ta soma kuka, badan Mama na
so ba tace ta taso ta tayata. Tsifan da ba’ayi ba ranan kenan, ita ta hana Mama yi
ita kuma bawai iyawa tayi ba.
Atare Baba da yaransa suka iso gida kaman ance Baba duba motanka yana kai dubansa
yaga letter A na mai sallama “subhanallai me wannan? Waya min wannan d’anyen aikin?
‘yan unguwa ko meh?”
“Laaa Baba gashi ma har a nan!” cewar Yasmeen da hanzari ya zagaya ya duba.
“Aiko ba’a tambaya ba ansan Zeezee ce” cewar Mariam, a rayuwa ba abinda tafiso
kan taga Baba da Zeezee suna fad’a. A fusace Baba ya nufa ciki su Mariam ne a sahun
baya suna binsa.

“Zeezee! Zeezee! Zo nan!” tana jin muryan Baba ta lab’e bayan Mama dake zaune kan
sofa a parlour. “Ba babanki bane yake kiranki? Kije mana!”
“O’o, Mama karki bari ya tab’ani jan baki shweet d’ina.”
“Me kika masa tukuna?”
“Bab-” bata k’are maganan ba sega Baba da gayyansa suna shigowa cikin parlourn,
cusa kanta tayi jikin Mama.
“Ya haka Alhj wani abu ne?”
“Zeezee!” Ya kira sunanta a tsawace, kakkarwa ta soma, “mesa kika zana min jikin
mota? Dan bana dukanki koh? Wayace ki zana min mota?” Shiru... “Dake fa nake
magana!” Ya sake fad’a a tsawace. Kuka Zeezee tasa “toh kayi hak’uri amman kad’an
ka gani wallahi ai nasha gaya maka kadena biyewa ‘yar nan bakaji ga irin ta ai.”
Ignoring what Mama said yace, “kika sake zana min mota sena zane k’afafuwanki da
tsintsiya ce miki akayi mota gun rubutu ne?” Hannu ta d’aga ta zagi Baba, baki kap
dukansu including Baban suka sake in shock.
“Zagi! Ni kika zaga Zeezee?” D’ayan hannunta ta d’aga ta sake zaginsa sannan daga
bisani ta sauk’e duka ta b’uya bayan Mama “ai kad’an ka gani nasha gaya maka adinga
taka mata birki bakaji yau kanka abin ya koma ai.”

“Waya koya miki zagi? Iyyeh! Zan zane kifa! Ni kika zaga? Toh ki sake ki gani da
wayan charger zan shod’e kafafunki!” ya tsawata mata sosai, kuka ta shiga yi sosai
ko ta kanta beyi ba yabar parlour’n.
Dariya kenan! Ibraheem and others dariya suke tsakanin su da Allah wane dan shi
aka turo su duniya, suna dariya suna yimata rawa da wak’ar shoki ita ko se k’ara
volume na kukan nata take Mama ce kad’ai ke lalashinta “yi hak’uri amman kema kar
ki sake, ba kyau zagin Baba ku kuma haka akeyi ne? K’anwar ku ce fah.”
“Ai Mama ajiye wanga zance a gefe” cewar Mariam in between laughter.
“Ahtoh! Bature beyi k’arya ba, 9 days for the thieve one day for the owner.” Omar
ya mara mata baya suka cigaba da yiwa Zeezee dariya ita ko se kuka take.
Da dariyan yayyun nata ya isheta ta fice musu daga parlour’n gabad’ai taje chan
bayan BQ ta baje a k’asa se kukanta take sha kan ba gobe.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 10

_Words can’t ever explain how much I love you *AUNTY SIS*, thank you for
everything, thank you for being that one great special person to me. ILY
eternally😘😘😘😘 I devote this page in special honour to you! Don’t thank me you
deserve more and more!_

_5 minutes later..._
Baba ya dawo parlour da alama ya huce yanzu, Mama kad’ai ya tarar a parlour’n
tana tsifa, “Ina Zeezee?” Ya tambaya.
“Oho yayun ta sun sata gaba suna mata dariya ta fice ban san ina ta shiga ba” ba
tare da ya amsa taba ya fice tsakar gida ya shiga k’olla wa Zeezee kira tana jinsa
tak’i amsawa har a yanzu kukan take. Nemanta ya shiga yi chan bayan BQ ya tsince ta
nishinta har wani sama-sama yake sekuma tabasa tausayi yaji dama be mata masifan
ba, a nitse ya k’arisa gabanta yace, “Zeezee” kanta ta kawar daga kallon sa.
“K’anwata yi hak’uri kinji? Tashi mu koma ciki” nan ma shiru. “Yi hak’uri kinji
K’anwata Baba is sorry amman kema karki sake zana min mota kinji? In rubutu kikeson
yi let me know sena baki paper ko book kiyi. Mota ba wajen rubutu bane kinji?” da
k’yar ya samu ya shawo kanta dan banzan zuciya irin na Zeezee, bayan ta yarda ya
d’auketa yace, “su Ibraheem sun yita miki dariya ko?” Ta gyad’a kai a shagwabance.
“Yi hak’uri toh muje su baki hak’uri” a k’aramar parlour Baba ya tadda yaran,
“waya miki dariya cikinsu?” Ya tambayi Zeezee.

“Dukan su” tayi pointing nasu da finger.


“Oya ku bata hak’uri.”
“Hak’uri?” Exclaimed Ibraheem, “meh muka yi mata da zamu bata hak’uri?”
“Uwarka kayi mata, d’an banzan yaro bata hak’uri nace!” Chan k’asa-k’asa alsmost
like mumbling Ibraheem yace, “yi hak’uri.”
“Ban jika bafa, ka bata hak’uri kace Zeezee kiyi hak’uri, oya ina jinka.”
“Wallahi Baba raina ni zatayi.” yayi protesting.
“Da kai da rainin duk uwaku, bata hak’uri nace!” Haka Baba ya sasu individually
sukayi ma Zeezee apologising.

“Shikenan koh K’anwata yi hak’uri” sauk’eta yayi tare da ficewa. Habaici ‘yan
uwan nata suka hau yi suna zaginta kota kansu batayi ba taje ta d’ibo baby dolls
nata da teddy bears ta jerasu kan table a waje sannan ta d’au ruwa cikin wani d’an
karamin bucket ta ajiye se sponge case nata ta shiga ta d’auko. Wanka ta shiga yima
dolls natan tafara da teddy’n kenan Allah ya fito da Mama “kai! Kai! Karki sa ma
teddy’n ruwa!” dakatawa Zeezee tayi tana kallon Mama, “‘yar k’auye kawai wayace
miki ana wanke teddy bear?”
“Ni shena wanke, tunda Baba ya shiyo min su bashuyi wanka ba.”
“Ce maki akayi mutane nesu? Karki sa musu ruwa nace!”
“Ni shena sa, Baba! Baba!”
“Na’am K’anwata, Hafsah dan Allah kifita daga harkan yarinyan nan, dan Allah nace”
Baba yayi maganan daga cikin d’aki.
“Teddy bears fa zata ma wanka.”
“Eh kibarta please.”
“Dama ai ta nan kafi kauri, d’aure wa k’arya gindi, gidan wa aka tab’ayi wa
teddy bears wanka?” Dawo da kallonta tayi kan Zeezee “kinji wallahi karki kuskura
ki shigo min da su ciki in kin jik’an kinaji ko?”
“Shena shigo dasun” tana kaiwa nan ta kwarawa teddies d’in ruwa tahau musu wanka
jak’ab ta jik’asu da ruwa tazo shigowa dasu Mama ta bud’e mata ido sosai koda Baba
yayi magana ta nuna mai she’s damn serious baza’a shigo dasu ba.
“Shikenan K’anwata karki kula Mama kinji? In sun bushe seki shigo dasu, jeki
cigaba da wasan ki” ciki tayi ta d’auko mai sannan ta bud’e kit na Mama ta zaro
scissors ta fice da wuri bayan ta bi baby dolls da teddies d’in ta goggoga musu mai
ta d’au d’ayan baby doll me uban gashin tasata gaba ta yayyanke gashin tas, haka
tayi da sauran gabad’aya tayi musu aski Yasmeen ce tafito ta kamata in the act.

“Laaaha’ila! Bade aski kika yiwa dolls nakin ba?” Dariya tasa ta kira Mariam,
“Adda Mariam! Zokiga wani abu” atare Mariam da sauran suka fito, dariya suka hau yi
ganin yadda Zeezee ta tand’e gashin kan baby dolls natan wane aikin wanzami. Dariya
suka tsaya yi har seda Mama dake kitchen ta fito “wai haka kuka ta dariya lafiya
dai ko?”
“Dubi fa Mama” Yasmeen tayi maganan tana k’ok’orin d’ago d’aya daga cikin dolls
d’in cizo Zeezee takai mata “kal ki tab’a min Baby na.”
“Zeezee yanzu aski kika ma baby dolls nakin? Meye amfanin hakan?”
“Gashin je fito ai, ba Mulan (cartoon) ma ta ashke gashinta ba kuma ya shake
fitowa, nashu shuma je fito.”
Habbaa!! Dariya dukansu suka sa gun, saura harda hawaye da k’yar Mama ta iya
tayi shiru tace, “sekuma aka cemaki wannan cartoon ne? Ai tunda kika aske musu bai
sake fitowa.”
“Sheya fito”****

Kasancewar yaran basu je islamiyya ba yasa bayan Sallan La’asr kowannensu ya


kwanta yin bacci, Mama ma can ad’akinta ta mik’e tana bacci Baba da Zeezee ne
kad’ai idonsu biyu shima don yana buga lisafi ne yana gamawa ya mik’e kan gadon
d’akinsa “K’anwata zo mu kwanta kinji? Ajiye Ipad d’in kinga kinje school yau
kamata yayi ki huta kema, bakiga sauran yayyun naki duk sunyi bacci ba?”
“Ni o’o banajin basshi.”
“Toh Allah baki hak’uri ni zan kwanta” nan da nan Zeezee tabar d’akinsa tayi nasu
Mariam kulle ta tarar da k’ofan nasu, ba kalan knocking da batayi na suna ji suka
k’i bud’ewa dan kanta ta nufi nasu Ibraheem suma haka suna jinta tana knocking suka
k’i bud’e mata. D’an shirme tayi a tsakar gida, data gaji don kanta taje ta samu
Baba a d’aki ta mik’e gefensa itama tana wasa da d’an gemun dayake ajiewa. Ahaka
har bacci yayi gaba da ita ba ita ta tashi ba se 7:35PM alokacin gari yayi duhu
shaarrr. Bayan ta fito daga parlour ta nufi parlour inda ta tarar da ‘yan uwan nata
suna kallo “ni ahad’a min tea shafe yayi.”

“Ke waya gaya miki safe yayi? 7pm nefa yanzu.” Cewar Yasmeen.
“Meh 7pm? Ni a had’a min tea shafe yayi.”
“Shareta Yasmeen fitina ne da ita ai Baba ya hanata shan tea da daddare ba abinda
za’a had’a miki.” Mariam tayi stating. Kuka Zeezee tasa awajen tana kiran sunan
Baba seda yafito tayi shiru, “K’anwata kin tashi neh?”
“Baba kace Adda Mayyam ta had’a min tea.”
“Babu shan tea da daddare yana saki fitsarin kwance, in kina jin yunwa a dafa
miki indomie da egg naki koh?”
“Yanzu ai shafe ne ba dale ba ni a had’a min tea.”
“Dan fa bata saba baccin yamma bane shiyasa take gani kaman safe ne yanzun”
Ibraheem yayi explaining.
“Ba shakka kam, K’anwata ba safe bane fa yanzu dare ne.” Mik’ewa tayi k’asa agun
tana birgima tana ihu ita a had’a mata tea, ba yadda Baba beyi da ita ba ta gane fa
ba safiya bane dare ne yanzun amman inaaa sam takasa ganewa ita tunda tayi bacci ta
tashi toh safe yayi don haka kuma a had’a mata tea. Haka Mariam ta had’a mata tean
itade Mama tausayin katifanta take gudun kar Zeezee ta tsula mata fitsarin kwance.

**** 8:23PM
Baba da kansa ya taya Zeezee suka yi mata homework, bayan sun gama yasa mata book
nata cikin jaka “sauran bacci ko K’anwata? Akwai school gobe.”
“Nishe an sha min beads ilin na Lubiee” nan Mama dake karatun Qur’ani ta juyo ta
watsa mata harara “waye boyi-boyin ki agidan nan? Jiya kice se an cire yau kice a
miyar? Kinyi k’arya.”
“Ni nace ke jaki shamin ne” tayi maganan tare da murgud’a wa Mama baki.
“Ai ko kince nima ba sa miki zan ba.”
“Toh ya isa haka da Allah, kisa ‘yar yarinya a gaba kina exchanging words da ita,
Zeezee asa miki beads?”
“Eh” ta gyad’a kai.
“Oya Hafsah ibo beads d’in maza ki sa mata.”
“Wallahi-”
“Ni banashon Mama Ya Omal nakeso” Zeezee tayi sauri katse Mama.
“Omar kuma?” asked Baba.
“Eh shi.”
“Toh Hafsah mik’a mata beads d’in taje ta same shi ya samata.” Bayan Mama ta
mik’a mata ta fice a k’aramin parlour ta tsinci yayyun nata suna kallon King Of
Hearts gaban Omar tasha yayi saurin fad’in “ya haka? Matsa min nikam” beads natan
ta nuna mishi “gashi ka samin.” Wani kallon rainin hankali ya sakar mata sannan
yasa dariya ba shi kad’ai ba har sauran ‘yan uwan nasa.
“D’an daudu ne ni da zakice in sa miki beads?”
“Ni kasha min.”
“Bazan san ba maras kunya kawai, matsa min ko na gaggaura miki mari inba iskanci
ba ki dubi Adda Mariam da Yasmeen ki wani ce wai ni zan sa miki beads bakida kai.”
Kuka tasa wajen har seda Baba ya fito tayi shiru, “ya haka? Meke faruwa?”
“Omal ne yashamin beads wai o’o.”
“Laha ila! Ni? Yaushe nace barin sa miki ba?” Cewar Omar.
“Munafiki na sanka sarai maza zaunar da ita ka fara sa mata” ba tare da ya sake
musu ba ya soma aiwatar da abinda aka sashi.
“Ni banashon wannan film asa min dijney junior.” Banza da ita sukayi kaman basu
jita ba.
“Ashamin dijney” ta k’are maganar a shagwabance.
“Shin baku jita bane?” Asked Baba.
“Ayyah Baba yanzu fa ze k’are” cewar Mariam calmly.
“Wayyayi kayya ne ni asamin disney.”
Dogor tsuka Ibraheem yaja ya sa mata disney’n “kalli fa Baba shirme ake.”
“Eh bar mata shi takeso” yana kaiwa nan ya fice, habaici yaran sukayi tayi
tsakaninsu suna zagin Zeezee a yayinda Omar keta samata beads na mugunta yana
d’ad’d’angale gashin bayan ya gama mata ta wuce d’aki ta kwanta tsakiyan su Baba ma
yau.

***Washegari...
_6:05AM_
Bayan Mariam ta shigo ta gaishe da Baba kaman jiya ta gaya mai dalilin zuwanta
da ‘toh’ ya juya ya shiga tada Zeezee dake ta sharb’an bacci.
“Zeezee tashi kinji? Akwai school yau ko bakison kije kiga Lubiee?” Shiru...
“Tashi kinji K’anwata.”
“Ni o’o bayin jeba.”
“School d’in?”
“Eh bayin jeba.”
“Yi hak’uri.”
“Ni o’o” ba yadda Baba beyi da ita ta tashi ba tak’i. Bayan sunci fiye da minti
goma Zeezee tak’i tashi Baba yace da Mama “to ke bazaki sa baki bane?”
“Ni asuwa? Wai daddawa acikin kunu, bayan kai Zeezee tana jin maganan wani a
gidan nan ne? Tsakaninku” tana kaiwa nan ta juya mai baya tare da jan comforter.
“Zeezee tashi kinji?”
“Baba ni bayin jeba” tasa kuka, kuka take tsakaninta da Allah ita bazata jeba, at
long last Baba ya amince mata “jeki Mariam, Zeezee bazata je school ba yau se
gobe.” Kai kawai ta gyad’a cike da mamaki sannan ta fice bayan ficewarta Mama tace,
“lallai ka cigaba da yima yarinyan nan duk abinda takeso muga ina ze kai ka da ita
duka” banza da ita Baba yayi yaja Zeezee sukayi kwanciyar su.

*** A takaice ranan ba abinda Zeezee ta tsinana banda yima Mama rashin kunya da
rashin ji, washegari ma da k’yar Baba ya iya tadata aka shirya ta school. Koda taje
yau ma tayita kukan shagwaba seda taga Lubiee hankalinta ya d’an kwanta. Cikin sati
Zeezee ta saba da school sede kullum kafin a tasheta se anyi drama ga zab’an wanda
zeyi mata wanka, sa mata uniform, yi mata polish na takalami sa mata, do komi.

_Saturday afternoon 2:32PM_


Bajewa Zeezee tayi a tsakar gida tana kukan banza ita se an kaita gidan su
Lubiee tunda yau ba school. Kota kanta Mama batai ba, hasali ma ignoring nata tayi
ta shige d’akinta ta kwanta 2:40PM Baba ya dawo gida as always ya tambayeta whats
the problem bayan ta irga masa ya share mata hawaye tare da fad’a mata ta kwantar
da hankalin ta ze kaita gidan su Lubiee tunda yanada lambar Alhj. Maitafseer. Ba
tare da b’ata lokaci ba ya kirasa bayan sun gaisa ya sanar dashi halin da ake ciki,
cike da jin dad’i Alhj. Maitafseer yama Baba bayanin gidan sa dake Old GRA. D’aki
direct Baba ya wuce ya tarar da Mama kwance “Hafsah! Hafsah tashi ko bacci kike?”
“Ya akayi Alhj? So nake in huta kafin La’asr please.”
“Hutu? Ai hutu be kama kiba.”
“Me kake nufi?” tayi maganan tare da miqewa zaune.
“Zaki shirya kanki da Zeezee yanzu in kaiku unguwa.”
“Unguwa? Unguwa a ina?”
“Zaki raka Zeezee gidan k’awarta Lubiee” yayi stating in an I-don’t-care manner.
“Lallai kuwa!” Mama tasa hannunta a kunkumi “ba inda zani, akan ganin k’awarta
za’a tauye min hak’k’i, ina nan ba inda zani.”
“Semuga in zaman kanki kike a gidan nan na baki minti talatin ki shirya kanki da
Zeezee wallahi in bakiyi haka ba ranki yana iya b’aci” nan ya sauk’e Zeezee k’asa,
“karki damu kinji K’anwata zan kaiki gidan su Lubiee.”
“Toh Baba” anan ya fice. Mama tafi minti biyar a zaune tana hararar Zeezee sannan
daga bisani ta mik’e ta hau shiri exactly after 30 minutes Baba yadawo d’akin ya
tarar da ita sun gama shiri tsaf, dad’i sosai yaji “kaiii masha Allah, Hafsah ta
bade kyau ba tsaya keda K’anwata in d’auke ku hoto.”
Dad’i sosai Mama taji dan yadda Baba ya yaba kyanta da kuma kwalyanta amman sede
me? Batason nuna masa ta huce kan abinda yayi minutes ago, burning face tayi kan
bataji me yace ba.

“Haba Hafsah ta? Menayi kuma yanzu? Hoton ne bakiso?”


“Ban sani ba” tayi speaking up finally.
“Yi hak’uri toh ki tsaya” remembering that tana son ta tambayesa kud’in ankon
bikin ‘yar k’awarta yasa ta saki fuska taja Zeezee ya d’auke su hoton. “Yauwa masha
Allah, gaskiya in godewa Allah da yasa a beautacious woman like you ta kasance mata
ta” yayi maganar yana editing picture nasun.
“Uhm! Alhj ba de zak’in baki ba.”
“Ai kema kin sani Hafsah, a kullum dad’a kyau kike.”
“Uhm Alhj nace bikin ‘yar Aunty SDY fa ya matso.”
“Toh Allah sa ayi a sa’a ya kuma bada zaman lafiya mu tafi ko? Inason in wuce
kasuwa bayan nayi dropping naku.”
“Ameen kud’in ashobe nakeso.” Ai take mood na Baba ya canza, a rayuwa ba abinda
ya tsana kaman a tambayesa kud’i.
“Ke shikenan kullum cikin tambayan kud’i kina ruining happy moments? Mu tafi da
Allah.”
“Bangane ruining happy momnts ba daga tambayan kud’i seka haura min sama.”
“Toh ni banida tashi mu tafi kina b’ata min lokaci.” Komawa tayi ta zauna tace;
“Ai wallahi ba inda zani ina nan seka bada kud’in nan had it been matter’n ya
shafi Zeezee da without a second thought ka cire kud’i ka biya mata buk’ata wallahi
nima ko ka bani kud’in ashobe dana gudumawa ko kuwa kaida K’anwarka kuyi ficewar
ku” tayi stating in a serious tone. Ganin eh fa dagaske take ba inda zata inbe bata
kud’in ba ya nisanta yace, “haka zaku k’are ai mutane sun d’au rayuwan k’arya sun
aza wa kansu wai ba’a zuwa gidan biki seda ashobe toh Allah ya shirya ku
wallahi”Zeezee kam se raba ido take ta kalli Mama ta kalli Baba.
“Ameen ka fad’i koma meh nide ka bani kud’in kawai shikenan.” Dogon tsuka yaja
“mschww! Nawa ne kud’in?”
“Dubu ishirin ne duka, dubu goma na ashobe goma na gudumawa.”
“Har dubu goma zaki kai as gudumawa saboda auren Aneesa ne?” (blood sister ta)
“Muna zumunci sosai da Aunty SDY da kunya in kai mata abinda ya gaza dubu goma
tunda akwai kawai ka kawo.”
“Mschw! Allah shiryaki wallahi” hannu ya sa a aljihu yaciro wallet nasa tare da
irga fifteen thousand (15K) “amshi.” Hannu ta mik’a ta karb’a tare da irgawa bayan
da tagama taga be cika ba, “ya haka Alhj? Sauran biyar d’in fa?”
“Abinda nake dashi kenan in na kwashe duka kud’in na baki me zamuyi cafani dashi
gobe? Ki cikata da kud’inki maza tashi mu tafi.” Chan k’asa-k’asa tace, “ko a babu
na rage hanya” wardrobe nata ta nufa ta adana kud’in sannan suka fice.

~* ~* ~*
Dai-dai 3:07PM suka isa gidan su Lubiee bayan sun fito daga motan Baba dake daga
ciki yace, “se bayan La’asr in shaa Allah zanzo in d’auke ku.”
“Kai balaka shiga bane Baba?” Asked Zeezee.
“A’a K’anwata keda Mama na kawo ku ba-bye.”
“Toh se anjima” cewar Mama tare da jan hannun Zeezee suka shige.

*** Cikin d’an k’ank’anin lokaci Mama da Ummin Lubiee suka saba se hira suketa
zubawa wane sun san juna dama da jimawa, a yayinda Zeezee da Lubiee ke chan suna ta
wasa, sosai Lubiee taji dad’in ganin Zeezee, su ci abinci ma sunk’i se wasa suke a
tsakar gida kasancewar gidan nasu nada sarari sosai. Chan suka shigo ciki suka sami
su Mama a parlour inda ake ajiyewa Lubiee motar wasanta wanda yake nan Babba sosai,
ciki ta shiga ta tuk’a sannan tasa Zeezee ma ganin Zeezee bata iya ba tad’au remote
control d’in tana driving nata dashi. A hankali Zeezee ta koyi driving d’in itama
seyi takeyi ana cikin haka Baba yayi wa Mama waya kan gashi shigowa zasu gaisa da
Abban Lubiee se su tafi.
Bayan sun gaggaisa Mama ta d’ibo takalaman Zeezee dan sa mata ai atafir Zeezee
tace bazata koma gida ba anan zata kwana in ma zata koma chan gida sede in da motan
Lubiee zata tafi.
“Shin motan naki neda zakice zaki tafi dashi?” Lectures Mama. Cikin kuka Zeezee
tace, “ni wayyayi shena tafi dashi” tana shure k’afa.
Se hak’uri parents na Lubiee da Lubiee ke bata amman ina se kaman ma sake
tinzirata suke, if only zasu iya cewa ta d’au motan, atlast Baba yayi speaking up
“taso toh K’anwata irin wannan kikeso?” Nan ta gyad’a mai kai.

_Bade sai mata zakace zakayi ba?_ Mama tayi maganan unbelievably a zuci.
“Toh shikenan za’a saya miki” Baba ya fad’a tabbatar wa Mama da zarginta.
“Alhj a ina ne ka sayo wa Lubiee?”
“Anan Central...” nan yama Baba kwatancen shagon.
“Toh thank you.”
“You’re welcome incase ya ganka Alhj ya bugeka price d’in is 42K.”
“Haha toh nagode mu tafi Hafsah” ya k’are maganan yana sharewa Zeezee hawaye.
Baki Mama ta tab’e batare da tace komai ba, har gun motansu parents na Lubiee
sukayi masu rakiya akayi ba-bye sannan Baba ya kunna mota suka tafi. A maimakon
yayi hanyan gida seya kama hanyan kasuwa da Mama ta gano hakan se kawai ta girgiza
kai “bade central d’in zaka wuce siyo wa K’anwarka motan ba.”
“Toh ina ruwanki? Ke bakiga kukan datake tayi bane?”
“Toh wallahi in haka ne nima se ka cika min dubu biyar d’in.”
“Se mugani ai” haka Mama naji tana gani Baba yaje ya siyawa Zeezee motar itama
sede nata har yafi na Lubiee ma girma, her’s costs 50K. Ba rigimar da batai wa Baba
ba amman yak’i cika mata wai se k’arshen wata itan da za’ayi biki tsakiyan watan
yau.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 11

Isarsu gida Baba yasa Ibraheem ya ciro motar Zeezee daga mota, duk yaran se
bin motan suke da kallo sun kasa zama gu d’aya a babban parlour ya dire motan
Yasmeen da couldn’t hold it in anymore tace, “Baba motan waye?” Kafin Baba ya amsa
Zeezee ta amsa, “nawa ne.”
“Ja chan gefe waze sai miki wannan k’aton mota?” Baban dake jinsu ko k’ala bece
ba.
“Baba kaji Yashmeen wai ba nawa bane.”
“Seta hanashi zama nakin ai muga.”
“Baba wai dagaske motan Zeezee ne wannan?” Asked Omar.

*** Around 9:23PM


Zeezee fa ba wasa se tuk’i take ta shiga d’akin Mama ta fito tayi d’akinsu Mariam
tayi parlour, ba inda bata shiga da motar tata har bathroom, Yasmeen da takeson
tad’an d’ana itama taje ta samu Zeezee kafin ta baro parlour. “Zeezee ta d’an ara
min motarki na nad’a kinji?”
“O’o manya bashuwa chiga.”
“Manya erinsu Adda Mariam da Ya Ibraheem ba? Yi hak’uri.”
“Ni o’o banasho.” Da k’yar Yasmeen ta iya shawo kanta ta yarda ta bata dan
d’anawa, dududu da shigan Yasmeen befi minti d’ai ba Zeezee ta soma k’iriniya ita a
bata motan ta Yasmeen da mota ya mata dad’i kuwa tak’i. D’an karen banzan ihu ta
saki tare Baba ya shigo yana tambayan ko lafiya “ya haka? Me kikeyi k’atuwa dake
cikin motan Zeezee?”,Yayi tambayar wa Yasmeen dake ta raba ido bayan ta fito daga
motar. Nan Zeezee tamai bayanin komi, “yi hak’uri K’anwata kekuma ki sake shiga
mata mota kiga k’atuwar banza kawai.”

Washegari da safe bayan sun karya Yasmeen ta saci jiki tayi store room da ledarta
a hannu, gongonin madaran Zeezee ta bud’e tana d’iba tana cikin haka Zeezee ta
shigo d’aukan juice ta ganta “laaaa!! Yashmeen!” Ihunta yasa Yasmeen b’arar da
madaran dake hannuntan. “Wayyayi sena gayawa Baba kina d’iba min madala” nan danan
Yasmeen tashiga tarawa “yi hak’uri Zeezee dan Allah karki fad’a mai zemin masifa.”
“Wayyayi shena fad’a” nan ta juya
“Tsaya kiji, zan had’a miki naki kema a leda seki sha da akwai dad’i sosai.”
“K’alya kina shon kimin wayo.”
“Wallahi ba k’arya ba” wasu ledan ta sake cirowa tasawa Zeezee madara da milo
ciki sannan itama tayi haka anata sede nata yafi na Zeezee yawa aikuwa uwar rigima
ta hau ihu “wayyayi naki yafi nawa yawa ki k’aya min.”
“Toh kiyi shiru mana sekin fallashemu ne.”
“Ni sekin k’ala min” tasake sa kuka ai kafin su hankara Mama ta diro d’akin tare
da kamasu red-handed. Take Yasmeen ta b’oye ledarta a baya Zeezee kuwa se fitina
take “ni ki k’ala min”
“Me za’a k’ara mikin?” Ido Yasmeen tama Zeezee nufin tayi shiru ta b’oye nata
itama amman ina ita bata nan take ba, “Yasmeen ne tasha min madala kad’an nata da
yawa.”
“Madara!” Exclaimed Mama, “Yasmeen ban hanaki d’iban madara kina sha ba?” Kame-
kame Yasmeen ta shiga tana b’arin baki.
“Ni ki k’ala min” Zeezee tayi breaking silence d’in.
“Oya kawo madaran nan dukan ku” ba musu Yasmeen ta kai nata “kema Zeezee bani
naki” kaman dagske ta nufa wajen Mama kamar kyaftawan ido tabi gefenta tasa gudu
taje ta samu Baba tasha madaranta tayi nak!

Da Azahar bayan fitan Baba, kowa na zaune tsakar gida yana harkan gabansa Mama
ta duba ta duba bata ga Zeezee ba haka kawai jikinta ya bata aduk inda take b’arna
take “Yasmeen jeki dubo min me Zeezee take, shirun yayi yawa” da ‘toh’ ta mik’e
cikin gidan kap ta duba bataga Zeezee ba chan bayan BQ ta tsince ta da irin manya-
manyan dusten goge k’afan nan ta had’a ruwan kumfa tana dirje k’afanta dashi in aka
tambayeta haka taga me wankin su nayi any moment ya gama wanki. “La ha ilaa!! Mama
zo kiga abinda Zeezee keyi dirje k’afanta take da dutsen Sabi’u.” Daga tsakar gidan
Mama tace, “wallahi Zainab ki tashi kibar wajen kamin na iso, ke ina kika ga k’afan
ma bale kice zaki wani dirje, bar gun nace kokuwa inzo in miki shegen duka gashi
dama Babanku bai gida.”

“Kuma wayyayi balin shake baki shweet d’ina ba tunda kin fad’awa Mama.” Zeezee
tayi maganan wa Yasmeen tana barin gun, koda tazo shigewa ciki bata ce wa Mama dake
ta faman kiran sunanta ko uffan ba. D’akin Mama ta nufa ta tara teddy bears nata
sannan ta bud’e turaren Mama ta zazzage kan teddies d’in k’amshi har waje malam!
“Tsaya wannan ba k’amshin turare na bane?” Mama tayi maganan tare da miqewa ta
nufi d’akinta. “Ai ba turare d’aya bama” cewar Mariam. Mama na tabbatar da hakan ta
kama Zeezee ta mammaketa bada jimawa ba Baba ya dawo sarkin d’aure wa k’arya gindi,
balbale Mama ya shiga yi bayan na ya lallashi Zeezee.

Can da yamma, bayan fitan Baba masallaci yaran kuma Islamiya Zeezee tayi
parlourn Baba kawai setaji bari ta gwada cin buttons na remote yau, one-by-one ta
soma bi seda ta cinyesu tas sannan ta ajiye. Ta ajiye kenan kafin ta bar gun Baba
ya dawo harfa yayi d’aki wani abu yace mai ya dawo dan yadda yaga Zeezee na raba
ido “Laaa’ila!” Yayi exclaiming, gudu Zeeze tasa zata bar gun ai tuni ya kamota
yana bin remote na Plasma TV’nsa da kallo yace, “meh haka? Remote abinci neh da
zaki kama ki cinye buttons d’in!” Lamo tayi tana kallonsa a yayinda idanunta ke
cikowa da hawaye “dan bana zaneki koh?” A dai-dai nan Mama tashigo parlourn “ya
haka nakejin hayaniya?”
“Kalli fah! Remote d’i TV’n ta cinye kap! Abin naki lafiya kuwa Zeezee?”
“Ahap! Ai kad’an ka gani wallahi wataran tab’arya zata d’au ta fasa TV’n nan naka
dashi ba wai kai komi tayi dai-dai neba, this is just the begining Zeezee kinyi
dai-dai.”

“Wani irin magana kike haka Hafsah, kamar ya zakice mata tayi dai-dai? Remote fa
ta ci.”
“Da take kira na da suna na kota zagen kota min b’arna me kake cewa? Yarinya ace
abarta koba haka ba? kaima seka barta yanzu yarinya ce, Auta ta taho muje kici
abinci” da gudu Zeezee tayi gun Mama ta d’aga ta.
“Wallahi kin kyauta ke kuma wai bakinki razor ba ki sake cimin remote kigani
mschww!”
“Ramin mugunta tauna shi gajere!” Mama tayi stating tare da baro parlourn.

~* ~* ~*
Monday morning as always and usual Zeezee tayi ta daru da k’yar aka samu aka
shiryata school seda taga Lubiee hankalinta ya kwanta.
Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa Zeezee, rikicin yau daban na gobe daban ga
wani masifaffen rashin kunyan da take tashi dashi kuwa ba wanda ya isa ya tab’ata a
gidan, ka tab’ata ma jikin ka ze ma bayani. Ba yadda Mama batai da Baba asa Zeezee
a islamiya ba sam yak’i wai seta k’ara girma. Ana cikin haka bikin ‘yar Aunty SDY
ya iso duk events da akayi Mama tasamu hallara, sauran kai amarya Kano da za’ayi da
kuma yin dinner da ya rage, cikin sauk’in kai ta tambayi Baba izini ya kuma bata.
Kayakin Mama ne baje kan gado se had’a akwatin ta take tana cikin yin hakan
Zeezee ta shigo d’akin delibrately matching Mama’s ironed clothes da motan ta.

“Sabon iskanci nekuma haka Zeezee kina ji kina taka min kaya matsa min!”
“Toh ba na miki honk ba” ta murgud’a baki.
“Dake da honk d’in uwaku.”
“Kema-”
“Wallahi kika kuskura kika zageni dukan ki zanyi a d’akin nan” Mama tayi saurin
katse ta. “Ni thank god ma gobe zanyi tafiya in huta wallahi.”
“Nima shena biki.”
“Ai da inyi tafiya dake gwara na fasa tafiyan” ba tare da Zeezee ta tanka Mama ba
taja motan ta tayi d’akin Baba kukan munafirci ta soma tana mishi bayanin abinda ya
faru ba tare da b’ata lokaci ba ya mik’e suka dawo d’akin Mama aiko tana ganinsa
jikinta ya bata Zeezee ce takai k’ararta. “Wallahi Ahj inma batun inbawa Zeezee
hak’uri kazo yi is better ka koma dan ba bata zanba yau abin nata is getting out of
hand.”
“Kinsan kinyi laifi kenan, anyways ba abinda ya kawoni ba kenan ki had’awa Zeezee
kayakin ta itama da ita zakiyi tafiyan.” Zumbur Mama ta mik’e tsaye tana zaro ido,
“da wa zanyi tafiyan? Wallahi baran je ko ina da wannan maras kunyan ba.”
“Kin de jini” ya fad’a authoritatively.
“Wallahi bazan yi tafiya da yarainyan da bata jin magana naba, kalan taje tabani
kunya a idanun jama’a, ace yarinya sede bata ga abu gun yara ba tace itama se an
siya mata kuma da kake wani cewa zata bini makarantar ta kuma fa? Kai zaka je
mata?”

“Ba yau Thursday ba, Friday ne kawai bazata jeba ai, Sunday kun dawo Monday ta
wuce school koba haka ba?”
“Wallahi ba haka ba, ba inda zanje da wannan yarinyan ehe!”
“Ni shena biki Hafsah!” Zeezee tayi maganar cike da tsiwa da fitsara.
“Nifa na gaya miki Hafsah.”
“Wallahi da inje da ita gwara na fasa tafiyan ai dama anyi me yawan, dinner ne
daman kawai ya rage se in fasa zuwa.”
“Eh sede ki fasan amman muddin zaki sekinje da Zeezee.”
“Eh nafasan...” Bayan ficewar Baba, Mama ta d’au wayarta takira Aunty SDY tayi
making up excuses kan bazata samu zuwa ba dan ta gwammaci missing bikin da tai
tafiya da Zeezee.
★★★
Haka Allah ya cigaba da raya Zeezee har takai matakin primary 2 a karatu tanada
actual 6 years kenan, tana girma se dad’a kyau take sede wani hanzari ba gudu ba,
hak’waran gabanta duk sun zube se gib’i kake gani in ta washe bakin hakan yasa
siblings nata suke making jess of her suyi ta mata dariya itako tayita kuka tana
jan Allah ya isa in Baba ya dawo ta gaya mai ya d’au mataki. Zeezee de kam ta
gagari kowa a gidan rikicin yau daban na gobe daban, bata jin maganan kowa se na
Baba.

_Saturday evening, 4:38PM_


Mama ce zaune tsakar gida tana gyaran farce Zeezee ta shigo sanye take cikin wani
‘yar kanti iya gwiwarta, kitson shuku biyu ne akanta wanda ya sha beads. “Mama!”
Banza da ita Mama tayi “Mama!” Ta kira for the second time.
“Meh? Meh? Meh kuma kikeso yau?” Tayi maganar tare da d’ago kai tana k’ura wa
Zeezee ido.
“Kibani d’ari cikin kud’in da Ya Zannah yabani ranan.”
“Wai shin an gaya miki kud’in naki haifafa yake ne? Dubu biyu ne kacal kuma a
tambayan k’ananun canji duk kin k’arar da dubu biyun, d’arin dana baki jiya shine
k’arshen kud’in naki.”
“Wallahi k’arya ne kina son ki kashe min kud’ina ne kuma wallahi bazan yarda ba”
tayi maganan tana bubbuga k’afa. Dirty look Mama ta watsa mata sannan ta cigaba da
yankan farcenta ganin haka Zeezee ta wuceta takai dab da shiga d’akin Mama kenan
Mama ta sa mata kira “Zeezee! Wallahi kika kuskura kika tab’amin kud’i kinji na
rantse dukan ki zanyi na gaya miki kud’inki ya k’are.”
“Wallahi zaki gani” cewar Zeezee in a very low voice hawayenta ta share sannan ta
d’au hanyan barin gidan “kuma ki dawo ki sa hula kafin ki fitan.”
“Barin sa ba” ta murgud’a baki sannan ta fice. Gidan Ummu Mufeeda ta nufa bayan
tayi sallama ta gaishe ta “yauwa sannu Zeezee yawo ba d’an kwali ko? Bakisan bakin
mutane kad’ai ya isa ya karya miki wannan sumar taki ba?” Shiru Zeezee tayi batace
komi ba as tana nazarin wani k’aryan zata mata chan tace, “yauwa Mama na ne ta
turoni wai in kinada N500 ki bata in ta samu zata miyar miki, batada cenji ne kuma
tana son ta sallami wani.”

“Ji Maman Zeezee de dawata zance meh d’ari biyar kuma?” Tayi maganan tana ciro
d’ari biyar d’in daga lalitarta “gashi kai mata.”
“Toh nagode” ta amsa tare da ficewa, kantin Ya Wakeel ta nufa ta kashe d’ari
biyar d’in tas cikin sayayyan shirmen banza sannan tadawo gida Mama na ganinta bata
ce mata komi ba ta wuce da ledar parlour. Bajewa tayi kan rug ta tab’a wannan ta
tab’a wancan tana cikin haka Mama ta shigo, ko d’ago kai ta kalleta batai ba se
shan chocolates nata take “ke ina kika samu kud’i kikayo wannan siyaya?” Shiru...
“Dake fa nake magana! Am very sure babu kalan wad’annan chocolates cikin na school
naki.”
“Haaa’ah! Nikam ba kud’in ki na d’auka ba ina ruwanki?”
“Kinsan Allah zan mauje ki, ina kika samu kud’i nace?”
“Nima ban sani ba.” Ganin Mama tayo kanta da nufin bugin ta tasa ihu “zan fad’a
zan fad’a.”
Oyya speak up!”
“Gidan Ummu Mufeeda naje nace kince ta ara miki d’ari biyar-”
“Ni?!” Mama ta dafe k’irji.
“Amman karki damu tace ta baki a kyauta kinga ba sekin biya taba.” Bata hankara
ba Mama ta fisgota ta hau nad’a mata na jaki bayan ta mata lik’is ta tattara
chocolates d’in tayi sadaka dasu wa almajirai. Kuka kenan! Kuka Zeezee tayi tayi
tana jan Allah ya isa har bacci ya isketa a garriage koda yaran suka dawo daga
islamiyya suka ganta kwance gun basuyi ta kanta ba dan sun san halinta sarai daga
tambayarta meya faru seta hauka da rashin kunya kokuwa in Baba ya dawo tace kai ka
tab’a ta.

Cikin bacci Zeezee taji k’aran security’n motan Baba, firgit ta mik’e ta shiga
rusa sabon kuka bayan yayi parking motar taje ta same sa tana hawaye “ya haka
K’anwata keda waye?”
“Maamaa!” Ta fad’a a shagwabance.
“Me ta miki yau kuma?”
“Duka na tayi haka kawai” d’aga ta yayi ya share mata hawayen sannan sukayi ciki
“Hafsah! Hafsah! Wallahi muguntan naki ya soma yawa kullum sede ba’a barki da ‘yar
nan ba se kiyi ta dukanta sekace ganga? Ina kike fito nace!” Da confidence nata ta
fito “ai bakaji me tayi yau ba...” nan ta kwashe labarin komi ta bawa Baba hoping
he’ll back her today, to her suprise bayan ya gama sauraronta yace, “toh laifin
waye? Da kin bata kud’in da ta tambayekin da duk hakan ya faru ne?”
“Lallai ma Alhj!” Mama ta fad’a short of words, “kana nufin tayi dai-dai kenan?”
“Bance tayi dai-dai ba amman you are partially to blame kuma karki sake tab’a ta
dan wallahi zan soma jan Allah ya isa.”
“Wallahi sede kaja amman muddin ta sake tafka rashin hankali kaman na yau banga
me hana ni dukanta ba abin kunya yarinya is 6 years old almost getting to 7 amma
banda fatiha da nas, falaq and ikhlas ba abinda ta sani” tana kaiwa nan tayi ciki.
“Kar ki jita kinji K’anwa ta zan nemo miki malami yana miki karatu a gida
islamiyya nede bara kije ba.”
“Toh Baba.”
Alwalan Sallan Maghrib suka shiga yi kasancewar yau Baba ne ze jasu a gida kowa
na alwala banda Zeezee datayi cross leg kan kujera tana game a ipad, fitowan Mama
daga bayi ta galla mata harara “ke bazaki tashi kiyi alwalan bane?”
“Barinyin ba!” daidai nan shigowan Baba d’akin kenan “ina yaran suke? Ku fito
muyi sallah.”
“Zeezeen fah? Baza tayi sallan bane?”
“Ke ina ruwanki yarinyan nan is just 6 kuma ko a muslince ma cewa akayi se yaro
yakai 7 a soma sasa.”
“Meh laifi idan an fara sata yanzu?”
“Kanki akeji Ibraheem ku fito.” Nan suka fiffito Baba yahau jansu bayan sun idar
Baba yasa Zeezee ta d’auko school bag nata dan yin homework nata.

“Zab’i wanda ze miki homework d’in amman banda Ibraheem kinga yana aikin project
nasa” (Ibraheem is now a petrochemical engineering student at ATBU) yana 400
level.)
“Ni shi nakeso.”
“Yi hak’uri k’anwata gobe shi ze miki amman yau ki zab’i daya cikin sauran kinji?
Maza jeki su miki kizo mu kwanta” ba tare da tace komi ba ta fice k’aramin parlour,
su Mariam ta tarar ba Ibraheem. “Ya Omar kamin homework d’ina.”
Omar dake jin dad’in chatting dayake ya d’ago kai tare da galla mata harara
“bazanyi ba bakiga ina amfani da waya na bane.”
“Kana chatting da budurwa de kuma sena fad’awa Baba kema Adda Mariam naji ranan
keda Ya Ibraheem kuna magana wai wani friend d’inshi na sonki duk sena fad’a.”
“Banza yanzu ma kije ki fad’a” cewar Mariam tare da watsa mata harara.
“Zaka min ne ko sena je na gayawa Baba?” tayi maganan tana hararsa da manya-
manyan idanunta.
“Kawo in miki” yayi maganan full of sarcasm, wurga mai jakar nata tayi “Verbal
Reasoning ne da Quantitative inka gama ka kaimin jaka na d’aki” ta k’are maganan
tana harararsa.
“Kutcee! Ya Omar kana jinta take ma wannan rashin kunyan?” Cewar Yasmeen.
“A’a’hah! Barta kekam” yadawo da kallonsa kan Zeezee, “in nagama zan kai miki
suke nan homwork d’in?”
“An bamu a handwriting ma shima kamin page 17.”
“Lallai! yanzu handwriting d’inma bazakiyi ba?” Yaseen ta fad’a.
“Ina ruwanki?” ta murgud’a mata baki “dan bance kimin ba kike da bakin magana
koh?”
“Ahh ahh! Kekam Yasmeen barta mana, jeki kwanta ‘YAR GATAN BABA.” Dad’i sosai
taji taje tayi ta game nata a d’aki koda Baba ya tambayeta assignment infa? K’arya
ta mai tace sun gama.
“Omar I don’t trust you what are you planning on doing? Yau kai ne Zeezee ke ma
rashin kunya haka baka ce komi ba” states Mariam.
“Bar ni da ita Adda Mariam ita ba hegiya ba, kwab’a mata homework d’in zan ta
kama zero yadda gobe za’ayi punishing nata da kyau.”
“Pwhahhah!” Suka kwashe da dariya “wallahi amman ka burgeni da haka zamuna
getting back at her fitsararriyar yarinya haka” Yasmin tayi maganan tana jin dad’i.

DON’T BE A SILENT READER TELL ME HOW U ACTUALLY FEEL, THINK ABOUT MY NOVEL

MIEMIEBEE
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 12
_Heres a page in honour of you sweetheart divas😻 *Maryam (Abmar), Deeylerhh*
and *MeenoUr,* my boo thang thang, ILY'all!💕_

9:14PM Omar yayi sallama d’akinsu Mama ya ajiyewa Zeezee jakarta tare da yiwa
su Baba seda safe. Bayan Mama ta fito daga wanka ta kalli Zeezee data d’ale
tsakiyan gado tana shirin bacci tace, “jibi abin kunya” sannan ta k’arasa gaban
mirror tare da jan kujera ta zauna ta soma shafa mai, jira take Baba ya tanka ta
taji yayi shiru hakan ya sake bata daman magana “ace yarinya shekarunta shida
almost getting to seven amman a tsakiyan iyayenta take kwana ko a ina aka tab’ayin
haka oho.”
“Ji yadda kike magana kaman kinyi mata d’aki tak’i kwana ciki, bansani ba ko a
parlour kikeson tana kwana.”
“Kamar ya a parlour? Baga d’akin su Yasmeen ba.”
“Wai kina nufin Zeezee ta soma kwana da su Mariam? Mugayen can!”
“Eh mana!” ta basa amsa take. “Ba yayyun ta bane?”
“A dalilin meh zan tura K’anwata kwana da wad’ancan mugayen? Ba abinda ze kai
Zeezee d’akinsu Mariam kiji ki sani.”
“Lallai kuwa!” Tayi maganan tare da miqewa ta nufa gun wardrobe nata searching
for her night gown “shikenan kullum damu zata na kwana?”
“Eh har sena mata d’akinta itama.”
“D’aki?! Ta zaro ido waje a ina zakayi mata d’akin?”
“Wannan kuma is for me to know and you to find out kin gama feshe-feshenki ki
kashe mana wuta, Allah bamu alkhairi” yana kaiwa nan yaja musu comforter da Zeezee
sukayi baccinsu comfortably as always.

~* ~* ~*
_Monday morning, 6:10AM_
“Ke! Zeezee wallahi ki tashi kona zuba miki ruwan sanyi iskancin banza shekaranki
nawa da shiga makaranta amman ace kullum sekin bawa mutum headache kafin ki tashi a
wani gidan ma ke za kina yin wanka da kanki, tashi!” Yasmeen ta k’are maganan cikin
sautin tsawa ganin ko kad’an Zeezeen dake baccinta tana tsotsan thumb finger’nta
bata motsa ba, hakan ya sake k’uludda ita “wallahi zan mareki tunda Baba bayi
gida.”
“Mareta wallahi” cewar Mama ai tana jinki. Tas! Yasmeen ta wanke d’uwawun Zeezee
da mari da force ta miqe zaune tare da sa ihu.
“Wallahi barin je makarantan ba muguwa kawai.”
“Huummm!” Yasmeen ta toshe hanci “ji warin baki sekace latrine, k’azama kawai tashi
da Allah!” haka da k’yar Yasmeen ta samu tasa Zeezee toilet nan ma zama tayi kan
toilet sit tak’iyin brushing da ya kamata tayin, bayan 2 mins Yasmeen ta dawo ready
to bath her taga ko brushing Zeezee batai ba hasali ma bacci take comfortably kan
toilet sit d’in, ruwan sanyi ta tsiyaya daga famfo ta fesa mata a fuska firgit har
tana neman fad’i daga kan sit d’in ta farka “meh haka? Muguwa kawai, Allah ya isa”
tasa ihu “Allah ya isa mumuna kawai.”
“Fad’i koma meh wallahi yau tunda Baba bai gida se kin gommaci kid’a da
karatu, maza sauk’o daga kan sit d’in.”
“Toh kin min tsarki ne da zan sauk’on?” Ta watsa mata harara.
“Yanzu fitsarin ma se an miki tsarki?”
“Pupu nayi.”
“Mschww dirty girl kawai”
“Niba ke ce zakimin ba Ya Omar nakeso.”
“In zaki tsaya ki tsaya” aiko Zeezee ta bijire mata itafa se Omar ze wanke mata
pupu. Mama ce tasa baki a k’arshe ta tura Yasmeen kirawo Omar.

***
Bayan ta samesa a d’akinsu ta isar masa da sak‘on.
“Wallahi bazan jeba kashin ya bushe a jikinta inde ni zan wanke mata.”
“Kaine kashi ze bushe a d’uwawunka ba ita ba d’an banzan yaro kawai maza tashi!”
Scolded Baba “bazaka tashin bane sena gaggaura maka mari?”
“Allah sarki Baba yarinyan nan fa yaci ace ta soma tsarki da kanta she is almost
getting to seven (7) years”
“Eh bazata wanken ba seta cika seven (7) d’in wuce nace mana!” Haka yana
kumbure-kumbure yaje ya wanke mata pupun Yasmeen ta mata wanka. 6:40AM Yasmeen ta
kawo wa Zeezee breakfast nata na chips and eggs aiko tana gani ta soma rigima “ni
bance chips nake so ba ni indomie zan ci.”
“Kinga ba time yanzu K’anwata yi hak’uri kici wannan d’in.”
“O’o tahau shure k’afafu ni indomie nakeso.”
“Oya Yasmeen kiyi sauri ki dafa mata kiyi amfani da ruwan kettle seya dahu da
wuri.” Kamar wacce zatayi kuka Yasmeen tace, “wallahi Baba ba ci zatayi ba yanzu da
indomien aka dafa cewa zatayi chips takeso neman sa mutum aiki ne kawai.”
“Banason suratan banza kije ki dafa mata nace!” In 18 mins indomie’n Zeezee ya
iso kad’an taci ta jagwal-gwala saura as expected, Mama ta zab’a wai ta sama ta
uniform, bayan an sa mata ta d’ago socks nata ta samata anzo sa takalmi aikuwa
Zeezee tace ba wannan zata sa ba yau bayan taga shi Omar ya mata polishing, haka
yana ji yana gani Baba yasa sa sake mata polishing wani sam be damu ba saboda yasan
meya shirya mata a school yau.

AT SCHOOL *~ *
“All stand!” Ordered Mrs. Audu (form teacher’n su Zeezee) nan da nan su Zeezee da
sauran class members nata suka mik’e suna nan har yanzu class da seat nasu d’aya da
Lubiee they must be best friends now. “Submit all of your homeworks row-by-row all
at once.” Nan da nan d’aliban suka fiddo da homeworks nasu su kayi kamar yadda
teacher’n sun ta buk’ata.

_7 minutes later..._
“Zainab Isma’il Yusouf!” Called Mrs. Audu angrily, “come here!” Zeezeen da
batasan me tayi ba ta mik’e a sanyaye “yes Ma’am.”
“Whats wrong with you? How can you fail all of your homeworks?”
“Me?” Zeezee ta dafe k’irji.
“Yes or do you need some proof?” Mrs. Audu ta d’ago mata zeron da takama a duka
homeworks natan “shame on you! class say shame on Zainab” nan ‘yan aji suka hau
yima Zeezee shame shame shame illa Lubiee ce bata mata ba. Kuka Zeezee tayi tayi
ranan ana fita break ta tarke wata Deborah a lungu tayi mata d’ankaren duka sannan
tayi warning nata kan inta kuskura ta kai k’ararta seta mata wanda yafi wannan.
Kuma badan komi ta daki yarinyan ba sedan wai ta lura da Aunty tasa su yi mata
shame duk Deborah tafi yi da ihu. Baba na zuwa d’aukanta ta nuna mishi homework da
Omar ya mata ta fad’i.

*** _Back home..._


“Omar! Omar! Zo nan!” Omar dayasan this was coming ya mik’e yaje “na’am Baba”
wulla mai littafin Baba yayi, “explain this, meh haka?” Bayan ya k’are wa makeken
zeron dake kan fejin kallo yayi k’ok’ari ya had’iye dariyan sa sannan yace,
“Jiya ina kiranta tazo muyi mata homework d’in tak’i ta gudu nikuma... Nikuma...”
“Kai kuma kayi deciding da kayi failing nata har kasa ayi mata wak’a gaban aji
koh? Toh maza ka bata hak’uri.” Ai atapir Omar yace baze bada ba seda Baba yayi
dagaske yabata hak’urin aka wuce wajan. Fita Baba yayi kafin nan yace, “kice
Mamanku tayi miki homework naki kinji?”
“Toh ba-bye”

Mama dake kitchen ne ta fito tana yi mata sannu da zuwa se gani tayi fuskan
Zeezee da alaman yak’ushi. “Ya haka waya miki wannan abu a fuska?”
“Babu” tabada amsa tana cigaba da tafiya.
“K’arya kike fad’a kikayi ko?”
“Nikam ki barni” daga nan ta wuce ciki, bayan tagama wulli da socks da takalmanta
as always tabar vest da panties zallah sannan ta fito da school bag nata zuwa
d’akin Mama “wai aji Baba kimin homework d’ina.”
“Yau kuma? Ki jira yayyun naki suka dawo su maki.”
“Ba kina gani ba Ya Omar ya jefar dani da gan-gan naci zero ni kimin.”
“Kawo toh” bayan ta fito da homework d’in Mama ta buk’aceta ta faddo da pencil
pack nata sede wayam ba komi ciki.
“Ina pencils nakin suka je?” Shiruu ba amsa, “dake fa nake magana? Ina sabin
pencils dana sa maki ciki jiya?”
“Haaa’a! babu sun b’ata ki d’auko min wani” hannu Mama takai bakinta ta bige da
k’arfi seda Zeezee tasa ihu, “idan baki bar min magana da rashin kunya ba na riga
buge bakin naki kenan.”
“Allah ya isa” ta fad’a tana riqe da bakin nata.
“Ina pencils d’in suke? Ko ki fad’a ko in miki d’ankaren duka.”
“Ni shikenam kullum kiyita duka na Allah ze sak’amin.”
“Ina pencils d’in?!” ta daka mata tsawa, itama a tsawacen ta miyar mata da amsar;
“Sun b’ata babu!”
“Toh wallahi ki bud’e wannan kunnuwan naki da kyau ki jini, zan sa miki wasu
biyun kika b’atar da wayan charger na zan chod’e wannan k’afafun naki kinji na
rantse” haka da rigima suka samu suka k’are homework d’in.

Baba na dawowa gida that was by 4:23PM kenan Mama taje ta irga mai kan Zeezee
taje tana fad’a a school, atapir Baba yace be yarda ba a kira Zeezeen yaga fuskan.
“Zeezee! Zeezee! Zo” Mama ta kirata, d’akinsu Mariam ta shiga da wuri ta lak’uto
foundation da concealer nasu ta shafa gun ta rufe tabon yak’ushin sannan taje
“meneh?”
“Zo ina gunda k’awar taki ta yak’ushe kin?”
“Nifa ba a yak’usheni ba.”
“Maqaryaciya kawo fuskan” ba musu taje Mama ta duba gun tarasa ciwon.
“Ina yake toh? Neman yima yarinya sharri kawai.”
“Wallahi Alhj akwai-” katse ta yayi “seki nuna ai in akwan!”
“Laaa! Bade foundation kika shafa ba?” Mama tayi maganan tana murza hannun ta don
gaskata abinda idonta ke fad’i mata. Jin haka Zeezee taja baya da wuri “Baba kaga
Mama tana min sharri ba?”
“Karki kulata K’anwata jeki sa hijabi yau malamin ki ze fara zuwa.”

“Yau Baba?!” Tayi exclaiming.


“Eh Zeezee zaki fara karatu.”
“O’o ni bana so suna duka.”
“Wannan bare dake kiba” haka da k’yar ta amince 4:30PM malaminta ya iso tayi
karatu tak’i tayita shiririta ita wai bataso. Haka rayuwan Zeezee ya cigaba da
kasancewa har ta gama primary one rigimin yau daban na gobe daban ta gagari kowa a
gidan.

Washegari da safe Baba yakai Zeezee asibitin ido kasancewar complaining da take,
bayan an auna idon nata aka gano tana suffering from short-sightness take gun aka
auna idonta aka bata eye glasses aiko Zeezee tace ita bataso ‘yan ajinsu zasu mata
dariya kasancewar wani film data kalla UGLY BETTY.
Suna dawowa gida tacire glass d’in ita bataso da k’yar Baba yayi convincing nata
ta miyar, Ibraheem da Mariam zaune suka tarar a tsakar gida kasancewar yau baida
lectures da safe ita kuma Mariam ta gama makaranta tana jiran admission. Gani kawai
sukayi Zeezee da glass se binta suke da kallo a yayinda take watsa musu harara
ganin sun kusan shiga ciki yayyun nata basuyi mata glass yayi kyau ba tasa kuka “ya
haka kuma? keda waye?” Baba ya tambayeta.
“Su Ya Ibraheem basu cemin glass d’ina yayi kyau ba ni banaso” tasake sa ihu har
seda Mama dake ciki tafito.
“Har kun dawo ne? Ya Zeezee da glass haka? Idon bai gani ne?” Ta tambaya, nan
Baba yayi mata bayanin komai “ayya auta ta Allah baki lafiya” maimakon Zeezee tace
ameen seta kuma rushewa da sabon kuka “toh ni kuma menace?”
“Bakice min yayi kyau ba ni banaso.”
“Haba! Kin ganki kuwa? Dr. kawai, Dr. Zainab.”
“Su Ya Ibraheem basu ce min yayi kyau ba.”
“Barsu, bara ku ce mata yayi kyau bane? Sam baku iya zama da k’annenku ba” Baba
yayi scolding nasu, da k’yar Mariam ta iya shanye dariyan ta “yayi kyau” suka fad’a
in unison.
“Aikin banza kawai mu shiga ciki K’anwata” haka koda su Omar suka dawo suma basu
cemata glass nata yayi kyau ba tayita kukan banza.

~* ~* ~*
The following day as always da k’yar aka samu aka shirya Zeezee, k’iriniyarta ta
yau tafi ta kowani rana sabida Baba baya gida, tun fitan sa sallan Asubah be dawo
ba da alama wa’azi ya rik’e shi. Bayan an gama shiryata Mama ta feffesheta da
turare sannan ta wuce gaban dressing mirror dan d’auko wa Zeezee eye glasses nata
wayam! Ta duba gun da ta ajiye jiya babu ta tambayi kowa a gidan duk sukace basu
gani ba, nan fa aka shiga neman glass na Zeezee ana cikin haka dai-dai 7:08AM kenan
Baba ya dawo gida “hope kun gama shiri, oya kufito mu tafi.”
“Alhj ko kaga eye glasses na Zeezee?” Mama tayi tambayar tana duban cikin
wardrobe nata.
“Ba gaban mirror kika ajiye jiya ba?”
“Toh gashi babu ba inda ban duba ba duk babu.”
“Kamar ya babu Hafsah? So kike kicemin glasses d’in yayi k’afa ko meh? Ni wallahi
bana son carelessness yanzu ya kikeson taje makarantar?”
“Alhj ji yadda kake magana kaman da gan-gan nayi misplacing ni wallahi am certain
agaban mirror na ajiye.”
“Seki d’auka ai in achan d’in kika ajiye.” Bin Zeezeen dake zaune kan gado Mama
tayi da kallo tace, “Ke ina kika kai glasses nakin?”

“Aww yanzu kuma sharri zakiyi mata? Kuma ban hanaki ce mata ‘Ke’ ba?”
“Ai tasan me nake nufi ina kika kai glasses d’in?”
“Ni ban d’auka ba, Baba kaga Mama koh?”
“Barta K’anwata zo abinki.”
“Ai tun jiya take cewa batason glass d’in ba tantama ita ta d’auka ta b’oye.”
“Kede kice kinason mata sharri kawai K’anwata ke kika d’auka?”
“A’a” ta kad’a kai.
“Tsakanin ki da wa?” Baba ya tambayeta, Shiruu Zeezee bata ce komai ba “Zeezee ke
kika b’oye wai?”
“Dagaske bani bane Baba.”
“Za kiyi wa Baba k’arya?” Kai ta kad’a “to gayamun ina glasses nakin yake?” Baki
ta turo “ni banaso.”
“Bakiji me Dr. yace bane Zeezee? Idon ki na ciwo only if kina sawa idon zasu
gyaru ko kinaso ki tsufa ba ido?”
“O’o”
“Good then you must wear your glasses temporarily kinji? Yi hak’uri kije ki
d’auko min.” Zatayi magana Baba yayi saurin katse ta “shhh! And je ki d’auko min”
haka ba yadda ta iya tabi Mama da dirty look sannan ta fice babban parlour inda ta
b’oye glasses d’in in between cushion na 3 seater tasa hannu ta zaro ta kaiwa Baba
yasa mata da kansa sannan suka fice se kumbure-kumbure take a motan haka har suka
isa school.

AT SCHOOL...

Kap ‘yan ajin su Zeezee se binta suke da kallo ganinta da sukayi da eye glasses
wanda ba k’aramin ci mata rai yake ba, ji take kamar ta cire glasses d’in ta b’oye.

Ana fita break Zeezee ta tarke yarinya a lungu tayi mata dukan tsiya itama de ta
bugu sede ba kamar yadda ta daki yarinyan ba agarin haka ta samu cizo babba a
hannunta. Suna cikin damben Allah ya kawo teacher wucewa nan da nan ya rabasu akayi
dasu admin block, tsawata musu sosai headmaster yayi sannan ya kira iyayensu sam
Baba yak’i yarda da aka cemai wai Zeezee tayi fad’a a school ashe de ba k’arya ba
Mama kemai ba last time data ce masa Zeezee tana fad’a a school. Hak’uri sosai Baba
da parent na d’ayan yarinyan suka tayi ta bawa headmaster d’in in bahaka ba yace
sam se an basu punishment na picking after every school day for the whole week.
Bayan an samu an shawo kan komi Baba yayi godiya yaja hannun Zeezee suka fice “haba
K’anwata wani irin hali ne haka na fad’a school? Bafa haka takwararki take ba.”

“Toh Baba kasan me tamin ne?”


“Koda me ta miki be kamata ki tuhumeta da dambe ba, kai k’aranta zakiyi wa form
teacher’nku.”
“Kai k’ara Baba ai se ‘yan class namu sumin dariya ni ta sake kallo na wallahi
dukanta zanyi.”
“Aww bazakiji maganan Baba ba kenan? Inda kuma yanzu kin ji mata babban ciwo ko
kin fasa mata kai fah?” Shiru tayi batace komi ba har suka isa gida, isarsu ta fito
ita kad’anta Baba na binta da jakanta da lunch pack suna shiga ciki sukayi karo da
Mama tana kwashe kayan shanya kan igiya sannu da zuwa ta musu data lura da yadda
Zeezee ke cinno k’aramin bakinta tagano da akwai matsala. “Mekuma ya faru yau? Alhj
ko kunyi fad’a ne?” Kan wanda bazeyi magana ba yace;
“Ke yanzu da zaran na fad’a miki meya faru seki hau cewa ai dama na gaya maka”
Baba na maganan Mama kuwa na bin Zeezee da kallo nan ta hango babban shatin cizon
dake hannun damanta.

“Hohoho dambe ma tayi yau a school kenan, no wonder ka fita d’auko ta yau da
wuri halan ma har headmaster’s office aka kaita ko? Ko sunsa sunanta a black list?”
“Ke da Allah bakin ya isa haka ba sunanta da aka sa a balck list.”
“Me za’a fasa dama mutuwa ko hisabi? Mena gaya maka kwanaki? Ai wallahi kad’an ka
gani wataran seta fasa ma wata kai a school a kaiku duka police station anan ne
zakuyi hankali.”
“Toh ya isa da Allah muguwa kawai abinda dama kika iya kenan baki wa mutane
instead kijata kiyi mata nasiha kina cewa har station se an kaita to tare zakuje
kiji in gaya miki.”
“Ai ba nasihar da zan mata kanku akeji tunda cikin sauran ‘ya‘ya na k’waya hud’u
ba wanda aka tab’a kawo min k’ararsa yana fad’a a school dan anyi akan Zeezee se
meh? Kai ka lalata mata tarbiyyarta saboda haka ba abinda zance mata kai d’in daka
b’ata seka gyara” tana kaiwa nan ta gama sauk’e kayakin daga igiya tayi ficewarta.

_Wednesday afternoon, 2:35PM_


Chess of drawer’n Mama wanda ake adana mata socks nata ta fito dasu, sanye take
da black english wear kanta a tsefe an kamasa sakwa-sakwa. A dai-dai tsakar gida ta
ajiye sannan ta d’ago new pair of socks tasa ta tattara teddy bears nata ta jerasu
kan table da bulala rik’e hannunta wai tana musu lesson. Mama na gama cin abinci
tafito kai plate kitchen ta tarar da Zeezee da socks tana yawo tsakar gida “haba!
Zeezee wani irin sabon salon iskanci ne wannan? An tab’a sa farin socks a gida ne?
Bana school bane?”
“Ni ki banni ai ba naki bane nawa ne.”
“Oya maza cire socks d’in ki mayar”
“O’o” ta fad’a stubbornly, idanun Mama na sauk’a kan drawern ta da Zeezee tayi
wurgi dashi tsakar gidan ta fusata, kanta tanufa ta nad’a mata na jaki ta kuma sata
ta miyar da drawer’n ciki, kuka Zeezee tayi tayi har seda Baba yadawo as always ya
bata gaskiya ya yita balbale Mama yana ikirarin ze soma jan Allah ya isa next time
ta sake tab’a masa Zeezee’nsa.

★★★★★
Days, months and even years passed by Zeezee nada eleven (11) years yanzu tana
matakin Jss 1 a LYS still, yarinya a kullum dad’a kyau take ga tsawo masha Allah
bata da wani kauri ‘yar slim to fashion take. Yasmeen kuwa nada seventeen (17)
years last year ta gama makaranta tana jiran admission a ATBU into physics
education. Omar kuwa is twenty and half (20½) years old an zama saurayi se rawan
kai yana ATBU shima studying computer engineering. Mariam kam ma preparation na
bikinta ake she is twenty-two (22) years old, last year tayi graduating daga ATBU
in microbiology, bikin ta bayan babban sallah in Allah ya yarda. Ibraheem yaya
babba kuwa is now twenty-four (24) years old, two (2) years back yayi graduating
from ATBU in Petrochemical engineering (course d’in manya!) Saurayi son kowa k’in
wanda ya rasa yayi service nasa yanzu haka ya fara aiki a NNPC, kud’i yake samu
sosai har ya sai motarsa k’irar Honda Anaconda new model.

*ZEEZEE...*

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 13

_I’ve recieved your message *Khadija Shehu Musa* and I want to thank you in
person for the love and support, ILY too💕 this page is dedicated to YOU #OneLove_

_*A/N*_
_Assalamu Alaikum everyone, I usually don’t say a thing on matters like this but
I think its high time I do now, ku sani your negative comments will never stop me
from continuing with what I’ve started. Na farko dana fara rubutun nan ba wacce na
cukume mata kwalar riga ko bakin zani nace dole seta karanta min littafi in kinga
bazaki iya karantawa ba fine quit it there are thousand of books out there sekije
ki karantasu amman kam BAZAN TAB’A TSARIN RUBUTA NA BA saboda tun farko dana fara
bada idea'n wata na fara ba dan haka dan ke ko ita bazan canza tsarin labarina ba
wacce taga bata k'aruwa dashi walillahil hamd seta bar karantawa. Duk me hankalin
da ya zauna yasan akwai babban darasi cikin wannan littafin saboda dole ILLAN GATA
ze biyo baya, ku baku tsaya kunga k'arshen littafi naba kuna judging d’ina, phew!
😅. Masu cewa wai zagin Mama da Zeezee takeyi is too much inku baku tab'a ji ko
gani ba toni nagani da idanu na inda 'ya ke zagin uwa infact abinda ke faruwa
mostly kenan a rayumar ta yau and dole agyara kokuwa muna tare da babban hatsari.
Ni ba anyhow nake rubutu ba duk books d'ina akwai life lessons ciki kamar yadda
wannan ma darusan suna nan fitowa one-by-one wanda already wasu masu tunanin har
sun fara gano hakan. I just want to tell y'all masu cewa littafi na baida direction
su sani cewa reading is not by force kamar yanda ban saki karantawa ba seki bari
dan kanki tunda yana b'ata miki rai ba dole a duniya. Fans dina masu sona kuma
thanks y'all for the support, I LOVE YOU ALL, INA TARE DA KU!_
***********
Tsaye take a tsakiyan d’akinta tana sanye da blue vest meh crossed arms seda ¾
black leggings, kanta kitson shade biyu ne wanda ta kama k’arshen da ribbon jaa da
alama neman abu take bata gani ba danko gabad’aya d’akin nata upside down yake,
d’aki ne me kyan gaske komi cikinsa combination na dark and light pink ne ba’a cewa
komai sede masha Allah, dogon tsuka taja sannan ta d’au laptop nata ta fice daga
d’akin a fusace tana k’walla wa Baaba meh aikinsu kira “Baaba! Baaba! Baaba!”
“Na’am” dattijuwar ta amsa tare da katse sharan da take.
“Ina kika kaimin USB na?”
“Meh kuma USB Zeezee ban tab’a kominki ba, d’akin naki kawai na share.”
“Bawanin nan kullum sede baki shiga min d’aki ba se na rasa abuna ni wallahi bana
so kije ki d’au min USB na kawai” ana cikin haka Mama ta shigo parlour’n “ya haka
Zeezee mawa kike d’agawa murya haka?”
“Ma Baaba haka kawai kullum tayita canza min position na abubuwa na ni banaso
abanza ta b’atar min da USB yanzu.”
“Bakida hankali ne? Baaban kike cewa haka? Batayi jika dake bane?”
“Wannan kuma ku ya dama nide kar a sake tab’a min abu na, ina wayana in kira Baba
ya sai min sabo” ta k’are maganan dai-dai ta shiga d’akinta ta musu banging k’ofar.
Binta Mama tayi da kallo sannan ta kad’a kai “yi hak’uri Baaba kinsan halin Zeezee
addu’a kawai zamuyi mata.”
“Ba komai Maman Zeezee ai yarinya ce.”
“Kuma daga yau karki sake share mata d’akin, tunda da kin share se tace abinta ya
b’ata.”
“Maman Zeezee beyi zafi haka ba.”
“A’a Baaba karki sake ni na fad’a miki.”

_Back in Zeezee’s room..._


“Hello Baba?” Tayi maganan a shagwabance.
“K’anwata ya haka? Meya sameki?”
“Baaba ce” tayi stating almost like crying.
“Me tayi miki kuma?”
“Ta b’atar min da USB na.”
“Shine abin damuwan? Bari yanzu zan aika Omar ya siyo miki kinji?”
“Toh yaje yanzu.”
“Angama K’anwata shikenan?”
“Eh shikenan nagode” tayi hanging. Data connection ta bud’e ta hau whatsapp,
group nasu na LYS STARS ta shiga tana glimpsing chats d’in data gama taje kan
contact na Lubiee tayi mata sending;
_‘Yan mata kinsan yau kika ce zakizo koh? I will be waiting for you_.
Kafin ta sauk’a Lubiee ta hau tayi replying nata back;
_Ina tuni Babe, Ya Salman nake jira by 3 in shaa Allah zan iso akwai gist fah,
Ahmed yace yana son Lailan Jss 1B se nazo deh!_ Zeezee na gama karantawa tayi
replying nata;
_Sekin iso I can’t wait_ nan ta kashe datan ta had’a wayarta chargy ta baro
d’akin.

~* ~* ~*
“Ya haka kana tsaki kai kad’ai?” Ibraheem dake sake da headphone akansa amman ba
komi yakeji ba ya jefa wa d’an uwansa Omar tambaya.
“Mschw! Wannan Baba da Zeezee mana wai inbar duk abinda nake inje in siyo mata
USB tayi misplacing nata.”
“Shine abin tsakin? Sekace sabon abu, yaci ace ka saba ai yanzu”
“Ai dole kace haka saboda kaga kai babba ne yanzu ana isolating naka a matters
haka wallahi yarinyan nan b’ab’b’ala ta zan mschww!”

“Wai ina Ya Omar ne beje ya siyo min USB’n bane? Inafa so inyi amfani dashi”
Zeezee tayi maganan tana shiga d’akinsu Omar.
“Ke ban hanaki yawo cikin gidan nan da vest da ¾ leggings ba? Ce miki akayi
gidan arna ne? Maza wuce kije kisa kaya” Ibraheem yayi scolding nata.
“Haaa’a! Jimin mutum, nikam ka barni sekace wani Babana ka tsaya kana wani gaya
min abinda zanyi bale ma ni ban maka magana ba kowa yayi harkan gabansa, Ya Omar
USB na” ta miqa hannu nufin ya sa mata.
“Ni kike gayawa magana?” Ibraheem yayi maganar a fusace tare da mik’ewa, ganin
haka tasa gudu amman ina taku d’aya yayi ya cafko hannunta “wayyo Allah Baba na
kayi hak’uri, wallahi bada kai nake ba dan Allah karka tab’ani na tuba.” rank’washi
me d’ankaren zafi ya danna mata akai “waye sa’anki anan?” Tana kuka tace, “wallahi
babu duk kun girmen kayi hak’uri dan Allah.”
“Shegiya me kan kwa-kwa kawai ki sake min rashin kunya kiga abinda zan miki” ya
turata seda ta fad’i, harara ta watsa masa ganin bai ganinta “mugu kawai” ta fad’i
chan k’asa k’asa yadda ita kad’ai taji me ta fad’an, miqewa tayi a wahalance ta
takai bakin k’ofa tace, “mugu kawai da wani farin fuska kaman k’osai Allah ze sak’a
min kai kuma Omar kaje ka siyomin USB na” tana kaiwa nan tasa gudu binta Ibraheem
yayi a guje se bayan Mama taje ta lab’e, “meh haka? Sakeni nikam! Kije kiyi rashin
kunya kizo kina b’uya min a baya, sakeni!”
“Wallahi Mama yarinyan nan ta kiyaye ni.” Ibraheem yayi maganan yana nunata da
yatsa.
“Ai kazo ka d’auke ta ka mata duk abinda kaga ya dace shegen rashin kunya ne da
ita.” Jin haka Zeezee ta sake dandame jikinta a na Mama tana ihu dan kanta Mama
tabawa Ibraheem hak’uri ya fice, “wallahi Zeezee ki sake kibar halin nan naki kin
mai da manyan yayyun ki tamkar kece babba bakijin tsoron idonsu?”
“Nikam da Allah! kullum sede kita scolding d’ina su baki ganin laifinsu ai nasani
Baba kad’ai ke sona a gidan nan kuma zaki gani” tana kaiwa nan ta shige d’akinta.

Bayan sallan Azahar Baba ya dawo gida har alokacin Omar beje ya siyo wa Zeezee
USB’n ba, d’akinsa ya wuce direct alokacin Zeezee ke fitowa daga d’akinta sukayi
clashing sekace ‘yar yarinya taje ta rungemeshi ya d’agata sama “Omar ya siyo miki
kuwa?” Kai ta kad’a “yak’i shikuma Ya Ibraheem ya nank’washeni a kaina.”
“Haka ya faru? Bari ina zuwa, kinci abinci?”
“A’a”
“Jeki d’iba kici ina zuwa” yana sauk’eta ta wuce kitchen su Mariam da Yasmeen ta
tarar se aiki suke da Mama tana tayasu.
“Ina abinci na?” tayi tambayan ma dukansu, ba sannu da aiki ba komai.
“Kinba ma waye ajiya kike wannan tambayar?” Yasmeen ta watsa mata harara. Hararan
ta miyar mata itama, “ma ke na baiwa, ni ina abinci na? Tun d’azu ku d’aura lunch
kunk’i sekun bari yunwa ya gara mutum.”
“Wai waye sa’anki anan? Zan gaggaura miki mari fah!” Mariam ta bud’e mata ido.
“Mschww!” Zeezee taja tsaki, ganin Mariam ta miqe Mama tayi saurin dakatar da ita
“yi hak’uri Mariam barta tana yima kanta ne” nan da nan suka sauk’e girkin Zeezee
ta matso da plate nata “asamin.”
“Baza’a san ba kinyi sallah neh?” Mama ta tambayeta, shiruu Zeezee batace komi ba
dan kuwa batayi sallan ba, “tambaya nake kinyi sallan Azahar?”
“Ni meh had’in abinci da Sallah kisa min kona fad’awa Baba.”
“Jeki gayan maras kunya kawai” dai-dai nan Baba yashigo kitchen d’in “yauwa Baba
kaga Mama tasamin abinci wai o’o.”
“O’o kamar ya? Sa mata abinci mana Hafsah.”
“Kasan kuwa yarinyan nan batayi sallah ba infact bata ma sallah kullum ko an sata
se baza tayi ba.”
“Bata sallah?” Baba yayi maganan unbelievably.
“Wallahi k’arya ne” cewar Zeezee.
“Toh kinayi neh?”
“Wallahi batayi Mama” cewar Yasmeen.
“Rufa min baki abinda kika iya kenan” Baba ya tsawata wa Yasmeen. “Zeezee wai
baki sallah?”
“Baba inayi wallahi kawai yanzu ne ban yiba saboda ina jin yunwa amman ina gama
ci zanyi.”
“Yauwa K’anwata I trust you ai” k’wace serving spoon na hannun Mama yayi ya zuba
wa Zeezee potatoe porridge d’in da nama biyar akai.
“Haba Alhj ya da haka? Mukuma sauran me zamu samu?”
“Ke ko kunya bakiji ba me zakiyi da nama tsohuwa dake?”
“Nide ba tsohuwa bace kuma naga wanda suka fini shekaru ma sunaci, kuma Mariam ku
d’ibi biyar-biyar d’in, yarinya ko aikin d’aga tsinke batayi sede taci tayi kashi
tayi rashin kunya kuma aka tashi ita za’a na bata duka naman miya.”
“Kanki akeji” plate ya ja ya d’iba nasa suka fice da K’anwarsa.

*** _2:45PM_
Baba ya tara iyalan sa a parlour dan raba musu kayan babban sallan su wanda will
take place in 3 weeks time. “Ina Omar?”
“Yaje siyo wa Zeezee USB.” Ibraheem ya amsa.
“Okay” yayi maganan yana zaro had’ad’d’un zannuwan dake cikin wani babban leda,
guda goman duka ya baza a kan carpet “ina K’anwata?”
“Na’am Baba” ta matso kusa dashi ta zauna.
“Zab’i guda hud’un da suka miki anan-”
“Haba! Haba! Alhj kayi adalci mana, Mariam Babban su ai ita ya kamata ta fara
zab’a” Mama ta fad’a.
“Zani ba zani bane kam? D’auka Zeezee da Allah kar kiji ta.” Gwalo Zeezee tayi ma
Mama sannan ta kwasa hud’u mafi had’uwa cikin goman. “Oya kema Hafsah d’au naki
guda biyu.”
“Biyu? Ita hud’u ni biyu kuma seda ta d’auka zan d’au wallahi banaso kabata
nawan, na hak’ura.”
“Kanki akeji” ya d’au guda biyu ya wulla mata sauran hud’un kuma ya bawa Mariam
ta zab’a biyu ta bawa Yasmeen biyu ana cikin haka Omar ya dawo nan Baba ya basu
shaddojinsu shida Ibraheem guda uku-uku had’d’d’u masu kyau, bayan nan ya sake jawo
wani leda ya zazzage laces biyar ciki nanma yace Zeezee ta zab’a biyu bayan ta
zab’a ya raba wa Mama da su Yasmeen ragowar haka kaman suyi kuka sukayi godiya suka
watse. D’aki Zeezee ta nufa da kayakin sallanta se tsalle take nata guda six (6) na
sauran 3-3 ganin ta wargaza wardrobe natan d’azu agarin neman USB kuma gashi tana
son sa sabin kayanta ciki yanzu gashi she is not in the mood of preparing her
wardrobe taje tasamu Baba tayi ta mai shagwab’a ita akira Yasmeen ta gyara mata
wardrobe nata, bayan taje ta kira Yasmeen Baba ya isar mata da abinda yakeson tayi
ai atapir tace ita baza tayi ba ai da gan-gan Zeezeen ta wargaza kayakin, ido sosai
Baba ya bud’e mata sannan ta amince se kumbure-kumbere take.
Nan da nan ta shiga gyara wa Zeezee wardrobe nata ana cikin haka Lubiee tazo,
parlour’n Baba Zeezee ta kaita suka yita hira kaman ba gobe suna game, bayan
Yasmeen tagama gyara mata wardrobe d’in suka koma d’akinta taciro wa Lubiee kayakin
sallanta seh 5:30PM Lubiee tace zata tafi bayan sallamarta da Baba yayi yasa
Ibraheem yayi dropping nata nan Zeezee tace se ta bisu itama. A bayan mota suka
zauna su biyu se k’us-k’us suke har suka yi dropping nata.

“Toh bazaki dawo gaba bane sena mauje ki?”


“Ayyi Ya-”
“K’aniyanki nan waye driver’nki? dawo gaba nace!” Harara me rai da lafiya ta
watsa mai batasan ko ya ganta ta mirror ba, bayan ta dawo gidan gaba ya seta kanta
ya sake mata rank’washi me zafi, “Allah ya is-”
“Meh kikace?”
“Babu” hannunta yakama da niyar murd’awa aiko tasaki ihu “dan Allah Ya kayi
hak’uri wallahi bazan k’ara ba.”
“‘Yar banza kawai ai ko kiyi behaving kanki ko na b’ab’b’ala ki kamin mu isa
gida wallahi” daga nan Zeezee bata sake ce mai komi ba dan lafiyarta tayi shiru on
their way back home budurwan Ibraheem Fateema ta mai waya kan tana buk’atan ganinsa
nan ya sha U-turn Zeezee na ganin haka tace, “ni wallahi ka kaini gida kafin nan
kaje gun Fateeman.”
“Magana kike?” Ya mata sending wani dirty look dan kanta tayi tsit ahaka suka isa
Ibraheem yasata tabar motan Fateema ta shiga. Se hira sukeyi tun Zeezee na hak’ura
taga bazata iya ba ta mik’e taje ta samesu “ni wallahi kashi nakeji hiran ya isa
haka.” Kallonta Ibraheem ya tsaya yi totally out of words.
“Zeezee toh muje in kaiki ciki kiyi?” cwar Fateema.
“Ni bana sharing toilet, na gidanmu nakeso” baki wangalau Fateema ta bud’e tana
kallon Zeezee dake murgud’a mata baki sama-sama “toh Baby se next time baby sis is
in need kuyi ku tafi.” Har a yanzu Ibraheem ya kasa cewa komai haka yana gani har
Fateema ta shige gidansu Zeezee ta bud’e motan ta shiga “toh kayi sauri mana Ya,
yafa matseni” bece da ita komi ba ya kunna motar suna cikin tafiya sunzo ta old GRA
ya yi parking gefen hanya “meh kuma zamuyi anan Ya?” Nanma bece komi ba ficewa yayi
kawai ganinsa tayi ya karyo itche d’anye yana nufan motan kafin tace zata bud’e
k’ofar ta har ya isketa, fincikota yayi ya hau zabga mata itchen a k’afafunta daman
‘yar guntuwar ‘yar kanti ne a jikin ta tana ihu tana basa hak’uri amman ina se
k’ara mata yake kasancewar hanyan shiru ba hayaniya, seda ya nad’a mata na jaki
sannan ya barta lokacin har wani sama-sama nishinta ke. “Kad’an kika gani bake
fitsara da rashin kunya ba? Muna tare dake ai gyara miki zama zanyi maza miqe ki
bud’e motan ki shiga.”toh kayi sauri mana Ya, yafa matseni” bece da ita komi ba ya
kunna motar suna cikin tafiya sunzo ta old GRA ya yi parking gefen hanya “meh kuma
zamuyi anan Ya?” Nanma bece komi ba ficewa yayi kawai ganinsa tayi ya karyo itche
d’anye yana nufan motan kafin tace zata bud’e k’ofar ta har ya isketa, fincikota
yayi ya hau zabga mata itchen a k’afafunta daman ‘yar guntuwar ‘yar kanti ne a
jikin ta tana ihu tana basa hak’uri amman ina se k’ara mata yake kasancewar hanyan
shiru ba hayaniya, seda ya nad’a mata na jaki sannan ya barta lokacin har wani
sama-sama nishinta ke. “Kad’an kika gani bake fitsara da rashin kunya ba? Muna tare
dake ai gyara miki zama zanyi maza miqe ki bud’e motan ki shiga.”

Har a yanzu kuka take wane dan shi aka turota k’afafunta har sun soma kumbura
sunyi jaa dan azaba, yi tayi kamar bata jisa ba, bulalan ya d’aga as if ze sake
zaneta “dan Allah kayi hak’uri zan shiga.”
“Oya!” Yayi commanding nata, motar ta bud’e ta shiga shima haka sede har a yanzu
bata bar kukan ba. “Kuma kimin shiru wallahi in bakiyi ba sena k’ara miki wanda
yafi wannan” kukan tacigaba dayi “aww! Baza kiyi shirun ba kenan?”
“Zanyi dan Allah kayi hak’uri.”
“Oya yi shirun kuma wallahi kikaje kika fad’awa Baba na dakeki ya kirani yamin
suratan banza zakiga abinda zan miki, kinfi kowa sani na” a da tanada niyyar sanar
da Baba abinda yayi mata amman jin ya kashe mata warning ta fasa saboda tasan halin
Ibraheem sarai mugu ne first class ma kuwa. Haka tana ta sobbing har suka samu suka
isa gida aranta tana meh tunanin wani abin zata yimasa ta rama.

Tana fitowa daga motan ta buga murfin wane zata b’alla ko uffan bece mata shide
da murfin motansa ya b’alle da seta raina ma kanta wayo. Karo taci da Baaba A’ee
gbam! “meh haka mutum na tafiya bai ganin gabansa” tayi maganan ba tare da tasan da
wa ma sukaci karon ba.
“Toh Zeezee lafiya dai koh?”
“Aww Baaba kece sannu nasha ma ‘yan iskan almajiran nan ne.”
“Sannu Zeezee ba gaisuwa?”
“Nikam da Allah kullum gaisuwa baki gajiya da amsawa ne?” Bata jira jin meh A’ee
zata ce ba ta wuce ciki, baki A’ee ta tab’e tace, “Allah shiryeki Zeezee.”

**** _8:17PM_
Tailor’n su ya iso nan kowa ya fito da zannuwansa bayan ya gama a’aunasu suka
zab’i styles nasu Baba ya bada advance har tailor yazo tafiya Baba ya tsayar dashi,
“yauwa Shaheed d’inkin nace ka tabbata seka gama dana Zeezee kafin ka fara na
sauran saboda kaga ita yarinya ce, su ko ba kayan sallah zasu iya yin sallan ka
gane ai?”
“Eh Alhj zan fara da nata in nasamu nayi koda biyu ne a natan sena tab’a na ‘yan
uwan nata.”
“O’o ni seka gama min duka six d’in” Zeezee tayi chipping in.
“Bakida hankali? Mu kuma fa? Shaheed please kar ka saurareta” cewar Mariam.
“Lallai sannu toh se an gama da natan za’a tab’a naku maras kunya kawai” Baba ya
sanar da ita.
“Allah sarki Baba-” inji Yasmeen.
“Allah sarkin K’aniya, sam ku baku san meh kara wa k’anwarku ba? Se an gama nata
a fara da naku ka jini ai Shaheed? Se mun jika nan da 2 weeks d’in.”

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 14

~* ~* ~*
Da Asubaah Mama da kanta tazo tada Zeezee daga bacci don yin Sallah ‘cause
anytime ta tura sauran bata tashi. Gbam! Gbam! Gbam! “Zeezee bazaki tashi ki bud’e
k’ofar bane?” Murya cike da gyangyad’i tace, “waikam ba naji ba? Ai zan tashi.”
“Shine nace ki bud’en k’ofan.”
“Toh wai ki shigo kiyi meh Mama? Ai zan tashi.”
“In baki tashi ba ma keda Allan ki” daga nan ta wuce d’akinta. Jin shiru hakan ya
tabbatarwa Zeezee Mama ta tafi, “ai wallahi bazan tashin ba” daga fad’an haka taja
comforter ta cigaba da baccinta se 7:00AM ta tashi tayi sallan ta sake komawa
bacci, kasancewar yau Sunday ba school. Se 10:30AM ta tashi tayi wanka tasa wani A-
shaped gown nata ta fito, a parlour ta tarar da Baba ta gaishesa sannan ta wuce
kitchen dan neman abin karin kumallo chan taci karo da duka sauran ‘yan gidan nasu
Mama kad’ai ta gaisar, dama on normal basis tana gaishe da Ibraheem ma amman data
tuna da dukan daya mata jiya se ta fasa.
“Ina breakfast d’ina?” Banza da ita duka sukayi Mama ce ta mik’a mata flask natan
tace, “in bazaki gaisar da sauran ba Ya Ibraheem fah?” Baki ta turo sannan ta watsa
mai harara dan ko kallonta baiyi “ina kwana?” Tace chan k’asa-k’asa almost like
whispering, ganin yak’i amsawa yayi banza da ita tace, “tafi nono fari karka amsan”
dai-dai zata karb’i flask nata Mama ta rik’e “amman fa yau akwai aiki kinga Baaba
bata ji dad’in jikinta ba so bata samu daman zuwa ba yau adalilin haka na rabawa
kowa aikin da zeyi, naki aikin share site nasu Ya Ibraheem da musu mopping neh”
seda tabari flask na abincin nata ya shiga hannunta tace, “chabd’i! Ni ce zan share
musu d’aki meh sauran kuma zasuyi? D’akina kawai zan share kowa ya share nasa.”
“Haka kika ce?” Mama ta tambayeta.

“Eh mana ni ba abinda zan share musu, Allah yayi wa kowa hannu” ta kama hanyan
fita daga fad’an haka.
“Tsaya ke! Kika gama breakfast d’in kizo zan aike ki shago” Ibraheem yayi maganar
in a serious tone. Shiru tayi kamar bata jisa ba, “ko baki jini bane?”
“Naji” ta watsa mai harara ganin bai kallonta nan ta juya ta hau gun-guni
“shikenan shi baida aiki se aikan mutum shago wallahi bazan jeba.”

_Back in the kitchen..._


“Wai Mama kinajin yarinyan nan bazaki buge bakinta ba?” Cewar Yasmeen.
“Barta tanayi wa kanta ne ai ba inda rashin kunya ze kai mutum se halaka Omar
Baba na kayi hak’uri ka share muku kaji? Yi hak’uri.”
“Mama wallahi haushi kike ban in kince tana yi wa kantan nan duka ne be isheta
ba.”
“Barta de ba muna nan tare da ita a gidan nan ba? Zan gyara mata zama” Ibraheem
yayi maganan tare da miqewa haka ranan kowa na aiki banda Zeezee dake kallon disney
channel, ita gabad’aya ma tama manta Ibraheem yace ze aike ta shiko yana sane time
ya bata inhar takai 12noon bata zo ba ita da shi ne!

11:56AM aiken da Ibraheem ze mata yayi ringing a kanta firgit ta mik’e duk kalan
rashin kunyan Zeezee tana d’an shakkan Ibraheem sanin halinsa.
“Gani” tace alokacin da ta shiga d’akin nasu bata damu da miyar wa Omar shara
bayan da tayi ba, gindin tsintsiyan ya seta k’afafunta ya rabga mata “bakiga shara
nake bane da zaki shigo kina miyar min da aiki baya?”
“Wayyo Allah! Allah ya isa na ni nasan kana sharan ne” kunnenta ya kama “meh
kika ce?”
“Babu dan Allah kayi hak’uri” murd’a kunnen nata ya shiga yi tana ihu Ibraheem
dake zaune yana kallonsu ko k’ala bece ba “ni kike jawa Allah ya isa?” Tana hawaye
tace, “a’a na tuba dan Allah kayi hak’uri.” Se anan ya saketa ta shiga share
hawayenta N2000 Ibraheem ya mik’a mata “siya min Glo na 2k.”
“Ya nima ka bani N500.”
“Da uban rashin kunyan kin zan baki N500? In kinason kici arziki na ki dena yimin
rashin kunya now b’ace min daga gani” bata ce dashi komi ba ta zarce d’akin Baba
takai k’ara nan ya turata ta kira Ibraheem d’in.
“Uhm Ibraheem Baba na kanada N1,000 kabani?” Baba yayi maganar cike da dabara.
“Eh Baba” nan ya zaro wallet nasa ya mik’a mai “shikenan?”
“Eh shikenan nagode koh?”
“Ba komai Baba kekuma kije ki siyomin ina jiranki.”
“Wai toh ba na jiba haa’a!” Bayan ficewan Ibraheem Baba ya mik’a mata dubu
d’ayan, “saura kuma kije kice dubun daya banin na baki ba ruwa na.”
“Barin fad’a ba Baba nagode” nan da nan taje ta sai masa katin itama ta sai
nata.****

Da Azahar friends na Ibraheem suka zo bayan sun dawo daga sallan Azahar ya tura
Yasmeen ta kira Zeezee, seda ta gama b’ata mai lokaci tazo tana tura baki, “meh?”
Kallo ya galla mata da kanta ta gyara zancen nata, “na’am Ya ka kirani.”
“Se kuma dana kiraki baki iya gaisuwa bako?” Kallo tabi friends nasan dashi Allah
yaso ba mumuna cikinku da kunga buro-uba tayi maganan a zuci.
“Ina wuninku” tayi murmuring, k’asa-k’asa suka amsa.
“Kije ki kawo musu drinks sannan Yasmeen tayi guiding naki ki dafa mana indomie
tunda ba ayi abinci ba tukuna.”
“Ni? In dafa muku indomie? Gaskia a’a Ya, ni ban ma iya dafawa ba kuma koda na
iya ma sekace wata boyi-boyi.”
“Magana kike? nace kice Yasmeen tayi guiding naki.”
“Ni wallahi Ya...” ta hau bubbuga k’afa tana tura baki “ni bazan dafa ba ina
kallon shake it up kawai kuyi hak’uri zan kawo muku snacks d’ina na school kusha da
drinks d’in.” Dariya sosai ta sa friends nasan d’aya daga cikinsu yace, “Mazaa
kabar baby sis nakan nan kawai dama ba yunwa muke ji ba, kawo mana ruwan kawai
kinji?”
“Yauwa Ya Suleiman” shide Ibraheem bece komi ba tunanin kalan dukan da ze mata
kawai yake, haka taje ta d’ibo musu drinks da snacks nata ta jera musu kan tray
dai-dai tazo ajiwa kenan Ibraheem ya cafke hannunta tare da sa mata nank’washi meh
uban zafi aka, k’ara ta saki tare da jan Alah ya isa nan ya k’ara mata “meh
kikace?” Tana kuka tace,
“Nace kayi hak’uri wallahi sabon kitso ne a kaina.”

“Mazaa let her be please” cewar d’aya daga cikin friends nasan.
“No kubar ni da ita me kika gama cewa d’azu?”
“Babu, Ya dan Allah kayi hak’uri wallahi bazan k’ara ba wayyo kaina.” Kunnenta
ya kama ya murgud’a da k’arfi.
“Argghh!” Ta saki k’ara “wayyo Baba na dan Allah kayi hak’hri.”
“In sake saki aiki kice min baza kiyi ba kiga abinda zan miki marasa kunya kawai”
ya saketa “get out!” Da sauri ta mik’e tana jan Allah ya isa har ta fice.

*****
Da daddare bayan su Baba sun dawo daga sallan Isha ya kirawo Zeezee d’akinsa,
“K’anwata bana kema zanyi maki yanka kinji?”
“Dagaske Baba?” Ta fad’a sounding thrilled.
“Sosai ma K’anwata” rungumosa tayi tana meh jin dad’i ana cikin haka Mama ta
fad’o d’akin “ya haka meke faruwa?”
“Baba yace zemin yanka wannan Sallan.”
“Yanka? Alhj yanka zakayi mata?”
“Eh in shaa Allah tunda Allah ya hore min.”
“Sauran kuma fah? Ai kamata yayi ka musu duka ka had’asu kan dabba d’aya.”

“Nifa kinga irin halinki da banso kenan, taya za’a had’asu duka? Allah kaimu next
year suma se ayi musu amman bana kam K’anwata kad’ai za’ayi wa yanka.”
“Hmmm Allah ya shirya ka toh partiality a filin Allah haka, kullum ina ma wa’azi
amman bakka ji.”
“Kanki akeji jeki huta K’anwata gobe kuna da school.”
“Toh Baba seda safe.” The next day Zeezee ta cika wa kowa kunne a gidan da waqan
za’ayi mata yanka za’ayi mata yanka. Yayyun nata tun abin na damunsu ma har sun
saba yanzu, hak’uri sukayi suka cire damuwan daga ransu in ba haka ba har ciwon
zuciya yana iya kamasu.***

~* ~* RANAR SALLAH ~* ~*

Bayan sun dawo daga Idi Baba ya biya ya siyo raguna manya-manya guda uku, ba tare
da b’ata lokaci ba yayi layyansa rago d’aya nasa, d’aya na Mama d’aya na Zeezee.
Nan da nan suka shiga aikin nama banda Zeezee dake mak’ale a d’aki tana kallo a
laptop nata.
“Shikenan Mama ita Zeezee ba aikin da zatayi tana zaune a d’aki sekace wata
sarauniya.” Yasmeen tayi maganar.
“Toh ya muka iya Yasmeen? Dama ace Babanku bai gida ne toh amman yanzu da ance
Zeezee ta d’aga koda tsinke ne se ya hau kan mutum da bala’i ki barta kawai.”
“Ai wallahi idan ku kun hak’ura ni bazan barta ba Zeezee! Zeezee! fito nan dan
k’aniyanki” cewar Mariam. Jin shiru ta nufa d’akin tan da kanta, miqe kan gado ta
sameta, “fito muje muyi aiki.”
“Wai aikin meh?”
“Aikin uwaki ‘yar banza kawai fito! Kin maida mutane boyi-boyin ki fito nace!”
“Ni ban iya ba wallahi kika tak’ura min zan had’aki da Baba.” Seda Mariam tayi
dagaske ta samu ta fito da Zeezee daga d’akin. Kujera ta nema ta bata ta zauna suka
hau gyaran kayan ciki banda toshe hanci ba abinda Zeezee ke chan kashi ya tab’a
mata jiki zumbur ta mik’e “ni wallahi na fasa yin aikin k’azantar nan ku bani wani
aikin daban.”
“Akwai wanke-wanke sekije ki kama.” Yasmeen tayi informing nata.
“Ni bazan yi wanke-wanke ba sede wani aikin.”
“Maza wuce kije ki kama wanke-wanken kona gaggaura miki mari maras kunya
kawai,karki ga dan ina barin ki wallahi kika b’ata min zan illata ki wuce nace!”
Mama ta bud’e mata “ba zaki wucen bane?”
“Ba naji ba wai kam” baki ta murgud’a sannan ta k’arasa wajen da aka tara wanke-
wanken ta hau yi for the first time, se kwab’awa take tanayi kuda suna mata yawo
ajiki abinda tafi tsana kenan! “Ha’aah nikam kudena tab’ani mana” tayi maganan da
kudajen wai. Dariya Yasmeen ta hau mata “daidanki kenan su cinyeki ma mu huta”
ganin kudan basu bar bi mata jiki ba ta je ciki ta d’au insecticide ta feffeshe
wajen wanke-wanken se anan tasamu tagama jagwal-gwala wanke-wanken tayi ciki bata
sake fitowa ba seda taji an soma gashi “ni ina rago na? Duk wanda ya cimin nama ban
yafe ba wallahi.”
“Gashi chan achan ba wanda ya tab’a miki namanki keda kanki zaki soya” Mariam ta
fad’a tana hararta.
“Ke wannan Adda Mariam kin kusan tafiya ma amman bazaki d’an canza hali aji
dad’inki kafin ki tafi gidan miji ba, kuma kar kowa ya tab’a min ragona.”
“Saidai in baza ayi sadaqa ba, in ba haka ba cinyan gaba da na baya duk sena yi
sadaqa dasu” cewar Mama.
“Wallahi kikayi sena gaya wa Baba ai dabba na ne, kiyi da naki mana.”
“Please Mama karki sake ce mata komi in aka zo yin sadaqan seta hana muga, banza
kawai” cewar Omar yana cigaba da latsa wayarsa. Harara da murgud’a baki ta mai
sannan ta koma d’akinta.

2 weeks after Sallah akayi bikin Mariam, biki yayi kyau masha Allah sede ace
Allah shi bada zaman lafiya. Chan Kano aka kaita.

★★★★★
_10 months later..._
Alokacin Zeezee na Jss2 tana neman shiga na 3 saboda sun ma gama exams na 3rd
term nasu sakamako yayi kyau sosai. Zeezee fa ba sauk’i an zama ‘yan mata yanzu se
palli da rawan kai, hali zanen dutse har yau bata fasa rashin kunyarta ba, infact
sede abinda ya k’aru ma. A month back Mariam da mijinta suka dawo Bauchi da zama
kasancewar an mai transfer a gun aiki, sosai Mariam tayi nauyi haihuwa nan da watan
gobe in Allah ya yarda, tunda Zeezee ta gano haka ta d’aga k’afa daga gidan Mariam
saboda sata aikin da take.
Yau Monday Mariam ta kira Mama kan atura mata Zeezee tad’an tayata aiki zatayi
bak’i, Zeezee najin haka tayi faking rashin lafiya ita sam bazata jeba seda Mama
tayi dagaske sannan ta shirya akwatinta kaya biyu kacal tasa ciki dan batason ta
jima, Ibraheem ne yayi dropping nata chan Fadaman mada inda gidan Mariam yake.
Bayan isan Zeezee ta wuce guest room ta dire jakanta sannan ta fito ta tarar da
Mariam zaune a parlour tana shan farin k’asa.
“Ina wuni? Ya k’arfin jikin?” ta gaishe ta sama sama.
“Alhamdulillah rice and stew zamuyi min Zeezee.”
“Rice and meneh? Kinfa san inba farin shinkafa ba, ba abinda na iya in zaki saki
jiki ki tashi kije kiyi stew naki toh in kuma ba haka ba se bak’in naki suci garau-
garau (shinkafa da mai da had’i) wai ace Uncle Mahmoud (mijin Mariam) kullum baida
aiki se kawo mutane gidansa chin abinci wallahi mijina be isa yamin wannan d’anyen
aikin ba.”

“Toh uwar fitsara seki bari idan Uncle Mahmoud d’in yazo ki fad’a masa.”
“Ni meya kaini? Ke matarsa bakiyi complaining ba seni, ni dama kun cigaba da
zaman ku a Kano wallahi.”
“Jeki kwashe tomatoes da sauran kayan miyan dake fridge d’in ki gyara ina zuwa in
d’iba miki albasa.”
“Wai Adda Mariam ni zanyi komi ke kawai zaki zauna nan kina ture-ture?”
“Inda da lafiya na ajinki ma zan ce kizo ki tayani ne?”
“Nikam gaskia bazan yanka albasa ba kema kinsan inada ciwon ido.”
“Se akace masu ciwon ido basu yankan albasa?” Haka suka ta drama har aka had’a
kan stew d’in Zeezee ta dafa shinkafa.

*** ★ ***
Kwana biyu Zeezee tayi ma Mariam taji duk rayuwan bayi mata dad’i, ita ke mata
wanke-wanke wai harda shara ma. “Ni wallahi yau zan tafi ban iyawa sekace ni nace
kiyi cikin.”
“Meh kika ce?” Mariam tayi snarling at her.
“Ni nayi magana neh?” Ta murgud’a mata baki. “Wallahi yau zan tafi, don ni ba
jaka bace.”
“Kanki akeji nide ki gama min shara da wanke-wanken kiyi duk abinda kika so yi.”
Haka bayan tagama aikin da cuwa-cuwa kamar yadda ta saba ta shirya tsaf ta d’au
wanka cikin purple lace, trolley’nta ta ja zuwa parlour inda Mariamke miqe a k’asa
“zaki tafin ne?”
“Eh” tayi maganan tana plugging earpiece nata.
“Toh ki gaida su Mama” daga nan ta rufe idonta danyin bacci. Few minutes later ta
bud’e idanun nata taga Zeezee tsaye inda take bata ko motsa ba. “Ya haka? Kin fasa
tafiyan ne?”
“Shamawai! Da zanzo inta miki bauta da mijinki ne bazaki sallamen ba! Lallai
kuwa!”
“Aww jira kike in sallameki?” Mariam tayi maganan a bit suprised tana dariya da
k’yar.
“Eh mana bake kad’ai ba har da Uncle Mahmoud ma.”
Cike da mamaki Mariam ta tafe hannu sannan tace, “Ahh lallai Zeezee, kin rik’a
toh nikam Allah yaga banida kud’in da zan baki seki tafi, Allah kaimu wani
lokacin.”
“Wallahi k’arya ne ni ki sallameni.” Zeezee tayi maganan stubbornly.
“In d’ari biyun mota ne bazan rasa ba.”
“Chab! Wallahi Adda Mariam ba wasa nake ba ki sallamen.”
“Kisani na dole, ke wato baki aiki tsakani da Allah bama wannan ba jinki ban sane
da sharan cuwa-cuwan da kike min neh? Duk dottin k’ark’ashin gado da kujera kike
tura su koba haka ba?”
“Wancan kuma damuwanki ai in kikayi bak’i ba leqa k’ark’ashin gadon ko kujeran
suke ba, nide ki sallameni in tafi.”
“Lallai kuwa you are not ready to leave inhar ni kike jira na sallameki, zama nan
ya kamaki” Mariam na kaiwa nan ta juya mata baya da k’yar. Tsaye Zeezee tayi wajen
if only tasan ina Mariam ke b’oye kud’inta, tana cikin wannan tunani ta jiyo k’aran
motan Uncle Mahmoud robe dake cikin handbag nata tayi sauri ta ciro ta shafa
k’ark’ashin idonta take ta soma hawaye dai-dai nan Uncle Mahmoud ke shigowa anan
Zeezee ta soma magana cikin kuka, “wallahi baki isa ba sekin biyani 5k na, ai ba
haka mukayi da ke ba wallahi kibani kud’i na” ta rushe da kuka. Mariam batasan
alokacin da ta mik’e zaune ba tana kallon wonders kafin tayi magana Uncle Mahmoud
yayi sallama, “wa’alaikumus-salam” ita da Zeezee suka amsa in unison “sannu da zuwa
Uncle” tace tana share hawayenta kaman dagaske.
“Yauwa sannu Zeezee ta, Hajiya Mariamu sannu da jiki.” Da ya lura da Zeezee seya
kamar kuka take, “ya da kuka kuma? Wani abu ne?” A rayuwa Uncle Mahmoud nason
Zeezee badan komi ba sede dan k’iriniyarta musamman inya tuna days back da inyaje
zance gun Mariam itama tafito tace se anyi zancen da ita.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄

www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 15
*December, 2016*

“Babu komai Uncle ni na tafi” taja jakarta kaman dagaske.


“Kaman ya ba komai? Gashi ina gani kina kuka kice babu, Hajiya Mariamu na me
kikayi wa K’anwar tamu take kuka?”
“Wallahi Dear ban mata komi ba ni kaina bansan meke damunta ba.”
“Ai dama haka zakice kin kama kin cinye min 5k kikace nazo tafiya zaki bani, baki
ban ba dole kice ai baki san meke damu na ba ni zan tafi.”
“Ni?!” Mariam ta dafe k’irji “yaushe na tab’a cin bashi gunki Zeezee?”
“Wait... Wait Zeezee na, Adda Mariam ce ta ranta kud’i gunki bata biya kiba?”
“Eh Uncle” ta fad’a tana gyad’a kai.
“Wallahi Dear karka jita sharri take neman min.”
“Tsaya mana Habibti muji daga bakin K’anwar tamu.”
“Wallahi karka jita sharri take neman min.”
“Wallahi ba k’arya bane Uncle Mahmoud if only Yasmeen was here data gaskata
hakan, a idonta Adda Mariam ta ranta kud’in.”
“Chab! Lallai Zeezee bakijin tsoron Allah.”
“Ai nasan baki k’arya Zeezee, nawa ne kud’in nakin?” Dad’i taji sosai tasa hannu
ta share hawayen ta “5K ne.”
“Dear Allah karka bata.”
“Ba ruwanki Hajiya Mariamu tsakani na da K’anwata” wallet nasa ya ciro ya irga
10k “gashi wannan duka naki ne” bayan ta amsa ta irga tsalle ta hau yi “duka nawa
Uncle?”
“Eh mana, stew na ranan yayi dad’i wannan tukuici ne.”
“Fa ba ita tayi stew d’in ba.” cewar Mariam.
“Wallahi nice ai Uncle ma yasani” pillow Mariam ta wurga mata “mak’aryaciya
kawai” gwallo Zeezee ta mata ganin Uncle Mahmoud bai ganinta “toh Uncle ni zan tafi
nagode Allah ya k’ara bud’i.”
“Ameen K’anwata bazaki jira in having lunch nayi dropping naki ba?”
“A’a Uncle karka damu zan tafi da kaina”
“Toh ki gaishe da Mama and everyone” bayan ba-bye taja jakarta ta tafi.

Isanta gida keda wuya ta wuce d’aki direct ta ajiye jakanta sannan ta fito tayi
d’akin Mama “ya har kin dawo neh?” Mama dake zaune bakin gado tayi maganar.
“Eh tace tana gaisheki haka Uncle ma kuma yabani 10k.”
“Toh masha Allah zan kira sa na masa godiya ina kud’in yake?”
“Me zakiyi dashi? Bade karb’ewa zakiyi ba!”
“Yo dama ‘yar yarinya dake sena barki da 10k?”
“Ni wallahi shiyasa banson fad’amiki ammin kyauta ni wallahi kibarmin kud’ina.”
“Haka kika ce?”
“Eh” ta amsa tana gyad’a kai “kinyi dai-dai, Allah kawo ranan da zakice na baki
kud’i kiga in ban gaggaura miki mari ba.”
“Allah bare kawo ranan bama ni zan fita gidan su Miss Rama sena dawo” bata jira
jin meh Mama zata ce ba ta fice.

*****
Cikin sati biyu Zeezee ta gama kashe 10k d’in cikin k’ananun siyayyan da basuda
amfani, ayau Monday suka koma school su Zeezee ‘yan matan Jss3. K’arfe 7:10AM ta
gama shirinta Ibraheem yayi dropping nata kasancewar Baba yayi tafiya, yana
dropping nata ya wuce office shima. Kasancewar yau ne first day at school basuyi
wani abin arziki ba se hira suka ta sha ita da Lubiee and others 2:30PM Ibraheem
yazo d’aukan Zeezee ko kad’an bata lura da motansa ba as she was busy gisting with
her friends, ransa ne ya mugun b’aci ya fito daga motar a fusace ya nufi inda suke
tsayen da hijabinta ya jata. Ashar ta hau d’urawa ba tare da tasan waya mata hakan
ba, tana juyawa tayi 4 eyes da angry Ibraheem. “Ya yaushe kazo?”
“Wa kike zaga?” Ya danna mata rank’washi a presence na friends nata “Allah ya isa
ni nasan kazo ne kuma seka kama ka jani da hijabi ka sakeni”
“Kinada bakin magana ko?” Kunnenta ya kama ta hijabin ya murd’a da k’arfi batasan
lokacinda ta soma kuka ba amman hakan besa tayi shiru ba se Allah ya isa take ja
mai a haka har yajata mota ya bud’e ya turata ciki se ihu take tana kuka a motan
ganin ya faka gefe guda tayi kum da bakinta gudun karya karyi reshe ya mata kalan
na kwanaki.
“Nayi shiru wallahi nayi dan Allah kayi hak’uri.”
“Marasa kunya kawai bari mu isa gida” yaja mota. Bayan isansu gida ta shiga bayi
a guje ta danna lock tana ji yana kiranta tak’i bud’ewa seda ta tabbata ya fita
masallaci ta fito ta nufa d’akinsu, wayarsa ta d’au ta shiga whatsapp ta tayi
sending had’ad’d’en break up message cike da zagi da cin fuska wa Fateemah
girlfriend na Ibraheem ta wuce d’akinta tasa lock tana me praising kanta.

Koda Fateemah taga message d’in dariya sosai taci dan kuwa she’ve trust in her
Ibraheem tasan sarai aikin Zeezee ne. Batasan me ta mata ba Zeezee ta tsaneta,
Ibraheem na dawowa ya shiga whatsapp yaga d’anyen aikin da Zeezee ta mai ita dan
sokanci ma bata goge chat d’in ba. Murmushin mugunta ya saki ta one side of his
face sannan ya kira Fateemah tana d’agawa ta k’yalk’yale da dariya “aikin Zeezee
koh?”
“Barni da ita Babe.”
“No Baby please karka tab’a ta kabarta.”
“Kamar ya na barta! Baki karanta message d’in bane?”
“I did but please let her be for me dan Allah.” Seda ya nisanta yace, “naji I
won’t beat her amman she’ll have to serve some punishment.”
“Eh better amman karka tab’a ta please” hira kad’an suka tab’a sukayi sallama
d’akin Zeezee ya nufa direct daman gashi Baba bai gida bale ya d’aure mata gindi
kamar yadda ya saba.
“Zeezee!” Bata san lokacin da ta saki fitsari a panties nata ba jin kakkausar
muryarsa, shiru tayi bata amsa ba.
“Zainab!” Ya kira sunanta more tensed this time around “wallahi before the count
of three ki bud’e k’ofan nan ko na b’ab’b’alki wallahi.” Safa da marwa take a
d’akin ta rasa nayi chan tace, “Ya ina toilet nefa.”
“I don’t care ki bud’e k’ofan nan nace kar kiyi pushing d’ina kisa na miki duka.”
“Bazaka dake niba idan na bud’e maka?”
“Nace ki bud’e!”
“Ya dan Allah kayi hak’uri” a hankali ta nufi k’ofan ta bud’e take tayi kneeling
“dan Allah kayi hak’uri” ko saurarenta beyi ba ya fincikota da hannu se side nasu
yayi wurgi da ita a d’akin. Gabad’aya Zeezee ta gama tsurewa se faman hak’uri take
basa “rufa min baki!” Ya daka mata tsawa “ce miki akayi dukan ki zanyi? Kuma koda
dukankin ma zanyi, you think wannan hak’urin kin could stop me?” Dan sanyi taji a
ranta, wajen laundry basket ya nufa ya fara fiddo da laundry’nsa duk anan kallonsa
take bata ce komi ba bayan daya gama ya wurga mata sabulu da omo “oya pack them
kije ki wanke min su tatas, isolate the white coloured ones from the rest and
believe me in har be wanku me kyau ba zaki sake and don’t think wai da washing
machine zaki wanke, uh-uh” yayi shaking kanshi “da bare hands naki now off you go.”

“Chabd’i! Nice zan maka wanki kuma wai da hannu? Allah yaga ko panties d’ina ban
tab’a wankewa ba seda machine, ko nama da washing machine kokuwa kayan naka su
zauna da dotti.” Belt nasa ya zare “meh kikace?” Nan ta maraice fuska, “Ya dan
Allah kayi min rai kayi hak’uri wallahi ban iya ba zan maka da washing machine.”
“Nace banaso tattara ki bani waje! Now!” Tana b’ari ta tattara kayakin tayi waje
da su waje ta nema ta zauna tana sharb’an kukanta tsakani da Allah tana sumbatu
tana kiran sunan Baba, ko uffan Mama bata ce mata ba da ta ganta, bayan data gama
shan kukan ta tsoma kayakin cikin bucket tana tunanin ya zata fara wankin. Ganin
Ibraheem tayi ya fito da belt a hannunsa take ta fara wankin without knowing how.
Kujera yaja ya zauna gefenta yana kallonta tare da instructing nata da zaran tayi
pausing kuwa ya d’aga mata belt tana kuka tana jan Allah ya isa ta samu ta gama
wankin sukaje gun shanya ta shanyasu tas har takama hanyan d’akinta tana tafiya
tana kallon yadda omon yaci mata faracu tana gun-guni Ibraheem ya kira ta “ke!
Where do you think you are going? Baki fa gama aikin naki ba.”

“Ni wallahi ba jaka bace, dubi wankin dana maka kawani ce ban gama ba” seta rushe
da kuka “wuce site d’ina nace kinada minti d’aya kiyi hakan” banzan kallo ta bishi
dashi “shegen jan fuska sekace tsuliyan biri, mugu kawai” tafad’a a hankali sannan
a hankali ta soma bin bayansa suna isa d’akin ya jata toilet “so nake ki wanke mana
bathroom d’innan tas! Banason naga slightest dotti ga harpic da hypo off you go.”
Kuka tasa tsakaninta da Allah “bazaki tashi bane?” Still sprawled a k’asa tace;
“Ya kayi hak’uri wallahi na tuba zan kira Aunty Fateemah na bata hak’uri.”
“Aww kinsan dama abinda kikayi ba dai-dai bane?”
“Eh nasani wallahi na sani sharrin shaid’an ne.”
“Kinsan ba kyau mesa kikayi?”
“Wallahi sharrin shaid’an ne na tuba.”
“Zaki k’ara?”
“Wallahi bazan k’ara ba ko wayanka bazan sake tab’awa ba.”
“Kai inaaa tashi kije ki wanke toilet d’in by then kayan da kika wanke sun bushe
kihau gogewa ban yarda da tuban da kikayi ba.”
“Ya wallahi na tuba bazan sake ba, na sake kamin duk abinda kaga ya dace.”
“Maza tashi ki bani waje ki sake tab’amin waya kiga” har da cin tuntub’e agarin
fita, d’akinta ta nufa straight taje ta mik’e kan gado.

A week later Mariam ta haihu ta samu ‘yarta Zeezee najin haka ta hau had’a
akwatinta zata gun me jego kodan cin kazan jego, itama Yasmeen na jin haihuwan
Mariam ta hau had’a akwati. D’aukan abu ya kawo Zeezee d’akin Yasmeen ganin tana
had’a akwati ta dakata, “Yasmeen ina zaki haka?”
“Bakiji haihuwar Adda Mariam bane? Zanje tayata zaman jego.”
“Chab! Ke asuwa? Wallahi na rigaki ni zanje mata.”
“Se mu gani ai! Keda ko aiki bakison yinne zaki tayata zaman jego?”
“Wannan kuma keya dama wallahi ni zanje dani za’a ci kajin jego ehe!” ganin
Yasmeen ta cigaba da shirya kayakin nata ta fice zuwa d’akin Baba kai masa k’orafi
ai kuwa ya goye mata baya just as expected, yace sam ita zataje ta taya Mariam
zaman jego ba yadda Mama batai dashi ya bari Yasmeen meh son aiki taje ba yak’i,
bayan Zeezee ta gama had’a akwatinta Omar yayi dropping nata a motan Baba.
Mariam dake expecting Yasmeen kawai se ganin Zeezee tayi. “Ya haka ina Yasmeen?”
“Tana gida” ta bata amsa a takaice.
“Tana hanya ko tana gida? Ba ita zata tayani 40 days ba?”
“Baba yace ni zan miki.”
“Ke! God help me wallahi aiki zaki zage kiyi kina jina koh?”
“Ai nasani ina baby’n take muga kota kwaso muninki.” Da yamma Mama da Yasmeen
suka iso tayi ma baby wanka.

Zeezee de tun daga ranan ba aikinta se ciye-ciye dake ba abinda Uncle Mahmoud
bai siyowa kowani rana kuwa se Mama tazo tayi ma jikarta wanka atimes su taho da
Yasmeen atimes nahh. Ba wani aikin arzikin da Zeezee ke yiwa Mariam banda in an
kawo kaji ta baje taci ta had’a tean ta me kauri tasha se in taga Uncle Mahmoud ne
tage zagewa tayi aiki saboda kud’in katin dayake bata anytime yaga tana aiki. Ahaka
har aka samu akayi suna yarinya taci sunan Ramlah (mom na Uncle Mahmoud.)
30 days Zeezee tama Mariam ta tattara kayanta tabar gidan saboda gajiya da tayi
da wanke panties na kashi, Mariam se aukin barin ‘ya ba pampers dalili wai ana zafi
ga Ramlah se aukin pupu any minute. Ganin haka Zeezee tace zata koma gida Uncle
Mahmoud da kansa yayi dropping nata ya bata 3k ai kuwa mutumiyar ta raina ta manta
d’ari biyu zuwa biyar da yake bata almost after every 3-4 days nasa kati a waya.
D’akinta ta wuce direct tayi whats needs to be done sannan ta fito tayi d’akin
Yasmeen, mik’e kan gado tana karatu ta tarar da ita “Yasmeen ina Baba?”
“Har kunyi arba’in d’in ne?”
“Su gama arba’in nasu lafiya wannan Ramlah take ko meh se aukin kashi minti-minti
na gaji da wanke pant na gudo.” Dariya sosai Yasmeen ta tsaya yi da k’yar ta samu
ta tsaida dariyan tace, “amman bakida mutunci wallahi sam!”
“Niba wannan ba ina Baba ya bani dubu biyu in cika in sai wani porche dana gani a
Jumia 5k.”
“Baba yayi tafiya ai yau.”
“Tafiya!” Tayi exclaiming “shine be fad’a min ba wallahi ya kyauta.”
“Ji mata! matarsa ce ke da seya sanar dake in zeyi tafiya, lallai kam.”
“Ni yanzu ki ranta min 2k, na gama sa rai Uncle Mahmoud ze ban 5k yakama yawani
ban 3k mschw!”
“Baki gode ba kenan.”
“Iyi kuwa ko bakin kasuwa naje na zauna zan tara dubu ukun, ranta min 2k d’in
kinji?”
“Dalili? Ke d’inda baki biyan bashi.”
“A da ba, da dabansan meye bashi ba amman Allah yanzu zan biyaki.”
“Tsakaninki da wa?”
“Da da tsuntsu ne? Da Allah mana.” Kallonta Yasmeen tayi taji kaifa bazata iya
rantawa Zeeze kud’i ba. “Kai! Ban yarda ba kije kice Mama ta baki.”
“Tana gida ne? Kai aiko tana gidan ma ba bani zatai ba ‘cause time da Uncle
Mahmoud ya ban 10k ban bata ko k’wandala ba.”
“Kinga erin halin naki ai, nide kije ki rok’eta kokuwa kije gun Ya Ibraheem ko
Omar nide na koyi lesson ban sake baki bashi.”
“Ya Omar? Wancan marowacin? Ko dubunsa ban tab’a ci ba, dama-dama Ya Ibraheem
d’inma de shikuma yanzu da naje ze kama min suratai please ki bani Allah zan mayar
miki nan da 2 weeks” da k’yar tasamu tayi convincing Yasmeen ta bata kud’in nan ta
biya buk’atar ta.
* ~ *~ _Few days later_...~ *~
_Wednesday night 12:46AM_ Zeezee ce miqe kan gadon d’akinta tayi ruf da ciki se
chatting take a wayarta not minding gobe tana da school ga kuma test da suke dashi
a Maths. Bacci ne yazo yayi gaba da ita batasan when and how ba. 5:00AM as usual
Mama tazo tayi knocking bisa k’ofar d’akintan gbam! Gbam! Gbam! “Zeezee tashi
Sallah” shiru ba response “Zeezee!” Se anan ta amsa uhmmm.
“Tashi Sallah ko kin manta da akwai school yau?”
“Ni banayi.”
“Yaushe ne kikace baki Sallah? Yauma kice bakiyi?”
“Toh date d’ina ya rikice ne” tayi stating sleepishly.
“Banson k’arya fa bud’en k’ofa!”
“Mama dan Allah ki tafi naji zanyi.”
“Kar ma kiyi ba yarinya ce ke yanzu ba ai” tana kaiwa nan ta fice Zeezee bata
tashi ba se 6:00AM alwala tayi, tayi Sallah ta koma gado ta mik’e a cewarta wai
6:30AM seta tashi tayi wanka ta shirya.

Kasancewar baccin da bata samu jiya ba tayi sleeping off 7:10AM Ibraheem ya
gama shirinsa tsaf yazo fita ganin ba Zeezee yayi ficewarsa yaso seta bi su Nanah
(maqotansu) bacci Zeezee tayi tasha se 9:06AM da Baaba tazo share mata d’aki ta
tashi sanadin knock da Baaba ke. Firgit ta miqe se yanzu ta tuna tanada Maths test,
agogo ta kalla taga 9:07AM “innalillahi! Maths test!” bayi ta fad’a tayi brushing
ko wanka batai ba har a yanzu knocking Baaba ke.
“Nikan dan Allah wa me cika min kunne? Koma waye ne ya koma seda na gama makara
zaku wani zo kuna wani min knocking mschw!” Ta k’are maganan tana zipping school
bag nata, drawer’nta ta bud’e taga ba uniform ciki duk sunyi dotti, jiyan daya
kamata ta wanke batayi ba tana ta chatting. Ihu ta qurma ta zarce d’akin Mama,
suprisingly Mama ta d’ago kai tana kallonta “ya haka? Ba school ne yau?”
“Ai dole kice haka” tayi maganan almost crying “Baba kad’ai ya damu da naje
school koko a’a wallahi sena kirasa na irga mai komai, tun tafiyansa nike tashi na
shirya kaina baku assisting d’ina gashi a banza yau nayi missing Maths test kuma
teacher’n bayayin make up test.”

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 16

*December, 2016*

“In kin fasa, banje na ta dake Sallah kika k’i tashi ba? Fice min daga d’aki
da Allah!” tsaye tayi gun tana mata mugun kallo ledan bread dake gefen ta Mama ta
d’aga ta wurga mata “ficemin nace!” Kuka Zeezee tasa ta nufi d’akinta ta kira Baba
a waya tana kuka cike da tashin hankali ya tambayeta ko lafiya nan ta irga masa
komi. “Haka suka yi maki? Kai wa Maman naku wayar” ai atapir Mama tace bazata amsa
wayan ba saboda tasan ita ta tada Zeezee itace tak’i tashi “Hafsah fa ina jinki
amshi wayan nace!”
“Wallahi bazan karb’a ba duk Alhj kabi ka b’ata yarinya se aukin rashin kunya nan
gaba aka tayar da ita zata tashi ai.”
“Aww haka kika ce koh?”
“Eh ai hakan ne.”
“Da kyau, Zeezee...”
“Na’am Baba” ta kashe speaker.
“Bari in na dawo zanje in samu teacher’n naku in shaa Allah ze baki makeup d’in
shi kuma Ibraheem zan kirasa bar kukan haka kinji K’anwata.”
“Toh Baba nagode ba-bye” yana katse wayan ya kira Ibraheem ya dinga balbalesa da
masifa. Da azahar Mama ta shigo d’akin Zeezee ta tarar da ita mik’e kan gado tasa
earpiece a kunne tana jin music tana kad’a kai.

“Laa’ilaa! Kid’a kikeji haka?” Earpiece d’in ta zare “ni wayace miki wak’a nakeji
shikenan mutum be isa yasa earpieace ba ace yana jin wak’a.”
“Toh me kike ji dashi?”
“Voicenote aka turon a whatsapp nake playing.”
“Yayi kyau mik’e kije ki share min d’aki ki kuma gyara kan gado kiyi mopping zan
shiga nan mak’ota.”
“Toh ba Baaba tazo ba”
“Baaba bata da lafiya bazata iya duka aikin ba.”
“Ni wallahi da erin wannan aiki gwara an sallameta mutum sekace me aids kullum
batada lafiya-” kafin ta hankara taji sauk’an mari fas! A bakin ta, “ki iya bakinku
kina jina koh?”
“Allah ya-”
“Mawa?” Mama tayi saurin katse ta dama cike da ita ta ke, nan ta rufe ta da duka
seda tayi mata lik’is sannan ta barta “marasa kunya kawai kuma ki kira Baban naki
yanzu ki cemasa nayi maki duka kiga in bansa Omar ko Ya Ibraheem sun k’ara miki
ba.” Kuka sosai Zeezee ke tsakaninta da Allah ana cikin haka Omar ya dawo gida inda
yaji hanayaniya ya zarce “ya haka Mama? Meke faruwa?”
“Barni da maras kunyan nan Omar zan fita ka tabbata ta share min d’aki tayi
mopping in bahaka ba kamata dukan tsiya nina baka izini.”
“An gama Mama sekin dawo” nan ya dawo da kallonsa kan Zeezee dake harararsa “me
kike jira har yanzu da baki mik’e ba?” Bayan fitan Mama yasa Zeezee gaba taje ta
d’au tsintsiya ta shiga sharan cuwa-cuwan data saba duk ta tuttura dottin
k’arkashin gado tanayi Omar na mata dariyan mugunta itako se zaginsa take a ranta.

Da La’asr Yasmeen ta dawo gida taci broke kona kati bata da, remembering tanada 2k
gun Zeezee ta mik’e taje ta sameta a d’akinta oya ke bani 2k na, ai ba haka mukayi
dake ba.”
“Ai nice zan ce ba haka mukayi dake ba, ce miki nayi se Baba ya dawo.”
“Lallai kuwa! Yaushe mukayi haka dake? Kinsan yaushe ze dawon nema? Kiban kud’ina
Malama”
“Seki d’auken ai tunda nima kud’i ne” tana kaiwa nan ta juya mata baya. K’arisawa
cikin d’akin Yasmeen tayi ta wanke ta da mari a baya “Allah ya isa kuma bazan bada
kud’in ba.”
“Haka kika ce?”
“Eh” kafin ace me suka b’arke da fad’a tun daga d’aki Mama takejin hayaniya “ya
haka? Meke faruwa?” Tayi maganan tana k’ok’arin rabasu, ko a babu Zeezee taci
k’aniyanta da k’yar Mama ta samu ta raba sun “wai kashe kanku kukeson yi neh?”
“Mama wallahi kice ta biyani 2k na” cewar Yasmeen tana huci.
“Meya faru tukuna?” Nan Yasmeen ta labarta mata komai bayan da Mama ta gama jinta
tace, “toh kema meya kaiki baiwa wannan bashi? Sekace bakisan halinta ba.”
“Wallahi tsautsayi kuma ma seda ta rantse kafin na bata.”
“Oya Zeezee nasan kinada kud’i pay her back her money.”
“Aiki nake da zan samu kud’i ta bari Baba ya dawo.”
“Sarai nasan kina saving break money naki ki d’au dubu biyu ki bata or else.”
“Or else what? Zaki cire mata daga cikin pocket money na da Baba ke baki?” Tayi
maganan unbelievably.
“Tabbas! Tun wuri ki d’au kud’inta ki bata.” Kuka Zeezee tasa “wallahi Allah ze
sak’a min ni se Baba ya dawo na bata.”
“Taho muje Yasmeen na baki a pocket money’n ta.” Ba kalan darun da Zeezee batayi
ba amman hakan be hana Mama d’au dubu biyunta ta bawa Yasmeen ba, yini tayi ranan
tana kuka gashi kota kira line na Baba bai shiga.

The following day tasa alarm nata da kanta ta tashi, koda taji Mama na knocking
k’in amsawa tayi bayan ta gama shirinta ta fito ta leqa dining wayam taga ba
breakfast nata daman aikin Yasmeen ne had’a mata breakfast Baba yayi appointing
nata.
Gbam! Gbam! Gbam! Knocking take bisa k’ofan d’akin Yasmeen wane zata b’alla,
sauti cike da gyangyad’i tace “wallahi kika sake knocking kinji na rantse zaki
school kina kuka yau.”
“Sekisa d’in ai muga iskanci kawai ina breakfast d’ina?”
“Cook d’inki ce ni da zaki tambayen?”
“Eh mana ai aikin kine Baba yasaki kina min breakfast.”
“Toh banyi ba yau saboda Ya Ibraheem yace baze karya ba danke kuma bazan yanke
bacci na ba.”
“Kutcee! wallahi bari Baba ya dawo zakiga!” Kitchen ta nufa ta fiddo da three
eggs da nufin soyawa sede sam ba ta iya ba at last ta k’ona k’wan itama ta k’one a
hannunta a takaice da coco pops tayi breakfast ranan sannan ta koma d’aki tagama
shiri ta nufi na Mama dan amsan break money’nta.
N200 d’in ta d’aga kan chess of drawer “Mama” ta kira sunanta “meh?” Ta amsa not
minding ta juya. “Ance fa mu sayi Evergreen solution na junior waec namu.”
“To ba seki jira Baban naki ya dawo ya baki ba.”
“Ai bansan ranan dawowan sa ba kuma yaune deadline d’in.”
“Yayi kyau seki tambayi Ya Ibraheem.”
“Ni wallahi a’a nasan ba bani zeyi ba kibani in tafi please zan yi latti” se anan
Mama ta mik’e zaune ta juyo tana kallonta “wai ma tsaya anya ba k’arya kike ba?
Anya kuwa ance kusai textbook d’in?”
“Eh mana da zan miki k’arya ne.”
“Nawa ne?” ta tambaya finally tare da mik’ewa.
“N2,000 ne.”
“Ke wai ni zaki raina ma wayo? Wato jiya dan na cire 2k daga kud’inki shine kema
zaki dampareni koh?”
“Allah ma sheda nane kibani wallahi kona kira Baba na sanar dashi.”
“Inma k’arya kike keda Allan ki” nan ta mik’a mata 2k d’in kwatsam ta amsa ba
godiya “dawo, dawo nan.”
“Menace miki duk lokacinda aka baki kud’i?”
“Inyi godiya” tayi maganan tana sa kud’in cikin jakarta.
“Mekuma kikayi yanzu?”
“Toh kud’in kashewa ne kika bani? Bana school bane? Kuma naga in nayi karatun
kema ze amfane ki mena godiyan?” Buge bakinta Mama tayi da k’arfi seda ya fashe ya
soma jini take idonta ya ciko da hawaye “karki iya bakinki ki koyi kalmasa
kalamunki kiga kullum inban riga bige bakin naki ba, kiyi godiya ko kiban kud’ina?”
Shiru tayi chan tayi mumbling “nagode” sannan ta fice rai a dak’ule “Allah ze
sak’amin kuma ko a babu na amshi kud’ina wallahi ba Evergreen da zan siya” garriage
ta nufa tana jiran fitowan Ibraheem ayayinda bakin nata ke tayi mata rad’ad’i
idanunta kuwa se cikowa suke da hawaye. 3 minutes more Ibraheem ya fito kallo d’ai
ya mata yagano da akwai matsala “meh haka kuma kike wani turo baki?”

“Ba Mama bane ta bigen a baki na.”


“Eh ai dai-danki kenan bake rashin kunya ba.”
“Ni tunda ba sannu zaka cemin ba save your wa’azi ka bud’e motan.”
“Meh kikace?” yayi maganan in a serious tone.
“Nace kad’an bud’en motan kar nayi latti.”
“Da yafi maki kam.” Bayan sun isa school d’in kafin ta fito daga motan ya kashe
mata warning “sauran kuma idan nazo d’aukanki ki shanyani like the other day kiga
abinda zan miki yau” bata ce komi ba seda taga yaja motarsa tace, “mugu kawai”
sauk’an mari tajiyo abayanta cike da tsiwa ta juyo ready to insult who ever it was
kawai setaga Lubiee.
“Ohh Lubiee!” Ta fad’a a bit startled.
“Ahhhh! ‘yan mata yau ma a tare muka iso kenan! Ya haka meya sameki a baki?”
“Hmm sekin tambaya ne? Mama ce mana anga Baba baya gida kowa secin zali na yake
wallahi Allah ze sak’a min.”
“Me kikayi mata?” Lubiee tayi tambayan tana dariya.
“Hmm kede bari! I’m taking you guys for a treat today” nan ta curo 2k d’in ta
nuna mata.
“Wannan ba kud’in Evergreen da akace mu saya bane?”
“Wannan kud’in kashewa zan ba Evergreen da zan sai se Baba ya dawo zan sake
tambayarsa” nan ta labarta wa Lubiee abinda ya faru jiya alokacin har sun isa class
suna zaune.
“Chab! Lallai Zeezee baki jin tsoron Allah, kina wuta ina binki da nuclear bomb!”
“Ke bazaki gane bane ‘yan gidan namu ne seda haka wallahi kawai dan Baba yafi
sona suke min bak’in ciki shima Ya Ibraheem sena tambayeshi kud’in”

*** During break Zeezee ta had’a friends nata both maza da mata ta kaisu school
kiosk nasu tayi musu siyayya kowa se hailing nata yake ana tashi taje ta tsaya
bakin gate yadda zata iya hango motan Ibraheem koda yazo, bada jimawa ba yazo ya
d’auketa suna isa gida ta zarce ciki Baba A’ee da Mama ta tarar zaune tsakar gida
suna shan iska daga lungu guda “sannu Mama” tace sama-sama “sannu Baaba.”
“Zo nan!” Mama ta kirata, ba gardama tajeta “gani”
“Baki iya gaisuwa bane kokuwa bakiga Baaba bane?”
“Ba nace mata sannu ba? Ko beyi ba?”
“Sannu gaisuwa neh?”
“Nikam da Allah daga dawowan mutum ko abinci beci ba ahau shi da surutu ina wuni
Baaba shikenan?”
“Ki cigaba kinji wallahi ba inda rashin kunya ze kaiki sannan kuma ina reciept na
textbook da kika siyan?” Kai tahau sosawa tana tunanin wani k’aryan zata had’a
“ehemm dake fa nake ina receipt d’in?”
“Ji Mama sekace school fees aka biya da za’a bada reciept.”
“Uhn-uhn fah!”
“Toh kije makarantar mana ki tambaya in baki yarda ba ni yunwa nakeji” tana kaiwa
nan ta bar gun.
“Oh!” Baaba da tun shigowan Zeezee bata iya tace komi ba ta sauk’e ajiyar zuciya
“abinda Zeezeen namu ta koma kenan muna ji muna gani? Gaskiya Alhj be kyauta ba ko
kad’an kuma kema da naki Hafsah bazan b’oye miki ba.”
“Kamar ya da nawa Baaba? Da ace ita kad’ai ce ‘ya a gabana se ya damen amman
inada wasu hud’un wanda ko a ina nasan za’a yaba da tarbiyyansu wallahi ko Allah
baze kamani ba, nayi magana har na gaji, tun yarinyan nan bata kai haka ba nake
yiwa Alhj wa’azi amman never once did he ever listened to me, me zanyi toh? Akanta
sena lalata rayuwar aure na? Inma zanyi sena bari sena aurar da Yasmeen. Ai munanan
tare wallahi wataran Alhj seyayi kuka da hawaye akan Zeezee tunda ya miyar da ita
*_YAR GATAN_* da batada flaws.”

“Amman haka zaki zuba ma ‘yar da kika haifa ido tana lalacewa?”
“Toh ya kikeso inyi? Daman duk inda aka tara mutan arziki ba’a rasa na banza
cikinsu, haka haihuwa ma wata nata gabad’aya haihuwan ma na asara tayi ba na arziki
cikinsu kuma bawai Allah yayi hakan bane dan bayi sonta sedan ya jaraba ta, ni kuma
da Allah yaban har hud’u masu hankali da tarbiyya se ink’i gode masa nayi hauka
sabida d’aya ta tab’arb’are min? Wannan ma jarabawace kinsan kalan halin Alhj
towards Zeezee a banza bazasu samin hawan jini ba wallahi is better in fita daga
harkansu khalas! Muna nan shi da kansa wataran zeyi regretting ba shi kad’ai ba
harta ita.”
“Allah shige mana gaba toh ya ganar dashi gaskiya since before its late.”
“Ameen deh da yafi mai dan wallahi in Zeezee ta cigaba da haka banga na mijin da
zezo ya iya da ita ba.”

★*★*★*★
_A week later..._
Sosai Zeezee ta gogu da bak’in wahala cikin sati biyun da tayi ba Baba, muguntan
yau daban na gobe daban take samu gun yayyunta gashi ko uffan Mama bata ce musu,
ita kuma ko yankata zasuyi bakinta baiyin shiru, Allah Allah take Baba GATAN ta
yadawo. A hanyan dawowa daga Lagos to Bauchi armed robbers (‘yan fashi) suka tari
motocin d’iban kayan Baba guda biyu daya cika su dim da kayaki suka gudu dashi basu
barshi da komai ba. It was such a great lost saboda gabad’aya kud’in account nasa
yayi emptying yayo wannan siyayya, abinda yarage a account d’insa sam baida yawa ko
kiran Mama ya sanar da ita wannan k’addaran da Allah ya turo mai ma be iya yayi ba
sede still kamar yadda Allah yace kowacce k’addara na tare da sauk’i, Allah yayi
armed robbers basu k’wace mai motan dayake ciki ba Subhanallahi! What a great lost.

_Three weeks later..._


A takaice kusan rayuwan kowa ya soya a gidan especially na Zeezee da batasan meye
k’addara ba balle ta rungumeshi, wai ahakan ma don da taimakon Ibraheem da Mama
atimes. Gatsau! Kamar yadda ta saba shiga d’akinsu Mama ba sallama ta fad’a yau ma,
direct wajen sa ta nufa, “Baba a canza min waya Abban Lubiee ma ya canza mata nata”
“Zeezee ina zan samu kud’in da zan sai miki sabon waya? Aiint you aware of what
happened to me? Na rasa komi fa Zeezee, ki cigaba da sani a addu’a Allah maido min
da arzikin da yafi wancan ba waya ba ko jirgi kikeso zan sai miki.”
“Har se yaushe kenan Baba? Haka zan yita zama da akwalan waya?”
“Zeezee sata kikeso inje inyi ne in sai mikin? Kema kinsan inda akwai zan saya
miki ko bakisan babu bane?”
“Ni wallahi a canza min waya” nan ta hau bubbuga k’afa.
“Zeezee nace babu kiyi hak’uri mana ke bakisan in babu bane?”

“Ina kuwa ta sani?” Mama dake zaune kan Sallaya tayi maganar bayan sauraronsu
datayi, “yarinya tun tana ‘yar k’arama ka saba mata da getting whatever she wants
whenever she’s in need, never once did you showed her akwai state of emergency,
baga irin ta ba yanzu yarinya is thirteen (13) years old amman batasan meh ake nufi
da babu ba, kad’an ka gani ai wallahi. Malam bahaushe beyi k’arya ba kaso d’anka
duniya tak’i sa, kak’i naka duniya ta sosa.”
“Kai! Kai! Kai! Meh haka da wannan zance? Meyayi zafi? Meya kawo zancen wani
kak’i d’anka duniya tak’i ta, me hakan?”
“Ai gaskiya d’aya ce Alhj kuma daga k’in jinta se b’ata you know right what I
mean kuma ka cigaba, kar fa ka manta Zeezee ‘ya mace ce in Allah ya barta rai da
lafiya dole wataran zatayi aure ka gayamin wani mijin ne ze iya taking halinta, ace
ance wa yarinya babu sarai tasan abinda ya sameka weeks back amman dake batada wayo
tazo tana ce maka ka sai mata waya ko ni zaka sai ka siya mata wayan bansani ba.”
“Toh ya isa haka! Zagin ya isa haka, ce miki akayi haka zata cigaba da zama ne?
Ai tana girma tana dad’a wayo yanzu ada da take k’arama har zagi batayi neh? Yes
tanayi yanzu kuma fah? Tun da ta shiga primary one ta sake d’aga hannu ta zageki ko
nine a gidan nan? Hak’uri duk zamuyi amman dekam karki sake cewa K’anwata batada
wayo.”
“Wannan kuma ku ya dama dan ni bazan cigaba da zama anan ‘yan unguwa suna zagi na
ba, ina aurar da Yasmeen zan koma garinmu incigaba da zama na kai da K’anwarka se
kusan inda dare ya muku gare ya waye muku” tana kaiwa nan tayi excusing kanta.

Sosai words na Mama suka ratsa jikin Baba amman sede shi bayason ganin fault in
Zeezee, hannunta ya kama ya zaunar da ita gefensa “karki jita kinji K’anwata? Ki
tayani da addu’a ina samun kud’i zan canza miki wayan kinji?”
“Toh” tace “zan koma d’aki.”
“Yauwa K’anwata kiyi hak’uri kinji?”
“Toh Baba Allah kawo kud’i.”
“Ameen K’anwata, ameen ameen.”

~* ~* ~*
D’akinsu Ibraheem ta wuce tayi sallama kaman ba ita ba “wa’alaikumus-salam” ya
amsa.
“In shigo Ya?”
“Eh shigo” bayan ta shigo tanemi gu a k’asa ta zauna for the first time, “Ya ance
mu sayi Evergreen solution na junior waec namu.”
“Nawa ne?”
“N2,000 ne.”
“Toh naji Allah ya kaimu gobe.”
“Ameen nagode” tana kaiwa nan ta mik’e ta koma d’akinta dubu biyun da ta karb’a
gun Baba jiya ta ciro sannan ta murmusa wayarta taja ta kira Lubiee bayan sun gaisa
tace, “ke yanzu na damparo Ya Ibraheem gobe yace ze bani.”
“Ohh! Zeezee yanzu bayan abinda yasamu Baba still sekinyi masa cuwa-cuwa.”
“Toh ai dubu biyu ne bawani kud’i dayawa ba kuma da nasan zan biya na Ya Ibraheem
kashewa zan.”
“Uhn-uhn fa Zeezee, atleast kid’an ji tausayin Baba kiga yadda yake sonki fah.”
“Ke! Dake da wa’azin uwaku kinji ba! Semun had’u a school gobe, bye!” Tayi
hanging.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 17

*December, 2016*

_I dedicate this page in honour of my dear supporters and huge fans *Amyna Malam,
Baby Amrah* and *Haleema Abdullah* ILY'ALL💕 #OneLove❤_

_Several weeks later..._


Rayuwa de ta canza daga dad’i zuwa rashinta. Ba abinda ke tafiya wa Baba da
iyalansa dai-dai komi ya tab’arb’are more especially ma Zeezee da batasan me
k’addara ba bale ta rungume sa. She is used to samun duk wani abinda takeso at that
very moment amman yanzu ko kud’in kati setayi dagaske take samu, kullum a cikin
complaining take ita tagaji da rayuwan talauci ita kaza ita kaza, harta ipad nata
sanda aka siyar danyi mata cikon school fees. Ibraheem na iya k’ok’arinsa dan har
na terms biyu kusan dubu d’ari biyu kenan yake biya wa Zeezee as school fees.
Without his help da anjima da cire Zeezee daga LYS.

A yanzu haka tana Ss1 tanayin sciences, Zeezee tana girma kyanta na ta
dad’uwa, doguwa ce dai-dai, ta kuma k’ara kauri kad’an kan sirantakarta wanda hakan
ya mugun fito da dirinta. Tun shigarta Ss1 ta rage karatu se aukin kula yeye
samari, kullum seta yini tana waya kokuwa chatting. Kasancewar ayau friends na Baba
daga Yola zasu zo yasa akayi lunch like no other, kap ‘yan gidan sun manta when
last akayi miya yaji nama kaman na yau stew ne had’ad’d’e wanda yasha nama tako ina
da coconut rice. 3:23PM Ibraheem ya dawo da Zeezee from school tana shiga ciki tayi
kitchen Yasmeen tasamu tana d’an d’auraye used plates babu ko sannu ta ja plate ta
shiga d’iban abinci, da wuri Yasmeen ta dakatar da ita.

“Ke wayace miki wannan namu ne? Ko bakisan Baba zeyi bak’i bane yau?”
“Semeh dan zeyi bak’i me had’i na da bak’insa? Nikan matsa min in d’iba abinci.”
“Mama! Mama! Kiga Zeezee wai abincin friends na Baba zata d’iba.” Daga ciki Mama
tace da Zeezee karta tab’a ga nasu na gida can agefe amman dake Zeezee banda
maganan Baba bana wanda takeji haka ta d’iba na friends nasan ta sa nama bakwai (7)
akai ta k’ara mai. Baba na dawowa gida Yasmeen taje ta fad’a mai, masifa ya shiga
yi mesa Mama bata hana Zeezee d’iba ba, “yanzu ina zan samu kud’in sai wani naman?”
“Toh kana blaming waye? Tana jin magana na ne? Bakai ka b’ata taba ai nace mata
karta d’iban tak’i jina se kasan nayi yanzu.”
“Aww haka ma zakice ko? Instead kija mata kunne.”
“Ai kai da ka b’ata ta kai zaka gyarata saboda haka ni kabar cika min kunne.”
“Kin kyauta Hafsah, dake yanzu kinga bani samu kaman da dole ki zauna kina
gayamin magana iya san ranki, kisani ba ahaka zan gama zama ba in shaa Allahu Allah
zemin bud’i”
“Aini ba haka nake nufi ba don’t misinteprete my words” D’akin Zeezee ya nufa ya
sameta secin abincin ta take tana chatting “sannu da zuwa Baba” tace dashi.
“Haba! K’anwata taya zaki kwashe nama har bakwai (7) ke kad’ai bayan kinsan halin
da muke ciki a gidan nan.”
“Shikenan Baba nama d’aya kakeso in d’auka?”
“Eh mana ai babu ne yanzu lokacin da akwai ba na miyan nake baki duka ba?”
“Nikam gaskiya ban saba ba.”
“Kikace meh?”
“Nace kayi hak’uri.”
“Naji amman karki sake yin hakan yanzu me kikeson na bawa bak’in in sun iso?” Bayan
Baba ya fita taja k’aramar tsuka “shikenan sekace ni na d’aura mana talaucin da
za’a hanani cin nama, wallahi sede in ba’a siya ba in bahaka ba senaci.”

~* ~* ~*
Ana cikin haka promotional exams nasu Zeezee ya zagayo sam batta karatu se
chatting da samari a daren da suke da Chemistry Mama tashigo d’akinta unexpectedly
kawai ganin Zeezee tayi ta baje kan gado rungume da pillow tana waya da saurayi
daman bata tab’a kama ta red-handed ba seyau, koda Yasmeen ta kawo mata k’orafi
cewa fa ga abinda Zeezee keyi bata yarda ba saboda bata d’au rashin hankalin Zeezee
har yakai ga haka ba. Wayar ta katse da wuri ta jawo littafinta ta soma karatu.
“Dawa kike wayan?”
“Kamar ya da wa kuma? Da Lubiee man na tambayeta formula ne.”
“Ni zaki raina ma hankali? Nace da wa kike wayan?”
“Da Lubiee mana nikam haa’an!” K’arisowa cikin d’akin Mama tayi a fusace “dawa
kike wayan nace? Da saurayi koh?”
“Nide bada saurayi nake waya ba.”
“Oya miqo min wayan naki keda shi sekun gama exams.”
“Haka kawai se kimin siezing waya saboda Yasmeen tace miki da samari nake waya ni
wallahi bazan yarda ba” nan ta b’arke da kukan munafirci ta miqe ta nufi d’akin
Baba don kai mai k’ara, a hanya ta lab’e tayi deleting call nata da Ammar “ya haka
meke faruwa?” Baba yayi saurin tambaya.

“Mama ce wai zata min siezing waya bayan ina browsing stuffs na school dashi.”
“Wallahi Alhj k’arya take kamata nayi tana waya da saurayi.”
“Saurayi?!” Exclaimed Baba.
“Laaa! Wallahi Baba sharri ne ni danake Ss1 ina naga ta kula saurayi, Yasmeen ce
taje ta sameta wai inada saurayi alhalin k’arya ne.”
“Wallahi kar ka saurareta in tasan tanada gaskiya ta mik’o wayanta a duba.”
Confidently Zeezee ta mik’a mata wayar, sede tayi duban duniya bataga kowani waya
dana miji a call log dinba “ina number’n kinsamu?” Baba ya tambaya.
“Wallahi Alhj nina jita da kunne na sede in gogewa tayi.”
“Wallahi Baba sharri ne, yaushe ne na gogen? Ni Allah banida saurayi.”
“Ai nasani K’anwata, ba kalan tarbiyyan dana baki ba kenan.”
“Aww ka yarda da k’arerayin nata kenan? Kuma ma wani tarbiyyan ka bata?”
“Why not? Zeezee tayi k’araman da za’ace tana kula samari she is just four-teen
(14) years.”
“Ba komai ka cigaba da d’aure ma k’arya gindi kamar yadda ka saba wataran zakayi
nadama” tana kaiwa nan ta juya tana kallon Zeezee “kekuma Allah na kallonki” gwalo
Zeezee tayi mata ganin Baba bai kallon direction nata, batare da Mama tasake cewa
komi ba tafice.
“Ungo wayarki nasan sharri ne bazaki tab’a watsa min k’asa a ido bako? Keda
saurayi sekin gama secondary school, promise?”
“Yes Baba nagode” ta amshe wayan tare da ficewa zuwa d’akinta tasa lock sannan ta
haye gado ta cigaba da wayarta daga inda ta tsaya. Ahaka har suka gama exams Zeezee
bata rubuta wani abin arziki ba kuma abin takaicin ma wai school mate nata take
dating tana Ss1 yana Ss2 sunansa Ammar, irin millonaire school bad boy d’innan ne.

_One week later..._


A yau su Zeezee zasu karb’i result nasu, 9pm tagama shiri Omar yayi dropping
nata, hira da selfie sukata sha da friends nata da kuma Ammar, yau ya kasance 3
months anniversary’n su da Ammar, shopping na k’in k’ari ya mata sannan suka d’anyi
small party’n su. Not long enough form teacher’n su Zeezee ya raba musu results
nasu, shi kansa sakamakon Zeezee ya mugun basa mamaki average nata daga 70.+ ya
dawo 49. Sam yace seya kira Babanta yace bata karatu, da k’yar ta iya ta shawo
kansa ya fasa. Correcting fluid ta nema ta gyara 49. d’in zuwa 69. Isarta gida ta
zarce ciki da gudu da ledojin da Ammar ya bata gudun kar Mama ta ganta, ai tuni
Mama taganta tabi sahunta da sauri “Alhj! Alhj! Kazo da kanka kaga yau” tayi
maganan tana tare Zeezee daga rufo k’ofar d’akinta. Nan danan Baba ya fito ya
samesu “meke faruwa? Har Zeezeen ta dawo ne, ya results d’in?” Tana kame-kame tace,
“yayi kyau.”

“Wad’ancan ledojin fa daga gunwa?” Mama ta tambaya, stammering Zeezee ta shiga


yi, “nn... Nna..”
“Na saurayi ba?” wabje ledan Mama tayi daga hannunta sannan ta zazzage komi a
k’asa. Sega prefumes da chocolates masu heart shapes “ka yarda? Nace ka yarda yanzu
aiko? Inba saurayi ba waze mata wannam siyayya? Ina result nakin?” kafin Zeezee
tayi k’wararren motsi Mama tasa hannu ta wabje side bag nata tare da ciro result
natan sede koda taga 69 gun tagane fake ne, ga kuma correcting fluid data gani gun
tuni jikinta ya bata Zeezee ce ta gyara, “yanzu Zeezee har kinyi kaurin canza
result naki kikawo wa iyayenki fake one gida? Innalillahi!” Result d’in Baba ya
amshe yaduba sosai yasha mamaki jikinsa ya mutu lik’is, yama kasa cewa komi se
kallon result d’in kawai yake ayayinda Zeezee tagama tsurewa se raba ido take. Daga
bisani ya d’ago kai yana kallonta “kin kyauta kenan Zeezee? Abin naki har ya kaiga
ki d’au correction fluid ki canza result naki ki kawo wa iyayenki gida saboda kin
rainasu basu je boko ba? Cikin yayyun ki kin tab’a jin wanda yayi haka?”

“Baba nifa ban canza result d’ina ba-”


“K’arya kike” Mama tayi interrupting nata “meze kawo correction fluid kan printed
result inba canzawa kikayi ba?”
“A’a barta Hafsah, barta” cewar Baba. “Mesa kikayi hakan?”
“Nifa ban canza ba Baba.”
“K’arya kike sake min? Laifi akan laifi, nace mesa kika canzan? Kuma what was
your actual average?” Shiru tayi bata ce komi ba “dake nake magana Zeezee, meh
average naki? Karki sa na kira form teacher’nku na tambayesa.”
“49.” ne tayi stating in a slow motion.
“49!” Mama da Baba sukayi exclaiming atare.
“49. Out of 100? Meya sameki Zeezee? Shin baki karatu ne? Kinsan fa da yaya ake
samu ake biya miki school fees kika kawo min wannan sakamakon, acireki a LYS d’in a
kawo ki Havardth kikeso?”
“A’a” tayi saurin amsawa tana kad’a kai.
“Then mesa kikayi failing woefully haka?”
“Seka tambaya ne?” Mama tasa baki, “samari take kulawa ai na gaya maka, kalli
wannan shopping data shigo dashi inba saurayi ba waze bata? Ai na gaya maka wallahi
in bakayi tsaye akan yarinyan nan ba seta janyo maka abin kunya” tana kaiwa nan ta
basu waje “kin kyauta kenan Zeezee? Duk kalan gatan dana baki da abinda zaki sak’a
min kenan? You are indirectly calling me a fool tunda har zaki iya canza result
naki ki kawo min gida sannan kiyi believing zan yarda because you are taking me as
a fool isn’t it? kin kyauta kenan?” Kai ta kad’a “a’a Baba kayi hak’uri.”
“Baki ganin yayyun kine da baza kiyi koyi dasu ba? Banason ina miki suratai
Zeezee kidena sani, samarin dagaske kike kulawa ko? How old are you?” Fad’a sosai
Baba yayi mata for the first time.
“Na tuba Baba bazan k’ara ba” bayan nan yayi mata nasiha sosai kamar dagaske ta
ringa rusa mai kuka wajen tanata ta tuba bazata k’ara ba harda wai zata tattara
kayakin ma ta miyar wa Ammar. Baba na barin wajen ta share hawayenta ta tattara
kayakinta tayi ciki sannan ta d’au wayarta ta kira Ammar nata.

★*★*★
Ahaka har aka soma azumi, sam kaman ba da ba. Ada acika kan dining table dam da
kayakin shan ruwa amman yanzu abin sam ba dad’i, Zeezee de kullum cikin k’orafi
take ita fa tagaji sede Mama ta kalleta ta tab’e baki. Anyi azumi goma Baba ya siyo
zannuwa irin ‘yan N5,000 d’innan masu kyau guda biyu nanma dan yayi k’arfin hali ne
bayan shan ruwa ya tara iyalansa a parlour “dukanku kunsan yadda abu ya kasance
min, yanzu da da ba d’aya bane ga zannuwa nan guda biyu d’aya wa Yasmeen d’aya wa
Zeezee, Ibraheem Baba na nagode da komai Allah ya k’ara maka bud’i, Omar se kayi
masa godiya shi ze maka kayan Sallah. Mamanku kuma ta k’ara hak’uri zuwa next week
nad’an samu abu zan sai mata zanin itama.”
“Ba komai Baba” cewar Ibraheem bayan Omar yamai godiya.
“A’a nikuma sekace yarinya kabari kawai ansan babu ai karka damu addu’armu de
Allah yayi maka bud’i.”
“Ameen Hafsah ta nagode.” Yasmeen ce ta numfasa tace, “ayyi Baba aini ko baka sai
min kayan Sallan bama tunda duk kowa yasan halin da ake ciki yanzu.”
“Aw bakiso? Sena had’a da naki ai, meh kayan sallah d’aya zeyi wa mutum? Ai
wannan abin kunya nema Lubiee taji anmin kayan Sallah set d’aya-”
“Ke jahilar inace?!” Ibraheem yayi interrupting nata angrily.

“Haa’a! Ni namaka magana ne? Ai baka min kayan Sallah ba bale kasamu bakin
magana.”
“Ya isa haka Zeezee!” Baba ya tsawata mata juyawa kowa yayi yana kallon Baba yau
shike ma Zeezee masifa a idon kowa! “Bakida hankali neh? Ma yayan naki kike gayawa
magana? Ko bakisan dabadon taimakonsa ba da kin jima da dawowa nan Havardth da
karatu, maza basa hak’uri.”
“Toh Baba ni na mai magana ne, wallahi Allah ze saqa min bayan talauci ga kuma
masifa da rashin kwanciyan hankali” ta k’are maganan tana kuka “ko waya an kasa
canza min tun jss3” zaninta dana Yasmeen ta had’a tabar gun a guje kowa se kallonta
yake daga bisani suka maido da kallonsu kan Baba suna basa kallon ‘its all your
fault’ kai ya girgiza “Allah shirya Zeezee toh.”
“Ameen” Mama tace “inta shiryuwan ce, Yasmeen muje mu had’a miyan suhoor
d’in.”***
Kuka Zeezee ta tayi a d’akinta ita an had’a ta da kayan Sallah d’aya, Baba daya
rage shi kad’ai a parlour se jin sautin kukanta yake. A sanyaye ya mik’e yayi
knocking a k’ofar kamar wacce bazata bud’e ba ta tashi ta bud’e ranta a dak’ule.
Bayan sun zauna kan kujera Baba ya shiga mata nasiha saboda shi kansa abin Zeezee
ya soma basa mamaki, yarinyar da nasiha ba shiganta yake ba ko a kwalan rigarta ita
zannuwan Sallah take so ba suratai ba seda Baba ya gama zuba tace, “nagode Allah
k’ara bud’i.”

Washegari Mama da Yasmeen suna aikin kayan bud’a baki Zeezee na a d’aki as
always tana chatting, dawowan Ibraheem ya taho da fruits bayan ya dire a kitchen
yayi musu sannu da aiki sannan ya tambayi ina Zeezee.
“Tana d’aki as always” Yasmeen tabada amsa.
“Ita bazata fito tayi aikin bane?”
“Ai na gwada yi mata magana tak’i, Mama tasa baki kuma wai a’a abartan.”
“Mama hakan da kikeyin fa ba taimakan ‘yar nan kike ba, wace ita da zata ce
bazata yi aiki ba?”
“Toh Ibraheem kana ganin laifi na ne? Katab’a jin nama Zeezee magana tajini?
Sede in kai da kake dukanta, nikam ba haka iyayena suka girmar dani ba, bazan iya
dukanta haka ba kullum. Ta cigaba da halin nata surely someday zatayi regretting”
ba tare da ya sake cewa komi ba yafice se d’akin Zeezee knocking yake gbam! Gbam!
Gbam! “Waye haka b’allan k’ofan za’ayi?” tayi maganar tana b’oye wayarta cikin
pillow case.
“Bud’e k’ofan nace maras kunya kawai bud’e!” jin muryan Ibraheem ta mik’e aguje
ta bud’e k’ofar sannan ta soma rik’e cikinta “maza wuce kitchen, wace ke ana aikin
bud’a baki kina kwance a d’aki?”
“Ya cikina ne yake ciwo wayyo Allah!”
“Sekisha magani ai wuce kitchen nace.”
“Ya ai ina azumi kuma period d’ina ne yakeson zuwa wallahi bazan iya mik’ewa
dakyau ba.”
“Ni zaki raina wa hankali? Ko bakisan nasan date naki bane wuce nace kona miki
d’an banzan duka kan azumin naki.” Ganin ya kamata, ta mik’e da kyau.

“Ni shikenan kullum mutum baida hutu agidan nan ni wallahi na gaji ga bak’in
talauci gakuma uban-” ai bata k’are maganan ba ya bige k’aramin bakin nata tare da
fisgota a tsakar gida ya yasar da ita. Tuni ta soma kuka “maza wuce kitchen kije ki
karb’i Mama, Mama fito daga kitchen d’in cinta za’a zo ayi ne? Ki mik’e wallahi
kona zaneki” yayi maganan yana cire belt nasa, ganin haka ta mik’e tayi kitchen
d’in. Da kansa ya fito da Mama daga kitchen d’in sannan ya tsaya kansu yasa Yasmeen
tabata aiki in batayi ba kuma ya mauje ta. Haka tana kumbure-kumbure ta shiga yi
bayan ta gama yamata nuni da ledan fruits d’in kan tashiga gyara water melon da
paw-paw d’in, “ni wallahi nagaji ai ba engine ce niba ita Yasmeen me zatayi?”
“Magana kike?” Ya mata sending wani dirty look, miyau ta had’iye ta d’au ledan ta
wanke fruits d’in sannan ta shiga yimusu gyaran walaqanci. Bada jimawa ba Ibraheem
ya fita, ko cikakken two minutes ba’ayi ba Baba ya dawo nan Zeezee ta soma kukan
munafirci “yada kuka kuma K’anwata?”
“Ya Ibraheem ne wai sena gyara wannan duka kuma cikina ciyo yakemin.”
“Ita Yasmeen ina take?”
“Tana d’aki.”
“Yasmeen! Yasmeen!”
“Na’am” ta amsa tare da fitowa “sannu da zuwa Baba.”
“Yauwa sannu zoki karb’i Zeezee kinji batada lafiya.”
“Baba wallahi k’arya take lafiyanta lau.”
“Baba wall-” tuna tana azumi ta gyara zancen nata, “dagaske ba k’arya bane Baba
wayyo Allah na.”
“Yi ki karb’eta Mama na Yasmeen yi hak’uri.”
“Wallahi kinci darajan Baba ne maras kunya kawai” gwalo Zeezee tamata sannan ta
mik’e ta nufi d’akinta ta cigaba da chatting from where she stopped.

Shigan Baba d’aki Mama ta mai sannu da zuwa sannan tace, “wallahi Alhj ka rage
biyewa Zeezee, nad’au kayi hankali bayan ‘yan abubuwan datayi days back amman ashe
ba haka bane.”
“Kamar ya Hafsah? Yarinyan nan she is not used to rayuwan da take living yanzu
koshi ya isheta damuwa be kamata muna d’aura mata da namu akai ba.”
“To mud’in mun saba da wahalan ne? Ai kowa hak’uri yake.”
“Toh ai ku manya ne ita kuma yarinya ce, kuyi mata uzuri mana please! ko waya na
kasa canza mata abarta hakan nan.”
“Yayi kyau, Allah kyauta amman de don’t come and cry to me when the head has been
cut off already.”

I MISS MY OLD ACTIVE BLOG READERS😵😵

*© MIEMIEEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 18

*December, 2016*

On the 20th of Ramadhan Zeezee ta tashi ba azumi, dad’i kasheta tun on 15th
take jiran date nata daman, se aukin son shan azumi da kuma k’in yin ramako. Ko
wannan karan ana weeks to Ramadhan Mama tasa Ibraheem tsaye kanta sannan ta biya
azumin nata. Da safe around 10:30AM ta tashi, wani irin sanyi ake wane a Moscow,
Malam bahaushe yace jifa yazo dai-dai da zama. Dama bason wankan take ba jin wannan
sanyi ta kwaskware jikinta ta canza inner wears tasa sabon kaya sannan ta fito a
parlour taci karo da Mama ta gaisheta.
“Se yanzu kika ga daman tashin?”
“Eh sanyi ake shiyasa.”
“Yayi kyau kinga Baaba harta gama aikinta ta tafi, in kin gama breakfast nakin
seki wanke plates da duk abinda kikayi amfani dashi sannan ki share kitchen ki sake
mopping.”
“Wai duka aikin nan ni zanyi? Ita Baaban nan sekace aljana wai harta gama aiki
mschw ni wallahi dama canza me aiki akayi.”
“Nide na gaya miki ga Ya Ibraheem na gida, in kinason kanki sekiyi abinda na saki
kona basa izini ya zane min ke k’azama kawai, dubi k’wansa a idonki amman de bakiyi
wanka ba ko?”

“Nayi mana” tayi maganan tana sa k’ark’ashin skirt nata tana ciro k’wansan.
“K’arya kike bakiyi ba nasan ki ai.”
“Toh a wannan uban sanyin mutum ya hau wankan safe sekace meh zuwa office, se can
anjima zan yi” tana kaiwa nan ta zarce kitchen tashiga had’a indomie abinda ta iya.

*~ *~
Da Azahar bayan sanyi ya ragu rana yayi taking over Zeezee tayi wanka tasa ¾
leggings nata da vest ganin Ibraheem bai gida, bayan tagama had’a lunch nata nanma
indomie ta d’au tabarma ta baje tsakar gida da kanta a bud’e tana cin abincinta
bad’an kunya taje d’aki taci. Tafe side-by-side Mama da Baba suke tana mai rakiya,
tana ganin Zeezee tahau surutu “haba Zainab! Meh hakan? Ke bakida kunya ne ko sekin
gaya wa duniya yau baki yin azumi ne? Maza wuce d’akinki da Allah sakariya kawai.”
“A’a Hafsah me kuma yayi zafi haka da zagi? Me aciki dan yarinya nacin abinci a
tsakar gidan Babanta?”
“Aww ma tambaya kake? What if ko friends nasu Omar suka shigo fah? Zeyi fasali
ne?”
“A’a gaskiya banason irin wannan tak’uri wallahi, kibarta kurum! ci abincinki
Zeezee.”
“Da kyau daman ka saba ai” bata k’arisa mai rakiyan ba ta dawo ciki. Bayan fitan
Baba bada jimawa ba Ibraheem da friends nasa about 4 of them suka shigo gatsau!
Kasancewar shine a gaba yana ganinta yamata ido kan tayi sauri ta fice aiko data
gano haka ta juya mai kai ta cigaba da cin abincinta. Yace da friends nasan su juya
kuma kunya yakeji haka suka zo wucewa suna kallon Zeezee ko ajikinta ba kayan
arziki ne sanye da ita ba, bama wannan ba ace agaban friends na yayanta tana cin
abinci a azumi. Bayan da tagama tayi dukkan aikin da Mama tasata da cuwa-cuwa kamar
yadda ta saba. Koda aka soma aikin bud’a baki yau tak’i sa hannu acewarta ai ba
azumi take dashi ba, saboda haka ba aikin da zatayi shide Ibraheem jira yake Baba
ya fita yayi mata d’ankaren duka.

★*★*★*★
Life moved on, abubuwa da dama sun gudana ciki harda samun bud’i kad’an kad’an
da Baba ya soma samu, abu fa kamar wasa arziki se dawowa yake fiye dana da, kowa se
murna yake a gidan suna cigaba da addu’a suna kuma yiwa Allah godiya babu kamar
Mama data d’au yanzu wai Baba yayi hankali, kodan abubuwan da suka faru a baya yaci
ace Baba ya koyi darasi yanzu ya dena biyewa Zeezee. Ashe de kam abu na cikin duhu
ne! Sabuwar ipad da waya k’irar iphone 6s ya sai wa Zeezee, ba ita kad’ai ba har
Yasmeen sannan a babban sallah yayi ma kowa d’inki kala bakwai-bakwai Zeezee kam
kala goma akayi mata wayyo ita dad’i kasheta. 2 weeks back sukayi resuming school
tana Ss 2 kenan yanzu with fifteen (15) years old. Ana takan zama budurwa se pallin
tsiya, sede fa har yanzu hankalinta na akan Ammar bawani paying attention d’in
kirkin da take a school.

Bayan Sallah da sati d’aya Mariam ta sake haihuwa tasamu ‘yarta Hafsah takwaran
Mama anyi hidiman suna lau, Allah shi raya Mama.

*~ *~ Saturday morning.
Zeezee as well as her other siblings duk suna gida, Omar ma recently ya gama
service ya shiga neman aiki.

Knocking Mama tayi bisa k’ofan d’akin Zeezee sannan ta shiga da sauri-sauri ta
b’oye wayarta ta soma faking bacci.
“Wai bacci kike? Tashi zaku gidan Kaka yau (Maman Babansu) kafin nan tashi mu
zab’i kad’an daga cikin kayakin ki zaku d’an bawa yaran da suke zama da ita kunce,
Yasmeen harta bada nata set biyar saura ke.” Zumbur Zeezee ta mik’e zaune, “meneh?
Bada kuncen kaya? Ni wallahi bazan bada komi ba shikenan abi asawa mutum ido kan
kayakinsa gaskiya a’a.”
“Kamar ya a’a Zeezee? Ke bakisan aikin lada bane, in Allah ya hore maka se ai ka
taimaki na k’asa da kai ke kanki bakisan yawan adadin kayakinki ba, ko wanda
Babanku ya d’inka miki recently bayan Sallah ma kd’ai sun isheki amman kice bazaki
bada kuncen kaya ba? Maza tashi ki zab’a min guda biyar nace karki bari raina ya
b’aci.”
“Ni wallahi banaso” tayi stating tana shure k’afafunta kan gadon.
“Zan kira Ibraheem fah!” Jin haka ta mik’e ta bud’e wardrobe natan, wasu
kod’ad’d’un kayakinta guda uku tun tana Jss3 tafito dasu ta ajiye kan gadon “gasu
nan ai sunyi ko?”
“Tsumman goge tiles nace kibada ko kayan sawa?” Bankad’eta Mama tayi ta ciro wasu
sabin kayakinta biyu sannan ta had’a da wanda suka d’an sha ruwa kad’an guda uku.
Ihu Zeezee ta k’urma tashiga k’wala wa Baba kira, unfortunately bayi gida haka
tayita kukanta har ta godewa Allah. Tana ganin Yasmeen nata shiri ita ko wankan ma
batai ba, seda sukazo tafiya Ibraheem ya tambayeta, “kefa bazaki bane?”

“Bazan jeba me ze kaini gidan Kaka ana zaman lafiya, ace ma mutuwa tayi mana
amman tana k’alau sena hau zuwa gidanta adafa wa mutane tuwo a kuma sasu cin dole
kuje Allah ya kare.”
“Mu tafi Yasmeen bar fitsararriyar nan anan.” Maman data d’au duka yaran suka
fita tana fitowa daga d’aki itama tayi shirinta zata fita kawai taga Zeezee “ya
haka? Baki bisu bane ke?”
“Meh ruwanki toh? Kin kama kin kyautar min da kayaki na” nan ta mik’e tazo shiga
Mama ta d’aka mata dundi a baya “shegiya fitsararriya kawai”
“Wallahi Baba ya dawo sena gaya mai kince min shegiya” tayi stating in a crying
tone, kota kanta Mama batai ba ta fice. Wayarta dake cikin pillow case ne ya soma
ruri, tana dubawa taga Ammar hesitantly ta d’aga, “halo Sweetheart.”
“Yes Pretty are you free?”
“Yes I am wani abu ne?”
“Ki shirya zanzo in d’auke ki we are going somewhere.”
“Zaka zo kuma Handsome? Ko ka manta inada brothers ne?”
“Holy sh*t suna gida kuma ko?”
“Actually no duk sun fita am home alone but they can come back at any moment.”
“Kawai de kice you are not interested shikenan, I’ll go look for another date,
hanging out fa za’ayi Ss2 Vs Ss3 kema kinsan you need to be there.”
“Haba Baby taya zakace am not interested wallahi I am naji zan shirya yanzu
sekazo.”
“Yauwa Sexy, dress hottie kinji?”
“Yes Boyfriend, I love you.”
“I love you too Babe” yayi hanging.

Tana ajiye wayan ta shiga cin faracunta she’s all confused batasan me zatayi
ba, what if lokacin da yazo Ibraheem ko Baba suke dawowa su kamata fah? Kai ta
kad’a amman inhar banje ba Ammar will be angry infact ze iya cewa ma lets break up
cause mata rushing akansa suke. Bayi ta fad’a tayi wanka a gurguje tayi applying
medium makeup sannan ta ciro wani red strapless gown tasa ta d’aura kanta me kyau
ta feffeshe da turare. In 3 minutes time Ammar ya kirata bayan ta rufo ko ina
agidan ta fita exactly kalan motan Ya Ibraheem Ammar yake hawa, da wuri-wuri ta
k’arisa gun motan, wani irin mayen kallo Ammar ke binta dashi musamman dayaga d’an
cleavage nata awaje. Ta bud’e motar dai-dai zata shiga kenan sega motan Ya Ibraheem
wane daga sama batasan alokacinda ta saki fitsari kad’an a panties nata ba. B’ari
ta shiga yi tama rasa nayi “Ammar ka fito! ka fito please” alokacin da Ammar ya
fito daga motar har Ya Ibraheem yayi parking motarsa shima yafito yana nufan gunda
suke in a swaying motion tace, “koya tambayeka waye kai kace you are my classmate.”
“Sannu da dawowa Ya” tayi stating in a cracky voice hannunta se had’a gumi suke
ayayinda zuciyarta keta harb’awa tana addu’a Allah ya sa karya mata abin kunya a
idon Ammar.
“Ina kwana?” Ammar ya gaishesa, ko amsawa beyi ba yace in a serious tone, “ina
zakije da wannan shirin? Sannan kuma waye wannan?”
“Ya ba inda zani, classmate d’ina ne yazo tambaya na materials da zai siyo mana
na physics practicals namu ne” ta k’are maganan tana b’ari.
“Nace waye wannan kuma ina zakije da wannan d’an iskan shirin?!”
“Zeezee I’ll get going se mun had’u Monday at school zanje na siyo materials
d’in” Ammar na kaiwa nan yaja motarsa ya tafi.

“Saurayi kika fara kawowa gida ko?” Kafin ta hankara ya kwad’a mata mari a
fuska, ihu tasa wajen tana kuka ahaka ya jawota ciki “ke ba wai ‘yar iska ba, zaki
gane kuran ki agidan nan” belt ya zare ya hau dukanta seda yamata lik’is sannan
yace, “nan gaba ko kwatancen gidanku bazaki wa ‘yan iskan yaran ba balle suce zasu
zo d’aukanki.” Da k’yar ta mik’e zata nufi d’aki tana kuka ya dakatar da ita “where
do you think you are going? Haka da kayan Baba zezo ya sameki yasan abinda kikeyi.”
“Ya dan Allah ka rufa min asiri wallahi na tuba bazan sake ba.”
“Karki b’ata miyan bakinki kina ban hak’uri saboda ba jinki zanba.”
“Wayyo Allah na! dan Allah kayi hak’uri wallahi na tuba bazan k’ara ba.” Ba kalan
had’a shi da Allan da batai ba yak’i hak’ura. Ana cikin haka Mama ta dawo nan ya
irga mata komi sam bata sha mamaki ba, saboda tasan wannan ne dalilin dayasa tace
bazata gidan Kaka ba kenan, not long enough Baba ya dawo shima Ibraheem ya irga mai
komi sosai yasha mamaki da har baison believeling abinda Zeezee tayi. Kuka tahau
musu a wajen tana rantsuwa akan k’arya ita sam wallahi ba saurayinta bane classmate
nata ne.

“Inhar classmate nakin ne meya zo yi?” Mama ta tambayeta, shi Ibraheem dan
haushi ma barin gun yayi.
“Amsan list na materials da ze siya mana na physics practicals.”
“Shi ne kikayi wannan shigan?”
“Toh ba nayi wanka bane zan d’au hoto yacemin gashi yazo na fito.”
“Kai! Yarinyan nan k’arya take wallahi, saurayinta ne, inada tabbacin kina sane
da zuwansa yasa kika k’i bin yayyun naki gidan Kaka.”
“A’a wallahi ba haka bane, Baba Allah ba k’arya nake ba, ba saurayi na bane.”
“Na yarda dake K’anwata ba saurayi sekin gama secondary ba?”
“Eh Baba.”
“Aww ka yarda da k’aryan data sharara ma d’in kenan? Humm wallahi Alhj ka cigaba
da take gaskiya, ka kuma guji ranan da yarinyan nan zata ma abin kunya” tana kaiwa
nan ta fice itama. “Zeezee kifad’an gaskiya shin dagaske saurayi ne yazo gunki?”
“Wallahi a’a Baba ai bazan ma k’arya ba.”
“Shikenan jeki huta yi hak’uri kinji? Zanma Ibraheem magana.”
“Bashi kad’ai ba har Mama d’azu ta d’ibe min kayakina wai za’a kai gidan Kaka.”
“Karki damu gobe Omar ze rakaki shago na ki d’au turame biyar masu kyau abinki.”
“Toh Baba nagode.”***

Haka nan Baba ya cigaba da d’aure wa Zeezee gindi agidan komi tayi koda kuwa
yasan ba dai-dai bane bayi tsawata mata ga kuma yadda yake spending money lavishly
akanta, bada jimawa ba akayi auren Yasmeen, ansha budiri sosai barin ma Zeezee dake
nan wane amarya itama dan yadda tasha gayu. Bayan biki aka kai amarya Yasmeen
Kaduna.

_Wednesday morning 11:30AM_


Kowani d’alibi na a class yana d’aukan lesson banda Zeezee da Ammar da suka keb’e
a wani empty class suna hira. Ana cikin haka wani teacher yazo wucewa ya kamasu. Ai
kuwa Zeezee ta tsure tarasa nayi dan inhar aka kira Baba aka sanar dashi nata ya
k’are. “What are you two doing here while classes are taking place?” Ya tambayesu
both in an angry tone. Kame-kame suka shigayi both of them har teacher’n ya zagayo
ya shiga class d’in “oya follow me to my office now!” Zeezee najin haka tayi ma
Ammar ido se kawai ta yanki jiki ta fad’i k’asa ta soma wani irin mahaukacin tari
da wani d’an banzan nishi wane ana cirewa kafiri rai, ganin haka Ammar da teacher’n
sukayi kanta “whats happening to her?” Yayi saurin tambaya.
“That was how I found her also Sir, I think she’s athmatic.” Ammar yayi stating
yana k’ok’arin d’ago ta daga k’asa. “Is that the reason why you two are here
alone?”
“Yyes Sir, I was passing by and then saw her unconcious that was why I rushed
in.”
“Hurry lets take her to the sick bay” haka ya kinkimi Zeezee zuwa bay aka kwantar
da ita har a yanzu bata bar tarin munafircin ba “is she asthmatic?” Nurse d’in tayi
saurin tambaya “yes” Ammar ya bada amsa. Inhaler sabuwa ta b’allo ta bata, zugi
biyu Zeezee tayi ta soma daidaita numfashinta kaman dagaske, bayan d’an hutawan da
tayi a bay ta koma class. Su Lubiee se tambayarta suke ko lafiya nan ta labarta
masu komi sukayi ta dariya.

_Closing hours_
Yau Baba da kansa yazo d’aukan Zeezee, dai-dai ta shiga mota kenan teacher’n
d’azun ya fito ganin Baba da prado jeep ya nufi motan nasu ya gaishesa, zuciyan
Zeezee se harb’awa yake Allah sa karya cewa Baba ya kamata dana miji su kad’ai a
class, kawai seji tayi yana cewa Baba akai ta asibiti d’azu asthman ta ya tashi.

Suprisingly Baba ya tambaya dama Zeezee nada asthma ne? Bayan ya sallami
teacher’n da N5,000 ya tafi. “K’anwata kinada asthma ne dama?”
“Wallahi Baba kawai yau ina zaune naji nishi na nawani sama-sama, chest d’ina na
tightning nayita attishawa kuma amman da sauk’i yanzu.”
“Kaman ya da sauk’i? Bari mu wuce asibiti Dr. Zakir ya duba ki, sannu ko?” Anzo
gurin Zeezee tace a ranta. “Baba cikina na min ciwo inason using bathroom mubari ko
gobe muje, wayyo!”
“Toh Allah kaimu goben sannu ko, amman ko inhaler ne asai miki ai ko?”
“Eh Baba” pharmacy suka wuce ya sai mata inhaler sannan sukayi gida. Haka kullum
Zeezee ke raina wa Baba hankali tak’i yarda aje asibiti daga k’arshe kiran Dr.
Zakir akayi aka irga masa symptoms na k’aryan da Zeezee keyi nan ya tabbatar musu
da eh asthman ne, magunguna yayi texting wa Baba aka sai mata. Itade Mama kallonsu
kawai take sabida tasan k’arya Zeezee ke. Tun daga ranan Zeezee ta samu sara ba
aikin da take agidan in Baaba batazo ba sede in Mama tayi shara da kanta danko
fakewa Zeezee ke tace asthman ta ze tashi idan tayi shara Baba ko ya d’aure mata
gindi as always.

_Few days later..._


Kwanan Baaba uku batazo ba kasancewar batada lafiya, through out Mama ke shara
Zeezee sede ta mata sannu da aiki. “Zeezee!” Mama ta kirata kan su wuce su share
mata d’aki dan kuwa rabon d’akin Zeezee da shara tun da Baaba tabar zuwa, “shiga mu
share miki d’akin mak’aryaciya kawai. Kalli wai wannan d’akin budurwa ko kan
gadonki baki iya gyarawa ba maza kakkab’e ki gyara” tana tura baki ta jajja ending
d’in ta tuttusa “gashi na gama.”
“Ahakan ne kin gyara? Kifa sani ‘ya mace ce ke kuma dole wataran zakiyi aure kina
gani ai ba Yasmeen ba Mariam yanzu next kece.”
“Ai zan koya in na gama secondary school.”
“Mschww!” Hannu tasa ta d’aga katifan ma gabad’aya dan share k’ark’ashin gadon.
Ai kawai sega maguna k’ark’ashin gadon Zeezee tamkar pharmacy, maguna barkace.
“Laaa’ila! Meh wannan? Drugs kike siyarwa?”
“Nikam ki sauk’e min katifa na zan share d’akin da kaina.”
“Ai dama nasani ba asthman da kike da, kuma wallahi a kunnen Babanku, ‘yar banza
kawai kullum kisa ayita siyan maki magani masu tsada baki sha?”
“Ina sha mana wannan fa ba maganin asthman bane na zazzab’in dana tab’a yi ne.”
“Allah yasa na haukan da kika tab’ayi ne.”
“Toh ki kawo tsinstiyan zan share amman karki gayawa Baba please Mama.”
“Mschww!” yasar da tsintsiyan tayi ta fice, Zeezee da kanta ta shiga share
d’akinta tana cikinyi Baba ya dawo ya tarar da ita “ya da haka? Mesa zakiyi shara
bayan bakida lafiya, Hafsah! Ban hanaki sa yarinyan nan shara ba.”
“A’a Baba ba ita ta sani ba kuma ma ai sharan kad’an ne karka damu I can manage,
sannu da zuwa.”
“Are you sure baze dameki ba? Kinsan fa bakida lafiya.”
“Eh karka damu Baba.”

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 19

*December, 2016*

Washegari bayan Ibraheem ya sauk’e Zeezee a school ta tuna da mantuwan TD


assignment nata datayi a gida, ga teacher’n mugu ne baya sauraron excuses. Form
teacher’nsu tanema tamai magana ya had’ata da Baba a waya tamai explaining komi.
Suna cikin yin second period nasu Ibraheem yashigo class nasu bayan excusing kansa
da yayi. Sanye yake da T shirt me long sleeve arms da not too tight pencil
trousers, yayi matuk’ar yin kyau ai tuni ‘yan matan class nasu Zeezee sukayi
falling masa cikin k’asaita kamar yadda ya saba gudanar da ayyukansa ya k’arisa
cikin class d’in suka gaisa da malamin sannan ya bawa Zeezee drawing natan yayi
ficewarsa. Ai ana fita break ‘yan matan class nasu Zeezee da wanda suke mata magana
da wanda basu matan sukayi layi a seat nata “wai meh haka? Ku matsamin mana ko
bakuga an fita break bane?” Zeezee tayi stating angrily.
“Zeezee don’t tell me that Hottie is your brother?!” Matan class nasun sukayi
exclaiming almost at thesame time.
“Ba brother na bane naku ne ai aikin banza, matsa mun nikam.”
“Please ki tsaya muyi magana” cewar Lieemarh “wallahi yayi min nikam omg! His
skin!”
“Skin ja kaman tsuliyan birin? Lallai kam matsa min mana ku!”

“Dan Allah meh IG handle nasa Zeezee?” Mjay ta tambaya.


“Wai tsaya son Ya Ibraheem dukkanin kun nan kuke wai?” Tayi pointing nasu da
yatsa.
“Eh ni wallahi yamin.” said Hajara. Dariyan rainin hankali Zeezee ta saki “Lubiee
kinaji wai Ya Ibraheem suke so, wai lallai kam kun tashi a aiki excuse me now, will
you?” Nan suka matsa mata suna fad’in “kije ki dawo ma tona.” Ta kai da bakin k’ofa
kenan mortal enemy’nta a class d’in wata Sumayya wanda Babanta ke mugun ji da kud’i
har mota ya sai mata. Ko kad’an bata wa mutane magana dan haka basu shiri da Zeezee
dan itama ‘yar iskan kanta ce. “Zeezee we need to talk please” tace da Zeezee.
“Sumayya ko? Aww! Dama kina wa mutane magana? LOL toh I aiint got your time
matsa min.”
“Please Zeezee lets keep our differences aside wallahi ko me kikeso zan miki just
listen to me.”
“You have two minutes to do so.”
“Its about the guy that came earlier waye shi?”
“Wanne? Be precise please kina b’ata min time” Zeezee tayi maganan as if bata
gane Ibraheem, Sumayya ke nufi ba.
“The tall, fair and good looking one daya kawo miki TD drawing naki.”
“Aww you mean my handsome brother, what about him?”
“Nothing really you mean he is your brother?” Ta tambaya kinda shocked.

“Ban kai na zama sister’sa bane kome kike wani zaro idanun nan naki waje haka.”
“No ba haka bane, abin ne yazo min da sauk’i I don’t need to suffer.”
“Like I don’t get you kuma kina b’ata min lokaci.”
“My apologies, dama bawani abu bane digits nasa nake buk’ata.” Dariya Zeezee da
Lubiee sukasa harda tafewa, “you mean digits na Ya Ibraheem?”
“Owww what a lovely name eh na Ya Ibraheem d’in.”
“Lallai ko kinyi kad’an na baki digits nasa, dana baki gomma na bawa su Salmah.”
“Please Zeezee lets talk business ki fad’an ko meh kikeso zan baki inhar zaki
bani digits nasa in return.”
“Like money?” Tayi maganar tana lasan lips nata.
“Eh wallahi ko nawa kikeso.”
“Interesting Lubiee deal ya taso, kibari yanzu zanje shop in na dawo we’ll
discuss it.”
“Okay am grateful Ameenah lets go” tace da k’awarta suka fice.

*~ *~
Zeezee na dawowa daga shop ta tara ‘yan class nasu da sukayi falling wa Ibraheem
gu d’aya sannan tayi clearing throat nata ta soma da cewa, “so all of you here have
fallen for my handsome brother kuma kunason digits nasa ko? Cikin ku takwas (8)
d’innan mutum d’aya zan baiwa.”
“Zeezee ni please” cewar, Ashnur da Xarah.
“Ai ba daganan take ba girls, sayar maku da digits nasan zanyi.”
“Ki fad’i ko nawa ne am ready to pay” Sumayya tayi stating arrogantly.
“Good I like that, so out of the eleven digits each number contains, kowani digit
d’aya N500 altogether making five thousand five hundred (N5,500) kenan who will
pay?” Ai kap suka d’aga hannu dake duk ‘ya‘yan masu kud’i ne ‘yan k’arya kuma.
Ganin haka Zeezee ta k’ara deal d’in zuwa one thousand (1,000) nan ma kusan duka
sun d’aga hannu haka tayita raina musu wayo har suka iso two thousand inda Sumayya
kad’ai ta d’aga hannu.

“Tam Sumayya kece winner ke zan bawa number’n Ya Ibraheem that is after I get
to see my tewnty-two (22) thousand.”
“Toh ai kinsan bada kud’i dayawa nake zuwa school ba but trust me gobe zan kawo
miki kiban contact d’in.”
“Uh-uh Babe, I don’t play that game, pay before service kina bani kud’i na ina
baki digits nasa” haka Sumayya ta hak’ura a washegari ta taho da 22k pil cikin
envelope ta danka wa Zeezee ita gata shegiya ‘yar gidan minister nan Zeezee ta bata
number’n Ibraheem not minding the consequences.

_Da La’asr._
Baba na zaune a parlour da friends nasa suna hira, Zeezee ta shigo bako sallama
bale gaisuwa ko sannu, wajen Baba ta nufa direct ta tsaya akansa “ya akayi
K’anwata, lafiya?” Kai ta kad’a nufin a’a.
“Toh baki gaishe da friends d’ina ba.”
“Ina wuninku Uncles?”
“Lafiya Zeezeen Baba” suka amsa in unison almost about 5 of them.
“Yauwa to meneh neh?”
“Baba pad d’ina ya k’are kabani kud’i na sai sabo.” Kunya sosai Baba yaji tamkar
ya nitse k’asa, dama seda Mama ta gaya masa yayi a hankali wataran se Zeezee tamai
abin kunya amman yak’i jinta ya mata kunnen shegu. Ga irinta ai yau!
Bending nata yayi dab da kunnenta yace, “haba K’anwata bazaki jira se friends
nawan sun tafi ba tukun?”
“Toh ai zanyi staining kaya na.” wani abin kunyan again! Cike da mamaki friends
nasan suke kallon Zeezee “excuse me please” cewar Baba tare da jan hannun Zeezee
izuwa d’akin Mama.
Koda Mama tagansu bata ce komi ba se kallonsu kawai take, “haba Zeezee! Meh
amfanin hakan? Bakiga inada bak’i bane?”
“Ya meya faru haka?” Mama tayi speaking up finally.
“Muna zaune da friends d’ina taje wai na bata kud’i ta sai pad.”
“Ahap! Ban fad’a maka ba dama ka guji rana kamar ta yau? Tunda Allah yayi ina
raye duk lokacin da take buk’atan abubuwa haka tazo ta sameni tamin magana sam kace
kai ba haka ba, duk abinda take buk’ata ta sameka ta maka magana, kad’an ka gani ai
wataran cewa zatayi kasa mata inde Zeezee ne expect more wallahi.”
“Toh ya isa haka! Ni nake gama wallahi bakinki yake kama mu, kullum sede bakiyi
magana ba se abin ta faru, dan Allah daga yau inkin san bazaki fad’i alkhairi ba
kija bakinki kiyi shiru.”
“Kanku akeji kai da ‘yar naka da bata da kunya.” Kuka Zeezee tasa wai Mama tace
mata batada kunya da k’yar Baba ya samu tayi shiru “amman kema karki sake tambaya
na stuffs haka in public kinji?”
“Koda zanyi staining kaya na?”
“A’a ni bance haka ba what I mean is nan gaba in na cikin mutane ki kirani gefe
kinji?”
“Toh naji.”
“Yauwa K’anwata Allah miki albarka” yayi maganan tare da zaro 5k daga wallet
nasa, “ungo toh in cenji ya rage ki d’auka na baki.”
“Toh nagode” tana kaiwa nan ta fice.
“Hmm kaide inba kuka Zeezee ta saka da hawaye ba bazaka tab’a yin hankali ka soma
ganin laifinta ba.”
“Kanka akeji” yana kaiwa nan ya bar mata d’akin.

_8:45PM_
Ibraheem na mik’e kan gadon d’akinsa yasa earpiece a kunne yana d’anjin beats,
kira daga new number ya katse mai waqansa bayan daya duba yaga fa besan lamban ba
seya k’i d’agawa se a karo na biyu “Halo” Sumayya tace cikin wata karuwar murya
sekace ba ‘yar 16 years ba.
“Yes Hello” yayi speaking finally.
“Uhm Ibraheem ne please?”
“Yes shine.”
“Ohh thanks Gee! Am Sumayya by the way, I know baka gane wacece ba ko nace
bakasan wacece bama thats why I need to introduce myself.” Har anan sauraronta
kawai Ibraheem yake totally specheelss, bayan data gama bayanin kantan yaji ma ashe
yarinya ce sa’ar k’anwarsa na chan baya-baya.
“So little baby dake a ina kika samu digits d’ina?” ya tambayeta finally.
“It doesn’t matter ni kawai kabani dama na fad’a maka meke tattarre dani.”
Murmusawa yayi ya sake mik’ewa kan gadon “meke tattare da ke ‘yar yarinya?”
“Right from the moment my eyes decended akan breathtaking face and body naka
heart d’ina yayi skyrocketing, I don’t know how to explain it to you but the truth
is I’ve fallen for you and I love you.”

“Woah! You’ve got such confidence, kafin nan answer me aina kika samu digits
d’ina Zeezee ce ta baki?”
“A’a ba ita bace.”
“Don’t lie to me kikayi hakan you’ll just ruin yourself and make me hate you.”
“Yes itace, but it does-” bata kaida idda maganan ba yayi hanging wayan tare da
mik’ewa a fusace yaja belt nasa dake rataye jikin wardrobe yabar d’akin sena Zeezee
gbam! gbam! gbam! Yayi knocking tana cikin irgen kud’ad’d’enta tace, “ina zuwa” da
sauri ta miyar tasa cikin pillow case nata sannan ta mik’e ta bud’e k’ofan. “Ya
lafiya?” Idanunta na kaiga belt dake nannad’e a hannunsa ta shiga b’ari kafin tayi
wani k’wararren motsi ya bankad’eta tare da sa kai cikin d’akin “wayyo Allah Baba
na wallahi ze kasheni!” tasa ihu, kota kanta beyi ba yayi locking k’ofan d’akin.
“What did you do at school today?”
“Bbb.. Babu.”
“I said what did you do today?”
“Ya dan Allah kayi hak’uri” d’aga belt d’in yayi ya shod’eta dashi nace, “what
did you do at school today?” Cikin sautin kuka tace, “nn... na bawa Sumayya
number’nka amman dan Allah kayi hak’uri wallahi sharrin shed’an ne it’ll never
happen again.”
“Meya kaiki bata number na? Sa’an kine ni? Ko bakida hankali ne?”
“Wallahi ina dashi Ya dan Allah kayi hak’uri na tuba” sake kai mata wani dukan
yayi “wayyo Allah Baba na!” sede duk ihun da take Baba bai gida bale ya ceto ta.
“Zan zane ki yadda duk ‘yan class naku suka ganki gobe se sun tambayi meya faru.
bayan nan kuma ko aljannah akace za’a baki kibada number na bazaki bayar ba.”
“Wayyo Allah Baba na Ya dan darajan Allah kay- wayyo Allah na!” Duka yayi mata na
k’in k’ari, Mama najin sautin kukanta tun daga d’akinta amman kota damu ta duba ta
saboda tasan dole laifi tayi ma Ibraheem.

Seda Zeezee ta shiga yin amai ya k’yaleta yana huci, “kad’an kika gani ke bawai
rashin kunya da fitsara ba? Sekece a kanki akayi wahayinsa ba? I’ll correct your
sitting settings, nan gaba zaki sake bada number na wa ‘yan iskan yaran class nakun
stupid kawai” yana kaiwa nan yabar mata d’akin. Kuka sosai Zeezee keyi abin tausayi
jikinta du yayi shati yayi ja yau ko Allah ya isan ma babu, anan bacci b’arowo ya
saceta. Se Asubah da Mama tazo tashinta shirin school ta tashi jikin nata du yayi
tsami. Bin jikin nata tayi da kallo sannan taja doguwar tsuka, “mugu kawai Allah ze
sak’a min ni makarantar ma na fasa zuwa, haka kawai bazan jeba su Sumayya su san
duka Ya yamin ba” tana kaiwa nan ta ja comforter ta cigaba da bacci.

6:50AM Ibraheem ya gama shiri yau, 5 minutes to 7pm ya lek’a ko Zeezee tagama
shirin itama, gani yayi ba kowa a parlour don haka ya tambayi Mama kota ga Zeezee.
“Ni ban ganta ba, ga can breakfast nata Yasmeen ta had’a mata bata fito taci ba. Ma
meya had’aku jiya naji kake dukanta?”
“Zagin Fateemah tayi.” yayi mata k’arya dan ma kunya yakeji ace mates na Zeezee
suna son sa.
“Zagi! Toh Allah shirya Zeezee kaje ka dubata a d’aki karta saka latti.”
“Toh Baba fah?”
“Yayi tafiya sammako yayi tun 6.”
“Ohh Allah dawo dashi lafiya toh” da ‘ameen’ da Mama tace ya fice zuwa d’akin
Zeezee. Knocking yayi sau biyu “wayene?” ta tambaya sleepishly.
“K’aniyanki ne bazaki fito bane? Ko sena tafi na barki?”
“Eh ka tafi ni bazan je school d’inba” k’ofan ya bud’e ya sameta nannad’e cikin
bargo tana bacci. “Meh haka?”
“Nace bazan jeba ka tafi” tayi maganan tana juya mai baya.
“Dalili?”
“Ka kama ka faffasa min jikin ne zanje makaranta wallahi Allah ze sak’a min.”
“Oya maza tashi ki shirya ina jiranki, ji maganan banza sabida jikin ki ya tashi
shine bazaki school ba?”
“Toh so kake naje su Lubiee sumin dariya.”
“Eh susan akwai me discipline naki a gida tashi nace! don’t let me repeat
myself.” K’afafunta tashiga shurewa kan gadon, “ai ba kai kake biya min school fees
ba yanzu ni wallahi bazan jeba” ganin ya soma dosan inda taken ta mik’e a guje “oya
wuce kiyi brushing ki shirya wankan me sekin dawo kiyi dan kuwa bazaki sani latti
ba.”
“Toh an tab’a zuwa school ba wanka ne?”
“I don’t care kinsan da hakan kika k’i yi tun d’azu? Oya you have 10 minutes ki
gama shiri, wallahi na dawo baki gama ba banga me hanani dukan ki ba.” Yana kaiwa
nan ya fice “mugu kawai da wani jan fuska sekace k’osai wallahi akan yaranka da
wannan Fateeman zan rama wannan mugunta duka.” Cikin 7 minutes ta gama kwaskware
jikinta tasa uniform, kasancewar skirt natan d’an guntu iya saman gwiwarta ne yasa
shatin belt na Ibraheem duk ya fiffito yadda da angani ansan dukanta akayi. “Oh!
Damn it!” tayi maganan tana bin legs natan da kallo, “yanzu haka zanje su Lubiee su
gani su san duka na akayi? What if Ammar ya tambayeni ina nasamu wannan marks da
bruises fa? Definately zesan duka na akayi.” Drawer’n socks nata tayi pulling ta
shiga neman white leggings nata don rufe k’afafun nata dashi.
Ba inda bata duba ba amman bata samu ba. Ana cikin haka Ibraheem ya shigo “ina
kike?” A zatonsa ma bata shirya ba ganin ta da uniform yace, “Allah ya soki oya
mutafi.”
“Toh ka tsaya mana na nemi leggings d’ina.”
“Dama kina zuwa da leggings ne, ba anklet socks kike sawa ba? Kina fa b’atamin
lokaci.”
“Ai dama bance ka jirani ba” tayi maganan k’asa-k’asa. Atlast ta samu leggings
d’in tasa sannan ta d’an kimtsa face nata suka fito. Dining ta nufa yayi saurin
tambayarta “ya haka? Wai karyawa zakiyi ina jiranki?”
“Eh mana ba kai kace sena jeba.”
“Bakida hankali, will you get up my friend!”
“Baba! Baba! Kaga Ya wai bazan karya ba zan tafi school” tayi maganan at the peak
of her voice.
“Thanks goodness Baba bai gida oya mik’e nace kinsan kina jin yuwa kika k’i
fitowa ina? Haka da yunwan zaki school” kaman zatayi kuka tabi bayanshi suka shiga
mota har suka isa school Zeezee na gun-guni. D’ari biyu ya wulla mata as break
money ai atapir tace bazata karb’a ba, ya hanata breakfast ya had’ata da d’ari
biyu?! Impossible tense. Ganin zata tara mai jama’a ya bata N500 sannan ta fice
bako godiya. Tana isa class aka soma mata kallon bakwai saura kwata, “ya da
leggings yau?”Asma’u ta tambaya.
“Meya miki zafi? Mind your damn business” waje ta nema ta zauna har anan kallonta
Lubiee ke, “seriously Babe mesa kika sa leggings yau?”
“Sanyi nakeji” tayi mata k’arya.

Not long enough Sumayya da clique nata suka shigo, bayan tayi dropping jakarta
ta nufi seat na Zeezee dake ta watsa mata harara tun shigowarta. Kafin tayi magana
Zeezee tace, Meh, Meh? kuma yau? Leave me alone please.”
“Oh common Darling don’t talk like that, actually we’ve got a major problem tun
jiya nake ta trying line na Ibraheem but yak’i picking atlast ma switching off
phone nasan yayi.”
“And? Seki d’au na Annabawa kiyi hak’uri or what do you expect me to do?”
“To make me way ofcourse!”
“LOL make you way?” Tayi maganan tana dariya “just listen to yourself, you know
right I can’t force him into loving you right? Win his heart is all you’ve got to
do. Now excuse me.” with a nod Sumayya tabar gun. Koda aka fita break kuwa k’in
fita Zeezee tayi, da Ammar ya tura a kirata nanma k’in zuwa tayi hakan ba k’aramin
b’ata mai rai yayi ba. The whole him?! Dama already yana da side chicks nasa. Kawai
Zeezee ji tayi ai Ammar yakai Fiddy school kiosk ya sai mata almost half of the
shop, Zeezee deh was left dumbfounded a wajen, Allah Allah kawai take taje gida
suyita ta k’ar.

Koda aka tashi seda ta bari aka d’an wawwatse sannan ta fito Allah ya sota tana
fita Ibraheem na zuwa. Suna isa gida ta d’au wayarta ta kira Ammar telling him what
he did earlier sucks how could he? Ai kuwa yaro ya haura mata sama a dalilin me
zece tazo tace bazata zoba? Itama dama gwana ce ta fannin tashin hankali haka suka
k’are da zage-zage. Kaca-kaca sukayi, sukayi breaking up a wajen tace masa they are
done sannan tayi hanging akansa exasperating him the more.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 20

*December, 2016*
★*★*★*★
Few months later...
Ba laifi yanzu Zeezee ta d’an maida hankali gun karatu tunda batada wani
distraction yanzu dan tun ranan da sukayi exchanging words da Ammar word be sake
had’a ta da shi ba, ko sun had’u a school sede suyi burning face suyi passing juna
dama seda Lubiee ta gaya mata ta guji Ammar d’an iskan guy ne tak’i. Preparation na
3rd term exams nasu suka shiga yi which will take place in a week time! Biology
teacher’n su na fita Zeezee ta koma seat nata da Lubiee ta zaro wayan Lubiee suna
hira tana kallon pictures. Kawai coming across the most breath takingly gorgeous
guy ever tayi, shi gashi nan kaman balarabe dan kyau, komi a fuskansa beauty off
neh I don’t have to go in details! sede ba fari bane skin nasa na nan wane na
buzaye ya had’e iya had’ewa ga kuma swags uwa uba. Rikicewa Zeezee tayi gun
gabad’aya har tana manta yadda ake breathing. “O my GEE! Lubiee don’t tell me
wannan guy is for real.”
“Wai waye kike wannan exageration haka, muga” Tayi maganan tana kar6e wayan “aww
wai Adeel?”
“Don’t tell me thats his name.”
”It sure is.” Chinyan Lubiee Zeezee ta buga friendrily “don’t tell me kinsan sa
please.”
“LOL nasan shi mana, brother’n sister in-law na ne (k’anin matar yaya na.)
“OMG! I’ve fallen wallahi, dan Allah aina yake?”
“Ke Zeezee me haka? Ki dena ba dani please da kinsan halinsa wallahi bazaki fad’i
haka ba.”
“Inma kankat ace yankan kai yake ina? Toh ni yamun ko a hakan wallahi I love him.
Jifa yazo dai-dai da zama gashi dama am single, tell me he is also please.”
“Ke wallahi inhar baki nitsu ba ban baki kowani info. akanshi.”
“Toh na nitsu meh IG handle nasa?”
“Adeel_Hussain amman he is private.”
“Damn it! I can’t follow an unknown guy” Zeezee ta buga hannun ta kan desk.
“Kiban details akansa please.”

“LOL okay, here we go. His name is Adeel Hussain like I told you, he is a
brother to my sister in-law, same Mom and Dad. This year ya gama karatun shi a
Florida in accountancy, his dad is filthy rich amman ya jima da rasuwa. Facaka da
kud’in gadonsa yake Mom nasu kuwa bata ce masa komi wai shine last born. Duk abinda
yake bata ce masa ko uffan hakan yasa ya zama tantirin d’an iska, first class
certified one ma. Shiyasa ban shiga harkansa, kullum cikin changing girlfriends
yake to cut the crap bayi dating one girl at a time ma, kuma a haka matan suke kai
kansu gunsa, mschw! But believe me Adeel ya had’u inde had’uwa ne wallahi.”
“Innalillahi! Ni wallahi ina sonsa a hakan kimin hanya please Lubiee.”
“LOL kema kinyi joining queue kenan?”
“Uwaki keh! Am serious”
“Yo! Taya zan miki hanyan? Wai bakiji bayanun dana miki bane?”
“Babe naji wallahi ahakan nake sonsa I can handle him, nayi handling Ammar ma”
“You sure can’t saboda wannan yafi Ammar trust me d’an banzan zuciya ne dashi.”
“Aswear I can”
“Toh naji you can, ya kikeso inyi? Ince mai kina sonsa?”
“Banza! Taya zakice haka? Ai seya raina ni, nide just hook us up together work
your magic Babe I trust you.”
“LOL toh naji amman nawa zaki biyan?”
“Yanzu Babe kud’i zaki karb’a waje na? Haba what are BFF’s for? Allah banida
kud’i.”
“Chabdi!” Lubiee ta galla mata harara “22k da kika karb’a gun Sumayya fah?”
“Toh naji zan baki 3k ciki.”
“A’a wallahi ya kasa 6k nakeso ko na fasa yin hanyan.”
“Shegiya mayyar cash wallahi dan shi kawai zan baki amman se kinyi hooking namun
tukuna.” Lubiee na dariya tace, “whatever way na yarda.”
“Its a deal!” Zeezee tayi exclaiming tana k’ok’arin sending picture’n Adeel to
her phone via whatsapp.

*~ *~
Tun ranar da Zeezee sukayi wannan magana da Lubiee take sa rai Lubiee zata kirata
tace mata the did is done. Everyday sede basu had’u da Lubiee ba seta ce mata ya
how far? Kullum kuwa amsan d’aya banje gidan Ya Salman ba kokuwa Adeel bezo gidanmu
ba. Ahaka har su Zeezee suka gama exams nasu ranar karb’an result as usual suka sha
kwalya aka ta d’aukan selfies.

_2 weeks later, gidansu Lubiee._


Sanye take da fitted gown lace kanta bako d’ankwali, bayan ta fito daga d’akinta
da baby sister’n ta tayi making way nata to Ummi’s parlour, achan ta tarar da Adeel
zaune kan 2 seater as always yadda ya saba ya mik’ar da dogayen k’afafunsa kan
centre table yana latsa wayarsa. Sanye yakeda black ¾ trousers da white T-shirt.
Ita ta rasa ya akayi jinin sa ya had’u da Ummi wani sa’in har kiransa take wai yazo
ya tayata hira sekace batada yara. Ko uffan bata ce mai ta nufi dining space ta
d’au ruwa dai-dai nan Ummi ke fitowa daga d’akinta “sannu Ummi” Lubiee tayi
greeting nata cike da ladabi, se anan Adeel ya d’ago kai yana kallonta. “Yauwa
Lubiee daman kina ciki ne? Seki taya baban nawa fira zan d’an shiga nan gidan Maman
Islam will be back soon.”
Neman excuse Lubiee ta shiga yi dan she can’t take rainin hankali irin na Adeel,
“uhm Ummi daman fa yan-” saurin katse ta Adeel yayi, “ohh no prob Ummi sekin dawo.”
“Yauwa Baba na na tafi toh” tana kaiwa nan ta fice. Tsaye Lubiee tayi gun sannan
daga bisani tayi texting Zeezee _emmata you won’t believe this! Adeel na gidanmu
right now come ASAP it might be your biggest chance!_

***
Zeezee na zaune gaban dressing mirror’n d’akinta, ta gama cancare kwalya tasa
wata light purple english gown se killing selfies take taga saqon Lubiee ai ba tare
da b’ata lokaci ba tayi replying _right away Baby!_ d’akin Baba ta nufa tace mai
akira Omar ya kaita gidansu Lubiee. In less than 20 minutes ta isa.
***
“Ke prob d’ina dake k’auyenci Luba” cewar Adeel mockingly.
“Banaso kadena cemin Luba!” Tayi stating angrily “and bani waya na ma.”
“I know where this is going Baby sis, you like me don’t you?”
“Mschww!! I aiint got your time bani waya na.”
“Gashi dillah! And please da wani kalan friends kike hanging out? Gabad’aya ba
Babe data min.”
“Bayan Babes da kake da you are still searching for more?”
“Trust me duk na basu red card yanzu” yayi maganan yana takan viewing photos yazo
kan wani pic na Zeezee data baza gashinta kan pillow tana a kwance, tayi pouting
mitsitsin bakinta, dai-dai nan take shigowa parlour’n k’amshin turarenta ne ya
mamaye gun gabad’aya tare su Lubiee suka juya suna kallonta. Ita kanta Lubiee
tsayawa tayi tana kallonta, daga bisani ta mik’e taje tayi hugging nata “Babe you
didn’t tell me you were coming.” Tayi maganar yadda Adeel zejita.

“I thought I might suprise you, so how are you?” Cewar Zeezee cikin wani muryan
da ban ta6a saninta dashi ba.
“Mu k’arisa ciki toh.”
“Nahh muje room naki it’ll be more comfortable there.”
“Okay toh Adeel hand me over my phone my BFF is here” tayi maganan tana dosan
inda yake. Sanda ya k’are wa pic d’in kallo sannan back to Zeezee again ya tabbata
itan ne ya mik’a ma Lubiee wayar. D’akin Lubiee suka zarce “ke Babe you killed it!
Kinganki kuwa? Duk kwalyan nan masa ne?”
“Believe me da nasan tuni yana nan senayi makeup dayafi wannan kyau.”
“Ke guy d’innan is fire kiganshi! Omg! Allah sa he’ve noticed me.”
“Ai da kin bari mun zauna a parlour’n so that ya k’are ma beauty’nki kallo da
kyau.”
“Ina Ummi? Ko zamu koma ne?” Cewar Zeezee all confused.
“Na yaushe kuma? Kin kopsa a-” bata k’are maganan ba idonta yakai ga kan screen
nata “omg! Wallahi picture’n kima yake kalla a wayana, Babe you nailed it!”
“Kamar ya what do you mean?”
“Gashi pic naki yake viewing a phone d’ina kin mai wallahi!”
“Don’t tell me please, wani pic? Allah yasa toh” ko good 20 minutes Zeezee batayi
ba tace zata tafi nan ma seda suka sake komawa parlour’n seyi suke kaman sunje shan
ruwa ne daga nan ta tsari napep ta dawo gida. Adeel na ganin Lubiee ta dawo daga
rakiya ya fita tare da shan gabanta. Ita kuwa knowing this was coming seta wani
burning face “ya da haka Mr. Player?”

“Oh common Baby sis don’t call me with this name a presence na Babe d’incan.”
“Wace kenan?”
“Your BFF, the one that left just now.”
“Aww you mean Zeezee? Toh kona kiraka da Mr. Player a gabantan ma so what? Its
not as if she’s your girlfriend.” Smirking yayi ta one side of his face sannan
yace, “she’s not but will soon be.”
“How?”
“Through my Mr. Handsome magic” yayi maganan yana shafa sajensa “kema kinsan all
girls I mean all fall for me at once and I’m very sure your friend did also ko ba
haka ba? Tace miki kiyi hooking namu up didn’t she?”
“You are crazy Adeel, to ba haka bane, Zeezee don pass your class excuse me.”
“Inhar haka ne dare me and give me her phone number.”
“A dalilin me zan baka number’n BFF d’ina? Saboda kayi toying da precious heart
nata and leave her heartbroken kamar yadda ka saba?”
“Common Baby sis, lets not make this hard on ourselves. Ke kin samu ma ina
tambayan digits na friend naki, you know it happens just once in a lifetime ban
tab’a tambayan digits na wata Babe ba se ita.”
“Dole ai ka tambaya saboda ita ta kai ne, not like your other hoes”
“Then give me.”
“I shan’t, shegen feeling d’in tsiya wai yazo tambayan abu amman yana gasa wa
mutum magana.”
“LOL you are afraid I will win over her heart in just 24 hours kenan.”
“No ba haka ba- ”
“Then give me her digits” ya katse ta. Haushi ne ya cikata, batasan a lokacinda
tayi mai dictating number’n ba offhand.
“Good girl wait for tomorrow kiga I’ll be going in Ummi tazo kice mata na tafi.”
“Mschw! Nak’i bazan fad’a ba.”
“LOL don’t be jealous Baby sis” ya kama d’aya daga jelan gashinta yana wasa
dashi, “zan had’aki da cousin d’ina Fahad.” Fisge kanta tayi “ce ma akayi nayi
kwante ne? Argghh!” Ta watsa mai harara sannan tabar gun. Shegen murmushinsa ya
saki sannan ya nufa E-class nasa ya fice.

***
Zeezee de tun isarta gida take jiran call from Lubiee. Not long enough ta kirata
ta irga mata yadda sukayi da Adeel sannan taja mata kunne kan no matter what she
should not say yes to him today tabari seta ja mai class if possible fiye da yadda
ta jawa Ammar ma amman inaa abin ba haka take ba ta side na Zeezee jinta kawai, ita
batak’i ma itace tacewa Adeel tana sonsa ba inhar he’ll say yes right away.

_9:20PM_
Tana miqe bisa gado taga incoming call from new number tsalle ta daka gun
tsabagen murna har ta mance ya ake answering phone call. Seda ya kusa ending ta
samu ta d’aga tare da yin shiru shima Adeel d’in shiru yayi se chan yace, “halo
Zeezee on the line please?” cikin sark’ak’k’iyar muryarsa.
“Yy... Yes.” tayi stammering.
“Cool pretty girls digits are really hard to miss.”
“Uhmm.. Who’s it?”
“Don’t worry Pretty you’ll get to know me soon, so remember the handsome guy you
saw earlier today at your friend’s residence?” Shiru Zeezee tayi tana nazarin tace
eh ne ko a’a finally tace “no.” Deep breath sarcastically Adeel yaja ya saki yace,
“woah! I never knew handsome faces can be ignored, Pretty you musn’t lie I know you
saw me.”
“You’ve got some nerve you know.”
“LOL so kin yarda kin gannin? Ko sena miki describing kaina zaki tuna? Well, I’m
the gold skinned, handsome, tall looking dude at your friend’s house earlier
today.”
“LOL you keep on saying you’re handsome bayan ni banga handsomeness d’inba.”
“Gosh! Don’t make a sin both you and I know am handsome and ahh! Kin ganni kenan
tunda kince bakiga handsomeness d’inba.”
“If I must admit, yeah I saw you.”
“Hah! I know right. So that aside, I’m Adeel Hussain” nan ya bata details about
him bayan daya gama ya buk’ace ta da tayi itama. Sun gama introducing juna yayi
clearing throat nasa, “so Pretty I won’t lie, actually your personality and
cuteness got my attention today in bazaki damu ba I will like us to be...” Se kuma
yayi shiru Zeezee ta k’osa taji me zece.
“I will like us to be friends if possible” Ihu ne kawai Zeezee bata saki ba just
friends? Ita girlfriend nata takeson zama ba friend ba, ina ma zata iya fad’a mai.
“Halo Pretty you there?”
“Uhm yeah.”
“So what do you say?”
“Sure why not? Request accepted.”
“As expected thanks tho.”
“you’re welcome.”
“I’m single and you?”
“I am too” ta amsa batare da tasan taya ba.
“Cool so after graduating where do you wanna proceed your studies to?”
“ATBU in shaa Allah.”
“Oh wow, we’ll get to be in touch kenan.” Hira sama-sama suka tab’a. Itade
Zeezee duk ranta a b’ace yake suna gama wayan ya jira tayi hanging sannan ya saki
wata mak’irar murmushi “you’ll have to beg for my love Zeezee.” pencil nose nasa
yaja sannan ya koma kan gado ya miqe.

*~ *~ *~
Haka nan tun daga ranan suka soma waya jifa jifa, Adeel seya jera kwana hud’u be
kirata ba, ita kuwa batak’i ace 24/7 suna waya ba. Gashi kota ce zata kirasa se
taji baza ta iya ba gudun karya bonsa ta. Bayan nan ga kuma yadda Lubiee ke mata
warning kullum kan she should play hard to get to him. Chatting ma sama-sama sukeyi
nan ma se a snapchat akwai sanda tamai magana a whatsapp yana gani yak’i replying
back koda yazo ya kirata daga baya kuma take cemai why did he ignored her message.
Arrogantly yace mata he wasn’t in the mood of replying messages at that instant.
Haka fa har watanni biyu suka shud’e ba improvement a relationship nata da Adeel.
Ko wuqa za’a sa mata a wuya bazata iya fad’in kalan relationship dake existing
between them ba, saboda they are morethan friends from the way yake calling nata da
pet names da kuma yadda yake acting amman kuma they are not in a relationship
saboda har sau biyu yana kawo mata case da girlfriends nasa kuma haka zata danne
zuciyarta ta basa shawarwari. Sede batasan meh ba ita duk kalan mazan da suke cewa
suna sonta ta kasa accepting nasu duk in sunzo korasu take tace tanada saurayi, ta
rasa dalilin hakan bayan gashi de bawai they are in a relationship bane da Adeel
toh why? She can’t answer.

2 weeks back da taje wani biki suka had’u da Adeel. To her suprise yak’i kulata,
infact yi yayi tamkar besan taba ma. Abun ba k’aramin ci ma Zeezee rai yayi ba dan
har kuka seda tayi. Ita kanta tasan mahaukacin so take mai amman until when zece
mata yana sonta? Bayan faruwan incidence d’in bata sake yi ta kansa ba 2 days later
ya kirata sede daga yadda take mai magana yagane bata tare da walwala, daya tambaya
kuwa bata b’oye mai ba ta fayyace mai komi to her suprise taji ya k’yal-k’yale da
dariya yake ce mata is she jealous? Ai ba saurayinta neba shi bale don ya shareta
yaje ya kula wata taji haushi shi gaskiya baya son haka they are just friends ba
ruwanta da dating life nasa. Kuka Zeezee tai tayi har seda garin Allah ya waye ta
kira Lubiee take irga mata yadda Adeel ke affecting nata like an infection or
rather disease.
Adeel d’an iska kuwa duk da gan-gan yakeyin wad’an nan abubuwa. So yake ya gama
toying da heart nata, ya zama he is the only one she wants kafin nan yace mata yana
sonta.

** **
Su Zeezee sun shiga Ss3 bada jimawa ba Adeel yayi asking nata out kan will she
be his girl? Ita kanta batasan a lokacinda ta amsa mai da ‘yes’ right away ba. Tun
daga wannan rana rayuwar Zeezee ta canza komi Adeel, kullum tana cikin snapchat
tana mai sending videos da pictures. Books nata na school gabad’aya sunan shine
kota ina. To cut the story short ko zaune take ita kad’ai muddin da biro a hannunta
toh believe me sunan Adeel zata hau zanawa a hannunta. Password nata na laptop,
waya, ipad komi Adeel, snapchat handle nata da whatsapp name ma ‘Adeel’s Very Own’
ta miyar. Haka wallpapers nata ma duk killer pictures nasa ne. Zeezee can die for
Adeel hakan yasa yake mugun bata wahala, abu kad’an ya hau mata zuciya kokuwa
masifa, ko kiranta yayi bata d’aga da wuri ba seya hau k’orafi. Shi ya iya sa
pictures na friends nasa mata a dp aman ita koda dan wishing na male friends nata
happy birthday ne ya hanata. Sam se yace wai she is cheating on him.
A haka fa suka samu sukayi one month in a relationship. Cikin wata d’ayan nan
akwai sanda Adeel yayi sati be kiran Zeezee simply because yaje school nasu ya
tarar da ita tana hira da friends nata maza. Cikin satin nan har ramewa sanda Zezee
tayi kullum cikin sending mai apology and ‘I love you’ messages take amman hakan
besa ya ragar mata ba. Dan haka yanzu tama bar kula mazan class nasu se in ta kama.
Ko liking pictures na instgran boys followers nata ya hanata amman yana chan shi
har commenting yanayi a nasa na female friends d’in. Zeezee de bata tab’a shiga
tashin hankali irin wannan ba a rayuwarta, Lubiee kullum cikin nadaman had’asu da
tayi take. Duk kalan masifa da tsiwa kalan na Zeezee when it comes to Adeel bata
iya gaya mai koda maganan banza ne, koda ita ce da laifi ita ke basa hak’uri.

_Nide Miemie nace Allah ne ya soma kamata tunda ta iya raina mahaifiyarta da
yayyunta._

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 21

*December, 2016*

_Assalamu Alaikum readers/fans, I will first of all like to thank you all for
your maximum support and love, I love y'all so very much, INA TARE DA KU forever!
So idan kun lura zakuga inda nayi mistake which is common to us all human beings
cause we aiint perfect. Tun a page 18 nace Yasmeen tayi aure se kuma a page 19 nasa
Yasmeen tama Zeezee breakfast, duk wani me tunanin daya zauna yasan slip of mind
ne, we are all human beings sabida haka we are prone to make mistakes so nima se
ayimin uzuri. Thank you once more, *TEAM ‘YAR GATA CE #YGC*_
★*★*★*
Cikin sa’a su Zeezee suka samu suka k’are first term nasu suka shiga hutu. Yau
ranar ta kasance Saturday tana zaune a gida. Wanka tayi ta shirya tsaf tanason zuwa
gidansu Lubiee bayan tagama komi ta zarce site nasu Ibraheem knocking tayi sannan
yace, “come in.” Da friend nasa Aleeyu ta tarar da shi bako gaisuwa tace, “Ya
inason ka kaini gidansu Lubiee.”
“Driver’n kine ni? Kuma baki iya gaisuwa bane?”
“Toh so nawa kakeso na gaishe ka?”
“Bani ba Aleeyu nake nufi.”
“Nikam zaka kaini ne ko a’a?”
“Zainab ki kiyayeni!”
“Haka kawai sekace wacce bata da abinyi kullum inyi ta gaishe maka da friends,
karka kan” tana kaiwa nan ta fice ta hau gunguni “to meye amfaninka a gidan tunda
ko kai mutum unguwa ma baka iya ba mschww! ni wallahi kayi kayi aure ma kowa ya
huta” d’aki ta koma rai a dak’ule. Data takeson ta bud’e amman tsoron kalan bala’in
da Adeel ze mata take, hakan yasa ta fasa bud’ewan ma totally. Daga d’akin Ibraheem
kuwa Aleeyu ne ya riga bashi hak’uri kan dan Allah ya kaita unguwan kawai, ba dad’i
tagama shiri ace ta fasa fitan. Bawan Allah kam ashe da biyu ne shi wai son Zeezee
yake dukda uban rashin kunyar tata.

15 minutes later Ibraheem yaje ya bud’e door na Zeezee “tashi in kaiki zanyi
dropping Aleeyu.” Dad’i sosai taji, nan da nan ta kintsa suka fito sede se kallonta
Aleeyu yake wanda har cikin jikinta takeji, tsabagen tsoron Adeel da take ko
kallonta wani d’a na miji yake setana ji kaman Adeel na ma gun ze mata masifa. Koda
suka shiga mota Aleeyu se satan kallonta yake ta mirror ahaka har suka sauk’eta on
their way to Aleeyu’s residence yace, “maza wannan sister’n taka fa tamin gaskia.”
Brake Ibraheem yaja unexpectedly. “Come again ban jika ba.”
“Zeezee, nace tamin ina so.”
“Zeezeen? Wancan fitsararriyar? Yanzu har akwai d’a na mijin da zece yana son
Zeezee?”
“Gani nide ina sonta.”
”Lallai kuwa baza ayi wannan abin kunyan dani ba wallahi ahaka ma ya na k’are da
ita bale wai taji friend d’ina yana sonta please ka rufa min asiri, ma me abin so a
jikinta please? Yarinya cefa.”
“Haba maza! Kai de kawai kace kana min rowa ne shikenan, ba seka tsaya kana raina
min hankali ba.”

“Seriously guy bawai batun ina maka rowa bane, had it been Yasmeen ce ko
Mariam kace kana so wallahi I’ll gladly give them to you amman banda wannan
fand’ararriyar.”
“Ka dena zaginta haka please.”
“Wai kai bakaga yadda tak’i gaishe ka bane?”
“Ni I don’t care Allah ina sonta.”
“Nide wallahi ba ruwana, kuma inhar kana sona as a friend please back off. In
budurwa kakeso zan ma Fateemah na magana tayi hooking naka da ko friend nata ko
cousin amman de banda Zeezee kam. I can’t take that raini wai friend d’ina na sonta
mschw!”
“Nide tamin wallahi ka bani go ahead kokuwa...”
“Kokuwa meh?”
“Ko kuwa naje na sameta na mata confessing Allah.”
“Dan Allah kaje in ka fasa.” ya fad’a angrily.
“Haka kace?”
“Eh saboda ba bakina aciki.”
“Naji ba bakinka aciki amman bani digits nata toh.”
“Wallahi ban bayarwa kaji na rantse don’t even beg me to.”
“Karka damu zan samu da kaina.” Rai a dak’ule Ibraheem yayi dropping na Aleeyu
kan hanya, ya k’arisa dashi ciki ma yak’i. Wajen Fateemansa ya zarce tad’an faranta
mai rai sannan ya koma gida waiting for Zeezee’s arrival.
Not long enough ta dawo. Har d’akinta ya bita yayi tsaye a bakin k’ofa yana galla
mata harara a yayinda haushinta keta running a veins nasa. Banza dashi tayi tahau
rage kayan jikinta, ba ko kunya. “Ke bakida kunya ne? Ina tsaye a kanki zaki hau
cire kaya?”
“Aww! Wai dama da mutum tsaye wajen ne? Toh bakayi sallama ba baka kuma yi
knocking ba ta ina zan san da mutum akaina? That aside ma naga ai nan d’akina ne ko
a d’akinka kakeson inje in cire kayan?” Ganin yayi kamar ze nufi inda take tasa ihu
“dan Allah kayi hak’uri kar ka tab’ani na tuba wallahi bazan sake ba.”
“Da yafi miki kam, so nazo nayi making it clear to you saboda bana son raini, duk
wanin da kika san na sani yazo yace wai yana sonki ko wani iskancin karki d’au da
bakina aciki dan ni ba sa’ar yinki bane count me out.”
“Toh nikuma meya kawo wannan magana yanzu?”
“Am warning you against the future, kar kiga wai dan wani wai shi friend d’ina
yace yana sonki kice zaki raina ni.”
“Chab! Allah kiyaye, wasu gajiyayyun friends nakan? Ai kai ma kasan nafi
k’arfinsu.” Mac powder’n ta dake kan dressing mirror ya d’aga ya wulla mata se
setin goshinta, wajen ta rik’e tana ihu “karki iya bakinki, su waye gajiyayyun?”
Shiru ba amsa... “nace su waye?” Ya nufi kanta da sauri tace, “friends d’ina ba
naka ba dam Allah kayi hak’uri” da k’afa ya gishimeta “marasa kunya kawai ni na ma
rasa abin so ajikin ki wallahi da har Aleeyu ze dage yace se ke. Ma yaushe kika
balaga?” Hawaye take tana binsa da harara ita kam. “Mschww!” Dai-dai ya juya ze
fita kenan wayarta dake kan gado ya soma ruri ai tana kai dubanta taga ‘My Very
Own’ yana flashing kan screen d’in. Kafin Ibraheem yayi glimpsing tayi sauri ta ja
ta b’oye. “Wake kiran naki?”

“Toh Ya ina ruwanka da wanda ke kira na? Ba waya na bane.”


“Baki bar kula samarukan nan naki ba ko? Nace wake kiranki?”
“Babu” tayi muting call d’in “ba gashi ba? Text message ne ya shigo, ni dan Allah
kayi hak’uri ka fita zan cire kaya na kokuma in cire a idonka wallahi.” Ganin bai
motsa ba ta hau cire vest dake jikintan tuni Ibraheem yabar d’akin “ai daka tsayan
inban ragar da bra kad’ai a gabanka ba tunda daman muharrami na ne kai.” Sefa a
yanzu ta tuna Ammar ne ya kirata bata d’aga ba. Ya kira bata d’aga da wuri bama ya
suka k’are bale ace yau bata d’aga ba. “Omg!” tayi stating sannan ta shiga dialing
number’n sa, har 3 missed calls beyi picking ba. Bawai kuma bayi kusa bane,
actually wayan ma na hannunsa d’agawan ne bazeyi ba shi wai me zuciya. Se a karo na
hud’u ya d’aga nan ma yayi shiru “hello My Very Own?” shiru ba response.
“Very Own please kayi hak’uri and let me explain.” Wayar ma ya katse gabad’aya
haka kamar jaka ta sake kira nanma se a karo na uku ya d’aga “Very Own please let
me explain kaima kasan dagangan bazan k’i picking up call naka ba, I was with Ya
Ibraheem shiyasa.”
“You are lying to me again.”
“No I’m not.”
“Yes you are, I don’t mean anything to you thats why har zan kiraki bazaki damu
ki d’aga ba, ba laifinki bane ai, ni na kiraki.”
“Wallahi ba haka bane Very Own dan Allah kayi hak’uri I can’t take it, you being
mad at me.”
“And am very mad at you right now am hanging up dan ko muryanki banason ji.”
“Please don’t meh zan maka ka hak’ura?”
“Nothing!” yayi snarling at her.
“Please mana I’m on my knees begging dan Alkah kayi hak’uri.”
“Kinsan this is the second time hakan ke faruwa ko? Na uku I think we’ll just
have to break up tunda I don’t mean anything to you.”
“Very Own wallahi thats not true you mean everything to me, kuma ka dena fad’in
wai zamu rabu, I belong to only you. I love you morethan words can ever tell.”
Dad’i sosai yaji amman ya dake “shine sena kiraki bazaki d’auka ba?”
“Na fa gaya maka yau Ya Ibraheem na tsaye kaina, the other day kuma wayar na
cikin jakana ne I didn’t hear it ring.”
“Daman I you wouldn’t hear it tunda you don’t care, I can’t talk right now am
hanging up.”
“Very Own wai baka hak’ura ba har yanzu? Gobe kazo ka d’aukeni and lets go
somewhere, I have a suprise for you.”
“I’m mad I can’t go out with you.”
“And I’m sorry my Handsome Bobo, it’ll never happen again ever!” haka da k’yar ta
samu ta shawo kan Adeel ya yarda a goben ze zo.

***
Washegari around 10:00AM Zeezee ta shirya tsaf cikin electric blue lace tasha
had’ad’d’en makeup sannan ta fito Mama na ganinta tace, “ina kuma zaki yau da safen
nan?”
“Gidansu Lubiee mana.”
“Kullum gidansu Lubiee? Jiya bakije bane? Anya kuwa chan kike zuwa bawani yawon
banza ba Zeezee?”
“Yawon banza? Toh me zan zauna inyi a gida ba Adda Mariam ba Yasmeen?”
“Wallahi inma yawon iskanci kike kina bin samari gwara tun wuri kin dena.”
“Baba! Baba!” Nan da nan ya fito daga d’aki “na’am K’anwata ina zuwa da safe
haka?”
“Gidansu Lubiee zanje shine Mama wai sam yawon banza da iskanci zani.”
“Kamar ya yawon iskanci? Hafsah baki yarda da tarbiyyan da kika bawa ‘yarki bane
da zakice zata yawon banza?”
“Ina kuwa na yarda dashi? Kullum ace wai se ‘ya ta fita kuma gidan su Lubiee
wallahi k’arya ne inma saurayi kike bi ranan da kika d’auko abinda yafi k’arfinmu
nan gabad’aya ke kika sani.”
“Kai! Meh haka?! Ya isa da Allah, kidena yima K’anwata baki in shaa Allah ba
abinda ze sameta” hannu yasa a aljihu ya zaro 1k ya mik’a mata “gashi ko Allah ya
kare.”
“Ameen Baba na tafi.”

Dai-dai ta fito bakin k’ofa kenan sukayi bumping into each other da Aleeyu.
“Awch!” Tayi exclaiming in pain.
“Sorry Zeezee didn’t mean to bump into you.”
“Is okay sannu da zuwa” tayi maganan tana wuce sa.
“Ermm... Zeezee can I have a word with you?”
“Ya Aleeyu right now am heading somewhere kabari in na dawo.”
“Just a minute will be okay.” Waje ta lek’a taga ba motan Adeel sannan tace, “toh
ina jinka kayi sauri please” nan fa gaye ya hau suburbud’o mata love words shi yana
sonta, kuma so na aure ba da wata manufa ba. Dai-dai ta bud’e baki tace mai ita
batayi kenan ta hango furious Adeel tsaye gefen motansa. B’ari ta shiga yi tama
rasa nayi.
“Wayyo Allah! na shiga uku!” ta aza hannayenta saman kai. “Ya Aleeyu dan Allah
ka shiga ciki, ka gama dani yau.” Sam be gane me take nufi ba se daya leqa wajen
yaga inda take kalla ya fahimci komi. Kafin tace zata k’arisa inda Adeel yake tuni
ya shige motansa ya fice not minding calls da take mai sending. Kuka ta shiga yi
wajen tasan koda zata had’a sama da k’asa Adeel will never listen to her, ai dan
dolenta ta fice zuwa gidansu Lubiee ba shiri, thank God Ummi bata gida.

“Ya haka Babe? Meya faru kike wannan kuka?” Lubiee tayi maganan tana caressing
bayan crying Zeezee ita a zatonta ma ko rasuwa akayi ma Zeezee.
“Lubiee am in trouble, nasan Adeel baze sake min magana ba.”
“Mschww! Yanzu akan Adeel kike wannan kuka? Oh ni Lubabatu! Wallahi da nasan da
haka da tun farko banyi hooking naku up ba.” Shiru Zeezee tayi se kuka take chan
Lubiee tace, “meya had’aku?” In a crying tone tayi ma Lubiee narrating komi. Bayan
data gama sauraronta tace, “yo ai wannan ba abin damuwa bane, call him up and
explain everything to him is all you’ve got to do.”
“Ke kina ganin ze saurareni neh? Fa bakisan Adeel bane, mugun kishi ne dashi ko
magana da mazan class namu ya hana ni, bale ace ya ganni da wani bakin k’ofan
gidanmu yau, kema kinsan da akwai babban tashin hankali, please help me out.”
“Dan Allah kibarsa da kansa ze sauk’o ni wallahi haushi kike ban idan kina ma
Adeel haka, sekace shine autan maza mschw!”
“Ni a wajena shine auta, wallahi I can sacrifice everything for him dan Allah
help me out.” Kallo Lubiee ta galla mata sannan ta d’au wayarta ta shiga kiransa.
Seda call d’in ya kusa tsinkewa ya d’aga nan ta hau mai tsiwa, “kai kuma sarkin
zuciya haka akace maka akeyi ne? How can you just jump into conclussion saboda kaga
Zeezee da wani bakin k’ofan gidansu? Baka tunanin ko friend na yayanta ne yake bata
saqo?”
“Ko d’aya, ni zakuyi playing? Inhar what you are saying is true why didn’t she
call me up herself and explain to me? Daman tace min she have a suprise for me and
I guess that incident was the suprise anyways tell her I enjoyed every part of it.
Am hanging.”
“Adeel don’t! Ade”- karap ya katse abinsa. Jin haka Zeezee ta sake rushewa da
sabon kuka haka ta tayi Lubiee na bata hak’uri har ta samu tayi shiru.

“Babe wallahi it hurts me seeing the way you can die for wannan useless Adeel
d’in, Allah yaga kina sonsa ne yake miki wannan iskanci. Forget him karki sakeyi ta
kansa believe me da k’afafunsa ze dawo.”
“Babe only if I could, wallahi bakisan yadda nake feeling Adeel ajikina bane,
I’ve never felt like this with anyone. Sonsa a jinina yake.”
“Naji amman please kidena tayar da hankalinki haka, ke bakisan hawan jini yana
iya kama ki a haka ba? Please ya isa don’t call him up zan kira shi anjima inya
sauk’o kukan is enough.” Se bayan La’asr Zeezee ta koma gida ba annashuwa ko kad’an
a tattare da ita. Miqe take bisa gado amman hankalinta sam baya jikinta. Daga
bisani ta miqe zaune, “wallahi wallahi Ya have to share this burden with me also,
duk laifin wannan mayen Aleeyun ne wama ze sake ce mai Yaya? Mschww! Kuma harda na
Ya aciki tunda friend nasa ne” trying Adeel’s line for the last time baya shiga
taje ta samu Baba da Mama a d’akinsu. Ba sallama ta fad’a tana kumbure-kumbure.

“Ya haka K’anwata wani abu ne?”


“Ke wai bazaki koyi yin sallama bane? Wawiya kawai.” Mama tayi scolding nata. Ai
dama a cike Zeezee take seta sa kuka unstoppingly “haba Hafsah! Yanzu ai kin huta
da kika sata kuka, zo K’anwata” har kan gado yayi beckoning nata over ta zauna
gefensa sannan ya share mata hawayen, “yi hak’uri kinji? Allah Hafsah kika sake
cema yarinyan nan wawiya you’ll answer to me.”
“Yo inba wawanci ba yarinya is sixteen (16) years old amman ace har yanzu barging
into our room take ba sallama.”
“Ba ruwanki, kiyi abinda ke gabanki. Ehem ina jinki K’anwata meya kawo ki? Ko
kinzo tayani hira ne?”
“Ba d’azu zan fita gidansu Lubiee ba?”
“Ehemm... Ina jinki” ya bata full attention nasa wanda ko Mama bata samun irinsa.
Itama Mama kasa kunne tayi tana sauraron Zeezee’n.
“Nazo zan fita kenan kawai sega friend na Ya Ibraheem Aleeyun nan, dana gaishe
shi seya cemin wai yanason min magana nace yabari anjima yata insisting then nace
masa ina jinsa, kawai ya hau cewa wai yana sona. Son ma wai na aure Baba bayan ni
ka hanani yin saurayi se after secondary school.”
“Haka shi Aleeyun yace?! Lallai yaron nan baida hankali, har gida na zezo ya nemi
K’anwata ba tare da ya tambayi izini daga guna ba? Allah kaimu rananda ze sake
zuwa!”
“Uhn-uhn Alhj don’t just jump into conclussion.”
“Like how Hafsah? Ke bakiji abinda Zeezee ta fad’a bane? Mu godewa Allah ma
Zeezee nada wayo in wata sakariyan ne ba sede ta bisa ba suzo su mana abin kunya.”
“Kai yanzu how sure are you Zeezeen naka ba k’arya take ba?”
“Wallahi wallahi ba k’arya nake ba kuma tun kafin yau dama ranan na jisu da Ya
suna maganan. Ya yake cemai wai ya basa go ahead.”
“Shi Ibraheem d’in? La’ila! Jeki kiramin shi.” Nan ta fice, “hmm Allah kyauta de
amman dekam I don’t believe this girl, itan da tun a Ss1 take kula samari dan yanzu
Aleeyu yace yana sonta wai take kawo ma k’ara? Akwai abinda ke cikin duhu.”
“Haka kuwa zakiyi ta nema ki gaji saboda ba abinda ke duhu, samari kuma tun Ss1
dana mata magana ta denayi” dai-dai nan Ibraheem yayi sallama “wa’alaikum salam”
suka amsa a tare. Wucewa Zeezee tayi taje ta zauna gefen Baba.
“Yanzu kai Ibraheem ka kyauta kenan a matsayinka na babba? Ina ganinka da hankali
amman seka tafka sakarci haka?”
“Gaskiya wannan bayi bane, taya a gaban K’anwarsa zaka tsaya kana mai magana
haka?” Mama tayi maganan a fusace.
“Ke dama ai tanan kika fi kauri, d’aure ma k’arya gindi. Dake Ibraheem ne me
sunan Babanki dole kik’i ganin laifinsa ai to ni kimi shiru.” Har anan Ibraheem
bece komi ba.
“Ehh Ibraheem? Hakan da kayi ka kyauta kenan?”
“Baba nifa ban fahimce kaba.”
“Batun friend naka Aleeyu nake magana. Taya zakayi haka? Kai bakasan a rashi na
kaine uba ga Zeezee ba? Seka kama ka bawa d’an iskan can go ahead, wato yayi komi
da k’anwarka kai baka damu ba ko?”
“Ni!” Yayi pointing kansa. “Yaushe na bawa Aleeyu go ahead? Infact ni koda
yacemin gashi gashi yana sonta ma ban yi backing maganan ba ce masa nayi Zeezee is
still a girl yabari ni ba ruwa na kuma ko ke Zeezee banje na sameki nace miki duk
wanin dana sani inya ce yana sonki kisan ba bakina aciki ba?”
“Ni! Yaushe akayi haka dani? Nide baka cemin komi ba.” Ibraheem was left
dumbfounded, lallai Zeezee!

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 22

*December, 2016*

“A’a barshi K’anwata, toh wallahi Ibraheem ka bud’e kunnuwanka ka saurareni


sannan kuma kaje ka samu d’an iskan Aleeyun can kace mai ya fita daga harkan
K’anwata banason ya rabawa yarinya attention nata, waec nata ne a gabanta and
nothing else. Kuma this should be the first and last inhar kasan ka gayyato friends
naka ma kadena kiran Zeezee side naku da Omar kana jina ai?” Shiru... “Ba da kai
bane?”
“Naji” yayi maganan harshly “zan iya tafiya?”
“Tashi ka tafi” seda ya galla wa Zeezee harara cike da horo sannan ya fice.
“Kuma Baba kace mai kar ya daken.”
“Barshi bare tab’a kiba, if he does ma let me know.”
“Toh Baba nagode.”
“Yauwa K’anwata Allah miki albarka.”
“Ameen” tana kaiwa nan ta fice.
“Hummm!” Mama ta numfasa, “Allah de kyauta ana ganin gaskiya amman ayita takewa.”

*~ *~ *~
Washegari around 9pm Mama tayi d’akin Zeezee ta sameta se bacci take sha. Bargon
data ruhu dashi Mama ta kwaye “oya mik’e kije ki had’a mana breakfast.”
“Wai shikenan sede ba’ayi hutu ba mutum barena samun bacci ba?”
“Tashi nace kona kira Ya Ibraheem ya zane min ke.” Seda tayi wasting several
minutes sannan ta mik’e finally tayi toilet. After a while tafito still Mama na
tsaye a d’akin nata tace, “chips zamuyi breakfast dashi” shiru tayi taqi amsawa,
“ko baki jini bane?”
“Naji.” Bayan fitan Mama ta gwada line na Adeel har sau biyu amman baya picking,
morning text message me dad’i tamai sannan ta fice. Nan da nan ta gama fere
dankalin ta aza mai kan wuta ta dawo d’aki ta hau chatting da friends nata. Twelve
(12) more minutes Mama ta dawo d’akin nata furiously “sekin mana setting gidan on
fire zaki samu sukuni ko?! Kin d’aura man gyad’a tun tuni kinzo kinyi zamanki anan
kina chatting? Mik’o wayan nace!” Zatayi magana Mama ta daka mata tsawa “miqo
nace!” Badan tanaso ba ta miqa mata ta fice se tura baki take gashi Baba bai gida.

Gishiri ta zabga wa dankalin tana sawa cikin mai yayi chaaa!! Kad’an ya rage be
zube mata a jiki ba. Dan yadda man yayi zafi da minti goma dankalin ya gama soyuwa
ya dawo bak’i k’irin. A garin kwashewa ta k’one kanta a hannu, nan fa tahau disco a
kitchen d’in ana cikin haka Mama ta shigo. “Ya haka Zeezee?”
“Ni dan Allah abarni, abanza ansa mutum ya k’one yau wayyo Allah na!” fridge ta
bud’e ta ciro k’wai tare da fasawa kan burnt hannun nata. Idon Mama na tozali da
k’onannen dankalin ta saki salati “meh wannan!”
“Dankali mana!” Zeezee ta bada amsa in an I-don’t-care attitude.
“Shine bak’i k’irin haka?” D’aya ta gwada d’agawa takai baki aikuwa bai tonuwa,
ciki ko alaman soyuwa beyi ba amman ga waje nan ya k’one k’urumus! Bayan nan kuma
ga uban gishirin data zabga. Wani abun se girkin Zeezee!

“Ji gishiri! Dagangan kika yi hakan koh? Daman tunda na saki aikin kiketa
gunguni, dagangan kika k’onan koh?”
“Kamar ya dagangan? Ni dan Allah kibarni, zanji da k’unan danayi ne kokuma
masifar ki.”
“Aww! rashin kunya zakimin akan asaran da kika min? Nasan maganinki, Ibraheem!
Ibraheem! Zo Babana.” Ba tare da b’ata lokaci ba yafito “na’am Mama.”
“Yauwa kalli abinda Zeezee tayi da breakfast namu ina mata magana kuma tana
gayamin maganan banza.”
“Meh wannan d’in wai?” ya tambaya dan kuwa ya kasa tantance ko dankali ne kokuwa
a’a.
“Wai dankali nace ta soya mana tayi wannan abu.”
“Ke bakida hankali ne?” yayi snarling at Zeezee, banza dashi tayi se hura ma
hannunta iska take.
“Dake fa nake magana!”
“Dama abinda ka iya kenan, toh dagangan nayi ne ai kuma kunsan ban iya soya
dankalin ba kuka sani yi” dama cike yake da ita gashi yasamu another reason na mata
duka. Waje ya tura Mama ya shigo kitchen d’in ya mata dukan tsiya, Mama dake waje
tana “ya isa haka Ibraheem” dan yadda Zeezee ke ihu amman ina se kaman k’ara mata
Mama tace yayi, kirb’anta yatayi seda ya huce haushinsa kap akanta sannan ya barta.
“Nan gaba ki sake had’amin waje gun Baba kiga inban miki wanda yafi wannan ba.”
Ball da ita yayi sannan ya umarce ta data mik’e abin tausayi se kuka take ta mik’e
duk jikinta zafi yake mata batasan da wanne zata fara ji ba.

“Oya d’iba dankalin ki sake ferewa ki soya me kyau kuma ko wallahi na miki wanda
yafi wannan.” Gabad’aya taci k’aniyanta yau ko bakin rashin kunyan ma babu “badake
bane?”
“Dani ne” nan ta nufi gun basket d’in ta d’iba yana tsaye a kanta ta gama ferewa
ta tsaga tasa mai, yana d’an yin zafi tasa gishiri dai-dai ta juye cikin man.
Ibraheem ya barta ta fita daga kitchen d’in kafin dankalin ya soyu ma yak’i haka
tana tsaye gun har dankalin ya soyu ta kwashe suka karya. Gabad’aya Zeezee ji take
dama ba’a k’addaro mata da wannan rana ba, gashi har yanzu ta gwada line na Adeel
koya shiga baya picking.

*~ *~ *~
Seda Azahar Baba ya dawo nan Omar daya gama tara kud’in siyan motansa yaje ya
samesa ya mai sannu da zuwa. “Baba dama cikon naira dubu d’ari biyar (N500,000)
nake so zan sai mota.”
“Iyyeh! Umari nawa ya girma harka tara kud’in sai mota? Wani model ne?”
“Honda DC ceh.”
“Ahh Honda nada kyau, so kanada gurantee na motan?”
“Eh duk mun gama magana komi is in place.”
“Toh bari zan maka transferring kud’in a account naka.”
“Toh Baba nagode Allah ya k’ara bud’i.”
“Ameen Allah maka albarka ya kawo mace ta gari” bayan yafita Mama tace, “oh! Yau
wata rana Alhj anyi abin kai toh Allah k’ara bud’i.”
“Ameen” yace mata “ina Zeezee nekam? ”
“Tana d’akinta tana bacci.”
“Ayyah K’anwata yayi kyau toh.”
A ranan Baba ya sawa Omar kud’in as promised, a washegari navy blue discussion
continue na Omar ya iso kowa ya taya sa murna barin ma Mama, ita deh Zeezee ko fita
taga motan ma tak’iyi dan bak’in ciki. Shikenan Ya Ibraheem, Adda Mariam da Ya Omar
suna da mota Yasmeen ma tace mijinta yace ze sai mata mota ita kad’ai ce bata da
mota. Kanta ta rufe a d’aki tayita kuka kaman ba gobe, tana cikin yi taji knocking
bisa k’ofar d’akinta kamar bazata amsa ba tace, “waye?”
“Baba ne Zeezee” jin shine ta mik’e ta bud’e mai “bade kuka kike ba K’anwata?”
Yayi maganan yana scruitinizing face nata. “Wani abu ne?”
“Babu” tace sama-sama tana share hawayenta.
“In shigo toh?”
“Ka shigo Baba” akan kujera suka zauna, “meya faru kike kuka K’anwata? In matsala
kike dashi bazaki sameni ki fad’amin ba seki rufe kanki a d’aki kiyita kuka? Ko
kinada gatan daya fini ne Zeezee?”
“A’a Baba.”
“Then why won’t you tell me your problem?”
“I’m sorry.”
“Then fad’amin mesa kike kuka?”
“Babu.”
“Kina son muyi fad’a ko?”
“Duk su Ya Ibraheem dasu Adda Mariam suna da mota Yasmeen ma tace min mijinta
yace ze sai mata mota ni kad’ai ce banida mota.”

D’an dariya ya saki kalan ta manya, “shine abin kukan K’anwata? Allah kaimu ki
gama secondary school mana kiga, kowani kalan mota kikeso zan saya miki.”
“Har sena gama Baba? Bayan ga ‘yan ajinmu su Sumee, Lieeymarh, Nafeesat, Billy
duk suna da mota, Lubiee ma Abbansu ya sai mata ita da yayanta.”
“Hakane?”
“Eh wallahi Baba.”
“Toh share hawayenki kinji? Muddin ina raye ba abinda zaki nema ki rasa, in shaa
Allahu nan da 2 weeks zan sai miki motanki kema.”
“Dagaske Baba?!” tayi maganan sounding thrilled.
“Eh mana K’anwata in ban farinta miki ba mawa zan farintawa?”
Tsalle ta daka ta d’ale cinyansa tare da hugging nasa “I love you so much Baba.”
“I love you too K’anwata” bata jima ba ta koma gefe ta zauna, “yauwa kuma banason
ki fad’awa kowa wannan magana kinji ko? Ko Mamanku ne karki fad’a mata.”
“Bazan fad’awa kowa ba Baba amman wani iri zaka sai min?”
“Don’t you trust me? Its a suprise.”
“I can’t wait! Allah ya k’ara bud’i Baba. Yauwa ance zamu iya fara kawo kud’in
neco registration namu.”
“Toh bari in kuka koma school ko a gobe kikeso kikai?”
“Eh a gobe.”
“Toh Allah kaimu.”
“Ameen Baba nagode.”
“Nima nagode” har waje ta rakasa sannan ta dawo d’akinta se tsalle take ita za’a
sai mata mota, fatan ta Allah yasa mercedes-benz ce, a rayuwa ba motar dake burgeta
kaman benz, benz is life!

★*★*★*★
Life moved on da k’yar abubuwa suka dai-daita tsakanin Zeezee da Adeel, a rayuwa
ba abinda tafiso kamar taga ita da Adeel are on good terms suna shiri. Duk wani
abinda tasan ze haddiso musu da matsala tana k’ok’arin kiyayewa saboda zaman
lafiyansu ya fiye mata komi a duniya.
Yau ranar ta kasance Tuesday da yamma around 4:30PM tana kwance a d’akinta ita
kad’ai. Ba kowa a gidan se ita Baba ya fita su Mama kuwa sun je gidan Kaka. Baba ne
ya kirata nan da nan ta d’aga “hello Baba.”
“Na’am K’anwata kina gida?”
“Eh.”
“Toh kifito bakin k’ofa yanzu.”
“Toh gani!” mayafinta taja da waya ta fice tana fita taga the most biggest
suprise of her life, sabuwar mercedes benz C300 ce fa fara k’al ko ledan jiki ba’a
b’are ba. “Omg!” Kawai take ta nanatawa, kuka ta soma tsabagen murna, da gudu taje
tayi hugging Baba. “Baba I don’t know the right words to use in thanking you,
bansan ya rayuwa na zata kasance without you ba, you mean the world to me you are
my hero, I love you so much, morethan you can ever imagine.”
“Zeezee na ta girma I love you as much K’anwata ga key naki nan.” Nan ya mik’a
mata, wayarta ta bud’e ta shiga snapchat ta musu selfie ita Baba da motanta tayi
adding caption _priceless gift from my Amiable Dad, ILH._ daga nan tayi ta d’aukan
motar hoto, saura tayi shi kad’ai saura ita dashi. Ana cikin haka su Mama suka dawo
a motan Omar. A gefen motan Baba sukayi parking suka fiffito “sannu Baba” suka yi
mai ya musu sannu da zuwa.

“Toh wannan mota fah? Suwa sukazo sukayi parking anan?” Mama ta tambaya.
“Bana mutane bane nawa ne Baba ya siya min” ta k’arisa gunsa tare da kwanciya
ajikinsa.
“Meneh? Dawo baya ban jiki ba” Mama tayi maganan disbelievingly a yayinda Omar da
Ibraheem sukayi tsaye gun dumbfounded.
“Mota na ne Baba ne ya siya min.”
“Mota! Alhj mota ka sai wa Zeezee?! Da shawaran waye? On hi Hafsah! Mota de?” Ta
k’arisa gun motan tana shafawa “kuma sabuwa ko hawanta ma ba’ayi ba.”
“Sabuwa?” Omar yayi maganan yana bin motar da kallo.
“Ni kibar shafamun mota, Baba kace tabar shafa min mota.”
“In bazaku fad’i alkhairi ba keda ‘ya‘yanki seku ja bakinku kuyi shiru.”
“Alhj amman wannan wani erin rashin hankali ne?”
“Sai ma K’anwar tawa mota shine rashin hankali? Ke kin manta kalan alkhairun da
marigayiya tayi min ne?”
“Ai marigayiya kace, wannan kuma ba marigayiya bace wallahi tun wuri a mai da
motan nan. Wani irin rashin hankali ne haka? Ban tab’a jin inda aka saima ‘yar 16
years mota ba.”
“Yau kinji ai tunda a gidan ki akayi, kuma ba miyar da motan da za’ayi, ina key
d’in mu shiga miki da motan ciki.”
“Gashi Baba” nan ta bashi key d’in, a parking lot daya gyara dan parking motansa
ya mata parking nata sannan ya kai nasa garriage, Mama da yaranta de suna ganin
ikon Allah yau. Kaka ta kira ta irga mata gashi fa Baba ya saiwa Zeezee mota bayan
ko gama makaranta batayi ba. Suna gama wayar Kaka ta kira Baba dan mai magana
aikuwa ya mata k’arya wai se Zeezee ta gama makarantar zata soma hawa.

Zeezee kam na can a d’akinta tana ta kan applying makeup tana gamawa taci farar
gown nata sukayi anko da motanta sannan taje ta cigaba da d’aukan selfie da motar
tata. Ranan snapchat seda yayi kuka haka instagram ma. Lubiee couldn’t believe it
dataga ansai wa Zeezee mota haka Adeel ma, shi shege girlfriend nasa na hawan C300
shikuma E350 4matic. Washegari Mariam tazo kallon motan *_‘YAR GATAN BABA_*

Cikin sati biyu Baba ya sa wani yaronsa ya koya wa Zeezee mota, tinting glasses
d’in tayi da darkest colour, hakan kuwa ba k’aramin karb’an motan yayi ba dake
farar mota ce. Kullum ba aikinta se wanke motanta, ko kad’an batason abinda ze
tab’a mata shi. Yau da La’asr ta d’au wanka ta feffeshe da turare sannan ta d’au
key’n motarta ta fice a waje taci karo da Mama “aikin kenan a penta fuksa a fita
yawon banza sa’o’inki suna karatun jamb da waec ke kullum cikin fita unguwa koda
shike ba laifinki bane na Baban naki ne tunda ya d’au mota ya baki.”
“Haters are gonna die.”
“Me kika ce?”
“Nace Allah barmin Maman Zeezee, gidansu Lubiee zani.”
“Zancen kenan kullum gidansu Lubiee. Seta gaji dake ai, ke bazaki zauna ki fara
karatu ba ko?”
“Wai Mama ce miki akayi yanzu ana karatun waec ne? Answer kawai ake suburbud’a wa
mutane.”
“Da kyau.”
“Eh man ku naku lokacin da ba’a baku ba flat F9 kuke fitowa dashi ba bayan
karatun da kuke, nide in Baba ya tambayi ina nake kice mai na tafi gidansu Lubiee,
ko akwai abinda kikeso?”
“Kan Uwarki nakeso ‘yar banza kawai.”
“Hohoho Maman Zeezee Allah barmin ke kiga ci gabana a duniya.”
“Mschww!” taja tsaki ta fice. K’arisawa gun motarta tayi ta hau gogewa akan
wankewan da tayi d’azu. Tana cikinyi Omar ya fito ya k’are mata kallo sannan yace,
“ke bud’emin gate.”
“Hehe! Su Ya Omar jiya ba yau bane fa. Levels don change yanzu, ni me sabuwan
mota pil bance a bud’en gate ba sekai da seda wani bature ya hau ya baka zakace na
bud’e maka?”
“Me kika ce?” yayi snarling at her.
“Babu nace barin gama gogewan na bud’e maka.”
“Da yafi maki kam” nan da nan ta gama ta bud’e mai yana fita itama ta fice. Music
nata ta k’ure tana kad’a kai tana driving ana tab’a rawan dab, hankalinta a ruwan
sanyi. Gidansu Adeel nata ta wuce, bayan ta samu gu tayi parking ta kirasa “hello
My Very Own.”
“Sweetest Love.”
“Kana gida ne?”
“Yup wani abu ne?”
“Nop just kafito bakin gate.”
“Okay right away!” nan yayi hanging. Wayoyinsa ya tattara sannan yayi glancing
kansa a mirror ya fice, yana fita bakin gate yaga Zeezeensa tsaye gefen motarta da
sunglasses maqale a fuskanta tana mai wani mayen murmushi, murmushin shima ya mayar
mata sannan ya k’arisa gun sukayi hugging as always kamar yadda suka saba sekace ba
‘ya‘yan musulmai ba. Bayan yayi releasing nata yayi pecking nata a kumatu “you are
looking super sexy Barbie.”
“I know right Very Own toh ya kake?”
“Lafiya, you didn’t tell me you were coming” yayi maganan yana wasa da siraran
yatsunta.
“I thought I might suprise My Very Own.”
“Best suprise ever!” ya sake pecking nata “so zamu shiga ciki ko we are going
somehwere?”
“Going somewhere just the two of us.”
“I love you Babe.”
“I love you much more My Very Own” ta mik’a itama tayi pecking nasa a cheeks
“lets go, hurry I’ll be the one to drive.”
“No way my Queen, allow your King to drive you.” Shi da kansa ya bud’e mata motan
ta shiga sannan ya rufe ya zagaya ya tada motan suka fice zuwa Hysaan beverages ya
siya musu roasted chicken da drinks daga nan suka wuce can bayan gari inda ba
mutane yayi parking. Suna cin kazan su suna hira har suka gama se kusan to 6pm
Zeezee ta isa gida.

*~ *~ *~``
Haka deh Allah ya cigaba da raya Zeezee har suka samu sukayi jamb nasu ta fito da
205 points. Ita kanta bata zata zataci ya kai haka ba saboda bawani karatun kirkin
datayi as always tana kan waya da Adeel nata. Dama Baba yayi promising nata kan
intaci fiye da 200 points ze sai mata duk abinda takeso, iphone 7s tace takeso
aranan aka sai mata shi, haka tayita cika ‘yan instagram da snapchat da pictures na
iphone 7s nata. Ana cikin haka bikin Ibraheem da Fateemah ya taso, preparation suke
sosai ‘cause this is the first time Baba da Mama suke aurar da d’an su na miji. Not
long enough aka soma wedding events, Zeezee de kam har ta kusa fin amarya shan kyau
dan kuwa har Abj ta tura akayi mata gowns nata. Makeup artist da tama amarya makeup
kuwa ita tayi mata nata.

Se palli take da rawan kai. A ranan dinner ta d’au mutane cikin motar tama tak’i
ba yadda Mama batayi da ita ba amman tak’i, agun dinner kuwa table nata ita da
Lubiee, Adeel, Uthman (boyfrined na Lubiee) seda friends nasu guda biyu ta tanadar
musu suka zauna. Angama komi aka kai amarya Abuja. Zeezee dad’i kasheta yanzu ba Ya
Ibraheem d’an shisshigi, cin duniyarta zatayi da tsinke hankalinta kwance. Wannan
kenan!

Tunda Ibraheem yabar gidan iskancin Zeezee ya k’aru, daman ba wani tsoron Ya Omar
take ba, hakan yasa ta sake raina Mama kota mata magana se in ta gadama tayi, cikin
sa’a suka soma waec nasu har suka gama saura neco suyi goodbye da secondary school.
D’an hutun dake tsakanin waec and neco Zeezee ta had’a akwatinta zata Abuja gun Ya
Ibraheem simply because taje taga kalan zaman da suke da matarsa badan wani abu ba.
Ta jirgi Baba ya biya mata, 1pm suka yi landing. Ibraheem da Fateemah duka sukaje
d’aukota daga airport bayan angama hugging da gaisuwa suka dawo gida. Baki Zeezee
ta sake data ga mansion na Ibraheem ashe de magabata basuyi k’arya ba irin wannan
gida! Mschww ita da tasan Ibraheem zexo yayi kud’i haka data had’a Aunt na Lubiee
da Ibraheem akan wanan Fateeman, haka kawai Zeezee ta tsaneta.

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 23

*December, 2016*

A guest room ta sauka, bayan ta watsa ruwa ta fito tana bin gidan da kallo, a
kitchen ta tarar da Fateemah tana had’a lunch “sannu Aunty Fatee” tayi maganan cike
da gatsine.
“Yauwa Zeezee har kin fito ne?”
“Eh ina Ya Ibraheem?”
“Yanzun ya fita ya koma office.”
“Ohh gidan Yaya na yayi kyau ba laifi.”
“Ko? Toh mungode” A zuciyarta tace _ya gode ko kun gode? Sekace tare kuka gina
gidan, over sabi._
“Chab! Amman kam Aunty Fatee kin k’ara k’iba abincin gidan Yayana na aiki.”
“LOL koh? Kije ki d’anyi kallo kafin na gama had’a lunch d’in” chan k’asa-k’asa
Zeezee tace, “da yafi maki kam dan ba assisting naki girkin zanba hutu na zoyi
ehe!”
“Na’am kikace meh?”
“A’a babu nace sannu da aiki ni zan d’an zagaya ta cikin gidan, naga kaman akwai
garden.”
“Eh akwai bismillah.” D’akin data sauk’a ta koma ta d’au wayarta sannan ta wuce
garden d’in se videon kanta take tana posting a snapchat haka ta tayi har seda
Fateemah ta kirata kan lunch is ready. Cikin nutsuwa suka gama cin abincin agun
Zeezee tabar plate nata, Fateemah da kanta ta tattara tayi wanke-wanke. Kallo
kad’an Zeezee ta tab’a ta koma d’aki ta hau waya da Adeel nata. Se 5pm da Ibraheem
ya dawo tafito ta mai sannu da zuwa nan sukayi proper gaisuwa ya mutan gida da komi
da komi. “Kinbar rashin kunya kokuwa har yansu halin naki na nan?”
“Ni daman ina rashin kunya ne?”
“Allah sa toh, bazaki ci abinci bane ke?” Yayi maganan yana zama kan kujerar
dining da Fateemah taja mai.
“Munci da Aunty Fatee d’azu.”
“Oh okay” nan Fateemah tayi serving nasa tare da zama gefensa tahau feeding nasa.
Baki Zeezee ta sake wangalau tana kallon ikon Allah. Yi tayi kamar tana kalllon TV
amman hasali hankalinta akan su yake bayan ya gama cin abincin ya rik’o hannun
Fateemah “zamu shiga ciki Zeezee feel at home.”
“ko baka fad’a ba ai” tace tana bin interwined hands nasu da kallo suna b’acewa
ta tafe hannunta “oh! iskanci a idona yau, kome zasuyi acikin d’akin kuma se Allah
hehehe! Su Ya Ibraheem manya” kallo ta tayi chan da kallon ya isheta ta hau
chatting. 6:30pm Ibraheem yafito sanye da jallabiya “lokacin Sallah yayi seki
tashi.”
“Toh ni banayi.”
“Ya miki kyau ni na tafi masallaci.”
“Allah kare toh” yana fita ta mik’e zunbur ta nufi d’akin da taga sun shiga
d’azu. Fateemah ta tarar da hand drier a rik’e a hannunta tana d’aure da towel both
a jikinta da kuma kanta. Wani shegen kallo Zeezee ta bita dashi ina irin nasan me
kukayin nan. “Uh Aunty Fatee ashe d’akinku na shigo na zata nawa ne.”
“A’a naki na k’arshen corrider by your left hand.”
“Aihoo amman wanke kanki kikayi ko?”
“Eh” ta amsa a takaice.
“Ohh amman meyasa? Naga sabon kitso ne akanki.”
“Ermm... Eh normally idan nayi wanka haka nake sena wanke kan.” tayi maganan tana
neman ignoring topic d’in.
“Wow wierd! Ga kuma ko ina tsaf a d’akin illa kan gado sekace anyi dambe akai.”
“Zeezee kije kiyi sallah kinji? Nima yanzu zanyi.”
“Nikam bana Sallah bazan taya ki gyaran gadon kafin Ya yadawo.” Ganin ta nufi
gadon Fateemah tayi saurin shan gabanta “a’a bari karki damu ai hutu kika zoyi ba
aiki ba zan gyara da kaina nagode.”
“Allah Aunty Fatee kibari na gyara miki.”
“A’a Zeezee kibari nagode” haka suka tayi seda Zeezee ta wahalar da ita ta
hak’uran tare da ficewa “‘yar is.. ai da kin bari na gyaran naga me kike b’oyewa,
ai wallahi sena hanaku sukuni keda Ya” tayi maganan tana mik’ewa kan gadonta.

Washegari ranar ta kasance Saturday ba aiki, tun 9am su Ibraheem suka tashi
banda Zeezee dake ta sharb’an bacci. Shi da Fateemansa suka had’a breakfast suka
karya sannan suka ajiyewa Zeezee nata se 12noon ta tashi tayi wanka ta shirya
sannan ta fito. A parlour ta tarar dasu suna hira suna kallo Fateemah ta kwanta
jikin Ibraheem comfortably sekace ‘yar baby. Seda Zeezee ta k’are musu kallo sannan
tayi gyaran murya nan Fateemah tahau k’ok’arin d’agowa daga jikin Ibraheem, ganin
haka shikuma yak’i saketa “toh in bazaku gyara ba ina kwananku.”
“Baby ka sakeni please” Fateemah tayi maganan can k’asa-k’asa.
“Ko gaisuwan ma bazaku amsa bane Lovey-Dovey?”
“Kin fara koh? Baki bar halin nan naki na rashin kunya ba ashe.”
“Hali zanen dutse, kuma ai naga akan gaskiya na nake, inba neman ku b’atani ba
taya kunji motsi na bazaku d’an gyara ba?”
“Yi hak’uri Zeezee ga can breakfast naki a dining.” Fateemah tayi stating
shamely.
“Apologies accepted, me kika girka?”
“Chips ne da omalet.”
“Nikam banason chips indomie nakeso.”
“Ga kitchen ai seki shiga ki dafa ko ita Fateeman kikeso ta girka miki?”
“Aiko tanason girkamin d’in ma ba barin ta zakayi ba yadda kawani damk’eta ajikin
ka sekace za’a sace maka ita, you may carry on na wuce kitchen.” Anan ta fice kai
kawai Ibraheem ya kad’a Fateemah na murmushi tace, “Zeezeenmu se a hankali.”
“Ai nakega kafin ta gama hutun nata seta bugu zatayi hankali, tad’an manta ni ne
two days”
“No Baby banda duka please.”
****
Bayan Sallan Azahar Fateemah ta shiga had’a lunch, Ibraheem na dawowa yaga
Zeezee zaune a parlour tana kallo while Fateemah nacan tana aiki. “Ke bazaki je ki
taya Aunty’n ki aiki bane?”
“Ya aiki nazo yi ko hutu? Danfa Mama na tak’ura mun agida yasa nazo nan dan na
d’an huta, nan d’in ma kace wai sena taya Aunty Fatee aiki? Da bani nan wake taya
ta?”
“Karkiga fa dan kinzo hutu ki zata wai bazan iya dukanki ba tam! is better kiyi
minding tongue naki.”
“Toh Ya amman nazo hutu kuma sekace senayi aiki.”
“Sekinyi tashi kije ki sameta.”
“Ni wallahi-” ganin ya nufi kanta ta mik’e a 360 se kitchen d’in tana cunno baki
tana gun-guni “lafiya dai ko Zeezee?”
“Wani irin lafiya wannan mijinkin wai sede nazo na tayaki aiki sekace ba hutu
nazo yiba.”
“LOL toh karki damu jeki cigaba da kallon ki yanzu ma zan gama.”
“Yauwa toh ki fad’a mishi yaji karya daken.”
“Baby! Aww sorry Ya Ibraheem!” ta kirasa.
“A’a ni koda Baby’n ma kika kirasa ba matsala nide in baze daken ba shikenan.”
“Yes Sweetheart” yayi magana yana k’arisowa kitchen d’in “me kike tsaye achan
bance kiyi assiting Fateemah ba?”
“A’a Baby kabarta please kaga ba dad’i hutu tazo let her be. Ai aikin ma ba yawa
yanzu zan gama.”
“Wai ance miki anayiwa Zeezee abinda takeso ne? Ko washing dishes ne kibata.”
“Seriously Babe let her be na gama komi jekiyi kallonki Zeezee.” Gwalo Zeezee
tama Ibraheem tazo wucewa ya danna mata rank’washi akai “Allah ya-”
“Me kika ce?” tana murza wajen tace;
“Nace Allah saka maka da alkhairi” ta gyara zancen nata. Ita de Fateema dariya
kawai take sha’anin Ibraheem da Zeezee se kallo.

★*★*★*★
Haka fa Zeezee ta cigaba da moran hutun ta gidan Ibraheem, ba aikinda take komi
Fateemah keyi koda Ibraheem yace tayi se Fateemah tace a’a tabari zatayi da kanta.
In garin Allah ya waye Zeezee sede tayi wanka tayita d’aukan hoto, chatting, waya
da Adeel da kuma kallo. Sekuma ta bari Ibraheem da Fateemah sunyi d’aki seta ruga
aguje ta shiga ciki ba notice ta hau ihu wai taga kyankyeso ko b’era. Gabad’aya ta
hana Fateemah sukuni dan ita Fateemah ta rage kalan love da take bawa mijinta amman
dukda haka Zeezee bata gani bale tad’an rage mata wani abun.

7:48AM Fateemah da Ibraheem suna tsaye gaban dressing mirror tana mai bottling
shirt, tana gamawa ta d’aura masa necktie dai-dai tazo basa goodluck kiss kenan
Zeezee ta bankad’e k’ofa yau harda ‘yar kukanta. A firgice Ibraheem da Fateemah
suka juya suna kallon ta, duk kunya yabi ya ratsa Fateemah “uhm Zeezee lafiya?”
tayi saurin tambaya. Kuka tasa gun ta k’arisa wajen Ibraheem da gudu tare da
hugging nasa tana kuka. “Wai meke danunki ne? Ko aljanu sun shige kine bamu sani
ba.” Ibraheem yayi maganan a bit confused. “Sakeni toh!” Sake matsesa tayi ajikinta
“Ya tell me its a dream Baba be mutu ba tell me please” ta hau rusa kukan
munafirci.
“Mutuwa kuma?”
“Maybe mafarki tayi” Fateemah ta amsa shi.
“Toh sakeni mana Baba be mutu ba da Allah mafarki ne.”
“Tsoro nakeji” ta cigaba da sobbing, hannu Fateemah tasa zata jata daga jikin
Ibraheem ta bata warm hug instead aikuwa Zeezee tak’i, haka ba yadda Ibraheem ya
iya yayi hugging nata back yana caressing bayan ta nan munafukan ta b’ullo da rabin
idonta tana kallon sauyin yanayin fuskan Fateemah dan dole taji tokari a zuciyarta
dukda tasan siblings nesu amman kishi irin namu na mata baze barta ba. Sun kusan
minti uku a haka sannan ta d’ago daga jikinsa “shikenan?” ya tambayeta
“Eh nagode.” Kai yayi nodding “koma kije ki kwanta toh ba abinda ya samu Baba,
zan tafi office if you need anything else ga Fateemah.”
“Toh Allah ya kare.” Nan ta fice tana murmushi ita kad’anta tana isa d’aki ta
baje kan gado “right timing nayi ashe, wannan Fateemah ta fiye iskanci wallahi
kullum cikin kissing Yaya shikuma sekace zombie yata biye mata mschww! Ai wallahi
muddin ina gidan nan sekun dawo salihan dole. Ko a babu nasan na sosa miki rai.”
Bacci takoma se 12noon as always ta tashi tayi wanka ta shirya tsaf sannan ta fita,
breakfast nata ta tarar a dining ta bud’e ta gama ci sannan ta shiga k’wala wa
Fateemah kira, daga d’akinsu ta amsa nan Zeezee ta bud’e ta shiga ta sameta zaune a
k’asa tana gyaran wardrobe nata.

“Sannu Aunty, gyaran drawer kike?”


“Eh wallahi Zeezee harkin karya?”
“Eh bazan tayaki.”
“A’a bari karki damu.”
“Allah kibari na tayaki” nan suka shiga gyara mata. Ashe dekam Zeezee da biyu
tace zata taya tan don tun kafin ayi bikin, cikin kayan lefen taga wani lace daya
mugun mata kyau ba yadda batayi da Ibraheem ya bata ba yak’i gakuma koda ta duba
shagunan Baba duk babu.
Tana cikin had’a mata wardrobe d’in taci karo da lace d’in ko d’inkawa ma
Fateemah batayi ba “wow!” Tayi exclaiming. “Aunty Fatee wallahi wannan lace ya
had’u gashi favorite color na black and red kap Bauchi na duba ban samu ba.”
“Haba kina so ne?”
“Sosai ma wallahi.”
“Toh shikenan ki d’auka na baki.”
“In d’auka?!” tayi maganan unbelievably bata d’au Fateemah is as sweet as this
ba. “Eh ki d’auka ba kina so ba? Na baki.”
“A’a Aunty ai naki ne.”
“Banason haka fah, nace ki d’auka.”
“Wow! To nagode Allah saka da alkhairi” nan ta cigaba da ninke mata kayakin tana
cikinyi taci karo da wani white blouse daya mugun mata kyau again gashi always same
as her size nanma tayita zuzuta shi haka Fateemah ta d’au ta bata a takaice seda ta
kwashi kayakin Fateema har hud’u da shoe and bag guda d’aya sannan taji dad’i. Cike
da jin dad’i taje tasa cikin akwatinta. Kitchen Fateemah ta zarce ta shiga had’a
lunch sede tun d’azu kasala ke damunta tana cikin soya kaza ta soma jin amai take
ta nufi sink ta shiga kwararowa, nan fa uwar gulma ta shigo kitchen d’in a 360 a
ranta tace _bade ciki ba!_
“Aunty Fatee lafiya? Subhanalli me kikaci haka? Sannu” nan ta tayata ta d’auraye
bakin ta.

“Dama bakida lafiya ne?”


“Kar ki damu am fine something just came over me.”
“Ahakan ne you are fine? Bari na kira Ya.”
“A’a barshi karki tada mishi hankali a off-” bata k’are maganan ba tasake juyawa
sink ta cigaba da kwararo amai tana iddawa Zeezee ta d’au waya ta kira Ya Ibraheem
kan gida ba lafiya. Not long enough ya iso hankali a tashe, Fateemansa ya tarar
zaune a kasalance kan kujera. ”Omg! Sweetheart whats wrong?”
“Babu nifa seda nacewa Zeezee karta kira ka tak’i jina, am fine.”
“Wallahi batada lafiya Ya amai tayi sau uku fitanka.”
“Baby kinci wani abu ne?”
“Wallahi I don’t know I keep on feeling nauseatic and weak.”
”Humm kinci wake kenan” cewar Zeezee. Sam Ibraheem be gane me hakan ke nufi ba,
ita Fateema data gane se kawai tayi shiru.
“Wake taci ya b’ata mata ciki?” Ibraheem ya tambaya.
“Ai bama ita taci ba Ya, kai ka bata dan haka se kuje asibiti.”
“Nikuma? Yaushe?”
“Yo ina zan sani abu acikin duhu kuje asibiti de kafin jikin nata yayi worse.”
“Uhm Zeezee d’an kashemin gas d’in muka dawo zan gama soya chicken d’in.” cewar
Fateemah.
“Ga Zeezee seta k’arisa ai kafin mu dawo.”
“Wallahi karna k’ona kace zakamin duka gomma na fad’a maka tun yanzu ban iya soya
kaza ba wallahi.”
“Ko kunya bakiji ba da girman ki mschww”
“To meh abin kunya aciki? Wanda taci wake bata ji kunya ba seni, ko ince wanda
yabada wake beji kunya ba seni?” kai kawai Fateemah ta kad’a.
“Wai me kike fad’a nekam? Wuce kije ki kashe gas d’in useless kawai. Kinsan gomma
kin nutsu kin fara koyan girki ko?”
“Ai nagama secondary school zan fara koya bari na d’au ma Aunty Fatee mayafinta
nima zan biku.”
“Kina gida ba inda zaki.”
“Allah sarki mana Ya.”
“Baby ni kawai kabarta taje jeki d’aukomin mayafi na akan gado Zeezee.” Da ‘toh’
ta fice. In less than 30 minutes suka isa asibiti nan akayiwa Fateema gwaji, not
long enough result ya fito nan aka tabbatar musu juna biyu ne d’auke da Fateema.
Dad’i kashe wannan happy couple banda Zeezee dake binsu da kallon tsiya “kome abin
murnan oho? Dama kam akayi ai dole sakamako ya fito mschw kunada aiki wallahi.” Se
anan Ibraheem ya fahimci zancen Zeezee na d’azu batun wai shiya bawa Fateemah wake
taci oh! Allah ya shirya masa Zeezee yarinya sam ba kunya. Haka suna isa gida
Fateemah tad’an huta tace zata cigaba da suyan sam Ibraheem ya hanata shida Zeezee
suka k’arisa suyan nan ma seda ta k’ona kanta ta k’ona shi duka.

Tun daga nan fa rayuwan Zeezee gidan Ibraheem ya soya. Wani irin d’an banzan
laulayi ne da Fateemah, ko tsayuwan kirki bata iyayi dan haka bata iya aikin komi,
duk wani aikin gidan Zeezee keyi banda girki saboda daman bata iya ba dan haka
Ibraheem ke cikin siyo abinci ba dafe ba dare. Zeezee kullum cikin k’orafi ita
wallahi hutun ma ya isheta zata koma gida.

*~ *~ *~
“Zeezee! Zeezee!” Ibraheem ya kira ta daga ciki.
“Na’am” ta amsa tana zaune a parlour seda ta gama d’ura ashar sannan ta mik’e ta
nufi d’akin nasu “gani.”
“Ki had’awa Fateemah custard.”
“Ni ban iya ba.”
“Baby she don’t have to kabarta please.”
“Had’a custard ma baki iya ba? Cinki za’a zo ayi ne?”
“Ni wallahi zan koma gida nagaji da ni nace tayi cikin.”
“Me kike ce?” yayi tambayan in a serious tone daya razana Zeezee.
“Babu nace barin je na had’a mata sannu Aunty Fatee” tana kaiwa nan ta fice in
less than 15 minutes ta had’a ta dawo kad’an Fateemah tasha Zeezee ta miyar da
sauran, ga wanke-wanke nan tun na jiya da rana bata wanke ba. Da yamma Fateemah
tad’an warware ta fad’a kitchen se gani tayi wanke-wanke nayi mata sallama. Kai
kawai ta kad’a ta shiga wankewa tana cikin yi Ibraheem ya shigo “Sweetie wanke-
wanken meh kuma bayan kinsan you’re sick, kibari Zeezee zatayi.”
“Naga kaman muna tak’ura mata dayawa kabari yanzu zan gama.”
“Kibari nace, Zeezee zo nan!” seda ta gama b’ata lokaci ta fito “gani.”
“Oya karb’i wanke-wanken ki gama.”
“Allah sarki Ya kabari ko zuwa gobe mana, yau fa nayi shara.”
“Meaning? In anyi shara ba’a wanke-wanke kenan?”
“Ni wallahi zan koma gida nagaji.”
“Ai tunda kika kawo kanki sekun kusa fara Neco zaki koma gida.” K’afa tahau
bugawa amman kota kanta beyi ba yaja Fateemah suka fice. Harara tabi wanke-wanken
da sannan daga bisani ta d’aga wuk’a ta yanke yatsanta dagangan nan jini yahau
bulbula. Wani irin rikicaccen ihu ta saki Ibraheem besan a lokacin da yafito ba
“amman lafiyan ki kuwa?”

“Wayyo Allah yatsa na, jinin jikina ze k’are na shiga uku!”


“Meya sameki?” yayi maganan yana k’arasawa gun sink d’in, kawai gani yayi hannun
Zeezee na jini sosai.
“Subhanallahi! ya akayi kika yanke haka?” Tap ya bud’e yasa yatsantan nata
underneath, se ihu take bayan daya gama mata dressing ya kalleta “dagangan kika
yanke hannun naki dan karkiyi wanke-wanken ko?”
“Mahaukaciya ce ni da zan yanke hannu na da kaina? Ni wallahi yana min zafi.”
bakinta ya bige paw! “Nikuma me nace? Wayyo Allah hannu na, wallahi yana min zafi”
“Toh dama ba dole ya miki ba mschww!” shi da kansa ya k’are wanke-wanken ranan.
In 2 days time suka samu meh aiki dan duk yadda zasuyi sun san Zeezee bame aiki
bace.
One more week ta musu Yasmeen ta haihu ta samu d’anta. Nan fa Zeezee ta had’a
akwatinta har airport su Ibraheem suka kaita ya sallameta da 10k Fateema kuma 5k da
kuma turmin zani d’aya. Daga Abuja ta wuce Kaduna inda ta had’u dasu Mama, d’an
Yasmeen kyakkyawa kaman Babansa anyi suna yaro yaci sunan Kakansa (baban mijin
Yasmeen) Sulaiman. Bayan suna su Zeezee suka dawo Bauchi. Ko nunawa Mama kud’in
dasu Ibraheem da mijin Yasmeen suka bata batayi ba seda ta gama kashe kud’in
tukunah ta fad’a mata.

Kowa na preparation na Neco banda Zeezee data sa yawo a gaba, yau ma as usual by
11am ta gama shiri ta fita, ta shiga cikin gari tana ta driving da gudu kamar yadda
ta saba ta k’ure music, wayanta ne ya soma ringing d’agawan da tayi don ganin waye
kawai the next abinda tayi noticing shine wani Baba tsoho dake dab da gabanta.
Kafin ta ce zata danna brake harta bigesa. Kan motan ta juya da wuri hakan yasa ta
buga kanta jikin wani pole. Kaca-kaca gaban motanta yayi, wani irin ihu ta saki
daga nan bata sake sanin meya faruwa ba. A sume kanta na jini aka ciro ta daga
motan, ita da tsohon data mai k’ariya biyu dakuma fashewan kai aka tattarasu se
Teaching Hospital. Baba aka fara kira aka sanar dashi halin da ake ciki.

_45 minutes afterwards, Teaching Hospital..._

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
beeenovels.blogspot.com

PAGE 24

*December, 2016*

Tsaye Mama da Baba suke a corridor’n k’ofan da Zeezee ke ciki, kallo d’aya
za’ayi musu asan suna cikin babban tashin hankali sam sun kasa zama gu d’aya se
safa da marwah suke wajen. Ana cikin haka k’ofan d’akintan ya bud’u, kusan da gudu
su Mama suka nufi gun “Dr. How is she?” Sukayi tambayan in unison.
“You two must be her parents, am I right?”
“Yes” Baba ya amsa a yayinda Mama ta gyad’a kai.
“Karku damu she is in a stable condition, alhamdulillah bataji wani ciwo ba kanta
kawai tad’an fasa ta gefe wanda a sanadin haka glass ya samu ya shiga amman mun
cire har anyi d’inki yanzu haka ma zaku iya shiga ganinta.”
“Alhamdulillah” kawai ke tashi wajen “mutumin data bigen fah?” Baba ya tambaya.
“Eh an kawo min report nasa d’azu, kariya biyu ya samu a k’afa seda gefen kansa
daya fashe shima bayan nan alhamdulillah.”
“Toh alhamdulillah mun gode Dr. Bari mu duba ‘yar tamu.”
“Excuse me” yana kaiwa nan ya basu waje. D’akin sukayi rushing kwance suka tarar
da Zeezee kan gado ta rik’e gefen kanta da hannu “sannu k’anwata sannu” Baba yayi
maganan yana dafe kafad’arta.
“Sannu Zeezee how are you feeling?” asked Mama. Kuka tasa musu, da k’yar suka
samu tayi shiru “Baba kaina ciwo.”
“Ai dole ne dama Zeezee mugode wa Allah ma anan abin ya tsaya beyi gaba ba.”
“Baba mutumin dana bigen fah? Ya mutu?”
“A’a yana raye be mutu ba.”
“Alhamdulillah” tace.
“Hmm aini shiyasa ban goyi bayan wannan motar da aka siya mikin ba, yanzu da
tsohon ya mutu azumi sittin (60) ya hau kanki, kai kuma inhar danginsa suka k’i
yarda seka biya diyya, duk wannan wani irin tashin hankali ne?”
“Qaddara bata wuce ranarta Hafsah, koni nan zan iya yin hatsari nakai mutum
lahira, bawai zancen dan Zeezee is too young to drive bane.”
“Ai dama kai bazaka tab’a shiryuwa ba inba wai kuka da hawaye Zeezee ta saka ba.”
“Toh ya isa, yarinya batada lafiya ba suratai yakamata muyi ta mata akai ba,
godiya wa Allah ya kamata muyi tunda anan Allah ya tsaida qaddaran. Sannu ko
K’anwata kina jin yunwa?”
“A’a ni akaini gida banason zaman nan.”
“Karki damu bari jikinki yayi k’arfi.”

★*★*★*★
5 days Zeezee tayi a asibiti akayi discharging nata. Kusan duk friends nata
including Adeel sunzo sun gaisheta, shida Lubiee kanma kusan kullum suna kanta. 2
weeks ya d’auketa kafin nan ta warke gabad’aya, bada jimawa ba suka fara neco.
Motarta kuwa tuni Baba yakai aka gyara mata yadawo sabo k’al ba kalan jan kunnen da
Mama bata mai ba kan yabari se in sun gama makarantar yaso ya gyara mata amman inaa
yak’i. Zeezee kuwa ko bayan incident d’in bata shiryu tabar speeding kan hanya ba,
ana gama paper zata tara su Lubiee and others su fita yawo. Ranar da suka yi
Geography Adeel yazo school ya d’auketa daga school bayan sunci abinci a Mr. Biggs
suka wuce chan bayan gari ya nemi waje yayi parking se hirarsu suke sha gwanin
sha’awa. Wayarta ya d’aga yayi entering sunansa as password sannan ya shiga cikin
photos yana kalla, yana cikin haka yayi coming across pic na wani d’an saurayi ai
take ya fusata “waye wannan?” Ya tambayeta harshly. Koda ran Mama ne ya b’aci
Zeezee bata rikicewa haka se in na Adeel ne, “Very Own wani pic?”
“Wannan!” Ya nuna mata wayan. “Ko zakice baki san shi ba.”
“Nasan shi but Very Own calm down wallahi ba komai a tsakani na dashi.”
“Then meh pic nasa yakeyi a wayanki? Ban hanaki barin photos na maza a phone naki
ba? You’re cheating on me with him right?”
“Omg No! Am not, wallahi ba komai tsakani na dashi, he’s just a friend-” ya barta
tayi explaining kanta nma yak’i, ita kanta ta manta dalilin daya hanata goge pic
d’in.
“You are lying!” dan banzan zuciya irin nasa besan a lokacin da yayi wurgi da
wayan nata ba seta k’ofa yayi, raga-raga yayi kan kwaltan. Hannu Zeezee ta aza kan
bakinta in shock, hawaye kawai tasoma zubarwa, wayyo iphone 7s nata!
“Adeel wallahi ba saurayi na bane kaima kasan I only belong to you be kamata ka
fasa min waya ba.”
“Na fasan do something about it if you can, just shut up and get out, dama tun
ba yau ba nasan am not the only one.”
“Adeel idan ka sauk’eni anan a ina zan samu abun hawa kayi hak’uri please.” Wai
shi ya fasa mata waya amman ita ke basa hakuri while actually she can’t remember
when last ta bawa Mama hak’uri amman in Adeel ne kullum cikin basa hak’uri take.
“I said get out!” Ya tsawata mata sekace wani mahaifinta.

Gefen titi guda ta nufi ta tsuguna tana me cigaba da kuka abin tausayi, tafi
minti goma haka sannan daga bisani Adeel ya fito ya nufi inda take tare da mik’ar
da ita har a yanzu kukan take. A hankali ya share mata hawayen nata “am sorry
kinji?” Hugging nasa tayi tana kuka sosai “wallahi ba saurayi na bane, am not
cheating on you Adeel please believe me.”
“Is okay I trust you, am sorry kinji?” Har mota ya sata sannan ya tattara broken
pieces na wayar nata ya cire sim d’in cikin, yaja mota ya kaita gida. Tun shigarta
gida take addu’a Allah yasa kar ayi noticing yau wayanta bayi tare da ita. Da
Maghrib Zeezee na zaune a d’akinta abin duniya sun mata yawa ita yanzu in Baba ya
tambayeta ina wayanta me zata ce mai? Tana cikin wannan tunani Mama ta kirata
zuciyarta na harb’awa ta mik’e a sanyaye ta fice, “na’am Mama, sannu Baba” ta
gaishesa.
“Yauwa K’anwata sannu, yau lafiya dai koh najiki shiru?”
“Lafiya Mama kin kirani.”
“Eh wayanki zaki aramun nawa airtime ya k’are.” Nanfa Zeezee ta shiga raba ido,
“baki jini bane?”
“Naji Mama wayana ya fad’a a ruwa d’azu so na shanya.”
“Shine baki fad’amin ba akai miki gyara?” Fad’in Baba.
“A’a karka damu Baba ze farfad’o in shaa Allah.”
“No wonder yau ba’ayi ta d’aukan selfies na asara ba, jeki shikenan.” Kwana zaune
Zeezee tayi ranan as tana nazarin ina zata sake samun wani iphone d’in.

The next day Adeel ya kirata ta d’ayan line nata wanda duk ‘yan gidansu ma basu
san tanada wayar ba kan taje ta samesa a so so place, suna gama paper’n taje ta
samesa da motar ta. Kallo d’aya ya mata ya gano da akwai matsala murmushi ya saki
sannan ya tambayeta ya paper.
“Lafiya qalau” ta amsa sama-sama “why did you call for me?” hannu ya mik’a a seat
na baya ya fito da wani packaged leather jikin attached with a small card.
“Meh wannan?”
“Naki ne open it.” Amsa tayi ta karance letter’n amar haka;

_I’m sorry Sweetest Love for going wild mad at you yestarday, I hope you can
find it somewhere in your precious heart to forgive me am sorry. ILY_ D’an murmushi
ta saki sannan ta bud’e pack d’in, sabuwar rose gold iphone 7pro taga aciki kafin
ta tambayesa nawaye ne yace, “naki ne Babe, I’m sorry accept my apologies.”
“Omg! Very Own! You’re the most sweetest thing that has ever happened to me
thank you so much.”
“Your sim is ready, I love you.”
“I love you too” tayi hugging nasa. Bayan ta kunna wayan yace;
“Akwai wani d’an party’n da clique d’ina sukayi organising a Yankari I want you
to be there” yayi maganan yana shafa hannunta.
“Har Yankari Very Own?”
“Nan da Yankarin ne har?” Yayi maganan a bit angry.
“I’m sorry please don’t be mad ba wai ina nufin bazan je bane, I mean kaga yanzu
fa 4:30pm har yaushe zamuje Yankari in koma gida? Baba ya hanani staying late at
night.”
“Shikenan ke baki kai ki kula da kanki ba? Such a Daddy’s girl.”
“Bawai haka bane Very Own understand mana.”
“Da fitowa fili kikayi kikace you don’t love me it would have been better.”
“Omg! Adeel” ta kama hannunsa da nata bibbiyu, “please kabar fad’in haka wallahi
I love you morethan so much.”
“If you really do then do this for me Babe, be there I really want you to be
there.”

“Very Own-” katse ta yayi;


“Zakije yes or no? Stop wasting my time.” Shiru tayi totally speechless “I guess
the answer is no” yana kaiwa nan ya bud’e motar ya fice not minding ya rufe mata
k’ofan. Bayansa tabi ta shiga k’wala mai kira amman kota kanta beyi ba. “Adeel
please don’t go ka tsaya please...” yana kaiwa gun motansa ya shiga ya fice. Hawaye
ta soma yi a wajen unstoppingly da k’yar ta k’arisa gun motarta ta share hawayenta
sannan ta d’ago wayan ta shiga kiransa sede har 5 missed calls be d’auka ba.
Hankalinta sam baya jikinta ta shiga driving, ikon Allah kad’ai ya kaita gida.
Tana isa tayi wulli da kanta kan gado ta cigaba da rusa kukan seda tayi me isarta
ta mik’e ta watsa ruwa ta sake gwada layin Adeel har 2 missed calls be d’aga ba,
texting nasa tayi _Very Own you don’t have to be mad anymore, your happiness means
the world to me text me your location I’ll be there. ILY_

**
Yana a d’akinsa yana kan shirin zuwa Yankari message na Zeezee ya shigo, da kaman
baze d’aga ba sekuma ya bud’e bayan ya gama karantawa ya murmusa sannan ya kirata
take ta d’aga “hello Very Own I’m sorry dan Allah kayi hak’uri it won’t happen
again.”
“Thats my lady I love you.” Sanyi sosai taji a ranta “I love you more so where
will I meet you up?”
“Zanzo in d’aukeki.”
“Toh I’ll be waiting.”
“Aha and also kinsan how you’ll dress koh? Party-like”
“Yes Baby.”
“Yauwa Babe sena zo” yana kaiwa nan ya katse. Da sauri-sauri ya gama shiri itama
haka. Crazy pencil jeans trousers nata tasha da wani top dake nan kaman vest saman
sa had’e yake da sark’a dogo me fad’i black colour. Mininal makeup tayi applying
tasa assesories nata sannan ta b’urma babban hijabi kai ta fito that was by 5:20pm
kenan. “Ina kuma zakije?” Mama ta tambayeta.
“Kati zan siyo anan shago.”
“Toh Allah sa” batayi ta kanta ba ta fice a dai-dai wani shagon dake bakin corner
ta tsaya ta kira Adeel in less than five (5) minutes ya k’ariso. Ba tare da b’ata
lokaci ba ta shige ciki sede Ya Wakeel me shago yaga shigewarta cikin motar.
Pecking nata yayi a kumatu sannan yace, “ya da hijabi kuma Babe?”
“Don’t worry” hijabin nata ta kwaye ta wurga back seat “thats my babe you are
looking super sexy.”
“Thank you.” Motan ya ja suka hau tafiya ayayinda take d’aura kanta. Sun d’au
tsawon lokaci kad’an suka isa Yankari inda duk sauran party rockers d’in suke.
“Mu fita koh?” Hannunsa ta rik’e “Very Own promise me I’ll be safe with you ba
abinda ze sameni please” tayi pleading. Tausayi ta basa, hannun nasa ya cire daga
nata sannan ya kwantar da ita ajikinsa “don’t worry Babe, you are safe with me
nothing will happen to you. ”
“I trust you and love you.”
“I love you too lets go then.”

***
Loud music ke tashi wajen, gabad’aya ba wuta se turning club lights, maqale
jikinta tayi ana Adeel duk tsoro takeji seyanzu takeji dama ta sani da bata biyosa
ba, what if abu ya sameta yanzu? VIP table ya kaisu suka zauna sam tak’i sakesa,
abinci akayi serving nasu taci tak’i gudun kar ansa abin bugarwa aciki taci ta
bugu.
“Babe aiint you hungry?” Kai kawai ta kad’a masa “you don’t trust me?”
“I do, inda banyi trusting naka ba zan biyo ka nan ne?”
“Toh why won’t you eat?”
“Am not hungry” ta k’irk’iro murmushi.

_7:12PM_
Zeezee ta warware sosai har tayi new friends wasu ‘yan iska first class wajen,
se rawa suke suna goga jikinsu dana maza. Wayanta dake pocket nata ne ya soma
ringing tana kai dubanta taga Amiable Dad dum! Zuciyarta ta buga hannun Adeel taja
zuwa waje “Very Own Baba na kira na me zanyi please?” Tayi stating all confused,
wayar ya amsa a zatonta ma picking zeyi tayi saurin fad’in “no please karka d’aga.”
Gani kawai tayi ya kashe wayan gabad’aya.
“Adeel Baba na ne fa yake kira, how could you?”
“Babe kin cika tsoro, let them be you are safe with me.”
“Kabani waya na!” Tayi maganan a tsawace, kallonta ya tsaya yi ransa na tafasa.
Wayar ya wurga mata “mani kike d’agawa murya? Gashi kiyi duk abinda kikeso,
bullshit kawai!” yana kaiwa nan yabar mata gun. Hawaye ta shiga yi ga wayan a
hannunta ta kira Baba ta kasa gashi bata taho da motar taba bale ta koma gida,
Adeel is her only way back home. Ita yanzu ba Baba ba bakuma Adeel ba, bazata iya
yin 2-0 ba. Waje ta nema ta zauna tasha kukanta har seda ta godewa Allah sannan ta
share hawayenta ta gyara makeup nata ta koma ciki in the midst of some bitches ta
samu Adeel zaune se hira suke suna dariya. Wani irin wawan kishi taji ya rufeta
tsam amman she can’t blame him ita ta jawo komi.
A nitse ta k’arisa wajen, koda ya ganta beyi ta kanta ba, gabansa ta nufa,
“Adeel I’m sorry” tayi maganan a hankali, yi yayi kaman be ganta ba, “I said am
sorry please” hannunsa ya mik’a mata sannan ta jasa zuwa wurin da akwai privacy.
“Adeel am sorry please” sekuma ta rushe da kuka, kallonta ya tsaya yi daga bisani
yayi hugging nata “Babe if you’ll do as I say bazamu na fad’a ba, kidena crossing
d’ina.” Hugging nasa back tayi “I wont ever please kadena kula wancan hoes d’in.”
“If you’ll give me all of yourself and listen to me I won’t.”
“I’m all yours Adeel just promise me bazakamin abinda ze tab’amin pride (budurci)
d’ina ba.”
“Never Babe, your pride belongs to me but only if mukayi aure so stop worrying
yourself on that kinji?” Kai tayi nodding “I love you.” Hawayenta ya share mata
suka koma ciki suka cigaba da partying.

_9:21PM Gidansu Zeezee_


Dawowan Baba gida kenan wannan shine fitansa na tara tun d’azu yake neman Zeezee.
Duk inda yasan tana zuwa yaje ba Zeezee ba labarinta, har report yakai wa police
hankalinsa ya matuk’ar tashi sosai, bashi kad’ai ba har Mama da Omar.
“Ina K’anwata ta shiga? Ina aka kaimin K’anwata? Ba halinta bane staying late at
night, duk laifin kine Hafsah be kamata kibarta ta fita shagon ba, tunda Omar na
gida mesa baki aikesa ya siya mata katin ba?”
“Kamar ya laifi na Alhj? Kasan de Zeezee ba magana na takeji ba koda nace mata
kada tafitan eventually se tayi.”
“Toh baga irinta ba yanzu yarinya ta b’ata, wallahi duk abinda ya sami K’anwata
kisani kece sanadi mschw!” Yana kaiwa nan yaja motansa ya sake fita for the 10th
time yana zagaya unguwa yana tambayan mutane ko sunga Zeezee. Sede duk inda ya
tambaya se suce mai sun ganta ne lokacinda take dawowa daga school. At last ya wuce
shagon Ya Wakeel daya raina, aikuwa Ya Wakeel yace tabbas ya ganta tana shigan wani
Mercedes-benz bak’a dawani saurayi ciki.
“Zeezeen! Kaga tana shiga cikin motan wani?!” Baba yayi maganan disbelievingly.
“Tabbas! Na ganta da idanu na Alhj.” kai Baba ya shiga kad’awa.
“Wallahi k’arya ne ban yarda Zeezee na zatayi wannan abu ba kai de kawai kace
kana son yi mata sharri ne shikenan in bahaka ‘yar 16 years zakace tabi d’a na
miji? To zuwa ina?! Wallahi k’arya ne ba kalan tarbiyyan dana bata ba kenan.”
“Shikenan Alhj amman nide kam naga Zeezee tana shiga motan wani.” Ko k’arisa
sauraronsa Baba beyi ba yaja mota ya koma gida a fusace still not believing any of
Ya Wakeel’s words sede his words kept on dancing in his head. “Ya Alhj? Any good
news?” Banza da Mama yayi ya wuce d’aki, sam brain nasa yakasa comprehending abinda
Ya Wakeel ya fad’a mai, what if its true? Kai yayi saurin kad’awa “noo it can’t be
possible, sharri ne.”
“Sharri mawa Alhj?” Mama dake zaune a gefensa ta tambaya. “Dan Allah ka gayamun.”
“Hafsah wallahi sharri ne, Zeezee bata bi wani namiji ba sharri ne.” Zumbur Mama
ta miqe tare da dafe k’irji, “Zeezee tabi wani na miji? Innalillahi wa inna ilaihi
raji’un nawa yak’are nashiga uku!”

For the 1000th time Baba ya sake gwada line na Zeezee switched off.
“Hafsah kin yarda Zeezee zatabi wani d’a na mijin waje? Kin yarda?”
“Alhj ba batun na yarda koko a’a bane fatan mu Allah yasa yadda ya d’auketa ya
dawo mana da ita lafiya ba tare da yamata wani abun ba dan Ya Wakeel babban mutum
ne bazeyi wa Zeezee sharri ba.”
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, mena ma Zeezee a rayuwa da zatayimin haka
Hafsah? Yarinyan nan bata tab’a neman abu tarasa a k’ark’ashina ba, koda banida
hali zan kwatanta, mesa zatayimin haka? Mesa zata nemi tozartani cikin jama’a?”
“Alhj yanzu duk ba wannan ba addu’a zamuyi Allah sa ta dawo gida lafiya. Dalilin
dukannin wannan abubuwa kuwa shine ILLAN GATA daman ni seda na gaya, sam tarbiyyan
daka d’aura Zeezee akai gurb’arcacciya ne kaima kasani amman kak’i saurarona, ba
abinda nafi guje mana kamar rana irin ta yau yanzu inhar wani abin b’atanci ya samu
Zeezee ya zamuyi? Ina zamu sa kanmu acikin jama’a? Bama wannan ba in ta kamu da
ciwon zamani kaman Aids fah? Wayyo Allah ka rufa mana siri ka dawo mana da Zeezee
safe and sound.” wayarta ta ja ta sake gwada layin Ummien Lubiee kan ko Zeezee ta
biya chan, sede har yanzu amsar d’aya ce bata zoba, Allah sa a sameta. Lubiee kanta
couldn’t believe it dataji Zeezee bata dawo gida ba har yanzu, where could she be?

*© MIEMIEBEE*
👄👄👄👄
www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 25

*December, 2016*

Line na Zeezee tayi dialing sede switched off yake ta cemata don haka ta kira
na Adeel kusan 4 missed calls tamai be d’aga ba.

_Party hall, Yankari._


Rawa su Zeezee ke tasha, gabad’aya filin an bata ita da Adeel se cashewa suke
daman gwana ce when it comes to dancing, a jikinta ba inda Adeel be ta6a ba. Ko
sallan Maghrib basuyi ba to talk more of Ishaa, bayan sun gama cashewa sun yi
taking dance floor, aka hau applauding nasu. Hannunsa taja suka koma gefe suka
zauna bayan tasha ruwa ta d’aga wayansa dake kan table dan duban time. To her
suprise taga 10:02PM “o my Gee! Na shiga uku! Very Own k’arfe 10:02 banyi sallah
ba, nashiga uku Baba must have gone crazy looking for me, wayyo Allah na mutu!”
Tayi maganan kamar wacce zatayi kuka all confused.
“Calm down Babe we’ll go and pray now soon zamu tafi.”
“Very Own dan Allah mutafi yanzu na shiga uku me zan fad’awa Baba? Please do
something.” Hannunta ya kama ya had’a da nasa “calm down okay? You are not going
home at this night saboda nasan Baba will be very furious at you kibari se gobe.”
“What?!” Tayi maganan unblievably “har gobe? Kana nufin yau ba a gidan Babana zan
kwana ba? Please karka min haka ba haka mukayi dakai ba Adeel save me please,
wallahi Baba ze kasheni.”
“I told you to stop crossing me, don’t you trust me? Kika koma gida a daren yau
sun saki gaba sun rik’a miki questions kenan ina kikaje, if you’re not lucky har
dukanki zasu iya yi amman kika bari gobe da safe kika koma seki tinkaresu da kuka
kice wani ne ya d’aukeki jiya ya gudu dake, addu’a kika tayi Allah ya dawo dake.”
“How is that even possible Adeel? My parents are not dumb dan Allah ka kaini gida
I can’t sleep outside my Dad’s house.”
“In kinga nabar nan toh safiya tayi ne, ke mesa ba’a gayamiki magana kiji ne wai?
Tun da muka zo nan acikin friends d’ina kinga wanda girlfriend nasa ke basa matsala
ne inba niba? Cut it out okay? This is bullsh*t!” Key’n motarsa ya zaro ya wurga
mata “gashi seki tafin ai tunda ke ba’a tab’a gaya miki magana kiji mschw!” Yayi
hitting table d’in so hard da hannunsa.

Kuka ta shiga rusawa wajen if only ta iya driving late at night da ta tafin, da
tasan da haka da bata biyosa bama in the first place. Taya iyayenta suna raye bawai
aure ko tafiya tayi ba zata kwana a waje? Ita yanzu bama wannan ba what if shed’an
ya rinjayi Adeel yayi mata wani abin da daddare fah? K’ara volume na kukan nata
tayi amman ko ta kanta Adeel beyi ba, hasali wayarsa ma yake ta latsawa seda tayi
me isarta sannan ta share hawayen nata. _Adeel is my only hope, dole nayi kamar
yadda yakeso kokuwa nice da asara_ tayi tunanin haka a ranta. Key’n motar ta ajiye
masa kan table d’in, adalilin haka ya d’ago kai yana kallonta “kin fasa tafiyan
ne?” Kai kawai ta gyad’a mai.
“Why?”
“Because I trust you Very Own.”
“Then why did you cross me?”
“Because I was afraid Very Own ban tab’a kwana a waje ba se yau tsoro nakeji”
miqewa yayi ya jawota jikinsa “I’m with you, you are safe kinji?” Kai ta gyad’a a
hankali seda hankalinta yad’an kwanta ya saketa suka fice zuwa wani hotel not too
far from Yankari. D’aki ya musu booking seperately anan suka biya sallolinsu sannan
suka ci abinci. Sam hankalin Zeezee yakasa kwanciya ta kunna wayarta ma tsoro take
gudun kar Baba ya kirata ya shiga.
Kafin Adeel ya kwanta ya nufi d’akinta dan dubata, “hope ba abinda kike buk’ata
ko?” Kai kawai ta kad’a mai. “Don’t worry kinji? I’ve got you, gobe first thing in
the morning zan kaiki gida, I love you” yayi pecking nata a forehead.
“I love you too” ta fad’a a hankali nan ya ja mata k’ofan ya rufe. Yana juyawa
sega friend nasa Anaconda da wasu mata guda biyu ta each side nasa “ya Adeel? Don’t
tell me you are sleeping alone?”
“I am” yabasa amsa a takaice.
“Babe nakan fah meya sameta ko kunyi fad’a ne?”
“Nahh bata sallah ne” yayi mai k’arya.
“Ohh I see kona baka d’aya daga cikin nawa ne?”
“No thanks seda safe” yana kaiwa nan ya fice zuwa d’akinsa.
Kwana zaune Zeezee tayi gabad’aya takasa bacci tsantsan tashin hankali, tunanin
ya iyayenta za suyi da ita gobe kawai take. Achan gida ma haka ne Mama duk ta kasa
bacci as tana tunanin wani hali Zeezee ke ciki, kwana Mama tayi tana Sallah Allah
dawo mata da Zeezee gida safe and sound. Abin ya bata mamaki yadda hankalin Baba ya
kwanta lokaci guda gashi koda ta tambayesa any news seya ce mata babu.

_5:56AM_
Adeel yayi knocking bisa door na Zeezee, ba tare d a b’ata lokaci ba ta bud’e
“morning Sunshine.” Yayi greeting nata.
“Morning Very Own.” tace sama-sama.
“Owww don’t tell me you didn’t sleep yestarnight.” Yayi maganan hannunsa
k’ark’ashin fuskarta, kai ta kad’a tare da sauk’e hannun nasa.
“I couldn’t force myself into sleeping shiyasa.”
“So lets have breakfast?”
“No Adeel dan Allah ka kaini gida kaji please kayi hak’uri bawai ina crossing
naka bane kawai inason inje gida ne” tayi asking pleadingly.
“Okay Babe lets go.”

45 minutes drive yakaisu corner’n gidansu Zeezee. Tun anan tahau kakkarwa
hannunta Adeel ya riqo “all is well kinji karki damu, ba abinda Baba ze miki you
are his girl just tell him someone tried ro run away with you.”
“I’ll try.”
“Duk abinda akwai call me up kinji? Thanks for yestarday, I love you” yayi
pecking kumatunta. “I love you too” tafad’a da k’yar sannan ta bud’e k’ofan ta fice
seda ta shiga gida Adeel yaja mota ya tafi shima. A dai-dai bakin k’ofan ta tsaya
takasa going any further. Wani erin mumunar harb’awa zuciyarta ke, tafi minti uku
tsaye wajen sannan daga bisani tayi _womaning_ up ta k’arisa ciki. A dai-dai
lokacin Mama da Baba suke shirin fitowa da alama don cigaba da nemanta ne, tana
ganinsu ta wani mugun razana.
“Zeezee!” Mama da Baba sukayi exclaiming in unison. Kakkarwan take har yanzu
takasa ce dasu komi.
“Zainab kece?” Mama tayi maganan some inches away from her tana shafa hannunta.
“Nnn... Nice Mama” tayi speaking up finally in a low cracky voice.
“Alhamdulillah! Alhamdulillah Alhj Zeezee ce Allah ya dawo mana da ita, ina kika
shiga Zeezee? Meya faru?” Har anan Baba bece komi ba as se gallawa Zeezee harara
yake.
“Mm... Mama wani ne ya gudu dani” se ta rushe da kuka kaman daga sama kawai taji
sauk’an mari fas! A fuskarta seda taga stars dan azaba, kafin ta hankara Baba ya
sake k’ara mata d’aya. A rayuwarta bata tab’a shan zafin mari kamar na yau ba,
never once did she ever imagined that Baba ze tab’a d’aga hannu ya mareta. Da sauri
Mama taja crying Zeezee gefe d’aya “Alhj dan Allah kayi hak’uri hakan be kamata ba,
mu godewa Allah ta dawo gida shine babba.”
“Ta dawo? Mesa bata bi shi d’an iskan sun gudu gabad’aya ba?”
“Alhj please calm down ka tsaya muji daga bakinta mana ko bakaji tace wani ne ya
gudu da ita ba?”
“K’aryan banza waye yaro anan da zata raina masa wayo? Ke!” Yayi maganan da
Zeezee “kalleni nan! Kalleni nace!” A hankali tana kare jikinta a na Mama ta d’ago
jajayen idanunta tana kallon Baba “meya faru jiya?” ya tambayeta finally. Shiru
tayi tama kasa magana se hawaye kawai take a yayinda inda Baba ya zuba mata mari
keta mata rad’ad’i. “Bazakiyi magana bane sena baki kashi kome?”
“Bb... Bb.. Baba wallahi wani ne ya gudu dan-” bata k’are maganan ba Baba ya hau
kanta a fusace, da wuri Mama tajasa baya “Alhj kace zaka biye wa yarinyan nan
wallahi kasheta zakayi ko ka illata ta, kayi hak’uri dan Allah.”
“Ba gwara ta mutun ba na huta akan ta b’ata min suna, kap cikin dangina ba wanda
ya ta6ayin iskanci, akanki kuma” ya nuna crying Zeezee da yatsa “baza a soma ba
kina jina ko? Ina kika je jiya nace? Wani d’an iskan ne yazo ya d’aukeki and ina ya
kaiki? Kuma wallahi kika kuskura kikamin k’arya kinji na rantse bazaki kwana da rai
ba yau.” Shiru Zeezee tayi ta kasa magana se zubar da hawaye take endlessly.
“Alhj dan Allah kayi hak’uri bamu sani ba ko dagaske wanin ne yaso guduwa da ita
tunda kaga tadawo tana kuka.”
“Aikin banza, ajinki bana sane ne da party’n da sukayi organising jiya a Yankari?
Police excuse suka karb’a dalilin da yasa ban samu na bita har Yankarin na bata
kashi a wajen ba kenan, in kuma baki yarda ba ta kwaye miki hijabin nata kiga
abinda ke k’asa. Kwaye hijabin nakin!” Ya buk’aci Zeezee ko motsawa batayi ba, “ki
kwaye nace ko sena kwaye miki da kaina?” salati kawai Mama ta hau yi.
“Baba dan Allah kayi hak’uri, na tuba dan Allah kayi hak’uri.”
“Ki kwaye nace!” Kafin Mama ta hankara ya turata gefe ya nufi kan Zeezee.
Fincikota yayi da hannu d’aya sannan yaja hijabin nata seda ya cire. Sega Zeezee
nan da shirin party’n ta na jiya, wani marin Baba ya sake kai mata fiye da biyun
d’azu. Wani irin ihu ta saki seda Omar dake bacci yafito a gigice yana kallon ikon
Allah.

“Hakane wani ya gudu dake? K’arya zaki sake yimin akan laifin da kika aikata?”
Ya d’aga hannu ze sake kai mata wani bugin Mama ta shiga tsakiyarsu “Alhj dan
girman Allah kayi hak’uri inma dukan tan zakayi kayi da bulala bada hannu ba, dan
Allah nace” turata gefe yayi ya sake kaiwa Zeezee wani marin ihu ta shiga yi sosai
tana had’asa da Allah.
“Omar do something karya illata Zeezee please” cewar Mama. Da k’yar Omar ya samu
ya k’wato Zeezee daga hannun Baba don se ball da Zeezee yake tamkar bashi ne
mahaifinta ba, bayan Omar ta lab’e se rusa kuka take.
“Iskanci zakiyi a gida? Iskanci? Waye ubanki nace! Eyye! Har wai zaki kwana a
waje, Mariam da Yasmeen ba yayyunki bane da bazakiyi koyi dasu ba? Miqo wayanki nan
kuma kije ki d’auko duka wani gadgets naki including your car key” ganin bata motsa
ba ya daka mata tsawa “ko baki jini bane?!” Tana b’ari cikin wata dashasshiyar
murya tace, “naji” wayar nata ta miqa wa Omar yabawa Baba “wannan ne wayanki?” Ya
tambayeta.
“Omar wannan iphone 7 nawa ne? S ceh?” Da Omar ya duba seyaga pro ce “a’a pro ce
Baba.”
“Waya saya miki wannan d’in?” Shiru ba amsa, “waya saya miki nace?!” Ya daka mata
tsawa.
“Baba dan Allah kayi hak’uri.”
“D’an iskan saurayin naki ko? Lallai yarinyan nan kinyi nisa har waya saurayi ke
siya miki sabida bakida uba koh? Zaki sha mamaki baki sanni bane” Buga wayar yayi a
k’asa seda ta rugurguje “wuce kije ki tattaro min gadgets naki, keda waya kuma ya
k’are sede miji ne ze sai miki, wuce nace kafin na illataki anan!” Da gudu tayi
d’akinta ta tattaro su ipad nata da komi ta kai ta ajiye a tsakar gidan tana ji
tana gani Baba yayi rugu-rugu da komi a wajen daga kan ipad nata da mac book duk ya
faffasa su sannan yasa key’n motarta ta a aljihu.

“Ke wai iskanci kika sa a gaba koh?” Kai tayi saurin kad’awa “naki ya k’are a
gidan nan inkinga kin sake taka wajen gidan nan toh gawarki za’a fita dashi kokuwa
mijinki yazo ya d’aukanki, dan aure zan miki bazan zauna ina gani kib’ata min suna
a gari ba. Ace ni! Ni naje masallaci ana nuna ni da yatsa ga wacce ‘yarsa tabi
saurayi wallahi kinyi kad’an Zainab kina jina ba? Kinyi kad’an. Ko banzan Necon ma
bazaki k’arasa ba sadaqa dake zanyi in huta. Kuma Hafsah ku shirya yanzun nan aje
ayi mata gwaji ko tana tattare da wani cutan zamanin insan nayi da ita tun wuri,
nan da 2 weeks kuma zaku sake komawa kuyi mata pregnancy test ‘yar iska kawai abin
naki hauka ne? Bakida hankali ne? Mene ban miki ba a rayuwa da zaki saka min da
wannan butulci? Tambayar ki nake! Rai ne kawai ban saya na baki ba Zeezee. Duk
bakiga wannan ba zaki fifita saurayi akaina ni uban ki ko?! Har ki bisa kuje ku
kwana a waje, Karuwa ce ke nace? Yaushe aka haifeki da har zaki fara bin sauarayi?”

“Haba Alhj! Meyayi zafi haka? Abun duk be kai ga haka ba please.” cewar Mama.
“Baki jini bane? Inje in dawo baki aikata abinda na fad’an ba kiga abinda zan
miki kema, kaji ai Omar maza ka kaisu nan Reemee a gwada ‘yar iskan nan” yana kaiwa
nan ya fice yabar gidan. Ihu Zeezee ta k’urma har k’asa ta sauk’a tana kuka wane
zata cire ranta.
“Mama dan Allah ki rok’i Baba yayi hak’uri wallahi na tuba wallahi ni ban kwana
da wani d’a na miji ba, Ya Omar dan Allah ka tayani bawa Baba hak’uri.”
“Da Allah ja bakinki kimin shiru!” Mama ta tsawata mata “da uban wa yace kibi
saurayi har ki k’i dawowa gida ki kwana waje?”
“Mama wallahi ban kwana dawani na miji ba Ya Omar please believe me.”
“K’arya kike!”
“Mama wallahi ba k’arya nake ba please believe me.”
“Dana yarda dake da ban yarda dake ba du d’aya ne Zeezee saboda bashi ze canza
mind na Babanku da fact that you slept outside ba, ni dan Allah ki mik’e mu fice
asibitin kafin ya dawo.” Haka Zeezee na kukan cire rai suka fice asibiti inda aka
gudanar da all tests d’in aka kuma sa gynaecologist ta duba Zeezee ta tabbatar musu
virgin ce ita har yanzu. Seda result na tests ya fito suka dawo gida. Ko bud’ewa
Mama batayi ba ta kaiwa Baba dake zaune a d’akinsa. “Ga result d’in” amsa yayi ya
duba komi negative ne, d’an sanyi yaji aransa. Numfasa Mama tayi tace, “Alhj
yarinyan nan bawai taje tayi iskanci bane a waje kawai de kamar yadda ka fad’a
party ya tsaidata tunda an dubata ba’a ga alamun komi ba ya kamata ka sassauta
mata.”
“Nifa ban yarda ba inba iskancin taje tayi ba meze hanata dawowa gida jiya? Ko
bakida labarin a hotel suka kwana ne?”
“Hotel Alhj?! Dan Allah ya isa haka tunda gashi de anyi tests bata d’auke da
komai, Zeezee zata k’arisa rubuta Necon ta karka mata ruining future please.”
“In ke kike ajiyeta seki kaita school d’in gobe, ita bawai iskanci tasa a gaba ba
zan koya mata hankali bata sanni hane wallahi.”

“Maganan gaskiya kaima da laifinka Alhj, infact kaine sanadin komi tun farko da
baka mayar da ita *_‘YAR GATAN_* da batada flaws ba da hakan duk be faru ba. Sau
nawa Zeezee zatayi abinda ba dai-dai ba kaima kasani amman kak’i bata laifi ka
d’aure mata gindi. Sau nawa nake cemaka Zeezee na bin samari kak’i jina? Da kaji
magana na da duk hakan ya faru ne? Kaima you’re partially to blame.”
“And I accept my mistake Hafsah nasan nayi kuskure amman ban tab’a sanin dan ka
bawa yaro gata seya ta6ar6are ba. Yara nawa ake basu gata kuma su tashi da hankali
da nituswansu, itade Zeezee batada wayo ne kawai. A tunani na Zeezee zatayi making
d’ina proud da kalan gatan dana bata.”
“Sam ba haka bane Alhj, duk d’an daya zamanto ba ai magana, iyayensa suna barinsa
yanayin duk abinda yakeso a lokacin da yaga dama a tunaninsu wai wannan gata ne toh
wallahi ba gata bane, illa 6ata tarbiyya kuma surely zasuyi regetting some day.
Yanzu cikin Mariam da Yasmeen akwai wanda ya ta6a tafka rashin hankali irin wannan
ne? Kai ka nunawa Zeezee she is never at fault sannan kuma duk abinda tayi dai-dai
ne toh wallahi in har baka taka mata birki yanzu ba, gaba abinda zata mana semunyi
kuka tunda gashi nan ta fara yin hanya yanzu. Ina kira ga dukkan iyaye masu
sakankanta yara dan wai su sunje boko shikenan koda yaro yana ba dai-dai ba baza’a
mai magana ba, wallahi tun wuri sudena kafin azo ayita ihu bayan hari. Kaima Alhj
daka jini da a baya da duk hakan be faru ba.”
“Tabbas Hafsah ba k’arya acikin zancen ki, ban tab’a sanin gata nada illa ba se
yau, na d’au yadda na bawa Zeezee gata zan zo inyi alfahari da ita, nad’au duk
cikin yaran seta fisu hankali da nitsuwa da komi badan komi ba sedan yadda na nuna
mata so amman tabbas GATA yana da BABBAN ILLA. Shiyasa bazan bari abun Zeezeen yayi
nisa fiye da haka ba, aure zanyi mata tun wuri in huta kafin tamin abinda ze iya
tsinka min zuciya na fad’i na mutu.”
“Alhj ni ban hanaka yi mata aure ba amma de kabari tak’are necon nata tunda ta
riga ta fara.”
“Ba abinda zata k’arisa aure zanyi mata, in kinga Zeezee ta sake laying foot a
gate na gidan nan toh ko tayi aure anzo fita da ita kokuwa mutuwa tayi my decision
is final.”
*© MIEMIEBEE* *TEAM#YGC!*
👄👄👄👄

www.beeenovels.blogspot.com

PAGE 26
*December, 2016*

_Here’s a page in honour of my dear supporters, *Lieeymarh, Humairah Melody,


Princess Salmah, Khadijah👑, Aunty Jeedderh, Nusaiba Musa, Ashnur Pyar, Cute Xarah,
Xee Yabour, Leemcy, Princess Haleemah, Sumee Luv, Fateemah Maid and Zainab. A* I
love y’all so much #OneLove💞_

_In Zeezee’s room..._


Kuka take tasha tsakaninta da Allah wane zata cire ranta, ga kuma yadda kanta
keyi mata sari har wani dishe-dishe take gani, tunda take bata taa6 buguwa kaman na
yau ba, dukan Baba is uncomprable to Ibraheem’s. Hakan ta cigaba dayi sannan daga
bisani ta miqe kan gadon ta bud’e k’ofa sanadin knock dataji, Mama tagani bayan sun
iso sun zauna Zeezee tace, “Mama kin basa hak’uri ya hak’ura?” Kai kawai Mama ta
kad’a mata “tukuna kema nakega sekin basa hak’uri amman ba yau ba ko zuwa gobe
maybe ya tausaya miki ya hak’uran ko gobe kinada paper?”
“Eh inada amman Hausa ne.”
“Ko baki yiba ba matsala?”
“Ba matsalan chan” tasa kuka.
“Toh kukan ya isa mana, gayamin meya kaiki kwana a waje jiya Zeezee kika min
k’arya kuma zan fita harkanki gabad’aya nima.”
“Wallahi nima banyi niyyan kwana a waje ba Mama, da dare yazo yayi ne nace ya
kawoni gida yak’i wai se gobe.”
“Waye shi d’in? Saurayinki?” Kai ta gyad’a a hankali “me sunansa?”
“Sadeeq” tayi k’arya.
“Yanzu da Sadeeq damu suwa sukafi k’ima da daraja a idonki Zeezee dahar zaki bisa
party keba muslima bace? Iyyeh? Kuma da wancan tsinannen shirin kikayi ta yawo a
wajen? Nashiga uku ni Hafsah zaki halakar dani da raina. Irin tarbiyyan da na baki
kenan bani bama ko Baban naku ya tab’a cemiki kije party ne?”

“A’a Mama dan Allah kuyi hak’uri wallahi sharrin shaid’an ne baran sake ba,
please kima Baba magana kada yamin auren dole wallahi na tuba.”
“Kinsan da haka kika d’au hanyan iskanci? Aure dole a aurar dake Zeezee shi
kad’ai ze sa ki nitsu kiyi hankali.”
“Mama wallahi na nitsu ban sakewa. Ni shikenan bazan k’arisa karatu na ba?”
“Zaki k’arasa mana idan kikayi sa’an miji dan koni bansan mawa Babanki zeyi
sadak’an dake ba, inkuma ba’a dace ba keda bokon se in anayi a lahira.” Wani irin
kuka Zeezee ta sakewa rushewa dashi daga k’arshe ma Mama fice mata tayi daga d’akin
dan ko tak’i yin shiru. Seda tayi ta godewa Allah ta nufi bathroom ta wanke face
nata sannan ta fito tasa lock a d’akin ta ciro wata k’aramar Samsung galaxy a
wardrobe nata ta nufi bayi. Lubiee ta shiga kira and not long enough ta d’aga.

“Zeezee!” Tayi exclaiming. Batasan a sanda ta fara kuka ba “na’am Lubiee.”


“Zeezee what happened? Ina kika shiga? We’ve all gone crazy looking for you.”
“Lubiee dan Allah ki taimaka min ina cikin tsaka meh wuya.”
“Subhanallahi! Kina ina ne yanzu?”
“Ina gida-” katseta tayi da “alhamdulillah tunda kin dawo gida ina ba guduwa dake
aka so yi ba?”
“Lubiee I followed Adeel to a party a Yankari...” Kap ta kwashe labarin komi ta
bata ba tare da ta b’oye mata komi ba. “Innalillahi! Zeezee how could you? Mesa
baki fad’a minba kafin ki bisan? What were you thinking?”
“Lubiee I wanted to make him happy, he really wanted me to go and I love Adeel
morethan words can ever tell.”
“Toh yanzu meh Baba ya miki after making your so called Adeel happy?”
“Ya mammareni yasa akai min all Sexually Transmitted Diseases (STDs) tests
acewarsa wai naje na kwana da Adeel ne.”
“Yaaa Salam!!!”
“Ba nan kad’ai ba ya fasa min duka gadgets d’ina, yayi seizing min mota yakuma ce
bazan k’arisa Neco exams d’ina ba wai... Wai aure zemin” ta kuma rushewa da kuka.
“Please help me out.”
“Aure! Innalillahi Babe why all this? Mesa dan Allah? Da kin fad’a min zaki bi
Adeel party dana hanaki no matter what yanzu gashi ya kaiki ya baroki. After making
him happy look at what you’ve cursed upon yourself. Wallahi he won’t escape it sena
fad’awa Abba ya kirasa yamai fad’a shima tunda duk shine sila.”
“Inhar kina sona you won’t.”
“What do you mean?”
“Please don’t drag Adeel into this mess kibarshi please banason abinda ze tab’a
min shi.” Cike da mamaki Lubiee tace, “lallai Zeezee na lura baki san ciwon kanki
ba, infact baki ma san ina ke miki ciwo ba. Are you crazy? Taya zakice kar ayi
dragging nasa into this after all everything started with him.”

“I don’t care ni kawai karki had’a kansa da Abba please I beg you.”
“Zeezee meh Adeel ya miki haka? Why are you defending him like this?”
“Because I love him please karki had’a kansa da Abba promise me.” Shiru Lubiee
tayi, “please” Zeezee ta sake pleading.
“Alright naji.”
“Thank you.”
“Yanzu Zeezee ya zakiyi?”
“Lubiee I really don’t know zan gwada basa hak’uri ni bama Neco na bane ke damuna
auren da zemin d’inne. After saying sena gama degree nayi aure yanzu Baba yace
zemin me kike ganin su Sumayya zasu cemin, not this auren ma bada wanda nakeso
zemin bafa I can’t marry anyone else than Adeel.”
“How comes ke tunaninki takan Adeel kawai yake zuwa? Ke baki godewa Allah bama
da Baba be koreki daga gidansa ba? Believe me in Abba ne wallahi tsine min zeyi ya
koreni the day ban kwana a gidansa ba, but ke all you can think of is Adeel? Adeel?
Haba!”
“Ni da kori nan ma yayi dayafi min wallahi, I know Adeel will take care of me,
wallahi I can’t live without him ni banma san ta ina zan fara sanar dashi wannan
news ba.”
“You must be insane to think that way Zeezee taya zaki fifita saurayi akan
mahaifinki? Akan iyayenki? Ko bakisan bakida kamansu bane?”
“I know Lubiee amman I can’t afford to lose Adeel wallahi” ta rushe da kuka. Da
k’yar Lubiee ta samu tayi shiru tace zata kirata anjima when she’s calmed. Katse
wayar Zeezee tayi tafito ta miqe kan gado. Not long enough wayarta yahau vibrating
tana dubawa taga Adeel ke kira ba tare da b’ata lokaci ba ta share hawayenta tare
da clearing throat nata sannan takoma bayin tasa lock tayi picking.
“Halo Sweetest Love.”
“Na’am Very Own.”
“Thanks Gee! I’ve been trynna reach you but can’t get through meya samu d’ayan
line naki?”
“Uhm... Na had’a a charging ne.”
“Is that so?”
“Yeah.”
“Oh okay then how did things work out for you and Baba?”
“He believed me we all good.”
“Wow! Cool, I love you Babe and thanks for yestarday.”
“I love you too I’ll call you later.”
“Okay Babe take care.” Tana katsewa ta sake rushewa da sabon kuka haka ranan
Zeezee ta yini tana kuka ko cin abinci tak’iyi. Baba kuwa anytime Mama ta d’auko
masa maganan Zeezee sede yaja tsaki yabar mata gun.

Washegari da safe Lubiee ta kira Zeezee kan ya Baba ya hak’ura ya barta ta


k’arisa Necon ne?
“A’a wallahi Lubiee bayama son maganan zuwa anjima zanje na samesa na gwada basa
hak’uri.”
“Toh Allah yasa ya hak’ura sorry kinji?”
“Uhum and please koda Adeel yazo school yau kice masa nariga na tafi gida kinji?”
“Tom naji bye.” Bayan breakfast Zeezee tayi sallama a d’akinsu Mama, Mama ce
kad’ai ta amsa bayan ta shiga ta nemi gu ta zauna a k’asa.
“Ina kwana Baba?” Ko kallonta ma beyi ba bale yasan tanayi.
“Baba dan Allah kayi hak’uri, na tuba wallahi bazan k’ara ba kayi hak’uri dan
Allah.”
“Tashi kifita kibar min d’aki kafin na sab’a miki!” Yayi maganan cikin kakkausar
muryan daya mugun razana ta. “Baba dan Allah kayi hak’uri” tayi stating in a crying
tone.
“Alhj kayi hak’uri ka saurari yarinyan nan tunda hak’uri zata baka ba wani abin
ba.”
“Bazan sauraretan ba bana buk’atar hak’urin ta, tashi kifita nace.”
“Baba I’m terribly sorry dan Allah kayi hak’uri.”
“Bazaki fitan bane?!” Har tana neman cin tuntu6e ta miqe ta fice tana kuka sosai.
“Alhj ya kamata ka yayyafa wa zuciyarka ruwan sanyi kayi hak’uri yarinyan nan ta
gama exams nata, yau mafa suna da paper amman bata je ba.”
“Semeh? Ba exams da zata k’arasa wai ni zata tozarta a idanun jama’a!”
“Wai toh kai bakajin hak’uri ne kuma naga da baka d’aura Zeezee kan wannan
gur6arcacciyar tarbiyan ba da duk hakan be faru ba so kadena blaming nata ita
kad’ai.”
“Ya miki kyau.”
“Amman Alhj kayi hak’uri” nasiha sosai Mama ta tayi masa amman sam yace shifa ba
makarantar da Zeezee zata sake komawa.

Da Maghrib Zeezee na zaune a d’akinta ta had’a kai da guiwa se kuka take Mama ta
shigo “Zeezee tashi muje Babanki nason miki magana.” A sanyaye tabi bayan Mama
sannan ta samu gu ta zauna “gani Baba.” Kamar wanda bazeyi magana ba yace, “toh ki
bud’e kunnuwanki da kyau ki saurareni, dan Mamanku kad’ai zan barki ki k’arisa
exams naki kuma hakan bawai na nufin na sauk’o bane daga laifin da kika min. Omar
will be the one to take you and bring you back home, inhar kika taka inda ba school
ba ban yafe miki ba Zainab kuma ina kan bakata har yanzu kina gama Necon duk wanda
yazomin zanyi sadaqar ki masa koma waye ne tunda ke rayuwan bariki kika d’au wa
kanki.” Tana hawaye tace, “nagode Baba, kuma kayi hak’uri nasan nayi laifi amman it
will never repeat itself again dan Allah kayi hak’uri ka barni in cigaba da karatu
na.”
“Tashi kifita kibani gu!”
“Alhj kayi hak’uri ka saurari yarinyan nan.” Hak’uri sosai Zeezee tayita bawa
Baba tana kuka tsakaninta da Allah, shida kansa yagaji da jin hak’urin yace, “naji
tashi kifita.”
“Nagode Baba in shaa Allahu bazan sake tafka rashin hankali irin wannan ba inna
sake kamin duk abinda kaga ya dace dani” tana kaiwa nan ta koma d’akinta.

Washegari tun 8:15AM ta gama shirinta ta zarce d’akinsu Mama ta gaishesu sede
sam ba fara’a tattare da Baba ko kud’in break yak’i bata. “Toh ni na tafi.”
“Allah bada sa’a” cewar Mama.
“Ameen” ta amsa tana jiran ko Baba ma zece mata hakan sede kota kanta beyi ba dan
kanta ta fice zuwa d’akin Omar, “Ya Omar na shirya.” In less than 20 minutes suka
isa school.
“Nasan halinki Zeezee baki ta6a jin magana koda an miki, the reason why su Ya
Ibraheem dasu Mariam basu san wannan abu da kikayi ba is because of me ni na rok’i
Mama da Baba kar a fad’a musu saboda there is no point doing so. Kinfi kowa sanin
yadda ran Baba ya 6aci dan kanki sekiyi whats good Allah ya bada sa’a.”
“Ameen nagode Ya Omar amman wallahi believe me ni banje na kwana da wani na miji
ba party kawai naje.”
“Naji goodluck.”

Sosai Lubiee taji dad’i ganin Zeezee sun gama paper 1 a intervals Zeezee ta
labarta wa Lubiee all thats been going on lately. By 3pm suka gama exams na yau
immediately Baba ya aika Omar yaje ya d’aukota. Da tafiyan su befi minti uku ba
Adeel yazo, Lubiee kad’ai ya tarar wani erin mugun kallo take mai “Baby Sis ina
girlfriend d’ina?”
“Ajiyanta kabani?”
“Ohh why the act? Meya faru?”
“Ban sani ba yanzu kai ka kyauta kenan? Seka d’auki Zeezee ka kaita party kak’i
dawo da ita gida se a washegari, don’t you know the implications of doing so? Karfa
kamanta Zeezee ‘ya mace ce koda ba abinda ya shiga tsakaninku her parents will
think taje tayi iskanci ne a waje.”
“What gibberish are you speaking? Give me a break please, we all good, I told her
to set up a lie, and she did Dad nata believed her what else do you want me to do?”
“Oh haka ne?”
“Don’t you know? Ba abinda Babanta ya mata.”
“Yayi kyau.”
“So ina take?”
“Ta tafi gida batajin dad’i sosai.”
“Ohh ayyah, thanks then na tafi ki gaishe da Ummi.” Lubiee na isa gida ta kira
Zeezee, “mesa baki fad’awa Adeel abinda yafaru ba?”
“Kamar ya?”
“Mesa baki fad’a masa for what he did ya b’ata tsakaninki da Baba ba?”
“Sabida I don’t want him to feel guilty.”
“But why? He have to take the blame Zeezee.”
“No he don’t have to, I’ll alone banason abinda ze tab’amin Adeel na gwammaci ni
nayita suffering akanshi so please let things be the way they are for me please.”
“Toh shikenan as you say se jibi in mun had’u a school.” Suna gama wayan Adeel ya
kirata “Babe I went to your school earlier Lubiee tace you left you aren’t feeling
too good.”
“Yeah wallahi Very Own amman karka damu da sauk’i”
“And you didn’t tell me.”
“Sabida banason abinda ze tayar naka da hankali ne, I love you way much.”
“And I love you as much, get well soon okay? Your man loves you so much.”
“I love you too bye zan d’an huta”
“Okay rest well” tayi hanging. Fitowa tayi daga bayin ta mik’e kan gado tana
tunanin ya rayuwar ta zata kasance without Adeel. Da ta rasa sa ta gwammaci ta rasa
ranta, wannan kenan!

★*★*★*★
Haka rayuwan Zeezee ya cigaba da kasancewa kullum cikin k’unci. Har a yau kuwa
bata sanar da Adeel gaskiya ba, kullum cikin bawa Baba hak’uri suke ita da Mama har
suka samu suka shawo kansa yaja baya da zancen auren sadaqan da zeyi da Zeezee. Se
anan taji sanyi a ranta finally zata kasance da Adeel nata. Cikin ikon Allah suka
gama neco exams nasu a ranan sukayita having fun like never se da yamma ta dawo
gida.
“Haka kuma kukayi da uniform nakun?” Mama dake fitowa daga kitchen ta kalli
Zeezee da tayi rugu-rugu da uniform nata ko ina jiki autographs ne da marker sannan
kuma sprays.
“Mama makaranta fa muka gama.”
“Toh Allah sanya albarka.”
“Ameen Baba na gida?”
“A’a ya fita amman soon ze dawo.”
“Oh okay sannu da aiki toh” tana kaiwa nan ta fice zuwa d’akinta ta hau waya da
Adeel.
“What is tomorrow?” ya tambayeta.
“Tomorrow is my man’s birthday, you think I could ever forget your birthday? I
might forget mine but yours NEVER!”
“Awwn! I love you Barbie.”
“I love you too.”
“I miss your arms around me two days, lets meet up today please.”
“Very Own I don’t think you miss me as much as I do miss you wallahi amman kasan
I have to be vigilant yanzu sabida abinda yafaru recently in bahaka ba Baba yana
iya gano ni.”
“Hakane kuma but know that I miss you.”
“I miss you too Cuddle bear, so what do you plan on doing for your silver jubilee
birthday?”
“Nothing much, I’ll just be celebrating it here at Zaranda.”
“Oh really? A grand party?”
“Yes a grand one Babe, I’ll be turning 25 dole ai.”
“So by what time?”
“Its starting by 8pm ending till down.”
“8pm?!” Tayi exclaiming itan data d’au da safe za’ayi yadda zata samu taje.
“Yes you know you need to be there ko?”
“Sure I’ll be there for you, if I don’t who will?”
“Number one reason why I love you so I’ll come and pick you up.”
“Toh sekazo I love you.”
“I love you too.” Tana hanging ta fito daga bayin tana me tunanin ya za’ayi tayi
attending birthday’n Adeel, tasani inhar wannan karan ta sake fita da daddare da
k’yar abu su dai-daita tsakaninta da Baba amman kuma abinda ta sani for sure is she
can’t miss her Very Own’s birthday, not ever! Seeing batada way out ta kira Lubiee
“hello Babe is the cake ready?”
“Yyess almost sede bada wancan picture nakun akayi ba fa, da wanda ku kasa polo
shirt black and white akayi using.”
“Why toh?”
“An kasa minimizing pic d’in chan.”
“Damn it! Banso haka ba amman yayi kyau?”
“Eh karki damu zan miki sending sneak pic ta whatsapp.”
“Okay toh amman Babe da akwai matsala fah.”
“Meneh kuma yanzu?”
“Yanzu Very Own yake sanar dani wai birthday’n shin fa da dare za’ayi.”
“Da dare?!” Lubiee tayi exclaiming.
“Eh wai Babe ya zanyi dan Allah?”
“Ya kuwa zakiyi? Tell him bazeyi kije da daddaren ba.”
“Tell him? That will be the last thing I’ll ever do.”
“Zeezee baki horu bane waikam? You mean zaki sake binsa goben ma after what
happened kwanaki?”
“No amman I can’t tell him that I can’t attend his birthday.”
“Why not?”
“Because he is my Man Lubiee can’t you get it, ya kike tsammanin zeyi feeling ace
girlfriend nasa guda can’t make it to his birthday?”
“Toh kice mishi time d’in is inconvenient to you acanza a miyar 2-5pm haka.”
“No I don’t wanna be a burden to him.”
“Zeezee get brain kina jina koh? You are not attending this party inhar da
daddare za’ayi ni na gaya miki am calling Adeel up.”
“A’a Babe please don’t zan masa magana da kaina kinji please.”
“Better senaji daga gareki” nan tayi hanging. Safa da marah Zeezee tahau yi a
bayin sam tarasa meke mata dad’i she can’t miss Adeel’s birthday for the world to
ya zatayi yanzu? Tafi minti biyar tana tunani sannan daga k’arshe tayi making up
mind nata she’ll call him up and tell him what happened last time data kwana a
waje. Number’nsa ta shiga dialing and not long enough ya d’aga.

*©MIEMIEBEE* TEAM#YGC*
👄👄👄👄
wwww.beeenovels.blogspot.com

PAGE 27

*January 2017*

_Miemiebee👄 is hereby wishing all of her fans across the globe a very lasting
and fruitful new year. I love y’all from the buttom of my heart. #OneLove💞_

“Hallo Barbie.”
“Yes Very Own dama...” Sekuma tayi shiru.
“Uhumm ina jinki Babe, akwai wani abune?”
“Actually yes.”
“Okay am all ears.”
“Very Own please I don’t want you to think that you don’t mean anything to me
shiyasa na maka k’arya, know that I did it for the best, for you.” Jikinsa yaji
yayi sanyi acewarsa ma cheating tayi a kansa “ina jinki” yayi speaking up finally.
“Very Own ina time da mukaje party a Yankari?” Wane tana gabansa ya gyad’a kai
sannan ta cigaba “wallahi I lied to you nace maka Baba believed abinda na fad’a
masa actually he didn’t tun kafin na dawo gida ma yasan party naje har hotel da
muka kwana yasani, that morning da kayi dropping d’ina Baba slapped me about 4
times in the face” sekuma ta rushe da kuka.
“What?!” Yayi exclaiming “he slapped you? And you didn’t tell me?”
“I didn’t want you worried shiyasa am sorry please bayan nan ya faffasa min all
gadgets d’ina ya karya min sim tare d seizing min mota and he also threatened me
kan zeyi auren sadaqa dani to whomsoever, Neco exams d’ina ma wai bazan k’arisa ba.
Har rana kamar na yau ban rubuta Hausa exams d’ina ba da k’yar na samu ya hak’ura
ya janye maganan auren. Daga school se school ya yarda ina zuwa any place apart
from it yaja min Allah ya isa but yanzu ya janye Allah ya isan.”

“Omg! Sweetheart why didn’t you tell me all these? Why?”


“Because I love you.”
“I really can’t tell you how sorry I am Sweetest love accept my apologies kinji?”
“Stop apologising please, I didn’t tell you to tell me sorry I told you so we can
figure out ya zamuyi about your birthday.”
“Inhar hakane you musn’t go Sweetheart, banason na sake jin an mara min soft
cheeks naki my heart can’t take it. Ki zauna a gida kawai kinji? Its no big deal.”
“Very Own I really wanna be at your birthday, by your side I don’t care being
slapped again your happiness means the world to me. My gown, cake and everything is
ready I really wanna go.” Shikansa Adeel mamakin kalan son da Zeezee kemar yake.
“Babe I can’t take it you being slapped again kawai ki zauna kinji? Akwai next
time in shaa Allah nima da zan iya rescheduling time d’in danayi but na riga nayi
booking musicans d’in. I also want you to be there.”
“And I’ll be there, I want to sing happy brithday to you along with others, cut
your cake and feed you with it.”
“And how is that possible Babe?”
“Very Own nima bansani ba think of a way please I trust you whole heartedly.”
“Okay Babe I’ll come up with a way I love you so much.”
“I love you much more Adeel, morethan you can ever imagine I’ll be expecting
your call” nan tayi hanging. Ajiyar zuciya ta sauk’e sannan ta koma d’aki ta zauna
bakin gado tana tunani.

_15 more minutes..._


Wayarta dake k’ark’ashin pillow ne ya shiga vibrating kasancewar bata d’akin
takai plate na abincinta kitchen, seda ta dawo taga missed call nasa kafin tace
zata kira ya sake calling nata nan ta fad’a bayi sannan tayi picking “yes Very
Own.”
“Sweetest Love how much do you trust me?”
“10 on scale 10, 100% completely and morethan I do trust myself.”
“Zakiyi duk abinda nace kiyi?”
“I will do everything you ask me to do.”
“Great! I’ve made up my mind lets elude after the party” (mu gudu.) Dum! Zeezee
taji zuciyarta ta buga “lets go somehwere far, far away from here and start our own
new life, I promise to love you with each breath I take, care for you and protect
you till my last breath.” Har a yanzu Zeezee ta kasa cewa komi “hello Sweetheart?”
“Uhmm...”
“Kinji? Lets leave I have lots of money.”
“Adeel is this a good idea?”
“Do you have a better one?”
“No”
“Then I think its good enough, you said you trust me then why aren’t you willing
to elude with me?”
“Bawai banason tafiya dakai bane, Adeel my parents and siblings and even
friends.”
“Bawai ai bazamu sake dawowa bane ba, surely zamu dawo bayan mun samu kid namu
muma.”
“I don’t get you.”
“Am planning on marrying you Zainab.”
“Aure?!” tayi exclaiming.
“Yes aure I want to prove to you just how much I love you.”
“No, no please Adeel think of a better plan no matter what I can’t leave my
parents, I just can’t.”
“You can’t? What of me? Don’t I mean anything to you.”
“You do mean the world to me Adeel amman bazan iya binka mu gudu ba am sorry.”
“Good thank you for rubbing it to my face how much you don’t care about me.”
“Ad- hello? Hello?” Layinsa ta shiga kira sede sam bayi picking missed calls goma
tamar yak’i d’agawa.

Zama tayi kan toilet sit tana rusa kuka bayan komi ya daidaita tsakaninta da
Baba yanzu se kuma ta gudu? No there has to be a way, _I can’t live without Adeel
as well as I can’t live without my parents but which of them matters to me more?_
Ganin batada amsar wannan tambaya ta mik’e ta fice takoma d’aki ta kwanta. Yini
tayi ranan tana tunanin tabi Adeel ne kokuwa a’a. Tasan yanzu muddin bata je
birthday’n saba da k’yar al’amura su sake daidaita a tsakaninsu tunda da farko yace
mata ba setaje ba taje setaje, secondly idan har ta yarda taje birthday’n nasa sede
in zata nemi wani uban ne dan kuwa Baba bazeyi accepting nata ba amman kuma ai
tanada Mama tasan KOMIN RINTSI (Hama Gee) Mama will never turn her back against
her. Amman kuma what if Baba ya koma bakansa na da na yin auran sadaqa da ita? Dole
tabi Adeel su gudu suje chan su fara sabuwar rayuwarsu dan bazata iya rayuwa ba shi
ba.
~* ~* ~*
Seda ta bari da daddare yad’an huce ta kirasa nanma kaman baze d’aga ba sannan
yayi picking tare da yin shiru.
“Hello Very Own” shiru yayi.
“Very Own I know kana jina dan Allah kayi magana.” Again shiru, kuka ta shiga yi
“Very Own mesa kakeson bawa zuciyar da take sonka wahala? Do you want my heart to
explode one day? Please talk to me.”
“Nace miki meh?” Yayi maganan in an I don’t care manner.
“Thank you for speaking, I’m sorry for misbehaving earlier I wasn’t thinking
staright kayi hak’uri kaji?” Shiru ba amsa “please am sorry am on my knees begging,
barin sake crossing naka ba.”
“Naji so what now?”
“I’ve made up my mind zani birthday’n ka no matter the consequences inhar kuma
Baba yace ze aura min wani I’ll follow you muyi eluding, you have my solemn words.”
“I love you Babe I promise to make you the happiest woman on earth.”
“I trust you Very Own please ka rage yimin zuciya Allah my heart can’t take it
wataran, sau nawa nake kiranka kak’i picking. Wallahi baka san yadda nake sonka
bane Adeel da baza kana sani kuka haka ba.”
“Is okay I’m sory kinji? Its never my intention to make you cry just that kidena
crossing d’ina okay?”
“Okay My King, I love you.”
“I love you too Baby Boo so se goben?”
“Yes I’ll await you” daga nan sukayi sallama. Ita kanta Zeezee she is not sure of
what she is about doing all she is sure of is tanason Adeel and wants to be with
him.

12:00AM Zeezee was the first to wish Adeel a lasting happy birthday. Long essay
ta had’a ta mishi sending sannan kuma a instagram page nata tayi posting 25
pictures nasa tunda 25 years ya cika. Adeel couldn’t ask for more tunda yanada
perfect girlfriend. Ga kyau, swags and most of all the way she can die for him.
11am da su Mama suka fita Zeezee tama Lubiee waya ta taho mata da had’ad’d’en
picture cake da tasa akayi ma Adeel nata as a birthday gift saman an rubuta _HAPPY
BIRTHDAY MY VERY OWN._
“Yanzu kam zan iya shan iska ko? Tunda ga cake naku nan.”
“LOL Babe thanks for everything, I love you” tayi hugging nata “so wannan ne
kad’ai gift nasan.” Lubiee ta tambaya.
“Haba! Birthday’n Very Own d’ina gabad’aya kice cake kawai zan kai masa tsaya
kiga” wardrobe nata ta nufa ta fito da wani leather sannan ta zazzage kan gado
black Magnianni Lace Detail Loafers ne guda d’aya which is worth 40K da kuma Grant
London white leather wrist watch which is worth 30k.

“OMG!” Lubiee tayi exclaiming. “Babe you can’t be serious wannan takalmi befi 30k
ba last time dana gani a jumia?”
“Its actually 40k duk kayan nan 70K.”
“70K?! Zeezee sata kika soma?”
“Kika san for how long nayi saving kud’i for Adeel’s birthday ne?”
“Yakai shekara ne? Aina kika samu 70K? Don’t lie to me.”
“Yarinyan nan kinfi kowa sani nafa, actually kud’in agogon dana school fees d’ina
na 3rd term na cika na saya.”
“What! You mean baki biya ba?”
“Yup to meh zanyi da neco d’in? Am sure zanci waec d’ina in shaa Allah ba school
fees da zan biya.”
“Humm Allah shiryeki Zeezee wallahi baki tsoro ko kad’an.”
“Niba wannan ba ki tayani wrappiing gift d’in ban iya ba sauran ki nad’amin na
mugunta kuma.” Nan da nan ta ciro wrapping sheet Lubiee ta mata wrapping me kyau.
“Toh yanzu da yaushe ne party’n?”
“Nan bada jimawa ba” Zeezee tamata k’arya.
“Zeezee promise me bazaki fita da daddare ba.”
“I promise.”
“Yauwa.” Rakiya Zeezee tayi mata sannan ta dawo ciki.

6:30PM bayan Zeezee ta idar da Sallah tasa lock a d’akinta ta shiga tsara
makeup, seda tayi spending one and half an hour sannan tagama penta face nata, hair
rollers nata ta d’ibo tayi rolling gashinta ta barbaza akan shoulders nata sannan
ta ciro white english fish gown nata tasa by 8:00PM Zeezee was ready, d’akinta se
tashi yake da k’amshin turare. Not long enough Adeel ya kirata kan gashi a inda
tace ya jirata. Babban hijabi ta 6urma ta tattara gift da cake nasan sannan ta
bud’e k’ofan d’akin nata Baba taga ya shiga d’akin Mama ya rufe wani hamdala ta
saki sannan ta maida k’ofan nata ta shiga tip-toeing sid’ak-sid’ak tana tafiya har
ta samu ta fita, addu’a take tayi Allah sa Baba besa kwad’o ya rufe gate ba aikuwa
tana isa ta tarar da k’ofan a rufe. “Nashiga uku!” Ta furta kwata-kwata ta manta da
akwai k’ofa a garriage seda taji Mama na k’wala mata kira ta tuna. A guje amman
kuma a nitse ta wuce garriage, hamdala ta saki ganin sakata kawai a kasa a guje ta
fice dai-dai inda tace Adeel ya jirata taga motansa seda ta duba da kyau taga bame
ganinta sannan ta k’arisa dama already a bud’e yabar mata motan tana shiga ta rufe.
“Phew!” Ta saki numfashi.
“You made it Babe” ya mik’a yayi pecking nata.
“Anything for you” tayi maganan tana cire hijabinta tare da wullasa back seat.
“Wow! Am speechless you are looking extra ordinary beautiful Babe.”
“Thank you” wayansa ya cire ya musu selfie “are you ready?” Kai ta gyad’a “yes
lets go” hannunsa d’aya ya had’a da nata gagam sannan ya shiga driving.

_Back home..._
“Zeezee! Wai ina yarinyan nan ta shiga bade bacci tayi ba, Zeezee!” Gbam! Gbam!
Gbam! Jin ba amsa ta gwada waina handle d’in karap ya bud’u tasa kai ciki “Zeezee!
Ko kina toilet ne? Zeezee!” kiran sunanta Mama tayita yi amman shiru daga k’arshe
bud’e toilet d’in tayi taga wayam ba kowa ciki. Mumunar fad’i gabanta yayi “where
could Zeezee be?” Gidn ta zagaya bata ga Zeezee ba.
“Zainab me kikeson yi a rayuwarki? Ina kika shiga dan Allah?” D’akin Omar ta nufa
ta samesa yana d’an aiki akan laptop. “Omar! Omar!” Ta kirasa cike da tashin
hankali.
“Omar kaga Zeezee?”
“Rabuwa na da ita tun Sallan Maghrib bata d’akinta ne?”
“Omar Zeezee ta sake guduwa bata gida ba inda ban duba ba bata nan wayyo Allah na
shiga uku!”
“Ta gudu?!” Yayi exclaiming tare da mik’ewa hawaye Mama take “dan Allah kayi
shiru kar Babanku yajika, in yaji ta fita yankata zeyi idan tadawo.”
“Innalillahi! Ina Zeezee zata shiga Mama are you sure kin duba ko ina baki ganta
ba?”
“Na duba ko ina Omar bata nan wayyo Allah ni!”

_Zaranda Hotel_
“One, Two, Three...” Atare Zeezee da Adeel nata sukayi cutting 5 steps cake
d’insa wanda a sama akayi stalking _HAPPY BIRTHDAY ZEEDAL_ akai. Piece kad’an tayi
cutting tayi feeding nasa dashi sannan ta basa wine akai. Anan ta miqa mai present
nasa, sosai yaji dad’i daya bud’e yaga ni kasancewar he is used to wearing
expensive stuffs, yana ganin shoe and watch d’in yagane masu tsada ne hugging nata
yayi in the presence of everyone tare da pecking nata. Daga nan sukaci abinci bayan
cin abinci DJ ya hau aiki, dance floor aka bawa Zeezee da Adeel nata, rawa sukayi
as if dan shi aka turosu duniya ba inda Adeel bai shafa ba jikin Zeezee seda
nishinsu ya kusa d’aukewa suka koma gefe suka zauna suna masu feeling love na juna
a zuqatansu. Daga nan birthday programmes suka cigaba, 3 musicians Adeel yayi
booking aciki harda favorite artist na Zeezee, Tiwa Savage ita tayi singing lastly
wanda a k’arshen song d’in tayi mentioning Zeedal ciki, sosai birthday nashi ya
had’e yakuma sa Zeezee sake feeling as his only Queen!

_10:30PM_
Mama ce zaune bakin gado abin duniya sun mata yawa har Baba da besan Zeezee bata
gida ba yazo ya zauna a gefen ta batayi noticing ba. “Hafsah!” Firgit ta mik’e
“na’am Alhj yauhse kashigo?”
“Tun d’azu, tunanin me kike haka?”
“Uhm Babu mu kwanta koh?” Addu’arta tun d’azu befi Allah yasa kar Baba ya nemi
Zeezee ba yau.
“Ina Zeezee? Kiyi mata magana inason mata magana.”
“Alhj da daren nan? Kabari mana se gobe.”
“Kamar ya se gobe Hafsah? Magana nakeson mata batun studies nata fa jeki kiramin
ita please.”
“Alhj please kabari gobe tayi bacci halan.”
“Toh naji” to her suprise kawai taga Baba ya mik’e yana barin d’akin gabansa
tasha da wuri “Alhj please kazo mu kwanta Zeezee tayi bacci.”
“Tayi bacci ko ta tafi party’n da zasuyi a Zarandan?”
“Party kuma?”
“Hafsah ni zaki raina ma hankali wai? Ko kin manta inada aboki police ne? Sun je
sun karb’i police excuse yadda bazama a tak’ura suba da kyau, Zeezee sede ta nemi
wani gida da uban ko itace kad’ai ‘yata a duniya na yafe ta.” Yana kaiwa nan ya
juya ya haye gado tare da kwanciya. Silent kuka Mama ta hau yi haka ta kasa bacci
ranan.

01:45AM akayi closing party’n. “Babe in kaiki gida ko se gobe?” Adeel yayi
maganan hannunsa zagaye a k’wank’wason Zeezee gabad’aya ta manne jikinta a nasa.
“No I’ll sleep here with you se gobe naje gida kawai kamin booking room.”
“Are you sure Babe?”
“I am saboda ko naje yau Baba baze barni na kwana a gidansa ba.”
“Is okay I’ve got you okay? You really made my day today.”
“I’m glad I did, muje kamin booking room am sleepy.”
“Right away Babe” pecking nata yayi sannan suka k’arisa reception ya mata booking
room. Har d’aki ya kaita sukayi Sallah seda ta kwanta sannan ya mata goodnight ya
fice. Peacefully Zeezee ta samu bacci not like the other time.

Washegari by 9:07AM su Zeezee suka gama karyawa, suna tsaye gun reception yana
k’ok’arin biya musu bill yace, “uhm Babe na bud’e miki mota go and wait inside
kinji banason kitsaya anan kowa yazo wucewa yana kallonki, am jealous.”
“Okay Very Own I love you” tayi pecking nasa a cheeks, “in baki key ki kunna AC?”
“No need ana sanyi already.”
“Okay heater fah?”
“Don’t worry Very Own am good”
“Tam jeki jirani ina zuwa yanzu.”
“Okay” tana kaiwa nan ta fice bata kaiga shiga motan Adeel ba taga wasu police
men guda biyu tsaye wajen, bata kawo tunanin komi a ranta ba ta k’arisa gun motan
kawai ji tayi hannu kan kafad’arta. A razane ta juya “ya haka Mr. Police man? Let
me go.”
“I’m sorry Miss, Babanki ne yabamu order mu kaiki gida.”
“No, no please dan Allah ku rufa min asiri and let me go” hannunta yakama yahau
janta. Ihu tashiga rusawa tana kiran sunan Adeel.
“Adeel! Adeel! Please help me zasu tafi dani, where are you?! Adeel!” basuyi
minding nata ba suka sata cikin motan da suka taho dashi, kuka take tayi cikin
motan tana had’asu da Allah amman ko a jikinsu saboda aikinsu sukeyi.

_Back in Zaranda Hotel..._


Adeel na gama settling bills nasu yafito ya k’arisa gun motansa ya bud’e tare da
shiga “Swe-” be k’arisa maganan ba yaga gefensa wayam ba Zeezee ba alamarta. Be
kawo wani tunani aransa ba yayi zaman jiranta ko maybe ta shiga bathroom, 2-3
minutes later jin shiru har yanzu bata dawo ba, ya fita ya shiga neman ta sede
she’s nowhere to be found. Tambayan mutanen gun ya shigayi duk sukace basu ganta ba
atlast gateman ya tambaya ya shaida masa eh wasu police men biyu sun zo sun tafi da
ita. Dum! Zuciyarsa ya buga oh no! Zeezeen sa!!!
*TEAM #YGC*
*MIEMIEBEE*
www.beeenovels.blogspot.com

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
2⃣8⃣

_I dedicate this page in honour to each and every *special member of my group,
MIEMIEBEE NOVELS GROUP.* Sorry for enticing you guys yestarday😅😝 I just couldn’t
help it, how you guys are so eager to see Baba cutting off Zeezee’s head. Mugaye
kawai!😂 That aside I love you guys so much, thanks for your maximum supports
#OneLove💞_

“Dan Allah bayin Allah ku rufa min asiri karku kaini gida wallahi kasheni zeyi,
kuji k’aina dan Allah” kuka tayita musu a motan tana had’asu da Allah amman kota
kanta basuyi ba suna isa bakin gate driver yayi parking suka fito da Zeezee neman
kwanciya tayi a k’asa amman haka d’ayan ya d’agata chak se cikin gida inda Baba,
Mama, Mariam da Omar suke tsaye. Wani sabon kukan ta rushe dashi ganinsu, “aikinku
yayi kyau nagode, you may leave” cewar Baba.
“Godiya muke” suka amsa almost a tare sannan suka fice. Taku d’ai Baba yayi ta
direction na Zeezee dake zube a k’asa tana kuka Mama tasha gabansa, “Alhj dan Allah
karka tab’ata” tunkud’eta yayi a zuciye sekace ba Hasfsar saba da wuri Mariam taje
ta tari Mama kafin ta gama fad’i. Hannun Zeezee yaja seda ta mik’e tsaye ko kallon
cikin idanunsa ta kasa. Mari lafiyayye ya sakar mata tas! Wani irin rikicaccen ihu
ta saki a yayinda take hango stars, kafin ta farfad’o daga marin ya k’ara mata
wata, Mama dake zaune a k’asa Mariam na tsaye a kanta tace, “Omar kaje ka karb’i
Zeezee dan Allah karya kasheta.” Omar na nufan wajen Baba ya bud’e masa ido
“wallahi Omar ka matso nan kaji na rantse maka zan tsine maka.”

Jin haka Omar yaja baya, hannun crying Zeezee Baba yaja zuwa d’akinsa yasa lock
“Baba dan girman Allah kayi hak’uri na tuba” dorina me baki biyu taga ya ciro daga
wardrobe nasa nan tasa ihu tana had’asa da Allah. Kir6ata ya shigayi, mutum na iya
rantsewa ba mutum Baba yake daka ba. Ya gwara ta da bango, yayi ball da ita ya
nausheta ba abinda beyi da ita ba, “Mama dan Allah kizo ki taimakeni Baba ze
kasheni!” Su Mama dake tsaye bakin k’ofar se bubbugawa suke suna bawa Baba hak’uri
amman se kaman sake tunzira sa suke, ya zabga mata bulalan yayi ball da ita sekace
ba Zeezeen’sa ba. Amai Zeezee ta shigayi amman hakan besa Baba ya barta ba, tun
tana ihu har yazamo hawaye kawai take.
“Alhj! Alhj! Dan Allah ka rufa mana asiri karka kashe yarinyan nan, Omar me kake
jira ka b’alla k’ofan mana!” Mama tayi maganan tana jijjiga k’ofan.
“Ba gomma na kasheta na huta ba, ni zatayi wa abin kunya? Kasheki zanyi na huta
ina adda na?”
“Adda?! Alhj kayi me dashi, dan Allah ka rufa mana asiri, Omar me kake jira ka
b’alla k’ofar mana.” wardrobe nasa ya nufa ya shiga neman addansa shi a dole se ya
yanka ta ya huta. Da k’yar Omar ya samu ya b’alla handle na k’ofan sukayi ciki da
gudu Mama tayi kan Zeezee dake ta kwararo amai dai-dai nan Baba ya sami addan nasa,
gaban Mama data tare Zeezee yasha “ki matsa Hafsah kona yanka ku tare.”
“Sede ka yanka mu taren kashemin ‘ya kakeson kayi? Meye amfanin haka?”
“Ki matsa nace!”
“Wallahi ba inda zanje.”
“Baba dan Allah kayi hak’uri she’ve had enough” cewar Mariam calmly.
“Kufita nace! Kubari na gama da ita kowa ya huta tunda ita iskanci ta d’au wa
kanta” hannu yasa ze finciko Zeezee daga hannun Mama amman dan yadda Mama ta
damk’eta ajikinta ya kasa. “Ko ke kad’ai ce ‘ya a gareni na yafe ki Zeezee-”
“Subhanallahi! Alhj karka zo kayi abinda zakayi nadama dan Allah kayi shiru haka
ya isa kayi hak’uri.”
“Na fad’a na yafeta taje ta nemi wani uban, shi saurayinki da kika fi jin
maganarsa akan nawa sekije ki samesa na baki nan da minti biyu ki tattara ina-ina
ki kibar min gida konasa ‘yan sanda su baki d’ankaren duka.” Ganin har yanzu crying
Zeezee bata motsa ba ya sake daka mata tsawa “bada ke bane?!” har a yanzu dan yadda
ta daku lik’is takasa motsawa “wallahi ba inda Zeezee zata je, kai bakasan yin
hakan sake ta6ar6arar da al’amarin bane? Wallahi k’afarta k’afata, muddin ka kori
Zeezee nima sede ka nemen a gidan nan, Zeezee nada laifi amman kaine sanadin komi.”
“Hafsah stay out of this kina jina koh? Ke bazaki tashi bane sena kira ‘yar
sandan ko ya? ‘yar iska karuwa kawai.”
“Baba dan Allah kayi hak’uri haka, Omar kabashi hak’uri” cewar Mariam.

“Ku fita daga d’akin nan ko dukanku na tsine muku albarka, ku fita nace!” A
sanyaye suka bar d’akin.
“Tashi kibarmin gida ‘yar iska kawai, saurayi zaki fifita akaina ni ubanki?
Yasmeen da Mariam ba yara bane? Ki tashi nace!”
“Alhj dan Allah kayi hak’uri” ganin har yanzu Zeezee bata motsa ba yasa hannu da
force ya fincikota daga jikin Mama yahau janta Mama na binsu a baya tana had’a sa
da Allah, dasu Mariam sunce zasu motsa Baba yace ze tsine musu har bakin gate suka
kai yakaiga bud’ewa Mama ta sha gabansa da k’yar “Alhj don Allah nace, dan
darajansa kayi hak’uri wallahi yanzu ka kori yarinyan nan sake lalacewa zatayi,
think mana! Yanzu da muke kanta ma ya ta k’are bale ace ta wayi gari bame hore mata
kayi tunani please.”
“Ina k’arshen iskanci shine karuwanci? Tou ta zama fiye da karuwa bare damen ba
tunda na yafeta ban san da zamanta ba again, barin zauna a gari k’aramar k’waro
kaman Zeezee ta b’ata min suna ba.”
“Alhj listen to yourself, koran yarinyan nan baida fa’ida wallahi sake lalata
wannan al’amari zamuyi kamata yayi yanzu kasa mata ido.”
“Ki matsa Hafsah kokuwa a bakin auren ki.”
“Shikenan zan matsa amman wallahi kasani Zeezee na barin gidan nan nima zan bari
kaji na rantse” Mama tayi stating in a serious tone.

“Haka kikace?”
“Eh wallahi haka nace ai kaji na rantse.” Kallo ya galla wa Zeezee dake neman
sulalewa k’asa a hannunsa sannan yayi wurgi da ita tamkar kashi a gun seda ta buga
kanta jikin gate, d’akinsa ya nufa a fusace. Nan su Mariam sukayi kan Zeezee, Omar
ya cinci6eta se asibiti sukayi inda aka duba Zeezee aka kuma yi mata treating minor
injuries. Se da Azahar suka dawo gida har alokacin Adeel bebar trying number’n
Zeezee ba amman ba response, tsoronsa kuma kar yaje gidansu Zeezee ya sake making
things worse than they already are.

Gabad’aya Mama haushi da tausayin Zeezee take a d’akinta ta kwantar da ita har a
lokacin bata bar kukan ba kanta gabad’aya an zagaye da bandage dan yadda Baba ya
faffasa mata shi. One last kallo Mama ta k’are mata cike da takaici sannan ta fice
izuwa d’akin Baba. Mariam ce ta matso kusa da Zeezee tana kallonta pathetically
“yanzu kin kyauta wa kanki kenan? Me amfanin hakan Zeezee? Look at the state of
yourself kin kyauta wa kanki kenan?” Da k’yar Zeezee ta iya ta kad’a kanta.
“Toh kukan ya isa mana da uban wa yace kifita kik’i kwana a gida? Ashe ma this
is not your first time me kike nema a duniya Zeezee? Kyau ne Allah ya baki, kinada
iliminki daidan gwargwado mesa bazaki kare mutuncin ki kiyi aure a mutunci ba?
Ajinki yanzu shi saurayin da kike bin ze yarda ya aure kine bayan ya riga ya sanki
a waje?”
“Adda Mariam wallahi ni ban tab’a sanin wani d’a na miji ba.”
“Then mesa kike kwana a waje?”
“Sabida koda alokacin da aka gama party’n nace zan dawo gida k’ofa a rufe ne.”
“Hmm amman ‘ya musulma dake me zai kaiki attending midnight party? Bakida hankali
ne?” Nasiha da fad’a sosai Mariam tayita wa Zeezee a yayinda Mama kecan d’aki tana
yi wa Baba nasiha shima dan sam yace Zeezee bazata kwana gidansa ba yau ya yarda
Maman ta bita su tafin. Ganin haka Mama tayita basa hak’uri da k’yar d’in k’yar ta
samu ta shawo kansa ya hak’ura da Zeezee ta cigaba da zama a gidan amman she is not
his responsibility.
“Kije kice mata ta kawo min wayan da suke communicating ita da d’an iskan
saurayin nata.”
“Wani erin waya kuma Alhj? Tanada wani wayan ne bayan wanda ka fasa mata?”
“Da dame kika d’au take communicating dashi? Kije kice tabani dan wallahi inhar
bata kawo ba zata bar gidan nan this very instant.”
“Naji zan mata magana” da wuri tayi d’akin Zeezee ta sameta zaune bakin gado se
rusa kuka take, harara Mama ta watsa mata sannan tace, “bani wayan, kika min k’arya
kuma wallahi zakisha mamaki.”
“Mama wani waya?” Tayi speking up finally.
“Aww k’arya zakimin? Inbar Baban naku ya sake miki dukan da yafi na d’azu ya
koraki ko?”
“A’a dan Allah kiyu hak’uri.”
“Then kawo.”
“Zeezee bada inhar akwai” wayar cewar Mariam. Hannu tasa a bra nata ta ciro
samsung d’in cike da mamaki Mariam ta tsaya tana kallonta amsar wayar Mama tayi
tana k’are mai kallo sannan back to Zeezee.

“Zainab me yaron nan ya miki? Mesa zaki fifitasa kan iyayenki? Shin wai damu
dashi suwa sukafi daraja a idon ki?”
“Mama wallahi na tuba dan Allah kuyi hak’uri.”
“A’a ki amsani damu dashi suwa sukafi daraja?”
“Ku Mama dan Allah kuyi hak’uri.”
“Kin kyauta” tana kaiwa nan tafice takaiwa Baba wayar rugu-rugu yayi da wayan
sannan ya karya sim d’in. Bayan da Baba ya tabbata duk sun fita sunbar d’akin
Zeezee itace kad’ai ragowa yajesa. Tana ganinsa ta hau 6ari “Baba dan darajan Allah
kayi hak’uri karka sake ta6ani, wallahi bazan sake ba” hannunta yaja a fusace se
ihu take tana kiran Mama da Adda Mariam. Yana kaiwa store room yayi wurgi da ita
ciki tare jan k’ofan ya datse kwad’o ta waje sannan yasa makullin a aljihunsa. Buga
k’ofan tashiga yi seda su Mama suka fito “ya haka Alhj? Bade rufeta kayi cikin
d’akin nan me window d’aya ba? Dan Allah kayi hak’uri ka bud’e kasheta kakeson yi?”
“Mama! Mama dan Allah ki taimakeni kice ya bud’emin k’ofan.”
“Alhj dan Allah kayi hak’uri ka bud’e mata.”
“In kinga na bud’e k’ofan nan toh gawanta za’a cire kuma duk wanda ya bud’e Allah
ya isa ban yafe ba.” Yana kaiwa nan ya fice yabar gidan. Kuka Zeezee tayita rusawa
tana bubbuga k’ofan, wani erin bak’in duhu ne da d’akin saboda d’an window d’ayan
ma ba haske yake kawowa ba. Ita kanta Mama batasan a lokacinda ta fara kuka ba da
k’yar Mariam ta samu tayi shiru.

*~ *~ *~
Bayan Sallan La’asr Baba yadawo cikin kuka Mama ta samesa tana had’asa da Allah
da ya bud’ewa Zeezee k’ofar ko Sallah ne tayi taci abinci amman haka Baba yak’i.
Rok’onsa tayita yi har Sallan Maghrib yak’i bud’ewa, haka Zeezee tayini cikin
d’akin takuma kwana ciki tun tana hawaye har hayayen nata suka k’are ya zammana ta
nemi waje kawai ta zauna tana jan numfashi.
***
Ta fannin Adeel ma hankalinsa ya matuk’ar tashi jin line na Zeezee bayi shiga har
yanzu, Lubiee ya kira ya buk’aceta da ta kira Mama taji daga gareta bayan Mama ta
mata bayanin komi Lubiee tayita kuka itama sannan ta kira Adeel ta irga masa komi
tana me blaming komi akansa. Sosai shima ya tausayawa Zeezeen’sa, ji yake inama ace
ze iya ceto ta right now su gudu suje somehwere far away and start a new life, a
daren ranan beyi bacci ba shima tunanin Zeezee ya hanasa.

Washegari ma da rok’an Baba Mama ta tashi amman sam yak’i jinta daga k’arshe
Kaka ta kira tata mata kuka, koda Kaka tasa baki k’in bud’e k’ofan Baba yayi.
Around 10am Lubiee da Ummi sukazo abin tausayi sede a leqa Zeezee ta window, take
away da Mama tabata ma na can a gefe bata ta6a ba, rabuwanta da abinci tun
breakfast na jiya. Ba yadda Lubiee batai da Zeezee ba ta taso ta ganta amman Zeezee
tak’i haka har su Lubiee suka tafi bataga idon Zeezee ba. Se bayan La’asr da Kaka
tata had’a Baba da Allah ya amince ya bawa Mama key taje ta bud’o Zeezee.
Kuka tasa tare da rungumota, tanayi Zeezee nayi. A hankali ta d’agata ta kaita
d’akinta tasata yin wanka da biyan sallolin ta sannan taci abinci.

★*★*★*★
Tun rana me kamar na ranan rayuwan Zeezee ya soya, gabad’aya Baba ya hana duka
friends nata visiting nata harta Lubiee. Ba inda take takawa daga toilet se
d’akinta, kullum cikin kuka take ba safe ba dare, uwa uba kuma ga rashin jin murya
ko motsin Adeel nata a kusa da ita, hakan ba k’aramin rama yasa tayi ba a sanadin
haka Baba yace sam se anje anyi mata pregnancy test waya sani ko ciki take dashi,
duk yadda ta rantse musu kan ita bata tab’a sanin wani na miji ba Baba yak’i yarda
hasali shi yanzu ko muryan Zeezee ma bayason ji. Sunje sunyi test result ya nuna ba
ciki, ita kanta Mama se anan hankalinta ya kwanta sabida rama erin wanda Zeezee
tayi itama ya tsorata ta.
Ta fannin Adeel shima hauka ne kawai beyi ba kullum yana gidan su Lubiee yana
roqarta tasan ya zatayi ta had’asa da Zeezee. Rana d’aya Lubiee ta kira Mama bayan
sun gaisa ta buk’aceta da ta had’ata da Zeezee. Kasancewar Baba ya hana yin hakan
da k’yar ta samu Mama ta bawa Zeezee wayar ta fice.
“Hello Zeezee.”
“Na’am Lubiee” tayi maganan wane maras lafiya.
“Ya kike? I missed you.”
“I missed you, ya gida da kowa sa kowa?”
“Lafiya qalau Zeezee Adeel ne ya dameni wai yanason ku gaisa.” Kuka kawai Zeezee
tasa, jin haka Adeel ya wabje wayan “hello Sweetest Love.” Da k’yar ta iya ta amsa
sa “na’am Very Own.”
“Sweetest Love I can’t tell you how sorry I am, only if I knew all this would
happen da bakije party’n ba, da banyi bama gabad’aya.”
“Its not your fault I was the one who insisted on going so stop blaming yourslf
please.”
“what now yanzu? Baba ya hak’ura?”
“Ko murya na baya sonji bale yaso ganin fuska na, Very Own am afraid I might lose
you sabida Baba yace aure zemin with whomsoever.” Kai ya shiga kad’awa “no... No it
can’t be possible Babe, you belong to only me please don’t accept the marriage.”
“Very Own danasan anyway possible dana bi dan kub’ucewa aukuwan wannan aure but I
can’t.”
“There has to be away, bazaki iya escaping ba?”
“Bazan iya ba 5pm ake rufe min d’aki gakuma masu gadi har biyu da suke gadi
kullum a waje theres no way out.”
“Damn it!” ya buga hannunsa jikin bango “I can’t lose you, I can’t” jin an murd’a
handle na d’akintan tayi saurin cewa, “Mama is here” tare da katse wayar. “Har kun
gama wayan ne?” Mama ta tambayeta
“Eh” ta amsa tana share hawayenta.
“Dama nazo fad’a miki Babanku ya dawo ne.”
“Nagode Mama.”
“Toh ni zan wuce d’akina” tayi maganan tana kar6e wayanta “seda safe.”
“Allah tashemu” Mama na ficewa Zeezee ta bud’e sabon chapter’n kuka 5pm on the
dot Baba yazo yasa kwad’o a d’akin nata as always. The next day Baba A’ee tazo
gidansu Zeezee ba shiri bayan jin labari da tayi a gari kan ga abinda ke faruwa a
gidan Alhj Isma’il. Mama na a kitchen ta fito tayi mata sannu da zuwa.
“Yauwa Hafsah, karki gayamin abinda naji a gar-” bata k’are maganan ba Mama tace,
“gaskiya ne ba k’arya ko d’aya aciki.”
“Zeezeen!” Ta dafe k’irji.
“Ita de Baaba amman dekam bawai taje ta kwana da na miji bane kamar yadda mutane
ke fad’i party ta fita har sau biyu bata kwana gida ba.”
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Duniya ina zaki kaimu? ‘Yar Zeezee? Kinga
irin abinda nake gaya mikin tun a da ko? Kingani ko?”
“Toh Baaba ya kikeson inyi?”
“Keko kike da yadda zakiyi, alokacinda abu basu 6aci haka ba na miki magana kan
kidena cewa ke ba ruwanki da tarbiyyan Zeezee, ke ce uwarta tarbiyyan ta a hannunki
yake ba ana Alhj ba, komin ya Alhj yake da Zeezee da kin tashi dagaske kika nuna
masa kefa wannan tarbiyyan daya d’aura ‘yarki akai gur6arcacciya ce bakiso wallahi
daya tsorata shikansa ya dena. Amman haka kika zauna kina zuba mai ido ga irinta ai
yanzu, ‘yan unguwa ba Alhj kad’ai suke zaga ba har dake tunda kece mahaifiyarta.”

Shiru Mama tayi saboda ba shakka dukkankin abinda Baaba ta fad’a gaskiya ne
shiyasa take kira ga iyaye mata masu zubawa mazajensu ido suna lalata musu
tarbiyyan ‘ya’yansu suce su ba ruwansu ciki da tun wuri suyi hattara su dena sabida
abubuwa suna ta6ar6arewa ba uban kad’ai za’a zaga ba, harda su matan tunda iyaye
mata dama aka sani da aikin bada tarbiyya.
“Gaskiya ne Baaba kinyi gaskia nima da hannuna acikin lalacewar tarbiyyan Zeezee,
da a lokacin nama Alhj wuta sosai na nuna masa ba’a gidana za’ayi haka ba da
tarbiyyan Zeezee be lalace haka ba.”
“Aikinga irinta yanzu, abinda nake gudu muku kenan ranar dana sani.”
“Tabbas Baaba nayi kuskure nima amman haka mu ‘yan Adam muke ajizai ne mu, nayi
alqawari daga yau koda akan titi na tarar da yara masu kalan halin Zeezee zan tsaya
na musu gyara se a inda k’arfi na ya k’are itama Zeezee yanzu zan sa mata ido sosai
fata na Allah ya shiryar min da ita.”
“Ameen da hakan kikayi ada da duk haka be faru ba, Allah shirya mana Zeezee toh.”
“Ameen Baaba nagode sosai”
“Ba komai ai D’A NA KOWA NE (Bebeelo) ina Zeezeen take itama?”
“Tana d’akinta Baban ya rufeta.”
“Kamar ya?”
“A kullum k’arfe biyar na yamma nayi yake sa kwad’o k’ofar d’akinta ko abincin
dare ta window nake mik’a mata.”
“Toh Allah ya kyauta in Alhj yazo ki gaishesa ni na tafi.”
“Bazaki jira dinner ba?”
“A’a nagode”***

★*★*★*★
Several weeks and months passed by. Matar Ibraheem Fateemah harta haihu ta samu
‘yarta Hafsah itama takwaran Mama. Koda Mama ke shirin tafiya ta rok’i Baba daya
bari Zeezee taje itama amman sam yak’i, haka Mama ita kad’ai ta tafi ta dawo. A
rashinta na sati Zeezee ji take kamar an cire wani gab’a ne daga jikinta, d’an waya
da suke da Adeel jifa jifan ma babu shi yanzu. Bada jimawa ba admission nasu Zeezee
ya fito duk friends nata sun soma registration amman banda ita, tayi kuka har seda
ta godewa Allah Baba ya hak’ura ya barta ta cigaba da karatu yak’i, Mama tasa baki
ta rok’esa amman yak’i ji ya riga ya yanke hukunci Zeezee bazata koma school ba se
inde a gidan mijinta. Gashi har yanzu al’amura basu daidaita tsakaninta dashi ba
dan ko zata mutu tana mai magana ba amsata ze ba, muryanta ma ba son ji yake ba.

Shikansa Baba abin ba k’aramin damunsa yake ba acewai ga abinda Zeezeensa ta


koma, shi kansa ya d’an rame dan yadda yake bin abin a zuciya. Ana cikin haka wata
rana wani friend na Baba yazosa gidansu Zeezee.
*© MIEMIEBEE TEAM #YGC!*
👄👄👄👄
wwww.beeenovels.blogspot.com

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2016*
2⃣9⃣

Abokin Baba ne amman ba agemates neba su, sabida Baba na fifty-five (55)
years old whereas abokin nasa MUHAMMAD AL’AMEEN SHETTIMA yana da forty-two (42)
years old. Soldier (soja) ne babba yana matakin MAJOR GENERAL third to the last
rank on list. Fari ne sol dukda kalan wahalan da soldiers ke sha a training besa
haskensa ya dishe ba, gashi tsayayyen na miji me jini a jik’a. Yanada tsawo
averagely da d’an kauri kad’an. Fuskansa bame fad’i bane yana nan siriri dai-dai,
idanunsa suna nan ba manya ba bakuma k’ananu ba da long eyelashes, yanada slim but
silky eyebrows wanda suke na wane anyi carving nasu. Yanada dogon hanci ba laifi
amman ba irin har bakan nan ba. Koban fad’a ba za’a san yanada pink lips saboda
farin fatarsa. A takaice de kallo d’aya za’a mai asan da akwai dangin Shuwa Arab
tattare dashi saboda yanayin gashin kansa, saje da kuma na jiki.
Sanye yake da uniform nasa na soldier dake mugun amsar sa har na k’in k’ari.
Tunda Major General Muhammad Al’ameen (Maj-Gen Al’ameen) yake be ta6a yin aure ba,
bakuma wai bayida ra’ayin yin bane lokaci ne beyi ba. Kasancewar girman rank nasa
yasa duk inda zasa da sojoji suna gadinsa yake zuwa. Da manya-manyan Prado (land
cruisers) guda biyu yazo gidansu Zeezee. Driver na parking d’aya daga cikin
k’ananun sojojin rik’e da bindiga ya fito daga d’ayan motan tare da bud’e mai motar
da yake cikin yana me saluting (sara) masa.

Cike da k’asaita kamar yadda ya saba gudanar da al’amuransa gentlemanly ya fito,


nan soldier’n ya rufe k’ofan sannan about four of them rik’e da bindigoginsu sukayi
walking nasa izuwa gidansu Zeezee. Baba na zaune a parlourn sa yana karanta
newspaper ya mik’e yayi welcoming aboki kuma k’anin nasa. Wato tun a Saudiya da
suka had’u suka k’ulla zumunta bayan gano juna da sukayi kan attending secondary
school thesame da suka ta6ayi sede tun kafin Maj- Gen Al’ameen ya iso secondary
level Baba har ya gama dan ratan dake tsakaninsu.
“Soldier ne gabad’aya yau a gidan nawa?” Baba yayi maganan fuskarsa d’auke da
murmushi yana me mik’a mai hannu suka gaisa. Dariya kalan ta manya cikin
sark’ak’k’iyar sweet manly not too husky voice nasa me sanya sanyi a zuciyar me
sauraro ya sakar tare da fad’in “gani nan de, I thought I might suprise my
Brother.”
“You’re welcome, please come in.”
“Wait for me here” yace da guards nasan nodding kai sukayi tare da saluting nasa
sannan yabi Baba suka koma parlour. Nan sukayi former greetings “ban zata ai zaka
iya gane kwatancen gidan nawa ba, yau shekara nawa?”
“Gashi de nagane, you have a very nice house.”
“Thank you Maj- Gen so ya aiki? Kullum baku zama gu d’aya.”
“Alhamdulillah da godiya, dawowa na daga Abuja kenan nace barin k’ok’arta naga
gidan Brother’n nawa yau.”
“Aiko ka kyauta wallahi, am very grateful.”
“Ya Madam da kids?”
“Alhamdulillah duk k’alau. Yara duk sunyi aure d’aya ce a gabana, Madam ta fita
ma bari ko ruwa ne a kawo maka. Zeezee! Zeezee!”
“Wow, toh masha Allah.”
***
Zumbur Zeezeen da ta manta when last Baba ya kirata ta miqe zaune kan gado tana
raba ido, me kuma tayi yanzu da wannan kira? Bade ya gane tana communicating da
Adeel ta wayan Mama ba. “Wayyo Allah na mutu gashi Mama bata gida.” faracunta ta
shiga ci unknowingly.
“Zeezee!” Baba ya sake kiranta. “Na’am” ta amsa tare da janyo bak’in gyale ta
yafa akanta daman wata bak’ar doguwar riga ne a jikinta. Har 6ari take ta fito daga
d’akin nata “na’am Baba gani” tayi maganan in a cracky voice zaue a k’asa. Tana
noticing bak’on Baba tayi saurin gaishesa “ina wuni?” A nitse ya juyo da kyakkywar
fuska yana kallonta sannan ya amsa “lafiya ‘yan mata ya karatu?” kai ta d’ago dan
kallonsa sabida yadda muryansa ya mugun mata dad’i, fiye dana Adeel nata.
“Lafiya alhamdulillah.”
“Masha Allah.”
“Jeki d’auko wa abokin nawa drink ko ta kawo ma abinci ne tunda daga tafiya
kake?”
“No not at all, don’t bother ruwan is okay.”
“Toh ki d’auko mai drink d’in.”
“Toh Baba” a nitse ta mik’e tare da ficewa, kawai ganin sojoji har hud’u rik’e da
bindigoginsu tayi tsaye bakin k’ofan. Wannan kuma gunwa sukazo? Bade d’aukana
zasuyi su tafi dani bako? Tayi tunanin haka a ranta. Sekuma datayi tunani kode
gadin abokin Baban suke? Wow he must be a big soldier ba tare da b’ata lokaci ba ta
had’a mai cup, ruwa, da frutta juice akan tray ta kai har gabansa ta ajiye tare da
zuba mai kad’an daga cikin juice d’in a cup, “thank you koh?” Kai kawai ta gyad’a
sannan kanta ak’asa ta juya ta koma d’aki.

Duk wannan abu da take idon Maj-Gen Al’ameen bebar kanta ba, tun dayake, tunda
ya san kansa be ta6a feeling like this with any other girl ba. Duk matan da Mamansa
ke had’ashi dasu duk basu tab’a mai kamar ‘yar Zeezee daya gani ba yanzu. Ga kyau,
ga fasali and above all ga tarbiyya (bari de abar kaza a gashinta!)
“Masha Allah wannan ‘yarka ce Brother?”
“Sosai itace last born d’inda nake fad’a maka ai.” Baba yayi maganan yana jin
dad’i.
“Wow! Seriously? Ashe kanada manyan yara haka.”
“Amfanin aure da wuri kenan.”
“Gaskiya in kace kai ka haifesu ma baza’a yarda ba.”
“Haha koh?”
“Sosai, toh Allah ya raya mana su” yayi maganan tare da sipping juice d’in. “So
wannan tana nan ATBU ne?”
“Eh tohh...” Baba ya shiga neman excuse, “sude suka gama makarantar this year
amman bata samu admission ba ita.”
“Ohh ayyah, maybe next time.”
“In shaa Allah, so Brother do you plan on marrying her to anyone now or karatu
zatayi?”
“Yyess, aure zan yi mata soon in shaa Allah jiran miji kawai nake.”
“Oh wow! Jifa yazo dai-dai da zama kenan.”
“Haha, ko kanada wanda zaka had’asu ne?”
“Will I make a good match?” Ya tambaya tare da d’age gira d’aya. Gyara zama Baba
yayi “Maj-Gen kai da kanka?! Kode wasa kake.”
“No seriously jokes apart yarinyar ka tamin sosai, like ban ta6a feeling this
love at first sight da kowa ba seda ‘yarka, tarbiyya da ladabinta ya gama min
komi.” Alhamdulillah kawai Baba keta nanatawa a ransa.
“Toh ai wannan ba wani abu bane Maj-Gen. Zainab taka ce duka.”

Zainab ya nanata sunan Zeezee a ransa. “Amma dagaske kake Brother?” Yayi maganan
a bit suprised.
“Sosai ma, daman neman meh amanan da ze rik’e min ita nake sekuma Allah ya kawo
ka gaka kuma na gida ba abinda zance ai sede Alhamdulillah.”
“Gaskiya yau da sa’a nake, mata a sama toh nagode Brother, so se muji daga bakin
ta in nayi mata toh inko a’a we can’t force her koya kace?” Ya sake sipping juice
nasa.
“Wannan ba wani abu bane ai Maj-Gen kasa aranka ma ta riga ta amince.”
“Toh hakane?” sanadiyar murmushin da yayi dimples nasa suka lotsa making him
worth more looking.
“Sosai mah kuwa.”
“Toh godiya nake Brother in shaa Allah zaka sameni me rik’e amana.”
“Nine da godiya nan da gobe zan sanar dakai duk abinda akwai in shaa Allah.”
“Toh am grateful, thank you.” Be jima ba yace ze tafi, fifty thousand (N50,000)
ya bawa Baba kan a baiwa Zeezee sam Baba yace baze kar6a ba amman Al’ameen yayita
insisting seda Baba ya karb’a yayi mai godiya. Har waje ya mai rakiya sannan ya
dawo shikenan atlast Allah ze rabasa da Zeezee shi bek’i ko a gobe a d’aura auren
ba Zeezee ta tare tabar mai gida. Allah-Allah yake kawai Mama ta dawo ya watsa mata
labari, Zeezee baiwar Allah dake d’aki batasan meke faruwa ba jira kawai take biyar
yayi azo a rufeta as usual setaji shiru yau.

To Maghrib Mama ta dawo gida, bayan dawowan Baba daga masallaci yashigo d’aki
tare da rage kayan jikinsa ya zauna bakin gado.
“Sannu da zuwa Alhj, naga yau baka kulle Zeezee ba ko punishment d’in ya k’are
ne?”
“Ya k’are mana tunda ta kusa aure.”
“Ko kayi mata miji ban sani ba.” tai maganan tana ninke kayanta.
“Ina abokin nan nawa yaron nan, Maj-Gen Muhammad Al’ameen wanda muka had’u dashi
a Saudiya lokacin da mukaje?”
“Eh wani farin sojan nan ko?”
“Shi!”
“Ayya na ganesa inade ba mutuwa yayi bako?”
“LOL ko kad’an d’azu ai yazo yace na gaisheki ma.”
“Ayyah ina amsawa.”
“Toh shi yaga wancan ‘yar iskan yace yana so.”
“Shi Maj-Gen d’in yaga Zeezee yace yana so?”
“Ni kaina abin yaban mamaki dan ban zata ma yanada ra’ayin aure ba saboda he is
almost 42 ashede lokaci ne beyi ba.”
“Alhj anya kuwa? Ba kai kamai tallan Zeezee ba?”
“Kamar ya ni namasa tallan ta? Inma tallan ta zanyi ai bazan yi a gun masu
mutunci kaman Maj-Gen ba sede a kasuwa.”
“‘Yarka cefa Zeezeen kake aibanta ta haka.”
“Aww dan bance zanyi sadak’anta masa ba kike neman gayamin magana, ina wayana
baki sanni bane.”
Da sauri ta d’ale gadon ta ja wayan nasa “wallahi baza ayi haka a gida na ba.”
“Bani wayan nace!”
“Ban badawa, kamar ya zakayi auren sadaqa da Zeezee? Astaghfirullah ko
handicapped (masu nak’asa) ma anbar yin sadaqa dasu se Zeezee yarinya da kyanta da
ilimi da budurcinta kace zakayi sadaqa da ita, wallahi a’a.”
“Kyan banza kyan wofi! Me kyan ya amfana mata? Su Yasmeen da Mariam sun fita
mutunci a idona, auren sadaqan zanyi da ita ta shiga hankalinta.”
“Haba Alhj! Wallahi koshi Maj-Gen d’in yaji sadaqar da ‘yarka zakayi zesan da
akwai wani b’oyayyen al’amari bayan nan ma koda bayan auren ne baze rik’eta da
mutunci ba as zena mata kallon ‘yar iska.”
“Toh mene ba ‘yar iskan bace? Sadaqan zanyi da ita ko sadakinta banason gani
yasan batada value a ido na.”
“Alhj inhar kana tsoron Allah kana k’aunan manzon sa baza kayi haka ba, kai yanzu
baka tunanin ya zamu b’ullo wa Zeezee da wannan al’amari kasani ko zata yarda koko
a’a?”
“Da Zainab tana so da bata so Maj-Gen. zata aura se in shine yace ya fasa kinji
na rantse.”
“Toh naji amman de ba bata shi sadaqa zakayi ba dan Allah nace” da k’yar Mama ta
samu Baba ya yarda ya fasa bada Zeezee as sad’aqa wa Al’ameen.
“Toh barinje in fad’a mata.”
“Wannan ke kika sa kanki don da kin sanar da ita da bakiyi ba auren ta da
Al’ameen ba fashi.” Ba tare da tace komi ta kama hanyan d’akin Zeezee.
As usual miqe kan gadonta ta tarar da ita “sannu Mama” tayi maganan tana
k’ok’arin zama.
“Yauwa sannu” Mama ta zauna a gefenta.
“Yau Baban naki be rufe ki bako?”
“Eh nima na rasa dalili.”
“Uhm d’azu ashe wani abokin Babanku yazo.”
“Eh wani farin soldier ko? Yazo har Baba ya kirani nayi serving nasa drink.”
“Ayyah, Zeezee ki bud’e kunnwanki da kyau ki saurareni toh. Kinsani har yau
Babanki yak’i hak’ura ko? Yana kan bakansa na yin sadak’ar ki with whomsoever
right?” A hankali Zeezee ta gyad’a kai “eh Mama amman ai zaki cigaba da basa
hak’uri ko? Kar yayi min auren sadaqa.”
“Sosai se a inda k’arfi na ya k’are.”
“Nagode Mama.”
“So kinga abokin Babanku da yazo d’azun ai? Sunansa Maj-Gen. Muhammad Al’ameen
Shettima ya ganki yace yana sonki da aure-”
“Aure?!” Zeezee tayi maganan unbelievably tare da miqewa.
“Aure kuma Babanku ya riga ya basa ke, ko ince ya mishi sadaqar ki.”
“Innalillahi wa inna ilaihi raji‘un My Very Own!” se kan gado tayi ta fad’i a
sume. “Zeezee! Zeezee!” Mama ta shiga tapping nata ganin ba response ta nufi d’akin
Baba aguje tana k’wala mai kira “Alhj! dan Allah kazo Zeezee ta sume min!”
“Ba inda zanje, ta mutu taga dama auran Al’ameen ne se tayi dan haka kibar cika
min kunne.”
“Alhj! Abinda zaka ce kenan?”
“Tabbas” batayi ta kansa ba ta koma d’akin Zeezee har yanzu she is unconcious.
Bayi ta nufa ta d’ibo ruwa ta yayyafa mata a fuska a hankali ta soma kefta ido,
wani hamdala Mama ta saki “Zeezee! Tashi kinji?” Kuka Zeezee ta shiga yi “Mama dan
Allah ku rufa min asiri, wallahi na tuba bazan sake ba dan Allah karkuyi sadaqa na,
na rok’e ku.”
“Zeezee calm down nayiwa Baban naku magana an fasa yin sadaqan dake amman hakan
bawai na nufin bazaki auri Maj-Gen. bane aure ba fashi, Muhammad Al’ameen shine
mijinki Zeezee.”

“Noo, noo Mama dan Allah karku min haka, what of My Very Own? Wallahi bazan iya
auran YaAl’ameen ba, bana sonsa yamin tsoho dayawa Mama karku lalata mi future dan
Allah in aurar dani Baba yakeson yi dan ya huta a gobe wallahi zan kawo mai miji ku
rufa min asiri dan Allah.”
“Dolenki ki auri Al’ameen da kink’i da kinso ‘yar iska kawai.” Fad’in Baba dake
tsaye bakin k’ofa “aure ba fashi, nan gaba ko kasheki za’ayi akace ki kwana a waje
baza kiyi ba. Kinma ci sa’a shi Al’ameen ne yace yana sonki wallahi da Ya Wakeel na
shago ne ya soma zuwa kokuwa me dry clean d’innan Uthman kinji rantsuwa ba kaffara
zan basu ke a sadaqa ma in huta dake. Tun wuri gomma kinsan ina ke maki ciwo, da
d’an iskan saurayin naki zaki kawo min kuma kike tsammanin zan aura miki shi?
Lallai bakida hankali.”
“Baba dan Allah kayi min rai, karka min auren dole na tuba, ka yanke min kowani
hukunci amman banda wannan Mama dan Allah kibasa hak’uri banason Maj-Gen. bazan iya
auransa ba.”
“Se muga meze hanaki auran nasa, muddin ba mutuwa kikayi ba wallahi Al’ameen
shine mijinki, Hafsah tashi kibar d’akin nata zan rufe.”
“Baba dan Allah kayi hak’uri wallahi bazan sake ba na tuba, Mama dan Allah ki
basa hak’uri, ku rufa min asiri dan Allah.”
“Alhj dan Allah ko na yau ne kabarni in kwana anan kaga condition nata.”
“Ki tashi nace karki b’ata min rai... Bazaki tashin bane?” Zanin Mama Zeezee ta
tattara ta rik’e tana kukan cire rai “Mama dan Allah kuyi hak’uri karku aura min
Maj-Gen wallahi na tuba”
“Bazaki saketa bane?” Kai kawai take jijjigawa tana me cigaba da kuka, “dan
Allah kuyi hak’uri wallahi bazan sake ba.” K’arisawa cikin d’akin Baba yayi yaja
Mama kamar baby’n roba sukayi waje sannan ya datsa kwad’o a k’ofan. Bin k’ofan
Zeezee tayi tana bubbugawa tana kuka sosai “Baba dan Allah kayi hak’uri, kamin duk
wani abinda kaga ya dace dani amman banda wannan dan Allah, karka aura min wanda
bana so, na rok’eka dan Allah fa nace” ta k’are maganan tana kuka tana jijjiga
k’ofar. Mama kanta batasan a sanda ta soma hawaye ba.
“Alhj dan Allah ka tausayawa yarinyan nan kabarni in kwana da ita yau” ko
sauraronta beyi ba yaja hannunta zuwa d’akinsu. “In har kika koma d’akin ‘yar iskan
can kuma ban yafe ba.”g

****
Kuka Zeezee ketayi a tsakar d’akin nata a yayinda kan ta keyi mata wani irin
sara. How? Taya Adeel na raye zata auri wani na miji daban, mijin ma wai abokin
Babanta wanda she is sure da yayi aure da wuri da ya haifi kamanta. Taya zata fara
sanar da Adeel wannan sad news? If only tasan ya zatayi ta gudu data gudu tabar wa
Baba gidan gabad’aya. She can’t imagine life without Adeel, her Very Own. Kukan ta
cigaba dayi har seda bacci 6arawo yayi gaba da ita a wajen.

Da Asubah Mama ta taho da key ta bud’e mata k’ofar. A hankali ta tayar da ita
“tashi Zeezee kiyi Sallah Asubah tayi, kinyi Isha ma kuwa?” Kai ta kad’a da k’yar
“Mama kaina ciwo”
“Tashi kiyi alwala toh bari na kawo miki magani.”
“Banaso bana buk’ata na gwammaci ciwon kan ya kasheni na huta tun wani zamani
aka dena auran dole wa mutum da Baba ze aura min tsoho kaman abokinsa.”
“Ya isa haka toh. Aww baki godewa Allah bama da ba sadaqar ki zeyi ba wato?”
“Ai duk d’aya ne me maraban dambe da fad’a? Taya zan auri sa’an Baba na Mama?
How?”
“Ke wayace miki Maj-Gen. sa’an Babanki ne? Shekara goma sha uku (13) nefa
tsakaninsu koni nan na girmeshi tunda he is 42 nikuma am 45, tashi kiyi Sallah.”
“Mama yanzu kema kin goyi bayan a aura min tsoho? Am just 17 fa sena kama auran
me 42 years old? Kun min adalci kenan? Dan Allah ki bawa Baba hak’uri inada wanda
nakeso in aurar dani yake sonyi a yau d’innan zezo su tauna ko sadaqa na ne seya
basa na yarda amman banda Ma-Gen please.”
“Wa? Kina nufin d’an iskan saurayin ki dake saki kwana a waje? Wallahi koni ne
bazan aura miki shiba. Inba ke da sokanci ba ajinki Sadeeq ne ko waye ze yi zaman
mutunci dake ne? Ya riga da yasan ‘yar iska ce ke koda kin auresa baze na ganinki
da mutunci ba.”
“Inde Ad- aww Sadeeq, inde Sadeeq ne wallahi I trust him he’ll never betray my
trust.”
“Kefa wawiya ce jekiyi Sallah da Allah!” Nan da nan ta biya Isha tayi Asubah Mama
ta b’allo mata panadol tasha. “Ke inbanda abinki mutum kaman Maj-Gen. yace yana
sonki kik’i? Mene ya rasa? Ga kyau, ga future gakuma hankali da sanin ya kamata,
nitsatstsen namiji kaman shi. Ko bakiga sojojin da suke guarding nasa bane? Babban
soja nefa.”
“To hell with all of that, ni bana sonsa, banason farin na miji banason auren
soldier and most of all banason auran abokin Baba na ni Very Own d’ina nakeso” tasa
kuka.
“Zakiyi ki gaji ki bari kuwa, ai dama bari nayi uban naki yayi sadaqan ki tunda
ke bakida mutunci. Gomma tun wuri kin tattara hankalinki gu d’aya ki nitsu ki bud’e
zuciyarki wa Al’ameen dan wallahi kece zaki wahala kizo ki tashi a tutan babu keba
Sadeeq ba keba Al’ameen ba.” Mama na kaiwa nan ta fice. Ihu Zeezee tasa kanta kaman
ze fashe dan ciwo amman hakan besa tabar kukan da take ba, ko breakfast tak’i ci
ranan.

*© MIEMIEBEE Team #YGC!*


www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2016*
3⃣0⃣

Bayan an k’are breakfast Baba ya kira Al’ameen ya sake jaddada masa kan
Zainab fa tasa ce sede inshi yace ya fasa and also karya saurari duk wani abinda
zata fad’a mai saboda yarinya ce batasan ciwon kanta ba har yanzu. Sosai Al’ameen
yaji dad’i ya buk’aci numban Zeezee inda Baba ke fad’a mai batada waya amman ze
masa sending na uwar yaso se suna gaisawa tacan. Sosai Al’ameen yaji dad’i yayi
godiya and not long enough Baba ya masa sending numban Mama. Mama na kitchen tana
d’an aiki wayarta ya shiga ringing ganin new number ta d’aga tare da yin sallama.
“Wa’alaikumus salam” Al’ameen ya amsa cikin sark’ak’k’iyar muryarsa me tafiyar
wa mutum da imani tare da gaisheta, sama-sama suka gaisa Mama tace bari ta kaiwa
Zeezee wayar. Kwance a tsakar d’akinta tana takan rusa kuka Mama ta tarar da ita
“ke tashi gashi ana neman ki.” Kaman bazata amsa ba tace, “waye?”
“Ina zan sani ki karb’a mana kina b’atamin lokaci.” Hannu ta miqa ta amsa seda
taga Mama ta fita daga d’akin tace, “waye?” Harshly.
“Uhm-uhm” Al’ameen yayi clearing throat nasa, “a farko de suna na Muhammad
Al’ameen-” wata doguwar tsuka cike da rashin kunya Zeezee taja. Dama yasan this was
coming, “Zainab is there a problem?” magana ta soma cike da tsiwa.
“Yes and you are my problem, haba mana bawan Allah mena tare maka da zaka ce
seni zaka aura? Wallahi kasani ni bazan aureka ba, bazan auri tsoho kaman ka ba in
kuma har kabari akayi wannan aure kaji na rantse wallahi seka gommaci kid’a da
karatu. Tun wuri gomma ka koma kaje ka samu Baba kace mai kai ka fasa. ‘yar 17
years dani zakace zaka aura? Kasani inada wanda nakeso kuma shi zan aura.”
Kasancewar Al’ameen ba mutum neba me son tashin hankali da hayaniya bece mata komi
ba yayi hanging wayar kawai. Ganin fa rashin kunya is not a solution tayi calling
nasa back bayan yayi picking tace, “I’m sorry ina kwana Ya Al’ameen? Dan Allah
karka gayawa Baba abubuwan dana ce maka kayi hak’uri sharrin shed’an ne” kai kawai
ya kad’a.
“Lafiya Zainab mun tashi lafiya?”
“Lafiya k’alau.”
“Uhm so I will believe kinsan kowaye ni and kinsan purpose na kiranki danayi koh?”
“Eh Mama ta fad’amin komai.”
“Masha Allah, so am I welcomed?”
“Ya Al’ameen dan Allah nace badon niba, ka dubi girman Allah SWT ka rufa min
asiri ka janye maganan auren nan wallahi sam kai ba taste d’ina bane bawai ina
nufin kai mumuna neba ko ka gaza ta wani fannin bane kawai inada wanda nakeso ne
kaji k’aina please my future lies in your hands karka rabani da masoyi na.”
D’an dariya ya saki, “Zainab you don’t even know me bale kice bakiya sona try
giving me a chance kinji?”
“Eh nide kayi hak’uri bani buk’atan sanin kanma. In mata kakeso akwai friends
d’ina dayawa da suke son fararen maza kaman ka sena had’aku dan wallahi ni bana
sonka banason farin na miji kuma farin ma wai soldier, soldier’n ma wai 42 years
old, kayi hak’uri dan Allah” tasa mai kuka. Dariya sosai ta basa “to mesa bakiya
sona? Give me one reason aside from I being fair and a bit aged, kinga bani na
hallici kaina ba ko? Kuma fa kema fara ce naga.”
“Eh ai ban kaika ba kuma ni fara sena auri fari? Ai sirkawa ake kai baka ga Mama
fara Baba bak’i neba? Ka rufa min asiri dan Allah.”
“Toh tell me the reason why you don’t like me.”
“Sabida inada wanda nakeso.”
“Oh is that so? Shikuma ya skin colour nasa yake?”
“Yana nan da haske kad’an d’an bak’i-bak’i ba fari bane shi.”
“Now I get where you are coming from, but Baba besan kinada wanda kikeson bane
yace yaban ke?”
“Yasani kawai bayason aura min shine.”
“Toh mesa?”
“Nikam sekace d’an jarida meh ruwanka da dalilin, ni kawai kace wa Baba ka fasa
aure na banida tarbiyya kaji please Maj-Gen.” Nanma dariya ya saki.
“Aikuwa ni bazan iya fad’awa Baba haka ba because through out my life ba gurl
data ta6a getting attention and mind d’ina kaman ki Zainab.”
“Ni dan Allah kadena banaso” ta sake sa wani kukan “wallahi inada wanda nakeso
inhar kana sona bazaka sani auranka ba tunda bana sonka ni kamin tsoho ma dayawa.”
Wani dariyan ya sakeyi sosai this time around gaskiya Zeezee is funny. “Toh naji
we’ll do it this way zan fad’awa Baba kince kinada wanda kikeso in yayi agreeing ze
aura miki shi saurayin nakin fine ni zan hak’ura if not kuma ni zan aure ki.”
“Ai kaima kasan ba yarda zeyi ba.”
“Toh mesa?”
“Sabida yace saurayin nawa d’an iska ne shikenan kaji reason d’in ka huta yanzu
zaka bar neman aure na?”
“Yes naji amman bawai zan fasa neman aurenki bane because I love you for the sake
of Allah Zainab try giving me a chance kinji? ke yanzu a d’an iskan kike sonsa?”
“Eh wallahi ni ahaka nake sonsa dan Allah karka shiga tsakani na dashi.”
“Nikuma ya kikeso nayi da son da nake miki Zainab?”
“Ka yafe shi zanyi ta maka addu’a Allah kawo maka macen da zata soka tsakani da
Allah kaima.” Nanma dariya yasa sannan yace;
“Toh ai kece macen Zainab.”
“Wallahi kaga ina maka sanyi-sanyi kake taking d’ina for granted ko? kasani fa na
iya suburbud’a rashin mutunci, inhar ka kuskura kabari akayi mana aure wallahi
you’ll rule the day you were born tunda ina baka girmanka na wanda ya haifeni baka
gani. Ko kai ace yanzu kanada ‘ya kaman ni zaka yarda ta auri me kalan shekarunka
ne? Kayi adalci mana Daddy.”
“Uhm-uhm” yayi clearing thraot nasa “beyi zafi haka ba Zainab naji bari zanyi wa
Baba magana.”
“Da yafi kam kace masa ni ban maka ba kawai.”

Tana katse wayar ta share hawayenta a yayinda Al’ameen ya kira Baba, “hello
Brother.”
“Yes Maj-Gen.”
“Uhm yanzu muka gaisa da Zainab but it seems theres a problem.”
“Problem? Wani iri kenan?”
“Tace tanada wanda takeso I can’t force her into marrying me nakega zan hak’ura
kawai.”
“Tanada wanda takeso haka tace maka? Lallai yarinyan nan she wants to die kabarni
da ita.”
“A’a Brother please calm down, inhar hakan ne why not ka aura mata shi d’in?”
“D’an iskan yaro ne kaide kanason Zeezee koko a’a?”
“Ina sonta inde so ne.”
“Toh kai zaka aure ta kada kaji duk wani shirmen da zata fad’a maka bata da wayo
ne kaji please?”
“Naji Brother am grateful.”
“Nine da godiya” yana kaiwa nan ya katse wayar se d’akin Zeezee, buga k’ofar yayi
seda ta razana. “Me kikace wa Al’ameen?” Ya tambayeta furiously.
“Bb... Babu” tayi stammering.
“Ina wasa dake ne? Nace me kikace mai ko sena baki kashi zakiyi magana?” Yayi
taking few steps close to Zeezee. B’ari tashiga yi “Baba dan Allah kayi hak’uri ce
masa nayi inada wanda nakeso bayan nan wallahi bance komai ba.”
“Uwarki nan da ke da wanda kikeson, kinji ba uwaku duka nace ‘yar iska kawai ni
zaki baiwa kunya? Nace na miki miji kice masa wai ke kinada wanda kikeso, iyyeh?”
Yi yayi kaman ze rufe ta da duka nan tashiga k’wala wa Mama kira and ba tare da
b’ata lokaci ba Mama ta fito daga kitchen. “Ya haka Alhj?” Tayi maganan tana jan
Baba baya.

“Kinji ba this should be the first and last time, Al’ameen ya sake kiranki kice
masa kinada wanda kikeso kiga abinda zan miki in ban baki wa Ya Wakeel na shago as
sadaqa ba ki canza min suna. ‘Yar iska dake ma kisamu gentleman kaman Al’ameen ki
tsaya kina mai yanga? Ajinki da yasan halinki ma zece yana sonki ne? Dake nake
magana!”
“A’a kayi hak’uri.”
“Wawiya kawai” yana kaiwa nan ya fice. Kuka Zeezee tasa tana sauqa har k’asa. “Ke
me kikace wa Al’ameen d’in Babanku ke fad’a haka?”
“Mama daman kinsan shi ya kira kika k’i gayamun?”
“Ba abinda na tambaya ba kenan, me kikace mai Babanku ke fad’a haka?”
“Gaskiya na gaya mai mana, banason abokin nasa.”
“Gomma kin nitsu fa Zainab tam! Ki nitsu dan k’aniyanki meh Al’ameen ya rasa da
zakice baki sonsa ko se an aura miki Ya Wakeel asalin tsohon zaki shiga
hankalinki?”
“Ni banason farin na miji-”
“Ked’in mene? Ba fara ce keba? Ni d’inma ba fara bace? Se a k’imu saboda kalan
fata?”
“Kece de fara nide wallahi ba fara bace sabida ban kaiki fari ba, haske ne kawai
dani. Ni wallahi bana sonsa gasa kuma soja, sojan ma tsoho har 42 wayyo Allah Very
Own d’ina!!”
“Zako ki gaji kibari wallahi dan koni nan na goyi bayan auran nan naku d’ari bisa
d’ari.” Mama na kaiwa nan ta fice. Wayar Mama Zeezee taja ta kira Lubiee and not
long enough ta d’aga “hello Babe, kwana biyu kin b’oye.”
“Lubiee dan Allah help me out.”
“Me kuma ya faru yanzu?”
“Aure Baba zemin wallahi harya min miji wani farin soldier wai shi sunansa
Muhammad Al’ameen kuma fa karki manta tsoho ne wallahi he is 42 years old.”
“Wow! A Soldier?!” Lubiee tayi exclaiming.
“Me wani wow? Karki ban haushi mana, think of a solution please.”
“Ke Zeezee bakisan auren kalan masu age na Ya Al’ameen yafi dad’i ba? Come to
think of it yanzu kallon yarinya yake miki duk wani abinda zaki masa koda rashin
hankali babba kika tafka gani zenayi yarinta ke damunki yana baki excuse and above
all sunfi iya soyayya wallahi. Incase of young brats kalan su Adeel naki kuma suma
kansu rawa yake, he is just 25 koda ba laifi kika mai ba, baze tab’a iya
overlooking slightest mistake naki ba sede ku taru kuyi ta fad’a da yarinta kullum.
Ga solution nan Allah ya kawo miki har d’aki Zeezee, ni wallahi tun ban gansa ba
nasan ya had’u soldier nefa! Its always my dream to marry a soldier me rank nasa?”
“Ke gidanku kina jina ko? Zaki bani shawaran ne kokuwa?”
“Toh gayamun me rank nasa.”
“Oho wai Major-General ne komeh ni ba abinda ke damu na ba kenan. Help me out
please, wallahi bana sonsa Babe, Very Own d’ina nakeso shi kuma zan aura.”

“Ke Zeezee wallahi baki san ciwon kanki ba har yanzu, me zakiyi da Adeel bayan
Allah ya kawo miki Soldier me future? Adeel fa malalaci ne ko aiki yak’i ya fara da
anmai magana yace kud’in gadonsa ya ishesa. Ahakan kikeson ki zauna dashi? Rananda
kud’in ya k’are fah?”
“Seya nemi aiki a lokackin” ta amsa a takaice.
“Akwai guarantee na samun aiki ne a wannan country namu?”
“Ke ni ko a talauci zan zauna da Adeel bale ma he’ll never go bankrupt ki
taimaken please Lubiee banason wannan Al’ameen.”
“Aiko banida shawaran dayafi nace ki bud’e zuciyarki wa Ya Al’ameen dukda bansan
sa ba nasan gentleman ne shi, eventually zaki fara sonsa just give it a try.”
“I can’t, my heart is with Adeel and him alone I thought a friend indeed is a
friend in need amman you aiint ready to help me thanks.”
“Ze-” katse wayar Zeezee tayi koda Lubiee ta kirata kuma k’in d’agawa tayi haka
ta rufe kanta a d’akin ta cigaba da kuka ita shikenan tana ji tana gani za’a raba
ta da Adeel nata and theres nothing she can do about it? There has to be a way!

*~ *~ *~
Washegari Al’ameen ya kira Zeezee still ta wayan Mama alokacin ma wayan na
gefenta tana ganin numban jikinta ya bata shine tak’i d’agawa ya kusa yankewa Mama
tashigo d’akin “wayana ne ke ringing?” Kafin Zeezee tace zata d’aga ya yanke. “Waya
kira?”
“Uhm... Uhm nima ban sani ba.” Amsan wayan Mama tayi ta duba nan ta gano
Al’ameen ne.
“Numban Maj-Gen d’inne zakice wai baki sani ba?”
“Aw shine?”
“Ohh k’arya zakimin? Inje in gayawa Babanki Al’ameen ya kira kika k’i d’agawa?”
“A’a, a’a dan Allah kiyi hak’uri ya sake kira zan d’aga.”
“Seya sake kira? Babban mutum dashi? D’aga ki kirasa maras kunya kawai!”
“Mama sena ce mai meh? Kibari mana ya sake kira.”
“Alhj!” Mama ta shiga kiran Baba.
“A’a dan Allah ki bari zan kira san, zan kira.”
“Oya amshi ki kira san!” Amsan wayan Zeezee tayi tana galla mai harara “ya what
are you waiting for?”
“Toh kifita mana kina tsaye akaina ne zan yi waya dashi?”
“Alhj!”
“A’a zan kira zan kira Allah” nan tayi calling nasa bada jimawa ba yayi picking.
“Hello...?” Shiru Zeezee tayi not ready to talk, mari Mama ta kai mata a baya
fas! “Baza kiyi magana bane?” Tana susa wajen tace, “ina kwana?”
“Lafiya Zainab, how are you?”
“Lafiya” ta amsa k’asa-k’asa se anan Mama ta fice nan Zeezee ta samu kanta “ka
kyauta ai daka kama kaje ka had’amin gu wajen Baba.” Dariya sosai ya tsaya yi
Zeezee bata gajiya da sasa dariya, “menayi kuma Zainab?”
“Bansani ba, nace kace masa baka sona ka kama kace mai wai nace maka inada wanda
nakeso saura k’iris yamin duka wallahi jiya.”
“Duka?!” Yayi exclaiming yana sake mik’ewa kan red california bed nasa, haka
kawai maganan Zeezee kesa sa dariya.
“Eh mana, ai dagangan kayi.”

Yana dariya yace, “ina ni Zainab! am sorry toh it’ll never happen again.”
“Wai mahaukaciya ce ni da duk maganan da nayi kayita min dariya? Kuma ina bazaka
ja baya da zancen auren nawa bako?”
“Mesa zan ja baya da maganan auren ki Zainab? Just give me a chance.”
“Aww ma tambaya kake? Wai kai rashin kunyan da nake maka bai damunka ne? Wallahi
ko Adeel bana gaya mai magana kaman yadda nake gaya maka.”
“I’m not Adeel I’m Al’ameen.”
“Oho maka ni inada abinyi Daddy se anjima kuma wallahi Daddy har ka bari aka mana
aure se kayi nadama.” Bata jira jin me zece ba ta katse. “Ai wallahi seka gommaci
kid’a da karatu muddin ka bari akayi mana aure dan ni ai belong to Adeel and no one
else.” Ganin Mama tayi bak’uwa tasa lock d’akinta tayi skyping Adeel “Hi Very Own.”
“Sweetest Love I thought ko nayi laifi ne yadda kikayi dumping d’ina a trash can
two days. I wanted calling you amman ina tsoro kar Mama ta d’aga, I really miss
you.”
“Wallahi I miss you more Very Own banji dad’i bane two days shiyasa.” ta gyara
kwanciyanta kan gado tare dayin ruf da ciki, shima copying style nata yayi.
“I should have guess, so how are you feeling now?”
“Much better don’t worry.”
“I miss you, I miss your arms around me.”
“I miss yours too, I miss your fragrance Very Own its hard living without you”
tayi stating as if though crying.
“Shhh! Babe we will be together soon enough. I believe in us, so ya kike da Baba
har yanzu, any progress?”
“Not at all har yanzu wai aurar dani zeyi to whomsoever.”
“Toh why not naje nace mai nazo neman aurenki?”
“He isn’t dumb Adeel kallo d’aya ze maka yasan you must be my boyfriend, though
har yau ban fad’a masa actual name naka ba duk da Sadeeq suka sanka.”
“I love you Babe.”
“I love you too...” Daga nan suka zarce hiran Lovey-Dovey dan kansu sukayi
sallama not long enough Lubiee ta kirata da kaman bazata d’aga ba sannan tayi
picking “meh na kira nan kuma?”
“Haba Babe menayi kuma? Gimmie a break mana!”
“Bansani ba ina ni zaki watsa ma k’asa a ido?”
“Bawai batun watsa miki k’asa a ido bane Babe understand mana, kinfa san koda
had’a sama da k’asa zakiyi Baba baze ta6a aura miki Adeel ba toh why not ki hak’ura
da Ya Al’ameen d’in. Kuma fa he is just 42 bawani tsoho bane ko kin manta Annabi
Muh’d SAW ma seda yakai 40 years aka basa annabci? Na miji at 42 wallahi ba tsoho
bane.”
“Oho damuwanki ni in sonsa kike wallahi ina iya had’aku.”
“Banza! taya zan sosa? Nima my own Soldier is there somewhere waiting for me.
Kinsan meh?”
“Sekin fad’a.”
“Why not to just go with the flaw?”
“Kamar ya to go with the flaw ban gane ba.”
“I mean koda bakison Ya Al’ameen pretend you do-”
“Chabd’i! Akan meh?” Ta katse Lubiee take.
“Ohhh! Ke ki tsaya mana kijini, will you?”
“Toh inaji” tayi maganan in an I don’t care tone.
“Ehem kina jina? Ko baki sonsa ki nuna a gida kin amince da auran saboda ladabi,
kinga you’ll then kill two birds with one stone infact naki ma three birds ne. Na
farko kinga ahaka ne zaki gyara relationship naki da Baba, na biyu Ya Al’ameen
nasan me kud’i ne saboda Maj-Gen ne arzikinsa zaki tatsa kaman nono wallahi. Bakida
waya yanzu kikace ya sai miki take zeyi saboda he wants to make you happy kema
eventually you will not know when you’ll fall for him.”

”LOL dama-dama first and second points nakin ma amman dekam banda na ukun dan ni
banga abinda ze sani son wannan Al’ameen ba.”
“Why not?”
“I have an alternative.”
“Which is?!” Lubiee ta tambaya a takaice.
“Kinga daman a gida kowa ya riga yayi believing ina son shi Ya al’ameen d’in ba?
Bayan biki sena gasa mai aya a hannu I won’t rest until ya sake ni kinga koda na
dawo gida kowa ze yarda shine ya cuceni yaganni ‘yar yarinya yayi taking advantage
d’ina only then I can marry my Adeel.”
“Uhm har haka Babe? Nifa da zaki bi nawa wallahi ki mance da Adeel trust me and
give Ya Al’ameen a chance he’ll definately win over your heart than Adeel did.”
“Ba ruwanki, nide kinban clue shikenan thanks.”
“Toh hope we good now? Tunda na share miki hawayenki yanzu?”
“Ofcourse Babe I love you, kud’in Al’ameen se yayi kuka wallahi shi ba wai
yaganni yana sona ba, ze sani!”
“Kide bisa a hankali.”
“LOL nagode semun sake waya probably a new line d’ina.”
“Haha shegge Babe kina wuta ina binki da nuclear bomb Allah yasa toh.”
“Ameen duk abinda akwai I’ll let you know.” Tana katse wayar ta ajiye tana
tunanin ya zata fara gudanar da wannan plan nata into action. Sanin 5pm Baba zezo
ya rufe mata d’aki, bayan sallan La’asr ta tabbata Baba na gida ta nufi d’akin Mama
tayi sallama.

“Wa’alaikumus-salam” shida Mama suka amsa.


“Sannu Baba, sannu Mama.”
“Yauwa sannu Zeezee” cewar Mama a yayinda Baba yayi banza da ita.
“Uhm Baba nazo ne na baku hak’uri akan abubuwan dana muku a baya, kuyi hak’uri ku
yafe min. Duk abubuwan da kuka min bangani ba dana tashi na sak’a muku da butulci
na 6ata muku suna a gari. Am truely sorry ina fatan zaku yafemin. Na tuba bazan
sake ba, maganan auren Ya Al’ameen kuma da nace da abaya banaso shima kuyi hak’uri,
wace ni da zaku yanke hukunci akaina nak’i bi? Ba Ya Al’ameen ba kowa kakeso na
aura zan aureshi Baba inhar yin hakan ze farinta maku rai da Mama. Bazan gaji da
baku hak’uri ba dan Allah kuyi hak’uri wallahi na tuba na kuma amince zan auri Ya
Al’ameen ko a gobe kukeson in tare zan tare. Farin cikinku ya fiye min komai a
duniyan nan sabida banida kamanku my dear parents am so sorry please find it
somehwere in your precious hearts to forgive your dear daughter.” Ta k’are maganan
cikin sautin kukan munafirci.

*Team #ADEEL🎀 OR Team #MAJ-GEN.AL’AMEEN❣??? nide nace...!!!*

*© MIEMIEBEE*

www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
[1/7, 3:04 PM]

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2016*
3⃣1⃣

Wani irin dad’i maras misaltuwa Mama taji a ranta a yayinda hawayen jin dad’i
suka soma gangarowa daga idanunta. Finally Allah ya amsa mata addu’arta ya shiryar
mata da Zeezee a lokaci guda. Ba ita kad’ai ba harta Baba yaji dad’i matuk’a,
saboda yadda Zeezee ta tsara maganan bame sanin wai duk plan ta had’a ga yadda take
kuka me tsuma zuciya full of regret. “Come here Sweetheart” Mama tayi beckoning
nata over. A nitse ta miqe, hugging nata Mama tayi suna kuka tare duk anan kallonsu
Baba yake seda Mama tayi releasing Zeezee yaja hannun Zeezee tare da hugging nata
shima. “Alhamdulillah! My old Zainab is back na yafe miki K’anwata, Allah ya cigaba
da shiryar mana dake.”
“Ameen” shida Mama suka fad’a.
“Baba ina me sake baka hak’uri.”
“Kema kiyi hak’uri K’anwata for what happened am sorry kinji?”
“Ni baka min komi ba Baba, I love you so much.”
“Allah cigaba da raya mana ke.”
“Ameen” nasiha sosai Mama da Baba suka ta mata a yayinda take ta sheqe kuka, sun
gama mata ta musu godiya ta fice a d’akin tana mejin dad’in completing first
mission of her plan. Sosai Mama da Baba sukaji dad’i se sawa Zeezee albarka suke
duk sun d’au dagaske ne Zeezee ta shiryu musamman ma Baba da abin yafi damunsa
nunawa ne kawai bayayi.

Washegari Zeezee na tashi da safe bayan tayi wanka ta nufi d’akinsu Mama ta
gaishesu cike da ladabi sannan d’akin Omar bayan nan ita da Mama suka shiga kitchen
for the first time. Dukda kwa6a take amman yau ta shiga kitchen d’in da sunan yin
aiki. Sun gama breakfast Zeezee ta ari wayan Mama da sunan zata gaishe da Al’ameen.
Ba tare da Mama ta kawo wani tunani a ranta ba ta bata wayan, seda ta rufe k’ofan
d’akin nata ta zauna kan kujera sannan tayi dialing number’n Al’ameen. Bejima ba ya
d’aga.
“Hello Ya Alameen ina kwana?”
“Wow! Zainab kece?”
“Nice mana, ina kwana?”
“Lafiya hope you slept well?”
“Yes I did I hope you too.”
“Alhamdulillah so you called? Am startled anya kuwa kece?”
“Nice mana, na kira ne dama na baka hak’uri game da rashin kunyan dana maka a
baya, am so sorry hakan ya faru ne bisa rashin tunanin da banyi ba amman I promise
it’ll never happen again. Kayi hak’uri please na amince zan aure ka, I welcome you
to my life wholeheartedly.” Al’ameen was left dumbfounded, anya kuwa Zeezeen daya
sani ce? Kode she is possessed by some kind of evil spirit ne? Kokuwa shiryuwa
tayi, but anya?
“Hello Ya Alameen? I know its hard for you to believe me but believe it or not na
tuba kuma ina neman gafararka.”
“Masha Allah Zainab, I think am the most happiest man on earth right now.”
“Am glad I made you feel that, so ka yafemin?”
“Ni bakiyi offending d’ina bama ai Zainab bale ki nemi yafiya na.”
“Hakane?”
“Sosai ma Zainab.”
“Toh nagode mesa kake cemin Zainab?”
“Isn’t it your name?”
“It is amman Zeezee ake cemin ai.”
“I prefer your actual real name, yana min dad’i sosai.”
“Thank you kaima sunanka na min dad’i.”
“LOL hakane?”
“Yes, so ya aiki?”
“Nad’an kar6i leave but alhamdulillah.”
“Toh masha Allah, ya kowa da kowa a gida? Kanada sisters? If yes meh sunansu?”
Haka Zeezee tayita jan Al’ameen da surutu ranan gabad’aya mamaki ya rufesa he can’t
believe actually its Zeezee. Shiko biye mata yayi ko breakfast ma beyi ba ranan
seda airtime na Mama ya k’are. Take ya kirata back tayita mai hiran shirmeh bayan
sunyi sallama yayi wa Mama VTU transfer’n 10k.

Wani maqirin murmushi Zeezee ta saki “ai wallahi Soldier seka gommaci kid’a da
karatu bakai wai Zeezee kakeso ba? Ha!” Ta cize lips nata. Haka nan tun daga ranan
Zeezee bayan 2-2 days take kiran Al’ameen. Atimes in bata kira ba shi yake kira
suyita hira kaman dagaske, Al’ameen could’nt ask for more, Zeezee is the most
happiest and sweetest thing that has ever happened to him. Tunda yake be ta6a son
‘ya mace kaman Zeezee ba kullum cikin zancenta yake wa elder Sis nasa Sadeeyah da
younger sisters nasa Salmah and Ayshah duk they are so eager suga Zeezee. Mamanshi
Hajiya Ameenah kam couldn’t ask for more finally Allah ya amsa mata addu’arta her
son is in love. Kullum Al’ameen cikin zancen Zeezee yake duk friends nasa sunsan da
zaman Zeezee, sonta yake tsakani da Allah, fiye da tsammanin d’an Adam, wannan
kenan!

****
Har a yanzu Zeezee bata sanar da Adeel halin da ake ciki ba kamar yadda tayi
hani wa Lubiee da komin rintsi karta fad’a mai itama when the right time comes
she’ll let him know. Everybody a gida believed Zeezee da Al’ameen soyayya suke
saboda har sau biyu yake zuwa mata Baba da kansa ya basu parlour’n shi suyita hira,
aduk zuwansa kuwa seyayi wa Zeezee kyautan kud’i wanda kaman dagake ta d’auka duk
ta baiwa Mama. Al’amura sun daidaita ras tsakanin Zeezee da Baba sun dawo kaman
yadda suke da sede har yanzu Baba bece ze sai wa Zeezee waya ba kamar kuma yadda
kuma be miyar mata da motarta ba.
*~ * ~*~
Yau ranar ta kasance Wednesday, 11:27AM Zeezee ta ari wayan Mama as always ta
kira Al’ameen bayan sun gaisa take cemai, “Ya Al’ameen tun d’azu naso kiranka Mama
bata tashi da wuri ba.”
“Ayyah ba komai My Princess, how are you?”
“As you are, did you sleep well?”
“I did I also dreamt of you.”
“Oh really?”
“Yeah” hira suka tayi chan yake fad’a mata ze koma aiki Abj anjima.
“Ayyah I will miss you.”
“Zanzo muyi sallama karki damu we’ll keep in touch.”
“Da wayan Mama da kullum ke hannuntan? Ina ma ace inada waya na sabida muna waya
kullum”
“Kuma haka fa yakamata ace kema kinada wayarki.”
“I use to have one.”
“Ya 6aci ne?”
“A’a Baba ne yayi seizing ya fasa lokacinda na ta6a yin wani laifi.”
“Will he agree if I buy you a new one?” Dad’i sosai taji finally her plan is
working.
“Ban sani ba seka tambayesa.”
“Toh karki damu My Princess zan taho miki da sabon wayanki yau in shaa Allah.”
“Really Ya Al’ameen?”
“Don’t you trust me?”
“Yes I do Ya Al’ameen thank you so much.”
“Shh! Lemmi take my shower my flight is by 1:30pm.”
“Tam sekazo see you” nan ta katse. “Mschww gaskiya na miji anyi soko wallahi yanzu
koshi Ya Al’ameen ne kome sunansa hankali baze basa duk faking nake ba? Ni ina zan
kai tsoho kaman sa? Anyways his own wahala my new phone is coming soon can’t wait
to skype my very own!”

12:19PM Al’ameen ya iso gidansu Zeezee da sabuwar wayarta cikin leather suna zaune
a parlour da Baba bayan sun gaisa yayi clearing throat nasa “Brother ina fatan
banyi gwaninta bako?”
“Name fah Maj-Gen?”
“Waya na siyo wa Zainab namu tace she is not confortable amfani da wayan Madam.”
“Oh hakane? Ba matsala toh.”
“Toh nagode Brother yauma zan koma Abj nazo muyi sallama da ita ne.”
“Toh bari nayi mata magana” Baba da kansa yaje ya kirawo Zeezee “K’anwata Maj-Gen
yazo wajenki.”
“Toh Baba ina zuwa” ta amsa tana murmushi, gyalenta taja sannan ta fice a k’asa
kamar yadda ta saba kullum ta zauna tare da mai sannu da zuwa. Duk da haushinsa da
takeji takasa ignoring kyan da Al’ameen ya mata, bata ta6a ganin hot man in uniform
kaman shi ba, farin fatarsa dake bata haushi ma yamata kyau yau amman ba hakan yasa
taji tana sonsa ba ita Adeel nata kawai takeso.
“My Princess bazaki zauna kan kujeran ba yanzu?”
“A’a Ya Al’ameen nanma yayi.”
“A’a ni ki hau ki zauna please.”
“Seriously nanma yayi karka damu.”
“Ni sekin hau toh.” Seda yayi dagaske sannan kaman dagaske Zeezee tahau kujera ta
zauna se wani kakkare fuskarta take. Hira kad’an suka ta6a yace ze tafi leather’n
wayan ya ajiye mata kan cinyarta. “As promised My Princess in colour’n be miki ba
let me know zan turo wani yaro na ya sai miki sabo.”
“Toh meh aciki Ya Al’ameen?” Tayi maganan tana bud’e leather’n black jet iphone
7s taga ciki “wow! Ya Al’ameen thank you!”
“Nifa na gaya miki banason godiyan nan, do you like it?”
“Yes I do thank you.”
“Am glad toh ni zan wuce.”
“Toh bari nafad’awa Baba” sede data duba alokacin Baba yashiga wanka dan haka ta
rakasa har waje tana ganin guards nasan ta wani had’a rai seda Al’ameen ya gano
hakan.
“Bakison ganinsu ne?”
“A’a” ta k’irk’iro murmushin k’arya “kawai tsoro suke ban da wannan guns d’in.”
“Next tim zanzo barasu zoba tunda baki son ganinsu.”
“Oh common karka damu Allah ya kare toh.”
“Ameen My Princess” Seda taga ficewarsu ta koma ciki wayar ta bud’e a garin haka
airtime na 10k da new sim card ya fad’o. Murmushi ta saki “wai! Zanyi skype da Very
Own har sena gaji!” Had’a wayar a charging tayi. Baba na fitowa daga bayi taje ta
fad’a mai. Nasiha sosai yayi mata and like a good girl tayi godiya ta fice.

****
Life couldn’t be better tun daga ranan da Al’ameen ya sai wa Zeezee waya ta rage
kiransa as 24/7 tana kan video or voice call da Adeel nata. Shima Al’ameen dake ya
koma aiki yanzu seya jera kwana uku be kirata ba in se in yasamu free time yake
kirantan, ita kuwa seta mai k’arya wai gari ba wuta shiyasa bata samun kiransa
itama wayarta ba chargi. Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa, wani new chapter’n
love Zeezee da Adeel suka bud’e. Da k’yar ranan Baba yabar Zeezee tajeta gidansu
Lubiee nan ma Omar yasa yayi dropping nata. Achan suka had’e da Adeel nata, wani
k’war jini taga ya sake mata cause she can’t remember when last ta sasa a ido tun
birthday’nsa se inde a video call. Hira da shafe-shafensu suka ta sha like never se
5:30pm da Omar yazo d’aukanta sukayi sallama nanma da Adeel yayi hugging nata ji
take kamar ta bisa su gudu karta koma gida remembering she has a better plan in
mind sukayi ba-bye ta fice.

Da daddare tana ta chatting abinta da Adeel da Lubiee. Lubiee tayi messaging


nata _Babe nifa har yau kink’i nuna min hoton Ya Al’ameen na k’osa naga angon
namu._
_Gaja ai Ya Al’ameen kome yake ba shine real ango naba ko kin manta Adeel ne? Ya
Al’ameen is the ladder that will take me to my dreams._
_Hmm nide ba ruwana kimin sending pic nasa kawai abinda na tambaya kenan._
_Yo ai banida pic nasa nikam Adeel ya hanani barin hotunan maza a waya._
_Babanki dake da Adeel d’in Babe please show me his pic or kishinsa kike ne?_
_Over my dead body wallahi banida pic nasa amman bari na duba dp’nsa ko yasa na
hankad’o miki._
_Yauwa do please._ Zeezee na dubawa aiko Al’ameen ya cire daman wani hotonsa ne
da uniform ya bala’in yin kyau.
_Ke Babe seki d’au na annabawa yacire pic nasan._
_Dang it! toh ask him mana ai he is your boyfriend._
_Fake boyfriend FYI plus a dalilin meh zan tambayesa pic nasa? Ba seya d’au sonsa
nake ba._
_Oh! Toh Allah shiryaki nide na gane rowansa kawai kike min._
_LOL Allah ya mayar zan miki sending._ chan dare kafin ta kwanta taga yayi
changing dp nasa ya miyar dana d’azun take tayi saving ta turawa Lubiee nanfa
Lubiee tayita hauka ita sam Al’ameen yafi Adeel kyau kuma ai in bawai an fad’a bane
baza’a d’au ma yayi 42 ba sede 38 haka. Zeezee mafa tasan da zaman haka amman dan
iskanci da neman take gaskia sam tace ita ba haka ba Al’ameen is too old.

_Several months later..._


Al’ameen har ya dawo daga Abuja angama magana ansa date na bikin aurensa da
Zeezee in 3 months time. Jin haka kuma Zeezee ta kariya ta soma kuka sosai ita bata
son auren. Karap Mama ta bud’e k’ofar d’akinta da wuri ta share hawayen nata. “Kuma
kukan me kike?”
“Niba kuka nake ba.”
“Banida ido ai nace kukan me kike?”
“Mama ni banason auren wallahi.”
“Baki so?! Dama bason Ya Al’ameen d’in kike ba?”
“Ina sonsa auren ne banaso.”
“Kinga banason shashanci kina jina ko? Auren ki nanda 3 months ba abinda muka
fara gobe zamu wuce Kano chan za’ayi maki siyayyan, kinji koh? Seki fara shiri.”
Shiru Zeezee bata amsa ba. “Bada ke bane?”
“Dani ne.” tayi murmuring. Washegari suka biya ta air to Kano achan suka gama wa
Zeezee siyayya, kud’i in abundant Baba ya bawa Mama ba abinda basu sai mata ba. A
guest house na Baba aka sauk’e kayakin kasancewar har yanzu Zeezee bata yanke
hukuncin wani gari take so ta zauna ba.

_Morning hours..._
Tana zaune a d’akinta damuwa sun mata yawa wayarta ya shiga ringing acewarta ma
Lubiee ce tana kai dubanta taga Al’ameen wani dogon tsuka taja haka tana gani har
ya yanke bata d’aga ba se a karo na biyu. “Hello My Princess” kamar wacce baza tayi
magana ba tace, “na’am ina kwana?” sede daga yadda tayi maganan yagano da akwai
matsala “any problem Zainab?”
“Babu” tayi stating sama-sama.
“Are you sure ko auren ne bakiya so a fasa?”
“Eh” ta fashe mai da kuka.
“A fasa?” yasa dariya.
“Am serious Allah dan Allah karka rabani da Mama da Baba kuma ka bar min dariya.”
“Toh nadena theres nothing to worry kinji? I’ve got you Zainab, I love you so
much.” Wani haushinsa ta sakeji sannan dan dole tace, “thank you.”
“So kinyi making up mind naki? Zaki zauna a Kaduna a family house kokuma anan
Bauchi alone ke kad’ai? Kinsan a Abj nake aiki Kaduna is more closer and zanfi
samun visiting naki frequently.”
“Chabd’i! A family house? Nice zan zauna da in-laws? Lallai kuwa! Ka sake tunani”
“Excuse me?” Yayi maganan suprised. Ita kanta Zezee batasan lokacinda tayi
maganan ba. “Uhm Ya Al’ameen I mean zama da in-laws d’innan gaskiya bana so
problems yake haddisawa.”
“Trust me, my family don’t have that problem.”
“I know kawai nice banaso gomma nan Bauchin ina kusa da Mama kai kuma koda jifa
jifan ne kana visiting d’ina its okay by me.”
“Are you sure?”
“I am ”
“Toh shikenan hakan za’ayi, I love you.”
“I know, thanks.” Tunda Al’ameen yake be ta6a jin Zeezee tace mai I love you ba
amman dake shiyasan yana sonta ne don Allah badan wani abu ba be ta6a damuwa ba.
“Toh semun sake waya, take care.”
“Bye” tayi hanging take ta kira Lubiee.

“Hello Matar Soja” cewar Lubiee.


“Babe ya zanyi dan Allah? Taya zan fara sanar da Adeel aure na is in three (3)
months time? I really dunno how please help me out.”
“Kefa Zeezee banza ce wallahi, forget Adeel wallahi Ya Al’ameen loves you.”
“That will be the last thing I’ll ever do kefa bakisan yadda nakeji da Adeel
bane.”
“Toh ya zakiyi yanzu? Kinason na fad’a mishi ne?”
“A’a please don’t zan fad’a mai da bakina.”
“Toh suit you well ni ya batun ashobe ne? Wanda muka fitar d’in sunyi?”
“Yeah leave that to me wallahi kap ashoben Ya Al’ameen ne ze biya tunda shi yace
yana sona.”
“Haba! Zeezee set ukun duka zakice shi? Pity him mana.”
“Shi yayi pitying d’ina ne daya kama yace yana sona seya auren? Ki ajiye kalman
pity agefe friends d’in duka ku nawa ne?”
“Mu 18 ne.”
“Tam karku damu kede kawai ki sanar musu a group namu na LYS STARS kan in three
weeks time suzo su karb’i ashobensu gidanmu.”
“Toh Matar Soja! Angama.”
“Mschwww! Banza kawai” tayi hanging. Al’ameen ta kira and har ya tsinke be d’aga
ba kasancewar bai kusa, itama missed call d’aya tamai dan iskanci.
****
Da daddare ta sake trying nasa be jima ba ya d’aga “hello My Princess you called
earlier bana kusa sorry.”
“Its okay dama batun ashoben friends d’ina ne a kace na tuna maka.”
“Okay, nawa kike buk’ata all in all?”
“Kaga friends d’ina are 18 in number each person kuma ten thousand five hundred
(N10,500) ne making one hundred and eighty-nine thousand (189,00) altogether.”
“Okay zan baki 200k incase kinsamu additional friends.”
“Tam sekuma na makeup artist, nida Lubiee kad’ai za’a mana.”
“Shikuma nawa?”
“Nawa 60k na Lubiee 25k through out the 5 events all together is 425k plus na
ashoben making 610k.”
“Wow! My Zainab is such a great mathemathecian zan miki transferring 650k hope
thats all koh?”
“Eh shikenan and karka min ta acct na Mama kayi ta nawa.”
“Toh My Princess anything for you shikenan?”
“Eh shikenan for now.”
“Okay feel free to call me up whenever your need arises.”
“I’ll thanks” tayi hanging. “Baho ai seka tsiyaye wallahi mschw ni yanzu ta ina
zan fara sanar da Adeel for God’s sake?” Tana cikin wannan tunani alert na 650k ya
shigo wayanta maqirin murmushi ta saki.

3 WEEKS LATER (2 months one week to Zeezee’s wedding) LYS GROUP CHAT.
Lubiee; _Announcment! Babes y’all invited zuwa gidansu Zeezee yau kuje ku amshi
ashobenku kala uku which is worth N10,500. Ba a buk’atan kud’inku saboda Soldier’n
mu which is our ango to be yariga ya saya muku._

Sumayya; _what?! You mean to say Zeezee zatayi aure? Tsaya wata Zeezee tukuna?_

Miss Aysha; _help me ask o bangane wata Zeezee ba nima._

Lubiee; _Zeezee nawa kuka sani a garin Bauchi? Zeezee Isma’il Yosouf FYI in
ashoben ne bakuso a baiwa wasu, mschww!_

Miss Xoxo; _weehoo!! Kuce angon namu DON ne ashoben N10,500 ya siyewa kowa?_

Lubiee; _abinku da Maj-Gen! So sekunzo wacce batazo a yau ba za’a baiwa nata ma
wata._

Sumayya; _LOL sekun ganmu toh su Zeezee amarya muna jiran pre wed._

Ilhamerh; _kefa gulmanki ya miki yawa Sumayya angon kike son gani kome?_

Mjay; _barta deh shegen gulma ne da ita._

Sumayya; _no bayan cika bakin da tayita yi kan seta gama degree tayi aure ne ai
nakeson ganin wazata auran wait guys ina Adeel nata fah?_

Rumaysa; _kema kinsan Zeezee bazata auri gaja anyhow ba ko bakiji Soldier bane?_

Lubiee; _ke wallahi Sumayya gulma ya miki yawa mschw! Ba wanda yasan destiny’n sa
kuma thank god ma had’ad’d’en miji zata aura wanda yafi Adeel_ pic na Al’ameen ta
musu sending ai sam Sumayya da k’awarta Ameena suka k’i amincewa da wannan
kyakkyawan soldier’n ne mijin Zeezee don black belle.

Miss Aysha; _can’t wait!!!_

*~ *~ *~
Da yamma friends na Zeezee suka hallaro amsan ashobe, bikin Zeezee de yazama talk
of the town sabida basu ta6a jin bikin da ango yayi ashoben 10,500 wa each friend
ba. Har rana me kaman na yau Adeel besan me ake ciki ba as Zeezee bata sanar dashi
ba bekuma ji rumor a gari ba.

*© MIEMIEBEE Team #YGC!*


👄👄👄👄
wwww.beeenovels.blogspot.com
[1/7, 3:04 PM] 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣2⃣

Jere aka shiga yiwa Zeezee achan gidanta dake New GRA layin Sunday Awoniyi
road, wannan gida shi ake kira da mansion I don’t have to go in details sanin kanku
ne gidan Maj-Gen ba wasa. Ana cikin haka Zeezee takai Lubiee gidanta suka duba se
yaba gidan Lubiee ke, gida sekace ba a Bauchi ba. A month to biki Mama ta d’aukowa
Zeezee me gyaran jiki daga Maiduguri wacce tayi wa su Mariam da Yasmeen. Sam Zeezee
tace ita bataso seda Mama tayi dagaske ta amince, magunan gyaran jiki da Mama ke
bata kuma har ayau ba wanda ta ta6a sha da an bata seta wulla cikin side drawer’n
gadonta.
Yau ma as usual da safe Mama ta shigo d’akin nata rik’e da roban drugs d’in
“ina kwana Mama?”
“Kin tashi lafiya?”
“Eh sannu.”
“Kinga yadda skin naki ya k’ara haske kuwa? Ai kin kamoni fari yanzu koma ince
kin fini, amman kice wai ke ba ruwanki da gyara? Bansani ba ko jiki kaman na
k’adangare kikeson kije dashi gidan Maj-Gen. d’in yadda zeji dad’in sako ki.”
“Ai daya kyauta.”
“Kika ce meneh?”
“Eh man ai gaskiya ne wallahi shiyasa banason wannan shirmen gyaran jikin ayita
miyarwa mutum fata ja sekace fuskan Ya Ibraheem.”
“Aww Baban nawa kike zaga?”
“Toh ai gaskiya ne, ayita murjewa mutum jiki sekace Aljannah za’a kai sa mschw!”
“Toh ya isa ke dama baki gaji mutunci ba, ga maganinki.” K’afa ta shiga shurewa
“wai Mama kullum magani magani sekace rashin lafiya nake ni wallahi na gaji
banaso.”
“Wawiya wannan ba shine ze gyara ki ta ciki ba, ko cemiki akayi gyaran waje kawai
ake?”

“Nide banaso.”
“Amshi nace banason zancen banza” haka Zeezee na gunguni ta amshi maganin ganin
Mama bata kallonta ta wurga goran k’ark’ashin gado. “Yauwa ni ranan ina na ajiye
makullin gidan naki ne?” Mama tayi maganan tana k’ok’arin jan side drawer’n kan
Zeezee wanda take tara duka magunan nata aciki. Ganin haka da wuri Zeezee tace,
“Mama baya cikin chan karki b-” bata idda maganan ba Mama taja kawai gani tayi
maguna suna mata sallama. Baki ta sake wide in shock totally out of words wato duk
aikin banza take kullum tayita kawo mata magani tayita kashe kud’inta duk a iska,
lallai Zeezee!
“Me wannan?!” Ta tambaya a fusace. Lamo Zeezee tayi zaune kan gadon tana kallon
k’asa. “Magana nake miki, meh wannan? Bazakiyi magana bane?”
“Mama kiyi hak’uri dan Allah.”
“Meh wannan nace?!”
“Magunan ne.”
“Magunan dana ke baki?” A hankali ta gyad’a kai mari lafiyayye Mama ta kai mata a
bare back nata seda shatin hannunta yafito nan Zeezee tasa ihu “dan k’aniyanki
inyita asaran kud’i na inasai miki abinda ze amfane ki ashe duk tarawa kike ba sha
kike ba? Iyye?!” Tana murza bayan nata ta kad’a kai “kiyi hak’uri kar Baba ya sani
dan Allah.”
“Inba rashin wayo irin naki ba dry d’inki haka kikeso ki jewa shi Maj-Gen d’in?
Ana baki abinda ze taimakeki kina shashanci? Ina wanda na baki yanzun?”
“Na shanye” tayi k’arya.
“K’arya zakimin? Ina yake nace?” Tsugnawa tayi ta zaro goran daga k’ark’ashin
gado “maza bud’e kisha ina ganinki.”
“Mama wallahi banaso da Allah kiyi hak’uri.”
“Bazaki bud’e bane ko sena kira Omar ya baki kashi?” Haka Zeezee na hawaye ta
kurb’e goran tas tun daga ranan Mama ke tsayawa akanta seta shanye maganin tas
sannan tabar kanta.

2 weeks to bikin aure Mama ta soma batun pre wedding pics saboda yadda sisters
na Al’ameen sunka k’osa kullum cikin kiran Mama suke awaya. “Zeezee! Zeezee!” Mama
ke kiranta.
“Na’am” ta amsa tare da zuwa ga koran “gani.”
“Ehem kinada labarin gobe zamu wuce Abj ko? Achan zakuyi pre wedding pics nakun.”
“Har Abuja?! Kuma ma wani pre wedding? Shi baze zoba sede ni na bisa? Ni wallahi
banason bidi’ancin nan ayi aure kawai ba shikenan ba.”
“Lallai kam! Keda shi waye babba? Ko bakisan he is busy bane yanzun ma squeezing
time nasa zeyi bama wannan ba se in in-laws nakin suka kiraki kice musu ke baza
kiyi ba nide na gayamiki anjima Omar ze amso miki d’inkunanki daga gun tailor seki
had’a akwatinki.” Tana kuka ta koma d’akinta, babban tsoronta shine kar Adeel yaga
pre wed’s d’in saboda tasan muddin akayi hoton dole ze gani, takira shi ta sanar
dashi yanzu kuma batada courage. Ta shiga contacts neman numban Lubiee Adeel ya
soma kiranta seda ta sa lock a d’akintan ta d’aga tare da clearing throat nata
“hello Very Own.”
“Sweetest Love ya kike?”
“Lafiya” ta amsa sama-sama.
“Why whats wrong? Muryanki sounds not okay.”
“Bakomai kawai na buga k’afa na ne jikin gado.”
“Awcchh! Sorry Hun.”
“Its okay so ya kake?”
“Am good Sweetest Love anya kuwa buga k’afanki kawai kikayi? Something sounds
really not okay.”
“Seriously...” Sekuma ta fashe da kuka. “Gosh! Did I say something wrong? Please
stop crying” kukan ta tayi da k’yar ya samu tayi shiru. “Yanzu zaki fad’a mun mesa
kike kuka?”
“Very Own babu.”
“So kike muyi fad’a abee? Tell me.”
“Very Own please no matter what happens know that I love you morethan words could
ever tell and that I can die for you.”
“I know that Babe and I love you as much but why the sudden words?”
“Babu I just want you to know that no matter what you are the only love of my
life.”
“I love you Babe, so much.”
“I love you too, what of now? In nazo gidanku neman auren ki still Baba will
suspect?”
“He’ll Adeel mubari nan da months ahead haka.”
“Babe what if before then wani ya rigani zuwa fah? I can’t lose you.” Wani kukan
ne yaso fin k’arfinta da k’yar ta danne sanin Al’ameen ya riga ya rigasa, batasan
da wani bakin zata soma fad’awa Adeel aurenta saura sati biyu ba.
“I’ll call you later, I love you.”
“I love you too” jira tayi yayi hanging sannan ta koma kan gado ta cigaba da
kuka. Da yamma kayakinta suka iso Mama da kanta ta had’a mata akwati a washegari
suka wuce Abj ita da Mama achan suka had’u da Al’ameen, he couldn’t take his eyes
off Zeezee dan yadda skin nata ke wani glowing. The following day best makeup
artist na Zeezee wato Oshewa Beauty ta cancare mata makeup sannan suka wuce
studio’n George Okoro sukayi pictures. Pictures are just lit and fire! Zeezee
bataso 6ata pre wed’s nata ba saboda mutane irinsu Sumayya masu bacci da ido d’aya.
Kafin ace me pictures se yawo yake a social media.
Kwana d’aya suka k’ara suka juyo ita da Mama.

3 days to biki Mama ta kawo wa Zeezee wani pepper soup na kazan daya sha had’in
maganin gyaran jiki banda rashin dad’i bakomi tattare da shi. Zeezee na kai bite
d’aya baki tace ita sam bazata ci ba, tsaye Mama tayi akanta da belt haka seda
Zeezee ta cinye kazan tas wane zatayi amai.

****
Adeel ne miqe kan gadon d’akinsa yana viewing pics a instagram, yashiga ta
explore kawai yaci karo da biggest and most shoking suprise of his life wato pre
wed pic na Zeezee da Al’ameen wanda take sanye da hulansa na soja akanta sun rik’e
da hannun juna suna dariya. Idanunsa ya shiga murzawa danko ya kasa believing what
he is actually seeing, gashi de a zahiri Zeezee yake gani a hoton amman ya kasa
believing itance. Tapping hoton yayi nan name nata da akayi tagging yafito assuring
him itance ba me kamanninta ba.
“No! No! It can’t be possible it just can’t, this is not Zainab me kama da ita
ne” yayi maganan yan kad’a kai still not believeing. Wani irin ciwo yaji a
zuciyarsa wanda be ta6a witnessing ba wurgi yayi da samsung J7 dake hannunsan seda
ta tarwatse. Wasu zafaffun hawaye ne suka soma sauk’owa daga jajayen idanunsa a
yayinda kansa ke masa wani irin sara. Da k’yar ya iya mik’ewa ya ciro iphone nasa
daga wardrobe ya kira Lubiee.

***
Tana shirin zuwa gidansu Zeezee ta tsaya tayi picking “hello Adeel?” Kawai jin
sautin kukansa tayi “omg! Adeel are you okay?” Shiru be amsa ba “kana ina ne?
Hello Adeel?”
“Lubiee tell me it aiint true kinji? Dan Allah tell me its not.”
“Whats not true? Ban fahimce kaba.”
“Z... Z... Zeezee.”
“Meya samu Zeezee kuma?!” Tayi maganan hankali tashe a cewarta ma kowani abunne
ya samu Zeezee.
“Aure Zeezee zatayi?” Dum! Zuciyarta ta buga ina kuma Adeel yasamu wannan labari
kode Zeezee ce ta fad’a mai? Kai No halan yaga pictures d’inne a instagram. “Answer
me please pre wed nata nagani dawani soldier, itace? Is she really the one? Is
Zeezee getting married to someone else? Ke kad’ai zaki iya amsa min wannan
tambaya.”
“Adeel calm down okay?”
“How can I calm down Lubiee? Zeezee zatayi aure and wani zata aura for all this
while she’ve been cheating on me shiyasa koda nace mata zan tura Uncle Abdul
gidansu take tamin corner-corner ashe this was it, she have someone already. I
should have guess.” ya k’are maganan sounding disappointed.

“Omg! Adeel stop saying all these kaima kasan kalan son da Zeezee ke maka, its
not what it seems.”
“Ni just answer me itace ko ba itace ba?”
“Itace amm-” katse wayan yayi a kanta koda ta shiga gwada line nasa kuwa bayi
shiga. Yini Adeel yayi ranan yana kuka indeed this is the biggest heartbreak daya
ta6a witnessing a rayuwansa.
Lubiee kuwa koda ta isa gidansu Zeezee takasa fad’a mata abinda ya faru sabida
batasan ta ina zata fara ba.

Da daddare Zeezee tayi trying both lines na Adeel sede switched off yake ta
cemata, sanin ba halinsa bane switching off phones nasa hankalinta ya matuk’ar
tashi. Lubiee takira right away “hello Babe meya samu line na Very Own bayi shiga?
Inason mishi magana, its high time I tell him the truth.”
“Ermm.. Ni... Nima ban sani ba fa tun d’azu nake trying.” Sede don yadda Zeezee
tasan Lubiee ta gano k’arya Lubiee ke. “Babe you are hiding something from me dan
Allah ki gayamun meya samu Very Own d’ina? Yayi accident ne? Is he badly injured?”
“Zeezee enough of the panicking please ba abinda yasamu Adeel nima nayi trying
line nasa it aiint going through.”
“Babe please don’t lie to me on this, I can sense it ba lafiya ba dan Allah meya
samu Very Own?”
“Zeezee wallahi babu abinda ya sami Adeel just that... Just that...” sekuma tayi
shiru.
“Just that what? Tell me please.”
“He has find out the truth already Zeezee.”
“Truth about my wedding? Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” sekuma ta fashe da
kuka “Babe how? I intended on telling him everything tonight dan Allah tell me its
not true, please...” ta sake rushewa da kuka.
“Please ya isa kuka is never a solution I know Adeel he’ll calm down soon enough,
if he does nida kaina zan mai explaining komi please kibar kukan haka.” Har anan
Zeezee kuka take, “Lubiee na fiki sanin Adeel wallahi baze ta6a sauk’owa ba, koda
zeyi ma ba nan kusa ba nikam na mutu na lalace, Al’ameen be kyautamin a rayuwa ba”
tana kaiwa nan ta katse wayar. Wurgi tayi da kanta bisa gado ta shiga rera kuka
tana sumbatu ahaka Mama tazo ta tarar da ita ba kalan tambayan duniyan da batayi wa
Zeezee ba amman Zeezee tak’i tankata. Daga k’arshe ma kawai tayi suggesting halan
kukan shagwa6an barin gida Zeezee ke.

Kwana ranan Zeezee tayi tana trying layin Adeel sede sam its not going.
Washegari Lubiee itama ta gwada line na Adeel bai shiga tana gama shiri tazota
gidansu Zeezee inda ta sameta se kuka take Mama na a tsaye a kanta ta zuba mata
ido. “Ina kwana Mama?” Lubiee ta gaisheta.
“Barka ma da kika zo Lubabatu, shin meke damun k’awar taki? Ba kalan tambayan
duniyan da ban mata ba tak’i fad’amin. Tun jiya take wannan kuka ga gida ya soma
cika da mutane banason a fara k’ananun magana cewa auren dole Babanta keson mata.”
“Shikenan Mama zan mata magana kije ba damuwa.”
“Yauwa please.” Mama na ficewa Lubiee taja crying Zeezee jikinta “Babe its okay
please kinga kukan nan baida amfani bashi ze dawo da Adeel ba, yau zanje gidansu in
samesa in person kinji?” Take Zeezee ta d’ago kai “please kije ni ko yanzu nema
kije ki samesa I need him badly.”
“I will amman sekin bar kukan nan.”
“Wallahi na bari” tasa hannu ta share hawayen nata. Sosai idanunta suka kumbura
sukayi water bags a k’asa.
“Toh bari naje na same san” anan Lubiee ta fice zuwa gidansu Adeel.

Mamin shi kad’ai ta tarar bayan ta gaiaheta ta tambayi ko Adeel na gida.


“Ai Auta na baya nan Lubabatu, be fad’a miki zeyi tafiya bane?”
“Tafiya Mami?!” Lubiee tayi exclaiming.
“Eh fah.”
“Amman lafiya dai ko?”
“Toh kinsan halin Auta baya son sanar dani problems nasa, nide all I know is tun
jiya ko lunch yak’i fitowa yaci yau da safe kuma na gansa fuskansa duk a kumbure
yana rik’e da akwati. Dana tambayesa ko lafiya kuma yacemin lafiya kawai ze wuce
Florida ne yaje ya huta achan yanzu haka yana Abuja d’azu ya kirani kan sunyi
landing.”
“What?! Florida ze wuce?”
“Eh wai.”
“Toh Allah sa lafiya ya kuma dawo dashi lafiya amman Mami ya gaya miki for how
long he’ll be staying there?”
“A’a gaskiya nima ban tambaya ba becika son tambaya haka ba.”
“Toh numbansa nakeso zan kirashi.” Bayan Mami ta bata layin tayi godiya sannan ta
fice a bakin gate ta kira layin Adeel thankfully ya d’aga “hello Adeel?”
“Lubiee?” Ya tambaya not sure.
“Eh ni, kai haka akeyi ne Adeel? Yanzu ka kyauta kenan tun jiya Zeezee ke kuka-”
_Disconnected_ taji tana dubawa taga hanging call d’in Adeel yayi kafin tace
zata sake kiransa har ya cire sim d’in ya karya. Tashin hankali! Kasa komawa
gidansu Zeezee tayi. Zeezee ko tun d’azu jiran Lubiee take jin shiru ta kirata da
kaman Lubiee bazata d’agaba sekuma ta canza mind nata “hello Babe I’ve been waiting
for you since, ina kika shiga?”

“Uhn Ummi ce ta kirani wallahi I had to go back home.”


“Oh ayyah kinsamu kinje gidansu Adeel d’in?”
“Uhm-”
“Please don’t lie to me, komin d’acinta ki gayamin wani yanayi kika tsinci Adeel
please.”
“Zeezee I’m terribly sorry, I went Adeel bai gida yana Abj as we speak now daga
can ze wuce Florida for a break regarding what happened.”
“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un! No! No! No please!!!” jefar da wayan nata
tayi ta ruga aguje zuwa bayi tasa lock. Bajewa tayi k’asan toilet d’in tana kuka
wane don shi aka turota. Hakan ta cigaba dayi seda hawayenta ya kusa k’arewa.
“Adeel why do you have to leave me please, why? You know right I can’t leave
without you please come back it doesn’t have to be this way.” Seda tayi calming
kanta ta fito ta d’au wayar several missed calls na Lubiee ta tarar nan ta kirata
back “thanks Gee!” Lubiee tayi exclaiming.
“Lubiee kimin sending digits na Adeel if kinada please.”
“Wallahi bani dashi sabo wanda Mamin shi taban ma yabar shiga maybe ya karya koya
kashe wayan. Yanzu ba lokacin damuwa da Adeel bane it might follow afterwards
kinsan fa jibi za’a fara wedding events naki inhar kikayi ruining su Sumayya sun
samu abin magana akai kenan. Please ba don ni ba don Allah ki manta Adeel for now
kinji? Kiyi hak’uri.”
“Thank you sekinzo gobe” nan tayi hanging. Haka koda Mama ta kawo mata maganinta
yau tasha ba tare da sunyi long drama ba takoma gado ta kwanta. Mama de harta gaji
da tambayan Zeezee whats her problem.
A washegari Yasmeen, Fateemah da mazajensu suka hallaro.

_PROGRAMS OF EVENT Starts..._


Da Tea party suka fara, event ya had’u iya had’uwa sede Zeezee sam ba walwala
tatattare da ita su Lubiee kad’ai sukayi enjoying party’n through out the event
tunanin Adeel Zeezee ke. The following day akayi English dinner Zeezee and Al’ameen
nailed it a wajen ba’a cewa komi se wanda yagani, naira yayi kuka. Bayan english
dinner akayi Kamu se sword crossing wanda yafi dukannin events d’in so far had’ewa.
The next day which is Friday aka d’aura auren MAJ-GEN. MUHAMMAD AL’AMEEN SHETTIMA
da ZAINAB ISMA’EEL YUSOUF akan sadaki naira dubu d’ari biyu.

Zeezee najin an d’aura aurenta da Al’ameen ta rikice musu a gida ranan. Kuka
tayita yi wane zata cire ranta. Ita abubuwan ma sun taru sunyi mata yawa. Na farko
ba wanda takeso zata aura ba, na biyu ga barin gidan da zatayi and above all rashin
Adeel nata. Su Mariam sun bata hak’uri har sun gaji, haka Lubiee, Fateemah da Mama
ma. Wani kukan ma seda dangin Ango sukazo d’aukan Amaryarsu. Zanin Mama ta kama
k’ememe tak’i sakewa se rusa kuka take tana sumbatu tana ita ta fasa auren. Ba
yadda basuyi ba a fito da Zeezee sun kasa daga k’arshe Baba aka kira tana ganinsa
ta ruga aguje ta nufi kansa tare da tattara jamfansa a hannu tana kukan cire rai
tana basa hak’uri dan Allah ya barta ta cigaba da zama a gida ta tuba bazata
sakeyin wani rashin hankali ba. Seda Zeezee tasa idon Baba yayi ja saboda yadda
take kuka sosai har se ji yake kaman yasa Al’ameen ya saketa a fasa auran amman
hakan bame yuwuwa bane.
“Yi hak’uri Zeezee, everything will turn out perfect kibi su Ayshah kinji? Muma
zamu taho daga baya, muna tare ai Hafsah zoki jata.”
“Baba dan Allah kayi hak’uri Mama please karku fitar dani daga gidan nan.” Haka
da k’yar aka fitar da ita aka sata mota zuwa gidanta, su Lubiee se hak’uri suke
bata. Not long enough aka hau shirin dinner, makeup na ranan shine beyi kyau ba
saboda yadda fuskan Zeezee ya kumbura bayan nan kuma tak’i ajiye fuskan nata se
kuka take. 8:30pm suka wuce Zaranda Hotel inda za’ayi program d’in. Ai ganin hotel
d’in kawai ta sake tunawa da Very Own nata. Suna zaune da Al’ameen a motar ta shiga
rusa mai kuka, beso mata magana ba saboda yasan theres no point doing so and koda
hak’uri ya bata ma sake worsening situation d’in zeyi dan haka kawai ya zuba mata
ido se aikin kukan take. Dai-dai driver yayi parking Al’ameen juya ya kalleta “My
Princess all shall be well kinji? Stop crying haka, our families awaits us.” Wani
wutan tsanansa ne ke ruruwa a zuciyarta ko kallonsa batayi ba, da k’yar su Lubiee
suka fito da ita daga motar. Tabari ya rik’e hannunta ma tak’i haka through out the
event tak’iyin murmushi bale dariya se tissue take sawa a idonta tana tare hawaye.

*™ MrAndMrsMuhammadAl’ameen.*💑

*© MIEMIEBEE Team #YGC!*


www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣3⃣
_Hummm! I can smell my birthday tomorrow☺😋_

_This page is in honour of *Zaynab Anka, Ummee, Feedy G Muh’d, Kabo Daughter,
Mom Nu’aym, Umm Aneesah, Maryam,* and *Maryam Wasagu* #OneLove❤_

Ana gama event su Zeezee suka dawo gida gabad’aya kowa ya watse a gidan daga
ita se Al’ameen se soliders kota ina suna gadi. Driver na parking ta bud’o k’ofa ta
fita gaban entrance door ta tsaya tana jiran Al’ameen ya bud’e mata k’ofa har anan
bata bar kuka ba wanda hakan ba mugun damun Al’ameen yake ba. Har tambayan kansa ya
somayi anya kuwa Zeezee na sonsa? Da guards nasa biye dashi ya k’arisa ya bud’e
mata k’ofan kai kawai tasa se a d’akinta ta tsaya ta baje kan gado tana me cigaba
da rusa kuka. Bayan Al’ameen ya bud’e kazan amarchi yasa mata a plate da farm fresh
a cup ya nufi d’akin nasu, sallama yayi ganin batada niyyan amsawa yasa kai ciki
kawai. A kan side drawer ya ajiye “Princess?” Ya kirata a hankali cikin
sark’ak’k’iyar muryansa. “Princess kukan ya isa kinji? Yi hak’uri” hannunsa ya
d’aga a hankali ya aza kan bayanta, jikinta ta ja da wuri tare da d’ago kanta tana
mai wani mugun kallo. “Don’t touch me Al’ameen don’t! Bak’in cikin daka jefani
kad’ai ya isheni ba seka k’ara min da wani ba. Ka rabani da iyayena and above all
ka rabani da saurayi na Adeel kasa yayi nesa dani kasani bazan ta6a yafe maka ba
Al’ameen. Ka cuceni I wish I’ve never met you.” ta k’are maganan hawaye na bin
k’uncinta.

“Zainab what are you talking about? Weren’t you the one that agreed to thsi
wedding in the first place? Dama ba sona kike ba kika bari akayi auren?” Ya
tambayeta suprisingly.
“Nayi ne saboda in farintawa Baba rai amman badon wai ina sonka ba, ban ta6a
sonka ba kuma bazan ta6a sonka ba. I hate everything about you, your skin and that
sweet irritating voice of yours Adeel nakeso I want you to stick that to your head
and please excuse me just looking at you disgusts me.” Ta k’are maganan tare da
watsa mai harara.
Mamaki ne sosai ya cika Al’ameen da har ya zama lost of words amman be damu ba
saboda gani yake har yanzu yarinya ce batasan ciwon kanta ba eventually al’amura
zasu daidaita tsakanin su, he believe. Murmushi me sake k’ayatasa ya saki “naji toh
My Zainab amman tashi kiyi having dinner seki kwanta kinji?”
“I am not yours and ba ruwanka da abinda zanyi tunda ba zaman ka nake ba, kuma
ka tattara kajinka kayi waje dasu banaso bazan ciba.” Tana kaiwa nan ta mik’e tare
da jan akwatinta ta ciro night gown nata ta nufi bathroom. Kai kawai Al’ameen ya
kad’a ya wuce d’akinsa shima ya watsa ruwa, koda yafito be koma d’akin nasu ba
atunaninsa bari ya bata space. A parlour ya zauna yaci ragowar kajin. To twelve
(12) ya lek’a d’akin nata yana sanye da ¾ wandon soldiers zalla, hakan ya sake
fiddo da how muscular and built up his body is making him worth more looking.
Kwance tana bacci ya tarar da ita tana sanye da wani pink sleeping dress me hannun
spaghetti da ¾ wando. Kajin data ce bazata cin bama ta cinye tas harda fasa k’ashi.
Murmushi me sake k’ayatasa ya saki sannan ya k’arisa d’akin tare da gyara mata
kwanciya yaja comforter ya rufeta sannan ya kashe musu wutan d’akin ya hauro suka
kwanta. Sam beyi niyyan mata wani abu ba a daren ranan saboda yasan koda had’a sama
da k’asa zeyi ba basa had’in kai Zeezee zatayi ba she needs some space.

12:50am Zeezee ta farka gabad’aya takasa gane meke damunta, tunda tasan kanta
bata ta6a jin abinda takeji ba yau, juye-juye tahau yi kan gadon duk anan Al’ameen
bacci yake peacefully besan meke faruwa ba. “Wayyo Allah na! Mama me kika samin a
maganin d’azu?” Sauk’a tayi daga kan gadon tana me cigaba da juye-juyen a k’asa
wani irin sha’awa kawai take jiyowa ita kad’anta ta rasa dalili. K’ara ta saki
sosai seda Al’ameen ya tashi ganinta kawai yayi se juye-juye take. A hanzarce ya
nufi kanta tare da sa hannunsa akan bare back nata kasancewar sleeping dress natan
show me your back ne, “My Princess are you okay? Meke damunki?” Da wuri taja
jikinta don d’an ta6a tan da yayi ba k’aramin affecting nata yayi ba kawai jin wasu
electric sparks suna bin jikinta ta tayi a yayinda degree na sha’awan nata ya sake
k’aruwa.
“Wayyo Allah zan mutu Mama kin kasheni dan Allah karka sake ta6ani I can’t take
it.”
“Mama kuma? Me ta miki?”
“Dan Allah kabarni in kanayi wa Allah karka sake ta6ani muryanka ma dad’a min
abinda nakeji yake in kanayi wa Allah ka tashi ka fita kokuma kasa kaya.” So take
ta miqe amman takasa se juyi take wajen, tuni Al’ameen yagano meke faruwa. “Tashi
toh muje mu kwanta.”
“Wai ana dole ne? Wayyo Allah na! Dan Allah ka tashi kabarmin kaina, Mama kin
kasheni yau! Nashiga uku!!” Murmushi kawai Al’ameen ke ba yadda beyi da ita ba ta
tashi suje su kwanta tak’i haka ya koma ya kwanta yana kallonta. Juyi Zeezee ta
cigaba dayi agun ganin abin bana sauk’i bane taja pillow ta danne kanta har anan
bata barjin abinda takeji ba. Ga sauk’i nan kawai taje ta samu Al’ameen amman
batajin zata iya basa kanta tayima Adeel alk’awarin budurcinta. Haka tayita wahalar
da kanta a daren ranan da k’yar d’in k’yar takoma normal ta haura gado ta kwanta.

Da Asubah ya tashi yayi alwala sannan ya zauna gefen sleeping Zeezee yana
k’arewa kyakkyawan fuskanta kallo then back to d’an mitsitsin bakinta me uban
tsiwa. Kallonta kad’ai na sanya masa farin ciki baze iya kwatanta yadda yakeson
Zeezee ba. “Zainab” yayi whispering name nata. “Zainab tashi muyi Sallah kinji?
Zainab!” yayi tapping nata. A hankali ta bud’e idanunta tare da kallonsa sekuma ta
juya mai baya. “Tashi muyi Sallah ko inyi nawa ni kad’ai?”
“Ban sani ba” ta amsa a takaice ganin batada niyyan tashi ya miqe ya hau yin
Sallansa. Seda ya kusa idarwa ta tashi itama tayi alwala. Koda ta idar bata
gaishesa ba ta koma gadon ta cigaba da bacci. Al’ameen kuwa na gama Azkhar nasa ya
fita waje ya samu men nasa ya hau training nasu har safiya be koma bacci ba.

Amarya kuwa se 10am ta tashi, bayi ta fad’a tayi wanka tana zaune gaban mirror da
towel zallah a jikinta tana shafa mai Al’ameen ya shigo ganin batada kaya yad’an
tsaya gun tare da clearing throat nasa ko zata gyara. Aiko maras kunyan yi tayi
kaman bata jisa ba ta cigaba da wangale santala-santalan cinyoyinta tana shafa mai.
Cikin d’akin ya k’arisa tare da zama bakin gado yana kallonta a yayinda wutan so da
sha’awanta ke running a veins and atteries nasa. Tana gama shafa man ta d’au inner
wears nata tasa sannan kayanta ko kunyansa bataji. “good morning My Princess tunda
bazaki gaisheni ba” yayi speaking up finally. Ko kallon direction nasa batayi ba
tafice izuwa kitchen tana tunanin dame zatayi breakfast. Tana cikin wannan tunani
idanunta sukayi tozali da take away akan counter. Ba tare da 6ata lokaci ba taja ta
bud’e chips da omalet taga ciki. Ai kujera kawai taja tahau ci seda tayi nak sannan
ta koma d’aki alokacin Al’ameen na gun wanka. Wayarta ta d’au taga missed call na
Lubiee take ta kirata tare da barin d’akin. “Hello Babe.”
“Matar Soja good morning.”
“Banaso ni na gaya miki banaso.”
“Toh yi hak’uri ya jiki-jiki?”
“Jiki-jikin k’aniya ce miki akayi banida lafiya?”
“Kamar ya?”
“Wai da kin d’au zan bawa Al’ameen kaina ne?”
“Aww yanzu ko Ya d’inma babu.”
“Bansani ba ai dana basa budurcina na gommaci na baiwa mahaukaci akan hanya.”
“Haka kika ce?”
“Eh mana.”
“Amman tsaya jiya kinsha maganin da Mama tabani na baki?”
“‘Yar iska daman kinsan abinda maganin zemin kenan kika k’i gayamun? Wallahi jiya
da k’yar na samu nayi bacci.” Dariya Lubiee tasa “kinshan ne kuma shine kikeson
nayi believing kan ba abinda ya shiga tsakaninki da Al’ameen?”
“Wallahi babu pillow nad’au na tare kaina.” Nanma wani dariyan Lubiee tasa
“wallahi ‘yar iska ce ke.”
“Niba abinda ke damuna ba kenan ya zancen Very Own fah? Line nasan ya soma
shiga?”
“A’a wallahi Babe.”
“Oh no! Na shiga uku.”
“Babe gomma tun wuri kin miyar da hankalinki kan aurenki kina jina ko?” Nasiha
Lubiee ta shiga yima Zeezee wanda tana cikin yi Zeezee ta katse wayar abinta.
D’akinsu ta koma ta tarar dashi yana shafa mai, la6ewa tayi bakin k’ofa tana kallon
yadda muscles nasa suke moving in sync in yana shafa man haka kawai take depriving
pleasure from staring at his naked body. Ta mirror Al’ameen ya ganta, murmushi
kawai ya saki ya cigaba da abinda yake chan yayi clearing throat nasa “My Princess
ki shigo mana.” Kunya taji sosai sannan ta fito daga la6en “nifa ba kallonka nake
ba k’ofan ne ya kama min kayana naga kana wani murmushi.”
“Toh ai bance kallo na daman kike ba, inma kallon nawa kike ai ba damuwa tunda am
all yours.”
“Kai kaji wajen kuma wai kai haka muryanka yake ne kokuwa iyayi ke saka magana
haka?” Dariya sosai ya tsaya yi in which Zeezee find him cute “meh muryan nawa ya
miki kuma?”
“Bayamin dad’i.”
“Nikuma naki na min dad’i sosai My Princess. ”

“Sau nawa zan gaya maka kadena cemin My Princess? I am not yours I belong to
Adeel kuma ka sa kaya banason ganin na miji other than my Adeel ba kaya, sannan
kuma kasa wad’ancan useless guards nakan da suke waje su kaini gida inason inje
inga Mama.”
“Toh dama Amarya tana fita unguwa ne?”
“Wai kai baya damunka ne idan na kira sunan Adeel da baza kayi zuciya ba kace zaka
sakeni?”
“Mesa ze damen Zainab? Duk wanin da kikeso nima dole in sosa ai.”
“Seka tayi ai wallahi da kanka zaka gaji ka sakeni, kuma ba amarya ceni ba
cause as far as am concerned banida aure.” Ignoring what she said yace, “kibari ko
zuwa next week ne seki fara fita kinji? Yi hak’uri.”
“Har next week?” Tahau tsiwa, “mezan tsaya yi a wannan gidan naka har zuwa next
week? In ganinka da wad’ancan useless guards d’inne na gaji dayi, wallahi ka kaini
gida” tasa mai kuka. Kai kawai ya kad’a “naji toh bar kukan shirya driver yayi
dropping naki nima zan d’an fita dama.” Tana share hawayenta tace, “da yafi ma
kam.” Wardrobe nata ta nufa ta ciro mayafinta tare da nannad’esa a one side of her
shoulder yadda ‘yan mata keyi bayan ita gata matar aure. Al’ameen na gama shiri ya
kalleta “mu tafi ko?”
Miqewa tayi tare da jan wayanta “wait haka zaki fita Zainab?” yayi maganan a
hankali.
“Ni wallahi muryankan nan...” ta zumburo baki “kuma da ya kakeson in fitan?”
“Ki rufe jikinki da gyalen mana Zeezee na, bakiga duk gidan maza bane?” Kishin
Soja ya k’osa!
“Toh ni nace ka d’ibo gang of soldiers ka tarasu a gidanka ne? In kaga bakason
kaga matar ka tana fita haka is simple seka sakeni daman niba san auren nake ba.”
“Yi hak’uri ki gyara kinji? Yi hak’uri bakisan beautiful things are left covered
ba? You are too beautiful to expose your body like this” ya k’are maganan some
inches away from her. Shiru tayi tana kallonsa, hannunsa ya miqa a nitse ya d’ago
gyalen daga kan kafad’arta tare da bud’ewa ya yafa mata shi me kyau sekace mace.
Juyata yayi yadda take kallon kanta a mirror “bakiga kinfi kyau haka ba?”
“Ni ka sakeni toh” taja jikinta. Murmushi ya saki sannan yace mata “lets go”
ganin ya shiga tafiya ta sake bud’e gyalen sannan tabi bayansa. Soldiers d’in suna
ganinsu suka hau saluting nasu wani dirty look Zeezee tashiga binsu dashi ita
haushi ma suke bata yadda sukeyi ma Al’ameen sekace wani god, mschw! D’aya daga
cikin prados na gidan d’ayan soldiers d’in ya bud’e mata tana shiga Al’ameen ma
yashiga aka rufe sannan suka fice.

Not long enough suka isa gidansu Zeezee. Nan soldiers na d’ayan motan suka fito
tare da jeruwa ta side na Zeezee d’aya daga ciki ya bud’e mata. Tazo fita Al’ameen
ya rik’o hannunta “ki gaishe da mutanan gida kinji? Da La’asr zanzo in d’aukeki.”
Kaman bazata amsa ba ta gyad’a kai tare da ficewa. Mama na zaune tsakar gida ita da
Omar Zeezee ta shigo.
“Amaryar! Lafiya dai ko?” Mama tayi exclaiming. K’arisowa tayi tare da gaishesu
“baki amsani ba lafiya?”
“Lafiya mana Ya Al’ameen ze fita ne shine nace yayi dropping d’ina nan gida tunda
ba abinda zanyi and yace yana gaisheki ma.”
“Kaman ya ba abinda zakiyi Zeezee girkin rana fah?”
“Nace zanyi yace no need ya d’aukemin girki wai.”
“Abun nema ya samu ba, dama ba son girkin ake ba.”
“Uhm ina Baba?”
“Ya fita kasuwa” cewar Omar.
“Ohh ni zan wuce d’akina.” Kallonta kawai Mama ke har seda ta fice “uhm su Zeezee
amarya.” Omar na murmushi yace, “kede bari kawai Mama Allah sa de auren yasa tayi
hankali.”
“Ameen Omar ya ko ka fasa fitan ne?”
“Eh zan koma d’akina kawai.”

****
Yini Zeezee tayi tana trying line na Adeel da Lubiee ta turo mata sede sam bayi
shiga. Gabad’aya ta rasa ina zata sa kanta se bayan La’asr Al’ameen yazo d’aukanta
har anan ma Baba be dawo ba, d’aya daga cikin guards nasa ya tura yayi ma Zeezee
magana kaman karta bisu takeji amman dolenta taje kada Mama tayi suspecting wani
abu. Sunyi sallama da Mama ta fice koda ta shiga motan bata ce da Al’ameen ko k’ala
ba shine ma yace mata sannu nanma banza dashi tayi. Dagangan dan neman magana ta
bud’e wayarta ta ajiye a tsakiyansu yadda Al’ameen na lek’awa yaga pic na saurayi
kan wallpaper’n nata wanda he is sure shine Adeel d’in. Kallonsa Zeezee ke a
yayinda yake kallon pic na Adeel a zatonta ma zeyi magana segani kawai tayi ya
kawar da kansa daga direction d’in, hakan ba k’aramin haushi ke bata ba, shikenan
shi ba aikinsa se ignoring nata? Mschww tafison suyi ta yinta har seya saketa
tukun, bata da burin dayafi wannan.

★*★*★*★
Ahaka fa har Al’ameen da Zeezee suka samu sati biyu da aure. Ba abinda ya ta6a
shiga tsakaninsu saboda ko gwada ta6ata bayi yi idan sun kwanta. Cikin sati biyun
nan Zeezee bata ta6a d’aga tsintsiya ba da sunan shara banda rashin kunya da
yarinta ba abinda take na Al’ameen, shikuwa duk abinda take mai overlooking kawai
yake saboda uzurin yarinta dayake mata for sure yasan da tasan ciwon kanta bazata
na hakan ba. Har a yau Zeezee bata ta6a hura wuta ba, breakfast, lunch and dinner
kullum siyo musu yake randa yace sufita suci ma gar da gar setace mai ita batason
aganta da tsoho. Rashin kunya kwando-kwando Al’ameen ke sha.

Yau Sunday Al’ameen ze koma aiki Abj leave nasa ya k’are. Zeezee dad’i kasheta
finally zata samu tafita yawo abinta. Koda Al’ameen keta had’a akwatinsa batayi
yunk’urin tayasa ba as she is busy playing game a wayanta har a yau kuwa kullum
setayi trying numban Adeel sede ko so d’aya be ta6a shiga ba. 1:30pm Al’ameen
yagama shiri da trolley’nsa rik’e a hannunsa ya kalli Zeezee da tayi banza dashi
“My Princess ni zan wuce toh ga pocket money naki nan incase need yayi arising bana
nan tho duk wani abinda zaki buk’ata ma na riga na tanadar miki, anytime you’re
hungry na bar miki two of my men they’ll be at your service.” Wayar nata ta ajiye
ta nufi gabansa tare da d’ago bundle na d’ari biyar daya ajiye matan. “Yanzu zakayi
tafiya shine d’an wannan zaka ajiye min? Nasan shekaru nawa zakayi a Abujan?
Wallahi bazan yarda ba ka k’aramin kokuwa k’afanka k’afana, taya agida Baba be
barni da yunwa ba kai kace zakayi hakan?”
“Yanzu wannan ya kasa Zainab?” Ya tambayeta suprisingly yana murmushi.
“Seka tambaya ne? Ya kasa mana me ‘yar dubu hamsin da ina iya kashewa a minti
biyar zata min?”
“Nawa kikeso toh?”
“Double mana” ta amsa a takaice. Be sake cewa komi ba ya k’ara mata wani bundle
d’in “shikenan?”
“Eh kuma se yaushe zaka dawo dan ba zaka ajiyeni a wannan k’aton gidan naka ni
kad’ai ba wallahi kai kaje chan kana mu’amala da mutane kabarni da wasu sojojinka
nan.”
“Shiyasa nace miki in kaiki chan family house a KD kika k’i.”
“Toh a dalilin me zan zauna da in-laws haka kawai abi a sawa mutum ido.”
“Uhm toh ni natafi ko?” Yi tayi kaman bata jisa ba “ba rakiya Zeezee?”
“Lallai baza kayi tafiyan ba kenan inhar ni kake jira nama rakiya” ta kai da
juyawa ya rik’o hannunta tare da pecking forehead nata “I love you My Peincess”
freezing Zeezee tati a wajen sabida wani sparks da takeji suna tashi a jikinta,
peck na Adeel be ta6a sata feeling haka ba. Kasa cewa komi tayi daya gano hakan se
kawai ya mata murmushi ya fice.

Tafi minti biyu tsaye a wajen immobile sannan tasamu ta dawo hayyacinta, hannu
tasa wajen tana murzawa in an tambayeta peck nasan take gogewa. Koda Al’ameen yayi
landing Zeezee bata damu ta kirasa tamai ya gajiya ba. Haka shi yazo ya kirata daga
baya nanma seda ta gama jan aji sannan ta d’aga “hello My Princess?”
“Nifa bacci nakeji.”
“Har kin kwanta ne? Its just 9:20pm fa My Princess.”
“Toh mezan tsaya yi awannan gida naka?”
“Uhm toh sleep tight Beautiful, I love you.”
“Naji” nan tayi hanging. Addu’an Al’ameen a kullum bayyafin Allah ya kawo rananda
al’amura zasu daidaita takaninsa da Zeezee. Lubiee Zeezee ta kira kan tazo mata
yini gobe Al’ameen bai gida.
Washegari tun 8am kasancewar Lubiee tanada lecture free day ta iso gidan Zeezee.
Ko breakfast batayi ba. Aikan d’ayan soldiers d’in Zeezee tayi ya siyo musu
breakfast suna cikin karyawa Lubiee ta ta6e baki “amman Zeezee kin ta6a share gidan
nan naki kuwa?”
“Zamansa nake da zan share mai gida? Ya saken ya auro matar da zata mai kokuwa
ya kawo me aiki.”
“Oh! Zeezee fa kina jin dad’i wallahi har yau baki soma girki bakuma ko?”
“Yo da wace boyi-boyinsa da zemai girki? Karki 6ata min rai please.”
“Se ke matar Soja se yaushe ze dawo?”
“Ohonsa ni yaga dama ma kada ya sake dawowa ba nemansa nake ba.”
“Hmm ma farin sojan kike ma wannan iskanci? Ma nawa ya ajiye miki tukunnah?”
“100k ofcourse yaban 50k nak’i amsa dan dolensa ya k’are kuma inhar yakai two
weeks be dawo ba seya k’aramin wani.”
“Haba! haba! Zeezee kinajin tsoron Allah mana.”
“Kanki akeji ni bud’en wayanki.” Ba musu Lubiee ta bud’e mata pictures Zeezee ta
shiga gani suna karyawa, mistakenly hannunta yashiga call logs nan taga sunan Adeel
gun as last person da Lubiee tayi waya dashi ayau. Kai ta d’ago tana kallon Lubiee
da mamaki. “Ya da wannan kallo haka?”
“Kinzo kin samu numban Adeel d’in kuwa? Kinsan wanda ke waje na bayi shiga.”
“Ermm... Uhm...” Lubiee ta shiga kame-kame “nima har yau bamu sake waya ba.”
“Hakane? Babe k’arya kika soma min yanzu? Number’n waye wannan? Wato d’azu ma
kunyi waya dashi kinsan how crazy I went looking for his number kin samu bazaki
gayamun ba, kin kyauta.”
“Zeezee yanzu da da fa ba d’aya bane matar aure ce ke yanzu be dace ace da
mijinki ba kina waya dawani. Its high time ki mance da Adeel saboda Adeel ya miki
nisa.”
“I will never forget about Adeel I believe zamu kasance tare someday and kaman ya
yamin nisa? Ba a Abj yake ba?”
“A da kenan, 4 days back ya wuce Florida achan yake yanzu kinga ko ya miki nisa
just forget about him.”

*© MIEMIEBEE Team #YGC!*


www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣4⃣
_I *Miemiebee* want to use this medium to say a very huge *THANK YOU* to each
and every single special soul that made my birthday worth it, indeed this is a
birthday I will forget never. Thank you all so much for making my birthday a
memorable one, I love y'all oceans and galaxies from the bottom of my heart.
#OneLove❤ ™YGC!🎀_

Kai Zeezee ta shiga kad’awa “no Babe thats not true, it can’t be true, it just
can’t.”
“It is Zeezee kiduba numban nasa kiga international number ne shiyasa nake son ki
manta da zancen Adeel kibawa Ya Al’ameen chance.” Zeezee na dubawa ta tabbatar da
hakan kuka ta shiga rusawa sosai bata d’au Adeel yad’au abin da zafi haka ba. “Wai
ko kukan me kike?” Copying numban Adeel Zeezee ta shigayi ba yadda Lubiee batayi da
ita ta bari ba tak’i. Se chan Maghrib Lubiee ta tafi gida bayan Zeezee ta idar da
sallan Isha tayi dialing line na Adeel har ya yanke be d’aga ba kasancewar bai kusa
da wayan, 2 missed calls ta masa sannan ta hak’ura.
Around 9pm yayi calling nata back and ba tare da 6ata lokaci ba ta d’aga
“hello?” Cewar Adeel. Muryansa kad’ai taji ta shiga zubda hawaye “hello??” Yayi
maganan a bit tensed this time around.
“Very Own...” Se kuma ta rushe da kuka.
“Zeezee?!” Yayi exclaiming sunanta cike da mamaki dakuma k’in yarda.
“Very Own its me your Zainab-” kawai ji tayi yayi hanging daman she knew this was
coming. Tana hawaye ta shiga nemansa ta masa missed calls ba iyaka amman yak’i
picking. Messages tayita mai sending tana had’a sa da Allah kan yayi picking. Seda
tasha wuya tasamu ya d’aga ba tare da yace komi ba “thank you for picking up.”
“Why did you call? Bayan na fara mancewa dake why do you have to ruin my life
again? A ina ma kika samu number na?” Daga yadda yake maganan za’a san cewa a 6ace
ransa ke.

“Haba Very Own I thought you’ll be the last person to believe that I’ll ever
cheat on you, kai kanka kasan yadda nake sonka kuma har rana me kamar ta yau sonka
a zuciya na be ragu ba se ma de k’aruwan da yayi.”
“Really? In ma dragging d’ina into trouble kikeson yi kisani I’ll not fall into
your trap ko a jinki bansan solider kike aura bane?”
“Adeel please trust me this once wallahi tallahi ban ta6a son soldier’n da aka
aura min ba, kafa san komi amman kake bani wahala haka. Wannan hukuncin da ka yanke
min yayi tsauri dayawa Allah kad’ai yasan the kind of hell that I went through for
the past few weeks da banji muryanka ba.”
“Aww! Ma aura miki shi akayi? LOL am not dumb Zeezee, you can fool your parents
amman you can’t fool me da idanu na naga pre wed naku and the way you were smiling
at him said it all, you love him.”
“Adeel me kakeson nayi maka ka yarda cewa auren dole akayimin da Al’ameen? Friend
na Baba ne shi, admission yafito bada jimawa ba yazo gidanmu ya ganni yace he wants
to marry me and Baba gladly gave me to him.”
“Why didn’t you tell me then?”
“I didn’t want you worried Very Own but wallahi believe me I've always had the
intention of telling you.”
“And meya hanaki?”
“A ranan da kayi discovering truth d’in daman naso sanar da kai se kuma kayi
finding out already please believe me Adeel wallahi ba k’arya nake maka ba, ban
ta6a son wani na miji kaman ka ba sonka a jini na yake, I love you morethan you can
ever imagine and am ready to sacrifice anything for your love.”
“What now? An riga an miki aure and nasan kin riga kin bashi kanki theres no US
again.”
“And thats where you are wrong, I’ve once promised you that my pride (budurcina)
belongs to only you and har yau promise d’innan na nan, ban bawa Al’ameen kaina ba,
bazan ta6a bawa wani na miji kaina ba se kai Adeel please believe me.” Dad’i sosai
Adeel yaji amman ya dake;
”If you want me toh mesa baki fad’awa Baba ke kinada wanda kikeso ba in the
first place kikayi agreeing to marriage d’in?”
“Adeel I tried, I really did amman Baba wouldn’t listen he even threatened me ze
aura min me shago” ta k’are maganan cikin sautin kuka.
“Is okay I believe you stop crying kinji?”Wani sanyi maras misaltuwa Zeezee taji
a ranta “you really do Very Own?” Tayi maganan tana share hawayenta “yes Sweetest
Love, I do.” Tana murmushi wane yana gabanta tace, “thank you, thank you so much I
can’t tell you just how much you mean to me.”
“So what do you plan on doing now? I don’t think we can be together anymore.”
“Sure we can Very Own just trust me.”
“How?” Ya tambayeta a takaice.
“Adeel I have a plan in mind, I won’t rest har se in Al’ameen ya gaji dani ya
sakeni.”
“Are you sure Babe?”
“I am cause all I want is to be with you.”
“And I promise to take care of you till my last breathe Sweetheart, I love you so
much.”
“I love you even more so are we good now? You are no more mad at me?”
“Had it been am mad at you will I tell you I Love you?”
“No kayi gaskiya” ta amsa tana murmushi, “amman yaushe zaka dawo 9ja you’re so
far away from me.”
“It won’t make any difference Babe, is better I stay here in har mukayi
accomplishing mission namu sena dawo right away muyi aure.”
“I can’t wait to be with you in your arms.”
“Me either” hira sosai sukata sha kan ba gobe shide Al’ameen ya rasa da wa take
waya sau biyu yana trying nata at different intervals amman se ce masa ake line is
busy with another call.

Cikin kwanciyan hankali Zeezee tayi bacci ranan. Wayarta dake k’ark’ashin
pillonta ne ya farkar da ita daga bacci sanadin ringing da yake. Da k’yar ta samu
ta ciro ganin wake kira ta ja doguwar tsuka sannan tayi picking “My Princess good
morning, kinyi Sallah?” Kaman baza ta amsa ba tace, “a’a.”
“Ahh to ki tashi kiyi kinji?”
“Waikam ina ruwanka da yin Sallah na ko rashin yinsa? In kuma bana Sallan fa?”
“Uhm-uhm to am sorry take care, I lobe you” Nan ya katse wayar. Doguwar tsuka
taja sannan ta koma bacci se 6am ta tashi ta idar sannan ta koma baccin.

*~ *~ *~
Tun rana me kaman na ranan Zeezee ta soma enjoying life nata. A rana seta fita
yawo sau biyu zuwa uku, ga kuma koda yaushe tana kan video or voice call da Adeel,
kafin ya kirata sau d’aya tayi sau biyu ko uku ita amman ko mistakenly ne bata ta6a
kiran Al’ameen ba. Ahaka har yayi sati biyu da tafiya Zeezee bata ta6a d’aga
tsintsinya da sunan shara ba kwatsam rana d’aya Mama tace mata gata a hanya tana
zuwa ita da Mariam da kids nata nan Zeezee tayi wur-wur ta samu ta share parlour da
d’akinta se kitchen da kuma dining space. Yini Mama sukayi mata ranan sosai Zeezee
taji dad’in zuwansu. Bayan tafiyan Mama Zeezee ta d’au waya for the first time
after their marriage ta kira Al’ameen. Mamaki sosai yasha ganin _My Princess_ na
flashing akan screen d’in.

“Hello My Princess.”
“Na’am ina wuni?”
“Lafiya ya kike?”
“Am good ya aiki?”
“Alhamdulillah ya Bauchi?”
“Cool nace se yaushe zaka dawo?”
“Wow are you missing me?” Yayi maganan yana dariya. Wani haushinsa takeji amman
ta danne zuciyarta “yeah sort of.”
“Shine baki ta6a kirana ba?”
“Uhm amman ai na kira yau ko?”
“And thats why I still can’t believe it!”
“Toh you better do, dama nace akwai auren friend d’ina ne da za’ayi jibi inason
zuwa.”
“Is that why you called?”
“Yes”
“Toh ba matsala My Princess na baki izini.” Ita dariya ma ya bata wai ya d’au ta
kirasa ne don ta tambayesa izini? Lallai kuwa yayi kad’an, ita kanta batasan sau
nawa take fita unguwa ba bayan tafiyansa ba kuma tare da izinin sa ba “Toh nagode”
tayi speaking finally “se kuma kud’in gudumawan da nakeson kai mata da kuma na
ashobe kasan nice best friend nata.”
“Wow! Ashe farin jinin Zainab d’inan ba gun maza kad’ai neba harda mata, kece
best friend ya kamata gudumawan ki yafi na kowa ko My Princess?”
“Yes Ya Al’ameen.”
“Nawa kikeson ki kai mata toh?”
“Zan d’an mata siyayya ne haka nasu dinner set da bedsheets haka.”
“Okay... Kaman nawa kike buk’ata?”
“Zan samu 50k?”
“Why not? Zan tura miki 100k seki k’ara akan pocket money naki.”
“Ba yanzu zaka dawo ba kenan?”
“Eh toh zan d’an k’ara koda two weeks ko one haka se hak’uri My Princess auren
soja seda hak’uri, kinji?”
“Bakomai Ya Al’ameen” a ranta kuwa cewa take ai hakan yafi dad’i. “Toh senaji
alert.”
“Yauwa My Princess take care I love you.”
“I know” ta amsa sannan ta katse. “Mschw! Ya Al’ameen ko baho? A dad’i na nide”
neman contact na Lubiee ta shigayi se gashi itama tana kiranta “hello Babe yanzu fa
nakeda niyyan kiranki.”
“Matar Soja! Sekuma na rigaki.”
“Toh ya kike?”
“K’alau wallahi ya preparation na bikin Hajar?”
“Gamu nan dai kud’in ashobe nason ya gagareni har 15k fa gakuma na d’inki again
gana gudumawa.”
“LOL karki damu zan biya miki na ashobe dana d’inki what are BFF’s for?”

“Se Matar Soja godiya nake, kice Ya Al’ameen ya baki kud’i kenan.”
“Ba dolensa ba, 100k yace ze turon.”
“Wallahi kina jin dad’i Babe I envy you Allah bani miji kaman Ya Al’ameen nima
such a gentleman.”
“Mschw! Sekiyi kuma gomma kin nitsu kin miyar da hankali kan karatun ki ehe.”
“Kefa baza kiyi ba? Ko remedials ne kiyi applying mana.”
“Haka Al’ameen ma yace nide ba abinda zanyi in turanci ne inaji na yafe karatun
Baba ya riga ya ciremin interest.”
“Toh Allah kyauta.”
“ Ameen semun had’u gobe” anan sukayi sallama.

****
Zeezee sekace ba matar aure ba gun bikin Hajar, gyalen ma ajiyesa tayi a gefe se
rawa suke ta takawa. Tarewa ma gabad’aya tayi zuwa gidan bikin yadda baza tayi
missing d’in koda event d’aya ba. Ranan Kamu da misalin k’arfe 5pm Mama ta turo
Omar kan ya kawo wa Zeezee miyan Eghusin da tayi sanin Eghusi is one of Zeezee’s
favorite. Omar yaje guards suke sanar dashi ai Madam bata gida ana bikin friend
nata so ta tare chan da mamakinsa ya dawo gida ya fad’awa Mama.
“Zeezeen?!” Tayi exclaining.
“Ita de, haka guards nata suka cemin.”
“Lallai yarinyan nan bata da hankali, agidan uban wa ta ta6a jin anyi haka? Bama
wannan ba shin mijin nata ya bata izini ne?” D’aki ta koma ta d’au wayarta tare da
kiran Zeezee, Zeezee ana ta cashewa bata ma san ina ta jefa wayar nata ba se chan
bayan Maghrib prayer taga missed call na Mama nan takira ta back. Masifa Mama ta
hauta dashi “ke bazaki ta6ayin hankali bako? Dan k’aniyanki kin ta6a gani na nayi
wannan rashin hankali da kika tafka? Saboda Maj-Gen bayi gari seki tare zuwa gidan
biki? Da izinin wa? Shi ya baki izinin?”
“Eh mana Mama seda na tambayesa ai.”
“Aww k’arya zaki yimin?”
“Mama ba k’arya bane Allah na tambayesa.”
“Kin tambayesa izinin zaki gidan biki kokuwa zaki tare gidan biki?” Shiru Zeezee
tayi tana nazari. “Dake fa nake?”
“Na tambayesa yace zan iya zuwa.”
“Bari na kirasa yace min ba haka ba kiga abinda zan miki.”
“Mam-” katse wayar Mama tayi ta shiga neman Maj-Gen.
Cin faracu Zeezee ta shigayi shikenan nata ya k’are inhar Baba yaji wannan batu
nata ya k’are sallama tayi da ‘yan gidan biki takira driver yazo ya d’auketa ASAP
ta koma gida, gabad’aya ta kasa samun sukuni.

Around 9pm wayarta dake kan centre table a parlour ya shiga ringing, har 6ari
take da take k’ok’arin duba wake kiran, ganin Maj-Gen akai ta sauk’e ajiyar zuciya
“thanks Gee ba Baba bane” ta furta tare da picking “Ya Al’ameen ina wuni?”
“Lafiya Zainab, ya hidiman biki?”
“Alhamdulullah gobe ma za’a d’aura aure.”
“Allah bada zaman lafiya toh.”
“Ameen.”
“Why did you do it?”
“Menayi Ya Al’ameen?” Binsa take a hankali karya tona mata asiri gun Baba.
“Lets not play games why did you do it?”
“Ya Al’ameen am sorry dan Allah kayi hak’uri karka fad’awa Baba wallahi dukana
zeyi.”
“Kinsan kinyi ba dai-dai ba kenan.”
“Eh nasani wallahi sharrin shed’an ne it’ll never happen again Mama ta kiraka
d’azu?”
“Yes she did.”
“And meka ce mata? Baka bani izini ba?”
“Eh.”
“Haba mana Ya Al’ameen kafasan dole zata fad’awa Baba.”
“Am kidding ban fad’a mata ba.”
“Amman nagode plenty phew!”
“It shouldn’t repeat itself again okay? Nan gaba duk inda zakije let me know its
for your own safety kinji?”
“Naji” tayi maganan tana murgud’a baki. “Seda safe.”
“Kina ina ne yanzu? Gida?”
“Eh na dawo.”
“Tam sleep safe and sound, I love you.” Yana katse wayar ta sake sauk’e ajiyar
zuciya atleast she’s save now.

Washegari bayan Zeezee ta dawo daga wuni ta kira Al’ameen a waya kaman dagaske
tana hawaye sosai. “Subhanallah Zainab whats wrong?” Kukan take har yanzu takasa
amsawa “Zainab are you there? Speak up please.”
“Ya Al’ameen...” Se kuma ta sake sa wani kukan.
“Zainab where are you right now?”
“Gida.”
“Alhamdulillah! Tell me meya faru? Mesa kike kuka?”
“Ya Al’ameen dan Allah kayi hak’uri wallahi ba dagangan nayi ba.”
“Yi meh? Calm down and tell me kinji? Don’t worry.”
“Ya Al’ameen a gidan biki ne yau...”
“Ehem ina jinki.” gabad’aya tasa hankalinsa ya tashi matuk’a.
“A gidan biki yau aka sace min white gold d’ina both d’ankunne da sark’a wallahi
bawai carelessness nayi ba.” Shi dariya ma tabasa “subhanallah amman yanzu dan an
sace miki gold naki kike wannan kukan Zainab?”
“You are not mad at me?”
“Why shall I? Qaddara baya wuce ranansa haka Allah ya qaddara za’a sace miki.”
“Na d’au fa zakamin masifa, na ajiye zan yi alwala kafin na fito an d’auke am
sorry please.”
“Stop apologising kinji? In zan dawo in shaa Allah zan taho miki da wani sabo
don’t worry.”
“Dagaske Ya Al’ameen?”
“Sosai My Princess your happiness means the world to me.”
“Thank you so much Allah dawo dakai lafiya” kaman dagske ranan suka sha hira
sosai se chan tace mai tana jin bacci, suna sallama ta 6arke dawani dariyan
shegantaka, wajen bag hanger ta nufi tare da zaro case na d’ankunnenta se kawai ga
white gold nata complete aciki meaning ba satan da aka mata duk plan ta had’a don
ta damfaresa. “Bari na 6oye wannan yanzu kafin yagani ya fasa sai min sabo ai
wallahi seka tsiyaye inde ni ne don kanka zaka gaji ka sakeni.” Tace da kanta
sannan ta bud’e kit nata tasa ciki ta rufe da key.

*~ *~ *~*
One week 3 days Maj-Gen ya k’ara sannan ya kira Zeezee musamman yace mata ze
dawo yau. Mutumiyar ko a bakin zaninta yau mijinta ze dawo daga tafiya, ba shara ba
mopping bale ayi maganan girki. Wankanta kawai tasha tasa wata shegiyar fiited
electric blue lace gown nata me black torches. Sosai tayi kyau dake kayan yad’an
bayyano da cleavage nata, video taping kanta tai tayi tana sending wa Adeel. 3:47pm
Al’ameen ya shigo gida alokacin Zeezee na zaune a parlour akan kujera se chatting
da Adeel take. Koda taga Al’ameen bata cemai komi ba se cigaba da chatting nata
take kai kawai ya kad’a ya k’ariso cikin parlourn ya zaua gefenta yana k’are mata
kallo a yayinda so da sha’awanta ke building a jikinsa. “My Princess am home.”
“I know” ta basa takaicaccen amsa.
“Kinyi kyau sosai My Princess.”
“Nasani ba seka fad’a ba.”
“Toh kina hutawa ne haka?”
“Ni ka dawo da suratan nan naka ko da wannan muryan naka, baka ga ko sannu da
zuwa ban maka bane ai kamata yayi kaima kayi zuciya karka min magana.”
“Ashe baki min sannu da zuwa ba!”
“Lallai ma! Wato baka ma san banyi maka sannu da zuwa ba?”
“Toh irin wannan shan kyan da kikayin ai gabad’aya ya tafiyar min da hankali.”
“Suit you well.”
“Bari na watsa ruwa toh” yana kaiwa nan ya fice doguwar tsuka ta bisa dashi. Not
long enough ya fito da white towel d’aure a waist nasa d’aya kuma ya ya6a a wuyansa
yana goga gashin kansa dashi kaman ance Zeezee d’ago kanki ta tsaya tana kallonsa
jaw dropped wide open. Theres no more denying Al’ameen is hot itama ta amince da
hakan yanzu, kasa dena kallonsa tayi kawai ji tayi yaja dogon hancinta. Da wuri ta
kyafta ido. “Kallon beyi yawa ba My Princess?”
“Nifa ba kallonka nake ba, I mean yes ina kallonka amman hankali na ba’a kanka
yake ba tunanin Adeel d’ina nake.”
“Hakane? Toh ina lunch d’ina? Am hungry.”
“Lunch ba a baku snacks bane a jirgin? Danni ba abinda na girka.”
“But I told you I was coming.”
“Meaning? Dan zakazo sena hau shiga kitchen? Lallai fah Soja dagaske kake.”
“I don’t mean kiyi girki but atleast ki tura koda guards ne su siyomin lunch am
your husband Zainab.”
“Toh banyi ba inji bugi da duka, nifa surutu ne banaso, ina zaman zaman na qalau
ka dawo zaka fara cikani da surutu, ai dama na gaya maka you must regret marrying
me gwara tun yanzu da kake da dama kayi whats right ka sakeni aikin banza kawai”
tana kaiwa nan ta nufi d’akinta. Binta kawai yayi da kallo sannan ya aika d’aya
daga cikin guards nasa ya siyo mishi lunch ya samu ya kora yunwa.

Koda Maghrib yayi shi kad’ansa yayi Sallansa sabida yasan there is no point yace
mata suyi tare don bayi zatai ba. Tana zaune a parlour tana kallo ya shigo ko d’aga
kai ta kallesa batai ba leda ya ajiye mata kan centre table nanma bata ce komi ba
“open it, its all yours.”
“Me aciki?” Tayi maganan cike da rashin kunya.
“Kede bud’e mana yi hak’uri.” Kaman bazata bud’e ba ta miqa hannu ta bud’e ganin
white gold d’an kunne, sarqa harda zobe tayi ciki wanda yafi nadan tan ma girma da
kyau. “Wow! Nawane wannan?”
“Naki ne Zainab ba an sace miki d’ayan ba?”
“Wow! Thank you Ya Al’ameen.” Shide yagane Zeezee yanzu idan yanason suna shiri
yana suprising nata da gifts. “You’re welcome My Princess ko kinason zuwa shopping
gobe ba inda zani se muje.”
“Dagaske?”
“Sure Dear.”
“I’ll have to think about it.”
“Toh My Princess ina mijinki ma sekin jamin aji? Anyways thank you for liking the
gift ni zan kwanta.”
“Toh seda safe.” Kallo ta cigaba dayi seda ta k’are series d’in sannan taje ta
canza zuwa night gown ta kwanta gefensa daga chan nesa, sede me? Ta fara bacci
sama-sama taji Al’ameen ya matso da pillonsa kusa da nata, batace dashi komi ba
seda taji furry hand na Al’ameen zagaye akan cikinta wani electric shock taji na
bin jikinta, ba kad’an ba every single touch na Al’ameen yake affecting nata. “Meh
haka Ya Al’ameen? Ka d’agani mana.”

*MIEMIEBEE Team #YGC!*


www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣5⃣
_Get well soon *AUNTY SIS* wishing you a jet recovery, ILY. I solemnly
dedicate this page to you alone *Queen Beelqees* you’re such a great fan and an
amazing sister, ILY._

“My Princess until when zaki bani hak’k’i na? Bakiya tausayi nane?”
“Kaman ya hak’k’in ka nifa bansan me kake magana akai ba kabar ni kurum bacci
nakeji.”
“Nikuma hak’k’i na nakeso My Princess, bakiya tausaya min neh? Yaufa watan mu
d’aya da aure ban ta6a nema ba se yau yi hak’uri kinji?”
“Ai nice abar tausayi ba kai ba dan Allah kayi hak’uri wallahi ba ‘yar iska ceba
ni.”
“My Princess kaman ya iskanci kuma? We are a couple fah.”
“Ni wallahi banaso, ba tarbiyyan da Baba yaban ba kenan.” Dariya sosai tabasa da
k’yar ya danne dariyan yace, “toh aina akace miki yin hakan iskanci ne?”

“Ni de wallahi banaso dan Allah kayi hak’uri.”


“Toh My Princess naji I’ll go easy on you.”
“Ai wallahi k’arya ne nasan halin soldiers ni dan Allah karka min wani abun, na
tuna ma wallahi bana Sallah ina kan period d’ina.” This time around kam seda yayi
dariya, “d’azu fa kikayi sallah My Princess.”
“Bb.. Bayan Sallan ne yazo Allah ba k’arya nake maka ba” Ignoring what she said
ya ja hannunta seda ta fad’a jikinsa, hugging nata yayi gagam wane za’a k’wace masa
ita, ihu da kuka Zeezee ta shiga rusawa tsakaninta da Allah badan komi ba kuma don
wai tayi promising wa Adeel pride nata. “Ya Al’ameen dan Allah kayi hak’uri wallahi
na tuba bazan sake ba” riganta ya shiga raba ta dashi nan ta k’ara volume na kukan
nata “wayyo Allah! na nashiga uku dan Allah ka rufa min asiri wallahi bazan sake
ba.” Shima Al’ameen baida niyyan mata komi kawai so yake yayi mata horo ko halan
zata d’an rage yimai rashin kunya. Yi yayi tamkar baya jinta seda ya rabata da
kayanta gashi daman shi kad’ai ne a jikinta nan ta shiga kare k’irjinta tana kuka
sosai har wani sama-sama nishinta take. “Ya Al’ameen wallahi bazan sake maka rashin
kunya ba kace sekayi abinda kakeso wallahi gawana za’a cire gobe a gidan nan. Ka
tausaywa min yarinya ceni wallahi bansan komi ba.”
Dariyansa ya danne da k’yar, “baki sanin ba yasa nakeson na koya miki yau ai,
I’ll go easy on you.”
“Wallahi banason sani ka rufa min asiri don Allah.” sam be saurareta ba ya shiga
sarrafata iya son ransa danko da hannu d’aya ya iya ya danneta. Ihu tasa “Mamana na
mutu yau! wallahi Ya Al’ameen bazan sake maka rashin kunya ba kaji na rantse dan
Allah ka rufa min asiri ka dena.” daman ya take k’arewa da slight touch nasa bale
yau da yake mata uwa uba. Kukan ga cigaba dayi amman Al’ameen be saurareta ba seda
ya kashe mata jiki lik’is yazamo jan numfashi kawai take sannan ya tambayeta;
“Are you sure bazaki sakemin rashin kunya ba?” da wuri sekace me jiran tambayan
ta amsa;
“I am pretty sure, na sake kamin duk abinda kaga ya dace bale ma bazan sake ba.”
Se anan ya saketa da wuri taja riganta ta miyar tana share hawayenta. Gani yayi ta
d’au pillonta tana neman barin kan gadon. “My Princess ina kuma zakije?” A farko
tayi niyyan sharesa remembering ze iya tarke ta yamata abinda take tsoro tace, “zan
kwana a k’asa.”
“Mesa?”
“Babu kuma dan Allah karka hanani.”
“LOL zo ki kwanta nan ba abinda zan miki.”
“Wallahi k’arya ne ni kabarni in kwana acan d’in kawai.”

“Ko ki hauro mu kwanta kona biki har k’asan na miki.”


“A’a dan Allah kayi hak’uri” gabad’aya ta gama tsorata da kalan abinda Al’ameen
yayi mata sede theres no denying she enjoyed every part of it. Ranan bakin yin
rashin kunyan ma babu.
“Kizo mu kwanta kinji? Ba abinda zan miki.”
“Ya Al’ameen ka rantse ba abinda zaka min wallahi yarinya ceni ka rufa min
asiri.”
“I swear bazan miki komi ba.” Se anan ta koma gadon ta kwanta daga chan nesa
gabad’aya ranan ta kasa bacci seji take kaman ze danne ta yayi mata wani abun, ina
ita ina soja?!

****
Da wajajen 11am Zeezee da Al’ameen suka shirya tsaf zuwa Jifatu Store siyayya
kaman ba gobe Zeezee tayi, sauran abubuwan ma ita kanta batasan me zatayi dasu ba
amman dan ta raba Al’ameen da kud’insa tayita d’iba duk haushinsa takeji da abinda
yayi mata jiya inda kuma yaci nasara akanta fah? Mezata cewa Very Own? Koda suka
isa gida fitowa tayi daga motan ta nufi ciki, guards nasa yasa suka fiffito masu da
kayakin. Miqe kan gado tana sanye da vest da skirt na lace da ta fita dashin ya
tarar da ita “My Princess lunch fah are you not hungry?”
“Toh ka siyo mana ne kaga banci ba?”
“Ni se yaushe zanci girkin Princess d’ina? Naki nakeso ba na waje ba.”
“Lallai ko zaka bushe, kaga na farko ni ban iya girki ba na biyu koda na iya ma
bazan ba, so tun wuri gwara kayi whats right, ko ka sakeni ka kawo wacce zata na
maka kokuwa kaje ka siyo mana.” Ba tare da yace da ita komi ba ya aika one of his
men, daya dawo seya zauna a parlour. Zeezee kuwa seta d’au ko ya fita ne nan ta
bud’o kit nata tare da ciro old white gold nata ta ajiye sa kan gado. Kwatsam! Taji
shigowan Al’ameen ba notice kafin tace zata b’oye har ya gani. Kallon gold d’in
yayi sannan back to her wanda tuni ta sunkuyar da kanta, murmushi kawai ya saki
tare da kad’a kai. “Toh ki adana mana My Princess kafin ya 6ata kinji?” Cike da
kunya ta gyad’a kai ita wai wani irin mutum ne Al’ameen? _Kode be gane cewa tsohon
gold nawan bane?_ Ya gane mana wata zuciyar tace mata. _Toh mesa bemin masifa ko
magana akai ba?_ Sabida halinsa ne hakan ignoring duk wani rashin hankalin da kike
mai ko kin manta me Lubiee tace miki ne? Duk abinda kike yanzu zena kallonsa ne a
matsayin yarinta, zuciyar ta sake amsata.
Kai ta kad’a da wuri “chan maka” ta furta a hankali. Bako kunya ta d’au gold
d’in ta miyar cikin kit nata. Abinci na isowa kuwa ita ta fara bud’ewa ta hau ci.
Bayan tacinye naman dake kan nata ta bud’e take away na Al’ameen ta cinye naman
nasa shima.

Yana fitowa daga bayi ya nufi dining space tare da bud’e nasa gani yayi ba nama
akai. “My Princess haka suka kawo abincin ba nama akai?”
“Ni na cinye dan na yau nama uku ne kacal akai nikuma in banci biyar zuwa sama ba
bana jin dad’i” tana kaiwa nan tabar masa dining table d’in. Kamar yadda ya saba
ignoring nata yayi ma yau sannan a hankali ya cinye abincinsa.
Da yamma da yunwa ya korata ta shiga kitchen tana tunanin mezata dafa. Fridge ta
bud’e ta ciro froze chicken tasa a ruwa bayan k’ank’aran jiki ya tafi ta d’ago
wuk’a zata yanka sede sam bata san how ba, cinya kad’ai tasamu ta cire sauran duk
yankan ganin damanta tayi. Tagama ta tafasa kamar yadda taga Mama nayi nanma ta
manta batasa albasa dan kora mata k’arni ba. Yana tafasa ta shiga soyawa anan
tayita k’ona kanta, bayan nan ta dafa indomie sannan ta nufi dining tahau ci. Dai-
dai nan Al’ameen ke dawowa ciki daga training men nasa “humm! me Princess ta girka
mana haka?” Yayi maganan yana k’arisowa inda take.
“Abincin yara na girka.”
“Manya basuwa cin indomie koh Princess?”
“Nide ban ta6a ganin Baba yaci ba.”
“Toh nida Baba waye babba?”
“Ai duk kanwan ja ce, me marabar dambe da fad’a?” yana dariya yace “to aci
lafiya” ya juya ze tafi kenan idanunsa sukayi tozali da k’uran da farin kayansa ya
d’iba wanda he’s sure jikin dining chair d’in ya kwasa. “Princess kin ta6a dusting
kujerun nan kuwa?”
“Meka ga?” Kayan nasa ya nuna mata. “Toh dama aiki na ne yin dusting? Ai wallahi
kamar yadda na gaya maka zan sake nanata ma yanzu ba tsaftace maka gidan da zanyi
inkaga bakason zama cikin dotti seka sallameni nakoma gun saurayi na aikin banza
kawai ni kayi ka koma Abujan ma ko zan samu iska.”
“Allah kaimu tonight” yace kad’ai da ita sannan ya fice. Jin haka kad’ai seda
yasa ta saki fitsari a panties nata. Koda dare yayi yau hijabi babba me hannu ta
6urma sannan ta d’au pillonta ta nufi kan couch dake d’akin ta kwanta tare da
lullu6e kanta. Not long enough Al’ameen ya fito daga bayi sanye da towel. Tana
ganinsa taja bargon ta rufe fuskanta dashi, batason ganinsa ba kaya saboda hakan ba
k’aramin affecting nata yake ba.

Cikin nitsuwa yagama kimtsa kansa sannan ya nufi inda taken nan tahau shaking
kafin yace ze yaye bargon ta mik’e zaune “Ya Al’ameen dan Allah kayi hak’uri karka
min wani abin na tuba wallahi.”
“Bani kikeyi wa rashin kunya ba d’azu? Ai yau ba abinda ze hanani amsan hak’k’i
na.”
“Wayyo Allah Mama na! wallahi kace zaka kar6a kana iya kaini lahira ba shiri ka
tausayamin wallahi yarinya ceni.”
“Ai ke kikace idan kika sake min rashin kunya namiki duk abinda ya dace wannan
hukuncin ne kuma ya dace ga duk wani me yima soldier rashin kunya.”
“Kuma nace kayi hak’uri bazan sake ba.” Ignoring nata yayi yashiga neman kwaye
mata hijabin, nannad’esa tayi gam a jikinta tana mai kuka tana had’a sa da Allah
“gobe in kika sake namiki meh?”
“Kamin duk abinda kaga ya dace amman banda wannan dan Allah bale ma bazan sake
ba.”
“Naji toh tashi muje mu kwanta.”
“Baza kamin komi ba?”
“In kika sake tambayana sena miki.”
“Toh nayi shiru muje mu kwantan.” Pillon nata ta d’aga tabi bayansa suka kwanta
sannan ya kashe musu wuta.

*~ *~ *~
Life moved on, rashin kunya de na yau daban na gobe daban duk yadda Al’ameen yayi
don daidaita tsakaninsa da Zeezee abin ya gagara. The only way is ya bud’e mata ido
ya fara discpline nata tunda dama ya karanci matsoraciya ce, kurun baki ne kawai da
ita bayan nan kuma na k’arfi da yaji ya amshi hak’k’insa anan ne zata soma ganin
girmansa amman dake kullum sede yayi warning nata shiyasa take abinda taga dama
amman meh? Shi bayison hakan bayason yayi taking nata da k’arfi yafison inma abu ze
shiga tsakaninsu yazamo da concent nata ne sabida he values her alot duk wani
abinda ze ta6a ta bayaso. All he knows for sure is he’ll never rest trying to make
her happy se har rananda tayi accepting nasa as mijinta tunda dama time heals.
The only time suke shiri da Zeezee shine in ya siya mata abun daya burgeta anan
kam zesha fara’a kaman ba gobe. Tun dawowansa kuwa yau kusan sati uku kenan Zeezee
kullum cikin yimai wak’an ya koma Abuja take saboda tasamu tayi waya da Adeel nata.
Ana sauran sati ya koma Abj bayan ya dawo daga training men nasa ya tsinci Zeezee
zaune kan dressing mirror da wani nickers iya saman cinyarta da kuma vest ajikinta
tana trying on lipsticks data siyo ran chan. Se aukin zama da k’ananun kaya tabi
ta tada mishi sha’awa dazaran yace ze neme ta kuma tak’i. “My Princess tashi ki
shirya zamu fita.”
“Kai kam ko maye albarka wallahi wai shin yaushe ne zakayi sticking it to your
head that I don’t love you Adeel nakeso? Ina kuma zamuje ni gaskiya banason yawo da
tsoho.”
“Yi hak’uri kinji?” ya fad’a cikin omg voice nasa.
“Ina zamuje ka fad’amin.”
“Its a suprise.”
“Sekuma Allah yayi banson suprises so save it.”
“Zakije kiyi passport ne.”
“Nameh? Haka kawai ana zaman k’alau sena hau yin passport? Thank God ba
mahaukaciya ceni ba.”
“Trust me kinji? Ko bakiya son kije aikin Hajj this year?”
“Hajj!” Tayi exclaiming tare da miqewa tsaye.
“Sosai ma next week zan koma aiki and zanyi morethan a month kinga ba amfani
kiyita zaman banza anan gomma kinje kinga d’akin Allah ko?”
“Dagske kake Ya Al’ameen zaka kaini Saudi?”
“Am damn serious Princess.” Bako kunya ta hau rawa wajen tana jin dad’i kallonta
kawai yake kaman doll baby. Nan da nan ta shirya suka fice inda tayi passport and
other stuffs acikin sati kafin ya koma Abuja ya samu yagama mata all processes daya
kamata. Zeezee de ta cika wa ‘yan gida da friends nata kunne kan zata tafi aikin
Hajj. Acikin sati biyu Zeezee ta samu tafiya, d’ankaren nan an had’a list na
abubuwan da za’a siya a Saudi tun kafin a isa. Mak’udan kud’i Al’ameen ya bata
wanda ita kanta seda tasha mamaki.

Zeezee de ba aikinta achan Saudi se yawo anan yawo achan da d’aukan selfies.
Tunda ta tafi sau biyu ta kira Al’ameen amman Adeel kam wai! 24/7 tana kan mai waya
dan sokanci ma idan tana d’awafi cewa take Allah sa Al’ameen ya saketa ta auri
Adeel, haka through out har suka gama aikin Hajj. Siyayya sosai Zeezee tayi wa
kanta kaya sekace na siyarwa bayan data gama da kanta ta tabbata bata buk’atan wani
abu ta sai wa su Baba da Mama dasu Lubiee harda ‘ya‘yen Mariam da d’an Yasmeen
kayaki amman ko k’asan Makkah ne bata d’iba ba da sunan wannan na Ya Al’ameen ne.

Safe and sound Allah ya dawo dasu Zeezee gida. Washegari su Mama sukazo sukayi
mata sannu da zuwa. Gifts kad’an ta basu kasancewar kayanta na kago. A ranan da
kagonsu ya iso a ranan Al’ameen yamata waya kan ze dawo, shi da kansa ya biya ya
amso mata akwatunan nata. Shi kansa mamakin ina Zeezee zata kai wannan kayaki yake.
Ya isa gida guards suka shiga ciki da kayaki sede yayi ta sallama Zeezee bata
amsawa. D’aya daga cikin guards nasan ne ya sanar dashi kan Madam ta fita bata
gida.
“Bata gida where did she go?”
“I really don’t know Sir all she told me was that she won’t take long.”
“Okay you are free to go.”
“Thank you Sir” ya fad’a tare da saluting nasa sannan ya fice, ciki Al’ameen ya
koma yana mamaki irin hali na Zeezee. Ace ya sanar da ita yau ze dawo amman ta
d’ibi k’afa ta fita? Bayan bata ajiye mai komi ba gakuma fita yawon da tayi, mawai
da izinin waye? Toh Allah shirya masa ita. Ba Zeezee ce ta dawo gida ba se bayan
Sallan Maghrib. Koda ta gansa zaune a parlour bata mai magana ba illa ma had’a ran
datayi, wucesa tayi takai ga shiga d’aki ya kirata kaman bazata amsa tace, “meh
kuma nayi?”
“Zoki zauna anan”yayi beckoning nata over.
“Ni gaskiya fitsari nakeji.”
“Jekiyi koma meh ki dawo ina jiranki” harara ta galla mai sannan ta k’arisa ciki
chan ta tarar da akwatunanta. Sallah ta idar da wuri-wuri sannan ta shiga bud’e
kayakin gabad’aya ma ta mance da kiran da Al’ameen ke mata shida kansa yagaji da
jiranta ya k’ariso ciki ya tarar da ita se gwada kayaki take. “Ban kira kiba
Zainab?”

“Ka kira” ta amsa ba tare ta nuna damuwa ba.


“Meya hanaki zuwa?”
“Na samu abinda yafi kiranka daraja, kai shikenan yau ka dawo zaka hau tak’ura
min ni wallahi bank’i ka koma bama a gobe.”
“Zainab this should be the last time zaki sake fita baki sanar dani ba clear? Ba
fata ba amman in fitanki wani abu ya sameki fah? Sede akirani acemin ga abinda ya
sameki ni banida masaniya akai?” yayi maganan in a serious tone wanda be ta6a using
da ita ba seyau amman dake rashin kunya yayi mata yawa ko damuwa batayi ba ta dake;
“Jimin bawan Allah? Nifa surutu ne banaso, da yini kakeso kullum inayi a gidan
nan naka da bakomi aciki? Kokuwa so kake kowani fita na nakira ka na gaya maka inda
zani? Lallai kuwa banida katin asara. Kaga rashin hankalin dana ke maka yayi yawa
its simple kana iya sallamata daman ni tun farko ma bason auren nake ba.”
“Haka kikace?”
“Haka yake kuma ni excuse me ina gwada kaya.” Bece da ita komi ba yafice yabar
gidan gabad’aya. Gwada kayakin ta cigaba dayi don kanta tagaji tabar sauran se
gobe, sannam tayi sorting out tsaraban da tayi ma mutanen arzikinta. Da safe bayan
ta had’a breakfast na iyaka bakinta ta fad’a bathroom tayi wanka tsaf sannan ta
shirya cikin d’aya daga cikin arabian dresses data siya. Dining ta nufa ta hau
karyawa da chips da omalet, tana cikinyi Al’ameen yafito shima all dressed up kamar
yadda ta saba da k’in gaishesa haka ma tayi yau. “Har kin had’a breakfast ne baki
jira sun kawo mana ba?”
“Inada inda zani ne shiyasa.”
“Toh yayi kyau ina nawa?”
“Ban girka ba.”
“Kaman ya baki girka ba bayan ga abinci a gabanki?”
“Eh toh na girka amman na baki na ni kad’ai in yunwa kakeji,kana iya aikan guards
naka su siyo maka.” Nan da nan ta kur6e tea’n ta ta k’are breakfast ta bar mai
wajen. Tsaraban su Mama ta tattara ta fito “toh ni na fita sauran kace ban
tambayeka izini ba.” Bece mata komi ba ta fice achan gida ta rabawa su Omar
tsarabansu, sosai Baba yaji dad’i se albarka yake ta sa mata haka Mama ma. Bayan ya
kira Maj-Gen. Ya tambayesa izini kan ze iya miyar wa Zeezee da motanta, Maj-Gen
yace ba damuwa Baba yad’au key’n motar ta ya bata bayan nasihan dayayi ta mata. Ita
de Zeezee dad’i kasheta.

Suna zaune a d’akinta ita da Mama, Mama ta tambayeta “mijinki fah? Me kika kawo
masa?”
“Da har da shine a tsaraban Mama?”
“Kaji ‘ya! Kar kisa na zageki Allah, ya biya miki kud’in Hajj gabad’aya amman
kice baki kawo masa komi ba? Haba Zainab mesa kike hakane? Wannan rashin hakali
dame yayi kama?”
“Nikam gaskiya hankalina beban haka ba.”
“Toh kina jina ba? Kina komawa gida ki d’au agogo da darduman da kikace zaki bawa
Ya Ibraheem ki bawa Maj-Gen kinji ko bakiji ba?”
“Naji” tayi murmuring.
“Bayan nan zan d’au d’aya daga jallabiyan Babanku ki had’a duka ki kai masa
sannan kuma ki basa hak’uri, ke ashe rashin hankalin kin har ya kaiga haka? Toh
Allah shiryeki Zainab don nabar zaginki da yi maki baki yanzu saboda bashida fa’ida
addu’a kad’ai zan miki Allah ya shiryeki.”
“Ameen ,harda jallabiyan Baba? Wallahi masu tsada ne kuma wa Baba na siyo wa.”
Bige bakinta tayi “ungo naki nan da masu tsadan.”

****
Tuni Zeezee ta tura driver’nta gida. Gidansu Lubiee ta wuce da motarta sannan
lastly gidan Mariam daga chan se gidanta. A parlour ta tsinci Al’ameen data shigo
sannu da zuwa yayi mata sannan ta amsa sama-sama ta wuce ciki. After a while ta
fito da tsaraban dole da Mama tace seta basa, a gefensa ta ajiye “gashi wai inji
Mama na baka.”
“Name fah?”
“Tsaraba daga Makkah.”
“Mama ne tace kibani?”
“Eh ko baka so ne?”
“D’auki abinki My Princess karki damu nasan bawani kikayi niyyan kawowa ba,
tattara kinji?”
“Aww wai bakaso? Aikuwa tafi nono fari wallahi daman agogon Ya Ibraheem ne kayan
kuma na Baba, karka kar6an.” Binta yayi da kallo seda ta 6ace sannan ya kad’a kai
yacigaba da kallon sports nasa.

*© MIEMIEBEE Team #‘YGC!*


www.beeeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣6⃣
_Just to let you know👌🏿 Masu karatu wai shin kun d’au ni kaina dad’i rashin
kunyan da Zeezee keyima Al’ameen d’inmu yakemin neh? Kusani Mahak’urci Mawadaci,
kuma me hak’uri shi kan dafa dutse yasha romo. Ita kuma Zeezee acewarku haka zan
barta ne taci bulus bayan dukkanin aikin haramun datake aikatawa? Ofcourse no dole
zata gir6e abinda ta shuk’a wataran. Duk wanda yayi ba dai-dai ba dole zega
consequences so nomore bina private ana cemin abinda Zeezee keyiwa Al’ameen yayi
yawa I know right what am doing ™YGC!💞_
_Ahh! Almost forgotten this page is honoured to *D Queen, Humairah,* and *Ummi
Ayshatu* #OneLove💞_

Few days later yar Maj-Gen. wato Hajiya Sadeeyah ta mai waya kan zata zo nan
Bauchi bikin ‘yar k’awarta zata kuma sauk’a a gidansa. Bayan sun k’are wayan yaje
ya samu Zeezee mik’e kan gado tana chatting da Adeel tunda ba halin yin waya Maj-
Gen. na gida. “My Princess” banza dashi tayi se a karo na biyu ta amsa “menayi kuma
yanzu?”
“Haba Princess give me a break mana ni bansan mena miki ba kullum kike cikin
6atamin rai, in wani abun na miki lemmi know sena gyara ko ke marital life namu na
miki dad’i? Kullum babu jituwa a tsakanin mu? Its hightime ki gyara ko ba haka ba?”
“In gyara? Me zan gyara? Kai babba bakace zaka daidaita komi ba seni zaka wani
cemin na gyara.”
“Me zanyi toh Princess? Duk yadda nasan zanbi dan daidaita tsakaninmu nayi
kink’i bada had’in kai.”
“Lallai kuwa, ka kama ka barni da outdated mota kam ai dole kace kabi anyway you
know how, ni kaga ba dogon surutu nakeson yi ba, uban nawa in Allah ya sake hore
mai ze canza min motar.”
“So kike a canza miki mota Princess?”
“Eh mana waye bayison sabon abu?”
“Shine kad’ai dalilin dayasa kike duk abubuwan da kike, akan mota ne kad’ai?”
“Kafa dena cewa kad’an nan Malam Soja tunda ka kasa canza min.”

Yana murmushi yace, “toh ai baki ta6a cemin na canza miki mota ba Princess.”
“Komi ne sena gaya maka? Hankali bayi gayawa mutum whats right ne?”
“Yana yi Princess toh am sorry it never blinked into my mind, za’a canza miki
mota inhar shi kikeso anything for My Princess.”
“Wani iri zaka sai min toh?” Tayi maganan finally tana murmushi.
“Duk kalan wanda Princess take so za’a sai mata.”
“Dagaske Ya Al’ameen?”
“Sosai ma Princess, wani iri kikeso?”
“Kalan Ford Jeep naka 2016 d’innan nakeso.”
“Irin nawa?!” Yayi exclaiming.
“Me wani kake zaro ido ba zaka iya sai min bane? Kokuwa kaima kana sahun mazajen
da suke cewa matansu basu hawa mota iri d’aya da nasu?”
“Ko d’aya Princes naga kaman wancan ya miki girma da yawa ba gara irin simple
cars haka ba, inaga jeep nan ya mik’i kato kona miji ma ya ake ganinsa ciki? But
inhar jeep d’in kikeso why not try out prado ko LR-3?”
“Banaso in bazaka saimin kalan naka ba shikenan dama haka kake ba abinda ka ta6a
min tunda ka auroni, agida ban ta6a neman abu gun Baba na rasa ba Allah ze sak’a
min ai” se ta 6arke da kuka tana Allah zeyi mata sakayya. Kallon yarintan ta kawai
Al’ameen yake yana murmushi, “toh ya isa haka Ford Jeep kikeso?” Kai tayi saurin
gyad’awa tana hawayen har yanzu. “Toh stop crying zan sai miki.”
“Dagaske Ya Al’ameen? Irin nakan nan fa nakeso amman fararta banason bak’ar
mota.”
“Ko pink kikeso za’a sai miki stop crying I don’t want you to think bana miki
komai, I’ll use the last kobo I have to make you happy.”
“Yeyy!! Nagode toh se zuwa yaushe toh zaka siyamin d’in?”
“Nan bada jimawa ba Princess, I want a favor from you also kinji?”
“Ahap ai dama nasani ba tsakani da Allah kace zaka sai min motar ba, nasani
zakace yau sena baka hak’k’in kane toh inhar haka ne ka riqe motar taka tunda kai
bakada tausayi ‘yar ni d’innan zaka ce zaka sa a gaba seka k’wato abinda yana iya
kaini lahira.”

“Ohh Zainab! Ashe haka masu sunan naku suke? Ki kwantar da hankalinki in hak’k’i
na ne na jima da yafe miki sabida banason tsinuwan mala’iku akanki se rananda kika
yarda tukuna, yanzu that aside gobe Hajiya Sadeeyah tace zata zo nan Bauchi bikin
‘yar friend nata.”
“Wata Hajiya Sadeeyah tukun? Sis naka babba?”
“Eh ita kuma na mata masauk’i anan-”
“Anan?” Tayi saurin katsesa “haba kaikuwa, mesa baka barta ta sauk’a a hotel ba.”
“Haba Princess wani irin magana kike? She is my blood sister fa, ke yanzu zakiso
ace in Yasmeen namu zatazo Bauchi takama hotel ne?” Kai ta kad’a da nufin a’a “toh
nima ai kinga be kamata nabar Hajiya Sadeeyah bako?”
“Eh be kamata ba kam amman kaga ai in Yasmeem ce zata sauk’a anan ba girkin da
zan mata komi ita zata na yiwa kanta amman incase of Hjy Sadeeyah kuma kaga fa dole
sena hura wuta kuma ni ban iya ba wallahi ba abinda na iya girkawa aside from
indomie da chips se dama-dama suyan kaza.”
“Duk ba matsala neba wannan Princess abinda nakeso dake shine kawai ki ajiye
wannan rashin kunya da yawon na kwana biyu har seta tafi kinji?”
“Haba! Haba! Daddy kayi adalci mana, shikenan don ita se a tauyemin hak’k’i?
Rashin kunya kuma in zakamin abinda nakeso ka sakeni ba wanda ze ji kanmu.”
“Its a favor am asking yi hak’uri kinji? Ko bakiya son Ford Jeep naki ne?”
“Inaso amman de-” hannunsa ya aza bisa lips nata;
“Yi hak’uri just this once.” hannun nasa ta cire;
“Naji Allah sa kar wani abin ya taso toh don gaskiya da sakel.”
“Nagode kinji Princess? I love you so much.”
“Naji toh, excuse me.” Be sake ceda ita komi ba ya yai finding way nasa out.
****
A washegari Hjy Sadeeyah ta iso, a tare Zeezee da Al’ameen sukaje suka d’aukota
daga airport. Se admiring nasu take, a rayuwa batada burin da yafi taga her only
brother da matarsa, hakan yasa takeson Zeezee sosai. Tin a mota se yaba Zeezee take
har suka iso gida. Bayan Zeezee takai mata akwatinta d’aki ta zarce ta had’a kan
dining sekace ita tayi girkin. Bada jimawa Hjy Sadeeyah tafito suka ci lunch sannan
Zeezee ta tattara wajen instead tayi wanke-wanke seta jibge kayan gu d’aya kawai
abinta ta dawo ciki.
Ganin Al’ameen nacan parlour da sis nasa suna hira tasa lock a d’akinsu ta hau
skyping Adeel.
“Very Own.”
“Yes Sweetest love howayou?”
“Am good and you?”
“Also, is it my eyes or kin k’ara weight ne?”
“K’iba? Well maybe.” tayi maganan tana checking kanta.
“Am jealous that soldier is finally making my woman happy tunda har take k’ara
weight.”
“Oh common Very Own please don’t say that kaima kasan no one will make me happy
than you will.”
“Hakane?”
“Yes Baby, ya Florida?”
“As it always is, party here party there.”
“Very Own nasan kana chan kanata shafa jikin sluts d’incan ko?”
“Toh kema ba kina chan ba kinayi da mijinki ba?”
“Wallahi thats not true ko ta6ani ban bari yayi.”
“LOL am kidding you ni naki ne ke kad’ai kinji?”
“Yauwa Very Own.”
“So har yanzu be sake kinba?”
“Am still working on it, mutumin ne bansan dame zanyi describing nasa ba, komin
me nayi masa baya gani yace ze d’au mataki akai he keeps on ignoring me.”
“Meaning baze iya sakin kiba kenan bale mu kasance together?” Yayi maganan haushi
yana building a voice nasa.
“No Very Own calm down ba haka bane, I will never rest until ya sakeni you have
my solemn words.”
“Alright Babe I trust you amman fa kiyi a hankali banason naji shima ya ta6amin
lafiyarki as Baba did kinsan soldiers d’innan.”
“Don’t worry wannan I don’t think ze iya d’aga hannu ya ta6ani.” Jin motsin mutum
tayi sauri tace mai “am cutting off he is here.” Da sauri ta katse sede daga yadda
take raba ido ana iya gano batada gaskiya.

“Princess me kike haka?”


“Mekaga? Babu ofcourse.”
“I thought I heard you on the phone with someone.”
“Toh shikenan yanzu ko waya ban isa inayi ba? Classmate d’ina ne ya kiran ko
shima zaka hanani waya dashi ne?”
“Are you sure?”
“Yoh jimin mutum kanason kaji da wa nayi waya? Da sauarayi na Adeel ne, nifa
tak’ura ne banso duk ladabin danayi wa Hjy Sadeeyah baka gani ba kanason 6atamin
rai shikenan ka rik’e motarka na rik’e ladabi na aikin banza kawai” tana kaiwa nan
ta bar masa d’akin. Binta kawai yayi da kallo.

****
Washegari da safe Zeezee ta tashi sid’ak-sid’ak tayi wanka ta shirya tsaf ko
karyawa batai ba wai seta isa gidan su Lubiee tukunnah. Motarta ta ja ta fice yawon
banzan data saba.

9:20am Al’ameen ya tashi yayi wanka ya shirya, d’akin Zeezee ya wuce kasancewar
ranan a nasa ya kwana, dabe ganta ciki ba se yayi tunanin ko tana kitchen ne sede
da yafito ya dudduba Zeezee was nowhere to be found. This is serious! Yaushe ta
fitan?

Yana juyawa yaci karo da Hjy Sadeeyah, “little bro ina kwana?”
“Ina kwana Hjy har kin tashi ne?”
“Eh kasan zuwa anjima zan fita” tayi maganan tana bin kitchen d’in da kallo, gani
tayi wanke-wanke kota ina kuda suna bi. “Maj-Gen!” Tayi exclaiming.
“Me wannan nake gani haka? Karka gayamin wanke-wanken jiya ne?”
“Erm..” Ya shiga kame-kame.
“I knew it all along, ko me kakeyi a kitchen d’in kuma yanzu? Ina fatan bawai
wankewa zakayi bako?”
“Oh common Hjy! Nazo d’aukan abu ne.”
“D’aukan abu ko neman matarka? Karka damu naga ficewarta d’azu.” Hannunsa ta
rik’o “zo nan” a parlour suka zauna “what is going on a gidanka Maj-Gen?”
“Seriously babu Hjy itama Zainab d’in biki suke dashi shiyasa tafita yau.”
“And you expect me to believe that? Yau ma ni kake yiwa k’arya Little Bro?”
“Ba haka bane Hjy please lets drop this topic.”
“What is going? Wahala Zainab take baka shine baka sanr dani ko Mama ba? Meye
amfanin family toh?”
“Gosh! Hjy enough please ba haka bane.”
“Toh yaneh? Gashi nan its written all over your face da akwai matsala, nikuma ba
haka nasanka ba, abu bai ta6a damunka inba wai yakai maqora ba. Waye ne? Zainab
ce?”
“Hjy I don’t know either I just can’t get her. Inason Zainab you know that.”
“I know Little Bro fiye da tsammaninka so meke faruwa?”
“Tunda aka d’aura mana aure ta canza gabad’aya, she is not the Zainab I use to
know, narasa dalilin dayasa take hakan bayan ban ta6a tauye nata hak’k’inta ba, duk
wani abinda takeso shi nake mata na kaita Hajj yanzu haka tace tanason na sai mata
irin Ford Jeep d’ina I agree zan saya mata but I don’t get anything good from her
tun abun bayi damuna ya soma. Hjy akwai wani abinda nake lacking ne as a man? Ko
kuwa akwai abinda mazaje keyima matansu ne don su sosu wanda ni bansani ba baniyi
mata? Let me know please.” Ya k’are maganan abin tausayi.

“Is okay kaji? Ba abinda ka rasa as a man Maj-Gen sabida haka kuma ‘yar yarinya
bazata tsaya tana baka wahala ba. Adalilin me? Allah dawo da ita gida I’ll confront
her myself wannan ai bayi bane.”
“No please don’t let her be time heals, eventually zata gano kuskuren yin hakan
wataran please karki mata magana kinji?”
“Kamar ya kar na mata magana Al’ameen? Yarinyan da ina iya yin jika da ita ne
zakace kar na mata magana bayan tanayin ba dai-dai ba? Wallahi k’arya ne. Tasan ina
nan zata kama ta fita ba tare da ta tanarda min breakfast ba? Haka akeyi?”
“Nasan tayi laifi am apologising on ber behalf kiyu hak’uri please but karki mata
magana kinji Big Sis?”
“Al’ameen...”
“Please for me.”
“Toh shikenan but promise me kai zaka mata.”
“I do, zan mata in shaa Allah nagode.”
“Gaskiya amman inhar bata shiryu ta shiga hankalinta ba dole a raba auren nan don
ina raye bazan bari wata tasawa Brother na hawan jini ba, I can’t take it.”
“Is okay ki shiga kiyi wanka bari na aika a siyo mana breakfast.”

****
Ba Zeezee ce ta dawo gida ba se bayan Maghrib a dai-dai bakin k’ofa ta kasa
kunnenta sanadin jin muryan dake tashi a parlour da tayi.
“Allah ka barni da ita senayi mata magana wannan rashin hankali har ina? Ace
yarinya ta fita tun safe har yanzu bata dawo ba kuma bawai ta tambayeka izini ba?”
cewar Hjy Sadeeyah a fad’ace.
“Hjy I said enough let her be please.”
“Shegiya munafuka irin kune koda kunje Makkah baku ganin Ka’abah ina ruwanki da
inda naje dakuma lokacin dawowa na gida mschww.” Zeezee tayi maganan a fusace a
kuma cike da rashin kunya sannan ta bud’e k’ofar, tsaye ta tarar dasu. Ba tare da
tace da ko d’ayansu uffan ba ta wuce ta nufi d’akinta binta kawai Hjy Sadeeyah tayi
da kallo.
“Ahakan kake cewa kar na mata magana? Matsa min tunda kai dama haka Allah ya
yika da shegen hak’uri, anason mutum me hak’uri amman ba irin naka ba.” Bin gefensa
tayi yana binta a baya suka shiga d’akin Zeezee alokacin harta rage kayan jikinta
ta ragar da vest da short zallah, koda taga Hjy Sadeeyah batayi niyan rufe jikinta
ba wayar hannunta ta cigaba da latsawa.

“In shi mijin naki ya saba ganinki haka don ni aikuma seki rufe jikin naki ko
ya?”
“Toh ai ba sallama akayi ba bale nasan da mutane akai na.”
“Ke Zainab! Ki kalleni ni zaki yiwa rashin kunya? Waye sa’anki anan?” Se
k’ok’arin janta baya Al’ameen yake a rayuwa inda akwai abinda ya tsana shine tashin
hankali. “No ka barni da ita tasamu waje ne ai, waye sa’an ki anan?”
“Aini ba rashin kunya nayi ba akan gaskiya ta nake naga nan gidan mijina ne duk
shirin dayamin zanyi amman haka kawai kizo gidana ki had’a kaina da mijina? Sanin
da haka ai tun farko nace bazan zauna a family house naku ba wallahi Allah ya isa
na, Allah ze sak’amin. Don kun ganni k’arama kuke d’aukan alhak’i na” tasa kuka
shark’af-shark’af kaman dagaske “kimin k’aninki yamin, in kinason Allah ki had’a
k’anin naki da Allah ya sakeni na koma gidan ubana nima inada gatana ai, dan ina
auran k’aninki bazaki tsaya kina gayamin magana son ranki ba kice mishi ya sakeni a
daren yau na koma gidan Baba na inhar kun isa ‘ya‘yen halak.”

“Enough ZAINAB!!” cewar Al’ameen a tsawace cikin wani erin kakkausar muryan da ba
wanda ya ta6a saninsa dashi apart from his soldiers se yau. Ba Zeezee kad’ai ba
harta Hjy Sadeeyah seda ta razana. “Hjy lets leave please let her be” da k’yar ya
ja Hjy waje akwatinta ta had’a tabar gidan at that instant saboda bazata iya ganin
‘yar datayi jika da ita ba tana gaya mata magana son ranta. Zama a parlour Al’ameen
yayi gabad’aya ya rasa meke masa dad’i, shin meyayi wa Zeezee take punishing nasa
haka? All he did was to love her. Yafi minti talatin a parlour sannan ya miqe ya
nufi d’akin nasu tana miqe akan gado ko uffan bata ce mai ba. “Tashi ki zauna
Zainab.” yayi ordering nata.
“In zauna kamin meh? Ka sake cin zali na?”
“Tashi ki zauna nace” yayi maganan in a serious tone da shegen tsoronta tuni ta
zauna “ki gayamin mena miki kika za6i ki wulak’anta sister na haka?”
“Ma har yanzu tambayana kake mekamin? Auro ni dakayi shine laifin daka min kuma
wallahi tallahi kaji rantsuwa ba kaffara inhar bakayi gaggawar saka na ba wataran
akan Mamanka ze fad’a.” Tsaye yayi wajen lost of words yana kallon Zeezee, abun
nata ba yarinta bane yanzu sarai tasan abinda take dagangan kawai take. Be iya yace
mata komi ba ya nufi d’akinsa inda ya kwana awajen ranan ma. Da safe ya shirya yaje
yasamu Hjy gabad’aya ranta ya 6aci ko kallonsa batason yi taya ze bari ‘yar yarinya
ta rainasa haka? Da girmansa. Dukda nature’nsa ne hakan hak’uri dakuma juriya amman
na Zainab is too much ita tsoronta befi Zeezee tasa ma k’aninta hawan jini ba tunda
be ta6a so ba se akanta. Ba yadda batai dashi ba kan ya saki Zeezee koda horata
zeyi, in mata ne tanada dubun da zata yimai amman yak’i bayi jin ze iya sakanta ya
lalata mata future at her very tender age ace tazama bazawara dukda de har yanzu da
budurcinta take amman ba kowa bane zesan da hakan bayan nan kuma yayi believeing
kan wataran komin dad’ewa Zeezee zata gano kuranta ta shiryu su fara zaman lafiya
shide baze gaji da farinta mata ba har se inda k’arfinsa ya k’are.

Tun lokacin wannan incident Al’ameen ya rage shiga harkan Zeezee as yanason ya
bata enough space ko hakan ze taimaka mata. D’akin nasu ma gabad’aya bar mata yayi
ya koma nasa inda yake kwana ya yini ciki. Ita ko wawiyar dad’i kasheta haka zata
hana kanta bacci da daddare tata waya ko video call da Adeel, atimes har abinda
take cewa da Adeel Al’ameen naji amman haka duk kalan kishi irin na soldiers dayake
dashi zeyi hak’uri ya danne zuciyarsa. Ana sauran sati biyu ya koma Abuja ya tahowa
Zeezee da sabuwar Ford Jeep nata fara k’al 2016 cikin ledarta.
Tana miqe akan gado as always da vest da nickers ya shigo d’akinta wanda baze
iya tuna when last yayi hakan ba “My Princess” yayi maganan cikin sark’ak’k’iyar
muryarsa. Ita kanta tayi missing sweet voice nasa “na’am” ta amsa.
“Kizo I have a suprise for you.”
“Takardan saki na ne? Inhar bashi bane save it banaso.”
“Yi hak’uri ki fito kinji? Seda ta gama 6ata mai lokaci sannan ta mik’e “muje”
tayi maganan tana mai dirty look.
“Toh kisa hijabi mana Princess kinfa san yadda gidan yake da maza kullum.”
“Toh ni nace kana kawo sune? Ai laifinka ne ga guards sannan ga ‘yan maula ni
gaskiya zafi ake banajin zan iya sa hijabi.” Da kansa ya nufi wardrobe nata ya ciro
hijabk ya miqa mata “yi hak’uri kisa sa” kaman bazata amsa ba sekuma ta kar6a tasa
tabi bayansa suna fita kawai taga sabuwar mota na mata sallama ita kanta bazata iya
descriing how motan ya birgeta ba amman dan ta k’untata mai ta dake “se yau motan
ya iso? Ina key’n?” Mamaki sosai tabasa wato ko d’an godiyan da take d’anyi adan ma
babu shi yanzu. “Gashi” ya miqa mata “My Princess ko motan be miki bane?”
“Me kaga?”
“Your face didn’t show and bakiyi godiya ba.”
“Daman don nayima godiya ka siyo? Ashe ba tsakani da Allah bane anyways kayi
kok’ari” tana kaiwa nan takoma ciki Lubiee takira tayita mata hauka kan Maj-Gen ya
sai mata Ford Jeep 2016. Lubiee de tun tana yiwa Zeezee wa’azi bataji har ya
zammana yanzu kawai sede tajita ta kad’a kai saboda Zeezee batajin magana kona
k’alilan.

*© MIEMIEBEE ™YGC!*
www.beeenovels.blpgspot.com
👄👄👄👄
[1/20, 9:01 PM]
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣7⃣
_Assalamu Alaikum, literally I don’t even know where to start from my family,
to friends, to fans, supporters, readers and to everyone who missed either my book
or me, know that I missed you guys as much and am so sorry for keeping you people
in such a non ending but now ended suspense and also that I can't reply back to
each and everyone of you that cared and stopped by to ask for me privately, or on
the blog or in groups or even tried calling me. The messages are over Alhamdulillah
I have such awesome people that care for me, nagode sosai for your maxi support,
care and love I love y'all oceans and galaxies❤❤. With your prayers, Allah ya dawo
dani safe and sound se muyi firing on da *™YGC*💞_

_2 days later..._
Ba inda Zeezee bata taka ba da sabuwar motarta a garin Bauchi tana bawa
mutane assignment. Duk mutan arziki sun taya ta murna barin ma Baba da Mama they
can’t ask for a better son-in-law than Al’ameen. They are sure ko bayan ransu ze
cigaba da kula da Zeezee, nasiha again Baba yata mata amman haka baiwar Allahn nan
ta ajiye mai abinsa a wajen da tazo tafiya.

_Afternoon hours..._
Kasancewar Al’ameen be ta6a jimawa haka a gari ba se wannan karan yasa mutanensa
da suke Bauchi duk suka soma hallaro gidan nasa suna zuwa yimai gaisuwa. Duk yadda
yayi dan kada su san yana gari abin ya gagara babban mutum kamanshi se a hankali.
Suna zaune da mutanen nasa a parlour yayi excusing kansa ya shiga d’akin Zeezee
alokacin ma waya da Adeel take wanda da sauri ta katse ganin Al’ameen. Kai kawai ya
kad’a yace da ita, “Zainab white rice nakeson ki dafa wa bak’in danayi sekiyi
slicing carrots akai dakuma peas da za’a sa akai kinji?”
“Kut! Nice zanma duka wannan aikin? Wallahi k’arya ne ni banida lafiya.” tayi
maganan cike da rashin kunya.
“Ki dafa white rice shine bakida lafiya Zainab? Bance fa zakiyi stew ba, na riga
nasa an siyo stew shinkafan kawai zaki dafa thats all.”
“Yo dama kace nayi stew’n mana in bakayi asaran kayan miya ba kuma ma wai su
abokan naka basuda mata ne kokuwa iskanci da son sa mutum aiki ne ke hanasu zama a
gidansu suci abinci se sunzo gidan mutane? Allah wadai d’in mutane kaman su wallahi
mschww.”
“Ya isa haka toh wuce kije ki dafa kiyi sauri.”
“Kuma wallahi in shinkafan be dahu yadda kakeso ba don’t blame me bani nace ka
kawo bak’i ba aikin banza.” Mayafinta ta taje ta fice mai, in less than one hour
shinakfan ya dahu yadda Al’ameen ya buk’ata sede ruwa yaso yi mata yawa kad’an
amman de tayi k’ok’ari. Ita bama haka taso ba, taso ace shinkafan yayi fate-fate
yadda ko a mafarki baze sake sata dafa mai abu ba.

A food warmer ta juye ta basshi a kitchen d’in sannan ta nufi parlour inda yake
zaune da mutanen nasa ta bisu da dirty look sannan tace, “Daddy kaje ga abincin
bak’in naka yayi.” Da mamaki friends nasan suka juyo suna kallonta taya zata kira
mijinta da Daddy? Ignoring this thought suka gaisheta kusan a tare dukansu tunda
ita tak’i gaishesu. “Ba gaisuwarku nake buk’ata ba ni, inda hali daga yau karku
sake zuwa gidana tunda kwad’ayin abinci ke kawo ku.” Tana kaiwa nan tayi d’akinta
binta da kallo duka sukayi wide in shock sannan back to Al’ameen “kuyi hak’uri dan
Allah, kuyi mata uzuri yarinya ce har yanzu.”
“Bakomai Maj-Gen Allah rufa mana asiri” cewar d’aya daga cikinsu. Haka dan kansa
yaje ya d’auko wa bak’in nasa abinci sukaci bayan tafiyansu ya tara plates yakai
kitchen. Banda kuda dake yawo suna bin wanke-wanke tun na shekaran jiya ba abinda
ke gudana a kitchen d’in. Beso ba amman dan dolensa ya nufi d’akinta be sameta ciki
ba kasancewar tana wanka zaman jiranta yayi. Kaman me haihuwa seda tayi spending
numerous minutes ta fito da towel nata iyaka tsakiyan cinyarta.

“Haka kawai ba sallama seka na fad’omin d’aki inda kuma ba komi a jikina na fito
fah?”
“Am sorry, in kin gama shiri kije ki rage wanke-wanken kuma its hightime ko sau
d’aya ne kibi gidan nan da shara Zainab, ko ke zama cikin dottin na miki dad’i sede
kiyita tsaftace jikinki amman banda na muhalli.”
“Look at who’s talking dan Allah” tayi maganan tana tafe hannu “bakason ganin
gidanka da dotti fine and good kana iya saka na right now ka auro wacce zatayi maka
wannan bauta. Kafa sani niba boyi-boyi bace bazaka na kawomin so called friends
naka suna taramin wanke-wanke ba and expect me to be washing the dishes for you,
uh-uh baka da wannan gatan Daddy.”
“Zainab mesa kike haka ne? Baki tsoron tsinuwan mala’ikun Allah ne ke? In ni ina
barinki sufa bazasu barki ba.”
“Ai tsoronsun yasa nake tambayar takarda na saboda in samu wanda zan na mai bauta
wanda nake so ba kai ba.”
“Naji bakiya sona but you can’t change the fact that am your husband koba haka
ba? Kije kiyi wanke-wanken nace” yayi maganan this time a bit tensed.
“Bazan yiba inma zan wanke se wanda nida kai mukaci abinci akai ba wanda
wad’ancan bak’in naka suka ci abinci akai ba in kanason ana maka wanke-wanke kana
iya kawo me aiki.”
“Naji zan kawo me aikin amman yanzu kije ki wanke na kitchen d’in in shaa Allah
zan d’auko miki me aiki.”
“Ma kanka de ba mani ba yanzu excuse me zan sa kaya.” Be sake cemata komi ba ya
fice. Nan da nan tagama shiri tafito kitchen kenan taji an danna door bell tana
dubawa taga Mama salati kawai tahau yi har anan Al’ameen na zaune a kan sofa be
motsa ba. “Ki bud’e k’ofan mana Zainab waye ne? ”
“Mama ce nawa ya k’are!” tayi maganan hankali a tashe. Murmushi me sake k’ayatasa
ya saki seda dimples nasa suka lotse sosai sannan ya kad’a kai ya kawar da kansa
daga kallonta. “Aww ma dariya kake min ko? Mugu kawai, mutum babba amman wai da
dimples mschw” Da k’yar ta bud’e k’ofan atare ita da Al’ameen suka yima Mama sannu
da zuwa. Drink da snacks ta kawo tayi serving Mama dashi.

“Ai na d’au ma ko ka koma Abujan ne Maj-Gen.” Maa tayi maganan tana cin kad’an
daga cikin cin-cin dake gabanta.
“A’a wallahi se next week in shaa Allah.”
“Toh Allah ya kaimu, bazan gaji da maka godiya bafa naga sabuwar motar da ka sai
wa Zeezee Allah k’ara bud’i mungode sosai.”
“Ba komai Mama an zamo d’aya ai yanzu, barin shiga ciki toh.”
“Nazo na koreka ko? Kayi zamanka de zamu shiga ni da ita.”
“A’a please kuyi zamanku anan” yana kaiwa nan ya fice. “Ke kin mai godiya kuwa
daya sai miki motan?”
“Nayi mana Mama nayi sosai ma.”
“Toh ki rik’e mijinki hannu bibbiyu Zeezee aljannarki a tafin k’afafunsa yake ba
a nawa ba yanzu duk lokacinda ya nemi had’a kwanciya dake karki hanasa sannan duk
abinda kika san bayaso ki kiyaye wanda yakeso kuma kina mishi kina jina ko?”
“Eh Mama inayi sosai nagode.” Hira kad’an suka ta6a can Mama tace zata kai plate
nata kitchen nan Zeezee ta dage atapir ita zata kai mata sanin kitchen natan bamai
ganuwa bane. “Kibari mana meh haka? Bak’uwa ce ni?”
“A’a amman kibari zan kai da kaina.”
“Matsa min da Allah kaman dagaske.” ta tureta ta shiga kitchen d’in, baki kawai
ta sake wide in shock tama kasa believing abinda idanunta ke gane mata. “Ke! Me
wannan? Kitchen d’in mahaukaciya komeh?”
“Mama wallahi nad’anyi rashin lafiya ne kwana biyu shiyasa wanke-wanken ya taru.”
“K’arya zakiyi min? Ba two days back bane Maj-Gen ya sai miki motan kika rik’a
fita yawo anyhow shine zaki cemin bakida lafiya iyyeh?” Mari lafiyayye Mama takai
mata a baya. “Rashin hankalin da kikeyi agidan naki kenan ko wanke-wanke bakiyi?”
K’walla na cika a idonta ta kad’a kai “wallahi a’a da Allah karki gayawa Baba
wallahi ze kasheni.”

“Me ze hanani gaya mishi? Ke bazaki ta6a shiga hankalinki bako? Wannan wanke-
wanke tun na yaushe?”
“Mama wallahi be jima ba kuma yau ma nakeda niyyan wankesu, MP ne ya sani gaba
shiyasa.”
“Na yaushene nace? Bazaki amsa bane? Kuma wallahi kimin k’arya kiga inban kira
Maj-Gen. ba na tambayesa, na yaushe ne nace?!”
“Wallahi na shekaranjiya ne.”
“Innalillahi! tun shekaran jiya? Yanzu na shekaran jiyan ne be jima ba? Ma’ana
har na sati kina tarawa kenan ko?”
“Wallahi a’a Mama wannan d’inma sharrin shed’an ne” Ajiye cup d’in Mama tayi ta
jawo hannun Zeezee sannan ta shiga kai mata mari kota ina, ihu Zeezee ta shiga
rusawa har seda Al’ameen ya fito da mamaki yayi sauri ya k’wato Zeezee yana bawa
Mama hak’uri.
Kama shirt nasa Zeezee tayi gagam tana b’oye jikinta a bayansa. “Ni zakiyi wa
abin kunya iyye? Kalan tarbiyyan dana baki kenan, tunda kike kin ta6a ganin wanke-
wanke ya kwana a gida na dake zaki bar har na shekaran jiya? Maj-Gen in kanayi wa
Allah dan Allah ka fita kabarni da wannan maras kunyan.”
“A’a Mama dan Allah kiyi hak’uri duk beyi zafi haka ba ita kanta tanada niyyan
wanke dishes d’in yau.”
“Aww ai dama nasan kai kake d’aure mata gindi, haba Maj-Gen. kai da ya kamata ka
gyara mata zama se kuma ka zuba mata ido tana rashin hankali iya son ranta gaskiya
am very disappointed in you. Wannan abu dame yayi kama?”
“Kiyi hak’uri Mama.”
“Ka gayamin bayan wannan wani rashin hankali kuma take again?” Shirt nasa Zeezee
ta shiga tukiukuyawa tana mai nufin kar ya tozarta ta.
“Babu wannan ne kad’ai kuma shima zata gyara ko Zainab?” Tana riqe da shirt nasan
ta gyad’a kai “eh eh wallahi.”
“Zan samo mata me aiki ma tana taimaka mata tunda gidan yayi girma da yawa.”
“Me aiki?” exclaimed Mama. “Wallahi bame aikin da zaka nemo ma wannan ‘yar, shara
da mopping d’inne shine se an nemo mata me aiki? Da wanke wanken da befi a k’irga
ba? Inhar kana k’aunan Allah kaja baya da wannan zance, ban yarda ba. Koda wasa
karka d’aukan mata me aiki, kajini ko?”
“Naji Mama amman-”
“Don Allah nace Maj-Gen kai wai bakasan halin Zeezee bane? ka fara mata da haka
by the time kuka zo kuka haifafa fah? Ya gidan naku ze kasance tunda yanzu da take
‘yar amaryarta ma baka barinta tayi aiki.”
“Toh Mama za’ayi kaman yadda kikace kiyi hak’uri.”
“Yauwa yanzu inason kabani waje kuma kabarni da ita kad’ai.”
“A’a Ya Al’ameen dan Allah karka fita wallahi dukana zatayi” Zeezee tayi maganan
tana sake matsesa a jikinta.
“Mama please kiyi hak’uri karki ta6ata zatayi wanke-wanken.”
“Naji bazan ta6a ta ba ka fita to mu samu mu had’a kitchen d’in.”
“Ya Al’ameen wallahi kafita duka na zatayi.” Seda Mama tayi dagaske tasamu ta
fito da Al’ameen. “Maza kama yin wanke-wanken wawiya kawai.” Nan da nan Zeezee ta
shiga washing dishes d’in sama-sama kaman yadda ta saba ashe duk kallonta kawai
Mama take, ta gama zata fara jerawa Mama tace, “dawo dawo dasu nan” cup d’aya ta
d’aga ta shafa jikin se maik’o kawai malam sekace be shiga cikin ruwan kumfa ba.
Lafiyayyen mari Mama ta kai mata a baya kafin tasa ihu Mama ta aza hannunta akan
lips nata tana mata alaman tayi shiru. “Wallahi kika bari Maj-Gen ya fito kinji na
rantse sena gayawa Babanki har nan ya biki ya baki d’ankaren duka” jin haka ta
had’iye ihun nata tare da shanye hawayen nata.

“Hakane kin wanke? Bazaki bar aikin cuwa-cuwan nan da kika saba bako? Kanki ma
yanzu zaki cutar tunda tun chan agida haka kikeyi.” Mama na tsaye a kanta Zeezee ta
sake bin wanke-wanken seda suka fita k’al sannan ta share kitchen d’in tayi mopping
ta goggoge kan counter dasu gas cooker and microwave. Bayanta kan ze 6alle, tunda
tasan kanta bayan aikin wankin da Ya Ibraheem ya ta6a sata bata sake aikatuwa kaman
na yau ba. “Shara fa kinayi?”
“Mama dan Allah kiyi hak’uri ki tafi gida wallahi nayi shara yau bayana yana iya
6allewa.”
“Ma’ana bakiyi kenan?”
“Zan fara gobe dan Allah kiyi hak’uri.”
“Maza d’ago tsintsiya ki bini ashe ba sharri idona suka miki ba tun shigowana na
karanci gidan naku da k’ura” haka Zeezee tana tura baki tana matse k’walla tabi
bayan Mama, kap gidan ranan seda Mama ta sata ta share ta kuma yi mopping harda
dusting sannan tabi gidan duka da turaren wuta. Tanayi tana kuka amman hakan besa
Mama ta k’yaleta ba.
“Wayyo Allah zan mutu!” tayi maganan baje akan tiles tana riqe da bayanta.
“Tashi kije ki kiramin Maj-Gen. d’in.”
“Mama wallahi bazan iya tashi ba.”
“Aww na saki share cikin gidan naki kenan ko?”
”A’a zan tashi zan tashi” tana bud’e d’akin nasa ta tarar dashi akan laptop yana
aiki “wai kaje Mama na maka magana.”
“My Princess ya haka da riqe baya?”
“Ban sani ba ai wallahi ka kyauta nikan kazo.” Bayanta yabi suka fice akan kujera
opposite na Mama suka zauna “gani Mama.” yayi maganan gentlemanly.
“Yauwa Maj-Gen ka bud’e kunnuwanka da kyau ka saurareni don Allah nace.”
“Toh Mama.”
“Take a look at your house now what can you say?” Yadda Mama ta buk’acesa yayi.
He couldn’t believe it ko ina se sparkling yake ga k’amshin turare na tashi. A
rayuwa yanason yaga muhallinsa da tsafta kaman haka “wow” yayi breathing “its
sparkling yayi kyau sosai.”
“Good toh haka nakeson gidanka ya kasance a kullum, alk’awarin abu d’aya nakeson
kamin, ka tabbata ko wani safiya Zeezee tayi shara tayi moppkng after each 3-4 days
kuma tayi dusting, wanke-wanke kuma ban yarda wanke-wanke ya kwana a gidanka ba
inba wai rashin lafiya take ba. Kar ya zamana takai sati bata wanke muku toilets
ba. Zancen me aiki kuma banason ka d’au ma Zeezee me aiki dukkanin aikin nan dana
lissafo ita nakeson tanayi can I count on you?”
“Uhmm Mama you see-”
“Bazaka iya min ba kenan?”
“A’a bawai haka bane-” saurin katsesa tayi “then can you promise me all that?”
“Yes Mama, I promise in shaa Allah.” wani mugun kallo Zeezee ke binsa dashi
sannan ta sauk’a har k’asa tana kukan munafirci “Mama dan Allah kiyi hak’uri
wallahi inhar na cigaba da aikatuwa haka kullum wataran gawa na zaku cire daga
gidan nan, kiyi hak’uri dan Allah kibar Ya Al’ameen ya d’aukomin me aiki I promise
tare zamuna yin aikin da ita Allah wallahi.”

“Zainab banason sakarci kina jina koh? In kinga Maj-Gen. ya d’au miki me aiki toh
wallahi se in kin haifafa hidiman yara ya fara miki yawa, kana jina ai Maj-Gen?”
“Eh Mama naji.”
“Good ke kuma addu’a zan yita miki Allah shiryeki don zagi bashida amfani, amman
kisani duk ranan da garin Allah ya waye baki aikata wannan aiki dana lissafo ba
bakuma dan wani k’wararren dalili ba Allah ya isa na yana kanki.”
“A’a Mama please, kiyi hak’uri in shaa Allah ma zata nayi ba sekin ja Allah ya
isa ba.” cewar Al'ameen.
“No ka barni da ita nasan halinta sarai ina barin nan bazata sake d’aga tsintsiya
ba tunda kai na lura baka mata magana.”
“Kin jini ko bakiji ba?” Shiru Zeezee tayi not ready to talk.
“Aw in kira Babanki na fad’a
mishi.”
“A’a wallahi naji, naji karki kirasa dan Allah” tayi maganan fear na building a
tare da ita. Da mamaki Al’ameen ke kallonta ashe duk rashin kunyarta tanada weak
point, da kyau. Hak’uri Mama ta sake bawa Al’ameen akan rashin hankali irin na
Zeezee sannan kuma a gabansa tayita yiwa Zeezee fad’a sosai sannan ta bisa da
nasiha.
Bada jimawa ba tace zata tafi wanda Al’ameen yasa driver’n sa yayi dropping nata.
Tana tafiya Zeezee ta zarce d’akinta tana me rusa kuka tsakaninta da Allah yanzu
shikenan ita hutunta ya k’are kenan? Kukan ta cigaba dayi koda Al’ameen ya ganta be
mata magana ba sabida yasan theres no point doing so in banda rashin kunya ba
abinda zata masa don haka ya zarce d’akinsa shima.

*~ *~ *~
Washegari Zeezee ta tashi da sassafe ta gama ayyukanta tas, ji take wane bayanta
ze 6alle dan azaba. Al’ameen na fitowa yaga ko ina sparkling clean ga kuma k’amshin
turare d’akin Zeezee ya nufa ya sameta miqe kan gado tayi ruf da ciki. A nitse ya
k’arisa ya zauna kan side drawer nan ta juya mai baya. “My Princess?”shiru ba amsa,
“My Princess sannu da aiki kinji? Everywhere is sparkling clean ga wannan tukuicin
aikin da kikayi.” ya ajiye mata bundle na N50.
Juyawa tayi don ganin meye tukuicin tana ganin kud’in ta d’aga bako kunya.
“Bayanki na miki ciwo ne?” Kaman bazata amsa saba se kuma ta gyad’a kai. “Do you
need a massage?” Tana so tana kaiwa kasuwa “ni banaso kafita min daga d’aki ai duk
kaine.”
“Yi hak’uri toh.”
“Ni kafita min.” Besake ce mata komi ba ya miqe, ya kaiga bakin k’ofa ta tsayar
dashi “kazo kamin wallahi bayana kaman ze 6alle” murmushi kawai ya saki yana
kallonta da take rage kayan jikin nata, bajewa ta sake kan gadon tana jiran ya fara
mata tausar. A hankali taji sauk’an hannunsa akan bare back nata, take heart nata
yayi skyrocketing ita kanta ta rasa dalilin da yasa every single touch na Al’ameen
yakeda strong influence akanta.
Massaging mata baya ya shiga yi a hankali wanda don dad’i har wani bacci Zeezee
ta soma ji, hakan ya cigaba da mata har seda tayi bacci. Kwanciyarta ya gyara mata
sannan yaja comforter ya rufeta da shi tare da rage speed na AC’n tunda batada
kaya. Dawowa yayi ya zauna akan side drawer yana k’are mata kallo a yayinda wani
irin wutan sonta ke sake ruruwa a zuciyarsa, he can’t wait for the day Zeezee
zatayi accepting nasa as her husband, surely that day will come shiyasa baze gaji
da trying to make her happy ba. What a gentleman!

Hannunsa ya d’aga a hankali ya aza akan fuskarta yana shafawa sam bata motsa ba
seda yaja hancinta. Hannun nasa ta kama tasa k’ark’ashin kumatunta duk a cikin
baccin, ta sake kuma tak’i ta sake hakan ya sanya Al’ameen murmushi sosai. Haka ya
cigaba da zama a wajen yana k’arewa beautacious innocent while at sleeping face
nata kallo, da k’yar ya samu ya iya ya zare hannun nasa tare da pecking forehead
nata yayi whispering “I love you Princess” sannan ya fice.

_5 days later..._
Gabad’aya rayuwan kanta tabar yiwa Zeezee dad’i dalili kuwa shine wannan aiki da
Mama ta aza mata shi na dole, domin haka tayi coming up da plan. Tana idar da
sallan Asuba yau ta d’au towel ta tsoma cikin warm water sannan ta mammatsa a
jikinta seda ya d’au zafi. Tana jin dawowan Al’ameen daga masallaci ta ruga gado ta
kwanta tare da jan comforter ta rufe duka jikinta dashi harda kanta ciki tana
kakkarwa. Not long enough ya shigo d’akin nata as usual don duba ko tayi Sallah
tunda yanzu ba kwana d’aki d’aya suke ba.
“Princess kinyi sallah?” Yayi maganan some inches away from her bed har anan
bata motsa ba. “Zainab?” Cike da kasala wane wacce batada lafiya ta leqo da
fuskarta waje “Ya Al’ameen...” Ta fad’a cikin wani irin muryan dake nuni da mutum
baida lafiya.
“Subhanallah! Princess are you okay?” Ya k’are maganan yana zaune akan gadon a
gefenta. “Meke damunki Princess?”
“Zazza6i nakeji.”
“Zazza6i?” Ya miqa hannu tare da feeling body tempreture’nta extremely high ya
jisa. “Subhanallah! Princess you are sick, sannu kinji?” Wutan d’akin ya kunna ya
shiga toilet tare da fitowa da bowl cike da ruwan sanyi kad’an. Matsa mata jiki
dashi ya shiga yi da towel d’in idan ya tsoma cikin ruwan. Ahaka har fake hot
tempreture’n nata ya sauk’o se kukan shagwa6a take ta mai.

“Sannu kinji? First thing in the morning za muje asibiti, sannu koh?” Comforter
yaja ya gyaggyara mata kwanciya, ya miqe ze fice kenan ta riqo hannunsa “Ya
Al’ameen Mama nakeso, dan Allah ka kaini wajen Mama ita kad’ai zata iya taking care
of me.”
“Toh karki damu sleep now, later on semu kaiki gida kinji?” Dad’i kasheta finally
her plan has finally worked out! Kai kawai ta gyad’a mai kaman dagaske. Yana barin
d’akin tahau daka tsalle sauk’a tayi daga kan gadon tare da jan d’aya daga cikin
trolleys nata tahau had’a kayakinta ciki. Ai ba jaka bace ita da zata riga shara
kullum tana dafa farin shinkafa, spaghetti kokuwa macroni wa bak’in Al’ameen gwara
taje gida chan ta huta abinta.

*© MIEMIEBEE ™YGC!*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
[1/20, 9:01 PM]

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*January, 2017*
3⃣8⃣

_09:34AM_
Zeezee ta gama shiri tsaf sekace wacce zata gidan biki. Tana kan pancaking face
nata Al’ameen yayi knocking bisa k’ofa tare da shigowa “My Princess har kin shirya
ne? I thought kina bacci ai.”
“A’a na tashi since.”
“Jikin da sauk’i kenan.”
“A’a wallahi kawai de na dage ne yanzu haka kaina ciwo yake min just now nayi
amai ma.”
“Subhanallah sannu ko? Muje mu karya toh muje asibitin yaso daga chan se nayi
dropping naki a gida zuwa Maghrib na d’auko ki.”
“Wai kai ka d’au yini kawai zanje inyi? Rashin lafiya fa nake” akwatinta ta
fiddo daga lungu “ina kuma zakije da wannan?”
“Gida mana.”
“Lafiya daiko?”
“Kaman ya lafiya zanje gida Mama ta kula dani mana.”
“Zainab yanzu sabida fever’n da be kwantar dake ba shine zaki had’a akwati zaki
gida?”
“Kamar ya be kwantar dani ba? Dan ya d’an sakeni yanzu sekace haka? Ai zuwa
anjima ze dawo.”
“A’a baza ayi haka ba, tunda ina gida i’ll take care of you yanzu muje asibitin.”
Bajewa tayi k’asa gun tahau rusa kuka haka kawai ze kama yayi mata ruining plan
wallahi k’arya ne. “Wallahi ni se ka kaini gida, ni Mama nakeso ba kai ba wayyo
Allah!!” Ihu ta cigaba dayi wajen tana kururuwa a yayinda yayi tsaye wajen kawai
yana mamakin yarintarta.

“Is okay toh naji tashi mu kaiki gidan bar kukan haka.” Hannu tasa ta share
hawayenta “anya kuwa Zainab ba faking rashin lafiyar nan kike ba?”
“Kaman ya faking? Ana k’aryan rashin lafiya ne? Kai kanka fa kaji yadda
tempreture na yahau d’azu Allah banida lafiya.”
“Toh get well soon.”
“Yauwa kuma ni bazan je wani asibiti bafa Mama zata kula dani.”
“As you wish lets have breakfast” nan da nan suka karya aka fito mata da
akwatinta, acikin mota Al’ameen ya kalli Zeezee daketa buga Candy Crush a wayanta
sannan yace, “Princess sekuma yaushe zaki dawo?”
“Idan fever’n yayi sauk’i kaman nanda one week haka.”
“Har one week?”
“Wani har nema? Dan bance zanyi wata ba?” Bada dad’ewa ba suka isa gidan nasu. An
bud’e mata k’ofa ta fita kuma seta k’i. “Any problem?” Ya tambayeta.
“Yanzu na taho gida bazaka d’an bani kud’i na rik’e a hannu na ba?”
“Yaushe ne na baki 20k Zainab?”
“Ni ba abinda na tambaya ba kenan in kud’in ne bazaka bayar ba shikenan.”
“Toh ni ban fito da kud’i ba” sarai da akwai kud’i a pocket nasa dakuma motar ma
in whole amman baze bata ba tunda rashin kunya tasa a gaba.
“Kar Allah yasa ka bayar d’in.” Buga masa murfin motan tayi wane zata 6alla
sannan guard yabita da akwatinta ciki, binta da kallo Al’ameen yayi tare da kad’a
kai.

****
Koda ta shiga ciki bata tarar da Mama ba saboda ta fita unguwa ana sunan ‘yar
k’awarta. Sallama tayi Baba dake shirin fita kasuwa ya fito “a’a K’anwata ya da
akwati? Lafiya dai ko?”
“Ina kwana Baba?” tayi maganan wane maras lafiya tare da tsugunawa har k’asa.
“Amsani de tukun meya faru?” acewarsa ma sakinta Al’ameen yayi, his biggest
fear.
“Lafiya k’alau Baba nice bana jin dad’i zazza6i yasani gaba chan kuma bame bani
kulawa Ya Al’ameen kullum bai gida shine yayi suggesting nazo nan nad’an huta.”
“Toh hakane? Amman don zazza6i shine har sekin dawo gida K’anwata?”
“Toh Baba bazan iya kula da kaina ba yanzu haka daga asibiti muke ammin allura.”
“Wai wai har allura? Sannu K’anwata sannu, k’ariso ciki toh.” Da kansa yaja mata
akwatinta (iyayen d’aure ma k’arya gindi ba.) Bada jimawa ba ya fice kasuwa nan
Zeezee ta samu kanta. Waya tahau yi da Adeel kaman ba gobe. Harda La’asr ba wanda
yadawo cikin su Baba. Se chan 5:46pm Mama ta dawo gida all exhausted ganin Zeezee
tayi a kitchen tana soya k’wai aikin kenan kullum, kafin tace zata 6oye plate d’in
har Mama ta ganta. “Zainab!”
“Na’am Mama sannu da zuwa.”
“Sannu de tun yaushe kike nan?”
“Tun safiya fah Baba yace kin tafi gidan suna.”
“Eh wallahi Fateey’n Maman Fateey ce ta haihu.”
“Ayyah sannu da zuwa, arghh! wayyo kaina!” Tayi faking exclamation.
“Me kuma ke damun kankin?”
“Oh! Ban fad’a miki ba ko? Wallahi zazza6i ne yasani gaba for the past three (3)
days shine Ya Al’ameen yace na taho gida zanfi samun kulawa.”
“Ban fahimci wai kidawo gida ba wai kina nufin harda akwatinki?”
“Eh toh achan bame kula dani.” Tafe hannu Mama tayi in suprise tana mamakin gut
irin na Zeezee “yanzu don zazza6in k’aryan da am sure kika k’irk’iron shine kika
dawomin gida da zama?”
“Mama wallahi ba k’ar-”
“Rufa min baki” ta katseta da wuri, “ni zaki raina ma wayo ko jinki bansan wannan
d’an banzan halin da kuke developing bane ‘ya‘yan yanzu? Da zaran kunga kun fara
aikatuwa a gidan aurenku seku d’ibo k’afa ku dawo gida da sunan wai bakuda lafiya
ko ba haka ba? To ki bud’e wannan kunnuwan k’ashin naki ki saurareni da kyau
wallahi ba a gidana za’ayi wannan iskanci ba kina jina ko? A da dabaki fara su
shara ba ai baki ta6a cewa bakida lafiya ba se yanzu. Maza-maza ki had’a kayakinki
kiyima Maj-Gen waya yanzu ya turo a d’aukeki.”
“Mama wallahi ba haka bane Allah banida lafiya ai Baba ma yaga shigowa na kuma
ya amince na zauna anan har sena samu sauk’i.”
“Babanku kam dama ai komi ma amince miki yake tunda shi har yau be koyi darasinsa
ba, maza ki kira Maj-Gen ba a gidana za’ayi wannan sakarci ba wallahi, kin ta6a
ganin Mariam ta dawo gida da sunan bata lafiya ne? Koda ta haihu batace zata dawo
gida ba nice naje na sameta mesa baza kiyi koyi da yayyun ki ba? Bazaki motsa
bane?”

Kuka Zeezee tasa gun ita a dole batada lafiya. “Wai jiranki nake ne?” Tana
tsugune gun tana ta k’irk’iro kukan k’arya tace, “wallahi Mama banida lafiya ki
kira Ya Al’ameen ki tambayesa abinda har allura mun d’auka min.”
“Wato se kinji na jaki zaki tashi ko?”
“Wallahi Mama banida lafiya dan Allah kibarni na zauna anan, ina warwarewa zan
koma gida na.” Ana cikin haka Baba da Omar suka dawo suka samu su Mama in the act.
“Sannu da zuwa Alhj, Omar sannu.”
“Yauwa sannu Mama.”
“Sannu Hafsah meke faruwa haka kikasa patient agaba?”
“Patient? Wace patient d’in?”
“Zeezee mana ko bata gaya miki ba tada lafiya bane?”
“Baba wallahi na gaya mata wai sam k’arya nake.”
“Ai k’aryan nema, rashin son aiki yasa kika gudo nan koba haka ba?”
“Wallahi ba haka neba.”
“Haba Hafsah! Ana k’aryan rashin lafiya ne? Kuma munyi waya da shi mijin nata ma
ya shaidamin batada lafiya.”
“Yo Maj-Gen kam ai dama haka zece maka tunda Zeezee tafi k’arfinsa amman wallahi
‘yar nan k’alau take.”
“Allah banida lafiya.” Omar dake tsaye wajen yana kallonsu don kansa ya nufi site
nasa saboda shima yasan k’arya Zeezee take.
“Ya isa haka Hafsah tunda ba’a kanki ‘yar nan zata kwana ba, ba ruwanki musamman
mijinta ya kawo ta saboda batada lafiya kice k’arya take?”
“Nikuma kaji na rantse da Allan da raina ke hannunsa baza ayi wannan rashin
hankali a gida na ba, wani rashin lafiya ne anan yarinya duk tayi kumatu saboda
yadda takejin dad’i a gidan miji amman don rashin son aiki ta gudo wai batada
lafiya? Wallahi bazan bari ba yanzu, yadda ka lalata tarbiyyan yarinyan nan ada
kayi ma yanzu, Zainab zata koma gidanta ko tana so ko bataso ni na gaya maka.” Ta
k’are maganan in a serious tone sosai tabawa Baba mamaki be ta6a jinta tana d’aga
murya haka ba hakan na nuni da yadda ranta ya matuk’ar 6aci kenan.
“Me yayi zafi haka Hafsah na? Yi hak’uri mana” yayi maganan in a soothing tone.
“Ai ba zancen hak’uri bane ‘yar nan bazata kwana gidan nan ba.”
“Naji toh yi hak’uri kinga Maghriba ya riga yayi yanzu kiyi hak’uri kibarta ta
kwana nan yaso gobe da safe seta koma chan gidan nata. In rashin lafiyan ya sake
tak’urata yaso sekije ki sameta ko?”

“Har se gobe ta koma gida? A yau d’innan zata koma, yarinya sam batasan ciwon
kanta ba ke bakisan da haka zakiyi creating space wa Maj-Gen. ya soma kula matan
waje bane? Saboda time da ya kamata kina tare dashi baki nan as kinzo nan kina
faking rashin lafiya ni na gaya miki a gobe zaki koma gidanki aikin banza kawai.”
Mama na kaiwa nan ta fice, kuka Zeezee ta shigayi shikenan Mama ta rusa mata plan
nata yanzu haka zata koma ta cigaba da bauta wa Al’ameen? Wayyo ita.

Hak’uri Baba yata bata da alama har ya mance da kalan rashin hankalin da Zeezee
tamai a baya be koyi darasinsa ba har yanzu. Zeezee na kwance a d’akinta se turo
baki take gabad’aya ji take kaman ta gudu taje somewhere tasamu Adeel nata. Video
call da sukazo sukayi da Adeel nema ya d’an farinta mata rai.
Kafin Al’ameen ya kwanta seda ya kirata don yi mata ya jiki amman dake a cike
dashi take, gani take duk laifinsa ne yasa ko d’aga wayan ma batayi ba.

*~ *~ *~
Washegari tun 8am Mama ta kira Al’ameen da kanta ta buk’acesa da ya turo
driver’nsa yazo ya d’auki Zeezee maza-maza kuma koda wasa kada ya sake bari ta baro
gida inhar Zeezee batada lafiya ne dagaske nan gaba ita da kanta zataje ta zauna
akanta, fad’a sosai tamai da yadena zubawa Zeezee ido tana abinda taga dama yana
mata fad’a sede shi yana ganin baze iya ba, ansan soldiers da fad’a da zafi but
when it comes to their loved ones they are damn sweet, calm and quiet!
Tara saura driver’n Zeezee ya iso, sam bata so tafiya ba. Fad’a Mama tata mata
kaman ba gobe.

***
Su Zeezee suna isa gida tafito daga motar a fusace not minding ta rufe k’ofar,
zaune bisa dining table yana having breakfast ta tarar da Al’ameen, wani d’an
banzan harara ta watsa masa sannan ta nufi d’akinta direct inda ta baje tayita kuka
kaman ba gobe. Seda tayi ta godewa Allah sannan ta nufi bayi ta wanke fuskanta
tafito ta zauna bakin gado tana tunani ya zatayi tasa Al’ameen ya saketa, shin wani
rashin hankalin zata mai da zesa ya rabu da ita? Gabad’aya ta shiga damuwa yanzu
saboda yadda Adeel kece mata bata damu dashi ba yanzu don kuwa da tayi da tuni ta
kashe auran nata (wa'iyya zubillah!) Dabara ce ta fad’o mata, wata maqirar murmushi
ta saki. A ranan gabad’aya word be had’ata da Al’ameen ba saboda ko shiga d’akinta
beyi ba shima.
Washegari bayan ta k’are chores nata sun karya Al’ameen ya shirya tsaf sannan
yazo yayi mata sallama kan ze fita ko ta kansa batayi ba banda dogon tsukan data ja
mai. Yana fita taja mayafinta itama ta nufi gidan k’awarta Hajar datayi aure
recently, bayan ta fayyacewa Hajar plan natan tayi promising nata 100k inhar tabata
had’in kai suka gudanar da wannan plan, kasancewar Hajar money monger ce tuni ta
amince.

_2 days later..._
Ana sauran kwana hud’u Al’ameen ya koma ABJ, yana zaune a parlour as usual
yana kallon sports aka danna door bell yana dubawa yaga bak’in fuskoki guda biyu
amman sede yana da tabbacin k’awayen Zeezee ne. Ya bud’e yayi musu sannu da zuwa
sede meh? Take Hajar tahau sa da tsiwa “ina matar taka take? Wallahi ta fito ta
biyani kud’ina ai ba haka mu kayi da ita ba, kota ban kud’i na kona kai k’aranku
duka police station tunda kaine mijinta.”
“Wait, wait what is going on here guards!” Take suka mammatso “kunsan wannan
faces?” ya tambayesu in an authoritative voice.
“No Sir sunce mana de k’awayen Madam ne.”
“And mena ce muku about letting strangers in?”
“We are very sorry Sir but they told us they are friends.”
“It shouldn’t repeat itself, am I clear?”
“Yy.. Yes Sir thank you” sukayi saluting nasa tare da ficewa.
“Baiwar Allah kode kinyi 6atan kaine?” yadawo da kallonsa akan Hajar dake ta
admiring kyansa ita bama wannan ba muryansa ne ke tafiyar mata da imani, me bawan
Allan nan ya rasa da Zeezee ke neman ya saketa? Ai ita wannan ma ya fiye mata Adeel
wallahi, dake wa tayi;
“Ba wani 6atan kai ko ba nan bane gidan Maj-Gen Al’ameen me mata Zainab?”
“Nan ne nine ma maigidan.”
“Good so nake ka fito min da matarka ta biyani kud’i na wallahi.”
“Kud’i you mean kina bin Zainab bashi? Since when?” yayi maganan damn suprised.
“3 weeks back.”
“Subhanallah, nawa kuma?”
“500k.”
“What?!” yayi exclaiming jaw dropped.
“Ai ka jini de kuma ba sharri nake mata ba wallahi tafito taban kud’i na ace
babban mutum kaman ka amman kabari matarka tana cin bashi awaje Allah wadai
wallahi, nide aban kud’ina konayi kururuwa in tara maku jama’a.”
“Ko kinsan a gidan soja kike kike wannan batu? And how can you accuse my wife?”
“Aww ma tambaya kake? Zainab!” ta shiga k’wala wa Zeezee kira “Zainab kifito
nan.” A farko Al’ameen yayi niyyan yasa guard nasa suyi mai waje da Hajar da
k’awarta amman ganin yadda ta dage kan sam wallahi da akwai bashinta gun Zeezee ya
shiga duhu shin har yaushe Zeezee taci bashin 500k besani ba? Wani irin kud’i ne
bai bawa Zeezee da zata nemi ta tozarta sa a idanun jama’a da girmansa da komi zata
mai haka meya mata? A gaban k’ananun soldiers nasa bujakai wanda basu kai sun kawo
ba sun tsaya suna gaya mai magana gaskiya abin Zeezeen kuma ya soma yin yawa “ina
zuwa” kad’ai ya iya ce dasu sannan yaje yasamu maqirar zaune kan gado, yi tayi
kaman bata da masaniya kan abinda ke faruwa.

“Zainab?”
“Meh? Menayi kuma yanzu?”
“Shin dagaske ne kin ranta bashin 500k gun k’awarki baki biya ba?”
“Sosai ma kuwa anyi haka.”
“Sabida mesa?”
“Kaman ya sabida mesa? Baka bani kud’i ishasshiya ba ba dole naci bashi ba.”
Magana ya soma a fusace sabida ransa ya matuk’ar 6aci, bayason abinda ze ta6a masa
suna.
“What nonsense Zainab? wani irin kud’i ne ban baki ba? White gold naki be 6ata
ba kince ya 6ata na sai miki sabo, I heard you the other day on the phone kina
ciniki zaki siyar da shi duk ban miki magana ba, yanzu kuma seki nemi tozartani ki
6atamin suna agari ace babban mutum kaman ni nabar matana tana cin bashi a gari?”

“Wow! Wow!” Ta tahau yin tafi “I like where this is going finally kafara fighting
back ai da hakan kakeyi tunda a baya da warhaka mun tarwatse, bakason sunan ka ya
6aci a agari? Fine and good seka bani takarda na yanzu-yanzun nan ko minto d’aya
kada ka k’ara aikin banza kawai baka bani kud’i ba ya kakeson nayi? Ko ka ta6ajin
Baba yace maka naci bashi lokacinda nake gidan shi ne? Kai ka d’aukoni ka kawo ni
nan dole kayi hak’uri da dukkanin abinda zan maka kuma believe me this is just the
start wallahi I will never rest until da hannunka ka d’au takarda na ka miqa min
mschwww!”
“Haka kikace?”
“Ai hakan nema, ko ka biyasu kud’insu kokuwa ka sakeni Baba na ya biya min tunda
ba matsiyaci neba shi.”
“Ya miki kyau” kad’ai yace mata sannan yaje ya rubuta wasu Hajar cheque na 500k
tare da basu hak’uri on behlaf of Zeezee.

Su Hajar suna isa gida tama Zeezee waya “Babe ga cheque nan fa har Ogan naki ya
bamu.”
“Aikinki yayi kyau gobe zan taho miki da 100k d’inki.”
“Toh ya yanzu? Yace ze sake kin?”
“Wannan mayyen? Ai inba maqora na kaisa ba, baze ta6a saka na ba.”
“Toh amman Zeezee meyasa kikeson rabuwa da miji kaman Maj-Gen.? Bawan Allan nan
banga abinda ya rasa ba ga kyau ga hankali most of all ga sweet voice.”
Allah ko? bari Ahmed (mijin Hajar) ya jiki ba ruwa na.”
“LOL but seriously.”
Toh ni duk feautures d’in ba burgeni suke ba, Adeel kawai nakeso.”
“Allah baki shi toh sena ganki goben.”
“Ameen bye!” nan tayi hanging yau ma kaman jiya word be sake had’ata da Al’ameen
ba ko duba ta da Asuba beyi ba saboda abinda ta masa ya mugun 6ata mai rai.

****
A washegari kaman yadda ta saba fita bada izininsa ba da sassafe ta tashi ta gama
ayyukanta ta karya sannan ta fice yawonta. Ba Al’ameen ya tashi ba se to 10am nan
yayi wanka shima jin ba motsinta yasan tafita yau ma, breakfast ya aika aka siyo
mai yana cikin karyawa wayansa ya shiga ringing yana kai dubansa kuwa yaga Hjy
Sadeeyah, batare da 6ata lokaci ba ya d’aga “halo Big Sis.”
“Na’am Little one kana gida?”
“Eh ban koma aiki ba tukun se jibi.”
“Oh to gamu da Mama mun yanko kwanan gidanka.”
“You mean kuna Bauchi?!” yayi exclaiming.
“Yes gamu nan ma a bakin gate yanzu.” Mumunar fad’i gabansa yayi yasan halin
Sadeeyah sarai ba shakka taje ta irgawa Mamansu halin da yake ciki ne Mama ta ibo
k’afa all the way from Kaduna ta taho nan. Tunanin me zeyi ya soma wanda beyi nisa
ba Sadeeyah ta danna doorbell. Jiki na k’yarma ya miqe ya bud’e musu. Salati kawai
Mama ta saki ganin yadda fuskan Al’ameen nata yad’an fad’a ba shakka Sadeeyah
batayi k’arya ba matar Al’ameen na basa wahala saboda ta samesa shiru-shiru bayi
magana. Al’ameen mutum ne da abubuwa basu cika damunsa ba inhar ko aka soma ganin
damuwa tattare da shi to abu ya 6aci ne kwata-kwata ba kanta.

“My Only Son?!” Mama datayi ageing about 67 tayi exclaiming tana shafa fuskansa
pathetically.
“Ai na gaya miki Mama, kinga yadda ya rame kuma believe me wallahi time dana zo
bekai haka rama ba.” Hannun Al’ameen taja suka shiga ciki suka zauna kan kujera
d’aya a yayinda Sadeeyah ke zaune oppsite them. “Al’ameen Babana meke faruwa? Meke
damunka?” Hannunta ya sauk’e da k’yar daga fuskan nasa, “babu Mama” sannan ya maida
kallonsa kan Sadeeyah, “Hjy me kikaje kiga gayawa Mama kika sa tazo all the way
from Kaduna, bakisan its bad for her health bane?”
“Akwai abinda yakai min rashin kwanciyar hankalinka tashin hankali ne Al’ameen?
Yanzu ace da raina amman bazaka sanar dani halin da kake ciki ba sede a bakin
Sadeeyah? Itama da Allah be kawo taba sede rana d’aya inji matar taka ta sa maka
ciwon zuciya ka fad’i ka mutu?”
“Mama what are you talking about? Bafa abinda ke faruwa ki kwantar da hankalinki
please ni banason abinda ze tayar miki da hankali.”
“Ai ka ajiye kalman kwanciyar hankali a gefe, ina matar taka take?”
“Uhm... Erm-” katsesa Sadeeyah tayi da wuri “ta fita yau ma kaman kullum ba? Ai
na gaya miki Mama, wallahi kullum da safe seta fita yawo kuma karki manta ba
breakfast take ajiye mai ba sekuma Magrib take dawowa.”
“Thats not true Mama karki jita, Hjy enough please” yayi defending kansa.
“Aww nice nake k’arya Lil Bro? Well lets see” dining space ta nufa sega take away
nasa dayake having breakfast with, kai ta kad’a ta d’ago ta kai wa Mama, “ba gashi
ba aikin kenan kullum cikin siyan takeaway, bata ta6a mai girki ba Mama meye
amfanin wannan auren? Wallahi ina raye wancan shegiyar bazata wahalar min da k’ani
ba, I just let her go kwanaki but not now not ever.”
“Barni da ita Sadeeyah, haka kawai tasa min Only Son a gaba sabida taga baya
magana? Ina matar taka take nace?”
“Sekin tambaya ne Mama? Ofcourse ta fita yawon banzan data saba mana.”
“Ina take Al’ameen answer me.”
“Mama bata gida ta fita amman da izini na ta fita.”
“Al’ameen yanzu ni zakayi wa k’arya? Ka kalli cikin idanu na kamin k’arya?”
“Mama please...” Sekuma yayi shiru.
“Da izinin ka tafita koko a’a? Karka min k’arya am damn serious.”
“Bada izini na ta fita ba but pl-” katse sa Mama tayi “Sadeeyah d’au waya ki kira
min iyayen yarinyar both baban da maman now! Za’a yita ta k’are yau.”

*© MIEMIEBEE ™YGC!*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄?
[2/3, 9:32 PM] 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febuary, 2017*
3⃣9⃣

Nan da nan Sadeeyah ta kira Mama as a matter of urgency kan ita da Baba suzo
yanzu-yanzu, ta fad’i ko lafiya kuma tak’i. Cike da tashin hankali Mama ta kira
Baba yana d’agawa tayi stating, “Alhj kana ina yanzu?”
“Ina hanyan zuwa kasuwa ne, lafiya?” Ya amsa.
“A’a wallahi ba lafiya ba ka juyo yanzu Sadeeyah yar Maj-Gen ta kirani kan ita da
Mamansu suna gari suna gidan Zeezee haka wai we are needed urgently.”
“Subhanallahi! Allah yasa de k’alau to gani nan zuwa.”
“Yauwa kayi sauri please.”

***
“Mama you are not doing this.” Al’ameen yayi maganan still not believing abinda
ke gudana.
“Ka tsaya kaga aiki da cikawa.”
“No Mama please drop all this Hjy call them back kice musu su fasa zuwa ni
banason tashin hankali, let Zeezee be eventually zata zo tayi learning truth,
yarinya ce har yanzu.”
“Yarinya fa kace Al’ameen? D’an yaron shekara d’aya ma ya iya ya tantace dad’i da
rashinsa sekace min zank’aleliyar mata kaman Zainab batasan ya kamata ba? Wallahi
k’arya ne raba auren nan za’ayi kowa ya huta ba yadda za’ayi ka kai yarinya Hajj ta
tsaya tana maka wannan iskancin.” Ta fada rai a b'ace.
“Ai Mama ban fad’a miki bane har mota ya sai mata kuma karki d‘au wai k’aramar
mota ce, sak irin nasa Ford Jeep d’innan ya sai mata.” Hjy tayi stating.
“Karki gayamun Sadeeyah!” Exclaimed Mama.
“Wallahi gashi ki tambayesa, kuma ina da tabbacin ita tace se kalan nashi
takeso.”
“Al’ameen kalleni, kalleni nace!” Ta tsawata masa a hankali ya d’ago kai yana
kallonta “ya kukayi da ita?” Shiru yayi not ready to talk, “aww bazaka gayamin ba
kenan? Kode asirce ka matar taka tayi?”
“Mama ni bata asirceni ba, wai ina baki hak’uri bazaki hak’ura ba yanzu? Please
kuyi dropping maganan nan I beg of you please.”
“Kanason in sa6a maka koh? inba asirce kan tayi ba then mesa bakason aga fault
nata? Ina maka tambaya bazaka amsani ba? Nace ya kukayi da ita?!”

“Tace tanason kalan mota na ne inda hali na sai mata thats all bawai forcing
d’ina tayi ba.”
“Lallai yarinyan nan batada kunya, Allah kawo iyayen nata.” Mama tayi maganan
unbelievably.
“Ameen” Sadeeyah ta amsa.
“Mama please inhar kina sona call them back kice su fasa zuwa, zamu iya mata
gyara within us base mun sa iyayenta ciki ba, karmu had’a kanta da parents nata
please.”
“Kai abinda ke damunka kenan? Kaji na rantse yau se an raba auren nan
billahillazi.”
“No Mama please dan Allah don’t do this to me, karki raba aurena da Zainab you
know how much I love her.”
“But she doesn’t love you Al’ameen zuciyarta bata tare da kai kadena wahalar da
kanka akan wacce is not worthy of your love.”
“I believe in US I believe wataran al’amura zasu daidaita tsakani na da ita, its
just a matter of time.”
“Time? Yau da bikinku watanni nawa? Beyi hud’u ba?”
“Yayi sosai Mama” cewar Sadeeyah “in beyi biyar bama kenan.”
“Akwai time dayafi wannan ne? watanni biyar da aurenku ko 6ari banji ‘yar nan ta
ta6a yiba kome dalili ban sani ba.”
“Mama wannan kuma wace irin magana ne? Haihuwa kam bana Allah bane?” Al’ameen
yayi saurin tararta.
“Wai Al’ameen in haifeka sannan kake tunanin zaka iya min wasa da hankali? Nace
meye dalili?”
“Nima ban sani ba gaskiya.”
“Lil Bro why defending her? ‘yar nan ba sonka take ba, she don’t deserve you, she
isn’t worthy of your love. Mama wallahi koda nazo kwanaki ba a d’aki d’aya suke
kwana ba and that means ita ta koresa daga d’akin tunda batason basa kanta, can you
deny it?”
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Al’ameen! Amman da hankalika kuwa?
Mahak’urci mawadaci amman naka hak’urin yayi yawa, Sadeeyah tell me this not true.”
“Wallahi it is Mama gashi ai seyayi denying inhar k’arya nake”
“La’ilaha illallahu! Ni Ameenah naga duniya, kai! Amman da hankalinka kuwa? Ka
biya sadakin yarinya sannan tak’i baka hak’k’inka kuma still ka tsaya kana farinta
mata rai da gifts? Are you that stupid Al’ameen? What is wrong with you? Dakai nake
magana!” Tun daga nan Al’ameen ya kasa fad’in komi again, kansa ya sunkuyar
ayayinda masifan Mama da Sadeeyah keta scattering masa k’wal’kwalwa take ciwon kai
me tsanani ya rufesa.

*~ *~ *~
In less than 30 minutes su Mama suka sa iso hankali tashe, gaisuwa sama-sama
sukayi da Mamansu Al’ameen. “Hajiya you called for us ina fatan lafiya?” Cewar
Baba. Zanin Mama Al’ameen ya shiga ja da nufin dan Allah tayi shiru amman ta fisge
zanin nata.
“Inason kafin mu fara komi ku kira min Zainab awaya ko wala Allah zataji
magananku ku iyayenta ta dawo gida tunda ta saba fita bada izinin mijinta ba.”
“Mama please thats enough” Al’ameen yayi pleading a hankali amma kota kansa
batayi ba
“Hajiya ban fahimci inda kika dosa ba” Baba yayi maganan with bewildered look on
his face, Mama kanma kasa cewa komi tayi.
“With time zaka fahimta Alhj, amman nafison ayi komi a gaban Zainab kada kuce
sharri akeyiwa ‘yarku.” Tuni ran Baba yahau tafasa waya ya zaro daga aljihunsa a
fusace ze kira Zeezee sanin halinsa Mama ta sauk’e hannun nasa “a’a Alhj kabari na
kirata da kaina dan Allah nace.” Kai kawai ya gyad’a mata yana wani irin zakin
nishi.

** _After a while..._
“Hello Zeezee?”
“Na’am Mama ina kwana?”
“Lafiya qalau nace kina ina ne? Ki dawo gida yanzu gani na zo.”
“Toh Mama I’m on my way.” Tana ajiye wayan tayi sallama da Hajar. Zama shiru
sukayi wajen ba wanda ya sake cewa komi seda suka jiyo k’aran bud’e k’ofan Zeezee
tana maida k’ofan ta juya taga biggest suprise of her life, idanunta na tozali dana
Baba ta tabbatar tana cikin babban tashin hankali yau, meke faruwa? Me tayi? Wayyo
nata ya k’are.
“Kinyi tsaye akan mu bazaki k’ariso bane?” Cewar Baba harshly. Jiki na rawa ta
k’arisa parlourn tare da zama a k’asa daga wani angle, cikin sauti me rawa ta shiga
gaidasu sede kowa ya amsa banda Baba, nan fa cikin Zeezee ya sake d’aukan ruwa.
“Masha Allah, Sadeeyah kiyi ma Saje (one of Al’ameen’s soldiers) magana.” Cewar
Mama Babba. In a minute taje ta taho da Saje, cike da girmamawa yabisu duka da
gaisuwa babu kaman yadda ya gaishe da Al’ameen. Shi kansa Al’ameen is confused me
kuma yasa za’a kira Saje acikin family matter’nsu? Bade su Sadeeyah sun had’a baki
dashi ba yana kai masu rahoto a kullum ba?

“Good ina son dukkannin ku nan kubani aron kunnuwanku wannan” tayi nuni da
Zeezee da tuni cikinta ya sake tsabagen rud’ani “Zainab ce matar Al’ameen d’ana.
Inason Alhj kaida Hjy Hafsah ku kalli Al’ameen ku kuma kalli Zainab ku gayamin inji
cikinsu waya k’ara weight bayan aurensu da akayi wanda ke neman watanni biyar.”
Mama kad’ai ce ta d’aga kai ta kalli Al’ameen banda Baba dake ta bin Zeezee da
dirty look tun beji dalilin dayasa aka tarasun ba yasan rashin hankali tai. Se anan
Mama taga kalan fad’awan da fuskan Alameen yayi whereas Zeezee kuma ta k’aru, ita
daman tasan Zeezee na bawa Al’ameen wahala proof ne kawai batada.
“Hjy its crystal clear Al’ameen ya fad’a ba laifi.” Mama ta fad’a finally.
“Good base na sake nanata muku ba, you guys are aware yaron nan ya kai Zeezee
hajj koba haka ba? Kuma inba wai yana sonta bane baze ta6a asaran sama da miliyan
biyu akanta ba am I right?”
“Hakane sosai ma” Mama ta amsa ayayinda Baba ya gyad’a kai “Al’ameen na son
Zainab sonda bana tsamannin akwai d’a na mijin da zeyi mata irinsa. Tun da nake da
Al’ameen ban ta6a ganinsa acikin damuwa ba se alokacinda yakeson Zainab, abun
mamaki anan shine kalan abubuwan da Zainab take yima Al’ameen d’ina har yasa ya
zube haka, tun bayi bin abin a zuciya har ya fara damunsa wanda ba haka nasan
Al’ameen d’ina ba kaima Alhj kasan halinsa tunda kuna zumunci.”
“Sosai Hjy ki gayamin me wancan ‘yar iskan tayi.” Cewar Baba.
“Alhj calm down dan Allah inma zakayi mata fad’a kabari se munje gida” Mama tayi
maganan yadda Baba kad’ai ya jita.
“Abubuwan da tayi kuma take kan yi suna da yawa tunda ta samu Al’ameen me hak’uri
take iya son ranta a gidan nan, tunda akayi musu aure bata ta6a aza mai girki yaci
ba, tana fita bada izininsa ba, be ta6a gaya mata magana tayi ba gar da gar take
zaginsa tana gaya mai magana iya son tanta, bata ta6a had’a kwanciya dashi ba ga
kuma wayan da takeyi kullum da sauarayinta wai shi sunansa Adeel, yanzu haka fitan
ta yau Al’ameen baida masaniya. Mota tace se irin wanda yake hawa takeso haka yaron
nan ya sai mata amman ta saka mai da butulci irin wannan? Don ita yaro na gabad’aya
ya zube ya sauya kamanni, it isn’t fair! Just recently taje taci bashin 500k gun
k’awarta badon komi ba don ta 6atawa Al’ameen suna a gari, haka tasa k’ananun yara
wanda basu kai ba suka zo suna gaya mai magana iya son ransu kan ya bari matarsa
tana cin bashi a waje wanda ba haka bane. White gold na ‘yar nan be 6ata ba tamai
k’arya ya 6ata haka ya sai mata sabo ta samu ta siyar da tsohon toh ni wallahi
gaskiya ina raye bazan bari a cutar min da d’a ba. Na kiraku nan ne badon komi ba
se dan ayita a gabanku ta k’are am cutting off this marriage Al’ameen baze cigaba
da zama da Zainab ba tana cutar dashi tunda daman ba sonsa take ba tanada
saurayinta wanda takeso as said.” Ta k’are maganan anger na building within her.
“Inalillahi wa inna ilaihi raji’un!” kad’ai Mama da Baba ke ambata, they are
both totally speechless wannan rashin hankali dame yayi kama? Tun auran Mariam da
Yasmeen in-laws nasu basu ta6a kiransu suka masu magana akan halayensu ba se Zeezee
da dududu auran ta befi watanni biyar ba? Gabad’aya Zeezee ta kasa cewa ko uffan
wajen all she knows is that nata ya k’are dan yankata Baba zeyi tun anan ta shiga
rera kuka a hankali. Al’ameen kuwa tun da Mamanshi ta fara magana bece ko uffan ba
infact tunda su Mama suka shigo ya gaishesu be sake d’aga kansa ba.

“In kuma har baku yarda ba inada proof, Saje kunna audio’n.” Cike da mamaki
Al’ameen da Zeezee suka d’ago kai suna kallon saje wani audio kuma? Suka tambayi
junansu a zuciya se yanzu suka gano Saje ne source of all informations da Mama ta
samu batun zaman aurensu wannan na nufin akwai recorder’n daya ajiye a d’akin
Zeezee dakuma parlour kokuwa kullum yana eavesdropping ta window anytime yaji
Zeezee akan waya seyana recording, this is serious!

“I’m very sorry Sir, please forgive me for intruding, it was an order from your
Mother” Saje yace da Al’ameen sannan ya kunna audio’n seji akayi muryan Zezee na
tashi tana waya da Adeel ba a samun jin abinda Adeel ke fad’a se nata love words
d’in har inda take sake ce mai budurcinta nasa ne kad’ai seda ya fito. Yana k’arewa
aka sa na wanda take cinikin white gold nata Baba be gama jin audio’n ba zuciyarsa
ta gama tafasa a zuciye ya miqe kafin Mama tace zata taresa yahau kan Zeezee tare
dayin wani d’an banzan ball da ita seda gun ya 6ullo take. Wani irin rikicaccen ihu
cike da azaba ta saki hakan yasa Al’ameen yayi saurin miqewa ya jata a yayinda Saje
ya ja Baba baya shima yana me basa hak’uri, idon Mama kuwa tuni suka kad’a sukayi
ja wannan wace erin rayuwa ce? Shin se Zeezee ta bata heart attack tukun zata huta?
Cikin wani irin dishasshiyar murya numfashi na seizing Baba ya shiga magana.

“Al’ameen ka saki yarinyan nan ka saketa nace! Shi saurayin naki Adeel ko wa
yake shi zan bashi sadaqar ki amman kisani Zainab bazaki gama da duniya lafiya ba
na rantse miki.”
“Subhanallahi Alhj calm down please karka illata ta hakan baida amfani” cewar
Maman Al’ameen a yayinda su Sadeeyah suke basa hak’uri.
“Wallahi seya saketa kunji na rantse seya saketa. Ai auran Al’ameen gata ne a
gare da wannan ‘yar iska la’ananniyar, da kai nake Al’ameen maza ka d’au takardan
sakinta ka rubuta mata shi yanzun nan kuma ba saki d’aya ko biyu nake so ba uku-”
tari ya shiga yi sosai, “saki uku zaka rubuta mata, ita wai saurayinta har yanzu
tafi fifitawa akan kowa ba? Shi za’ayi mai sadak’ar ki wallahi bazaki gama da
duniya lafiya ba Zainab” Baba yayi mata baki again. Salati Mama ta hauyi sabida shi
kad’ai ke fitowa a bakinta, har anan Zeezee na abayan Al’ameen tana rusa kuka.
“Alhj calm down please kaga har numfashinka na neman d’aukewa” cewar Maman
Al’ameen “nima na goyi bayanka ayi sakin nan amman ba uku ba, saki d’aya ma ya
wadatar tunda dan a hora Zainab ne.”
“Wallahi uku za’ayi bazan yi rantsuwa a iska ba, kuma ko ke kad’ai ce ‘ya a
gareni na yafeki Zainab na cireki daga cikin jerin ‘ya‘yan dana haifa ko a lahira
kika ganni ki canza hanya. Ni? Ni zaki nemi ki 6atan suna a idan jami’u ki
tozartani, na d’au miji me hankali da hak’uri kaman Al’ameen na baki amman ki tauye
masa hak’k’i bayan nan ki ringa waya da saurayi a gidansa kinayin abinda kika ga
dama? Bazan ce zan miki duka ba dan wallahi-” ya tsaya yana tari sosai a yayinda
idonsa suka kad’a sukayi ja wur “ya isa haka haka Alhj dan Allah kayi hak’uri”
cewar Saje har anan Mama datake zaune jugum a kan kujera ta kasa fad’in komi ko
motsi ta kasa seda taji fad’uwan abu rigijib! A k’asa. Take dukkaninsu mutan wajen
suka kai dubansu ga inda sukaji k’aran, sumemmen jikin Baba suka gani, innalillahi
wa inna ilaihi raji’un kad’ai ke tashi a wajen “Alhj!!!” Mama tasa wani erin
d’ankaren ihu tare da rugawa a guje ta nufi kan Baba ta aza kansa a cinyarta tana
hawaye sosai tana tapping kumatunsa sede sam bayi motsi, nishinsa ma wani sama-sama
yake fita. Nan da nan duk sauran suka nufi wajen banda Zeezee dake sprawled a k’asa
tana kukan cire rai daga inda take. “Ta kashemin miji, ta kasheshi wayyo Allah na!
Na mutu na lalace!!” A 360 aka kinkimi Baba se Teaching Hospital gabad’aya hankalin
kowa ya matuk’ar tashi, Mariam ma tuni Omar yasanar da ita ta taho ba shiri a
corridor’n emergency room da Baba ke ciki ta tarar da kowa da gudu taje ta rungume
Mama datayi jugum wajen banda hawaye ba abinda takeyi, kuka suka shigayi a tare a
yayinda su Sadeeyah ke basu hak’uri daga bisani Mariam ta d’ago kai tare da watsa
wa Zeezee dake tsaye acan ita kad’ai tana kuka harara. Kamar a kyaftawan ido ta
risketa tare da bata wani irin hot slap cike da tsana da haushi, wajen Zeezee ta
riqe da k’yar tana hawaye endlessly kafin ta farfad’o daga marin Mariam ta k’ara
mata d’aya a other side d’in. Da wuri Omar yajata baya a yayinda Al’ameen ya kare
Zeezee “kin kyauta kenan? Kin kashe mana Baba kin kyauta? What kind of a sister and
a daughter are you Zainab? Wallahi kisani inhar wani abun ya samu Baba none of us
your family will forgive you, bazamu ta6a yafe miki ba” ta k’are maganan tana kuka
sosai, rungumeta Omar yayi yana bubbuga bayanta.

_45 more minutes..._


A dai-dai nan ne red globe dake a bakin k’ofan da Baba ke ciki ya mutu and within
second counts k’ofar ya bud’u tare da bayyano da wani Dr. daga ciki. Kusan a tare
dukansu dake wajen suka nufa gun Dr’n da gudu kowa da abinda yake tambaya which is
none other than ya jikin maras lafiyan yake banda Zeezee dake baje a k’asa achan
inda Mariam ta tsinka mata mari tana kukan cire rai. “Calm down okay? Ku kwantar da
hankalinku haka in shaa Allahu ze samu sauk’i we pray so.” Salati ne ya biyo baya,
“Dr. Ka gaya mana meke damunsa dan Allah, am his wife please tell me wani hali
mijina yake ciki dan Allah karka 6oye mana wani abin dan Allah nace” Mama ta k’are
maganan tana jan hanci.
“Toh muje office d’ina tunda kece matar tasa please.”
“No Dr. I can’t wait till then duk nan family ne ka gayamana wani hali yake ciki
please.”
“Yes Dr please” cewar Omar da Mama Baba. Clearing throat Dr yayi “kaman yadda
kuka sani shi patient d’in nada hawan jini ko?”
“Eh amman rabuwan jinin nasa daya hau ya jima Dr.” Mama ta amsa immediately.
“Yasamu heart attack ne wanda a dalilin haka yayi leading masa to heart
failure-”
“Heart failure?!” Sukayi exclaiming in unison. “Dr dan Allah karka cemin ya mutu
I can’t afford to lose him” jan Mama Mariam tayi a jiki tana bubbuga bayanta.
“Calm down be mutu ba mun bashi kulawan gaggawan daya kamata yana bacci yanzu in
shaa Allah zuwa anjima ze farfad’o sede inason jin meya jawo attack dayasa har
heart nasa yayi failing, saboda munyi all tests is not as if yana suffering from
wani infection ko disease kokuma yana shaye-shaye.”
“Baya shaye-shaye Dr. ‘yar sa ce ta tsinka mai zuciya abinda ya faru kenan” Mama
tayi explaining in a crying tone.
“Shikenan Hjy kibar kukan haka in shaa Allah mijinki ze samu waraka zamu d’aurasa
akan diuretics da cardiac drugs sede yazamo dole abar breaking masa sad news kuma
if possible koda ya tashi kar kushiga cikin d’akin nasa da ita ‘yar nasa data jawo
mai attack d’in sabida by just looking at her zuciyan nasa tana iya tsinkewa
again.”
“In shaa Allah Dr. Mungode mungode sosai” Maman Al’ameen ta amsa.
Komawa duk sukayi suka zauna atleast Baba be mutu ba yanzu, har anan ba wanda
yayi takan Zeezee.

_20 more minutes..._


Alokacin har Mama Baba da Sadeeyah sun koma gida, Nurse ta sanar dasu Mama kan
Alhj ya farka, godiya dukkanin su sukayi wa Allah sannan Mama kad’ai ta shiga
d’akin, hawaye tasoma zubarwa wane lalacaccen famfo ganin har oxygen seda akayi
supplying wa Baba. A nitse ta k’arisa wajen taja kujera ta zauna, “Al... Alhj?”
Hannunsa yakeson d’agawa amman ya kasa data gano hakan seta d’aga ta had’a da nata
“Alhj Allah ya baka lafiya, Allah baka lafiya Alhj” cikin wani dishasshiyar murya
ya amsa da “ameen kukan ya isa haka, Al’ameen ya saki Zainab?” Abinda ya fara
tmbaya kenan.
“Alhj kabar damuwa da zancen Zainab its not fit for your condition.”
“Ki gayamun ya saketa?”
“Ya saketa Alhj” tamai k’arya ganin hannunsa ya soma shaking.
“Hafsah nayi nadama, nayi nadaman maida Zeezee *_‘YAR GATA_* gata bashida wani
amfani, tabbas da naji maganarki da a baya da duk hakan be faru ba, ina alfahari da
Mariam da Yasmeen Allah ya cigaba da musu albarka.”
“Ameen Alhj duk wannan ba abinda zaka damu kanka dasu bane yanzu, lafiyanka ne a
gaba su Mariam suna nan kanason ganinsu?”
“Eh ki shigo min dasu” sauk’e hannunsa tayi a hankali taje ta kira su Mariam inda
ta sanar da Al’ameen komin rintsi yacewa Baba ya saki Zeezee saki uku kaman yadda
ya buk’ata. Bayan Mama suka bi suka shiga ciki da gudu Mariam da Omar suka nufi kan
Baba suna kuka sosai a yayinda shi kansa yake hawaye, “‘ya‘yan albarka ku yafemin,
ku gafarceni na rashin adalci danayi a tsakaninku ku yafemin please.”
“Baba dan Allah kabar neman yafiyanmu ba abinda ka mana mude fatan mu Allah ya
baka lafiya” cewar Mariam
“Sannu Baba” cewar Al’ameen “Allah ya baka lafiya”
“Ameen” Omar da Mariam suka amsa.
“Al’ameen nagode Allah saka maka da alkhairi.”
“Ameen Baba bakomai.”

*** Tsaye Mama ke a bakin k’ofar d’akin Baba tana bin Zeezee dake ta kuka har a
yanzu da harara, wani wutan tsanan Zeezee ne ke ruruwa a zuciyarta. Jiki na k’yarma
Zeezee ta doso inda Mama ke tsaye tare da kneeling a gabanta tana kuka me tsuma
zuciya, “Mama dan Allah kiyi hak’uri, kiyi hak’uri dan Allah na tuba bazan sake
ba.” One more dirty look Mama ta watsa mata sannan ta bar mata gun tare da shigewa
d’akin domin batajin zata iya mata magana.

*© MIEMIEBEE ™YGC!*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄
[2/3, 9:32 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febuary, 2017*
4⃣0⃣

Wani irin kuka Zeezee ta rushe dashi, kanta har wani sara yakeyi mata. Tafi
minti goma tsugune a wajen tana kuka, seda su Al’ameen suka bud’e k’ofa taja gefe
har anan su Mariam basu ce mata ko uffan ba. Gida Mama ta aika Omar dan kwaso mata
abubawan da zata buk’ata tunda a asibiti zata kwana yau. Sallama duka sukayi sannan
Mariam ta koma gida. Al’ameen yazo tafiya ya kalli Zeezee dake ta aikin kuka har
yanzu sannan a hankali yace mata “Zainab tashi mu tafi gida.” Da kaman bazata miqe
ba sekuma ta tashi ta share hawayenta tabi bayansa, kuka ta cigaba dayi cikin motan
wanda ko k’ala Al’ameen bece mata ba, sun isa gida ya faka suka fito. Tsaye suka
tarar da Mama da Sadeeyah a parlour wane jiransu suke dama.

“Ya jikin Baban nata?” Mama ta tambaya.


“Alhamdulillah da sauk’i.” Al'ameen ya amsa.
“Allah k’ara mishi lafiya toh” cewar Sadeeyah atare Mama da Al’ameen suka amsa da
ameen. “Yauwa Al’ameen ga biro da takarda maza ka rubuta ma Zainab takardanta tabar
min gida yanzun nan, yarinyar data iya tasawa Mahaifinta hawan jini har kashe
mijinta zata iya, wanda nikuma bazan iya affording rasa kaba, maza amshi ka rubuta
mata saki d’ayanta ta tattara kayakinta tabar gidan nan at this instant.”

“Mama do I have to do this?” Ya tambaya a maraice.


“Yes Al’ameen inhar bawai so kake na sa6a maka ba, na baka nan da minti ashirin
inhar baka saki yarinyan nan ba forget it that am your mother” tana kaiwa nan ta
wuce ciki, kafad’ar Al’ameen dake riqe da biro da paper Sadeeyah ta dafa “do whats
right Maj-Gen.” itama daga nan tabi sahun Mama. Waje ya nema ya zauna ta ina ze
soma rubutawa Zeezee takardan saki yanzu? Kai ya d’ago yana kallonta a yayinda take
kallonsa itama da jajayen idanunta. “Me kake jira? Ka rubuta min ka huta mana tunda
kasa Baba ya la’anceni ya cireni daga jerin yaran daya haifa its what you've ever
wanted dama” One more look yamata sannan ya rubuta mata takardan sakinta as

_Ni Muhammad Al’ameen na saki mata ta Zainab saki d’aya._ folding yayi a nitse
sannan ya tashi ya miqa mata “gashi Zainab, amman kisani it was never my intention
to divorce you, duk abinda na miji keyiwa matarsa don farinta mata nayi miki, Allah
sheda na ne ban ta6a cin zalunki ba a iya zaman mu, kuma I want you to know that
duk rashin hankalin da kika min na yafe miki Zainab, Allah fiddo da alkhairi daga
wannan lamari, I love you so much and I’ll continue to do so till my last breathe.”
Ita kanta taji ba dad’i amman ta dake tare da share hawayenta ta wabje takardan
“finally am free.” D’akinta ta nufa ta had’a akwati har guda uku sannan tafito,
cikin booth na motanta tasa boxes d’in sannan taja motarta ta fice.

_Back inside..._
Zaune Al’ameen yake shiru akan kujera gabad’aya ji yake inama ba’a k’addaro masa
da rana kaman ta yau ba, yana son Zainab be ta6a kawowa a ransa zasu rabu ba. Duk
da kalan rashin mutuncin da take masa he still loves her and so much. 20mins later
on the dot Mama da Sadeeyah suka fito dag ciki ta tambaya “ka saketan?”
“Na saketa saki d’aya kamar yadda kika buk’ata Mama, har ta tafi ma.”
“Yar banzan yarinya ko hak’uri bata iya badawa ba.” Cewar Sadeeyah.
“Ai gwara da bata badan ba hakan yafi sauk’i yanzu ba shikenan ba” Mama tayi
maganan tana neman zama gefen Al’ameen. Matsa mata yayi kad’an ta zauna “kayi
hak’uri Baba na ni kaina nasan what you did was not an easy thing, I know how you
love Zainab amman its hight time kayi hak’uri ka gane cewa bata sonka, don da har
tana sonka da bazata bari ka rubuta takardan nan ba but see ko hak’uri bata bamu
ba. Fatan mu shine Allah yasa rabuwan ku shi yafi alkhairi ina nan ina kan yimaka
addu'a a kullum d’ana.”
“Nagode Mama, I love you so much."
“I love you more My Son” tayi hugging nashi.

***ZEEZEE

“Hello Very Own? Ban ganka ba har yanzu ganifa gaban Wikki hotel d’in.” Zeezee
tayi maganan tana zaune cikin motarta da wayarta maqale a kunnenta.
“Sweetest Love am on my way” answered Adeel, daga nan tayi hanging. In second
counts sega sabuwar maroon Genesis G80’n Adeel ya shigo htl d'in tare da parking
not too far from Zeezee's car. Da gudu Zeezee ta fito daga motan nata ta nufi nasa
yana fitowa ta fad’a jikinsa tana kuka sosai hugging nata yayi tightly, he can’t
remember when last yayi hakan. “Shhh! Sweetest Love I’ve got you okay? Stop
crying.” Kukan ta cigaba dayi da k’yar ya samu tayi shiru sannan ta d’ago daga
jikinsa tana kallon cikin idanunsa a yayinda wani sabon sonsa yake shiganta. “Very
Own Baba yayi disowing d’ina banida kowa sekai yanzu, Mama dasu Adda Marima duk
they are extremely mad at me, you are the only one I have” ta k’are maganan tana
kuka.
“I’ve got you Baby its okay, I love you so much, kikace Al’ameen d’in ya sakeki?”
“Yes" ta amsa tana gyad’a kai takardan ta zaro daga jakarta ta miqa mai bayan ya
karanta ya yayyaga into pieces “a gobe Uncle Abdoul zeje ya samu Baba ayi mana aure
mubar hell dayake nan and go back to Florida.”
“I love you Adeel” tayi hugging nasa. Hotel room ya mata booking inda ta sauk’a
achan se bayan La’asr Adeel ya tafi dan zuwa ya sami Uncle nasa.
Cikin sauk'in kai Adeel yama Uncle nasa magana tare da stating masa conditions
d'in kan sadaqar masa da Zeezee Babanta yace zeyi dalili kuma shine dan taje
birthday'n sa. Da wannan reason Uncle Abdoul ya samu Mama ya zana mata komi itama
ta amince don kuwa yadda Adeel ya tsara maganan se kaman Baban Zeezee wani Malami
ne ustaz da bayison yahudanci ko kad'an, maman Adeel kuma datayi girman London bata
d'au zuwa party wani babban laifi ba don haka tayi welcoming Zeezee wholeheartedly.
Kwana biyar Baba yayi a asibiti aka sallamoshi, alhamdulillah yasamu sauk'i da
k'arfin jiki sosai ba laifi. Har ayau Mama batasan ina Zeezee ke kwana ba saboda ta
tambayi Mariam ko ta mata masauqi a gidanta Mariam ta sanar da ita a'a. Labarin
sakin Zeezee kuwa tun a daren ranan da Al'ameen ya saki Zeezee, Mama Babba ta
kirata ta sanar da ita.
A yau su Mama suka dawo hida suna isa abinda Baba ya soma buk'ata shine akira
masa Zeezee tazo da saurayin nata dakuma magabantansa yayi ya sadaqar da ita ya
huta.

“Alhj dade ka fita daga harkan 'yar nan ina gudun maka ciwonka, kade ji abinda
likita yace” Mama dake 6allowa Baba meds nasa tayi maganan a nitse.
“A'a Hafsah hankalina baze ta6a kwanciya ba se ranan da naji shi Adeel ne ko
waye ya bawa Zainab kashi ya illata min ita kokuwa ya kasheta ya kai ta lahira.”
“Subhanallahi wai Alhj bazaka share maganan Zeezee ba se ciwon naka ya sake worse
tukuna? Kuma da kake magana haka baza tayi zaman idda bane? Ko haka kawai zamu sake
mata wani auren?”
“Zaman idda fa kikace Hafsah? Ko kin manta la'ananniyar bata ta6a had'a
shimfid'a da mijin nata ba?”
“Amma-”
“Ki kiramin Zainab nace” ya fad'a in a serious tone. Shiru tayi ta gama 6alla
masa Meds nasan sannan tad'au wayarta ta shiga kiran Zeezee.

Wayan nata (Zeezee) na a hannun Adeel suna zaune akan gado a htl room wayar ta
shiga vibrating kasancewar a silent take. “Babe Mama is calling you” ya sanar da
ita in an I-dont-care tone.
“What Mama???” Ta fad'a unbelievably.
“Yup” ya amsa tare da miqa mata wayar. “Pick it up” yayi instructing nata, ba
musu ba gardama ta d'aga tare da sawa a handsfree ”Assalamu Alaikum Mama? Ina
kwana?”
“Wa'alaikumus-salam kizo Babanki na nemanki, ki taho tare da Adeel nakin da
magabatansa kinji?” Zuciyarta na har6awa ta amsa da “toh” tare da jira Mama tayi
hanging. A hankali ta zare wayan daga kunnenta. Kallo d'aya Adeel yamata ya gano
hanklinta ya tashi matsowa kusa da ita yayi tare da kwantar da kanta a chest nasa
“all is going to be well okay? I've gotchu.” Kai kawai ta iya ta gyad'a mai.

****
Bada jimawa ba Zeezee, Adeel da magabantansa suka hallara gidansu Zeezee saidai
shi sam Adeel d'in yak'i shiga ciki. Har parlour Zeezee takai in-laws to-be nata
sannan taje tayo sallama d'akin Mama inda iyayen nata suke. Mama kad'ai ta amsa
murya na rawa tana kare jikinta a bayan k'ofa tace, “sunzo suna parlour Mama.”
“Naji kije waje ki jirani.”
“Ta fita min daga gidana gabad'aya ta k'ara koda minti d'aya ne Allah ya isa ban
yafe ba.” Hak'uri takeson basa amman jin haka ta d'ibi k'afa tayi waje ta samu
Adeel. Cikin mintuna k'alililan Baba yayi sadaqar Zeezee wa Adeel da shaidu uku
kacal se waliyai ya amshi sadakinta ma yak'i. Suna kammala duk abinda ya kamata
Zeezee da mijinta dakuma in-laws nata suka dawo gida. Achan Mamin Adeel ta had'a
grand celebration nata luncheon sukayi na kece raini wanda gun event d'in seda
Zeezee tayi kuka kasancewar duk inda ta juya bata ganin nata sena Adeel seta tuna
bikinta da Al'ameen dangi har sunyi mata yawa ga kuma sisters nata uwa uba
mahaifiyarta nan kome aikin gidansu babu. Anyi event lafiya sumul ba yadda Mami
batai da Adeel ba yabari su kwana nan gida da Zeezee yak'i shi sam se a hotel, can
d'in suka nufa suna isa d'akinsu suka watsa ruwa one after the other sannan sukaci
abinci.

Sede daga yadda Zeezee ke acting Adeel yagano she is missing home tana zaune a
one end of the bed tayi shiru ya k'ariso ya zauna kusa da ita, “Sweetest love?”
Jikinsa kawai ta fad'a tare da sa wani irin kuka me tsuma zuciya, solacing nata
yayi tayi seda tad'an rage kukan, cikin sautin kuka tace, “Very Own please promise
me that you'll never leave my side, and that you'll love me forever.”
“Ofcourse yes Sweetest Love you know how much I love you right? Add more to it,
I'll never leave your side for better or for worse.” D'an sanyi aranta taji batasan
cewa na miji ba d'an goyo bane. Hira sosai Adeel ya riqa janta dashi seda ta
warware, ba wanda yayi tunanin yin sunnah raka'a biyun da ma'aurata suka saba yi.
To twelve yace su kwanta kafin nan seda ya 6allo wasu capsules k'waya biyu da ruwa
a cup ya miqa mata. Tana miqe kan gado ya tada ta, “Sweetest Love here tashi kisha
kinji?” Tana miqewa ta tambayesa “magani kuma Very Own?”
“Yes” ya amsa.
“What for?”
“Don't you trust me Babe?”
“I do very well Very Own but what are they for?”
K'arya ya mata “pain killers.”
“But am in no pain Very Own.”
“Come on! Sweetest Love” yayi maganan tare da zama a gefenta “must I dictate it
out? Ko kin manta tonight will be our...” Sekuma yayi shiru. Gano abinda yake nufi,
seta saki murmushi kad'an “don't worry I can bear that pain.”

“Nahh you can't, and even if you can I wont let you kar6a kisha kinji lets
sleep.”
“Anything for you Very Own, thank you” amsa tayi ta had'iye seda yaga wucewan
k'wayayin a gullet nata ya miyar da cup d'in tare da kashe musu wuta suka kwanta
warm and close inda a daren ranan Adeel ya kar6i hak'k'insa as yadda Zeezee tayi
promising nasa. Ba k'aramin dad'i yaji ba jin shi ya bud'e ta shine first man to
know her, dama its what he has ever wanted pride nata. A daren ranan jinsa yake on
top of the world. Wahala sosai yabawa Zeezee amman don yadda takeson sa takuma
keson ta farinta mai rai bata nuna masa sosai ba. Seda ya gamsu iya gamsuwa sannan
ya barta alokacin har wani sama-sama nishin Zeezee ke don azaba da wahala hawaye se
ambaliya suke a fuskarta.
A jikinsa ya kwantar da ita tare da pecking gashinta yana share mata hawayen,
“thank you Sweetest Love you made me the most happiest man on earth today, I wont
ever forget this, I love you.” Da k'yar ta iya zagaye hannunta akan cikinsa “I love
you more Very Own morethan you can ever imagine.” Yana rubbing bayanta back and
forth har ya samu tayi bacci sannan shima yayi.

****
Basu suka tashi sallan Asubah ba se kusan to 7am. Nanma da k'yar yasamu ya d'aga
Zeezee ya kaita bathroom sukayi wanka sannan alwala sukayi Sallah, pain killer ya
bata suka koma bacci se after 11 suka tashi Zeezee is feeling a bit better yanzu.
Wanka Adeel ya shiga yayi yana fitowa Zeezee itama ta shiga alokacin ne Mami ta
turo musu breakfast, shi da kansa yayi feeding nata. Da suka gama ci ne y juya ya
kalleta anan ya gano she is weak k'arfin hali kawai take. “Sweetest love?” Ya
kirata romantically. “Na'am Very Own” ta amsa a kasalance.
“Are you still feeling the pain?” kai ta kad'a masa amman yasan k'arya take
sekuma ta basa tausayi daya tuna yadda yayi forcing kansa a cikinta jiya. “Am
sorry” ya fad'a a hankali.
“For?” Ta tambayesa all confused. Hannunta ya had'a da nasa sannan yace, “for
last night-” da sauri ta katsesa “you don't have to Very Own I'm all yours, my
pride is yours and you've taken it away why are you apologising?”
“Is that so?” Ya d'aga mata gira teasingly, d'an murmushi ta saki ”yes Very
Own.”
“Thank you okay? Yestarnight was great I can't tell you how happy you made me I
love you.”
“I love you too” ta amsa shi nan ma a hankali. Wuyansa yayi bending tare da
owning lips nata for some time sannan yace mata, “are you ready?”
“For?”
“To fly to Florida.”
“Florida kuma how?” Ta tambaya confused.
“Yup there I promised you, zamu bar nan for now muje chan and get a break from
all these... You know tension.”
“Very Own but how-”
“How did I got ur passport?” Ya katse ta. “Don't worry acikin jakanki na d'auka
the other day, so are you ready?”
“Are you serious Very Own?”
“Yes Sweetest love are you ready?”
“Definately” ta amsa all excited. Pecking nata yayi a lips “good then flight namu
is by 1am tonight.” Hugging nasa tayi “I love you so much.”
“And I do too.” Yayi responding.

*~ *~ *~
Through out Zeezee ta wuni ranan tana expecting call from Mama amman shiru abun
ba k'aramin damunta yake ba amman batason ta nuna wa Adeel. A rayuwa in akwai
abinda ta tsana shine tashin hankalin Adeel, wannan kenan!
Zuwa 9pm na dare tana maqale jikin Adeel ta d'aga wayanta for the 1000th time
don ganin ko Mama ta kirata, da Adeel ya lura da frequent duban screen da take se
yayi deciding da bazi ya tambayeta. “Babe?”
“Yes Very Own?”
“Are you expecting a call?”
“Nnn... No” ta fad'i finally.
“Are you trying to lie to me?” Ya tambaya a hankali.
“Am sorry is just that na d'au ko Mama zata kirani amman shiru Very Own Mama dont
care about me anymore.”
“But I do Sweetest Love, you have me, I shall never turn my back against you I
promise.”
“I know Very Own but it still isn't enough she's my mom.”
Gashinta ya shiga shafawa a hankali in a soothing manner “I know Babe am sorry
kinji?”
“Its not at all your fault.”
“I can be anything for you Babe, a father if you need me, a mother, a brother
and also a sister so kidena tada hankalinki let them be and move on okay?” Kai ta
gyad'a tana share hawayenta “should I call her instead?”
“You don't have to ita da kanta zata kiraki idan ta jiki shiru.”
“Are you sure Very Own?”
“You don't trust me then , idan na samu misunderstanding da Mami ko Papa before
he died da kansu suke nema na ko suban hak’uri ma so karki damu, or dont you trust
me?” Take ta d'ago daga jikinsa tare da rik'o hannunsa “stop saying that you know I
do alot.”
“Thats my woman get some sleep zuwa 12:00 zamu wuce airport.” Har ta miqe sekuma
ya riqo hannunta “but first your medication.”
“Very Own am really okay no more pain.”
“I insist” kad'ai yace mata sannan ya b'allo capsules d'in ya bata yauma kaman
jiya seda ta had'iye yabar wajen. Kamar yadda ya fad'i 12am d'in ya tasheta suka
shirya zuwa airport kafin su fara boarding Zeezee taso kiran Mama atleast ta sanar
da ita amman duk tsoro take kar Adeel ya kamata idea'n tura text message sam bezo
kanta ba haka tana ji tana gani ya amshi wayan nata ya musu switching off tare da
nasa.

*****
Few days later, jin shiru Mama ta saci jiki ganin Baba na bacci tayi site na
Omar ta gwada kiran layin Zeezee don jin ko lafiya tunda tun ranan da aka bata wa
Adeel bata sake jin motsinta ba. Abun mamaki kota kira switched off takeji Lubiee
ta kira a k'arshe inda take sanar da ita ai Zeezee na Florida ayanzu haka. Mamaki
ne ya ziyarci zuciyan Mama, har Florida? Ta tambayi kanta. Shin Zeezee wacce irin
d'iya ce ace zata tafi har Florida amman bazata sanar da ita ba, ba k'aramin b'aci
ranta yayi ba wanda yakaiga koda da Lubiee ta tura mat digits na Zeezeen ma k'in
kirarta tayi, aga wanda ze nemi wani.

*~ *~
Life moved on, Maj-Gen yakasa moving on se a hankali al'amarinsa ya soma dai-
daita ya fara rage tunanin Zeezee if not ata farko-farko har Mama Babba ta soma
regreting sasa sakan Zeezee da tayi saboda ita sheda ce akan kalan son da Al'ameen
keyiwa Zeezee but tasan hakan is for the best shiyasa koda yasamu ya kar6i leave a
office tasasa ya dawo gida a wajenta ita da sisters nasa ya zaun suna kula dashi,
alhamdulillah yanzu an samu massive improvemet physically tunda har ya koma office
amman psychologically kullum seyayi tunaninta always all the time saidai bayi nuna
musu.

Adeel de a kullum be fasa baiwa Zeezee capsules dayake bata ba wanda koda
zatayi mar tambayan duniya ba fad'amata zeyi ba ganin ransa na 6aci anytime tA
tambayesa maganin menene yasa tama dena tambayar nasa yanzu ita wai she trusts him.
Duk wani abinda tasan yana iya had'asu ma hasali avoiding take, bata chatting kap
dakowa inbanda friends nata mata sanin kishi irin na Adeel. Hakan yasa basu ta6a
samin wani understanding dashi Adeel ba, kullum saidai suyi wanka su fita yawo
shikenan, duk abinda yagani me kyau ne yana k'ok'arin siya mata suna zaman
lafiyansu lau, ahaka har suka samu 3 months Zeezee bata sake ji daga gida ba.
Koda Mama ta bawasu Ya Ibraheem labarin abinda Zeezee tayi mata fusata sosai
yayi yace sam se Mama tabasa digits na Zeezee ya kirata yaci mata mutunci amman
Mama ta hanasa surely one day she'll need them saboda jini ba abu bane na wasa.

Su Adeel sun samu 3 months 1 week a Florida yace shi zaman chan ya ishesa
yanason ya dawo gida. Zeezee tafison zaman chan sabida gabad'aya ta manta da
problems nata har wani kauri ta k'ara, tanason cemasa sud'an sake prolonging zaman
nasu amman tasan halinsa bayi son ana questioning actions nasa. Haka cikin
kwanciyar hankali suka shirya suka dawo Bauchi, Nigeria inda ya d'au musu d'aya
daga cikin 2 of his inherited houses as duk sauran ya siyar dasu ya k'arar da
kud'in a hosting parties, siyan motoci and other useless expences. Bayan sunyi
settling Zeezee ta samu time ta kira Mama a waya suka gaisa ko nuna mata abinda
tayi ba dai-dai bane Mama batayi ba saboda there is no point ai ba yarinya bace.
Lafiya k'alau suka gaisa sukayi sallama.

*MIEMIEBEE*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febuary, 2017*
4⃣1⃣

_One week later..._


Da dawowan su Zeezee from Florida one week kenan. Tun dawowansu Mami ce ta
d'auki nauyin kai musu breakfast, lunch and supper, tayi haka na sati na marmari
wato itama ta gaji.
Yau da safe bayan su Zeezee sunyi wanka fes sun shirya sukaji shiru fa yau ba
alaman Mami zata kawo abinci ba tare da 6ata lokaci ba ta shiga kitchen ta musu
frying chips da omalet komi yayi suka karya. Sun gama breakfast Adeel ya fita ya
rage Zeezee kad'ai a gida, chatting suke da Lubiee ganin Lubiee nason cika mata
kunne yau ma da zancen da bayi wuce na bata kyautawa Ya Al'ameen ba ta kashe datan
nata ma gabad'aya. D'an goge-goge tayi sannan ta sake wanka tahau jiran dawowan
Adeel. Bata aza girki ba a tunaninta in Mami bata kawo musu ba shi Adeel ze siyo a
hanyan dawowa gida shiko Adeel tunda Mami bata kawo breakfast ba it shows that ba
lunch kenan dole Zeezee zata yi musu girki don shi ya gaji da cin abincin waje he
is fade up with it. Kusan 2:15pm ya dawo gida as always tayi welcoming nasa da
kisses and hugs. Kasa 6oye mar yunwan da takeji tayi ta tambaya a hankali “Very Own
baka siyo mana lunch ba?”
“Sayan lunch kuma? Baki gaji da cin abincin waje ba kullum nikam am fade up,
Mami bata kawo ba?” Kai zallah ta kad'a mar. “Wow meaning ta gaji kenan so da
kikaji shiru you didnt cook anything for us? Am hungry.”
“I didn't, I thought zaka siyo mana its what Ya Al'ameen normally does” ta fad'a
a hankali ashe kuwa ya jita.
“What?!” Yayi maganan a fusace “Ya Al'ameen kowa kika ce?”
“Very Own calm down” ta gwada rik'e hannunsa ja yayi da k'arfi “seki je ki samu
Al'ameen d'in tunda shi haka yakeyi bullsh*t kawai a gidana kina kiramin sunan wani
mschww!” A fusace ya miqe ya shiga d'aki tare da shutting door d'in gbam! Hawaye ta
shigayi a yayinda take binsa da kallo. Share hawayenta tayi tabi sahunsa “thank
god” ta furta a ranta jin besa lock ba, miqe kan gado yana fuskantan ceiling yana
chatting ta samesa wanda yana ganinta yawani juya mata baya. Har gabansa tajeta ta
zauna bakin gadon sede banza da ita yayi tamkar besan da halitta gun ba.

Da abun ya isheta a maraice tace, “Very Own am sorry please don't be mad I
didn't mean it in a bad way” har anan be tanka taba “am sorry kaji I can't take it
you being mad it wont ever happen again kayi hak'uri” anan ne yayi gefe da wayan
yana kallonta “pleaseee...” tayi pleading se anan yayi magana “its okay” yace da
ita. Dad'i taji sosai wanda koda Allah yi miki albarka Mama tace mata baza taji
kalansa ba “you are no more mad?”
“Am not” ya amsata cike da ji da kai. Kwanciya tayi a jikinsa “I love you so much
Adeel.”
“I know Babe and I love you too.” Sun jima a haka sannan ta d'ago a hankali “so
me zakaci?” Seda yad'an 6ata lokaci yace, “spaggetti da minced meat akai.” Anzo
wajen tace a ranta tunda take bata ta6a girka jollof na spaghetti ba ina ma fari
yace seta masa heating stew na jiya so take tace masa zata dafa musu fari amman
tasan halinsa yanzu seyace ta raina sa tana gaya mai abinda zeyi. “Kinyi shiru Babe
am starving.”
“Uhmm I was carried away by something don't worry gimmie an hour” pecking nata
yayi lightly a lips sannan ta miqe ta fice.

A kan centre table dake parlour ta d'aga wayarta tare da kiran Lubiee dan
guiding nata kan ya ake dafa spaghetti.
Seda Lubiee tamata iskancin duniya sannan tayi agreeing zatayi helping nata out
haka da prescription and describtion na Lubiee ta samu ta dafa sede gardaman da
tayi mata, Lubiee ta bata amount na maggi da amount na red sauce sam tak'i ji ta
k'ara nata akai abincin yayi wani irin d'an banzan zak'i da yaji seda ta sauk'e ta
d'ana taji tukun “omg!” Ta fad'a tare da kiran Lubiee.
“Babe am dead I should have listened to you wallahi abincin yayi zaqi da yaji
over what am I gonna do?”
“I told you.”
“Shut up and give me a solution” ta katseta a fusace.
“Jimin mata nina 6ata miki girki ne kike neman had'iye ni sede kuci haka kokuwa
ku hak'ura.”
“Awww ma haka zakice good!” kafin Lubiee tayi magana Zeezee tayi hanging. Eating
up nails nata ta shigayi totally out of idea ta zubar ne ta girka sabo? “Kai! It
will take long Adeel can't wait for long me zan yi to?” Ba kalan karkataccen
shawaran da bata bawa kanta ba amman duk it aiint working daga k'arshe tace kawai
zata zubar ta girka sabo zat using ruwan heater. Ta kaiga d'aukan tukunyan kenan
Adeel ya fad'o kitchen yunwa yaci maza mehn!

Firgita tayi har tana neman cin tuntu6e “Babe easy!” Yayi exclaiming “abincin
beyi bane? am starving“ yayi maganan hannunsa rike da cikinsa.
“Uhm... Ermm...” Ta shiga kame-kame next abinda taji kawai hannunsa akan nata
yana neman amsan tukunyan kafin tayi wani k'wararren motsi har ya amsa ya aza kan
cooker ya bud'e. A ido abincin soo yum! Yum! Gabad'aya yawunsa ya tsinke ga
k'amshin curry'n dake tashi. Fork kawai yayi grabbing shi bek'i yaci a tukunyar
bama.
“Ade-” kafin ta qarisa kiran sunansa harya kai baki within seconds count
kamannin face nasa ya sauya, kansa ya juya ya zubar dana bakin nasa a sink sannan
hurriedly ya nufi dispencer ya tsiyaye ruwan sanyi ya kora yajin dashi duk anan
binsa Zeezee ke da kallo tana kakkarwa tana jiran masifa kawai. Seda ya kora yajin
hankalinsa ya dawo dai-dai tukun ya nufi gabanta “what is this?” Ya tambaya a
tsawace. Shiru tayi danko batasan na cewa ba
“Yes... Am talking to you what is this? Dagangan kikayi kome? Saboda you weren't
in the mood to cook, is that it?”
“No Adeel ba-”
“Then yayane?” yayi saurin katseta still a tsawace, tana shaking hawaye na
forming a idonta tace, “am sorry ban iya girkin bane this is my first time.” Dala-
dalan idanunsa ya zaro waje unbelievably “like seriously?” ya tambayeta still not
believing. Kai tayi nodding a hankali. Dariyan rainin hankali ya saki “LOL baki iya
girki ba? And you call yourself a lady? How is that even possible? Me amfanin
auroki danayi then if you cant make me a dish inci?”
“Ver-”
“Shhh!” Ya katseta “dont Very Own me kingannin nan bana wasa da cikina you know
that inhar you cant make me a meal to eat then bazamu shirya dake ba inada mata I
can't depend on buying meal always a waje its two of one, its either ki koyi girki
or I should figure out what to do with you.” Tana share hawayenta tace, “like how
figure out what to do with me Adeel?”
“Yes Zeezee you give me no choice how can I depend on buying food always bayan I
have a wife?”
“To da ban iya bafa?”
“Seki koya its never to late.”
“Adeel in cire kud'i ne baka sonyi I have lots of money zan na saya mana.”
“Owww haka kuma table d'in yayi turning into? Ni zaki nunawa kinada kud'i? You
mean to say banida kud'i kenan right? Saboda kinga kina hawan wancan so called Ford
jeep ko? For a record kisani Genesis G80 na yafi naki taada way much its just the
size, you've got some nerves you know” ya k'are maganan yana watsa mata harara.
Gabad'aya hankalinta ya tashi se hawaye kawai take “omg! Adeel yaushe nace haka?
Thats not what I mean believe me.”

“Oh you're even asking me again? Kin kyauta bravo super woman” be sake jiran jin
me zatace ba ya fita yabar mata gidan gabad'aya. Har k'asa ta sauk'a tana kuka gun
tafi minti ishirin se tuna time da Mama zatace mata tabi Yasmeen kitchen tana ganin
koda abinda takeyi ne amman haka zata ki ga irinta ai yanzu girki nason shiga
tsakaninta da Adeel nata, kukan ta cigaba dayi seda tayi me isarta ta sake aza
sabon tukunya tana cikinyi ta manta wani step again ta kira ta tambayi Lubiee kuma
bataso ta 6ata mata rai d'azu haka tayi kwa6an ta shima bayi cuwuwa. Tana kuka ta
zuba duka a leather bag ta zubar a dustbin sannan t had'a golden morn tasha.
Har 5pm Adeel be dawo ba, wayarta taja ta shiga kiransa haka har ta tsinke bai
d'agawa haka ta rufe kanta a d'aki ranan ta yini tana kuka. Abu fa kaman wasa har
8-9-10 kai har 12 na dare Adeel be dawo b gashi yanzu ma kwata-kwata kashe wayan
nasa yayi. Ba inda Zeezee batasa kanta ciki ba gabad'aya baccin dake idonta ya
watse tayi kuka har ta godewa Allah. A parlour bacci ya risketa se 6:30am ta tashi
nanma bataga Adeel ba. Ta shiga d'akinsu donyin alwala taji kaman motsin mutum a
bathroom in seconds count k'ofan ya bud'u revealing Adeel, binsa da kallo ta
shigayi ma'ana ya dawo ya wuceta kwance a parlour be damu ya tadata ba koya d'agota
ya kawo ta ciki ba kenan. Ganin kallon bana k'arewa bane ya d'aga towel dake a
wuyansa ya shiga goge gashin kansa ahaka har yazo ya wuceta ya nufi wardrobe yana
neman kayan sawa. Guiwowi suna kakkarawa ta juyo direction nasa sannan cikin wani
erin murya me nuni da tsan-tsan damuwa tace, “Adeel ina ka kwana jiya?” Banza da
ita yayi yana me cigaba da harkan gabansa.
“Adeel am talking to you” yanzu kam ta soma hawaye.
“Somewhere better than here” ya amsata in an I-dont-care tone.
“Baka fa kwana a gida ba Adeel, I waited for you for so long har kusan 1am baka
shigo ba.”
“Ke kika so dan ni bance ki jirani ba” anan ya ciro kayan da zesan ya juya kenan
da gudu Zeezee taje ta fad'a jikinsa tana wani irin kuka me tsuma zuciya, hugging
nasa gagam tayi se kukan take, kayan nasa ya wulla kan gado amman yak'i hugging
nata back. Tana kukan ta soma cewa;
“Adeel am sorry, am so sorry dan Allah kayi hak'uri that wasn't my intention
please stop being mad in girki kakeso na koya I'll but stop staying mad please I
beg you...” Ta k'arasa da kuka kaman bazeyi hugging nata ba sekuma ta basa tausayi
shi kansa yasan punishment daya bata yayi tsauri, a hankali ya d'aga hannayensa ya
zagayesu a bayanta tare da sake kwantar da ita a jikinsa “its okay stop crying am
sorry also just dont try it next time okay?”
“I wont, ever.”
“Shikenan toh bar kukan” a hankali ya samu tayi shirun sannan y d'agota daga
jikinsa tare da share mata hawaye “is okay, kinyi Sallah?” Kai ta kad'a as a
response.
“Jekiyi toh.”
Zaka sake fita ne?” Ta tambaya a hankali cike da damuwa.
“I was amman na fasa yanzu” with a nod ta nufi toilet tayi alwala tafito tayi
sallah. Koda Adeel ya koma bacci ita ta kasa as tana tunanin ya za'ayi ta koyi
girki daga k'arshe ta yanke hukuncin registering online cookery class.

****
By 10:30am su Zeezee suka gama breakfast yauma chips tamusu frying da scrambled
egg. Suna zaune a parlour Adeel na kallon sports whereas ita tana chatting tayi
focusing sosai se murmusawa take da alama tana enjoying chat da take. Catching her
always for 3 times tana murmushi Adeel yayi deciding daya tambayeta dawa take
chatting.
“Babe who are you chatting with?”
“Its no one” ta amsa a takaice chan tace “just a friend.”
“Gender?” Ya tambaya a take.
“Oh calm down Adeel childhood friend d'ina nefa kawai.”
“Amman ban hanaki chatting da maza ba?”
“Ad-”
“Yes or no?” Yayi cutting nata off.
“No I mean Yes but-”
“Pass me your phone” ya buk'aceta “Adeel this isn't fair kaima fa kana chatting
da female friends naka amman ni just this once ma bazaka barni ba” tayi explaining
a nitse.
“Owww you're comparing us kenan pass me your phone nace” kaman bazata miqa mai ba
kawai ta basa ta tashi ta bar mai parlourn ma gabad'aya a zuciye ta nufi d'akinta.
Warning ya kashe wa friend natan sannan ya goge contact nasa daga wayar tata
gabad'aya. Seda Azahar ya lek'a d'akin nata yaga tana bacci, wayar kad'ai ya ajiye
mata kan dressing mirror sannan ya k'arasa yayi positioning nata tare da pecking
nata ya fice yawonsa.
Da La'asr da Zeezee ta tashi bayan tayi Sallah ta leqa waje as expected bata ga
motansa ba. Ita ta rasa ina yake zuwa kwana biyu kullum bai gida. White macaroni da
sliced carrots and peas ta dafa musu sannan tayi heating stew na Mami ta had'a
dining table. Ganin har 4:30pm be dawo ba ta d'iba nata taci, ba Adeel ya dawo gida
ba se Maghrib. Sun idar da Maghrib in a soothing manner ta tambayesa yadda baze
fusata ba “Very Own nace d'azu ka fita baka sanar dani ina zaka ba.”
“Yeah na shiga naga kina bacci, I visited a friend.” D'an sanyi kad'an taji a
ranta “ohh okay then” dining suka nufa sukaci abinci suna hira, sun gama Adeel ya
nufi bayi ya watsa ruwa se gani tayi ya ciro kaya da alama fita yake da niyan yi.
Zama tayi a bakin gado tana binsa da kallo tana ganin supras da ya zaro ta gano
party zasa. Zuciyarta ne ya mugun fad'i yanzu Adeel yana nufin da igiyan auranta
akansa zena fita midnight party? Yaushe Al'ameen ya ta6a yi mata haka? Shin da ba
kyautata masa ma take ba. Yana gama turare jikinsa ya doso gabanta tare da pecking
nata a cheeks “Babe zan d'an fita I'll be late so sleep early, I love you ahh! Meds
naki” nan da nan yaje ya 6allo ya bata sede tak'i amsa.

“Sweetest Love kina 6atamin time fah I'll be late, kar6i mana.”
“Late? For the party?” Kaman da ze mata k'arya sekuma ya fad'a mata gaskia “yes.”
“Very Own yanzu party zaka fita da daren nan baka ma san lokacin da zaka dawo ba
kana ganin ka kyautamin kenan?”
“What gibberish are you saying Babe? Its not as if I'll be gone forever zan dawo
zuwa gobe ina?”
“Nikuma hak'k'i na a matsayi na na matarka fa?”
“In hak'k'in ki kikeso ai akwai gobe sena baki gobe take ur meds please.”
“Bazan sha ba.” Ta fad'a in a low tone.
“Kikace?” Sanin ta sake nanata abinda ta fad'a suna iya yin fad'a kaca-kaca tace,
“nothing” tare da amsa ta had'iye haka tana ji tana gani ya fita yabar gidan. Jin
moisture kawai tayi akan fuskanta, tana ta6awa tajiyo hawaye. Kuka ta shigayi sosai
Allah sarki seta tuna Al'ameen inhar baya gida toh yana office ne in ba haka ba
kullum yana gida dukda bawai farinta masa rai take ba amman hakan besa kullum yana
fita waje ba. Seda tayi kukam me isarta sannan ta watsa ruwa finally ta kwanta da
k'yar bacci 6arawo ya sace ta.

**
6:34am the following day Adeel ya dawo gida sid'ak-sid'ak ya nufi d'akinsu ya
rage kayan jikinsa sannan ya haura gado ya sameta suka kwanta se pass 9 ta tashi ko
da ta gansa a gefenta batayi ta kansa ba. Wanka tayi ta had'a musu breakfast bata
jirasa ba tayi nata. Se pass 12noon Adeel ya tashi yayi wanka yafito parlour inda
ya tsinceta tana goge TV stand. Idanunsu na had'uwa tayi saurin kawar da kanta daga
direction d'in danko har yanzu bata sauk'o daga abinda ya mata jiya ba. Shima d'an
rainin hankali ignoring nata yayi ya nufi dining ya karya wanda yana cikin yi yaga
Zeezee ta nufi d'aki bayan mintuna kad'an ta fito all dressed up. “Ni zan fita zani
gidansu Lubiee.”
“Kuma da izinin waye?”
“Kaman ya da izinin waye? Am letting you know.” Ganin ranta fa a 6ace yake ya
tashi ya nufi inda take tare da patting both shoulders nata. “Are you still mad
Baby?” Banza dashi tayi, gyalen data ruhu dashi ya cire a hankali ya ajiye a gefe
sannan jakar nata “kin fasa kar6an hak'k'in kine?”
“Nafasa banaso you are wasting my time please.” Ta fad'a ba tare da ta kalli
direction nasa ba, hannunsa ya aza kan face nata yana rubbing in a romantic way
“haba mana Sweetest Love it was a friend's birthday I can't miss it for the world
amman trust me I didn't touch any girl there.” Se anan ta kewayo da idanunta kansa
“how do you expect me to believe that?” Wani mayen kallo yake mata yana lasan lips
nasa, “like this” ya amsata kafin ta gane me yake da niyyan yi kawai taji ya
d'agata sama a hannunsa just like a bride. “Keep me down Adeel banas-” her last
word was crashed on his lips. Kissing nata ya shigayi wanda tun tana neman turesa
seda tayi giving in atlast. D'akinsu ya kaita tare da direta kan gado anan nikuma
na basu privacy.

****
Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa, Adeel da Zeezee basu ta6a yin good two or
three days basuyi fad'a ba as yakasa dena zuwa midnight parties, abinda Zeezee tafi
tsana kenan fiye da komi. Ita kuwa ko gidansu Lubiee tace zata se yayi ta mata
corner-corner at last ya hanata zuwa. Rayuwar aurenta de yabar mata dad'i a
takaice, ita she is trying her possible best to make him happy amman it aiint
working. Ga massive improvement a girkinta duk don su zauna lafiya amman abu ya
gagara, kuma ita harga Allah ta gaji yanzu is like sex machine Adeel keson maidata
kullum baya gida da zaran ya dawo kuma har ya sake fitan yana kanta, tagaji ita
shikenan batada wani amfani mai se desire or need nasa ya taso abin yafara isarta.

Yau ma kaman kullum bayan Adeel yagama biyan buk'atansa da ita ya tashi yashiga
bayi ita tana nan miqe kan gado har yanzu. Few minutes afterwards Adeel ya fito da
towel d'aure a waist nasa yana goge gashin kansa. Mutum d'aya ne ya fad'o mata a
rai which is none other than Al'ameen, se tuna how muscular and builded up his body
is take, packs gasunan a fili har shida, she misses staring at his naked body.
“Tunanin me kike haka?” Adeel dake neman zama akan stool yayi maganan da man
shafawansa rik'e a hannunsa. Kai ta kad'a da wuri “babu” tamai k'arya “you seem
carried away.”
“Erm Adeel nace da bikin mu how many months now ya kai six?”
“Six I guess, yes six months... One week... Three days exactly today.”
“Kana ganin lafiya kuwa?” Tayi maganan not sur of her words.
“As in?” Ya tambayeta da sauri.
“Very Own its been six months amman ko 6ari ban ta6a yi ba.” Ita dariya ma tabasa
wai dama bayan magunan da yake bata take ta sha ba fashi how can she get pregnant?
“Adeel you are laughing.” Ta fad'a da mamaki.
“Yes I am” ya amsa confidently within laughter.
“Its no joking matter Adeel, matarka maybe cannot concieve kai kuma kana dariya?”
“Not so fast wai ke dama you are ready to be a mother ne?”
“What are you talking about Adeel? Daman meye amfanin auren badon a haifafa
bane?”
“To some not to all.” Yana kaiwa nan ya miyar da man ya nufi wardrobe yana fiddo
da kayan da zesa.
“What do you mean Adeel?”
“I mean am not ready yet to be a father am still young for God's sake Zeezee am
just 26 going to 27.”
“Adeel wani irin magana kake haka? 'Yan 20 ma sukayi aure suka haihu bale kai?
You mean to say you are happy that maybe I cannot concieve kenan?”
“Your words not mine” yasa kayansa sannan ya nufi gaban dressing mirror yana taje
gashin kansa yana cikin yi wayansa dake kan side drawer yahau buzzing. Kasancewar
Zeezee na akan gado tayi saurin leqawa sede kafin tagama karance wake kiran fyayi
sauri ya d'auke wayar.

*MIEMIEBEE*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febuary, 2017*
4⃣2⃣

_I'm hereby honouring this page to none other than my *BLOG FOLLWERS AND
READERS* thank you for making it a lit👌🏾there, it was impossible before but with
you its now possible. Thank you so much for your inspiring comments, love and care!
Am proud to have and know you guys, I love y'all oceans and galaxies❤❤❤ #OneLove❤_

“Kekuma mena leqa min a waya?” Yayi maganan yana duban wake kira.
“Inga wake kira is it a crime?”
“It is banason shisshigi“ zata sake magana ya aza hannunsa bisa lips nasa nufin
tamai shiru, shirun tayi tana kallonsa. A nitse yayi picking call d'in “Halo?” Ya
fad'a cikin sanyin murya. K'ure kunne Zeezee tayi donjin muryar ta mace ce kona
miji aikuwa taji a lady's voice. Take gabanta ya fad'i sede ta kasa jin me matar ke
fad'a and after a while Adeel yayi responding da “okay am on my way, see you” tare
da hanging. Dnqaree!
“Who is she?” Ta tambaya zalla cike da kishi
“A friend koda me kikeson ji?”
“Adeel you are lying wacece ita?”
“A friend ha'a nifa banason tak'uri dayawa sekace wata Boss d'ina kina asking
d'ina questions.”
“Da kyau, yanzu bayan ka gama biyan buk'atanka dani zaka barni kaman kayan wanki
kaje ka samu 'yan matanka a waje right?”
“Kanki akeji ni banida time na small talks d'innan” bata sake cemai komi ba har
yagama feffeshe jikinsa da turare ya fice dan kuwa Adeel mamaki yake bata yanzu.
Hawaye kawai taji yana bin k'uncinta she have to find out ko Adeel dagaske ne yayi
budurwa a waje amman kafin nan meyake nuf'i d'azu dayace "am not ready to be a
father?"
“Oh God no!” Tayi exclaiming cike da tashin hankali “what if... What if... No it
cant be possible Adeel baze ta6a bani abinda ze cutar dani ba.” Degree of rolling
tears nata ne ya k'aru “what if he did?” Hannu tasa ta miyar da gashinta baya tare
da jan vest nata dake kan gadon tasa sannan ta miqe all confused. Wardrobe nasu ta
nufa ta bud'e side nashi, ita kanta batasan me take nema aciki ba amman haka tayita
searching tana duba cloth after cloth chan a last counter ta zaro kwalayan maguna
guda biyu sunan ta karanta ta sake miyarwa.
After a while ta sake zaro su tare da jan stool ta zauna, jikin kwalin ta shiga
karantawa to her biggest suprise tagano maganin hana d'aukan ciki ne. “Innalillahi
wa inna ilaihi raji'un this can't be true” fito da capsules d'in tayi har 6ari
hannunta ke don tabbatar da zarginta aiko tana 6alla d'aya ta tabbatar shine
maganin da Adeel yayi ta bata for the past 6 months ba fashi.

Hawaye kaman lalacaccen famfo se fitowa suke ba makawa. Kuka tayita yi abin
tausayi what have she ever done to him to deserve this? Mesa be fito fili ya gaya
mata bayason haihuwa ba yaso seta fara family planning amman yayita d'ura mata
maganin da she is sure yanada side effects. Ashe dama back then daya ta6a ce mata
suyi eluding suje suyi aure and have their own kids was all a lie, tabbas na miji
ba d'an goyo bane. Yanzu shikenan ita bazata ta6a ganin jininta ba kenan? “Ashe
Adeel never loved me he was just after my body and thats all, how could you Adeel?”
Ta tambayi kanta cikin tsan-tsan takaici da nadama. “I regret it, I regret every
single bit of it, I shouldn't have gave my pride to you Adeel, ba kai ka cancanta
ba Ya Al'ameen ne ya cancanta. Why didn't I thought of all these before? Adeel was
never my true love Ya Al'ameen is nasan komin meye nayi wa Ya Al'ameen baze ta6a
6ata min rayuwa as how Adeel did ba. Shi d'inda ban ta6a kyautata masa ba, ban ta6a
yimai abinda yakeso ba amman dai-dai da rana d'aya be ta6a cutar dani ba, hasali ma
kyautata min yake akan wulak'anci da zagin da nake sak'a mishi dashi. Oh! Allah na
tafka babban kuskure na auran Adeel, Ya Al'ameen please forgive me nasan alhak'inka
ne yake bina” ta k'are maganan tana kuka me tsuma zuciya. Tafi minti ishirin zaune
gun tana kuka sannan daga bisani ta nufi bayi tayi wanka cikin k'ank'anin lokaci ta
shirya tsaf cikin doguwar riga tad'au kwalin maganin ta fita dashi.

Asibiti direct ta nufa ga layi kaca-kaca amman haka tayi zaman jira har seda
turn nata ya iso that was around 3:12pm. Takai ga shiga ganin Dr wayanta dake rik'e
a hannunta ya shiga ringing tana kai dubanta taga Very Own na flashing akai, wani
haushi da tsanansa taji na running through her veins inhar dagaske abu ya samu
mahaifarta bazata ta6a yafewa Adeel ba. Kashe wayar tayi gabad'aya ta miyar jaka
sannan ta shiga d'akin bayan sun gaisa da Dr ya tambayeta meke damunta. Kwalin
maganin ta zaro daga jaka ta miqa mai “Dr please I need all information about this
drug” amsa yayi ya duba sunan “are you married?” Ya soma tambayarta.
Kai ta gyad'a a hankali.
“Ke kike sha?”
“Yy... Yes” tayi stammering.
“But why? Yanada side effects sosai in haihuwa ne bakiso nan kusa you should
have simly gone for one out of the numerous family planning methods, this is a bad
idea for how long kike sha?”
“Dr for about six months now” ta k'are maganan moisture na filling a idonta.
“What!” Ya zaro ido. “Are you serious? 6 months fa kikace?”
“Yes Dr nima ban ta6a sanin shi nake sha ba se yau mijina ne yake bani dan Allah
tell me what damage it has done to me already.”
“Am sorry Ma'am but I fear it has destroyed your womb.”
“Inna lillahi wa inna ialihi raji'un!” Ai seta hau kuka gun ba yadda beyi da ita
ba tayi shiru tak'i seda tayi me isarta sannan tad'an yi pausing. “Calm down okay?
Karki tada hankalinki zamuyi scanning mu duba mugani miracles happens, tunda ke
bakiyi niyyan sha ba baki ake Allah na iya duban niyan ki ya miyarwa mijinki da
aniyansa just pray Allah yasa be miki damage da muke gudu ba.”
“Dr nasan damage kam has already been done dan ko 6ari ban ta6ayi ba for six
months after marriage, abu d'aya nakeson sani Dr please tell me the truth” ta tsaya
ta sharr hawayenta.
“Ina jinki Ma'am.”
“Yanzu koda na bar sha daga baya bazan zo in iya concieving ba?” Shiru yayi
nad'an tsawon lokaci. “Please Dr just tell me mahaifata ta 6aci kenan kwata-kwata?”
“Gaskiya to be frank with you tunda har kince for six months kike sha zeyi wuya
ace zaki iya concieving baby saboda ko bamuyi scanning ba I know ya riga ya miki
damaging womb cause there was a lady also data sha for just a month, mahaifarta ta
b'aci gabad'aya daga k'arshe surgery akayi mata aka cire aka yasar dan ya zama ba
amfani. Amman kinsan kowa da yanayin jikinsa maybe naki baya jin magani da wuri.”

“Innalillahi! Yanzu Dr kana nufin bazan iya ta6a haihuwa ba kenan?” Kasa tare
hawayen tayi se zuba suke.
“Zeyi wuya to be frank Ma'am amman kinsan akwai miracles, babu abinda yakai ikon
Allah mamaki saboda ba yadda Allah baya abinsa kisa a ranki wataran zaki haihu kema
kuma ki dage da addu'a in shaa Allahu you wont be disappointed.”
“Shikenan Dr nagode.” Tayi managing ta fad'a.
“Bakomai sauran muyi scanning muga shape na mahaifar naki ko?”
“No please, bazan yi ba banason inji nima se an yanke min nawa koda ya 6aci ne
abarmin shi a jikina.”
“But Ma'am yakamata kiyi scanning d'in still.”
“A'a wallahi Dr tashin hankalin danake ciki ma kad'ai ya isheni damuwa basena
k'ara wani akai ba thank you” tana kaiwa nan ta miqe se soaking with tears tissue'n
hannunta yake “Ma'am! Ma'am!” Dr ya shiga k'olla mata kira, kasa amsasa tayi ta
fita da sauri inda ta nufi motarta ta zauna ta bud'e sabon dandalin kuka.
Takasa tayi shiru, hawayen har kaman so suke su k'are ga d'an banzan yunwan da
takeji. Babu abinda yafi bata takaici kaman in ta tuna batada gatan iyaye yanzu, da
ace auren mutunci akayi mata da albarkan Baba da Mama aciki da hankali kwance zata
je ta irga musu komi da yardan Allah kuma suyi mata tsaye akan case d'in se an
k'wato mata 'yancinta. Amman yanzu fah? Ba yadda ta iya haka zata hak'ura kokuwa
taja Allah ya isa.

Se 4:36pm Zeezee ta isa gida alokacin har Adeel ya gaji da trying number'nta,
jira kawai yake ta dawo ya hauta dan kuwa ya hanata fita bale wai yau bada izininsa
ba. Ta bud'e k'ofan parlour ta tarar dashi zaune bisa sofa da remote rik'e a
hannunsa. Bata bari idonsu ya had'u ba ta kawar da kanta da wuri. Ji kawai take
kaman ta d'au wuk'a ta cakka mai for what he did to her.
“Ina kikaje? Ma tukun ban hanaki fita ba?” Ya tambayeta cike da tsiwa. Ko d'aga
kai ta kalli direction nasa batayi ba, hakan ya sake k'ullar dashi. “Zeezee am
talking to you, are you deaf?” Nanma shiru hannu ta zira a jakarta ta ciro kwalin
maganin sannan ta nufi har gabansa ta ajiye akan centre table. Mamaki ne karara ya
bayyana a fuskansa be tsamman zata iya tatso magunan ba a inda ya 6oye don haka
jikinsa yayi sanyi, “a ina kika samu wannan?” Ya tambayeta finally.
“Wow! Abinda kad'ai zaka iya tambaya kenan? A ina na samu? Ba dogon surutu
nakeso ba just tell me menayi maka a rayuwa da ka za6i daka 6atamin mahaifa Adeel,
mena maka?”
“What are you saying?”
“Don't play dumb sarai kasan maganin nada side effect amman dake you are a beast
a horrible one you proceeded on and kept me taking it wallahi kasani bazan ta6a
yafe maka ba for what you did.” Miqewa yayi ya tsaya, “look at you daman nace ki
yafemin ne? Please don't ever forgive me, am not ready to be a father and that was
the only decision to make.”
“Ashe maqaryaci ne kai ban ta6a sani ba, waya ta6a cemin we should elude muyi
aure and have our own kids?”
“Don na fad'a doesnt mean I meant it and koda wasa karki sake referring d'ina da
maqaryaci I wont let it go.”
“Mene inba maqaryacin ba? Me zakamin? Kasheni? I wouldn't be suprised tunda har
ka iya ka kashemin mahaifa hakan na nufin zaka iya kasheni nima mugu kawai.”
“ENOUGH OKAYY!!” Ya tsawata mata amman ko firgita batayi ba “its not enough until
I say it is kabani takardana this instant.”
“LOL” ya saki dariyan rainin hankali. “In baki takardanki? Sekuma kije ina? Ko
kin manta bakida gun zuwa ne? Well if you do lemmi remind you, Babanki yayi
disowning naki bakida kowa se ni gomma kin bini a hankali ‘yar sadaqa ma dake ko
kin manta a kyauta Babanki yabani ke? Don haka bakida value ko kad'an a idona. Bama
wannan ba ajinki akwai na mijin da ze zauna da macen da bazata iya haihuwa bane
yanzu? You are nomore a complete woman Zeezee your womb is bad you can't concieve
so is better ki bini a hankali nine kad'ai gatanki a duniyan nan. ”

Karyewa gabad'aya zuciyarta tayi, tabbas ba k'arya a zancensa amman sede duk
abubuwan da suka faru shine sila da tun lokacin taji maganan Lubiee da Adeel
bashida bakin da zai mata gori har yace da ita 'yar sadaqa. Hawaye kawai taji na
forming rapidly a idanunta kafin ta hankara taji sauk'ansu kan cheeks nata. “Gomma
kukan de shi ze rage miki takaici” yana kaiwa nan ya bar mata parlourn. Sauk'a har
k'asa tayi gun tana kuka me tsuma zuciya, tayi nadama, tayi nadaman kawo Adeel
rayuwarta.

***
Through out ranan word be sake had'ata da Adeel ba dan tunda ta shiga guest room
bata fito ba seda taji k'aran engine na motansa, anan ne ta fito ita ko htl ne ta
gwammaci tayi zamanta ciki kafin ta samu permanent place don batajin zata iya
cigaba da zama da mugun halitta kaman Adeel, if only tasan true colour'nsa da bata
aure sa ba. “Oh Allah! am missing you Ya Al'ameen please forgive me” ta furta a
ranta. D'akinsu ta shiga ta had'a akwati d'aya da wuri-wuri tazo da fita ta murd'a
handle seji kawai tayi a rufe, “like seriously? Rufeni Adeel yayi?” Rattling k'ofar
tayita yi amman ina sam bayi bud'uwa, kuka ta shigayi amman hakan besa ta hak'ura
ba seda k'arfin jikinta tas ya k'are sannan ta tattara kanta tayi guest room. Har
after 9pm Adeel be dawo gida ba, yunwa ne ya korata ta nufi kitchen ta had'a oats
tasha sannan ta sake komawa d'aki gabad'aya tunanin duniya ya sata gaba. A haka har
bacci yayi awon gaba da ita.

Adeel kuwa se dab da Asubah ya dawo gida bayan ya idda Sallah ya koma bacci se
pass 10 ya tashi yayi wanka tsaf sannan ya leqa parlour. A dining table ya tarar da
ita tana had'a tea, gefenta kuwa indomie ne da sardines aciki seda fried egg a
gefe, kafin ta hankara kawai taga ya d'aga plate natan “Adeel ya da haka give me
back my plate.“ Tayi stating angrily.
“In ke kike siyan abincin seki amsa aikin banza kawai, ki sake girka wani am in
a hurry zan fita.”
“Ina ruwana da fitanka give me back my plate.”
“Ki amsa idan kinada k'arfi mschww!” tunkud'eta gefe yayi seda ta kusan fad'i
sannan ya k'arasa had'a tea'n nata yakoma d'aki. Hawaye ta soma without knowing
how, a hankali ta share ta koma guest room ta baje kan gado ta cigaba da aikin
kukan.

15 more minutes taji an bankad'e mata k'ofa which she is sure is no one other
than Adeel ko juyawa ta kallesa ma batayi ba “Ke!” Ya kirata cike da raini da nuna
isa. “Ke! Baki jina ne? Don't let me repeat myself turn around.” Seda ta d'au
tsawon minti d'aya sannan ta juya a hankali tana kallonsa kayan wankinsa dake
hannunsa ya zuba a k'asa “gashi do my laundry in kika gama seki girka min spaghetti
for lunch, up you go.”
“Nice zan maka laundry?” Ta tambayesa in a low tone cike da mamaki.
“Baki tab'a ganin mata suna yima mazajensu wanki bane?”
“Bana d'aya daga cikin jerin matayan can don haka bazan wake komi ba, ko ka wanke
da kanka kokuwa ka kai laundry su wanke maka.”
“What? Me kikace? Come again.”
“Bazan wanke ba nace ai ba 'yar aikinka ce niba.”
“LOL toh ai baki sani ba Zeezee, me aiki ma yafiki min ke k'ima da daraja a ido
saboda su atleast da kud'i zan d'auko su kekuma fah? A sama fa na sameki don haka
kibar 6ata min lokaci and do as I ask.” Tana hawaye tace, “bazan yiba“ isketa yayi
lokaci guda zuwa kan gadon tare da fincikota da hannunta. Wani irin riqo ya mata
wanda tuni k'arfin kukanta ya dad'u dan azaba. K'ok'arin kar6e hannunta take amman
takasa. “Adeel ka sakeni” ta fad'a in between tears.
“In saki aiki kice baza kiyi ba?” Ya sake dandame rik'on daya matan k'ara ta
saki a sanadin haka. Da zafin ya isheta tana kuka sosai tace “zanyi, zanyi ma
wankin don Allah ka sakeni.”
“Repeat it again.”
“I'll wash your clothes for you ka sake min hannu please.” Ta qare maganan tana
kuka sosai, se anan ya saketa wajen har yayi dark pink colour tsan-tsan azaba.
“Don't try crossing me again” yana kaiwa nan ya fice, kan gadon ta koma ta
cigaba da rusa kuka sosai na haqiqa.

Seda tayi me isarta sannan ta tashi taje ta wanke mai kayakin tas ta shanya ta
kuma aza mai girki. Dad'i sosai taji ganin be rufe k'ofa ba, nan da nan taje ta
d'auko akwatinta sede kash tana isa bakin gate ta tarar dashi a rufe. Kulle idonta
kawai tayi se hawaye suka soma fita, abin tausayi ta koma ciki ta cigaba da kuka
tana cikinyi taji buzzing na wayarta, Lubiee taga ke kira amman batajin zata iya
amsawa haka har ya tsinke tana gani.

*~ *~ *~
Rayuwa kuma haka ta canza, Zeezee kullum cikin kuka ba kalan azaban da Adeel bai
galla mata. Ta yini a aiki takuma ta tashi da aiki gashi koda wasa ta gwada cewa
bazatayi ba threatening nata yake sosai, daga yasata yimai wanki, se girki, gashi
ya tashi dawowa daga yawonsa yanzu da gan-gan se ya taro ambaliyan friends nasa
about 5-6 of them suci lunch. Zeezee kullum tsaye bakin gas, da iskancin Adeel ya
tashi ma yace shi yabar siyan Gas d'in wai tayi tsada charcoal stove ya sai mata
haka kullum tana waje tana mishi girki da friends nasa which she don't get any
thanks in return. Se tunawa kawai take da bawan Allah Al'ameen. Shin ma ta ina zata
soma neman yafiyansa? Dukkanin rashin hankalin da take mai dai-dai da rana d'aya be
tab'a wulak'anta taba ko tsawa bayi mata a kullum cikin missing Al'ameen take se
yanzu ta gano the true definition of Love and Adeel was never her true love
Al'ameen is amman tasan its too late now maybe yanzu Al'ameen ma yayi aure ya manta
da ita.
Abin da yafi bata takaici kuwa shine yanzu koda ta kira Mama, Mama bata picking
calls nata ba ita kad'ai ba harta sauran 'yan uwan nata. Inhar ba aiki Zeezee keba
toh tana kwance a d'aki tana kuka ne, cikin sati biyun nan ba k'aramin zubewa
Zeezee tayi ba don har haskenta ya ragu sosai, gata nan ne kawai kullum cikin
nadama take.
****
Yau da safe tana girka breakfast a waje kan charcoal ta baro wayarta a kitchen.
A dai-dai lokacin da wani friend nata Imam ke turo mata saqo a dai-dai lokacin
Adeel ke shigowa kitchen ganin haske yayi flashing kan screen natan yayi sauri ya
leqa kasancewar iphone na reading notifications ya samu ya karanta saqon as
“morning dear ya kike?” Wani banzan kishi ne ya tokaresa d'aga wayan yayi yasa a
aljuhunsa wanda a dai-dai nan Zeezee ke shigowa da soyayyen doyanshi da sardine
sauce. Bata cemai komi ba ta wuce dining ta ajiye ta dawo kitchen d'aukan wayarta
taga babu sede kallo d'aya tama Adeel ta gano shi ya d'auka. “Kabani wayata.”
“Bazan bada ba, iskanci zaki soma kawomin gida? Waye Imam and why is he
referring to you as a Dear One?”
“Ina ruwanka kai kullum da kake waya da 'yan matanka na ta6a yima magana ne?”
“Are you talking back to me?” Fuskanta ta wajen bakinta ya kama da k'arfi ya
maqure, “don't you dare banason raini kina ganewa ko?”
“Let me go you're hurting me” ta iya fad'a kad'ai don azaba seda yaga tana
wahala sosai ya saketa. “Mugu, azzalimi kawai Allah ze saqa min kuma ka bani wayana
ai ba kai ka siyamin ba don haka you have no control over it.“
“Haka kikace?”
“Yes give it back.” Hannu ya zira a pocket nasa yafito da wayan da mamakinta
taga ya tarwatsar dashi a k'asa da duk k'arfin da Allah ya basa “I guess I do have
a control over it now.” Yana kaiwa nan ya fice sauqa tayi har k'asa gun tana kuka
abin tausayi. Yanzu kuma a ina zata samu wani wayan tunda ko bakin gate bayi
barinta ta taka. Seda taji ya fita tayi d'akinta. Landline ta d'au ta kira Lubiee
tana kuka sosai gabad'aya hankalin ta ya tashi daman tasan ba lafiya ba yadda taji
Zeezee shiru kwana biyu.

“Babe please calm down and tell me meya faru? Kina gida ne inzo right away?”
Lubie tayi stating hankali duk a tashe. Hanci taja sannan tace, “ko kinzo ba ta
inda zaki shiga locking d'ina yake baya bari na in taka koda bakin gate.”
“Subhanallah shi waye?”
“Adeel.”
“Adeel? Adeel fa kikace kunyi fad'a ne?”
“Kaca-kaca Babe ashe Adeel ba sona yake ba tunda ya ringa bani wani capsules
seda na rasa mahaifata.”
”Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!” Labarin komi Zeezee ta bata wanda ya mugun
bawa Lubiee mamaki bata ta6a sanin Adeel is as wicked as this ba. Ranta ya matuqar
6aci tayi hanging call d'in tare da kiransa. Se a karo na biyu ya d'aga.

*MIEMIEBEE Team #YGC!*


www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febuary, 2017*
4⃣3⃣

_Its my biggest pleasure giving this whole page to you guys alone *MIEMIEBEE
FANS❤* Group, its indeed a blessing having you guys. Funny how you'd spend the
whole day talking about Zeezee, Adeel and Mag-Gen LOL well it gives me pleasure
going over and over your chats I never get tired of it. God bless you for me AMEN I
heart y'all to pieces, a big heart for y'all ❤ #OneLove❤_

“Halo Lubiee?”
“Haba Adeel! Haba what's wrong with you?”
“Kekuma menayi kike scolding d'ina haka?”
“Harma tambaya na kake? Mesa kakeyi wa Zeezee haka? Me tai maka da har zaka riga
d'ura mata magani kana destroying mata womb?”
“Oww haka tace miki? Toh nayi kinga please am busy right now I dont have time for
this” bejira jin me zata sake fad'i ba ya katse wayar, mamaki ne sosai ya rufe
Lubiee shiyasa ita tun farko bata so Zeezee ta koma gidansa ba, mutuncin sa kad'an
ne.
Se 9pm Adeel ya dawo gida yana watsa ruwa ya nufi d'akin Zeezee ya tarar da ita
zaune a one angle cikin d'akin ta had'a kai da guiwa. Koda taji shigowansa bata
d'aga kai ba, “Ke Zeezee!” banza dashi tayi “am talking to you tun ba ayi nisa ba
har kin soma kire-kiren waya kina yad'a what's going on between us? Ke kika jawo
komi inda kin bini a hankali da duk haka be faru ba, apologise to me and we will be
back as how we use to be before.”
“Apologize to you?” Ta d'ago kai finally ta furta da mamaki, “menayi ma da zan
baka hak'uri? Ni da kai waya kamata ya baiwa wani hak'uri? Kamin destroying mahaifa
an kana expecting d'ina na baka hak'uri? For what? Adeel koda kaine autan maza na
yafe ka, na hak'ura abinda kamin ko maqiyi na bazemin ba.”
“Haka kikace? Kece zaki cutu just apologies to me and it'll bygone.”
“Never! Am never apologising to you again wad'an dana maka da a baya suma inda I
can take them all back da nayi, ka cinye kanka kaga dama, nayi nadaman saninka
Adeel, I wish I've never met you, inda Allah ya nuna min halinka da ban rabu da Ya
Al'ameen na aureka ba.”
“Call his name the way you want ba shi ze sa ki koma gidansa ba, in kinga
k'afafunki sun taka waje believe me gawanki akazo fita dashi. You wanna play the
game? Lets play it. Now ki tashi ki had'a min dinner am starving.”

Hannu tasa ta share hawayenta, sannan tabisa da dirty look ta miqe ta nufi
kitchen d'in, potatoe porriadge ta had'a mai sannan tayi setting dining ta koma
d'akinta.
Tana zama kan gado telephone dake kan bedside drawer yafara ringing and ba tare
da 6ata lokaci ba ta d'aga “Hello Zeezee?” Lubiee tayi stating in a swaying motion.
“Na'am Lubiee.”
“Ya kike?“
“Lafiya.“
“Zeezee am so sorry please dana san da haka da ban fara hooking naku up ba since
from the beginning.”
“Lubiee its not your fault ni nayi insisting back then so stop apologising.“
“Am sorry please kiyi hak'uri we have to figure out what to do ko Mama ne mu
kira.“
“Theres no way out Lubiee, Mama is also mad at me haka Adeel ya sani a gaba back
then da zamuje Florida yace karna kira Mama nikuma na biye masa, hakan ba qaramin
6atawa Mama rai yayi ba koda na kirata bata picking I have no one left Lubiee seke”
ta k'are maganan tana kuka sosai.
“Subhanallah Adeel is such a horrible beast kiyi hak'uri please and kisa a ranki
kinada Allah yanzu ya zamuyi nasan is of no use kiran Maminsa saboda bata ganin
laifinsa ko kad'an.”

“Lubiee just ki tayani da addu'a that's all I ask.”


“In shaa Allah best franndd.”
“Lubiee I just don't get it, mena ta6a yiwa Adeel da zemin haka? All I've ever
wanted is to be with him and make him happy, I loved him with all that I had aman
this guy failed to see it I dunno why.” Taja tissue tana share hawayenta.
“Masani se Allah amman Zeezee bazan 6oye miki ba alhak'in Ya Al'ameen ne yake
binki, kamar yadda kikace you loved Adeel with all that you got shima hakane,
mutumin is ready to sacrifice anything for you amman baki gani ba kema kikace se
Adeel, alhak'in sa ne ke binki.”
“Hakane Lubiee bakiyi k'arya ba, duk kalan rashin hankalin danayi wa Ya Al'ameen
mutumin nan be ta6a wulak'antani ba ko tsawa zan iya irga sau nawa yamin lokacin ma
dan nayi rashin kunya wa yarsa ne. Ban ta6a coming across a gentle and caring soul
like Ya Al'ameen ba I just failed to noticed it, dama hakane we never know the
value of what we have until we lose them, Lubiee I can't tell you how much am
missing Ya Al'ameen and my family only if I can reverse time and make things
right.”
“Hakane Zeezee all shall be well ki dage da addu'a nima zan tayaki kikuma k'ara
hak'uri a fact says when things aren't going well God is still working so mu jira
muga me Allah ke shirin miki in shaa Allah alkhairi ne.”
“Thank you Lubiee, thank you so much.”
“You are most welcome get some sleep okay?”
“Okay goodnight babe.” Lubiee na hanging Zeezee ta miyar da wayan ta ajiye. Nan
da nan ta canza kayan jikinta ta kwanta.

*~ *~ *~
Life proceeded on, wulak'anci ba wanda Zeezee bata sha gun Adeel, bazata iya
tuna when last ya kwana a gida ba kusan kullum seya fita midnight parties in ya
tashi dawowa kuwa ya dawo da ambaliyan friends nasa suci abinci. Zeezee gabad'aya
ta fita daga kamanninta don damuwa da wahala gashi ko kad'an bata iya talking back
to Adeel kaman yadda ya kamata' kota fara seta kasa tasa kuka unlike yadda tasamu
Al'ameen da bayi magana ta riga gaya mai baqaqen kalamu.

***
Yau tun safe Adeel be fita yawon daya saba ba, yana zaune a parlour bayan yayi
breakfast yana kallo chan telephone dake kan centre table ya shiga buzzing yana
dubawa yaga Ruky Mama new Babe insa ke kiransa. Seda ya murmusa sa'annan yayi
picking “Halo Pretty One.” On the other side ta amsa da “My Handsome.”
“Good Morning ya kike?”
“As how My Man is.” K'aran bud'e k'ofa yaji yana kai dubansa yaga Zeezee ce
k'aramar tsuka yaja sannan ya amsa Ruky Mama da ”ya gajiyan jiya? You made my day
yestarday and for that you owe me big ki shirya by 2pm I'll come pick you up.” Wani
irin mumunan fad'i gabanta yayi ita iskancin Adeel d'inma batasan da wanne zata
fara ji ba yanzu dagaske budurwa ya samu? Ashe kullum gunta yake zuwa waya sani ko
har kwana tare ma sunayi, subhanallah ta furta a ranta sannan ta ruga d'aki a guje
tayi picking telephone tare muting sannan ta d'aga se karara gashi tana jin
abubuwan da suke fad'i take. Banda zallan soyayyan da ko ita Adeel be ta6a nuna
mata ba, ba abinda suke haka kaman mayya tana hawaye tana sauraro amman tak'i
kashewa seda suka gama wayan tas sannan hannu na 6ari ta miyar ta ajiye. Kuka ta
cigaba da rusawa wajen chan ta tashi ta had'a lunch. Not long enough taga ya fito
ya shirya tsaf cikin qananun kaya se qamshi yake. Dining ya nufa yaci abinci yana
gamawa Zeezee ta fito daga gun 6uyarta.

“Ina zakaje Adeel?”


“Ina ruwanki kuma da inda zani? Fita zanyi.”
“Adeel what have I ever done to you? A iya zaman da mukayi da kai ban ta6a cutar
dakai ba all I've ever wanted is to be with you and make you happy amman daka tashi
seka saqa min da butulci ta hanyan rabani da mahaifata bayan nan yanzu kuma 'yan
mata ka soma yi? Dududu auren namu yakai shekara ne da har zaka fara neman mata a
waje? Acikin gidana kana min waya dasu kana ganin ka kyauta kenan?”
”Ke da kike waya dani time da kike gisan Soldier'n can kin kyauta masa? Abinda
fa kema kinyi ne don haka karki taquramin plus mata hud'u Allah ya halatta min kuma
na gaji da ke sabuwa nakeso.”
“Hakane amman kasani duk wani rashin kyautatawan danayi wa Ya Al'ameen harda
iyayena kaika jawo kai kake tunzira ni-”
“Wait wait wait” ya katse ta “kaman ya nike tunziraki? Na ta6a kamaki nace in
bakiyi abu kaza ba zan kasheki ne? Ke kika ga dama saboda haka kidena blaming
d'ina.”
“Adeel kasani Allah ba azzalimin bawa bane kaman yadda nasan due to abubuwan
danayi wa Ya Al'ameen Allah ya turoka kai kuma ka saqa mai nima Allah ze had'aka da
wacce zata baka wahala its just a matter of time. Kuma dole kace ka gaji dani tunda
ka miyar dani sex machine a gidan nan but I want you to know that har abada bazaka
sake kusanta taba, kamar yadda bazan iy hanaka kula 'yan matan waje ba nima haka
bazaka sake forcing d'ina into sleeping with you ba.”
“Wannan kuma keya dama there are thousands of virgins out there pleading for me
to sleep with them kinga ko dan wacce zumanta ya k'are kamanki tace bazata ban
kanta ba I wont care bale ma in a yanzu inason kusantarki you can't stop me Zeezee
ko ayita ta dad'i kokuwa kece zaki sha wahala niba ruwana.” Yana kaiwa nan ya fice,
kuka ta shigayi sosai abin tausayi tsugune a wajen indeed tayi nadaman all the
misdoings tayi da a baya. Tun lokacin bata sake ganin Adeel ba se after 2 days nan
ma da daddarre around 10:30pm ya dawo gabad'aya a bige yake tun dayake be ta6a shan
maye ba se yau a birthday'n Friend nasa. Allah ne kawai ya kawosa gida gabad'aya ya
jiqe daga ruwan saman da ake ta rafkawa. D'akin Zeezee direct ya nufa thankfully ya
samu a bud'e lokacin ma har tayi bacci abinta.

Wutan d'akin ya lalumo da k'yar ya kunna anan ne Zeezee ta soma bud'e ido
kasancewar baccin nata beyi nisan chan ba, ba qaramin razana tayi ba ganinsa. “Wani
irin abu ne haka Adeel taya zaka shigomin d'aki ba sallama sannan kuma ka kunna min
wuta?”
“Anyi, gidanki ne kokuwa ke kike da iko da kanki?” Yayi maganan a bige tun anan
ta gano a bige.
“Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!” Tayi exclaiming “Adeel shaye-shaye ka
soma?” Few steps yayi taking forward kusa da ita anan warin barasan dake tashi a
jikinsa ya sake cika mata hanci da wuri taja baya tare da toshe hancinta, hakan
yasa ya samu ya zauna gefenta “take off your clothes” ya buk'aceta don yadda ya
bugu har wani kakkafewa idanunsa suke.
“What non sense are you talking about? Maza! Ka tashi ka fita min daga d'aki.
Kaje ka gama gantalinka kazo kana gayamin maganan banza get out I said” tamai nuni
da k'ofa.
“I said take them off.”
“I won't ai ba baiwar kabace ni kokuwa sex machine da zakazo any moment you feel
like to and sleep with me, ma don rainin hankali kayi da matan waje kazo kace zaka
nemeni nima? Nasan wasu cututtukan ne tattare dakai yanzu? In anan zaka kwana fine
am excusing you” bata kai ga miqewa ba yaja hannunta “let me go” tashiga k'ok'arin
k'wato kanta sede sam takasa da d'ayan hannunsa ya shiga cire mata hijbin dake
jikin nata kuka ta shiga rusawa sosai batasan alokacinda ta soma had'a sa da Allah
ba.
“Adeel don Allah ka rufa min asiri ka barni na rok'eka da Allah ka bari.” Ko
jinta beyi ba haka seda ya cire hijabin nata daman zallan vest ne da free size knee
length wando a jikinta nan ta shiga kare k'irjinta shikuwa se anan wani sha'awanta
ya sake taso mai gashi daman a bige yake.
“Adeel don Allah badon niba kayi hak'uri kadena, am not ready for it.”
“Keep quiet! I don't care” Ya daka mata tsawa kum taja bakinta tayi tsit sekuma
6arin da ta shigayi sosai. Laluban lips nata ya soma wanda tuni ta had'asu ciki ta
rufe ba yadda beyi ta fito dasu ba tak'i chan da abun ya ishesa yayi spinning nata
kan gadon tare da hayewa kanta ya danne ta yadda ko motsin kirki bata iyawa. Kayan
jikinsa ya rage kap nan tasa wani d'ankaren ihu anan ne yayi using opportunity'n
yayi owning lips nata, hannayenta da take k'ok'arin shuresa dasu ya kama ta each
side of her head ya zamanto ba abinda Zeezee ke se hawaye. Don kanshi ya gaji da
kissing natan sannan yayi ripping kayanta gabad'aya. Kuka take sosai tana had'asa
da Allah da yayi hak'uri ya bari amman se kaman sake tinzirasa take. Sarrafata ya
shigayi chan ya d'auro niyan shiganta nan ta had'e k'afafunta gu d'aya not letting
him access, ba yadda beyi da ita ta bud'e ba amman tak'i basa access da k'arfinsa
sosai ya samu ya wangaleta.
“Adeel please don't don Allah kayi hak'uri kadena na had'aka da Allah” ta fad'a
cikin wata dashasshiyar murya, amman dake a bige yake kuma bako d'igon imani
tattare dashi haka ya hau riding akanta duk anan hawaye kawai Zeezee ke zubarwa
kaman lalacaccen famfo. Wahalan da Adeel ya bata ranan is indescribable seda yayi
yayi harya gaji sannan ya barta alokacin hawayen ma ba fita suke sosai ba. Gefenta
ya koma ya kwanta wanda cikin seconds bacci yayi awon gaba dashi.

Tashi takeson tayi amman takasa tsan-tsan azaba da rad'ad'i. Da k'yar ta iya jan
kayanta ta miyar sannan a sannu a sannu ta samu ta tashi tabar mai d'akin zuwa wani
d'aki na daban. Achan tayi warming kanta sannan tayi wanka ta dawo ta kwanta.
Kwata-kwata ba bacci a idonta kuka ta cigaba dayi har se inda qarfinta ya k'are.

****
Washegari da safe around 8:43am Adeel ya tashi wani miqa yayi sannan a kasalance
ya gwada miqewa se jinsa yayi bakomai underneath mamaki ne ya bayyana karara a
fuskanshi. Anan ne ya soma tuna events na last night although he couldn't remember
all of it he remembered most of it. “Ina take?“ Ya tambayi kansa a fili. Ganin
baida masaniya ya miqe yaja kayansa ya miyar sannan ya nufi d'akinsu yayi wanka
yayi alwala sannan yayi Sallah. Sauran d'akunan ya dudduba be ganta ba nan fa
hanklinsa ya tashi bade ta samu ta gudu ba. D'akin da take ciki ya duba last seyaji
a rufe anan hankalinsa ya kwanta knocking yayi amman tanaji tak'i tashi se aikin
kuka take.
“Zeezee!” Ya kirata “I know you are in there open up.” Banza dashi still tayi
“ki tashi ki had'amin breakfast kinji ko? ” Still no answer bubbuga k'ofan yayi
tayi amman tak'i responding nasa gashi besan inda ya wullar da spare keys na gidan
ba. Haka yayi ta jiran fitowarta amman taqi fitowa at last ya shirya kawai ya fita.
Itako se chan ta fito bayan ta tabbata ya fita. Oats tayi having for breakfast.
Tana kan shara Lubiee ta kirata ta landline nan da nan tayi picking suka gaisa
and as much Zeezee tayi qoqarin 6oyewa Lubiee halin da take ciki saboda bazata iya
bata labarin kalan wulak'ancin da Adeel yayi mata jiya ba.
“Babe how are things with you?” Cewar Lubiee
“Alhamdulillah ya school?”
“Muna hutu ai.”
“Ayyah yayi kyau.”
"D'azu na baro gidansu Meela wallahi zatayi aure har ashobenki ma taban wai she
wants you to be there tayita trying numbanki but it aiint going through.”
“Ayyah Allah bada zaman lafiya, ai da baki amshi ashoben nawa ba saboda ba zuwa
zan ba koda inason zuwa Adeel baze barni ba.”
“Yana ina ne shi yanzu?”
“Baya gida ya fita-“
“D'an kutu-“ sekuma tayi shiru ganin zagin baida fa'ida “wato shi kullum bai gida
kekuma dake ya miyar dake baiwarsa ya hanaki fita?”
“Lubiee kibari kawai abin se addu'a abinda Adeel kemin wallahi ko kece kikace
min gashi zemin abu haka zan k'aryataki.”
“Why don't you retaliate?”
“Adeel mahaukaci ne har duka na yana iyawa I know him.”
“Wallahi be isa ba, ai shirun da kike masa yasa yake cigaba da miki iskanci ai
ba haka kikeyi wa Ya Al'ameen dake miki mutunci bama bale wannan tantirin. Ya dawo
gida yau kice masa zaki bikin friend naki next week karki tambayesa kud'in komi
d'inkin kima zan miki.”
“Are you sure Lubiee?”
“Yes Zeezee in bahaka ba ya riga cutar dake kenan aiko a musulince hak'uri nada
kyau amman in kaga bazaka iya haquran ba kana iya ramawa amman dai-dai yadda aka
cuceka don haka kema start fighting back dont let him do whatever he wants with
you.”
“I'll try telling him nagode.”
“Haba what are friends for? Senaji daga gareki.“
“Yauwa bye ki gaida Ummie.”
“I'll bye.”
Kafin Adeel ya dawo Zeezee har tagama had'a mai lunch ta koma d'akinta. Tun
abinda ya faru a tsakaninsu bata sake bari sun had'a ido ba as bata tashi fita daga
d'akinta se in bai gida in ko yana nan toh tana a d'akinta. Hakan ya faru for
almost 4 days se a na biyar tayi gathering confidence ranan yana zaune a parlour
yana chatting ne da alama ta fito ta samesa, tsayuwa yayi yana kallonta its been
long rabonsa daya sata a ido. Ya bud'e baki zeyi magana tayi saurin katsesa. “Nazo
sanar dakai ne Tuesday gobe zani bikin friend d'ina” ta fad'a confidently. Shiru
yayi for about a minute sannan ya amsa da “bazaki fita ba sanin kanki ne na hanaki
fita.”
“Ka hanani fita? Kai da kake d'aukan kwana biyu zuwa uku baka gida na ta6a yima
magana ne? Wallahi fita kam senayi baka isa ka hanani ba.”
“I thought permission kikazo asking and the answer is no."
"Ni yes kunne na suka jiye min yaso goben seka hanani fitan muga" tabisa da
harara sannan ta koma d'aki inda ta bud'e dandalin kuka daman tasani ba barinta
zeyi ba yanzu shikenan ita zaman gida ya aureta? Bari tun wuri na kira Lubiee nan
da nan taja landline tayi dialing nata and ba tare da 6ata lokaci ba ta d'aga
"Hello Babe?"
"Na'am Lubiee ya kike?"
“Qalau naji shiru da nace bari in kiraki ko lafiya sekuma gashi you called.”
“Eh wallahi Babe I can't make it to the wedding I asked him yace ba inda zanje I
know he means it."
"Kaman ya ba inda zaki? Adeel is such a son of a b*tch. Toh wallahi sekinje ai
kinji na rantse."
"Lubiee how?"
"Allah kaimu goben ke kawai ki shirya ina ze fita gobe?"
"Kullum ai shikam seya fita."
"The moment ya fita ki kirani kinji?"
"Okay Babe thank you."
"Don't mention." Anan sukayi sallama.
Washegari as always da safe tamai breakfast ta kimtsa ko ina sannan ta nufi
d'akinta tayi wanka ta tsara makeup tanajin fitansa tayi sauri ta kira Lubiee.
Cikin 17mins Lubiee da wani mechanic suka iso gidan Zeezee.
"Ga gidan nan Mal. Bala wallahi mijin ya rufe ta na kusan sati yayi tafiya dan
Allah ka taimaka ka 6alla kwad'on ka ceto rai kaima."
"Wanne wannan me black gate d'in?"
"Eh shi."
"Oya muje" nan suka sauk'a da zarto ya samu ya raba kwad'on into two. "Thank you
so much" N1000 ta miqa mai sannan yayi godiya ya fice. Nan da nan Lubiee tayi ciki
thankfully tasamu qofan parlour a 6ude take ta shiga ta shiga k'wala wa Zeezee kira
nan da nan tafito daga d'akin da take kaman a mafarki taga Lubiee a gabanta, da
gudu taje tayi hugging nata sun jima a haka sannan Lubiee tayi releasing nata.
"Toh kukan me kuma? Hurry mu tafi."
"Lubiee ni am leaving forever bazan sake dawowa ba ko htl room ne zan kama
temporarily."
"No Babe you are not doing this, yin haka babban had'ari ne ba yadda za'ayi kina
mace kice zaki soma zaman kanki. Tunda koda kin koma gida ba accepting naki su Mama
zasuyi ba kiyi hak'uri ki cigaba da zama anan d'in d'akin mijinki ya fiye miki
atleast ba wanda ze zageki ammn kika koma htl room wasu suna iy cewa karuwanci kika
fara and koda labari ya iske su Mama suma baza suji dad'i ba kiyi hak'uri."
"Shikenan Lubiee nagode."
"Yauwa ga ashobenki hurry up and change mu tafi ko Kamun ne kije mata sauran
zance mata bakida lafiya shiyasa."
"Toh" nan da nan ta canza "in d'au mota na ko kin taho da naki?"
"Na taho da nawa mu tafi" ana suka fice.

***
Adeel kuwa tun 3:46pm ya dawo gida a bakin gate ya tarar da suprise. Yazo bud'e
kwad'o, kwad'o yace sede ka nemeni. Mamaki ne sosai ya rufesa "how? Wa ta samu ta
turo yayi wannan aiki? Ma tukun ba na fasa wayarta ba ta ina take communicating da
mutane? Damn it!" Ya buga hannunsa jikin gate d'in "that god damn landline
mschww!"da sauri sauri ya nufi ciki don dubata.

*MIEMIEBEE Team #YGC!*


www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄

🎀🎀🎀 ‘YAR GATA CE!


*BY MIEMIEBEE*
PAGE 44
*Febuary, 2017*
Ciki ya dosa da wuri hankalinsa gabad'aya a tashe yake, d'akunan ya soma bi yana
qolla mata kira amman ko ina shiru ba Zeezee bakuma alarmarta. D'akin data koma da
zama ya duba last har cikin bayi bai ganta ba. Wardrobe da take adana kayanta ya
bud'e yaga wayam bakomai ciki kasancewar ita dama tayi shirin guduwa ne gabad'aya
Lubiee ce ta hanata, danqaree! Ya furta a ransa “ta gudu!” dining chair yaja ya
zauna akai yana nazarin dawa take communicating har tasamu tayi escaping. After a
while ya zaro wayansa ya kira Lubiee sanin how intimate they are. Itama seda ta
gama ja mishi ajin duniya sannan ta d'aga nan ma don bata son yayi suspecting nata
ne.
“Ya da kira na kuma Malam?”
“Ina kika kai min matata? Ina kika kai Zeezee?“
“What rubbish are you talking about?”
“Dont play dumb Lubiee nasan da bakinki a wannan lamari.”
“Kaga Malam gidan biki nake kuma wallahi inhar wani abin ya samu Zeezee bazan ta6a
yafe maka ba tunda you are too careless over your possessions har ka bari matarka
ta 6ata.” Bata jira jin me ze sake fad'i ba ta katse wayar. Hankalin Adeel ne ya
sake tashi matuqa da kalan kalamun Lubiee. “Yanzu ina zan shiga neman wancan me
kunnen qashin? After telling her not to ever step a foot outside taqi jina abee?
Allah dawo dake kokuwa Allah had'amu koda akan layi ne.”
****
Zeezee bazata iya tuna when last tayi walwala kaman na yau ba, gabad'aya harta
manta da problems nata se cashewa suke tayi and ko kad'an Lubiee bata nuna mata
Adeel called her ba gudun tashin hankalin da take iya jefata. 5:48pm Zeezee ta kira
Lubiee gefe “Babe mu tafi yanzu please inason in leqa su Mama koda they won't let
me in amman susan I care about them and that am missing them.”
“Toh Zeezee mu wuce barin yiwa Meela sallama” nan da nan taje ta dawo suka d'au
hanyn gidansu Zeezee. Gaba da gidan kad'an Lubiee tayi parking nan Zeezee ta sauk'e
ajiyar zuciya, “should I follow you?” Lubiee ta tambaya calmly.
“You don't have to nasan da k'yar ma su barni.”
“Have faith kinji best franndd?” With a nod Zeezee ta fice daga ciki chan nesa
tayi sallama har sau uku sannan Omar ya fito sanye da singlet da wandon jamfa,
murza idanunsa yayi don tabbatar da abinda suke gane mai ”Zeezee?” Yayi exclaiming
unbelievably.
"Na'am Ya Omar.”
"Kece?"
"Nice Ya Omar, ina uni?" Ta sauqa har qasa abinda bata ta6a mai ba ta gaishesa.
"Lafiya tashi abinki, kina nan dama?"
"Ina nan Ya Omar Mama fa tana gida?" Kai ya gyad'a mata yana mamakin yadda ta
rage haske takuma rame tabbas yasan tana cikin damuwa "shima Baba haka?"
"A'a bayi nan ya fita." Ajiyan zuciya ta sauqe, "Ya Omar dan Allah alfarma nakeso
kayi wa Mama magana don Allah tafito na ganta koda bazata min magana ba."
"Naji ina zuwa. "
Ciki ya nufa ya tarar da Mama na karatun Qur'an kamar yadda ta saba every evening.
Sallama yayi wanda bata amsa ba seda ta kai qarshen ayan datake karantawan.
"Wa'alaikumus salam Babana hira kazo min ne?"
"Mama Zeezee ce tazo fah."
"Toh wata Zeezee kuma?"
"Zeezee autan mu."
"Zainab!" Tayi exclaiming tare da zaro reading glasses nata. "Zainab fa kace Omar?"
"Eh Mama tana waje wai don Allah kije ku gaisa."
"Kace mata ina bacci." Dan kuwa kwata-kwata Zeezee ta fita mata a rai yanzu.
"Mama please karkiyi haka kema, yarinyan nan tana cikin damuwa wallahi bakiga yadda
tayi duhu takuma rame ba."
"Omar-"
"Please Mama" ya katseta a nitse. Seda ta d'au tsawon mintuna biyu tana nazari
sannan tayi making up mind nata ta miqe "muje" tace dashi. Labule ya d'aga mata ta
wuce sannan yabi bayanta. Tsugune yadda yabar Zeezee suka tarar da ita. Ganin Mama
kad'ai yasa ta zubda hawaye sosai bata zata tayi missing home as this ba, so take
tayi hugging Mama and feel her warmth again amman kuma tsoro takeji karta hanata.
"Mama" ta fad'a a hankali abin tausayi hawaye na tsiyaya daga idanunta. Se kallonta
Mama take a yayinda zuciyarta ke mara mata kode wani cutan zamanin ne da Zeezee
yadda ta rame haka. "Zeezee?"
"Mama!" Ta amsa tana kuka sosai batasan lokacinda taje ta fad'a jikin Mama ba tana
kuka me mugun tsuma zuciya, matseta tayi gagam jikinta tana kuka itama Mama tuni
zuciyarta ta kariya da k'yar ta iya ta danne kukan dake neman qeto mata, sede har a
yanzu ta kasa hugging Zeezee back, don kanta (Zeezee) ta gaji tayi breaking hug
d'in sannan ta sauqa har qasa tana me cigaba da kuka. "Mama don Allah kiyi hak'uri,
kiyi hak'uri ki yafemin abubuwan dana miki please indeed nayi regretting komi, I
shouldn't have took my boyfriend over my family dan Allah kuyi hak'uri, Ya Omar a
so sorry please..." hak'urin ta cigaba da basu duk seda ta basu tausayi.
"Shikenan Zainab tashi ya isa haka" Mama ta fad'a finally "tashi kukan is okay."
"Mama ki yafemin please badon hali na."
"Naji tashi ki tsaya" a nitse ta miqe sannan Mama ta qura mata ido "meke damunki
Zeezee?" Ta tambaya finally.
"Babu Mama banda missing naku da nake ba komai again."
"Are you sure? Karki min k'arya."
"Mama bab..." se kuma ta rushe da wani irin kuka da k'yar su Mama suka samu tayi
shiru sannan Omar ya shimfid'a musu darduma suka zauna duka akai. "Ina jinki
gayamin meke damunki kika rame kika kuma yi duhu haka."
"Mama tabbas duk d'an da bai jin maganan iyayensa kokuwa iyayensa suke baqin ciki
dashi yana cikin babban had'ari. Mama ko baki fad'a ba nasan ke da Baba are
extremely angry at me fushinku ba qaramin abu bane agareni, Mama nayi nadaman qin
jin magananki dana Baba, inda nasan haka halin Adeel yake da ban auresa ba. Mama
banda bak'in wahala ba abinda nake sha a gidan Adeel ko fita yau ma seda nayi
dagaske na samu na fita kaman kazan poultry haka ya rufeni gida bana zuwa ko ina ko
waya banida yanzu azaban yau daban na gobe daban, wulak'anci ba wanda baya d'uramin
nasani alhak'in ku dana Ya Al'ameen ne ke bina abinda kad'ai nakeson ku sani shine
na tuba kuma nayi nadaman komi gafararku nazo nema nasan koda zan had'a sama da
k'asa Baba baze ta6a yafemin ba amman Mama nasan ke ba haka kike ba haka Ya Omar ma
don Allah ku gafirceni."
Dogon nishi Mama taja ta sake sannan tace, "bakomai Zeezee ni na yafe miki kaman
yadda nasan Omar ma ya yafe miki ko Babana?" Kai ya gyad'a as yes. "Sauran 'yan
uwanki ma zan musu magana kekuma Allah ya kawo sauk'i cikin lamarinki zan tayaki da
addu'a nima. Inda za'a bi ta nawa ko komawa gidan Adeel bazakiyi ba amman nasan
Babanku baze ta6a yarda ba shiyasa nakeson ki k'ara hak'uri no situation is
permanent okay?"
"Hakane Mama nagode sosai Sakillahu khairan Ya Omar nagode zan koma, idan Baba
yazo ku gaishesa."
"Toh Zeezee sannu ko se haquri" ta miqe kenan suka jiyo k'aran security switch na
motan Baba, wani irin ruwa cikin Zeezee ya d'au ba ita kad'ai ba harta su Mama.
Kafin suce zasuyi wani qwararren motsi har ya shigo ciki inda yana shiga sukayi ido
hud'u da Zeezee. Tsayawa yayi yana tantancewa shin Zeezee ce 'yarsa da yayi
disowning kokuwa me kama da ita don shi kansa kamanninta yaso 6ace mar.
"Baba" ta fad'a hawaye na cikowa a idanunta.
"Hafsah me wannan take min a gida?" Ya tambaya a fusace. Shiru Mama tayi, "dake
nake magana fa kai Omar meya kawo wannan gida na? Se naja Allah ya isa tukun zaku
shiga taitayinku ko? Maza!" yayi nuni da Zeezee "fita kibar min gida." Kuka take
sosai tana neman tsugunawa don basa hak'uri "ki fita nace!" Ko sena sa polisawa sun
min waje dake? kuma kika sake taka min cikin gida ke koda gate kika tab'a zanyi
filing police report." Volume na kukan nata ne ya dad'u jin yadda wannan kalamu ke
fita daga bakin mahaifinta cike da tsana zallah. One more look tayi wa su Mama
sannan tace, "kayi hak'uri Baba inhar hakan ze farinta maka rai bazan sake zuwa nan
ba kayi hak'uri farin cikinka ya fiyemin komi, Mama, Ya Omar na tafi anan" ta fice.
Ita kanta Mama despite kalan abubuwan da Zeezee tayi mata bataji dad'in abinda Baba
yayi ba more especially ma dataji halin da Zeezee ke ciki wai nan ma don Zeezee
bata gaya mata lalacewar da mahaifarta yayi ba duk sanadin Adeel.
*~ *~ *~
Acikin mota ba abinda Lubiee ke se tambayar Zeezee meya faru dan ko bata ga shigan
Baba ba as tun fitar Zeezee take ta chatting a wayarta.
"Zeezee kin min shiru? Kiji koda Mama basuyi accepting apology'n kiba eventually
they'll kede ki dage da addu'a kinji?" Kukan ya isa please. Kanta ta d'ago finally
daga kan cinyanta, "Lubiee Mama tace ta yafemin but Baba? Ko bani chance beyi ba he
is still angry at me wallahi nayi nadaman komi."
"Is okay kinji one day all shall be well mu tafi?" With a nod Lubiee taja mota suka
fice. Dai-dai gaban gate ta sauqe Zeezee "lets go in." Ta sanar da ita.
"Kaman ya?" Zeezee ta tambaya with bewildered looks.
"Muje namai explaining komi in naga abun banayi ba kid'au akwatinki mu tafi
gidan mu zanyiwa Abba da Unmie bayani."
"No Lubiee please duk beyi zafi haka ba, kinga banason Adeel yasan ke kikayi
helping d'ina out we don't know what he is capable of ki tafi kawai duk abinda
akwai I'll let you know."
"Are you sure Babe?"
"Yes karki damu" tayi forcing smile out. "Toh ga wannan" tasa hannu a pocket dake
kujeran baya tare da fito dawata samsung J1 "ga wannan ki riqe incase ya d'auke
landline d'in semuna waya tanan ki qara hak'uri."
"Lubiee thank you so much" nan tayi hugging nata "you are just like a sister to me
Allah yabar zumunci."
"Ameen best frandd."
"Toh se anjima" anan sukayi sallama seda Lubiee taga shigewar Zeezee ta fice itama.
***
Tafi minti biyu tsaye a entrance door amman ta kasa shiga da k'yar at last ta bud'e
ta shiga kafin ta miyar da k'ofan taji footsteps na Adeel a bayanta nan fa ta shiga
shaking tama kasa juyawa ta fuskancesa. "Seki juyo aiko?" Cewar Adeel tad'au almost
a minute sannan ta juyon kanta a qasa. "Sannu ko kinyi qoqari, wato ke ba wanda ya
isa ya gaya miki magana kiji, ko da shike dama wacce bataji maganan mahaifinta ba
taya zata ji na mijinta? Menace miki akan fita unguwan? Bance miki baza ki jeba
ba?" Shiru tayi har anan "dake fa nake magana ki daina maidani mahaukaci when ever
am talking to you." Ji kawai take kaman ta cakka mai wuqa ta huta don haushin
dayake bata maganan ma ta fasa bazata masan ba.
Gefensa ta gwada bi zata fice nan ya wani fincikota seda d'aurinta ya kunce "ina
miki magana kina tafiya irin ga mahaukaci na ihu ko?" Waina hannun nata ya shiga yi
da mugun qarfin dayake ji dashi cike da mugunta, tun tana iya daurewa ta soma kuka.
"Adeel ka sakemin hannu please da zafi."
"Ina kikaje nace?" Ganin bata da niyyan magana ya sake murd'a hannun nata. "Adeel
please you are hurting me" ta fad'a a wahalance tana kuka. "You are not ready to
talk kenan nasan maganinki" janta ya shigayi izuwa d'akinsa.
"Adeel me zaka min let me go, ka sakeni don Allah." Ta qare maganan cikin kuka.
"Ina ni zaki mayar mahaukaci ina miki magana?" Jefata yayi kan gado ya haye
kanta nan ta qara volume na kukan nata, k'ok'arin rabata da kayanta ya shiga yi se
ihu take tana had'asa da Allah.
"Don Allah kabari banaso, ka dena please am begging you Adeel please, stop it
already please" Ko sauraranta beyi ba yayi ripping mata kaya tas haka cike da
mugunta da wulak'anci ya sake biyar buqatansa da ita yau, ba abinda Zeezee ke se
kuka seda ya gamsu sannan ya tashi ya koma gefe yana binta da wani pathetic look
"next time kika sake crossing d'ina zaki sha mamaki wallahi" yana kaiwa nan yaja
trousers nasa ya bar mata d'akin. Kuka take wane don shi aka turota duniya wannan
wace erin rayuwa ne? Lallai ashe iyaye ba abin wasa bane duk wanda ya bari d'aya
daga cikin iyayensa kokuwa duka sukayi mai baki ko kuwa suke fushi ko baqin ciki
dashi toh tabbas baze qarasa da duniya lafiya ba.
Sam ta kasa sauqowa daga kan gadon don azaba, seda tayi dagaske sanan ta samu ta
tashi ta miyar da kayanta tabar mai d'akin. A parlour ta tarar dashi yana kan waya
da Ruky Mama.
"Hold on Babe please" yace da Ruky Mama sannan ya miyar da kallonsa kan Zeezee, "ke
kije ki had'a min dinner am starving" yace da ita yana wani mata mugun kallo. Shiru
tayi tsaye gun "bazaki amsa ba sena kira wani qato a waje yayi abinda yaga dama
dake ne ko kuwa?" Da mamaki ta d'ago kai tana kallonsa lallai Adeel yanzu har
tunanin ya d'au matarsa yabawa wani k'ato yayi lalata da ita yake tunanin yi?
Gaskiya ne ya tabbata bashida imani bayahude ne shi.
"Kina kallo na kina ganin bazan iya bane? Don amfaninki kenan for sex and cooking
zaki min dinner'n ne ko sekinga aiki da cikawa?" Sanin sarai ze iya ya kira wanin
kuma tana ji tana gani yayi amfani da ita tunda har ya fad'a da bakinsa yasa ta
gyad'a kai "zan girka maka."
"Da ko kinsha mamaki." da hannu yayi dismissing nata sannan ya cigaba da wayansa.
D'akinta ta nufa ta d'aura towel sannan ta nufa bayi donyin wanka, kuka ta shigayi
kaman lalacaccen famfo yanzu abinda take gani a american films shi Adeel keson kawo
mata gida? Wani irin rashin kishi ne da zaisa mutum ya d'au matarsa ya bawa wani
wai yayi duk abinda yakeso da ita? Shin anya ma kuwa Adeel musulmi ne? "Wani irin
rayuwa na jefa kaina ciki?" Kuka tata yi seda ta godewa Allah sannan ta idar da
wankan da alwala ta fito tayi Sallah. Ba tare da 6ata lokaci ba ta had'a mai dinner
yana ci ya d'au wanka koba a tambaya ba ansan gun budurwa zasa. Kukan zuci ta soma
ita sede yayi biyan buqatansa da ita ba godiya babu dad'ad'd'un kalamu sema tunanin
bawa wani la'ananne ita yake amman gashi zasa gun budurwa yanzu yaje yana gaya mata
love and soothing words. "Ya Al'ameen don Allah ka yafemin abubuwan dana maka, I
can't tell how much I miss everything about you." D'akinta ta nufa ta taqure kanta
gu d'aya kan gado tana me kuka sosai.
*GIDAN ALHJ ISMA’EEL YUSOUF*
Tsaye Mama take jikin wardrobe nasu bayan ta ciro wa Baba kayan baccinsa ta miqa
mai tare da sauqe ajiyar zuciya. "Alhj" ta kirasa a hankali.
"Na'am Hafsah." Waje ta nema ta zauna gefensa "Alhj don Allah badon niba ka
saurareni."
"Toh Hajiya Hafsah wani magana kuma kikeson min haka?" Yayi maganan yana canza
kayan nasa.
"Batun Zeezee ne." Ta fad'a tana shakkansa.
"Banason jin wani maganan daya shafi wancan 'yar iskan."
"Subhanallahi Alhj 'yarka cefa."
"Kada ki sake sa Zainab cikin jerin 'ya'yan dana haifa."
"Alhj-" katseta yayi da wuri "ya isa Hafsah inba wai fad'a kikeso muyi ba ki ajiye
maganan nan ni na gaya miki."
"Naji zan ajiye amman kasani 'yar ka na wahala sosai gidan yaron can kaima kasani
kaga yadda ta rame ai."
"Aini bazan ta6a sanin tana wahala ba senaji ya kasheta kowa ma ya huta annoba
kawai."
"Haba mana Alhj-"
"Ya isa Hafsah in kinsan maganan da zaki tayi kenan zan bar miki d'akin" yana kaiwa
nan yayi pulling trousers nasa ya fice zuwa guest room inda ya kwana can ranan. Duk
yadda yayi a daren ranan dan kawar da tunanin Zeezee daga k'wak'walwansa ya kasa
saboda shi kansa ta basa tausayi amman idan ya tuna da kalan abin kunyan da tamishi
gaban uwar Maj-Gen seyaji ya sake tsananta.
****
The following day tun 7am Adeel yazo ya tayar da Zeezee kan ta had'a mai breakfast
yanada gun da zasa which is none other than gun Ruky Mama. Haka ta katse baccinta
ta had'a mishi breakfast kamar yadda ya saba ba godiya ba sannu haka yauma yaci
abincin yabar plate d'in gun. Ya kaiga fita wayansa ya shiga buzzing a lokacin
Zeezee na tattara dining table, "Halo Babe gani nan zuwa ki qara hak'uri kinji? I
love you."
I love you d'in banza Zeezee ta furta a ranta meye amfanin ayita soyayya a waje in
anyi aure kuma a miyar da mutum kashi banza? "ba haka Ya Al'ameen yake ba" ta fad'a
a fili sede be jita ba kasancewar ratar dake tsakaninsu. Yana ficewa takai plates
d'in kitchen tayi wanke-wanke sannan ta dawo d'akinta ta baje kan gado.
"Shikenan ni yanzu ina ji ina gani Adeel ze auro min wata?" Ta tambayi kanta,
nan ta shiga rera kuka a hankali duk kalan rashin hankalin da take yiwa Ya Al'ameen
koda wasa be ta6a ambaton kishiya mata ba amman wannan wanda besan darajan d'an
Adam ba, ba abinda bata mai duk bayi gani shi aure ze k'ara. Hannu ta miqa dan
d'ago landline ta kira Lubiee taga babu, nufi kenan Adeel ya d'aga ya 6oye. Har ta
shiga yin sabon kuka seta tuna da wayan da Lubiee ta bata da wuri ta miqe ta d'auko
daga inda ta adana. Bud'ewa tayi taga 3 missed calls tana dubawa taga lamban Lubiee
take tayi calling nata back and hopefully ta d'aga.
"Gosh Babe you made me worried sick na d'au ko beast d'in can ya ta6a mana
lafiyarki."
"Lubiee am tired bazan iya d'aukan abubuwan Adeel ba anymore wai fa shirin aure
yake."
"Aure?!" exclaimed Lubiee.
Wallahi wai aure zeyi gashi har ya d'aga gini a gefe kuma site nata yafi nawa
girma. Ina ni ina zama da kishiya dan Allah ina ma ace yana sona ne kuma yanada
adalci da bazan damu chan ba amman wallahi nasan banda boyi-boyi ba abinda Adeel ze
maidani."
"Subhanallah! Kinsan wacce ze auro makin?"
"Ban santaba amman de wai sunanta Ruky Mama-"
"Ruky Mama!" Lubiee ta sake exclaiming fiye dana d'azu.
"Kinsan tane?"
"Niko nasan Ruky Mama, ke wallahi da biyu Adeel keson auro miki ita kinsan kuwa she
is a university graduate?"
"Babe don't tell me please. "
"Wallahi kuwa naji tana yin masters nata ma yanzu haka a ATBU, wallahi karki yarda
ya auro miki 'yar boko kut! Wallahi Adeel shege ne." Kuka kawai Zeezee tasa saboda
she is totally out of idea tasan ko had'a sama da k'asa zatayi Adeel baze fasa
auren ba danko bayi magana biyu se in dagangan.
"Toh kuma kukan meh?"
"Lubiee na cuci kaina a rayuwa wallahi 'ya mace kar ta ta6a auran wanda takeso sede
wanda yake sonta. Right from the start nasan nafi son Adeel shikuma he took it for
granted words can't tell how much am missing Ya Al'ameen if only I can meet him
once more to apologize to him and tell him just how much I love him" ta qare
maganan tana kuka sosai.
"Is okay Babe we can't reverse time ki dena tunanin Ya Al'ameen sake tsanan kanki
kawai zakiyi 6arna kam kin riga da kinyi sede ace Allah kiyaye aukuwan na gaba.
Kina jina?" Kai ta gyad'a wane Lubiee na gabanta sannan ta bisa da "eh" tana share
hawayenta.
"Shiru-shirun da kikeyi ma Adeel should end this moment ki k'wato 'yancinki da
kanki its the only way you can escape."
"Kamar ya kenan Lubiee? Ban fahimce kiba."
"I mean confront the bastard ki gaya masa ke lalle school zaki koma yanzu."
"Wallahi nasan he'll never agree to it shi d'inda ko unguwa bayi son bari na inje
bale school."
"Allah se ya barki bayan nan kuma kice masa ya za6i either ke ko ita Ruky'n don ke
bazaki zauna da kishiya ba"
"Hmm Lubiee kema kinsan ita zece tunda baya sona yanzu, I mean nothing to him."
"Kema kin fad'a in yace ita seya sallameki don wallahi zaman zawarci yafiye zama
da miji irin Adeel."
"Hmm Lubiee kina magana nan ma don ban gaya miki sauran abubuwan ba kinsan there
was a night ya taho min gida a bige yayi taking advantage d'ina tun daga ranan ya
miyar dashi abinyi without my concent yake kusanta ta da naqi dana so, to cut the
story short sex machine kawai Adeel ya miyar dani."
"Wa iyya zubillah!" Abinda kad'ai Lubiee ta iya fad'a kenan.
* MIEMIEBEE TEAM #YGC!*
www.beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
Miemiebee Novels
Tuesday, 7 February 2017
‘YAR GATA CE!
*BY MIEMIEE*
PAGE 45
*Febuary, 2017*

Kiyi hak'uri Babe it shall come to pass one day, kiyi abinda na fad'a mikin muji me
mara imanin zaice."
"I'll try" tayi maganan tana and shassheqa.
"Have faith nifa ba haka na sanki ba Babe keda kike abinda kika ga dama mesa kike
tsoron Adeel haka?"
"Kinsan mahaukaci ne shi ze iya illatani."
"In shaa Allh bazeyi ba its hight time kiyi fighting wa kanki."
"Is okay Babe I'll try my best nagode sosai."
"Don't mention senaji daga gareki" anan ta katse. Tunanin ya zata (Zeezee)
gudanar da wannan aiki take batta tsammanin zata iya abinda Lubiee ta sata dalili
kuwa itama bata sani ba all she is adamant of is that she can't talk back to Adeel
yadda ya kamata, agun ta ajiye wa Lubiee maganarta.
Har yamma Adeel be dawo ba da zaman gidan ya isa Zeezee ta d'au wayarta tasa
lamban Mama sannan ta kirata.
"Assalamu Alaikum" fad'in Mama a lokacin da ta d'aga wayar.
"Wa alaikumus salam" Zeezee ta amsa cikin sanyin murya, "ina ini Mama?"
"Lafiya Zeezee ce?"
"Eh nice Mama."
"Toh wannan layi fah?"
"Lubiee ne taban shi Adeel ya fasa waya na yakuma karya sim d'in."
"Subhanallahi shiya sai miki ne?"
"A'a fa tun wanda Ya Al'ameen ya saya min ne."
"Ikon Allah wai dama yaron nan ba sonki yake ba Zeezee kika dage seshi?"
"Mama ni kaina bansan meke damun Adeel ba gabad'aya ya canza."
"Toh ya kuke ciki yanzu?"
"Mama wai aure ze sake" sekuma tasa kuka.
"Aure de? Da aurenku ya shekara ne?"
"Kwata-kwata 8 months nefa."
"Toh Allah kyauta ya rufa asiri"
"Ameen Mama ya Baba don Allah ki bashi haquri on my behalf."
"Am trying my best Zainab."
"Toh Mama nagode, I love you so much."
"Ba komai ki qara hak'uri kinji? Akwai Allah."
"In shaa Allah nagode."
"Yauwa se anjima."
"Aha ki gaida Ya Omar."
"Zeji" sannan tayi hanging. Bada dad'ewa ba Baba ya dawo daga d'an strolling daya
fita "sannu da dawowa Alhj" tayi maganan tana zaro mai ruwa daga fridge.
"Yauwa Hafsah ta sannu." Sede kallo d'aya ya mata ya gano abu na damunta.
"Lafiya dai ko?" Ya tambaya.
"A'a wallahi" ta fad'a sounding honest.
"Toh ina jinki."
"Alhj yanzun nan Zeezee ta kirani wallahi tana cikin damuwa sosai wai ma mijinta
aure ze qara yi."
"Nawa ze auro mata? Uku ko biyu?"
"Haba de Alhj wai baka tausayawa 'yar nan?"
"Ba ita tace tana sonsa ba? Har fiye da yadda takeson iyayenta ai kad'an tagani
wallahi yamin dai-dai ya qaro mata uku ma yaga dama daga k'arshe ya korota."
"Ahhh ahh " Mama ta saki baki tana kallonsa "toh Allah shi kyauta."
"Ameen" anan ya nufi bayi don watsa ruwa.
****
Life moved on, abubuwa sun kasa daidaita tsakanin Zeezee da Adeel shi ya dage
sam seta basa haquri inhar tanason su koma shiri itako she sees no reason why da
zesa ta basa hak'uri after all she isn't the one at fault. Gini ake tayi mansion
daya ninka wanda Zeezee ke ciki girma sai shi sure zeyi, tun abin na damunta kullum
setayi kuka har ta soma rage bin abin a zuciya. Gashi anytime tace zatayi
confronting nasa bata iyawa gabad'aya setayi losing courage haka shiko Adeel yake
taking advantage nata kullum azaban yau daban na gobe daman.
Yau Zeezee na zaune a d'akinta tana had'a kayan cikin wardrobe nata Adeel ya
bankad'o k'ofan d'akin kaman yadda ya saba "Ke tashi ki had'a rice and stew me kyau
yau Ruky zata dawo daga tafiya and she'll be visiting zatazo taga gidaanta." Yau
kam bata tsammanin zata iya barinsa, "ai ba rainin hankalin daya kai wannan" ta
fad'a finally cike da tsiwa. "Ina ruwana da banzar budurwarka ko karuwarka da
zatazo? Wallahi kaji na rantse bazan girka ma wata shegiya abinci ba ko kaje ka
siyo muku kokuwa ta zauna da yunwa" ita kanta bata tsamman zata iya gaya mai magana
haka ba. Tsayuwa yayi yana kallonta lallai ma ta raina shi, raini na sosai.
"Come again me kikace?"
"Ai ka jini ba kurma bane kai bazan girka ma wata shegiya abinci ba."
"Haka kikace? Zaki sha mamaki."
"Ina qarshen mamakin da zaka bani shine ka d'auko kwarto yayi zina dani? Toh
kasani Allah ya fika Adeel kuma dad'in abin bana sallah amman inhar jahilcinka
yakai level da zaka bari a kusanceni ina al'ada get on with it."
"Sa'anki d'aya kuma, ki tashi kije kiyi abinda na saki kona illata ki."
"Bazan yiba ka illatanin kamin abinda Allah bemin ba, aini da illatanin ma zakayi
daya fiyemin yadda hukuma zata tsaya min akai se an raba auren namu tunda cutar
dani kake." Ganin tanada gaskiya yabar mata d'akin totally rai a daqule lallai kuwa
Zeezee zatayi regretting gaya mai magana da tayi. Koda ya d'auko Ruky Mama daga
airport restor ya wuce da ita direct inda suka ci abinci sannan suka biya ta gida
don taga gininta, duk kalan qarya irin nata bata raina gidan ba saboda yadda ya
had'u. Kasancewar itama 'yar duniyar kanta ne da Adeel bece mata ta shiga ciki su
gaisa sa Zeezee ba se itama bata tambaya ba. Ta gama ganin gini Adeel yayi dropping
nata a gida.
Yawonsa ya wuce daga nan se Maghrib ya dawo gida inda yasa Zeezee frying masa
doya tagama ta had'a mai kan dining. Da singlet da nickers yafito ya nufi dining se
abinda ya jima be gani ba yake gani yau, Zeezee tsaye kan dining d'in tayi akinbo
batare da yace da ita k'ala ba ya ja kujera ya zauna ya soma serving kansa har anan
bata motsa ba bata kuma yi magana ba.
"Ke hada haka? Taya zaki tsaya min aka while inason cin abinci?"
"Makaranta nakeson na koma nagaji da zaman gida haka ba abinda nake tsinana wa
kaina ni ba 'ya'ya ba bakuma karatu ba baze yuwu ba."
"LOL da ai fitowa fili kikayi kikace za a auro miki masters holder kema kinason
ki rufe k'ofan gori zaki fara degree naki, toh kisani ba a gidana ba tunda bakiyi
karatu gidan ubanki ba bazakiyi a nawa ba kin gane?"
"Seka hanani yi muga thank god inada kud'in da zanyi registration da komai,
approve it or nah am starting school."
"Please Zeezee koda wasa ki gwada taka k'afafunki waje ina raye kiga aiki da
cikawa useless kawai."
"Kai kuma macuci azzalimi ba" ba tare da ta tsaya jin mezece ba tayi ciki. Ita
kanta tasan barazana duka kawai take amman bawai zata iya aikatawa bane tsan-tsan
tsoronsa da take. Tun daren ranan bata sake sa Adeel a ido ba se after 3 days daman
haka ne anytime Ruky Mama ke gari bayi kwana a gida. A kwana na ukun ne ya samu ya
zo kusan da yamma haka. Alokacin nema Zeezee ke sauk'e indomie'n ta daga wuta tana
rufo k'ofan kitchen tagansa tsaye a tsakar parlour. Gani tayi ya soma dosan inda
take nanfa guiwoyinta suka shiga shaking amman don ta nuna masa bata tsoronsa again
ta dake ahaka har ya isketa, jiran yauma yaja hannunta yaje ya biya bukatansa kamar
yadda ya saba take setaji ya wabje plate na hannun nata.
"Ya da haka Adeel? Ka miqa min abinci na."
"Nawa ko naki ke kike siya?"
"It doesn't matter as long as nina girka."
"Seki amsa muga aikin banza kawai kije ki dafa wani am starving."
"Ita karuwarkan bata iya girki bane data barka ka dawo haka bayan kwana ukun
dakayi mata?" Ba tare da yace da ita komi ba ya ja kujera ya zauna ya shiga cin
indomien. Yana gamawa ya nufi d'akinsa se 8:30pm ya fito alokacin Zeezee na zaune a
parlour tana gyaran farce. Ganinsa tayi tsaf ya shirya da alama fita zeyi again. Da
wuri ta ajiye nail cutter'n dake hannunta ta miqe "ina kuma zakaje?"
"Ke waye da zaki tambayan inda zani? Karfa kiga ina barinki kwana biyu kice zaki
raina ni."
"Ai repect is reciprocal duk wanda be bawa kansa ba baza a basa ba, harga Allah
nagaji ba yadda za ayi ace kullum baka yini baka kwana a gida nikuma ka barni da
gadi."
"Ya kika iya toh?"
"Niko nake da yadda zan yi."
"Go ahead then matsa min."
"Ina nan wallahi bazaka gun wancan karuwar ba."
"Kada ki sake kwatanta Ruky da karuwa, ke ba'a ce dake karuwa ba se ita? Inba
karuwa ba wace zata na fita midnight party?"
"Dole kamin gori ai yau, amman bayan parties da kake sani zuwan dole ka gayamin
wani party ne kuma ka sake jin naje."
"Ki dena cewa na saki cause ke kikayi niyyan zuwa saboda dama da akwai ra'ayin
iskancin a zuciyanki, matsa min banida lokacin ki."
"Wallahi ba inda zaka je ina nan, bazaka gun karuwar can ba."
"Karki sake ce mata karuwa."
"Karuwa na sake fad'a inba karuwa ba wace zata riqe mijin wata harna kwana uk-"
bata idda maganan ba taji sauqan mari fas a kumatun ta. Wajen ta riqe da mamaki
tare da d'ago kai tana kallonsa "mari?" Ta tambaya still not believing, hannunta
maqale da gun. "mari? Adeel ni ka d'aga hannu ka mara yau akan karuwarka? Ni
Adeel?"
"Kad'an daga cikin abinda zan iya miki kenan muddin kika sake zagin Ruky."
"Lallai Adeel kacika butulu yanzu akan wata banza zaka d'aga hannu ka mareni a
fuska ta?"
"Matsa min" ganin bata da niyyan matsa mai ya tunkud'eta a zuciye yayi
ficewarsa. Sauqa tayi har qasa a gun a yayinda hawaye ke bin k'uncinta, kuka take
na sosai Wani irin rayuwa ta jefa kanta? Koda wasa bata tab'a kawo wa a ranta Adeel
ze iya d'aga hannu ya mareta ba, gaskiya ne na miji ba d'an goyo bane. Kodan yadda
ta fifita sa akan iyayenta be kamata yayi mata haka ba, amman komi ya manta yana
mata wulak'anci harda mari yanzu.
Da k'yar ta iya ta tattara kanta ta nufi d'aki, sede har anan takasa dena kukan
saboda yadda yakeyi mata zafi, se chan ta share hawayenta ta zauna gaban mirror
tana kallon kanta, "wallahi bazaka cigaba da cutar dani haka ba, abin ya isa haka."
Tayi assuring kanta.

A waje ranan ma Adeel ya kwana se a washegari ya dawo ya nufi d'akinsa dan watsa
ruwa anan Zeezee tayi sid'ak-sid'ak ta shiga d'akin inda yake ajiye keys nasa ta
nufa ta zaro na kwad'on dayake rufe gate dashi tasa a bra nata sannan ta mai
replacing da fake one. Da wuri ta fice, yana gama shirinsa ya fito dining yaci
lunch zuwa La'asr ya shirya ya sake fita, ya kaiga bud'e kwad'on don datsewa yanemi
key'n da ze shiga ya rasa ganin zai 6ata mai lokaci kawai ya fice a tunaninsa ai
tasan kullum yana rufe gate baza tayi tunanin fita ba.
Itako a ciki tanajin ficewansa ta shirya tsaf zata unguwa itama, makullin
motarta ta d'auka tabi sahunsa. Gidajen friends nata data jima bata jeba ta jeta
yau, yawo kam seda ya isheta ranan. Ba ita ta tashi dawowa ba se 7:40pm nan ma don
bata iya tuk'in dare bane tana tsoro.

Adeel kuwa yana fita bada jimawa ba ya dawo ranan anan yayita kiran Zeezee amman
bata nan, zaune yake a yanzu haka a parlour yana jiran shigowarta. Ana cikin haka
Zeezee ta shigo bayan ta miyar da k'ofa ta juyo seda suka had'a ido hud'u sannan ta
kawar da kanta tahau tafiya. "Ke!" Ya kirata a tsawace sede sam yi tayi kaman bada
ita yake ba hakan ba qaramin 6ata mai rai yayi ba "wallahi kika barni na sake
nanata kaina zaki sha mamaki."
"Ai ba da ke aka yanka min ragon suna ba if you wanna talk to me address me with
my name."
"Wow!" Ya tafe hannunsa, "I'm starting to like this wato finally zaki soma
retaliating ko? Toh bani key'n da kika satan 6arauniya kawai."
"Kar ka sake cemin 6arauniya."
"B'arauniya na sake fad'a."
"Kaima 6arawo."
"Kikace meh?"
"Nace kaima 6arawo kamin abinda Allah bemin ba." Ransa ne ya mugun 6aci, kaman a
kyaftawan ido ya doso gabanta tare da fincikota da hannu yana me murd'awa cike da
mugunt, duk zafi da azaban da takeji besa ta nuna masa ba don kansa ya gaji ya
saketa. "Wallahi kar kiga ina barin ki kizata tsoron ki nake, kika cigaba da hakan
belt zan d'au in baki kashi."
"Yanzun me kake jira don ka dakeni sai meh? I am not the first woman to be beaten
up by her husband neither will I be the last, get on ka daken d'in amman kasani
kaima wataran wani ze daki 'yarka kaima."
"Useless kawai" kad'ai yace da ita sannan yabi gefenta ya wuce har ya kaiga
shiga d'akinsa ya dakata, "kuma maza ki wuce kitchen na siyo kaza pepper soup
nakeso." Yi tayi kaman bata jisa ba ta shiga tafiya "dake fa nake!" Ya fad'a a
tsawace.
"Senace maka eh naji ne tukun zaka san na jikan? Mschww!" tana kaiwa nan ta nufi
d'akinta bayan ta idar da Sallah ta canza kaya ta fito ta sarrafa masa kazan tana
gamawa ta d'ibi nata, cinya d'aya da wasu parts masu kyau k'waya biyu again tasa,
ragowan tasa a flask takai masa. Kafin yafito harta cinye nata ta kora da ruwa.

Fitowan Adeel ya nufi dining cike da zumud'insa ya bud'e flask d'in in search
of cinyoyinsa biyu don yaci, sede ya gama dubansa amman d'aya kad'ai yake gani haka
daya gwada neman other parts d'inma duk d'ai-d'ai yake gani. Danqaree!
"Ke Zeezee! Zeezee! Ina kike?" Seda ya kirata kusan sau biyar sannan ta fito
batare da ta amsa ba.
"Ina kika kai min sauran parts d'in?"
"Cikina."
"Cikinki? Naki ne da zaki cinye? Kokuwa ni na baki?"
"Ko d'aya amman naga hak'k'i na ne dole inci tunda ni na girka."
"B'arauniya ba, toh kisani kinci haramun."
"Kanka akeji." Tana kaiwa nan ta koma d'akinta. Later during the night Zeezee ta
fito sanye da bombshot da vest tana latsa wayar da Lubiee tabata. Zama tayi kan
kujera tare da kunna power button tana kallon TV tana chatting. To 10:30pm Adeel ya
fito sanye da pajamas nasa zasa d'auko ruwa a fridge. Tsayuwa yayi yana kallonta,
yayi hakan na mintuna biyu ya kad'a kai ya wuce dining ya d'auko bottle na ruwa duk
anan Zeezee bata san da halitta tsaye gun ba. Har ya kaiga shiga d'akinsa yaga baze
iya hak'ura ba, "Ke a ina kika samu wannan wayan?"
"Sata nayi ina ruwanka tunda ba kai ka siya min ba?" tana gama amsa sa tasa
dariya da alama da chatting da takeyin ne. Hakan ba qaramin 6atawa Adeel rai yayi
ba shi bayison yaga tana walwala yafison yata ganin ta cikin hawaye kullum "Kuma da
wa kike chatting?"
"Wai kam ina ruwanka? In kana waya da Ruky kowa take na ta6a yimaka magana ne?
Please kadena cikamin kunne."
"Ajiye wayan kizo." Ya fad'a more like a command.
"Nazo kamin meh?"
"Kizo nace dont let me repeat myself."
"Bazan zoba in fad'an abu zakayi say it ina jinka."
"Kizo haqqi na nakeso."
"Lallai ko kayi 6atan kai in haqqin ka kakeso kana iya zuwa gun ita karuwar taka
ta baka amman kasani bakada haqqi akaina."
"Zeezee karkisa na miki na k'arfi."
"Kayin ai dama abinda ka saba yi kenan." Fusata yayi lokaci guda wai ita waye da
zece yanason haqqinsa tace bazata bada ba, goran ruwan ya ajiye ya nufi gabanta, ko
tsorata bata yi ba hannunta yaja seda ya miqar da ita daga kan kujeran "ina ayi ta
dad'i bakiya so?"
"Ka sakemin hannu mugu azzalimi kwai let me go." Janta ya shiga yi, ganin haka ta
sulale k'asa "ki tashi nace!"
"Ai wallahi na gaya maka bazaka sake samun wani abun aguna ba, I belong to Ya
Al'ameen."
Haka kikace? Bale ma shi Ya Al'ameen d'in me zeyi da wacce bata haihuwa? Mschww!"
Eh ka fad'i koma me, bashi zesa na baka kaina ba."
"Ajinki ko anan bazan iya yin abinda nakeso bane?" Sauk'a k'asan shima yayi ya
had'e hannayenta biyu a sama yana wani erin shunshuna wuyanta wane ze had'iyeta
"Adeel stop it banaso! Stop it already." Ko sauraranta beyi ba, dabara ce ta fad'o
mata, ta seta k'afanta dai-dai kan abin nasa ta gullesa. Take yabar abinda yaken
tare da sakar da wani mugun k'ara abin nasa ya riqe yana matse ido anan Zeezee ta
samu ta tashi tareda rugawa d'akinta a guje.
"Wallahi you won't get away with this" yace da ita lokacin da take sa lock jikin
k'ofar tata. Yafi minti biyu tsugune agun sannan finally ya miqe ya nufi d'akinshi.

The following day, ba yadda Adeel beyi da Zeezee ta fito daga d'akinta ba tak'i,
wanki ya loda mata bakin k'ofan yau harda iron "gashi in kika fito ki wanke min su
duka kuma ki goge wallahi in bemin ba zaki sha mamaki." Yana kaiwa nan ya fice seda
ta tabbata ya fita sannan ta fito baki ta sake ganin yawan kayakin da kaman bazata
wanke ba sekuma ta tuna da abinda ta mai jiya muddin ta bari ta sake yimai wani
abin yau yana iya zaneta sabida tsab ze rina. Kamar wacce zatayi kuka ta tattara
kayakin nasa ta wanke mai suna bushewa tabisu da guga, bayanta wane ze 6alle. Seda
ta gama mai nasa sannan ta shiga yin nata itama, se tunawa take time da take gidan
Ya Al'ameen da zaran wankinta ya taru shi da kansa yake sawa a wanke akuma yi mata
guga. She can't tell how much she is missing him.

_Few months later..._


***
Maganan aure fa ba fashi, gini har an kammala an soma jere, ba aikin Zeezee
yanzu se kuka kullum, bazata iya zama da kishiya ba, kishiyan ma wai wacce taji
boko fiye da ita. Tunanin kalan rayuwan da zata shiga muddin ta bari Adeel ya auro
Ruky Mama kawai take tasani tamkar baiwa ze mai da ita, she can't take it.

Yau da misalin k'arfe d'ayan rana Adeel ya shigo gida da almajiri biye dashi
yana riqe da akwati na tsakiya k'waya d'aya. A parlour ya umurci yaron ya ajiye mai
sannan ya sallemesa. Anan ya shiga k'walla wa Zeezee kira "Ke Zeezee! Ina kike ki
fito da Allah kina 6ata min lokaci."
Tana kwance bisa gado tana aikin kuka ta miqe tazota, da k'afa ya tura akwatin
side nata "gashi wannan naki ne kayan fad'an kishiya kome ake kira." K'arisowa tayi
a nitse ta tsuguna ta bud'e akwatin dududu befi atamfofi biyar ciki ba nan ma ba
super ko makamancin haka ciki, seda wasu local inner wears k'waya biyar da shampoo
na 'yan N350 guda d'aya aciki se dubu biyar a gefe. Kai ta kad'a sannan ta miqe
tsaye tana kallonsa "Adeel koda tinkiya ce zaka auro mata wata bazaka kai mata
wannan abu ba bale ni mutum. Meh wannan yanzu? Kana ganin kamin adalci kenan?
Akwatuna nawa ka kai gidansu Ruky Mama 24 am I right? Amman ni dake ka miyar dani
tamkar wacce ba haifanta akayi ba zaka kawo min wannan tsummakaran, Ahaka ne kake
tunanin zakayi adalci tsakani na da wacce zaka auron?"
"LOL bakisan wani abu ba wannan d'inma banyi niyyan kawo miki ba, mutumin danayi
siyayya a shagonsan ne yace lallai sena kawo miki wani abu, kuma tun wuri is better
kidena had'a kanki da Ruky kinga na farko ita ba sadaqarta za'ayimin ba, da kud'i
na zan aurota unlike ke da aka wulla min ke na biyu Ruky tafi minke tunda ita
masters holder ce ke kuwa ko degree bakida, na uku garau take at any moment tana
iya d'aukan ciki ta hihu ba kaman ki da bakida amfani ba, kinga ko anan ma zakisan
matsayinku ba d'aya bane. Ki taimaka wa kanki kibar comparing d'in ku."
"Haka kace?"
"Haka yake ma so ni zan koma."
"Dan tsaya" ta buk'acesa. Kitchen ta nufa da wuri bayan second counts ta fito
riqe da galon na kero da ashana. Baki ya saki yana kallonta lokacin da take bulbula
keron akan kayakin, seda ta tsiyaye tas sannan ta kyasta ashana ta wulla akai
balbal ya soma ci.
"Kasani koda a sadaqa ka sameni ba a wahala ka tsintoni ba da zaka kawomin
k'ananun zannuwan dubu uku kayi tsammanin kuma zansa su."
"Ke!" Anan ne bakinsa ya bud'u "asaran dukiya zakiyi min? Dama inba zanin dubu
uku-ukun ba ki gayamin wani zanin ne yafi cancanta da 'yar sadaqa?"

*MIEMIEBEE TEAM #YGC!*


beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀‘YAR GATA CE!
*BY MIEMIEBEE*
Page 46
Febuary, 2017

_I solemnly dedicate this page in honour of my sweetheart in disguise *MAMAN


FADEEL* Thank you for everything Big Sis your Lilly loves you so much, Allah yabar
zumunci❤❤❤❤_

Tana hawaye sosai tace, "Adeel mena ta6a yimaka a rayuwa? Mesa ka tsaneni haka
ka lalata min rayuwa? Don kai na rasa komi nawa har iyaye na na yafe saboda na
kasance tare da kai amman kake wulak'antani haka? Wallahi a da ko had'e sama da
k'asa za'ayi acemin ga abinda zakazo kamin bazan yarda ba." Sosai ta qare maganan
tana kuka. Bayan ya samu yayi stopping fire'n da estinguisher yace, "toohhh!" cike
da mamaki "yanzu kuma what lead to all these nonsense talks? Saboda zan miki
kishiya? Wai tsaya tukun mata nawa Allah ya halitta min? One, two, three upto 4 dan
nace zan k'aro d'aya bama biyu ko uku ba kike neman gayamin magana? Kuma fa auren
nan da zan qara inada dalili na-"
"Meye dalilin naka Adeel?" Ta katse sa "Mene bana maka as a wife? Ina maka girki
ina k'ok'arin baka farin cikin daya kamata a kullum, baka ta6a neman had'a kwanciya
dani na hanaka ba koda kuwa am not in the mood me kakeso nayi maka again? Na lasa
tafin k'afanka ko me kakeso?"
"Naji kinayin all the above stated activities amman zaki iya bani family ne?
Nagaji yanzu haihuwa nakeso, kekuma bazaki iya ba your womb is damaged shikenan so
kike dukan mu biyu muyi asaran auren da mukayi?"
Hannu tasa ta share rolling tears nata, "Adeel ji yadda kake magana as if daga
halitta nane mahaifata batada kyau tun farko, kaine nan fa ka lalatamin mahaifa
amman ji yadda kake magana kayi adalci mana."
"Kifa dena kawo min zancen adalci dan kema bakisan ma'anarsa ba, inhar da
kinsani da bazakiyi wa Al'ameen abubuwan da kika mai ba."
"Hakane Adeel thank you so much for teaching me such a valuable lesson in life I
shall never forget it. Tabbas na tafka babban kuskure rabuwa da Ya Al'ameen masoyi
na na haqiqa na aureka."
"Sede nadaman kam dan se in a lahira keda ki sake rayuwa dashi zaman ki a gidan
nan dindindin! Kafin na dawo kuma ki tattara nan ki dafa min lunch ni na gaya
miki." Anan ya fice ita kuwa ta sauqa har qasa tana kuka na haqiqa bazata iya
kwatanta kalan nadaman da tayi ba ashe Al'ameen shine masoyinta bata ta6a sani ba?
Seda tayi ta godewa Allah sannan ta shiga had'a mai lunch.

Tsabagen tashin hankali ko yunwan ma bataji, tana baje a kan tiles a d'akinta
wayarta ya shiga ruri tana dubawa taga Mama bazata iya tuna when last Mama ta kira
taba don haka ta d'aga without wasting time.
"Assalamu Alaikum ina ini Mama?"
"Wa'alaikis salam ya kike Zainab?"
"Laf-" sekuma ta rushe da kuka.
"Helo Zeezee?" Cikin sautin kuka ta amsa da "na'am."
"Kukan me kuma?"
"Mama fa har ansa date na bikin nasu bakiga abinda ya kawo min as kayan fad'an
kishiya ba. Mama ban gaya miki bane amman yanzu bazan iya concieving ba."
"Subhanallah! Aina aka tabbatar miki da hakan?"
"Asibiti Mama."
"Subhanallah! Are you sure matsalar daga kece kuwa?"
"Daga nine Mama for six months Adeel yata d'uaramin wasu capsules ban ta6a sanin
na hana d'aukan ciki bane seda ya gama rusa min mahaifa."
"Ya Salam!! Wannan abu dame yayi kama? Amman Zeezee bakida wayo ne da zaki
tashan magani har na tsawon watanni shida without asking him name ne?"
"Mama I trusted Adeel with all that I got ban ta6a tsammanin ze cutar dani haka
ba gashi yanzu har gori yakemin yana kira na da 'yar sadaqa kokuwa wacce bazata iya
haihuwa ba Mama inda nasan da haka da ko Ya Wakeel kukace in aura zan aura saboda
za6in iyaye is always the best kuyi haquri ku gafirceni wallahi naga gwagwarmaya a
rayuwa kuma bayan family mutum baida kowa again, nayi nadaman dikkannin abubuwan
dana aikata muku tun ina k'arama."
"Ya isa Zeezee ki k'ara haquri wataran se labari no situation is permanent
kinji?"
"Naji Mama nagode ya Baba?"
"Yana nan k'alau."
"Toh ki gaida min shi harda Ya Omar ma, Ya Ibraheem ma don Allah kibasa haquri,
kona kirasa bai d'agawa he is still mad at me."
"Zan masa Allah rufa mana asiri ya kawo sauqi cikin lamarinki."
"Ameen Mama nagode sosai."
"Yauwa se anjima" anan ta katse wayar. Tunanin ya zatayi ta jawo hankalin Baba
kan Zeezee take amman takasa saboda anytime ta taso mai da maganan Zeezee ko
sauraronta baiyi.

*^*^*
Haka fa preparation na biki ya cigaba da gudana, Zeezee de aikin kullum itace ta
kuka gashi sede zance be had'ata da Adeel ba seya zageta koya gaya mata baqar
magana had'e da goranta mata ba. In banda dad'a rama ba abinda take yi. Ahaka har
watan bikin Adeel da Ruky Mama ya iso, cikin ikon Allah aka soma biki aka gama
lafiya wanda cikin duk events d'in ba wanda Zeezee taje kullum tana maqale a d'aki
tana kuka.
A daren randa aka d'aura musu aure aka kawo amarya gidanta. Convoy ne sosai
motoci se shiga ciki suke har ya zammana saura ba inda zasu samu shiga seda suka
faka a waje. Zeezee na leqe ta window tana kuka se tuna time na bikinta da Al'ameen
take itama yadda convoy ya had'u mata amman nata da Adeel wane akuya aka d'auko
daga ita se shi aiko anan ma ya isa ya mata gori "why didn't I thought of this
before?" Ta tambayi kanta. Daren ranan gabad'aya ta kasa samun sukuni ita rabonta
datasa Adeel a ido ma tun kamin a soma wedding events nasun, any time tunanin yanzu
haka Adeel na tare da wata suna shan soyayyansu yayi hitting nata se ta rushe da
kuka haka seda garin Allah ya soma wayewa ta samu tayi bacci.

Some hours afterwards... Site na Ruky Mama @ 11:46am.


Kwance take bisa jikin Adeel hannunta d'aya akan chest nasa tana wasa da
d'ad'd'aikun gashin k'irjinsa "Baby am hungry" ta fad'a a shagwabance. Ruky Mama ta
kasance 'yar duma-duma za a iya cewa tana da k'iba dake a k'oshe take b'ul-b'ul
tana da kyau dai-dai gwargwado uma tsayayyiyar mace ce.
"Toh ki tashi kiyi warming kanki kink'i." Yace da ita yana shafa fuskarta.
"Bazan iya ba the pain is too much."
"Yi haqur kinji? Nasanki fa da juriya."
"Toh Baby breakfast fah? Will I be the one to cook?"
"Haba! Meye amfanin Zeezee a gidan nan da har zakiyi girki?"
"Are you sure Baby? Zata fyarda ta girka mana?"

"Yes Sweetheart karki damu." Kissing nasa tayi passionately "I love you."
"I love you more."
"Nifa ban yarda da wannan I love you d'in ba nasan kaje ka sameta abinda zakana
gaya mata kenan itama."
"Inji wa? Rabona dana sata a ido I can't even remember seriously wancan batada
wani amfani I use her for sex and cooking kuma kinga gaki yanzu kin fita zuma da
dad'i ba abinda ze sake shiga tsakani na da ita."
"Are you sure Baby?"
"Dont you trust me?"
"I do Love."
"Good tashi toh muje kiyi warming kanki." A hankali cike da so da k'auna ya samu
tayi warming kanta sannan sukayi wankan sunnah suka fito. Nan ma da kansa ya shafa
mata mai se wani binta yake sekace 'yar gwal sun gama shiri fes suka koma suka
kwanta tana manne a jikinsa. Hannu ya miqa ya d'au Wayansa tare da kiran Zeezee
sede har 2 missed calls bata d'aga ba se ana uku.
"Yauwa Ke Arrange breakfast for us ki kawo immediately kinji?" Lallai ma ta
furta a ranta sannan ta kashe wayan. "Hello? Hello? This rascal wants to die" ya
furta angrily.
"Babe ka barta kawai ka siyo mana."
"No way meye amfaninta? Excuse me kinji I'll be right back."
"Don't take long okay?"
"Okay Sweetie" nan yayi pecking lips nata sannan ya fice. Chan a d'akinta yaje ya
tarar da ita tana aikin kuka bubbuga k'ofan yayi seda ta juyo tana kallonsa da
swollen eyes nata. "Hanging call zakiyi a kaina?" kaman a kyaftawan ido ya nufi
gadon tare da fincikota daga kai cike da mugunta. "Magana nake miki!" Ya fad'a a
tsawace "ko sekinji sauqan mari zaki ansani?" Kai ta kad'a abin tausayi tana me
cigaba da kukan.
"Zaki had'a breakfast d'in kokuwa sekinji na jaki?"
"Zan had'a muku" ta furta tana kuka sosai.
"Maza wuce ina kallonki" anan ya saketa and ba gardama ta nufi kitchen ta fere
doyan ta tafasa sannan ta musu doya me k'wai a jiki sannan fried egg separate a
gefe. Cikin food warmers nata tasa takai dining table ta ajiye duk anan Adeel na
zaune a parlour yana jiranta.
"Ke anan kuma zaki barsu? Cemiki akayi Ruky zatazo nan?"
"Aina kakeson na ajiye?" ta tambaya a hankali abin tausayi.
"Site nata zaki kai mata."
"Adeel nida ita waye babba? Waye uwar gida?"
"Wannan kuma keya dama inma kece kakar gidan can ta matse miki nide ki kai wa
matata breakfast natan."
"Wallahi Allah bazan kai ba kai bakada imani ne? In zakayi adalci nida ita waya
kamata ya kawo ma wani abinci?-"
"Ke ya kamata ki kai mata" ya katseta "and sai kin kai d'in, ce miki akayi Ruky
sa'ar kice?"
"Bazan kai ba abun kuma ai ya koma iskanci." Belt nasa taga ya zare yana
nannad'awa a hannu "zaki d'auka kikai kokuwa?" Kallonsa ta tsaya yi totally short
of words dagaske yanzu dukanta yakeson yi? "Kina kallo na ajinki bazan iya baki
kashi bane anan in kuma saki ki kai matan?"
"Zaka iya tunda kai mahaukaci ne zan kai mata amman kasani wallahi kaima Allah
baze barka ba Adeel idan baka gani akanka ba toh kajira akan 'ya'yanka."
"Aikin banza d'aga ki kai mata" one more look tamasa sannan ta kad'a kai ta jera
flasks d'in kan tray ta shiga tafiya inda yake binta a baya. Zaune kan kujera a
parlour suka tarar da Ruky Mama dagangan bayan fitan Adeel ta canza outfit nata
tasa bomb short da vest da rabin nononta a waje suke. Koda taga Zeezee batai niyan
karb'anta ba illama miqewa datayi tana twisting ass nata gasu sunyi ukun na Zeezee
ta nufi inda Adeel ke tsaye tare da pecking nasa a lips "Babe it took you so long."
"Am sorry kinji? Lets eat nasan you are starving." Anan ne Zeezee ke ajiye musu
abincin kan dining seda Ruky ta bari Zeezee ta juyo sannan ta sake kaiwa Adeel wani
hot kiss d'in me tsayi fiye dana d'azu. Kawar da kai Zeezee tayi sannan tahau
tafiya dan basu space takai da fita Adeel ya rik'o hannunta.
"Baki iya gaisuwa bane?" Kallonsa ta tsaya yi full of suprise, murd'a mata hannu
cike da mugunta yayi ganin she's not ready to talk, hawayen datake ta neman
had'iyewa taji sun soma tsiyaya daga kumburarrun idanunta "ina kwana?" Ta gaishe
da Ruky Mama tare da miyar da kallonta kan hannun nata da Adeel yak'i sakewa har
yanzu. Seda Ruky ta gama k'are mata kallo sannan tana sake lumewa jikin Adeel ta
amsa da "lafiya sannu da aiki mungode sauran kuma lunch ko Babe?"
"Yyess" ya amsa jiki na rawa "me kikeso for lunch?"
"Fried rice and with chicken of course."
"So kinji ko?" Ya maido da kallonsa kan Zeezee ganin batada niyyan amsawa ya sake
murd'a hannun nata. Tana hawaye sosai tace "naji" se anan ya sakota wajen ta riqe
da other hand nata tana kare mai kallo yadda yayi pink shar sannan ta fice tana
kuka me tsuma zuciya.

Ruky kam a cinyan Adeel ta zauna gabad'aya ta dak'ula mai lisafi da wannan annen
shirin dake jikinta, yaci ya bata ahaka har suka samu suka gama karyawan a yayinda
Zeezee ke chan a kitchen nata tana gyaran kaji tana duban sauce na fried rice, tana
aikin tana kuka har ta samu ta gama ta kai musu. Batayi sallama ba ta fad'a cikin
parlourn nasu ko d'aga kai ta kallesu batayi ba se k'aran kisses da suke exchanging
kawai takeji, da wuri-wuri ta ajiye musu ta fito ta nufi site nata inda ta cigaba
da kukan daga inda ta tsaya.

Da irin wannan rayuwa da take leaving tasan na lahira ma yafita jin dad'i. If
only she can talk back to Adeel tace mai bazata sake yimai girki ba da tayi amman
sanin mahaukaci ne shi yana iya mata duka ya illatar da ita ya cuceta na har abada
yasa kawai bata biye masa takeyi mai abinda yakeso tunda no situation is permanent
she believe one day she'll be free from misfortunes na Adeel.

Haka Adeel ya cigaba da wulak'anta Zeezee a gidan. Har Ruky ta samu sati bata
ta6a hura wuta ba a gidan as girkin safe, rana da dare duk Zeezee keyi tana kai
musu nan ma duk shiganta seta tarar da baqin ciki don daga ta kamasu suna kissing
juna se Ruky na zaune a cinyansa suna romancing juna. Cikin satin nan Adeel be ta6a
ya kwana a site na Zeezee ba in short bayida ma niyyan dawo mata kullum yana maqale
da Ruky suna baza love.
Yau Lahadi exactly one week one day da bikinsu Adeel kenan, kaman kullum da
safe bayan shida Ruky'nsa sun yi wanka sun shirya tsaf ya tambayeta me takeson
karyawa dashi bayan ta fad'i mai ya d'au waya ya kira Zeezee seda ya kusa tsinkewa
ta d'aga tare da yin shiru.
"Kin d'auka kinyi shiru k'ona min airtime kikesonyi kome? Mschww! Ni tashi ki
had'a mana breakfast indomie Ruky ta keso ni kuma chips."
"Haba Adeel in anyi na marmari da amarci kuma ai yanzu is high time Ruky'n ta
soma girki itama kayi adalci mana."
"Bazan yiba ko kin manta matsayinki ne a gidan nan? Cooku kin gane? Zaki girkan
ne ko bazaki girka ba?"
"Gaskiya bazan girka ba ai ba baiwar kuce niba" tana kaiwa nan ta katse wayar.
"Babe ya kukayi da ita?" Ruky dake kwance jikin Adeel tayi maganan.
"Excuse me Bebe yarinyan nan wants to die ina zuwa."
"Wai bazata girka ba?"
"Barta" ya fad'a fusace.
"Calm down kaji? Ka barta d'in kawai zan girka mana."
"No way ita zata girka ina zuwa" yana kaiwa nan ya fice wani maqirin murmushi ta
saki "a sannu a sannu zan kashe auren naku" tace a ranta tana murmusawa.

Site na Zeezee ya nufa direct izuwa d'akinta. Banging k'ofar yayi wane ze 6alla
seda ta firgita "kikace meh?" Yayi maganan yana nannad'e belt dake hannunsa.
"Bazan girka ba na muku na sati na gaji." Dosan gabanta yayi "repeat it again!
Har in saki aiki kice bazakiyi ba?" Anan ya d'aga belt d'in sama ready to beat her
up, "repeat yourself."
"Zane ni zakayi yanzu Adeel?"
"Ba zana kad'ai ba Zeezee faffasa miki wannan fitsararren bakin naki zanyi zaki
girka kokuwa a'a?"
"Bazan girka ba-" kafin ta hankara tajiyo sauqan belt zuwaat! A bayanta nishi
taja dan zafin da taji, tare da matse idanunta take hawaye suka soma tsiyaya "zaki
tashi ne ko sena k'ara miki?" Tana kuka na haqiqa tace;
"Adeel ni ka d'aga belt ka zana yau akan wata?"
"An zane kin, kuma inhar baki miqe ba zan qara miki d'aya."
"Adeel bana blaming naka akan kalan abubuwan da kake min saboda nasan gir6e
abinda na shuqa nake, alhaqin iyaye na dakuma na masoyina Ya Al'ameen ne ke bina
amman kasani muddin nagama gir6ewa zaka nemen kamin wannan wulaqancin ka rasani
kasani no situation is permanent. Kana ganin kayi sabuwar mata kake neman maida ni
kashi a bola wallahi Allah yafika kuma shi ba azzalimin bawansa bane, girki kakeso
zanyi muku tunda nida kaina na jefa kaina cikin wannan situation amman inhar ka
sake d'aga abu ka ta6a min lafiyan jiki kasani bazan ta6a yafe maka ba wannan ma
ban yafe ba."
"Ki fad'i koma me girki ne in bakiyi ba jikinki ze gaya miki Ruky indomie nikuwa
chips." Hawayenta ta share sannan ta miqe a nitse tabar mai d'akin tana yi musu
girkin tana kuka ahaka har ta samu ta gama ta kai musu.
Bayan sun gama ci Ruky ta langwab'e fuska "Baby" ta kirasa wane zatayi kuka.
"Na'am Babe."
"Baby wanke-wanken nan yau nakega sede su kwana na samu cut a hannu na d'azu" ta
nuna mai inda ta manna bandage dagangan.
"Awch! Sorry Babe."
"Its okay ko Zeezee zata iya wanke min na yau?"
"Why not barin kirata tazo ta tattara." Nan ya d'au waya ya kira Zeezee alokacin
tana miqe kan gado tana kuka tajiyo ringing na wayarta tana dubawa taga shine, bata
6ata lokaci ba ta d'aga "kizo da wuri" yace da ita tare da katsewa. Without
wasting too much time ta wanke face nata sannan taje ta ga kiran nasa. Daga bakin
k'ofa ta tsaya "ki k'araso ki tattara plates d'in ki wanke Ruky ta yanke a hannu."
"Aunty Zeezee se hak'uri wallahi yankewa nayi jiya garin yankan albasa."
"Ma hak'urin me kike bata?" cewan Adeel "ba aikinta bane zo ki tattara." Kallonsu
both tayi sannan ta kad'a kai ta qarasa ta tattara plates d'in ta fita dasu, nan da
nan ta wanke ta shanya su. Chan da La'asr Adeel da Ruky suka shirya tsaf zasu
unguwa har sun fito se Ruky cike da qissa da dabara kamar yadda ta saba tace, "Baby
bazamu sanar da Zeezee zamu fita ba? Karta leqa mu taji shiru hakan ba dad'i."
"Mesa kike damuwa da ita ne wai? Lets go da Allah."
"Please for me lets tell her where we are going."
"For you only muje" dad'i sosai taji nan suka nufi site na Zeezee alokacin tana
zaune kan dining ga abinci a gabanta amman takasa ci gabad'aya ta fad'a kogin
tunani har suka shigo bata sani ba "uhm-uhm" Adeel yayi clearing throat nasa se
anan ta maido da kallonta garesu. Ganin haka Ruky tayi saurin kama hannun Adeel ta
had'a danata "sannu Zeezee dama zamu fita ne Baby ze kaini shopping nan Jifatu nace
bari mu sanar dake karki jimu shiru." Data gama sauraronta kawai seta kad'a kai ta
d'au plate nata ta miqe "Allah kare" tace dasu ba tare data kallesu ba ta fice zuwa
d'akinta. Achan ta bud'e sabon dandalin kukan, bazata iya tuna when last Adeel ya
kaita shopping ba Allah shi kyauta. Ruky kuwa shopping sosai Adeel yayi mata kaman
ba gobe bayan sun dawo gida ta babbaje kayakin kan gado turare d'aya ta d'ago ta
miqa mai "gashi wannan ka kai wa Zeezee kaji Baby."
"Naki ne ina ko bakiya so ne?"
"Inaso ai biyu na siya ka kai mata wannan kaji?"
"Mesa? Ki manta da ita mana."
"Please Babe matarka cefa itama yakamata yau kaje ka kwana mata ma ai."
"Kin gaji dani ne haka?"
"Haba wane ni nagaji da kai ai abin marmari ne kai kawai inason wa 'yar uwata
abinda nakeso wa kaina ne kaje kaima ka bata haqqinta I know she must be missing a
lion as you!" Dad'i sosai yaji yadda takirasa da lion "are you sure Babe? Nifa nace
bazan sake kwana mata ba bana buk'atar ta again."
"Yi haquri de Baby na ita tanayi nasani."
"Naji amman se later during the night toh."
"Yauwa kaga kafin nan nima seka bani abinda ze d'ibe min kewanka."
"Come here" ya buk'aceta jikinsa taje ta fad'a nan suka fad'a wani duniyan na
daban***

9pm Ruky tasa Adeel gaba sam seya kwana da Zeezee yau, har doorstep na Zeezee
tayi mai rakiya sannan takoma site nata, seda yaga tayi shutting door nata yashiga
ciki direct d'akinsa ya nufa ya watsa ruwa sannan ya fito ya nufi nata d'akin. Miqe
kan gado ya tarar da ita amman ba bacci take ba.
"Ke tashi ki dafa min indomie" shiru tayi kaman bata jisa ba "ko bakiji ba?" ya
tambaya a fusace.
"Naji" ta amsa a hankali sannan ta miqen ta nufi kitchen nan da nan ta had'a
mishi takai masa dining inda yake zaune ta ajiye zata juya kenan ya riqo hannunta.
"Zauna kema" ya umarce ta, batayi musu ba ta zauna be sake ceda ita komi ba as se
cin abincinsa yake seda ya gama yayi nak sannan ya miqe "tashi muje mu kwanta."
"Kaje bana jin bacci" ta amsa a hankali.
"Muje nace karki 6atan rai" bata mai musu ba ta bisa izuwa d'akin. Hijabin
jikinta ya rage mata duk anan bata ce dashi k'ala ba, daga nan ya kashe musu wutan
d'akin kamar wacce batada feelings kuma baibiya haka tayi mai a daren ranan duk
abinda yace tayi yitake ba gardama, a haka har ya samu biyan buk'atansa da ita,
sede shi kanshi beji dad'in abinda ta riga mai ba sekace wacce batada feelings?
Hijabinta taja ta 6urma sannan ta miqe ta dim light ya ga miqewanta "ina zakije?"
Ya tambayeta.
"D'akina I guess amfani na ya qare anan" bece mata komi ba tafice ta ja mai
k'ofa. Tana isa d'akinta ta jefa kanta bisa gado ta shiga aikin kuka.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
Miemiebee Novels
Saturday, 11 February 2017
‘YAR GATA CE!
BY MIEMIEBEE
PAGE 47
February, 2017

Life moved on... girki de kullum Zeezee ce meyi ba safe ba dare. Ba aikin Ruky
agidan sede tayi wanka su fita outing da Adeel. Koda wasa Zeezee tace zata fita
koda kuwa gidansu Lubiee ne bayi barinta. Yanzu kuwa Zeezee komin meh Adeel ya sata
yi bata mai musu bale gardama, komin aikin daya sata inma masa kokuwa wa Ruky yi
take, be sake ya nemeta kwanciya ba kuma ta hanasa sede har ya gama abinda yake
kaman gunki haka take tsaya mai ba feelings ba komi. Se Adeel yayi wa Ruky kwana
uku ko hud'u sannan yayi ma Zeezee d'aya, a d'ayan nan ko seya nemeta sau uku
atimes har hud'u bata hanasa, gabad'aya ta zama abin tausayi a gidan. Weekly a
gabanta Adeel ze irga pocket money 20k ya baiwa Ruky itako dukda bautan da take
musu ko naira bayi ya had'asu don kanta ta d'auke idonta akan abun hannunsa.
Addu'anta a kullum baifin
_Rabbana Atina Fidduniya Hasanatan Wa Fil Akhirati Hasanatan wa kinna Azzaban
nar_ kullum se ta tashi Sallan dare tana kuka wa mahaliccinta daya kawo mata sauqi
cikin lamarinta, sosai ta tattara hankalinta kan addininta kullum tana kan google
tana benefiting from it har online islamic classes tayi joining inba aiki take ba
toh tana maqale a d'aki tana kaaratun Al-qur'ani kokuwa tana istighifaar. Sosai ta
shiryu tayi kuma nadaman dukkanin misdoings data aikata da a baya.

3 weeks after bikinsu Ruky tayi resuming school hakan ya maida ita very busy
kod'an sharan da takeyi dasu mopping bata samunyi data dawo gida se tayita
complaining ta gaji. Koda Adeel ya gwada kawo mata zancen me me aiki kuwa a fili
tak'i wai zasuyi mata snatching miji.

"Toh Babe ni bansan ya kikeso muyi ba." Adeel yayi maganan yana latsa wayarsa.
Tana zaune a gefensa ta karb'e wayan cike da dabara ta ajiye a gefe "Baby talk to
Zeezee ko zata na d'an taimaka min tunda ita bataza zuwa school kaga mun kusa exams
karatu nake nima."
"Nifa banason tana shigowa nan akawo miki me aikin dont worry they wont snatch
me away."
"Gaskiya you are too handsome inbarka a gida da me aiki ni kawi kayi ma Zeezee
magana" ta qare maganan kaman wacce zatayi kuka.
"Toh kuka kuma zakiyi?"
"Eh mana bakace komi ba."
"Kema kinsan duk abinda kikeso shi za'ayi, Zeezee kikeso tana miki aiki?" Kai ta
gyad'a tana wasa da gashin kansa "shikenan toh miqon wayana." Cike da jin dad'i ta
d'ago wayar ta miqa mai nan da nan ya kira Zeezee a lokacin tana karatun Al~Qur'ani
mai girma, da hankali koyan baqinta yake qwarewa. seda ta kammala ayan da take
sannan ta d'aga wayantan be jira tayi sallama ba yace "Ke kizo yanzu" cike da nuna
isa.
"Toh ina zuwa" ta amsa ba yabo ba fallsa sannan ta miyar da Qur'anin ta ajiye
tajeta. A parlour tayi sallama kasancewar suna daga ciki basu jiyota ba haka tayi
zama wajen se chan suka fito d'aukan abu anan suka tarar da ita. "Kinzo kin zauna
anan baki iya sallama bane?" cewar Adeel.
"Nayi baku amsa ba" ta amsa ba tare da ta d'aga kai ta kallesa ba.
"You are well aware that Ruky na ta fara school ko? So batada time da zatana yin
ayyukan daya kamata in that case nakeson kina rage mata."
"Aikin meh da meh ma zatayi maki Babe?"
"Kace shara da wanke-wanke ba se dusting daba kullum ba amman banda d'akin mu ni
zanna sharewa."
"Toh kinji ko?"
"Naji" ta amsa zuciyarta na mata quna sosai. "Yau zan fara ko gobe?"
"Gobe will be fine" cewar Ruky, "nagode." Ba tare da ta sake ce da d'ayansu komi
ba tayi taking leave nata. Da harara Adeel ya bita ba abinda yafi basa haushi kaman
abinda take masa in yana kusantar ta. "Babe whats wrong with Zeezee two days bata
magana bata musu komi kace tayi yi take?"
"Taga haza mana, taga ba amfanin retaliating datake takeyin abin arziki don
lafiyan kanta."
"Kokuma don tanason ta karkatar da hankalinka izuwa gareta ba."
"Haba Babe ya kike magana haka? Mezanyi da matar da bazata iya haihuwa ba?"
"Are you sure?"
"Yes Babe"
"I trust you lets go and shower" zeyi magana tayi shutting nasa da kiss "lets go
please" ba musu yabi bayanta. A washegari Zeezee bayan ta gama share site nata
takuma tabbata Ruky ta tafi school ta nufi site nata dan share mata kaman yadda
Adeel yasata. Tana cikin mopping kitchen tajiyo qaran bud'e k'ofa razana tayi
gabad'aya danko bata zata da mutum a gidan ba cause bata tarar da motan Adeel a
waje ba ashe dashi Ruky ta tafi school yau. Tana cikin wannan saqe-saqe taga Adeel
tsaye bakin k'ofan kitchen d'in da nickers kad'ai a jikinsa da alama daga bacci ya
tashi. Batare da tace dashi komi ba ta cigaba da mopping nata ruwa ya qarisa ya
d'auka sannan ya kur6e tas har ya fita seya sake dawowa "Zeezee" ya kira sunanta
tana jin haka tasan buk'atanta yake. "Dake fa nake" ya fad'a sounding angry.
"Na'am" ta amsa ba yabo ba fallasa "meke damunki?" Ya tambayeta amman Ita dariya
ma tambayan nasa ya bata yanzu bayan dukkanin abubuwan da yake mata har yanada gut
da ze tambayeta meke damunta? Lallai kuwa. Murmushin takaici ta saki sannan tace,
"babu" tana me tsiyaye ruwan mopping d'in cikin sink. "Kin samu ina tambayanki meke
damunki kike min yanga?"
"Nace maka babu karatun Qur'ani na ne yaqi zama shine yake damuna."
"Not that I mean psychologically."
"Babu nasan where you are heading to se kayi hak'uri banida tsarki in Ruky tazo
tana iya biya maka buk'atanka" takai da bakin k'ofa dai-dai gabansa kenan tace,
"excuse me" ba musu ya matsa mata nan tayi ficewarta taje ta cigaba da koyon
haddanta.

Ana cikin haka wata rana Zeezee na cikin dusting dining table na Ruky taji
k'aran bud'e k'ofa, a guje Ruky Mama ta fito ta nufa kitchen se amai shima Adeel
cike da tashin hankali ya bi bayanta aman ta cigaba dayi a yayinda Zeezee ta tsaya
tana kallonsu daga inda ta tsaya.
"Sannu Babe sannu kinji? How are you feeling?" Yayi maganan yana ja mata kujeran
dining ta zauna har anan kallonsu Zeezee ke tasan sarai shigan ciki ne da Ruky
cause exactly haka Fateeman Ya Ibraheem take time da take da ciki itama.
"Baby am feeling nauseatic."
"Sannu kinji tashi muje asibiti."
"No need" ta amsa a takaice.
"Why?" Ya tambaya a take. "You are sick."
"I think am pregnant saboda nayi missing period d'ina this month." Dum! Zuciyar
Zeezee ya buga Allah sarki ita, daba don abinda Adeel ya mata ba da yanzu itama da
'yarta kokuwa d'anta yana ibe mata kewa, ace shekaranta d'aya da watanni aka da
aure amman ko 6ari bata ta6a yiba se wacce dududu 3 months ne da aurenta har ta
samu ciki, amman Allah ze saqa mata.

"Pregnant!" Yayi exclaiming "are you serious Babe?!" Gabad'aya ya kid'ime don
dad'i tsugunawa yayi ya shiga kissing nata anan Zeezee ta yasar da towel d'in ta
ruga a guje izuwa site nata ta baje kan gado ta shiga rusa kuka. A ba cikin ma ya
ta qare da wulak'anci bale yanzu da Ruky ke d'auke da juna biyu? Tabbas tasan nata
ya qare. Haka ta cigaba da kuka har seda ta jiyo qaran bud'uwa da ruhuwan gate
tabbacin su Adeel sunfita asibiti kenan. Anan ta sake rushewa da wani kukan.
It didnt took them long suka dawo da wuri ta miqe ta shiga leqensu ta window
sede wani tattalin dataga Adeel nayiwa Ruky wato tafiyan ma bazata yiba d'agata
yayi chak har ciki nan fa kumburarrun idanunta suka shiga zubda sabon hawaye tana
cikin yin kukan wayanta yahau ringing ko bata duba ba tasan Adeel ne ba tare da ta
duba screen din ba tayi answering "gani ina zuwa" ta furta tare da katse wayar. Nan
da nan ta wanke fuskarta ta fice, zube a parlour ta samesu se faman sannu Adeel
keyiwa Ruky wanda take ta shagwaba.
"Ga Zeezee'n nan toh me kikeso?"
"Custard nakeso."
"Kinji Zeezee had'a mata custard me kyau anan yi sauri, our baby is craving"
gabad'aya Zeezee ma hankalinta ba a gun yake ba tayi zurfi cikin tunani "dake fa
nake Malama! Ko baqin ciki kike mana don mun samu qaruwa? So kike kowa ya zauna
kaman ki ba cigaba?"
"A'a Allah raba lafiya Ruky" ta fad'a tana danne hawayenta.
"Ameen nagode kiyi sauri please." Nuni da kitchen d'in Adeel yayi mata nufin
tayi sauri nan ta miqe in less than 15mins ta kawo wa Ruky Custard nata ta miqe
zata tafi kenan Ruky tayi sauri taja Adeel ta rad'a masa abu a kunne.
"Tsaya Zeezee" chak ta tsaya "massage Ruky's legs for her suna mata tsami."
"Nikuma?" Ta tambaya suprisingly.
"Baki san mata masu ciki hakan na faruwa dasu bane? Koda shike ko 6ari baki ta6a
ba bale ki sani."
"Naji ban ta6a yin kida 6ari ba amman suma ai se in cikin yayi girma ne. Amman
nata ko 6ullo kai yayi ne?"
"Ja chan gefe da Allah! Ke mema kika sani game da mata masu d'auke da juna biyu?
Ko 6ari baki ta6a ba don haka kimin shirru kiyi abinda na saki." Kai zallah ta
kad'a sannan ta qarisa nan Ruky ta aza mata santala-santalan k'afafunta bisa
cinyarta. D'ago kai Zeezee tayi ta kalleta sannan ta shiga massaging mata dagangan
Ruky tasa ihu. "Arghhh!"
Nan Adeel dake gefensu yana latsan waya ya juyo "ya haka Zeezee?"
"Baby kace tamin a hankali."
"Da da k'arfi take miki? Kefa banison mugunta kina jina ko? Ba yadda za'ayi ke
kin kasa d'aukan ciki wacce ta d'auka kuma kina yi mata mugunta tell her sorry."
"Ad-" ta gwada explaining kanta.
"I said tell her sorry!" ya katse ta angrily.
"Kiyi haquri" ta fad'a tears na forming a idonta seda Ruky ta soma gyangyad'i
Adeel ya yarda Zeezee takoma site nata achan ta cigaba da kukan abin tausayi.

Hakanan tun daga ranan Adeel yake bawa Ruky extra ordinary kulawa, ciki sekace
dashi aka fara a duniya kuma shine na qarshe. Kusan a kullum se sun fita shopping
wa unborn nasu. A rana se Zeezee tayi girki kusan kala uku zuwa hud'u duk Ruky tace
bataso tamkar baiwa haka Zeezee ta zame a gidan se ramewa take tana duhu. Yauma
kaman kullum Adeel ya kirata bayan taje ta tarar da Ruky kwance bisa cinyan Adeel.
"Baby kikace me kikeso?"
"Miyan gauta." Ta ansa a kasalance.
"Kinji miyan gauta takeso, na siyo d'azu seki d'auka a fride ki mata da tuwon
semolina ko?"
"Eh" ta gyad'a kai.
"Oya Zeezee tashi."
"Adeel mene kuma miyan gauta? Bansan shiba ban kuma iya ba ta za6i wani abin na
daban."
"Shi baby'nmu yakeson ciki don haka shi zaki girka mata."
"Da ban iya bafa?"
"Seki koya a daren yau ko da yunwa kikeson Baby machine d'ina ta kwana?"
"Allah huci zuciyarka" tana kaiwa nan ta miqe ta ciro gautan daga fridge sannan
ta nufi site nata, tunanin ya za'ayi ta girka ta shigayi chan idean ta kira Mama ya
fad'o mata nan da nan tayi grabbing phone nata ta yi calling Mama.
"Hello Zeezee?"
"Na'am Mama ina yini?"
"Lafiya ya kike?"
"Lafiya qalau ya Baba?"
"Shima qalau."
"Toh Madallah Mama dama nace ko kinsan ya ake miyan gauta?"
"Miyan gauta kuma Zeezee? Meya kaiki?"
"Ermmm kawai inason cine. "
"A'a ke tuwon ma yaushe kike ci, gayamun gaskiya."
"Mama Adeel ne keson na girka wa matarsa kinsan tana d'auke da juna biyu."
"Tohhh kece cookursu kenan? Ko yarinyan tanada hankali ne?"
"Eh Mama-"
"A'a gayamun gaskiya" ta katse ta. Ai kasa magana tayi se hawaye da kuka kawai
seda tayi tasamu tayi shiru sannan Mama ta tambayeta meke faruwa. Bata 6oye mata
komi ba ta labarta mata komi. Sosai Mama taji tausayin 'yarta ina ma ace zata iya
cirota daga cikin wannan hali da take ciki.
"Kina jina ba Zeezee? Bazaki girka ba ai don ya sameki a sadaqa doesn't mean a
talauci ko wahala ya tsintoki da ze maidaki baiwa haka. Oh God! Duk fa kece Zeezee
kikace ke bazaki ji maganan kowa ba se na wannan d'an iskan da besan darajarki ba,
ga irinta ai yanzu."
"Mama wallahi I deeply regret every single action of mine back then ban ta6a
sanin za6in iyaye is the best ba kuma iyaye nada haqqi akan 'ya'yansu haka ba se
yanzu ku gafirceni Mama."
"Nikam na yafe miki Zainab Baban nakine har yanzu na gagara karkato da
hankalinsa."
"Karki gaji dani don Allah Mama, daga Allah seke nakeda."
"Kin ta6a jin inda uwa ta gaji da 'ya'yanta ne? Kome kika min ina sonki Zainab
saboda ni kad'ai nasan zafin haihuwarki."
"I love you so much Mama❤" ta fad'a tana kuka sosai.
"Kibar kukan haka kuma bazaki dafawa kowata shegiya ba abinci in bayi son ta
kwana da yunwa ya je ya sai mata abincin mana."
"Mama dole na na girka mata shine kwanciyan hankali na."
"Kamar ya Zeezee?"
"Mama inbar girka ba duka na zeyi wallahi."
"Duka fa kikace? Wa iyya zubillah! Zana de? Abin nasa gaskiya ya soma wuce gona
da iri Zeezee I cant take it anymore haifanki fa nayi ba akan bola na tsince kiba
wallahi na gaji sede yin hakan ya zama sanadiyar rabuwana da Babanki amman gobe
gobe zanzo gidan naku in d'aukeki kimin kwatance."
"A'a Mama please karkiyi haka, banason abinda ze shiga tsakaninki da Baba da
hakan ya faru gomma ace har qarshen rayuwa na haka da Adeel zan qare yata galla min
azaba, ba laifinki bane after all nine nan na jefa kaina cikin wannan yanayi da
kaina don haka kibar damuwa kuma ai Allah baya d'aurawa bawansa jarabawan da baze
iya d'auka ba."
"Hakane Zeezee amm-"
"Toh kinga Mama zan cigaba da haqura surely one day Allah ze yayemin wannan
bala'i nide yanzu kawai ki bani ingredients da procedure karki damu."
"No way bazan bayar ba."
"Please Mama in babaka ba ze dakeni wallahi" don dukan kad'ai data ambata yasa
Mama ta gayamata yadda ake yi. Godiya sosai tayi sannan ta shiga hura wuta, tana
gamawa takai mata.

*^*^*^
Haka Zeezee ta cigaba da azabartuwa a gidan, na yau daban na gobe daban. A haka
har cikin Ruky ya samu 5 months yasoma nunawa, nan fa iskanci da iyayi ya qaru.
Bata zama a gidan seda vest yadda cikin ze sake nunowa gashi seta bari Zeezee na
aiki seta zo tana ture-turen tsiya kokuwa ta soma fitowa da ledan gashi kokuwa
tsire wanda she is sure Zeezee ta manta rabonta data d'ana nama a baki.

Yau ma as always Zeezee na cikin mopping parlour da wuraren 6:15pm na yamma


Adeel da Ruky suka dawo daga kasuwa anje anyi shopping kayan baby kan ba gobe. A
parlour suka dire kayakin ko sannu da aiki ba wanda yayiwa Zeezee cikinsu itako
Allah-Allah take tagama ta fita. Bada jimawa ba Adeel yace ze fita, "ina zakaje
Baby?" Ruky ta tambaya tana ninke kayakin baby'n nata.
"Zan anso abu ne I'll be right back."
"Toh shikenan kadawo ka sameni a site na Zeezee zanje na tayata hira."
"Is that necessary Babe? Ba gomma kin kwanta kin huta ba."
"Dont worry seka dawo, Baby and I love you so much."
"I love you both too" nan ya bata light peck sannan ya fice. Timing nasa tayi
seda ta bari ya kusa dawowa sannan ta nufi site na Zeezee tayi sallama kaman
dagaske. Nan ta shigo ta gaisheta and ba yabo ba fallasa Zeezee ta amsata "dama
nace barinzo na gaisheki ina d'an zagaya cikin gida kinsan abinki da me juna biyu
seda strolling in ba haka ba k'afafun se su kumbura."
"Hakane Allah raba lafiya" kadai Zeezee tace mata anan suka jiyo k'aran bud'uwan
gate se shigowan motan Adeel seda Ruky ta tabbata yafito kuma sunyi dashi idan ya
dawo yazo ya sameta anan, seta zaro wani jan bakin dake nan kaman jini ta goggoga a
gefen bakinta tare da zare ribbon nata ta barbaza gashinta kan fuskarta alaman
tasha wuya d'innan. Kafin Zeezee ta tambayeta yada haka har ta sauqa k'asa tare da
wulla wa Zeezee wani d'an k'aramin wuqa da mamaki Zeezee ta cafke wuqan without
knowing how, danko still takasa comprehending me Ruky ke shirin yi haka.
"Ruky lafiya dai ko? Wuqan name kuma?" Anan ne Adeel ke shigowa nan Ruky data
goga rope k'asan idonta ta shiga ihu na sosai tana sumbatu "don Allah kiyi hak'uri
Zeezee karki kasheni ki kashemin abinda ke ciki wayyo Adeel! Please come back zata
kasheni." Dumbfounded Zeezee ta tsaya wajen tama kasa magana as Ruky bata isheta da
kallo ba.
"Innalillahi! Kisa!" Exclaimed Adeel alokacin dayake tsaye tsakiyar parlour'n.
"Meke faruwa? Me nake shirin gani haka?" Da gudu Ruky ta miqe ta fad'a jikinsa tana
wani irin kuka fuskarta ya d'ago yaga duk alaman jini "metayi miki? Me kika mata
nace!" Ya daka wa Zeezee tsawa wanda sanadin haka Ruky ta sake lumewa jikinsa don
yadda ta firgita inaga wacce akayima tsawan Har anan Zeezee ta kasa magana sema
kallon wuqan dake hannun tan take hawaye na forming rapidly a idonta sbin taysayi.
"Dake nake magana kashe min mata kikesonyi saboda ke kin kasa d'aukan abinda ke
jikinta? Jahilar ina ce ke? Iyye?!" Cikin sautin kuka Ruky ta soma magana, "wallahi
ni zamana ya qare a gidan nan ka za6i niko ita kawai a banza bazan zauna tazo ta
kasheni ba cikin dare tunda gashi da rana ma ta kasa hak'ura."
"Kaman ya na za6a Babe? Mezan da wacce bata haihuwa?"
"Ni wallahi ka za6a kafin nan zan koma gidan Babana" wani haushin Zeezeen da
banda raba ido tana hawaye ba abinda take har yanzu yake a fusace ya nufi inda take
tare da damqo ta da wuyan hijabinta, mari lafiyayye ya zuba mata a kumatu nan fa
Ruky tahau murmusawa finally plan nata has worked out seta raba auren su a yau.
Kumatun nata ta riqe da d'ayan hannunta hawaye nabin k'uncinta.
"Bakida hankali ne? Dake nake magana!" Adeel yayi maganan yana jijjiga Zeezeen
da har anan ta kasa cewa komi, banda kukan da take theres nothing more.
"Bazaki amsani ba?" Y sake kifa mata wani. Belt nasa ya zare a gun ya shiga nad'a
mata na jaki se kuka take ba sauti. Duk anan kallonsu munafukar take tana jin dad'i
seda taga Adeel na neman illata Zeezee sannan kaman dagaske ta shiga tajasa baya.
Se huci yake "matsa min Ruky sena fara kaita lahira kafin nan ta kaiki, muguwa
azzalima kawai." Jina-jina yayi wa Zeezee. Hawaye kawai take har anan ta kasa cewa
komi, nishinta ma ba fita yake sosai ba gakuma jinin dake yoyo ta hancinta dakuma
baki. Kaca-kaca Adeel yayi mata.

"Maza tashi kibarmin gidana annamimiya me kisan kai kawai tashi kibar min gida
na sawwaqe miki, na sakeki saki d'aya, biyu ki tashi ki fita nace! banason sake
ganin fuskarki koda a mafarkine. Kuma kikayi wasa har kotu sena kaiki kowa yasan me
kisan kai ce ke. Na rasa ya iyayenki suka girmar dake, banda rashin hankali ga
mugun hali again" Tana kuka sosai ta furta Alhamdulillah a ranta dukda de bata san
ina zata jeba a daren nan amman tasan koma ina ne ze fiye mata gidan Adeel. Miqewa
takesonyi amman don yadda jikinta yayi tsami ta kasa "bazaki tashi bane sena gama
hallakaki komeh?"
"Baby please let her be she have had enough mu tafi site namu zata tafi ai ka
riga ka sawwaqe mata" tayi maganan wane tana tausayawa Zeezee but deep inside ba
wanda yakaita murnan wannan saki. Da k'yar ta samu taja Adeel suka fice nan ma se
hak'uri yake bata tabari ya goge mata ciwon nata ma taqi sanin na qarya ne karta
tozarta kanta.

Zeezee kuwa seda tayi dagaske sannan ta samu ta miqe da k'yar ko wanke fuskarta
batayi ba tashiga had'a akwatunanta tana kuka na haqiqa. gabad'aya jikinta ya
tashi yayi pink. Nan da nan ta shirya kayakinta kap ba abinda ta bari har anan kuma
bata bar kukan da take ba, tambayan kanta ina zata je take. Ma wacce erin rayuwa ta
jefa kanta at her tender age ace auranta har biyu duk sun mutu? Wani irin bala'i ne
haka? A yau da zata tarar da watan da take neman bijire wa iyayenta data zauna ta
bata labarinta don rayuwar ta rayuwa ce dake cike da abin koyo da darusa. Bijire wa
umarnin iyaye ba abu bane nayi, tabbas ba wanda zeji labarinta yakuma ce still ze
bijirewa umarnin iyayensa. A yau ace ga mahaukaci Baba ze miqa ta gashi as sadaqa
wallahi bazata k'i ba ta koyi lesson a rayuwarta daman we are learn from our
mistakes. Allah rufa mana asiri Ameen.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!*


beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
Page 48
FEBRUARY , 2017

Jikinta ba k'wari yana mata ciwo sosai tasamu da k'yar taja luggages nata ta fita
dasu tasa a booth. Hamdala ta saki ganin da mai a ciki, ba tare da b'ata lokaci ba
tayi shoving kanta cikin motar ta kunna, koda su Adeel suka jiyo qaran motarta
basuyi ta kanta ba. Gate na recognising motarta ya bud'u mata ta fice sede kash
bata iya tuk'in dare ba bayan nan kuma bata san ina zata dosa ba gidansu Lubiee ne?
Gaskiya ba fasali koda Baba baze barta ta kwana mai a gida ba theres no place like
home ya kamata iyayenta ne su soma sanin wani hali take ciki, bazata sake tafka
sakarcin da tayi da a baya ba, don haka gidan zata wuce sede bata da courage.
Parking tayi gaba da layin gidansu kad'an ta shiga rusa kuka sosai, tissue tajawo
tare da kunna wutar motar nata ta shiga share jinin dake fuskanta inda Adeel yayi
mata jina-jina sede don zafi ta kasa gogewa don haka ta yasar ta kunna motar ta
shiga tuqi. Unguwansu dutsan tanshi ta nufa cikin ikon Allah tana driving a hankali
har ta isa gida alokacin ana neman wuraren 7:12pm gari be gama yin duhu shar ba.
Sam ta kasa fitowa daga motan da k'yar tayi gathering courage ta shiga ciki tana
rik'e da medium sized akwatinta. Mama ta tarar a tsakar gida tana zaune bisa
sallaya da alama yanzu take idar da Sallah. "Assalamu Alaikum" Zeezee tayi sallamar
tsoro na building acikin muryarta.
"Wa'alaikumus salam" Mama ta amsa cike da zumud'i jin muryan Zeezee. To her
suprise ta ganta riqe da akwati kobata tambaya ba tasan korota Adeel yayi ga kuma
yadda fuskanta yake duk jini tagun bakinta.
"Subhanallahi!" Tayi maganan tana dosan gaban Zeezee, kuka kawai Zeezee tasa tare
da fad'awa jikin Mama tana kuka me tsuma zuciya, hugging nata Mama tayi tana
bubbuga bayanta.
"Ya isa kiyi haquri bar kukan."
"Mama ya sakeni kafin nan seda yamin d'ankaren duka."
"Kiyi haquri Zeezee in shaa Allahu kin rabu dashi kenan har abada wuyarki ya
k'are ya isa kukan." Janta Mama tayi suka zauna kan darduma, "gayamin meya faru."
Tana kuka tana bawa Mama labarin k'azafin da Ruky Mama tayi mata da kuma yadda
Adeel na zuwa ba tare da ya bata chance tayi explaining kanta ba ya rufeta da duka.
Sosai Mama ta tausayawa 'yarta. Suna zaune a wajen Mama na ta kan bata haquri Baba
da Omar suka dawo from Masjeed. Da hira suna murmushi suka shigo amman Baba na
ganin Zeezee ya tamqe fuska shikansa yadda ta sake fad'awa ya basa mamaki amman ya
dake, "Hafsah me wannan 'yar iskan takemin a gida? Menace miki batun kawo min ita
gida? Ke bazakiyi hankali ba sena sa polisawa sun baki kashi ne komeh? What part of
na cireki daga cikin jerin yaran dana haifa don't you get? ban sanki ba Zainab
kidena shigo min gida" Ya qare maganan yana watsawa Zeezee dake ta zubda hawaye
mugun kallo. Bakinta na 6ari ta soma dacewa "Baba don Allah badon niba kayi haquri
ka yafemin abubuwan dana maka wallahi bijirewa umarninka danayi shine babban
kuskuren dana afka a rayuwa na, nayi nadama fiye da yadda zaka ta6a tsammani banida
kamar ku da Mama inhar ka cigaba da fushi dani wallahi Allah baze ta6a yafemin ba.
Baba Adeel dana fifita akanku bisa rashin tunani ya sakeni har saki biyu bayan
wulaqanci da azaban daya ta gallamin a gidansa wallahi dana ta6a sanin haqqin iyaye
haka yake da koda wasa bazan ta6a take magananka ko na Mama ba bale har umarninku.
Baba in baka yafe min ba bazan ta6a iya yafewa kaina ba ka dubi girman Allah ka
yafemin Baba don Allah badon niba" ta qare maganan tana kuka sosai.

"Saki biyu kacal ya miki ai da yayi uku sannan yamiki dukan da ze kaiki har
lahira, nadama kuwa har yanzu bakiyi shiba maza tashi kibar min gida 'yar iska
kawai." Shiru Omar yayi gun gabad'aya tausayin Zeezee ya kamasa haka ma Mama daga
bisani ta bud'e baki tace, "haba Alhj! Yarinyan nan abar a tausaya mata ne, batada
kowa daga Allahnta se mu. Ga takaicin rashin haihuwa gana wulak'anci da azaban da
tayita sha gidan miji da kuma kishiya, gana rabuwa da miji dukda ba sonta yake ba
amman still ba dad'i sannan kuma ace uwa uba gana iyaye? Ka tausaya mata mana Alhj
'yarka cefa ka korata yanzu ina kakeson taje, gidan mijin nata daya saketa?"

"Koma ina ne taje amman bazata kwana min a gida na ba ai bani nace tun farko ta
auresa ba kuma bazan tausaya matan ba and idan kika sake kwatanta 'yar iskan nan da
'yar cikina ban yafe ba. Kija bakinki kimin shiru, ai komin nan da kika lisafo ita
ta janyoshi wa kanta wai har zata fifita saurayi akaina ni da rai ne kawai ban d'au
na bata ba wallahi for the last time kifita min daga gida inhar kinga kin kwana a
gidan nan toh bani raye maza ki fice nace ko sena kira polisawa tukun?" Har qasa
Zeezee ta durk'ushe tana kukan cire rai tana bawa Baba hak'uri amman haka yak'i
hak'ura yayi turning blind eye, harda zaro waya shi ze kira polisawa. "Ya isa haka
Zeezee tashi abinki, Alhj ba seka kira wasu polisawa ba gidanka ne zata fice ma
amman kasani ko Allah akayi mai laifi yana yafiya muddin aka tuba."
"Kina nufin kice min ke kin yarda da tuban wannan munafikar? Sau nawa take kalan
tuban nan ta sake komawa gidan jiye? Ta tashi tabar min gida abinda na buqata
kenan."
"Baba wallahi wannan ba kalan tuban dana sabayi da a baya bane, naga rayuwa Baba
wallahi na tuba na haqiqa har abada bazan sake take umarninka ba ko mahaukaci kace
zaka auramin inhar hakan ze farinta maka rai am ready to do it please believe me
Baba banida kowa bayan kai da Mama please." Ta sake fashewa da kuka.
"Tashi ki fita nace" ya fad'a as if though beji dukkanin abinda tace dashi ba.
"Mamana tashi bada haqurin ya isa haka" cewar Mama cike da tausayi. "Ko gidan
Mariam ne kiya je ki kwana amman Alhj kasani ba haka akeyiwa yaro ba kuma tun farko
da baka d'aura Zeezee akan gur6arcacciyar tarbiya ba da duk hakan be faru ba kasani
you are partially to blame for all these."
"Ki fad'i koma me Hafsah and ba gidan Mariam da zata inhar kikaje kika kwana a
gidan wani nawa wallahi kisani Allah ya isa ban yafe ba" jin haka Zeezee ta sake sa
wani kukan har wani sama-sama nishinta ke dan kuka, bata ta6a sanin Baba ze tsaneta
haka ba tabbas tayi kuskure a rayuwarta. "Kifita nace!" Tana kukan ta shiga jan
akwatinta "ki wuce gidan k'awata Mrs Muktar zanyi mata magana." Mama ta sanar da
ita tana mejin zafin abinda Baba yake sekace bashi ne silan komi ba.
"Sede taje chan d'in kam 'yar iska kawai ai kad'an kika gani wallahi, duniya
kad'ai ta isheki."
"Toh Mama nagode, Baba kaikuma bazan gaji da baka haquri ba I pray one day we
will be the US we used to be before" tace sannan tafice cikin motarta ta koma inda
ta sake bud'e sabon dandalin kuka me tayi ma kanta haka? Shikenan ita haka zata
qare rayuwarta da fushin mahaifinta akanta? Tayi a k'alla minti biyar agun sannan
daga bisani ta tada motarta ta nufi gidan Mrs Muktar dake unguwansu inda already
dama tana jiranta Mama ta riga ta sanar da ita komi.

Wuraren k'arfe sha d'ayan dare Mama dake bacci ta farka don gyara kwanciyanta se
ganin Baba tayi zaune bama alaman bacci a idonsa. Alhj? Ta kirasa. Sede sam be amsa
ba kasancewar yayi zurfi cikin kogin tunani. "Alhj!" Tad'anyi tapping nasa. Se anan
ya amsa da "na'am" ad'an firgice not paying attention to her.
"Lafiya?" Ta tambaya.
"Lafiya" ya amsa sama-sama.
"Toh meya hanaka bacci?"
"Babu komai koma baccinki."
"Hm dade kabar 6oyewan ka fad'i gaskiya. Tunanin Zeezee kake koh ba haka ba? Ai
kai kanka kasan baka kyauta mata ba 'yarka cefa ta cikinka. Dubi yadda ta tuba
amman kace bazaka yafe mata ba da gidan ubanta amman se inde na turata gidan
k'awata taje ta kwanta."
"Ni bance miki tunanin ta nake ba saboda haka ki dena kawo min zancenta."
"Its written all over your face Kade yi a hankali kasan me likita yace maka game
da tunani dayawa in jikin ka ya tashi ba ruwana." Ba tare da ya sake cemata uffan
ba yaja bargo ya rufe kansa sede sam ya kasa bacci tunanin ina zaisa kansa a
idanun jama'a yake danko da kunya ace yarinya 'yar 18years aurenta biyu duk sun
mutu wai kuma da iyayenta akanta, da tunanin haka bacci 6arawo ya sacesa.

>*^>*>
Washegari a gidan Adeel.
Kasancewar yau ba school se bacci Adeel da Ruky'n sa suke sha. 11:47am kamar
yadda suka saba tashi yau ma sukayi, bayan sunyi wanka suka fito tare as always
dama se su tanadar da breakfast nasu Zeezee ta had'a musu amman yau kan dining
wayam ba komai. Dukansu sunji wani iri a jikinsu daga bisani Adeel yace, "muje mu
siyo breakfast ko zaki zauna a gida inje na dawo?"
"Kaje ka dawo Babe bana jin zan iya fita." Pecking nasa tayi a cheeks sannan ya
fice.

***
Tun da Baba ya tashi yau ba aikinsa se tunani Mama tayi mai magana kan ya rage
tunanin saboda lafiyarsa amman yaqi jinta. Duka yayyun Zeezee Mama ta kira ta
jaddada musu halin da Zeezee ke ciki. Yasmeen da tausayi sosai ta tausayawa Baby
Sis nata banda Ibraheem da har yanzu haushi abinda Zeezee tayiwa Mama da a baya
yake.
Tun dawowan Zeezee gida take gidan Mrs Mukhtar tana zaman iddarta, da safe
zata tashi tayi assisting nata aiki kasancewar batada me aiki, shara, wanke-wanke
da shirya yara school duk Zeezee keyi har girki ma. Inba aiki take ba toh tana
maqale a d'aki tana kuka. Abubuwa sun kasa dai-daita tsakaninta da Baba yau da
dawowarta gida sati biyu kenan amman sau d'aya data sake komawa dan basa hak'uri
haka yayi mata kaca-kaca har ciwon sa seda ya kusan tashi tun daga wannan rana Mama
ta bawa Zeezee hak'uri ta kuma haneta da sake visiting home. Addu'a de Zeezee bata
fasa ba batada burin da ya fiye mata Baba ya yafe mata.

Ta fannin Adeel da Ruky kuwa daman shi Adeel ba ma'abocin siyan abincin waje
bane Allah-Allah yake Ruky ta kare exams ta soma masu girki. Cikin ikon Allah suka
gama, yau Thursday Ruky na zaune kan kujera a parlour wuraren k'arfe 12 na rana
Adeel ya dawo daga d'an fitan da yayi ransa a murtuk'e gabad'aya ba komi kuma ya
haifo da hakan ba illa duban bank acct nasa da yayi yaga is low, shi kansa mamaki
yasha duk uban kud'in dake ciki ace ya k'are besani ba shi kud'i suna ne. Kuma
bayan kashe-kashen da yayita wa Ruky ba dole ba. "Baby sannu da dawowa" tace dashi
a hankali. Kujera opposite da ita ya zauna tare da jan wata doguwar tsuka, da
mamaki ta tsaya kallonsa "tsakin meh kuma? Did I say something bad? Am hungry ina
lunch d'ina." Wani kallo ya galla mata ransa a mugun 6ace sannan yace, "yana
kitchen ki tashi ki girka mana nima yunwan nakeji."
"Kamar ya na girka lunch? Ba siya mana kake kullum ba?"
"Kud'in gabad'aya ya qare kin huta aiko? Mschw!"
"Kamar ya kud'i ya qare Baby? Kana nufin ba komai a bank acct naka?"
"Eh mana bayan siyayyan danayi ta miki ba, komi ya qare ba abun arzikk bane ya
rage."
"Toh ka tambayi Mami mana."
"In tambayi Mami? Na miki kalan me maula ne? Karki 6atamin rai please" ya fad'a a
fusace.
"Kamar ya kada na 6ata maka rai? Nice de zan ce karka 6atan rai. Meaning what
yanzu bakada kud'i ni zan fara girki kenan akan shara dakuma mopping danake duk
akan wannan cikin?" Tayi pointing cikinta.
"Sosai ma kuwa Zeezee da takeyi ba mutum bace ita? Ko sata kikeso nayi na kawo
me dafa abinci dame aikin?"
"Ba sata ba amman de ka nemi abinyi ko aiki ne kana iya applying."
"Aiki? Nine zanje miki aiki? LOL Ruky you are funny."
"Dariyanka ko ze koma kuka Adeel, bikin friends d'ina twins ya taso kake min
zancen bakada kud'i dame kakeso naje bikin nasu?"
"Lallai fa Ruky!" ya kalleta cike da mamaki "da bakina zaikije, kinji? banida
kud'i and all you can think of and worry about is auren god damn friends naki?
Bakiya tunanin in abincin mu ya qare aina zamu samu sabo?"
"Wannan kuma ai ba damuwana bane tunda kaine magidancin bani ba all am adamant of
is that in ba kud'i there will be trouble don wallahi ban iya rayuwan talauci ba."
"Zako ki koya." Ya fad'a yana bata nasty look.
"Wallahi a'a tun wuri kasan nayi dani ba fa yadda za'ayi ace mace me ciki kaman
ni zatana girki shara da sauran tarukuccen aiki" a ranta tace dama ban d'aura
sharri wa Zeezee ba wallahi da yanzu ita zatana min komi.
"Yanzu tashi and get us something to eat" ya buk'aceta.
"Mekuwa? Kaje ka siyo mana de."
"Banda kud'i nace miki kuma ma bayan nan nagaji da siyan abincin waje. "Purse
nata dake gefenta ta d'aga tare da zaro 5k "gashi kaje ka siyo mana toh tunda
bakada kud'i" Bata ma ishe sa da kallo ba uwarsa ma gabad'aya bayi tambayan ta
kud'i bale matarsa "ni kike bawa kud'i?"
"Kace baka da shi." Ta amsa atake.
"Meaning? Ajinki you can give me donations ne? This should be the first and last
koda wasa kada ki sake cewa zaki bani kud'i banaso."
"Sekaje ka siyo mana ai toh."
"'Ke al'ada hannunki ke da bazaki girka ba? Yau watannin ki nawa a gidan nan kin
ta6a aza tukunyan girki ne? Ba Zeezee kullum keyi ba? A rashinta kekuma meye
amfaninki?"

"Nide wallahi ba abinda zan girka saboda banida lafiya."


"Kikace meh?"
"Ba abinda zan girka" ta sake nanata kanta.
"Har in saki aiki kice bazakiyi ba?"
"Ai akan gaskiyata nake wallahi inhar kanason zaman lafiya tun wuri kaje ka nemo
mana me aiki da zatana taimaka mun."
"Lallai ki sake tunani Ruky, shekaran Zeezee d'aya da watanni a gidan nan ban
ta6a d'aukan mata me aiki ba saboda haka kema ba me aikin da zan d'auko miki esp ma
yanzu da banida kud'i kiji ki sani."
"Lallai kuwa cin abincin Mami ya kamaka."
"Sa'anki d'aya Ruky abinda ke jikinki-"
"Da meh?" Ta tambaya tana zaro mai idanunsa cike da raini "duka na zakayi yadda
kayima Zeezee? LOL wai akace ido wa ka raina yace wanda nafi gani kullum, kaima
kasan ni ba kalan matan da mazaje ke duka bane haka kawai dan ka ibo buhun
talaucinka bazaka zo kana sauqemin aka ba ehe!" Tana kaiwa nan ta miqe da k'yar ta
nufi d'akinsu tare da sa lock, binta Adeel yayi a fusace yana rattling door in
amman taqi bud'ewa. Ba kalan surutun da beyi ba taqi da Zeezee ce da shi kansa
besan kalan dukan da zeyi mata ba.

*~ *~
Abu fa kaman wasa al'amura se kuncewa suke tsakanin Adeel da Ruky Mama har yau
taqi aza tukunyan girki musu haka baida kud'i amman dan dolensa seya siyo musu
abinci kokuwa tace zataje ta cire cikin sanin how desperate he is ya zama Father
yanzu. Gabad'aya ya rasa damuwan Ruky ko dan taga tana d'auke da juna biyu ne oho
bayi ta6a sata aiki tayi. Besan meh ba sekuma ya soma missing Zeezee yanzu. Dukansu
suna matuqar missing Zeezee a 6oye sede ba kaman yadda Adeel keba, he just misses
everything about her. Shifa be ta6a sani bane amman Zeezee tafi Ruky iya komi he
really wants her back.

*****
Cikin ikon Allah Zeezee ta gama zaman iddarta a gidan Mrs Mukhtar har rana me
kamar na yau fushi da ita Baba yake gashi seya yini yana tunanin Zeezee which is
very bad for his condition. Sosai Mrs Mukhtar takejin dad'in zama da Zeezee. Anan
ne watan haihuwan Ruky ya kama tun tashiwarta da safe bayanta keta azabartar da
ita, gashi jiya suka haura sama da Adeel sukayi fad'a kaca-kaca ita seya bata
kud'in ashoben bikin friends nata, shikuwa jiya yayi spending last kobonshi ya siya
musu dinner kud'in daya rage a gunsa shine na hospitality'nta. Tana miqe a qasa
tana aikin juye-juye Adeel ya fito daga bayi gabad'aya haushinta yakeji. Koda ya
ganta beyi ta kanta ba, da ihun nata ya ishesa ne yace, "ke wai meh haka? Akanki
aka soma yin ciki ne?"
"Adeel baya na wayyo zan mutu!" A ransa yace ki mutun mana ko zan d'an sha iska
nima.
"Adeel dan Allah ka kaini asibi-" bata idda maganan ba water'nta yayi breaking se
anan Adeel ya miqe cikin hanzari ya d'ago maternity bag nata sannan ya cinci6eta se
asibiti suka nufa. Achan akayi labour room da ita, tunda tasan kanta bata ta6a jin
azaba kaman na yau ba. Bayanta wane ze 6alle dan ciwo gabad'aya tafita daga
hayyacinta.

Iyayenta Adeel ya kira ganin har tayi 5 good hours bata haihu ba. Azaba kan
azaba shima Adeel gabad'aya ya kid'ime se gani yake kaman Ruky zata mutu tabarsa,
ya zauna a labour room d'inma ya kasa se safa da marwah yake a corridor na d'akin.
Ganin taci har 8 hours bata haihu ba likita ya yanke hukuncin yimata CS da k'yar
Mami ta samu Adeel yayi signing papers d'in. Itace ma zata biya kud'in aikin danko
Adeel bayida gashi da shegen pride ya kar6i kud'in da take basan ma yaqi na aikin
ma don bayida nayi ne. Ana biyan kud'i akayi da Ruky Mama OR kafin nan seda Ruky ta
nemi da akira mata Adeel.
Hannunsa ta riqe da nata tana kuka sosai, "Adeel if today should mark my last
day don Allah kaje kasamu Zeezee on my behalf ka bata hak'uri please ta gafirceni"
Ta qare maganan kalamunta basu fitowa sosai.
"Hak'urin me Ruky what are you talking about?"
"Adeel I lied to you, sharri nayi mata koda wasa Zeezee bata ta6a ta6a lafiyar
jikina ba bale hartace zata kasheni."
"What?!" Yayi exclaiming tare da jan hannunsa daga riqon datayi mai. "What
gibberish are you talking about?"
"Adeel nasan nayi laifi babba banason na mutu da haqqin Zeezee a kaina don Allah
ka bata haquri, ban sani ba ko bazan sake fitowa daga OR d'innan ba please."
Wace irin munafuka ce ke? Kisani koda Zeezee ta yafe miki ni bazan yafe miki ba"
yana kaiwa nan yafice a fusace not minding the calls she's sending him haka tana
kuka sosai aka wuce da ita OR a yayinda Adeel ke haraban asibitin ya zauna gu guda
hannunsa duka biyu manne a fuskansa. Kallo d'aya za a masa a gano yana cikin tashin
hankali. "Why?" ya tambayi kansa "why didn't I listen to you also na yanke hukunci?
Zeezee ashe you meant it time da kikace zan nemeki wataran nayi kuskure na sakan ki
danayi Ruky ya kamata na saka ba keba. I'm so sorry Zainab" tunanin Zeezee yacigaba
dayi instead of na matarsa da rai ke a hannun Allah.

1 hour later Dr'n da yayi wa Ruky Mama aiki ya fito daga d'akin nan Mamanta da
shima Adeel da suke zaune a corridor'n suka dosa gaban Dr'n. Mahaifiyar Ruky ce ta
tambaya "Dr how is she? Was the operation successful?"
"Alhamdulillah lafiyanta k'alau shine babba." Ya amsa.
"Alhamdulillah" ta sake cewa da "ya baby'n nata kuma fa Dr?" Har anan Adeel beyi
magana ba inbanda tunanin Zeezee ba abinda yakeyi. Kai ya kad'a tun daga nan Adeel
ya gano baby ba rai.
"Am sorry mun samu mun ciro baby saidai ba rai tun a ciki ya koma ga mahaliccinsa
Allah baku haquri I'm sorry kuna iya shiga ganinta excuse me please." Sam komawan
baby'n be bawa Adeel mamaki ba saboda yasani bayan abin da Shida Ruky suka tayiwa
Zeezee dole hakan ya faru. "Adeel kayi shiru, bakaji me Dr yace ba?" Cewar Maman
Ruky.

*MIEMIEBEE Team #YGC!*


Beeenovels.blogspot.com

🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
4⃣9⃣

_Assalamu Alaikum Readers/Fans. I know kuna hak'uri but ku k'ara please. Am very
occupied ne these days bana samun time na typing thats why kuka jini shiru two days
and zaku cigaba da jina shirun for some days ahead now till everything gets back to
normal. Thank you for your maxi support, care and love. I heart y'all to pieces.
Team *'YAR GATA CE!🎀* OneLove💞_

"Naji Mama."
"Zaka shiga ka ganta ko na soma ganintan?"
"No kishiga tukuna after you."
"Se hak'uri Allah kawo rayayye." Da nod daya mata ta shige d'akin inda ta tarar
da Ruky banda kuka ba abinda takeyi.
"Haba kekuwa kukan me kuma? Fatanmu Allah sa me ceto ne kukan ya isa haka."
"Mama I didn't get the chance to hold my baby, banida burin dayafi in riqe d'ana
in shayar dashi Mama ya koma baya sona."
"Yana sonki Ruky shiyasa ya koma saboda yana son ya ceceki ranan qiyamah. Na
miji ne ko mace?"
"Na miji Mama" ta sake rushewa dawani kukan da k'yar Mama ta samu ta lalasheta
sannan ta shigo da Adeel ita kuma ta basu waje. Seda ya k'are mata kallon bakwai
saura kwata sannan yace;

"Kin sani ba a haka kad'ai Allah ya rabaki da d'anki bako? Be greatful ma be


had'a da naki ran bama ya tsaya akan abinda kika haifan."
"Adeel wace erin magana kakeyi? Yanzu abinda zaka fad'amin kenan bayan abinda ya
sameni?"
"Da ta'aziyya kikeson na miki? Kisani kin cuceni a rayuwa Ruky kuma I shall never
forgive you for what you did. Haka kawai kika sa na saki Zeezee saki biyu bama
d'aya ba gashi nan kema abinda nake expecting daga garekin shima na rasa."
"Ya kake magana kaman laifi na ne ni kad'ai? Kaima ai ka rasa d'anka kuma da
alhaqinka kaima, da tun farko ka nunamin Zeezee nada mutunci a idonka da duk hakan
be faru ba."
"Aww haka ma zakice?"
"Eh mana kai ka fara bani room ai saboda haka kadena blaming d'ina fault ne dukan
mu munada laifi."
"Yayi kyau in kin gama abinda kikeyi anan seki koma gida ni zan wuce bikon
Zeezee."
"Gidan Babana zan koma sena warke sannan na dawo, gidanka da ba komi aciki me
kakeson inaci har in warke?" Be sake cewa da ita komi ba ya fice nan fa Ruky tasa
sabon kuka.

Gidansu Zeezee direct Adeel ya nufa sarai yasan in ya shiga ciki direct there
will be trouble, bama wannan ba yanzu how sure is he Zeezee na gida? Rashin wannan
amsar yasa ya kira Lubiee don ji daga bakinta. Seda ta gama ja mishi class sannan
a karo na biyu ta d'aga tare da jan tsaki sekuma ta katse. Da ace ba neman abu
Adeel ke a gunta ba yau da sena lahira yafita jin dad'i. Shegen zuciyansa ya ajiye
a gefe ya sake trying nata about 3 missed calls se ana hud'u ta d'aga tare da
fad'in "Malam fa kana taqura min yada kira haka?"
"Lubiee mesa bakida mutunci ne?"
"LOL mutunci? dama kasan da zaman wannan kalma kayiwa Zeezee abinda kayi mata?"
"Lubiee please that aside we can't ammend the past ni just tell me aina zan samu
Zeezee yanzu?"
"A kaina tunda kabani ajiyarta maci amana kawai."
"Wai meke damunki haka?"
"Rashin mutunci" ta amsa a takaice.
"Sena rok'eki zaki sanar dani? I will tunda am in need please ina zan samu
Zeezee?"
"You'll be the last person to come to know where she is daga bakina don wallahi
Adeel ko mutuwa zakayi I won't let you know, she's had enough finally Allah ya
hutar da ita daga monster erinka sannn kace in gaya maka inda take, for what?
Saboda kaje ka sake hargitsa mata rayuwa? You are sick you know."

"Kina da daman zagina the way you want tunda nayi hurting miki best friend but
kisani I really want her back."
"Aww really? I should have guess, kana neman cooku, me shara da wanke-wanke harma
dame wanki da kuma sex machine ai dole kace you want her back to kasani Zeezee tayi
maka nisa wallahi ko a mafarki bazaku sake had'uwa ba nayi regretting had'aku tun
farko."
"Are you telling me where she is or not?"
"I'd rather die" tace dashi tare da katse wayar. Kansa ya riqe gabad'aya out of
idea yanzu aina ze sami Zeezee? Fita yayi daga motan tare da yin sallama dawasu
'yan unguwa koji daga bakinsu ko Zeezee na gida sede duk cemasa suke basu ganta ba
da k'yar tana gida. Tambayan ya tayi don kansa ya gaji ya koma gida inda ya d'au
wayansa don trying number'nta. Yamata about 10 missed calls amman taqi d'agawa
bawai kuma bata kusa bane actually wayan na a gefenta d'agawan ne bazatayi ba cause
she don't think akwai wani abinda ze sake shiga tsakaninta da Adeel. Chan da yamma
Lubiee ta kirawota suka gaisa sede sam Lubiee bata nuna mata Adeel called her ba
saboda bata son dawo mata da memory'nsa bayan she is now moving on.

A daren ranan Adeel ya kasa bacci, ko kiran Ruky yaji ya jikinta ma beyi ba,
jana'izan d'an nasa kawai yaje ya dawo se trying line na Zeezee yake amman bata
picking chan dabara ya fad'o masa. Landline ya d'aga ya kirata dashi and ba tare da
takawo tunanin komi a ranta ba ta d'aga tare da yin sallama. Seda ya sake jin
zazzaqar muryarta yasake sanin yayi missing nata. Ma kasa amsa sallaman yayi seda
ta sakeyi for the second time. "Wa'alaikumus salam Zeezee."
Bazata ta6a mancewa da wannan murya ba, take jikinta yahau rawa "Adeel?" Ta
furta tana shakka.
"Zeezee- " sekuma ta kashe wayar akanshi "hello Zeezee? Zeezee?" Trying nata ya
shiga yi amman ina bata picking, daga k'arshe ma kashe wayar tayi still be haqura
ba ya tura mata saqo kamar haka;

_Zeezee please stop shutting me down we need to talk I really need you back so
badly, Ruky ta haihu yau, na miji but ba rai I know hak'k'in abubuwan dana miki
bisa rashin sani ke bina har ma da ita Ruky'n, I came to know that k'azafi ta miki
regarding that event please pick up my call I love you_

Bata samu daman karance message d'in ba se a washegari da Asubah bayan ta idar
da Sallan Asuba ta gama azkhar nata. Tana gama karancewa ta goge bata son sake ji
ko ganin abinda ze sa ta da Adeel in contact she've learnt her lesson suje chan su
k'arasa da Ruky'nsa ta gwammaci tagama rayuwarta a haka data koma d'akin Adeel.
Ganin fa Adeel ya dameta da kira ta cire sim d'in gabad'ai ta karya se anan ta samu
shan iska.

Acikin sati biyun da Adeel yayi ba Ruky ba Zeezeee ba k'aramin damuwa ya shiga
ba, abinci sede kullum yaje gida yaci. Tun rabuwansa da Ruky a asibiti kuwa kota
kanta be sakeyi ba. Yau Asabar Mamanta tasata ta shirya kayakinta tsaf sannan tayi
dropping nata da kanta. Layin Adeel ta kira kasancewar k'ofar a rufe take, seda
yagama 6ata mata lokaci sannan ya fito ya bud'e mata ko sannu da zuwa beyi mata ba
ya koma ciki a yayinda take binsa a baya. D'aki ta nufa ta ajiye akwatinta sannan
ta fito parlour ta tarar dashi zaune kan kujera se faman tunani yake.
"From all seeing Zeezeen taka bata dawo ba, ashese tanada wayo." Banza da ita
yayi hakan yasa ta cigaba "ai dama ba wawiya bace da zata dawo maka yanzu da bakada
komi konima don yazama min dole ne."
"Kinsan me Ruky? In baki ja bakinki kin min shiru ba zaki kwashi hak'waranki a
k'asa. Saboda kinga ina barinki a baya ne kisani that was because bakida lafiya
amman yanzu da kike garau faffasa miki baki zanyi."
"LOL incredible! Nikuma ce maka ayi zan tsaya ina kallonka kamar yadda Zeezee
keyi? Ai ba qarya nayi ba bakada komi yanzu se uban pride d'in banza." Har maqora
ta kaisa a zuciye ya nufi gabanta tare da yi mata wani irin riqo a hannu wanda tuni
tasa d'ayan hannunta tana k'ok'arin jan kanta. Kasancewar a k'oshe take tuni tasamu
ta fincike hannunta daga riqon dayayi matan "koda wasa wallahi kada ka sake riqemin
hannu haka ka kallen da kyau ba Zeezee bace Ruky Mama ce."
"Ignorant fool" yace da ita sannan ya d'au wayansa ya nufi d'akinsa shi inbanda
Zeezee ba abinda yakeso. Da yamma me aiki ta kawo masa abinci as always kasancewar
Mami batasan Ruky ta dawo ba. Alokacin yana zaune a waje yana shan iska yajiyo
qaran bell da kansa yaje ya bud'e ya anso abincin sannan yayi ciki dashi.

Tsaye a gefen fridge tana shan ruwa ya tarar da ita ko k'ala be cemata ba ya
sauqe abincin sannan ya d'iba duka bebar komi ciki ba "ina nawa nikuma?" ta
tambaya.
"Naki? Bakida hankali ashe."
"Kamar yafa?"
"Ki dafa da kanki ai gaki ga kitchen."
"Lallai ko zaka sha mamaki" bece mata ko k'ala ba ya nufi d'aki. Kitchen d'in ta
shiga tayi garnishing had'ad'd'en spaggetti amman rabin leda yadda ita kad'ai zata
iya cinyewa. Koda Adeel yazo fita daya ganta be mata magana ba acewarsa dukansu ta
girka musu harda kiran Mami ya sanar da ita ba seta sake kawo mishi meal ba Ruky ta
dawo.

Se kusan to 8pm ya dawo gida all exhausted. Dining direct ya nufa ya bud'e flask
se gani yake ba komi ciki an sud'e tas kaman ance d'ago kanka ya d'aga se ganin
Ruky tayi tana picking hak'orinta da alama yanzu tagama cinyewa.
"Ina nawa?"
"Yana kitchen kaman yadda ka fad'i min d'azu nima" ta ansa ba tare da nuna
damuwa ba.
"Ina nawa nace dont play games with me ba d'azu kinyi girki ba."
"Eh nayi ga flask nan ai a gabanka."
"Then ina nawa?"
"Ban girka ba." Ta miyar masa.
"As in how?"
"Eh toh nayi girki amman ma kaina kad'ai kai ba kanada uwar dake sonka tana kawo
maka ba seta cigaba dayin hakan ta huta sheni nima."
"Ruky ki kiyaye ni wallahi karki ganki 'yar buskud'a kiga wai bazan iya baki
kashi ba."
"Ai bazama ka iyan bane is better kabar cika baki."
"Mschww wuce ki dafa min koda indomie ne."
"Bazan girka ba wai a jinka na mance da kalan wulaqancin dakamin ne lokacinda na
haihu? Ai wallahi seka bani haquri mukoma shiri."
"Lallai ko zaki bushe kaman k'anzo inde ni kike jiran na baki hak'uri."
"Shikenan kaima bushewan zakayi idan ni kake jira na dafa ma abinci" bata jira
jin me zece ba tayi d'aki abinta. Ji yake kaman ya bita ya nad'a mata na jaki amman
ina yasan hakan bame yuwu bane yadda take 'yar buskud'an nan yayi wasa seta zauna a
ruwan cikinsa gasa d'an siriri. Haka da kanshi ya dafa indomie'n zuwa 10 haka ya
gama abubuwan da zeyi ya je ya sameta a d'aki tana shirin kwanciya itama.

"Ke bakisan kibawa mutum haqqinsa bane?"


"Nifa bazaka lalatamin jiki ka mai dani sex machine ba, kabarni in huta tukuna."
"Ki huta ba sadakin ki na biya ba?"
"Semeh dan ka biya? A'a wallahi Mallam bazaka tsufar dani ba."
"Banza ma dake inba don a rashin Zeezee ba shan ma zan nemeki ne?"
"Eh ai komin rashin dad'i na nafi babu dai ko? Kuma haka zaka kwana da
sha'awarka, don ni ba abinda zaka samu daga gareni" ji yake kaman ya danne ta yayi
mata na qarfi amman wane shi? Yace ze biyemata har gadon asibiti ana iya kwantar
dashi akai. Allah sarki se kawai ya tuna da Zeezee yadda koda she's not in the mood
haka don ta farinta mai rai zata basa kanta yayi duk abinda yakeso ba tare da tace
mai tagaji ba kokuwa bataso ba, amman wannan fitsararriyan da bata ma kai Zeezee
d'and'ano ba se uban iskanci ai sa'arki d'aya wannan girman naki ya fad'i hakan a
ransa ina ma ace a lokacinda take amarya ne. Amman yanzu tunda ta haihu tasake
bud'uwa ta qara k'iba. Hakanan ranan ya kwana da zalamansa.

Rayuwarsu haka ta cigaba da kasancewa, Ruky yin abinda taga dama take Adeel ko
be isa ya mata magana ba cause shikansa ma tsoronta yake. Girki ma idan tayi na
safe dashi na rana seta k'i haka sede in ya biya gidan friends nasa yaci. Bayan nan
kuma ga habaicin da zata zauna tayita yi tana zaginsa batun rashin aikinsa. Haka ma
se lokacin da taga dama take basa kanta, Adeel can't tell just how much he is
missing Zeezee. Ahaka ne har abun ya ishi Adeel don kuwa shi kansa be saba ba da
zama ba kud'i don haka ya shiga neman aiki inda rabonsa ya ratse yasamu a NGO
albashinsa a wata dubu d'ari biyu da hamsin. (250k)

Yana amsan first salary'nsa ya kashe almost all of it wa kansa akan kayan sawa
saura kuma yayi cafenin abinci dashi, besani ba amman kallonsa kawai Ruky take.
Bayan ya jibge kayakin akan gado ya nufi bayi ya watsa ruwa sannan yafito da full
confidence nasa don za6an d'aya daga cikin kayakin yasa ya tarar da kan gadon
wayan!
"Ke ina kayaki na?" Ya tambayeta in a serious tone.
"Tukun nan ka gyara kanka ba KE anan."
"Kinsan ba sa'anki neni bako? Karkiga don ina d'aga miki k'afa kid'au wai bazan
iya zaneki bane."
"LOL harka ban dariya, I would love to see you try."
"Mschww ina kayakina?"
"Na 6oyesu." Ta fad'a confidently.
"Kin meneh?" Ya tambayeta not believing.
"Ka jini ai na 6oye nace."
"Kayan k'aninki ne da zaki 6oyen? Fito min da abuna."
"Nak'i." Ta buga kafad'a.
"Ruky kifa sani I am not your mate."
"Ai dama ba cewa nayi ba kai sa'a nane. Kayaki nede na 6oye bazan fito dasu ba."
"Dalili?" Ya tambayeta yana cike, ji yake kaman ya goga bakinta jikin bango."
"Aww har ma tambaya na kake? Rabonka dakamin d'inki since when? Kai kanka bazaka
iya tunawa ba, yanzu kuma da arziki ya soma shigowa instead kayi mana siyayyan tare
a'a kai anyi maka wahayin selfishness and greediness you can't ka kama kacika kusan
akwati da sabin kayaki toh wallahi niba wawiya bace da zan yarda, konima ka bani
kud'i inje in sai nawa kokuwa bazaka sake ganin sabin kayakinka ba."
Lallai ma ya furta a ransa cike da mamaki jibi yadda take mai magana kaman wani
d'an cikinta. Fusata yayi besan a lokacinda ya damqota ba da hannu "ni kike gayawa
magana?" Da k'arfin da Allah yabata ta waina hannun nata ai tuni Adeel ya sake
danko idan Ruky batayi biyun Zeezee ba tayi kusan hakan.
"Kalleni da kyau idan banyi biyun Zeezee ba nakusan yin hakan bale kace zakayi
maltreating dina kaman yadda ka saba mata. Koda wasa don't you dare try this
again."
"Mschw! Kinyi asara wallahi bani kayakina."
"Nima kabani kud'i na sai sabo." Ba yadda Adeel beyi da itaba ta basa kayakinsa
taqi if only ze iya dukanta dataci k'aniyanta. Haka don dolensa fa seda ya irga 20k
ya watsa mata aikuwa taqi amsa seda ya qara goma akai nanma taqi wai seya biya ta
kud'in cefanen data musu da a baya.
"Kaman ya kud'in cefane? Anniyan ina ce ke? Cafenin k'aniya! Bani keyin cefani
ba?"
"Da ka samu aiki yanzu ba" tayi maganan tana irga kud'in daya batan incase yad'an
zare saura. "Ka gayamin kafin ka samu aikin wakeyin cafenin gidan?"
"Girkin da ko kinyi sekin ga daman samin d'in kikeson na miyar miki da kud'in ki
yanzu? Lallai ki sake tunani yarinya."
"Ai kaima ka sake tunani wallahi dan seka miyar min da kud'i na." Shareta yayi ya
zaro jeans and shirt nasa sabi yasa duk anan kallonsa take seda ya gama feffeshe
turarukansa sannan tasha gabansa "Malam my money."
"Ki matsa min" yayi stating in a serious tone.
"Nak'i" ta tanka ba tsoro. Tunkud'eta yayi sede kaman gunki tana tsaye wajen "ai
wallahi ba inda zanje ina nan seka biyani kud'in cefanin danayi da a baya."
"Me k'iran yarabawa kawai" yace da ita disgustedly.
"Whatever kud'i nede se ka bayar kokuwa ba inda zaka." One more hiss ya mata
sannan ya irga 5k ya watsa mata se anan ta matsa mai ya fice. Kaman kullum ma yau
ya nufi unguwansu Zeezee yayi parking a dai-dai tsakar unguwan inda yana iya hango
almost all of the activities taking place there. Shikansa besan dalilin sa na zuwa
nan kullum ba all he is adamant of is that komin jimawa zega Zeezeensa wataran
saboda jikinsa na basa anan d'in Zeezee take. Ba yadda beyi da Lubiee ba ta sanar
dashi inda Zeezee take amman tak'i, bataga dalili ba. 5pm na bugawa yaja motarsa
yakoma gida.

5:14pm Zeezee tafito kanti don siyan kati inda take a layin shagon taji wasu
maza a bayanta suna gulmanta ko dagangan suke don taji ko basu san itan bace masani
se Allah.
"Ina Zeezee'n gidan Alhj Isma'eel danake maka magana akai the other day
d'innan?" Cewar d'ayan.
"Eh wacce kacemin yarinya ce sosai amman auranta biyu duk sun mutun nan ko?"
D'an uwan nasa ya amsa sa. Hakan yasa ya cigaba;
"Exactly!" Yayi exclaiming "aitoh bakasan meh ba, jiya Mustapha yake cemin wai ya
ganta a gidan matar Uncle nasa yana sonta."
"Kai haba deh! Yanzu har akwai mutumin da zaiso zaman aure da yarinyar nan?
Lallai!"
"Tayani ji deh, wai ta masa kyau."
"Kyan banza kyan maciji, ace yarinya wai ko ashirin bata kai ba da aure biyu suma
wai du sun mutu, haba mana!"
"Kuma ai bakasan wani abu ba uban nata ne silan komi shiya sagaltata ta 6aci
hakan."
"Toh Allah shi kyauta ya raba 'ya'yanmu da iyayen banza." Kasa rik'e kukan nata
tayi kawai ta juya a guje ta fice se anan d'ayan ya saki baki yana binta da kallo
"kai! ba itace Zeezeen ba?" Nan wanda ya soma kawo maganan yace, "dafa? Ai sanin
tana nan na d'auko zancen don taji tasani kyau ba komai bane inba hali."

**
Tana isa gidan Mrs Mukhtar inda ya zame mata tamkar gidansu ta nufi d'akin da
aka bata, ashe Mrs Mukhtar taga shigewarta ciki ga dukkan alamu kuwa ba lafiya ba
don haka ta bi sahunta. Zeezee najin motsin ta tayi sauri ta shiga share hawayenta
amman sede ina takasa hanasu zuba.
"Subhanallah! Kukan me kike haka Zainab?"
"Babu" ta furta a hankali covering her face.
"Ya isa toh yi hak'uri kinji? Komi meh wucewa ne wataran se labari."
"Aunty na riga na 6ata rayuwa na ashe duk mutanen da muka ga sun d'auke k'afa
daga nema na 'yan unguwa ke basu tarihi na."
"Inji waye Zeezee? Karkice haka."
"Aunty yanzun nan naji da kunne na, shikenan ni haka zan qare rayuwana cikin
k'unci da bak'in ciki sam ban kyauta wa kaina ba wallahi."
"Karkice haka Zeezee always have in mind that Allah na tare dake."
"Nasani Aunty amman abinda nayin ne yayi yawa, if I'll be granted one wish right
now it'll be na koma gidan Ya Al'ameen I miss him so much" sekuma ta rushe da kuka.
Hugging nata Mrs Mukhtar tayi tana bubbuga bayanta "Zeezee is high time ki cire Ya
Al'ameen daga zuciyarki, banason kizo kizama disappointed daga baya its been
morethan a year yanzu bamu sani ba ko bawan Allan ya sake aure. Ke de ki dage da
addu'a in Maj-gen rabonki ne still zaki koma d'akinsa amman kidena bi a rai kinji?
Inko ba haka ba Allah ze kawo miki wani na garin da ze kula dake."
"Naji Aunty, amman ni bazan sake welcoming wani na miji a rayuwa na ba" Zeezee
tayi maganan tana d'agowa daga jikin Mrs Mukhtar "nagode Aunty barin kar6eki
girkin."
"A'a no kibari zan gama da kaina ki huta abinki kinji?"
"Toh nagode" nan Mrs Mukhtar ta fice nan Zeezee ta koma aikinta na kullum wato
tunanin masoyinta na haqiqa Ya Al'ameen . If only tasan ina zata samesa da taje ta
samesan ta fayyace mai abinda ke ranta takuma nemi gafarsa. She don't care koda
fad'a mai tana sonsa ze rage mata self esteem and dignity saboda she loves him so
much ba wanda takeson ta kasance dashi kaman Al'ameen bayan iyayenta. Tunanin Adeel
kuwa koda wasa batayi roqon Allah tayita yi Allah ya yaye mata son da take mai
gabad'aya saboda Adeel bashida wani amfani a rayuwarta yanzu koda shine autan maza
ta yafe shi.

****
Sanin koda ya (Adeel) wuce gida yanzu, Ruky bata dafa abinci dashi ba saboda
zatace tayi lunch bazata yi dinner ba yasa ya wuce gidan Maminsa kawai. Achan tayi
serving nasa dinner suna cikin ci ta lura da yadda Adeel is lost in his thoughts.
Gyaran murya tayi still be motsa ba.
"Auta?" Tayi patting shoulder nasa. Ad'an razane ya d'ago kai daga kan plate
nasa yana kallonta.
"Yes Mami."
"Meke damunka Auta? Tunanin me kake? Meke damunka?"
"Babu" yayi mata k'arya.
"Kamar ya babu? Kai da matarka ne?" Kai zallah ya kad'a mata.
"Toh dawa?"
"Mami I miss Zeezee, I want her back."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
5⃣0⃣

_Yo! Assalamu Alaikum Beautiful ones, I know I've been keeping you guys in such a
suspence and for that MIEMIEBEE is sorry. To those who think they know me, well I
don't think you know know me if you don't know that *Aunty Sis* and *Lubabatu
Maitafseer* are my buddies😻. You guys are just simply amazing, my life is a blast
with you two. Know that I love you so much and that may ALLAH SWT guide us together
and may we continue to prosper. I'm indebted to you two. This page is in you
honors. #TheThree❤#youKnowWhatIMean😂🤳🏻_

"Tooohh" Ta saki baki cike da mamaki. "Auta kasan da haka ka buga mata saki
biyu lokaci guda?"
"Mami wallahi sharrin shaitaan ne, I didn't mean it wallahi ina son Zeezee."
"Ruky fa?"
"Mschww!"Yaja k'aramar tsuka "ina miki maganan mutane kina kawomin na beyerabiyar
can."
"Oh! Da Alama gida ba lafiya kenan, toh kaje kayo bikon Zeezeen mana."
"Bansan ina take ba naje gidansu bata nan da alama Dad nata be yafe mata ba har
yanzu, bansan ina zan sameta ba her line is not going through."
"Tooh kuma... ka tambayi Lubiee mana." Tayi suggesting.
"She will not tell me tana ganin naci amanar best friend nata she'll never tell
me."
"Ko na kirata ne?"
"Zaki 6ata lokacinki ne I know Lubiee batayin abu se in tayi niyyah."
"Toh Auta ka cireta daga ranka kawai ka rungumi k'addara."
"I can't Mami I love her." Ya fad'a a tsawace.
"Kai don Allah free me bafa ni nace ka sake taba, kunje kun samu misunderstanding
da matarka zakazo kana sauqe min fushinka."
"Everywhere is just hell!" ya buga plate nasa kan table d'in "na tafi." Ko seda
safe bata mai ba tana kallonsa har ya fice. Getting to 9 ya isa gida bayan yayi
parking yafito instead ya zarce site nasa da Ruky seya nufi na Zeezee wanda tun
tafiyar ta ko tako varendar be ta6ayi ba se yau, gun yayi k'ura putuk! Key'n k'ofar
dake had'e da car key nasa yasa sannan ya juya ya bud'e tare da sa kai. K'ura ne da
cobwebs ya mamaye ko ina. Yana tafiya guiwa ba k'arfi ya samu ya qarasa har cikin
d'akinta. Wardrobe nata ya bud'e yaga wayam! Ba abinda tabari komi ta kwashe Allah
sarki Zeezee ya furta a ransa.

Side drawers yashiga ja yana dubawa kozega wani abinta amman duk ba komai,
kominta ta tattara. A na qarshen ne yaci karo da wedding albums nasu guda biyu ciki
ba wanda Zeezee ta tafi dasu nufin bata sake buk'atansa a rayuwarta kenan. Wani
heart break ya sake ji. Bakin gadon yad'an kakka6e sa'annan ya zauna ya shiga
viewing lovely photos d'in. Even though a ranan hankalinta baya jikinta tana
tunanin gida, hakan be hana photos nasun yin kyau ba. Kalla ya rigayi har seda ya
jiyo k'walla. Gabad'aya yaji ya tsani kansa yanzu meyasa ya hanke hukunci ba tare
da yin dogon bincike da nazari ba? Addini beyi qarya ba dayace kafin a yanke
hukunci ya zamanto anyi dogon bincike ga irinsa ai yanzu. Missing d'inta bil adadin
ya shiga yi har don haka ya kakka6e gadon ya gyara ya kwanta gun yana rungume da
photo album d'in ahaka har ya samu yayi bacci, Ruky kuwa koda tajisa shiru setayi
zaton ko yana parlour ko sauran d'akunan don haka tana gama kallon series nata tayi
kwanciyarta itama.

*^*^*^
Haka rayuwa on both sides ta cigaba da kasancewa ba dad'i. A kullum Adeel da
tunanin Zeezee yake tashi ya kuma yini, Ruky abinda taga daman yi shi take Adeel be
isa ya mata magana ba har wani shakka-shakkanta ma yake yanzu. On Zeezee's side
kuwa tama bar fita waje yanzu kwata-kwata koda kuwa don siyan kati ne ta gommaci ta
aika almajirai saboda abinda 'yan unguawa keyi mata sede bata fita waje ba shikenan
sun shiga habaici suna zaginta kenan, abinda yafi cimata rai shine harda zagin Baba
ma da suke.

Shi kansa Baba basu barsa ba, basuyi a gaban idonsa amman a bayan idonsa
dandalin hira da zaginsa suke bud'ewa. Yau kamar kullum Baba da Omar sukaje
masallaci an idar da Sallah ana zaune ana tasbih wasu maza daga bayansu Baba wanda
basu gane Baban bane zaune a gabansu suka bud'e dandalin hira suna zagin Zeezee
suna aibanta Baba, kalamu ba dad'in ji duk anan Baba na jinsu se k'ona da rad'ad'i
zuciyarsa keyi masa. Omar na sallame nafilarsa ya hau bayin Allan da masifa da
k'yar aka samu aka sasantasu if not cewa yayi seya musu duka danko yafisu k'arfi ko
kodaga mere look. Dama kullum ana gayawa Baba abubuwan da 'yan unguwa ke cewa
akanshi be ta6a ji da kansa ba se yau, jikinsa ne yayi sanyi a lokaci guda da k'yar
suka samu suka k'arisa gida da Omar as tafiya kad'an yayi se sun tsaya ya huta. Sun
shiga gida Baba ya wuce d'akin Mama ko tanka Mama dake musu sannu da zuwa beyi ba,
miqewa yayi bisa gado yana riqe da zuciyarsa dake masa ciwo sosai.

"Omar lafiya? Meya sami Baban naku? Ko kunyi fad'a ne?"


"A'a Mama kede go and calm him down kar ciwonsa ya tashi."
"Gayamin meya faru Omar?"
Be b'oyewa Mama komi ba ya fad'i mata abinda ya faru. Cike da tashin hankali Mama
ta shiga d'akinsu inda ta tarar da Baba kwance akan gado sede meh? Baya motsi wani
irin rikicaccen ihu ta saki sannan ta biyosa da "inna-lillahi-wa-inna-ilaihi-
raji'un. Alhj!" Da gudu ta nufi kan gadon tana tapping nasa sede at all baya
responding. Omar ta shiga kira seda ya fito a rikice jin yadda take ihu "Omar
Babanku, don Allah kayi wani abu." Shima Omar d'in gabad'aya ya rikice ya nufi
kansu yana kiran Baba sede baya amsawa. Bayan nan ga kuma yadda heart nasa ke
beating a hankali. Seda sukayi dagaske suka samu suka d'aga Baba ba tare da 6ata
lokaci ba sukayi dashi asibiti inda aka wuce dashi emergency ward.

Banda kuka ba abinda Mama keyi a corridor'n d'akin da lokitoci da Baba ke ciki
suna aikin ceto ransa. Omar ne ke k'ok'arin calming nata don shima hankalinsa
gabad'aya a tashe yake fatansu kar Baba ya tafi ya barsu don tun ba yau ba Mama
take lura da yadda Baba kebin abin Zeezee a rai. Ya yafe mata komi ya wuce yaqi, ga
irinta nan ai yanzu. Me za'ayi da gata a rayuwa? Dama-dama ma ace gatan da hankali
ke d'aukawa ake bayarwa yaro ba erin wanda Baba ya riga bawa Zeezee ba.
****
"Zainab! Zainab!" Kirar Mrs Muktar ga Zeezee wanda tuni ta gudu izuwa bayi ta
6uya a zatonta ma tayi bak'o ne shine Mrs Mukhtar ke kirarta dan kuwa ta rantse
bazata sake kula wani na miji ba face Ya Al'ameen nata wanda she is sure shima
yanzu ya riga yayi aure ya mata nisa.
"Zeezee! Ina kike ne?" Mrs Mukhtar tasake kiranta a yayinda tashin hankali ke
building a voice nata.
"Zeezee!" A yanzu kam ta shigota d'akin.
"Na'am" Zeezee ta amsa tare da fitowa daga bayin, tashin hankali ne kwance karara
a fuskar Mrs Mukhtar wanda tun kafin ta fayyace wa Zeezee komi, tayi saurin tambaya
"Aunty lafiya?" Kai zallah Mrs Mukhtar ke kad'a mata "Zeezee Babanki."
"Baba!" Tayi exclaiming "meya samu Baba Aunty? Please tell me."
"Ya sake samun heart failure Zeezee yanzu haka yana asibiti su Mama sun kaisa."
"Innalillahi-" kasa qarisa salatin tayi se kuka wane lalacaccen famfo.
"Zeezee ba kuka bane abinyi, ki sanya hijabin ki mu fice, yi hak'uri in shaa
Allahu ze samu sauk'i."
Hakanan through out the drive Zeezee ke ta kuka. Suna isa asibitin suka nufi inda
su Mama dasu Mariam suke already se kuka suke. Da gudu Zeezee ta nufi inda Mama ke,
sede kafin ta k'arisa Mariam tayi mata katanga stopping her.

"Kin halaka Baba, Maman ma bazaki barta ba?" Tayi maganan idanunta na tsiyayar
da hawaye sosai. Cikin kuka da tsan-tsan tashin hankali Zeezee ta soma da cewa;
"Adda Mariam don Allah kiyi hak'uri and let me hug her I beg you please."
"No way ki koma daga inda kika fito, tunda aka haifeki you've been nothing but
badluck to us Zainab, wallahi idan abu ya samu Baba kisani I won't ever forgive
you."
"Adda Mariam ya isa please yanzu ba lokacin yin tashin hankali bane" cewar Omar
a yayinda Zeezee tasake rushewa da kuka tana kiran sunan Mama amman itama Maman yau
ta kanta take bata iya tacewa Zeezee komi ba. Mariam ta bari Zeezee ta zauna kusa
dasu ma tak'i. Tana kuka Mrs Mukhtar tajata zuwa wani benchi dake chan gefe ta
zaunar da ita tana lalashinta amman se kaman sake tunzirata Mrs Mukhtar ke.

Not long enough Dr ya fito inda ya kira Mama zallah ya buk'aceta data bisa office
nasa. Tana kuka tabi bayansa inda ya bud'e k'ofar ta samu tashiga tare da jan
kujera ta zauna tana shessheqa.
Tissue ya miqa mata tare da sanar da ita "please calm down mijinki na cikin
critical condition bazan 6oye miki ba."
"Subhanallah!" Ta furta tana kuka sosai "Dr is he going to make it?"
"Agaskiya bazan 6oye miki ba, chances na rayuwansa is not upto 30% kunsan
condition nasa be kamata ba kuna barinsa yana tunani haka. His heart is all damaged
yaci ace zuciyar ma ta buga yabar aiki amman Allah be k'addara hakan ba. Ku sashi a
addu'a bamu san me Allah ke ciki ba."
"Dr dan Allah ba abinda zaku iya masa? He can't die don Allah ka taimakeni da
'ya'yana." Ta k'are maganan cikin kuka sosai.
"I'm sorry Ma'am but we've done all we can sauran mun bar wa Allah kuyi hak'uri.
Kuna iya shiga ganinsa amman please Karki kuyi abinda ze tayar mai da hankali Allah
basa lafiya."
"Amin Dr" ta amsa tana share hawayenta.

***
Mama ya jikin Baban? Mariam tayi saurin tambaya. Kai zallah Mama ke kad'a musu,
nan fa hankalin yaran ya sake tashi binta kawai sukeyi a yayinda take heading to
d'akin Baba. Ganin haka Zeezee itama ta miqe zata bisu sede kafin takai da bakin
k'ofan Omar yasa hannu yana kareta ayayinda Mama ta juyo in crying tone tayi
stating "taya zakice zaki shiga Zeezee bayan kinsan kece silar rashin lafiyan nasa?
Kiyi hak'uri ki tsaya anan kibari nida yayyunki mu shiga."
"Mama yanzu bazan iya ganin Baba ba? Don Allah kuyi hak'uri kubarni inga
mahaifina na rok'eku please."
"Ya kike magana kaman baki gane abinda Mama ke nufi ba?" Cewar Mariam
spitefully. "So kike mu barki ki shiga ki gama halaka mana shi?"
"Ya isa Mariam" Mama ta katse ta "mu shiga." Ba tare da ta sake cewa uffan ba
suka shiga tare da shutting door a face na Zeezee. Nan fa baiwar Allah abin tausayi
ta kuma sauk'a har k'asa tana kuka a yayinda Mrs Mukhtar keta bata hak'uri.

Kallo d'aya iyalan Baba suka iya suka mishi idanunsu ya cike dam da hawaye.
Banda kuka ba abinda suke iya yi. Kallo d'aya za'ayi wa Baba asan da k'yar ya kwana
yau Alhamis ya kwana da rai. Hakan ba k'aramin sake tayarwa family'nsa hankali yayi
ba. Da gudu Mariam da Omar sukayi kansa, shi Omar na miji amman se kaman yama fi
Mariam yin kuka musamman idan ya tuna fa just a while ago suke zaune a masallaci
lafiya k'alau. Har Mama ta kasa barin kuka.

"Ya'yan albarka ina kuke?" cewar Baba in a low and cracky voice.
"Gamu nan Baba" cewar Mariam "sannu Allah ya baka lafiya."
"Ameen" Mama da Omar suka amsa in unison. Hannunsa dake ajiye a gefe yake son
d'agawa amman ya kasa, da Mariam ta gano haka seta d'aga ta had'a da nasan, shima
Omar ya miqo hannunsa duk suka had'a gu d'aya.
"Masha Allah suwa dawa ne anan?" Ya tambaya gashi de a zahirce idanunsa a bud'e
ne sede ko bayi gani dasu ne masani se Allah.
"Mariam da Omar ne anan Baba" cewar Omar yana share hawayensa da d'ayan
hannunsa.
"Sannu 'ya'yan albarka Allah yi muku albarka."
"Ameen Baba" Mariam ta amsa "sannu." Se kuka suke sosai saboda raya musu da
zuk'atansu ke na cewa Baba baze kwana ba yau.
"Mariam" Baba ya kirata cikin dashasshiyar murya.
"Na'am Baba gani."
"Mariam 'yata ki yafemin rashin adalcin da nayi a tsakaninku tun kuna 'yan yara,
ki gafirceni don Allah."
"Baba wace erin magana kake haka? You've never once offended me don Allah kabar
seeking forgiveness d'ina, what we are after at is your health."
"Nasani Mariam amman inji da kunne na kin yafemin." Hannunsa ta sake matsewa gam
cikin nata tana me sake kuka "Baba inhar abinda kakeson kaji kenan shikenan, ni
Mariam 'yarka na yafe maka komi da 6oyayye da kuma bayyananne duniya wa lahira,
Allah ya baka lafiya."
"Ameen masha Allah Mariam nagode, Omar Baba na kaima ka yafemin rashin ad-" be
idar da maganan ba Omar ya katse sa in a crying tone yace, "na yafe maka Baba, na
yafe maka komi Allah baka lafiya."
"Nagode 'ya'yan albarka, Allah ya albarkaci rayuwanku ya baku zuri'ah d'ayyiba,
sannan kuma ya haneku dayin rashin adalci a tsakanin 'ya'yayenku kunga abinda hakan
ya haifar min. Kumin alqawari ko akan layi kuka ga iyaye suna rashin adalci a
tsakanin 'ya'yayensu zaku tsaya ku musu wa'azi."
"In shaa Allah Baba Allah baka lafiya." Mariam kije ki ibo su Hafsah daga
islamiyya." Mama ta fad'a da k'yar.
"Mama bazan iya barin Baba haka ba."
"Karki damu nida Omar zamu kula dashi, tashi kije Mamana." Ba tare da tayi
gardama ba ta share hawayenta, "toh Baba zanje in ibo su Ramlah daga islamiyya."
"Toh sannu Mariam d'ina."
"Yauwa Baba, zuwa anjima zan dawo Mama."
"A'a Mariam ki zauna da yaranki if not waze kula dasu mijinki bayi gari."
"Mama koda me aiki ne zan barsu."
"A'a ban goyi bayan hakan ba gani ga Omar duk abinda Babanku ke buk'ata ni da
Omar zamuyi masa."
"Are you sure Mama?"
"Yes Mariam karki damu."
"Toh shikenan amman if something goes wrong please don't hesitate to call me."
"In shaa Allah ki shafa min kan takwara na."
"Toh Mama" nan ta juyo tana kallon Baba da hannunsa ke rik'e dana Omar har yanzu.
"Baba gobe in shaa Allah zan dawo get well soon Allah baka lafiya." Kai zallah ya
gyad'a mata, anan ne ta samu ta fita.
Zaune ta tarar da Zeezee kan bench tanata aikin kuka har yanzu, ko niyyan magana
Mariam batayi mata ba hakan yasa Zeezee ta miqe tana kuka sosai takira sunan
Mariam.
"Adda Mariam?" Banza da ita tayi tana me cigaba da tafiya.
"Adda Mariam don Allah kiyi hak'uri ki sanar dani halin da Baba yake ciki ba don
hali na."
Kaman bazata amsata ba tace, "da sauk'i" sannan ta fice ba tare data sake
sauraronta ba. Kasa daina kukan Zeezee tayi har seda Omar ya fito daga d'akin shima
kasancewar aiken sa gida da Mama tayi domin ya ibo mata abubuwan dazata buk'ata don
kwanan asibiti.

"Ya Omar" ta kirasa tana k'ok'arin miqewa daga kan benchin.


"Na'am Zeezee." Ya amsata ba yabo ba fallasa.
"Ya Omar ya jikin Baba?"
"Da sauk'i."
"Ya Omar ka fad'amin gaskiya please, I tried to talk to Adda Mariam but she is so
mad at me."
"Da sauk'i Zeezee addu'ar mu kawai yake buk'ata."
"In shaa Allah Ya Omar, how I wish I can see him also and hold his hand." Tayi
maganan k'walla na cikowa a idonta. "I miss my Dad Ya Omar, I miss him so much. I
can't ever forgive myself for letting him suffer like this, nice sanadin rashin
lafiyarsa." Ta rushe da kuka sosai. Shi kansa Omar tausayi ta basa dukda kuwa
haushinta yakeji saboda ita ta fara haifarwa Baba da wannan rashin lafiyar. Dan
irin kukan da Zeezee take me tsuma zuciya yasa Omar yajata jikinsa tare da hugging
nata yana bubbuga bayanta. Hugging nasa back tayi tana me cigaba da kukan.

"Ya isa, he is going to be alright in shaa Allah." Kai ta gyad'a seda tad'an yi
shiru ya saketa nan ta shiga share hawayenta. "Ki zauna ina zuwa."
"Gida zaka?"
"Eh."
"Zan bika."
"Are you sure?"
"Yes please."
"Okay toh muje." Anan suka fice, Zeezee ce ta had'awa Mama dukkannin abinda zata
buk'ata.

*****
"Hafsah?"
"Na'am Alhj" ta furta tana k'ok'arin shanye kukan dake neman kub'uce mata.
"Kina ina?"
"Gani nan Alhj" nan ta sake matsowa kusa dashi tare da had'a musu hannayensu.
"Hafsah ta ki yafeni kinji?"
"Alhj kuma wani irin magana kake?"
"Nide ki yafeni don Allah nasan sau dayawa nakan miki abubuwan da bakiso kiyi
hak'uri ki yafemin please."
"Alhj please ka dena, kabar magana haka. Ya kake ta neman yafiya sekace mutuwa
akace maka zakayi? Please ka bari ya isa haka."
"Hafsah ta inaji a jikina today will mark my last day, zuciyana namin ciwo
sosai." Hawaye ne suka soma tsiyayowa daga kumburarrun idanunta. Jin shiru yace,
"baza ki iya yafemin ba Hafsah ta? Yi hak'uri ki yafemin kinji?"
"Alhj me kayi min da zaka nemi gafara na? Ni nace kayi offending d'ina ne?
Please kabar maganan haka lafiyarka ce a gaban mu yanzu."
"Baki fad'a ba amman nasan da hakan."
"Alhj inhar jin yafiya na kakeson ji toh ni na yafe maka duniya wa lahira."
"Nagode Hafsah."
"Nima nagode Alhj Allah baka lafiya, Hjy (Maman shi) ta kira d'azu k'afafunta ke
ciwo taso fitowa yau amman tace zata bari zuwa gobe."
"Toh ba matsala, Allah kaimu."
**^^**
Har dare around 9pm Zeezee tak'i barin asibitin, ba yadda Omar beyi da ita ba ta
ya kaita gidan Mrs Mukhtar amman tak'i ita tanason taga Babanta.
9:30pm Mama ta fito waje don yima Zeezee magana. Alokacin Zeezee na miqe akan
benchi tayi lamo "Zeezee" Mama ta kirata.
"Na'am" ta amsa tare da miqewa a kid'ime.
"Me kike har yanzu baki koma gida ba?"
"Mama ya jikin Baba?"
"Da sauk'i yana bacci ma."
"Allah ya bashi lafiya."
"Ameen tashi Omar yayi dropping naki Mrs Mukhtar nata kira."
"Mama zan kwana anan."
"Anan a ina Zeezee?"
"Ko akan benchin I want to be anywhere close to Baba."
"Zeezee kiyi hak'uri ki koma gida."
"Mama don Allah kimin hanya, ina son inga Baba in gani da ido na wani halin yake
ciki please Mama don't refuse my offer, I cannot forgive myself for what I've done
to him."
"Zeezee dama Allah ya riga ya k'addara wannan rashin lafiya wa Babanku sede kice
ta sanadin ki hakan ya faru Wanda dama komi seta sanadin wani yake faruwa, so kibar
blaming kanki ki taya shi da addu'a Allah shi basa lafiya."
"Ameen Mama yanzu don Allah ba yadda za'ayi na gansa kafin na tafi?"
"Zeezee kin fini sanin abinda hakan ze haifar."
"Mama kince fa yana bacci."
"Even still Zee-"
"Mama please I beg you don Allah, this is all I ask." Zeezee tayi pleading abin
tausayi. Mama zata sake magana Zeezee ta sake had'ata da Allah, she can't say no
now. Muje.

"Nagode Mama, thank you so much" a nitse tabi bayan Mama suka shiga d'akin inda
ita Zeezee ta tsaya daga bakin k'ofar a yayinda Mama ta k'arisa ciki ta sake duba
fuskan Baba don ta tabbatar da baccin yake. Hannu tayi wa Zeezee nan ta k'ariso
ciki.
Kallo d'aya Zeezee tayi wa Baba ta rushe da kukan zuci se hawaye kawai take
tsiyayarwa. Binsa kawai take da kallo tana me sake tsanar kanta na sanya mahaifinta
cikin wannan hali, duk anan kallonta kawai Mama take. Hannu Zeezee ta d'aga a
hankali ta d'aura akan na Baba a hankali. Har Mama ta bud'e baki zatayi magana,
ganin Baba be farka ba ta barta.
"Baba I'm so sorry, Allah ya baka lafiya, your daughter loves you so much if
only I can take away your pain." Tayi kusan minti biyu akansa sannan da k'yar Mama
ta samu ta turata waje "kije gida Zeezee, Omar na jiranki a mota in shaa Allah gobe
seki dawo."
"Toh Mama take care of Baba please Allah bashi lafiya."
"Ameen seda safe."
"Allah tashemu." Tana kaiwa nan ta juya ta fice. Ciki Mama ta koma ta idar da
shafa'i da wutr nata, ta shiga canza kayan sawanta tana cikin haka ne taji Baba
yaja doguwar nishi. Rabin kayan na jikinta rabi ta cire ta k'arisa kansa "Alhj?" Ta
kirasa cike da tashin hankali. "Alhj?" Tayi tapping nasa "na'am Hafsah." Ya amsa at
long last.
"Alhamdulillah! Ka tashi kenan?"
"Eh" ya amsa sama-sama.
"Ya jikin toh?"
"Alhamdulillah."
"Barin canza kaya na ina zuwa." Da nod daya mata ta koma ta canza kayan nata zuwa
na bacci sannan ta dawo ta zauna a gefensa.
"Hafsah ina Ibraheem da... da... da Yasmeen?"
"Ibraheem na Abj Yasmeen kuma Kd amman gobe in shaa Allah zasu d'auko hanya don
dubanka."
"Ina son ganinsu yanzu kiyi musu magana kice suzo."
"Alhj ba gari d'aya fa muke dasu ba, Mariam, Omar da Zeezee ne muke gari d'aya
dasu."
"Ibraheem da Yasmeen fah?"
"Suna chan Abj da Kaduna Alhj karka damu gobe zasu shigo."
"Inason yi musu magana Hafsah."
"Toh in kira maka su a waya?"
"Zamu samu muyi magana?"
"Sosai ma."
"Toh kiramin Ibraheem shine babba aiko?"

*MIEMIEBEE. Team #YGC!*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
👄Page 51
*FEBRUARY, 2017*

Blog readers how are you guys coping with this version? Lemmi know your opinions
please, ILY'all❤

"Eh Alhj" nan da nan Mama tayi placing Ibraheem on the line. A lokacin wayan
nasa na a hannun Hafsah 'yarsa wacce suke kira da Maamah tana game. 'Yar tasa sak
shi ba abinda ya rabasu, haskensa ne kawai bata gama ibowa ba ta d'an had'a da
duhun mahaifiyarta. Ganin hoton Mama yayi displaying akan screen d'in tayi saurin
kai wa Ibraheem da Fateemah da suke zaune a d'akinsu wayar.

"Daddy! Daddy! Maman Daddy is calling you."


"Dagaske? Kawo in gani toh Maamah na."
"O'o Daddy ina game."
"Yi hak'uri muna gamawa zan baki."
"Ni o'o."
"Yi hak'uri Maamah ki basa kinji?" Cewar Fateemah dake lullub'e cikin bargo da
alama laulayi ke damunta.
"Zan baki nawa."
"Ni banashon naki."
"Yi hak'uri kiban ze yanke, ga chan ice cream naki a fridge jeki d'auko."
"Yeyy!" Kai mai wayan tayi da gudu sannan ta nufa fridge ta d'au ice cream d'in
ta shiga sawa a armpit (hammatarta) hakan ba k'aramin dad'i yake mata jin sanyi-
sanyin. Fateemah na kallonta aman batajin zata iya mata magana saboda tasan 6ata
lokacinta kawai zatayi dan kuwa ba jin magana Maamah ke ba, halinta sak na Zeezee
dukda taka mata birkin da Ibraheem ke, gado ba gwaninta ba.

Kasancewar wayar ta yanke yayi calling Mama back.


"Assalamu Alaikum Mama."
"Wa'alaikumus salam Babana ina wuni?"
"Lafiya Mama ya gajiya? Kin kira wayan na hannun Maamah tak'i bani."
"Takwaran nawa ko? Ya jikin Fateemah kuma?"
"Alhamdulillah da sauk'i" ya amsa yana kallon Fateemar, daga nesan tamai
whispering "kace mata ina gaisheta and ta gaida Baba da jiki." Nodding yayi sannan
yace, "tana gaishe ki da Baba da jiki, ya jikin nasa?"
"Toh alhamdulillah de shi yace in kiraka ma yanzu yana son kuyi magana."
"Allah sarki ki bashi toh."
"Yauwa" a speaker phone ta danna sannan ta matso wa Baba da wayar kusa dashi "ga
Ibraheem d'innan Alhj."
"Aina?" Ya tmbaya nan Ibraheem ya amsa "gani nan Baba sannu ko? Allah baka
lafiya."
"Ameen Ibraheem Babana, Allah yayi maka albarka."
"Ameen Baba gobe in shaa Allah zan shigo in duba ka."
"Toh Allah ya kaimu Baba na nace ka yafemin rashin adalcin danayi a tsakaninku
tunda kuke yara, Baba yayi kuskure ka yafe mishi kaji?" Jin haka Ibraheem ya d'au
k'afa ya fice daga d'akin nan Maamah ta shiga binsa tana kiransa da wuri Fateemah
ta tareta tare da dawo da ita cikin d'akin. Dining chair yaja ya zauna gabad'aya
jikinsa yayi sanyi, "Baba wani irin magana kuma kake haka?"
"Yi hak'uri ka yafemin Babana."
"Baba nifa ba abinda kamin, ni yakamata in nemi tuba a gareka ba kai ka nema a
guna ba."
"Bazaka iya yafemin ba Baba na?"
"Baba inhar yafiya na kakeson ji toh ni na yafe maka duniya da lahira, Allah baka
lafiya kaji? Gobe da sassafe zan shigo in shaa Allah."
"Nagode d'a na Allah maka albarka ya baka ikon yin adalci a tsakanin 'ya'yayenka
nan gaba."
"Ameen Baba nagode, sannu kaji?"
"Yauwa ina Yasmeen kuna kusa?"
"A'a tana Kaduna bari incewa Mama ta had'aku."
"Toh Babana nagode."
"Sannu Baba, Allah baka lafiya" nan Mama ta d'aga wayar tare da cireta daga
speaker phone. "Hello Ibraheem?" Cikin wani irin murya cike da tashin hankali
dakuma tsoro da fargaba Ibraheem yace, "Mama what is wrong with him? Jikin nasa
yayi tsanani haka ne?"
"Ibraheem se addu'a."
"Innalillahi! Mesa baki sanar dani ba tun d'azu ko a yau d'in in shigo? Mama mesa
Baba yake magana haka?"
"Ibraheem I don't know also" ta amsa hawaye na ciko mata a ido chan bakin k'ofa
ta nufa tace, "Dr yace min chances na rayuwansa be kai 30% ba I don't know what to
do Ibraheem." Shima Ibraheem besan a lokacinda idanunsa suka cike da hawaye ba "why
didn't you tell me he is in a critical condition like this?"
"Banason hankalinka ya tashi kai kad'ai na sanar wa hakan k'annenka duk basu sani
ba."
"Allah bashi lafiya Mama please take care of him."
"I'll Ibraheem sekun shigo goben ka gaishe da Fateemah" anan ta katse wayar tana
me share hawayenta. "Hafsah? Hafsah ina kike?"
"Gani nan Alhj" tayi maganan tana dosan gabansa. "Hafsah Yasmeen fah? Ki had'ani
da ita itama."
"Toh Alhj" ba musu ta shiga trying line na Yasmeen sede sam bata samunta saboda
d'anta bayi bar mata wayarta kullum cikin siyan sabuwar waya take dan kuwa sede
Suleiman be gani ba seya jefata cikin ruwa. Atlast dana mijinta ta kirata anan ne
ta same ta haka itama Baba yayi ta neman gafararta a yayinda take ta zuba kuka
cikin wayan da k'yar ta iya fad'i mai ta yafe mishi itama. Tana ajiye wayan ta
fad'a jikin mijinta tana kuka sosai, hak'uri yayi ta bata yana assuring nata in
shaa Allahu Baba ze samu sauk'i and first thing tomorrow morning zasu wuce Bauchi.
"All is going to be alright kinji Queen? Bar kukan haka ko kina son kisa Abba
shima?" Kai zallah ta kad'a masa.
"King Baba bashida lafiya I don't want him to die."
"Subhanallah! Kiyi istigfaar wayace miki Baba ze mutu? Ze samu waraka in shaa
Allah just have faith kinji?" Nan ma kai ta gyad'a mai. Pecking forehead nata yayi
"tashi mu kwanta zuwa anjima mu tashi muyi Sallah mu rok'i Allah wa Baba koh?"
"Thank you My King, I love you."
"I love you more Queen tashi mu kwanta toh."

****
Ibraheem kuwa tun gama wayansu da Mama ya kasa komawa d'akin se hawaye yake
zubdawa tsili-tsili. Ahaka har Fateemah ta kwantar da Maamah sannan ta fito ta
tsince shi zaune kan kujerar. A nitse ta k'arasa gunsa tare da kwantar da kanshi a
dai-dai cikinta tana shafa gashin kansa to and fro. "Everything is going to be
alright in shaa Allah Baba ze samu sauk'i Daddy'n Maamah lets just pray for him
kaji?" Da k'yar ya iya mata nodding kai "he is in a very critical condition Momy'n
Maamah ina ji ajikina bazan sake sa Baba a ido ba."
"Shhh! Daddy'n Maamah please kadena fad'in haka, Baba ze warke in shaa Allah have
faith okay?" Kai ya gyad'a da k'yar "tashi muje mu kwanta gobe da safe se mu wuce
in shaa Allah."
"Bakida lafiya, you aiint going."
"Baba is like my own father, dole zan bika I love him as much as you do."
"Thank you Fateemah I love you."
"I love you also Daddy'n Maamah tashi muje mu kwanta na ciro maka kayan
baccinka." A hankali ya miqe tare da kwantar da ita a jikinsa a haka suka isa
d'akinsu suka gama shiri suka kwanta sede sam Ibraheem ya kasa bacci haka Fateemah
ma ta zauna awake with him har lokacin da bacci yazo ya saceta. Gyara mata kwanciya
da Maamah yayi sannan ya miqe yayo alwala ya shiga yin nafilfili yana taya
mahaifinsa da addu'a.

*****
Mama na gama shirin kwanciyar ta ta shimfid'a darduma a k'asa ta hau shirin
kwanciya ganin haka Baba ya kirata, "na'am Alhj kana buk'atan wani abu neh?"
"Ruwa nakeso Hafsah." Tashi tayi ta d'au masa Faro sannan ta rigingina kansa
jikin gadon ta sa mai a baki tas ya kur6e ya sake neman k'ari. A karo na biyun ma
shanyewa yayi yana me sake neman k'ari. Hakan ba k'aramin tsoro ya sanya Mama ba
saboda sau dayawa tana jin ana cewa wasu idan suka zo mutuwa ruwa suke sha kaman ba
gobe. Batasan a lokacinda kuka ya ku6uce mata ba.

"Hafsah ta kuma kukan me kike?"


"Babu Alhj" ta fad'a da k'yar duk yadda taso hana kanta kuka ta kasa. Kanta ta
d'aura a k'irjinsa "Alhj kasani ina sonka sosai, no matter what kaine mijina na nan
duniya dakuma lahira, bazan ta6a mancewa da kai ba."
"Masha Allah Hafsah ta nagode sosai kuma kisani nima ina sonki sosai daga ke har
yaranmu ina sonku duka." Kukan ta cigaba dayi tama kasa amsa sa "toh kibar kukan
haka mana, ko so kike nima inyi?"
"A'a Alhj Allah baka lafiya."
"Ameen Hafsah ina... ina Zeezee?"
"Zeezee?!" Tayi exclaiming tare da d'ago kanta da jikinsa cike da mamaki.
"Eh ita ina take?"
"Tana gidan Mrs Mukhtar k'awata."
"Gobe in Allah ya kaimu kice mata ta koma gida ta cigaba da zaman ta achan
kinji?"
"Alhj kana nufin ka yafe mata kenan?"
"In shaa Allahu Hafsah, na yafewa Zeezee dukkanin abinda tamin nima inaso zuwa
gobe idan suka zo duka dasu Ibraheem in nemi gafararta saboda itama ba laifinta
bane Hafsah ni na 6ata mata tarbiyya. Su Mariam da ban 6ata nasu ba ai basu ta6a
yomin abin kunya ba, itama Zeezee da ban 6ata nata tarbiyyan ba da dukkanin abinda
suka faru basu faru ba. Da itama yanzu tana d'akin mijinta, meya fiye mata wannan?
Ki ce mata tayi hak'uri ta yafemin don ni na yafe mata komi da bayyananne da
6oyayye duniya wa lahira kice mata I missed being with her, tell her she'll forever
be my sister, I love her so much." Wani sabon kukan Mama ta sake rushewa dashi "in
shaa Allah Alhj, gobe da kanka zaka fad'a mata hakan Allah ya kaimu kawai. Nasan ba
wanda ze kai Zeezee jin dad'i a duniya gobe, saboda batada abinda ya fiye mata
yafiyanka a gareta."

"Naji dad'i na faranta mata, Allah yayi ma rayuwarta albarka ya bata 'ya'ya
nagarin da zasu zo su kula da ita nan gaba ya bata miji na gari da kuma ze riqe ta
amana ya rabata da sharrin dukkanin me sharri."
"Ameen ameen Alhj nayi farin ciki matuk'a tun ba yau ba nake jiran rana kamar ta
yau, ranar da hak'k'in iyaye ze tashi daga kan Zeezee." Murmushi kawai ya iya ya
mata "Allah baka lafiya kaji Alhj? Kasani Zeezee na sonka sosai kuma tayi nadaman
what she've made you gone through."
"Ameen Hafsah nima ki gaya mata inasonta sosai."
"In shaa Allah Alhj"
"Masha Allah, baki k'aramin ruwan ba Hafsah."
"Alhj gora uku be maka yawa ba?"
"Beyi ba Hafsah k'ishi nake ji." Tana hawaye ta k'aro wani ta basa, rabi ya
kwankwad'a sannan da kansa yace mata ya k'oshi. Gyara mai bargo tayi sannan ta miqe
zata koma kan dardumanta da wuri yace, "Hafsah mu kwana tare anan." Cikin sautin
kuka tace, "Alhj ai gadon nan baze d'auke mu ba kuma kaga bakada lafiya."
"Karki damu ki taho mu kwanta tare kinji? Inason mu kwanta tare yau." Bata sake
mai musu ba taje ta kwanta a gefensa a tak'ure.
"Nagode Hafsah ta Allah miki albarka ya biyaki dukkanin abubuwan da kikayimin da
gidan Al~Jannah."
"Ameen Ameen Alhj."
"Yauwa karki manta saqo na wa Zeezee fah? Kice mata Babanta ya yafe mata inason
ta kuma ta koma gida da zama."
"In shaa Allah Alhj ka kwanta kaji?"
"Toh Hafsah Allah bamu alkhairi."
"Ameen" ta amsa. Da mintoci kad'an Baba ya samu yayi bacci banda Mama da bacci ya
k'aurace mata kwata-kwata. Imagining life without mijinta kawai take...

MARIAM**** @11:40pm
Wayarta dake ajiye a gefen tane ya shiga ruri wanda tana dubawa taga 'Dear' na
flashing akan screen d'in, ba tare da 6ata lokaci ba ta d'aga "hello Sweetheart."
"Na'am Dear" ta amsa tana sobbing.
"Baki bar kukan ba har yanzu? Kiyi hak'uri kinji? We are in this together, in
shaa Allah Baba ze samu sauk'i muna ta kan mai addu'a gobe in shaa Allah nima zan
dawo."
"Allah yasa, meetings naka fa?"
"Nayi cancelling nasu already lafiyan Baba ya fiye mana komi."
"Thank you Abban Ramlah I love you."
"I love you more my princesses mother, ki samu ki huta kinji? Sena shigo goben."
"Toh Allah ya kaimu."
"Ameen, su Ramlah sun kwanta?"
"Eh tun d'azu."
"Kema ki kwanta kinji? I don't want you worried Baba will get well soon in shaa
Allah."
"Thank you ka huta gajiya."
"Kema Sweetheart seda safe" anan ya jira ta katse.

ZEEZEE**** @01:48am
Juyi take tayi akan gadonta a yayinda taketa kuka kaman ba gobe. Tunanin
mahaifinta kawai take, don kuka har sara kanta keyi mata tana gani dishe-dishe.
ganin ba mahalicci se Allah kawai yasa ta miqe da k'yar ta d'auro alwala sannan ta
shafa robe akanta don rage mata ciwon kan da takeji ta shiga yin nafilfili.

*^*^*
Sallah Ibraheem yayi tayi har pass 01 pm inda Fateemah ta farka tare da shafa gun
kwanciyarsa taji wayan, hakan yasa ta miqe zaune anan ta gansa yana takan sallah.
Itama alwalan taje ta d'auro tare da tada kabbara tayi joining nasa, hakan ba
k'aramin farin ciki ta sanya Ibraheem ba.

*^*^ Yasmeen ma haka k'arfe biyun dare mijinta ya tayar da ita sukayi alwala
yajasu sallan nafila inda suka yita roqon Allah wa Baba.
On Zeezee's side and Mariam ma haka ne sallan suke suma ba wasa.

•^••^•••^
Yau Juma'ah k'arfe hud'u dai-dai Allah yayi wa Baba (Alhj Isma'eel Yusouf)
cikawa, wanda mutuwarsa tazo masa cikin sauk'i a hankali a hankali Mala'ika ya d'au
ransa wanda Mama dake gefensa tana bacci ma bata ji komi ba.
Asuban fari Mama ta tashi ko ganewa gawan Baba ne a gefenta batayi ba saboda be
wani kumbura ba cikin ikon Allah, murmushi ne kwance fal a fuskarsa. Bayan ta samu
ta miqe ta miyar basa da bargon sannan ta zarce bayi tayi brushing tayi alwala
sannan ta fito. Tana sanye da hijabi ta nufi kan gadon tare da zama a gefe "Alhj"
ta kira sunansa a hankali.
"Alhj tashi kaji tashi in taimaka maka kayi alwala kayi Sallah Asubah tayi."
Shiru nan ma.
"Baccin ne yayi nisa haka?" Ta tambayi kanta. "Alhj?" tapping nasa ta shigayi, ba
k'aramin razana tayi ba ganin ko motsawa Baba baiyi. Hakan yasa ta matso da
kunnenta dab da hancinsa dan jin futan nishi amman shiru takeji ba numfashi ba
alamansa. Hannunta ta aza akan heart nasa cike da tsan-tsan tashin hankali don
feeling heartbeat nasa, hukuncin da zuciyarta ta gama yanke mata na cewa Allah yayi
wa mijinta, uban 'ya'yayenta cikawa ne ya mugun sa kanta ya sara. "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un" ta furta tana hawaye sosai. "Alhj! "Ta k'wala mai kira "Alhj!
Don Allah kar ka tafi, innalillahi!" rungumesa tayi ta shiga sunbatu tana kiran
doctors da nurses da muryan da Allah ya bata.

Ahaka ne har wata nurse tazo ta sameta, da wuri ta je ta kirawo Dr'n daya duba
Baba jiya, da k'yar nurses suka samu suka fita da Mama waje inda take ta leqe ta
window tana kuka sosai. Dr na duban Baba ya kad'a kai ba amfanin basa pulse saboda
har ya gano d'an kumburin da Baba yayi, tests kad'an suka yi akansa dan gano time
of death nasa which was exact by 4:02am today being Friday (babbar ranar da Allah
ke yafewa dukkanin bawansa da ya rasu a ranan tambayoyin kabari, Allah yasa Baba
yayi mutuwar shahada, yasa k'arshen wahalarsa kenan. Allah ya dubi girman tuban da
yayi ya yafe mai k'urak'uransa yabasa gidan Al~Jannah ya kyautata mana k'arshen mu
yasa mun d'au darasi daga rayuwan Baba mu bawa 'ya'ya'yen mu tarbiyya na gari,
AMEEN.)

Tun da Mama ta hango ana rufe fuskan Baba da k'yalle tasani shikenan Baba ya
tafi ya barta. Wani irin kuka ta sa tana sauk'a k'asa a haka Dr ya fito ya tarar da
ita. Kansa a k'asa yace, "am so sorry Ma'am theres nothing we could do, mijinki ya
riga ya cika tun wajen k'arfe hud'un dare, fatan mu Allah yasa ya cika da imani ku
kuma Allh ya baku hak'uri, verily every soul shall taste the pain of death, I'm
sorry" yana kaiwa nan ya fice. Nurses d'inma one by one sukayi wa Mama ta'aziyyah
sannan suka fice. Ta d'au about 10 minutes a wajen tana kuka sannan daga bisani ta
miqe ganin kukan batada wani amfani, ta koma cikin d'akin ta idar da Sallanta cikin
natsuwa, tagama tofe addu'o'inta sannan ta ja kujera ta zauna kusa da Baba tare da
yaye k'yallen da suka rufe mai fuska dashi. Hawaye ta soma a hankali se ji take
kaman idan tayi mai magana ze amsa ta, ya kira sunanta kamar yadda ya saba. Wani
irin zafaffun hawaye ta shiga kwararowa "ina sonka Alhj, amman nasan Allah ya fini
sonka shiyasa ya d'auke ka ya kaika kusa dashi, Allah yasa mutuwa hutu ce a gareka,
kasani ban ta6a nadaman kasancewa dakai ba, Allah ya had'a fuskokinmu a gidan
Al~Jannah ya tura rahamarsa kabarika, Ameen"

Mama ta d'au mutuwar Baba as k'addara ta kar6esa hannu bibbiyu, sam batayi irin
haukan nan da wasu keyi idan anyi musu rasuwa ba, suna suratai suna cewa sun mutu
sun lalace. Kukan zafin rabuwa bayan an zama d'ayan daya zama dole kawai tayi bayan
nan tayi masa Addu'an da akeyiwa mamaci sannan ta biyosa da dukkanin addu'o'in data
sani akanta ta tofe masa. Bayan nan da kanta tayi mai wanka ta suturcesa, har anan
ba wanda yaji rasuwan Baba.

Ibraheem Mama ta d'aga waya ta soma kira, lafiya sumul suka gaisa inda yake
sanar da ita yanzu haka ma sun gama shiri zasu kama hanya.
"Ibraheem ina son ka saurareni da hankali a matsayin ka na babba cikin yarana da
musulmin da aka sani da tawakalli, kasani cewa duk wani me rai mamaci ne." Tun anan
jikin Ibraheem yayi sanyi jira kawai yake yaji Mama ta furta mai abinda ransa ke ta
raya masa.
"Ibraheem Allah yayi wa Babanku cikawa yau da daddarre wajajen k'arfe hud'u."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya furta a hankali a yayinda idanunsa suka
kad'a sukaji ja zirrr lokaci guda.
"Mutuwa abu ne me zafi amman yazama dole muyi tawakalli mu rungumi k'addara,
dukkanin me rai mamaci ne kaman yadda Babanku ya tafi muma wataran turn namu zezo.
Sekun shigo, da sallan juma'ah a nan Gwallaga za'a sallace shi, Allah yasa mutuwa
hutu ce a gareshi."
"Ameen" kad'ai ya iya furtawa tare da yasar da wayansan a k'asa. Hakan yayi dai-
dai da shigowar Fateemah don sanar dashi breakfast is ready sede ganin idanunsa ta
gane cikawa mahaifinsu yayi. Itama take idonta suka cike dam da hawaye da gudu taje
ta samesa tare da hugging nasa nan suka fashe da kuka sosai abin tausayi ba na miji
ba mace.

Hajiya (maman Baba) next Mama ta kira ta sanar da ita inda itama tayi salati tare
da sa kuka sosai. Yasmeen ta gama yima Suleiman wanka ta shigo dashi riqe a hannu
sannan ta ajiye sa kan gado ta kira sunan mijinta dake maqale da waya a kunne da
"King, Wankan fa sauran kai." Kasa juyawa ya kalleta yayi bayan sanar dashi mutuwan
Baba da Ibraheem yayi. "Abban Suleiman?" Ta sake kiransa "zamuyi latti fa." Yana
kaffa-kaffa ya juyo a hankali emotion dake fuskarsa kad'ai says it all.
"Abban Suleiman is something wrong? Why the face?"
"Yasmeen" ya kirata a hankali tun anan jikinta ya bata Baba ya rasu ne kai ta
shiga kad'awa "no no don Allah kar ka cemin Baba ya rasu please don't" gudu tasa
zata bar d'akin sede kafin nan mijinta yayi sauri ya jata tare da forcing nata ta
kwanta a jikinsa.
"Sshhh he is in a better place in shaa Allah." Kuka take sosai tana sumbatu "he
can't die please ka fad'amin wasa kake be mutu ba."
"Yasmeen kiyi hak'uri Baba lokaci yayi Addu'an mu yake buk'ata ba kukan nan ba
kiyi hak'uri." Ai kaman sake tunzirata yake ta kasa barin kukan ganin haka Suleiman
ma ya sa kuka.

Mariam ta gama shirya Ramlah school, Ummie kuma day care text message from Ya
Ibraheem ya shigo wayarta tana kai dubanta taga biggest suprise of her life salati
kawai ta saki sekuma aikin kuka, makarantar da yaranta basu jeba kenan ranan. Ko
kiran da mijinta ke mata ma ta kasa picking se kuka kawai. Hakan yasa Ramlah da
Ummie ma kuka, se hak'uri me aiki ke bata amman ina abin ya gagara.

Zeezee was the last person to come to know about their father's death.

* MIEMIEBEE. TEAM #YGC🎀*


Beeenovels.blogsot.com

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
5⃣2⃣
Tun wajajen 7am Mrs Mukhtar taji rasuwan Baba wanda Mama ta sanar da ita
ta broadcast mssg da aka yiwa kowa, amman ta rasa ya zata fara sanar da Zeezee. Da
k'yar ta samu tayi gathering courage bayan k'arfin guiwan da mijinta ya bata ta
shiga d'akin Zeezee tare da yin sallama. Alokacin har Zeezee tagama shirinta tsaf
sauran tafiya kawai take jira don taje ta duba lafiyan mahaifinta. "Wa'alai kumus
salam. Ina kwana Aunty?" Ta gaisheta cike da ladabi.
"Lafiya Zeezee har kin shirya ne?"
"Eh, Aunty."
"Bazaki karya ba toh?"
"A'a sena dawo zanje naga lafiyan Baba tukunah." Nan fa Mrs Mukhtar ta sake jin
bazata iya sanar da Zeezee ba mutuwan mahaifinta but tasan she have to.
"Zainab." Daga yadda ta kira ta yasa gaban Zeezee fad'uwa danko bata ta6a kiranta
da Zainab ba sede Zeezee.
"Na'am Aunty?"
"Zeezee..." sekuma tayi shiru.
"Zeezee kinsani cewa duk me rai mamaci ne ko? Kowa a duniyan nan ze mutu wataran
ya koma ga mahallicinsa ko ba haka ba?" Dum! Gaban Zeezee ya sake fad'uwa sede sam
bata kawo a mind nata wai rasuwa mahaifinta yayi ba.
"Aunty me kike nufi?" Kad'ai ta iya furtawa tana kad'a kai a yayinda hawaye ke
forming rapidly a idanunta wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba.
"Zeezee you are no more a child ya kamata in sanar dake gaskiya, Baba lokaci
yayi, Allah yayi mai cikawa yau da daddarre wajajen k'ar-" bata kai da idda maganan
ba kawai taji rigijib! Fad'uwan abu a k'asa. Da gudu ta yo kan Zeezee only to find
her fainted (a sume.)

"Innalillahi! Zeezee! Zainab!" Bangida ta nufa ta ibo ruwa ta yayyafa mata sede
ko motsawa Zeezee batayi. "Mukhtar! Mukhtar!" Tashiga k'walla wa mijinta kira wanda
ya fito a gigice.
"Mukhtar! Zeezee, Zeezee please do something."
"Jeki d'auko key da wuri" ya buk'aceta a yayinda ya cinci6i Zeezee se asibiti
suka yo inda akayi emergency ward da ita. Taimakon gaggawa aka shiga bata a yayinda
hankalin Mrs Mukhtar ya kasa kwanciya. Cikin ikon Allah Dr's suka samu suka
farfad'o da Zeezee sede gabad'aya bata cikin hayyacinta banda "Baba, Baba" da take
ta furtawa.

"Dr how is she?" Mrs Mukhtar tayi saurin tambayan Dr'n hankali a tashe.
"She'll be okay in shaa Allah amman kome ya sameta?"
"Dr rasuwa akayi mata, mahafinta ne ya rasu. In the process of breaking the news
to her seta yanki jiki ta fad'i."
"Ohh ayyah, Allah yaji k'anshi da rahma."
"Ameen" both suka amsa.
"Shi dama mutuwa haka yake but karku damu in shaa Allah zata samu sauk'i. She is
just psychologically affected wanda hakan is normal."
"Toh Dr mungode" cewar Mukhtar.
"Zamu iya shiga ganinta?" Asked Mrs Mukhtar.
"Sure please, excuse me" Dr'n ya amsa tare da ficewa. Nan suka shiga d'akin
Zeezee inda take nan kwance bisa gado tamkar wata zararriya ta koma, se ambaton
"Baba, Baba" kawai take. Duk kalan suratai da sannu da Mr and Mrs Mukhtar suke mata
ba jinsu take ba.
"Ku kaini gun Baba, Baba be mutu ba inya ganni ze tashi ya koreni saboda ya
hanani taka duk inda yake. Ku kaini gunsa please nasan be mutu ba."
"Zeezee bakida lafiya, kibari zuwa anjima idan kika d'an ji sauk'i." Mrs Mukhtar
tayi explaining calmly.
"Ku kaini gun Baba don Allah ku kaini wajen shi" kuka take sosai me tsuma
zuciya. Ganin yadda take kuka sosai yasa dole Mr Mukhtar yama Dr magana akayi
discharging nasu. A sannu a sannu Mrs Muktari tasa Zeezee a mota suka nufi TH inda
su Mama suke.
A lokacin da suka isa ma su Mama da sauran dangi suna shirin komawa gida ne da
gawan Baba don cigaba da kar6an gaisuwa achan. Ko ta kan Mama Zeezee batayi ba da
gudu taje ta rungume gawan Baba dake a lullu6e kan gado.

Kuka take wane don shi aka kawota duniya, ba wanda yace da ita k'ala illa ma
kallonta da suke suma suna kukan.
"Baba nasan baka mutu ba, nasan kana jina, please say something you can't die, we
need you alive. Baba bazeyi ka mutu ban nemi tubanka ba, please come back Baba. I
need you to forgive me please come back. Baba ni ya kamata in tafi saboda kasamu
kasha iska, ba kai ka tafi ka barmin duniyan ba. Please come back" ta k'are maganan
tana jijjiga gawan Baba.
Ihu ta rushe dashi ganin be mata magana ba har yanzu assuring her he is gone
forever no coming back. Matse jikin Baba tayi a nata tana hugging nasa sosai.
Mariam ce tayi k'arfin hali tace da Mama, "Mama ki fad'a mata Baba ya yafe mata
please." Ita kanta Zeezee ta bata tausayi, itan da sukayi sharing happy moment with
Baba ma kenan kafin lokacinsa, bale ga Zeezee da Baba ke fushi da ita for a very
long time. A nitse Mama ta miqe ta nufi kan Zeezee tare da patting bayanta.
"Zeezee ya isa haka kinji? Taso yi hak'uri."

"No Mama don Allah kar ku fita da Baba wallahi be mutu ba yana jina, ku tsaya
kuga ze tashi yace in fita mishi daga d'akinsa. He is not dead listen to me
please."
"Zeezee kibar magana haka da rungumar k'addara aka san musulmi. Baba lokaci yayi
amman jiya ya bani wasiha na fad'a miki. Yace _ya yafe miki duk abubuwan da kika
masa duniya wa lahira, da 6oyayye da kuma bayyananne. Yace min yau in Allah ya
yarda ki koma gida ki cigaba da zaman ki achan, chan ne gidanki. Yace min he wants
you to know that you'll forever bs his little sister and daughter and that he loves
you so much Allah ya miki albarka ya baki 'ya'ya na garin da zasu kula dake ya kuma
baki miji nagari and lastly kema ki yafe masa abubuwan da ya miki._" Mama ta k'are
maganan cikin kuka sosai wanda seda yasa duk wani mahalukin dake gun kuka banda
kaman Zeezee. Within seconds kuma se aka ji kukan nata ya d'auke. "Zeezee?" Mama
tayi saurin tapping nata only to found her fainted body. Sumanta na biyu kenan, nan
da nan akayi next room da ita inda aka shiga bata taimakon gaggawa ciki harda drip
da aka samata saboda low water and sugar level data samu a safiyan yau, bayan nan
ga yunwan da yaci jikinta wanda ke neman haifar mata da gastric ulcer. Alluran sa
bacci aka yi mata, seda Dr ya tabbatar wasu Mama she'll be alright hankulan su
yad'an kwanta. Mrs Mukhtar da Mariam aka bari akanta a yayinda sauran duk suka nufi
gida don cigaba da kar6an gaisuwa achan.

******
One hour sleep Zeezee ta samu sannan ta tashi da gaggaramin yunwa. Fuskan Mariam
ne ya soma mata sallama, da wuri ta share hawayenta tare da mata "sannu" sede wani
irin kallon da Zeezee keyi mata. Kafin ta hankara kawai taga Zeezee na neman 6alla
connection na drip da aka sa mata. Da wuri Mariam ta haneta da yin hakan. "Ki
sakeni Adda Mariam."
"Zeezee What are you trying to do?"
"Rayuwa ta bata da sauran amfani Adda Mariam I can't bear the thought that ni na
kashe mahaifina."
"Inji wa ke kika kashe Baba?" Mariam tayi maganan still not letting her go
saboda yadda Zeezee keta faman k'watan kanta.
"Ni na kashe shi Adda Mariam, nice silar rashin lafiyan dayayi sanadiyar
mutuwarsa, I killed my own father Adda Mariam" ta rushe da kuka sosai.
"No you didn't Zeezee, Baba lokaci yayi ba abinda muka isa muyi, rashin lafiya
kuwa Allah ya riga ya k'addara masa shi tun kafin ya shigo duniya so stop blaming
yourself kinji?"
"That's not true, that's not true Adda Mariam just go leave me in kashe kaina
nima yaso naje na sameshi achan lahira in nemi tubansa."
"Wani tuba kuma again Zeezee bayan Baba yace ya yafe miki?"
"That's still not true kawai Mama ta fad'a ne don kar hankalina ya tashi nasani
Baba be yafemin ba nikuwa bazan iya cigaba da rayuwa da hak'k'in Baba akaina ba I'd
rather commit suicide."
"Get your senses together Zeezee, Baba ya riga ya yafe miki shike neman
yafiyarki kema."
"Meya ta6amin da ze nemi yafiya na?" Ta ce tana kuka sosai.
"Kede kice kin yafe mishi saboda muma duka kafin... kafin" sekuma ta rushe da
kuka "kafin lokacin sa yayi seda ya nemi tuban mu don haka nakeson kice mishi kema
kin yafe masa."
"Tunda Baba yake raye ban ta6a farinta mai ba, banda asara, bad luck da ciwon
zuciya ba abinda na jawo mishi Adda Mariam, I know I am his worst daughter and
child I can't ever forgive myself gani nake my hands are stained with his blood.
Inhar abinda Baba ya buk'ata kenan kafin ya tafi ya barmu, toh ni na yafe masa har
abada."

Hugging nata Mariam tayi inda suka cigaba da kuka sosai. Tsan-tsan yunwa ko
tsayuwan minti d'aya Zeezee ta kasa, wai ahaka ma don da taimakon drip da aka bata.
Ba yadda Mrs Mukhtar batayi da ita ba taci abinci tak'i. Da k'yar suka samu tasha
black tea se kuka take tana su kaita gida gun Babanta. Ta gama kur6e tea'n suka
d'au hanyan gida.
Dam gidan nasu yake cike da mutane da k'yar suka samu gu sukayi parking, da
k'yar Zeezee ke tafiya ahaka ne har suka k'arisa ciki suka cigaba da aikin kuka.

***
11:40am su Yasmeen suka iso a yayinda su Ibraheem suka iso wajajen 12::50pm.
Kuka de ba babba ba yaro. Tabbas iyalan Late Alhj. Isma'eel Yusouf sunji wannan
mutuwa na sosai sabida tun da suka taso wani na kusa dasu be ta6a mutuwa ba se akan
mahaifinsu wanda suke matuqar sonsa fiye da yadda suke son kawunan su, its indeed a
great lost to them, Allah ya jik'an Baba ya kai rahama kabarinsa, Ameen thumma
ameen.
K'arfe 01:20pm aka zo fita da gawan Baba wanda yake ajiye akan makara a d'akinsa
inda aka fito dashi tsakar gida aka ajiye don bawa iyalansa daman yimai kallo da
kuma addu'a na k'arshe. Hajiya Mama, mahaifiyarsa ce ta soma fitowa da taimakon
k'annen Baba aka kaita gaban gawan d'anta. Banda kuka ba abinda takeyi. Da k'yar ta
iya ya ta yaye laqafanin izuwa wuyansa sannan a sannu a sannu ta aza hannunta kan
fuskarsa tana shafawa in a soothing yet pathetical manner "Allah ya ji k'an ka
d'ana, har a kullum ina alfahari da kai ban ta6a nadaman haifanka ba. Na yafe maka
dukannin abubuwan da kayimin na 6oye da bayyananne, ko da gan-gan ko rashinsa.
Allah yayi maka rahama ya dubi kalan alkhairun da kayimin a rayuwa ya saqa maka da
mafificinsu, ya d'aukaka darajarka a cikin shiryayyun bayinsa kuma ya maye maka
bayanka a cikin wad'anda ka bari, yasa mutuwa hutu ce a gareka, ameen." Add'uan da
akeyiwa mamaci ta biyosa dashi wanda duk gun suka amsa da "ameen."

Mama was tha next person, itama guiwa ba k'arfi ta k'arasa gun da gawan ke
shinfid'e. Kuka take sosai itama ta yaye fuskar nasa, nan fa sabon kuka ya sake fin
k'arfinta. Addu'o'i sosai tayita yiwa Baba akan wanda tayi mai d'azu bayan data
gama yimai addu'an ta had'a musu hannunsu se kuka kuma, ta tashi daga gun ma ta
kasa seda su Mariam ne suka d'agata. Ibraheem ma kuka yake sosai ya k'ariso gaban
gawan tare da yaye liqafanin, kuka yake sosai wane d'an yaro daga k'arshe yayi mai
addu'a shima sannan ya tashi ya koma. Next was Mariam itama se kuka, duk according
to their ages suka rik'a fitowa suna kuka sosai suna yiwa mahaifinsu addu'a.
Kasancewar Zeezee ce auta, ita aka buk'ata last ta tako zuwa gaban gawan ma takasa,
Yasmeen ce tayi assisting nata. Zubewa tayi a wajen se kuka tama kasa ta6a gawan
bale tayi mai addu'a. Hannunta 6ari yake sosai ta d'aga da k'yar ta iya ta yaye
liqafanin, nan fa ta sa wani irin kuka me tsuma zuciya. Hugging nasa tayi sosai
"Baba I cannot live without you, you need to come back nasan baka mutu ba kanaji
na, please say something inason inji da kunnuwa na ka yafemin, I want to be in your
arms one last time, please come back you can't die. I want to make you happy one
last time, nasan tunda aka haifeni I've been nothing but bad luck to you, Baba don
Allah ka dawo nayi alk'awari to make you happy and proud. I'll never go against
your command not even your wish, please Baba come back" ta sake sa wani erin kuka.
"Mariam kuje ku d'agota" cewar Mama ganin kukan Zeezeen bana k'arewa bane. Guiwa
ba k'arfi Mariam ta miqe ta nufi gun Zeezee tare da jan hannunta "tashi Zeezee yi
hak'uri Baba ya riga ya yafe miki muma duk mun yafe miki."

"Thats not true, ki sakeni ki barni dashi don Allah."


"Zeezee ya isa please za'a fita dashi yanzu." Ganin abin ya gagari Mariam,
Yasmeen ta shiga taimaka mata sede ina sun kasa d'ago Zeezee daga jikin Baba don
yadda ta matse sa gagam a jikinta. Kuka take sosai na hak'ik'a tana sunbatu. Daga
k'arshe seda Mama tasa Ibraheem daya je ya d'ago Zeezee. Shima seda yayi dagaske ya
samu ya d'agata nan fa ta tada bori ita subarta a jikin babanta. Wani abin ma seda
aka zo d'aukan gawan Baba za'a fita dashi.
"Baba! Don Allah ku dawo min da mahaifina wallahi be mutu ba, karku tafi dashi
don Allah I'm begging you guys please don't take him away." Idanunta da suka canza
launi da komi ta d'ago tana kallon Ibraheem daya rik'eta gagam pathetically.
"Ya Ibraheem nasan kana son Baba please don't let them take away Baba from us,
ka musu magana su dawo mana dashi I beg of you please." Kuka yake har anan ya kasa
ce mata komi nan ta kewayo da kallonta kan Mariam da keta faman kukan itama.
"Adda Mariam, I know you love Baba so much please don't let them take him away."
Anan datayi maganan har mutanen sun kai ga fita da gawan waje, wani irin ihu ta
k'urma wanda tuni Ibraheem ya sake ta nan tasa gudu. Ta kaiga iskesu wasu maza suka
samu suka rik'eta nan Omar ya kar6eta daga hannunsu. Se bori take tana ihu a dawo
mata da Babanta. "Mama don Allah karki bari su fita mana da Baba wallahi be mutu
ba." Da k'yar Omar yaja ta tare da zaunar da ita gefen Mama, ganin tana da niyyan
tashi su Yasmeen suka danne ta. Sahun gawan su Ibraheem suka bi domin samun
sallatan mahaifinsu.

Tunda aka fita da gawan Baba, Zeezee ta tabbata fa yanzu shikenan Baba ya riga
ya tafi ko shadow'nsa bazata sake gani ba bale taji muryansa kokuwa dariyansa, ya
tafi kenan har abada no coming back. Nan ta fita daga hayyacinta gabad'aya, gatanan
a zahirce a gidan amman hankalinta bayi nan ko kad'an. Ta had'a wani tagumi se
hawaye kawai take zubarwa wane lalacaccen famfo.

***
Cikin yardan Allah aka sallaci Baba a Gwallaga Central Mosque inda ya samu
thousands and thousands of people da suka sallacesa suka kuma rakasa makwancinsa.
Ibraheem da Omar akayi susa gawan Babansu a kabari amman ina sun kasa tsan-tsan
tausayi da kuka. K'annensa biyu suka sa sa tare da yimai final addu'a sannan aka
bisine sa. Allah yaji k'ansa ya kyautata k'arshen namu muma, ameen.

****
Gida se cika yake ba ko inda mutum ze sa k'afa. Dangi from other states
gabad'aya sun samu zuwa se aikin kuka ake ba babba ba yaro, inda wasu ke hirar
mamaci. Dayawa ke cewa Zeezee ce silar mutuwan Alhj Isma'eel tunda a sanadin ta ne
ya soma kamuwa da ciwon zuciyar da har yayi leading to mutuwarsa, a inda wasu kuma
ke cewa itance ma ta kashe sa kawai. Wannan maganganu su suketa yad'uwa har a cikin
gari. Daga k'arshe fita Zeezee tayi daga gidan da gudu gabad'aya ta nufi gidan Mrs
Mukhtar dan kunnenta bazasu iya cigaba da jiye mata wad'ancan munanan kalamu ba na
cewa ita ta kashe mahaifinta. Kallon hannunta kawai take se gani take wai ga jinin
Baba nan kwance jina-jina akai. Hak'uri Mrs Mukhtar keta bata. Tun daga wannan
lokaci Zeezee bata sake sanin inda take ba.

A washegarin rasuwan ne Adeel yajiyo rasuwan Babansu Zeezee wanda ya mugun


tausaya mata sosai har hawaye seda ya zubar mata, tuna yadda take jijji dashi even
before suyi aure. Koda yace tayi abu se tace ita Babanta fa, har ma yake neman
tasokanarta da 'Daddy's girl.' Gani yake he is partially to blame shima saboda shi
yasata ta bijire wa mahaifin nata wanda yayi causing masa wannan cutar da tayi
sanadin mutuwarsa.
Tsaf shida Ruky Mama suka shirya suka zo yin ta'aziyya, hannu bibbiyu aka kar6esu
duk da sanin komi started with Adeel. Bayan ya gaishe da Mama yayi mata ta'aziyya
ya buk'ci ganin Zeezee inda Mama ke sanar dashi cewa bata gida a haka ma yanzu
batada lafiya. Still yayi insisting yana son ganinta a tunaninsa kawai hanasa ganin
Zeezee Mama keson yi. Seda Mama ta fayyace masa gaskiyan al'amari na cewa koda
zeezee ta gansa yanzu ba gane shi zatayi ba saboda condition da take ciki. Ko jiya
da Mama ta aika aje a duba mata ita chan gidan Mrs Mukhtar bata gane su Mariam ba,
sede tayita kallon mutum tana kallon hannunta amman ba kalman k'ala.

Wani irin tausayawa Zeezee ya sakeyi if only there's something he can do. Fatan
lafiya yayi wa Mama sannan ya ajiye carton na maltina biyun daya kawo musu suka
koma da Ruky. Itama Ruky gabad'aya ta tsorata da mutuwan Baba tuna fa alhak'in
Zeezee na sharrin data yi mata na kanta har yanzu, dole ta nemi tuba.

Al'ameen kuwa a sadaqan uku ne Mama Babba ke sanar dashi rasuwan Baba. Sosai ya
tausayawa Baba dakuma iyalansa most especially ma Zeezee da har yanzu take da gurbi
a zuciyansa. Dukda auren da Mama Babba keson had'asa da wata 'yar uwarsa Murjah,
hakan besa ya dena son Zeezee ba ya kuma fara son ita Murjan. Infact her love
increases in him every single heart beat. Auren biyayya kawai zeyi saboda shi har
yau bega mace ba bayan Zeezee, sonta a jinin sa yake despite abubuwan da tayi mai
he still loves her like so much.

A ranan da yaji rasuwan ba tare da 6ata lokaci ba ya kira Mama yayi mata
ta'aziyya, yaso ace yana gari don ya samu daman expressing masu condolences nashi.
Layin Zeezee itama ya buk'ata don yimata ta'aziyyan saboda ya gwada wanda ke gunsa
it aiint going through.
Anan ne Mama ke sanar dashi halin da Zeezee ke ciki. Sosai masoyin hak'ik'an ya
sake tausayawa Zeezee. If only there's something he could do.
Abu fa kaman wasa se worsening condition na Zeezee ke tayi, se kaman neman
zarewa take ne oho, abun kaman hauka. In anji sautin muryarta toh tana kuka ne.
Magana ma tabar yi, ko bayi takeji in bawai anyi timing nata bane an kaita sede
tayi a jikinta, cin abinci, sallah komi nata ya tsaya kat! Abu kaman wasa-wasa har
akayi sadak'an bakwai Zeezee bata san inda take ba gata nan ne kawai se yadda akayi
da ita. Bayan sadak'an bakwai ne lokacin da mutane suka gama watsewa, wanda suka
rage befi a k'irga ba. Se a nan ne hankalin Mama da sauran yaranta ya dawo jikinsu
akayi wur-wur aka d'auko Zeezee daga gidan Mrs Mukhtar aka kaita asibiti. Bayan
dogon nazari da bincike da Dr yayi ya nuna musu cewa ba abu neba na damuwa saboda
hakan is normal ga duk wanda mutuwa ya ta6a sa sosai, she is psychologically and
even mentally affected at her own case, but in shaa Allah bayan d'an wani lokaci
she'll be back to normal. Wanda kafin nan ya zama dole a kullum ana karanta mata
labarai masu dad'i masu sanya nishad'i dakuma kaita leisure places saboda yayi
erasing bad memory'n dake lingering akanta na cewa ita ta kashe mahafinta. Har
izuwa ga wannan lokaci kuwa koda wasa kar a mata furucin da bashida dad'i. A haka
ne su Ibraheem suka dawo da ita. The next day Ibraheem da iyalansa harma da Yasmeen
suka juya, inda suka ajiyeta a KD sannan suka zarce Abj. Mutuwan Baba har a yau
kaman sabo yake a memory'nsu, they shall never forget about their beloved father.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*
*Febraury, 2017*
5⃣3⃣

Sabuwar rayuwa kowa kuma ya soma living, as for Mama ta shiga zaman
takabarta inda take kuma kula da Zeezee, kwana ma tare suke yanzu, don kuwa har
yanzu ba wani progress da aka samu game da condition nata. Mama keyi mata komi, da
yamma wajajen 5:00pm kuma bayan Omar ya huta from office seya kaita waje zuwa wajen
shak'atawa susha iska inda zeyita karanta mata stories. Itama Mama anytime she is
less busy tana k'ok'arin karantowa Zeezee stories.
Anyi haka na kusan sati biyu da 'yan kwanaki Zeezee ta soma magana wanda da
kalman 'Baba' ta bud'e bakinta. Mama ta ajiye ta kan couch a d'akinta tana shirya
wardrobe nata ta tajiyo muryan Zeezee da she can't remember when last ta jisa. Da
gudu ta nufi wurinta tare da riqo hannayenta sede Zeezee tayi saurin wabje su.
"Baba" ta sake nanatawa.
"Zeezee? Mama ce ba Baba ba kinji?" Bayan data k'are wa Mama kallo na kusan
mintuna biyu se kuma ta miyar da kallonta kan hannunta da take gani jinin Baba ne
akai.

"Baba" ta sake furtawa. Hannun nata Mama ta rufe da nata, "ba Baba anan kinji?
Hannunki ne wannan."
"Kefa wacece ce? Leave me alone please, Baba! Baba!"
"Mama ce Zeezee baki gane ni ba?"
"Mama? Nasan kine? Ni Baba nakeso, ina yake?" Zuciyarta taji ya sake karyewa jin
wannan kalamu daga bakin 'yarta, kamar ya Zeezee bata gane taba? How is that even
possible? Danne zuciyarta tayi ta amsata;
"Baba yayi tafiya kinji?" Tayi maganan kuka na neman ku6uce mata wanda da k'yar
ta samu ta had'iye.
"Ina yaje? Kice mishi ya dawo shi nakeso ba ke ba."
"Inda ya tafi ba a dawowa Zeezee, duk wanda ya tafi ya tafi kenan ba dawowa."
"Ina son in bisa nima ki kaini gunshi."
"When your time comes zaki bisa kema kinji? In kaiki bayi kiyi alwala kiyi
sallah?"
"Sallah? Meshi kuma? Ni Baba nakeso." Sosai Mama tasake shan mamaki. Me hakan ke
nufi? Zeezee ta mance da kowa da komai kenan? Omar ta kira ta gwada tambayan Zeezee
waye shi inda ta nuna musu bata san shi bama at all shima. Cike da tashin hankali
Mama ta kira Dr tayi mai bayanin komi, "calm down Ma'am I think she must have lost
her memories-" katse sa tayi saurin yi da "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Dr
memories fa kace? Kana nufin bata san kowa ba kenan yanzu?"
"Yes but fatan mu Allah yasa temporarily ne ba permanent ba."
"Innalillahi! Yanzu in kuma permanent d'in ne fa?"
"I'm sorry but it'll take morethan a year kafin ta sake ganeku but inhar
temporary ne within months zata tuna komi. You can only make this possible by
staying close to her always, karki ta6a barinta ita kad'ai. Kuma never give up from
making her happy, duk abinda takeso kina yimata kina tuna mata da ko ke wacece, in
shaa Allah as time passes by she'll get back her memory."
"Toh Dr data ce ko Sallah bata sani bafa?"
"Komi ai yanzu ta mance dashi, her memory is as fresh as that of a baby."
"Ya Salam!" Ta furta a hankali.
"Ku cigaba da sata a addu'a in shaa Allah she'll be back to normal."
"I pray so Dr, thank you."
"In 3 weeks time call me back muga in har akwai improvement."
"I'll Dr thank you."
"You're welcome." Kai zallah ta kad'awa Omar daya saurari wayan da sukayin. "In
shaa Allah zata warke Mama don't give up hope." Ya fad'a soothingly.
"I pray so Omar, dududu da rasuwan mahaifinku sati nawa ne wannan masifa ze sake
afka mana."
"Subhanallah! Mama kisani Allah baya d'aura wa bawansa musibar da baze iya
d'aukawa, muyi tawakalli kawai."
"In shaa Allah Omar thanks for the reminder." Nodding kai kawai ya mata sannan a
tare suka dawo da kallonsu kan Zeezee dake ta faman kallon hannunta.
"Zeezee?" Mama ta kirata soothingly amman ko d'aga kai ta kalleta Zeezee batayi
ba se a karo na uku. "Zaki ci abinci Mama na?" Kallon Mama kawai take totally lost.
"Abinci, zaki ci? Kina jin yunwa?" Har anan kallonta Zeezee kawai take. Suratai
ba wanda Mama batayi ba wanda ciki ba wanda Zeezee ta amsa. Kuka ta soma without
knowing how, "Omar tabar maganan kuma again.
Ina zan sa kaina?" Hugging nata Omar yayi yana tapping bayanta. "Shhh! Have faith
zata samu sauk'i bi izinillah." Da k'yar ya samu ya fito da Mama daga d'akin yaje
ya tsuguna gaban Zeezee dake ta kallonsa shima, se gani take kaman ta sansa. Badon
komi ba kuma illa don kaman da Omar da sauran yaran suke ne da Baba, dama chan
Zeezee ce kad'ai me kamannin Mama. Hannunta ta aza a hankali akan fuskarsa tana
shafawa a hankali. "Baba?" Ta kirashi.
Kai ya kad'a mata yana murmushi, "Suna na Omar am your big brother ba Baba bane,
Omar suna na."
"Omar? Toh ina Baba?"
"Yayi tafiya, mesa kika k'i yi wa Mama magana?"
"Wace Mama?"
"Farar matar data fita yanzu."
"Ni ban santa ba."
"Ni kin sanni? Kin gane ni?"
"Ba kai bane Baba?"
"I'm Omar, Ya Omar remember me?"
"No kaine Baba, ashe ba jinin ka anan" ta nuna mai hannunta. "Babu" ya fad'a yana
mata murmushi, "hannunki ne ba komai kinji?"
"Naji Baba." Kaman ya sake ce mata shifa ba Baba bane sekuma yaga ba amfani.

"Zaki ci abinci?" Kallonsa ta tsaya yi nufin bata fahimta ba. "Yunwa" yayi
pointing cikinsa "zakici abinci?" Yayi tambayan yana immitating da body movement.
Kai ta gyad'a masa nufin yes.
"Toh bari inyi ma Mama magana ta kawo miki." Da wuri ta kama hannunsa ta rik'e
"ni o'o kai nakeso."
"Ga Mama zata sa miki." Kafad'a ta buga "yi hak'uri Baba ni kai nakeso."
"Toh naji sakeni ina zuwa."
"Zaka sake tafiya ka barni?"
"Ai ban ta6a tafiya na barki ba Zeezee" ganin kalamunsa na neman dak'ula mata
lisafi yace, "tashi toh muje" haka tana rik'e da kayansa suka k'arisa kitchen yasa
mata abincin, tabari Mama tayi feeding nata ma bataso, sam in taga Mama se tayi as
if bata magana. Bayan ta gama cin abincin yace da ita "sauran Sallah ko?"
"Me ma Sallan nanne?"
"Kin manta Sallah Zeezee?"
"Eh Baba mesa baka cemin K'anwata yanzu?" Allah sarki seya tuna da Baba,
murmushin dole ya k'irk'iro sannan yace, "toh K'anwata sauran Sallah ba?"
"Baka fad'amin ba meh shi Sallan ba ai."
"Sallan da yazama wajibi akan kowani musulmi da zaran ya mallaki hankalinsa,
wanda ake yinsa 5 times daily, Subh, Zuhr, Asr, Maghrib-"
"And Isha!" tayi saurin katse sa.
"Excellent" dad'i sosai yaji ganin memory loss nata beyi affecting educational
stuffs nata ba. "Kin tuna shi?"
"Eh Baba na tuna."
"Good tashi toh kije kiyi alwala." Nan ma tace batasan me alwala ba seda yayi ta
mata kwatance sannan ta soma tunawa, yana alwala tanayi har suka idar sannan yayi
mata shimfid'a tare da d'auko mata hijabi.
"Raka'ah nawa zanyi toh Baba?"
"Yanzu kinga tunda kika fara rashin lafiyarki baki samu dama kinyi Sallah ko sau
d'aya ba, Sallah kuwa idan ba mutuwa ba ba'a yimai uzuri so yanzu zakiyi La'asr
raka'a hud'u-hud'u sau biyu, haka zaki cigaba dayi duk Sallan da zakiyi sekina
yinsu bibbiyu zuwa nawani tsawon lokaci, innallaha gafurur raheem."
"Toh Baba" ta fad'a ba musu. Yana zaune agun har ta idar. Da Maghrib ya shirya
zasa Masjid nan ta tukuikuiye mai kaya ita karya fita ya barta, ya kaita gun Mama
kuma tak'i.
"Toh kinga idan baki bari na kaiki gun Mama ba zan tafi bazan sake dawowa ba."
"A'a Baba please karka ce haka nayi al'kawari bazan sake sa6awa umarnin kaba."
"Good girl tashi muje wajen Mama toh, ba abinda zata miki actually tana sonki ma
sosai, bakiga kuna kama ba?"
"Kama a ina?" Ta tambaya. Tuna halan ma fa yanzu batasan kamanninta ba yasa yace,
"bari idan na dawo daga Masjid yanzu tashi in kaiki gun Mama."
"Baba kace bazata min komi bako?"
"Eh K'anwata tashi muje." A nitse ya kaita gun Mama tare da umurtanta da tayi
alwala tayi Sallah.

Tana idar da Sallan Mama ta juya ta kalleta "har kin idar Mamana?" Shiru tayi
not ready to talk. Danne zuciyarta tayi tace _"kin ta6a jin inda uwa tak'i
'ya'yanta ne? Kisani Zainab kome kikayi min ina sonki saboda ni kad'ai nasan zafin
haihuwarki."_ Take Zeezee ta juya tana yima Mama wani irin kallo as if though
trying to remember something. Toh aina nasan wannan matar? Ta tambayi kanta.
Dawowan Omar yaje ya d'auko family album nasu tare da ajiyewa gaban Zeezee dake
mak'e a jikinsa. Picture'nta da Mama su kad'ai ya zaro ya miqa mata "wace wannan?"
Ya tambayeta yana nuna mata kanta. Kai ta kad'a alaman bata san wace ba, "wannan
fa?" Ya nuna kan Mama. Kai ta d'ago tana kallon Mama sannan tace, "itace Matar da
kake kira da Mama ko?"
"Exactly" hannu ya miqa kan dressing mirror tare da d'ago k'aramar mirror ya bata
don kallon face nata "laaa! Wannan ba itace na hoton nan ba Baba?"
"Kinga kuna kama ko? Toh ai kece wannan d'in."
"Kana nufin nice a hoton nan da kuma madubin?" Kallon kanta ta sakeyi a mirror'n
sannan back to the picture, tafa tabbatar itance but how comes? "Taya muke kama da
ita toh?"
"Bari kiga" ya amsa ta. Allah sarki hotonsa da Baba ya ciro ya ajiye mata, "su
waye wannan?" Kallon pic d'in take bewildering, ga wanda de take ce mai Baba nan
amman kuma k'wak'walwarta na soma ce mata babba na hoton ne asalin Baban nata. Wani
irin sara da juyi kanta ya shiga yi mata wanda da wuri Mama ta kar6e album d'in
gudun kar ya haifar mata da something bad. Rufe idonta da tayi kawai se bacci,
sallan isha da k'yar Omar yasata a gaba tayi ta sake komawa baccin. Da wai sam ita
a d'akinsa zata kwana seda yayi dagaske ta yarda zata kwana da Mama.
Banda mafarke-mafarken Mama data yitayi ba abinda ta tsinana a baccin, se raya
mata mind nata ke tasan Mama.

Haka a hankali a hankali Omar ke flashing wa Zeezee da old memories nata back har
tazo ta gane ba shine babanta ba, toh ina Babanta yaje? Ta fannin Mama kuwa, ta
soma sakewa da Mama ganin how free they are da Omar, a kullum idan suna zaune da
Mama ba abinda take banda flashing mata back memories nata cikin ikon Allah Zeezee
ta soma tuna Mama da sauran 'yan uwanta anan ta gane Omar ma ashe yayanta ne. Duk
hakan yafaru ne within 3 weeks da Dr ya fad'a.

Yau tana zaune a parlour ita kad'ai chan Mama ta shigo d'aukan ruwa, binta da
kallo Zeezee tayi seda tazo gab da fita ta furta "Mama" a hankali. Wani dad'i sosai
Mama taji wanda ta kasa 6oyewa seda ta zubda k'walla.
"Mama, kece?" Ta tambaya Tana kallon cikin idanunta.
"Nice Mama na, Mama ce Zeezee" da gudu Zeezee ta miqe taje tayi hugging Mama tana
kuka sosai, itama haka Maman.
"I love you Mama, I love you so much."
"Ya Allah thanks for bringing back my daughter for me, I love you more
sweetheart."
"Ina Ya Ibraheem, Mariam, Omar and Yasmeen?"
"Duk suna nan kina son musu magana?"
"Eh Mama amman kafin nan ina Baba?"
"Kin manta inda Baba yaje Zeezee?"
"Wai yayi tafiya inji Ya Omar amman k'arya ne ko?" Kai Mama ta gyad'a mata a
hankali.
"Tell me ina yake toh?" Chan k'asa-k'asa tace;
"kin manta Baba lokaci yayi?"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Take idanunta suka sake kad'awa, "Mama
yanzu Baba ya tafi ban nemi tubansa ba kenan? Baze sake dawowa ba?"
"Zeezee Baba ya yafe miki" hak
kalamun da Baba yace ta fad'awa Zeezee Mama ta sake nanata mata su "kinji? Ya yafe
miki for a very long time now."
"Mama ba k'arya kike min bako?" Ta tambaya tana hawaye.
"Taya zan miki k'arya Zeezee? Babanki ya yafe miki komi, he asked me to tell you
in person and that he misses being with you."
"Nima na yafe masa Mama, I miss him so much" tasa kuka. "Shhh!" Mama tayi
hugging nata "he is in a better place in shaa Allah." Kuka Zeezee ta shiga yi
sosai, da k'yar Mama ta samu ta sata tayi shiru sannan tayi waya ta had'ata da
Ibraheem. Sosai Ibraheem yaji dad'in having his little sister back. Tubansa Zeezee
ta nema inda ya nuna mata ya yafe mata for a very long time now, haka Mariam and
Yasmeen ma.
Getting to 4 Omar ya dawo from work, tun a bakin k'ofa Zeezee ke jiransa. Tana
ganinsa ta mai oyoyo shima tare da neman tubansa, he can't ask for more his little
sister is back. Dr, Mama ta kira ta sanar dashi this great news.
"Semu godewa Allah gashi within three weeks d'in tayi getting back memories nata,
am so happy for you people."
"Thank you Dr, thank you so much."
"Allah k'ara mana lafiya gabad'aya."
"Ameen" ta amsa "se anjima mun gode."
"Yauwa sannu" yayi hanging.

***
Tun daga ranan Zeezee ta sake maida hankalinta kan ibadan ta sosai, a day never
goes by ba tare da tayi tunanin Babanta ba ta zubar da hawaye, kullum kuwa cikin
yimai addu'a ita da Mama suke. 2 weeks after samun sauk'in ta akayi rabiyar gado
inda magada suka samu d'imbin arzikin mahaifinsu. Dukansu sunyi amfani da kud'in
sunyi aikin lada dashi inda suke baran Allah ya kai ladan kabarin mahaifinsu. Banda
Zeezee data yi amfani da rabin kud'in gadon nata gabad'aya don tallafawa addinin
musulunci zallah. Saura takai masallatai da gidan maryu saura gidan television da
radio na yad'a muslinci da sunnan annabi. Inda tayi baran Allah da ya kai ladan
duka kabarin mahaifinta. Zeezee bata tunanin komi yanzu banda addinin ta,
mahaifinta da kuma Ya Al'ameen nata ko tunanin Adeel da Mama ta bata labari cewa ya
kawo cartons na Malt guda biyu a rasuwan Baba batayi saboda ta riga ta ciresa a
ranta kwata-kwata. Ya Al'ameen ne kawai a ranta.
Islamiyya tayi joining inda kullum take cikin nik'af da dogon hijabi saboda
batason ana gane mata fuska don har a yau tasan baza a rasa mutanen da zasu na
kwatanta taba da wacce tayi sanadiyar mutuwan mahaifinta. A takaice de Zeezee an
koma ga Allah.
Sau dayawa takan zuwa gidan Mariam ta kwaso Ramlah da Ummie suzo suyi mata
weekends, ba k'aramin son babies Zeezee ke ba yanzu musamman idan ta tuna ita
bazata iya haihuwa ba. Tsaf zatayi musu wanka ta shiryasu ta kaisu gidan kitso
kokuwa shopping suka zo kwana ma a d'akinta suke kwana. On working days kuma tun
safe zata tashi tayi shara tayi mopping ba aikin da Zeezee batayi wa Mama, har
wanki atimes. Kullum cikin sambad'a mata albarka Mama take tana cewa da Babanki na
nan he would have been damn proud of you.

***
Ta side na Adeel kuwa har yau ya kasa cire Zeezee daga ransa, da tunanin Zeezee
yake tashi ya sake yini. Rayuwarsa da Ruky sam ba dad'i. Acikin ikon Allah Ruky ta
sake samun wani cikin wanda a 5 weeks tayi 6ari komi ya 6antare, yanzu haka ma tana
gida. Adeel daga ya dawo daga aiki se zaman d'aki wane amarya ko kira yaji ya jikin
Ruky ma baiyi. Da yamma yau ya watsa ruwa ya shirya tsaf ya nufi unguwan su Zeezee,
gaba da gidansu kad'an ya faka sannan ya fito daga motar yana dube-dube wanda shi
kansa be san fa'idar yin hakan ba.
5:30pm su Zeezee suka taso daga islamiyya, cikin nik'af nata take takowa gida.
Don yadda Adeel ya mugun saninta daga tafiyar ta ma yagane itan ce sede he is still
doubting. Da sauri-sauri har yana neman cin tuntu6e ya tinkareta tare da yin
sallama. Wani irin mumunar fad'uwa gabanta yayi jin muryan Adeel, saboda a rayuwa
baza ta ta6a mancewa da muryanshi ba. Kasa d'aga kai ta kallesa tayi a yayinda
hawaye ke forming rapidly a idonta.
Gefensa tabi da wuri ta wucesa sede kafin tayi nisa ya sake shan gabanta.
Gefensan ta sake kuma bi wanda yanzu da sauri yayi blocking nata, d'ayan side nasa
ta koma zata bi, nan ma yayi blocking nata.
"Zeezee please answer me, koda bazaki min magana ba ki amsa sallama na." Har
anan takasa d'aga kai ta kallesa. "Zeezee bada wata manufa nazo miki ba, ta'aziyya
nakeson miki-" katse sa tayi da wuri, "naji nagode Allah ya bada lada, excuse me."
Ta fad'a a takaice.
"Zeezee please one more thing."
"Malam inba wai so kake na tara maka jama'a ba ka matsa min a gabana."
"Zeezee pl-"
"One..." ta shiga counting "two..."
"Am sorry" ya katse ta ganin how serious she is, "inhar hakan kikeso so be it but
kisani Zeezee I will never rest until kinyi forgiving d'ina I want you to know that
nayi regretting dukkanin abubuwan dana miki. Sharrin shaitaan ne ba komi ba
wallahi, I love you morethan I can ever explain Zeezee please forgive me. Wallahi
hak'k'in ki har a yau bina yake da Ruky, at first ta haihu d'an ba rai yanzu ta
sake miscarrying baby'n forgive us please."
"In don wannan ka d'ibo k'afafunka all the way here kasani ni na jima da yafe
muku abubuwan da kuka yimin. We are all human beings and not above making mistakes,
ni kaina me laifi ce, Allah ya yafe mana gabad'aya." Tayi maganan not looking at
him at all. Ba k'aramin burgesa kalamunta sukayi ba, "thank you Zeezee, thank you
so much I shall never forget this. You are indeed one of a kind, Allah saka miki da
mafificinsa, ameen." Ba tare da ta sake cewa dashi k'ala ba tabi gefensa ta fice.
Wani irin farin ciki ya tsinci kansa ciki atleast ya sauk'e wani abin, yanzu
tunanin ya zeyi ya dawo da ita gidansa yake. From yadda Zeezee ke acting yasan
it'll be hard for that to happen amman karkacaccen mind nasa se tunzirasa yake kan
lallai fa ya dawo da ita. Shigan Zeezee ciki kuwa bata nunawa Mama Adeel yazo
wajenta ba saboda bata ga amfanin hakan ba. Uniform nata ta tu6e taje ta samu Mama
a kitchen suka gama had'a dinner.

Washegari exactly time da Adeel yaga Zeezee jiya yau ma ya shirya yana jiranta.
5:35pm sega tanan, da wuri yaje ya sameta yana mata sallama sede ko sauraronsa
batayi ba, binta yake tayi har seda ta kusan isa gida sannann yasha gabanta.

*MIEMIEBEE👄. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
Page 54
*FEBRUARY, 2017*

"Zeezee please kiyi hak'uri ki saurareni, slap me, insult the hell out of me,
hit me anywhere you want and how but please don't shut me out. Wallahi Zeezee tun
rananda na sake ki na shiga wani gaggarimin yanayi, give your very own one last
chance please I beg of you, its all I ask."
"One last chance?" Ta d'ago kai tana kallonsa ta nik'af nata finally cike da
mamaki. "One last chance so you can maltreat me again? One last chance so ka sake
duka na? force me into bed? make me do yours and wife's laundry? cook for you?
sweep-" katse ta yayi da wuri "no, no please-" ya fad'a wane zeyi kuka.
"Then why? Saboda kana nunamin Ruky ta fini k'ima da daraja a idonka?"
"No Zeezee enough of that please, I want you back because I love you and miss
everything about you, your smile, fragrance, body, hair, everything about you. I
miss it."
"I should have guess, ko ka manta am of no use to you tunda bazan iya haihuwa ba
yanzu."
"I don't f*cking care Zeezee, all I want is you."
"You should have thought about that earlier kafin ka dakeni ka kuma buga min
saki biyu."
"Zeezee please! Cut it out. Meh kikeson in miki kigane cewa I've regretted every
single action of mine back then? In Ruky kikeson in saka I'll at this instant
because I don't love her, ke nakeso Zeezee please pity your very own."
"What I want? What I want is for you to f*cking stay away from me Adeel plus you
are nomore my very own, you never were. Bana k'aunar ka anymore Adeel ka riga ka
fitamin a rai na, bana sonka. You came to me jiya da sunan tuba na kake nema and I
did forgave you don't make me change my mind please."
"Zee-"
"I said go away!" Ta katse sa a tsawace.
"No Zeezee please listen to me, lets solve this out, Zeezee haka kikeson ki
k'arisa rayuwarki as bazawara? Bana son ganinki haka, you are worth than this."
"Am I? Baka son ganina a haka ka buga min saki biyu? Mschww! am running out of
patience just go away and never come back I don't ever need you in my life again."
"No, that's not true, you can't forget me this soon-"
"I can't?" Ta tambayesa "I was never in love with you Adeel, ko a da inma ba
sonka nake ba. I came to realise that I was just afraid of you, a monster. Ya
Al'ameen is the one I love and not you."
"That's not true Zeezee you still love me I know that please come back."
"Never."
"Haka kikeso ki cigaba da zama?"
"Koda hakan zan cigaba da zama meya maka zafi? Besides am going back to my truest
love Ya Al'ameen."

"No Zeezee please don't, karki tafi ki barni I beg you please. Kimin komi amman
karki koma gidan Maj- Gen."
"Give me one reason not to. Gidanshi zan koma I've made up my mind." Tana kaiwa
nan tabi gefensa zata fice da sauri ya rik'o hijabin ta stopping her. Chak ta
tsaya, kuka kawai taji ya fara kaman d'an yaro wanda itama tuni ya karya mata
zuciya ta soma kukan.
"Zeezee please" yayi pleading in a crying tone. "Please don't leave me" ya
k'arisa maganan yana sauk'a akan guiwowinsa a idanun jami'un da ke wucewa. "I beg
you please karki koma gun Ya Al'ameen come back to me and let me prove my love to
you one last chance, please Zeezee don't refuse my offer." Kuka ne sosai yaci
k'arfinta yadda words na Adeel ke getting to her. Tanayi yana yi, "let me go, ka
sakeni" kad'ai ta iya furta mai. Kai yake kad'awa still in the kneeling position.
"Zeezee please." Fincike hijabin nata tayi ta ruga ciki a guje tana kuka sosai. As
always Mama na kitchen taga wucewan Zeezee da gudu yau unlike always da zata tsaya
tayi mata sannu. Barin duk abinda takeyi tayi taje ta samu Zeezee dake baje akan
gado tana kuka me tsuma zuciya.
"Subhanallah!" Tayi exclaiming. "Ya da kuka haka? Meya faru?" Tayi maganan
hannunta manne akan bayan Zeezee data kasa koda d'ago kai har yanzu.
"Zeezee? Yi hak'uri ki amsa ni kinji? Meya faru?" Da k'yar ta iya tsagaita kukan
tace, "babu."
"Kamar ya babu kuma? Kina nufin haka kawai yau kika d'auro niyyan dawo min gida
da kuka?" Kanta ta d'ago finally tare da share rolling tears nata. "Babu an yi mana
wa'azi ne me ratsa jiki a islamiyya akan mutuwa se kawai na tuna da Baba."
"Allah sarki, in shaa Allah Babanku is in a better place kinji? Mu cigaba da
yimai addu'a yi hak'uri kukan ya isa haka Mamana."
"In shaa Allah Mama thank you."
"Tashi ki tu6e uniform d'in toh." Da nod da tayi wa Mama, Mama ta fice. Duk yadda
tayi don kawar da tunanin Adeel daga k'wak'walwarta ta kasa, haka ta kwana ranan da
tunaninsa.
Washegari kuwa ko zancen zuwa islamiyya Zeezee batayi wa Mama ba, pass 3pm Mama
ta shigota d'akinta, miqe kan gado ta tarar da ita tayi dunk'um tana tunani.
"Bade tunanin Baba kike ba yau ma?Zeezee shin wai sekin haifar wa kanki ciwon
zuciya sannan zaki huta? Da rasuwan Babanku sati nawa but kin kasa ki daidaita
rayuwarki, haba mana! Mutuwa da zafi amman ya zama dole ki hak'ura."
Tasowa tayi ta zauna "nifa ba tunanin Baba nake ba, ai kince in dena kuma ina
iya k'ok'ari na ganin na ragen."
"Toh me kike zaune yi haka tun d'azu? Tun da kika gama ayyukan ki ban sake jin
motsinki ba."

"Babu." Ta amsa blankly.


"Toh islamiyyan fa? Babu ne yau?"
"Akwai Bazan jeba ne" ((dalili kuwa shine bata son yau ma su sake had'uwa da
Adeel she is simply avoiding him.)
"Lafiya dai ko?"
"Lafiya" tayi faking smile.
"A'a ban san ki da haka bafa, gayamin mene"
"Allah babu Mama, bana jin dad'in jiki na ne."
"Kinsa tunani a gaba ba dole ba, bale ma I don't trust this silly excuse, gayamin
gaskian zancen meya hanaki zuwa islamiya yau? Keda baki ta6a fashi.l
"Mama babu."
"Zainab!"
"Na'am" ta amsa.
"Tell me, mene?"
"Mama..." sekuma tayi shiru. Isowa kusa da ita Mama tayi ta zauna a gefenta tare
da rik'o hannunta "gayamin kinji? Am here for you."
"Mama its Adeel" ta fad'a hawaye na forming rapidly a idanunta.
"Subhanallah! What about him?"
"Mama shekaran jiya yazo har nan bakin gate on my way back home daga islamiyya na
ganshi..." nan ta kwashe labarin komi tabawa Mama bata ragar da komi ba.
Ajiyar zuciya Mama ta sauk'e "ikon Allah! Ke yanzu me zuciyar ki ke raya miki?"
"Mama I don't know I've had enough of his torture, I don't need some more."
"Bakiya sonshi yanzu?" Kai ta gyad'a a hankali.
"Are you sure?" Sekuma ta kad'a kai da nufin a'a. "Mama its hard for me to admit
that bana son Adeel saboda he was my first love, I loved him with all that I've
got."
"I know Zeezee you must not repeat it again. Kina ganin ke ya tuba, tuban gaske?"
"He did Mama saboda he even knelt down in front of me, but it still isn't enough
compared to abubuwan dayamin da nake gidansa, Mama ban ta6a fad'a miki bane but har
forcing d'ina in to bed Adeel nayi, sometimes ma he'll be drunk and then sleep with
me forcefully" ta k'are maganan cikin kuka sosai. Hugging nata sosai Mama tayi cike
da tausayi. "Its okay Sweetheart baza ki komawa Adeel ba unless you want to kinji?
Kibar kukan haka." Kai tayi nodding "thank you Mama."
"Always dear, share hawayenki ki shirya islamiyya idan aka tashi zan sa Omar
yaje ya d'auko ki kinga ta hakan Adeel baze iya sake tsayar dake ba."
"Are you sure Mama?"
"I'm definitely am."

Ba tare da ta sake cewa uffan ba ta shirya tsaf ta wuce islamiyya. Sede yau ma
kaman jiya, bayan Omar ya d'aukota daga islamiya suka tarar da maroon Genesis G80'n
Adeel parked gaba da gidansu kad'an.
""Ya Omar gashi chan." Tayi stating ba nitsuwa a tattare da ita.
"Waye Zeezee?"
"Adeel, gashi chan don Allah do something." Tana idar da maganan sega Adeel yana
fitowa daga motarsa, ita se yau ma ta lura da bak'in da Adeel yayi.
"Go inside Omar" ya buk'aceta. Da sauri ta bud'e motan ta fita nan Adeel ya
shiga k'walla mata kira sam tayi kaman ba ita yake kira ba, tana kaiwa ciki tasa
lock. Juyawan da Adeel zeyi yaga Omar, although besan saba amman jikinsa na basa
wan Zeezee ne.
Hannu Adeel ya miqa masa sukayi sallama sannan Omar ya tambayesa purpose of
being here inshi.
"I know ba lallai bane ka sanni, I'm Adeel Zeezee's husband-"
"Ex husband" Omar yayi correcting nashi. Baki na 6ari yace, "yes ex husband, Yaya
please bikon Zeezee nake sonyi, ku yafemin ku dawo min da ita, I love her."
"Kasan kana sonta shine ka wulak'an tata ka buga mata saki bama d'aya ba har
biyu? Please Mallam pack your wahala and go bamu buk'atanka."
"Yaya please karka min haka, idan ita Zeezee yarinya tamin haka, kai babba be
kamata kamin haka ba kaima. Wallahi sharrin shaitaan ne I never meant to divorce
Zeezee believe me."
"Bazaka tafi ta ruwan sanyi bane sena sa an maka koran akuya?"
"Yaya please..." ya sake pleading. Ganin Omar na neman tara masa jama'a yasa
kawai ya tafi badon yana so.

Adeel be fasa zuwa gidansu Zeezee a kullum ba, infact he decided to make it a
hobby. A kullum kuwa idan yazo da Omar suke had'uwa dan kuwa Zeezee a mota Omar ke
barinta shi ya fito ya zazzage wa Adeel buhu-buhun rashin mutunci amman ba hakan
zaisa gobe yak'i zuwa ba. Akan Zeezee ya ajiye pride nasa a gefe, inhar ze sameta
he is ready to loss everything like everything. Kusan sati biyu Adeel ya jera yana
zuwa gidansu Zeezee kaman maye. Ruky Mama sede ta kallesa saboda ko maganan arziki
bayi had'asu don Adeel ya fita harkarta gabad'aya. In sunyi magana toh Ruky money
monger tazo kar6an kud'i ne, wanda da yak'i da ya so dole ya bata kokuwa ta b'oye
key'n motarsa. Yau ma kaman kullum yajesa gidan su Zeezee, bayan Omar ya korasa ya
dawo gida rai a dak'ule only to find the gate locked harda kwad'o. Danqaree! Ya
furta a ransa sannan ya shiga bubbuga k'ofan yana me sauk'e haushinsa akai. "Ruky!
Rukayya! Ina wannan bayerabiyar ta shiga? Mschww!" Ganin fa bata gida yasa ya zaro
wayansa daga aljihu a fusace ya shiga nemanta. Several missed calls yayi mata wanda
ciki ba wanda ta d'aga as tasa wayar a silent se bidirin biki suke sha.

*^GIDAN BIKI^*
Wak'an girgiza k'wank'waso ke tashi wane ze har6a zuciyan mutum. Ruky da friends
nata ne ke tsaye se rawa sukeyi, chan wata friend nata ta buk'aceta da sanin time,
anan ne Ruky ta zira hannu tare da zaro wayanta nan taci karo da 28 missed calls
from Baby. Tsuka taja sannan ta sanar da k'awarta ta.
"Toh ni nasan zaka dawo da wuri ne? Ina kullum se bayan Maghrib kake dawowa,
mschww!" Fita tayi zuwa less crowded area ta shiga Calling nasa back wanda tuni ya
d'aga kasancewar wayan na a hannunsa yana tsaye bakin gate d'in wane me maula.
"Ke mahaukaciyar ina ce? Gidan naki ne da zaki kama ki rufeni a waje?"
"Abeg Mallam free me oo, kai kanka ka fad'a ka ta6a dawowa gida at this time ne?
Base bayan Maghrib kake dawowa ba?"
"Aww! Ma abinda zaki ce kenan saboda bakida tarbiyya koh?"
"Ai gaskiya ne."
"Da izinin uban wa kika fita? Na baki izini ne?"
"Kaman ya kabani izini, baka gida izinin wa kakeso in tambaya?"
"Aww kuma bakisan ki kirani ki sanar dani a waya ba wato."
"Banida kati" ta amsa a takaice.
"Yanzu da bakinki kika kirani ai."
"K'awata ce ta samin."
"Whatever come back home this instant kizo ki bud'e min gidana."
"Gidan biki fa nake."
"Allah yasa gidan mutuwa kike ki dawo Ruky bana wasa dake."
"Gaskia nikam da sakel wallahi."
"Zan sa6a miki kina jina? Wallahi na baki 20 minutes." Ding yayi hanging. Doguwar
tsuka taja wane zata cire bakinta. "Allah ya sawaqa wallahi." Dai-dai nan isowar
friend inta kenan, "ahh! Ruky Mama ya ana bidiri ke kina anan?"
"Kibari kawai Mamx, Adeel ne wai ya dawo gida."
"Meaning?" Ta tambaya tana tauna chewing gum.
"Meaning na koma gida."
"Dalili?" Ta sake tanbaya.
"Nayi locking gida kafin na fito kuma ba key a gunsa."
"Yo! Bashida gidan friends da zasa kafin nan ne? Nifa banison tak'ura a rayuwa
wallahi shiyasa bazan iya zaman aure ba, shikenan mutum bashida 'yancin kansa se
abinda wani ya fad'a, mschw!"
"Kibari kawai Mamx kuma fa be ta6a dawowa gida war haka ba."
"Ke kinsan meh?" Kai Ruky ta kad'a "ki sharesa kawai, kibari se Maghrib ki koma
gida by then an gama duk abinda za'ayi anan."
"Ke bakisan Adeel da surutu bane wallahi."
"Ce mai zakiyi key'n motarki ta 6ace da k'yar kika samu."
"Amman fa kin kawo point wallahi, hakan za'ayi." Hi five sukayi sannan suka koma
ciki suka cigaba da karya kwankwaso.

Adeel har ya gaji da kiran Ruky Mama, gashi har tak'ara 15mins kan 20'n daya
bata amman bata dawo ba, wannan raini dame yayi kama? Cikin motansa ya koma yayi
zaman jirarta. Se chan 7:45pm ya hango wutan motarta yana nan zaune a motar har
yanzu. A nitse ta fito ta bud'e gate d'in sannan ta k'arisa gun motar nasa tayi
knocking bisa window, ko d'aga kai ya kalleta beyi ba, yin hakan sau biyu yasa ta
koma motar ta tashiga, tana cikin kunnawa Adeel yasa kai ya shige gidan sannan ya
jirata tayi locking kwad'o ta iso ta bud'e musu entrance door. Seda ta shiga yabi
bayanta, a parlour ya tarar da ita "sa'an wasanki ne niko?" Yayi snarling at her.
"Kaman ya sa'an wasa na kuma Adeel?" Binsa takeyi a hankali gudun ya hanata
kud'in kashewa.
"Bansani ba, minti nawa na baki kuma mintuna nawa kika k'ara akai?"
"Toh ka tsaya mana ka saurari dalili na. Key'n mota na ne ya 6ata a gidan bikin
da k'yar na samu."
"Da kin ganni sanye da pampers ne sekice min haka and expect me to believe you.
wallahi Ruky ki sani ba tsoronki nakeji ba just because ina d'aga miki k'afa ina
ganin bakida lafiya doesn't mean I can't beat you up, wallahi kinji na rantse idan
kika sake taka waje bada izini na ba Allah ya isa na as your husband na kanki, idan
kuma bakisan ma'anan hakan ba try it keda mahaliccinki." Yana kaiwa nan ya fice
zuwa d'aki inda ya hau tunanin Zeezee.

Doguwar tsuka ta bisa dashi, "wallahi k'aryanka ne" sekuma ta kad'a kai "ya zanyi
yanzu don Allah? Gobe dinner I can't miss it for the world, shi wannan Adeel yanada
problem wallahi, mazajen kowa na barinsu suyi yawo amman banda shi mschw wallahi
sa'an ka d'aya kafini gaskiya anan dana zaune kan cikinka." D'ayan d'akin ta nufa
ta canza kayan jikinta zuwa a light and simple one sannan ta fito ta nufa kitchen.
Spaghetti me rai da lafiya ta dafa tare da had'a mai mango juice sanin its his
favorite. A dining ta jera sannan ta koma d'akin data fito ta feffeshe jikinta da
turare tare da sake seducing shirin dake jikinta. D'akin nasa ta nufa inda ta tarar
da shi miqe bisa gado ya zura wa ceiling ido, ko bata tambaya ba tasan tunanin
Zeezee yake, ita tun tana kishi ma har ya zame mata jiki, Zeezeen ma ta dawo ita
batada case as long as zena bata kud'i ze kuma barta tana fita unguwa ba matsala.
Kan gadon ta k'arisa tare da hayewa ta end d'in da yake ta zauna.
"Baby" ta kirasa cikin wata tantiriyar murya. Ko kallonta ma beyi ba bale yasan
tanayi. "Haba! Baby am sorry don Allah." Nan ma banza da ita yayi.
"Baby yanzu bazaka d'ago ido ka kalleni bama? I said am sorry dagaske key'n mota
na ne ya 6ata kaima kasan bazan shanya ka haka kawai a bakin gate ba ai ko? Yi
hak'uri kaji I'm sorry."

Se anan ya juyo yana kallonta, sake bank'aro mai da k'irjinta tayi "tashi muje
kaci abinci dinner is ready."
"Kije kici bana jin yunwa" yayi maganan yana kawar da kallonsa daga gareta cause
he is not in the mood, tunanin ya ze dawo da Zeezee ne ke gabansa.
"Babe kaci lunch ne da zakace baka jin yunwa? Yi hak'uri muje I'll be the one to
feed you." Haka tayita lalla6asa seda ya tashin, bayan tayi serving nasa tace
zatayi feeding nasa sam yak'i shiwai shi zeci da kansa. Zama tayi gefensa se
daddad'un kalamu masu sanya sanyi a zuciya take tayi mai, chan da lokacin bacci
yayi ta sake d'aukan wani wankan tasa wasu arnan sleeping dress nata gata daman ba
kad'an ba. Shisshige mai ta rigayi daren ranan seda tayi turning nasa on. A ranan
ba k'aramin pleasure ta bawa Adeel ba. Da Asuba ta tashesa sukayi wanka sukayi
sallah and in the morning ta had'a mai breakfast tare da shiryasa for office. Suna
cikin karyawan ta kirasa a hankali yet romantically "Baby." Kaman baze amsa ba
yace, "meh?"
"Baby baka hak'ura ba har yanzu?" Yi yayi kaman be jita ba. "Na fa san kana
jina, me kakeso in sake maka domin ka hak'ura? Am sorry kaji?"
"Naji ya wuce."
"Meaning kayi hak'urin?" Nodding kai yayi mata "thank you Baby I love you." Nan
ma kai ya mata nodding "toh Baby kaja baya da Allah ya isan kenan daga kaina?"

"That's it" yayi exclaiming "ai dama nasan ba tsakani da Allah bane kike duka
wannan abubuwan nan da kikeyi."
"Allah tsakani da Allah ne please kaja baya da Allah ya isan yi hak'uri, bazan
sake fita ba seda izinin ka amman incase of state of emergencies kaga ya zama dole,
da Allah ya isanka a kaina kuma kaga ai da akwai matsala." Shiru yayi se cin
abincinsa yake "Baby ba zaka ce ka yafe ba? Me kakeso for lunch yau?" Kai ya d'ago
yana kallonta kaman bazeyi magana ba chan yace, "naji naja baya da batun Allah ya
isan, you are free."
"Yeyy! Thank you" nan da nan ta taimaka masa yagama breakfast, sa6anin kullum
yau har gun mota ta rakasa "Baby zan samu 5k please?"
"Again!" Yayi maganan yana tadda engine d'in motar. "Ke wai ATM machine kika
maida nine ko meh? Kullum cikin tambayan kud'i naga ko shi ATM machine d'inma wani
sa'in cewa yake ba kud'i."
"Haba mana don Allah bikin k'awata fa ake shikenan se ana yimata manni ni se in
tsaya ina kallonsu? Yi hak'uri please."
"Ruky banida kud'i kiyi hak'uri yau, dubu nawa na kashe miki tunda muka shiga
month d'innan?"
"Ni ba dogon surutu na buk'ata ba, zaka bani ne kokuwa a'a?"
"Kema kin amsa da kanki ai."
"Yama kyau wallahi" tana kaiwa nan tabar mai wajen "sekace ATM machine kullum
bani wannan bani wancan, bazan bada ba."
Itama a ciki se gunguni take tana zaginsa "wallahi ba abincin ranan da zan girka
da kai aikin banza kawai." Tuna tasan inda yake ajiye wasu kud'ad'ensa yasa ta saki
murmushi sannan ta nufi d'akin. Cikin pocket na wani suit nasa tasa hannnu ta zaro
d'imbin kud'ad'de, dubu goma ta zara ta miyar da sauran sannan nan da nan ta shirya
gidan biki abinta, dinner'n da se dare za'a soma amman dan neman yawo tun yanzu
zata ita.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com

Page 55
February, 2017

Yau ne kawai Adeel be jesa gidansu Zeezee ba, instead yaje sa gida gun Maminsa.
Bayan sun k'are cin lunch take tambayarsa ya rayuwa. Kai zallah ya kad'a mata.
"Wai kai da Ruky ne har yanzu?"
"Mami in kinayi wa Allah ki dena d'auko min zancen Bayerabiyar chan anytime we
are together."
"Toh Allah baka hak'uri meke damunka?"
"Zeezee, I want her back, for the past two weeks ina zuwa gidansu amman
brother'nta yak'i hak'ura ya barni inyo bikonta."
"Itan ta yarda zata dawo ma ne?"
"Bata yarda ba but I know she'll eventually."
"Uhm Auta nida zaka ji nawa da hak'ura da ita kawai-"
"I can't" yayi saurin katse ta. "I love her way much, I can't sacrifice her love
to anyone."
"Toh me kakeso ayi?"
"Kuje da Uncle kumin bikonta."
"Wannan abin kunya har ina? Despite yadda ka wulak'anta yarinyan nan."
"Kema haka zakice wato? Wai akwai wanda baya making mistake ne a duniyan nan? I
miss Daddy wallahi nasan da yana nan in an eye blink yamin abinda nakeso, kar kujen
zan cigaba da trying luck d'ina har sena samu na shawo kanta da family'nta."
"Me yayi zafi kake magana haka Auta? Sanin kanka ne ina sonka sosai-"
"Shine bazaki iya zuwa kiyi ma Mom na Zeezee magana ba?" Ya katse ta. "Ina love
anan?"
"Abinda kakeso kenan?" Gira ya d'age mata. "Toh shikenan Allah shi kaimu gobe
zanyi ma Baffan naka magana."
"Yauwa ko kefa Mami? Thank you kinji?"
"Ba komai amman Allah ka dena min magana gatsau-gatsau haka, uwarka ce nifa ko
dan bani dukan ka ne?"
"LOL duka fa kikace Mami? Wuce nan ai yanzu." Yi tayi kaman zata maresa take ya
miqe daga kan kujeran tare da jan baya, "toh ni zan koma gida se goben."
"Toh Allah kaimu ka gaishe da Ruky."
"Ki kirata ku gaisa ni bazan gaisheta ba."
"Heh! Su Auta manya" yana murmushi ya fice se bayan Maghrib ya dawo gida a
lokacin Ruky na gida tana shirye shiryen fita dinner.

"Har ka dawo ne?" Tayi maganan tana jawo k'ofan d'akinta.


"A'a ina hanya ne" ya amsata ba tare da ya kalleta ba.
"Toh ni na tafi" bece mata k'ala ba taja motarta ta fice. Chan getting to 10
Adeel ya shiga d'akinsa tare da d'auko suit dayake saving kud'ad'ensa. Zaro su duka
yayi ya irga sede a maimakon yaga 100k se 90k yake gani, sau uku yake irgawa amman
ba gomansa. Danqaree! Aiko ba 6era suke dashi ba bale ace su suka cinye goman, kuma
he is adamant be zare ko d'ari ba daga cikin d'arin how comes?
"Ruky! Ruky sata ta fara min? Kut! Allah dawo dake gida wallahi zaki yaba wa aya
zak'inta." Bacci yakeji amman yak'iyi yana jiran dawowan Ruky. Se pass 11 ta dawo
gida all exhausted so kawai take ta kwanta. Tana stepping foot nata a parlour Adeel
ya jefa mata tambaya, "ina kud'i na? B'arauniya."

"Kamar ya kuma kud'inka? Ka bani ajiya ne? Kuma ka dena cemin b'arauniya."
"Na k'ara b'arauniya kawai! Zan k'arisa gun in goga wannan bakin naki a k'asa
wallahi, ina kika kaimin 10k d'ina?"
"Ni ban d'auka ba" ta fad'a tana cire goggoron dake kanta. "Se kinji na jaki
sannan zakiyi magana? Ina yake? Ko sena gayawa Babanki kin fara min d'auke-d'auke
tukun?"
"Toh ai laifinka ne, I asked you nicely kak'i bani ba dole nayi following other
alternative ba."
"Ohh is that so? Nasan maganinki wallahi bake ba allowances daga nan zuwa next
two months. Wani irin rayuwa ne wannan? Zeezee dako k'wandala bayi had'a ni da ita,
she never once stole from me. What kind of a woman are you? Mark me, kinyi na farko
kinyi na k'arshe kenan wallahi." Baki ta murgud'a mai "kada ka bayar d'in" ta fad'a
a lokacin da ya shige d'akinsa. "Barka na d'an rage wasu canjin anan."

_Washegari. Gidan Lt Alhj Isma'eel Yusouf._


Zaune Mama da Omar suke a tsakar gida inda suka jiyo sallaman babban mutum daga
waje. Sauri Mama tayi ta koma ciki sannan Omar ya amsa, bak'in fuska ya tarar sede
kallo d'aya yayi wa Mami yagano mahaifiyar Adeel ce, yana kan wannan nazari ne yaga
Adeel biye a bayanta. Welcoming nasu yayi suka wuce parlour suka zazzauna bayan
gaisuwa suka yimai ta'aziyya sannan suka fayyace mai purpose na zuwansu inda Mami
ta buk'aci Omar daya kaita gun Mama tana son yimata magana. Se kallace-kallace
Adeel ke ko zega Zeezee not knowing bata gida taje ta gidan Adda Mariam. Ba musu
Omar ya kaita gun Mama sannan ya dawo ya samu Adeel da Baffansa. Hak'uri suka yita
bawa Omar inda Baffan Adeel ke sake jaddada masa batun nadaman da Adeel yayi and
how bad he wants Zeezee back, achan ciki ma abinda Mami keyi kenan. At last Mama da
Omar suka ce musu hakan ba damuwa bane zasuyi wa Zeezee magana idan har ta amince
she wants to go back so be it, if not kuma they can't force her. Godiya sosai Mami
sukayi sannan Omar yayi musu rakiya kasancewar Mama bata gama zaman takabarta ba
har yanzun.

Ko cikakken minti d'aya da tafiyansu Adeel beyi ba Zeezee ta dawo, bayan tayi
parking motarta ta fito ta k'arisa ciki tare da yima su Mama sannu inda sukeyi mata
sannu da zuwa.
"Suwa suka zo Mama? Naga wani mota yabar gidan nan just now." Kallon Omar Mama
tayi sannan back to Zeezee "zoki zauna kinji." Ba gardama ta zaunan, "Adeel, Mom
and Uncle nasa ne sukazo Zeezee."
"Me suka zo yi?"
"Sunzo bikon ki" nan Mama ta zana mata yadda komi ya faru "so mu duk abinda
kikeso shi zamuyi miki, in har kinga zaki iya komawa Adeel fine if not kuma a yanzu
Omar na kiran Uncle nasan ya sanar dashi." Shiru tayi a yayinda hawaye ke forming
rapidly a idonta. "Ko kina neman time to think?" Kai ta kad'a "Mama I don't need to
think bana buk'atan Adeel a rayuwa na again, I've had enough."
"I know Sweetheart amman still zan baki daga nan zuwa gobe kiyi making up mind
naki kinji? Tashi kije you are free."
"Nagode Mama, nagode Ya Omar Adda Mariam tace in gaishe daku."
"Toh muna amsawa" Mama ta amsa, nan Zeezee ta fice. D'akinta ta nufa tare da
bajewa kan gado inda ta fad'a kogin tunani, gabad'aya she is lost bata san me
zatayi ba. Lubiee her only adviser ta kira bayan gaisuwa take sanrar da ita halin
da take ciki.
"Haba Babe! Yanzu har sekin tambayen shawara regarding wannan matter? I thought
you've had enough, me zaki sakeyi da Adeel? Although nasan abu me kyau ne a sasanta
amman what Adeel did you is unforgettable, kodan yadda kika nuna kinfi sonsa fiye
da parents naki kad'ai ya isa ace baze ta6a wulak'anta ki ba, but he did it
anyway."
"Yes Lubiee nima ba son in koma masa nake ba."
"But you still love him don't you?"
"I will be lying if to say no kema kinsan he was my first love."
"I know Babe, but please karki koma masa in shaa Allahu Allah ze kawo miki wanda
ya fisa kinji? Have faith in faith."
"Yes Babe thank you."
"Always barin gudu muna da exams gobe."
"Toh success" anan ta katse. Wahsegari da Asubah bayan sallah Mama tashigo ta
d'akin Zeezee, bayan sun gaisa take tambayar ta have she made up her mind.
"Mama ku kirasu ku ce musu suyi hak'uri don ni bazan sake komawa Adeel ba."
"Are you sure this is what your heart wants?"
"Yes Mama."
"Amman Zeezee ai Adeel ya tuba naga, kuma ke haka kikeso kiyita zama,
mahaifiyarki na zaman zawarci kema haka?"
"Mama please don't talk like that, I believe one day Ya Al'ameen ze dawo min."
"Hmm idan beyi aure ba kenan."
"Ko da matansa uku ne inhar he is willing ya cikata dani in zama ta hud'u I'll
accept his marriage Mama because I love him so much."

"Zeezee bana son kizo kiyi 2-0."


"Mama please..."
"Shikenan zan yima Omar magana ya sanar dasu final decision naki ko?" Kai ta
gyad'a "good" cewar Mama. "Amman Zeezee just because you're holding on to the
feeling that Ya Al'ameen ze sake dawo miki hakan baze sa kina shutting bak'in da
suke zuwa miki ba, banason k'arama dake jikin ki ya saba da zaman haka, d'akinki
shine k'ima da darajar ki kinji?"
"Naji Mama."
"Wanda keda nistuwa ya fara zuwa ta wajen yayanki Omar semu basa dama muga iya
gudun ruwansa in ya dace a had'aku walillahil hamd ke bakison ki koma d'akinki ne?"
"Ina so Mama."
"Yauwa 'yar albarka tashi ki koma bacci."
"No ban gama azkhar ina ba tukun. "
"Toh se zuwa safen."

A yau d'in bayan sallan Azahar Omar ya kira Baffan Adeel inda ya sanar dashi
final decision da Zeezee ta yanke tare da basu hak'uri. Sosai Baffa ya fahimce shi
ya kuma mai godiya sannan yayi hanging wayar. Mami ya soma kira ya sanar da ita,
rasa yadda zata fara breaking wagga news wa Adeel tayi inda ta buk'aci Baffa da
yayi hak'uri shi ya fad'a ma shi Adeel d'in. Adeel na zaune a office wayarsa ya
shiga ruri ganin 'Uncle A' yayi saurin picking.
"Hello Uncle?"
"Na'am Adeel kana ina ne?"
"Office." Ya amsa.
"Toh ba dan komi na kiraka ba illa don in jaddada maka outcome da muka samu,
kasani kowani musulmi da k'addararsa a rayuwa kuma idan Allah ya aza wa mutum so
ake ya danne zuciyarsa yayi accepting ya kuma dage da addu'a Allah fito mai da
alkhairi daga hakan kana jina?" Jikinsa ne yayi sanyi matuk'a, "Uncle just tell me
tace she isn't coming back huh?"
"Eh Adeel kayi hak'uri, we can't force her."
"Shikenan nagode." Nan ya katse wayar, jakansa kawai ya d'aga ya fice. He can't
bear the thought Zeezee is gone forever bazata sake dawo mishi ba, why didn't he
ever appreciate her time da take nan seda ta tafi? its true indeed that we don't
know the value of what we have until we loss them. Bar (gidan sai da giya) kawai ya
nufa inda yaje ya bugu iya buguwa. Be tashi dawowa gida ba se quarter to 9pm.
Alokacin Ruky na kallon series abinta. Se buga k'ofan Adeel ke gbam! Gbam! Gbam
wane ze b'alla shi daga hinges nasa. "Ina zuwa mana Adeel ka tsaya mana ha'a! 6alla
k'ofar zaka yi ne?" Bubbugawan ya cigaba dayi har seda ta bud'en. Bankad'eta yayi
ya wuce inda tajiyo warin barasan dake tashi daga jikinsa.

"Adeel!" Ta kira sunansa cike da mamaki. "Me nake shirin gani? Dama kana shaye-
shaye ne?" Jajayen idanunsa ya d'ago yana kallonta nan fa ta shiga tsoro, "wallahi
idan baki ja bakin ki kin rufe ba zan kashe ki this instant in huta, tunda na rasa
Zeezee kowa ma yana iya mutuwa."
Kum! taja bakinta tayi shiru sanin yaufa ba a cikin hankalinsa yake ba. Sid'ak
sid'ak ta wuce d'akinta tasa lock kallon ma ta yafe, kwanciyarta tayi inda shima
Adeel d'in a parlour bacci ya sacesa. Cikin bacci amman se name na Zeezee yake ta
furtawa.
Asuban fari ya tashi da wata masifaffiyar ciwon kai, lalla6awa yayi yayi Sallah
sannan ya koma ya kwanta se 9:44am ya tashi ya karya ko k'ala be had'asa da Ruky
ba. Seda yazo fita take tambayarsa ina zasa.
"Ina ruwanki da inda zani? Ke kike ajiye ni ne?"
"Mallam daga tambaya? I beg free me o, just cause Zeezee tace bazata dawo gareka
ba doesn't mean zaka na sauk'e min fushinka akaina, ehe!"
"Kina magana ne?" Yayi snarling at her, shiru tayi seda taji ya bud'e k'ofa
tace, "baka bada kud'in cefane ba in ka dawo baka tarar da girki ba don't blame
me."
"Karki girkan mschww." Yawonsa ya fice ranan instead of office, da yamma wajajen
k'arfe 5:40pm ya nufi unuguwan su Zeezee one last time yaji daga bakinta bazata
koma masa ba ko ze samu sukuni dan har yanzu ya kasa yarda.

Yau wai acewarsu Mama tunda an riga an sanar dasu Adeel Zeezee aiint going back
to them ai shima baze sake tako k'afansa nan ba, with this thought Omar beje d'auko
Zeezee daga islamiyya ba ta tako da kanta. Achan wani corner Adeel yayi parking
motarsa sannan ya tako zuwa kusa da gidan su Zeezee tare da yin tsaye, tun daga
nesa yake hangenta se dab data kusa shiga gida ya fito da wuri tare da sa mata
kira. Chak ta tsaya jin muryan Adeel kafin tace zata bud'e k'ofa ta gudu ciki kuma
har ya sha gabanta. Hannunta yaja seda ta fad'a jikinsa. Sa'an su d'aya ba mutanen
dake wucewa sosai, shuresa ta shiga yi, "Adeel let me go ka sakeni meh haka?" Sake
matse ta yayi a jikinsa "Zeezee please stop fighting it and just listen to my
heartbeat, just listen to how much it's beating for you. Wallahi I can't do without
you, hit me all you can, slap me but please karki ce bazaki dawo gida na ba. I'm
truly sorry for maltreating you, I shouldn't have done that kiyi hak'uri please ki
dawo I love you so much."
Kukan itama ta rushe dashi jin yadda shima yakeyi, bar kai masa bugin tayi. Tana
kuka yana yi, there's no denying tasan tana son Adeel but that is still not enough
reason for her to go back to him, she have to be strong for herself. Sun d'au
tsawon lokaci ahaka sannan da k'yar ta samu ya saketa tare da d'ago face nata yana
goge mata dangling tears nata. "I love you Zainab, I love you so much wallahi."
"What do you want Adeel?" Ta furta tana sauk'e hannayensa daga kan fuskartan.
"I want you back Zeezee, I really do."
"Why?" ta sake tambayarsa.
"Because I miss you, I miss being with my lady."
"Mami bata sanar dakai decision d'ina bane?"
"Uncle did, but ban yarda ba Zeezee, I know bazaki min haka ba cause you love me
just as much as I do love you, we are meant to be Zeezee please don't say no and
come back to me. In gidanki kikeso in canza miki so be it, I just want to make you
happy one last time."
"You know what will make me happy once more?" Kai ya kad'a "idan kadena bothering
d'ina ka fita daga harkata gabad'aya."
"Zeezee thats not possible because I love you, I can't."
"Just stick it to your head and mind that am gone forever and not coming back to
you Adeel." Kai ya shiga kad'awa continuously. "Please don't say that, I really do
want you back, Zeezee wallahi nayi nadaman aikata duka abubuwan da na miki, if only
'I'm sorry' can bring us back the way we use to be, give me one last chance please
to prove my love to you."

"No Adeel please stop making this hard on ourselves. Idan har abinda ya kawo ka
nan don kaji daga bakina final decision d'ina ne so be it, bana sonka anymore
Adeel, bana buk'atarka a rayuwa na anymore, koda kai ne autan maza na yafe ka, da
in koma gidanka na gommaci mutuwa na, I don't love you okay?" Kuka take sosai take
wannan magana saboda how difficult it is for her to admit that bata son Adeel.
"I've once loved you but not anymore, they say first love never dies and na
yarda da hakan saboda har yanzu kana da gurbi a zuciya na Adeel, na maka son da ban
ta6a yima wani mahaluk'i a duniyan nan ba, na fifita ka akan iyaye na, I could die
for you but not anymore, I'm hoping that one day Allah ze had'a ni da true love da
ze ya burying first love da nake maka. Inhar kana sona, zaka so yimin abinda nake
so by simply staying away from me" Hanky yasa ya share hawayensa sannan a hankali
yace "me kikeso Zeezee? Tell me and zan miki shi saboda ina son kisan just how much
I love you."
"I want you out of my life Adeel, bana son sake ganinka, I want you to forget
that you've ever had Zeezee in your life and move on."
"Shikenan Zeezee, I'll try as much to get out of your life dukda nasan hakan abu
ne mai wuya but tunda abinda kikeso kenan zan miki. I just want you to know that no
matter how distant you are away from me, your heart is always here with me." yayi
nuni da zuciyanshi. "Kuma I want you to know that I'll die loving you. Farewell
Zainab, I pray Allah ya had'aki da farin cikinki kema, nikuma ya bani ikon iya jure
rashin ki, I love you so much and thank you for once loving me." Mugun
uncontrollable kuka ne yafi k'arfinta da irin heart melting words d'innan. Kaman
kayan wanki tayi tsaye wajen tana aikin kuka, the next abinda tayi noticing is how
Adeel yajata da hannu tare da shigar da ita cikin gidan nasu, before tayi
comprehending wani abu taji lips nasa akan nata. Kissing nata yake hungrily yet
passionately, k'in basa access tayi se hawaye kawai take tana beating against his
chest da duk wani k'arfin ta. Shiko ya kasa hak'ura abubuwa da dama yayita mata har
seda tayi gasping anan yayi using opportunity'n yayi owning lips nata fully, tun
tana k'in basa had'in kai daga baya daya gama kashe mata jiki lik'is ta soma moving
in sync with his move. Sun d'au tsawon lokaci suna abu d'aya sannan a hankali ya
saketa, lasan swollen lips nata tayi tare da miyar dasu ciki tana me cigaba da
kukan.
"I will forever love you Zainab" yace da ita yana kallonta. Gudu kawai tasa ta
shige ciki se d'akinta ta nufa tasa lock tare da wurgi da kanta bisa gado tana
kukan cire rai, hanneyenta rik'e da kanta se juyi akan gadon take. Shima Adeel
tsaye yayi wajen yana tsiyayar da hawaye sannan daga bisani ya fita ya koma cikin
motarsa guiwa ba k'wari. Kuka sosai ya shigayi cikin motar, ba Zeezee rayuwarsa
bata da wata ma'ana again. What else does he have to live for? His advice to all
mankind is to appreciate what they HAVE before life makes them appreciate what they
HAD verily nothing last forever, after all the life itself is temporary.

****
"Zeezee! Ki bud'e k'ofar mana sekin sa min hawan jini ne tukuna?" Har anan se
sautin kukan Zeezee kawai takeji. "Zeezee please upon up."
"Mama am sorry please go away I need to be alone, kiyi hak'uri don Allah."
"Zeezee bazan iya barinki haka ba ki tashi ki bud'emin ko sena yi kuka tukuna."
"No Mama I beg of you dan Allah kiyi hak'urri ki tafi." Ta k'are maganan tana
jan hanci. K'in tafiya Mama tayi har seda Zeezee ta taso ta bud'e mata don dolenta.
Fad'awa jikin Mama tayi tana kuka me tsuma zuciya. A sannu a sannu Mama ta k'arisa
da ita cikin d'akin tare da zaunar da ita bisa kan gado.
"I'm here for you, I've gotchu." Kuka tayita yi Mama na bata hak'uri tana
soothing nata. Se chan ta tsagaita kukan. "Can you tell me what happened?" Kai
zallah take kad'awa nufin no, "remember am here for you kinji? Tell me meya faru?
Keda Mallamin islamiyyan ku ne?" Kai kawai ta kad'a mata. "Then who?"
"Adeel Mama."
"Again? Meya faru kuma? Kina son ki koma mishi ne?"
"Mama he left just now, Adeel ya tuba kuma yana son in koma mishi he kept on
crying like a baby yana gayamin how much he wants me back. Yadda yake kuka nima ya
sani Mama."
"Shhh! all shall be well kinji? Bar kukan haka."
"Mama I love Adeel also."
"I know Zeezee kiyi hak'uri ki danne zuciyarki ki koma mishi nasan yayi nadama
tunda abinda zuciyarki keso kenan."
"I can't Mama, d'akin Ya Al'ameen nakeso-" katse ta Mama tayi "Zeezee bamu san ko
Al'ameen ya sake aure ba or not we don't even know either Mamanshi zata bari ki
koma masa."
"I still don't care Mama shi nakeso gareshi kuma zan koma."
"Allah sa hakan yafi alkhairi toh."
"Ameen Mama nagode."
"Ki huta kinji? Kukan ya isa."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
5⃣6⃣

_For all the love and support you've shown to my special soul AUNTY SIS, for all
the hardships you've been through and still didn't give up on her, AUNTY SIS wants
to show her deepest appreciation to y'all. This page is yours members of THE TEAM._

Tun daga ranan da Adeel yaji daga bakin Zeezee da kuma kunnuwansa kan ta
tafi bazata sake dawo masa ba, he can't ever have her back ya miyar da life nasa
useless. Ba aikinsa sede kullum yaje bar and get himself drunk, aikin office ma ya
yanke zuwa ba kuma wai ya tura musu notice bane, Mami tayi surutu har ta gaji.
Sa'an sa d'aya, Boss nashi was once a friend to his Dad if not da tuni yayi firing
nashi.
Ruky kam kullum cikin habaici da zaginsa take musamman ma idan ta tuna da about
2weeks kenan yanzu ya yanke mata weekly allowances nata. Sam ba jituwa a tsakaninsu
kullum cikin tashin hankali sekace Tom and Jerry. Adeel bema aza Ruky aka ba ko
zaginsa take sede ya saurareta ya kad'a kai saboda rashin Zeezee kad'ai ya ishesa
damuwa, da haka fa Adeel ya soma neman mata amman bawai fasik'anci yake dasu ba
sede yayi dating nasu suci mai kud'i ahaka har suka dace da wata 'yan mata wanda a
birthday'n wata cousin nasa suka had'u da ita, abu kaman wasa-wasa Adeel idan ya
fita tun safe se kusan goman dare ko sha d'aya ya dawo as kullum yana cikin
partying. Office daya koma ma ba kullum yake zuwa ba, sosai staying late nashi ya
soma damun Ruky, she can't remember when last ma abu ya shiga tsakaninta da Adeel,
she needs her husband atleast. Yau ma as always se 10:56pm Adeel ya bugo Genesis
nasa ya dawo gida, alokacin Ruky na tsaye a parlour tana jiransa tana sanye ne da
free size rigan bancinta riga da wando. Yana bud'e k'ofan sega tanan tsaye, tsuka
yaja sannan ya maida k'ofan ya rufe.

"Adeel!" Ta kirasa in a serious tone.


"Lafiya?" Ya amsa in an I dont care tone.
"Daga ina kake?"
"Daga k'aniyan ki nake, mschw! Ina ruwanki da inda naje? Wake ajiye wani tsakani
na dake?"
"Ba abinda na tambaya ba kenan daga ina kake nace?"
"So kike kiji? Daga french party'n friend d'ina, aikin banza kawai!"
"Party? Ko kunya baka ji ba? Da aurenka kake zuwa party?"
"Kunya? Sata nayi? Da da muke zuwa taren ba auren Zeezee a kaina ne?"
"Zeezee kace nikuwa Ruky Mama ce, ita taga zata iya nide wallahi ba'a gidana ba,
ba yadda za'ayi ka fita chan kana partying nikuma ka barni da yima gadi, wai bama
wannan ba rabonka da kabani hak'k'i na since when?"
"LOL. Ai seki fito fili kice Adeel I need you bawai ki tsaya kina bin long
process ba."
"Wait, wait tsaya Mallam karka kuskura wallahi koda wasa, kace zaka soma kula
matan wajen nan don wallahi bazan yarda ba."
"Zeezee ma ta hak'ura bale ke d'in banza, kin gadama kada kiyi mschw!" Yana
kaiwa nan ya nufi d'akinsa.
"Adeel baka sanni bane wallahi baka san Ruky Mama ba" tace da kanta, "idan
Zeezee ta barka kasani Ruky baza ta barka ba, mu zuba mu gani." Rai a dak'ule ta
wuce d'akinta. Washegari Ruky ta kira wata friend nata party rocker akan tayo mata
bincike either dagaske Adeel nada girlfriend a waje or not.
"I've got this Babe karki damu."
"Yauwa Ammatas thank you." Ahaka sukayi sallama. Tun safe as always yauma ya
shirya ya fita, da yamma friend na Ruky tayi calling nata back inda take jaddada
mata cewa yes its true Adeel is currently dating wata Babe sunanta Nusaiba amman da
Nusee ake kirarta.
"Babe are you serious please?" Ruky tayi maganan cike da k'in yarda.
"Wallahi, ko jiya ma sunje wani French Party da ita." Nan Ruky ta sake gaskata
zancen saboda Adeel da bakinsa jiya ya gaya mata daga French party yake.
"Thank you Ammatas, aikin ki yayi kyau."
"Take it easy Babe na sanki."
"Wani irin easy? Barni dashi."

Da goshin Maghrib Adeel ya dawo gida yau unlike yadda ya saba, Ruky na kallonsa
ya wuce d'akinsa seda ta tabbata ya shiga bayi ta bi bayansa, jin alaman gudun ruwa
ta tabbata wanka yake, hakan yasa ta k'arisa ciki ta d'au wayarsa, unluckily ta
samu yasa lock na pattern. Dabara ce ta fad'o mata ta lak'uta vaseline kad'an ta
shafa kan screen d'in yadda da zaran ya zana pattern d'in design d'in ze fito. Fita
tayi da sauri jin ya kashe tap d'in. Anan ta la6e bakin k'ofa tana kallonsa. Kaya
yasa me kyau ya feffeshe jikinsa da turare, duk anan kallonsa take seda taga ya
d'aga wayansa ya bud'e sannan ta fad'a d'akin da sauri stopping him from what he is
about doing.

"Lafiya? Zaki fad'o min d'aki ba sallama?"


"Baby wallahi tsaka! Tsaka a parlour."
"Mschww! Shine me?"
"Baby please ka kashe wallahi bana son abin ko kad'an."
"Ni dake waya yi kalan zefi wani iya kashe tsaka? Abeg fita min daga d'aki."
Isowa tayi har gabansa a maraice "Baby please kayi hak'uri ka kashe min, Allah
banason abin" Kallonta ya tsaya yi yana nazari nan ta samu daman amshe wayan nasa a
nitse "please Baby."
"Yana ina?" Ya tambayeta yana mata mugun kallo.
"A parlour Baby."
"Muje."
"Kayi hak'uri kaje kai d'aya wallahi tsoro nakeji."
"You are not serious, nasan ta inda yake ne da zakice inje ni kad'ai?"
"Ta wajen 2 seater." One more look yayi mata sannan ya fice nan ta rufe wayar
nasa nan pattern daya bi ya zana yayi unlocking wayar nasa ya bayyana. Bi tayi ta
zana and luckily ya bud'u, rufewa tayi ta sake gwadawa, biro taja da wuri cikin
drawer ta zana pattern d'in a hannunta. Tana cikin yi tajiyo kiran Adeel "Ruky!
Ruky!"
"Na'am Baby" Tayi maganan tana miyar da pen d'in. "Zo!" ya buk'aceta. Kaman
dagaske ta fice tana wani kaffa-kaffa irin tana tsoron nan.
"Ina tsaka yake anan?"
"Allah akwai Baby ka duba da kyau."
"Kinsan ba d'anki bane ni da zakina min wasa da hankali ko?"
"Baby dagaske ba wasa da hankali nake maka ba, I saw it se inde ya gudu ne."
"Mschww!" yaja tsuka tare da yasar da broom dake hannunsan ya koma d'aki. Binsa
tayi da harara "bari in tabbatar da zargina zaka sani." Within two minutes ya fito
tsaf ba k'aramin shigansa shirin yayi ba. "Baby ina zaka je?" Tayi maganan tsaye a
dining area.
"Fita zanyi kinada case ne?"
"A'a wani irin case kuma? nace ko zakaci diner before going out."
"Basshi bana jin yunwa."
"Haba mana Baby se inyi ma girki kace kuma bazaka ci ba?"
"Ruky" ya kirata yana me k'ura mata ido tare da examining nata.
"Na'am Baby." Ta amsa cikin sanyin murya.
"Stop baby'ing me and tell me what you are upto I know you."
"Kaman ya kuma Baby?"
"Inma kud'i kikeso ki kwantar da hankalinki kisa shi a ruwan sanyi bazaki samu ba
dan har yanzu ban sauk'o daga satan da kika min ba."
"Yanzu Baby ni shikenan ban isa inyi maka abu ba sekace dan kud'i nakeyi?"
"Ai halinki ne money monger kawai."
"Toh ni ba masifa nakeso ba abinci ne na girka maka kazo kaci."
"Banaso."
"Please mana" tayi maganan moving closer to him, hannunsa ta d'aga ta had'a da
nata tana murzawa pleasurably "zo muje kaci I'll be the one to feed you." Zeyi
magana tayi saurin katsesa, "don't say no please." A nitse tajasa zuwa dining table
d'in tare da ja mai kujera ya zauna nan ta iba masa a plate sannan ta shiga feeding
nasa. Suna gamawa ya miqe "toh ni zan fita."
"Seka dawo Baby, Allah ya tsare."
"Ameen" har ya fita sekuma ya dawo ya ajiye mata 2k akan table d'in.
"Name wannan kuma?" Ta tambaya as if bata buk'ata.
"Kisa kati a wayanki."
"Baby you don't have to inada kati a wayana."
"Ki d'auka banason dogon surutu, mutum yana so yana kaiwa kasuwa." Ignoring what
he said tace;
"Toh nagode, I love you." Kai kawai ya mata nodding sannan ya fice.

****
Duk irin baccin dake tak'ura mata ranan tak'i yi ta zauna jiran dawowan Adeel.
Wani arnen sleeping dress dake exposing jikinta gabad'aya ne a jikinta, tasha
kwalya sosai se k'amshi ke tashi daga jikinta. Kamar mayya tak'i bacci se to 12am
tajiyo shigowan Adeel, nan ta koma ciki ta sake feffeshewa da turare sannan tazo ta
bud'e k'ofar alokacin da yake k'ok'arin bud'e wa shima.
"Wow!" Yayi exclaiming a bit scared. "Ruky?"
"Na'am Baby welcome back" tayi maganan tana matsa mishi don ya wuce, mamaki ne ya
cikasa yayi tsaye wajen.
"Ka shigo mana kar sauro su cika mana ciki." Bayan ya shigo ya tambayeta "me kike
bakiyi bacci ba har yanzu?"
"Jiranka nake, na kasa bacci." Se yanzu ma ya k'are ma face and body nata kallo
"wannan kwalyan fah?"
"Kaman ya kuma? Naka ne mana, muje na had'a maka ruwan wanka." Kallonta yake har
yanzu cike da mamaki. Haka ta jasa d'aki ta miqa mai towel tare da zaman jiransa.
Wayansa ta shiga nema kafin ya fito amman ta rasa da alama ya shiga bayin dashi,
hakan ba k'aramin haushi ya bata ba. Bayan ya fito ta mai grabbing pajamas nasa
yasa.

"Zaka ci abinci?"
"No I'm full" yayi maganan yana mik'ewa akan gado. "In kin fita ki kashe min
wutan."
"Anan zan kwana."
"Tooohhh, d'akin kifa?"
"Adeel I miss you can't you get it? I want my husband."
"Koba husband ba" yayi maganan can k'asa-k'asa yana daidaita pillonsa tare da
juya mata baya. Kashe wutan d'akin tayi tare da hayewa gadon "wai me zakiyi min a
d'aki ne?" Ya tambaya finally.
"Kabani hak'k'i na ni kawai."
"Kinga am stressed out bacci nakeji ba abinda zan iya baki." Mak'irin murmushi ta
sakar se mu gani tace a ranta tare da matso da pillonta kusa da nasa. Shisshige
masa ta rigayi tana yimai abinda conciousness nasa baze iya d'auka ba tun yana
shareta har seda tayi turning nasa in suka wula wata duniyar.

***
Seda ta tabbata Adeel yayi bacci ta lalla6a a hankali yadda baza ta tayar dashi
ba tasa hannunta k'ark'ashin pillonsa tare da zaro wayansa. Pattern d'in ta zana
tsaf ya bud'u. Messages nasa ta soma shiga taga ba komi wajen hakan yasa ta duba
call logs nan ma munafikin ya goge komi, ba kalan binciken da Ruky batayi ba a
wayan Adeel but didn't find anything suspicious, hakan ba k'aramin haushi ya bata
don dolenta ta koma gefensa ta kwanta.

Washegari bayan Adeel ya fita office ta sake kiran friend nata tare da buk'atar
ta da komin yayane tayi ta samo mata number'n Nusee kota k'ak'ani k'ak'a ne. Anan
friend intan ke sanar da ita she should cool down and consider this work done!
Ahaka ne sukayi sallama, Ruky gabad'aya ta kasa samun sukuni, ita idan Zeezee ze
dawo mata da ita she don't care amman banda wata shegiya inji ta da fad'i.

Har dare shiru bata ji daga bakin Safiyya (K'awarta) ba. Yau ma se 10:45pm Adeel
ya dawo gida unlike jiya yau ko yimai sannu da zuwa ma Ruky batayi ba. D'akinsa ya
nufa direct ya watsa ruwa bayan ya fito ya sa pajamas nasa yana cikin fesa turare
wayarsa ya shiga ruri wanda tun daga parlour Ruky ke jin ringing d'in don yadda
hankalinta ke a d'akinsa. Wane ita ake kira ta tashi a guje tare da lab'ewa bakin
k'ofan d'akin nasa tana kallonsa. Not long enough taji yayi picking "hello My
Special Star?"
My Special Star? ta nanata a ranta bata jira ya sake wata maganan ba ta shige
d'akin a zuciye. Cike da mamaki ya d'ago kai yana kallonta "ke lafiyarki kuwa?"
Kafin yasake cewa wani abu har Ruky ta kar6e wayar daga hannunsa "karuwar banza
karuwar wofi me bin mazajen mutane, Allah wadai dake wallahi."

"Bakida hankali ne?" Adeel yayi maganan ransa na tafasa, yaushe Zeezee ta ta6a
yimai wannan sakarci? Hannu ya miqa ze amshe wayan wanda tuni Ruky ta miyar da
hannun nasa baya da nata ta rik'e gagam restraining him.
"Hello Karuwar bata jina ne?" Har anan shiru Nusee tayi. "Ruky wallahi zan sa6a
miki."
"Sede in na sa6a maka kai da karuwar taka, maras kunya kawai dukanku." Nan ta
dawo kan wayar "Nusee kike ko waye-" ding! Taji anyi hanging akanta. "Aiko ya fiye
miki da sekin sha zagin da tunda asararriyar babarki ta wullo ki duniya baki ta6a
sha ba karuwa kawai" tayi maganan tana glaring akan screen d'in wayan. "Bakida
hankali ne? Mahaukaciya kawai!" Adeel Yayi maganan yana k'ok'arin k'wato hannunsa
daga rik'on da Ruky tayi mai amman sam ya kasa dan irin d'ankaren k'arfin da takeji
dashi.
"Zan mareki fa, ki saken hannu, sa'an ki ne ni?"
"Wallahi ka mareni inyi zaune a ruwan cikinka. Kai wai wani irin butulu ne? Ko
kunya bakaji zaka tsaya kana min firar banza firar wofi da wata karuwa a gida na?"
K'arfin jikinsa kap yayi gathering sannan ya samu ya fisge hannunsa daga rik'on da
tayi mai.

"Bani waya na." Ya buk'ata.


"Bazan bada ba" tayi stating confidently.
"Ki bani nace!" Ya fad'a a tsawace.
"Bazan bayar ba ka k'wata idan kanada k'arfi, wata shegiya wai ita Nusaiba Allah
yasa Musiba ce wallahi baka isa ka kawo min ita gidan nan ba don gobara ne ze
tashi."
"Bayerabiyar banza, bayerabiyar wofi a haka ai zaki k'are fighting your husband
kinyi asara wallahi."
"Ka fad'i koma me waya nede bazan bada ba."
"Idiot kita rik'ewan Allah yayi bashi kad'ai ne waya a guna ba, kuma son Nusee
ne yanzu na fara sede ki mutu."
"Ai ku maras kunya ku zaku soma mutuwa kuma za muga ya auren nan ze aiku, you are
messing with the wrong bitch Adeel."
"Jahila fita min daga d'aki, ki fita nace me k'iran samudawa kawai."
"Ahaka ka gani kace kana so kai kuma me k'iran fulani ba" tana kaiwa nan ta kama
hanyan fita da wayan nasa a hannunta. Timing nata yayi a lokaci guda ya fisge wayan
nan take ta juyo. "Wallahi one more step and I'll slap you" yayi glaring at her
yana nuna mata tafin hannunsa. Sanin shima Adeel mahaukacin kansa ne yana iya
marintan kuma itace da asara yasa ta galla mai harara sannan ta fice. "Useless
kawai" yace da ita. Tana fita yasa lock a k'ofansa. Kayan baccin nasa ya sauya zuwa
wasu had'ad'd'un englisgh wears sannan ya fito yabar gidan ma gabad'aya. Ruky bata
ji fitansa ba seda tajiyo k'aran gate a lokacin kuwa she can't stop him.
"Ka fita ka dawo lafiya mark my words yau ne fitan ka na k'arshe, baka san da wa
kake zancen ba wallahi." Data zo kwanciya ne ta kiran Safiyya dan jin how far with
the so called Nusee's number.
_The following day..._
Har 11am Adeel be dawo gida ba tun fitansa jiya, hankalin Ruky gabad'aya yabi ya
tashi tuna yanzu fa halan Adeel na can da Nusee suna shan love abinsu.
Ta fannin Adeel kuwa tun jiya k'ok'arin shawo kan Nusee yake amman ya kasa saboda
gabad'aya tabi ta tsorata jin kalamun Ruky, dama gata 'yar pengel-gel kaman Zeezee.
Da k'yar d'in k'yar yasamu ya shawo kanta ta hak'ura bayan yayi assuring nata idan
sunyi aure chan 1000 houses inda yake da gida zeje ya ajiye ta yadda Ruky ma baza
ta tak'ura taba saboda ratan dake tsakanin su. Seda ya yo mata shopping sosai
sannan hankalinsa ya kwanta ya dawo gida. Alokacin Ruky na tsaye bakin k'ofa tana
jiransa. Yana gama shiga parlourn ta sha gabansa. "Ki matsa min kafin kiji sauk'an
mari a wannan kumatun fanken naki."
"Nak'i wallahi sede na maru amman seka bani kud'in ashoben bikin auren k'awata."
"Allah yasa kud'in ashoben bikin mutuwan Babanki ne bana bikin auren k'awarki ba,
bazan bada ba."
"Ai wallahi bazata saku ba wai bindiga a ruwa, koban tambaya ba nasan wannan
shegiyar budurwar taka kecin kud'inka ni kuma matar ka kake hanani."
"Ina kud'in yake bale taci? Out of my way please cause ba abinda zaki samu a guna
banida kud'i."
"Ba kada kud'i? Ajinka wai bansani bane? Ba jiya aka biya ku albashi ba?"
"Naji inada, bazan bayar ba ki daken ki kar6a."
"Kaima kasan dukanka ba abu bane da ze gagara wallahi, kud'ina ina jira." Mugun
kallo ya watsa mata sannan yazo bi ta gefenta inda tuni ta sake shan gaban sa,
"kina son kisha mari da alama."
"Wallahi se ka bani ba yadda za'ayi ita karuwar taka Nusee take kome tana cin
arziki ni matarka da arzikin ka halal a kaina ka hanani."
"Me marabarku toh? Ai du d'aya ne tun da kikazo gidan nan kin ajiye min wani abu
ne?"
"Aiko baza ka min gorin haihuwa ba tunda na hafi d'aya ya koma ne, besides ma ka
fad'i koma meh wallahi kud'i ne seka bayar 10k ina jira." Ta ciro hannunta tana
nuna mai nufin ya ajiye mata kud'in. Ita dariya ma tabasa ta d'ayan side nata yabi
wanda har ya kaiga shiga d'akinsa tayi sauri tasha gabansa tare da rik'e handle na
k'ofan "seka bani wallahi, kaji na rantse."

Drama sosai suka shiga yi, ba yadda beyi ba don jan hannun Ruky daga jikin
k'ofan amman ya kasa don irin k'arfinta, haka ba yadda ya iya don dolensa ya zaro
ragowan kud'ad'en dake wajensa ya shiga irgawa don bata abinda take buk'ata. Har ga
Allah dama dubu bakwai yayi niyyan bata, taje ta nemi sauran ta cikata. Yana cikin
irga kud'ad'en tayi timing nasa karap! Yaji ta k'wace duka tare da sa gudu.
"Ke meh haka? Kibani abuna kina ji ko banason sata." Dubu goma ta irga ras sannan
ta ajiye masa sauran kan kujera "gashi goman na d'auka don bazaka min wayo ba" tana
kaiwa nan ta nufi d'akinta ta barsa tsaye wajen out of it. "Bayerabiya" kad'ai ya
iya furtawa sannan ya tattara ragowan ya wuce d'akinsa shima. "Wai yanzu shikenan
haka zata na yimin abinda takeso and I can't do anything to her?" Ya tambayi kansa
yana miqe kan gado. "I've got to show her am the boss even if its for once."
A daren ranan Safiyya ta turo wa Ruky da number'n Nusee, oh she can't wait to
discipline shegiya gobe.
The following day bayan Adeel ya tafi office da misalin 01:18pm Ruky ta shirya
tsaf taja motarta se zuwa gidansu Safiyya da take nan always as same size as Ruky.
"Babe kikace kinsan gidansu ko?"
"Eh mana ai baze 6ata min ba a ta gun Reemee clinic gidansu yake."
"Oya oya muje kafin Adeel ya wuce gidansu don nasan ko office shegiyar bata
barinsa yaje."
"Kai Ruky Mama!" Tayi maganan tana hailing nata "Allah ki kwantar da hankalin ki,
kin d'an ganta ne kuwa? A tsaye bazata ma kai Zeezee ba wallahi, taga masu irin
k'iran mu ai jiki na rawa zatayi as we ask" Murmusawa Ruky tayi ta gefe sannan ta
tada mota suka fice. A dai-dai gaban gidansu Nusee tayi parking tare da tambayan
mai gadi ko nan ne gidansu Nusee.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
5⃣7⃣

_I'm giving this whole page to my newest most adorable, friendly, nice and
lovely group members of, *MIEMIEBEE NOVELS GROUP TWO* having to come know you guys
is My biggest experience, I heart y'all to pieces. Together we keep it moving
#OneLove, Team #YGC💕_

"Mallam ko nan ne gidansu Nusee?"


"Eh nan ne Hjy, a bud'e muku gate ne?"
"A'a yanzu zamu fito kada ka damu."
"Yauwa sannun ku da zuwa toh." Maza-maza suka fito suka shiga ciki inda suka soma
yin sallaman tsiya.

"Sallama de!" Cewar Ruky tana bubbuga entrance door in gidan. "Mutan gidan basu
nan ne wai kam?"
"Suna nan" cewar Maman Nusee dake zaune a gefen 'yarta akan dining table suna
having lunch.
"Toh kunyi bak'i" cewar Safiyya.
"Toh ana zuwa" Mama tayi maganan da d'an k'arfi yadda zasu jita sannan ta
sassauta muryarta wa Nusee "tashi kije ki bud'e musu." One more spoon ta kai baki
sannan ta tashi ta bud'e musu "sannunku da zuwa" ta fad'a cikin innocent voice nata
cike da fara'a.
"Yauwa sannu kece Nusee ne ko Nusaiba?" Asked Ruky.
"Itace mana bakiga pengelgel legs natan bana?" cewar Safiyya tana bin legs na
Nusee dake cikin leggings da dirty look. Ignoring her tace "eh nice, bismillah ku
shigo."
"A'a nan ma yayi" cewar Ruky tana hararta. "ina wuni toh?" Cewar Nusee.
"Wuni?" Asked Ruky. "Wuni yana gidan biki dan uwarki. Kinji ba? Nace kin barosa
a gidan biki." Kafin Nusee tayi comprehending wani abu Ruky tasa hannu tajawota
waje kaman doll baby. Nan Mama ta miqe da gudu tayi wajen ita ma. "Bayin Allah ya
da haka, meke faruwa?"
"Ikon Allah" answered Safiyya tana me hararan Mama.
"Ku sake min 'ya meh haka?"
"Ank'i" cewar Ruky tana sake matse rigan Nusee a wuya tana cukuikunawa. Har anan
Nusee ta kasa cewa k'ala se raba ido kawai take, ita de ko a mafarki bata ta6a yin
gamo da any of them ba, toh me tayi musu?

Ganin Mama ta ibi k'afa zata k'wato 'yarta Safiyya tasha gabanta da sauri "uh-
uh-uh Mama tsayawa zakiyi kiji abinda ya kawo mu bawai kiyi mana tashin hankali
ba."
"Wasu irin wawayen mata ne ku? Kuma daga ina kuke?"
"A'a fa Mama wallahi ki dasa aya kafin na sauk'e girman danake baki na had'aki da
'yar taki na cii maku mutunci duka" Ruky tayi stating comfortably tare da dawo da
kallonta kan Nusee. "Ke kin sanni?" Kaman bazata amsata ba se ta kad'a kai. "Tunda
ba alak'a da mahaukata nake ba ina zan ku?"cewar Nusee.
"Ke!!! Ki iya bakin ki wallahi domin bamuda mutunci, se muyi reaping naki naked
muci uwarki don laifin dake kanki." Cewar Safiyya.
"Ammatas barni da k'aramar k'waron nan, dama nasan da hakan so bari nayi miki
introducing d'in kaina. Suna na Ruky Mama matar Adeel da kike neman aura kin gane?"
Se anan hankalin Mama da Nusee ya buga, no wonder.
"Wallahi na zo ne na kashe miki warning da ki fita daga harkan mijina tun wuri,
in bahaka ba zaki yaba wa aya zak'inta." Hannu Nusee tasa don kar6e kanta amman ta
kasa. "So what dan kece matar Adeel? Mata nawa Allah ya halitta mai da zaki zo kina
cemin in fita daga harkansa? You're insanely crazy idan baki sani ba ki sani yau
auren Adeel ba fashi." Sake cukuime mata wuyan riga Ruky tayi a yayinda zuciyarta
ke tafasa "ke! K'aramar k'waro kamar ki har kinada bakin magana? Toh bari kiji in
gaya miki ko shi Adeel nakin bayi min iskanci bale ke" ta jijjik'ata irin nothing
as a shell d'innan. "Yadda kike nan kaman lafiya be ishekin nan ba wallahi zama
zanyi kan ruwan cikinki sekin harar da hanjin cikin ki, ki iya bakinki ba sa'ar
wasar ki bace ni. Mama!" ta kirata tare da dawo da kallonta kan Mama tana rik'e da
kwalar rigan Nusee har yanzu
"Naga alaman 'yarki har yanzu bata gama sanin ciwon kanta ba, as her mother
nasan ke kinyi. Wallahi warn her, warn her sosai saboda idan ta kuskura ta taka
k'afanta a gidan Adeel toh wallahi sede ki sake haifar wata Nuseen dan kasheta
zanyi da hannu na, ga k'awata nan kuna iya tambayar ta waya fitar da first wife
tasa Zeezee a gidan. Nice nan Ruky Mama, wai ita uwar gidan data fini sanin kan
gidan ma kenan bale wannan" ta maido da kallonta kan Nusee. "Wallahi k'ona ki zanyi
da kalanzir sekin zamo toka. Kad'an daga cikin aikin Ruky Mama kenan, idan kunne
yaji...?"
"Jiki ya tsira" Safiyya ta k'arisa mata.
"Yauwa Ammatas so shawara ya rage wa me shiga rijiya, idan har bawai kin gaji da
zaman duniya bane kinason na lahira daga yau bazaki sake kiran mijina ba or else"
ta wani turata seda Nusee ta fad'i a k'asa. "Mutuwa" taja layi a wuyanta da
hannunta tana mata nuni. "Lets go Ammatas" harara suka bi Mama da Nusee dashi
sannan suka fice inda a hanyan fita suka ci karo da geese nasu Nusee, shima Ruky
bata barsa ba seda ta kwad'a mai dutse. Wai wannan ma agwagwan gidan ne inaga
mutanen gidan?

Da sauri Mama tayi kan Nusee, "Nusaiba are you okay?"


"I am Mama" ta amsa tana mik'ewa da taimakon Mama. "You?"
"I am also, Nusaiba wannan tashin hankali da mai yayi kama? Dama Adeel d'in
yanada aure ne?" Kai Nusee ta d'aga a hankali.
"Shine kuma still kikeson ki auresa?"
"Mama bansan matar tasa mahaukaciya bace se yau."
"Yanzu fa? Are you still willing to marry him?"
"Yes Mama auren Adeel ba fashi bazan bari wannan barazanar da tayi ya hanani
abinda nayi niyyah ba, inason Adeel."
"Lallai bakida hankali Nusaiba, toh wallahi kiji ki sani idan har ni na tsuguna
na haifeki bazaki auri Adeel ko wa yake ba, bakida hankali ne? Kina ganin ko
agwagwan nan bata bari ba bale ke? Lallai ya tabbata bakida hankali."
"Kamar ya Mama? Saboda wannan mahaukaciyan sena bar masoyina?"
"Ke baki tunanin wani hali zakisa kanki aciki idan kika auri mijin matar nan?
Wallahi yadda tace zata k'ona ki da kalanzir tsab zata iya saboda mahaukaciya ce."
"So be it then."
"So be it? Toh ni ban gaji da ganin kiba wallahi bazaki auri Adeel ba se inde
wannan mahaukaciyar ta mutu bata raye, Babanku zan kira in gaya mishi yanzun nan."
Tana kaiwa nan tayi ciki inda tabar Nusee tsaye tana aikin kuka. Cikin itama ta
nufa inda ta kira Adeel tana kuka sosai, da k'yar ya samu ta tsagaita kukan nata
sannan tabasa labarin abinda Ruky tayi mata da Mamanta. Adeel yasan Ruky
mahaukaciya ce amman be tsamman haukan nata yakai wannan matakin ba.

"Kiyi hak'uri please Beautiful wallahi I have no idea how she found out about
your address, dan Allah kiyi hak'uri ni nasan hukuncin da zan mata."
"Its of no use Adeel saboda Mama ta riga ta rantse inde ba mutuwa taji Ruky tayi
ba she aiint letting me marry you."
"Please don't give up on us, let's show them how strongly and deeply in love we
are, please Nusee I love you, you remind me of My Zeezee."
"Adeel I don't know what to do ni kaina I am fearing abinda Ruky zata iya min,
she's so evil."
"Ki sa a ranki bazata iya miki komai ba se abinda Allah ya k'addara, kibarni da
ita I know what's right for her. Ni ke nakeso if it takes me to divorcing her I'll,
bana sonta ke nakeso."
"I love you too, just do all you have to do amman de karka saketa, it'll only
worsen the situation."
"Kiyi hak'uri please kinji? I'm on my way." Anan ya katse, barin office d'in
yayi yaje gidansu Nusee inda seda ta saci idon Mama sannan ta samu ta fito.
Hak'urin ya cigaba da bata yana sake jaddada mata shifa ita yake so. Seda ya
tabbata she is okay sannan sukayi sallama ya nufi gida zuciyarsa na tafasa sosai.
Banging k'ofar yayi tare da sa ma Ruky kira.

"Ruqayya! Ina kike mahaukaciya kawai! Ki fito nace!" Cike da isa ta fito daga
d'akinta tana sanye da vest da skirt na atamfa. "Gani wani abu ne?" Isa gabanta
yayi "jahilar ina ce ke iyyeh? Level na haukan ki har ya kaiga kije gidan su Nusee
kici mutuncin ta kici na mahaifiyarta?"
"Aww wai kana nufin ita shegiyar karuwarkan?" Tayi magana finally.
"Repeat what you just said now" yayi glaring at her.
"Shegiyar kar-" bata idda maganan ba tajiyo sauk'an hannun Adeel tas! A fuskarta,
sosai marin ya gigita ta saboda tunda tasan kanta ba'a ta6a marinta ba se yau.
Wajen ta rik'e da hannunta bibbiyu tana kallonsa da mamaki. "Ni? Adeel ni ka d'aga
hannu ka mara akan wata shegiyar da bata taka kara ta karya ba?"
"An mare kin, kika sake zaginta wallahi sena k'ara miki wani."
"Lallai!" tayi maganan tana sauk'e hannayen nata. "Lallai zakayi nadaman mari na
da kayai kaji na rantse wallahi tallahi rantsuwa ba kaffara bazaka auri Nusee ina
raye ba, idan kaga ka angwance to Ruky bata numfashi."
"Haka kikace?"
"Eh kuma ka tsaya kaga ikon Allah."
"Me kika isa kiyi? Banza dake ne zaki hanani yin abinda nayi niyya? Toh wallahi
ki bud'e kunnawanki da kyau ki saurare ni, idan bakiyi complying hankalinki gu
d'aya ba kika nitsu wallahi a bakin auren ki, sakan ki zanyi in huta kema ki huta
dan bakida wata amfani mani."
"Hehehe!" Ta sa wata maqirar dariya tana shewa. "Ni zaka saka? LOL this is where
you are wrong, Ruky Mama bata sakuwa wallahi ko ka sakeni ba inda zani ina nan a
matsayin matarka kuma uwar gidan ka a gidan nan. Nan gani nan bari sadakin
bazawara. In fact wallahi idan ka kuskura ka sakeni believe me bazaka so ganin
ta'addancin da zanyi wa Nusee ba."
"Me kika isa kiyi mata?"
"Me kuwa? Wanka da acid zanyi mata from head to toe. Idan kuma kana ganin wasa
nake try divorcing me ka gani, aikin banza kawai! Warning dana kashe wa Nusee idan
har Uwarta tana sonta bazata barta ta aureka ba so shawara ya ragewa me shiga
rijiya, koka nitsu mu cigaba da zaman mu kokuwa wallahi kowa ya mutu, don a kanka
kowa na iya mutuwa Adeel you are mine and mine alone." Bata jira jin me zai sake
fad'a ba ta yi hanyar d'akinta. Ji Adeel yake kaman ya buga mata saki uku take but
sanin aljanu da ipiritu na yawo akan Ruky ya fasa dan tsab zata iya tayi ma Nusee
wankan acid d'in kamar yadda ta fad'a.
Wani irin bala'i ne wannan? Tun farko daya rufa wa kansa asiri yayi zamansa da
Zeezee dake sonsa da duk haka be faru ba. Gashi nan yanzu yaje ya auro abinda yafi
k'arfinsa, Ruky tafi k'arfinsa, ina ma ace ze iya sakanta ya huta.

Ba yadda Adeel beyi ba don convincing Maman Nusee amman abun ya gagara. Seda
ya kusan giving up sannan Mama ta amince bayan rantsuwan da yayi mata na cewa ba a
nan garin Bauchi ze ajiye Nusee ba bayan sunyi aure. A chan Katsina ze kaita where
he is sure Ruky batasan kowa ba kuma agun aikinsa ma ze nemi transfer zuwa chan
d'in. Bayan komi ya sake daidaita tsakaninsa da su Nusee ne Ruky taji labari akan
Adeel na shirye-shiryen yin aure inda taje ta gidan su Nusee ta sake buga wani
rashin hankalin fiye da wanda tayi da a baya.

Ruwa ta cika cikin wani white mini galon tajeta gidan su Nusee dashi inda ta
ringa ikirarin acid ne undiluted one ma kuwa, and that seta k'ona Nusee dashi.
Had'ata da Allah suka rik'ayi ciki harda K'awarta Safiyya da suka had'a baki.
"Wallahi sena k'onaki tukun yaso hukuma ta kamani amman de nasan na lalata miki
rayuwa."
"Ruky kiyi hak'uri" cewar Safiyya.
"Nak'i ina ita da uwar nata kunnen uwayen shegu ne dasu wallahi basu sanni
bane." Da d'ayan hannunta ta d'ago gallon d'in kaman dagaske dama d'ayan hannunta
na rik'e da kwalan rigar Nusee ne, ita kanta Nusee ta gama tsurewa yau, mamanta kam
banda kuka ba abinda take. Ganin dagaske Ruky na neman bulbula wa 'yarta ruwan da
suka d'au acid ne yasa ta saki ihu sosai stopping Ruky.
"Dan Allah baiwar Allah karki k'ona min 'ya, in harkan mijinki kikeson tafita you
have my words ko bayan ranki bazata auri mijinki ba, don Allah karki illata min
ita."
"Kunsan da haka kukamin kunnen uwayen shegu wancan karan? Kun d'au wasa nake
abee? Zaku ga aiki da cikawa wallahi I'll prove to you both that ba'a wasa da Ruky
Mama."
"Ruky don Allah nace karki zuba mata." Cewar Safiyya.
"Kifa bar had'ani da Allah don sena zuba."
"You heard me right wallahi Nusaiba ba zata sake kula mijinki ba." Mama ta
fad'a pleadingly.
"Naji daga bakinta tukunah."
"Nusaiba tell her yourself har abada bazaki sake shiga harkan Adeel ba, kin bar
mata kayanta." Banza Nusee tayi da Mama hakan yasa Ruky sake matso da gallon d'in
ready to shower her with it.
"Ruky please karki zuba mata, zata fad'a don Allah."
"One..." Ruky ta shiga counting "two...-"
"Bazan sake shiga harkan mijinki ba" Nusee ta fad'a a wahalince tana kuka sosai.
"Banji ba ki sake nanatawa."
"Bazan sake shiga harkan mijinki ba, nabar miki abinki har abada."
"In kika kuma fa?" Asked Safiyya.
"Bazama ta sake ba in shaa Allahu" cewar Mama a rud'e.
"K'aramar k'waro kawai Allah ya soki wallahi da kinyi sallama da wannan
kyakkyawan fuskar taki yadda ba Adeel kad'ai ba kowani na miji ma seya k'yama
ceki." Tureta tayi seda taci karo da bango sannan ta rufe gallon d'in tare da cewa
"mu tafi ammatas, a word is enough for the wise." Kuka sosai Nusee tasa da suka
fita, itama Mama tana kuka tana lalashin 'yar tata.

****
Da yamma bayan Adeel ya taso daga office ya biya mini mart yayo siyayyan
chocolates kaca-kaca ma Nusee. A gaba da gidansu kad'an yayi parking kamar yadda ya
saba sannan yayi beckoning mai gadi over da yayi mai Nusee sallama.
"Sede kayi hak'uri Ranka Shi Dad'e."
"Kaman ya fa Baba bata gida ne?"
"Alhj baka da labari ne?"
"Labarin me fa?"
"Abinda Uwar gida tazo tayi d'azu." Ido sosai Adeel ya kwararo waje, "kana nufin
Ruky ta sake zuwa nan?"
"Sosai ma kuwa tazo tayi abinda ko a jarida na jima banji anyi ba."
"Innalillahi! Me tayi?"
"Ita da K'awarta..." labarin duk yadda aka yi Baba me gadi ya basa. Wani wutan
tsanan Ruky ke ruruwa a zuciyansa ji yake as if yaje ya bugu ya taho yayi mata
d'ankaren dukan da seta kwana biyu a asibiti ba tare da tasan inda take ba. Still
yak'i yarda da maganan Mai gadi ya d'aga wayansa ya shiga neman Nusee. Sede yayi
mata several missed calls duk tak'i d'aukawa ita kanta ta tsorata da actions na
Ruky earlier. For the love of herself zata yi hak'uri da soyayyan Adeel.

"Tun ranan da na rabu dake Zeezee na tafka babban kuskure a rayuwana, I miss you
so much" k'aramin hauka ne kawai Adeel beyi ba sanadin Ruky yanzu ya rasa two most
beloved mata a rayuwansa, gashi yana ji yana gani ba abinda ya isa yayi mata if not
tace zata yima Nusee wankan acid. Ba inda yake zuwa kwana biyu banda bar yaje ya
bugar da kansa don rage tunanin Zeezee da Nusee, office ma ya yanke zuwa. Yayi
hakan na over a week ya soma getting mind nasa back together by resuming office.
Tun kuma abinda Ruky tayi masa be sake shiga harkanta ba, girki ma ko tayi bayya
ci. Ba ruwansa da ita.
Yau da misalin k'arfe 9:29pm Adeel ya d'au wanka sannan ya fita ba tare da ya
sanar da Ruky inda zasa ba. Tun anan jikin Ruky ya bata party zasa, "aiko baka isa
ba wallahi." K'awarta Safiyya ta kira "Ammatas please kiyo min bincike akwai inda
za'ayi hosting party yau?"
"Ai yanzu haka ma shiri nake akwai wani a Larema htl sannan akwai wani a
Zaranda."
"Please do find out for me, wanne d'aya Adeel yaje saboda he just left home now,
kwana biyu kaman ya shiryu ashewa am wrong."
"Kai Babe! Baki barin wannan mijin naki fah."
"Yo taya zan barsa? Ina kishin abuna wallahi."
"Toh naji don't worry"
"Yyauwa and also gobe ki sake min confirming idan da akwai party lemmi know
please."
"Toh Babe an gama!" Anan tayi hanging. Gabad'aya ta kasa bacci ranan kasancewar
ko kwana a gida Adeel beyi ba. Da Asubah Safiyya ke sanar da ita kan taga Adeel a
party'n da akayi na nan a Zaranda kuma in bawai wasa idanunta suke mata ba ta gansa
da wata chick.
"Chick fa kikace?"
"Wallahi kuwa wata wai ita Xarah."
"Ai kuwa wallahi ze sha mamaki be sanni bane, shi ba wai neme-neme ba? Nikuwa
kore-kore ce, Allah yana samunsu ina korarsu har seya gaji ya dena."
"Pwhahhaha kai Babe bakida dama fah."
"Ahtoh bari muga zuwa nan da one week if they are getting along se muyi making
move namu amman kafin nan ki nemo min numban shegiya in ajiye saboda tsaro."
"Zuwa anjima toh."
"No prob nagode fa Ammatas."

Washegari wuraren 9:12pm Ruky tayi timing Adeel saboda Safiyya ta sanar da ita
akwai wani party tonight. Seda ta bari ya shiga bayi sannan ta shiga d'akinsa ta
d'ago keys nasa. Back and front door tabi tasa musu key sannan ta je d'akinta ta
6oye key'n acikin pillow case nata. Tsaf yau ma ya shirya gwanin sha'awa ya fito
ready to party. Sede yayita waine-wainen handle, k'ofa bai bud'uwa. Key holder'nsa
ya zaro ya shiga neman key'n k'ofar shima babu, "ha'a! Ina key'n ya shiga newai? "
D'aki ya koma yayi ta dube-dubensa amman be samu ba. Ta baya yabi nanma same story,
jikinsa ne kawai yabasa Ruky is behind this. D'akinta ya nufa direct inda ya tarar
a rufe don haka ya shiga bubbugawa. "Ruky! Ruky! Ki fito kibani makullin."
"Kabani ajiya ai dole kace na baka."
"Ki taso ki bud'e k'ofan."
"Dalili? D'akinka ne? Kamar yadda kake korina daga d'akinka nima bazan barka ka
shigo min nawa ba" tayi maganan tana buga candy crush a wayarta hankali kwance tayi
ruf da ciki.
"Ruky! Kinsan bani wasa dake koh? Ki fito ki bud'en k'ofan am running out of
time."
"Time for what? Saboda kaje party kana meeting new girls kana iskanci dasu? Ai
wallahi inba wai ta ceiling zaka fita ba, ba inda zaka yau kaji ka sani."
"Ke wai dan k'aniyanki me kika mai dani ne a gidan nan k'aninki ko meh? Don't
let me repeat myself ki taso ki bud'e k'ofan nan nace."
"Wallahi bazan bud'e ba." Tuna yanada spare key ya nufi d'akinsa and in a bit ya
fito rik'e da key'n, wainawa yayi ya bud'e nan ya sameta tana buga game.
"Ina wasa dake ne? Ina key'n nace?" Yayi maganan moving closer to her. Ko d'aga
kai ta kallesa ma batayi ba bale tasan yanayi hakan ba k'aramin haushi ya basa ba,
besan a lokacinda ya d'aga hannu ya sake mata mari tas a bayan taba.
"Ai wallahi ka mari banza, dan ba marinka ze sa na baka key'n ba kaji ka sani
idan kuma ka sake marina ramawa zan da ba jakar ka bace ni. Idan kaga ka fita daga
gidan nan toh gobe zaka fita aiki ne." Ba kalan zagin da beyi mata ba amman tayi
mai turning deaf ears don kansa ya gaji ya bari ya koma d'akinsa. Har mak'ora ta
kaisa daren ranan haka yana ji yana gani yayi missing party'n and above all yayi
missing chance na had'uwa da Xarar sa.

The following day da safe ta bud'ewa Adeel k'ofa sanin zasa office. Haka fa
rayuwa ta juya kuma, idan har Adeel ya fita yaga Xarah toh idan an tashi daga
office ne kafin ya dawo gida seya biya mata, but any moment yace wai ze fita party
da daddare lock Ruky ke sawa ta rufe ko ina.

_If you know you miss MAJ-GEN. MUH'D AL'AMEEN, let Miemiebee see your hands up👆🏾👯
our Legend will be coming back next chapter in shaa Allah_

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
5⃣8⃣

_I solemnly give this page to all of Team Maj-Gen. Muh'd Al'ameen our legend
fans. If I am to call names it'll be H. Jidderh, Mjay, Sumy and Serdee of YGC
Fansclub and to all members of HAUSA NOVELS GROUP (Na Chuchu) I heart y'all to
pieces. #OneLove💞_

Daga baya dabara ce ta fad'owa Adeel inda ya bari seda Ruky bata gida ya
kawo me gyara ya canza mai lock na k'ofofin duka, musamman ya tanada gun ajiye keys
nasa inda hankalin Ruky baze ta6a bata ba. Da daren ranan Ruky na zaune a dining
table tana had'a golden morn taga fitowan Adeel tsaf yasha supras nasa ready to
party. Dariya ta qyalyalqe da "wanga wanka se muga ina zakaje" tayi stating
confidently tare da shigewa kitchen dan d'auko abu. Fitowan da zatayi taga k'ofa
wangale a bud'e. "Bade na mance ban sa key ba?" First abinda ta soma tambayar kanta
kenan."Kode ya binciko inda nake ajiye keys d'inne?" Ajiye saucer'n dake hannunta
tayi ta nufi d'akinta kamar yadda ta ajiye ta tanadar da keys d'in nufin be ta6a ba
"to how?" Ta sake tambayar kanta. D'aukan keys d'in tayi taje ta gwada a jikin
k'ofan, sede yayi k'ara kaman ya kullu amman ba kulluwan zahiri yayi ba ma'ana
Adeel ya canza lock kenan. Lallai kuwa Allah yayi tana da mai gyara itama. Ko kwana
a gida Adeel beyi ba ranan akuyan d'aure ya samu saki, washegari kawai da safe ya
dawo yayi wanka ya wuce office. Anan ne Ruky ta kira me gyaranta ya canza mata lock
d'in itama zuwa na da. "You wanna play the game? Then let's pray it" tayi maganan
tana 6oye makullin nata. Yau dagangan ta fito parlour ta zauna tana zaman jiran
fitan Adeel. Bada jima ba kuwa ya fito cikin shirin party like se k'amshi yakeyi.
Magestically ya nufi k'ofan tare da gwada sa key nasa sede yayita wainawa amman
k'ofa bai bud'uwa. Abu kaman fa wasa but his key aiint working, "what could be the
problem?" Ya tambayi kansa. Juyawan da zeyi yaga Ruky na shirin dariya, wani dogon
tsuka yaja.
"Allah yaso tsaka ake yiwa tsaki, zaka gaji ka bari, the earlier the better
gomma kaje ka kwanta kanada office gobe." Bata jira jin me zece ba takai plate nata
kitchen tazo wucewa d'akinta kenan ya danna mata kira da "Ke!"
"Ba suna na ba kenan."
"Whatever me kike nufi?"
"Me kuwa? Abinda kayi nima shi nayi."
"Kina nufin kin canza min lock na k'ofan gidana?"
"Sosai ma kuwa, kaima ba haka kayi ba?"
"Amman yarinyan nan bakida hankali wallahi."

"Hankalin ne ya jawo hakan ai seda safe."


"Wallahi Ruky bana wasa dake, kizo ki bud'en k'ofan nan."
"Saboda kaje ka samu mata a waje kana shafasu? Inaaa Adeel I won't let that
happen." Da wuri ta shige d'akinta tare dasa lock. Tsaye yayi wajen totally out of
it, wai shin meya auro wa kansa ne? Ba yadda ya iya ranan dole yayi cancelling
fitan nasa. Washegari kuma da safe taje ta bud'e mai k'ofan, kaman shekaran jiya
yau ma ya kirawo mai gyara ya sake canza mishi lock yadda da daddare ya samu ya
fita party abinsa. The next day itama Ruky ta kirawo mai gyaranta ya sake canza
mata lock d'in haka fa suka cigaba da wasan yara. Shi Adeel seya biya kud'i ake
canza mai lock d'in. Itako Ruky a kyauta me gyaran yake mata saboda na gida ne shi.
Ganin kud'insa na iya k'arewa a hakan ya hak'ura kawai ya barta. Ya zammana yanzu
ba kullum yake zuwa party ba randa zasa tun safe idan ze wuce office se ya d'au
kayan da zesa ya fita dashi sekace dole. Daga office ya wuce gidansu Xarah ya
d'auketa outting byan Maghrib ya wuce gidan Mami yaci abinci ya watsa ruwa ya wuce
party abinsa.

Ruky de tashiga damuwa dan kuwa ba abinda yafi ci mata rai kaman taji Adeel na
zuwa party. Time suka sa ita da Safiyya suka shirya tsaf suka jesu gidan su Safiyya
bayan dogon binciken da sukayi har suka gano gidan nasu. Kaman abinda suka yima
Nusee haka sukayi ma Xarah ma sede ita Xarah idanunta a bud'e suke, kaca-kaca
sukayi da Ruky wanda daga k'arshe seda Ruky ta rufe ta da d'ankaren duka a idon
mahaifiyarta da Safiyya tayi mata rik'on da bata iya k'watan kanta. Lik'is ta daka
Xarah dake nan 'yar pirit. Sannan ta koma mota ta fito da gallon na ruwan da take
cutan mutane tace acid ne. Ita sam seta watsa wa Zarah. Nan fa Xarah da Mom nata
suka kid'ime wannan wace erin mahaukaciya ce. Xarah bata son abinda ze ta6a mata
fuska don haka tayita rok'on Ruky tana had'ata da Allah kan bazata sake shiga mata
harkan miji ba. Seda Safiyya tasa baki kaman dagaske sannan Ruky ta hak'ura suka
fice. Tun fa daga wannan rana Xarah bata sake picking call na Adeel ba ita tasan me
ta gani. Daga bakin 'yan unguwa Adeel yaji abinda Ruky ta sake yimai, gida ya koma
ya kwakkwad'eta inda take threatening nasa kan idan har ya sake ta6ata wallahi seta
k'ona Xaran shi kuma tayi zaune kan ruwan cikinsa.

***
Life loved on, duk girlfriend da Adeel yayi Ruky na sane da ita, seta bari
relationship nasun yayi k'arfi sannan tajeta da gallon nata ta tada bori ta
tsoratar da bayin Allah. Haka Adeel ya kasa yin gaba, bayan nan kuma ga k'ananu-
k'ananun d'auke-d'auke da take yimai. Saboda ba kud'i yake bata ba yanzu gashi har
yanzu ita ta kasa samun aiki, sena lecturing ita kuwa wai bata so its stressful.
Daga yau ta sata mar dubu biyunsa, se gobe dubu d'aya kai atimes har biyar. A
dalilin haka yabar ajiye ko k'wandala a gida, gabad'aya rayuwarsa ta gama
hargitsewa da kalan tashin hankalin Ruky, he can't explain just how much he is
missing Zeezee. Divrocing Zeezee is the biggest mistake he has ever done, haka
kawai bata mishi komi ba ya d'au karan tsana ya aza mata ya riga maltreating nata,
why? He can't answer.

Cikin ikon Allah Ruky ta sake samun wani cikin, wanda yana 5 weeks again ta
sake miscarrying baby'n. Abun ba k'aramin damun Adeel yake ba, ba shida burin daya
fiye mai yaga jininsa yanzu. Ya dawo daga rakiyan neman mata saboda ko yayi ba riba
se ma asara, yayi ta kashe musu kud'i daga k'arshe Ruky ta kora masa su. Gashi nan
ne kawai da Ruky suna maneji.

^*^*^_ZEEZEE_*^*^*
Da rasuwan Baba watanni da d'an dama kenan yanzu, getting to 5 months. Zeezee has
finally moved on lokaci-lokaci take zubar da hawaye idan ta tuna da rauswan sa,
amman kusan a kullum kam setayi tunaninshi. Ta fannin heartbreak nata ma yanzu ba
laifi saboda gabad'aya ta manta da Adeel on occasional purposes kawai take tunawa
dashi, sede wani hanzari ba gudu ba, a day never goes by batayi tunanin Ya Al'ameen
ba bata da mafarkin daya fiye mata ta sake kasancewa matarsa again saboda ta
farinta mishi and show him just how much she loves him.
Manyan mutane da dama sun leqo kai don neman hand d'in Zeezee in marriage amman
gabad'aya sede tayita raina musu hankali ita she believe one day she'll be MARRIED
AGAIN to Ya Al'ameen. Fateemah matar Ibraheem ma ta sake haihuwa inda ta samu 'yar
ta again wanda shi Ibraheem da ita Fateemah suka yima Zeezee takwara kasancewar
situation nata na rashin haihuwa. Mama tayi-tayi da ita suje asibiti a duba ta don
sake tabbatar da komi da kuma duban ko da akwai taimakon da za'a iya mata a gyara
mahaifar amman tak'i saboda batason abinda ze sake jefa mata ryuwarta cikin k'unci.
Zeezee ta d'au son duniya ta d'aurawa 'yar Ibraheem me sunanta. Ko a mafarki
bata ta6a kawowa a ranta Ibraheem zeyi mata takwara ba, d'aya daga cikin alkhairin
daya fito daga tafiyan Baba shine jituwa dakuma so tare da had'in kan daya sake
yad'uwa a tsakanin yaran shi. Kowa yayi mata farin cikin wannan takwara data samu,
atimes idan ta rik'e mini Zeezee se kawai ta fara kuka tuna ita fa yanzu shikenan
bazata ta6a ganin jininta ba, Adeel ya cuceta na har abada. Ko bayan suna ma Zeezee
tak'i dawowa gida seda ta k'ara musu wani sati biyun sannan ta dawo ta. Unlike
before wannan karan Fateemah taji dad'in zama da Zeezee, komai Zeezee keyi mata
wanka wa Maamah, shirya ta school, dafa abinci. Wanke-wanke da shara ne kawai me
aiki keyi. Ibraheem couldn't ask for more, shiri sosai suke yi da Zeezee yanzu
saboda tadena yimai rashin kunya. Har atimes yake neman tsokanarta wai tad'an yi
mai rashin kunyan nan nata mana he misses beating and kicking her around. Kafin
Zeezee ta baro Abj seda wani friend na Ibraheem ya ganta ya kuma yaba mata da tayi
mai sosai and yana sonta da aure. Unlike before da idan friend nasa yace yana son
Zeezee yake jin haushi wannan karan murna yake yazo ya sanar da Zeezee sede sam ta
nuna mai she is not interested tare da yimai k'aryan wai ita bata son danginsa suzo
suna goranta mata akan rashin haihuwarta but deep inside don tana son tazo ta
komawa Al'ameen ne take avoiding d'in kowa.

^*^*^
Zeezee tayi nisa sosai ba laifi ta fannin haddanta, tana neman izu goma sha
bakwai kenan, hadda ras a kanta. Wani jin wak'a duk ta dena se jifa jifa. Ana cikin
haka ne rana d'aya over the weekends bayan Zeezee ta d'auko yaran Mariam ta kawosu
nan gida, suka jiyo ana knocking daga bakin gate. Alokacin ma abinci take baiwa
Ummie, Ramlah na gefe tana cin nata. Ramlah na jin knocking tamiqe a guje zata je
ta bud'e. Haka take ita mayyar bud'e k'ofa ce, kuma bata tanbayan ko waye kawai ita
bud'ewa take which is not good.
"Ramlah dawo nan" Zeezee tayi maganan tana k'ok'arin tashi daga zaune. Sanye
take da wata purple lace me torches na black and white, kanta a bud'e ta kama
gashinta gu d'aya tare sa lank'washe jelar.
"O'o ni zan bud'e Aunty Zeezee."
"Kidawo nace zan bud'e." Ai ko sauraronta Ramlah batayi ba ta k'arisa da gudu ta
bud'e se gani kawai tayi kan bindiga na mata sallama. Da gudu ta koma bayan Zeezee
tana la6ewa "ahtoh! Maganin wanda bai jin magana kenan, keba wai bakiya jin magana
ba wataran d'aukeki zasuyi su tafi da-" bata k'arisa maganan ba taga the most
breathtakingly gorgeous soldier ever which is non other than *Maj-gen Al'ameen.*
Sanye yake da killer uniform nasa me sake k'ayata shi, d'ayan hannunsa na d'auke da
wayoyinsa while kuma the other hulansa, gefensa da kuma bayansa sojojinsa ne suna
guarding nasa. Wani k'war jini ya sake yimata, dama Ya Al'ameen nada kyau haka? Ta
tambayi kanta a zuciya. Ita da ta d'au kyan farintaka ne kawai dashi ashe ba haka
abin yake ba, Ya Al'ameen koda za'a fenta sa bak'i kyan na nan yadda yake sede
farin na k'ara mai ne kawai. Wow! Kawai take ta furtawa a zuciyarta ta kasa keeping
eyes nata off him gashi wani fresh daya k'ara gaskiya ba k'arya time da suke tare
yad'an fad'a all due to abubuwan da take yimasa.

Shima kallon nata yake long time no see, dukda Zeezee tad'an k'ara weight da
haske compared to lokacin da ta fito daga gidan Adeel, amman har a yanzun bata kai
kauri dakuma hasken da take da shi ba time da take gidan Ya Al'ameen. Anytime ya
kalle ta banda kyau datake k'ara yi masa theres nothing more. He stared at her for
about 2 minutes sannan ya kawar da kansa itako har anan ta kasa dena kallon nasa
tama manta ba d'ankwali bale hijabi a jikinta.
"Uhm-uhm" yayi clearing throat nasa ganin kallon nata bana k'arewa bane. Shi
tambayan kansa ma yake me Zeezee keyi a gida? Instead of her matrimonial home dan
bashida labarin ta rabu da Adeel at all. Toh kode tazo yini ne? He can't judge.
Baki na 6ari guiwa suna shaking tace, "Yya... Ya Al'ameen?" Still not believing her
eyes ashe Allah ze sake kawo mata rananda zata sa masoyinta acikin idanunta, addu'a
d'aya take yi a ranta a yanzu haka. Allah yasa miji na garin da Baba yayi mata fata
kafin ya rasu shine Ya Al'ameen.
"Na'am Zainab" ya amsa cikin OMG voice nasa me sake tafiyar wa mutum da
imaninsa. Nan fa heart na Zeezee yayi skyrocketing daga earth zuwa pluto (Lubna🤣)
bata san tayi missing Ya Al'ameen ba seda tajiyo wannan zazzak'ar muryan nasa.
"Aunty Zeezee kinsan wannan me bindigan ne? Wayyahi mu gudu kafin ya mana dush-
dush mu mutu." Cewar Ramlah tana 6oye still a bayan Zeezee. Dariya ta bawa Al'ameen
wanda hakan yasa ya murmusa sosai revealing his two sided pointed dimples and
making him worth more looking, Zeezee couldn't stop staring and falling in love all
together.
"Inji wa Baby? Ba Wanda ze har6eki kinji? Zo abinki" ya nuna mata hannunsa.
Shima Al'ameen gwana ne when it comes to son yara, kafad'a ta buga "o'o zaka min
dush-dush in mutu." Widening dariyan nasa yayi tare da cewa men nasa "excuse me, ku
jirani a waje." Se anan Ramlah ta d'an ji iska, "zo yanzu toh kinga sun tafi."
"Inje Aunty Zeezee?"
"Kije Ramlah, this is your Uncle ba abinda ze miki." Ba gardama tajeta ya d'agata
sama ya shiga jero mata questions se hira suke wane tun da sun san juna.
Kasa dena kallonsu Zeezee tayi tana me sake tsanar kanta, da bata biyewa Adeel
ba ta rungumi k'addara tayi wa iyayenta biyayya da yanzu haka sede Al'ameen farin
cikinta yad'au baby'nsu yana cuddling mata ko masa.
Chan Al'ameen ya dawo da kallonsa kan Zeezee data kasa dena kallonsa tun d'azu,
bata bari idansu ya had'u ba tayi sauri ta kawar da idonta akansa tare da maidosu
kan Ummie tana wasa da hannunta. Shi kam ma ya d'au Ummie 'yarta ce saboda Ummie na
nan sekace wacce batayi two years ba sam bata da tsawo Ramlah ta fita girmah.

"Ramlah wace wancan? Baby'n Aunty Zeezee ce?"


"Wacce Uncle Soldier?" Dan sunan data sa mai kenan. Murmushi ya mata sannan ya
nuna Ummie.
"Ohh Sunanta Ummie."
"Ummie" ya nanata "Yar Aunty Zainab ce?"
"Laaaa!" Tayi covering mouth nata with both of her palms "Aunty Zeezee fa batada
baby, k'anwa nane."
"Aww haba ashe shiyasa naga kuna kama, Ummie Baby zo kinji?" Aiko ta buga kafad'a
tare da kama k'afafun Zeezee gagam. Question nasa na "wancan 'yar Aunty Zainab ce?"
ya tsaya wa Zeezee a wuya, bata hankara ba tajiyo idanunta na neman cikewa da
hawaye da k'yar ta samu ta had'iye kukan sannan tayi womaning up tace "ka shigo
ciki Ya Al'ameen bari inyi wa Mama magana."
"Okay tana cike ne?" Ya tambaya yana bata full concentration nasa cike da
dignity.
"Eh bismillah." Bayan ta yabi yana wasa da Ramlah dake ta faman shafa sajen
fuskarsa tana cewa irin na Daddy na. A parlour tace ya zauna ita kuma tayo d'akinta
inda ta d'au gyale ta yafa, har anan kaman jela Ummie keta binta. Kitchen ta nufa
tare da d'auko masa ruwa da 5 alive ta kawo har gabansa ta ajiye. "Ai da kin bari
Zainab."
"A'a Ya Al'ameen koban tambaya ba nasan daga tafiya kake" tayi maganan tana
tsiyayar masa da juice d'in a cup.
"Toh nagode."
"Bari inyi wa Mama magana." Tana miqewa Ummie ma ta shiga bin bayanta, "Ummie
bazaki bar Aunty Zainab ba kizo mu gaisa?"
"Ai Uncle Soldier kabal Ummie nima haka take min wataran kaman bata sanni ba
nima sena shareta kawai, kaima ka shareta, ni kad'ai ma na isheka wasa." Kai kawai
Zeezee ta kad'a sannan ta shiga ciki ta sanar da Mama dake fitowa daga bayi bayan
tayi wanka.
"Allah sarki Maj-Gen. kice mai gani nan zuwa, kun gaisa ne ke?"
"A'a yanzu zanje mu gaisa."
"Yauwa jeki nima gani fitowa."
Back in the parlour ta tarar dashi da Ramlah se game take bugawa a wayansa tana
zaune bisa cinyansa. Daga can nesa adjacent to him ta zauna tare da zaunar da Ummie
a gefenta.

"Ina yini Ya Al'ameen?"


"Lafiya Zainab" ya d'ago kai yana kallonta. "Mun yini lafiya?"
"Lafiya k'alau ya gajiyan hanya da kuma aiki?"
"Alhamdulillah, ya mukaji da hak'uri Baba lokaci yayi."
"Alhamdulillah Baba Lokaci yayi."
"Toh Allah ya jik'anshi ya gafar ta mishi ya kuma kai rahma kabarinsa, our
prayers are with him."
"Ameen ameen nagode Ya Al'ameen."
"What for? Sannun mu da hak'uri ko? Tun tuni nakeson shigowa wallahi but Allah be
nufa ba, an kai mu Maiduguri saboda state of emergency shiyasa kuka jini shiru aiki
yamin yawa. Da akayi rasuwan kuma I called you but bana samun ki, Mama tace bakida
lafiya."
"Ayyah ba komai Ya Al'ameen ko yanzu da kazo ai bakayi latti ba, zuwan shine
babba ai, da rasuwan nima banji dad'i bakam shiyasa."
"Ayya ya jikin toh yanzu?"
"Alhamdulillah da sauk'i sosai."
"Toh Masha All-" be gama maganan ba Mama tayi sallama tare da shigowa nan ya
shiga neman sauk'owa daga kan kujerar don bata girma inda tayi saurin hanasa.
Gaisawa sukayi sosai inda yayi mata ta'aziyya itama yake kuma bata hak'uri na
jinkirta zuwa ta'aziyyan da yayin, su Hajiya Mama duk suna gaishesu. Bayan gaisuwa
yayi wa Baba addu'a sosai, seda Zeezee ta zubda k'walla se gani take kaman jiya-
jiya Baba ya rasu.
"Mungode sosai Maj-Gen. Allah shi biya."
"Ameen Mama" d'ayan wayansa ya d'aga ya kira men nasan kan su shigo da drinks
d'in. Carton na malts da other canned drinks ne har guda biyar ya kawo musu, sosai
Mama tayi appreciating tayi kuma masa godiya haka Zeezee ma.
"Toh ni zan tafi Mama dawowa na kenan daga tafiya zuwa jibi haka nakega zan
koma."
"Toh, toh a huta gajiya Maj-Gen mungode fa sosai ina zuwa." Nan ta koma ciki. Tun
tun d'azu kallonsa Zeezee take ko kyafta ido bata iyawa tana ganin ze juya seta
kawar da kanta haka ma yanzu, kallon Ummie dake zaune akan cinyarta yayi sannan
yana murmushi yace "anya kuwa wannan ba 'yar Aunty Zainab bace Ramlah?" Murmushin
dole ta k'irk'iro sannan
tace, "ba 'yata bace Ya Al'ameen."
"Kai ban yarda ba dan kin dace ki zama Maminta kyanku d'aya."
"Kai Ya Al'ameen 'yar sister na ne Mariam, dukansu biyu da Ramlah."
"Ayyah toh Allah ya raya mana su, ina namu toh?"
"Allah be kawo ba tukuna" ta amsa tana forcing out a smile.
"Toh Allah kawo rayayyu masu albarka."
"Ameen ameen."
"Ya mai gidan naki da kowa?"
"Alhamdulillah" kaman da tayi mai k'arya tace yana lafiya seta ga kuma ba amfani.
"Na dawo gida ai yanzu." Sam be fahimci me take nufi da ta dawo gida ba yanzu,
"baza a iya rabaki da gida ba Zainab, kin dawo yima Mama weekends kenan."
"A'a" ta kad'a kai "actually mun rabu dashi tun kafin rasuwan Baba ma." Ido ya
kwararo waje da kyau yana sauraronta amman Adeel be kyauta mata ba, shi bayi ma
tunanin kalan rashin kyautatawan da tayi masa, rashin kyautatawan da Adeel yayi wa
Zeezee ne ke damunsa (see true love.)

"Subhanallah!" Sam beji dad'in hakan ba, she's of too tender age ace aurenta
biyu duk babu no wonder ashe yaga tad'an zube not as before. "Allah rufa mana asiri
toh."
"Ameen nagode." Tayi forcing out a smile "ya Madam kuma? From all seeing tana
kula mana da kai."
"Haha" yad'an murmusa "toh gamu nan de, har yanzu ban sake..." sekuma yayi shiru
da kaman yace mata yana shirye-shiryen sake aure se kuma ya fasa. Dukda be k'arisa
zancen nasa ba Zeezee ta gane be sake aure ba yake nufi. Only this thought is
driving her crazy.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*Febraury, 2017*
5⃣9⃣

Toh kode ya fad'a mata ne? Shawara ya tsaya yi, dai-dai lokacin da ya yanke
hukuncin gaya mata gaskia batun auren da ze sake yi a dai-dai lokacin ne Mama ke
fitowa daga d'aki da alama ta koma tasa kaya ne. "Ahh barka baka tafi ba, ai na sha
ma koka riga ka wuce."
"A'a Mama ina jiran fitowanki ne toh ni zan wuce." Yayi maganan yana miqewa da
Ramlah a hannunsa.
"Ke kuwa Ramlah haka akeyiwa bak'o ne? Seki d'ale jikinsa haka." Cewar Mama da
mamaki.
"A'a Mama bar jikar takin nan zan zo in d'auke ta ta kwana min ma."
"Dagaske Uncle Soldier?" Tayi maganan with zealous flavor.
"Ji wani suna wai Uncle Soldier" Mama tayi maganan tana dariya. Raka Al'ameen
duka sukayi seda yayi dagaske Ramlah ta yarda ta sauk'a. 5k ya bata inda Mama tayi
godiya sannan taja hannun Ramlah dake ta faman yiwa Al'ameen ba-bye shiko se biye
mata yake, dana Ummie sukayi ciki.
"Toh Zainab zan wuce."
"Toh Ya Al'ameen ka huta gajiya mun gode."
"Ba komai" har an bud'e mai k'ofan mota ya kusan shiga Zeezee ta kirasa a nitse.
A hankali ya juyo yana kallonta wani k'war jini taga ya sake mata all she wants is
HIM.
Shiru tayi kuma ta kasa magana se kallonsa take "Zainab?" ya kira sunanta.
"Na'am." Ta amsa a hankali idonta a k'asa.
"Lafiya koh?" Takawa tayi seda ta matso d'an kusa dashi kad'an sannan ta soma da
cewa;
"Ya Al'ameen don Allah kayi hak'uri ka yafemin rashin hankalin da nayi ta maka
lokacin da nake gidanka, I want you to know that I've regretted every single thing
I've done to you. Alhak'inka ba k'aramin bina yayi ba, please forgive me Ya
Al'ameen am truly sorry." Totally speechless ya tsaya yana kallon Zeezee dama tana
da hankali ta kuma iya tsara magana haka? this is where she is wrong saboda tun
rananda ya sake ta ya yafe mata komi. Tausayi sosai Zeezee ta basa, he never wished
for her life to turn out this way. Me take nufi da alhak'insa ya riga binta? Is
that the reason why suka rabu da mijinta? Maltreating nata yayi tayi shine har ta
zube ta rage haske haka? (Wai anan ma don be ganta time da ta fito sabo-sabo ba
daga gidan Adeel.)
"Zainab..." ya kira sunanta finally cike da tausayi.
"Ya Al'ameen I know its hard for you to believe me but wallahi na tuba please
forgive me ko I can be free nima."
"Zainab" ya sake kiran sunanta this time more slow.
"You can't forgive?" Hannu tasa ta share rolling tears nata, "I've asked too much
huh? nasan abubuwan da na maka are unforgettably unforgivable ina me sake baka
hak'uri Ya Al'ameen. Even though bazaka yafemin ba just know that I'm deeply sorry
for the fact that I disrespected you as my husband, I can't ever be in peace har se
in ka yafemin, thank you listening to me anyway." Tana kaiwa nan ta juya cikin kuka
zata koma ciki. Da sauri ya rik'o hannunta restraining her, kasa juyawa ta kallesa
tayi saboda yadda kuka yaci k'arfinta wanda ba mugun d'agawa Al'ameen hankali yake
ba.
"Zainab" ya sake kiran sunanta a hankali. "Turn around kinji?" Sam ta kasa
juyawan "turn around and look at me." Da k'yar ya samu ta juyan da water bags a
idanunta.

"Look at me" ya buk'ace ta. Kai zallah take kad'a masa. "Look up kinji?" Instead
ta kalle san se kallon hannunsa daya rik'e nata take. Da ya gano hakan se yayi
sauri ya saketa "I'm sorry" ya fad'a calmly. Nan ma kai ta kad'a mai nufin its
nothing.
"Zainab I'm sorry kinji? I'm sorry for what you've gone through. Ni na jima da
yafe miki a very long time ago regarding dukkannin abubuwan da kikayi min fid
duniya wal akhira, kinji?"
"Are you sure Ya Al'ameen?" Ta d'ago kai tana kallonsa a yayinda hawaye ke
ambaliya akan kumatunta. "Ka yafemin duk abubuwan da na maka? All of it?"
"All of it Zainab." Hawayen jin dad'i ne kuma suka shiga tsiyaya daga idanunta.
"Thank you, thank you Ya Al'ameen finally my mind can be at ease." Hannu ya mik'a a
aljihunsa ya fito da hanky tare da mannawa akan cheeks nata yana share mata rolling
tears natan a hankali. Duk anan binsa da kallo kawai take a yayinda wutan sonsa ke
sake ruruwa a zuciyarta. She don't think akwai wanda ze iya gane mata just how much
she loves Al'ameen. Seda ya gama share mata hawayen sannan ya d'aga hannunta ya sa
mata hanky'n a ciki tare da kullewa da other hand nasa. "Don't cry again kinji?
"Kai tamai nodding tana forcing out a smile. "Thank you Ya Al'ameen."
"Always welcomed Zainab, koma ciki kinji?" Be shiga mota ba se da yaga shigewar
Zeezee ciki.

Zeezee na k'arisawa ciki ta ruga d'akinta a guje tare da wurga kanta bisa gado
ta shiga rusa kuka. Hanky'n daya batan ta rungume tsam-tsam a daidai wajen
zuciyarta tana kuka sosai. Tana cikin wannan kuka Mama da jikokinta suka shigo,
tana ganinsu ta juya musu baya tana me cigaba da kukan.
"Granny mesa Aunty Zeezee ke kuka?" Cewar Ramlah.
"Ungo Ramlah rik'e hannun Ummie kuje kuyi wasa a parlour banda duka, ina zuwa."
"Toh Aunty Zeezee fah? Mesa take kuka?"
"Kuje ina zuwa." A hankali ta fito dasu Ramlah sannan ta koma ciki ta samu
Zeezee.
"Zeezee kuma kukan meh haka kike a idon su Ramlah?" Banza da ita Zeezee.
"Keda Ya Al'ameen ne?"
"Mama I love him and I want to go back to him." Tayi maganan in between tears.
"Toh Zeezee kika sani ko ya sake wani auren?"
"Mama be sake ba he told me himself."
"Zeezee kin manta da labarin Maman shi da sister'n shi ne?" Ita Zeezee gabad'aya
ma ta manta da rashin hankalin da tayi musu se yanzu da Mama tayi maganan su.
"Mama I'll call them each and ask for their forgivenesses I love Ya Al'ameen."
"Zeezee kina ganin yin hakan ba komai?"
"Mama bana son wata ta rigani auran Ya Al'ameen I can't take it."
"Toh nikam bansan me zance ba a irin wannan al'amari sekace Ya Al'ameen d'inne
autan maza."
"Just pray for me Mama, its all I ask."
"Toh Zeezee."
"Thank you."
"Toh kibar kukan haka ya isa."***

Kwana zaune Zeezee tayi a daren ranan tana tunanin ya zata 6ullowa Al'ameen da
wannan lamari, shi kam tasan mutum ne me sauk'in kai, problem d'in da za'a samu
daga gun Mom nasa ne da sistersa Sadiya. Washegari Zeezee ta saci idon Mama ta d'au
wayarta ta shiga contacts inda ta k'wak'ulo numban Mama Babba dana Hjy Sadeeyah ta
zuba a wayarta. D'akinta ta koma inda seta soma dialing numban Mama Babba sekuma ta
katse, tayi hakan kusan sau hud'u ana biyar ne tabari ya shiga inda tayi mata one
missed call amman bata d'aga ba kasancewar bata kusa. Se a karo na biyu ta d'aga
tare da yin sallama nan itama Zeezee ta amsa tare da gaisheta.

"Ina kwana Mama?"


"Lafiya k'alau" ta amsa ba fara'a sosai kasancewar bata gane wake maganan ba.
"Zainab ce Mama."
"Toh Zainab, Zainab wacce kenan 'yata?"
"Zainab ex wife na Ya Al'ameen."
"Aww Zeezee?"
"Eh Mama."
"Kina nan ashe, sannun toh Zeezee."
"Ina nan Mama."
"Ya hak'uri kuma? Baba lokaci yazo yayi, Allah ya jik'anshi da rahama ya cigaba
da baku ikon juriya."
"Ameen ameen Mama nagode. Mama don Allah kiyi hak'uri regarding abinda nayi maki
da Hjy Sadeeyah back then, I was young and stupid ku gafirceni don Allah na tuba
bazan k'ara ba."
"Masha Allah, Zainab naji dad'i da har kika gano kuranki kika gyara sannan kuma
kika nemeni musamman don jin yafiya na, I want you to know a matsayinki na 'yata na
yafe miki kinji?"
"Alhamdulillah Mama, jazakillahu khairan. Naji dad'i sosai thank you so much
Mama."
"Ba komai Zeezee ya mamanki?"
"Lafiyarta k'alau tana gaishe ki ma."
"Toh ina amsawa, ya mai gidan naki kuma?" Shiru Zeezee tayi tama kasa amsata
"hello Zeezee?"
"Na'am Mama?"
"Ba ki jina ne? Nace yamai gidan naki?"
"Mama ina gida ne yanzu, auren nawa ya jima da mutuwa tun kafin Baba ya rasu.
Wallahi hak'k'in Ya Al'ameen, da naku dana su Mama da Baba shi ya rink'a bina
tabbas nayi nadaman duk wani abinda na aikata, rashin kyautatawa Ya Al'ameen dana
rink'ayi shi na tarar a gidan Adeel, I hated myself for going against umarnin Baba
and disrespecting you guys all, ina me sake baku hak'uri."
"Allah sarki Zeezee, we all learn from our mistakes ina fatan de bazaki sake
tafka wannan mistake ba saboda shi mu'mini ba a sokinshi a rami biyu."
"In shaa Allahu Mama nagode."
"Ba komai, ina miki fatan Allah kawo miji na gari." Da k'yar ta iya cewa "ameen"
a zatonta ma ko Mama Babba zata ce mata zata dawo da ita gidan Ya Al'ameen ne,
amman ashe ba haka abin yake ba.
"Jiya ma Ya Al'ameen yazo nan har gida yayi mana ta'aziyyah."
"Ayyah Allah ya bada lada, yazo Bauchi duban abu ne kinsan ya kusa aure shima zamu
aura masa wata 'yar uwarsa anan Kaduna." Dum! Zeezee taji zuciyarta ta buga sosai,
she couldn't hold back the tears anymore, zuba kawai suka soma shikenan abinda take
gudu ya riga ya faru, wata ta riga ta sa'an Ya Al'ameen. Just how bad ta cuci kanta
a rayuwa? Da k'yar ta iya cewa "ayyah, Allah shi basu zaman lafiya."
"Ameen" Mama Babba ta amsa.
"Toh Mama se next time nagode ki gaishe dasu Aysha."
"Yauwa ki gaishe da Mamanki zasu ji" anan ta katse. Kuka me sauti sosai Zeezee ta
rushe dashi a d'akin.

Bata bar kukanba har seda bacci 6arawo ya saceta. Koda Mama ta dawo daga
islamiyyar safenta ta tarar da ita tana bacci bata kawo tunanin komi a ranta ba
taja mata k'ofar. Se chan da Azahar tazo tada ita Sallah inda anan tayi noticing
yadda idanun Zeezee suka kumbura.
"Lafiya da kumburarrun idanuwa haka Zeezee?" Kai zallah ta gyad'a tana k'ok'arin
shiga bayi.
"A'a dawo nan, dawo ki zauna."
"Mama babu zanyi alwala ne."
"Nace ki dawo" bata sake gardama ba tazo ta zauna a gefenta.
"Kuka kikayi koba haka ba?" Batayi k'arya ba ta gyad'a kai.
"Dalili?"
"Mama..." sekuma tayi shiru.
"Ehemm ina jinki."
"Mama I called Mama Babba..." duk yadda sukayi da Mama Babba ta gayawa Mama tana
kuka sosai. Kwantar da kanta Mama tayi a jikinta tana bubbuga bayanta "shhh its
okay kinji? Kede ki cigaba da addu'a kawai Allah ya kawo miki miji na gari ba
lallai se Ya Al'ameen ba."
"Mama but ni shi nakeso, banason kowa se shi."
"Toh Zeezee ya zakiyi? Wata ta riga ta rigaki dole ki rungumi k'addara kiyi
hak'uri."
"Mama banjin zan iya hak'ura da kalan soyayyan da nakeyi wa Ya Al'ameen, this
feeling has never happened to me. Gani nake as if idan ban sake kasancewa matarshi
ba ina iya rasa raina gabad'aya." Da sauri Mama ta d'agota daga jikinta, "kinada
hankali kuwa? Banason sake jin maganan nan daga bakinki kina jina ko?"
"Mama all I want is to be with him and make him happy, I love him so much."
"I know shiyasa nace ki dage da addu'a, idan you and Ya Al'ameen are destined to
be together once again you two shall remarry have faith okay?"
"Okay Mama thank you."
"Tashi kiyi alwala kiyi sallah na riga na had'a lunch."
"Toh Mama thank you." Mama na ficewa ta nufi bayi tayi alwala ta idar da
sallanta. Hanky'n Al'ameen daya bata jiya wanda ta adana sa ta ciro tare da kaiwa
kan hancinta tana shunshuna daddad'an turarensa me sanya mata kwanciyar hankali.
Kaman jiya yau ma ta yini tana tunanin Al'ameen. Da daddare kamin ta kwanta ta kira
Hjy Sadeeyah inda ta gaisheta, bayan gaisuwa Hjy Sadeeyah tayi mata ta'aziyya
sannan Zeezee ta nemi gafararta itama sosai. Tun Hjy Sadeeyah batayi niyyan yafe
mata ba amman jin yadda Zeezee tad'an bata highlights kad'an daga kalan rayuwar
auren da tayi living with Adeel yasa tuni ta yafewa Zeezee takuma tausaya mata
sosai inda tayi mata addu'a kan Allah ya kawo mata miji na gari daze kula da ita.
Zeezee na son sanar da Hjy Sadeeyah akan tayi mata hanya ta dawo da ita wa Ya
Al'ameen koda kuwa as his second wife ne zata dawo, she don't care tanaso muddin
she'll be able to show him love and comfort amman ta kasa gaya matan saboda batada
courage haka tana ji sukayi sallama. Kuka kuma ta d'auro daga nan har bacci 6arawo
ya sace ta inda tayita mafarke-mafarken Al'ameen. Washegari da safe bayan ta gama
chores nata ta lalimo wayan Mama ma yau ta kofi numban Ya Al'ameen. So take ta
kirasa taji idan still yana gari amman ta gagara seya kusan shiga seta katse. At
long last ta samu ta kira san.
"Hello" ya fad'a a lokacin da yayi picking. Muryansa da bata iya ignoring ne ke
neman wullata dreamland wanda tayi sauri ta amsa da "Ina kwana Ya Al'ameen?"
Yana jin muryar ya gane nata ne, "Zainab."
"Na'am Ya Al'ameen ina kwana?"
"Lafiya kin tashi lafiya?"
"Lafiya ya gajiya kuma?"
"Alhamdulillah."
"Uhn nace kana gari ne ko har ka tafi?"
"Ina nan se gobe zan tafi yau zan kammala abinda ya kawoni in shaa Allah."
"Toh Allah ya taimaka, ko me ya kawo kan amma?" So take taji ko ze iya fad'a mata
da bakinsa aure ze sakeyi. Shiru yayi na d'an wani lokaci sannan ya amsata finally,
"Allah ya sake azurta ni ne Zainab, I'll be getting married in some couple of
months." Hannu tasa a face nata inda tajiyo hawaye sosai nata kan zuba, rawa
muryanta ke tace "Allah sarki, Allah baku zaman lafiya toh ya kuma tabbatar da
alkhairi. Whoever she is, she should know that she is lucky to be blessed with an
affectionate and patient husband as you, Allah bata ikon farinta maka." Besan me ba
amman seyaji dama be sanar da ita ba, ko be tambaya ba yasan kuka Zeezee ke don jin
yadda muryarta ke rawa sosai. Amman kuma why is she crying? Does she wants him
back? So take ta dawo mishi ne komeh? But anya? Ai Zeezee never loved him. Ignoring
this thought ya amsa addu'o'in da tayi mai da "ameen Zainab thank you kema Allah
had'aki da wanda zaki so ya kuma soki." A ranta tace that person is you.

Hawayenta ta share sannan tace, "kana gida ko?"


"Eh ina gida Zainab wani abu neh?"
"Lunch nakeso na kawo maka."
"No please you don't have to karki gajar da kanki zansa asiyomin."
"No please I insist Ya Al'ameen don't reject my offer please."
"Zainab seriously I don't want to be a burden to you."
"Shikenan toh" tayi maganan sounding sad and defeated.
"But in kinga its okay with you, ba komai nine da godiya."
"Thank you Ya Al'ameen."
"It is I who should be thankful."
"Sena shigo toh."
"Ki taho min da Ramlah."
"Ramlah zata islamiyya by then" ta amsa da murmushi kad'an a fuskarta wane yana
gabanta.
"Ayyah to ki gaishemin ita."
"Yauwa se anjima" jira tayi yayi hanging sannan ta sauk'e wayar ta ajiye a gefe.
Tunanin me zata girka masa ta shiga yi amman kwata-kwata she can't think of
anything. Haushin kanta taji for not paying attention before to know what dish was
her husband's favorite. Zama tayi ta shiga tunani sosai wani abinci yafi son siya
adan? miyan ganye da tuon shinkafa yafi siya da kuma rice and stew. Sanin bata iya
yin miyan ba yasa ta yanke hukuncin yi mai rice and stew.

In less than 3 hours Zeezee ta gama had'a basmati rice and stew nata daya sha
kaji dakuma co-slow nata a gefe together with kidney sauce. Cikin had'ad'd'un food
warmers na Mama da ake sawa Baba abinci aciki ta zuba mishi abincin, tana d'ago
flask d'in kawai ta tuna da Baba. Zama tayi a kitchen din tayi mai addu'a da dama
harda 'yar k'wallarta sannan ta tofe ta juye abincin ciki ta shirya komi cikin wata
fancy basket sannan ta ajiye kan counter ta nufi d'akinta don yin wanka ganin sha
biyu ya wuce.

Tana cikin wankan ne Mama ta dawo daga islamiyya inda ta nufi kitchen dan shan
ruwa, achan ta tarar da basket da Zeezee ta had'an. Bata ta6a ba ta wuce d'akin
Zeezee anan ta tarar da ita tana wanka. Zama tayi ta jira fitowarta inda take
tambayarta "waya kawo basket dake kitchen?"
"Ba kawowa akayi ba Mama."
"Ba kawowa ba? Ban fahimta ba."
"Ni na girka naki dana Ya Omar nakan dining table."
"Wancan kuma fa?" Tayi maganan tana pointing direction na kitchen.
"Na... na..." sekuma tayi shiru.
"Ki gayan mana na waye?"
"Na Ya Al'ameen ne."
"Oh ni Hafsah! Yanzu girki kikayi ma bawan Allan da bakisan ko yana gari ba
kokuwa a'a?"
"Mama I called him and asked yace min se gobe ze tafi."
"Toh me had'in ki da kai masa abinci? Se ya fassaraki tukun ko?"
"Mama fassaranin nake so yayi saboda yasan I love him ko ze tausaya min ya dawo
dani koda as his second wife ne ni ban damu ba."
"Oh! Toh nikam babu bakina acikin wannan abu."
"Eh naji amman please kice Allah bani sa'a kinji Mama?" Shiru Mama tayi danko
Zeezee bata isheta da kallo ba. "Please..." ta sake pleading.
"Naji Allah baki sa'a."
"Ameen Mama thank you."
"Ze aiko masu gadinsa ne su zo su kar6o koya?"
"Ni zan kai masa."
"Oh! Zainab!"
"Please Mama karki min baki kince Allah bani sa'a ya isa kinji please." One more
look Mama tayi mata sannan ta miqe tare da ficewa.

Nan da nan Zeezee ta shafa mai tasa kaya tayi Sallah sannan tayi applying light
makeup wanda ya mugun amsarta ba kad'an ba. Material gown na tiger design red and
brown tasa tare da yafa red gyale a kanta ta nannad'e a wuyanta. Shoe and bag nata
ma red tasa, tana cikin aikin feffesa turare wayarta ya shiga ruri. Ganin Ya
Al'ameen na flashing akai tayi sauri ta d'aga "hello Ya Al'ameen?"
"Zainab nace ba sekin fito ba I'll send Saje yazo ya kar6a abincin kinji? " Shi
Al'ameen besan zuwanta da biyu bane, k'arya ta had'a mai tace ta riga ta fito
saboda zata wuce gidan friend nata daga nan.
"Oh, toh shikenan sekin iso." Nan ya katse. Tana gama abinda zatayi tayi sallama
da Mama sannan ta fice. Tun rabuwanta da Al'ameen bata sake taka corner'n gidan
nasu ba se yau, ji take ina ma ace ya dawo da ita d'akinta ne. Tana k'arisawa gaban
gidan tayi parking a waje sannan ta fito da basket d'in ta danna bell. Within
seconds guard yazo ya bud'e tare da yi mata sannu da zuwa. Basket d'in yaso amsa
amman ta hanasa, sebin gidan take da kallo a yayinda take sake missing gidanta
sosai. A parlour ta tarar da Al'ameen yana sanye da farar vest revealing his
muscular body da kuma sky blue wandon jamfa. Tana shigowa ya miqe tare da yi mata
sannu da zuwa, se kallonsa take ta kasa dena staring. "kuma su Saje suna kallonki
basu kar6eki ba?" Kai tayi shaking da wuri;
"No ni na hanasu, its no big deal" ta amsa tare da ajiye basket d'in kan centre
table.
"Toh Zainab thank you kinji? Ya Mama."
"Lafiyanta k'alau" ta amsa still a tsaye tana wasa da bakin gyalenta. So yake
yace mata ta zauna amman kuma ganin how awkward it'll sound yayi shiru. "Toh ni zan
koma."
"Toh Zainab thank you" d'aya daga cikin throw pillows dake kan kujeran da ya
tashi akai ne ya d'aga tare da d'ago kud'in dayasa cikin wata envelope.
"Zainab" ya kirata alokacin da har ta juya ta soma tafiya. Chak ta tsaya tare da
amsawa "na'am?"

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣0⃣

Takawa yayi har izuwa gabanta sannan ya miqa mata envelope d'in. K'in amsa
tayi instead seta tsaya tana kallonsa bewildering. "Amsa Zainab naki ne."
"Nawa kuma?"
"Don't reject my offer also amsa kinji." Kai tayi saurin kad'awa "no Ya Al'ameen
thank you ni don Allah na kawo maka."
"I know ni kuma as kyautatawa nake son na baki, amsa kinji?"
"No tha-" bata k'arasa maganan ba ya d'aga hannunta ganin haka tayi saurin kulle
tafin hannun nata. "Yi hak'uri ki kar6a kinji?" Kai kawai take kad'a mai, "in kira
Mama ince na baki kyauta kin k'i kar6a?" Nan ma kan ta sake kad'awa. "Toh bud'e ki
kar6a kinji?" Seda yayi dagaske sannan ya samu ta bud'e hannun yasa mata envelope
d'in tare da kullewa. "Thank you kinji?" Me yake shirin gani? Kuka Zeezee ta rushe
dashi a wajen.
"Oh God! Zainab did I say something wrong? I take it back" Kai kawai take kad'a
mai ta kuma kasa dena kukan. "I'm sorry Zainab please kibar kukan, in kud'in ne
bakiya so I'll take it back but please stop crying" yayi maganan har yanzu yana
rik'e da hannunta. Ba kalan surutun da Al'ameen beyi ba gabad'aya Zeezee ta tayar
mishi da hankali gashi duk maganan da yayi mata sede ta kad'a mai kai. At long last
tayi magana tace, "ba kai bane Ya Al'ameen." D'an relief yaji "toh wayene?" Ya
tambayeta sede Shiru ba response. "Tell me kinji? Is this about your Ex?"
"No."
"Then waye?"
"Ya Al'ameen I want you back, I want to go back to you, I want to be your wife
once more." Ta furta tana kallon k'asa. Hannunsa dake rik'e da nata ya sake a
hankali cike da mamakin jin wannan kalamu daga bakin Zeezee. Da sauri ta d'ago kan
ta tana kallonsa. "I know am wrong to say this, you'll be getting married in some
couple of months but I can't keep it in again. I love you Ya Al'ameen, I love you
so much that I can't afford to lose you for the second time, koda as your second
wife ne bring me back, I just want to make you happy one last time." Tunda ta fara
maganan kallonta Al'ameen ke as yadda take kallonsa itama tana hawaye. He never
expected to hear all of these words from Zeezee. Since when ta fara sonshi? Why him
and not Adeel yanzu? Meya faru tsakaninsu da bata maganansa yanzu? Wani irin
cutarwa yayi mata har yasa bata sonsa haka yanzu?
"Zainab..." ya kirata a nitse.

"Please don't say no Ya Al'ameen, in kana ganin Mama ko Hjy Sadeeyah bazasu yarda
ka dawo dani bane thats not true. I've called them both and have asked for their
forgivenesses kuma sun yafe min. I just want to be with you and make you happy, I
want to prove to you just how much I love you Ya Al'ameen. I can wait, koda it'll
take me eternity ne muddin ka amince zaka dawo dani d'akina, please don't say no.
I'm sorry if my words have offended you but I just need you to know how I feel
about you." Ta k'are maganan cikin kuka sosai wanda ta mugun bawa Al'ameen tausayi.
Just what hell did she went through a rayuwar ta da Adeel? Ji yake kaman yaje ya
6a66alla Adeel into pieces for hurting Zeezee like this. Jin yayi shiru har yanzu
tace, "I should go, thank you for listening to me." Hannunta ya rik'e immediately
tana juyawan, chak ta tsaya kanta na pointing downwards. Hannu yasa a aljihunsa ya
zaro hanky sannan ya d'ago face nata ya shiga share mata rolling tears nata
affectionately. "Don't cry again kinji?" Da k'yar ta iya nodding masa kai saboda
wasu sabin hawayen da takejin suna shirin 6allo mata. Hanky'n kawai ta kar6a ta
juya ta fice a guje se gun motarta inda ta zauna tayita shar6an kuka, gidansu
Lubiee da take son zuwa ma bata jin zata iya zuwa yanzu. Seda ta tsagaita kukan
nata sannan taja motarta ta koma gida inda har ta isa d'akinta Mama bata ganta ba.
***
Abincin da ta kawo mishi ya d'iba kad'an a plate amman ko kad'an ya kasa ci
saboda tunanin Zeezee zallah da yakeyi. Duk irin aromatic taste da abincin nata
yayi masa ya kasa yaci kamar yadda yakamata don tunaninta dayake tayi. He knows
exactly what she must be going through, saboda he went through it before shima.
Baze iya zama yana ganinta tana shan wahala haka ba knowing there's something he
can do. Tausayinta yake sosai but inhar Mama tace she ain't letting him ya dawo da
Zeezee dole ta hak'ura kaman yadda shima ya hak'ura ya cireta daga ransa lokacinda
ta auri Adeel. Even though har yanzu yana son Zeezee, but not as before ko a yanzun
ma ze dawo da ita ne saboda abinda take so ne not because he loves her as he does
before. Yanzu bama wannan ba, Mama Babba zata yarda ne ayiwa 'yar uwarta Murja
kishiya? Ji yayi tunaninsa gabad'aya ya dak'ule mai dan dole ya fita ya shiga
training men nasa in order to let go off tunanin nata. Kamar yadda take son miyar
da tunanin Al'ameen hobby, haka yau ma ta yini ta kuma kwana da tunaninsa. Koda
Mama ta tambayeta ya suka k'are da shi ce mata tayi babu ta kai mai abincin ne
yabata kyautan d'imbin kud'ad'd'en data nuna mata d'azu.

Washegari Al'ameen ya shirya ze koma Kaduna, half of him is telling him ya sanar
da Zeezee while half of him na ce masa ya basar. Har ya shiga mota sun d'au hanya
se kuma yaga be kyauta mata ba don haka yayi asking driver'nshi da yayi parking
sannan ya kirata. Kaman me jiran call nasa kafin ya shiga ringing ta d'aga tare da
yin sallama.
"Wa'alai kumus salam Zainab."
"Ina kwana Ya Al'ameen?"
"Lafiya ya gajiyan ki na jiya?"
"Ba gajiya."
"Kaman kinsan rice and stew is my fav, thank you kinji? Ashe Zainab namun is
such a great cook."
"Kai Ya Al'ameen banda zugi."
"Seriously fa ga ragowan nan nayi heating kafin mu isa KD zan tsaya inci."
"Aww har kun d'au hanya ne?"
"Eh nace bari na sanar dake."
"Toh Allah ya kare hanya ya kaiku lafiya Ya Al'ameen."
"Ameen Zainab thank you ki gaishe da Mama."
"Zata ji in shaa Allah safe journey."
"Thank you" yace tare da katse wayar. Wayar ta miyar kan heartbeat nata tare da
rungumewa tsam, ji take as if Ya Al'ameen d'in take hugging. Remembering the
thought that jiya fa bayan data fayyace mai abinda ke zuciyarta har izuwa yanzu
bece komi ba taji she is broken again. Bata da fatan da yafi Allah yasa Al'ameen ya
dawo da ita d'akinta, she know she can count on him saboda yadda yake sonta se inde
time da sukayi spending apart yasa ya mance da ita, which she believes not.

*****
Isan Al'ameen gida wato Kaduna ya nufa site nasa direct inda aka shirya mishi
komi tsaf for his arriavl. Bathroom ya fad'a ya watsa ruwa. Yana fitowa yajiyo
knocking daga bakin k'ofa, sanin its no other than Mama yaje kai tsaye ya bud'e
mata. "Oyoyo my only son" ta fad'a tare da hugging nasa not minding how wet his
body is.
"Kai Mama, har kin tashi kenan" yayi maganan yana k'ok'arin k'wato kansa daga
rik'on da Mama Babba tayi masa "Shigowa na gateman yace min kina bacci."
"Eh mana shigowanka yasa na nemi baccin nawa na rasa, ya hanya?"
"Lafiya" ya amsa sama-sama.
"Toh kuma bazaka matsa min in shiga ba se nace ka matsa tukun?"
"Mama kije zan zo in sameki, kinga bako kaya a jikina."
"Jimin d'a!" Tayi exclaiming "mene a jikin naka ban ta6a gani ba mschw! matsa min
do Allah." Ganin baida niyyan matsawan ta tunkud'esa tasa kai abinta. "God help me"
ya furta a ransa sannan ya koma d'aki inda ya barota a parlour. Three quarter wando
ya sanya da free sized T shirt sannan ya fito. "Harka sa kayan ne?"
"Eh."
"Muje dining kaci abinci."
"Bana jin yunwa."
"Ka taso daga tafiya kace bakka jin yunwa? How's that possible?"
"Naci a hanya."
"K'arya ne ai baka tsayawa a hanya da sunan cin abinci."
"Noo daga Bauchi na taho dashi."
"Toh! Wace 'yar albarkan muka samu achan tama girki?" Murmusawa yayi alokacin da
yake neman zama kan kujera a gefenta sannan yace, "Zeezee."
"Kai dan Allah Son!" Tayi exclaiming.
"Dagaske fa."
"Ayyah Zeezee, yarinyar tayi hankali yanzu wallahi d'azun nan ma ta kirani tace
min kana hanya yau."
"Ayyah." Ya amsa yana unlocking wayansa.
"Kaji wai sun rabu da mijinta ko?"
"Haka take fad'amin."
"Da alama kuma tasha wuyan auren don har take cemin in yafe mata alhak'inmu ne
yak'i barinta mu yafe mata don Allah, nide na yafe mata haka Hjy mah."
"Ayyah wallahi ko baki fad'a ba Mama, Zainab kaman ba ita ba ta rame ta rage
haske."
"Ayyah toh Allah kawo mata miji na gari da ze kula da ita ya kuma rik'e ta amana,
marainiyar Allah."
"Ameen" ya amsa cike da tausayinta. Kaman ya bud'e baki zeyi magana sekuma ya
fasa. Take Mama ta gano hakan "Son kayi shiru fah?"
"Dama magana nake ne?"
"Kaman zakayi se kuma kayi shiru."

"A'a forget, Mama ina son in d'an huta gobe zan koma office kindly excuse me
kinji? I love you."
"K'arya kake Al'ameen, ina nan ba inda zani, there's something going on your
mind, what is it?"
"Babu Mama" yayi insisting "I just want to rest that's all."
"Karka fad'a tayi tsami ma ji, rest well." Tana kaiwa nan ta fice mai anan ya
miqe kan kujeran yana me tunanin Zeezee. Yana cikin hakan yajiyo ringing d'in
wayarsa, da kai dubansa yaga Zainab na flashing akan screen d'in, without
hesitation yayi sliding. "Hello Ya Al'ameen?"
"Na'am Zainab."
"Ya hanya? Ka isa lafiya?"
"Lafiya Alhamdulillah."
"Toh Masha Allah just called to check up on you."
"Toh Zainab thank you."
"You're welcome" daga nan ta jira yayi hanging. Hannayensa ya had'a gu d'aya a
k'eyarsa yana me zura wa ceiling ido. Through out ranan a ciki ya yini, tonight
Mama Babba ta kawo masa dinner da kanta tayi serving nasa sede har yanzu yak'i kai
spoon baki. Zama tayi a gefensa tana k'are mai kallo. Ba haka Al'ameen nata yake ba
what must be wrong with him?
"Al'ameen?" ta kira sunansa sede sam hankalinsa bayi jikinsa bale ya amsata.
"Muhammad Al'ameen!" Ta kirasa da k'arfi. Spoon dake hanging a hannunsa ya yasar
a rikice. "Ka jini ai yanzu."
"Haba Mama! Kunne na."
"Rufa min baki do Allah, duk k'arfin murya na yakai na bindigan da kuke har6awa
kullum ne?"
"Ni bacci nakeji, akwai tafiya a gabana gobe." Yayi maganan da nufin tashi, shirt
nasa ta kama forcefully making him to sit back.
"Ai sekaci abincin nan wallahi bazaka min kwante da abincin rana ba na daren ma
kace haka seka ci."
Toh ki sake ni."
"Nak'i se kaci wallahi ai na rantse."
"Mama wai in tambayeki."
"Ina jinka amman zauna tukuna." K'in sake sa tayi dan dolensa ya zauna, "how old
am I?"
"43 going to 44 koba haka ba?"
"Toh kema kin fad'a am 43 kinga ko am old enough to take care of myself, ba sekin
rik'a sani cin abincin dole ba."
"Ai ni kallon yaron da na yaye sa jiya nake maka gomma kaji ka sani don haka
zauna kaci abincin nan, kai kam Murja na ta huta da girki wallahi sam kaman ba na
miji ba bazaka zauna ka gabzi abinci ba? Zauna nace!"
Chan k'asa-k'asa ya ce "gobe zan tafi ma ai kowa ya huta."
"Na jika kuma, ka ga dama ka tafi a daren yau ma abinci ne sekaci." Haka dan
dolensa ya shiga cin abincin seda yaci rabi Mama Babba ta yarda taja plate nata
gefe. Kaman d'an yaro haka take tattalin Maj-Gen tana bala'in sonsa da kuma ji
dashi kodan shi kad'ai ne d'anta oho. Har d'aki ta rakasa sannan ta zauna gefen sa.

"Al'ameen?"
"Na'am Mama."
"Meke damunka?"
"Babu wani abu ne?" Hannu ta mik'a ta make sa a hannu. "Awch! Whats that for?"
"For lying to me, Wai in haifeka kake tunanin zaka iya 6oyemin wani abu? Gayan
meneh? Batun Murja ne?" Kai zallah ya kad'a mata. "Baka koyi sonta ba har yanzun?"
"Mama ba ita bace please."
"Then wace ce?"
"Zainab ce."
"What about her? Bade wai kanason ka dawo da ita d'akinta ba?" Shiru yayi mata
"da kai fa nake magana Al'ameen? Murja fah? Bama wannan ba ita Zeezeen tace maka
tana son dawo maka ne da zaka ce kai zaka dawo da itan?" Tashi yayi ya zauna, "what
if she really did? " Ya tambayeta.
"Did what Maj-Gen.?"
"Did ask me to bring her back."
"No thats a lie, k'arya ne har Zeezeen ne zata ce ma tana son ka maido ta
d'akinta?"
"Mama zan miki k'arya ne?"
"Bazaka min ba kam am-"
"Aswear to you, she came to me crying like a soaked puppy in the rain tana
pleading d'ina kan nayi hak'uri na dawo da ita d'akinta koda as second wife zan
dawo da ita, bayan Murja kenan she don't care, I so much pity the girl Mama." Hannu
kawai Mama ta dafe a bakinta, totally out of it. "Kai me kake gani yanzu? Kana
ganin dagaske take bawai so kawai take ta sake cin kud'in ka ba?"
"Not all Mama" nan ya zana mata yadda sukayi da Zeezee kamin ta yarda ta amshi
kyautan daya batan mah.
"Oh ni Mama Babba! Amman kenan seda shi Adeel nata ya juya mata baya zata zo tace
tana sonka? You are like her second option fa kenan."
"I don't think thats so, ko ban tambaya ba Mama nasan shi mijin natan nason dawo
da ita yanzu saboda Zainab ta cika 'ya mace aduk inda ake neman hakan."
"Kana nufin to say Zeezee na sonka kenan yanzu fiye da yadda takeson Adeel ne ko
waye d'in?"
"Exactly, her words said it all."
"Allah sarki marainiyar Allah, Al'ameen kace da bakinta tace maka ka dawo da ita
d'akinta?"
"Da zan miki k'arya ne Mama abinda yake ta bothering d'ina kenan nima, ta gaji
da zaman zaurancin da takeyi cause she told me tun kafin rasuwan Baban nasu suka
rabu da mijin. Kinga its been a while kenan."
"Tabbas! So kai me kake gani yanzu Al'ameen? Zaka dawo da itan?"

"I don't know Mama, koda zan dawo da ita ma ai se keda Hjy kunyi approving tukuna
regarding abinda ya ta6a shiga tsakaninku."
"In don wannan ne ka ajiye a gefe saboda ni na yafewa Zeezee, abin a tausaya mata
ne yarinyar, matsalar daga kaine yanzu."
"Daga ni kuma Mama kaman ya?"
"Kana ganin zaka iya rik'e mata biyu ka kuma yi adalci a tsakaninsu?" Kai yayi
saurin kad'awa "gaskiya no Mama I can't assure you of that saboda ni auren mace
fiye da d'aya baya daga cikin tsari na."
"Toh kaji inda matsalar take kenan.
If you have to choose tsakanin Zeezee da Murja wa zaka d'auka?"
"I don't know either, but kinsan right from the start ni Murja bata wani kwanta
min ba, bawai ta gaza ta wani fannin bane kawai bata cikin tsarin matan da nake so
ne."
"And Zeezee?"
"I love her Mama even though not as before but har yanzu she holds a special
place in my heart."
"Toh Son nikam bansan ya zamuyi ba gaskiya, dole cikin su d'aya ta hak'ura tunda
baka iya ajiye mata biyu kace."
"I know Mama zan bawa Zeezee hak'uri kawai."
"Why?"
"Saboda I can't keep two wives."
"But kace baka son Murja."
"Yeah bana sonta amman ai ke kina sonta ko?"
"You mean don ni zaka auri Murja?"
"Your happiness means the world to me."
"Iyyeh Yaro na ya girma, yanzu ka gaya min wa kakeso ka aura acikinsu, Zeezee or
Murja?"
"If I'll have to choose Zeezee, but Murja fah? She loves me also and I don't want
to hurt her."
"Karka damu Murja d'iya ce me hankali da kuma tunani. Ni na soma had'aku ai zanyi
mata magana muji me zata ce inhar ta nuna zata iya yafe son da takeyi maka kaga
shikenan seka dawo da Zeezeen ka saboda ni abinda kakeso nima shi nakeso."
"Are you sure about this Mama?"
"I am Son, tunda har Zeezee ta iya tinkararka ta fad'i maka da bakinta akan ka
dawo da ita d'akinta kam ai abu ya lalace am sure no matter what she won't ever
hurt you again."
"Thank you Mama" ya tashi da niyyan hugging nata.
"Matsa min do Allah! d'azu dana ke maka oyoyo ba tureni kake ba? Kaima ka d'ana
bouncy'n kaji idan da dad'i." Yana dariya sosai wanda ya bayyano da white perfect
teeth nasa yace, "hakane Mama? Shikenan nayi accepting bouncy'n but can I hug you
now?" Murmushin ta miyar masa sannan sukayi breaking into a mother-son hug. "Am
damn proud of you Al'ameen Allah ya cigaba da yima albarka yakuma farinta maka
kaman yadda kaima kake farinta min."
"Ameen Mama thank you." Ya fad'a tare da breaking hug d'in.
"Allah yasa decision naka na dawo da Zeezee d'akinta ya zamo the most best
decision of all."
"Ameen I love you."
"Toh kar tsohuwarka ta cika ka da surutu bari na barka ka kwanta naji se k'orafi
su Aysha suke wai da zaran ka dawo nake share su."
"LOL tell them gobe ma zan koma."
"Ai kuwa deh kwanta ka huta Baba na seda safe."
"Allah ya bamu alkhairi Mama."

****
Washegari da safe Al'ameen ya wuce Abuja. Kafin Mama taje ta samu iyayen Murja
da ita Murjan kanta seda ta tambayi shawara gun Hjy Sadeeyah inda itama ta goyi
bayan shawaran sa Mama da Al'ameen d'in suka yanke d'ari bisa d'ari. Anan ne itama
take sanar da Mama kad'an daga cikin wahalallen rayuwan da Zeezee tayi living a
gidan Adeel, giving Mama Babba more reason to return Zeezee back to her only son.
Cikin tsan-tsan fahimta da nitsuwa Mama Babba da family'n Murja suka fahimci
juna, inda itama Maman Murjan take sanar da Mama cewa daman Murja itama nada wanda
takeso amman dan nauyi da kuma girmamawan da sukeyi ma Mama Babba yasa koda ta fara
kawo shawaran had'a Al'ameen da Murja basu nuna mata hakan ba, so walillahil hamd
yanzu zasuyi mai magana ya turo magabatansa. Hak'uri Mama Babba ta sake basu insa
suka sake nuna mata sufa ba komai bata yi musu komi ba. Fatan Allah bawa Al'ameen
da matarsa zaman lafiya sukayi mata inda itama in return tayi musu haka. Bayan ta
dawo gida ne ta kira Zeezee kasancewar tayi saving lambarta ranan. Be jima ba
Zeezee ta d'aga tare da yin sallama suka gaisa sannan Mama Babba tayi moving
straight to the point without hesitation.

"Uhm so Zeezee jiya Al'ameen yake sanar dani dukkanin abinda ya gudana a
tsakaninku, ina so ne inji daga bakinki tsakaninki da Allah kike kina son ki dawo
d'akinki nan gun Al'ameen?"
"Wallahi tsakani da Allah ne Mama, I can't tell you guys how sorry I am."
"We know Zeezee, ki gayamin meyasa kikeso ki dawo mishi?"
"Saboda ina son shi Mama, ban ta6a sanin Ya Al'ameen shine masoyina na hak'ik'a
ba seda Adeel wanda nayi mai sacrificing komi ya wulak'anta ni ya nuna min dabba ma
ya fini daraja a idanunsa. Yanzu haka shi Adeel har ya gaji da zuwa yana bani
hak'uri batun na koma mishi, harta magabatansa da mahaifiyarsa ya turo da su bani
hak'uri na koma mishi amman nak'i saboda na dawo daga rakiyarsa bana sonsa Ya
Al'ameen nakeso badan komi ba kuma nake son na dawo mishi illa don na farinta mishi
rai na kuma biya shi alkhairun daya min da a baya."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣1⃣

"Toh Masha Allah, in shaa Allahu zaki dawo d'akinki Zeezee, Al'ameen ze dawo
dake kinji?" Wani irin dad'i maras misanltuwa ne ya ziyarci zuciyan Zeezee wanda
tuni hawayen farin ciki suka soma tsiyaya daga idanunta. Kasa 6oye farin cikinta
tayi, "dagaske Mama? Kin yarda kuma Ya Al'ameen ya amince ze dawo dani d'akina?"
"Sosai ma Zeezee in shaa Allahu bade kuka kike ba?"
"Mama I have to, ban ta6a tsammanin zanyi witnessing rana makamancin na yau ba,
indeed you and your family are special souls sent from heaven to me. Nagode sosai
ban zata zaku yafe min haka har ki sake bani wani chance d'in ba. Allah ya saka
muku da mafificinsa ya kuma farinta muku kamar yadda kuma kuka farinta min. In shaa
Allahu zaku sameni me ladabi da biyayya da kuma kula muku da Ya Al'ameen da
dukiyarsa in all thank you so much." Mama na murmushi ta amsa da "ameen" a rayuwa
batada burin dayafi taga Allah ya kawo ma Al'ameen nata matar da zata sosa kamar
yadda Zeezee ke nunawa tana son Al'ameen nata yanzu. "Allah ya baku zaman lafiya,
ya kuma baku zuriyya d'ayyiba. Zanyi ma Mamanki magana in shaa Allahu in two weeks
time Al'ameen ze dawo dake saboda inason muyi celebrating re union naku." Kunya
sosai Zeezee ta jiyo, "Mama is that necessary please karku sa kanku wahala,
bazawara dani ma."
"Yimin shiru nikam kede kawai stay beautiful komin da zaki sa Aysha da Salmah
will take care of it."
"I will be lying to tell you just how grateful I am Mama nagode sosai, Allah
yabar zumunci."
"Ameen" anan Mama ta katse. Ji Zeezee ke kaman a mafarki dukannin abubuwan nan ke
faruwa wai ita da Major General Muhammad Al'ameen united again! She can't wait to
witness their married life again yadda zatayi showering nasa da soyayya zallah,
she'll love him with all that she have. Da gudu ta fice zuwa d'akin Mama domin
sanar da ita wannan great news inda taji Mama ma na akan waya, d'an tsayawan da
tayi ta fahimci da Mama Babba suke wayar. D'akinta ta koma ta kira Lubiee inda tayi
ta mata hauka, Ya Al'ameen ze dawo da ita and akwai party celebration da za'ayi
holding. Sosai best friend nata taji mata dad'i sosai suka yita murna.
Mama na gama waya da Mama Baba ta kirawo Zeezee, bayan Zeezee tazo ta zauna Mama
tayi gyaran muryarta.
"Zainab?" Ta kirata.
"Na'am Mama." Ta amsa a nitse.

"Ki bud'e kunnenki da kyau ki saurareni kinji ko?"


"Ina ji Mama." Tayi maganan kanta a k'asa.
"Kinfi kowa sanin the kind of hell you went through a gidan Adeel, don Allah yana
sonki ne shiyasa ya ku6utar dake daga hannunsa yakuma sake dawo miki da masoyinki
wanda both you and I couldn't believe so. Mama Babba ta sanar dani yadda komi ya
faru and tace she wants you back as her daughter-in-law again. Kinfi kowa sanin me
hakan ke nufi Zeezee, inhar tun yanzu kinsan bazaki zo ki kula mata da d'a ba tun
wuri ki sanar dani na fad'a mata. Kinfi ni sanin yadda matar nan ke son d'anta."
"Mama wallahi ina son Ya Al'ameen kuma am ready to sacrifice anything just for
his happiness, ina sonsa sosai and I'll take care of him as his wife."
"Allah yasa toh ya kuma baki iko."
"Ameen Mama."
"So tace min mu saurareta nan da two weeks tace da ba don Al'ameen is a bit busy
ba da a jibi anyi komi an k'are amman saboda yadda aiki ya mai yawa zasu ga nan da
sati biyun."
"Ba komai Mama Allah ya kaimu, nima kinga senayi amfani da wannan dama na d'an
yi gyaran jikina."
"Exactly" cewar Mama "kin kawo shawara." Nasiha sosai ta d'aura wa Zeezee akai.

****
Kamar yadda Mama Babba ta fad'a a cikin sati biyun suka samu suka had'a komi,
gobe in Allah ya yarda zasu wuce Bauchi where the luncheon will take place. Abinda
ya kama daga gown, takalmi, accessories duka da Zeezee zata sa Mama Babba tasa
Aysha da Salma sun tanadarwa Zeezee. Al'ameen sam be goyi bayan wannan luncheon
d'in tsiyan ba saboda how busy he is, da k'yar ya samu ya kar6i excuse nan ma don
ana ganin girmansa ne aka basa just some few days. Shi bek'i kawai a d'auko mai
matarsa ba a kai masa gida.
On Zeezee's side kuwa ba k'aramin gyara tasha ba, wani fari da kyau ta k'ara.
Magunan gyaran jiki na ciki dana waje da take sha da kuma amfani dasu kuwa sam bata
wasa dasu unlike before wani sa'in ma ita ke cewa Mama na gunta ya k'are a sake
amso mata wani. Anan ne Mama ta sake tabbatar da cewa lallai Zeezee is willing to
go back to Ya Al'ameen. 'Yan uwanta gabad'aya sun samu hallaro wannan taro, they
are damn happy for Zeezee for finally getting back the love of her life again.
Friends nata kap tayi inviting wannan re-union party inda suma suka ci ashobensu.

(Nima Miemiebee na gayyato manya-manyan bak'i na 'yan team Maj-Gen Al'ameen


erinsu Aunty Sis, Maman Fadeel, Maman Sultan, Queen Bilqees, Safiyya Galadanci, H.
jiddah, Mjay, Mrs. Muhammad, Ilhamerh, Shukrah, Fadeela Sagir, Bilkisu Babayo, Ummi
Hambali, Sa'adah Umar, Zainab. A, Sugrah, Aysha me littafi, Miss Fancy, Aasmaa Isa
Muh'd, Ummu Aysha, Biebiee dee, Ramlah Gokaru, and to all of members of team maj-
gen Al'ameen in my most honoured group miemiebee novels 2, my blog followers, YGC
fanclubs 1&2, miemiebee fans club 1,2 and 3 and to all members of Team Maj-Gen
around the globe. Duk na ganku kuna kwaso shoki😅👍)

Black gown me torches da adon white taci da black head inda Al'ameen yasha farar
babbar riga da aikin bak'i shima. Kallo d'aya mutum zeyi musu su tafi mai da
imaninsa. They just nailed it, ba abinda ya sake k'ayata party'n nasu kamar fara'ar
Zeezee ko wani juyi Mama Babba tayi sede ta kama Zeezee na murmushi unlike last
dinner'n su da tunda aka fara har aka gama ko hak'waranta basu gani ba. Zeezee
couldn't take her eyes off her man. Koda aka buk'aci couple da su tashi suyi rawa,
bayan Zeezee ta tashi ita ta miqawa Al'ameen hannu she is proud to show to the
world that this is the man, the love of her life. Sam ta kasa sake hannunsa, rawa
sama-sama Al'ameen yayi haka Zeezee ma. Seda Mama Babba suka fiffita ne ta zage
tayi rawa sosai dasu Lubiee tare da fans.

Indeed that day was an unforgettable one for Zeezee. Wane sabuwar amarya haka su
Mama Babba ke tattalin ta bayan sun gama luncheon suka wuce wani d'an opening again
inda sukayi bud'an kai suka yita wankan naira suna rawa, anan ne Zeezee ta tuna da
Baba se kuma tasa kuka, tana farayi Yasmeen ta kar6eta, se kan Maryam har Mama
sanda tayi kukan itama. Kafin a hankara suka maida gun wajen kuka, don dole aka
rufe taron aka wuce da Zeezee gidanta da aka share, akayi mopping aka kuma turare
se k'amshi ke tashi kota ina. K'arfe 8:24pm aka sauk'e Zeezee a d'akinta. Har anan
ta kasa dena kuka, se dawo mata events na rasuwan Baba suke if only Baba was here,
taso ace Baba zeyi witnessing re-union nata da Al'ameen, ya d'auketa kaman yadda
yayi a da ya dank'a wa Al'ameen ita halak malak. She really miss her Dad.

Da misalin k'arfe 10:45pm, lokacin kowa da kowa ya watse daga Al'ameen se Zeezee
se kuma guards nasu. Kuka take har yanzu takasa tsagaitawa. Da plate cike da kaji a
right hand nasa, left kuma juice a cup Al'ameen ya k'ariso gaban k'ofan d'akin
Zeezee inda ya ajiye cup d'in kan wani chess of drawer'n irin wall mirrors d'innan
sannan a hankali yayi knocking bisa k'ofan. Ba abinda yake ji banda sautin kukan
Zeezee wanda sam bayi k'aunan ji. Jin shiru ya kira sunanta "Zainab? Zainab? You
there?"
"Ka shigo Ya Al'ameen" ta fad'a cikin murya me rawa. A hankali ya bud'e k'ofan ya
k'ariso ciki tare da ajiye mata abinda ya taho dashin akan side drawer'n dake
gefenta.
"Are you still crying Zainab?" Kai tayi saurin kad'a mai tana share hawayenta.
"Stop it kinji bana so." Maimakon ta jisa ta tsagaita kukan a'a se kaman k'ara
volume na kukan naki yace da ita. Ai seta sake 6alle masa da wani sabon kukan
shark'af-shark'af. Rasa nayi kwata-kwata ma yayi da k'yar sannan ya zaro hanky ya
matso kusa da ita tare da d'ago wet face nata from tears ya shiga share mata
hawayen. "Na sha gaya miki Zainab banason ina ganin kina kuka haka."
"I miss him so much Ya Al'ameen I've never been a good and proud daughter to
him."
"Kiyi hak'uri kinji? Aduk inda Baba yake yanzun nasan he is damn proud of you."
Jikinsa kawai ta fad'a tare da hugging nasa sosai tana me cigaba da kukan, chak ya
tsaya kaman gunki ya kasa hugging nata back. Se daga baya a hankali sannan ya aza
hannayensa both a bayanta yana bubbugawa a hankali "its okay kinji? Our prayers are
with him zamu cigaba da yi masa addu'a Allah ya cigaba da kai rahama kabarinsa."
"Ameen thank you."
"Shhh! Kukan ya isa toh" yayi maganan yana d'agota daga jikinsa. Hannu tasa ta
share hawayen nata tare da komawa gefe ta zauna "I'm sorry" ta mai apologising.
"You don't have to gashi ci ki samu ki kwanta kinji? You must have been
exhausted."
"Thank you Ya Al'ameen kai fah?"
"Don't worry bana jin yunwa."
"Are you sure? You can have my plate."
"No Zainab ci ki kwanta ina zuwa."
Yana kaiwa nan ya fice, binsa tayi da kallo seda ya baro d'akin sannan ta shiga
cin kajin a hankali don koran yunwa through out yau bata sa komi a bakinta ba banda
malt da Lubiee ta bata.

Why isn't he calling me his princess again? Ta tambayi kanta. Ya dena sona ne
yanzu? Oh na cuci kaina. Tayi tunanin haka a ranta. Bayan ta k'oshi ta nufi bayi
inda ta watsa ruwa sannan ta fito tasa night gown nata ta sake feffeshewa da
tuarare, har anan Al'ameen be sake lek'owa ba. Ji take as if ta fita taje ta duba
sa ko lafiya, har ta kai bakin k'ofa sekuma ta fasa ta dawo ciki, ganin thats not
the right thing to do kawai ta haye gado abinta ta kwanta, tun tana jiran
shigowarsa har bacci 6arawo ya saceta be dawo ba.
Ba Al'ameen ya tashi dawowa d'akin ba se pass 12 inda ya tarar da Zeezee se
baccinta take tasha. Sanye yake da knee length wando me pattern na soldiers da kuma
farin T shirt. Tsaye yayi a kanta yana k'are wa innocent face nata data aza
hannunta d'aya akai tana bacci. Tsugunawa yayi sannan a hankali ya sauk'e hannun
nata aiko karap ta cafke hannun sa cikin baccin tare da aza kanta k'ark'ashi just
like a pillow. "Oh God no!" ya furta yana tunanin ya zeyi ya k'wato hannunsa, sanin
idan yayi da k'arfi tana iya tashi yasa ya shiga jan hannun nasa a hankali. Sede
seya kusan gama ja se Zeezee ta sake miyarwa, da k'yar ya samu ya zare abinsa
sannan ya gyara mata kwanciyarta ya rufeta da bargo ya fice tare da kashe mata
wuta. D'ayan d'akinsa daya saba kwanciya aciki ya koma ya kwanta yau ma inda da
tunanin Zeezee bacci yayi awon gaba dashi.

Da Asuban fari Zeezee ta farka don yin sallah. Gefenta ta soma shafawa inda
taji wayan, toh ko de har ya fita masallaci ne? ta tambayi kanta. Wutan d'akin ta
kunna inda ta tabbata cewa Al'ameen ba a d'akin ya kwana ba saboda ba ko alaman
wrinkle a d'ayan side d'in. Hakan ba k'aramin breaking mata heart yayi ba, she
thought yanzu they'll be back as how they were before. She miss him so much tayi
wasa sa damarta, Al'ameen baya sonta yanzu.
Al'ameen kuwa bayan ya dawo from Masjid ya wuce d'akin Zeezee don tada ita yin
Sallah inda ya tarar da ita har ta tashi ma ta idar da sallan, tana zaune kan
sallaya tana azkhar. "Assalamu Alaikum" ya fad'a yana tsaye daga bakin k'ofan.
"Wa'alaikumus salam" ta juya tare da gaishesa "good morning Ya Al'ameen."
"Morning Zainab, har kin tashi?"
"Eh."
"Dama nazo tada ke Sallah ne."
"Oh ayyah thank you."
"You're welcome, ya gajiyan jiya?"
"Alhamdulillah, you?"
"Also, ki huta kinji? Get some sleep."
"You too." With a nod ya juya, har ya bud'e k'ofan ze fita Zeezee ta kirasa, "Ya
Al'ameen?" hakan yasa ya tsaya tare da juyowa. "Na'am wani abu ne?" So take ta
tambayesa dalilin daya hanasa kwana jiya a d'akinta amman kuma jin nauyinsa take.
"Zainab?"
"Na'am" ta amsa kanta a k'asa.
"Tell me meneh?"
"Bbb... babu, I just want to thank you, nagode."
"For?"
"For everything."
"You're welcome get some sleep." Yana kaiwa nan ya fice. Kanta ta jingina jikin
gadon tana me sake tsanar kanta, da alama Ya Al'ameen baya sona yanzu, "ya manta
dani, daga gani ma ya dawo dani ne saboda yana tausaya min bawai don yana sona ba,
oh! Na cucu kaina a rayuwa, daman bature yace opportunity comes once in a life
time, nayi wasa da daman dana samu a baya, taya zan sa Ya Al'ameen ya fara sona
again?" Da k'yar ta kammala azkhar nata ta kom ta kwanta****

Tun wajajen 8am Al'ameen ya tashi yasa Saje ya siyo mishi breakfast yaci suma
suka ci nasu sannan suka shiga training. Ba Zeezee ce ta tashi ba se pass 11 tsan-
tsan gajiya. Bathroom ta fad'a tayi wanka tsaf abinta sannan ta fito tasa d'aya
daga cikin sabbin d'inkunanta, ta tsara light makeup sannan ta fice parlour. Jin ba
hayaniya a waje yasa ta koma baya don duban Al'ameen. Kasa kunnenta tayi a bakin
k'ofan d'akinsa inda ta jiyo muryarsa yana kan waya. Dad'i sosai taji jin yana
gida, a 360 ta d'au hanyan kitchen inda ta tarar da farar leda kan dining table.
Bud'ewan da tayi taga chips ne da egg sauce, wani haushin kanta ta ji, duk laifin
ta ne da bata saba masa da siyan abinci ba da kowani wayewan gari sede ya jira tayi
musu abin karin kumallo. Duk da hakan bata hak'ura ba ta wuce kitchen tayi boiling
doya sannan ta tsara had'ad'd'en kidney sauce. Bayan data sauk'e ta zuba a
had'ad'd'un food warmers nata sannan ta jera a dining. Tunanin ya zata je ta fito
dashi daga d'akinsa take amman sam ta kasa battada caurage. Ana cikin haka ne
Al'ameen ya fito tsaf cikin sky blue kaftan da hula shirin ya mugun amsar sa ya
kuma sake bayyano da how fit he is, tun daga bakin k'ofa Zeezee ke kallonsa ta kasa
d'auke idanunta daga kansa, wai shin ko wani irin kaya ne ke kar6ansa shi? She
can't tell how fascinating he is looking. Takowa ya soma izuwa parlour'n cike da
k'asaita magestically. Ganin kallon bana k'arewa bane yayi gyaran murya which shook
Zeezee back to reality. "Good morning Ya Al'ameen" ta fad'a tana kallon k'asa.
"Morning Zainab har kin tashi?"
"Eh."
"Good ga breakfast naki a kan table, kin gani?"
"Eh na gani, but na girka mana breakfast, you should have woke me up in mana ai a
maimakon siyowan da kasa akayi maka. Its my obligation to cook for you."
"I know Zainab, karki damu you were sleeping shiyasa banso in tadake ba despite
gajiyan da kika sha jiya."
"It stil doesn't matter, come over and eat."
"No thanks I'm full kici ke kinji?" Mood nata yaga gabad'aya ya sauya.
"Ya Al'ameen even if its a bite please kazo kaci."
"Zainab chill kinji? Zuwa anjima zanci but right now am full nayi breakfast
d'azu."
"Ban iya girki ba shiyasa baka son kaci ko? I'll keep on practicing sena zamo
best chef just for you."
"You are a best chef already Zainab." Kai zallah ta gyad'a mishi amman sam bata
ji dad'i dayace mata he is full ba baze ciba. Ita kanta ta gane yanzu Al'ameen baya
sonta kaman da. Bataso nuna mishi yadda ranta ya 6aci ba ta danne zuciyarta tace,
"kayi kyau Ya Al'ameen, kaftan d'in ya kar6eka sosai."
Murmusawa yayi sanda dimples nasa suka lotsa ciki gabad'aya "thank you kema
kinyi kyau."
"Thanks also, zaka fita ne?"
"Eh zan duba wani friend d'ina, I won't take long." Nan ma bata ji dad'i ba tasan
avoiding nata kawai Al'ameen yake if not shi ba ma'abocin fita yawo bane.
"Toh Allah ya kare, be back safely."
"I'll in shaa Allah thank you, kina buk'atan wani abu?" A zuciyarta tace yes, you
I need you. Amman a fili ta kad'a kai "babu."
"Okay then" Tana kallonsa har ya fice, hawaye kawai ta soma yi a hankali, me
zata yiwa Al'ameen ya koma sonta as before? Da k'yar ta iya ta karya inda ta sake
cooking musu spaghetti da yasha kayan had'i as lunch, wannan karan bawa ita kad'ai
da Al'ameen bane harda su Saje ma da masu gadi duk tayi girkin dasu. Bayan ta kai
musu nasu ta dawo ciki tayi sallah ta sake d'aukan wani wanka sannan ta zauna a
parlour tana jiran dawowan Al'ameen. Kaman wasa Al'ameen har after 3 be dawo ba,
bata san lokacinda bacci ya saceta kwance a gun ba.

Har La'asr yayi bata ji ba bale ta tashi tayi Sallah, da La'asr d'in Al'ameen
ya shigo inda ya tarar da ita kwance a parlour, kayanta na yanzu har yafi nada
amsanta se kawai ya tuna back then da idan har Zeezee tayi kwalya ko tasa kaya me
kyau a gida is either zata fita unguwa kokuwa zatayi hoto ta tura wa Adeel ne amman
kam on normal basis bata kwalya don mishi. Murmusawa kad'an yayi sannan ya wuce
dining inda ya bud'e food warmer'n, spaghetti ya tarar had'ad'd'e ciki kafin yace
ze rufe Zeezee ta tashi daga baccin tana kallonsa. "Har kin tashi?" Ya tambayeta a
bit disgraced lokacin da idanunsu ya had'u beso ba ta kamasa yana bud'e flask. Kai
tamai nodding, "yaushe ka dawo? Sannu da zuwa."
"Just now thank you."
"Oh sannu da zuwa, zaka ci abinci neh?"
"Nah am full I had lunch a gidan friend d'ina." Sad expression ne ya bayyana
karara a fuskarta tasan sarai da gan-gan Ya Al'ameen yake k'in cin abincinta, halan
gani yake kar ya saba ci tazo tace ta dena yimai girki,well he is wrong. Danne
zuciyarta tayi da k'yar tace, "oh I'm sorry."
"Kinyi Sallah?" Ya canza topic d'in. Kai zallah ta kad'a mai.
"Tashi toh kiyi, and also Taheer yace min kin sa musu abinci, don't stress
yourself out next time ina basu kud'i suna sayan kinji? No need."
"Ya Al'ameen you don't have to, am your wife hak'k'i na ne in ciyar dasu and you
as well."
"But-"
"Please let me do this." Ta katse sa a hankali.
"As you wish Zainab tashi kiyi sallah." Ba musu ta miqe ta nufi d'akinta.

Da daddaren daya ce mata zeci abincin ma ba ci yazo yayi ba, ba kad'an abin ke
daminta ba ta rasa ina zata sa kanta. All she know is that she'll never give up on
him because she loves him. Bayan ta gama shirin kwanciyarta ta fito ta tarar da shi
a parlour, "kin shiga zaki kwanta kenan?" Ya tambayeta yana sanye da vest da wandon
kaftan na d'azu.
"Eh" seka shigo take son ce masa amman tasan ba shigowan zeyi ba. "Seda safe."
Ta k'ara akai.
"Sleep safe and sound." Kai ta gyad'a mai ta koma d'aki. Tana kwance bisa kan
gado kawai ta soma kuka, so take ta kira Lubiee ta sanar da ita but she wants to
give Al'ameen some time ai yama yi k'ok'ari daya dawo da ita despite kalan rashin
kyautatawa da rashin kunyan data mishi da a baya, yayi sacrificing virgin duk a
kanta saboda haka zata basa some space. Da tunaninsa yau ma tayi bacci.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣2⃣

_Assalamu Alaikum y'all Beautiful people. I will first of all like to show my
deepest appreciation fort the love and support you guys are giving to YGC!🎀 It
really means so much, MIEMIEBEE na alfahari daku. I am head over hills in love with
you, OneLove❣_
_So kamar yadda kuka sani d'an Adam ajizi ne, totally na mance ban sa an sake
d'aura wa Maj-Gen. da Zeezee aure ba a last page saboda shagalin events ya tafi min
da mind🤣 so ayimin afuwa. Lets fire on!_

As early as possible ta tashi yau ta had'a mishi breakfast had'ad'd'e sannan ta


koma tayi wanka tayi kwalya tsaf abinta kaman a gudu da ita don kyau, ga kuma
k'amshin dake tashi daga jikinta. Wajajen 8am Al'ameen ya fito daga d'akinsa yana
sanye da vest da irin free size wandon exercise d'innan. Tana zaune akan kujera ta
sauk'a har k'asa sannan ta gaishesa cike da ladabi.
"Me haka kuma Zainab? Bazan amsa ba sekin tashi." Kuma dagasken yak'i amsawa
seda ta tashin sannan ya amsa suka gaisa. "Meya tada ke yau haka da wuri? Zaki fita
ne?"
"A'a I made you breakfast."
"Uh-oh" zallah yace.
"Zaka fita ne?" Ta tambayesa.
"No zanyi Training men d'ina ne."
"Since before ka karya Ya Al'ameen?"
"It won't take long karki damu."
"A'a nikam ka karya please kafin nan already na kai musu nasu su."
"Zainab karki damu kinji? Actually yau ina azumi" Allah ya soshi yau Thursday
ne.
"Oh is that so?" Tayi maganan sounding disappointed.
"Yeah thanks kinji?" Yana kaiwa nan ya fice, itama k'in karyawan tayi inda ta
zarce d'akinta tana me kuka sosai bata san ya zatayi da ranta ba. Bayan Al'ameen ya
gama training men nasa ya koma ciki yayi wanka ya shirya tsaf cikin k'ananun kaya
da ya sake fidda shi sosai sannan ya nufi d'akin Zeezee inda ya tarar da ita tana
bacci. Smiling kad'an yayi at her view sannan ya fice. Bayan Azahar Zeezee ta tashi
inda take tambayan me gadi ko Al'ameen ya fita ne yake sanar da ita eh yace he
won't take long ze dawo. Wani takaici ta jiyo. D'aki ta koma ta kirasa wanda bada
jimawa ba ya d'aga "hello Ya Al'ameen?"
"Na'am Zainab har baccin ya isheki ne?"
"Ya Al'ameen baka dawo ba har yanzu?"
"Zan dawo soon karki damu."
"Toh kana azumi baka sanar dani me kakeson shan ruwa dashi ba."
"Actually, Zainab na karya azumin nawa kaina ke ciwo sosai d'azu." Tasan k'arya
yake he is just looking for a reason karya ci girkinta. Danne zuciyarta tayi tace.
"Ayyah Allah k'ara sauk'i toh se anjima."
"Yauwa take care." Sauk'e wayan tayi a hankali sannan ta shiga aikin kuka da
k'yar ta samu ta idda sallah ta kira Mama suka gaisa inda ta nuna mata everything
is fine. Bayan La'asr Al'ameen ya dawo a lokacin Zeezee na a d'akinta kayan duniya
sun isheta, she can't tell how she is missing Al'ameen.

Kasancewar gobe Al'ameen ze koma Abuja yau bayan Sallan isha ya shigo d'akin
Zeezee ya sameta zaune bakin gado ta zurfafa cikin tunani sosai. Seda yayi gyaran
murya sannan tayi noticing shigowansa. "Uhn Ya Al'ameen I'm sorry banji shigowan ka
ba."
"Tunanin me haka kike Zainab?"
"Babu" ta mai k'arya.
"Erm nazo sanar dake ne gobe zan yi resuming office."
"Har gobe Ya Al'ameen?" Tayi maganan sam bata ji dad'i ba.
"Eh Zainab kinsan sun kaimu Maiduguri."
"Ayyah, banji dad'i ba nad'au sun baka erin 2 weeks d'innan ne."
"No, kiyi hak'uri kinji?"
"What for?"
"Auren Soldier seda hak'uri Zainab, I can't stay with you for a long time."
"I totally understand you Ya Al'ameen Allah ya taimakeka ya kuma kare ka."
"Ameen thank you."
"Bazaka ci dinner ba?"
"Nasha black tea bana jin yunwa."
"Toh shikenan."
"Toh seda safe."
"Allah bamu alkhairi" ta fad'a hawaye na forming rapidly a idonta she don't think
she can hide it anymore. Har ya bud'e k'ofa ze fita Zeezee ta kira sunansa chak ya
tsaya tare da juyawa. A nitse ta miqe ta k'arisa gabansa kanta a k'asa ta fara da
cewa "Ya Al'ameen am sorry."
"What for Zainab?" Yayi saurin tambaya.
"Ya Al'ameen stop pretending as if things are good between us nasan har yanzu
kana min kallon dump, stupid, disrespectful and disregarded Zainab but thats not
true, I've changed am not the Zeezee you use to know."
"Zainab what are you talking about?" Finally ta d'ago kanta tana kallonsa, "you
don't love me anymore do you? Please be sincere and tell me the truth, ka dawo dani
ne badon kana sona ba illa don kana tausaya min, am I right?" Shiru yayi ya kasa
cewa komi a yayinda degree na rolling tears nata ya dad'u. "I should have known-"
katse ta yayi "Zainab-" itama da sauri ta sake katse sa.
"You don't love me anymore, and I don't blame you Ya Al'ameen saboda laifi na
ne, I was dense and stupid then I wasn't thinking straight, I failed to realize
that you are my true and perfect love, I love you Ya Al'ameen ina sonka, I can go
the whole day shouting I love you because I can't get enough of you." By now kuka
take sosai "Zainab enough okay?" Yayi fad'a at last.
"Its not okay Ya Al'ameen tunda baka cin abincin dana dafa maka, baka iya
kwanciya a inda nake, you don't call me your princess anymore taya kakeso in samu
peace of mind? Wallahi da zan iya reversing time da nayi and make things right, I
love you Ya Al'ameen" ta d'ago both hands nasa ta had'a da nata. "I love you so
much, morethan you could ever imagine. I've never had this feeling with anyone not
even Adeel. I love you Ya Al'ameen please ka tausaya wa rayuwa na kadena punising
d'ina haka. Anytime kace bazaka ci girki naba ji nake as if in d'au wuk'a in kashe
kaina, if only nasan ya zanyi maka describing just how much I love you I would have
done it a long time ago."

"Zainab..." ya sake kiran sunanta a hankali gabad'aya ta bashi tausayi yadda


take kuka.
"Please kar kace no, please don't." Hannun nasa ta sake kawai tayi hugging nasa
gagam "I'm truly sorry" tayi stating cikin kukan. "Forgive me please, forgive your
Zainab and kabani one last chance."
Tausayi sosai ta bashi he never expected these words from her a hankali ya zagaye
hannunsa a bayanta "stop crying okay? Ya isa haka kukan." Kai ta kad'a "unless you
tell me you love me also in ba haka ba bazan iya dena kuka ba, I need you to tell
me please tell me." Da k'yar ya jata daga jikinsa sannan yayi cupping face nata "I
love you Zainab, you know that already koba haka ba?"

"Then why are you punishing me like this?"


"I'm not punishing you Zainab I just don't want to be a burden to you."
"Haba Ya Al'ameen! Taya zakace haka? I'm your wife remember?"
"I know bar kukan haka toh." Kanta ta sunkuyar sannan tace, "meaning zaka dawo
nan da kwanciya?" Shiru yayi yana mamakin Zeezee yadda she can't hide how much she
loves him anymore, shima he loves her as much saidai bayason ya nuna mata ne gani
yake like har yanzu ba sonsa take ba, but now he does.
Jin yayi shiru tace, "baza ka dawo ba? Well, I'm sorry" ta k'are maganan tana
share hawayenta. One step back tayi taking wanda da wuri ya kama hannunta "we'll do
it anyhow *My Princess* wants it" ya sanar da ita yana murmushi. Kasa 6oye farin
cikinta ta tayi, jikinsa kawai ta shige tana mishi wani irin hug cike da so da
k'auna. "Thank you *My Soldier* I love you so much." _My Soldier_ yaji dad'in name
d'in.
"I love you too My Princess" yayi maganan tare da hugging nata back. Sun d'au
tsawon lokaci ahaka, se shaqan daddad'an k'amshin jikin juna suke barin ma Zeezee
dake ji wane a aljannan duniya aka tsunduma ta, Ya Al'ameen is her world. Se chan
Al'ameen yayi breaking hug d'in.
"My Soldier?" ta kirasa tana kallon hannayensa data rik'e a cikin nata.
"My Princess" yayi answering back.
"I so much love the name, call me again." Murmusawa yayi "and that smile also, I
love it. Say it again please."
"My Princess."
"I love your voice, I love you in whole Ya Al'ameen, words can't tell how just
much I love you."
"Zainab I love you as much also, you are my princess."
"I love you you more My Soldier and I don't think so, I love everything about
you, your voice, smile, dimples, abs (packs), muscles, height, just everything
about you drives me crazy." Ta fad'a sincerely. Murmushi yake sosai by now, "I love
you also Princess, I love your pretty face, long hair, smile, charisma, and
everything."
"Your Princess loves you more, muje kaci dinner kaji?"
"Princess am not hungry." Fuska ta maraice, "you call me your princess amman
bazaka iya cin girki na bako? Shikenan." Fuskanta ya d'ago da hannunsa.
"Don't be sad kinji? You'll be the one to make me breakfast gobe."
"Amman bazaka ci na yau d'in ba?"
"Princess what part of I'm not hungry don't you get? Ko so kike se cikin nawa ya
fashe tukun."
"Toh ina ma tunbin yake bale cikin ya fashe? Kai de kawai kace bazaka ci ba
saboda ban iya girki ba."
"Shh! Kema kinsan thats a lie, har yau ina mafarkin rice and stew in kincan."
"Toh in haka ne muje ko kad'an ne ka ta6a."
"Princess tunbi kikeson inyi ne?"
"Ai jikinka is fit bazaka ta6a yin tunbi ba muje kaji? Ko kad'an ne seka ci, I
need My Soldier to eat dinner before going to bed."
"As you wish Princess." Hannunsa ta kama cike da jin dad'i har suka isa dining
d'in sannan ta ja mishi kujera yayi godiya tare da zama, na gefensa taja ta zauna
itama sannan ta shiga serving nasa.

"A'a'ahh Princess ya isa, ina zan kai wannann abinci?"


"Here" tayi pointing cikinsa.
"Karki k'ara ya isa, am full already." K'in jinsa tayi seda ta kusan cika mai
plate sannan ta tura mishi plate d'in gabansa "eat ko nayi feeding naka?" Dariya
sosai ya tsaya yi due to her statement in which Zeezee finds him cute. Zama tayi se
kallonsa take, da k'yar ya tsagaita dariyan nasa ya mata apologising "I'm sorry."
"Keep on laughing, you have such a cute smile, I love it."
"I'm sorry" ya sake apologising.
"Toh ma dariyan me kake haka? Dan nace zanyi feeding naka?"
"Eh mana, tsoho dani." Baki ta sake wide in shock tana kallonsa, "waye tsohon?"
"Ni mana."
"Allah ka sake kiran kanka tsoho zanyi kuka."
"Aww ba tsohon bane toh?"
"A'a wallahi, don bana ce maka Baby shine zaka ce kai tsoho ne? Please kar ka
sake banaso."
"Toh Princess bazan k'ara ba."
"Yauwa My Soldier finish your meal." With a nod ya kai spoon d'aya baki inda ya
tsaya yanata exaggerating dad'in abincin, itako banda kallonsa ba abinda takeyi, he
is way adorable cin abincinsa ma daban yake dana mutane. Spoons less than 10 yayi
yace ya k'oshi.
"Har ka k'oshi My Soldier? Me kaci anan?"
"Are you kidding me Princess?"
"Yi hak'uri ka k'ara koda spoon biyar ne kaji?"
"Princess on normal basis ma naci 15-20 spoons na k'oshi bale yau da am already
full."
"Yi hak'uri ka k'ara."
"Bakisan bana cin abinci sosai bako?"
"Aysha once told me amman Yi hak'uri ka k'ara. Kasan wani abu?" Kai ya kad'a
nufin a'a. "Kai spoon d'aya tukuna se in fad'a maka."
"Am full Princess."
"Bakason kaji kenan."
"Inaso, tell me."
"Toh ka kai spoon d'ayan first." Haka tayita masa wayo har seda ya kai 5 more
spoons sannan tace, "are you ready?"
"I am." Yayi maganan tare da picking cloth ze goge bakinsa inda da sauri Zeezee
ta kar6e, "let me" ta fad'a tana yimai murmushi. Kallonta kawai ya tsaya yi a
yayinda ta shiga goge masa bakinsa a hankali in a romantic manner "you are way
handsome My Soldier, bana gajiya da kallon ka." Tayi informing nasa.
"Ban kai ki kyau ba ai Princess."
"Ka zageni de kaji dad'i."
"Uhm so me kikeson fad'amin duk kinsa na k'osa."
"I can die for you, you know?" Ta fad'a mockingly.
"Princess!" ya saki baki totally speechless yana kallonta "all these spoons?
Kawai don kice min you can die for me neh? Kema kinsan I can die for you a thousand
times if needed."
"I'm sorry kaga yanzu ko bakayi breakfast ba gobe bazaka ji yunwa ba, muje in
had'a maka akwatinka."
"Na riga na had'a karki damu."
"Oh toh thats good." Daga nan kuma se duk sukayi shiru suna tunanin abubuwa daban-
daban. Chan Al'ameen ya kirata, "My Princess?"
"Na'am My Soldier." ta amsa tare da d'ago kai tana kallonsa.
"Since when kuka rabu da Adeel?" Take yaga mood nata ya sauya.

"I'm sorry didn't mean to kiyi hak'uri, in bakiya son ayi maganan shi so be it."
Hannun su ta ta had'a musu, "you are My husband Ya Al'ameen I have no hidden secret
for you."
"Are you sure?" Kai tamai nodding sannan ta amsa, "getting to 10 months now."
"Wow!" Yayi exclaiming "kana son kaji sanadin rabuwan mu da kuma rayuwar da nayi
living a gidan shi?"
"In har ze miki ruining mood naki and make you cry banaso." Murmushin takaici ta
sakar masa sannan ta fara kaman haka "tun ranan da na rabu da kai na cuci kaina Ya
Al'ameen..." labarin komi ta basa ba tare da ta 6oye mai wani abun ba, abinda ya
kama daga kan fasa mata waya da Adeel ya soma, staying late at night, kula 'yan
mata, sata yimai wanki, dad'o aure, forcing nata into bed, wulak'anta ta komi seda
ta basa a yayinda take hawaye sosai. Shima Al'ameen sosai ya tausayawa Zeezeensa,
just how bad have she suffered? Abinda Zeezee bata fayyace wa Al'ameen kad'ai ba
shine na lalacewar mahaifarta, gudun karya ji ya tsaneta shima just like how Adeel
did. Be k'arisa jin labarin nata ba ya mik'e tare da janta jikinsa yayi hugging
nata yana bubbuga bayanta a yayinda volume na kukan ta keta k'aruwa. Da k'yar ya
samu Zeezee tayi shiru se anan ya d'agota daga jikinsa yana share mata hawayen nata
da hannunsa.

"You are forever free from him Zainab, I'll never let you leave my side, I will
never torture you like that, I will love you like there's no tomorrow, I'll take
care of you like an infant baby. I will never hurt you than to make you cry, I'll
always be there as your Soldier to protect you Zainab, you are the love of my life,
I love you so much." Hawayen jin dad'i ne suka soma tsiyaya daga idanunta, bending
yayi a hankali yayi pecking (light kiss) kan rolling tears natan. Idanunta ta matse
gam a yayinda wutan son Al'ameen ke running through her veins. Hugging nasa tayi
tana me cigaba da hawayen, "thank you for coming back to my life, Ya Al'ameen I
love you so much."
"Shh! Bar kukan haka."

****
Some hours later...
Al'ameen na zaune a bakin gado a d'akinsu da Zeezee a yayinda ita kuma take
bathroom tana wanka, few minutes later ta fito sanye da towel sama da guiwarta
kad'an "My Soldier sauran kai." Smiling mata yayi sannan ya mik'e ya amshi towel
nasa da take miqa mai ya shige bathroom d'in kafin ya fito har ta kintsa kanta tsaf
cikin baby pink silky sleeping gown nata. Tana miqe kan gadon idanunta na akan
Al'ameen, kowani move yayi binsa da kallo take. A rayuwa bata k'i ace tayita
staring at Alameen's builded body ba har abada. Packs d'innan ba mugun tafiyar mata
da imani suke ba, she can't get enough of him. Gani tayi ya d'au hanyan barin
d'akin, da sauri ta miqe zaune "Ya Al'ameen where are you going?"
"Nowhere Princess."
"Kana son ka gudu min ko?" Dariya sosai ta basa amman ya basar "zan je inyi
picking up kayan da zansa ne."
"Gashi na kawo maka" hannu ta miqa ta jawo daga kan chess of drawer sannan ta
mik'e ta kai masa idanunta not moving from his abdomen tana k'arewa packs nasa
kallo har seda ya gano hakan. K'aik'ayi hannunta ke mata sosai tana son ta shafa
kan packs d'in taji amman tana tsoro da kuma kunya. "Your hand?" Ya buk'aceta tare
da d'ago mata hannunsa nufin tasa nata ciki. All confused ta d'aga hannun nata ta
aza akan nasa dake hanging, se gani tayi ya miyar da hannunta kan cikinsa ya ajiye
a wajen, "I'm all yours Zainab don't hesitate to touch me okay?" Kunya sosai taji
ashe de tun d'azu ya gane kallonsa take worst part d'in har ya gano so take ta ta6a
sa. Sh*t! Ta fad'a a ranta.
"Ya Al'ameen..." ta kirasa tana neman sauk'e hannunta daga kan cikin nasa
idanunta a k'asa. Da sauri ya sake miyarwa "don't feel shy My Princess, I am all
yours as you are mine also." Kai ta d'ago a hankali tana kallonsa cike da
adoration, "say it again, you're all mine? All of you?"
"Yes My Princess, I am all yours, all of me belongs to you, just you." Da
murmushi a fuskanta ta shiga exploring abs nasa (cikinsa) tana bin kan packs nasa a
hankali, hakan ba k'aramin dad'i yake mata ba. Tun chan da kafin tayi aure take
sha'awan na miji me packs ga a time d'in Adeel siriri ba shida komi but Ya Al'ameen
nata? Omg! Wane na Ronaldo. Dai-dai beyi yawa ba be kuma kasa ba gasu nan guda
shida ana ganinsu. Duk anan binta da kallo kawai yake don kanta ta gaji duk kunya
ma takeji ta rasa dalilin dayasa ta kasa 6oye mai kwad'ayin ta6asa da take son yi.
Hugging nasa kawai tayi, gano kunya take ji se kawai ya murmusa k'ok'arin d'agata
daga jikinsa yake amman kaman doll baby ta manne tsam tak'i tashi. "My Princess
look up at me."
"I can't" ta fad'a danko bazata iya ba.
"Mesa?" Shiru tayi ta kasa amsa shi. "Kunya na kikeji?" Ya fad'a in between
laughter. Kai ta gyad'a kad'an.
"LOL ba mijin ki neba ni? Ai ba kunya a tsakaninmu." Nan ma shiru tayi, "taso
kinji?" Again shiru tana nan manne a jikinsa.
"My Princess bacci nakeji" jin haka ta sake sa da wuri ta juya se kan gado taje
ta kwanta tare da covering face nata da pillow not minding calls da yake mata
sending. Kayansa yasa sannan ya haye gadon tare da kwanciya ta d'ayan end d'in.
Kallon Zeezee da har yanzu fuskarta maqale da pillow yayi sannan ya kirata "My
Princess?" Shiru.
"Sekin shak'e kanki tukun zaki sauk'e pillon? Toh zan kashe wutan seki bud'e face
nakin kinga acikin duhu bazan iya ganin shy-shy face nakin ba." Jira yayi ko zata
amsa sa, jin shiru se kawai ya miqa hannu ya kashe wutan d'akin, har anan Zeezee
tak'i bud'e face nata kunyan abinda tayi ita kanta take ji.
"Seda safe Princess, I love you." Murya can ciki a hakali tace, "Allah bamu
Alkhairi, I love you more." Daga nan Al'ameen be sake cewa komi ba saboda in less
than 10 minutes bacci yayi awon gaba dashi.

Banda Zeezee dake ta faman tunanin Ya Al'ameen nata, chan ta kira sunansa a nitse
in a low tune. "Ya Al'ameen?" Shiru ba response "My Soldier?" Again shiru. "Kayi
bacci ne?" Jin shirun na neman yin yawa ta d'aga wayarta tare da haska handsome
face nasa, anan taga yayi bacci me nauyi ma kuwa. "Damn cute" ta furta a ranta
lokacinda take kallon nasa, slight gemun da yake tarawa wanda ya had'e da sajensa
ne yafi mata kyau fiye da komi a fuskansa. Matsowa kusa dashi tayi tare da aza
hannunta a hankali akan face nasa. Ramin dimple nasa tasa hannu ciki back to sajen
dage kwance a fuskarsa luf-luf, daga nan kuma ta koma silky thick eyebrows nasa,
chan kan hancinsa duk anan bacci yakeyi baiko jita ba. Lips nasa ta ta6a k'arshe
ganin yad'an motsa taja bargo ta rufe face nata da wuri. jin be tashi ba ta sake
fitowa ta cigaba da tatta6asa ahaka har ta soma jin bacci. Hannunsa da yake kwance
akai taja a hankali sannan tasa a k'ark'ashin fuskarta a dai-dai tafin hannunsa
just like a pillow, sake matsowa kusa dashi tayi ta kwantar da kanta akan arm nasa
ta wajen elbow'n shi. Chan taga hakan ma beyi mata ba ta sake matsowa kusa dashi
yadda take jin k'arfin nishinsa sosai, cikin jikinsa sosai ta shige tana me shaqan
daddad'an fragrance nasa, tana me murmusawa ita kad'ai.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣3⃣

_As I promised Sweetheart, AUNTY SIS. 5 consecutive pages will all be


dedicated to you because you morethan deserve it. No need for long essay because
the love is always there, I love you💋 Here's to page one of dedication._

"Ya Al'ameen, you are nothing compared to Adeel" ta fad'a a fili amman kuma a
hankali. "You are not after my body, bazan iya tuna when last muka kwanta da Adeel
be nemi hak'k'insa a guna ba, he is just after my body, but you?" tayi maganan tana
sake matsowa kusa dashi as if zata shiga cikin cikinsa. "You are not like that, you
love me for who I am and nothing more, nad'au this night zaka ce zaka nemi
hak'k'inka ashe am mistaking love isn't about sex, love is all about sacrifice and
wanting for your spouse what you want for yourself, I love you Ya Al'ameen." Daga
nan ta rufe idanunta tajira bacci yayi awon gaba da ita.

Ko wani Asubah Zeezee na tashi amman banda na yau. Tun da take tana ganin bata
ta6a samun peace and tranquillity acikin bacci ba kaman na yau, Ya Al'ameen is just
like an Angel to her. Asuban fari Al'ameen ya tashi, ji yayi gabad'aya nauyin mutum
akansa, da k'yar ya iya ya miqa hannunsa ya kunna bedside lamb don yadda ta danne
sa nan yaga Princess nasa tukunkune a jikinshi tana takan bacci. Hannunta d'aya ta
ya6a akan cikinsa ta zagaye dashi, d'aya kuma ta kama collar riganshi da shi tana
bacci. He can't get enough of her innocent face, tsayuwa yayi gun yana kallonta,
yaushe har ta matso this close to him amman be jita ba? Ganin lokacin Sallah na iya
wucesa idan ya biye wa kallonta yasa a hankali ya sauk'e hannunta dake rataye a
cikinsa without waking her up. D'ayan hannunta data kama collar rigarsa ne ya kasa
cirewa don yadda ta kama gagam.

K'ok'arin rabawa yake amman ya kasa har seda Zeezee ta tashi in the process. A
hankali ta bud'e idanunta ta aza akan kyakkyawar fuskarshi dake nan wane ba daga
bacci ya tashi ba. Murmushi ya mata wanda itama ta miyar mishi tare da ja baya
kad'an don ta karanci tashi yakeson yayi.
"I'm sorry" ta furta a hankali.
"What for Princess?" Yayi maganan tare da barin kan gadon.
"For being a burden to you last night."
"You weren't Zainab, last night was great I had a wonderful sleep barin yi
alwala." Kai ta gyad'a masa sannan ta bisa da kallo har seda ya shige bayin. Just
kawai ta tsinci kanta tana murmushi ita kad'ai ba gaira ba dalili har Al'ameen ya
fito bata sani ba. Bak'in Jallabiya yasa sannan yayi gyaran murya "uhm-uhm." Anan
ne hankalinta ya dawo jikinta, "good morning My Soldier."
"Morning My Princess tashi kiyi alwala kiyi Sallah nima zan wuce Masjid."
"My Soldier can I ask of a favor please?"
"Sure My Princess ina jinki."
"Kayi Sallah a gida yau please."
"But why?"
"Inason ka jani Sallah one last time kafin kayi tafiyan."
"Shikenan abinda kikeso?" Kai tayi nodding a hankali, "toh tashi kiyi alwala am
waiting for you." Bata tsamman ze amince so easily haka ba, "dagaske Ya Al'ameen?"
"What My Princess wants she gets it." Dad'i sosai taji ta miqe ta shiga bayi,
after a while ta fito ta tarar da Al'ameen rik'e da hijabinta.

"Gashi sa" yace da ita, wani irin murmushi me sosa zuciya ta sakar masa sannan
ta miqa hannu zata kar6a, se ji tayi yaja hannun nata a hankali ya matso da ita
kusa dashi sannan ya shiga sanya mata hijabin a hankali, ita ko duk anan ta kasa
d'aga eyes nata daga kan shi se kallonsa take cike da adoration. "Can we pray now?"
Ya tambayeta. Kai Ta gyad'a mai, "thank you for everything Ya Al'ameen, I love
you." Smiling zallah ya mata sannan ya shiga jansu Sallah, wane Sudeis haka take
jin muryan Al'ameen idan yana raira Al~Qur'ani. Koda suka idar da Sallan ji take as
if tace masa su sake yin wani, bata gajiya da jin muryansa. Sun gama Azkar nasu
suka koma suka kwanta kasancewar flight na Al'ameen na k'arfe d'aya ne there's
nothing to rush about. From each bed end suka kwanta, "My Princess" ya kira sunanta
a hankali.
"Na'am" ta amsa tare da juyowa tana facing nasa, hannunsa taga ya bud'e mata as
if though ya karance mind nata she can't tell how much she wants to be close to
him all the time. Ba tare da 6ata lokaci ba ta matso tare da shigewa jikinsa,
rufeta yayi da hannunsa making her feel more at home. "I love you My Soldier."
"Shh! Sleep okay?" Kai ta gyad'a a hankali daga nan wani baccin ya sake yin awon
gaba da ita, Haka Al'ameen ma.

As early as 9am Zeezee ta tashi, har anan Al'ameen ko bacci yake yi, kallonsa ta
tsaya yi sannan a hankali ta zame jikinta daga rungumar daya mata without waking
him up. Pecking (light kiss) nasa tayi a cheeks nasa sannan ta mik'e ta nufi
kitchen ta shiga had'a musu breakfast. Bayan ta gama ta koma ciki tayi wanka tasa
wata royal red gown nata me strapless arm tare da applying light makeup. Sumarta ta
taje tayi oiling tayi packing into a bunny style sannan ta k'arisa kan gadon da
Al'ameen keta bacci adorably har yanzu. Zama tayi a gefensa tana tunanin ya za'ayi
ta tadashi, chan ta kai hannunta kan fuskansa dai-dai kan whole na dimples nasa
tasa yatsarta tana wasa dashi, ganin yak'i tashi har yanzu ta sauk'o zuwa light red
lips nasa ta shiga bi a hankali da yatsanta, tayi hakan sau uku ana hud'u Al'ameen
ya shiga bud'e idanunsa. Murmushi ta sakar ganin plan nata has worked out, yana
gama bud'e idanunsa ya fara cin karo da face na Zeezee dake d'auke da beautician
smile ever! "Morning My Handsome Soldier" ta mik'a tayi pecking nasa a cheeks nasa.
Kallonta kawai ya tsaya yi full of wonder and adoration. "Tashi muje kayi wanka,
breakfast is ready."

"Princess?" Yayi magana finally.


"Na'am My Soldier."
"You are looking ravishing."
"Thank you Sweetheart tashi ko in d'aga ka ne?" Dariya kad'an yayi "can you?"
"Ma dariya kake? Wait and see." Mik'ewa tayi ta shiga jansa da hannunsa, nishi
take sosai tana faman jansa amman ko motsi baiyi se faman dariya yake mata chan ya
mik'e da kansa wanda a sanadin haka ta fad'a jikinsa "oops! Am sorry" tayi maganan
tana neman tashi daga kan cinyansa.
"I told you bazaki iya d'agani ba."
"Maybe saboda ban karya bane banida energy yanzu."
"Baki yarda ba still kenan?"
"Eh mana, you are My Baby after all tashi kayi wanka." Mik'ewa yayi at a time,
hannunsa ta rik'e sannan ta kaishi har izuwa bakin k'ofan bayin, "your towel is
inside, seka fito." Murmushi kawai ya iya mata saboda he can't explain how much he
loves her. Kafin Al'ameen ya fito daga wanka har Zeezee ta ciro mishi three quarter
wandon da zesa da kuma T shirt me pattern na sojoji. Yana bud'e k'ofan ta d'aga kai
tana kallonsa, packs nasa precisely daga bisani tace, "come over Sweetheart" tayi
mai nuni da gefenta. Bece komi ba ya k'ariso ya zauna gefenta, "ga cream naka ko in
shafa maka?"
"Haba Princess am I a baby? Zanyi da kaina."
"Yes mana, you are My Baby, toh shafa ina jiranka." Zama tayi tana kallonsa wane
TV ba abinda yafi tafiyar mata da imani like how muscles nasa suke motsawa, suke
going up and down idan yana shafa man. Yana gamawa ta mik'a mai kayansa tare da
basa privacy. Timing nasa tayi a dai-dai lokacin daya gama sa kayan ta dawota
d'akin sannan tajasa izuwa dining table tayi serving nasa. Suna karyawa tana yimai
hiran soyayya kala-kala.
Wajajen 12noon Al'ameen yasa Saje ya fito mar da akwatinsa, tun anan fa mood na
Zeezee ya sauya, bata son tafiyarsa saboda she don't wanna miss him. 12:15pm
Al'ameen ya shirya tsaf cikin uniform nasa, Zeezee na zaune akan gado fuskarta ba
walwala ko kad'an. Har gabanta ya k'ariso sannan ya miqa mata hannunsa nufin tayi
grabbing, kaman da baza tayi ba se kawai ta sa nata ciki, a nitse ya mik'ar da ita.
"My Princess why the sad face?"
"I don't want you to go" ta fad'a sincerely.
"And why?" Kai ta d'ago tana kallonsa "because I don't wanna miss you Ya
Al'ameen, it's infectious to me." Ta k'are maganan wane zatayi kuka, "shh! Don't
cry please, we'll keep in touch Princess, kuma ai ba tafiya zanyi kwata-kwata ba
maybe nan da 2 weeks na dawo." Kuka kawai tasa, "har two weeks Sweetheart ? Kuma
shima maybe ne? Ya kake so in rayu ba kai Ya Al'ameen?"
"Bana son ganin kukan nan" hannu yasa ya share mata hawayen nata, "in shaa Allah
in two weeks time zan dawo."
"Promise me Ya Al'ameen."
"I promise Princess." Hugging nasa tayi tana me cigaba da kuka "I love you so
much Sweetheart, please don't take long ka dawo kaji?"
"Naji Princess I won't in shaa Allah but first kibar kukan nan."
"I can't." Lalashinta yayi tayi har seda tayi shiru sannan ya d'agota daga
jikinsa, "smile toh." Kai tayi saurin kad'awa, "please mana Princess I badly need
that smile."
"I badly need you also."
"I love you Princess, I love you so much." Dad'i sosai taji wanda bata san
lokacinda ta shiga smiling ba, "thats My Woman!" yayi exclaiming duban rolex agogon
hannunsa yayi yaga its getting to 12:30 ga flight nasa 1pm ne. "I should get going"
hannu yasa a pocket nasa ya zaro bundle na N100 "gashi ki rik'e wannan."
"Nayi me dashi My Soldier?"
"Ki rik'e incase any needs arises."
"Yayi yawa, balle ma I don't need any cash, komin da nake buk'ata akwai keep your
money kaji?"
"I insist ki kar6a ba fata ba but something bad might happen to you buk'atan
kud'i kuma yayi rising."
"Toh ka rage yayi yawa."
"Princess bana son muna musu" akan gado ya wulla mata "gashi, se munyi yawa toh,
I love you make sure you take care of yourself kinji? You are free to go anywhere
you want na baki izini saidai don't stay late at night, okay?" Yana kaiwa nan ya
sauk'e hannunta dake cikin nasa a hankali sannan ya juya, be kaiga fara tafiya ba
Zeezee da hawaye ya cike dam a idonta ta kama hannunsa tare da juyo dashi.

Lips nasu kawai tayi crashing akan na juna ta shiga kissing nasa with all that
she got not minding a sh*t. Hannayenta ta zagaye a wuyansa, kissing him the more a
yayinda shi kuma a hankali ya zagaye hannayensa a tiny waist nata tare da bending
height nasa kad'an giving her more access. Moving in sync with each of her move
yake, he didn't make any move rather following nata kawai yake. Sun d'au tsawon
lokaci a haka sannan a hankali Zeezee ta sake shi tare da hugging nasa gam-gam wane
za'a k'watan mata shi. "I love you more My Husband, you are the most sweetest thing
that has ever happened to me. Allah ya kare min kai ya kaika ya kuma sake dawo min
da kai lafiya, safe and sound. Allah ya raba ka da dukkan wani sharri da masu
sharri, may you live long and prosper, your Wife and also your Princess loves you
way much." Hugging nata back yayi yana me sake jin sonta na shigansa, "ameen My
Princess thank you so much." A hankali ta raba hug d'in sede har yanzu bata sake
kallon cikin idonsa ba, ita kanta bata d'au zata iya kissing nasa as how she did
ba, atleast kissing him was worth it, his lips are sweeter than that of Adeel's.
"You should go kar kayi missing flight naka" tana fad'in haka ta juya mishi baya da
wuri don bata son yaga kalan hawayen da takeyi, shima he can't take her crying
anymore kuma yasan muddin ya cigaba da tsayuwa anan kukan ze cigaba da sata, "I
love you Princess" yayi whispering mata sannan ya fice.
Wani kukan ma se da taji an tada engine na motan Al'ameen. Bajewa tayi kan gado
tana kuka sosai wane zata cire ranta, never once have she ever imagined that she'll
love Al'ameen like this. Sam ta kasa dena kukan, drawer'n gefenta tasa hannu ta
zaro wedding album nasu nan ta bud'e ta shiga viewing tana me sake wani sabon
kukan, a haka ne har bacci 6arawo ya saceta. Se kusan after 2pm ta tashi tayi
alwala tayi Sallah ta kuma ci abinci. Wayarta ta d'aga don kiran Al'ameen inda ta
tarar da two missed calls nasa, take tayi calling back wanda shima se a karo na
biyu ya d'aga kasancewar bai kusa.
"My Princess" ya fad'a cike da k'auna.
"Na'am My Soldier" se kawai memory'n how tayi kissing nasa ya soma dancing a
kanta, kissing him was the best feeling ever.
"Nad'au kinyi fushi dani ne ai."
"Ai baka laifi bale nayi fushi da kai Sweetheart, how was your trip?"
"Alhamdulillah kin bar kukan yanzu ko?"
"Nabari but I'm missing you already."
"I know and me either, kinci abinci?"
"Eh kai fah?"
"Also, meh kikeyi yanzu?"
"Babu, yanzu na idar da Sallah."
"Princess se pass 2 kikeyin Sallah, why?"
"Ba dagangan bane I slept over shiyasa bazan sake wasa da Sallah ba."
"Yauwa Princess, I'll be heading to a meeting yanzu, take care okay? I love
you."
"I love you more." Kiss ta mai blowing a wayan "muahh." Yana murmushi sosai yace,
"thank you" tare da katsewa. Through out a gida Zeezee ta yini, waya da Lubiee
kawai suka tayi kafin ta kwanta around 10pm ta gwada layin Al'ameen inda ta mai har
two missed calls be d'aga ba kasancewar kansa yayi zafi da aiki. Taso jin muryansa
kafin ta kwanta amman hakan be yuwu ba don haka ta mai sending message as follows,
_My Handsome Soldier, just called to check up on you before going to bed, my
bed is empty without you. Your Princess miss you badly, take care I love you._
takai 10mins rik'e da wayan tana jiran reply nasa amman shiru don haka kawai ta
kashe wuta ta kwanta.
Ba Al'ameen ya sake sa wayansa a ido ba se 12am dayazo kwanciya missed calls
nata da text mssg ya tarar, har ya shiga dialing numbanta amma ganin pass 12 na
dare kawai ya katse yace ze bari se gobe kar yayi interfering wa baccinta. Da
Asubah bim ake sanar dashi zasu koma Abuja, tafiya ba shiri gabad'aya ya mantar
dashi da kiran Zeezee daya keson yi, itako batayi zuciya ba dukda rashin calling
nata back da Al'ameen beyi ba ta sake yi mai wasu two missed calls d'in yau da safe
had'e da good morning text message. Aiki ne sosai ya rik'e Al'ameen se a daren
ranan ya samu time na kansa, baccin bala'i yake ji amman yasan he needs to hear
from his Princess ya take. Kiranta yayi har kusan 3 missed calls amman tak'i d'auka
by now tayi zuciya itama.

Facetime Video call ya shiga mata wanda shima se kusan a karo na uku ta d'aga,
nan ma k'eyarta ta juya mishi wai baze kalli face nata ba tunda yake shareta haka.
"Haba Princess turn mana."
"O'o" tace still backing him, "missed calls nawa na maka se yanzu kaga daman kira
na, kasan yadda hankali na ya tashi kuwa?"
"Princess am sorry give your Soldier a chance to explain kinji?" Nanma kafad'a ta
buga "please Princess I want to see that beautiful face" yayi maganan tamkar zeyi
kuka jin haka ta juyo da wuri, anan ya samu daman kallonta shima, fuskarta na
d'auke da light makeup "wow! You are looking spectacular, I'm missing you
Princess."
"Nasan nice kawai ke missing naka, kaida tunda ka tafi sau d'aya ka kirani."
"Princess kema kinsan I won't do that on purpose." Explaining komi dallah dallah
yayi mata wanda ta fahimce sa sosai itama ta kuma basa hak'uri game da saurin
fushin da tayi. Lovey-dovey hira suka ta sha seda taga Al'ameen na gyan-gyad'i
sannan ta barsa ya kwanta. Kaman yadda ta saba tun tafiyarsa, yau ma ta d'auko
shirt nasa ta sak'ala a hancinta tana shaqan daddad'an turaren jikinsa har tayi
bacci.

Haka kuma rayuwarsu ta cigaba da kasancewa anytime Al'ameen is less busy ze kira
Zeezee ko yayi mata video call suyita hira, a kullum dad'a son juna suke barin ma
Zeezee da take ganin bazata iya rayuwa idan ba Al'ameen ba. Idan ta gaji da zaman
gida se ta leqa gida chan gun Mama kokuwa gidansu Lubiee, last weekend ta d'auko su
Ramlah suka taya ta yin weekends.
Yau ne cur two weeks da Al'ameen yace zeyi ya cika, tun jiya Zeezee ta kasa
samun sukuni she can't wait for today, da safe yau ta kirasa bayan su gaisa sun
gama gaya ma juna how much they miss each other take tunasar dashi batun yau fa
yace ze dawo. Anzo gurin yace a ransa domin yasan dawowansa wannan satin ma baze
yuwu ba balle wai yau, shine kaman babba yanzu manya biyu zuwa ukun da suke gabansa
duk an sauk'e musu aiki shi ke komi, its damn hectic.
"Hello Sweetheart kayi shiru fah."
"Princess." Daga yadda ya kira sunanta ta gane he can't make it.
"Princess I'm so sorry." Kuka kawai yaji tasa ta cikin wayar, "Ya Salam! Princess
please cut it out, kukan me kuma kike? Ya isa please, I'm sorry I can't make it
this week kiyi hak'uri kinji? Aiki ne yamin yawa."
"Its okay" kad'ai tace masa sounding disappointed sarai yasan its not okay kawai
ta fad'a ne.
"I know its not kiyi hak'uri kinji? I miss you also."
"Shikenan."
"Princess you are still mad, I can sense it."
"Am not" ta k'arya tasa.
"Tell me you love me if you are not toh." Shiru tayi danko she is really mad
d'in, ta gama sa rai yau ze dawo kuma yace aiki ya rik'e shi? Bata so haka ba.
Hak'uri yata bata da k'yar ya samu ta hak'ura suka ta6a hira kad'an sannan yayi
excusing kansa. Mama Babba ta kira suka gaisa sannan Hjy Sadeeyah.

Sati uku Zeezee ta kwashe bata sa Al'ameen nata a ido ba in bade Video call
sukayi ba, she miss him so much. A ranan daya kamata ya shigon ma be samu dama ba,
kuka Zeezee tayita mar da suke Video call bayan daya sanar da ita cewa he can't
make it ranan. Ba irin hak'urin da be bata ba amman tak'i hak'ura haka tayi mai
fushi bata sake kiransa ba.
Hakan ba k'aramin damun Al'ameen yake ba, squeezing time nasa yayi sosai ya samu
ya zak'ulo hutun sati d'aya zuwa biyu haka wanda yak'i sanar da Zeezee yana son
suprising nata. Ko ya kirata yanzu bata zagewa tayi mai hira as before shiko bai
gajiya da bata hak'uri, se daya k'ara three more days akan actual date daya kamata
ya dawo sannan ya samu ya kammala abubuwan da yake gabansa. Zuwan bazata yayi mata
ko kad'an be nuna mata a yau ze shigo gari ba.

Tun tashiwar Zeezee yau tayi wanka ta gama ayyukanta ta kwanta a parlour tana
kallo, chan da kallon ya isheta tayi tunanin zuwa gidansu Lubiee. Tsaf ta shirya ta
fice, da misalin k'arfe uku Al'ameen ya shigo gari, 3:30pm dot ya masa a gida, ciki
Saje ya shiga masa da akwatinsa. Ganin ba motan Zeezee Al'ameen ya tambayi me gadi
inda yake sanar dashi just now ta fita gidan k'awarta Lubiee amman tace she won't
take long. Kai yamai nodding sannan ya shigo ciki inda ya tarar da ko ina tsaf ba
dotti ga kuma k'amshin turaren wuta, kayan jikinsa ya rage ya watsa ruwa ya fito
parlour yayi zamansa. Around 4:30pm Zeezee ta dawo gida inda tayi parking daga
waje-wajen parking lot shikuma driver can cikin garriage yakai motan Al'ameen hakan
yasa Zeezee bata gani ba. All exhausted ta bud'e k'ofa ta shiga ta sake miyarwa,
mutumin data gani zaune akan kujera a gabanta ne ya mugun bata mamaki tare da
jefata cikin wani irin farin ciki.
"Ya Al'ameen! My Soldier!" Tayi exclaiming sunansa unbelievably. Miqewa yayi a
nitse yana sanye da vest da free sized black sports trousers. Hannunsa ya bud'e
mata "My Princess" ya kirata cikin zazzak'ar muryansa. Yasar da handbag natan tayi
ta ruga a guje taje tayi hugging nasa.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣5⃣

_Here's to third page of dedication My Special Star ⭐ AUNTY SIS, my love for
you is like tears from the sky thanks for everything._

Washegari bayan sallan Azahar Lovebirds d'in suna zaune a parlour suna
shak'atawa. Zeezee ta kwantar da kanta bisa cinyan Al'ameen suna kallon sports.
Chan ta juyo tana kallonsa, "Princess wani abu ne?" Ya tambayeta.
"Ya Al'ameen dagaske yanzu this week zaka koma?"
"Princess haven't we talked about this? Kiyi hak'uri nima fa ba son tafiyan nan
nake ba."
"Toh ka fasa mana."
"Its not possible they need me."
"And I need you also."
"Princess am here for you ain't I?"
"For the time being ba, wai ma aurenka suke ne da zamu na sharing time naka. Ni
wallahi banaso, you are mine alone."
"Princess who says am not yours? Am yours alone Kiyi hak'uri kinji? I won't take
long zan dawo."
"Bawani nasan ka tafi sena sake ganinka ne" tana kaiwa nan ta fice zuwa d'akinsu.
Kuka ta shiga yi a rayuwa bata son abinda ze nisantar da ita daga Al'ameen nata.
Tana cikin rera kukan taji hannunsa akan bayanta, ignoring nasa tayi sema dad'a
k'arfin kukan nata da tayi.

"Princess why are you punishing me like this? Yanzu da gan-gan kike wannan kukan
ko sanin banaso." Banza dashi tayi se kukan take. Zagayowa yayi ta gaban ta da wuri
ta gwada juyawa wanda tuni Al'ameen ya rik'o face nata. A hankali ya d'agata tare
da zaunar da ita, "I'm sorry kinji? Nasan kina hak'uri but ki k'ara, its never my
wish to leave you all by yourself." Hawayenta ya share mata da hannunsa, hugging
nasa kawai tayi "not a tear again please Princess." Da k'yar ta danne kukan sannan
ta d'ago daga jikinsa tana kallonsa. Kallo d'aya ya mata ya gano tana buk'atar
mijinta ne, shikuwa duk abinda take so shi zeyi mata. Ba k'aramin dad'i Zeezee ta
jiyo ba ganin yau bata nemi Al'ameen ba amman ya biya mata buk'atar ta.

***
Da La'asr bayan sun idar da Sallah Zeezee taje ta samu Al'ameen dake miqe kan
gado ta kwanta a gefensa, "Sweetheart?"
"Yes Princess."
"Am bored mu d'an fita please, tunda kazo ba inda muka je."
"Ina kikeson muje?"
"Ko ina ni ka kaini." Matso da ita jikinsa yayi "bari zuwa 5 haka yanzu mu d'an
huta kinji?" Kai ta gyad'a mai a hankali sannan ta aza kanta bisa k'irjinsa "I love
you Ya Al'ameen, you are My Everything."
"As you are to me also Princess lets get some nap." Daga nan duk sukayi shiru
inda a hankali bacci yayi gaba dasu. 5:20pm Al'ameen ya tashi, a hankali ya raba
jikin Zeezee daga nasa sannan ya fad'a bathroom yayi wanka ya shirya sannan itama
ya tada ita. Cikin k'ank'anin lokaci duk suka shirya sunzo fita Zeezee ta kalli
Al'ameen a marainace.

"What is it Princess?"
"My Soldier kullum ne bodyguards nakan nan se sun raka ka duk inda zaka?"
"Why? What is it?"
"I want us to go out just the two of us, be the one to drive us."
"Is that what you want?"
"Yes Sweetheart."
"Toh chill, your wish is my absolute command. Ahmad and co, ku koma posts naku
I'll be the one to drive today."
"With all due respect Sir we are being assigned to guard you anywhere you go."
Ahmad yayi explaining.
"And my wife says no, she wants me to drive her today, any question?"
"No Sir" cewar Sadeeq a tare sukayi saluting nasa suka ja baya. Dad'i sosai Zeezee
taji ganin yadda da zaran tacewa Al'ameen ga abinda take so yake kwatanta yi mata.
"I love you Sweetheart" ta fad'a tare da pecking nasa a cheeks nasa, murmushi ya
mata sannan da kansa ya bud'e mata motar ta shiga "thank you My Soldier."
"You're most welcome Princess."
Su biyu abinsu suka fita yau ya kaita shopping daga chan suka wuce Ice Cream
shop ya saya mata sannan suka dawo gida.

A daren ranan da Al'ameen ze koma Abj Zeezee ta shirya masa akwatinsa tsaf
sede komi sime-sime takeyi, don bata son ya tafi ji take as if tayi faking rashin
lafiya yace ya fasa tafiyan. Daren ranan Al'ameen keta shisshigewa Zeezee itako se
basar dashi take ta na nuna mai bata so badan komi ba kuwa don yasan she is not
happy ze tafi ya barta gobe ne. Shiko yasan halinta sarai bayan tafiyansa tana iya
kiransa ma tace koda ze tafi be bata hak'k'inta ba yasa yak'i hak'ura yata binta
har seda yayi turning nata on daman yasan she can't ignore him. Sosai ya gamsar da
ita daren ranan making he forget all of her problems.

Da Asubah yau tare ma sukayi wankan sannan sukayi Sallah, Zeezee bata koma bacci
ba kasancewar flight na Al'ameen 8am ne. Chores nata ta gama ta yi musu breakfast
sannan taje ta tada Al'ameen yayi wanka. Kallonta yake tayi tun da suka idar da
Sallah yau take ta faman had'a mishi rai. She couldn't hold her tears back anymore
a lokacin da Saje yazo ya fita da akwatin Al'ameen. Juyawa tayi da suri zata wuce
d'aki inda ya rik'e hannunta restraining her. "Princess in duk wani tafiya na
zakina kuka haka ya kikeson ina ji a jikina? Gani nake like ni ke saki kukan." Ya
fad'a cikin zazzak'ar muryansa a hankali.
"Ba kai bane Ya Al'ameen just go."
"I can't leave you kina kuka haka."
"Ya Al'ameen I don't want you to go" tayi maganan cikin kuka sosai, bending yayi a
hankali yayi owning lips nata be barta ba seda yaji tabar kukan da takeyin. "I
won't take long zan dawo in shaa Allah kinji?" Kai ta gyad'a a hankali hannayenta
dake cikin nasa ya d'ago yayi pecking both sannan back to her forehead, cheeks,
nose, jaw and neck by now dariya take sosai.
"Thats My Woman don't cry again okay?"
"I won't, go hurry don't be late." Har bakin mota ta rakasa seda taji driver ya
kunna motar kuma taji bazata iya ba, a guje ta ruga ciki ta baje kan gado tana kuka
sosai. Shima Al'ameen ji yake as if ya fasa tafiyan, layinta ya shiga dialing wanda
tana ganin call d'in amman ta kasa d'agawa tsan-tsan kuka. Agun bacci 6arawo ya
saceta ba ita ta tashi ba se bayan Azahar, a hankali ta nufi bayi tayi alwala ta yi
Sallah sannan ta d'ago wayarta inda ta tarar da countless missed calls na Al'ameen
so take ta kirasa amman bata jin zata iya saboda tasan how infectious jin muryansa
ke a gareta, yanzun seya sake sata sabon kuka. Layin Lubiee kawai ta kira wanda
tayi picking immediately.
"Ya tafi kenan?" Abinda Lubiee ta soma tambayarta. Rai a dak'ule Zeezee tace,
"wa?"
"Wa kuwa inba Soldier'n mu ba."
"Mschww!" taja tsuka.
"LOL" Lubiee ta k'yalk'yale da dariya "my question has already been answered. Ai
dama na sani, se idan mijin naki ya tafi kike neman mutane."
"Lubiee wallahi zanci k'aniyanki akan haushin dake damuna yanzu."
"See me see wahala! Tell me Babe meya faru?"
"Bansani ba." Tayi maganan tana murgud'a baki wane Lubieen na gabanta. "Easy mana
Babe meya faru ne?"
"Ya Al'ameen ya tafi."
"Ahaap! Ai dama na sani, wato ke se in Ya Al'ameen Ya tafi ne zaki tuna dani ko?
Nima am busy, tun yaushe nake trying numbernki bai shiga, sede inta ganin story'n
ki kina posting pics and vids na Ya Al'ameen na miki magana still shekaran jiya a
snapchat d'in kika k'i replying."
"Babe ba haka bane, bazan iya raba hankalina bane idan Sweetheart d'ina na gida,
I need to take care of him closely kamin wasu shegu chan a waje su min gaba da
abuna."
"Tohhh su masu Sweetheart manya nima am busy, saurayi na na jira na a waje."
"Wallahi Babe kika katse wayar nan sena ci k'aniyanki banason tsiya."
"Akwai wanda ya kaiki tsiya ne? Sheggur kawai."
"Uhm niba wannan ba kina gida ne yau?"
"Wai zuwa zakiyi?"
"Eh."
"Hehe Amaryar Ya Al'ameen, ba'a ganinki se mai gida bai gari."
"Mschww! da alama fad'a kikeso muyi nama fasa zuwa gidan naku zani gun Mama."
"Yi hak-" karap Zeezee ta katse wayan abinta. Bata kaiga ajiye wayan ba taga
video call na Al'ameen na shigowa. Kaman bazata d'aga ba se kuma taga ya bata
tausayi tayi picking tare da juya ma wayan baya yadda baze ma iya ganin fuskarta
ba.

"Thanks Gee!" Ya furta "thanks for picking up Princess." Shiru tayi not ready
to talk, "Princess baki hak'ura ba?" Still shiru. "Okay lemmi go down on my knees."
Da sauri ta juya "no please don't."
"Princess mesa kike min haka ne? Kuka kikeson in soma yi neh?" A hankali ta kad'a
mai kai "look up at me, yi hak'uri ki kalleni am already missing your eyes on me."
"I miss you more" tayi maganan finally tana kallonsa. "Shhh! Don't cry again
kinji? I love you so much."
"I love you more Sweetheart."
"Princess please nan gaba don't punish me like this, sau nawa nake kiranki baki
d'aukawa."
"Its because I don't wan to listen to your voice."
"But why?" Ya tambayeta cike da mamaki, "is my voice that bad."
"Oh God no! Kai kanka kasan muryanka ya fiye min komi dad'in sauraro a duniyan
nan."
"Then mesa kika k'i picking?"
"It is infectious to me, muryanka ba k'aramin affecting d'ina yake ba
Sweetheart."
"Hakane princess?"
"Sosai kuwa Sweetheart"
"Toh da ana changing voice da nayi."
"See you, kai baka san voice naka ba d'aya daga cikin abubuwan da nakeso a
tattare da kai ba? Your voice is damn sweet."
"Just like yours."
"Uhm yauwa My Soldier ni zan koma gida gun Mama kafin ka dawo."
"Bakiya son zama ke kad'ai ko?" Kai ta gyad'a a shagwa6ance, "in ni kad'ai ne I
keep on missing you."
"I'm sorry Princess se ki koma gun Mama before in dawon I don't want you to be
feeling lonely."
"I am lonely already Sweetheart, I miss you bansan ya zan cigaba da rayuwa
before ka dawo ba."
"Haba Princess! We'll always keep in touch ai, we are in touch already."
"Se waya da video call kawai can I hug or kiss you? Ko kuma zaka iya bani hak'k'i
na ne ta wayan?" Tayi stating rai a dak'ule.
"I know that's not possible shiyasa nake baki hak'uri Princess."
"Ni bana son hak'urin ka kai nakeso, hak'k'i na nakeso."
"Don't worry zan dawo soon enough in baki hak'k'in ki Princess nima kuma in
kar6i nawa."
"Ai naka is available all the time nine de abar tausayi." Dariya sosai ta basa,
"aww dariya ma nake baka? Ai abar a tausaya min d'ince ga miji but when am in need
of him baya nan, akwai abin tausayin da yafi wannan ne?" Da k'yar ya iya ya
tsagaita dariyan nasa amman ya kasa magana.

"Eh kayita min dariyan."


"I'm sorry Princess" ya fad'a murmushin fuskansa na bunk'asa. "Princess Ji yadda
kike magana fa as if rabuwan ki dani irin months d'innan ne."
"Ai kaman months d'inne a minute without you is like a thousand days to me."
"Haba Princess" yayi frowning face nasa. "Jiya-jiya ma fa we..." se yayi shiru.
"Toh yau kuma fa? Gobe fa? Ni wallahi bazan iya ba I need you" ta k'are maganan
as if though zatayi kuka.
"Princess the more kike cewa bazaki iya ba the more bazaki iyan ba, yi hak'uri
kinji? Yi hak'uri Princess kije gida gun Mama."
"Eh saboda ka samu more reason to stay in Abuja ba."
"Oh God Princess! Toh shikenan kiyi zaman ki a gida."
"Saboda inyi ta missing naka ba? Dad'i kake ji idan kaji nace am missing you."
"God help me" ya fad'a tare da dafe goshinsa. "Do whats suit you toh."
"Saboda you don't care ba no problem zanje in samu Mama."
"Wai Princess senayi miki kuka tukun zaki san ina missing naki over ne? Kisani I
miss you more fah, kawai bana nuna miki ne saboda bana son ki shiga damuwa." Sekuma
ya bata tausayi.
"Toh I'm sorry."
"I should be the one who's sorry, kinyi hak'uri?"
"Nayi My Soldier ai baka laifi." ta fad'a tare sakar mai da murmushi.
"Thats My Woman so zaki gun Maman ne?" Kai ta gyad'a "okay toh in kinje ki gaishe
min da ita kinji?"
"I'll."
"Yauwa Princess I love you okay?"
"I love you too" tayi mai blowing kiss.
"Take care of yourself for me."
"I'll semun sake magana" tace dashi tare da katse vid call d'in.

Akwatinta ta shiga shiryawa wanda tana gamawa ta kira Mama don sanar da ita da
zuwanta. Abinda Mama ta soma tambayarta ne ya mugun bata mamaki. "Ya tafi kenan?"
Sak abinda Lubiee ta tambaya itama, shiru Zeezee tayi mamaki kwance a kan fuskarta
"kin min shiru nace ya tafi kenan?"
"Mama-"
"Baki amsani bafa Zeezee." Ta katse ta.
"Eh ya tafi." Ta fad'a a hankali.
"Ba shakka, se in Ya Al'ameen yayi tafiya ne kike sanin sauran mutane suna raye
koh?"
"Mama me kike fad'i wai?"
"K'aniyanki duba wayanki missed calls nawa na miki?"
"Mama yaushe?"
"K'aniyanki nace, ace ata kiran mutum bayi picking waya! Aljannah kike bawa Maj-
Gen d'inne?"
"Mama kinsan bai cika zama ba, idan ya dawo kuma... kuma..."
"Kuma akace ki dena picking calls ba."
"I'm sorry, ina yini?"
"Lafiya ya mijin naki?"
"D'azu da safe ya wuce."
"Ayyah, ya gida toh?"
"Alhamdulillah ya Ya Omar?"
"K'alau yake."
"Uhm Mama nace zan zo gida."
"Lafiya dai ko?"
"Eh lafiya, Ya Al'ameen ne yace zan iya zuwa saboda ze d'an jima wannan
tafiyansan kinga nima sena d'an leqa islamiyya."
"Toh ba matsala kina iya zuwa."
"Toh gani shigowa."
"Yauwa sekin zon." Ahaka sukayi sallama. Tsaf ta d'au wanka ta koma gida inda ta
sauk'a a d'akinta, sharewa tayi, tayi mopping da kuma 'yan goge-goge sannan tayi
joining Mama a kitchen suka had'a dinner. Bayan Sallan Maghrib ta had'a wa Omar
dinner'n shi kan table takai mishi site nasa. Knocking tayi a hankali ya buk'aceta
data shigo. Akan centre table ta ajiye masa "sannu Zeezee thank you."

"You're welcome Ya Omar, me kakeyi haka?"


"Aiki am about to finish though."
"Ohh!"
"Yeah, me ya kawo ki gida kuma?"
"Sweeth-" da sauri ta ko6e bakinta "sorry I mean Ya Al'ameen yayi tafiya kuma ze
jima wannan karan yayi suggesting inzo nan."
"Oh baby sis manya, su Sweetheart."
"Kai Ya Omar halin kannan na nan deh."
"Me za'a fasa? Ya kike toh?"
"Lafiya ya aiki?"
"Alhamdulillah."
"Kizo ki zauna mana kinyi tsaye achan sekace soldier, ko auran Soldier'n yasa
kema kika fara aikinsu?" Murmushi ta saki sannan taje Gefensa ta k'arisa ta zauna
"wai kai Ya Omar yaushe zaka kawo mana sister in-law namu?"
"Very soon Mama bata sanar dake bane?"
"Nahh."
"She did mana ranan tace min ta kiraki."
"I think maybe shine lokacinda ban d'auka d'innan ba."
"Yauwa!" Yayi exclaiming "wai ma ina kike ajiye wayanki ne? I called you also
kusan sau biyu baki picking."
"Ya Omar bazaka gane bane."
"Ohh wato in mijinki na gari baki da time na kowa se nasa abee?"
"Eh mana" ta amsa tana murmushi as if Al'ameen na gabanta.
"Da kyau kin ko yi missing, se bikin ya matso zakisan amaryar."
"Haba mana Ya Omar."
"Don't even beg me."
"Kar ka fad'an zan rok'i Mama ta gayamin."
"Ai nace mata karta sanar dake thats your punishment." Ta bud'e baki zatayi
magana wayan Omar dake kan table ya shiga ruri kafin tace zata duba wake kira har
ya d'aga amman sede taga picture Identity na wacce ke kiran kamar tasan ta, wacece
toh?
"Hello Babe, I'll call you later ina tare da talkertive d'innan yanzu, I love
you." Da sauri ya kashe gudun kar Zeezee ta jiyo muryan Babe tasan.
"Toh yanzu dan rashin mutunci nice talkertive d'in Ya Omar? Kuma ma tsaya kaman
nasan Babe nakan nan. D'an samin hotonta ingani please."
"Ai kaman na miki revealing identity nata kenan."
"Tsaya ma wallahi na santa, Lubiee ce?"
"Lu waye?" Yawani yamutsa fuska "wace Lubiee kuma?"
"Lubiee my best friend."
"Omg!" Yasa dariya "you expect me to date your friend haba! Wuce nan ai."
"To wacece?"
"Bazan fad'a ba."
"Ma wallahi itance kaman pic nata na gani tanada same pink mayafin nan."
"Silly reason, Lubieen taki kad'ai ce me Pink veil?"
"Ba ita bace amman-"
"Abeg Zeezee free me, ni ba abinda ze kaini dating friend naki to talk more of
marrying her."
"Toh wacece please ka gayan."
"Nak'i." Rok'onsa tatayi amman yak'i sanar da ita, se kusan to 10 sukayi sallama
ta koma site nasu da Mama, she really enjoyed spending time with Omar. D'akin Mama
tajeta inda ta tarar da ita tana waya da Ibraheem.

"Mama please ki bani wayan idan kun gama" ta fad'a alokacin da ta zauna gefen
Mama. Wani dirty look Mama ta bita dashi "pleaseee" ta maraice fuska "inason inji
ya takwarata take ne." Seda su Mama suka gama hirarsu da Ibraheem sannan ta miqa wa
Zeezee wayar. "Halo Ya Ibraheem."
"Mara mutunci ba."
"Kaman ya mara mutunci Ya Ibraheem?"
"Eh mana kin ta6a d'aukan waya kin kirani kinji ya takwararki take ne tunda Ya
Al'ameen naki ya dawo dake d'akin ki?"
"Laaa Ya Ibraheem ba haka bane wallahi, takwara na kullum tana raina na bawa Ya
Al'ameen sak'o ma yakai muku yau ya wuce Abj shima."
"Toh ya kike?"
"Lafiya ya Aunty Fatee, Maamah da Sweetheart d'ina?"
"Lafiya k'alau takwaranki se kuka gabad'aya ta ramar min da Fateemah ta."
"LOL nide takwarana na sani a kula min da ita, da Aunty Fatee ta yaye ta da seku
kawo min ita hutu."
"Uhm, hakan za'ayi nakega idan aka yayetan."
"Yauwa ka gaishemin da Aunty Fatee."
"Toh zata ji goodnight."
"Sleep well" ta katse wayan. "Ashe shima baki ta6a kiransa ba" Mama tayi maganan
tana mata wani kallo.
"Mama ba haka bane fa."
"Naji toh ficemin a d'aki bacci nakeji."
"Yauwa Mama da Allah wace matar da Ya Omar ze aura?"
"Aiko ban fad'a, yace kar na fad'a miki tunda ya kiraki musamman don sanar dake
kika k'i d'agawa."
"Mama please mana" nan ma rok'an Mama tata yi amman Mama tak'i sanar da ita haka
don dolenta takona d'akinta inda ta watsa ruwa ta haye gado ta kwanta tare da kiran
Al'ameen nata suka ta hira har seda ta fara gyangyad'i.

***
Life moved on, rayuwar Zeezee a gida na mata dad'i sosai sede be kai mata kaman
idan TANA TARE DA Ya Al'ameen ba. Da safe zatayi duk kan ayyukan daya kamata da
yamma kuma ta wuce islamiyya. A weekends kuwa ta d'auko Ramlah da Ummie. Ita da
Al'ameen nata whenever they are less busy suna kan video or audio call, a kullum
dad'a fad'uwa tarkon soyayyan juna suke.
Sati uku Al'ameen ya d'auka amman bayi ma zancen dawowa nan fa hankalin Zeezee
ya tashi ita ta gaji she wants him back. Yau da daddare bayan ta kwanta ta kirasa
suka gaisa sannan take tambayarsa yaushe ze shigo.
"Princess har zama gun Mama ya isheki ne?"
"Eh mana ni zama da kaine kawai bayi gundira ta."
"Uhm toh Princess ki k'ara hak'uri kinji?"
"Ya Al'ameen kullum shikenan ni cikin hak'uri, rabo na da kai fa 3 weeks akwai
hak'urin daya fi wannan neh?"
"Babu Princess amman ya muka iya? Haka schedule na job d'ina yake."
"Ni toh ka fasa aikin mana, am not after your money Sweetheart am after you, kai
nakeso kuma ko a talaka kake ahakan zan cigaba da sonka."
"LOL I know Princess amman thats not possible kema kinsani ai, I'll see zuwa next
week idan zan iya shigowa."
"Nasan ma ba shigowan zaka yi ba kar ma nasa rai nazo na zama disappointed."
"I'll make it up to you Princess I promise."
"I hope you do, I love you."
"I love you too, get some sleep kinji?"
"I'll and you too seda safe."
"Allah bamu alkhairi" yace tare da katse wayan.

*MIEMIEBEEE. Team #YGC! 🎀 *


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣6⃣

_Here's to fourth page of dedication AUNTY SIS⭐ ILY❤_

Life moved on, koda Al'ameen yace ma Zeezee ze shigo zuwa next week d'in
hakan be samu ba. Se a sati na gaba ya samu hutu wanda be sanar da Zeezee nan ma ba
saboda har yanzu ta kasa sabawa da rashinsa, koya kirata bata zagewa tayi mai hira
sede tayita kumbure-kumbure. Da Azahar ya iso gida bayan ya watsa ruwa abinshi ya
sanya three quarter wando me patterns na sojoji zallah ko vest babu yayi zamansa a
parlour yasan how bad Zeezee tayi missing packs nasa and him in all. Layin Zeezee
ya kira wanda bata jima ba ta d'aga.
"Hello Princess?"
"Sweetheart, ina wuni?"
"Lafiya ya kike?"
"Lafiya yau kuma ba aiki ne?"
"Me kika ga?"
"Naga baka ta6a kirana irin war haka bane ai."
"Haba Princess so kike kice nafi bawa aikina muhimmanci akanki kenan ko me?"
"Your words not mine."
"Uhm kina ina yanzu?"
"Gida gun Mama."
"Ki taho gida yanzu na tura wani da sak'o ya kawo miki."
"Har sak'o ma? In kud'i ne ni banaso, wato ma ba yanzu zaka dawo bako Ya
Al'ameen?" Tayi maganan tana neman yin kuka. "Wallahi aikin nan naka na tauye min
hak'k'i yau getting over a month kenan rabo na danasa Champion d'ina a ido and
abinda zan samu daga gareka shine sak'o? Ka kira yaron naka ka sanar da shi ya
miyar da kud'in bana buk'ata wanda ka ban ma ban ta6a komi a ciki ba har yanzu."
"God help me Princess, yanzu de yi hak'uri ki taho ki kar6a."
"Bana so" tayi stating stubbornly.
"Yi hak'uri fa nace."
"Se yaushe zaka dawo toh?"

"Zuwa next week."


"Hmm Allah yasa toh."
"Zaki zo ki kar6an?"
"Do I have a choice, kace mishi ina tahowa."
"Yauwa Princess I love you so much."
"Toh naji."
"Yau babu I love you too?"
"Babu se randa ka dawo." Murmushi yayi sannan ya katse wayan, ba tare da 6ata
lokaci ba tayafa mayafinta taja mota se zuwa gidanta. Da kaman tayi parking a waje
sekuma wata zuciyar tace mata ta shiga ciki dashi bayan tayi parking daga waje-
wajen lot ta fito tana tambayar me gadi wani yaro ya kawo sak'o?
"A'a Madam but Sir ya kirani yace wani ze zo."
"Mschww ze 6ata min lokaci nida Ya Al'ameen ma yabari inada kud'i a guna."
"Sorry Ma'am you said?"
"No not you, I'll wait for him inside."
"Okay Ma'am." Anan ta wuce ciki tana gwada sa key taji a bud'e bade tun tafiyarta
haka ta barsa a bud'e ba Allah yasota da akwai masu gadi. Da sallamarta ta shiga
inda taga shirtless Al'ameen tsaye daga tsakiyar parlon fuskarsa d'auke da
murmushin dake mugun k'ayatasa.
"My Soldier!" ta fad'a sounding morethan suprised. "My Soldier is it you?"
"Yes Princess, oyoyo!" Da gudu taje ta fad'a jikinsa yau ma ya d'agata sama
kaman ranan. Duk sun kasa breaking hug d'in saboda yadda sukayi missing juna da
k'yar sannan Al'ameen ya sauk'e ta k'asa inda tayi d'agel d'in k'afa da wuri ta
shiga kissing nasa, tana yi yana miyar mata da martani. Kasa rik'esu k'afafunsu
sukayi inda suka fad'a kan kujera se kissing juna suke suna abubuwa kala-kala. Chan
suka ga kujeran ma baze iya d'aukansu ba and like a bride Al'ameen ya d'aga Zeezee
ya hau yin hanyan d'akinsu da ita anan d'inma ta kasa barinsa se kissing nasa take
suna shiga d'akin yayi shutting door d'in se k'aran sauk'an abu naji rigijib akan
gado. Nide nace ayi a hankali.

One hour later...


Shirtless Zeezee da Al'ameen ne kwance kan gado inda tayi pillow da chest nasa,
"My Soldier you keep on suprising me, mesa baka fad'a min zaka dawo ba." Tayi
maganan tana kallon cikin idanunsa.
"Ko na fad'a miki ba yarda zakiyi ba." Miqawa tayi a hankali tayi pecking nasa a
cheeks. "I can't get enough of you Ya Al'ameen you simply complete me, nagode da
wannan wonderful suprise d'in I can't tell you just how much you made my day like I
missed you so much."
"I missed you more Princess" yayi maganan tare da pecking forehead nata shi kuma.
Hugging nasa tayi gagam a kwancen sannan a hankali bacci yayi awon gaba da ita,
shikam ya kasa bacci tunanin just how lucky he is to have Zeezee as his wife yake,
duk abinda yake nema daga gun mace Zeezee nada shi. Gata nan kullum dad'a zuma
takeyi he just love her way much. Pecking forehead nata ya sakeyi "I love you
Zainab."

****
Ai tun dawowan Al'ameen Zeezee taji kowa ya fita mata a rai, ta koma gida ta
kwaso kayakinta ma tak'i daga k'arshe driver akasa ya d'auko mata, gashi daga
dawowan Al'ameen har ta rufe sim nata wayar ma taso kashewa gabad'aya amman don
pictures da takeson d'aukansa anytime ta bari. Da daren ranan ma seda suka sake
gamsar da juna abinsu ita da Al'ameen nata. Washegari bayan sun karya Zeezee na
sanye da vest da free sized knee length trouser se aiki takeyi. Bayan ta gama ta zo
ta fad'a jikin Al'ameen all exhausted.
"Kin gaji ko Princess?"
"Sosai fah kasan rabon dana share gidan tun tafiyarka"
"Sannu da aiki, in kina ganin aikin ze soma miki yawa mu nemo miki me aiki mana,
akwai wasu a gidanmu a KD Jeeddah, Mjay, Maryaty da Kwaiseh" (🤣✌🏽)
"Wai!" Tayi exclaiming "wad'ancan?"
"Kin san su ne?"
"Ai Aysha taban labari koba sune ba wanda suke sonkan nan?" Murmushi ya saki
"inji waye? Aysha baza tabar yad'a rumor bako?"
"Ai gaskiya ne adalilin me zan kawo su gida na haka kawai su samin miji a gaba,
no way fa inason abu na" ta miqa tayi kissing nasa lightly on the lips.
"Toh ai baki san wani abu ba Princess ke kad'ai nakeyi ma kallon mace a cikin
mata sauran duk kallon dabbobi nake musu, my eyes are on you only."
"Really Ya Al'ameen?"
"Really! Sweetheart only you, am yours alone."
"Yeyy! MINE!"

***
Life moved on, har sati biyu Al'ameen yayi ma Zeezee kuma bayi ma zancen komawa
Abj hakan ba k'aramin dad'i yayi wa Zeezee ba, kullum suna maqale da juna abinsu a
parlour ko a d'aki. Jifa-jifa suke fita unguwa. Ana cikin haka ne watan bikin Omar
ya taso wanda har a nan Zeezee batasan wacece amaryar ba. Suna zaune abinsu yau a
parlour ita da Al'ameen, Zeezee ta d'aga kai ta kalli agogo ganin lokacin aza lunch
yayi ta dawo da kallonta kan Al'ameen da kansa ke aze a kan cinyanta. "Sweetheart?"
"Yes Princess."
"Sweetheart me kake so kaci yau? Tun jiya nake tunanin abinda zan dafa mana amman
na kasa."
"Come on don't stress yourself out kome kikeso ki dafa mana."
"Wa kai d'in? Da wannan shegen za6an girkin naka, tell me meh kakeso."
"Anything Princess matso kusa kiji." Ba gardama ta sunkuyo da kanta seji tayi
yayi owning lips nata yana kissing nata, it was a short but yet very romantic and
heart melting kiss ji tayi kaman karya saketa yata kissing natan. "What was that
for?" Ta tambayesa lokacinda ya saketa se faman lasan lips nata take.
"Just to let you know I love you."
"I love you too Ya Al'ameen so much so me kakeso kaci for lunch tell me
anything."
"Anything? lemmi think."

Chan yace, "na jima banci tuwo bafa."


"Tuwo Sweetheart sekace tsoho?"
"Toh mene dama-" bakinsa tayi covering da wuri "wallahi kace kai tsoho ne se
munyi fad'a da kai. D'an 44 da kai d'inne tsoho ni banaso." Hannu yasa ya d'ago
hand natsn daga lips nasa a hankali "44 d'inne ba tsoho ba Princess? Nide tuwo nake
so yau."
"As you wish Sweetheart da miyan me kakeso? Please karka ce kuka."
"LOL karki damu am not a fan of kuka nima kinsan irin miyan da 'yan Maidugurin
nan sukeyi miyan ganye amman su se su sa mishi yakuwa a cikin nan?" Kallonsa take
totally out of words har yaushe Al'ameen yasan su yakuwa? Bama wannan ba meye
had'insa da girkin 'yan Maiduguri?
"Sweetheart har yaushe kasan yadda 'yan Maiduguri suke yin girkinsu?"
"LOL are you kidding me Princess? Kin manta d'an can ne ni?"
"Ohh yeah Shuwa exactly."
"Lallai Princess baki ma san d'an ina ne ni bako?"
"Ai ni kullum cewa nake larabawan Yemen ne ku." Hancinta yaja cike da wasa,
"kekuma ta Saudi ba."
"LOL na gane miyan akwai wata friend d'in Mama Mrs Muhammad itama 'yar Maiduguri
ce kuma tana yin miyan sosai time dana je gidanta a Maiduguri."
"Cool zaki iyamin nima? I miss it alot dama Mama ne kemin always."
"Sure why not? What My Soldier wants he gets it."
"Am grateful Honey nasan idan kikayi naki seya fi na kowa dad'i."
"Sweetheart banda huramin kai o."
"Kema kinsan you are an excellent cook ai."
"Toh thank you but first sena aika me gadi ya siyo min allayyahu, yakuwa da kuma
albasan ganye inada kayan miya da nama na already."
"Right away, nima yau da ni za'ayi girkin na koya."
"Toh kayi me dashi kai kuma da kake office kullum?"
"Who knows rananda bakida lafiya kowani abun fah? Kinga se Soldier'n ki ya miki
girki koba haka ba?"
"Hakane Sweetheart."
"Good koba wannan ne favorite naki ba kema?"
"It is among my Favorite, kasan duk wani abinda kakeso nima inaso." Pecking nata
yayi akan hanci sannan ya miqe yaje ya aiki me gadi. Cikin d'an k'ank'anin lokaci
yaje ya dawo nan da nan Zeezee ta wanke ingrediants d'in da salt sannan ta shiga
yankawa. Tayi kad'an Al'ameen dake tsaye a gefenta da apron nasa shima yace, "kawo
zan tayaki."
"Haba My Soldier kaje parlour please zan gama komi don't worry."
"No I'll assist My Princess today in ba haka ba meye amfani na?"
"Are you sure My Soldier kasan ni banason abinda ze wahalar min da kai."
"Nima haka shiyasa nakeson in tayaki."
"Are you sure Sweetheart."
"Yes Princess."
"Awww thats so sweet of you my Mr. Romantic thank you."
"Shhh!"
"So ka gane yadda zakayin?"
"Leave that to me." Matsa mai kad'an tayi ya amshi knife d'in da mamaki ta tsaya
ganin yadda Al'ameen ke slicing allayahun akan chopping board so gentlemanly.
Wayarta ta d'auko ta kunna ta shiga yimai pictures da videos be mata magana ba be
kuma hanata ba don kanta ta gaji ta ajiye wayan sannan ta shiga had'a kayan miyan
ta markad'a ta kuma wanke nama. Su biyu abinsu gwanin sha'awa suka had'a girkin
sede wani hazari ba gudu ba Zeezee ta mance yadda ake zuba ingrediants d'in
accordingly. She has no choice than to call Mrs Muhammad. Satan idon Al'ameen tayi
ta gudu d'aki ta kirata bayan sun gaisa ta tambayeta inda Mrs Mukhtar tamata bayani
zallah-zallah.

Tana dawowa kitchen d'in ta samu Al'ameen na musu picking grabes har ya gama
slicing komi da komi. "Ina kika je Princess?"
"Na had'a waya na a charging ne" ta mai k'arya. "Har ka gama slicing komi?"
"Yup gasu chan akan counter."
"Thank you Sweetheart you are so sweet." Adeel kam sede a dafa yaci ya kuma zagi
mutum be ta6a assisting nata girki ba. Wink ya mata ya cigaba da picking grapes
d'in. K'arisowa ciki tayi ta had'a miyan tare da aza pot na tuo. In less than
another hour ta sauk'e ta shirya komi ta kai dining sannan ta kai wasu Saje nasu.

"Hummn! Princess kinsan ba wanda ya kaiki iya girki ko?" Yayi maganan a
lokacinda k'amshin girkintan ya buga hancinsa.
"Kai My Soldier, ai girkin yau yayi dad'i ne saboda kasa hannu."
"You think so?"
"Yap."
"Thank you okay?"
"For what?"
"For making me my favorite dish."
"Oh come on Ya Al'ameen kai fa miji na ne hak'k'i na ne nayi maka girki, kanaso
inyi feeding naka?"
"Se inde nayi feeding naki, come over." Ya mata nuni da laps nasa. Dariya take
sosai "no way."
"Kizo ko nayi fushi Princess."
"Swe-"
"Please come on" bata da wata option dole taje ta zaune kan cinyan nasa. Tuon ya
yanka kad'an ya had'a da miya sannan yace mata "ahhh!"
"Under one condition."
"Meneh?"
"Ka bani nima zan baka."
"A'a ni kad'ai zan baki yau."
"Please mana My Soldier" tayi maganan as if though zatayi kuka.
"Toh naji Princess ahhh." Pecking nasa tayi a kumatu sannan ta bud'e bakinta
slightly yasa mata abincin, da gan-gan dan neman magana ta cize hannun nasa.
"Awchh!" Yayi exclaiming. "Princess!" Ya kira sunanta tamkar zeyi kuka a yayinda
take mai dariya. "Me nayi kuma harda cizo?"
"Just to let you know I love you" tamai murmushi, murmushin ya miyar mata itama
sannan ta had'a tuon da miyan k'ato tace mai "ahhh"
"Hhaba Princess ta ina wannan k'aton tuon ze shiga baki na?"
"Kai baka iya loman maza bane? Kaga loman Ya Ibraheem kuwa? Kaman kan mutum, kai
Baba ma gwana ne when it comes to loman tuon miyan kuka so kaima kayi in gani."
"LOL wato in mutane suna cin abinci ke lomansu kike sa eyes akai ko? Nikam bazan
ci ba kafin nima ki kaini gaba kina kwatance dani."
"LOL come on Sweetheart kaima kasan bazan yi haka ba ai ahh ka kar6a."
"Sekin rage." Aiko yak'i kar6an seda ta rage haka suka cigaba da yi har suka gama
cin abincin sannan Zeezee tayi clearing table suka yi Sallah suka hau gado don
hutawa.

Tana kwance bisa chest nasa tana bin pattern na packs nasa da hannunta yace da
ita "Princess."
"Yes My Soldier" tayi maganan tare da d'ago kanta tana kallonsa.
"Kinsan wani abu?" Kai tayi saurin kad'awa "tell me."
"Kina son ki koma school?"
"School?" Ta nanata da mamaki.
"Yes bakiya son kiyi obtaining degree naki kema?"
"Inaso last time I asked Adeel yace min idan naga na sake attending school toh se
inde anayi a lahira which is idan na mutu."
"Don't mind him Honey kinji? You'll go back to school har PHD idan kina so
zakiyi, kinga it'll keep you busy kema idan nayi tafiya."
"Yeah thats true amman kuma idan ka dawo fa? lectures d'ina will be keeping me
away from you."
"Don't worry Princess atleast kowani dare muna tare ko ba haka ba?"
"Yes Sweetheart I love you" tayi hugging nasa. "I love you more and more" ya
fad'a tare da pecking cikin gashinta.
"Ya Al'ameen how can I ever repay you? Ban ta6a neman abu a k'ark'ashinka na rasa
ba, kasan meh? Haushin kaina nake sosai."
"Subhanallah but why?" Kanta ta d'ago tana kallon cikin idanunsa da she can be
lost in them forever.
"Haushi nake ji Ya Al'ameen ban baka pride (budurcina) d'ina ba, duk fad'in
duniyan nan ba wanda ya cancani pride d'ina bayan kai but I failed to understand
that before naje na bawa wanda ko taka inda nake be kamata yayi ba, it hurts me,
I'm sorry." Ta k'are maganan tana neman fara kuka.
"Shh! Princess it doesn't matter either kin bani pride naki or not, what matters
is wanda kika bashin ta dalilin aure ne bawai a waje kika je kika basa ba, am I
right?" Ta gyad'a mai kai. "Good kuma kin gani ko yaya kike ina sonki Zainab, I
love you for the sake of Allah shiyasa ko bayan rabuwan mu dake nakasa aure, ba
macen data ta6a kwanciya min a rai kaman ki, ke ta daban ce Zainab, KE ALHERI CE."
Hawaye kam take yanzu sosai, "I love you so much Ya Al'ameen, but nasan da kaine na
mijin daka fara sani na da son da kake min seya fi haka if only ana siyar da
budurci a kasuwa dana siyo just to make you happy."
"Kibar damuwa da wannan Princess ban fad'a miki bane but the first time we mate
you were totally like a virgin, and that was why na biki a hankali" ya k'are
maganan yana tickling da hancinta.

"Ya Al'ameen thats not true kawai ka fad'a min ne don inji dad'i."
"Zainab I love you bazan ta6a yaudarar kiba, I am not flattering you gaskiya nake
fad'a miki a kullum in zan shige ki ji nake tamkar virgin kike shiyasa bana iya
gajiya dake Zainab."
"Toh mesa Adeel back then yake cemun zumana ya k'are banida wani abinda ya rage
tattare dani am like an empty shell? It hurts me har yau na kasa mancewa da maganan
shin nan."
"Subhanallah!" Yayi saurin toshe mata baki "don't ever say such a thing like that
okay? Adeel k'arya yake miki, he was just trying to make you feel low and a nobody
but thats not true ai bazan miki k'arya ba inda ace kaman yadda yake fad'an kike
actually kema kinsan da tuni nasa an kawo min Murja ko kuwa na sake yin wani auren
but bakida difference da wad'ancan inma akwai kad'an ne. Inaso ki cire wannan
damuwan a ranki, your husband loves you the way you are, I'm proud of you Zainab."
Hawayen jin dad'i ta shiga zubarwa face nata yayi cubbing tare da kissing kan tears
natan. "Cry nomore kinji? I love you the way you are kin fiye min dubban mata
Zainab thats why I chose you instead of Murja da zata kawo min pride nata ma."
"Ya Al'ameen why are you so sweet like this?"
"Because I am married to the world's best woman." Sake lumewa jikinsa tayi sonsa
na shiganta, "I love you fiye da yadda nake son kaina Ya Al'ameen, you're such a
sweetheart."
"Shhh! I love you more."

Shiru ne ya ratsa d'akin chan wayan Zeezee ya shiga ringing kasancewar wayar na
ta kusa da Al'ameen ne ya mik'a hannu ya d'aga mata. "Waye ne?" ta tambaya.
"Best friend" ya karance yadda tayi saving. "Lubieen ki ke kira." Kafad'a ta
buga "ka ajiye ni bazan d'aga ba."
"Princess why?" Ya tambayeta cike da mamaki.
"Bana son in raba attention d'ina when am with you, kabari ko zuwa anjima idan
ka fita Masjid sena kirata."
"Princess me kikeson mutane su soma cewa akaina? That ina saki k'in sada zumunci
se bana nan ne zakina picking calls nasu? Please pick up."
"No My Soldier ni banaso." Ze sake magana wayar ya yanke wanda within seconds
Lubiee ta sake calling back.
"Pick up Princess."
"Ni o'o."
"I'll pick up then."
"No don't-" aiko yak'i jinta ya d'aga tare da manna mata wayan a kunne rai ta
had'e mar a yayinda yake mata murmushi yana shafa gashin kanta dake a hargitse.
"Halo Babe?" Cewar Lubiee.
"Eh Babe ya akayi?"
"Soldier'nmu ya koma ne?"
"Wani magana kuma kike yau?"
"Ai gaskiya ne baki picking up call na nutane se in bayi nan."
"Toh ki cinye kanki Sweetheart na gari yana gefe na ma yanzu."
"Allah k'arya ne."
"Let me prove you wrong" dawo da kallonta tayi kan Al'ameen "Sweetheart kaji wai
k'arya nake sam baka gari inji ta."
"I told you, haka kowa ma zece tunda se in bana nan kike picking calls nasu."
"Kaima haka zakace ba?" Miyar da wayan kunnenta tayi da wuri Lubiee tace, "kinga
ba? Shima Soldier'n namu ya fad'a gaskiya."
"Mschw toh why did you call? Kina shiga min hak'k'in Sweetheart fa."
"Princess easy" cewan Al'ameen "ko nayi excusing naku ne?" yayi maganan a
hankali. Hannunsa dake wajen gashinta ta rik'e "kana nan" sannan back to Lubiee
"ina jinki."
"Please ba sekin min tsiya ba ashobe zan kawo miki."
"Na bikin wa?"
"Na bikin Ya Al'ameen."
"Lol wani Ya Al'ameen d'in kam ba nawa ba."
"Shegiya sena zo."
"Toh bafa wai zakizo ki cikani da surutu bane, saboda Sweetheart na gida kinji
ba?" Dariya kad'an-kad'an Al'ameen yake har ta katse wayan.

"So Princess ni kad'ai ne ke nan kike d'aga min k'afa ko?"


"Eh mana Sweetheart kasan kai na daban ne, I love you so much" tayi maganan
moving closer to him and finally kissing him. Seda suka d'au tsawon lokaci sannan
tayi pulling back, "Princess baki fad'a min response naki ba, zaki koma school
d'in?"
"Kana son in koma?"
"Ni abinda kikeso zamu miki."
"I know I just need your opinion kana so in koma?"
"I'll be happy if you do Princess."
"Consider it done, I'll be going back to school ko dan kai ma zan koma bale nima
ina so."
"Thats My Woman" pecking cheeks nata yayi.
"But Sweetheart ba'a kulle registration na jamb ba?"
"No akwai room for late registrants ai don't worry zan miki processing komai."
"I love you Ya Al'ameen My Very Own Handsome Soldier."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣7⃣

_Here's to last page of dedication, promise fulfilled! How I wish these


dedications will continue to come Sweetheart Aunty Sis, no need for long essay know
that you are always in my heart I l love you._

Suna nan a d'akin Lubiee ta iso ta soma knocking. "Princess is like Lubiee ta
iso." Banza dashi tayi.
"Princess bazaki je ki bud'e mata ba? Kinga se in barku ku biyu ma inje in samu
men d'ina nima."
"Kagani ba ni shiyasa nace bazan d'au wayan Lubiee ba, nasani ka tafi gun men
nakan nan ban sake ganinka se dare."
"Thats not true."
"Ni bana son kaje gunsu, ashobe kawai zan amsa in dawo."
"LOL Princess wai baki gajiya da ni ne?"
"Ni wallahi bana gajiya da kai, please karka fita."
"Naji toh."
"Promise me first."
"I promise Princess."
"Toh kiss me."
"Princess, Lubiee is knocking."
"Kiss me first." Idanunta ta rufe waiting for him to kiss her. kallonta yayi yana
murmushi sannan ya matso da face nasa kusa da nata, lips nata ya yi owning a
hankali dai-dai zata fara kissing nasa back kenan se yayi pulling out da gan-gan
fuskansa d'auke da wani mak'irin murmushi "Sweetheart what was that? "
"You asked of a kiss right?"
"Toh ai wannan ba kiss bane."
"Toh mene Princess?"
"You just teased me."
"Princess, Lubiee is knocking fah."
"Bazan jeba" tayi maganan tare da had'e rai.
"Yi hak'uri mana." Juyawa tayi a zuciye zata bar mai kan gadon inda da sauri ya
rik'o hannunta tare da kwantar da ita kan gadon ya bata the kiss of her life, tun
tana shuresa tazo tayi giving in suka shiga kissing juna with all that they got. A
hankali yayi pulling out, kad'an daga cikin nauyinsa na a akanta, hannunsa a
bayanta yana yi mata wani irin kallo. Se nishi Zeezee ke a yayinda wani irin son
Al'ameen ke dad'uwa a zuciyarta.
"Shifah? Was that a kiss?" Hannunta duka ta zagaye a wuyansa pulling him closer
to her, seda ta had'a musu hanci sannan tace, "yes, I love you Sweetheart." Tana
murmushi sosai.
"I love you too, go get the door kinji?"
"I'll" pecking nasa tayi a nose tip nasa sannan ya d'agata taja rigarta tasa ta
fice inda Al'ameen ke binta da kallo yana murmushi shi kad'ansa. By now har Lubiee
ta soma tunanin komawa gida ta kusa minti ishirin bakin k'ofar sannan finally
Zeezee ta bud'e mata.
"Haba Babe ai seki cemin keda ogan naki kuna busy bawai kizo ki shanya ni ba a
bakin k'ofa."
"LOL yi hak'uri shigo toh."
A parlour suka zauna sannan Zeezee ta kawo mata drink da ruwa. "Ya Babe ashoben
waye ne?" Ciro mata ashoben Lubiee tayi. Ganin red colour ne d'ayan lace d'in yasa
Zeezee exclaiming "wow!
Ya min kyau red is my favorite."
"Yayi kyau?" Lubiee ta tambayeta. "Wallahi sosai Babe" ashobe ne kala uku, d'aya
lace d'aya material lace d'aya kuma atamfa duk bana aibantawa a gun. "Babe bikin
wace wannan please?"
"Ashoben ya miki ne?" Kafin Lubiee ta kai ga amsata suka ga Al'ameen ya fito daga
d'aki yana sanye da vest da sports trousers. Kallonsa Lubiee ta tsaya yi lallai
Zeezee tayi sa'an kyakkyawan na miji, da wuri ta kawar da kanta sannan ta sauk'a
k'asa ta gaishesa.
"Princess kicewa friend nakin bazan amsa gaisuwan ba seta koma kan kujera ta
zauna." Muryansa ya sake sa Lubiee mamaki, shi toh bawan Allan nan meya rasa?
Gaskiya Zeezee is so lucky.
Zeezee na jin dad'i tace, "Babe koma kawai ki zauna dan ba amsawa zeyi ba haka
yake." Dad'i sosai taji yadda ya kirata da Princess gaban Lubiee. Komawan Lubiee
tayi ta zauna se anan Al'ameen ya amsa suka gaisa inda yake tambayanta ya karatu
and all.

"Sweetheart yanzu fitan zakayi after promising me you won't."


"Ba fita zanyi ba Princess I promised ai, ruwa zan d'auko na d'akin ba sanyi."
"Ai da ka kirani in d'auko maka toh."
"Its not bad zan d'auka da kaina kar ki damu." Murmushi ta masa as a response
sannan ya wuce ya d'au ruwan ya koma ciki. Ta6a ta Lubiee tayi "kai Babe! Wannan Ya
Al'ameen nakin yaaaaa had'u like irin totally d'innan dole idan yana gari ki mance
da kowa."
"Hehe" tasa dariyan jin dad'i. "I know shiyasa nake sonsa over."
"Uhm kar Baby na yaji ina yaba mijin wata."
"Shegiya ba, so nace ashoben wata chick d'inne wannan?"
"Wai sunyi kyau ne?"
"Wallahi sosai."
"LOL na biki na ne."
"Allah tsine ma me k'arya toh."
"Ameen wallahi."

"Babe da Allah jokes apart, bikin wa?"


"Wallahi kuwa Babe nawane."
"Ke kallen." Kallon nata Lubiee tayi "da Allah aure zakiyi?"
"Wallahi kuwa, ga ashobe na kawo kiga idan yayi mu fitar."
"Omg!" Mik'ewa tayi tare da hugging Lubiee "omg! Babe I'm soo happy for you
wallahi, you are finally getting married."
"I am" ta fad'a tana jin dad'i.
"So gayamun waye mijin? Soldier'n kika samu?"
"No someone far better than a soldier."
"Omg! Really? Aina yake aiki? Is he handsome?"
"He is, ba fari bane saboda ban cika son fararen maza ba yana da haske, very
good-looking and tall, he is a computer engineer by profession."
"Wow what a nice course erin na Ya Omar, you get his pic?"
"Why not pics ma ba pic ba."
"Show me da Allah."
"Yo ai kin sansa ma already."
"Haba waye ne?"
"LOL my best friend's brother."
"Wow your best frien... ke come again wata best friend nakin tukuna?"
"Best friend d'inan guda nawa ne? Guda d'aya ne and kece bayan ke ba kowa."
"Babe ban gane ba kina nufin yayana zaki aura? Ya Omar precisely?" Tayi maganan
not believing her words herself.
"Yessur Ya Omar naki." Ja baya Zeezee tayi cike da mamaki, "Ya waye?"
"Ya Omar d'inde."
"No k'arya kike wallahi."
"Toh shikenan karki yardan."
"Babe mana please waye mijin?"
"Wallahi Ya Omar ne zan miki rantsuwa akan k'arya ne?"
"Omg! Ban yarda ba!" Ta fad'a sounding thrilled.
"Bari na gaskata miki toh." Kan contact na Omar da tayi saving as Mine ta shiga
kira bada jimawa ba ya d'aga "Baby." Yace da Lubiee.
Zeezee na jin muryan ta gane na Omar ne take ta amshe wayan. "Ya Omar?"
"Zeezee?"
"Ya Omar kaine?"
"Ji iskanci baki san muryana bane?"
"Nasani I just can't believe it wai Lubiee ce matar taka dama?"
"Yup Lubiee ce fiancée'n tawa."
"Omi'god! Ya Omar thunder fire you shine kak'i ka gayamin ranan? Kai ni ban yarda
ba."
"LOL kina iya kiran Mama ai kiji, abeg pass the phone to Baby." Amsa Lubiee tayi
"Mine wai har yanzu tak'i yarda."
"Barta karta yardan."
"Bye se mun sake magana anjima."
"Okay, I love you."
"I love you more" ta fad'a tare da katse wayar. Hugging d'in Lubiee Zeezee tayi
"Babe I am so happy for you, like I can't believe this, dama Ya Omar zaki aura?
Yeyyy! My best friend is now my in-law."
"Thank you Best Friend" tayi maganan tare da breaking hug nasun. "Thank you
Babe."
"Shegiya! Ya kuka fara had'uwa?"
"LOL long story."
"Da Allah gist me."
"Tam, kusan a year ai yanzu, don tun kafin rasuwan Baba, tun kina gidan Mrs
Mukhtar naje gidan ku ranan Ummie ta aikeni kaima Mama sak'o." Se kuma tayi shiru
da gan-gan.
"Ehemm ina jinki."
"LOL nazo fita muka had'u da Ya Omar bayan na gaishe shi ya buk'aci digits d'ina
romantically, kai Babe I love your Brother."
"Lol ban gane ba."
"Shegiya I mean tunda daman ina crushing nasa."
"Omg! Like seriously?" tayi maganan tare da kai mata friendly punch. "Shine baki
ta6a gayamin ba?"
"Yo gani nake like he is out of my league barin ma dana ji rashin mutuncin da Ya
Ibraheem ya ma su Sumayya lokacin da tace tana sonsa sena tsorata nima kar Ya Omar
yamin haka. Nayita crushing nasa abuna."

"LOL Babe you could have told me senayi hooking naku up, Ya Ibraheem da Ya Omar
are two different people, Ya Omar nada sauk'in kai."
"Nima se yanzu na gano hakan Ya Omar is so sweet."
"Is so sweet" tayi imitating nata, "toh Allah baku zaman lafiya, ansa date na
bikin naku?"
"Yup in 2 months time."
"Iyye BFF ta kusa amarcewa su Ya Omar za'a sha k'amshi kenan."
"Banason iskanci fah."
"Heheh toh Allah sa kar bikin naku yazo lokacin da Sweetheart d'ina yake gari."
"If it does fah?"
"Of course bazani ba mana, I can't leave him shi kad'ai da daddare he needs me"
ta k'are maganan tana mata signal.
"Shegiya Allah shiryeki." Hira kad'an suka ta6a Lubiee ta k'ara mai. Dawowan
Zeezee ciki taga har Al'ameen yayi bacci gefensa ta k'arisa ta zauna tana kallonsa.
"Ayyah har ka gaji da jirana bacci ya tafi min da kai" blanket taja ta rufeshi tare
da pecking nasa a forehead. Zata juya kenan yaja hannunta seda ta fad'a kansa.
"Omg! Sweetheart dama ba bacci kake ba?" Idonsa a kulle ya amsa da;
"Na fara shigowanki na tashi."
"Am sorry."
"What for?"
"For waking My Soldier up" tayi maganan tana k'ok'arin d'agowa daga jikinsa wanda
tuni ya sake matse ta restraining her. "Toh ban maka nauyi a haka bane Sweetheart?"
Tayi maganan tare da d'ago kanta tana kallonsa. Kai ya kad'a mata "you weigh
nothing Princess."
"Uhm kasan wani abin mamaki Sweetheart?"
"Tell me."
"Lubiee zata auri Ya Omar!"
"Wow are you serious?"
"You can't believe it either right?"
"Yeah thats great news."
"I know."
"Allah basu zaman lafiya toh."
"Ameen muma ya k'ara mana kuma."
"Ameen Princess" maida kanta tayi ta kwantar da shi bisa k'irjinsa. "I just love
you Ya Al'ameen."
"I love you more and more Princess" a haka sukayi bacci se Maghrib suka tashi.

***
Life proceeded on, Zeezee harta rubuta jamb nata kuma cikin ikon Allah taci ta
fito da 215 points inda tayi applying for Geology kuma cikin ikon Allah ta kusa
samu. On the other side kuwa preparations na bikin Lubiee aketa kai wanda se
Al'ameen yayi dagaske Zeezee ke fita taje ta samu Mama ita tafison idan gari ya
waye har dare yayi suna tare da Al'ameen nata. Exactly a month yayi ma Zeezee
sannan yace ze koma office. Nan fa Zeezee ta shiga had'a mai rai se gani take as if
wai jiya-jiya ya dawo. Ana gobe ze koma tak'i mai magana se had'e rai take, ba
yadda Al'ameen beyi da ita ba amman tak'i mai magana, ko daya gwada kissing nata
nanma shutting kiss nasan tayi ta shiga had'a mishi akwatinshi. Duk anan yana kan
gado yana zaune yana bin every move nata da kallo. Tana gamawa ta juyo ta kallesa
kafin idansu ya had'e tayi sauri ta kawar da kanta, "muje kaci abinci."

"Bazan ci ba."
"Kafa san da tafiya a gabanka gobe muje kaci ka samu kayi wanka." Tayi stating
ba tare da ta kallesa ba. A nitse ya mik'e ya tako har gabanta wanda da sauri ta
kawar masa da kanta. Hannayenta ya d'aga ya had'a da nasa yana murzawa in a
soothing manner. "Princess yanzu ke kenan kowani tafiya na se kinyi min haka?
Kinsan yadda yake damuna kuwa? Ace yau tunda garin Allah ya waye har izuwa yanzu
banga murmushin kiba, ina kikeson insa kaina Princess? Hutun three weeks fa na samu
amman don bana son na barki all by yourself na k'ara one week akai still baki gani
ba kike punishing d'ina haka? I'm sorry kinji? If only I change my job schedule da
nayi kokuma da zasu barni in tafi dake da mun tafi tare, its really not my
intention to leave you Princess, I'm sorry." Tausayi kuma sosai ya bata jin yadda
yake magana tamkar zeyi kuka hannunta ta k'wace daga nasa tare da zagayesu a
wuyansa. A hankali ta shiga kissing nasa slowly yet affectionately. Sun d'au tsawon
lokaci ahaka sannan a hankali tayi pulling out tare da manna goshinta akan ha6arsa.
"I'm sorry also Sweetheart ni ya kamata in baka hak'uri for acting so childish,
but nima ba a son raina nake ma hakan ba, is just that am used to you, ko minti
d'aya nayi ba a kusa da kai ba se inji wani iri bale in shafe weeks ban saka a ido
ba you know how that is infectious to me right?"
"I bave a suprise in store for you but semun kwanta."
"Aww really? I can't wait, you are My One Last Standing Soldier." Pecking
forehead nata yayi "I love you Princess."
"I love you more and more and more muje kaci abinci ba se kayi wanka?" Kafad'a ya
buga mata wane d'an yaro "why? Bazaka ci abinci ba?"
"No wankan nakeso muyi tare."
"My Soldier d'azun fa nayi nawa da Maghrib d'innan."
"I don't care ni inason muyi tare gobe fa zan tafi Princess."
"Consider it done My Soldier, duk abinda kakeso shi zanyi maka muje kaci
abincin?"
"Thank you Honey." Hannunsa ta rik'e har ta kaisa kan table taja mishi kujera ya
zauna, suna cin abinci suna hiran soyayya abinsu har suka gama sannan suka shiga
bayi dan yin wanka. Achan ma suka yita wasan ruwansu, da k'yar suka yi wankan
sannan suka fito. 10pm ya musu akan gado kamar yadda yayi promsing nata haka ya
gamsar da ita tonight. After all the fun and love making at last sukayi falling
into a wonderful and beautiful sleep.

Washegari kuma ta tashi ta shirya Al'ameen, sede sam Zeezee ta kasa sabawa da
tafiyan Al'ameen. Duk lokacin da yazo tafiya se tayi kuka sosai as if its his first
time. A washegarin da Al'ameen ya tafi itama ta koma gida gun Mama saboda
preparations na bikin Lubiee. Kowani yamma kuma abinta zata je islamiyya. Haka
Rayuwa ta cigaba da gudana har inda Allah ya kawo ranan bikin Omar da Lubieensa.
Buduri aka sha sosai, gashi har anan Al'ameen be dawo ba, ba event da Zeezee tayi
missing out, ita da Lubiee sekace amare biyu, an sha budiri anyi wankan naira
sannan a k'arshe aka tofe komi da fatiha. A garin Bauchi unguwan Old GRA aka kai
Lubiee inda suka sha kuka kaman ba gobe. Washegarin rananda aka kai Lubiee Zeezee
ta kirawota a waya tayita mata tsiya tana tambayarta ya jiki-jiki, tayi kuka ne?
Lubiee da ita kad'ai tasan kalan rad'ad'in da takeji ko biyewa Zeezee batayi ba.

****
A week da Zeezee zata fara fita lectures ne Al'ameen ya dawo. Sa6anin ko wani
dawowansa wannan karan ya sanar da Zeezee inda ta shirya masa kan table dam da
abinci kala-kala se wanda ya za6a. As always sukayi hoge-hogensu da kisses sannan
takaisa dining yaci abinci sukayi wanka tare, later during that night ya fiffito
mata da tsarabunta. Ita de bataga tafiyan da Al'ameen zeyi be kawo mata tsaraba ba,
like duk abinda ya gani seya siya mata. First day da Zeezee zasu soma attending
lectures ma Al'ameen ne yayi dropping nata da kansa tare da wishing nata success,
hijabin ta three quarter tasa ta fita gwanin sha'awah. Se 3 ya turo driver ya
d'auketa. Sosai ta galabaita ranan gashi tuna fa yanzu tana isa gida dole seta aza
girki ta sakejin wani gajiyan batak'i tana isa gida ta kwanta ba.

Da sallamarta ta shigo ciki inda ta fara jin k'amshin girki na buga mata hanci.
Bata wani shiga duhu ba taga Al'ameen na fitowa da plates a hannunsa from kitchen
ya ajiye akan dining table.
"Sweetheart!" Ta kira sa sounding delighted, ganinsa kad'ai yasa ta nemi gajiyar
tata ta rasa.
"Oyoyo Princess is back." Yayi maganan tare da bud'e mata hannunsa ready for a
hug. Jakarta ta ajiye kan kujera ta k'arasa tayi hugging nasa. "How was your first
day at school?"
"Alhamdulillah but hectic gashi kuma I missed you."
"Am here Honey muci abinci muje ki huta ko?"
"Yes Sweetheart bade girki kayi ba?"
"Yup I thought I might suprise you."
"Omg Sweetheart you're so sweet, me ka iya ka dafa mana?"
"Miyan ganye irin na ranan, ban iya tuk'a tuo ba nasa Saje ya siyo mana a
restor."
"Awwn! My Man is damn sweet. Like am starving." Kujera yaja ya zauna sannan ya
zaunar da ita akan cinyansa ya musu serving abincin kan plate d'aya sannan da kansa
ya shiga bata. "Hummm yummy! Sweetheart sure kai ka girka wannan miyan kuwa?"
"Me kika ga?"
"Yayi dad'i ne like over, anya kuwa ba siya kayi ba?"
"Don't be suprised ranan a gaba na kika girka ai, I understood komi."
"What a fast learner, Am damn proud of you Ya Al'ameen, I love you."
"I love you too yi kici muje ki watsa ruwa semu huta." Cike da so da k'auna, yaci
ya bata har suka cinye abincin sannan ta tattara kan dining d'in suka zo sukayi
wanka se kuma bacci.
Haka nan tun daga ranan idan Zeezee ta fita school kafin ta dawo atimes Al'ameen
ya musu girki ko kuwa ranan da be samu yi ba seya aika a siyo musu. A weekends da
kuma Fridays da take da lecture free days ita keyin komi, subi su yini a d'aki suna
shan zallan soyayya. Sati uku Al'ameen yama Zeezee ya koma, sede har yanzu Zeezee
ta kasa sabawa da tafiyansa. Kukan ta tasha sosai seda bacci ya d'auketa har ma
bata samu zuwa lectures ba a ranan. Tun komawan Al'ameen kuwa ta fi miyar da
hankalinta kan karatu kasancewar batada wani abinda zeyi distracting nata yanzu,
tests nata gabad'aya tana k'ok'arin passing. Karatu take sosai kodan to make
Al'ameen proud, anytime she is less busy kuwa kiran Al'ameen nata take either audio
or voice call susha hira sosai, shima haka. Idan ko ya dawo hutu kullum da daddare
suna tare kasancewar da rana tana school.

***
Ana cikin haka ne Allah ya azurta Lubieen Ya Omar da juna biyu. Dad'i kashe
wannan happy couple, Lubiee can't wait to have her own baby. Bayan Omar, Zeezee was
the second person to come to know about wannan k'aruwa da suka samu. Sosai tayi ma
BFF nata murna amman kuma samun k'aruwan Lubiee ba k'aramin digging wa Zeezee past
nata na rashin haihuwa yayi ba. Gashi nan Lubiee da akayi bikinta just 3 months ago
har ta samu juna biyu, ita kam gata nan tana neman shekara gidan Al'ameen amman ko
6ari bata ta6a yi ba. She knows koda Al'ameen bayi nuna mata dole deep inside
rashin haihuwar nata zena damunsa barin ma idan ta tuna yadda yake son yara, ba shi
kad'ai bama tasan harda su Mama Babba duk by now zasu fara jin haushinta shiyasa ta
dage da kiransu kwana biyi sosai suna gaisawa kar abin yayi yawa.
She don't think she can hide it anymore, its high time Al'ameen yasan gaskia,
she can't continue fooling him forever dole wataran gaskiya ze bayyana gomma tun
wuri ta sanar dashi. Tana zaune kan gado da books a baje a gabanta tana karatu take
wannan tunani, finally ta mik'a hannu ta kirasa. Bayan sun gaisa take tambayarsa
yaushe shigowansa.

"Princesse I won't lie to you amman shigowa na yana iya kai nan da next week,
ina fatan zaki fahimceni kin fi kowa sanin how bad am missing you right?"
"I know Sweetheart and I totallay understand just know that am missing you okay?
take your time kaji? Duk lokacinda ka samu hutu seka zo min, I love you." Be ta6a
tsammanin jin wannan calming words daga Zeezee ba, finally ta fara gane mishi kan
abin.
"Dagaske Princess? You are not mad?"
"Why should I be? Nasan inda kanada dama a yanzu ma zaka dawo min koba haka ba?"
"Sosai ma kuwa to kiss those sweet lips of yours that I can't get enough of
them."
"I know Sweetheart kaga ma this week ina kan period d'ina ko kazo it wont be fun
I pray ka samu ka shigo zuwa next week d'in."
"In shaa Allah Princess I'll try my absolute best naga na dawo next week."
"Your Princess is waiting for you, yauwa Ya Al'ameen idan ka dawo ina son muyi
wata muhimmiyar magana kaji? Kuma banason ka d'auka wai don bana sonka ne ko don
ban damu da kai bane nak'i fad'a ma gaskiyan zancen ina son kasa a ranka saboda ina
tsoron zaka tsane ni ne ka cireni daga rayuwarka yasa nayi hakan."
*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣8⃣

_Where are you Lubna Sherrif? Here is your page._

"Subhanallah Princess don't ever talk like that okay? Kisani ni duk abinda
kika yimin a duniyan nan I will never hate you, sonki a jini na yake it will never
die." Hawaye ta shiga zubarwa a hankali, "Princess are you crying? Oh God! toh ni
na yafe abinda zaki fad'min d'in banason ji tunda yana saki kuka." Se kuka kawai
take tama kasa magana, lalashinta ya shiga yi na sosai da k'yar ya samu tayi shiru.
"Ya isa kinji? I don't wanna hear you crying again."
"Na dena Sweetheart."
"That's My Princess, ya karatu kince min kinada test gobe."
"Eh ina kai."
"Toh Allah bada sa'a okay? I love you let me leave you to your books."
"I love you more, goodnight."
"Chocolate dreams" ya fad'a tare da katse wayar. Karatun ta samu ta k'arisa da
k'yar saboda gabad'aya hankalinta baya jikinta. Tun daga ranan da sukayi wannan
magana Zeezee ta shiga damuwa a kullum tunanin yazata 6ullo wa Al'ameen da wannan
lamari take, ana cikin haka ne watan dawowan Al'ameen ya kama. Girki iri-iri tayi
mai ranan sannan ta d'au wanka finally cikin wasu k'ananun kayan da suka mugun
tafiya da body figure'nta. Da Azahar Al'ameen ya iso tama kasa jiransa ya shigo
ciki tun a waje ta tarosa sannnan suka k'ariso ciki. After the kisses and hugs
takai shi bayi ya watsa ruwa sannan suka je suka soma cin abinci. Sede wani hanzari
ba gudu ba, se Al'ameen gani yake as if Zeezee tad'an rame, to meye dalili
makarantar ne? Kai a'a inda shine ai da tun ta farko zata ramen ba se yanzu da
jikinta ya saba ba.

"Princess?"
"Na'am Sweetheart."
"Princess whats wrong?"
"Aina My Soldier?"
"With you, meya faru? Kin rame kuma ni ba haka na tafi na barki ba."
"Dagaske?" Tayi maganan sounding sad "maybe gajiyan school ne." Ta mai k'arya.
"No thats not true."
"Dagaske Ya Al'ameen kokuma dan am missing you."
"It still not true." Mik'ewa yayi a hankali ya nufi gabanta tare da tsayar da ita
itama, kallon k'asa ta shiga yi wanda yasa yatsan sa d'aya ya d'ago face natan.
"What is it? Why are you looking so sad? Bakiso in dawo bane?"
"Ya Salam! Sweetheart taya zaka ce haka? Kai kanka kasan thats not true."
"Toh mene? Meya zubar min dake haka?"
"Babu" tayi mai k'arya.
"So bazaki fad'a wa mijinki problems naki bako Princess?"
"Ba haka bane My Soldier." Tayi maganan wane zatayi kuka.
"Then yaya ne?" Hannunsa d'aya ta d'aga tasa a cikin nata tana wasa dashi.
"Ya Al'ameen am afraid I might lose you, bazan iya juran rashinka ba wallahi, I
love you fiye da duk wani imagination bazan iya rayuwa ba kai ba." By now kam
idanunta sun cike dam da hawaye.
"And who says I am going to leave your side? Inba mutuwa ba Zainab kisani I'll
never leave your side INA TARE DA KE now, always and forever."
"I know My Soldier" tayi maganan tana d'ago both hands nasa da suke cikin nata
zuwa chest level nata. "You are too kind and sweet, Ya Al'ameen you are to good for
me, you deserve someone better than-" da sauri ya katse ta ransa har 6aci yayi a
fusace yace, "bana son sake jin wannan maganar." Cikin wani muryan da bata ta6a
saninsa dashi ba, ba shakka ransa ya 6aci beso jin abinda ta fad'an ba.
"I'm sorry Ya Al'ameen don't be mad please bazan sake ba." Tayi apologising
hankalinta a tashe ganin yadda ran Al'ameen ya 6aci. Shikuwa ganin hankalinta ya
tashi yayi calming kansa, beso ba taga 6acin ransa haka, shi kansa be san lokacinda
ya fusata ba.
"I am not mad kawai karki sake am sorry kinji?"
"It is I who should be sorry, I promise bazan sake ba."
"So tell me meya ramar dake haka? Don't lie to me ba halin ki bane."
"Ya Al'ameen Lubiee is pregnant."
"Wow! Am so happy for her, Allah ya sauk'e ta lafiya." Yayi maganan sounding
delighted.
"Ameen" ta amsa tana kallonsa na sosai, har seda ya tambayeta dalili. "Princess
are you okay?"
"Me kaga?"
"Why are you starring at me like that?"
"Ya Al'ameen gayamin whats going on on your mind?"
"Kaman ya Princess?"
"You also want your wife to get pregnant ta haifo maka baby right?"
"Waze k'i karuwa Princess? Muma Allah kawo mana namu am not in a rush." Tasan
kawai fad'a yayi but thats not true, Kasa amsa shi tayi saboda yadda kuka yaci
k'arfinta. Da sauri ya zaro hannunsa daga nata tare da cupping face nata "Princess
why are you crying? Did I say something wrong?" Kukan nata ne ya tsananta dole ya
rungumeta yana bubbuga bayanta, ya rasa meyace ya sata kuka haka? What exactly is
wrong with his princess? Duk laifinsa ne only if yana tare da ita a kullum daya san
meke damunta.

"Princess I'm sorry please in wani abin na fad'a ya 6ata miki rai am sorry I take
it back." Yayi stating kaman zeyi kuka. Da k'yar ta iya tsagaita kukan nata tare da
d'ago kanta daga rungumar da yayi mata.
"Ya Al'ameen please stop apologizing baka min komi ba, nice ya kamata na baka
hak'uri please kabar bani hak'uri haka."
"Princess then why are you crying like this? I can't take it please karki sake,
my heart can't take it."
"I'm sorry Ya Al'ameen please forgive me for hiding the truth away from you, kayi
hak'uri don Allah."
"What truth are you talking about exactly Zainab?" Kai ta shiga kad'awa.
"Ya Al'ameen please karka tsane ni saboda wannan sirrrin nawa dana 6oye maka ina
tsoron zaka kuje ni ne idan har ka gano gaskiya."
"Zainab that is something I'll never do, bazan ta6a gujan kiba." Gabad'aya ta
sasa a duhu ya kasa gane ina ta dosa.
"Ya Al'ameen I can't provide you a family, bazan iya haihuwa ba saboda mahaifata
tana da matsala, I can't even conceive shiyasa kaga har ina neman shekara a gidan
nan amman ko 6ari ban ta6a yi ba. I'm sorry I can't give you what you wan-"
hannunta yaja seda ta fad'a jikinsa katseta daga k'arisa maganan data fara. Hugging
nata yayi gagam a yayinda yake jin wani irin tausayinta na running fiye da jini a
veins nasa. Zeezee don't deserve to suffer like this.
Kuka take sosai amman sam be hanata yiba be kuma bata hak'uri ba, hugging natan
kawai yayi. Yasan how it's hurts mace tasan cewa bazata ta6a iya haihuwa ba, he
knows exactly what Zeezee must be feeling right now. A hankali kukan nata ya d'auke
se anan ta d'ago daga jikinsa "Ya Al-" da sauri ya aza hannunsa akan lips nata
shutting her up. "Shhh! Not a word Princess." Hannunta yaja a hankali izuwa kan two
seater inda suka zauna.
"Princess waya ce miki bazaki iya conceiving ba? Saboda kinga har yanzu baki
haihu ba shine sekice bazaki iya haihuwa ba? Bakiji tarihin Annabi Zakariyya AS da
se a old age nasa Allah ya basa haihu ba, bale keda you are just 18 please don't
ever say bazaki ta6a iya haihuwa ba again. Zaki haihu someday in shaa Allah, I know
you will." Hawaye ta shiga yi sosai tana kad'a kanta.

"I won't ever Ya Al'ameen kaikam kana iya ganin jininka saboda at any moment
idan kanaso zaka kawo lafiyayyar mace ta haifo maka golden kids but ni? I can't
ever."
"Wai bazaki bar magana haka ba Zainab? So kike mu 6ata ko? Nace stop saying these
gibberish saboda kinga Lubiee da akayi aurenta a bayanki ta rigaki samun ciki
shikenan seki hau cewa ke bazaki haihu ba? Koma baki haihun ba me aciki? Nana Aysha
R.A ta ta6a haihuwa ne? Da haihuwa wani abu ne da Allah se yafi bawa Nana Aysha
haihuwa akan kowa but he didn't saboda da wadda ya haihu da wanda be haihu ba duk
d'aya suke agun Allah Zainab, wani Allah na hanashi haihuwan ne saboda yaga idan ya
basa d'an ze wahalar dashi, ki sani don Allah be baka haihuwa ba doesn't mean he
doesn't love you, atimes yana hakan ne saboda yana sonka Zainab. And you can't even
conclude that bakiya haihuwa, this is just your first year of marriage, lets have
faith and pray for zuri'ah d'ayyiba okay?" Ya k'are maganan yana mata murmushi sede
ta kasa smiling back masa, how can he be so sweet kawai take fad'a a ranta.
Hannunsa ta d'aga a hankali ta had'a da nata "Ya Al'ameen I do believe in all that
you've said amman ba wai haka ne kad'ai na yanke hukuncin bana haihuwa ba, I have a
strong reason."
"What are you saying Zainab?"
"Ya Al'ameen ban ta6a fad'a maka bane but for six months Adeel yata d'ura min
wani maganin hana d'aukan ciki ban sani ba." Salati kawai Al'ameen ya sakar a
zuciyansa, wani irin mugun mutum ne Adeel da zeyi torturing precious halitta irin
Zeezee haka? Kuka kawai tasa na sosai wanda tuni yayi hugging nata yana shafa kan
gashinta soothingly. "Alokacin dana zo na gane maganin hana d'aukan ciki yake ban
it was too late na riga na rasa mahaifata saboda side effects nasa."
"Shhh! Cry nomore Zainab, I love you for who you are I don't care ko kina
haihuwa ko bakiya yi, ni ke nakeso and nothing else."
"Ya Al'ameen am sorry nasan yadda kakeson yara but I can't provide you your
happiness which is a family, kayi hak'uri don Allah."
"Zainab stop apologizing, in akwai wanda ze bada hak'uri anan Adeel ne and no
one, kibar kukan haka ai dama ba yarjejeniya mukayi dake ba kafin na dawo dake akan
zaki haifo min yara ba so I have no right to be mad or furious at you."
"It'll be more happier idan muna da yaranmu muma, Ya Al'ameen in kai ka yarda
zaka cigaba da zama dani haka what of Mama Babba? Don't you think tana da urge na
ganin jikanta daga gareka?"
"Princess Mama is not like that, she'll totally understand everything."
"Are you sure Ya Al'ameen? Bana son in tauye maka chance naka na meeting da
jininka, yaranka tamkar yarana suke kar kaji nauyi don zaka auro wata da zata iya
baka wannan arziki I am totally okay with it."
"Zainab idan kika sake magana haka zamu 6ata dake am serious, I'll pack my
stuffs and go back to Abuja na gaya miki ke kad'ai ce, kuma a hakan nake sonki bale
ma ban yarda wai mahaifar ki ta 6aci ba gabad'aya. Which Dr told you so?" Kai ta
kad'a mai nufin a'a.
"You mean to say ba Dr'n daya tabbatar miki da cewa your womb is damaged?" Yayi
tambayan cike da mamaki.
"Babu but yabani labarin wacce tayi using drug d'in for just 2 months and seda
aka cire mata mahaifar tata saboda yadda ta lalace."
"Princess that isn't enough reason kema kice naki ya lalace."
"It is Ya Al'ameen gashi kana gani har yanzu na kasa conceiving, ko 6ari ban ta6a
yi ba."
"No I don't believe in that zamuje asibiti a duba ki only then zan yarda."
"No please."
"Yes Princess."
"No" ta fad'a tare da shigewa jikinsa tana rusa kuka sosai "please don't inhar
kana sona kaman yadda kake fad'a you won't force me zuwa ganin wani Dr again, na
yarda da k'addara na kuma na kar6esa hannu bibbiyu amman bazan je wajen Dr ba ya
sake tayar min da hankali please don't force me Ya Al'ameen." A hankali ya shiga
hugging nata back, "its okay Princess ni duk abinda kikeso shi zan miki, bakiya son
zuwa ganin Dr so be it but I assure you mahaifarki bata lalace ba, you are still
very young. I believe some day zaki kawo min little Soldier or Princess d'ina into
this world okay?"
"I really do pray so also, ba abinda nakeso kaman inga nayi blessing naka da
yara, tun akan Ramlah na gano kai kids lover ne."

"And you will Zainab, its just a matter of time, cry nomore."
"I love you Ya Al'ameen, I love you so much na d'au bayan kaji wannan sirrin nawa
zaka tsane ni ka koreni gida a yinin yau."
"Subhanallah sekace wanda be san addini ba zanyi haka? Kina nan a gidan nan
Zainab mutu kan raba." Dad'i sosai taji inda ta lume jikinsa tana shak'an daddad'an
turaren jikinsa.
"Tashi muje I need My Woman."
"I need My Man also" cike da so da k'auna ya d'agata in a bride like style ya
direta kan gado achan na basu privacy nikuma.

Tun daga ranan da Zeezee ta sauk'e wannan maganan da take gani tamkar hak'k'i a
gareta tad'anji iska. Yawancin kullum zata tashi cikin dare tayi ta nafilfilu tana
miqa wa Allah kukanta. Rayuwa ta cigaba da kasancewa da dad'i wa Zeezee se gani ma
take like seda Al'ameen ya gano wannan matsalar dake damunta ya fara nuna mata wani
sabon son simply because he wants her to know shi ba don haihuwarta yake sonta ba.
Prolonging zamansa yayi har na sati biyu Zeezee couldn't ask for more, kullum suna
tare da Al'ameen nata, lectures ma ji take as if tabar zuwa saboda yadda bata son
barin Al'ameen nata shi kad'ai a gida.
As always wannan tafiyansan ma seda tasha kuka abinta. Bayan tafiyan nasa kuwa
ta cigaba da maida hankalinta ga karatu, ana cikin haka ne Lubiee ta haihu inda ta
samu 'yarta suka yi wa Mama takwara, ita de Mama takwaran nata har sun mata yawa
gana Mariam, gana Ibraheem sannan kuma na Omar. Ranan suna sun sha budiri sosai,
'yar sak Lubiee ba abinda ya rabasu.

Life moved on, a kullum dad'a son juna Al'ameen da Zeezee suke wane jiya-jiya
akayi musu aure. Lokaci ba wuya Zeezee harta ci rabin karatunta or so, da auranta
da Al'ameen shekara biyu kenan. Yanzu haka suna rubuta exams na 2nd semester'nsu
for their second year, Lubiee kuwa this year tayi graduating, 'yarta Afrah dake nan
sak ita ta girma sosai.

Ta fannin Adeel da Ruky Mama kuwa har yau gasu nan ne kawai, sam sekace ba mata
da miji ba idan an gansu gu d'aya to hak'k'in d'ayansu ya had'a su, if not kowa
kaman zaman kansa yake, hakan ba k'aramin damun Ruky Mama yake ba, tana son Adeel
nata sosai amman abubuwan da tayita masa yasa ta fita daga kansa gabaki d'aya.
Gashi har yanzu ta kasa ajiye d'a a gidan, da ta d'au ciki bayi kai 3 months yake
zubewa, sau d'aya kuma ta sake haihuwa ta mace bayan kwana uku ta koma itama. Kukan
da Ruky tasha yasa har asibiti sanda aka rik'e ta, sosai ta bawa Adeel tausayi
kawai bai nuna mata ne saboda gani yake abin ma yafi damunsa akan ta. Tunani Ruky
ta soma yanzu, anya ko ba alhak'in Zeezee ke binta ba? In haka ne ya zama dole taje
ta nemeta ta kuma nemi tubarta.

*****
Karatu Zeezee take sosai, sanin sunkusa fara exams Al'ameen yak'i dawowa gida
koda ya samu hutu sabida bayason yayi distracting nata he knows right Zeezee bata
iya karatu idan yana kusa da ita. Labarin ciki de har yanzu shiru, Zeezee de ba
k'aramin damunta hakan keba but idan taga yadda Al'ameen is care free yake kuma
nuna mata so se itama taji damuwan nata ya gushe. Ko da wasa kuwa Mama Babba bata
ta6a kawowa Al'ameen zancen haihuwa saboda tasan shi hakan daga Allah ne.
Cikin sa'a su Zeezee suka k'are exams nasu. A daren ranan Al'ameen ya kirata
bayan sun gaisa yake tambayarta ya last paper.
"Alhamdulillah My Soldier wato kaje ka mak'ale a Abj kak'i dawowa ko? Ka mance da
Princess taka."
"Ina ni! I might forget myself but you? Bazan ta6a mancewa dake ba Princess
banso dawowa bane saboda time d'in kuna exams Princess, banason na zame miki
distraction yanzu haka flight dina nake jira yau zan dawo." Ihu ta k'urma cikin
wayan "yeyyy!!! Are you serious Sweetheart?Yau zaka dawo?"
"I miss you like hell."
"Awww I mis you more me kakeso in dafa maka?"
"Anything yummy."
"Toh wallahi sauran kuma kace min kaci abinci a jirgi a k'oshe kake."
"LOL kar ki damu yau kam da empty stomach zan taho."
"That's My Man so seka shigon ko? Kasan wani abu?"
"No tell me."
"Mafarkin events na second anniversary'nmu nayi yau wai mun sake zuwa Washington
amman wannan karan da kids namu wai mace da miji, na mijin ne babba, they both look
exactly like you, it was so adorable."
"In shaa Allahu we will one day Princess zamu sake komawa Washington da kids namu
kamar yadda kikayi mafarkin its just a matter of time."
"Allah yasa Sweetheart."
"Ameen so sena shigon ko?"
"Safe flight your Princess loves you so much."
"I love her way over." Yana katsewa Zeezee ta rage kayan jikinta ta shiga
kitchen ta hau had'a ingredients na fried rice.
A lokacin da ta gama kwalyanta se k'amshi ke tashi a jikinta tana zaune a
parlour tajiyo k'aran bud'e gate. Kamar yadda ta saba kowani dawowansan yau ma ta
kasa jiransa ya shigo, tun a waje taje ta tar6esa. Se kallon Zeezee kawai Al'ameen
yake yadda ta k'ara wani haske, cika da kuma kyau. Bayan ya watsa ruwa suka fito ta
shiga feeding nasa da kanta. Suna cikin hakan ne ta lura da irin kallon da Al'ameen
ke mata ita ta d'au ma ko wani abu ne ya faru, "Sweetheart?" Ta kira sa a hankali.
"Yes Princess" yayi maganan tare kawar da idanunsa daga gareta.
"Sweetheart is there a problem?" Maido da idanun nasa ya sakeyi a kanta. "Me kika
ga?"
"You've been starring at me since, is something wrong with my makeup?"
"God No Princess, your makeup is perfect."
"Toh mene kake ta kallo na tun d'azu?"
"Tun shekaran jiya da mukayi video call naga kin k'ara haske se na d'au ko kawai
camera ne but its not dagaske ne kin k'ara hasken, your skin is glowing Princess
bakiga yadda kikayi kyau ba and har k'iba ma kin k'ara."
"Oh come on Ya Al'ameen don't tease me please exams fa na gama."
"Seriously Princess" yayi maganan tare da miqa mata hannunsa, tana grabbing ya
jata ya zaunar da ita a cinyansa. "Me sirrin ne Princess?" Hannayenta ta zagaye a
wuyansa. "Sirrin?" Ta tambayesa, nan take yayi nodding. "Saboda Sweetheart d'ina na
bani all that I need and ask for. Kula danin da kakeyi yasa na k'ara haske harma da
weight bakaji Mama na teasing d'ina ba ranan wai na kaita k'iba yanzu."
"Oh thats not true My Princess is slim and elegant." Lips nata ya lalumo a
hankali ya shiga kissing nata inda take miyar mishi da martani itama daga chan suka
wuce d'aki ganin nan d'in baze iya containing nasu ba.

Later during the day wuraren k'arfe 5:35pm Zeezee na mik'e akan gado tayi lamo
wane wacce batada lafiya. Fitowan Al'ameen daga bayi kenan yana sanye da towel ya
tsaya kallonta. "Ka fito?" Kad'ai ta iya tambayarsa a kasalance.
"Yes Princess are you okay?" Nan ma kai ta gyad'a mishi. "Sorry naso fito maka
da kayan da zakasa amman banjin zan iya." Da wuri-wuri yayi grabbing shirt da
trousers yasa ya k'araso kan gadon ta gefenta ya zauna. "Princess you are not okay"
ya fad'a yana scrutinizing face nata, da sauri ta kawar da kanta "na fad'a maka I'm
fine."
"No you are not you are looking pale and weak Princess."
"Karka damu zuwa anjima zan dawo normal."
"How sure are you?"
"Saboda kusan kwana hud'u kenan hakan kemin, da zaran yamma ko safiya yayi senaji
banida lafiya cikin some hours kuma sena ji am back to normal karka damu."
"Yanzu Princess har na tsawon 4 days kike fama da hakan baki fad'a min ba? I'm
very angry."
"Please don't" tayi maganan tare da rik'e hannunsa "ban gaya maka bane saboda
banason ka shiga damuwa, its nothing to worry about." Hannunsa ya cire daga rik'on
da tayi mar tare da shafa side na fuskarta "bakida lafiya kuma kice its nothing to
worry about? Ya kika samu kika k'arisa exams nakin ma toh?"
"Cikin dare nake tashi inyi karatu ko da rana please kabar damuwa."
"I can't Princess we need to see a Dr."
"What for?"
"Ya dubamin ke saboda bakida lafiya."
"Kasan me nakeso Sweetheart?" Kai yayi saurin kad'awa "just hold me, I want to
sleep in your arms." Pecking forehead nata yayi sannan ta matsa mishi kad'an ya
kwanta wajen tare da kwantar da ita a jikinsa. Ba k'aramin zafi ba jikin Zeezee
yayi wanda har yabawa Al'ameen tsoro sosai, toh wani irin rashin lafiya ne wannan?
Just earlier she was perfectly okay yanzu kuma batada lafiya? Ji yake ina ma ace ze
iya kar6a mata rashin lafiyan shi yayi suffering instead.

"Princess jikinki yayi zafi in d'auko towel in matse miki to cool it down?"
"No just hold me please."
"Shhh! Get well soon okay? I'm here for you, I love you."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
6⃣9⃣

Kai zallah ta iya ta gyad'a mar saboda yadda takeji ajikinta. Sake
rungumeta yayi gagam dukda yadda baya jin dad'in hot temperature'n tan amman don da
tace he should hold her. A hankali bacci yayi gaba da Zeezee, Al'ameen kuwa har
yanzu hankalinsa ya kasa kwanciya. Tun aurensu da yayi shekara biyu yanzu be ta6a
Ganin Zeezee a irin wannan situation ba, duk rashin lafiyanta baifin ciwon kai kona
ciki wato menstral cramp, he is so worried ganinta a irin wannan condition. A
hankali da k'yar wahalallen bacci ya d'aukesa shima se Maghrib ya tashi ya kwantar
da Zeezee a gefe sannan ya fice bayi yayi alwala ya fito. A hankali ya sake gwada
temperature'nta inda yaji ya sauk'a sosai, dad'i sosai hakan ya sanya sa. A hankali
ya shiga tada ita har seda ta bud'e idanunta tayi setting nasu akan handsome face
nasa.
"Princess how are you feeling?" Kai ta gyad'a mishi as an answer.
"Kin d'an ji sauk'i ko muje asibiti?"
"I am feeling normal Sweetheart kawai wanka zanyi in warware."
"Are you sure?"
"Yes ai na gaya maka, fever'n come and go ne."
"Alhamdulillah toh tashi na had'a miki ruwan wanka kiyi se muyi sallah."
"Zamuyi a gida?" Ta tambaya murmushin face nata na dad'a bunk'asa a rayuwa
tanason Al'ameen yana janta sallah.
"Yes Princess."
"Yeyy! Thank you." Da kansa ya d'agata chak a sama har bayin ya direta, da
wankan ma cewa yayi ze mata amman tak'i don haka ya bata privacy. Tana fitowa tasa
kayan daya cire mata suka idar da Sallan.

Wajajen 8:30pm Al'ameen ya fito daga d'aki ya samu Zeezee dake kwance a parlour
bisa kan kujera. "Princess bazaki ci komi ba ke zaki kwanta?"
"Bana sha'awan cin komai Sweetheart don't worry, come over." Ba gardama yaje ya
zauna gefenta inda ta kwanta a jikinsa before 9pm har bacci ya saceta. Yana gama
kallon sports nasa ya d'auketa ya kaita d'aki sede mamakin lamarin Zeezee yake.
Bata ta6a kwanciya bata ci abinci ba se yau, bayan nan kuma a kullum duk rananda ya
dawo daga tafiya Zeezee bata barinsa as suna satisfying needs na junansu amman yau
ko ta kansa bata yi ba. Da wannan tunani a ransa ya kwanta gefenta tare da janta
jikinsa yayi bacci.
Washegari ma haka suka sake tashi Zeezee ba lafiya ta yarda suje asibiti kuma
tak'i ganin ya dage se sunje tashiga yi mai kuka dan dolensa ya yarda sukayi zaman
gidan kamar yadda takeso. Breakfast ma shi ya musu yau, taci ma ta kasa da k'yar ya
samu tad'an ta6a ta sake komawa bacci. Ciwo kaman me aljanu, sha biyu na wucewa
kuma ta dawo old self nata ta girka musu lunch se anan take neman hak'k'inta gun
Al'ameen, yamma na sakeyi kuwa ta sake falling sick. Har tsoro rashin lafiyan nata
ya soma bawa Al'ameen sekace me jinnu. Sunyi hakan na kusan kwana hud'u ana biyar
suna zaune akan dining suna having lunch bayan Zeezee tayi biting kaza tana ci
kawai taji yana tada mata zuciya, se kawai tajiyo amai a guje ta ruga bayi ta shiga
kwararo amai shima Al'ameen da sauri ya bi bayanta.
"Ya Al'ameen please karka k'ariso it's disgusting." Tace dashi a wahalince. Be
saurareta ba ya k'ariso cikin bayin tare da aza hannunsa akan bayanta yana shafawa
back and forth a hankali yana me mata sannu. Aman ta cigaba dayi wane zata harar da
kayan cikinta. Tana gamawa ya tayata wanke bakinta sede ko tsayuwan arziki Zeezee
bata iyawa don jiri, daman ba wani abincin arziki take ci ba kwana biyu ta kuma
sake yin amai. "Princess zaki iya tsayuwa?"
"Zan iya Sweetheart don't worry." Tana gwada mik'ewa daga tsugunen da taken
kawai ta fad'a jikinsa ba control don jiri, da sauri ya taro ta. "Zainab you are
terribly sick we need to see a Dr." Daga nan ya d'agata ya kaita d'aki tare da
kwantar da ita akan gado. Hannunsa ta rik'e kafin ya juya, "Ya Al'ameen stay with
me please."
"Zainab zan kira Dr ne from all seeing bazaki iya zuwa asibiti ba, ina zuwa."
"You can call her later yanzu please stay with me." Be sake mata musu ba ya
kwanta a gefen nata, a nitse ta aza kanta bisa k'irjinsa. "Zainab?"
"Na'am" ta amsa sanyi-sanyi.
"How are you feeling?"
"Sick Ya Al'ameen" ta ansa sincerely. "Ji nake kaman zan mutu."
"Shhh! Bazaki mutu ba in shaa Allah zaki samu sauk'i I'll call a Dr."
"Thank you."
"But Zainab what do you think is wrong with you?"
"Ya Al'ameen I don't know am not a Dr."
"Symptoms shows that you are pregnant" ya fad'a shi kansa besan how and when ba
kawai abinda zuciyarsa ke raya masa kenan.
Bata san a lokacin da ta miqe zaune ba duk da rashin lafiyan da takeji "pregnant?"
Ta nanata cike da mamaki. Sekuma ta shiga kad'a kai, "no it can't be possible Ya
Al'ameen, I can't ever get pregnant please karka sa ranka I don't want you
disappointed."
"Zainab listen to me, when last kika ga period naki?"
"Ya Al'ameen please..."
"Just answer me Zainab when?"
"Ya kamata shekaran jiya yazo bai zoba but nasan zezo soon enough."
"Zainab you are actually pregnant shi yake jawo miki wannan morning and evening
sicknesses d'in."
"Sweetheart ba pregnancy bane kad'ai ke jawo hakan, it might be a malaria fever
ni nasan I can't ever be pregnant shiyasa nakeson kaima ka cire a ranka tun wuri
please."
"And ni na fad'a miki juna biyu ne dake, here look at the mirror bakiga kin
k'ara haske da k'iba ba?" Kallon kan nata tayi sannan back to him "well it might be
ko dan ina jin dad'i ne."
"Dad'in exams ko kuma na rashi na? You have no reason to add weight like this
Zainab except for you are pregnant."
"Am not Ya Al'ameen."
"We'll see about that nide nasan akwai little soldier na ko Princess anan, zan
kira Dr Sammy" Yayi maganan hannunsa aze akan flat cikinta. Hannunsa tabi ta d'aura
nata akai "Ya Al'ameen are you sure about this? Do you really think that am
pregnant?"
"Yes Princess evidences sun nuna, two days ko nema na bakiya yi unlike before
this is another strong symptom."
"Ya Al'ameen bana son in yarda da hakan, banason se Dr ta iso tace mana am not
pregnant I don't want to disappoint you, please kabar fad'an ina da ciki."
"You are pregnant Princess I won't ever stop saying so."
"I really do pray so, ba wanda ze kaini murna da farin ciki idan har Dr ta
tabbatar mana da eh cikin ne dani, banida burin daya fiye min inga na azurtaka da
zuri'ah Ya Al'ameen, ina son inga kids namu sun saka a tsakiya kuna wasa, inason
inga na cika maka gidan nan da cute kids just as you are, imagine just how cute
it'll look."
"And in shaa Allah that time has come Princess, nasan akwai little sodlier na ko
Princess anan soon enough zasu fito, I love you Princess I love you so much."
"I love you more" ta amsa alokacin da yake neman kissing nata, da gan-gan yayi
hakan. Shutting kiss nasan tayi tana turasa da wayo "Princess I need you, I need My
woman."
"Ya Al'ameen please kayi hak'uri ko zuwa gobe am feeling weak yanzu."
"See!" Yayi exclaiming "I told you ciki ne dake kink'i yarda gashi you are
loosing interest in this which is another sign ai da gan-gan na tambayeki."
"My Soldier do you really think so?" Tayi maganan itama tana soma yarda da batun
eh cikin ne da ita. "Yes Princess bari in kira Dr" anan ya mik'e ya kira Dr Sammy
inda ta sanar dashi tana zuwa. Hannu Zeezee ta aza akan flat cikinta tana shafawa a
hankali what if am really pregnant? Ma'ana mahaifata bata 6aci ba kenan? Oh Ya
Allah! Ka tabbatar min da hakan, ba abinda Mijina yake so kaman yaga jininsa ya
Allah ka tabbatarmin cikin ne dani tayi add'uar cikin ranta. Komawa kan gadon
Al'ameen yayi yajata jikinsa ta kwanta. "Princess yaushe little Princess d'ina zata
shigo duniya ne? I want to meet her."
"Sweetheart nothing is certain yet, bari Dr tayi mana confirming tukuna."
"Ai ni na riga nayi confirming, Dr kawai zata duba min how old My Little Princess
or Soldier is, amman ciki kam akwai. Akwai a jiya na anan" yayi maganan tare da aza
hannunsa kan cikinta yana shafawa a hankali. Kai ta d'ago tana kallon cikin
idanunsa a hankali tace, "I love you My Soldier."
"I love you more" ya fad'a tare da pecking forehead nata. Bada dad'ewa ba Dr
Sammy ta iso inda har d'aki Al'ameen ya shiga da ita. Dr'n so cute tana setting
eyes nata akan Zeezee dake kwance amman tana neman zama ganin shigowar Dr'n, tun
anan ta gano juna biyu ne da Zeezee."Congratulations Brother."
"What for Dr?" Al'ameen Ya tambayeta a cikin duhu.
"Your wife is pregnant!" Farin cikin da Al'ameen da Zeezee suka tsinci kansu
ciki is indescribable.
"I told you Princess, you are carrying my baby." Yayi maganan sounding
delighted. "Dr are you sure?" Zeezee tayi tambayar hannunta dafe kan cikinta still
not believing, a yayinda Al'ameen ya k'ariso gefenta ya zauna.
"Yes Dear, ba semun miki wani gwaji bama, yanayin ki kad'ai ma shedan kina d'auke
da juna biyu ne."

"Alhamdulillah" cewar Al'ameen totally out of words bema san na cewa ba tsan-
tsan farin ciki. Hugging Zeezee yayi "we've finally made it Princess, thank you."
Ya sanar da ita a kunnenta tare da pecking forehead nata. Murmushi ta mar tare da
d'ago kanta daga jikinsa ta tambaya;
"Dr but how is that even possible? Nayi kusan shekara uku ban ta6a yin koda 6ari
ba saboda wani maganin hana d'aukan ciki da akata d'ura min for good 6 months,
yanzu kuma kice am pregnant? Side effects d'infa? You mean to say Mahaifata bata
lalace ba kenan?"
"Wow! Thank God Mrs Al'ameen, shi dama magani da aikinsa a jiki da kuma side
effects nasa Yana determining environment na mutum ne, genes structure and also
kalan abin da mutum ke ci matters. Wani zakiga yayi ta shan magani amman bayi mai
aiki wani kuma da zaran ya sha yake samun waraka. Same goes to the side effects of
drugs, ke daman tun chan Allah be k'addara miki haihuwa bane se yanzu, if not
mahaifarki is good tunda har kika iya kika d'au ciki but if you still don't believe
me, muna iya k'arisawa asibiti na mu duba miki mahaifar muga if maybe abu kad'an ya
sameshi kinga se ayi treating da wuri sannan kuma mu duba cikin naki how many weeks
or months ne." Kwantar da Zeezee dake zubda hawayen jin dad'i da farin ciki
Al'ameen ya kuma yi a jikinsa "cry no more Princess, kinji bayanun Dr Sammy ni dama
I told you nothing is wrong with your womb, still kina son a duba mikin?"
"Kai kanaso a dubamin ne Sweetheart?"
"Nifa na gaya miki ba abinda ya samu womb naki Zainab, haihuwa ne Allah be kawo
ba se yanzu."
"Toh shikenan zamu bita kawai ayi scanning mana baby'nmu ko?"
"Yes Princess." Ya fad'a tare da pecking forehead nata. Excusing nasu Dr Sammy
tayi sannan Al'ameen ya shirya Zeezee da kansa duk suka fice asibitin.

Achan aka yo scanning cikin Zeezee inda aka gano tana d'auke da cikin d'an d'aya
which is a month old! Printing photos d'in Zeezee tasa akayi mata, har yanzu ta
kasa believing komi gani take tamkar mafarki take wai ita ke d'auke da cikin
Al'ameen nata yau? Wow! Yau kamata yayi ta kwana tana godewa Allah wai bama na bata
daman d'aukan cikin Al'ameen ba, a'a na hanata d'aukan cikin Adeel saboda ayau
tasan da ace Allah ya sanya rabo tsakaninta da Adeel da har yanzu mak'ale mata ze
nayi yana using d'ansu ko 'yarsu as a reason.
Maguna kad'an aka rubuta musu na hana zazza6i da kuma amai suka dawo gida. Wani
irin tattalinta Al'ameen ya shiga yi sekace gold ko zama da tashi shike tayata yi.
"My Soldier Baka san too much of GATA ba kyau ba?" Tayi maganan kanta na aze akan
cinyansa suna zaune a kan kujera a parlour.
"Meya faru kuma?" Tasowa tayi ta zauna, "tunda muka dawo daga asibiti mana, ko
zama zanyi kace kai zaka zaunar dani."
"It's because I love you Princess, kuma fa yanzu ba ke kad'ai bace, akwai little
Princess d'ina anan." Murmushin jin dad'i ta sakar mishi. "Toh idan ka saba min da
gata haka kuma ranan da baka nan fah? Gashi dama ba zama kake ba nasan zuwa next
week zaka ce zaka koma" ta k'are maganan with a sad face.
"Oh come on Princess, taya zan tafi in barki a wannan condition d'in, I'm staying
here with you."
"Dagaske My Soldier?"
"Yes Princess zan rok'esu sumin extending stay d'ina."
"Oh! I love you so much" ta fad'a tare da hugging nasa sosai, hugging nata back
shima yayi suna masu feeling love na juna. A hankali ta raba hug d'in tace,
"Sweetheart I can't believe that I am actually pregnant with your baby I love you
beyond expectations." Hugging nata yayi a hankali yana shafa bayanta "I love you
more Princess, you are my happiness." Zatayi magana kenan wayan Al'ameen yashiga
ringing a tare suka kai duban su suka ga Mama Babba ke kira, without hesitation
Al'ameen ya d'aga bayan sun gaisa ta tambayi ya Zeezee ya amsa da lafiya sannan
yace, "Mama I have a huge suprise for you" maganan yayi yana kallon Zeezee yana
mata murmushi, itama murmushin take mai.
"Toh Only Son wani suprise kuma yau Mama ta samu?"
"Are you ready?"
"Al'ameen wai kakar ka ka miyar dani ne zaka gayan abu ma seka yita jamin rai?"
"Uhm-uhm its about Zainab."
"Meya sameta? Kace min fa k'alau take."
"Your grandchild is on board Mama, Zainab is one month pregnant." Abinda Mama ta
dad'e tana jiran ji kenan rananda zataga jikanta daga only son nata, gaskiya ne
mahak'urci mawadaci, ada har shaytaan raya mata yake tayi ma Al'ameen magana game
da rashin haihuwar nasu jin shiru, su Aysha ma gabad'aya sun k'osa kullum cikin
tambayarta suke yaushe matar Ya Al'ameen zata haihu, se gashi Allah ya kawo ranan.
Tsan-tsan murna Mama tama rasa na cewa. "Al'ameen dagaske kake?" Abinda kad'ai
bakinta ya iya furtawa kenan. "Dan wallahi idan na gano wasa kakemin zaka gamu
dani."
"Mama zan miki k'arya ne? Zainab is preganant."
"Oh! Allah! Alhamdulillah! dan dad'i banma san ina zan sa kaina ba Al'ameen,
ashe lokaci ne kawai beyi ba? Toh Allah ya bata lafiya ya inganta yakuma sauk'e ta
lafiya. Kai! Naji dad'in wannan labari, finally jika na zai iso daga gun Only Son
d'ina kace in soma had'a akwati na kawai."

"Aifa ki fara in 8months time jikanki ze iso." Se dariya k'asa k'asa Zeezee dake
gefensa take bond na Al'ameen da mamanshi ba k'aramin burgeta yake ba itama wataran
tanason taganta haka da d'anta.
"Ina Zeezeen bata please" Kallon Zeezee yayi wanda da sauri tayi mai ido nufin
yace bata kusa don kunya ma takeji.
"Ermm tana bacci."
"Ayyah toh dama kana barinta tana hutawa kaji ko?"
"Mama kuma wani irin magana kike?"
"A'a gaya ma nake ai nasan ku yaran zamanin nan, idan kaga kuma bazaka iya
hak'ura ba seka tattara kayakin ka kadawo Abuja don yanzu hutu Zeezee ke nema."
"Oh Allah! Help me." Kad'ai ya furta.
"Help Zeezee de, nide na gaya maka Al'ameen kana barinta tana hutawa, kuma duk
abinda takeso kana yi mata kaji ko?"
"Naji Mama" ya amsa don a rabu lafiya kawai.
"Yauwa d'an albarka, bari su Salmah su dawo in sanar dasu wannan great news, ka
gaishemin da Zeezee please nima zuwa anjima zan kirata."
"Toh."
"Yauwa ka kula da ita fa sosai aikin k'arfi du ba nata bane yanzu, kar a tak'ura
wa jika na."
"Toh Mama am hanging up."
"Uhum sannu Al'ameen d'ina." Tana fad'in haka ta katse wayan. Nan Zeezee ta 6arke
da wani mahaukacin dariya har rik'e cikinta take, wani kallo Al'ameen ya bita dashi
"kuma dariyan me kike haka?"
"Babu" ta fad'a in between laughter.
"Aww don Mama tace min ina barinki kina hutawa kike min wannan dariyan?"
"No I'm sorry Sweetheart ba dariyan ka nake ba" tayi saurin fad'a sede ta kasa
tsagaita dariyan har yanzu.
"Wai ni Mama me ta d'auke ni ne? Bunsuru kome da zata wani cemin in barki ki
huta, ai Allah ma sheda na ne." Ya k'are maganan tamkar zeyi kuka. "Haba My
Soldier" tayi maganan tare da matsowa kusa dashi tayi cupping face nasa "kai ma
kasan thats not true, kai da sena neme kama kake bani hak'k'i na tukuna, kasan waye
asalin bunsuru?" Kai ya kad'a yana bin bakinta da kallo.

"Adeel, Adeel is the true defination of bunsuru, Mama kawai ta fad'a maka ne
incase in ba haka ba nima shedar kace you are not a sex addict Sweetheart." Ta
k'are maganan tana yimai murmushi. Dad'i sosai kalamunta suka sanya sa. "Thank you
Princess."
"Most welcome Sweetheart, can I kiss those sugar lips?" Tayi maganan tana bin
kan lips nasa da yatsarta. Da wuri ya kad'a kai tare da sauk'e hannunta daga
fuskansa, "meh kikeson Mama tace? Ina kina jin warning data kashe min anan? Ni zan
koma Abj ma gobe."
"Ai wallahi k'arya ne" tayi maganan tare da had'e gira tana tura mai bakinta.
"LOL Princess wake k'aryan? Ni?"
"Ni bance kaiba amman de k'arya kace zaka koma Abj gobe."
"Zaki hanani ne?"
"Sosai wallahi, I need you to stay" tayi maganan tare da zagaye hannayenta akan
wuyansa, kafin yayi wani k'wak'k'waran motsi tayi owning lips nasa suka fad'a kan
gadon da baya.****

*****
Allah da iko yake, abinda ya kama daga kan Mama har izuwa kan Yasmeen all
couldn't believe that Zeezee is pregnant, seda kowa ya cire rai sannan Allah yayi
making wonders nasa, murna da farin ciki kam yakasa gushewa a zuk'atansu. Duk se
fatan Allah ya sauk'e ta lafiya suke. Zeezee fa batada sana'ar data fi tayita aza
hannunta kan flat tommy'n ta tana shafawa a kullum har yanzu gani take wane a
mafarki ne wai tanada ciki, cikin ma na Ya Al'ameen nata. Even though tana shan
maguna hakan besa zazza6in safe da yamman dake daminta ya dena ba sede kam ya ragu
ba laifi. Tayi kusan sati uku ana abu d'aya kullum sannan a hankali ya d'auke.

****
Zeezee na zaune bisa sallaya bayan ta idda sallan isha Al'ameen kuwa ya fita
masallaci ta jiyo ringing d'in wayarta. A nitse ta miqe ta d'aga cike da jin dad'i
ganin Ya Ibraheem ke kira.
"Halo My Ya Ibraheem."
"Na'am Autan mu tawa ta kaina."
"Na'am, Ina yini?"
"Lafiya ya kike ya Maj-Gen?"
"Lafiya qalau ya takwarana da Aunty Fatee dakuma Maamah?"
"Kowa lafiya ashe wata taci wake ban sani ba." Shima wai ze rama abinda tayiwa
Fateensa lokacinda ta keda cikin Maamah.
"Wake kuma Ya Ibraheem aina?" Tayi maganan cike da rashin fahimta.
"Eh wani yaba wata wake itako ta kar6a ba."
"Laaaaa! Ya Ibraheem!" ta fad'a cike da kunya alokacin data gano inda ya dosa.
Kare fuskarta ta shiga yi as if yana gabanta.
"Eh ko ba haka bane?"
"A'a nikan bansan me kake fad'a bama."
"LOL toh Allah sauk'e ki lafiya we are all here for you okay?"
"Thank you Ya Ibraheem I love you all so much."
"Allah sa wake biyu de kikace ki sambad'o mana twins."
"Kai Ya Ibraheem wato kaima ka rama wa Aunty Fatee ko?"
"Wata taci wake de."
"Wani kuma ya bawa wata wake ba."
"Ai Fatee na is not pregnant kede kikaci wake." Mocking nata yata yi yana neman
tsokanarta har seda Al'ameen ya dawo sannan sukayi sallama.

"Toh wa kuma Princess ta samu take ta wannan dariya haka?" Alameen yayi maganan
yana k'arisowa kan gadon bayan ya rage kayan dake jikinsa. Itama hijabin nata ta
cire sannan ta matso ta kwanta gefenshi tace, "sannu dazuwa Sweetheart."
"Thank you Princess" janta yayi ya kwantar da ita a jikinsa.
"Waya saki dariya haka?"
"LOL nida Ya Ibraheem ne fa yake neman tsokana na."
"Ayyah how is he and his family?"
"Duk suna lafiya."
"Masha Allah yau ma bazaki ci abinci ba zaki kwanta?"
"Nasha corn flakes d'azu am full just hold me inyi bacci." Hannunsa d'aya tana
kwance akai d'aya kuma yana k'ark'ashin rigarta yana feeling baby'nsu. "As you wish
Baby machine, sleep like a baby, I love you okay."
"I love you more My Soldier Daddy'n unborn d'ina.." Da haka sukayi falling into
a beautiful sleep.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣0⃣

_Copying from me won't ever make you be ME, I'm me you are you. So
why don't you just improve your skills and stick to being YOU? #WordsOfWisdom_

Washegari Zeezee ta tashi garau sa6anin yadda ta saba tashi da zazza6i,


hannun Al'ameen dake k'asan rigarta ta zare a hankula sannan ta raba jikinta da
nasa ta shiga bayi tayi brushing ta fice kitchen inda ta had'a musu had'ad'd'en
breakfast daga nan ta d'ago tsinstiya ta shiga shara wanda in the process Al'ameen
ya fito sanye da vest da shorts.

"Princess?" Yayi maganan unbelievably. "Me nake shirin gani haka? Me kikeyi?" A
hankula ta d'ago kai tana kallonsa sannan tace, "shara nakeyi har ka tashi? Good
morning Sauran wanka."
"Shara? Da izinin waye?"
"Sweetheart kaman ya da izinin waye kuma? Rabon gidan nan da shara since when?
Yau kuma nad'anji sauk'i se bazan yi aiki ba?" K'arisowa gaban ta yayi da niyyan
kar6an tsintsiyan wanda tuni ta 6oye a bayanta.
"Bani." Ya fad'a in a serious tone. Kafad'a ta buga.
"Princess bani."
"O'o."
"Am serious" ya mik'a hannu a bayanta don kar6e tsinstiyan nan ta shiga 6oyewa,
da k'yar ya samu ya kar6e. "Ka bani mana Ya Al'ameen."
"Nak'i."
"Toh meh dalilin ka haka kakeson abar gidan da dotti? Jibi k'ura fah."
"Za'a nemo me aiki tanayi ke bakiji abinda Mama tace bane?"
"Naji amman ai shara bawani aiki neba meh wahala kuma ni wallahi banason me
aiki."
"Why?"
"Saboda suna snatching wa mutane mazajensu, ni banaso."
"LOL Princess ni yaushe ma nake zama a gari bale sumuki snatching d'ina?"
"Oho nide banaso ka bani tsintsiyan nayi shara na kai kuma kaje kayi wanka."
"Bazakiyi ba Princess am serious, me aiki za'a d'auko miki ke bakisan in the
first trimester na pregnancy babu kyau mace tana yin aiki masu k'arfi ba? Saboda
placentation be gama taking place ba har yanzu, pregnancy'n baida k'wari little abu
yana iya jawo miscarriage, banason mu rasa little Princess namu." Murmushi tasa
sosai a yayinda sonsa ke sake beating a heart nata "kai kuma yaushe ka zama Dr
Sweetheart?"
"LOL kina wasa da ni ko Princess? That aside kibar sharan zamu nemo me aiki."
"Ni wallahi bana so."
"Toh naji anytime masu aikin naki sukazo zan shiga d'aki se sun tafi in fito,
okay?" Shiru tayi tana nazari. "Okay?"
"Promise ko d'aukan ruwa bazaka fito yiba."
"LOL Princess I promise."
"Toh shikenan."
"Kinbar sharan?"
"Sweetheart d'ina bayaso ba dole in bari ba." Ta amsa mai tana murmushi.

     "Thats My Baby Machine." Ya sanar da ita murmushi kwance fal a fuskarta.


  "Muje kayi wanka toh breakfast is ready."
   "Har yaushe kikayi setting dining table Princess? Banason kina wahalar da kanki
da kuma little Princess d'ina."
   "Wahala kuma? You are My Only Soldier in banyi ma bauta ba mawa kake so inyi
wa?"
   "Ni banason abinda ze gajiyar min dake ne all I need you to do is to rest."
   "Don't worry chips ne kawai kuma you keep on saying little Princess ni Little
Soldier nakeson in haifa, exactly as you saboda koda kayi tafiya se yana keeping
d'ina company."
  "Ni kuma little Princess nakeso ranan da kikayimin wannan zuciyan naki setana
keeping d'ina company."
   "LOL ba kaine kake tafiya ka barni ba kaga dole in haifi little Soldier."
    "Nop Princess little Princess zaki haifa kuma zaki gani."
  "Nop" tayi sauri ta kad'a kai "I told you little Soldier zan haifa."
  "Hakane? toh lets bet."
  "lol Sweetheart kai zakayi loosing wallahi lets not even start."
  "See this Princess o telling me ni zanyi losing" yayi maganan yana janta jikinsa
and finally wrapping his arms around her tiny waist a yayinda ta zagaye nata a
wuyansa. "Ko kin manta ni nayi ajiyan achan? Nasan meh na ajiye kuma Princess na
ajiye." Da murmushi d'auke a fuskarta tace, "no amman d-" her last word was crashed
on his lips. A hankali yayi owning lips nata ya shiga kissing nata, sun d'au tsawon
lokaci a haka sannan yayi breaking kiss d'in in a teasing manner. "Its a little
Princess." Ya fad'a with no room left for arguement.
  "No problem ai munyi betting, idan har na haifi Little Soldier zaka bani izini
inyi naming d'inshi after duk name daya min no questions, idan kuma vice-versa na
mace na haifa kai zakayi naming nata after who ever you want I won't ask
questions." Yana wasa da jelan gashinta da suka faffad'i bisa shoulders nata yace,
"are you ready to lose?"
    "I am ready to win over My Soldier."
  "Good! Zamu ga toh."
  "Zamuga Little Soldier'n mu ba." Ta fad'a mockingly.
  "Princess zan..." sekuma yayi shiru.
   "Zakayi meh? You want me on bed with you?" Ta fad'a tana dariya sosai. Tsayuwa
yayi yana adoring nata cause she have the most perfect smile, "you know I can do
that anytime I wish to right?"
  "Ka manta meh Mama ta fad'a maka ne? Cewa tayi ka barni in huta."
  "Aww ma haka zaki ce koh?" Gira ta d'aga mai tana mai gwalo.
  
   "Bari in kira Saje yazo ya shirya min akwati na now now now ko da mota ne in
wuce Abuja." Hannunsa ta cafke da wuri kafin ya juya "you are not doing that."
   "Zaki gani ai."
  "O'o" ta maraice fuska. "Wallahi wasa nake maka kasan I need you badly than how
you need me ko a yanzu kakeso muje na yarda banda zancen tafiya please." Ganin
yadda ta rud'e yasa shi dariya sosai har da rik'e ciki. "Eh ka samu mahaukaciya ba
dole ai kayita mata dariya, bari little Soldier na ya iso kaga ko zan na damuwa da
stay naka ma."
  "Haba! Princess" yayi cupping face nata, "you know right how much I love you, ba
inda zani ina nan to watch over my little princess growing up in my Princess, I
can't wait to see that baby bomb."
   "Ni kuma banaso" tayi maganan tare da had'e rai.
  "But why Princess?"
  "Saboda ka samu abin teasing d'ina ba kana neman tsokana na."
  "LOL Princess inji waye?"
"Eh mana gashi tun yanzu ka soma yi, in ba haka ba mey abin kallo a baby bomb? Ni
banaso."
  "Princess it'll suit you, ai kinada tsawo infact bomb d'in ma zebi tsawonki your
tummy won't grow big."
  "Are you sure Sweetheart?"
  "Yes Darling Baby Machine."
"Kasan mazajen yanzun nan da zaran sunga cikin matayensu yayi k'ato se su dena
sonsu har kunya suke su ce wannan matarsu ce kum-" da sauri ya aza yatsansa bisa
lips nata yace, "shhh!" tare da kad'a kai. "Don't ever say such a thing Princess, I
am not that kind of men, I am Al'ameen Zainab's lucky husband, bazan ta6a tsanan
kiba, I love you and its true." Yayi maganan tare da d'ago hannayenta yayi pecking
kansu.
   "Awwwn! Sweetheart you are so sweet, I can't ask for a better husband when I've
got the best. Allah ya bar mu tare ya k'ara mana dank'on soyayya, I know our love
will never die."
  "Ameen Princess, it'll never because its true love."
  "Kaga se surutu muke zubawa bakayi wanka ba har yanzu muje muje kayi." Hannunsa
ta kama har bayin ta rakasa sannan ta basa privacy. Kafin ya fito ta cire masa
kayan da zesa ita ma ta sake gyara makeup nata. Cike da so da k'auna suka k'arisa
dining suka karya, yau se surutu Zeezee ke tayi wa Al'ameen su ba sabon ba yau jiki
da sauk'i.

***
  Haka kuma rayuwarsu ta cigaba da kasancewa, cikin tsan-tsan so da k'auna da kuma
biyayya wa juna. Sanin kowa ne yadda Soldiers suke respecting matayensu. Gatan da
Zeezee ke sha gun Al'ameen kam sede muce Allah kawo mana mazajen da zasu kula damu
muma haka, ma'aurata kuma ya k'ara dank'on soyayya a tsakaninsu, AMEEN.

     Kusan 2 months Al'ameen yayi ma Zeezee, kula da Zeezee yake sosai, basu wasa
da pre natal appointments nata, Zeezee can't ask for more!
'Yan gun aikinsa kuwa sunka ishesa da lalle fa ya dawo aiki ya musu yawa they
need him, gashi ma Zeezee needs him. Gashi nan cikin nata d'an kad'an ya 6ullo kai.
Kullum Zeezee na gaban mirror tana dubawa she can't get enough of herself, she is
now 3 months pregnant, ji take kaman ta jawo watan haihuwarta don tabawa Al'ameen
family'n da he has always longed for.

******
   Zeezee na kwance rabi akan gado rabi jikin Al'ameen ta jiyo wayansa na ruri
kasancewar baccin nata beyi nisa ba yasa takejin dukkanin abinda ake fad'a mai da
kuma abinda shima yake fad'a a wayan. Hak'uri yake ta bawa manyan da suke kansan da
su d'an k'ara mai hutun koda na 2 weeks ne amman sunk'i saboda they need him badly,
Al'ameen is such a great warrior, soja ne me aiki da kuma k'uzari, bayi tsoro
saboda haka they can't do without him. Ba kalan pleading nasu da beyi ba amman se
hak'uri suke basa suna cewa ba yadda suka iya ne suma yayi hak'uri haka shima he is
left with no option dole yabar Zainab tasa. Yana katse wayar ya miyar da hannunsa
kan k'aramin cikin Zeezee yana tunanin ya zeyi ya tafi ya barta. Ba Zeezee kad'ai
ba yanzu, shi kansa Al'ameen he is addicted to her saboda a kullum suna tare befi a
sati su fita sau biyu ko uku ba nan ma sede gida gun Mama ko asibiti sam baya son
tafiya shima yanzu yafi son yayita ganin Little Princess tasa tana girma a idonsa,
he can't tell just how much he loves Zeezee.

   Zeezee data jiyo komi a waya tace a ranta wallahi baza ku tafi min da Sweetheart
ba. Plan ta had'a abinta, seda ta bari Maghrib yayi Al'ameen yazo tashinta Sallah
sannan ta langwa6e tana wani abu sime-sime tana ishh! ashhh! washhh! ita bata jin
dad'i bata da lafiya.
   "Princess are you okay?"
   "Ya Al'ameen am not" tayi maganan tamkar zatayi kuka.
   "Oh God! Meya sameki? Meke damunki? Ina ke miki ciwo?" Cikinta tayi pointing
"nan."
   "Little Princess d'ina ne take damunki?" Kai ta gyad'a cike da shagwa6a "harda
baya na ma" tayi adding.
  "Sorry Baby Machine, me kikeso toh yanzu? Muje asibiti?"
   "Arrghhh! Cikina Ya Al'ameen do something please." Gabad'aya ya kid'ime yama
manta da sallan dake kansa. "Ina... inaaa waya na?" Ya shiga i'ina.
  "Dr zaka kira?"
  "Eh ta duba min ke sannu."
  "Ni o'o banason Dr ni kai nakeso."
  "Toh Princess ya kikeson inyi? Am not a Dr."
  "Arrggh! Baya na!" ta sake sa wani ihun. "Omi'god am so sorry kinji? Yi hak'uri
ki bari in kira Dr."
  "Ni kar ka kira Dr."
  "But why Princess?"
  "Ni banaso kawai stay with me in muna tare ina jin rashin lafiyana na d'aukewa.
You are the remedy to all of my sicknesses." Murmushi ya sakar mata me sake kwantar
da hankali.
  "I love you Princess and am here for you, Sallah fa? Zaki iya tashi?"
  "Eh tayani in tashi."
  "Zaki iya? Are you sure?" Kai zallah ta gyad'a mishi sannan ya kaita har bayin
tace mishi she can manage from here. Gabad'aya hankalin bawan Allah ya tashi besan
duk set up na Zeezee bane. Tana ganin ficewansa daga bayin ta sharo k'wallanta tana
murmusawa sosai "ai wallahi ko sunfi mamannin su k'ok'ari se sun bar min kai ka
k'ara koda sati biyu ne ko d'aya, iskanci kawai." Nan da nan ta d'auro alwala ta
fito daga bayin ma tak'i kira ta sa mishi chak yazo ya d'auketa ya direta kan
sallayan daya shimfid'a mata tare da sanya mata hijabin.
  "Zaki iya yin Sallan a tsaye ko zakiyi a zaune?"
  "Zan iya kar ka damu, Matar Soldier cefa ni."
    "Thats my superwoman I love you."
  "I love you more and more, muyi sauri ciki na." Nan da nan ya jasu sallah cikin
nitsuwa, tattalin Zeezee yatayi yinin ranan ya ma kasa sanar da ita ya kusa komawa
Abj ganin condition da ta shiga gashi da zaran yace ze kira Dr Sammy seta ce ita
bataso. Tabi ta tada mishi hankali har ya rasa nayi, ya had'a mata tea tace bata
so, custards, oaths duka tak'i sha idan yana kallonta tayita matso k'wallan tsiya
da zaran ya juya tasa dariya ciki-ciki. Kiran 'Yan office nasu back Al'ameen yayi
inda ya musu stating critical condition da Zeezee ke ciki, ya kuma rok'esu da don
Allah su d'an k'ara masa hutun koda sati biyu ne. Sun ka ko amince amman da
sharad'in idan ya dawo aiki se ya musu 2-3 months tukuna ya koma, ba yadda ya iya
hakan ya yarda. Suna gama wayan ya dawo d'akin nasu, nan fa pretender ta soma awwch
da washhh. K'arisosa gabanta yayi ya zauna fuskarsa d'auke da damuwa, a rayuwa baya
son abinda ze ta6a masa Princess nasa. "How are you feeling Princess? Har yanzu
little Princess na damunki?"

   Ita kanta ya bata tausayi ganin yadda hankalinsa ya tashi matuk'a amman ya ta
iya? She have to keep on the pretense idan ba haka ba seyace ze koma Abj dan ita
bata ma san yayi waya da 'yan office nasan ba yanzu.
   "Har yanzu Sweetheart."
  "Sannu kinji? Kiyi hak'uri gobe muje asibiti ni bansan me zan sake miki ba, an
not good in this only if I can take away your pain." Hannunta ta zaro daga bargon
da take lullu6e dashi tare da rik'e hannun Al'ameen cikin nata tana murzawa
soothingly.
   "I love you this way Sweetheart, I love you for who you are, thanks for staying
with me."
   "I owe the pleasure Princess, zaki sha koda black tea? Karki ce no kinji yi
hak'uri kar Little Princess namu tayi starving."
  "Toh ka had'a min zan sha." Ta sanar dashi face nata d'auke da smile. Dad'i sosai
yaji wanda ya kasa 6oyewa don kuwa tun safe suke abu d'aya. "Ina zuwa kinji?" Ya
fad'a tare da pecking forehead nata. "Wait Sweetheart yanzu this week d'in zaka
koma aiki ka barni ni kad'ai?" ta k'are maganan wane zatayi kuka wearing a most sad
face

   "Shhh! Don't cry Princess taya zan tafi in barki a wannan condition? Kema kinsan
its not possible. Na rok'esu da k'yar suka k'ara min sati biyu."
  "Sati biyu!" Tayi exclaiming cike da murna harda mik'ewa zaune tayi watsi da
bargon da take lullu6e dashin, tama manta tana faking rashin lafiya tsan-tsan farin
ciki. Ido da baki wangalau Al'ameen ya bud'e ya tsaya kallonta da mamaki itan da
tace ko k'arfin d'aga jikinta batada saboda yadda take jin zazza6i amman kuma shine
ta daka wannan tsalle? Ganin fa yana iya gano faking rashin lafiyar take daga yadda
yake ta kallonta yasa ta d'an rigingina da gadon tana ta6a kan cikinta "d'an ihun
danayin nan yasa bayana ciwo Sweetheart kawai naji dad'i ne bazaka tafi ba se in 2
weeks time. I love you."
   "I love you more My Baby Machine." Ya fad'a still checking her, anya kuwa? Ya
tambayi kansa "bari in had'o miki tea'n ina zuwa." Yana mik'ewa Zeezee tasa
murmushi k'us-k'us tana me jin dad'in Al'ameen baze tafi ba ya barta ba har da wani
YES! nata irin mission accomplished d'innan. Shiko har ya juya se kuma ya sake
turning back to her ba shiri don tambayarta koya sa mata madara ne a tea'n ko bak'i
takeso.
    Nan fa ya kama Hajiyar red handed tana dariya bama murmushi ba wanda tuni ta
tsuke fuska ganinsa amman inaaa ya riga ya gan ta.

    "Princess?" Da wuri ta sauk'e idanunta a k'asa. Komawa yayi ya zauna gefenta


"Princess?"
  "Na'am" ta amsa not looking at him.
  "Look at me." Da wuri ta kad'a kanta.
   "Kuma murmushin me kike? Princess anya kuwa?"
  "Anya meh?" Finally ta d'ago kanta tana kallonsa.
  "Anya ba faking rashin lafiyar nan kike ba Princess?"
  "Kaman ya Sweetheart? Dan ba kai keda cikin ba ai dole kace faking nakeyi, ni
kad'ai nasan abinda baby'n ka kemin." Ta qare maganan tana zum6uro baki.
  "In haka ne toh dariyan me kikeyi? Wanda bashida lafiya yana dariya ne? Kuma ina
juyawa kika sake fuskar."
   "Haaa'a! Ni murmushi nayi ba dariya ba. Yanzu ma murmushi ban isa inyi ba
Sweetheart shikenan ya zama abin magana akai?"
  "Yanzu Princess kina kallon cikin idona kina min k'arya koh?" Sekuma taji ta
kariya. "Nifa ba k'arya nake ba."
  "Ga jikinki ma ba zafi."
  "Alright alright naji ka kamani ina maka k'arya I'm sorry, I just can't help it
and wannan plan d'inne kawai solution gashi yanzu sun k'ara maka hutun sati biyu
ai, it worked!" Da mamaki ya tsaya kallonta har tayi fooling nashi haka be gane ba?
Lallai kuwa ta fisa wayo, "so duk kuka-kuka da su awch da wash na d'azunnan duk
k'arya ne?" Kai ta gyad'a mar a hankali "am sorry."
"Haba! Princess kinsan yadda hankalina ya tashi kuwa?"
   "I'm sorry Sweetheart but kaima inda kaine a shoes d'ina you'll do exactly the
same thing bana son ka tafi, I want you by my side."
   "Yanzu kenan duk sharri kikayi ta wa Little Princess d'ina?"
   "Ba Princess bace, Soldier ne kuma nasan ze yafe min kaman yadda Daddy'nsa ya
riga ya yafemin ko?" Tayi maganan cike da shagwa6a.
    "Am very mad Princess." Hannunsa ta kama ta had'a da nata tana murzawa
soothingly, "Sweetheart please don't be I'm sorry."
   "Kinsan yadda hankalina ya tashi kuwa? Ban nuna miki bane fa kawai, har kai na
sanda yamin ciwo bana son ganinki ba lafiya."
  "I'm sorry Sweetheart please forgive me, I couldn't think of a better plan
shiyasa, ka gane mana bana son ka tafi ka barni ne."
  "Uhmm" zalla yace.
   "Baka hak'ura ba har yanzu?" Hannun nasa ta sake ta kama kunnuwanta both "I'm
sorry My Soldier I won't do it again, please." Kallonta yayi na 'yan seconds sannan
ya miqa hannunsa ya sauk'e hannayen nata. "Promise?"
  "I cross my heart."
   "Toh na hak'ura."
  "Thats My King!" Ta fad'a tare da shigewa jikinsa tana hugging nasa, shima
hugging nata yayi back yana shafa bayanta a hankali, "but my plan worked atleast
you are staying with me for the next two weeks, it isn't bad or is it?"
   It is yake son ce mata dan kuwa idan ya tafi yanzu bai sake zagayowa se nanda 3
months, tafiyan da be ta6a yi ba zeyi wannan karan. Yasan idan har ya sanar da ita
akwai tashin hankali.
    "Is it?" Ta sake tambayarsa jin shiru. Breaking hug d'in yayi tare da cupping
face nata "it is not Princess actually nima ba son tafiyan nake ba, we get to spend
two more weeks together." Hannunta ta aza akan nasa dake rik'e da fuskarta tana
shafawa a hankali.
  
   "I love you My Soldier, gani nake like bazan iya rayuwa ba idan ba kai, na
gommaci in rasa komi a duniyan nan harta rai na da akan in rasa ka, banida burin da
yafi inga muna tare kuma ina sanya ka farin ciki. I love you eternally." Kissing
lips nata yayi lightly but with so much emotions, assuring her he is with her
forever. A hankali yayi pulling out, "I love you more Zainab, for all my life ke
kad'ai ce macen dana ta6a so. Despite all the different types women I met during my
time in school, despite all those Mama introduced to me, duk cikinsu ba wacce ta
ta6a yimin, but ke? For the first time that I set my eyes on you Zainab, my heart
skyrocketed, alokaci guda naji ina sonki even though I've never experienced love I
know it was love, alokacin banida burin da yafi in mallekeki and make you happy-"
   Katsesa da wuri tayi sounding disappointed "and a lokacin I failed to see you
for who you are, I was dense and stupid and blinded by Adeel's playful love na kasa
baka chance."
"Don't talk like that Princess, here we are together today ready to die for each
other, it is all that matters right?" A hankali ta gyad'a mishi kai, "I love you
Habeebi kasan haka Fannah ke kiran Anas wani love story dana karanta and sunan
yamin dad'i sosai."
"I love you more Habibtee, bari in had'o miki tean."
"Muje mu had'a lunch tunda ba rashin lafiya again."
"LOL pretender kawai, You sure about this?"
"Yes Sweetheart." Hannunsa ya miqa mata tasa nata ciki sannan ya mik'ar da ita a
hankali suka fice kitchen. Macaroni me rai da lafiya suka girka da minced meat all
over se k'amshin girki ke tashi a gidan. Atare suka ci abincin sannan suka fito
waje gun garden suka zauna suna shan iska kamin Maghrib ya shiga.

*MIEMIEBEE. Team #YGC🎀*


Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣1⃣

_Where is the Most Sweetest Angel of them all? MY SUPER STYLISH BITCH. Just
in a swift motion kika zame YAR GATAN MIEMIEBEE, know that I am head over hills in
love with you, ina godiya da kalan soyayyar da kike nunawa ZAIMEEN🔥 and YGC🎀 in
whole. You guys are always on my mind Mio 17 Babe Cute Xarah, Ashnur Pyar (indian
Babeh) and Queen Meemi. A big shoutout to you Lovers #OneLove💞 Team YGC!🎀_

***
Life moved on, cikin Zeezee se dad'a girma yake a hankali a hankali. Two
weeks d'in ya k'ara mata, cikin two weeks d'innan Zeezee ji take just like a Queen
se abinda takeso Al'ameen yake mata.
Tun ana saura kwana biyu Al'ameen ya koma Abj Zeezee ta soma kumbure-kumbure, shi
kuwa binta yake a hankali saboda condition nata. Murmushi ma ta d'auke yi masa. A
ranan da ze tafi ya d'ago akwatinsa dan shirya kayakinsa ciki. Dama on normal basis
Zeezee ke tayasa su shirya atimes kan ma ita ke shirya masa ita kad'ai amman banda
yau. Juya mai baya tayi tana kwance bisa kan gado Tana game abinta.
"Princess?" Banza da shi tayi sanda ya tako har zuwa gabanta, take ta gwada
juyawa wanda tuni ya kama hannunta. "Princess yau bazaki tayani shirya kayakina
ba?" Baki ta tura mai tare da had'e rai without saying a word. "Haba mana Princess
ke shikenan kullum muna abu d'aya kenan?"
"Ni ka sake min hannu bacci nake ji."
"Bacci? Yaushe kika fara bacci by 8pm?"
"Yau" ta fad'a a takaice.
"Bazaki tayani ba kenan?"
"Eh mana ni banason ka tafi meyasa zan taya ka shiri?"
"LOL toh shikenan zanje in had'a abu na." Har ya miqe seta rik'o hannunsa tare da
jansa da iya k'arfinta seda ya fad'a kan gadon a gefenta. "I don't want you to go."
Ta fad'a tana lumewa jikinsa, hugging nata yayi gagam.
"And I don't wanna go either." A hankali ta raba jikinta daga nasa ta miqe "muje
mu had'a maka."
"Kin huce?"
"Nop kawai zan taya kane bana son ka gaji kai kad'ai is better mu gaji
together." Pecking forehead nata yayi sannan suka k'arisa gun wardrobe d'in. Sede
wani hanzari ba gudu ba yau Zeezee ta lura da yawan adadin kayakin da Al'ameeen
keta iba.
"Sweetheart kayakin nan na zuwa ina ne?"
"Abj of course."
"I know I mean sunyi yawa."
"You think so?" Yayi maganan chan ciki ciki wane me 6oye abu yana susan back head
nasa.
"Sweetheart you're hiding something away from me." Ta fad'a bayan dogon nazarin
da tayi.
"I'm not Princess."
"Toh mesa kake iban kayaki dayawa haka? Shekara zakayi ne achan d'in?"

"Shekara kuma Princess? Saboda incaseties ne kawai."


"Ban yarda ba, zaka jima ne ko? Maybe dan k'ara maka sati biyun da sun kayin ne
sukayi demanding prolonging stay naka achan d'in am I right?"
"What are you talking about Princess kin d'auka wai ni tafiyan nan dad'i yake min
ne? 2 months kawai zanyi in dawo."
"Are you sure My Soldier?"
"In shaa Allah." Murmushi kad'an ta saki masa a yayinda shima ya miyar mata but
deep inside tunanin ya zeyi ya 6ullo mata da al'amarin yake yasani shi da ya sake
dawowa se nan da 3 months ko fiye da haka ma. Suna hira suna shirya kayakin har
suka gama suka watsa ruwa sannan suka kwanta cozy under the blanket.

Kamar yadda Zeezee ta saba ko wani tafiyan Al'ameen se tayita kuka haka wannan
karan ma, ko rakosa waje ta kasa, everlasting kiss ya bata sannan wa baby'nsu ya
fice. Tun safiya ta kama kuka har seda bacci 6arawo yayi gaba da ita se bayan
Azahar ta tashi inda ta tarar da several missed calls nasa. Seda ta idar da Sallan
ta dawo ta kirasa.

"Hello Princess?"
"Na'am Sweetheart kunyi landing lafiya?"
"Lafiya, kinbar kukan haka ko?"
"Ai zan soma sabo yanzu."
"Yi hak'uri Princess banason ki samun little Princess d'ina a damuwa."
"Shine ni ka tafi ka barni, akwai damuwan daya kai wannan ne?"
"I'm sorry kinji? Zan dawo soon enough."
"Wallahi gidan ba dad'i inba kai."
"Ko zaki koma gun Mama ne toh?"
"Nop no need mun kusa resuming school ai probably next week."
"Oh god no! School ze sake stressing min ke out."
"Toh ya muka iya?"
"Allah bada sa'a okay? I love you rananda bakiya jin dad'i ba sekin fita lectures
d'inba stay at home and rest."
"Okay My Soldier zan fita gidan Lubiee, am I permitted?"
"Ina kika kai kunneki d'azu da nake ta ce miki na baki izini kije duk inda kikeso
just don't stay late at night?"
"Ina ta kuka zaka barni ina kuwa na jika."
"Uhm toh ni na baki izini kinji?"
"Toh thank you, bari in shirya."
"Toh ki gaishe min da mother in law na."
"Toh Afrah zata ji bye, I love you."
"I love you more" ya fad'a tare da hanging. Nan da nan ta shirya ta wuce gidan
Lubiee, chan suka had'u da Omar ma inda suka ta hira kaman ba gobe se kusan Maghrib
ta dawo gida.

Life moved on, in a week time su Zeezee 'yan 300level suka koma school, sosai
ta miyar da hankalinta ga karatu, anytime she is less busy kuwa zata kira Al'ameen
nata ko tayi mar video call suta hira. Baby'n su na nan cikin k'oshin lafiya sam
bata wasa da appointements nata. Ahaka fa har sukayi spending 2 months apart nan
Hajiyar ta soma matsawa Al'ameen da yaushe ze dawo at first k'arya ya mata yace
zuwa next week ze shigo saboda besan ta ina ze soma sanar da Zeezee ba. Haka har
satin ya cize be dawo ba nan ma ta sake kiransa harda 'yar k'wallarta, and again ya
sake yi mata k'aryan in 5 days time ze dawo. Kuka ta fashe mar dashi ita she can't
take it anymore she needs him, shikuma ya sanar da ita sauran masa 3weeks infact
4weeks saboda 'yan gun aikin nasa sun mai prolonging zaman nasa for a week more ya
kasa. Da k'yar ya samu ya lalasheta ta yarda akan cewa in five days time d'in ze
dawo.
Al'ameen ya shiga damuwa sosai saboda besan kuma wani k'arya ze sake shiryawa
Zeezee ba next time if she calls, he don't think he can keep on the pretense also,
is better ya sanar da ita su yita ta k'are.

_5 days later... exactly ranan da Al'ameen yace ze dawo._


Sanin daman idan har ze shigo yana sanar da ita kokuwa idan beyi bama bayi wuce
3pm be dawo gida ba yasa Zeezee ta yafe lectures na ranan, even though ta tashi ba
seti saboda leg cramps dake ta kamata kasancewar cikin nata yayi girma ba laifi
getting to 6 months now. Hakan besa ta kwanta ba aiki sosai tayi ranan abinda ya
kama kan shara, mopping, goge-goge sannan ta girka favorite na Al'ameen tuo da
miyan ganye, tayi setting dining itama ta d'au wankanta tasa wata doguwar rigarta
daya mugun amsan figure'nta da d'an k'aramin cikinta dake 6ullowa idan tasa loose
kaya. Rabonsu da waya tun jiya, bata damu da kiransa ba saboda tasan mostly rananda
ze dawo ba'a cika samun wayansa ba. Tun 2pm data idar da Sallah tayi zaune a
parlour tana jiran dawowan Al'ameen sede shiru. Abu fa kaman wasa har 4:30pm
Al'ameen be shigo ba by now kam tayi giving up tasan baze dawo ba he just tricked
her daya ce mata ze dawo yau, toh why? Duda Tasan zargi zunubi ne kuma ba halin
Al'ameen bane kula mata amman se raya mata shaitaan ke da Al'ameen ya fara cheating
ne akanta. Time da zeyi tafiya yace 2 months zeyi, yazo yace ze k'ara sati yazo
yace 5 days yanzu gashi yau d'inma ba alamansa. With this thought running on her
mind kawai seta fara kuka a rayuwa bata son tayi sharing Al'ameen da wata, tasan
its so selfish ta fad'i hakan amman she can't help it, tana sonsa fiye da tsammanin
kowani d'an Adam. Wani sa'in har kishin 'yan uwansa Aysha da Salmah ma take ganin
how they are free with him, barin Aysha dake auta har cinyansa tana d'alewa to talk
more of side cheeks she can't handle them. Kuka ta shiga yi sosai tana shessheqa,
in the process wayanta dake gefen ta ya shiga ruri kaman karta duba don haushi
amman ta dage ta leqa gani tayi Al'ameen na kira.

Shima tun safe ya kasa samun peace of mind, ko aiki ya kasa fita yau saboda beyi
fulfilling promise daya d'au wa Princess tasa ba, yasan sarai she is mad shiyasa
tak'i kiransa har yanzu thats why yayi calling nata instead. Tana ganin call d'in
har ya tsinke bata d'aga ba, video call next ya shiga yi mata nan shima tak'i
d'agawa, again ya shiga calling nata wanda in the process ta kashe wayar nata
kwata-kwata. Nan fa hankalin Al'ameen ya sake tashi, guards nasa biyu da ya bar
mata a gida ya kira ya buk'ace sa daya kai wa Zeezee wayar. Tana zaune kan kujera
ta since d'aurin data sha ta ajiye a gefe se kuka take shark'af shark'af ta jiyo
knocking. Sanda ta share hawayenta ta tambaya.
"Waye ne?"
"Sadiq ne Madam."
"Lafiya?" Tayi maganan tana clearing voice nata.
"Uhhm Madam please ki bud'e." A hankali ta mik'e ta bud'e mishi k'ofan. "Lafiya?"
Ta sake tambaya. Wayansa yake miqa mata "Boss ne ya kirani yace in had'aku ta nan
gashi yana kan wayan." Duk anan Al'ameen na sauraronsu.
"Princess yi hak'uri ki amshi wayan kinji?" Ya fad'a cikin zazzak'ar muryansa me
narkar wa Zeezee da zuciya ta speaker phone. Shiru tayi wane me nazarin abu.
"Princess? Am sorry yi hak'uri ki kar6a kinji?" Ganin bata ko motsa ba and bata
da niyyan hakan Sadiq yace, "please ki kar6a Madam Boss is so worried." Kallonsa
tayi sannan ta miyar da k'ofanta ta rufe. Me kuma Al'ameen ze sake ce mata bayan
evidence sun nuna he is cheating on her. D'aki ta wuce ta cigaba da kuka abinta
hannunta rik'e da cikinta.
"Am sorry Sir, ta rufe k'ofan she is not ready to talk."
"Its okay Sadeeq thank you."
"No please don't thank me again Sir, its my job."
"Good" ya fad'a tare da katse wayan. Yau ina zesa kansa? Tunda yake Zeezee bata
ta6a yimai fushi kaman na yau ba meke faruwa haka? Shi da yasani da tun da a baya
ya yi maning up ya sanar da ita actual batun but he was afraid kar gabanta ya fad'i
abu ya samu baby'nsu.
Bacci ne yayi awon gaba da Zeezee se Maghrib ta tashi tayi Sallah har anan
tak'i kunna wayar tata shiko Al'ameen yini ranan yayi yana trying numbers nata and
duk basu shiga haka ya kasa bacci ranan. Ace for a whole day beji muryan Princess
tasa ba be kuma sata a ido ba ai wannan k'anin mutuwa ne. Apology messages yata
tura mata wanda se a washegari da ta kunna wayar ne ta gansu still bayan ta karance
su bata ji ta sauk'o ba da abinda Al'ameen ya mata. Taya zeta wasa mata da hankali
haka? Idan har budurwarsa tacan ne ta ke rik'esa he could have simply told her akan
wasa da hankalin daya ta mata. Wayan na a hannunta Al'ameen ya shiga kira nan ma
tana gani tak'i d'agawa. Yayi mata missed calls bil adadi da text messages yana
pleading nata da tayi hak'uri ta d'aga he is so sorry and damn missing her sweet
voice. Seda ta gama basa wuya sannan ta d'aga wayan tare da yin shiru.

"Thanks Gee! Thank you for picking up Princess." Shiru tayi bata amsa ba,
"Princess you there?" ya tambaya jin shiru.
"Ina kwana?" ta gaishesa briefly.
"Princess please kiyi hak'uri and let me explain banason inga kina fushi dani
haka ko bacci na kasa yi jiya I've been thinking about you the whole night."
"Me kayimin kake bani hak'uri haka? Ni nace kamin wani abu ne? I didn't."
"Come on Princess, ni kaina nasan me laifi ne ni shiyasa nake son in baki hak'uri
da ki yafe min, I'm sorry."
"Laifin me kamin Ya Al'ameen?"
"Yau ko Sweetheart babu, Oh God Princess am sorry please."
"Ni wai nace kamin laifi ne?"
"Baki fad'a ba amman ni nasan na miki, Princess bawai ina yaudarar ki bane ko
wani abu, I just didn't want to tell you saboda gudun abinda ze haifar. Ba a banza
'yan office d'ina suka k'aramin 2 weeks d'incan ba, seda suka min prolonging zama
na har na zuwa 3 months and I accepted it saboda I thought you were sick lokacin,
yanzu kuma sun k'ara min 1 week again akai probably in 3 weeks time zan shigo in
shaa Allah kiyi hak'uri please."
"All these and you didn't tell me Ya Al'ameen? Taya kakeso in yarda yanzu? I
asked you at first kace min a'a se yanzu kuma kake jeromin wannan bayanan? It would
have been better idan fili kafito kace min akwai wacce ke rik'e ka a chan akan wasa
da hankalin da kake tayi min, I was sick yestarday, leg cramps ke damuna sosai
amman na tashi ba kalan aiki da girkin da ban maka ba duk ya tashi a iska, kasan ba
tahowa zakayi ba why messing with my brain and making me look like an idiot, tell
me taya bazan ji haushi ba Ya Al'ameen?"
"Yaaa Salam! Princess wani irin magana kuma kike haka yau? I am sorry please."
"Thats what your actions are telling me Ya Al'ameen sau nawa kake ce min zak
shigo amman har yau shiru, idan ba rik'e ka wata take ba explain the reason for all
these lies."
"Princess I can't stop you from imagining and thinking of whatsoever kikeso
saboda you have every single right to but ki sani wallahi I am not cheating on you,
I will never cheat on you. Inada perfect wife why will I search for a better one?
Its not possible. I love only you Princess and no one else and am sorry for lying
to you all these times, banida enough courage da zan sanar dake ne da nayi a long
time ago kiyi hak'uri please, I'm sorry and I love you so much." Kasa cewa komi
tayi saboda yadda kalamunsa suke melting mata heart. Meyasa tayi judging nasa da
sauri haka? Gaskiya ne Al'ameen baze ta6a cheating akanta ba amman kuma meyasa
zuciyar ta takasa yarda da hakan har yanzu?
"I'm sorry also" kad'ai ta iya cewa dashi.
"You are still mad I can sense that, just know that I'll never give up har se
kinyi believing d'ina I love you morethan I do love myself."
Nan ma "thank you" zallah tace dashi. Ba k'aramin damunsa I don't care short
responds nata suke ba.
"Ya k'arfin jiki?"
"Alhamdulillah." Ko ya aiki tak'i tambayarsa.
"How's my Little Princess?"
"She's fine." So yake ya sata surutu amman se basar dashi take, da a da ne cewa
zatayi ba Princess bace Soldier ne, he miss her being herself.
"school fah?"
"Muna tests ma."
"Wow really? Not so fast, Allah ya taimaka ya bada sa'a I love you."
"Ameen thank you zanyi karatu se anjima."
"Toh Princess, I love you."
"Aha bye" tana kaiwa nan ta katse wayar.

Daren ranan Al'ameen ya kasa bacci se tunanin Zeezee yake besan ya zeyi ba ya
gyara tsakaninsu yasan koda ze had'a sama da k'asa 'yan office nasa baza su barsa
ya koma gida ba. Haka nan tun daga ranan idan ba wai Al'ameen neba ya kira Zeezee
ita bata d'aukan waya ta kirasa. She is damn missing him har wani rashin lafiya
rashin sa ke sata but she can't help it ta kasa gane dalilin da zesa yayi ta mata
k'arerayin da ya mata, meya miyar da ita? Doll baby? koda tace zatayi believing
abinda ya fad'a mata seta kasa. Sunyi haka na two more weeks Al'ameen da k'yar ya
samu ya kar6a break bayan k'aryan daya musu na cewa matarsa batada lafiya nan ma
one week break kad'ai ya samu da k'yar. Sam be sanar da Zeezee ba yanason suprising
nata. A ranan da ze taho da safe ya kirata dan su gaisa. Seda call d'in ya kusa
yankewa ta d'aga "hello Ya Al'ameen?"
"Na'am My Princess ina kwana?"
"Ina kwana Ya Al'ameen?"
"Lafiya ya kike? Ya Little Princess d'ina?"
"We are all good."
"Leg cramps sun dena?"
"Da sauk'i yau."
"I miss you Princess, I miss your crazy talks, your smile I miss everything, I
promise to make it up to you."
"Uhm ya aiki?"
"Na gaji da shi I want to come back to my Princesses."
"Ina d'an aiki kad'an will call you up later." Zaune take a d'aki tana buga
candy crush amman take cewa tana aiki.
"Princess haka kike avoiding d'ina yanzu?"
"Ba avoiding naka bane inason in k'are aikin da naken ne, ga baby se kicking yake
gabad'aya ya dameni."
"Awcch! Sorry Princess, just some months to go finally zamuyi meeting Little
Princess namu."
"Allah ya kaimu."
"Ameen Habibtee."
"So sena kira ka anjiman."
"I love you so much."
"I know se anjima" tana kaiwa nan ta katse.

Cikin d'an k'ank'anin lokaci hadari ya had'e a garin Abuja gashi dai-dai time na
flight na Al'ameen kenan noway jirgi ze iya tashi. Driver'nsa dake Abuja yayi wa
magana akan ya taho zasu tafi by land. Driver ya rasa why Al'ameen is so desperate
haka, mostly rananda wheather bashida kyau yana fasa tafiyan amman wannan karan ba
yadda beyi da Al'ameen ba yak'i jinsa. Haka suka d'au hanya wajajen k'arfe hud'u su
Al'ameen suka shigo su garin Bauchi.

*****4:30pm Zeezee na zaune a parlour ta baza agwalu6a a gabanta se sha take da


book akan cinyarta tana karatu ta jiyo rurin wayarta. Ganin Al'ameen taji kaman ma
kar ta d'aga har yanzu bata hushe ba ita, sanda ya kusan tsinkewa tayi picking up
"hello Ya Al'ameen?" Jin different voice from na Al'ameen ya sata cikin duhu.
"Please ina magana da matar me wayan nan ne?" Ba k'aramin rud'ani ba question
na mutumin ya jefata.
"E... eh itace matarsa ce."
"Toh Madam please ki kwantar da hankalinki ki taho Teaching Hospital yanzu."
"Teaching hospital?" Ta zabura tana zaro ido a yayinda cikinta yake mugun
d'aukan ruwa. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Teaching hospital? Meya same sa
please? Teaching hospital na wani gari?" Take ta shiga zubda hawaye.
"Na nan garin Bauchi."
"Bauchi? Ba a Abuja yake ba? Bawan Allah anya kuwa ka gane da wayan wa kake
magana? Ya Al'ameen miji na fa a Abuja yake ba a Bauchi ba."
"A hanyarsu na tahowa Bauchi yau ko ince bayan shigowansu Bauchi a bayan gari
armed robbers suka yi attacking nasa da driver'nsa. Shi mijin naki sun har6esa-"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta fad'a tare da katse sa, "Ya Al'ameen!"
Tasa wani irin d'ankaren ihu na bakin gate na iya jiyota. Kawai ji tayi jini na bin
k'afafunta tsabagen kalan tashin hankali da tsan-tsan masifan data tsinci kanta a
ciki. Se k'aran fad'uwan abu kukeji a k'asa rigijib! "Hello? Hello?" Mutumin ketayi
amman ba response kasancewar sumewan da Zeezee tayi. Sakamakon ihun da tayi yasa
Sadeeq shigowa don tabbatar da ko lafiya knocking ya tayi bisa k'ofan jin ba
response kawai ya fad'a ciki nan ya samu Zeezee cikin pool of blood a sume. Da gudu
yayi kanta tsoron ta6ata ma yake ganin he is running out of time yasa kawai ya
cinci6eta se Teaching Hospital achan aka shiga bata taimakon gaggawa don stopping
bleeding d'in before yayi affecting baby'n nata. Kafin nan kuma Sadeeq ya kira
layin Al'ameen inda yata ringing ba a d'aga ba. Mota ya shiga ya wuce gidansu
Zeezee inda yake sanar da Mama halin da ake ciki. Nan da nan tasa hijabinta suka
fice kwata-kwata basuda labarin halin da Al'ameen yake ciki.

_30 more minutes..._


K'ofan d'akin da Zeezee ke ciki ne ya bud'u revealing a Dr da sauri Mama tayo
kansa. "Dr how is she?"
"Calm down Ma'am she is fine ki kwantar da hankalinki."
"Alhamdulillah! Baby'n nata fah?"
"Both the Mother and child are fine, mun samu munyi stopping bleeding d'in before
it went any far yanzu ma zaki iya shiga ganinta."
"Alhamdulillah! Alhamdulillah! Thank you Dr Allah ya biyaku."
"Ameen excuse me please." Bata kai da shiga cikin d'akin ba Sadiq ya iso gun yana
gudu yana hak'i. "Hajiya! Hajiya" Chak ta tsaya tare da kewayowa.
"Sadeeq lafiya?" Kai zallah yake kad'a mata "Hajiya I just received a call."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


*ZAIMEEN flames🔥🔥🔥*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣2⃣

"Call daga wa kenan?"


"Daga colleague d'ina regarding Boss."
"Boss? Wani Boss kenan?"
"Your in-law mijin Madam."
"Kana nufin Ya Al'ameen? Meya samesa?" Tayi maganan cikin tsan-tsan tashin
hankali.
"Hajiya Boss is in a very critical condition, yanzu na gano dalilin dayasa Madam
ta sume, a hanyan dawowansa yau daga Abuja 6arayi suka taresu suka gudu da motanshi
suka kuma har6esa kusa da heart nashi Driver'nsa kuma suka mai d'ankaren duka yanzu
duk haka suna nan a Teaching Hospital a emergency ward."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, what?! Da wanne zanji yanzu? An shiga da Ya
Al'ameen d'in OR ne?"
"Eh Hajiya."
"Innalillahi! Ka samu dama ka gansa kai?"
"Yes Hajiya he is in a very critical condition he is bleeding through
everywhere."
"Subhanallah! Allah ya bashi lafiya Allah ya fito dashi yasa ayi a sa'a bari na
leqa Zeezee mu koma chan d'in." Nan da nan ta shiga d'akin Zeezee inda ta tarar da
ita se aikin kuka take. A gefenta ta zauna tare da had'a musu hannayensu. "Sannu
Mama na sannu, ya jikin?" Kai zallah Zeezee ta gyad'a mata "Mama ina Ya Al'ameen?
Please tell me its not true tell me ba a har6esa ba, and also my baby please tell
me banyi miscarrying baby na ba. I can't afford to lose my family" tayi maganan
cikin kuka sosai.

"Zeezee ki kwantar da hankalin ki please kinga kema ba lafiya kike dashi ba,
baby'n ki na nan lafiya ba abinda ya samesa."
"That's not true Mama kawai kina fad'a min ne."
"Am not lying to you Zainab ki ta6a cikinki kiji your baby is fit." A hankali
ta aza hannunta kan cikinta cike da fargaba, feeling bomb d'in yasa taji d'an sanyi
a ranta "Ya Al'ameen fah? Please kar ki gaya min ya mutu Mama." Kuka take sosai,
hugging nata Mama tayi "shhh! Its okay please anyi OR dashi in shaa Allah he is
going to make it muyi mishi addu'a kawai."
"A ina suka har6esa Mama?"
"Zainab-"
"Please answer me I need to know."
"Zai-"
"Mama please I beg you" ta k'ara rushewa da kuka.
"A kusa da heart nasa ne Zainab."
      "Innalillahi! Mama I killed my Husband, na kashe Ya Al'ameen."
  "Kaman ya kin kashe sa Zeezee? Armed robbers su har6esa kice ke kika kashe sa."
  "Mama its all my fault, about 3 weeks now kullum ina cikin fushi dashi I failed
to believe him daya cemin he wasn't cheating on me, I killed him also." Sake
hugging nata Mama tayi "shhh! Ya Al'ameen be mutu ba kuma in shaa Allahu baze mutu
ba kinji? Mu mushi addu'a kawai."
    "I can't afford to lose him Mama."
  "You won't in shaa Allah Zeezee, ina zuwa bari inje in duba shi."
   "Zan biki."
  "Kaman ya zaki bini Zeezee? Kema bakiga gado aka baki ba."
   "I don't care about myself Ya Al'ameen is all I care about."
"No Zainab ba inda zakije kina nan so kike kije kiga condition da yake ciki abu ya
samu lafiyan abinda ke cikin ki?"
  "Mama please karki hanani ganin Ya Al'ameen please."
  "Zainab-"
  "Please Mama." Hannu Mama tasa ta share mata hawayen nata sannan a nitse ta
mik'ar da ita suka shiga takawa har suka isa izuwa ward d'in. Sadeeq na ganinsu ya
miqe tare da basu waje don su zauna, "Sadeeq ina Ya Al'ameen?" Zeezee ta tambaya in
a cracky voice. K'ofan d'akin kawai ya nuna musu "basu fito ba har yanzu?" Asked
Mama.
  "Eh har yanzu."
   "Sadeeq how bad is his condition? Please karka min k'arya." Zeezee ta tambaya.
  "Critically bad, acikin jini suka wuce dashi he seemed so lifeless." Kwanciya
kawai Zeezee tayi jikin Mama tana kuka sosai da k'yar suka zauna har anan Zeezee ta
kasa barin kukan da take yi. Hajiya Babba ne ta kira Mama inda take tambayarta ya
jikin Al'ameen nata, ana ruwa a KD bazeyi ta shigo ba please a kula mata da
yaronta.
   "In shaa Allah Mama Babba kibar kukan haka please addu'ar mu kawai yake
buk'ata."
  "Nagode Maman Zeezee Allah yabar zumunci."
  "Ameen ki gaida Hjy Sadeeyah."
  "In shaa Allah zataji, nima ki gaishemin Zeezee da jiki please ta kuma kwantar da
hankalinta kar abu ya samu lafiyan d'an nata."
  "In shaa Allah zan gaya mata sannu."
  "Yauwa sannu se anjima."

   Few minutes more k'ofan d'akin da Al'ameen ke ciki ya bud'u. Kusan a tare suka
dosa gun duk tashin hankali bayyane a fuskokinsu karara. "Dr how is he?" sukayi
maganan dukansu uku in unisons.
   "Kune family'nshi?"
  "Eh" Mama ta amsa.
  "Am his wife and this is my mother" Zeezee tayi explaining "so tell me how is my
husband doing inside there please, karku cemin ya mutu don Allah."
  "Zainab calm down please" cewar Mama.
   "Kuyi hak'uri amman bazan 6oye muku wannan lamari ba. Mijinki is in a very
critical condition rai a hannun Allah yake, mude munyi abinda ya kamata bullet a
cardiac walls ba abu ne ba na wasa. Mun samu mun cire bullet d'in amman har yanzu
pulse nasa is not responding ya tsaya gu d'aya baya picking."
   "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Suka ambata a tare. Rushewa cikin wani
irin kuka me tsuma zuciya Zeezee tayi tana sumbatu tana ta kashe mijinta a yayinda
Mama ke calming nata down. "Kuyi hak'uri kuyi mishi addu'a wala Allah ko zuwa nan
da gobe pulse nasa yana iya dawowa idan be dawo ba kuma... I'm sorry."
   "No! No! No! Please this can't be true it can't be. Ya Al'ameen can't die don
Allah Dr do something baku iya aikinku bane da zaka cemin sorry? Kana nufin mutuwa
zeyi kenan? Kasan ko waye shi? He is my husband the father to my unborn child,
banason d'a na yayi witnessing a day without a father please you've got to do
something and save him he can't die."
  "Kiyi hak'uri Ma'am I know how it feels amman ba abinda zamu iya ne, munyi duk
abinda ya kamata sauran mun bar wa Allah."
   "No there is still something missing-" katse ta Mama tayi "thank you Dr mungode
Allah ya biya."
  "Ameen excuse me please zaku iya shiga ganinsa." Har k'asa Zeezee ta sauk'a Mama
na tarota tana kuka sosai. "He can't die Mama he can't yanzu shikenan baby na ya
zama maraya kenan?"
   "Wayace miki ya zama maraya Zainab? Ce miki akayi Ya Al'ameen ya rasu? Yana nan
da ransa fatan mu Allah tashi kafad'an shi, ki shiga ki gansa kinji?"
  "I can't Mama bazan iya kallonshi acikin wannan critical condition d'inba sanin
ba abinda zan iya masa I can't."
  "You have to Zainab, Ya Al'ameen bayida kaman ki go inside kije ki gansa."
  "Please Mama."
  "Go Zainab jeki gansa." Jiki ba k'wari ta mik'e tsaye a hankali ta shiga takawa
har ta isa cikin d'akin. Kasa juyawa ta kallesa tayi se hawaye kawai take
unstoppingly. Da k'yar sannan ta iya ta juyan, sight nasa data gani dad'a mata
volume na kukanta yayi, sosai guiwowinta suka shiga shaking har ta k'arasa kan
gadon nasa. Oxygen supply nasan ta aza shaking hands nata akai sannan back to
gashin kansa tana shafawa soothingly. Duk kalan treatement and bandage da kan ciwon
nasa yasha be hana jini fita ba har yanzu, just how much have he suffered? In a
cracking tune tayi stating "I'm so sorry Ya Al'ameen, I'm terribly sorry I should
have believe you when you told me you weren't cheating on me, I'm terribly sorry
please don't die kar ka tafi ka barni I need you, I love you our unborn child needs
you please don't go." D'ayan hannunsa da babu connections jiki ta d'aga ta had'a da
nata tana shafawa a hankali "please kar ka tafi Ya Al'ameen" a hankali ta aza
hannun nasa akan cikinta, kaman baby'n nasu na jinsu se yayi kicking. Hakan ba
kad'an yasa Zeezee kuka ba. "See? Our baby needs you, kar ka tafi ka barshi please
you need to wake up." Kuka ta cigaba da yi wajen tana shafa gashin kansa a hankali.
Chan ta d'ale gadon tare da kwanciya dage gefensa ta had'a musu hannu a haka har
tafara bacci itama.

Jin shiru Mama ta gwada lek'asu inda ta tarar da Zeezee kwance a gefensa tana
bacci. Murmushi tayi at their site sannan tace "Allah baka lafiya Al'ameen Zainab
loves you so much." A nitse ta miyar da k'ofan taje ta samu Sadeeq ya kaita gida
inda ta taho masu da abinci tasan sarai Zeezee must be hungry.
2 hours sleep Zeezee ta samu a gefen Al'ameen nata ta tashi. Se gani take as if
idan ta kirashi da Sweetheart ze amsa ta cikin zazzak'ar muryansa yace mata My
Princess, she is missing him over. Hawayen dake neman gangarowa kan cheeks nata ta
tare da wuri "you've once told me to believe in our love, you promised to never
give up on me Ya Al'ameen and I will be holding on to that promise nasan bazaka
tafi ka barni ba please wake up." Ko motsawa beyi ba ga pulse nasa na nan yana
hanging tun d'azu. "Sweetheart please wake up ko finger ne kamin shaking ko
hankalina ze d'an kwanta wallahi idan ka tafi bazan iya rayuwa ba. I can't bear the
thought that nice silar mutuwan Baba and now yours dan Allah karka min haka Ya
Al'ameen I need you to wake up, wake up please." Suratan ta cigaba dayi tana kuka
har Mama ta shigo d'akin ta tsinceta.
"Yo! Zainab kin tashi kuma a maimakon kiyi sallah kike zaune gun har yanzu?"
"Mama he is dying and I can't do anything to save him" ta fad'a cikin kuka sosai.
"Ya Salam Zeezee" tayi maganan tana k'arisowa gefenta. "Kibar magana haka don
Allah, waya ce miki mutuwa zeyi? In shaa Allahu ze tashi."
"Mama da ze tashi da yayi, ba irin suratan da ban mishi ba he is not responding,
duk ni ne, laifi nane. A kullum baya bin land se air amman nata tada mishi
hankalinsa har seda ya gommaci yayi risking life nasa haka. Am very stupid to think
that Ya Al'ameen will eve cheat on me, be kamata na sak'a mishi da haka ba despite
all abubuwan da yayi min a baya. Da be biyemin ba ya cigaba da zamansa achan."
"Bayan yadda kike tada mishi hankali Zainab? Sadeeq told me everything yakamata
kina yima Maj-Gen uzuri kisani shima fa bawan Allan nan ba a son ransa yake tafiyan
nan yake barinki ba, har ace ya kira Sadeeq yace ki amshi waya ki k'i Zainab? Haba
mana! Dole hankalinsa ya tashi yace ko ta motan ne ze biya just to make you happy."
Wani kukan Zeezee ta sake rushewa dashi "Mama please karki ga laifi na sonsa da
nakeyi ne yasa bana iya juran rashinsa a kusa dani, kinfi ni sanin hakan tunda
mutuwa ya d'auke miki Baba. But wallahi I hate myself right now koda missing nashin
da nake be kamata ina nuna fushi na akanshi ba saboda be dawo min ba kamata yayi in
rik'e aciki."
"Exaclty Zainab."
"We all learn from our mistakes in shaa Allahu zan gyara daga yau, Ya Al'ameen
poor thing" tayi maganan tare da miyar da kallonta kan lifeless Al'ameen. "Mama I
killed My Soldier."
"Kika sake cewa kin kashe shi zan sa6a miki kina jina ko? Tashi kije kiyi alwala
kiyi Sallah na kawo miki abinci."
"Toh nagode." Bayan ta idar da Sallan Mama ta sata cin abincin dole ta gama
sukayi zaman amsan gaisuwa ta waya, se kira mutane suke sunayi wa Al'ameen fatan
samun waraka.

Ko wani minti-minti idon Zeezee na akan Al'ameen tana son taga first move nasa
amman har ta gaji da checking on him be motsa ba, hakan ba k'aramin sake karya mata
zuciya yayi ba. Idan Al'ameen ya mutu ina zata sa kanta? Nowhere. Da misalin k'arfe
tara Zeezee taje ta samu Mama a wajen corridor, "Mama bazaki tafi ba dare fa yayi,
bari inma Sadeeq magana ya mai dake gida."
"Are you sure Zainab zaki iya kula da kanki da kuma Ya Al'ameen kema fa kinsan
bakida lafiya I was thinking I should spend the night with you."
"Ayyah no need, I'll manage Mama you've done so much for me, please kije ki
huta."
"Toh shikenan duk abubuwan da zaki buk'ata akwai anan?"
"Eh nasa Sadeeq ya kawo min d'azu."
"Okay toh Allah bashi lafiya kuma kibar kukan haka nan kema ba ishasshen lafiya
gareki ba."
"In shaa Allah Mama thank you." Har wajen mota ta rakata sukayi sallama sannan ta
dawo ciki ta canza kayanta zuwa na bacci sannan a hankali ta d'ale gadon ta kwanta
gefen Al'ameen, hannunsa ta d'aga tare da azawa kan cikinta kamar yadda ya saba yi
idan zasu kwanta. Tana hawaye tsilli-tsilli har bacci yayi awon gaba da ita.

Abu fa kaman wasa har washegari pulse na Al'ameen be soma beating ba, kuka kam
Zeezee ta shasa kaman ba gobe. Da misalin k'arfe 7pm Mama ta kira Zeezee wanda da
k'yar ta iya picking saboda yadda kuka yafi k'arfinta. "Assalamu Alaikum Zainab?"
"Wa alaikumus salam Mama" ta ansa da k'yar cikin kuka.
"Subhanallah Zeezee meke damunki ne wai? Kuka kike har yanzu?"
"Mama he is dying his pulse is not picking up har yanzu, please do something
bazan iya rayuwa ba shi ba."
"Lets have faith Zainab in shaa Allahu ze tashi. Kibar kukan haka please, kinji?"
"Uhumm."
"Ki turo Sadeeq ya amso miki breakfast."
"Bana jin yunwa."
"Idan ke bakiya ji d'an naki naji kice Sadeeq yazo ya kar6a miki kinji? Kuma ki
dage kici koda kad'an ne."
"Toh nagode."
"Yauwa zuwa anjima zan shigo."
"Sekin zo." Anan sukayi sallama. Kallonta ta miyar kan lifeless looking Al'ameen
ji tayi tana sake tsanar kanta, yanzu saboda he just wanted to make it up to her
shine yayi sacrificing life nasa? Why is he to good?

Wajajen 9am Dr da kansa yazo ya duba Al'ameen yake sanar da ita ba any
improvement tattare dashi his pulse isn't beating har yanzu. Kuka ta shiga yi musu
a wajen tana had'asu da Allah da su ceto mata ran miji. Har Mama dasu Lubiee suka
zo suka koma still Al'ameen be motsa ba KD har yau weather isn't clear su Mama
Babba
basu samu tahowa ba.

***
Bayan sallan La'asr Zeezee na zaune akan sallaya se faman addu'a take tana kuka
taji pulse machine d'in yayi making sound da hanzari ta miyar da kallonta wajen to
her biggest suprise taga daga 40 ya buga ya dawo 39. Meh hakan ke nufi? Mutuwa
kenan Al'ameen nata zeyi? Abinda ya kamata yana gaba-gaba taya zeyi baya? "Nurse!
Nurse!" Ta sa ihu da iya k'arfinta har seda tayi drawing attention nasu a lokacin
pulse d'in har ya sauk'o zuwa 34.
"Nurse what is wrong with him please? Meyasa pulse nasa yake decreasing instead
yayi increasing? Don't tell me he is dying please."
"Sister please take her out" cewar Nurse d'in wa 'yar uwarta. In a minute Dr ya
iso yana sanya gloves a hannunsa.
"Take her out please" ya buk'aci nurses d'in. "Ma'am we are sorry."
"Ma'am please lets go." Cewar nurse d'in.
"No I'm staying here tun jiya kuyi mishi abinda ya kamata kun k'i seda kuka ga ya
kusa mutuwa zaku nemi basa taimako? What is wrong with y'all people ko bakusan
aikin ku bane? Mijina ne fah."
"We are sorry Ma'am lets go outside please." Da k'yar aka samu aka jata waje inda
take leqe ta window tana kuka sosai. Se sauk'a pulse na Al'ameen yake har izuwa 17.
Pulse Dr ya shiga basa sede inaa heart nasa yak'i beating se ma dad'a decreasing da
pulse d'insa ke. Kusan sau uku sunayi ba improvement sukayi giving up finally.
Ding-ding pulse machine yake bugawa 7.. 6.. 5.. 4.. 3... 2..1. Se ya d'auke. Wani
irin ihu Zeezee ta k'urma seda ta jawo attention na kowa a arean gun.
"Ya Al'ameeeennnnn!!!"
"Time of death 4-" Dr be kaiga k'arisa karance time d'inba Al'ameen ya kad'a
index finger'nsa kad'an wanda Zeezee tagani da idonta. Pulse nasa ne kuma ya shiga
beating fast-fast ding-ding 1.. 5.. 9.. 10.. haka ya cigaba dayi to everyone's
suprise. Zeezee na hawaye tana murmushi all at thessme time sanda ya kai 99 sannan
yayi stopping. Wani hamdala ta saki tana murmushi, ta window'n Dr'n ya d'aga hannu
yayi mata thumbs up. Drip suka sa mishi sannan suka cire oxygen supply d'in, nishi
yake a hankali sede har yanzu be bud'e idonshi ba.

"Am so happy for you Ma'am your husband's condition is now stable." Dr Ya sanar
da ita yana cire gloves na hannunsa alokacin daya fito daga d'akin.
"Thank you Dr, thank you so much I won't forget this."
"You're welcome."
"Zan iya shiga ganinsa?"
"Why not excuse me please." Yana ficewa tasa kai cikin d'akin inda a hankali taja
kujera ta zauna gefen Al'ameen tana k'are wa kyakkyawan fuskansa kallo. Fingers
nasu tayi interwining a yayinda hawaye ke forming rapidly a idonta. Miqawa tayi
tare da kissing forehead nasa.
"Thank you for choosing not to leave me My Soldier, da ka tafi da bansan ina
zansa kai na ba. Thank you for keeping your promise with me, I can't ever repay
you. I love you so much please shake a finger for me again." Hannunsa ta tsaya gani
amman ko motsawa beyi ba.
"Sweetheart idan har KAN TARE DA NI please shake a finger again, just a finger
kaji? Your Princess loves you so much, I'm here, I'll never leave your side because
I love you so very much, just shake a finger for me its all I need now." Idanunsa
taga sun d'an motsa kad'an kaman ze bud'e se ya sake miyar dasu, hakan ba k'aramin
farin ciki ya sanyata ba. "I know you'll never fail me My Soldier" a hankali ta
miqa ta sake kissing forehead nasa in the process drop na hawayenta ya d'iga akan
idonsa kafin tasa hannu tace zata goge taga a hankali Al'ameen na bud'e idonsa har
ya bud'esu gabad'aya yayi setting nasu akan fuskanta. Even though blurred images
yake kalla hakan besa yayi noticing ramewan da Zeezee tayi ba in just a day.

"My Soldier!" ta furta unbelievably tana hawaye sosai, "My Soldier you're back!"
Kwantar da kanta tayi bisa chest nasa ta inda ba a har6esan ba tana kuka sosai.
"I'm so sorry Sweetheart, I'm terribly sorry for making you pass through so much
pain like this ka yafemin please." Cikin wani irin dishasshiyar murya kaman ba nasa
ba ya furta "Princess" a hankali. A take ta taso tana kallonsa "I'm so sorry
Sweetheart." Kai ya kad'a mata "cry nomore" hannunsa ta side dake da lafiya ya
d'aga a hankali ya shiga share mata hawayen nata. Kallonsa kawai take amman ta kasa
dena kuka.
"Why did you do it Sweetheart? Mesa baka hak'ura ba se idan wheather ya gyaru ka
taho ba? Why do you have to risk your life like this?"
"Because I want to make it up to you Princess, banason inji kina cewa I am
cheating on you, I'll never cheat on you Zainab ke kad'ai nakeso and no one else.
Ranan da kika fara cemin I was cheating on you kasa bacci nayi ranan, I can't bear
the thought that na baki room na zargi na, can you please believe me yanzu that am
not cheati-" yatsan ta tayi sauri ta aza akan lips nasa shutting him. Cikin tsan-
tsan hawaye tana me nadaman abubuwan da tayi wa Al'ameen tace, "I'm terribly sorry
Ya Al'ameen, please ka gafirceni for acting childish to you. I should have believed
you da kace min you weren't cheating on me I'm sorry I just couldn't help it, it's
because I love you so much, se gani nake like kana min wasa da hankali ne da kake
ta cemin zaka shigo amman baka shigowan."
"I'll never do that to you Princess I love you eternally it just that na kasa
bringing kaina in sanar dake halin da na tsinci kaina a ciki ne, meya sameki kika
fad'a haka are you sick?"
"Ya Al'ameen I thought mutuwa zakayi ka barni" tayi stating hawaye na forming a
idonta. "Pulse naka gabad'aya yabar beating I couldn't help it bazan iya rayuwa ba
kai ba."
"I'll never leave your side in shaa Allah kibar kukan haka kinji? Am here for you
and for our little Princess and more to come Baby machine." Murmushi kad'an ta mar;
"Thank you for not leaving me." Murmushin dake fuskarsa taga ya gushe, da sauri
ta tanbayesa "Ya Al'ameen is everything okay?"
"Princess sun tafi da motan, I shopped for you and my Little Princess I thought I
might suprise you sun tafi da kayakin, I'm sorry."

*MIEMIEBEE. TEAM #YGC!🎀*


*ZAIMEEN flames🔥🔥🔥🔥*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣3⃣

"Sweetheart I don't care about that all I care about is you, bazan iya kwatanta
maka kalan farin cikin da nake ciki ba yanzu. This is like your second life saboda
you nearly died, and for this I am renewing my vows to you. Na farko I promise
bazan sake zarginka ba saboda I trust you fiye da yadda na yarda da kaina, secondly
bazan sake tada maka hankali ba ko nayi maka kuka ko zuciya saboda baka dawo min
gida hutu ba nasani kaima ba a son ranka kake tafiyan ba. Thirdly bazan sake
posting pictures naka a snapchat ba, and lastly I will love you like there's no
tomorrow, I'll take care of you with all that I got, I'll cherish our love with
care, compassion and seal it with trust. This is just how much I love you."

Murmushin dole ya k'irk'iro "thank you Princess and In shaa Allah I will
never betray your trust, I love you even more." A hankali ta kwantar da kanta bisa
d'ayan gefen chest nasa "our Little Soldier missed you so much kullum cikin kicking
d'ina yake where is daddy where is daddy."
"Little Princess de."
"No Soldier ne."
"Time shall tell, so tell me meya sameki haka kika rame? Am sure ba tension d'in
gudun rashina bane kawai."
"Seriously shine Sweetheart."
"Princess!"
"Promise you won't freak out koda na gaya maka" tayi maganan tare da d'ago kanta
a hankali tana kallonsa.
"Okay I promise."
"Are you sure?"
"Come on Princess."
"I nearly miss carried our child b-"
"What!" Yayi exclaiming "Princess taya ya? Me kikayi aiki ko?"
"Oh God! Sweetheart you promised baza kayi freaking out ba."
"Na karya promise d'in little Princess d'ita ce fah, aiki kika tayi koh?"
"Sweetheart ba aiki ban-"
"Aiki ne na sani" ya sake katse ta.
"Ba aiki bane da aka kirani aka sanar dani cewa you were attacked ne shine gabana
ya fad'a trust me ba aiki bane yamin yawa."
"What of now is the baby's condition stable?"
"It is."
"How sure are you Princess? Taya zan yarda ma."
"Kawo hannunka" a hankali ya d'aga tasa a nata sannan tayi placing akan bare
cikinta, "ka tsaya kaga soon enough zeyi kicking."
"In batayi ba kinsan da akwai matsala ko?"
"Zeyi ju-" kicking da baby'n yayi ya hanata k'arisa maganan data fara.
"See I told you" ta sanar dashi tana dariya.
"How adorable I can't wait to finally meet my Little Princess."
"Nikuma a sani a trash can ba."
"Habba! Princess kece root d'in happiness d'ina kinsan there's no how zan saki a
trash can."
"I love you" a hankali tayi pecking cheeks nasa "bari in kira Mama in sanar da
ita ka farfad'o and Mama Babba also daman da yau sun taho amman wheather condition
ba kyau."
"Ayyah ba amfani ai tunda ba mutuwa nayi ba I'll call her up ince mata su fasa."
"Kabarsu mana ai kad'an ya rage baka mutun ba kai naji tsoro Sweetheart I can't
imagine life without you na rasa Baba banjin zan iya rasa most beloved male person
again a rayuwa na."
"I am here for you Princess" ya sanar da ita affectionately.
"And I appreciate that My Soldier." Nan da nan ta kira Mama ta sanar da ita harma
ta had'asu wayan suka gaisa haka ma sukayi da Mama Babba, ita kam dan murna har
kuka sanda tayi duda hakan tace zata shigo gobe amman Al'ameen ya hanata baya son
tazo ta wahala saboda ko tazo ma ba abinda zatayi Zeezee can take care of him. Da
k'yar ya iya convincing nata ta yarda kan bazata zo d'inba.

Dinner me rai da lafiya Mama ta kawo musu da kanta suka sake gaisawa da
Al'ameen tayi masa ya jiki. Bayan tafiyan ta Zeezee tayi assisting Al'ameen yayi
wanka sukayi alwala sannan sallah ta zuba musu abinci da kanta take serving nasa
har suka gama ci yasha anti-biotics nasa. Kayan baccinsa tayi assisting nasa yasa
sannan tasa nata itama tayi shimfid'a a k'asa zata kwanta da wuri Al'ameen ya
tsaidata.
"Princess me kike shirin yi haka?"
"Zan gyara wajen kwanciya na ne."
"Nan kuma fa?" yayi nuni da gefensa.
"Sweetheart naga baka da lafiya I don't want to be a burden to you kuma kasan
yanayin kwanciya na."
"I still don't care Princess taya ni zan kwanta akan gado ke da kuma little
Princess d'ina a k'asa its not possible zo mu kwanta."
"Come on Sweetheart its nothing kar ka damu I can manage down here."
"I insist Princess kizo mu kwanta anan, I miss you, I miss your arms and legs
wrapped around me kinji? Zo mu kwanta." One last look and smile ta masa sannan ta
kashe musu wuta a hankali ta taka taje ta kwanta a d'an space dayayi creating mata
suna sharing same pillow.
"Princess?"
"Na'am My Soldier."
"Yau haka zamu kwana?"
"Is something missing kana buk'atan wani abu ne? Tell me."
"I miss your head on my chest, nafison inyita shak'an k'amshin shampoo na
gashinki har inyi bacci." Dad'i sosai taji ta shiga blushing "is that so My
Soldier?"
"Yes Princess place your head over my chest."
"Sweetheart ka manta akwai ciwo ne a wajen yanzu? Banason in fama maka."
"You won't ai ta side da babu ciwon ne zaki kwanta please do, I miss everything
about you." Ba gardama ta aza kanta bisa k'irjinsa a hankali tare da aza hannunta
kan cikinsa. "Thats My Woman" ya fad'a tare da zagayeta da d'ayan hannunsa shima.
"I love you Sweetheart."
"And I love you more lets sleep." A hankali beautiful sleep yayi taking over
control nasu duka.

Washegari ko school bata fita ba saboda kula da Al'ameen da take, breakfast


kala kala daga gun masu kawo gaisuwa suka samu se wanda Zeezee ta za6a. Ba k'aramin
kishi tajiyo ya tokareta ba dataga nurse tazo yiwa Al'ameen dressing ciwonsa ba
abinda yafi bata haushi kamar yadda hannun nurse d'in ke ta6a naked body'n Al'ameen
nata. Don tsan-tsan kishi tasa hankali taga yadda nurse d'in ke dressing d'in ta
kuma k'udurta a ranta cewa next itace zatayi wa mijinta. Taso ace a sallamesu a yau
amman hakan be yuwu ba sede gobe inji Dr'n. A d'akinsa suka yini ranan se hira suke
suna telling juna just how much they missed each other and kissing each other away
like there's no tomorrow. A washegari da Nurse tazo dressing Al'ameen Zeezee ta
amshe tray d'in daga hannunta ba shiri. Da mamaki both Al'ameen da Nurse suka tsaya
kallonta "sorry Ma'am excuse me zanyi mishi dressing ciwon sa ne."
"You are excused" Zeezee ta juyo cike da rangwad'a tana sanye cikin wani purple
strapless silky gown daya mugun amsanta. Ta kama gashinta a tsakiya jelan na yawo.
"Na iya I'll dress my husband myself." Murmushi Al'ameen ya saki don tun jiya da
nurse d'in ke dressing nasa ya lura da kalan kallon da Zeezee keyi mata, Zeezee'nsa
kam bade kishi ba.
"But Ma'am-"
"Let her please ta iya she can dress me" Al'ameen ya fad'a giving no room for
arguement. Shegiya nurse sam bataji dad'i ba tafison tayi masa saboda tana ta6a
muscles nasa indirectly. Wani haushi Zeezee ta jiyo kan ta mutu, ba yadda ta iya
tace, "thank you" tare da ficewa. Seda ta rufo k'ofan Zeezee ta kawar da kanta daga
gun tare da furta "shegiya snaatcher kawai" ai kuwa se kunnen Al'ameen. Ba yadda
beyi ba don basarwa ya had'iye dariyan nasa amman ya kasa. Sosai ya tsaya yana
dariya har gun ciwonsa na mai zafi amman ya kasa yayi shiru, adorably kuma cike da
haushi Zeezee ta tsaya tana kallonsa da ace wani mumuna ne da tuni ta juma da
sauk'e haushinta a kansa. Although dariyan nasa haushi ke bata but she still finds
him cute yadda dimples nasa suka lotse dakuma yadda perfect teeth nasa suka
bayyana.
"Eh kata dariyan kai kuma." In between laughter yace, "I'm sorry Princess I just
can't help it me tayi da zaki kirata da shegiya ita kuma, aikinta fa kawai take."
"Aikinta? Are you kidding me Ya Al'ameen? Kai bakaga yadda take rubbing hands
nata a jikinka bane? Lallai! Aikinta ko shafamin jikin miji ai kaga reaction nata
da nace ni zan maka."
"Uhm-uhm toh ke yanzu Princess kin iya ne?"
"I had to practice yestarday banason ana ta6a min kai anyhow."
"Ashe Princess ta iya kishi haka."
Bayan ta k'ariso gabansa ta ajiye tray d'in akan table tace, "nifa ban ta6a nuna
maka bane Sweetheart amman harta su Ayshah blood sisters naka ina kishi dasu I
don't know why but bana son inga kowa kusa da kai se ni sekuma baby'nmu" ta k'are
maganan both hands nata akan cikinta. Murmushi ya sakar mata tare da sake matso da
ita kusa dashi.
"You" ya nuna ta da yatsa "and our baby" ya aza hannunsa akan cikinta "completes
me, you don't have to get jealous don kin ganni dasu Ayshah, sister-brother bond
kad'ai ke tsakaninmu but deep inside nafi sonki fiye dasu fiye da kowa bayan Mama
Babba."
"I know right Sweetheart shiyasa nima nake sonka kaman zan mutu." A hankali yayi
kissing kan cikinta "I love you even more Princess."
"So are you ready to cry?"
"Cry kuma what for?"
"For the dressing, nasan ka da saurin kuka ga kuma yadda d'aye bandage keda zafi
ka dage kar kayi kuka kaji? Zan baka sweet."
"LOL" ya furta sa'annan ya tsaya dariya sosai "soldier'n? Soldier'n kike cema
rago Princess harda zaki basa sweet? Oh! Now I know the sweet you are talking
about."
"Wann- Kai Sweetheart!" Tayi exclaiming gano inda ya dosa "Baby na ya zama bad
boy, which sweet were you thinking of?" Gira ya d'age mata yana neman zaunar da ita
kan cinyansa, "oh come on karka d'au wannan spell d'in zeyi aiki a kaina fa, you
are sick seka samu sauk'i tukuna."
"Har yaushe kenan Princess?"
"As long as it takes I'll wait."
"Nikam I can't wait cause I missed you so much."
"Really?" Tayi maganan tana zagaye hannayenta a wuyansa. "You missed my legs
wrapped around you?"
"Seriously Princess nafi missing naki fa kawai bana nuna miki ne." Zama tayi a
hankali kan cinyansa "you know nafi missing naka atimes har kunya nakeji yadda bana
iya hak'ura da kai yadda nake tambayan hak'k'i na frequently."
"Shh! Princess don't talk like that we are husband and wife ba kunya a tsakaninmu
we are one and kinsan wani abu?"
"No tell me."

"Anytime kika cemin in baki hak'k'in ki or na gano kina buk'ata na kinsan how
you always make me feel?" A kunyace ta kad'a kanta. "I feel like the World's best
man ina gani like duk duniya ba wanda ya kaini iya komi ace a precious soul like
you is asking and is in need of me I feel like a King and hakan ba k'aramin k'ara
miki so yake a zuciya na ba anytime you ask me in bed son da nake miki alokacin is
like tears from the sky it never ends so kar kiji kunya na kinji? I love it anytime
you ask me, alokacin sha'awan ki ke building rapidly in me." Lamo tayi tana baza
ido a k'asa. "Kinji Princess?" A hankali ta gyad'a kai "so nima am asking you for
bed now I need you." Cike da kunya ta d'ago kanta tana kallonsa "Sweetheart you are
sick I don't want to stress you out mubari kad'an samu k'arfin jiki kaji? Don't
think saboda banyi missing naka ba nayi rejecting naka. Wa ya isa yace beyi missing
a lion as you ba, kasani saboda I want the best for you ne nayi hakan nasan koda a
yanzu mukayi mating we both won't enjoy ourselves kamar yadda ya kamata saboda
bakada k'arfi sosai, next time okay?"
"Okay Princess your wish is my absolute command, I'll patiently wait."
"I love My Man." A hankali yayi owning lips nata ya shiga kissing nata inda take
miyar mishi da martani, sun d'au tsawon lokaci suna abu d'aya sannan a hankali tayi
pulling out tare da kwantar da kanta bisa chest nasa. "A kowani heart beat d'ina
dad'a sonka nake Ya Al'ameen." sannan ta d'ago kanta "so are you ready to cry?"
"LOL Princess kinfa iya neman tsokana zan rama ai your labour time is coming."
"Ce maka akayi ni zanyi kuka a labour room? Kaide kar kayi kuka don nasan cire
bandage da akwai zafi especially masu saurin kuka irinsu Sweetheart."
"Hah! Zamuga ni dake wa zeyi kuka ma yanzu."
"Nine da ciwon da zanyi kuka? lallai ma!" Ta juya zata sanya gloves kenan a garin
haka ta buge cikinta jikin edge na table d'in da k'arfi.
"Arrrggghh!" Ta saki Kara cike da azaba tare da rik'e cikin nata a yayinda
hawaye ke forming rapidly a idonta. "Princess!" Al'ameen yayi maganan a rikice tare
da miqewa tsaye ya kama d'ayan hannunta data sauk'e daga kan cikinta ya zaunar da
ita kan gadon yana me mata sannu. Hawayen take har yanzu tana rik'e da cikinta,
"Princess sorry, am sorry please stop crying in kira Dr?" Dan azaba tama kasa amsa
sa seda taga ya miqe tayi sauri ta rik'o hannunsa "just stay with me" ta fad'a da
k'yar. Komowa yayi ya zauna a gefenta tare da kwantar da kanta akan laps nasa yana
shafa gashin kanta soothingly. "Sannu kinji?" A hankali ta gyad'a kai, sunyi about
5 minutes a haka sannan Zeezee taji pain d'in ya d'auke kad'an-kad'an take ji.

"Sure kar in kira Dr? Maybe kinyi hitting kan little Princess."
"No don't bother yabar min ciwo she'll be fine."
"Sannu kinji?" Hannunsa ya aza kan cikinta a hankali yana shafawa, da murmushi
kwance fal a fuskarta ta aza hannunta kan nasa. Seda ya tabbata she is back to
normal yace, "zaki kwanta in kira nurse d'in tamin dressing wound d'in?"
"No way ni zanyi maka."
"You are wounded Princess."
"No I'm not." Da taimakonsa ta miqe ta buk'acesa daya miqo mata tray d'in a
hankali ta shiga 6are bandage d'in itan da ba a jikinta ciwon ke ba amman itace
meyin awch! Wash! Kallonta Al'ameen ke yana murmushi bayan ta gama 6are bandage
d'in taga irin girman ciwon "omg!" Tayi exclaiming "Mutanen nan are so cruel, ji
yadda suka miyar min da chest na Sweetheart d'ina? Allah ze sak'a mana sannu kaji?"
Tayi maganan tana neman fara kuka.
"Princess you are not crying are you?" Hannu tasa ta share hawayen nata
"Sweetheart baka ga girman ciwon bane? It is worth crying."
"Ai nasani I told you se kinyi kuka, nikuma bana son ganin hawayenki zan kira
nurse in chan ta gama min kawai."
"Wallahi no way na gwammaci ina kuka inyi maka da wancan shegiyar ta ta6a min
kai." Nan ma dariya ta basa "Princess me tayi na ce mata shegiya kuma?"
"Ban sani ba" haka tana hawaye ta samu tayi mai dressing ciwon tasa sabon bandage
tayi sealing. "Thank you Baby Machine, I love you."
"I love you more get well soon. Yau zamu koma gida ba?"
"Yes Princess."
"Bari in shirya mana kayakin mu toh."
"Zan tayaki."
"No no way baka da lafiya rest yanzu zan gama okay?"
"Okay Princess" pecking nasa tayi a cheeks sannan ta miqe a hankali ta shiga
tattara musu kayakinsu. Da yanmacin ranan suka koma gida. Mutan arziki se kiran
Al'ameen da Zeezee suke a waya suna musu jaje wasu kuwa suna zuwa har gida ma. Next
call da Al'ameen yayi receiving ne sam be gane wace ba dan kuwa bashida ma lambarta
amman be wani damu ba saboda a tunaninsa jaje tayi mai kawai and thats all.
Washegari suna zanne a dining suna having lunch lamban ya sake kira kasancewar
wayan na a hannun Zeezee tayi sauri ta miqa mishi seda ya karance number'n yaga it
seems familiar. "Sweetheart won't you pick up?"
"Am doubting the number meshi ta kirani jiya ta gaisheni yau kuma fah?"
"Pick up kaji mana yi sauri." Da kalamunta yayi picking up amman besa a handsfree
ba Zeezee kanma harkan gabanta take tana tattara kan dining table. "Hello Ya
Al'ameen."
"Na'am" ya amsa sama-sama.
"Ina yini?"
"Lafiya" nan ma yace.
"Ya jiki kuma?"
"Alhamdulillah."
"Baka gane wace ba ko?"
"Yeah not really."
"Ayyah Khadeejah ce."
"Pardon? Khadeejah daga ina kenan?"
"Uhm... K'awar Zeezee."
"K'awar Zeezee? Kuma a ina kikayi picking digits d'ina?"
"Please kar ka damu ita ta bani nace mata zan yi maka jaje ne."
"Oh I see, Weren't you the one that called yestarday?"
"Eh nice."
"In jaje ne ai na jiya ma ya wadatar ko ba haka ba Khadeejah?"
"Eh hakane na kira in gaishe kane kawai yau."
"Are you also married?"
"Uhm..."
"I asked a question."
"Yes I am but-" katse wayan yayi karap a kanta dai-dai lokacin da Zeezee ke
fitowa daga kitchen kenan. "Har ka gama wayan ne?" Ta tambayesa.

"Princess come over" ya buk'aceta tiryan tiryan taje ta samesa ya zaunar da ita
bisa cinyansa. "Kinsan any Khadeejah?"
"Meya faru?"
"You'll know about it soon but answer me first."
"Okay inada about 4 friends Khadeeja's amman am in contact with two only sauran
tun secondary school rabuwan mu."
"Wacce da wacce kike tare dasu yanzun?"
"Well akwai Khadeeja Baffah ita batayi aure bama tana BUK tana karanta medicine
se da Khadeejah Saje ita kuma tana da aure anan garin Bauchi."
"Khadeejah Saje definitely" ya fad'a silently.
"Why ka santa ne?" Tayi maganan bewilderingly.
"Kinga number'n daya kirani anan?"
"Ehem" ta fad'a tana gyad'a kai curiously.
"She is your friend Khadeeja Saje, ta kirani jiya yau ma ta sake kira and she
told me ke kika bata digits d'ina." Ido da baki Zeezee ta bud'e to her ultimate
suprise "Khadeeja Saje!" Ta furta. Yarinyar dake da aure take neman mata miji?
Lallai akwai world war.
"I know thats not true."
"It is not Sweetheart nasha giya ne da zan d'au numbanka inbaiwa wata?"
"Abinda ya d'aure min kai kenan aina ta samu?" Bayan dogon nazari Zeezee ta
furta "omg! Sweetheart yarinyan nan munafuka ce, I can vividly remember everything.
Ina ranan nan da nace maka wata friend d'ina ta tambayen wai a ina nasami balarabe
innan?"
"Yeah uhumm..."
"So I saw tayi taking screenshots d'in picture nakan ta biyoni whatsapp tayita
yaba wa kyanka har na mata sending wani again ma nima dan sokanci. So se was it
last 3 weeks mukaje sunan wata friend d'inmu acan muka had'u tace na bata wayana
definitely anan shegiyar ta kwashi digits naka. Lallai she's messing with the wrong
bitch, Ya Al'ameen d'ina takeso?"
"God! Zeezee ni bance miki tana sona ba please."
"But alamu sun nuna ai, idan ba sonka take ba taya zata hau kiran ka frequently
haka? Wallahi se na nuna mata rijiya ba wajen wasan yaro bane, where is my phone?"
Ta miqe kenan Al'ameen ya sake zaunar da ita ta sake mik'ewa. "Sit."
"No am not."
"Princess sit."
"No."
"I said sit Princess" ya fad'a calmly
"Sweetheart-"
"I know sit down okay? We'll take care of it" badan tanaso ba ta koma ta zauna
akan cinyan nasa, ji take as if taje ta maquro wuyan Khadeeja.
"Sweetheart wannan ba time nayin abu sanyi-sanyi bane taya zata min haka?"
"I know Pr-" shigowan call na Khadeeja ya katse sa, "itace ko? Itace ko? Pass me
the phone." Ta fad'a zuciyarta na tafasa.
"No Princess kice mata meh?"
"What needs to be told."
"Kinga bakida lafiya banason ki tayar da hankalinki akan abinda be kai ya kawo
ba."
"Toh yanzu kai me zakayi?"
"Wa'azi za'a mata." Yana kaiwa nan yayi picking ashe duk anan kallonsa Zeezee ke
seda tayi timing nasa sannan ta fisge wayar ta miqe da sauri "Princess bring it
back" ko jinsa batayi ba ta fad'a kitchen tasa lock.
"Toh munafukar Allah, shegiya la'ananniya me siffan 'yan wuta." Zuciyar
Khadeejah taji ya buga dum! Jin muryan Zeezee. "Kuma wallahi idan kika katse wayar
nan yanzu zan bugo mota na nazoni har gidanki in sanar da mijinki abinda kikeyi dog
kawai."
"Zeezee please kiyi hak'uri duk beyi zafi haka ba."

*MIEMIEBEE. TEAM #YGC!🎀ZAIMEEN flames🔥🔥🔥*


Beeenovels.blogspot.com 👄

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣4⃣

"Hak'uri? Kin barosa gun baabarki shegiya dama haka kike? Mijina kikeso dan
cin fuska? For all these while ashe duk targeting nasa kike? Wallahi kinyi kad'an
Ya Al'ameen ya kula ki, uwarki ma ba a haifeta ba." Tatas Zeezee tayiwa Khadeeja
seda ta sata kuka duk anan Al'ameen na tsaye bakin k'ofar yana sauraronta kawai
daman on normal basis ma ya aka k'are da masifan Zeezee bale yanzu da ga juna biyu
ga kuma an ta6o ta. Seda tayi mata tatas sannan ta katse wayar tare da deleting
number'n Khadeejah daga logs d'in.

_Toh gareku matan aure masu posting pictures na mazajenku on social media, you
guys should be extra vigilant ta sharing pics na BAE a social media don anan duk
wani ha'inci da munafirci yake somawa. Pictures na mijinki ya zama a wayanki ne
zallah ba a face na social media ba be ware and warned._

Tana gama gogewan ta fito daga kitchen d'in fuskanta har wani red colour yayi
tsabagen masifa ga gumi all over. Ganinsa tayi tsaye bakin k'ofar, ba tare da tace
dashi k'ala ba ta mik'a mai wayan sede be amsa ba instead se ya ja hannunta calmly
tare da hugging nata tightly da hannunsa d'aya.

"Calm down okay? All shall be well kibar tada hankalinki."


"Ya Al'ameen I can't." Tayi stating as if though zatayi kuka.
"I've heard everything in shaa Allah she won't call me again."
"Ya Al'ameen baka san who Khadeeja is bane, when she sets her mind to getting
something she must get it."
"And I assure you Princess she won't ever get me saboda you got me first calm
down kinji? Am yours alone."
"Sweetheart nayi kuskure dana riga posting pictures naka da videos online."
"Mistake is the best teacher kinga yanzu bazaki sake ba am I right?"
"I won't ever."
"Thats My Woman so chill incase Khadeeja take kowa ta sake kira na I'll change my
number completely I just want you to trust me." A nitse ta d'ago daga jikinsa.
"I trust you Ya Al'ameen, I trust you with all my heart."
"Thank you Princess."

***
Life continued, a hankali a hankali Al'ameen ke samun sauk'i a yayinda cikin
Zeezee keta girma baby na cikin k'oshin lafiya. School ma ba kullum take samun fita
ba saboda leg cramps bayan nan wataran kuma zazza6i. Sun shafe kusan 2 months 2
weeks da Al'ameen atare saboda break da aka basa na seya ji garau ya koma aiki,
Zeezee can't ask for more kullum da ta dawo daga school tana jikin Al'ameen nata.
D'aki musamnan suka ware Al'ameen yasa aka gyara into a baby's taste. At first
yace komi pink za'ayi saboda wai shi mace Zeezee zata haifa itako ta dage tace sam
na miji zata haifa sabida haka sede ayi komi blue, daga k'arshe 50-50 sukayi rabin
kayaki and other stuffs blue rabi pink paint ma akayi rabi blue rabi pink, d'akin
is just how jiran baby's arrival kawai ake.

Cikin Zeezee nada 8 months yanzu, tayi nauyi sosai tashi da k'yar zama da k'yar
Al'ameen ke assisting nata yin komi. Suna kwance a d'aki bisa kan gado Zeezee ta
miqe tsaye da k'yar se nishi take tana son taje parlour. kallon cikinta Al'ameen ya
tsaya yi atimes har tsoro cikin nata ke basa don yadda yayi girma shima se gani
yake anya ba na miji bane kuwa? Suyi scanning su gano sex d'in kuwa sunk'i saboda
bet da suka ta6ayi. Gashi da daddare ta cinye space na gadon gabad'aya da yayi
magana tace ba ita kad'ai bane su biyu ne. "Bazaka bar kallo na haka bako?" Tayi
maganan wane zatayi kuka. Kai yayi saurin kad'awa yana son yayi dariya amman yasan
idan yayi da akwai trouble don haka yayi k'ok'arin matsewa but still seda ta
kamasa. "Kuma dariya kakeson yimin ko?"
"Inji waye zanyi dariya? Ba dariya zan yiba."
"Kayin ma mana ai na kusan rabuwa da cikin se kowa ya huta."
"You'll get pregnant again ai."
"Wa? Ni?"
"Yes Princess."
"Lallai kuwa ai ban sake d'aukan ciki tunda kullum bakada aikin daya fi kayita
min dariya."
"Princess ni fa ba girman cikinki ke sani dariya ba I love your baby bomb."
"Toh mene idan ba shi ba, gabad'aya ya 6ata min figure na."
"Wannan ture-turen da kikeyin ne" ya k'are maganan yana dariya sosai. Pillow ta
d'aga ta wulla mishi "seka tayin ai sena kira 'yan office naka ma in ce musu ka
warke garau kawai kak'i resuming ne."
"Ai ina nan har due month naki. "
"Banason ka, ka tafi."
"I know you don't mean that."
"My handsome Soldier kawai."
"LOL my Beautiful Princess zo kinji?" Kafad'a ta buga "o'o"
"Haba! The Queen of Queens."
"Nak'i fa the King of Kings."
"Please My heart race and beat." Ya miqa mata hannunsa.
"No I won't My Price possession."
"Kinsan you are my ride or die right?"
"And thats why I love you" tayi maganan finally tare da sa hannunta cikin nasa a
hankali ya jata ta zauna akan cinyansa. "Kinsan wani abu?" Kad'a kai tayi tare da
sa hannunta cikin gashin kansa tana wasa da shi. "You get beautiful everyday."
"Just as you do My Soldier." A hankali yayi owning lips nata after a short kiss
yayi pulling out yana mata murmushi, murmushin ta miyar masa tana arranging mai
gashin kansa data hargitsa. "Rest okay? Ina zuwa karka fito fa kayi bacci."
"Kefa Ina zakije?"
"Zan duba abu ne a chan d'akin Little Soldier" tayi mai k'arya.
"Lets go in tayaki."
"No don't worry nasan inda yake zan d'auko ne kawai."
"Are you sure Princess?"
"Yes Sweetheart" pecking nose tip nasa tayi sannan a hankali ta miqe tana takawa
a hankali har ta fice. Tsintsiya ta d'au ta shiga shara saboda yadda gidan yayi
k'ura har na fitan hankali, tabari a d'aukan mata me aiki kuma wai bata so. Ta d'au
tsawon lokaci amman befi rabin parlour'n kad'ai ta iya ta share ba se nishi take.
Jin shiru daga ciki Al'ameen yace bari ya leqo ta. Tana jin k'aran bud'uwon k'ofa
ta shiga neman inda zata 6oye tsintsiyan tasan kalan masifan da ze mata idan har ya
ganta tana shara. Kafin tace zata wulla tsintsiyar bayan kujera har ya kamata.

"Princess!" Yayi exclaiming sunanta unbelievably. Kid'imewa gabad'aya tayi tama


rasa nayi se raba ido da take a k'asa. Ba tare da 6ata lokaci ba ya doso inda take
fuskarsa ba alaman annuri ko kad'an. "Princess am talking to you." Har yanzu tak'i
d'ago kanta bale ta amsa.
"Ban hanaki sharan nan ba?"
"Swee-"
"Answer me first." Ya katse ta calmly and not rudely.
"Ka hana" ta fad'a still not looking at him.
"Then me kikeyi yanzu?"
"Sweetheart baka ga yadda gidan yayi k'ura bane sekace ba mutane ke zama ciki
ba."
"A d'auko miki me aiki ina kika k'i? Final discussion yanzu me aiki zan sa a
kawo miki all the way from KD."
"Ni banaso-"
"Period Princess bana son musu za a kawo miki me aiki." Ya katseta. Wani haushinsa
take ji right now, daya san sharrin masu aiki da bazeyi tunanin kawo mata ba. Rai
tata had'a mai a yinin ranan shiko ignoring nata yake as in kwata-kwata nuna mata
yayi bema san tana fushi dashi ba yata cracking mata jokes yana neman tsokanarta
ita kuwa se manna mai hauka take a dole tayi zuciya.

Can dare bayan ya dawo daga Masjid ya wuce kitchen ya had'a had'ad'd'en egg
sauce nasa sanin its one of Zeezee's favorite. Tana miqe akan gado tana playing
candy crush ya shigo, k'anshin na bugan hancinta ta ajiye wayan a gefe ta shiga
binsa da kallo har seda ya zauna tukuna. Spoon yasa ya shiga ci a hankali yana wani
"hummm!" Irin delicious d'innan. Duk anan kallonsa take a yayinda miyau d'inta ya
gama tsinkewa, gani take kaman idan bata ci ba cikinta na iya zubewa even though
its impossible. So take tace mar zataci amman tuna yadda tun safe yau bata sake
yimai magana ba ga kuma koya mata tayita ignoring nasa taji bazata iya ce masa zata
ci ba saboda da kunya kunya.
Se fa ci Al'ameen yake har yaci fiye da rabi bema Zeezee tayi ba itako kallonsa
kawai take ko kyaftawan arziki bata yi. Wai Ya Al'ameen baze min tayi ba? Ta
tambayi kanta a zuciya. Kafin ta hankara taga Al'ameen ya cinye tas! last spoon
d'aya ya rage kacal shi d'inma har ya tattara a spoon sauran kawai yasa a baki.
"Sweetheart karka cinye!" Tayi informing nasa da wuri da kuma k'arfi shiko da
gangan ya kai baki sannan yace, "baki fad'a da wuri ba, aww ma dani kike? Wow! I
thought kinbar min magana." Fuska ta maraice tamkar zatayi kuka.
"Yanzu Sweetheart seka cinye wannan egg sauce d'in duka bazaka min tayi ba kasan
its my favorite bayan nan kuma kasan condition d'ina ka kyauta."
"Ha'ah! Princess kefa kika bar min magana inason in tambayeki d'azu ko zakici
amman nasan ko nayi in vein ne bazaki amsani ba."
"Amman ai still da ka tambaya kokuwa da kazo ci seka min tayi."
"I thought kina fushi dani bazaki ci abinda na girka bama."
"Ka kyauta wallahi" tayi stating tana maquro hawayen munafirci. "Ka cinye d'akin
naka ni a guest room zan kwana yau." K'ok'arin miqewa ta shiga yi wanda tuni
Al'ameen yayi sauri ya rigata tashi tare da nufan side nata.
"Ka matsa min" tayi stating in a serious tone.
"Let me assist you Princess kinga kinyi nauyi dayawa."
"Banaso, kasan nayi nauyin kayi cooking favorite d'ina ka hana ni."
"Yi hak'uri toh."
"Nak'i bana so matsa min." Ba gardama ya matsa mata ta tattara wayanta da ice
block da take sha ta fice zuwa guest room. Tana fita yabi bayanta ya wuce kitchen
daman da gangan yayi hakan its the only solution da zesa su fara magana. Inda ya
ajiye mata nata egg sauce d'in ya nufa ya ciro sannan ya d'auko mata chapman nata a
fridge ya nufi guest room d'in. Thankfully bata rufe ba, a hankali ya bud'e ya
shiga, koda ta jiyo k'aran shigowan mutum bata damu ta juya ba sema rufe ido da
tayi as if tana bacci. A kan side drawer'n dake gefenta ya ajiye yana kallon
fuskarta ko zata motsa, seda ya bud'e plate d'in k'amshin girkin ya soma tashi seya
ga Zeezee ta bud'e ido d'aya. "Yauwa bud'e duka toh Princess."
"Me kazo yimin a d'aki excuse me bacci nakeji." Ido yayi ya nuna mata plate d'in.
"So?" Tayi maganan irin she don't get him d'innan while deep inside har imagining
kanta tana ciki take.
"Tashi ki zauna kici here's your favorite drink also." Kallon plate d'in tayi
sannan back to his smiling face. "Yi hak'uri kinji?" Baki ta turo tare da fad'in
"bazan ciba."
"Yi hak'uri fa nace."
"Dama akwai a kitchen shine don ka sani kwad'ayi ka 6oye kayi pretending as if na
wajenkan ne kawai ya rage? Granny'nka ka miyar dani ko?"
"Haba! Taya Princess zata koma Granny? I'm sorry yi hak'uri kici."
"Bazan ciba excuse me."
"Toh shikenan" ya furta tare da d'aga plate d'in ya d'iba a spoon ze soma ci, duk
anan kallonsa Zeezee ke, seda ya kusa kaiwa baki sannan ta bige spoon d'in ya zube
a k'asa tare da wabje plate d'in "yanzu dagaske seka cinye don nace bazan ci ba?"
"Toh zubarwa kikeso inyi?"
"Wallahi Allah kabar so na yanzu, a da kai da kanka kake sani cin abinci amman
yanzu da naci da banci ba du be dameka ba."
"You know thats not true, wasa nake miki taya zan cinye ban baki ba? Infact i'll
be the one to feed you."
"Seda na rok'a bana so."
"Kar a ji kanmu mana Princess" cike da dabara ya amshi plate d'in ya jata jikinsa
sannan ya shiga bata a hankali har ta cinye sannan suka miqe kan gadon tana manne a
jikinsa "Mu kwana anan yau Sweetheart kaji?"
"Anan kuma? Can fah?"
"Kawai ina son mu kwana anan ne yau."
"No please chan yafi" yayi maganan as if ya tuna da abu.
"Why? Mesa baka son nan?"
"Ermmm..." ya shiga neman excuse "kinga AC'n nan is not connected to a stabilizer
kuma wutan ba k'arfi."
"Wannan wutan ne ba k'arfi? You are hiding something Sweetheart."
"Am not kawai mu kwana achan."
"Nikuma se ka gayamin actual reason da yasa bakason mu kwana anan."
"Promise bazaki ji haushi ba."
"LOL I promise Sweetheart."
"Toh kinga bed d'innan be kai na d'akinmu girma ba..." se kuma yayi shiru.
"Soo?" Tayi maganan waiting for him ya cigaba.
"So achan d'inma kina birgima ki hau kaina gabad'aya ki hanani bacci bale anan,
muka kwana anan nasan bazan iya bacci ba mu kwana achan please." Tana dariya sosai
tace;
"Aikuwa anan d'in zamu kwana muyi renon cikin tare kai ka d'auka abu ne na wasa
ba? Kasan ko juyi zanyi se nayi dagaske kaima ka d'ana."
"Please mana Princess."
"A'a fah Sweetheart nan d'in zamu kwana in haura kan ka gabad'aya ma in turaka ka
fad'i a k'asa kaima ka sha wuya."
"Zan koma Abj ma ai."
"Kana nan ba inda zaka sena haihu."
"LOL Allah ya kaimu toh waya ga su Princess a labor room akwai show kam ranan."
"LOL tare zamuyi show d'in ai dan bazaka barni ni kad'ai ba a labor room."
"Da so kike in shiga nima?"
"Kana gefe na ma kuwa."
"Inaaaa! I can't."
"Why?"
"Saboda I don't want to see you suffer."
"And I need you by my side."
"And I'll be by your side Princess I love you, throw your legs na miki massaging
nasan sun kumbura da sharan da kikayi d'azu." Ba musu ta aza k'afafunta akan
cinyansa ya shiga yi mata tausan. Adorably ta tsaya kallonsa.
"I love you more Sweetheart zaka min wani favor?"
"Why not? Tell me."
"Please ka janye baya da zancen kawo me aikin nan I promise bazan sake yin shara
ba har se na haihu."
"Uhn-uhn Princess we've talked about this already zan sa akawo miki me aiki
saboda nasan ki anytime bana kusa zaki ce zakiyi sharan."
"Bazan yiba Allah."
"No za'a kawo miki me aiki period."
"Toh ni wallahi tsohuwa za a kawo min dattijuwa ba 'yan mata ba."
"Ko sa'ar Mama Babba kikeso za'a kawo miki amman de se an kawo me aikin nan tana
yin ayyukan gidan."
"Dattijuwar ma ba bahaushiya ba irinsu Igala ko Nupen nan sunfi daraja mutum
amman hausawan nan fitsararru ne."
"Naji fa ko TIV kikeso za'a kawo miki."
"Toh bar min k'afa na a haka bana so tunda seka kawo me aikin."
"Nak'i sakewa kuma me aiki se an kawo." Ido ya kashe mata take ita kuwa ta
murgud'a mai baki, murmushi ya sakar mata. A garin jan k'afan nata ta buga cikinta
"awcch!" Ta saki k'ara a yayinda Al'ameen da sauri ya dawo ta setin kanta yana mata
sannu gabad'aya ya kid'ime. Da wuri ta zagaye hannayenta a wuyansa in which da
mamaki ya tsaya kallonta "Princess! Dama k'arya ne baki buga Little Princess d'ina
ba?" Tana dariya tace;
"Nima na rama ne" tare da owning lips nasa, suka shiga kissing juna hungrily.

In three days time aka kawowa Zeezee me aikinta, wayyo ita bak'in ciki kasheta,
ita data ga munin matan nema hankalinta ya d'an kwanta, ina irin munana first class
d'innan. Dattijuwa ce da tsagan Nupe a fuskanta karara. Dad'i sosai Zeezee ta jiyo
saboda billen tan nan kad'ai baze bar Al'ameen ya iya ya kalli fuskanta sau biyu
ba. Dogon rigarta Al'ameen ya miqa mata ta sanya sannan ta miqe daga kan gadon da
k'yar.
"Princess yaushe ne due date naki?"
"Ban sani ba" ta murgud'a mai baki.
"Toh nikuma me nace yanzu?"
"Ai da fili ka fito kace min Zeezee cikin ki yayi k'ato ya soma bani tsoro da
yafi ma ba sekayi using style d'innan ba."
"God help me! Ni de bance ba."
"Kama cen mana."
"Ina kuma zakije?"
"Zanje in samu Baaba sauran kuma ka fito kaji ba?"
"Idan inason d'auko ruwa fah?"
"Zan d'auko maka amman ban yarda ka fita ba."
"Toh Maj-Gen Muhd Al'ameen's only wife, your wish is my command." Dad'i sosai
taji game da ikirarin dayayi mata tace, "thats My Soldier" tana murmushi. Ficewa
tayi a nitse inda taje ta samu Baaba ta shiga lisafo mata rules nata na aiki, ba
kazai any how zata na gaishe da Al'ameen ba, ba kuma had'inta da shiga d'akinsu.
Idan ita da Al'ameen suna cin abinci akan dining to ko parlour ne karta fito har se
idan sun k'are cin abincin.
"Toh Hajiya zan kiyaye."
"Yauwa toh Baaba akwai abincinki akan table na ajiye miki seki d'auka kici bayan
kin gama kiyi ayyukanki abinda baki gane ba kina iya min magana."
"Toh Hajiya godiya nake."
"Yauwa sannu" tana kaiwa nan ta koma d'aki ta samu Al'ameen.

****
Later during the night wajajen k'arfe 12:48am Zeezee se juyi take akan gadon
gabad'aya ta mamaye ko ina ta tura Al'ameen dungu guda abin tausayi yana bacci.
Ganin fa bazata iya hak'ura ba ta shiga tayar dashi daga baccin.
"Sweetheart" tayi whispering a kunnensa. "Ya Al'ameen wake up! Wake up kaji?"
"Princess please kiyi hak'uri mu kwanta ko in sauqa k'asa in bar miki kan gadon
ne?"
"No."
"Toh mu kwanta."
"Ni wallahi yunwa nakeji ka tashi" tashiga jijjiga shi.
"Okay, okay naji me zakici? Akwai ragowar fried rice na jiya in miki heating?"
Har yanzu be bud'e idonshi ba.
"Ni ba shi nakeso ba Shawarma nake so." Firgit ya miqe zaune tare da kunna bedside
lamp.
"Kikace?" Ya tambaya cike da mamaki.
"Shawarma" ta sake nanata kanta.
"Princess kalli agogo pass 12 ina zan samo miki shawarma?"
"Nima ban sani ba nide shi nakeso please ka nemo min yunwa nakeji Sweetheart."
"Oh God help me, ina zuwa Allah yasa baki cinye na fridge d'in ba." Kitchen ya
nufa ya bud'e babban fridge nasu and luckily ya samu pack d'aya na shawarman daya
ajiye, yasan da a k'aramin fridge ya ajiye da ta jima da cinyewa. A plate ya juye
mata ya kai mata, tun ganinsa da tayi da plate ta shiga washe hak'wara. "Woww!"
Tayi maganan tana d'igan miyau. "A ina ka samu Sweetheart?" Bata jira ya zauna bama
ta amshe plate d'in ta shiga ci.
"Kici kawai kinji?" Shirun tayi ta cigaba daci a yayinda Al'ameen ya zauna yana
kallonta cike da adoration.
*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀 ZAIMEEN flames🔥🔥🔥*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣5⃣

     Cikin d'an k'ank'anin lokaci ta cinye tas. Shi Al'ameen tsoro ma cin Zeezee ke
basa yanzu, just some hours back taci fried rice da kaji yanzu kuma take kukan
yunwa.
  "Are we good to go?" Ya tambayeta idonsa cike dam da bacci. Kai ta gyad'a a
hankali "thank you for being the perfect husband Sweetheart I love you." He was mad
kad'an amman jin kalamunta seyaji ya huce. "I love you more" ya fad'a tare da
matsowa kusa da ita ya kashe musu wuta suka kwanta.

****
    Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa seda Zeezee ta kusa haihuwa ta soma d'an
banzan masifa da wani irin wawan chi da shan k'ank'ara. Kullum cikin fad'a Al'ameen
ke mata data rage ci or else tazo haihuwa zata sha wuya idan ta tashi seta ce mishi
ai ba shi ze haihun ba saboda haka ba ruwanshi da ita.
   Ga masifa, abu kad'an ta haura sama tayita masifa shi Al'ameen yasan depression
na labour ke damunta shiyasa yake binta a hankali koda ta mai masifa seya sak'a
mata da love and calming words sekuma daga baya taji kunya tazo tayita basa
hak'uri. Tun ana sauran one week due date na Zeezee Al'ameen ya shirya maternity
bag nata suka zama ready. Ganin date ya matso kusa fa Zeezee ta shiga tsoro a
k'alla a kullum setayi kuka ita tana jin tsoro batason ta haihun kuma.

   Tun safe Al'ameen ya fita yau, Zeezee ce kad'ai da Baaba a gida. Yau ma bayan ta
gama shan kukanta tayi alwala tayi sallah da k'yar sannan ta d'ibo ice blocks daga
fridge ta faffasa tasa cikin bowl sannan tayi d'aki ta zauna kan gado tana sha tana
buga game. Tana cikin sha kawai tajiyo muryan Baaba nayiwa Al'ameen sannu da
dawowa. Kid'imewa tayi gun gabaki d'aya tama rasa nayi ta wulla bowl na ice blocks
d'in k'ark'ashin gado ne ko yaya? Al'ameen ya hanata sha saboda mutane na cewa
yawan shan k'ank'ara nasa a haifo yaro da pneumonia ko kuwa asthma. Kafin tace zata
miqe ta wulla bowl d'in k'arkashin gado har Al'ameen ya bud'e k'ofan ya shiga.
Pillow tayi sauri ta aza kan bowl d'in a tunaninta wai Al'ameen bega bowl d'inba
shiko tun shigansa idanunsa sukayi tozali da bowl d'in wanda he is sure k'ank'ara
ne aciki.
      "Sweetheart sannu da zuwa"
   "Yauwa Princess sannu da hutawa."
  "Uhn amman bada mota ka shigo ba ko?"
   Seda ya k'ariso gefen gado yace, "a waje na sauk'a Abba ze wuce dashi car wash."
Ba yabo ba fallasa ya amsatan as if bata yimai komi ba. Ganin yana neman zama kan
gadon kuma idan yayi hakan yana iya gano abinda take 6oyewan tace, "karka zauna
anan ruwa ya zube." Da sauri.
  "A ina?" Ya juya yana kallon wajen.
  "Nan." Tayi pointing da yatsa.
  "Nan d'inne a jik'e Princess kode kina 6oye wani abu ne?"
   "B'oye abu kuma? Me zan 6oye?"

    "D'aga pillon muga."


  "Babu komi fah Sweetheart."
  "Princess k'arya kuma kika soma yimin yanzu? Ba halin ki bane fa, ban san ki da
k'arya ba." Sekuma taji ba dad'i.
  "I'm sorry."
  "Ban hana ki shan k'ank'aran nan ba?"
  "Sw-"
  "Yes or no?" ya katse ta.
  "Yes ka hana."
  "Mesa kike sha toh?"
  "My Soldier wallahi dad'i yake min idan ban sha ba har wani rashin lafiya
nakeji."
  Matsowa yayi kusa da ita tare da riqo hands nata cikin nasa "Princess bawai ina
son tauye miki hak'k'in ki bane na hanaki shan k'ank'aran, lafiyan baby'nmu zaki
duba the more kina shan k'ank'aran nan the more kina exposing d'inshi ko ita the
risk na kamuwa da pneumonia ki dena please."
  "I'm sorry Sweetheart bazan sake ba."
  "Can you promise me?"
  "Do I have to?"
  "In bakiyi ba bazaki bar shan k'ank'aran ba kenan."
  "Toh I promise."
  "Sure?"
  "Yes ai sauran befi sati ba due date d'ina bazan sake ba anything for My
Soldier."
  "Thats My Princess tashi ki shirya muje mu siya miki shawarma ko bakiya so?"
  "Inaso wallahi."
  "Tashi toh mu shirya ki." Da kansa ya ciro mata wani had'ad'd'en dogon riga da
hijabi tasa sannan suka fita.
 
*^*^*^
      Dare d'aya Al'ameen da Zeezee suna kwance suna bacci wajajen 11:47pm Zeezee
ta farka sanadin ciwon cikin da tun da tasan kanta bata ta6a yin irinsa ba not even
menstral cramps. Juyi take so tayi amman dan yadda cikinta yake k'ato tama kasa, ta
zauna kuma murd'in cikin baze barta ba. Hawaye kawai ta shiga yi a hankali duk anan
kuwa Al'ameen na bacci besan meke faruwa ba, ta tadashi kuma bata so tuna yadda yau
ya yini yana training men nasa tasan he must be exhausted. Da k'yar ta iya ta
sauk'o daga kan gadon ta tukuikuye kanta akan tiles tana rik'e da cikinta. Tsan-
tsan azaba da murd'in da cikinta keyi mata har tambayan kanta ta soma anya kuwa ba
mutuwa zatayi ba? Ganin zafin is getting out of hand ta shiga kiran Al'ameen cikin
k'aramin murya.
   "Ya Al'ameen! Ya Al'ameen!" Shiru be jita ba dake in a low tune take kiransa shi
kuwa baccinsa yayi nisa.
  "Ya Al'ameen please wake up zan mutu, ka tashi don All- argghhhh!" Ta saki wani
irin k'ara wane ana cire wa kafiri rai sanadin murd'awan da cikinta yayi. A firgice
Al'ameen ya tashi yana kiran sunanta "Princess!" A cewarsa ma mafarki yake saboda
jin sautin ihunta. Ta6a gefensa yayi yaji wayam tashin hankali! "Princess!" Ya
fad'a tare da kunna bedside lamb. Har anan be ganta ba dake tana maqe gefen gadon
tana ta kuka ba sauti.
   "Princess ina kike?"  Yayi maganan tare da barin kan gadon.
  "Ya Al'ameen" ta furta cikin wani irin murya. Da sauri yayo wajen salati ya saki
ganinta kwance k'asa a gun. Da hanzari ya k'arisa ya aza kanta bisa cinyansa yana
share mata hawayenta a hankali "Princess what's wrong? Mesa kike kuka haka? Me
kikeyi a k'asa?" Hannunta ta aza akan nasa dake kan fuskarta sannan tana kad'a kai
tace, "I'm sorry Ya Al'ameen I don't think I can make it saboda mutuwa zanyi."
  "Subhanallah! Wani irin magana kike haka Princess? You are not going to die
please kibar fad'in haka, cikinki ne ke miki ciwo?" Kai ta gyad'a a hankali ta
bud'e baki zatayi magana cikin nata ya sake yimata murd'i. K'ara ta saki nan ma
sosai se kuma kuka "I think you are in labor bari insa kaya in d'auko maternity bag
naki mu wuce asibiti" yayi stating all confused kwata-kwata ya rasa meke masa
dad'i, tun da yake be ta6a ganin Zeezee cikin bad situation kaman wannan ba. Pillow
yaja yana son aza kanta akai, "Ya Al'ameen please don't leave me karka barni in
mutu ni kad'ai stay with me please."
  "Zainab please bazaki mutu ba kibar fad'in haka in shaa Allahu zaki haihu safe
and sound kinji?"
  "Toh dan Allah karka tafi ka barni you promise not to ever leave my side."
  "I am not leaving your side Princess maternity bag naki zan d'auko mu wuce
asibiti kinji? Hold still I love you." Kai ta  gyad'a a wahalince. Pecking forehead
nata yayi ya miqe ya sanya jallabiyansa da sauri sannan yaje ya kira Baaba daga
d'akinta ta fito musu da maternity bag d'in.

    Seda yayi dagaske sannan ya samu ya d'agata ya sata a mota suka fice asibiti.
K'arfe 12-:24am na dare akayi labor room da ita. Al'ameen na tsaye bakin k'ofan
d'akin gabad'aya he is out of it besan meke masa dad'i ba again, nayi ma besani ba.
Yafi minti ishirin tsaye bakin k'ofan yayi nan yayi chan finally ya zaro wayansa
daga aljihunsa har ya shiga kiran Mama se kuma ya fasa kada ya tayar mata da
hankali da daren nan sanin ba wanda ze kawo ta asibitin  a yanzu tunda ba driving
take ba ita. Mama Babba ya kira right away wanda seda call d'in ya kusa yankewa ta
d'aga.
  "Hello Al'ameen da daren nan Allah yasa lafiya."
  "Mama" kad'ai ya furta sounding sad and worried. Tuni Mama Babba ta miqe zaune
jin yanayin muryan d'anta. "Subhanallah Al'ameen lafiya dai ko? Kayi magana don
Allah ina kake yanzu?"
  "Mama Zainab ce." Yadda yake magana mutum na iya imani yana kuka ne tsan-tsan
tashin hankali.
  "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Meya sameta Al'ameen? Meya samu Zeezee?"
  "Mama she is dying and ba abinda zan iya mata, labour'n ta yayi hitting."
  "Kuna asibiti ne yanzu?" Tayi maganan sounding relieved kad'an cause at first ta
d'au ma ko mutuwa Zeezee tayi.
  "Eh."
  "Ka kwantar da hankalinka kaji? Shi dama labor haka yake, kata yi mata karatu
kawai su ayyatul kursiyu d'innan in shaa Allahu zata sauk'a lafiya kaji?"
   "Mama am afraid I don't want to lose Zainab."
  "You won't lose her Al'ameen trust me okay? Ka nitsu ka yimata karatu sosai nima
zan tashi nan inyi sallah mu rok'a mata Allah, Allah ya sauk'e ta lafiya."
  "Toh Mama thank you."
  "Ka kira Hajya Hafsah ne?"
  "A'a banason in tayar mata da hankali se idan naga abin nason fin k'arfin Doctors
d'inne se in kirata."
  "Kayi tunani me kyau Allah ya sauk'ar da Zeezee lafiya."
"Ameen."
"Ka kwantar da hankalinka kaji? Zeezee zata sauk'a lafiya in shaa Allahu."
  "Toh Mama Allah yasa, thank you duk abinda akwai I'll let you know."
  "Yauwa Son semun sake magana." Ahaka sukayi sallama. Leqa ta windown d'akin ya
gwada yi amman ba abinda yake gani sema k'aran ihun Zeezee dayake ji. Ji yake kaman
yayi kuka there is his Princess suffering, fighting for her life shi yana tsaye
anan doing nothing. How he wish ze iya kar6an mata pain d'in yaso se shi yayi
suffering.
   
   Safa da marwah ya shiga yi wajen ya zauna ya nitsu yayi mata karatu kaman yadda
Mama Babba ta fad'a mishi ma ya kasa. Ana cikin haka ne aka bud'e k'ofan d'akin da
Zeezee ke ciki. Da sauri ya miqe ya sami nurse d'in.

   "Nurse how is she please? How is my wife?"


  "Still no improvement."
  "Please is she going to make it?"
  "Idan har kana TARE DA ITA, yes. She needs you inside mu shiga daga ciki please."
Ji yake kaman yace mata baze iya ba saboda baze iya sauraron sautin kukan Zeezee ba
standing beside her and doing nothing, on the other side kuma tuna ya ta6a d'aukan
mata alk'awarin cewa he'll always be by her side harta labor room nata yada yayi
manning up kawai.
  "Muje please Sir tana jiran ka tak'i pushing wai se kana kanta tukuna." Hanky ya
zaro a pocket nasa ya share gumin dake ta kan k'eto masa sannan yabi bayanta suka
k'arisa ciki. Kallo d'aya yayi wa Zeezee ya kawar da kansa baya jin ze iya sake
sata a ido gumin da take had'awa ko wanda ke cikin oven albarka.
   "Ya Al'ameen" ta kira sunansa cikin wani irin sauti. "Ya Al'ameen please don't
go don't leave me." Guiwa ba k'arfi ya k'arisa kan gadon nata tare da rik'e
hannunta d'aya cikin nasa duka yana pecking kai "shhh! Am here Princess am never
gonna leave your side." Hanky ya zaro next ya share mata gumin nata tas sanna yayi
pecking forehead nata tare da fad'a mata, "we are in this together Princess I love
you so much morethan you can ever imagine."
   "Ya Al'ameen bazan iya ba, please forgive me."
  "You can do this Zainab because am here with you, we are in this together kinji?"
   "Try pushing okay? " Cewar Dr Sammy dake expecting baby.
  "I can't I can't please do something Ya Al'ameen." Zeezee ta fad'a tana hawaye.
  "Yes you can Zainab, you can just do as yadda Dr ta fad'a kinji? Ke kad'ai kike
da ikon kawo mana Little soldier'nmu into life and I trust you push okay am here
for you."
   "I can't Ya Al'ameen zan mutu its too painful."
  "I know Princess and kina k'ok'ari ma sosai just push kinji koda so d'aya ne I
love you, after the count of three sekiyi pushing. Ready?" Kai ta gyad'a da k'yar
bayan data gama 6ata musu lokaci. "Okay, here we go 1... 2... 3 push!" Aiko tak'i
pushing d'in ita tana jin tsoro se kuka take. "Princess you have to push if not
Little Soldier'n mu baze fito ba fah."
  "Ya Al'ameen I can't I feel like am dying, I need some air please." Wani file
yaja a gefe ya shiga yi mata fifita dashi a yayinda take ta jan numfashi. Ya mata
na kusan 2 minutes tace she is okay, "so zakiyi pushing yanzu?" Da sauri ta kad'a 
kai "I can't."
  "Yes you can, ko kin manta matar wacece ke Princess? Matar Soja ce fa, matan
sojoji kuma kuma ba ragwaye bane ko bakison kiga Little Soldier'n mu muga da wa
yake kama?"
  "Ina so."
  "Good you have to push then." Kai zalla ta gyad'a mishi.
   "Zakiyi for your Soldier?" Nan ma kai ta gyad'a "thats My Woman so after the
count of three okay? One... two... three!" Pushing d'in tayi da iya k'arfin jikinta
har seda jijiyoyin goshinta suka bayyano. "Wayyoo! Zan mutu" Tasa k'ara bayan
pushing da aka samu tayi. "I can't I can't Ya Al'ameen ni kubarmin baby na aciki
kawai I can't force him out kuka ce senayi kashe ni zakuyi kubarmin shi a ciki na
yafe ganinsan." Sosai d'ayan nurse d'in ta tsaya da dariya yau tana ganin labor
kam.

   "A bar shi kuma Princess? Taya za'a barsa yi hak'uri ki sake pushing." Kai tayi
saurin kad'awa tana kuka ita a miyar da ita gida, abu fa kaman wasa Zeezee tayi
pushing tak'i. Su Dr Sammy basu ta6a ganin abu haka ba, daga k'arshe ma tsayawa
sukayi daga gefe suna k'are ma Zeezee da Al'ameen dake ta faman calming nata yana
rok'anta da tayi pushing kallo. Sun yi morethan 30 minutes suna abu d'aya Al'ameen
nata rok'onta da tayi pushing da k'yar finally tayi agreeing to push anan suka
marmartso. Fiye dana d'azu ta sake wani push d'in, nan kam har Dr Sammy ta soma
ganin kan baby'n, se kuma yanzu wani sabon azaba da zafin labor ya sake hitting
Zeezee.
   "Ga baby's head nan two more push in shaa Allah ze fito push again kinji
Zainab?" Dr Sammy tayi information tana murmushi.
  "I can't ni kubarni please kun d'au pushing d'in wasa ne? Ni Mama nakeso nasan
ita bazata ce in yi pushing in kashe kaina ba, kaima Ya Al'ameen ban zata mugu ne
ba kai se yau, Allah ze sak'a min ba pushing da zan sake in kashe kaina ni ku kira
min Mama." Kuka take sosai tsakanin ta da Allah. K'us-k'us nurses suka shiga dariya
jin wannan kalamu na Zeezee.
  "Naji kuma na yarda ni mugu ne Princess amman yi hak'uri ki sake pushing ko sau
d'aya ne."
  "Nak'i bazan yi ba ni ka fita min daga d'aki mugu kawai" ta rushe da kuka. Yasani
sarai she don't mean any of those words azaba ne kawai yayi mata yawa. "I am here
with you Princess I am never leaving your side."
  "Just go I don't love you anymore ni Mama nakeso, duk kaine wallahi bazan sake
kwanciya dakai a d'aki d'aya ba." Dariya sosai har Dr Sammy ta tsaya yi.
   "Toh naji Princess amman yanzu yi hak'uri kiyi pushing."
  "Ni Mama nakeso kuma ka sake cemin push zan ja Allah ya isa."
  "Princess you don't need Mama, kema Maman kanki nefa bakiji Dr tace taga kan
baby'nki ba? Push a bit seya k'arisa fitowa yi hak'uri."
  "Ni Mama nake so" ta sake rushewa da wani kukan.
   "Breathe Zainab you can do this." cewar wata nurse "idan kikayi pushing baze
baki wahala ba." Wani d'an banzan kallo Zeezee ta bita dashi "Inba hancin ki kikeso
in ara inyi nishin ba kan bansan wani irin nishi kikeson iny- arghh!" Wani irin
rik'o tayi ma Al'ameen sanda faracunta suka tsattsaga mishi skin, "labor'n ya sake
hitting" cewar Dr Sammy "Maj-Gen ask her to push idan muka ci sa'a tayi yanzu
baby'n na iya fitowa."
 
  "Push kinji Princess? Yi hak'uri Mama na zuwa na mata waya."
   "Argghhh! no please I can't."
  "Yes you can in bakiyi ba Mama ain't coming fa." Sake gangamesa tayi which in the
process take yak'ushinsa sosai gabad'aya hannunsa ya tashi shima da rabon
labor'nsa, danne zafin yayi sanin tana cikin more pain. "I hate you Ya Al'ameen
wallahi Allah ze sak'a min tunda shi ba azzalumi bane" ta k'are maganan cikin kuka
sosai.
  "I know Princess ni kuma I love you push okay?"
  "Bazan yi ba mugu kawai."
   Haka suka ta drama cikin labor room d'in tayi pushing tak'i. A takaice seda tayi
wasting another 20 minutes sannan da k'yar Al'ameen ya iya convincing nata tayi
pushing. Da tayi da k'arfi da an wuce gurin yanzu amman dake raguwa ce kad'an tayi
pushing hakan yasa only rabin kan baby'n ya fito they need one more push. Kafin
Zeezee tayi one more push d'innan su Dr Sammy sunji jiki barin ma Al'ameen da har
k'odewa yayi ga yak'ushin da Zeezee keyita masa, hannunsa gabad'aya ya 6aci da
shati ga uwa uba masifa da zagin data shiga yi masa bashi kad'ai har Dr Sammy ta
samu share nata.

_4:19am_
  After all the struggles, cries and screams Zeezee tayi pushing one last time da
iya k'arfin jikinta suuul Dr Sammy ta jawo baby. Wani irin relieved sigh Zeezee ta
saki ji take kaman ansa mata sabon rai, like dama iska na blowing haka shine take
ta had'a gumin nan? Se yanzu tama soma jin fresh air'n dake hurata tun d'azu ta
d'au a oven na gasa biredi take.
   "You did it Princess!" Al'ameen yayi alerting nata sounding delighted he can't
believe baby'nsu Dr Sammy ke rik'e da. "Wow we have a bouncing LITTLE SOLDIER here"
tayi informing nasu tare da juya musu baby'n suna kalla, se wani mammatse jikinsa
yake yana tukuikuye kansa gu d'aya wane me jin sanyi. Butt nasa Dr Sammy tad'an
buga wanda hakan yasa sa sakar da k'ara which was damn adorable. "Awwwwn! He's so
cute Sweetheart." Zeezee ta furta tana kallon Little Soldier'n ta she cant believe
that wannan d'anta ne "congratulations Maj-Gen and wife, bari a shirya shi a kawo
muku, amsa Nafeesa." Dr Sammy ta fad'a tare da miqa wa nurse dake gefenta ita kuma
ta fice. A nitse Zeezee ta dawo da kallonta kan Al'ameen "you did it Princess" ya
sake fad'a mata fuskansa d'auke with the most expensive smile.
  "I couldn't have done it without you My Soldier, I love you."
 

*MIEMIEBEE.    Team #YGC!🎀 ZAIMEEN Flames🔥🔥🔥*


Beeenovels.blogspot.com 👄

🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣6⃣

"I love you more" a hankali yayi bending tare da owning lips nata, one of
the best kisses of her entire life ya bata sannan a hankali yayi pulling out,
guminta ya shiga share mata a hankali, a dai-dai lokacin nurse d'in ke kawo musu
jaririn nasu. "Wow let me see wannan little mr. handsome kuma da wa yake kama"
Kallon Zeezee tayi sannan back to Al'ameen "toh wai mesa yawancin 'yan fari ke kama
da Daddies nasu ne?" Murmushi both Zeezee and Al'ameen sukayi sannan ta miqa baby'n
wa Al'ameen "congratulations once more" ta fad'a tare da ficewa. Kallon kyan
jaririn duk suka tsaya yi a yayinda yake juyi kad'an kad'an cikin baby blue showel
nasa, cuteness overboard.
"I told you it was a Little Soldier Sweetheart, a cute one." Ta sanar da Al'ameen
idonta not moving away from her baby.
"Yes Princess you won next time in shaa Allah little Princess ce me kama dake
right?"
"In shaa Allah Sweetheart."
"Na manta ashe Princess tace bazata sake haifan min cute babies ba."
"That's not true ko yara goma kakeso zan haifa maka Sweetheart because I am after
your happiness."
"Thank you, thank you for this most expensive priceless gift Princess I love
you, gashi hold him and name him after duk wani name daya miki."
"Are you sure Sweetheart?"
"I promised so zanyi fulfilling." A hankali ya ajiye mata d'an ta saman cikinta
har anan kallonsa Zeezee ke se kawai gani take like Al'ameen take kalla, kamannin
nasu ya mugun 6aci ba abinda ya rage daga fuskan Daddy'nsa komi seda ya d'auko. "He
is cute" ta furta tana shafa soft hannunsa a hankali.
"Indeed he is Princess."
"Kuma kuna kama sosai, what else can I ask for Sweetheart? I have two wonderful
soldiers a gida na."
"And we love you so much root of happiness so wani suna zaki sa mishi?" Idanunta
ta kulle nad'an lokaci, tana bud'ewa ta kalli baby'n sannan back to Al'ameen as if
yayi reading mind nata suka furta.
"ISMA'IL" a lokaci d'aya sunan Baba me rasuwa.
"How could you have guess Sweetheart?"
"Because thats the perfect name that suits our Little Soldier."
"Ka amince asa mishi?"
"Sekin tambayeni confirmation ne Princess? Ai sunan Baba ne ya dace dashi, Allah
ya ji k'an Baba ya cigaba da kai rahama kabarinsa."
"Ameen na sanya mishi Isma'il da al-kunyan KHALEEFAH."
"Toh Princess Allah raya mana Isma'il akan addinin muslinci ya albarkaci
rayuwanshi yasa mahaddacin Al~Qur'ani ne."
"Ameen ya rabbi world's greatest Dad I love you."
"I love you more world's most Sweetest Mother, up for a selfie?" Murmushi ta
sakar mar tare da gyad'a kai nan ya zaro wayansa ya kashe musu selfie dukansu were
wearing the most expensive smile. Bada jimawa ba Khaleefah ya shiga kuka "omg!
Sweetheart he is crying me zan mishi ya dena?" Tayi stating hankali a tashe a kuma
rud'e.
"Princess calm down."
"Sweetheart baka ga kuka yake bane? Bana son yana kuka please do something."
"He is hungry I guess."
"Hunger? toh ai ba abinci anan me zamu bashi yayi shiru?" Ita gabad'aya ma ta
manta da breastfeeding.
"Kin manta shi abincinsa is always ready and available ne?"
"A ina kenan?" A hankali ya miqa hannunsa ya shiga un-bottling mata rigar nata,
"ko kin manta abincinsa na nan?"
"Omg!" Tayi exclaiming sounding relieved "gabad'aya na mance Sweetheart kayi
sauri ka kirawo nurse ni ban iya ba, tazo ta gwada min."
"Me zata gwada miki?" ya tambayeta cike da mamaki.
"How to breastfeed Khaleefah" tayi stating tana turo baki dan kuwa ko ita kanta
taji kunya.
"Breastfeeding d'inne baki iya ba yanzu Princess? How funny."
"Eh kayita min dariya kabar Khaleefah na kuka, Khaleefah sweet cuddle bar kuka
kaji? Mummy is here." Tayi maganan tana jijjiqa shi a hankali. Murmushi Al'ameen
yayi at her sight sannan yayi positioning Khaleefah dai-dai yadda ze sha abincinsa
ba tare da yabi kansa ba. "Sweetheart what are you doing wai kai ka iya shayarwan
ne?" Ta tambaya da mamaki.
"Tsaya mana kiga."
"Toh a haka milk d'in baze bi kanshi bane?"
"Just wait and see" bayan daya tabbata position na crying Khaleefah yayi se a
hankali ya miqa hannunsa cikin rigan Zeezee ya fito da mamanta d'aya tare da seta
dai-dai bakin Khaleefah ya sa mishi, duk anan binsa da kallo Zeezee ke tana riqe da
Khaleefah. Aiko kaman jira Khaleefah yake ya kama nipple nata da k'arfinsa ya
shiga sha, wani k'ara Zeezee ta saki. "Arrghhhh! Zan mutu Sweetheart please ka
cire, ka cire please zafi omi'god" tayi maganan a rud'e harda d'an guntun
k'wallarta.

Dariya yake son yi mata amman sanin halinta yayi k'ok'ari ya maqe. "Princess
kaman ya kuma a cire? Khaleefah kuma fah?"
"Okayyy... tun ba ayi nisa ba ka fara nuna kafi son Khaleefah fiye dani ko?"
"Who said so Princess kefa Ummu Khaleefah ce son Khaleefah na bayanki."
"Bawani gashi nace ka cire yana min zafi kak'i."
"Toh I'm sorry in cire yanzu?"
"Ban sani ba seda ya dena" ta fad'a tare da murgud'a mai baki.
"Yi hak'uri ki amsani in cire?"
"Eh ka cire" ta fad'a. Hannu ya miqa kama dagaske ze zaren, ganin haka Zeezee
tayi saurin cewa "ka bari wasa nake, barshi yasha har seya k'oshi."
"Awww how adorable, kin gan ku kuwa? Like a gudu daku kawai cuteness overboard."
"I know Sweetheart it has always been my dream, tun da nake banida burin daya fi
inga ina shayar da d'ana ko 'yata daga jikina and here I am today breastfeeding
Khaleefah, I can't ask for more."
"Masha Allah I once told you zaki haihu."
"Yes you did Sweetheart."
"Yanzu sauran ki haifo mana Little Princess tamu se muje Washington and make
that your dream a true come one."
"Allah ya nuna mana Sweetheart, I can't wait to get pregnant with your baby
again." Ta fad'a tare da dawo da kanta ga Khaleefah tana kallon yadda yake shan
abincinsa a hankali.
"Ameen Princess. Shine d'azu kikace bazaki sake haifa min babies ba harma da
cewa you won't sleep with me again."
"Duk a cikin zafin labor ne if not I don't mean any of those words."
"I know Ummu Khaleefa my Princess, I love you so much."
"I love you more Abban Khaleefah my kast standing Soldier." duban screen na
wayansa yayi yaga Asubah ya kusa. "Barin yi alwala Ummu Khaleefa zani Masjid."
"Okay Sweetheart be back safely." Peck ya mata placing a forehead nata sannan
wa Khaleefah, in the process ta hango hannunsa da tayi mai jina-jina. "Omg!
Sweetheart a ina ka samu wannan ciwo haka?"
"Where?"
"Gashi a hannunka."
"Ohhh! Wad'annan?"
"Eh su."
"Ermm... na k'urjine ne d'azu a jikin bango."
"Dame ka k'urjine? Bango? Wannan beyi kalan k'urjini ba kaman yak'ushinka aka
tayi daba dan ba da senace fad'a kayi."
"LOL me kika miyar dani ne Princess am a Dad taya zanyi fad'a se son d'ina yamin
dariya ai, barin je inyi alwala."
"No" tayi sauri taja hannunsa "seka fad'a min ina ka samu wannan wounds d'in
tukuna."
"Na gaya miki k'urjinewa nayi jikin bango d'azu."
"So you are lying to your Princess now? Ni ka hanani yima k'arya amman kai kana
min ba damuwa." Tana kaiwa nan ta kawar da kanta daga kallonsa.
"Come on Princess bade zuciya zaki min ba, today is supposed to be the most
happiest day of our lives."
"Gashi kuma kanason kayi ruining by lying to me ba."
"Toh turn and look at me zan gaya miki." Banza dashi tayi se a karo na biyu,
"d'azu da labour yayi hitting naki ne shine kika rink'a yak'ushi na."
"Omi'god!" ta furta not believing abinda tayi wa Al'ameen nata. "Sweetheart am so
sorry you could have left akan ka bari nata yak'ushinka haka."
"I promised never to leave your side remember? Karki damu nan da two days duk
zasu warke."
"Am sorry kaji?"
"Ai wannan ba komai bane ganga da cemin da kikayi you hate me ni mugu ne." Ya
k'are zancen as if zeyi kuka ganin haka tayi frowning face nata acutely "you know I
don't mean that Sweetheart."
"That is why am still here."
"Je kayi alwala don't be late nima sena samu nayi wanka na kintsa jikina kaga har
Khaleefah yayi bacci." Bayi ya fice nan da nan ya d'auro alwala. Anan itama Zeezee
ta kwantar da Khaleefah ta shiga bayi tayi wanka ta kimtsa kanta sannan ta fito ta
tarar da Baaba zaune daga bakin k'ofa. Gaisuwa da barka ta mata itako ta amsa da
fara'a "har yaushe kika zo Baaba?"
"Ai tare muka taho duka halan zafin labor ya hanaki lura dani."
"Ayyah sannu toh."
"Nace in leqa jaririn namu ne?"
"Eh bismillah yana bacci ma." Daga fad'in haka ta d'au wayarta inda ta had'a
broadcast na mssg ta sanar da dukkanin dangi, k'awaye da kuma mutan arziki k'aruwan
data samu yau. Tun fa daga nan wayanta ya zama kaman call centre se kira kawai ake
ana mata barka. Da safe Mama, Lubiee da 'yarta da Mariam suka zosu harda su Ramlah,
aikuwa Ramlah taje ta maqale wa Uncle Soldier yau ma suka ta hira gashi ta k'ara
wayo sosai yanzu haka Ummie ma. Wajajen k'arfe 10am aka sallamo Zeezee daga asibiti
suka yo gida. Murna akan murna da Zeezee ta sanar da Mama cewa takwaran Baba tasa,
ba ita kad'ai ba har Mariam. Akwati sundum Mama ta sauk'e wa mijinta, se lalla6a
jariri suke, d'akin gabad'aya Al'ameen yabarwa masu jego ya koma d'ayan. Sosai
Zeezee da Khaleefah suke samun kulawa daga gun Mama sede ba kaman da ba a kullum
bata tare da Al'ameen nata a rana befi ta gansa sau d'aya ba nan ma sede daga nesa
bawai ta samu ta matso jikinsa ba. She misses his hugs and kisses more especially
his infectious sweet voice. Ana jibi suna rananda su Mama Babba, su Yasmeen, dasu
Ibraheem zasu zo kenan, bayan Mama ta had'a wa Zeezee ruwan wankanta ta fice
kitchen don cigaba da aiki. Anan Zeezee ta d'au wayarta ta kira Al'ameen da
alokacin yana waje da friends nasa sunzo masa barka shima. Ganin ita ke kira ya
sanya sa farin ciki sosai, excusing kansa yayi yaje gefe ya d'aga.
"Princess I miss you." Ya fara cewa.
"I miss you more and more and more Sweet voice, am feeling incomplete without
you."
"So as I, yaya kike da little Soldier'n mu?"
"Gashi nan a gefe na akan gado yana bacci."
"Send my kisses to him."
"I'll, kana ina ne?"
"Ina waje."
"Mu had'u a bayan BQ kaji?"
"Are you sure? Mama zata barki?"
"Ni I miss you zan saci idonta inzo, kaje ka jirani achan kaji?"
"Will it be possible ki fito da Khaleefah? I miss him also."
"Anything for you Sweetheart."
"Thats My Princess sekin zo toh."
"Alright am on my way" nan ta katse. Karap taji an bud'e k'ofa ganin Mariam ne
hankalinta yad'an kwanta.
"Adda Mariam!"
"Ya baki shiga wankan bane? Se ruwan ya huce tukuna?"
"A'a na shayar da Khaleefah ne yanzu zan shiga."
"Toh kiyi sauri, Ummie bata shigo nan bako?"
"D'azu na ganta da Afrah a backyard."
"Okay toh bari na duba can d'in wanka nake son yi mata."
"Uhumm" daga haka taja mata k'ofan ta rufe. Hijabi babba Zeezee 6urma sannan ta
tattara Khaleefah a hannunta da wayanta ta bud'e k'ofan sid'ak-sid'ak tana takawa
addu'anta baifin Allah kar ya kawo Mama path nata ba, cikin sa'a kuwa harta fice
basu had'u ba achan BQ ta tarar da Al'ameen zaune kan kujera yana backing nata, a
hankali ta tako har bayansa be jita ba. Tsugunawa tayi a hankali tayi pecking
kumatunsa daga gefe se anan ya juya a bit startled. "Princess!" Yayi exclaiming
hugging nata yakeson yi amman Khaleefah yayi cikas. Zaunar da ita yayi a gefensa
tare da amshe Khaleefah yata showering mishi kisses duk anan kallon sa Zeezee ke
cike da so dakuma k'auna, tarasa dalilin dayasa koda kwana d'aya tayi bata sa
Al'ameen a idonta ba seta ga ya k'ara mata k'warjini da kyau. Seda ya gama
showering kisses wa little soldier'n su sannan ya dawo kan Zeezee, matso da ita
kusa dashi yayi sosai sannan a hankali ya furta "I missed you Ummu Khaleefah I
missed everything about y-" his last word was crushed on her lips. A hankali tayi
owning lips nasa kissing him like domin shi aka turota duniya, shima with same
hunger and intensity yake kissing nata back basu saki juna ba seda Khaleefah ya
fara k'ananun kuka. A lokaci guda sukayi pulling out suna kallon Khaleefah. "Why
does he have to ruin this happy moment for us Sweetheart?" ta tambaya tana mai
murmushi.
"Ko yunwa yake ji?" Ya amsa tare da zaro hannunsa daga bayanta.
"It might be miqo min mishi." A cinyanta ya ajiye sa sannan ta d'aga hijabinta da
riganta ta shiga feeding nashi a hankali shiko se sha yake da zafi da zafi.
Murmushi Al'ameen ya saki at their cute and lovely sight. He can't ask for a better
family saboda Allah ya riga ya basa BEST!
D'an cewa da yayi bari ya gyara hijabin Zeezee gani yayi like ya fad'a kan fuskan
Khaleefah kawai yaga yaro ya d'aga hannunsa ya dafa kan d'ayan maman Zeezee dashi
ina irin its mine d'innan don't touch it. Dariya shida Zeezee suka 6arke dashi,
"Princess kina ganin min wonders yau."
"Ai fa nashi ne kar ka ta6a."
"Nifa bama ta6awa zanyi ba hijabin ki nakeson in gyara naga ya tare mai fuska."
"LOL toh shikam ya fassara."
"Ahh lallai kam don na hak'ura na barshi yana sha shine zemin haka ko?"
"Toh ya ka iya ai yanzu ya tashi daga naka ya dawo nasa."
"A'a thats not true."
"Toh ya ka iya?"
"The whole of you is mine Princess yanzu de na hak'ura na bashi amman nan da
shekara d'aya da abu kika yaye shi kinga ya dawo property na again as it always
have been."
"Ko a yanzun ma naka ne My Soldier don't mind Khaleefah."
"Thats my Woman." Seda Khaleefah yayi dam sannan ta miyar da abinta cikin riga
ta sauk'e hijabin. Kanta ta kwantar a k'irjin Al'ameen nata a yayinda ya zagaye
hannayensa a bayanta yana shafawa soothingly.
"I miss us cuddling, I miss your muscular and fragrant body Sweetheart."
"I miss your arms and legs wrap around me, my nights are so so boring without
you, you lit my entire life Ummu Khaleefah."
"As you do to mine also Daddy'n Khaleefah" ta d'ago kanta tana kallonsa.

A hankali ya shiga matso da face nasa ready to kiss her again saboda na d'azu
Khaleefah yayi ruining musu. Se gab da lips nasu ya kusa had'ewa wayan Zeezee ya
shiga ringing ruining thier moment again. Kaman zatayi kuka ta furta "damn it!"
Tare da had'e rai a yayinda Al'ameen ya tsaya yana murmushi sosai. Ganin wa ke kira
yasa ta zaro idanunta waje a dalilin haka Al'ameen ya tambayeta ko waye ne.
"Mama ce Sweetheart na shiga uku, tace nayi wanka da kanta ta had'a min ruwan
zafin nak'i nazo nan inata kissing naka."
"LOL calm down."
"What do you mean calm down? Dan ba kai zata masife ba ko?"
"Toh kawo in d'aga in cemata muna tare."
"Ta yankani kakeso wato, tace muna meh?"
"Kissing of course" ya fad'a mockingly yana mata dariya.
"Ai ba laifinka bane nida na fiton ne-" shutting nata yayi da another hot kiss me
ratsa jiki, tsan-tsan pleasure har yasar da wayan Zeezee tayi Khaleefah ma daba don
Al'ameen ya taresa ba da ta yasar da shi, sun d'au tsawon lokaci suna abu d'aya
sannan chaaaan Al'ameen yayi pulling out a hankali teasing her the more. "I love
you Ummu Khaleefah My Princess."
Jikinsa ta lume tana sake rik'e Khaleefah gagam a jikinta. "How I wish this
moment will last forever Sweetheart, idan ina tare da kai I tend to forget all of
my problems, I love all of you, your curves and edges, your perfect imperfections
you mean the world yo me Abu Khaleefah." Hannunsa yasa a bayanta drawing her closer
to him. "I love you more Princess you are my worst distraction, you are the most
happiest thing that has ever happened to me, just a mere thought of you tends to
make me forget all of my problems, anytime am near you I tend to be problem free
you are the remedy to all of my sicknesses, you are the reason why I'm still
breathing today because without you am breathless." Murmushi take sosai tana
blushing jin wannan daddad'an kalamun daga bakin heart race nata. "Thank you Abu
Khaleefah thanks for loving me."
"What for Princess? Nine da godiya ba ke ba."
"I have to thank you for coming into my life, for chosing me amongst all of the
women in this entire universe."

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


*ZAIMEEN❣ Flames* 🔥🔥🔥
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣7⃣

"Its my biggest pleasure Princess am lucky dana kasance guy da yayi


stealing heart naki and am also happy da kikayi accepting d'ina into your life when
I came. Yau she ne bikin sunan Khaleefah jibi koh?"
"Yes Sweetheart."
"I have a suprise for you."
"Awww!" Tayi exclaiming tare da tasowa daga jikinsa tana positioning Khaleefah
kada ya fad'i. "What suprise Sweet voice?"
"Princess ana gayawa mutum suprise ne kuma?" Ya had'e rai acutely.
"Ba'ayi amman ai kai zaka iya fad'a min tunda mu biyu ne kawai anan."
"LOL toh ai ked'in ce banason kiji."
"Please manaaaa." Ta fad'a tana bubbuga k'afanta.
"Yi hak'uri manaaaa" shima ya koikoyeta.
"Ka fara ko?"
"Allah kaimu jibi Princess." Shiru tayi not ready to talk, "bazaki ce ameen ba?
So kike in mutu kafin nan?"
"A'a ameen, ameen thumma ameen" ta amsa da wuri. Yana murmushi yace, "you should
get going kije kiyi wanka kar Mama tayi fushi."
"OMG! Mama! Na shiga uku, Sweetheart wallahi na manta totally ina waya na?"

Neman wayan suka shiga yi wanda Al'ameen ya samu k'ark'ashin kujeran da suke
zaunen. "You won't believe this!" Yayi exclaiming yana kallon screen d'in.
"What is it?"
"20 missed calls, 6 from Mama, 5 from Mariam, and 9 from Lubiee."
"OMG Mama will skin me alive."
"Muje in rakaki I'll explain everything to her."
"What! Are you kidding me? So kake tamin duka? Tasan ma gunka nazo kenan, how
comes I didn't here it ring?"
"Maybe daya fad'i ne ya shiga silent."
"Uhn rik'en Khaleefah na miqe" amsan Khaleefah yayi seda ta miqe ya miyar mata
dashi nan suka shiga takawa dai-dai bakin corner'n suka tsaya "kar Mama ta ganni
I'll stop here" yayi maganan tare da kama hannunta cikin nasa yana murzawa a
hankali.
"Thank you."
"I love you okay?"
"I know Sweetheart."
"Take care se mun yi magana."
"I love you more Sweetheart I'll take care of myself and Khaleefah for you."
"I know you will, you should get going." Sam bata son tafiyan a hankali ta shiga
takawa har anan Al'ameen be sake hannunta ba the more tana takawa the more hannunta
ke neman zamewa daga nasa suna masu kallon juna har seda ya gama zamewan gabad'aya,
kafin ta juya Al'ameen ya mata blowing kiss murmushi ta sakar masa sannan ta juya
seda yaga ta shige ciki sannan ya fito ya koma gun friends nasa.

Tana shiga d'akin nata taga Mama tsaye da Mariam a gefenta gabad'ayan su tashin
hankali ne bayyane karara a fuskokinsu. Kallon da Mama ke mata kad'ai ya isa yasa
ta sakin fitsari. Don kanta tace, "Mama kiyi hak'uri don Allah."
"Na d'au ai guduwa akayi da ke kokuma da kin koma gun shi wanda ya rik'ekin ya
cigaba da miki zaman jegon."
"Mama me kuma kike fad'i?"
"K'aniyanki nake fad'a amso min Khaleefah kiyi mar wanka Mariam haka su Mama
Babba zasu zo su sameki ai da dotti ke kuma." Bayan Mariam ta amshi Khaleefah ta
tub'e mishi kaya ta shiga yimai wanka.
"Kina tsaye gun bazaki shige bayin kiyi wanka bane?" Mama ta tsawata mata.
"Mama yanzu da d'ana ma haka zaki tayi min masifa."
"Aww dan ban gaura miki mari ba ko? Wajen Ya Al'ameen kikaje ko?"
"Ni ba gunsa naje ba."
"Wajen uwarki kika je halan missed calls nawa na miki? ba ma ni ba harta su
Mariam duk kika k'i d'agawa ke gaki me miji ko?"
"Mama nifa ba gunsa naje ba."
"Zan kwad'e ki wallahi kice min ba gunsa kika je ba ina kikaje?" Tana turo baki
tace; "ba gunsa ban-"
Ganin Mama ta d'auro niyan yo kanta dan kai mata bugi ta falfala da gudu tayi
bayi tare da sa lock. "Me kan gwanda kawai mutum ya haihu ma bazeyi hankali ba,
maza kiyi wankan dama ki kuma k'ara ruwan zafi akai don nasan ya huce."
"Mama da zafi fah."
"Banason shirirta fa Zeezee kinsan amfanin ruwan zafin nan agareki kuwa?"
"Mama so kike in k'ona jikina in dawo bak'a dama already Ya Al'ameen da Khaleefah
sun fini haske."
"Uwaki nace nima haka nasha gashi ba gomma ku bama namu da suruka ke shod'e mu da
tsumagiya cikin ruwan zafi fah? Allah ki k'ara ruwan zafin nan kona nemo spare key
na bud'e da kaina na yi miki wankan."
"Ai Ya Al'ameen baze barki ba."
"Shi Ya Al'ameen d'in kenan, Mariam miqo min key'n a side drawer'n chan naga
achan suke ajiyewa."
"A'a please kiyi hak'uri zanyi da kaina zan k'ara ruwan zafin kuma."
"Maras kunya kawai." Nan da nan tayi wankan ta fito ta tsara kwalyarta. Da yamma
su Mama Babba harda Hajiya Sadeeyah dasu Yasmeen and Ibraheem suka iso even though
su Ibraheem ne suka iso at last. After the hugs and pecks sukayi mata barka sannan
sukasa wa Khaleefah albarka kowa se yaba kyansa yake yana cewa yaro sak Babansa.

~~~*RANAR SUNA*~~~
Tamkar bikin aure haka aka k'ayatar da bikin sunan Khaleefah, fili musamman
sukayi renting inda aka k'ayata shi da abubuwan tafiyar wa mutum da imani, su
Mariam harda ashobe sukayi abin se wanda ya gani gwanin sha'awa. Haka zalika 'yan
Tm Maj-Gen Al'ameen dukaninsu da ashobensu se kwaso shoki suke. Souvenirs sekace
hauka customized agogo, robobi, jaka, key holder, memo and pen ba abinda Al'ameen
beyi ba suna ne like no other. Abinci har yaso yin kwante, everything was in
abundant supply. Waleemah akayi na k'in k'ari sannan daga k'arshe suka cashe harta
Mama seda su Zeezee suka sata rawa haka Mama Babba ma, kad'an suka taka suka koma
suka zauna suka barwa su Zeezee filin. Se maghrib suka rufe taron.

**
Wajajen 9pm Zeezee na zaune kan gado a d'akinta se dudduba d'unbun kayakin da ita
da Khaleefah suka samu take, wanda Mama Babba da Hjy Sadeeyah suka kawo mata
kad'ai ya iya had'a kayan lefen wata, gana Ya Ibraheem shima sosai yayi k'ok'ari
dan ko akwati ya had'o mata. Ya Omar da take ce mai ba a cin arzikinsa shima yayi
abin kai ya kawo mata zannuwa biyar biyu super sauran ukun kuma wasu masu tsada da
kayan baby dozen, Mariam da Yasmeen kuwa akwati suka had'o mata su biyu. Anty Fatee
da Lubiee suma had'e kai sukayi suka kawo mata akwati, kayaki de sun mamaye d'aki
se mutum yayi dagaske yake samun gun sa k'afa. Tana cikin duban kayakin Yasmeen ta
shigo da sallama bayan Zeezee ta amsa tace, "ki fito waje Ya Al'ameen na neman ki."
"Mama na ina?"
"Tana wanka" tayi mata k'arya.
"Toh kice mishi Ina zuwa."
"Tam" tana kaiwa nan ta fice. Duban Khaleefah tayi ta tabbata baccinsa yayi nisa
sannan ta sake pancaking face nata ta yafa gyalenta ta fice tiryan-tiryan. Ta bud'e
k'ofa ta fita tana rufewa kawai taga haske yana bayyana daga nowhere, hakan ya
cigaba dayi har seda ya isa wani spot da aka yisa inform of heart shape "omg!" Ta
furta ganin sabuwar mota k'irar latest model na Ford jeep motarta tada. Sabuwa gal
ce pil fara kuma fake acikin heart spot d'in. Kaman a kyaftawan ido ta hango
Al'ameen tsaye gefen motan fuskansa d'auke with the most beautician smile ever!
"Happy third anniversary! ZaiMeen" taji people from nowhere suna wishing nata.
Ashe yau ne third anniversary'nta amman gabad'aya ta mance dan hidima. Bata san a
lokacinda ta fara zubar da hawayen jin dad'i ba ashe wannan suprise ne Al'ameen
keda in mind mata ranan, this is one of her best suprises. A nitse yake takawa
majestically ya iso bakin k'ofan inda take tsaye ya rik'o both hands nata cikin
nasa yana mata murmushi "Happy Third Anniversary Ummu Khaleefah My Princess, I love
you so much may we continue to prosper together till death do us path." Pecking kan
hannun nata yayi a hankali dan dad'i tama kasa cewa komi kawai jansa tayi ta shiga
hugging nasa "I'm totally out of words Sweetheart you took me by suprise, I can't
stop shouting I love you because you're damn so sweet Khaleefah and I are so lucky
to have you in our lives, thank you so much for this wonderful suprise and happy
anniversary to you also, I love you." A hankali tayi breaking hug d'in. Hannu yasa
a aljihunsa tare da zaro key'n motar yasa mata a hannu "the car parked over there
is yours here is your key, muje kiyi parking a lot."

"Why are you so sweet?"


"Because am married to the world's BEST wife and a mother." Ya sanar da ita yana
me murmushi sosai. A hankali tasa hannunta a nasa suka shiga takawa inda mutanen
gun ke binsu da tafi har seda suka shiga motan. Reverse tayi sannan tayi gaba ta
paka motan a space da akayi creating mata next to motan Al'ameen. Wutan motan ya
kunna anan taga wata k'aramar pack dake ajiye a tsakankaninsu. "Sweetheart not
again please."
"Naki ne open it."
"How can I ever repay you? Allah kad'ai ze iya biyanka min, addu'a na a kullum
maka baya fin Allah ya farinta maka ranka kamar yadda kake farin tamin nima, I love
you so much."
"I love you more." Grabbing pack d'in tayi ta shiga 6a6alla glues da sheet d'in
har seda tayi discovering wasu had'ad'dun diamond earrings and necklace da kuma
wani bracelet na pure silver da akayi forging ZAIMEEN akai. "Omi'god how I wish zan
iya nuna maka kalan farin ciki da dad'in da nake ji yanzu."
"Its already written everywhere on your face here" yayi pecking goshinta, "here"
cheeks nata na dama, "here" yayi ana hagu haka yabi face nata gabad'aya yana
kissing nasu lightly teasing her in the process se dariya take which is damn cute,
seda ya tabbata kisses nasa suna raining a face nata sannan ya zari bracelet d'in
daga cikin pack d'in ya bud'e mabud'in sannan ya jawo hannunta ya shiga sanya mata
shi, bayan da yayi clipping yace, "beautiful just as I imagined or even more inason
ki ringa sashi kullum don't ever take it out, can you promise me that?"
"Anything for My Sweet Hubby duk abinda kakeso shi zan maka muddin be sa6awa
addinin muslinci ba, kamar yadda kasa min yau inba wai kai kazo ka cire ba ni bazan
ta6a cirewa ba se ranan da kuma kai ka ce in cire you have My solemn words."
"Thank you Princess."
"Nice da godiya, I miss those sugar lips."
"Not as how I missed yours can I kiss them?"
"They are yours remember? Kai kake da iko dasu." A hankali yayi owning lips nata
sukayi breaking into the most heart melting kiss assuring each other how much they
love each other, kaman kar su sake juna suke ji, da k'yar tayi pulling out tayi
placing kanta a ha6ansa a yayinda wani wutan sonsa ke sake mamaye mata zuciya. Anya
kuwa zata iya rayuwa ba Al'ameen? Kai! She don't think so.
"Ina Little Soldier'n mu?"
"Na barosa aciki yana ta bacci ya wahala yau a hannun mutane yadda kasan ince
abani abuna."
"LOL" ya saki dariya kad'an "da kuwa an zagaya Princess d'ina a gari ace game
rowan baby."
"Haha kai bakasan yadda nake ji da Khaleefah bane amman fa bekai yadda nake ji da
kai ba."
"I know Sweetheart naso tare kuka fito dashi tun shekaran jiya ban sake sasa a
idanu na ba."
"Ayyah I know how that must feel, zaka jirani anan inje in d'auko maka shi?"
"Mama zata barki?"
"I pray she'll idan ma bata bari ba na saci idonta."
"LOL Princess bakiya tsoro ko? Toh idan kinzo ki sameni a new site d'incan."
"Toh kai kad'ai ne ba?"
"Ai in da wani aciki barin bari kije ba saboda kishinki nake sosai Princess."
"Awww!" taja hancinsa "I'll be right back."
"Yauwa until you do" sanda yaga shigewanta ciki sannan ya nufi new site daya koma
ciki yanzu saboda wanda suke ciki da Zeezee a da mutane sunyi yawa.

Zeezee ta d'au Khaleefah tazo fita kenan suka ci karo gbam! Da Mama kad'an ya
rage basuyi gware ba. Cike da fargaba tace, "phew! You startled me Mama."
"Eh baki da gaskiya kam ai dole kice kinji tsoro."
"Mama please karki hanani Ya Al'ameen nason yaga Khaleefah ne I won't take long."
Shiru Mama tayi wane me nazari "please Mama."
"Kije kika bari wani abin ya shiga tsakanin ku kuma ni ba ruwa na."
"Haba Mama se kace wacce batasan addini ba banida tsarki fa kin manta ne."
"Ni na san muku ne."
"Inje?"
"Kije ko na hanaki ma nasan zaki saci idona."
"Yeyy! Thanks Mama I love you."
"Naji fice." Nan da nan ta fice achan new site d'in ta samu Al'ameen zaune a
bakin gado. Yana ganinta ya miqe ya amshi Khaleefah da tashinsa kenan da daga
bacci.
"Kaga wai da yazo hannun Daddy'nshi ya bud'e ido."
"Father-son bond kike ji."
"Aww haka ne? Bari in sambad'o Little Princess d'ina mana kaga, nima sak me
kamanni na zan haifo."
"LOL ai jini na yafi naki k'arfi duka yaran mu in shaa Allah dani zasuyi kama."
"Allah k'arya ne da ni ne." Tayi maganan wane zatayi kuka.
"Kisa wasa, ai gashi kin fara gani daga kan Khaleefah."
"Ai idan na haifi d'aya again naga me kamanninka ne toh na yafe sauran ban sake
haihuwa."
"Ai sede ki yafen amman kin kafa haifan masu kamana kenan."
"lol ma da sauk'i ai kai d'in kyakkyawa ne atleast koda sun yo kamannin naka ba
laifi tunda suna yin kyau."
"How I wish zamu kwana tare yau Princess I miss you."
"Ba kai kad'ai ba harta ni Sweetheart I miss you."
"Can't we sleep just for today?"
"Mama zata kashe ni gobe."
"Zan sa Mama Babba tayi mata magana, mu kwana anan kinji?"
"Yau nida Khaleefah baza muyi wankan dare ba kenan."
"Zaku yi mana ga bathroom da komi a ciki."
"As for me yes but shi se a cikin bath tub nasa ake masa kuma ni ban iya bama."
"Ni na iya zamuyi masa a cikin jacuzzi."
"Uhn-uhn fa Sweetheart karka jefa min yaro a cikin jacuzzi tam!"
"LOL Princess shin wai se yaushe ne zaki dena under estimating d'ina ki yarda ni
d'innan inada basira da baiwa."
"Hehe toh idan ba neman surutu ba meh had'inka da wanka wa jariri?"
"Time da aka haifi Aysha kullum a idona ake yi mata wanka time d'in na gama
first degree d'ina ina hutu a gida."
"Wow really! My legend ba wasa, Toh idan ka mishi wani kaya zesa? Babu ko d'aya
anan."
"Bari in kira Addar mu Yasmeen in rok'eta ta d'auko miki kayan baccinki dana
Khaleefah ko?"
"Eh ayi hakan Yasmeen nada sauk'in kai unlike Adda Mariam zatayi mana." Nan da
nan ya kira Yasmeen ya rok'eta da ta taimakesu ta kawo musu kayakin baccin Zeezee
da na Khaleefah, sanin itama tayi hakan lokacinda ta haifi first born nata yasa ta
gane how exactly Al'ameen and Zeezee must be missing each other nan da nan ta kai
musu kayan ta fice bayan dogon godiyan da Zeezee tata yi mata.

Ai da mamaki Zeezee ta tsaya tana kallon yadda Al'ameen keyi wa Khaleefah wanka
wane na mace, a hankali yake binsa so gently sekace ba na miji ba. Wanke sa yayi
tas ko kuka Khaleefah beyi ba har aka gama sannan ya shafa masa lotion nasa ya sa
masa pampers tukuna ya sanya masa overall nasa. Duk anan banda ido ba abinda Zeezee
ke binsa dashi, ko ita bazata iya yin abinda Al'ameen yayi ba gani take like idan
ta rik'e yaron ze su6uce mata a hannu.

"Sweetheart you are such a genius, I can't ask for more."


"Kin yarda yanzu?"
"100%."
"Sauran ke ko kema na miki wankan?"
"O'o ni zanyi da kaina."
"Tam kije Khaleefah and I are waiting for you." Ba tare da 6ata lokaci ba ta
shiga bayin.
On Mama's side kuwa 10pm na bugawa ta shigota d'akin Zeezee don yi ma Khaleefah
wanka. Sede to her ultimate suprise taga ba Zeezee. "Bade 'yar nan bata dawo ba har
yanzu?" ta tambayi kanta. Dai-dai nan shigowan Yasmeen da baby'nta dake 8 months
old me suna Jameela amman suke kira da Iman. "Yauwa Yasmeen ina Zeezee ta shiga
ne?"
"Uhn, nima ban ganta ba fa tun d'azu." Har Mama ta yarda amman sanin duk
lokacinda Yasmeen zatayi k'arya seta soma da 'uhn' yasa ta fahimci k'arya take yi
mata. "Yasmeen! Maman Suleiman da Jameela."
"Na'am Mama."
"Ina Zeezee nace?"
"Uhn nima fa ban gan taba."
"Eh raina min hankali de, ko a jinki ban san k'arya kike yimin bane? Ina Zeezee
nace?"
"Mama please ki barta ta kwana achan."
"La ha ilaaaa!" Ta fad'a tana tafe hannu cike da mamaki.
"Me kike nufi dana barta ta kwana achan? Bade abinda keda mijinki kukayi a
haihuwar Suleiman ba su Zeezee keda shirin yi?" Shiru Yasmeen tayi ta shiga bawa
Iman frisco nata. "Dake fa nake kin min shiru se kinji sauk'an bugi ko?"
"Mama eh."
"Na shigesu ni Hafsah! Yaran zamani wai ce muku akayi ana haka ne? Shin me
mazajen naku suke baku dako sati baku iya jura idan baku kusa dasu?"
"Soyayya mana Mama da me?"
"Aww ma har haka kike cemin wato."
"Kefa kika tambaya nikuma na baki amsa." Ganin Mama zata yo kanta da nufin kai
mata bugi tasa ihuu "Mama please kar Iman ta fad'i" don haka kad'ai Mama ta barta.
"Zakuyi bayani maza je ki kirata kice ta dawo."
"Sunyi bacci fa by now."
"K'aniyanki da by now d'in, kije ki kirasu do Allah."
"Allah sunyi bacci."
"Toh baza suyi wanka bane? Ni ban damu da Zeezee bama amman mijina fah?"
"Karki damu zasuyi masa, sun sani na d'auko musu kayakin baccinsa da duk wani
abinda ya kamata d'azu."
"Kice da ke aka had'a baki kema munafuka, yayi kyau zata gamu dani gobe." Tana
kaiwa nan ta fice d'akin data sauk'a ta kwanta.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


*ZAIMEEN❣ FLAMES🔥🔥🔥*
Beeenovels.blogspot.com
👄👄👄👄👄
🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣7⃣

"Its my biggest pleasure Princess am lucky dana kasance guy da yayi


stealing heart naki and am also happy da kikayi accepting d'ina into your life when
I came. Yau she ne bikin sunan Khaleefah jibi koh?"
"Yes Sweetheart."
"I have a suprise for you."
"Awww!" Tayi exclaiming tare da tasowa daga jikinsa tana positioning Khaleefah
kada ya fad'i. "What suprise Sweet voice?"
"Princess ana gayawa mutum suprise ne kuma?" Ya had'e rai acutely.
"Ba'ayi amman ai kai zaka iya fad'a min tunda mu biyu ne kawai anan."
"LOL toh ai ked'in ce banason kiji."
"Please manaaaa." Ta fad'a tana bubbuga k'afanta.
"Yi hak'uri manaaaa" shima ya koikoyeta.
"Ka fara ko?"
"Allah kaimu jibi Princess." Shiru tayi not ready to talk, "bazaki ce ameen ba?
So kike in mutu kafin nan?"
"A'a ameen, ameen thumma ameen" ta amsa da wuri. Yana murmushi yace, "you should
get going kije kiyi wanka kar Mama tayi fushi."
"OMG! Mama! Na shiga uku, Sweetheart wallahi na manta totally ina waya na?"

Neman wayan suka shiga yi wanda Al'ameen ya samu k'ark'ashin kujeran da suke
zaunen. "You won't believe this!" Yayi exclaiming yana kallon screen d'in.
"What is it?"
"20 missed calls, 6 from Mama, 5 from Mariam, and 9 from Lubiee."
"OMG Mama will skin me alive."
"Muje in rakaki I'll explain everything to her."
"What! Are you kidding me? So kake tamin duka? Tasan ma gunka nazo kenan, how
comes I didn't here it ring?"
"Maybe daya fad'i ne ya shiga silent."
"Uhn rik'en Khaleefah na miqe" amsan Khaleefah yayi seda ta miqe ya miyar mata
dashi nan suka shiga takawa dai-dai bakin corner'n suka tsaya "kar Mama ta ganni
I'll stop here" yayi maganan tare da kama hannunta cikin nasa yana murzawa a
hankali.
"Thank you."
"I love you okay?"
"I know Sweetheart."
"Take care se mun yi magana."
"I love you more Sweetheart I'll take care of myself and Khaleefah for you."
"I know you will, you should get going." Sam bata son tafiyan a hankali ta shiga
takawa har anan Al'ameen be sake hannunta ba the more tana takawa the more hannunta
ke neman zamewa daga nasa suna masu kallon juna har seda ya gama zamewan gabad'aya,
kafin ta juya Al'ameen ya mata blowing kiss murmushi ta sakar masa sannan ta juya
seda yaga ta shige ciki sannan ya fito ya koma gun friends nasa.

Tana shiga d'akin nata taga Mama tsaye da Mariam a gefenta gabad'ayan su tashin
hankali ne bayyane karara a fuskokinsu. Kallon da Mama ke mata kad'ai ya isa yasa
ta sakin fitsari. Don kanta tace, "Mama kiyi hak'uri don Allah."
"Na d'au ai guduwa akayi da ke kokuma da kin koma gun shi wanda ya rik'ekin ya
cigaba da miki zaman jegon."
"Mama me kuma kike fad'i?"
"K'aniyanki nake fad'a amso min Khaleefah kiyi mar wanka Mariam haka su Mama
Babba zasu zo su sameki ai da dotti ke kuma." Bayan Mariam ta amshi Khaleefah ta
tub'e mishi kaya ta shiga yimai wanka.
"Kina tsaye gun bazaki shige bayin kiyi wanka bane?" Mama ta tsawata mata.
"Mama yanzu da d'ana ma haka zaki tayi min masifa."
"Aww dan ban gaura miki mari ba ko? Wajen Ya Al'ameen kikaje ko?"
"Ni ba gunsa naje ba."
"Wajen uwarki kika je halan missed calls nawa na miki? ba ma ni ba harta su
Mariam duk kika k'i d'agawa ke gaki me miji ko?"
"Mama nifa ba gunsa naje ba."
"Zan kwad'e ki wallahi kice min ba gunsa kika je ba ina kikaje?" Tana turo baki
tace; "ba gunsa ban-"
Ganin Mama ta d'auro niyan yo kanta dan kai mata bugi ta falfala da gudu tayi
bayi tare da sa lock. "Me kan gwanda kawai mutum ya haihu ma bazeyi hankali ba,
maza kiyi wankan dama ki kuma k'ara ruwan zafi akai don nasan ya huce."
"Mama da zafi fah."
"Banason shirirta fa Zeezee kinsan amfanin ruwan zafin nan agareki kuwa?"
"Mama so kike in k'ona jikina in dawo bak'a dama already Ya Al'ameen da Khaleefah
sun fini haske."
"Uwaki nace nima haka nasha gashi ba gomma ku bama namu da suruka ke shod'e mu da
tsumagiya cikin ruwan zafi fah? Allah ki k'ara ruwan zafin nan kona nemo spare key
na bud'e da kaina na yi miki wankan."
"Ai Ya Al'ameen baze barki ba."
"Shi Ya Al'ameen d'in kenan, Mariam miqo min key'n a side drawer'n chan naga
achan suke ajiyewa."
"A'a please kiyi hak'uri zanyi da kaina zan k'ara ruwan zafin kuma."
"Maras kunya kawai." Nan da nan tayi wankan ta fito ta tsara kwalyarta. Da yamma
su Mama Babba harda Hajiya Sadeeyah dasu Yasmeen and Ibraheem suka iso even though
su Ibraheem ne suka iso at last. After the hugs and pecks sukayi mata barka sannan
sukasa wa Khaleefah albarka kowa se yaba kyansa yake yana cewa yaro sak Babansa.

~~~*RANAR SUNA*~~~
Tamkar bikin aure haka aka k'ayatar da bikin sunan Khaleefah, fili musamman
sukayi renting inda aka k'ayata shi da abubuwan tafiyar wa mutum da imani, su
Mariam harda ashobe sukayi abin se wanda ya gani gwanin sha'awa. Haka zalika 'yan
Tm Maj-Gen Al'ameen dukaninsu da ashobensu se kwaso shoki suke. Souvenirs sekace
hauka customized agogo, robobi, jaka, key holder, memo and pen ba abinda Al'ameen
beyi ba suna ne like no other. Abinci har yaso yin kwante, everything was in
abundant supply. Waleemah akayi na k'in k'ari sannan daga k'arshe suka cashe harta
Mama seda su Zeezee suka sata rawa haka Mama Babba ma, kad'an suka taka suka koma
suka zauna suka barwa su Zeezee filin. Se maghrib suka rufe taron.
**
Wajajen 9pm Zeezee na zaune kan gado a d'akinta se dudduba d'unbun kayakin da ita
da Khaleefah suka samu take, wanda Mama Babba da Hjy Sadeeyah suka kawo mata
kad'ai ya iya had'a kayan lefen wata, gana Ya Ibraheem shima sosai yayi k'ok'ari
dan ko akwati ya had'o mata. Ya Omar da take ce mai ba a cin arzikinsa shima yayi
abin kai ya kawo mata zannuwa biyar biyu super sauran ukun kuma wasu masu tsada da
kayan baby dozen, Mariam da Yasmeen kuwa akwati suka had'o mata su biyu. Anty Fatee
da Lubiee suma had'e kai sukayi suka kawo mata akwati, kayaki de sun mamaye d'aki
se mutum yayi dagaske yake samun gun sa k'afa. Tana cikin duban kayakin Yasmeen ta
shigo da sallama bayan Zeezee ta amsa tace, "ki fito waje Ya Al'ameen na neman ki."
"Mama na ina?"
"Tana wanka" tayi mata k'arya.
"Toh kice mishi Ina zuwa."
"Tam" tana kaiwa nan ta fice. Duban Khaleefah tayi ta tabbata baccinsa yayi nisa
sannan ta sake pancaking face nata ta yafa gyalenta ta fice tiryan-tiryan. Ta bud'e
k'ofa ta fita tana rufewa kawai taga haske yana bayyana daga nowhere, hakan ya
cigaba dayi har seda ya isa wani spot da aka yisa inform of heart shape "omg!" Ta
furta ganin sabuwar mota k'irar latest model na Ford jeep motarta tada. Sabuwa gal
ce pil fara kuma fake acikin heart spot d'in. Kaman a kyaftawan ido ta hango
Al'ameen tsaye gefen motan fuskansa d'auke with the most beautician smile ever!
"Happy third anniversary! ZaiMeen" taji people from nowhere suna wishing nata.
Ashe yau ne third anniversary'nta amman gabad'aya ta mance dan hidima. Bata san a
lokacinda ta fara zubar da hawayen jin dad'i ba ashe wannan suprise ne Al'ameen
keda in mind mata ranan, this is one of her best suprises. A nitse yake takawa
majestically ya iso bakin k'ofan inda take tsaye ya rik'o both hands nata cikin
nasa yana mata murmushi "Happy Third Anniversary Ummu Khaleefah My Princess, I love
you so much may we continue to prosper together till death do us path." Pecking kan
hannun nata yayi a hankali dan dad'i tama kasa cewa komi kawai jansa tayi ta shiga
hugging nasa "I'm totally out of words Sweetheart you took me by suprise, I can't
stop shouting I love you because you're damn so sweet Khaleefah and I are so lucky
to have you in our lives, thank you so much for this wonderful suprise and happy
anniversary to you also, I love you." A hankali tayi breaking hug d'in. Hannu yasa
a aljihunsa tare da zaro key'n motar yasa mata a hannu "the car parked over there
is yours here is your key, muje kiyi parking a lot."

"Why are you so sweet?"


"Because am married to the world's BEST wife and a mother." Ya sanar da ita yana
me murmushi sosai. A hankali tasa hannunta a nasa suka shiga takawa inda mutanen
gun ke binsu da tafi har seda suka shiga motan. Reverse tayi sannan tayi gaba ta
paka motan a space da akayi creating mata next to motan Al'ameen. Wutan motan ya
kunna anan taga wata k'aramar pack dake ajiye a tsakankaninsu. "Sweetheart not
again please."
"Naki ne open it."
"How can I ever repay you? Allah kad'ai ze iya biyanka min, addu'a na a kullum
maka baya fin Allah ya farinta maka ranka kamar yadda kake farin tamin nima, I love
you so much."
"I love you more." Grabbing pack d'in tayi ta shiga 6a6alla glues da sheet d'in
har seda tayi discovering wasu had'ad'dun diamond earrings and necklace da kuma
wani bracelet na pure silver da akayi forging ZAIMEEN akai. "Omi'god how I wish zan
iya nuna maka kalan farin ciki da dad'in da nake ji yanzu."
"Its already written everywhere on your face here" yayi pecking goshinta, "here"
cheeks nata na dama, "here" yayi ana hagu haka yabi face nata gabad'aya yana
kissing nasu lightly teasing her in the process se dariya take which is damn cute,
seda ya tabbata kisses nasa suna raining a face nata sannan ya zari bracelet d'in
daga cikin pack d'in ya bud'e mabud'in sannan ya jawo hannunta ya shiga sanya mata
shi, bayan da yayi clipping yace, "beautiful just as I imagined or even more inason
ki ringa sashi kullum don't ever take it out, can you promise me that?"
"Anything for My Sweet Hubby duk abinda kakeso shi zan maka muddin be sa6awa
addinin muslinci ba, kamar yadda kasa min yau inba wai kai kazo ka cire ba ni bazan
ta6a cirewa ba se ranan da kuma kai ka ce in cire you have My solemn words."
"Thank you Princess."
"Nice da godiya, I miss those sugar lips."
"Not as how I missed yours can I kiss them?"
"They are yours remember? Kai kake da iko dasu." A hankali yayi owning lips nata
sukayi breaking into the most heart melting kiss assuring each other how much they
love each other, kaman kar su sake juna suke ji, da k'yar tayi pulling out tayi
placing kanta a ha6ansa a yayinda wani wutan sonsa ke sake mamaye mata zuciya. Anya
kuwa zata iya rayuwa ba Al'ameen? Kai! She don't think so.
"Ina Little Soldier'n mu?"
"Na barosa aciki yana ta bacci ya wahala yau a hannun mutane yadda kasan ince
abani abuna."
"LOL" ya saki dariya kad'an "da kuwa an zagaya Princess d'ina a gari ace game
rowan baby."
"Haha kai bakasan yadda nake ji da Khaleefah bane amman fa bekai yadda nake ji da
kai ba."
"I know Sweetheart naso tare kuka fito dashi tun shekaran jiya ban sake sasa a
idanu na ba."
"Ayyah I know how that must feel, zaka jirani anan inje in d'auko maka shi?"
"Mama zata barki?"
"I pray she'll idan ma bata bari ba na saci idonta."
"LOL Princess bakiya tsoro ko? Toh idan kinzo ki sameni a new site d'incan."
"Toh kai kad'ai ne ba?"
"Ai in da wani aciki barin bari kije ba saboda kishinki nake sosai Princess."
"Awww!" taja hancinsa "I'll be right back."
"Yauwa until you do" sanda yaga shigewanta ciki sannan ya nufi new site daya koma
ciki yanzu saboda wanda suke ciki da Zeezee a da mutane sunyi yawa.

Zeezee ta d'au Khaleefah tazo fita kenan suka ci karo gbam! Da Mama kad'an ya
rage basuyi gware ba. Cike da fargaba tace, "phew! You startled me Mama."
"Eh baki da gaskiya kam ai dole kice kinji tsoro."
"Mama please karki hanani Ya Al'ameen nason yaga Khaleefah ne I won't take long."
Shiru Mama tayi wane me nazari "please Mama."
"Kije kika bari wani abin ya shiga tsakanin ku kuma ni ba ruwa na."
"Haba Mama se kace wacce batasan addini ba banida tsarki fa kin manta ne."
"Ni na san muku ne."
"Inje?"
"Kije ko na hanaki ma nasan zaki saci idona."
"Yeyy! Thanks Mama I love you."
"Naji fice." Nan da nan ta fice achan new site d'in ta samu Al'ameen zaune a
bakin gado. Yana ganinta ya miqe ya amshi Khaleefah da tashinsa kenan da daga
bacci.
"Kaga wai da yazo hannun Daddy'nshi ya bud'e ido."
"Father-son bond kike ji."
"Aww haka ne? Bari in sambad'o Little Princess d'ina mana kaga, nima sak me
kamanni na zan haifo."
"LOL ai jini na yafi naki k'arfi duka yaran mu in shaa Allah dani zasuyi kama."
"Allah k'arya ne da ni ne." Tayi maganan wane zatayi kuka.
"Kisa wasa, ai gashi kin fara gani daga kan Khaleefah."
"Ai idan na haifi d'aya again naga me kamanninka ne toh na yafe sauran ban sake
haihuwa."
"Ai sede ki yafen amman kin kafa haifan masu kamana kenan."
"lol ma da sauk'i ai kai d'in kyakkyawa ne atleast koda sun yo kamannin naka ba
laifi tunda suna yin kyau."
"How I wish zamu kwana tare yau Princess I miss you."
"Ba kai kad'ai ba harta ni Sweetheart I miss you."
"Can't we sleep just for today?"
"Mama zata kashe ni gobe."
"Zan sa Mama Babba tayi mata magana, mu kwana anan kinji?"
"Yau nida Khaleefah baza muyi wankan dare ba kenan."
"Zaku yi mana ga bathroom da komi a ciki."
"As for me yes but shi se a cikin bath tub nasa ake masa kuma ni ban iya bama."
"Ni na iya zamuyi masa a cikin jacuzzi."
"Uhn-uhn fa Sweetheart karka jefa min yaro a cikin jacuzzi tam!"
"LOL Princess shin wai se yaushe ne zaki dena under estimating d'ina ki yarda ni
d'innan inada basira da baiwa."
"Hehe toh idan ba neman surutu ba meh had'inka da wanka wa jariri?"
"Time da aka haifi Aysha kullum a idona ake yi mata wanka time d'in na gama
first degree d'ina ina hutu a gida."
"Wow really! My legend ba wasa, Toh idan ka mishi wani kaya zesa? Babu ko d'aya
anan."
"Bari in kira Addar mu Yasmeen in rok'eta ta d'auko miki kayan baccinki dana
Khaleefah ko?"
"Eh ayi hakan Yasmeen nada sauk'in kai unlike Adda Mariam zatayi mana." Nan da
nan ya kira Yasmeen ya rok'eta da ta taimakesu ta kawo musu kayakin baccin Zeezee
da na Khaleefah, sanin itama tayi hakan lokacinda ta haifi first born nata yasa ta
gane how exactly Al'ameen and Zeezee must be missing each other nan da nan ta kai
musu kayan ta fice bayan dogon godiyan da Zeezee tata yi mata.

Ai da mamaki Zeezee ta tsaya tana kallon yadda Al'ameen keyi wa Khaleefah wanka
wane na mace, a hankali yake binsa so gently sekace ba na miji ba. Wanke sa yayi
tas ko kuka Khaleefah beyi ba har aka gama sannan ya shafa masa lotion nasa ya sa
masa pampers tukuna ya sanya masa overall nasa. Duk anan banda ido ba abinda Zeezee
ke binsa dashi, ko ita bazata iya yin abinda Al'ameen yayi ba gani take like idan
ta rik'e yaron ze su6uce mata a hannu.

"Sweetheart you are such a genius, I can't ask for more."


"Kin yarda yanzu?"
"100%."
"Sauran ke ko kema na miki wankan?"
"O'o ni zanyi da kaina."
"Tam kije Khaleefah and I are waiting for you." Ba tare da 6ata lokaci ba ta
shiga bayin.
On Mama's side kuwa 10pm na bugawa ta shigota d'akin Zeezee don yi ma Khaleefah
wanka. Sede to her ultimate suprise taga ba Zeezee. "Bade 'yar nan bata dawo ba har
yanzu?" ta tambayi kanta. Dai-dai nan shigowan Yasmeen da baby'nta dake 8 months
old me suna Jameela amman suke kira da Iman. "Yauwa Yasmeen ina Zeezee ta shiga
ne?"
"Uhn, nima ban ganta ba fa tun d'azu." Har Mama ta yarda amman sanin duk
lokacinda Yasmeen zatayi k'arya seta soma da 'uhn' yasa ta fahimci k'arya take yi
mata. "Yasmeen! Maman Suleiman da Jameela."
"Na'am Mama."
"Ina Zeezee nace?"
"Uhn nima fa ban gan taba."
"Eh raina min hankali de, ko a jinki ban san k'arya kike yimin bane? Ina Zeezee
nace?"
"Mama please ki barta ta kwana achan."
"La ha ilaaaa!" Ta fad'a tana tafe hannu cike da mamaki.
"Me kike nufi dana barta ta kwana achan? Bade abinda keda mijinki kukayi a
haihuwar Suleiman ba su Zeezee keda shirin yi?" Shiru Yasmeen tayi ta shiga bawa
Iman frisco nata. "Dake fa nake kin min shiru se kinji sauk'an bugi ko?"
"Mama eh."
"Na shigesu ni Hafsah! Yaran zamani wai ce muku akayi ana haka ne? Shin me
mazajen naku suke baku dako sati baku iya jura idan baku kusa dasu?"
"Soyayya mana Mama da me?"
"Aww ma har haka kike cemin wato."
"Kefa kika tambaya nikuma na baki amsa." Ganin Mama zata yo kanta da nufin kai
mata bugi tasa ihuu "Mama please kar Iman ta fad'i" don haka kad'ai Mama ta barta.
"Zakuyi bayani maza je ki kirata kice ta dawo."
"Sunyi bacci fa by now."
"K'aniyanki da by now d'in, kije ki kirasu do Allah."
"Allah sunyi bacci."
"Toh baza suyi wanka bane? Ni ban damu da Zeezee bama amman mijina fah?"
"Karki damu zasuyi masa, sun sani na d'auko musu kayakin baccinsa da duk wani
abinda ya kamata d'azu."
"Kice da ke aka had'a baki kema munafuka, yayi kyau zata gamu dani gobe." Tana
kaiwa nan ta fice d'akin data sauk'a ta kwanta.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*


*ZAIMEEN❣ FLAMES🔥🔥🔥*
Beeenovels.[truncated by WhatsApp]

[3/29, 21:07] +234 810 030 0159: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀


🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣8⃣

Suya da malt Al'ameen ya tura Sadeeq ya siyo masa da Zeezeensa inda


suka baje a kan rug suka ci abin su, ya bata ya ci har suka cinye a yayinda
Khaleefah keta baza bacci akan gado tun wankan da Al'ameen yayi masa yaji dad'in
jikinsa. Hira suka tayi se kusan to 1am suka kwanta su biyu maqale da juna da
Khaleefah a tsakiyansu. Ba tare da 6ata lokaci ba bacci yayi awon gaba da Zeezee
tsabagen gajiya da hidimomin data sha a ranan.

_3:05am_
    Kaman meh alarm Khaleefah ya farka ya shiga kuka, itama Zeezee ji take as if
like tayi kukan bata son wannan tashi tsakan dare na Khaleefah, yata bacci safe da
rana se tsakar dare ya tashi ya hana mutum bacci. Da k'yar ta iya bud'e idonta ta
d'auro niyan d'agasa kenan taga Al'ameen ya bud'e ido shima.
  "Am sorry Khaleefah ya tada kai kaima."
  "Its no big deal ki koma bacci abinki."
  "Shi kuma fah kaga fa kuka yake har yanzu."
  "I'll take care of him, nasan kin gaji jiya rest kinji?"
  "Awwwn! Toh bari na bashi nono yasha seka d'auke shi."
   "Ba akwai wanda kikayi saving mishi a feeder ba d'azu? Don't worry zan bashi."
  "Thank you Sweetheart."
  "Shhh! Go back to sleep I love you."
  "I love you more." Bargo ya ja mata ya rufeta tare da pecking nata a cheeks
sannan ya d'ago crying Khaleefah ya miqe dashi.
    
      Kan dressing mirror ya nufa ya d'ago feeder'n sannan yaja kujera ya zauna ya
shiga bashi, seda ya kusa shanye feeder'n tas sannan ya k'oshi sede har yanzu beyi
bacci ba. Murmushi Al'ameen ya saki tare da miqewa ya kwantar da Khaleefah a
jikinsa yana zagaye d'akin dashi yana bubbuga bayansa. Ido d'aya Zeezee ta bud'e
tana kallonsa, just how lucky is she having Al'ameen as her husband? Ba abinda baya
mata girki, kula da yaro, tsifa komi yana mata she can't ask for more. Bata san
lokacinda bacci yayi awon gaba da ita ba. Al'ameen kuwa yafi 30mins suna zagaye
d'akin da Khaleefah anytime ya duba face nasa sede yaga yaro na zaro dara-daran
idanunsa yak'i yin bacci daga k'arshe zama yayi akan wani wrecking chair ya kwantar
da Khaleefah a kan kafad'ansa yana jijjiga shi kad'an kad'an, ahaka bacci yayi over
taking nasu both.

   Asuban fari Zeezee ta tashi ta6a gefenta tayi taji wayam! Bed side lamp ta
kunna, cike da tashin hankali ta miqe zaune da niyan sa ihu ganin ba Al'ameen ba
Khaleefah. Bata kai ga sake ihun ba ta hango most adorable soldier'nta and son suna
bacci peacefully. Murmushi ta saki at their sight sannan ta miqe ta tako gun a
nitse, hannu ta miqa ta gwada d'ago Khaleefah in the process Al'ameen ya bud'e ido.
"Sorry didn't meant to wake you up."
  "I know you didn't mean to Princess, good morning."
    "Morning, Khaleefah ya hana min kai bacci ko? Mesa kuka kwana anan ba a kan
gado ba?"
   "Ban san yaushe nayi sleeping off anan ba nima yak'iyin bacci se kawai muka
zauna anan."
  "Ayyah kawo in kar6esa toh Asubah yayi seka samu kayi sallah." Da "toh" da ya
fad'a ta amshi Khaleefah, Al'ameen ya fice bayi fitowansa ya sanya jallabiyansa ya
tarar da Zeezee zaune gefen Khaleefah tana binsa da kallo. "Princess bazakiyi
sallah ba baza kuma kiyi bacci ba?"
   "I wanna watch you pray."
  "Zanje Masjid ne."
  "Har Masjid?"
  "Har ne Princess? Masjid dayake gida."
  "Ni na fison kayi a nan."
"Princess ni kad'ai sekace maye?"
  "Eh ai nima haka nake sallan ni kad'ai ranan da kace se kaje Masjid so kaima kaji
how it feels like yau."
  "Nop ni zanje Masjid."
  "Please Sweetheart I just wanna watch you pray, bana gajiya da jin sautin qira'an
ka."
  "Zolayan de."
  "Am serious kasan bazanyi teasing naka ba ai." Murmushi ya mata sannan ya
shinfid'a sallaya ya shiga yin Sallah a yayinda Zeezee ta nitsu tana sauraron
sautin Al~Qur'anin da Al'ameen ke rairawa. Yana idarwa yayi azkar nasa sannan ya
hayo gadon suka kwanta kaman yadda sukayi d'azu. Anytime his arms are wrapped
around Zeezee bacci bayi mata wuya nan da nan ta koma bacci shikuwa sam ya kasa
komawa saboda tunanin tafiyan da ke gabansa a yau gashi be sanar da Zeezee ba.
Wajajen k'arfe takwas ya miqe a hankali ya zare hannunsa daga rik'on da Zeezee tayi
masa ya nufi bayi yayi wanka daman akwatinsa a shirye yake. Paper ya 6alla ya
rubuta wani note a jiki ya ajiye a gefen side drawer'n kanta sannan ya miqa yayi
pecking nata a forehead sannan a cheeks nata then Khaleefah, daga nan ya fice.

   9:30am Kukan Khaleefah ya tada Zeezee, cikin bacci ta jasa jikinta ta sa mishi
mama a baki kum yayi tsit ita ko ta cigaba da baccinta. Sha Khaleefah ya cigaba da
yi har seda wani baccin ya sake d'aukan shi. Ba Zeezee ta tashi ba se kusan to
11am. Bayan dogon miqan da tayi ta dafe gun Al'ameen taji wayam da sauri ta bud'e
idonta ta tarar ba yi nan se tayi zaton ko yana bayi ne amman jin ba alaman motsin
mutum a bayin ta sake shiga duhu, to ina ya shiga? A garin mik'ewa daga kan gado
hannunta ya bige letter'n daya mata dropping akan side drawer. Da sauri ta d'aga ta
bud'e ta shiga karantawa kaman haka;

    _My Sleeping Beauty is now finally awake to read this short note of mine. I'm
sorry I couldn't bring myself yestarnight and even today's morning to tell you zan
wuce Abuja, saboda ina tsoro banason hankalinki ya tashi, I pray it don't now. I
love you to the square of infinity, take care of yourself and our little soldier
for me, ban da kuka please and kiyi hak'uri don't get mad at me saboda ban sanar
dake ba I just couldn't bring myself to you. Will call you up immediately idan na
isa. Yours Soldier XoXo._

   Murmushi kad'an ta saki tana me share k'wallarta "I will never go mad at you
again Sweetheart Allah isar da kai lafiya." Bata kai ga ninke letter'n ba wayanta
ya shiga ruri tana dubawa taga Al'ameen ne ke kira without hesitation ta d'aga
wanda hakan ya mugun basa mamaki ya d'au ma bazata d'aga ba. "Assalamu Alaikum" ta
fad'a sounding thrilled and happy.
  "Wa Alaikumus salam Princess, good morning."
  "Morning My Soldier ya kake? How was your trip?"
  "Alhamdulillah munyi landing tun d'azu naso kiranki amman nace kar nayi waking
naki up from your beauty sleep."
  "Ai kuwa yanzu na tashi Khaleefah kam nata bacci."
   "So Princess you are not mad?"
  "Why should I be Sweetheart? Na fahimci komai, I totally do so kar ka damu kaji?"
  "Thank you Princess thank you so much for understanding, na d'au zakiyi min
zuciya ma kik'i picking call d'in."
  "I'll never ignore your calls again, never."
  "Am pleased."
  "Watanni nawa zaka yi?" Be 6oye mata ba yace, "2 months 2 or 3 weeks."
  "Ayyah toh Allah bamu tsawon rai, I will be patiently waiting for your return I
love you."
  "I love you more Princess ba k'aramin farin ciki kika sanya ni ba yau d'innan."
  "Glad I did, kar na cika ka da surutu barin je inyi wanka nima in shirya nakega
zan bi Mama in k'arisa arba'in d'ina a chan gida gashi dama in 3 weeks time zamu
bud'e school."
  "Oh toh ba matsala hakan ma yafi ai, school kam ya kusa zuwa k'arshe ai Princess
keda kike final year yanzu, Allah kawo ranan da zaki gama muyi grand celebration."
   "Awww really?"
  "Yes Princess I want to make you the most happiest woman on earth."
  "Am already happy Sweetheart thanks for everything se mun sake waya I love
youuuuu muahhhh!" Tamai blowing kiss. 
  "I love you more" jira yayi seda tayi hanging tukuna. 

***
   Life continued, da d'ad'd'aya da dad'd'aya jama'a suke watsewa har suka gama
watsewa sannan Zeezee tabi Mama suka koma gida. Ba k'aramin ji da sabuwar motar nan
tata da Al'ameen ya sai mata take ba kullum tana cikin wankewa da kanta, in three
weeks time d'in suka bud'e makaranta, duk da irin rikici na Khaleefah hakan besa
Zeezee taja baya kota kariya da karatun ta ba, yaro na girma yana dad'a kyau yana
kuma sake kama da Babansa, gashi da k'iba plumpy dashi saboda shan nono ne dashi.
Mama na assisting Zeezee sosai wajen kula da Khaleefah amman idan Zeezee tayi mata
rashin kunya ko kuwa suka samu misunderstanding seta fake a gefe tana kallon Zeezee
na drama da Khaleefah tana mata dariya. Haka yau ma fad'a ya had'asu da Mama,
Zeezee ita wai sam shan nonon Khaleefah ya isheta zata had'a masa da madara Mama
kuma tace ita bata ji abinta haka ba idan ma za'a fara bawa mijinta madara se idan
yakai 5 months, haka itama ta wahala da Zeezee time da take baby haka Baba Allah ya
jik'an rai yake tisata a gaba yace seta shayar da ita.
  "Wallahi ni na gaji yaro kullum shan nono seya miyar min dasu slippers tukuna
bayan nan yata sani jin yunwa ba gaira ba dalili."
  "Eh haka zaki hak'ura kamar yadda na hak'ura nima."

   "Wallahi bazan iya ba madara zan had'a mishi dashi, idan na fara tests ko exams
fah?"
  "Kinji na rantse Zeezee bazaki bawa yaron nan madara ba watanninsa nawa ne? Ina
jiya yayi biyu? Nonon zeta sha seya tsotse su tas su zama ledan pure water bama
slippers ba, d'agasa ki basa ko baki jin kukan da yake ne?" Banza da ita tayi se
tura baki take tana bin Khaleefah dake ta faman kuka da dirty look. "Aw sena mareki
zaki d'agasa?"
   "Wallahi Ya Al'ameen zan kira" tayi maganan tare da d'ago Khaleefah ta nufi
d'akinta dashi. Akan gado ta baje seda ta gama hararan crying Khaleefah sannan ta
zaro maman d'aya ta sa mishi a baki nan yayi shiru sekace bayi gidan se shan abinsa
kawai yake. Layin Al'ameen ta shiga gwadawa, seda ya kusa tsinkewa ya d'aga
kasancewar yana bacci. "Uhn-uhn" yayi clearing voice nasa. "Halo Princess?" Ai
kawai ta saki masa kuka, kukan ma irin me k'aran nan cike da shagwa6a wane 'yar
yarinya. Cike da tashin hankali ya hau tambayarta ko lafiya. "Princess what's
wrong? Why are you crying like this? Its okay please kinji? Am here for you."
  "No you are not" ta fad'a still tana kukan.
  "I am Princess meya faru? Bar kukan ki fad'amin zanyi iya k'ok'arina inga na
share miki hawayenki. Keda waye ne? Lecturers at school?" Kai ta kad'a wane yana
gabanta sannan tace, "a'a."
  "Mama?" Nanma "a'a."
  "Lubiee?"
  "Nooo" yana kaffa-kaffa yace, "Khaleefah?"
  "Ehhhh shi, Khaleefah." Ita dariya ma ta basa yanzu akan Khaleefa take wannan
kuka? Lallai kuwa akwai aiki danne dariyan yayi sanin halinta ya tambaya;
  "Meh Little Soldier na kuma ya miki?"
  "Ya fiye shan nono dayawaaa" ta fad'a tana jan k'arshen zancen tana me cigaba da
rusa kukan shagwa6anta tsakani da Allah. A rayuwa idan akwai abinda Al'ameen beyi
gajiya dashi shine shagwaban Zeezee, idan tace zatayi kuka tsakaninta da Allah
takeyi tamkar 'yar yarinya.

   Tunda take da Al'ameen bata ta6a jinsa yayi dariya haka ba irin na yau, k'walla
yake sosai amman hakan besa yadena dariyan ba, don dariyan da yake har yana neman
sata yi itama amman ta cije ta matse sema dad'a 6ata mata rai da yayi, sake sa wani
kukan tayi dagaske abinta, ganin Al'ameen yak'i yin shiru ya saurareta se kawai ta
katse wayan. Tsan-tsan dariyan da yake  bema san ta katse ba seda ya tsagaita
dariyan tukuna yace, "Princess am sorry please. Halo?"  anan ya gano tayi hanging
ma ashe. Without hesitation ya shiga kiranta wanda har yayi 3 missed calls bata
d'aga ba se a karo na hud'u tana me kukan har yanzu.
   "Oh come on! Princess meh abin kuka haka don Allah? Ai abin priding nema ace
d'anki na shan mama sosai, kinga nonon ki nada kyau kenan kuma ke bakiga yadda
Khaleefah ke k'ara haske da k'iba ba? Don't you know you are the reason behind it
all?"
  "Abinda zaka ce kenan? Kai baka tunanin wahalan da nake sha, 24/7 fa ina kan shan
tea kullum saboda samo masa ruwan nono idan ya tashi sha d'aya seya zuk'eni tas, ya
shanye wannan ya shanye d'ayan baya bari na da komi."
  "Toh Princess ya kika iya? Dole kiyi hak'uri ko da yunwa kikeson ki fara barinsa?
Remember Baba ne fah."
"Ni bance da yunwa ba madara nake so in had'a mishi dashi Mama wai bazan yi ba."
  "A 2 months d'in Princess? Haba ki tausayawa Baban mu mana yayi k'arami ai
dayawa."
  "Ya Al'ameen wallahi ban iyawa, so kake ya zubar min da nono nan da nan kace ka
gaji dani ni banaso."
  "LOL inde nine karki damu da hakan ko ya kike I love you balle ma don Khaleefah
kad'ai ba abinda ze samu mamanki kiyi hak'uri kinji? Ko na k'ara miki salary'nki
ne?"
  "Ni bana so."
  "A'a zan k'ara miki 100k yayi?"
"Nifa bance ka k'ara ba."

   "Ni nayi intending ko halan ze d'an toshe bakin kuka da k'orafin nan, next
salary'nki 100k zan tura miki in shaa Allah."
  "Toh na gode amman Sweetheart kasan bazan zo in iya da feeding Khaleefah ba ko?
Especially idan na fara tests da exams d'ina."
  "We'll think of a solution Princess idan ya kai 5 months seki fara basa milk
d'in."
  "Har 5 months abinda Mama tace kai ma zaka ce? Ai dama nasan ba ka sona yanzu se
Khaleefah."
  "La la la you know thats not true." Da k'yar fa ya samu Zeezee ta yarda se
Khaleefah ya kai 5 months ta fara basa milk, da dabaransa kuma ya sata tayi
promising nasa zatana feeding Khaleefah whenever he is hungry.

   Se da Al'ameen yayi watanni uku cus sannan ya buga waya wa Zeezee waya yace ze
dawo, dad'i kasheta she can't tell how much she missed him a kullum idan sukayi
waya so take ta tambayesa when will he be back amman tuna alk'awarin da tayi mai na
bazata sake sasa a damuwa ba yake sa ta yin shiru. Da wata d'aya kenan tun maganan
da sukayi on phone call regarding complain na too much shan nonon Khaleefah izuwa
yanzu ba k'aramin weight Khaleefah ya k'ara ba ga gashin nan tubarkallah sam Zeezee
bata yimai aski sede sau d'aya ta ta6a mai trimming saboda yadda yayi tsawo. Bata
isa ta shiga ATBU ba da Khaleefah saboda tsoron masu kanbun baka da take, last time
data shiga dashi dan dole ta sake dawo dashi gida kowa seya tsaya ya amshe sa ya
yaba kyansa which is very dangerous. Kayakinta kap ta shirya Mama ta mata rakiya ta
buga motarta ta dawo gida. Fav na Al'ameen ta shiga had'awa amman Khaleefah yak'i
barinta tayi aiki gashi tabawa Baaba hutu tun komawan ta gida, a ranan ta kira
Baaba tace gobe ta dawo. Duk uban kayan wasan Khaleefah ta fito masa dasu amman
yak'i yayi shiru yayi wasa se kuka yake. Dolenta seda ta had'a tea tasha ta samu
ruwan nono ta shayar dashi da k'yar ta samu yayi bacci sannan ta cigaba da aikinta.
Bayan ta sauk'e girki tayi shara dasu goge-goge sannan lastly tayi wanka tayi ma
Khaleefah ta feffeshesu d a turare ta shiga yi musu selfie har seda taji ana
bud'ewa Al'ameen gate. Khaleefah ta tattara a hannunta kafin ta isa parlour har
Al'ameen ya shigo da sauri-sauri taje ta samesa tayi hugging nasa da Khaleefah a
tsakiyansu, sede don yadda yayi missing nata hakan be masa ba, amsan Khaleefah yayi
ya ajiye sa kan kujera sannan ya matse Zeezee gagam a jikinsa yana bata wani irin
demanding but yet affectionate hug. A hankali ya saketa yayi owning lips nata basu
san yaushe suka fad'a kan kujera ba, kad'an ya rage basu zauna kan Khaleefah ba.
Sun zurfafa suna abu d'aya kawai suka jiyo ihun Khaleefah da sun ma manta yana gun
tsabagen yadda hankalinsu yabi abinda suke. Cike da kunya Zeezee tayi pulling out
tana lasan lips nata a hankali shima Al'ameen haka.
   "Smart guy ko kaima kanaso kayi joining in ne?" Al'ameen ya tambayi Khaleefah.
Tana murmushi sosai tace, "tsiya de irin nasa shi baya son yaga am enjoying myself
ne kawai yanzu ka dawo ma baze barni in more ka ba."
   "Ai har sekin gaji dani Princess hutun 2 months ba wasa bane."
  "Are you serious Sweetheart?"
  "I am Ummu Khaleefah."
   "Yeyyy!" Ta fad'a jikinsa "I missed you so much, morethan I can ever tell
  "Not as I do Princess rabo na dake tun kafin ki haifi Khaleefah har wani rashin
lafiya nake ji."
   "Baka kaini ba Sweetheart I miss My Hot Lion."
  "Yau kam sekin d'ebe min duka kewanki da nake."
  "Allah yasa Khaleefah ya barmu toh."
"LOL" ya furta tare da dawo da kallonsa kan Khaleefah ya d'aga sa sama yana masa
wasa "little man wai dagaske baka barin Mummy?" Da mamaki suka ga yana dariya sosai
harda sauti. "Ai kuwa kaji ya amsa ka yace eh baya bari na wallahi da daddare bana
iya bacci idan ya kafa shan nono, gashi koda yayi bacci na zare seya kuma tashi,
dole seda maman a bakinsa muke bacci ban isa in ce zan cire ba."
  "Ayyah Princess gashi harkin d'an zube kad'an ko zamu fara basa madaran ne
yanzu?"
  "No mu bari seya kai 5 months d'in he is 3 yanzu ai."
  "Toh Allah kaimu sannu ko? Allah kad'ai ze biyaki karki gaji da mu."
  "Why should I? Tashi muje kayi wanka muci abinci I cooked your favorite."
  "Thats My Woman."

*•*•*•*
      Duk kalan fitina da k'iriniya irin na khaleefah hakan be hana Zeezee da
Al'ameen gamsar da junan su ba a daren ranan, they really enjoyed each other's
company. Tun dawowan Al'ameen yake kula mata da Khaleefah aikin ta baifin ta bashi
mama shikenan but abinda ya kama yi mai wanka, wanke mai pupu duk Al'ameen ya
d'auke mata hakan ya bata daman concentrating sosai akan project nata, love
tsakaninta da Al'ameen kuwa a kullum dad'a k'aruwa yake a birnin zuk'atansu. Cikin
ikon Allah su Zeezee suka soma tests nasu har suka gama lafiya, basu kai da fara
exams ba Al'ameen ya koma sam bata so tafiyan sa ba amman kuma bata nuna mai hakan
ba gudun sasa a damuwa. Kamar ko wani tafiyansa seda ya bata everlasting kiss a
daren jiya kuma suka yi satisfying juna sosai. Tun tafiyan sa ta maida hankalinta
gun karatu Baaba ke kula da Khaleefah acikin sa'a suka fara exams suka gama, su
Zeezee an zamo gardaute ta fito da GP me kyau tana ranking second class upper.
Kamar yadda Al'ameen yayi promising nata hakan ya cika, da ya dawo ya had'a mata
grand celebration na gama university.
 

  *MIEMIEBEE.     Team #YGC!🎀*


*ZAIMEEN Flames🔥🔥🔥🔥*
  Beeenovels.blogspot.com 👄
[3/29, 21:08] +234 810 030 0159: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
7⃣9⃣

****
      Life moved on drawing us closer to our graves, Khaleefah se dad'a girma da
wayo yake ga uban k'iriniya be bar komi ba a halin Zeezee, itako sanin ILLAN GATA
yasa bata cika biye mai ba, sau dayawa idan yaga abu gun yara ya hau kuka yana
shessheqa shima se an siya mishi, atimes tana siya mai wani sa'in kuma tak'i saboda
bata son 6ata sa ya zamanto duk wani abinda yake so yana samu hakan ba gata bane,
shide Al'ameen ko uffan bayi ce mata when it comes to tarbiyya saboda yasan uwa aka
sani da bada tarbiyya baze sa baki ba yayi ruining tarbiyyan yaransa. Duk wani
tafiyan Al'ameen kuwa kamin ya dawo se Khaleefah ya manta dashi yayi ta masa k'uiya
se a hankali tukuna yake sake sabawa dashi. Cikin ikon Allah har Khaleefah ya cika
one year old, nan ma grand birthday Zeezee da Al'ameen suka yi masa organising fiye
dana lokacinda ya cika 6 months had'ewa. Yaro kyau wane d'an larabawa. Kayan wasan
da Al'ameen yayi gifting masa as present ranan ita kanta Zeezee tasha mamaki mota
guda aka sauk'e na kayan wasan Khaleefah. Haka rayuwarsu ta cigaba da kasancewa
cikin so da k'auna. Ba kad'an ba Al'ameen ke ji da Khaleefah kayakin wasan yaro ya
cika d'akinsa ya cika store room.

      A haka har Zeezee ta soma service nata ta k'are lafiya, koda Al'ameen ya
tambayeta a nemo mata aiki kuwa cewa tayi bata so, daya tambayi dalili kuwa tace
masa tunda ba lecturing ko wani aikin asibiti zatayi da ze taimaki al'umma ba bata
ga amfanin aikin ba, daman inba don taimakon al'umma ba don samun kud'i ake aiki,
ita kuwa bata da maraba da masu aikin ma ko tace tama fi wasun su samu cause kud'in
da Al'ameen ke bata don yawa save kawai ta bud'e tana ajiye musu for future use.
Idan ya tashi na abincin Khaleefa kawai se ya ajiye 20-30k.
     Amsan Zeezee ba k'aramin dad'i yayi wa Al'ameen ba especially the part that
tace she'll be his full house wife. A kullum tana tare da Khaleefanta idan Al'ameen
bai gari yau su fita nan gobe su fita chan wataran kuma su yini suta wasa kawai a
gida. Sosai Khaleefah ke neman tasowa da gagara amman kasancewar Zeezee na taka
mishi birki yasa yake rage wasu abun amman fah har yanzu tana fama dashi kunsan shi
gado ba gwaninta bane.  Sau dayawa yana lalata mata waya da miyau, idan ta bashi na
wasa kuma yak'i amsa se na gaske.

   ****
   Khaleefah nada one year seven months, dare d'aya Zeezee ta soma feeling
nauseatic, ga kuma fever da take ji again gabad'aya de ta tashi ba seti ranan.
Gashi Khaleefah ya ringa yi mata wasa kaman d'an biri kenan ya hau kanta tanan ya
sauk'a ta can. Haka yanzu ma tana kwance akan gado bata jin dad'i shiko yana zaune
akan bayanta yana doki, chan yaga haske na flashing akan screen na wayan Zeezee
hoton Al'ameen daya bayyana as identity na wanda ke kira yasa Khaleefah riding
faster akan Zeezee yana "Da da" Da da! Da da!" Kaman yadda yake kiran Al'ameen.
   "Da da ne yake kira?" Ta tambayeshi idonta a kulle. "Da da!" Ya cigaba da kira
har seda Zeezee tayi picking up call d'in nan fa ya nitsu yana kallonta.
   "Mamin Khaleefah My Princess."
  "Na'am Da dan Khaleefah My Last Standing Soldier." Ta fad'a da k'yar don jirin da
takeji.
   "Princess is something wrong? Yana ji muryan ki so low? Are you okay?"
  "I am karka damu."
  "Kin manta munyi promising juna baza mu sake yiwa juna k'arya ba ko?"
  "Am sorry."
  "Tell me toh." Ta bud'e baki zatayi mai stating bata jin dad'i kenan taga
tabargazan da Khaleefah yayi mata da pillow, wannan hak'waran nasa sunfi razor ci.
Pillow ya yaga da teeth nasa ya ciro abin cikin yana watsi dasu one-by-one. Seta
tuna ranan da ya gantsara mata cizo a bakin nono, har kwad'e sa seda tayi ranan
Al'ameen yayita mata masifa. "Haba! Haba! Haba! Baby mesa kake min destroying komi
na ne? Haka jiya ka yage bedsheet d'in nan I had to change it yau kuma pillow na ka
tsaga haka?" Dariya Al'ameen dake jinta ya saki a yayinda Khaleefah ya tsaya yana
yi mata murmushi har yau dan tsiya bayi kiranta da komi amman tuni yabawa Al'ameen
suna, ko pic nasa ya gani ya hau kiran 'Da da! Da da!' Kenan to her ultimate
suprise taji yau yace, "Mammy."
  Ido ta zaro in disbelief "say it again Darling, say Mammy again" gabad'aya ta
nemi rashin lafiyar nata ta rasa ma tsabagen farin ciki. For how long have she been
waiting for this day? "Say it again kaji Cuddle Bear? Say Mammy" duk ana sauraronsu
Al'ameen ke dake Zeezee tasa a speaker phone. Shiru Khaleefah yayi ya had'e rai
kaman ba shi ne yayi magana just a while ago.
  "Come on say it! Zan baka mama" ta yaye sa amman take son ta zolayesa. Ba surutun
da batayi ba ya sake cewa 'Mammy' yak'i.
   "Yak'i fad'a Sweetheart" ta sanar da Al'ameen sounding disappointed.
   "Se hak'uri Princess" ya fad'a mockingly yana yi mata dariya.
  "Ka cigaba idan na haifo little Princess d'ina seta soma kirana kamin kai."
  "Time shall tell."
  "Mammy!" Cewar Khaleefah da k'arfi again.
   "Ya sake kirana ya sake!" D'agasa sama tayi tana juyi dashi "say it again kaji
Sweetheart?"
  "Mammy." Dad'i kashe Zeezee yau finally Khaleefah ya bata name itama ko Al'ameen
ze rage mata wani abin yanzu ada cewa yake wai sam Khaleefah baya sonta se shi don
kawai yaga yaro ya basa suna gaba da ita.
   Seda ta gama wasa wa Khaleefah gabad'aya ya gajar da ita lik'is gashi daman ba
dad'i take jiba ta dawo kan Al'ameen. "Ina Khaleefah?" Ya tambayeta.
    "Yayi pupu Baaba zata wanke mishi."
  "Oh!"
  "Yes seka nemi wani abin teasing d'ina yanzu tunda de Khaleefah ya bani suna,
sunan da yafi naka ma dad'i."
   "See this Princess of mine, meye a cikin Mammy? What a common name amman Da da
fa ina kika ta6ajin yara na kiran Daddy'nsu da Da da? Se Khaleefah kad'ai."
  "Oho de Mamy yafi dad'i meh Da da sekace Dada na fulani."
  "LOL ai ba hausa pronounciation bane Da Da not Dada."
  "Whatever, Khaleefah ya gajar dani yau d'innan gashi dama bada seti na tashi ba
ya office?"
  "Office alhamdulillah meke damunki?"
  "Wallahi zazza6i-zazza6i nakeji."
  "Subhanallah kije asibiti mana gobe ba kyau zama da rashin lafiya."
  "Eh zanje in shaa Allah don tun shekaran jiya yake damuna se worsening kuma
yake."
  "Sannu kinji? Get some rest I love you."
  "I love you more, send my kisses to Khaleefah tell him Da da loves him so much."
  "I'll sleep like a baby and dreams about me."
  "Definately and you too good night."
  "Aha night" nan ta katse. Bada jimawa ba Baaba ta kawo Khaleefah da diaper nasa a
hannunta tun d'azu ya bari ta sa mishi yak'i seta kwantar da shi zata sa mai seya
miqe ya sa gudu. "Mamin Khaleefah ga Khaleefah nan tun d'azu yak'i a sai mai
pampers."
  "Ke kuma meye a fuskanki haka Baaba?" Shafe fuskar nata tayi taga farin powder
kota ina. "Na shiga uku Khaleefah ne ya fesa min." D'an murmushi Zeezee ta saki
"Sweetheart kana son kasha bulala ko?"
  "Mammy" ya fad'a sounding delighted yana miqa mata hannu ta kar6esa. Miqewa tayi
da k'yar ta amshe sa, "ki had'a min frisco na shi please yasha yanzun nan yayi
bacci ko zan huta nima."

^^^^^
    Washegari da safe Zeezee ta shirya ta shirya Khaleefah suka wuce asibiti. Da
mamaki ta tsaya tana kallon likitar data ce mata zatayi mata pregnancy test like
how can she get pregnant when Khaleefah is not even upto two years? Fargaba tashiga
sosai, yanzu inhar cikin ne da ita meye Al'ameen zece mata akuya kome? Koda Dr ta
miqo mata result d'in kasa bud'ewa tayi seda Dr'n da kanta ta d'aga ta bud'e "kamar
yadda na fad'a" tayi maganan tana murmushi. "Mr Handsome ya zama big bro your
little sister or brother is on board, congratulations Ma'am."
   "Dr taya hakan ze faru? Ina kan planning fah Khaleefah is just 1 year 7 months
old kuma kice ina da wani cikin yanzu?"
  "Ai faruwan hakan shi yafi yawa, arziki Allah ya kawo miki Hajiya kinga be kamata
kice tayaya ba."
  "Hakane kam nagode."
  "Yauwa saura scanning ko?" Ma wata nurse Zeezee ta miqa Khaleefah da k'yar suka
samu ya yarda ta kar6e shi sannan aka yo mata scanning aka gano cikin d'an d'aya ne
nanma d'auke da ita which is just 3 weeks old. Maguna d'aya zuwa biyu aka rubuta
mata sannan aka bata next appointment nata. Ita gabad'aya Zeezee hankalinta ya
tashi inta itane she is fine with it amman tunanin ya zata soma 6ullowa Al'ameen da
wannan zance take ya ze d'au maganar? Sun isa gida bada jimawa ba ya kirata don jin
ya jikin nata.
  "Alhamdulillah da sauk'i."
  "Kin samu kin je asibitin?"
  "Eh yanzu dawowa na."
  "I hope ba wani abu serious bane?"
  "Yaushe zaka shigo?"
  "Princess!"
  "Na'am."
"Meke damunki?"
  "Babu in ka dawo zan sanar da kai ba maganan waya bane."
  "Ya Salam mesa kikeson tsinka min zuciya ne Princess? Meke damunki please?"
  "Seriously idan ka shigo zan sanar da kai, se yaushe kenan?"
  "This week zan shigo."
  "Toh seka shigo."
  "Princess please promise me ba abinda ya sameki."
  "Wallahi babu am perfectly fine kaide seka shigo kawai, I love you okay?"
  "I love you more ki shafa min kan Khaleefah zuwa anjima zan miki facetime video
call ki had'ani dashi."
  "Toh Da dan Khaleefah bye."

   Zeezee ta kasa sanar da kowa labarin wannan k'aruwa da ta samu don tunanin
k'aramar k'wak'walwa irin tata wai gani take za'ayi mata dariya idan tace tanada
wani cikin yanzu bayan gashi ko shekara biyu Khaleefah be cika ba. Wannan cikin
natan be kai na farkon bata wahala ba, sam be kwantar da ita ba befi kawai atimes
tana jin amai da jiri ba thats all. Ranan da Al'ameen ze dawo ita da Baaba sukayi
major cleaning sannan ta girka fried rice had'ad'd'e da kayan marmari akai.
  3pm Al'ameen ya dawo as always ta tare sa cike da so da k'auna. Al'ameen na
dawowa Khaleefah ya k'auracewa Zeezee shi a dole d'an GATAN Da Da.
   Da misalin k'arfe biyar da mintuna aka na yamma Zeezee da Al'ameen suna manne a
jikin juna as always, Khaleefah ko yayi bacci an kaisa d'akin shi. "Yauwa Princess
am home tell me meh Dr ta gaya miki da kikaje asibiti?"
  "Promise me first no matter what you won't freak out and zaka min kyakkyawan
fahimta baza ka zageni ba."
  "Princess meyasa zan zageki? I promise."
  "Okay ina zuwa." A nitse ta miqe ta shiga bayi ta b'allo test strip tayi carrying
out test d'in ta jira yayi reading positive sannan ta fito ta buk'acesa daya
k'ariso. A tsakar d'akin ya iso ya sameta. "Your hand" ta buk'ata, nuna mata yayi
ta placing mai strip d'in akai. With bewildered eyes ya tsaya yana kallonta "me
wannan kuma Princess?"
  "Strip ka duba kaga." Ido yasa ya ga ya nuna layi biyu nufin positive kenan sede
har yanzu be gane waye keda cikin ba.
  "It says positive who is pregnant?"
Kar ki kariya cewar zuciyarta. Da k'yar ta furta "I, I am pregnant again
Sweetheart." A rud'e ta shiga jero jawabi "please don't be mad wallahi nima bansan
ya hakan ya faru ba, ina kan plan-" crashing lips nasa yayi akan nata giving her
the kiss of her life, mamaki sosai hakan ya bata meaning he is not mad that she is
pregnant again kenan? Kissing nasa back ta shigayi itama with same intensity se
chan yayi pulling out tare da d'ago fuskarta setin nasa suna kallon idon juna.
  "You are not mad Sweetheart?" ta tambayesa chan k'asa k'asa.
   "Why shall I get mad or furious saboda Allah ya sake azurtamu da wani arzikin
Princess? Sekace wanda be san addini ba. I am so happy for the both of us, I can't
wait to be a daddy again, thank you Princess I love you so much Allah ya inganta ya
sauk'e ki lafiya."
  "Ameen My Soldier ban san da wani bakin zan yi maka godiya ba, you are so so
sweet I am head over hills in love with you."
   "I love you more, yanzu kam Princess zaki haifo mana me kama dani ko?"
"Princess me kama dani deh."
"LOL zamu gani, yaushe zamu je muyi scanning Princess namu?"
  "Nayi ai."
  "Really? how many weeks."
  "Just 3."
  "Wow! We have a long way to go, I'll be by your side through every hardship
because I've got you."
  "Thank you Sweetheart."
"Gobe zamu fita first shopping." Da mamaki take kallonsa how he is getting excited
and happy as if wannan ne first karonsa na jin tana da ciki. "Right?"
  "Sweetheart baka ta6a gajiya dani ne wai kam? Wannan fa ba shine karo na farko
ba."
  "Princess if you'll get pregnant for the 10th time it will always be like the
first time to me cause I love you."
  "I love you more." Turesa baya-baya ta shigayi seda ya fad'a kan gado ta fad'a
akansa suna masu ragewa juna kayan jikinsu. Ganin abin na son fin k'arfin idona
nima na buga legediz benz d'ina na ja musu k'ofa.

    Life continued, cikin k'oshin lafiya cikin Zeezee yake girma sosai take samun
kulawa daga gun Al'ameen nata har izuwa lokacinda ya koma Abj.
  Alokacin da cikin Zeezee yake 8 months yayi k'ato ya fito sosai, rana d'aya
Khaleefah dake 2 years 4 months kenan yanzu ya soma magana kad'an kad'an ba laifi
dukda ba sosai kalamun nasa suke fitowa ba amman don son surutunsa baze barsa yayi
shiru ba. Seda ya bari yana a tsakiyan Mammy'n shi da Da da ya kira Al'ameen.
  "Da da."
  "Yes Little Man ya akayi?"
  "Mammy" ya dawo da kallon sa kan Zeezee. "Yes Sweetheart."
  "Da da why is Mammy's tommy vely biggg?" shi a kullum abin mamaki yake basa don
ba haka yasan Mammy'nsa ba. Shiru Zeezee tayi tana jiran Al'ameen ya amsa sa. "Uhn-
uhm" yayi clearing voice nasa. "Mammy will bring our little Princess into life
Little Man, ba kaga d'akin da aka gyara shi a gefen nakan nan ba? Toh na little
Princess ne, Mammy is carrying her here." Yayi pointing cikin Zeezee.
  "Ahhhhh!" Ya bud'e baki wide open tare da dafe hannayensa kan chubby cheeks nasa.
"Da da akwai baby in Mammy's tommy kenan?"
"Exactly smart guy, akwai baby." Ai se ya sa kuka both Zeezee and Al'ameen sun
rasa dalilin hakan. "Sweetheart why are you crying?" Cewar Zeezee tana neman jawo
sa jikinta aiko ya sake sa wani kukan "don't touch me" da sauri ya fad'a jikin
Al'ameen yana me cigaba da kuka. Da k'yar Al'ameen ya samu yayi shiru bayan
promising nasa da yayi gobe tare zasuyi training men nasa da shi. Khaleefah nason
ana training dashi wai yana son ya zama soldier shima harta uniform sanda aka
d'inka mishi. "So tell me what made you cry Lil man."
  "Mammy is wicked che... che swallowed a baby." Haba dariya sosai Zeezee da
Al'ameen suka kwasa. Da k'yar Al'ameen ya tsagaita dariyan nasa yace, "that's not
true Honey, Mammy bata had'e baby ba."
  "Toh how?" Yana son yayi dogon zance amman maganan be zauna ba.
  "A market muka siyo se aka sa mata." Wayaga a market, dariya Zeezee keson yi
amman ta maqe.
  "How?" Ya sake tambaya.
  "Through her stomach she didn't eat up a baby okay?"
  "Ejit tlue Mammy?"
  "Yes Sweetheart why will I eat up a baby? Mammy is not a bad guy."
  "Yeyy!" Jikinta ya koma tayi hugging nasa. "That's My Little Soldier."

   In two weeks time Al'ameen ya koma Abuja Zeezee taso ace yana nan zata haihu.
Two more weeks ahead due date nata ya shiga tun asuba ta fara labour tun anan ta
kira Al'ameen ta sanar dashi. Har Azahar Zeezee ta kasa haihuwa, da laborn
Khaleefah da na wannan bata san na wanne yafi bata wahala ba sema gani take like na
wannan, ko pushing ta kasa ganin abin nason fin k'arfinta tace ita a kira mata
Al'ameen yazo. Nurse d'aya aka turo waje da tace Al'ameen ya shigo. Nurse na zuwa
ta samu Mama dake d'auke da Khaleefah a cinya, "Sannu Mama please Al'ameen na nan?"
  "A'a yana Abuja ko ya 'yar tawa ta samu ta sauk'a?"
  "A'a Mama abin ya gagara har yanzu ko pushing ta kasa yi wai se Al'ameen na nan
zata yi."
  "Na shiga uku ni Hafsah! Ya Al'ameen dake Abuja ya take son ayi? Don Allah ku
bata hak'uri tayi pushing a wuce wajen."
   "Tak'i Mama maybe ki shigo kiyi mata magana halan taji ki ke." Wa Baaba Mama ta
ajiye Khaleefah ta bi bayan nurse. Zeezee na ganin Mama ta sake sa wani kukan,
gabad'aya ta fita daga kamanninta da hayyacinta Mama na iya rantsewa bata ta6a
Ganin Zeezee cikin bad condition irin na yau ba ko rasuwan Baba albarka. Take wani
irin wawan tausayinta ya mamaye zuciyarta da gudu ta nufi kan 'yarta tana share
mata hawayen nata dakuma gumi duka da bakin mayafin ta. "Sannu Mama na, sannu
kinji?"
  "Mama zan mutu please forgive me."
   "Shhh! Bazaki mutu ba Zainab, just push kinji?"
  "Mama I can't."
  "Yes you can Zainab am here for you."
  "Mama please don Allah ku kira min Ya Al'ameen."
  "Zeezee Ya Alameen na Abuja ya kikeson yazo nan?"
  "Mama I don't care ni don Allah ku kira min shi I need him please." Ganin yadda
Zeezee ke kuka yasa Mama fitowa daga d'akin ta shiga neman Al'ameen daman wayan na
gefensa shima tun sanar dashi da Zeezee tayi ta shiga labor yau ko office ya kasa
shiga se tunanin wani halin take ciki yanzu yake. "Halo Mama ina yini?"
  "Lafiya Al'ameen ya kake?"
"Lafiya Mama ya Zainab ta sauqa?"
  "Har yanzu fa Maj-Gen ba yadda ba'ayi da ita ba tayi pushing tak'i wai se kana
wajen zata yi ni bansan ya zamuyi ba, ba kalan rok'an ta da banyi ba tayi hak'uri
tak'i wai akira ka kazo."
   "Oh God! Ya zamuyi yanzu? Ga pilot na Private jet d'inmu yayi tafiya, Mama
please ki rok'eta nasan zata ji maganan ki she is in so much pain."
  "Maj-Gen. ba yadda banyi da ita ba tak'i jina bari na had'aku a wayan muga." Nan
da nan takaiwa Zeezee wayan tasa a speaker. "Princess?" Ya kirata cike da tashin
hankali.
   "Ya Al'ameen" ta fad'a cike da azaba da wahala.
  "Princess calm down and breathe kinji calm down am here."
  "Ya Al'ameen I need you I can't do this without you please come."
   "Am here Princess am here for you, Khaleefah is also here fo you ke kad'ai zaki
iya kawo mana Princess namu into live and I trust you. I love you so much."
  "I love you also."
  "Good breathe along with me, in... out. In... out" sunyi hakan kusan sau biyar
sannan yace, "thats My Princess now is time to push."
  "No Ya Al'ameen bazan iya ba."
  "Zaki iya Princess I trust you remember kin cemin you'll never break down my
trust, haka ne?"
  "Haka ne."
  "Good so I trust you I know you can do this. In the count of three se kiyi
pushing kinji? Kinji?"
  "Uhum."
  "One... two... three push." Pushing d'in tayi da iya k'arfin ta amman ko 6ullo
kai baby beyi ba. Jin ihun Maminsa tun daga waje yasa Khaleefah 6arkewa da kuka
daman tun d'azu se turancin where is my Mammy and Granny yake yiwa Baaba kasancewar
ba jin turancin take ba se ce mai take eh takalmin ka yayi kyau d'an kyakkyawa.
Kansa ya rik'e yana toshe kunnuwansa "Mammy!" Ya kira ya na kuka nan ta fito dashi
harabar asibitin tana jijik'a shi.

*MIEMIEBEE.   Team YGC!🎀 ZAIMEEN flames🔥🔥🔥*


  Beeenovels.blogspot.com 👄
[3/29, 21:24] +234 810 030 0159: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*👸🏻
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee👄_*

*March, 2017*
8⃣0⃣

Back inside mutuwa ne kawai Zeezee batayi ba har airtime na Mama ya k'are ta
kasa wani push d'in shima Al'ameen sau biyu katin sa na k'arewa yana sake loda new
pin. Da k'yar ya samu Zeezee ta sake wani push d'in anan Dr Sammy Tayi exclaiming
"the baby's head is finally showing we need three more push, you are doing good
Zeezee."
"Thats My Princess kinga saura just three pushes one for Mama, one for Khaleefah
and one for me ko? Muje na Mama toh."
"Ya Al'ameen ji nake like zan mutu ku bani fresh air please." Bayan fifitan da
akayi mata aka samu ta sake wani push d'in. Sun mugun shan wahala sannan aka samu
tayi remaining two pushes d'in. Suul Dr Sammy ta jawo baby "wow its a girl!" Wani
ajiyan zuciya Zeezee ta sauk'e wearing the most expensive smile. "You did it
Princess!" cewar Al'ameen sounding delighted.
"I wouldn't have done it without you Sweetheart, I love you so much" sannan ta
dawo da kallonta kan Mama "thanks for not giving up on me Mama I love you so much
also."
"We love you more" cewar Mama "so Maj-Gen. Bari a kintsa little Princess taka za
ayi maka sending picture'nta."
"Toh Mama thank you, take care okay Princess I love you." Ji yake ina ma yana
tare dasu suma yaga little Princess nasa finally.
"I love you more" Cewar Zeezee, daga nan Mama ta katse wayan. Baby'n aka wanke
aka kawo wa Zeezee ita nannad'e cikin pink showel. Se tace tunda tasan kanta bata
ta6a ganin kyakkyawar hallita ba kaman wannan little angel dake hannunta ba, gashin
kanta ya sauk'o har kan goshinta seda ya had'e da gashin girarta. K'ara ta saki
kad'an se kuma tayi shiru tana nonnok'e kanta cikin showel d'in which is damn cute.
Bin every move nata Zeezee ke da kallo, "she is soo cute Mama."
"Masha Allah, Allah ya raya mana ita."
"Ameen Mama." D'aukanta Mama tayi a hoto ta wayan Zeezee tayi ma Al'ameen sending
ta whatsapp take yayi updating nata ya kira su.
"Princess little Princess is damn beautiful." Ya fara fad'a. Mama dake jinsu
kasancewar a speaker phone suke wayan tace, "saboda wannan karan ta d'auko kamannin
both parents nata shiyasa tayi kyau dayawa, tubarkallah." Murmushi Zeezee ta saki
"nima tun d'azu kallonta nake na kasa gane dawa take kama nasan wannan hanci na ne
a fuskanta."
"Lips nata kuma da eye brows irin nawa ne." Cewar Al'ameen yana me jin dad'i.
"Yess shape na face nata kam nawa ne her eyes kuma..." Zeezee bata k'arisa
maganan ba baby'n ta bud'e idonta "irin na Maj-Gen!" Shouted Mama.
"Yeyy! Ta d'au lips d'ina, eyes amd eyebrows nose na Princess ne kawai."
"Inji wa? Harda shape na fuska. Ai inade ba kamanninka duka ta d'auko ba kuma ma
yawan gashin kan goshintan nan irin nawa ne."
"Amman kamanni na yafi yawa ai."
"Naji toh, wani suna kasa wa Lil Princess tamu?"
"Sunan Mama Babba AMEENAH da al-kunyan AFREEN."
"Masha Allah, Allah ya raya mana surika ta akan addinin muslinci ya albarkaci
rayuwarta."
"Ameen" su uku suka fad'a in unison.
"Toh Sweetheart se mun sake waya zan shiga wanka yanzu."
"Toh Princess take care okay? Mun gode Mama."
"Ba komai Maj-Gen." Anan Mama ta katse wayan ta amshe Afreen daga hannun Zeezee,
Zeezee ta shiga bayi bada jimawa ba Baaba da Khaleefah suka shigo, wajen Mama ya
nufa da gudu "Granny where is Mammy?"
"Mammy ta shiga wanka."
"Who ish this toy Granny?"
"She is not a toy Mijina, wannan Little Princess taku ce your baby sister."
"My sister?"
"Yes your Sister Mammy ta haihu, wannan ne Princess da tasa cikinta yayi k'ato."
"Ohhhh! Ches cute."
"Yes she is."
"Sunanta Plincess?"
"Afreen Da da ya nad'a mata sunanta Afreen." Ai kawai yasa musu kuka dalili kuwa
wai sunan Afreen yafi nasa dad'i shi baze yarda ba.

***
Kusan da Maghrib aka sallami su Zeezee. Son Afreen Zeezee ke sosai, yarinyar
abar so ce kodan kyanta gata bata kuka like Khaleefah tun da aka haifeta har izuwa
yanzu bata sha nono ba ruwa kawai tasha se bayan isha Zeezee ta sa mata mama a
hankali ta kama, kad'an tasha ta sake. In three days time Al'ameen ya iso dad'i
kashe Zeezee yau mafarkinta ya zamo gaskiya. Gashi ta haifi yara har biyu mace da
miji sauran su koma Washington kawai yanzu dream nata yayi coming true.
Suna wane sunan d'an fari haka wannan ma mutane suka cika, abubuwan da Al'ameen
yayi a bikin sunan Khaleefah haka sak yayi ana Afreen Zeezee da 'yarta sun sha
kyautuka sosai abin ba'a cewa komi. Zeezee na nan fit sekace ba wacce ta dire yara
biyu ba. Ko da aka yi suna Al'ameen be koma Abuja ba hakan yasa Mama ta k'ara mata
kwanaki hud'u kawai ta koma gida, Al'ameen keyi wa Afreen wanka da kansa atimes
kuma Zeezee shide Khaleefah ya kasa gane feeling da yake yi wa Afreen atimes ya ji
yana sonta atimes kuma yaji ya tsaneta yata kuka wai se an mayar da ita asibiti
inda suka d'aukota sam wai Zeezee bata sonshi se Afreen, d'an banzan kishi ne
dashi. Idan iskancin sa ya tashi kuwa yace shima seya sha nono musamman idan yaga
Zeezee na breastfeeding Afreen, ba k'aramin drama suke sha ba. Akwai rananda
Al'ameen ya kama Khaleefah na toshewa Afreen hanci don mugunta kawai, kad'an ya
rage Zeezee bata mai duka ba ranan.

Haka kuma rayuwarsu ta cigaba da kasancewa, what a family they are now kullum
Zeezee na cikin kamawa Afreen gashinta into different and stunning styles saboda
aljanun gashi ne da Afreen sekace ba yarinya ba. Cikin runfan Allah yara suke ta
girma a yayinda soyayya tsakanin iyayensu ke sake dad'uwa a kullum.

_3 years later..._
Da gudu Afreen dake 3years old yanzu ta fito daga d'akin Khaleefah tana sanye ne
da penal 4 uniform nata na school da alama yanzu suka taso daga. Kanta an kama mata
into two ponytails, shima Khaleefah da gudun ya fito yana paparota. He is now 5
years 4 months old yaro ya zama saurayi sanye yake da wandon uniform na school nasu
shima da singlet hannunsa d'aure dawani blue agogon ben 10 na roba. Kitchen Afreen
ta fad'a tana kiran "Mammy Mammy!" Da gudu ta k'arisa tana 6uya Bayan Zeezee.
Khaleefah na k'arisowa ya wuce direct zeje ya fincikota wai, da sauri Zeezee taja
sa baya "what is wrong with you Khaleefah? Get your senses together, ban hanaka
biyo Afreen kitchen ba?"
"Kullum ni kita scolding d'ina Mammy, kinsan me tamin ne?"
"Zan saka kneeling k'ark'ashin rana fah! Manners!"
"I'm sorry, book d'ina fa ta d'auka tana drawing ABCD wai nata ne."
"Afreen Princess give him back his book."
"No! Ba naci bane its mine!"
"Its mine keda kike Nursery 1, ita da zaran taga 1 akai kawai setace nata ne,
nima ba primary 1 nake ba, give it back."
"No I won't its mine."
"Princess let me have a look at the book." Cewar Zeezee calmly.
"O'o nawa ne."
"I know lemmi have a look."
"O'o zaki bashi."
"Bazan bashi ba in gani." Da k'yar Zeezee ta iya ta amshe book d'in "Princess
wannan ai na Khaleefah ne."
Zaune tayi akan tiles tana shure k'afafunta tana kuka "nawa ne ga one akai."
"Tsaya kiga, kinga ke sunan ki daga letter 'A' ya fara nashi kuma daga 'I' now
tell me the Princess with brains what letter is here?"
"Number I." Ta fad'a confidently. Dariya Khaleefah yasa "jita wai number I dolo
kawai, letter 'I'"
"Mammy kinji yana shemin dolo ba." Hannu ta d'aga ta zage shi. "Laaa a kunnen Da
da Afreen na zagi."
"Zagi" Exclaimed Zeezee "ban hana zagi ba Princess?"
"I didn't insult him."
"Yes you did, she did Mammy."
"Toh kaima meya kaika ce mata dolo? Ban hanaka ba?"
"Kin hana" ya fad'a yana kallon k'asa "ni bani book d'ina in koma d'aki na." Miqa
mai littafin Zeezee tayi "oya hold your sister's hand kuje ka cire mata kayanta
kasa mata leggings da crossed neck vest nata all in blue, na aiki nanny'n ku
kasuwa. Kai kuma kasa shorts naka da shirt."
Ni bazan cire mata ba rashin kunya ne da ita. Kuma ni banason shorts full length
trouser zan sa."
"Khaleefah! Manners!"
"Am sorry amman kice karta min rashin kunya."
"Princess banda rashin kunya kinji? Khaleefah is your big bro."
"He ish not." Tayi maganan tana zuba mai harara.
"Kingani ba Mammy?"
"He is Sweetheart bisa ya cire miki uniform naki se kuzo muci abinci zamu fita
shopping kunsan next week zamu je Washington ko?"
"Yeyy! We are going to fly!!!" Afreen tasa ihu.
'Yar k'auye kawai me acikin flying d'in?" Cewar Khaleefah yana wani basarwa.
"Ba laifinka bane ai saboda bana maka malu kake wannan iyayin gobe zan kaika
barbing salon a kwashe wannan gashin duka."
"No please Mama I'm sorry bana son malu."
"Then behave yourself."
"I will Afreen lets go."
"Mammy kishe mishi yashe min Plincess."
"Call her a Princess Khaleefah."
"Why shall I Mammy? Neither you nor Da da is a King or a Queen taya ta zama
Princess?"
"Mammy tell him to call me a Plincess."
"Call her a Princess Khaleefah!"
"No Mammy."
"Aje ayi maka malu?"
"Alright, alright Afreen Princess muje in cire miki uniform naki, shikenan?"
"Yeyy! I am a Plincess."
"Yes you are Sweetheart" pecking nata tayi a forehead sannan wa Khaleefah ai kuwa
shi babban yaro yasa hannu ya share "ni banason kiss d'innan kinayi wa Afreen
zallah."
"Ai sena aske gashin nan zaka shiga hankalinka." Be sake cewa komi ba ya shiga
jan hannun Afreen "banda duka ko fad'a Khaleefah duk wanda yayi fad'a baza a je
Washington da shi ba." Seda suka 6ace daga kallonta ta hanzarta ta k'arisa lunch ta
yi setting table, gashi Al'ameen ze shigo gobe she is damn busy.
Bayan sun ci abinci sun kuma wani wankan suka fice Jifatu shopping mall. 100k
each Al'ameen yama Zeezee sending akan tayi musu siyayyan kaya, duk abinda yaran
suka ce suna so shi take siya musu tunda Baban su ya bada kud'in. Sunyi shopping
kaman ba gobe sunzo fita kenan se k'iriniya Khaleefah da Afreen suke kaman yadda
suka saba, basu mintuna biyu gu d'aya basu yi fad'a ba.

Khaleefah na rik'e da stickers daya sa Zeezee ta siya masa zeje ya manna a


d'akinsa Afreen ta sa hannu ta wabce tasa wani d'ankaren gudu tsantsi ne ya kwashe
ta gab da ta kusa fita daga exit d'in, ta kusa fad'i kenan wani mutum ya tare ta
daba don haka ba data sha k'asa. Gaban Zeezee ya mununar fad'i a rayuwa batason
abinda ze ta6a mata lafiyan Afreen ko Khaleefah. Khaleefah ko dariya yake haushi ma
yaji da aka tarota yaso ta fad'i ta buga bakinta nan gaba bazata sake guduwa da
abinda ba nata ba.
"Afreen!!!" Zeezee Tasa ihu. "Alhamdulillah!" Ta fad'a sounding relieved, da
sauri ta k'arisa wajen tare da jan hannunta "bawan Allah thank y-" bata kai ga
k'arisa maganan ba mutumin ya d'ago kansa, fuskan data gani ne ya mugun jijjigata.
"Adeel?!" Ta furta with ultimate suprise and disbelief. Shima kallonta yake ya
ma kasa cewa koda uffan. Da ba don ya ma Zeezee sani na sosai ba da seyace wata ce
me kama da ita saboda wani haske na musamman data k'ara da kuma k'iba, a takaice
tafi da yin kyau. "Zeezee, kece?" Ya fad'a shima disbelievingly.
"Laaaa!" Afreen tayi covering bakinta da hannu "Khaleefah a stranger just called
Mammy Zeezee, ba Da da ya hana ba?"
"Ke da Allah kima mutane shiru and give me back my stickers"
"Its mine."
"Give it back." Ganin suna neman fara wani sabon fad'a Zeezee tayi seizing
stickers d'in "oya kubi driver ku wuce mota."
"But Mammy its mine."
"Do as I ask Khaleefah to the car."
"Mammy my stickers." Cewar Afreen.
"Se munje gida, to the car now."
Mammy why are you talking tona stranger? Da da ya hana."
"He is not a stranger Honey sunan shi Uncle Adeel."
"Da da ya san shi?"
"Kibi Khaleefah ku wuce mota we'll discuss it later okay? I love you both."
Hannun Afreen Khaleefah ya rik'e suka fice. "I should get going also Adeel, thanks
for saving my daughter from tripping." Har yanzu Zeezee bata ishe sa da kallo ba a
gaskia yayi babban rashi a rayuwan shi na rasa Zeezee gadhi nan ita har yara biyu.
allah ya azurta ta dashi, kyawawa sasu wane yaran larabawa. Gaskiya ne Allah ba
azzalumin bwansa bane, duk yadda yaso destroying wa Zeezee mahaifatrta Allah be
yarda da hakan ba tunda she was innocent gashi nan shi yanzu yana neman shekara
tara (9) da aure ko rabin yaro baida, a rayuwa koda wasa kar mutum ya yarda ya d'au
alhak'in wani. Seda tazo gab da fita bakinsa ya iya bud'uwa.
"Zeezee ko gaisawa ai sai muyi... please." Kaman bazata tsaya ba se kuma ta
tsaya, "ina yini?" ta gaishesa briefly.
"Thousands of days, how have you been great I guess."
"Alhamdulillah ya kake da kuma Ruky?"
"Lafiya, were those two your-" katse sa tayi with a "yes. Yarana ne babban
Khaleefah, k'aramar Afreen."
"Masha Allah time heals, Allah ya raya mana su."
"Amin, nagode ya naka yaran?" Kai ya kad'a mata "sorry?" Ta tambayesa
bewildering.
"Allah be kawo rayayye ba har yanzu Zeezee, sau uku kenan tana haifa ba rai
miscarriages kuwa ba iya ka yanzu haka she is 8 months pregnant duk tsoro saboda
idan ta haifa ba rai suke fitowa kokuwa su koma kafin suna."
"Subhanallah am sorry, Allah sa masu cetoh ne ya kuma kawo maku rayayyu."
"Ameen Zeezee thank you, Zeezee nasan hak'k'inki ne yake binmu har yanzu Ruky
have been searching for you Allah be ta6a had'aku ba. Naji har kinyi obtaining
degree naki na miki murna sosai."
"Ayyah thank you nikam na jima da yafe muku Adeel, dukan mu masu laifi ne kuma
innallaha gafur rahim ku cigaba da addu'a Allah shall see you through in shaa
Allah."
"Zeezee am so happy for you, indeed rabuwa da ni da kikayi shine alkhairi a
gareki ko ban tambaya ba nasan Maj-Gen na kula dake sosai and for that Allah ya
biyashi da gidan Al~jannah."
"Uhm, Ameen nagode nima, I should get going yara na suna jira na I don't wanna
keep them waiting."
"Achan ko?" Ya nuna motan da Khaleefah da Afreen suke ta fad'a a ciki.
"Yes."
"Nice ride also."
"Thank you se wataran Adeel ka gaishe da Ruky kace ina mata fatan Allah ya
sauk'eta lafiya ya kawo rayayyu."
"Ameen Dear Friend In shaa Allah, ko zaki bani number'nki ta kiraki she've been
wanting to do so."
"Sure" wayansa ya miqa mata ta zuba mai sannan sukayi sallama ta fice yana me
binta da kallo seda motansu yabar haraban mall d'in.

*^ADEEL^*
Home shopping na provisions Adeel yayi bayan daya gama instead ya koma gida se ya
wuce gidan wani friend nasa saboda har yanzu shi da Ruky Mama kawai tura tafiyan
suke for all these years al'amura basu dai-daita ba a tsakaninsu.

_9pm_
Miqewan Ruky Mama kenan daga kan gado da k'yar saboda yadda tayi nauyi da alama
cikin nata na 'yan biyu ne cause of irregular girman shi. Bayi ta k'arisa a dafe ta
d'auro alwala tayi Sallah. Wayanta dake kan gado ta miqa hannu ta d'aga tare da
duban lokaci ganin after 9 kuma Adeel be dawo gida ba kawai tasa kuka.
Verily, tayi regreting dukan abubuwan da tayi wa Adeel and above all Zeezee.
Neman lamban Zeezee take ido a rufe, Adeel kuwa bata san me zata sake yi mai ba a
rayuwa ya koma sonta kaman da, ba kalan neman tubansa da batayi amma har yau
al'amura sun kasa daidaita a tsakaninsu da bak'in pentin data shafawa kanta da a
baya har yanzu yake kallonta da shi, be sani ba ta shiryu yanzu she is really a
changed woman. Sau dayawa yakan ce mata shifa ya yafe mata past is past amman
tasani koda ya yafe mata be mance da misdoings natan ba. Idan ba wai ita ta nemi
Adeel ba bayi ta6a nemanta idan kuma har ya zama affectionate and caring towards
her to fa a lokacin tayi miscarriage ne kokuwa ta haifa d'an ya koma koya fito ba
rai bayan nan Adeel bayi ma sanin wani yanayi take ciki, bazata iya tuna when last
Adeel ya leqo d'akinta ba. Ci da sha kam bata rasa ba, bayan nan kuma ko wani
k'arshen wata yana bata dubu goma, ba k'aramin kunyan abubuwan da tayi masa take ji
ba.
Ita yanzu ta hak'ura ya auro duk macen da tayi masa muddin itan zata faran ta
masa rai amman yayi hak'uri ya bata chance su gyara tsakaninsu. For how many years
now suke cikin abu d'aya? Shi be k'ara aure ba bai kuma bata chance da take nema ba
a kullum, she misses her fulani guy, her Adeel. Bata da burin daya fi taga ita da
Adeel are back as the lovebirds they were before. Layin Adeel da tayi saving as.
_Baby_ tayi dialing sanda ya kusan tsinkewa ya d'aga.
"Halo Baby?"
"Yes Ruky."
"Ina yini?"
"Lafiya ya jiki?"
"Da sauk'i, Baby ina ka shige? Yau ma bazaka kwana a gida ba? Please kayi hak'uri
ka dawo I'm sorry." Ta k'are maganan cikin tsan-tsan kuka.
"God! Kukan me kuma kike? Yaushe mukayi dake bazan dawo ba? I'll come home soon."
"Dagaske Baby?"
"Yes so stop crying its not good for your health."
"Toh seka shigo, I love you."
"Aha, bye." Sanyi sosai taji a ranta yau wata rana Adeel ya damu da condition
nata. Duk da kasalan da takeji hakan be sata ta fasa garnishing wa Adeel nata
had'ad'd'en jollof na spaghetti ba tayi setting table.

10:23pm ta jiyo k'aran bud'uwan gate, makeup nata ta gyara. Sanye take da wani
electric blue maternity gown, fitowa parlourn tayi sai dai kafin ta isa da bud'e
k'ofan ya bud'e. "Sannu da zuwa Baby" tayi mishi tana neman amsan ledojin dake
hannunsa.
*MIEMIEBEE. Team #YGC!🎀*
*ZAIMEEN flames🔥🔥🔥*
Beeenovels.blogspot.com 👄

?????? ??????
??❣??
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*????
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee??_*

*March, 2017*
8⃣1⃣

"Yauwa sannu, don't bother bakida lafiya zan k'arisa." A kitchen ya ajiye
ya fito. "Meya hanaki bacci?" So yake yace mata tayi kyau amman ya gommaci
reserving comment nasa.
"Ina jira ne ka dawo, kayi sauri na had'a maka ruwan wanka a bathroom kaje ka
watsa ruwa kazo kaci abinci I cooked your favorite please kar ka ce you are full."
"Me ya kaiki yin girki bayan kinsan condition naki?"
"I just want to make you happy Baby don't worry about my condition."
"Toh thank you."
"I owe the pleasure." Yana ficewa taja kujera ta zauna ta shiga zaman jiransa
bayan ya kintsa kansa shi kuwa ya fito se k'amshin turare yake sanin kowa ne Adeel
d'an gayu ne. A gefenta ya zauna wanda hakan ya mugun bata mamaki da kuma farin
ciki duk a lokaci guda, yaushe rabon Adeel da yayi hakan, kallonsa take wane yau ta
soma sa sa a ido. Da alama be shafa mai ba bayan wankan da yayi hakan yasa skin
nasa glowing and looking fresh. Har yayi noticing kallon da take mishin amman ta
kasa dena starring. D'an gyaran murya yayi, "uhm uhm."
"I'm sorry." Ta mar apologising. Serving nasa tayi ya mata godiya sannan ya
shiga ci duk anan kallon handsome d'an fulaninta take, ta kasa reserving comment
nata dole tace mishi "Baby you are looking dope and fresh, kayi kyau." Murmushi me
sake k'ayata sa ya saki sannan yace, "thank you and you also, lipstick naki ya min
kyau and your makeup in whole."
Shin wai yau a ina zata sa kanta? Rabon Adeel daya yaba ma kyanta ko
kwalliyarta since when? Blushing ta shiga yi "thank you Baby" ta amsa tana murmushi
sosai tare da aza hannunta bisa k'aton cikinta tana shafa kan a hankali.

Kaman ya gano yunwa takeji, toh mesa bazata ci abincin ba? Ya tambayi kansa.
Kaman ya basar se kuma ta basa tausayi. "Kefa baza kici ba? Seems like you're
hungry yadda kike rubbing min kan twins." Wane me jiran ya mata magana ta amsa shi
atake, ko dake jiran dama take se tashi-tashi Adeel ke mata magana wane wani
celebrity haka ganinsa da kuma jin motsi da muryansa ke a gareta. "Bazan iya ci ba
ko naci hararwa zanyi, tea nake son sha kuma na duba ba madara se milo."
"I'm sorry for that, har ya k'are ban sani ba, na sayo miki amma."
"Ba komai Baby thank you barin je in had'a."
"Uhum" nan ta fice kitchen shi kuwa ya cigaba da cin abincinsa, not long enough
ta dawo ta samesa. Shiru ne ya ziyarce su duka bayan da Adeel ya gama yace da Ruky
"seda safe zan je in kwanta" gabad'aya ma ya mance da amsan numban Zeezee da yayi
don bata.
"Baby please I need us to talk."
"What again Ruky?" Sauk'a tayi daga kan kujeran ta sauk'a har k'asa akan knees
nata. "Ruky what ar you doing?" Ya tambayeta da mamaki "get up ke bakisan bakida
lafiya bane? Get up" Cikin kuka sosai tace, "Adeel am very sorry please, I'm
terribly and deeply sorry, don Allah ka yafe min misdoings dana maka a baya na tuba
bazan sake ba."
"Get up I said." Kai ta jijjik'a mai tana me cigaba da kukan. A hankali ya
k'ariso gabanta ya miqar da ita, "don't ever do that again idan kika sake zanyi
fushi dake sosai."
"Kayi hak'uri I just can't help it Adeel, duk cikin friends d'ina ban tsammanin
akwai wacce ta yi ma mijinta abinda na maka, kuka yake sani idan naje gidajensu
naga yadda mazajensu ke sonsu just like yadda kake sona a da kafin na 6ata kaina a
idonka, how I wish we will go back to how we were before." Duk maganan nan da take
tana hawaye takeyi kuma tana kallon k'asa, a hankali ta d'ago kanta tana kallon
fuskan Adeel da emotions kusan biyar suka bayyana akai. "Please give me one last
chance and accept me into your heart and life again, kai kanka kasan yadda nake
sonka Adeel I don't have to tell you again but if you really need to know then I'll
saboda ban tsammanin zan iya rayuwa ba kai nayi nadaman abubuwan dana yi maka so
dayawa kana cewa kai ka yafe min amman nasan baka manta dasu ba. I know any moment
you look at me kallon abubuwan banzan danayi maka kake shiyasa har rana me kaman na
yau baka damuwa dani kuma I don't blame you saboda laifi na ne amman kayi hak'uri
don Allah, I'm sorry na yarda ka auro duk matar da tayi maka in ma mata uku zaka
dad'o min kayi ni I don't care anymore, muddin hakan ze sanya ka farin ciki am
good and fine by it. All I want and need is your attention, care and love for me as
your wife please Adeel."

Jikinsa yaji yayi sanyi matuk'a although today isn't the first time Ruky ta soma
neman tubansa amman na yau ne yayi reaching unto his heart, ta basa tausayi matuk'a
yasan exactly what she is going through now saboda he passed through it time da
yake neman dawo da Zeezee d'akinsa. Yasan exactly how bad she'll feel idan yayi
turning nata down bayan nan kuma ga condition da take ciki. Shima yau da yaga
Zeezee seyaji he wants to make things right between himself and wife. He can
vividly remember murmushi da kuma dad'in daya ziyarci Zeezee a lokacinda ya kira
sunan mijinta shima yaji yana kwad'ayin hakan. Ya zamanto idan an kira mai sunan
Ruky Mama wannan same farin cikin ze ziyarce sa shima but how? That is by giving
her this one last chance she is asking for. Shi kansa sheda ne gameda irin son da
Ruky Mama keyi masa yanzu.
"Please Adeel don't turn me down" ta sake fad'a jin yayi shiru har yanzu.
Hannunsa ya d'aga a hankali ya shiga share mata hawayen ta abinda bata ta6a
tsammani ba kenan. "Cry nomore kinji? Bana son ganin tears d'innan na sha gaya miki
I've forgiven you a long time ago and now am forgetting it all, I won't hold any
grudges on you again because I love you. Give me a chance also to make our love
story a hit." Wani irin dad'i maras misaltuwa ta tsinci kanta a ciki.
"Baby are you serious? Do you mean all these?"
"Yes Honey." Dan murna tama rasa abinda zatayi, a hug is all she needs, hugging
nasan ta gwada yi sede inaa k'aton cikinta baze barsu su matse juna ba kaman yadda
ya kamata. Hakan ya sanya ta murmushi sosai and him also. "Twins namu bazasu bari
Sugar lips d'ina tayi hugging d'ina bako?" Ya tambayeta. Da murmushi kwance fal a
fuskarta ta amsa shi.
"Ai fah and I really need that hug." Ta one side ya kwantar da ita a jikinsa
"I'm sorry Darling for letting you suffer as I did."
"Shhh! Nice ya kamata na baka hak'uri."
"Muje mu kwanta? Am feeling very sleepy."
"And me too barin tattara kan table d'in."
"No kibari gobe me aiki zata tattara banason kina gajar da kanki." If only ze iya
d'aukanta da yayi amman ta mai nauyi dayawa don haka suka taka side-by-side har
izuwa door step nata. Da mamaki ta juyo tana kallonsa "a nan zamu kwana?"
"A ina muke kwana da?"
"A nan" ta amsa tana blushing.
"Good anan d'in zamu cigaba da kwana nabar chan har abada in shaa Allah."
"Aww I love you so very much Adeel my Baby."
"I love you too Ruky my price possession." Ahaka suka k'arisa d'akin shida kansa
ya zak'ulo mata night gown nata ya tayata ta sa sannan suka kwanta, kanta ya aza
akan chest nasa tare da kewaye hannunsa a bayanta. "Thank you Baby."
"I owe the pleasure aha! Kin ma tuna min."
"Mene Baby?"
"I met Zeezee earlier today at Jifatu."
"Dagaske?!" tayi maganan unbelievably tana neman d'agowa amman ya mai data.
"Allah sarki Zeezee how I wish ni na ganta, yaya take please?"
"Idan kin ganta ma ba ganeta zakiyi ba tayi k'iba sosai ta k'ara kyau kaman ba
ita ba and guess what?"
"Ayyah tell me please."
"Yaranta har biyu she had even told me their names amman na manta babban de
Khaleefah ne. Very cute kids kaman arabs idan kin gansu."
"Ayyah Zeezee am so happy for her, ashe de mahaifarta bata lalace ba lokaci ne
kawai beyi ba."
"Ni kaina na mata murna and at thesame time I felt bad for what I did to her."
"Tunda ta yafe maka ai da sauk'i Baby nice de har yanzu hak'k'inta ke bina."
"Kema tace ta yafe miki ki dena damuwa kinji? Na amsa miki numbanta ma seki
kirata kiji da kunnenki."
"Aww thank you Baby na jima ina neman numbanta finally my mind can be at ease
idan har ta gayamin ta yafe min."
"Tama yafe miki Babe don't worry, naso kiga kids nata wallahi duk kyantan nan
sunfi ta."
"LOL nima zan gansu some day in shaa Allah, I once heard mijin nata na kama da
larabawa ai."
"Yana ma kama dasun ai, I think Shuwa Arab yake by tribe ta ta6a gaya min they
are lucky to have each other as we are also lucky to have each other right?"
"Right Baby, am the most luckiest since I have you." Pecking kanta yayi a hankali
"lets sleep okay? Our twins needs rest tunda yau kika yi aiki kika gajar min dasu."
"Uhmm, I really hope this time zasu fito da rai Baby I can't bear to lose both of
them at a time, Baby its will be so painful and hurtful."
"Shhh! In shaa Allahu this time rayayyu Allah ze kawo mana shiyasa ya had'a mana
biyu a lokaci guda Babe, just hold on and have faith Allah shall see us through."
"Allah yasa Baby."
"Ameen Babe of them all I love you."
"I love you more you know that" a haka beautiful and everlasting sleep yayi
taking over control nasu duka.
Washegari Adeel na gefenta ta kira Zeezee se a karo na biyu Zeezee ta d'aga
kasancewar game da Afreen ke bugawa ta kuma k'i ta bata wayan. "Halo?" Cewar Zeezee
nicely.
"Assalamu Alaikum" Ruky tayi sallama gabad'aya seta ji baza ta ma iya neman
tuban Zeezee ba saboda girman laifin data yi mata na k'azafi. Kallon Adeel take
wanda ya bata nod tare da matse hannunta cikin nasa assuring her he is with her.
"Wa'alaikumus salam."
"Zeezee good morning."
"Morning yaya kike?" Tayi maganan still bata gane waye ba sede she's sure tasan
wannan murya but a ina? She can't remember.
"Lafiya qalau, kwana dayawa Ruky Mama ce Adeel's wife your ex co-wife."
"Wow! Ruky! Kwana dayawa yaya kike?"
"Lafiya qalau Alhamdulillah your side?"
"Lafiya qalau ya yaran mu kuma?Adeel jiya yazo ya dameni wai yaga yaran Zeezee
kaman larabawa."
"Hahaha Adeel harda k'arya de nafa fisu kyau." Murmushi Adeel dake gefe ya saki.
"Uhmm, toh Allah ya raya mana su." Daga nan ta sanar da ita main reason na
kirarta da tayi, anan Zeezee tace ita fa ta jima da yafe mata Allah yafe masu
gabaki d'aya. Godiya sosai Ruky tayi mata, yau babbar rana ce a gareta tunda ta
sauk'e hak'k'in Zeezee daga kanta.

*^ZEEZEE^*
_Later during the day... 10:57am_
Aiki Zeezee ta tashi dashi sosai yau kasancewar yau Al'ameen nata ze dawo.
Before 3pm duka da yaranta suka shirya suna jiran dawowan Hero'n su. 3:12pm suka
jiyo k'aran bud'e gate nan Afreen da Khaleefah suka shiga daka tsalle sun kasa
jiran shigowan Da dansu ma, da gudu suka fita suna "Da da oyoyo!" Yana fitowa daga
motan ya d'aga Khaleefah sama yayi pecking nasa a cheeks sannan Afreen itama,
itakam har juyi Al'ameen yata yi da ita a sama sannan yayi pecking nata itama,
Khaleefah ya sake d'agawa ya rik'esu both a hannunsa suka k'ariso ciki inda suka
tarar da Zeezee rik'e da camera tana jiran musu hoto.
"Wow!" Al'ameen ya furta a lokacin da yayi setting eyes nasa akan Zeezeen sa she
is looking so takeaway. Anytime yayi spending time apart from her seya ga ta dad'a
yi masa kyau. Ya d'auro niyyan ajiye su Afreen ya d'aga Princess tasa kenan tayi
sauri tace, "not so fast Sweetheart tsaya in d'auke ku hoto tukuna." Ji yake like
baze iya jira ba, yatsa d'ad'd'aya Khaleefah da Afreen suka sa a bayan kan Al'ameen
seya fito like rabbit ears suna dariya Zeezee ta d'auke su hoton. Yana sauk'esu
yace, "Sweethearts go to your rooms okay? Saje ya shiga muku da toys dana siyo muku
go and check them out, hurry!"
"Really Da da? Ka siya min Princess gown da crown harda magic wand?"
"Yes Little Princess all that hurry!"
"Nifa Da da ka siya min all the different types of guns da na nuna maka a Disney
XDbda 3D video game d'in?"
"Why not My Little Soldier go check them out."
"Yeyyy!" Cewar Afreen "Da da carry me up I want to kiss you." D'agata yayi ta mai
placing kiss a cheeks nasa sannan light one a lips nasa. "I love you lil Princess."
"I love you too Da da sauk'eni inje inga gown d'ina." Yana sauk'eta ita da
Khaleefah suka fice a hanyan ma seda suka yi fad'a wai sam se de itace a gaba shi a
baya shi kuma wai ai shine babba shi ya kamata yana tafiya a gabanta tana binsa a
baya. Seda duk suka shige d'akunan nasu Al'ameen ya maido da kallonsa kan Zeezee
dake kallon corridor'n d'akunan yaran then back to her Soldier.

"Princess didn't miss me or did she?" Ya tambaya yana frowning face nasa. "Oh
come on Sweetheart you know that's not true."
"Gashi nazo har yanzu bakiyi hugging d'ina ba bale in samu kiss ma." Murmushi ta
saki sannan magestically ta taka ta k'ariso wajensa yadda ratan dake tsakaninsu
befi 2 inches ba. "I missed you like hell Sweetheart."
"I missed you more, you are looking elegant."
"Thank you My Soldier so as you." A hankali ya zagaye hannayensa a waist nata
drawing her more closer until jikinsu ya manne. "May I go for a kiss?" Seda ta
zagaye nata hannun a wuyansa tace, "it is done." Lips nata yayi owning a hankali
suka shiga kissing juna slowly yet passionately. Sun yi nisa suna enjoying
company'n juna kawai Khaleefah da Afreen suka fito a guje from nowhere, tana ce mai
se tariga sa nuna wa Da da gown nata. Wani irin birki suka taka dukansu ganin
abinda Mammy da Da da keyi. Se k'wararo ido waje suke barin ma Afreen, da sauri
Khaleefah ya aza hannu ya rufe mata ido shima ya rufe nashi. "Let me go, I want to
shee Da da and Mammy" ta shiga shuresa anan hankalin Zeezee da Al'ameen ya buga da
sauri sukayi releasing juna, Zeezee kan ma ta kasa kallon direction na yaran nata
don kunya. "Ahhh Princess!" fad'in Al'ameen yana susan k'eyansa "your gown is so
elegant."

"Mammy, Da da what where you tw" da sauri Khaleefah ya rufa mata baki "lets go
back in."
_Ka sakeni_ take son ce mar amman don yadda ya toshe mata baki ta kasa se
shuresa take shiko yak'i saketa seda suka k'arisa d'akin ta.
"Khaleefah is such a smart guy" cewar Al'ameen yana bin fuskan Zeezee da touches
which is damn sending her electric sparks.
"He is indeed Sweetheart, Afreen kuma baki ba."
"LOL ba dama kam, I believe itama don lokacin ta ne remember Khaleefah shima da
yake shekarunta yaga pant-" da sauri ta toshe mai baki "haba mana Sweetheart kai
kullum seka d'auko zancen nan how many years now?"
"LOL nayi shiru na dena toh, kawai yadda Khaleefah yayi hanging pan-"
"Again!" ta katse sa kaman zatayi kuka. Dariya yake sosai "am sorry nayi shiru
toh."
"Zaka gani ai na tafi strike yau ba ni ba kai till further notice."
"Strike Princess? Meyayi zafi?" ya had'e gira. "Kinsan how I've been waiting for
this day kuwa? 3 months fa ba ke Princess it's not easy."
"Aww ashe har 3 months kayi a Abj ban sani ba."
"Princess!" Yanzu kan tamkar zeyi kuka.
"Muje ka watsa ruwa."
"Kin yafe strike d'in?"
"A'a fa na rage de se next week zan baka kaina."
"Na shiga uku Princess you want to kill your last standing Soldier ne?"
"Oho ba ka iya neman tsokana ba muje kayi wanka the kids must be hungry ka fito
muci abinci."
"Ba matsala" ya fad'a da biyu irin ya hak'ura d'innan, "muje to ki rakani." Shi a
dole zeyi mata wayo.
"Nan da bathroom d'in?"
"Princess yanzu haka kika dena yayi na? Da wankan ma cewa kike zakimin yanzu ki
rakani bathroom d'in ma bazaki yi ba?"
"Eh kaje ina jiranka."
"Shi kenan ba matsala nasani Khaleefah da Afreen sun k'wace min GATA na yanzu."
Ganin ya juya ze shiga tafiya ta kama hannunsa da wuri tare da amshe hulan uniform
nasa tasa a kanta "wasa nake maka Sweetheart duk duniya ba wanda ya isa ya amshe
maka GATAN ka a birnin zuciya na kai baka sani bane ko? your other name is D'AN
GATAN Zeezee." Dad'i sosai yaji yaja cute nose nata, "hulan suits you alot."
"Really? Tsaya mu d'au selfie to" kir-kik ta d'au kesu selfie a wayanta.
"Zakiyi adding a story'nki ne?"
"A ina?"
"A Snapchat" ya fad'a da gangan yana son jin me zata ce.
"Chabd'i! Me ze kaini ai nabar posting pictures naka they belong to only me."
Hannunta a cikin nasa suka k'arisa d'akin su da ta k'ayata kan gadon da red roses
se k'amshin turaren wuta ke tashi. "Wow! Princess this is lovely."
"I know Sweetheart do you like it?"
"I love it and I love you more." Key ya waina jikin k'ofan, "Swe-" da sauri yayi
covering lips nata with his, baya-baya ya cigaba da turata har seda suka fad'a kan
gado. Abubuwan dake birkita mata lisafi Al'ameen ya shiga yi mata, tuni yayi
turning nata on suka wula duniyar ma'aurata.

_30 more minutes..._


"Gbam! Gbam! Gbam!" Afreen ke knocking bisa k'ofan d'akin su Zeezee.
"Afreen stop it kizo muje mu jira su a parlour." Cewar Khaleefah yasan its in
appropriate ana barging into parents room anyhow.
"O'o you can go, ni am shiteying here."
"Gbam! Gbam! Gbam! Mammy!!!" Ido wuru-wuru Zeezee ta kwararo waje in a whispering
tune tace, "Sweetheart ka gani ba? Shiyasa nace maka ka bari zuwa dare kak'i."
Kafin ya amsata Afreen ta sake sa wani ihun "Mammy!!!"
"Na'-" da wuri Al'ameen ya katse Zeezee ta hanyar covering mata baki da hannunsa.
"Shhh!"
"Mammy ij that you? Open up!"
"Lil Princess?" cewar Al'ameen.
"Da da! Open up."
"Princess jeki jira mu a parlour kinji? We'll be back in a bit."
"No open up!"
"Afreen lets go." Cewar Khaleefah.
"No I want to shee Mamamy."
"Mammy is coming then." Cewar Zeezee daga ciki.
"Are you mlsure Mammy?"
"Yes Darling ina zuwa yanzun nan se muyi having lunch ba."
"Yes I want to show you My Princess gown and you too Da da."
"Toh lil Princess we are coming right away." Cewar Al'ameen. Miqawa Khaleefah
hannunta tayi yayi grabbing suka wuce parlour, nan ma sanda suka
yi fad'a ita wai sam asa mata Disney Junior shikuma yace sede Disney XD gashi koya
ajiye mata remote ba iya canza channel d'in tayi ba.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!??*


*ZAIMEEN flames??????*
Beeenovels.blogspot.com ??

?????? ??????
??❣??
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*????
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee??_*

*March, 2017*
8⃣2⃣

_Back inside._
"Sweetheart ka d'agani in tashi the kids are waiting for us."
"Princess why can't I get enough of you?" Yayi maganan yana showering kisses ma
wuyanta and deep down tickling amd turning her on the more.
"Sweetheart please stop it kasan I can't resist you and the kids are waiting for
us."
"They'll have to wait a bit saboda I miss My Princess badly" daga fad'in haka
yaja bargo ya rufesu.****

It took them quite a long time sannan Zeezee ta samu da k'yar tayi ma Al'ameen
wayo ta miqe daga kan gadon kafin ya kuma kamota, jikinta na nannad'e da bargon
ruhuwansu.
"Princess wato yau rowan kanki kike min ko?"
"Wai rowa, upon all the..." se kuma tayi shiru.
"I still need you Princess."
"I promise tonight amman yanzu muje muci abinci muyi wanka muyi sallah."
"I want you now."
"Su Afreen fah?"
"They'll wait" yayi maganan yana neman kamota. Gudu tasa sede kafin tayi nisa ya
samu ya kama k'arshen bargon.
"Wallahi Sweetheart idan ka ta6a ni zan tara maka jama'a."
"Su waye jama'an anan? My kids or men?"
"Duka."
"Let's see about that."
"No Sweetheart please karka sake kwantar dani kan gadon nan am feeling hungry."
"Let's feed each other then nima yunwa nakeji" yayi maganan yana neman fara janta
da ragowan bargon dake hannunsa.
"Sweetheart wai me ka sha yau ne? Please ka bar jan bargon kafa san dashi kad'ai
na dogara."
"I don't care ki matso toh."
"O'o ka dena please nasan idan na matso da k'yar in iya sake k'watan kai na."
"Shikenan na cigaba da ja kenan har seya sum6ule." Jan ya cigaba dayi.
"Please mana Sweetheart se nayi maka kuka tukun ko?"
"Toh kizo da kanki."
"Promise baza ka min wani abin ba."
"LOL da me zan miki Princess?"
"What bad boys do."
"Fa kina 6ata min lokaci Princess kizo ko senaja blanket d'in ya fad'i tukuna."
"Eh kaja tunda yanzu ka zama bad boy."
"Zan ja fa."
"Ka ja d'in." Ganin da gaske yake ze ja tayi gudu ta fad'a jikinsa tare da turesa
ya fad'a kan gadon da baya "yanzu Sweetheart dagaske ja d'in zakayi?" Tayi maganan
kwata-kwata ratan dake tsakanin fuskansu befi inchi d'aya zuwa biyu ba.
"You promised tonight right?"
"Yes I promise."
"Toh ko kad'an ne be mine yanzu Princess."
"Akan wanda kayi d'azu Sweetheart? our kids are waiting for us tashi kasa kayanka
muje muci abinci."
"After a kiss."
"Ahh! Ahh!"
"Please manaaa." Bending tayi a hankali ta bashi the kiss of his life. Se anan
yaji d'an dama-dama, kayakinsu suka miyar suka fito. A parlour suka tsinci
Khaleefah da Afreen se bacci suke sha TV nata aiki. So cute suka kwanta, kan Afreen
na akan cinyan Khaleefah da alama bayan fad'an sunzo sun shirya. Murmushi both Da
da and Mammy suka saki at their kids lovely sight sannan Al'ameen ya k'arisa ya
d'agasu duka ya kai each of them d'akinsu ya dawo ya tarar da Zeezee tana arranging
throw pillows da suka hargitsa.

"Haka kawai kika hana ni kanki yau Princess gashi toh suma sunyi bacci."
"Wane ni Sweetheart? Taya zan hanaka kaina? Kaga yunwa ne ya musu yawa har
sukayi baccin, I promise to make it up to you tonight seka gaji da ni." Ta k'are
maganan tana mai signal da gira.
"Abinda bazan ta6a yi ba kenan."
"Muje muyi wanka toh muyi sallah kafin nan suma sun tashi se muyi having lunch."
"Together?" Ya tambayeta.
"Yes together let's go." A tare sukayi wankan suka d'auro alwala sannan sukayi
sallah suka fito parlour suna zaune suna hira before kids nasu su tashi. Chan suka
jiyo k'aran bud'uwan k'ofa da kuma rufewansa. In a minute Afreen ta bayyano rai a
had'e tana susan ido ta wani had'e rai wane hadarin yamma.
"Owww little Princess is finally awake" cewar Al'ameen.
"Da da, Mammy I'm feeling hungry" ta fad' tare da rushewa da kuka da sauri Zeezee
ta mik'e ta d'agata "cry nomore Darling je kiyi brushing kafin nan Khaleefah ya
tashi se muyi having lunch ko?" With a nod Zeezee ta sauk'eta.
"I love you lil Princess." Cewar Al'ameen.
"I love you too Da da." Maimakon tayi d'akinta seta bi na Khaleefah, toilet nasa
direct ta shiga ta d'ago brush nasa, ita wai wayo bazata yi brushing da nata brush
d'inba se nasa simply cause bata son nata ya tsufa tafison anytime Da da yace kowa
yayi showing brush nashi aga nata ne sabo. Shiko Khaleefah idan da akwai abinda ya
tsana shine yaga Afreen na brushing da toothbrush nasa.

Seda tagama tazo fitowa kenan lokacin shima Khaleefah ke miqewa daga kan gado.
"Khaleefah ka tashi lets go and have lunch."
"Tsaya what are you doing inside my bathroom?"
"Nothing" tayi maganan tana sauri zata fice.
"Come back Afreen" da gudu tasa se waje, da hanzari ya k'arisa bayin brush nasa
ya soma d'agawa jinsa a jik'e yasan tabbas dashi Afreen tayi. "Oh this girl!" Ya
furta agitated sannan ya fice yana k'walla mata kira "Afreen! Afreen! Where are
you?" Achan parlour a bayan Da da ya sameta.
"Mr. handsome kaima ka tashi?" Cewar Zeezee. "Evening Da da evening Mammy." Ya
gaishe su.
"Ya akayi lil man? Why the furrowed eyebrows?" Asked Al'ameen.
"Da da how many times do I have to tell Afreen ta dena yimin brushing da
toothbrush d'ina but she wouldn't listen."
"Haba Princess" cewar Al'ameen tare da dawo da kallonsa akan Afreen dake ta raba
ido. "I didn't Da da he is lying."
"No I'm not she did brushed her teeth with my toothbrush."
"No I did not don't lishen to him Da da." Ta sake k'aryata sa.
"Uh-uh Afreen don't lie kinji Sweetheart? Did you or did you not brush with his
toothbrush?" Zeezee tamata tambayan calmly ai kuwa tasa kuka tana kama jikin
Al'ameen. "Da da see mummy is trying to call me a liar, ni banyi blushing da
toothblush na Khaleefah ba.l
"Shh! Sweetheart enough okay?" Yayi maganan finally tare da aza ta bisa
cinyansa. "I know you didn't bar kukan haka, Khaleefah yi hak'uri kaji kaje store
ka d'au sabo." Hararan Afreen yayi sannan ya fice nan Zeezee ta maido da kallonta
kan Afreen dake faman murmushi. "You know lying is not a good habbit ko?"
"Princess let her be please." Cewar Al'ameen.
"No Sweetheart you are not helping her at all, idan kana mata haka ta cigaba dayi
kenan kuma zata tashi da k'arya. Now Afreen look at me." Kafad'a ta buga. "I said
look at me" Zeezee ta fad'a sounding serious. Kuka ta shiga neman yi "Da da tell
Mammy to stop scolding me."
"Shhh! Sweetheart don't cry okay?" Ya share mata d'an hawayenta "and listen to
Mammy, turn and look at her." Kaman baza tayi ba seta juyo tana kallon Zeezee.
"Did you or did you not brush your teeth with Khaleefah's toothbrush?"
"No. "
"Pretty girls don't lie only the ugly ones does idan kika min k'arya ke mumuna ce
kenan."Kuka ta kuma sawa tana ihu "niba mumuna bace I am beautiful."
"Then tell me the truth."
"I did."
"Toh why? Ba ya hanaki ba yace baya so?"
"Ni nafison nasa."
"Why Princess kowa Da da ya siya mishi nashi kowa se yanayi da nashi."
"Ni o'o."
"Yi hak'uri kinji? Kinga idan bakiya brushing da naki Da da baze sake siya miki
sabo ba."
"Is that tlu Da da?" Kaman yace mata no se Zeezee tayi mai ido "yes Princess kina
brushing da naki kinji? Yana tsufa sena siya miki new one okay?"
"Okay" ta fad'a sounding defeated.
"That's my girl" Zeezee tayi praising nata tare da pecking nata a forehead. Dai-
dai lokacin Khaleefah ke fitowa kenan, "now go and apologize to your brother tell
him bazaki sake using toothbrush nasa ba."
"Do I have to Mammy?"
"Yes Princess you have to."
"Really Da da?"
"Yes Sweetheart go okay?" Da kansa ya sauk'eta ta taka ta samu Khaleefah "I am
sorry Khaleefah." Murmushi ya saki mata sannan yace, "its okay." Hugging nasa tayi
shima yayi hugging nata back "they are so cute and lovely" Cewar Zeezee tana
kwanciya bisa chest na Al'ameen, zagaye hannunsa yayi a bayanta "indeed they are
Allah ya rayasu ya cigaba da had'a kansu."
"Ameen Sweetheart and we also." Pecking nata yayi a forehead.
"Mammy am hungry" fad'in Afreen.
"So am I" cewar Khaleefah.
"Lets have lunch toh." Kamar yadda suka saba zama kullum haka ma sukayi yau,
kujera Khaleefah ya jawa Afreen ta zauna tare da yimasa godiya sannan shikuma ya
zauna adjacent to her and opposite to Al'ameen a yayinda Zeezee ke zaune ita kuma
adjacent to both Al'ameen and Khaleefah and opposite to Afreen. "Mammy what do we
have as lunch?" Afreen ta tambaya tana goga fork da knife dake hannunta gu d'aya.
Sanin ta tsani beans Zeezee tace da ita "beans porridge Honey."
"Nooo! Not that I don't want that" ganin zata soma yi musu kuka Zeezee tace,
"just kidding Darling Mammy cooked your favorite."
"Wow! French fries?" Suka tambaya a tare.
"Yes Sweethearts" nan da nan tayi serving kowa suka shiga ci kowa yayi shiru
banda Afreen data kasa learning table manners nata har yanzu se surutun da ba kai
take ta yi musu na class teachersu da classmates.
"Honey surutun ya isa mana can't you see Khaleefah? Yayi shiru yana cin abinshi.
Its a very bad table manner mutum na cin abinci yana surutu, Sweetheart talk to her
kai baka ta6a yi mata fad'a duk abinda takeyi dai-dai ne a idonka ko?"
"Princess ba haka bane, its her time-"
"No its not " ta katse sa nicely "kayi mata magana."
"Okay" ya fad'a tare da maido da kallonsa kan Afreen "Lil Princess?"
"Yes Da da."
"Yi shiru mu cinye abincin yaso seki bamu labarin teacher'n naku okay?"
"Kaima kana biyewa Mammy ko?"
"No Sweetheart why should I?-" da sauri ta katse sa as if though ta tuna wani
abu. "Aha!!! Da da ka hana mu magana wa strangers ba?"
"Yes Princess I did ba kyau suna guduwa da mutane."
"So yestarday when we went shopping Mammy talked to a stranger and he even passed
her his phone tasa wani abu aciki right Khaleefah? We saw them through the window."
Mintsinin ta yayi nufin tayi shiru. "Awwyy Da da kaga yayi pinching d'ina ko?"
Shiru Al'ameen yayi yana kallon Afreen ya sani tabbas yaro bai k'arya se idan yaga
abu gashi reaction na Khaleefah ma kad'ai amsa ne ga tanbayan dake running mai a
mind. He don't want to believe Zeezee is cheating on him yasan its not in her to do
so amman me kalamun Afreen ke nufi? He trusts her komin me za a ce mishi a fad'in
duniyan nan he'll never believe his Zeezee is cheating on him har se idan ya gani
ne da idonsa. What he is worried about is why Zeezee bata sanar dashi sun had'u da
wani ba jiya and even today bayan shi duk abinda ya faru koda nemansa wata mace
keyi yana sanar da ita. Why is she hiding this away from him? Is there really
something going on between them two?

"Aha! tace min sunan shi... meh ma Khaleefah? Uncle... uncle..." duk anan Zeezee
ta kasa cewa koda uffan.
"Keep quiet Afreen you talk too much." cewar Khaleefah.
"Eh d'in Da da ka ganshi ba? Big head kawai aha! Uncle Adeel right Mammy?" Dum!
Al'ameen yaji gabansa ya fad'a Adeel? Me ya kawo Adeel kuma again? Shin dagaske ne
ya miqawa Zeezee wayansa ta zuba abu aciki like yadda Afreen ta fad'a? Toh mema
zata sa mai cikin wayan idan ba number ba, wow! Allah sa suspicions nasa are not
true he can't bear the thought that his Princess is still in touch with Adeel.
Lunch da suka kasa k'arisawa kenan nan da nan Al'ameen yace he is full. "I'll
be in my room okay Sweethearts? Zan huta idan kun gama cin abincin ku kuje kuyi
wasa amman fa banda fad'a da rough play Khaleefah don't bully your little sister
and Afreen don't disrespect your big brother."
"He is not my big bro ni kaine big bro d'ina."
"He is Sweetheart bakiga kullum shi yake kula dake ba in my absence or Mammy's?"
"Hakane Mammy?" Ta tambayi Zeezee. Da a da ne quite sure Al'ameen ze juyo ya
kalleta amman yanzu ko kallon direction nata beyi ba "yes Honey" ta furta da k'yar.
"Okay then."
"That's My Princess I love you okay?" Kiss ya miqa tayi mai placing light one
akan lips nasa sanann Khaleefah ma ya mishi a cheeks. "Da da Mammy fah? Won't she
kiss you also?" Ba kalli direction na Zeezee ba yama Afreen murmushi "her mouth is
full seta gama okay?"
"Okay Da da I love you."
"I love you too Sweetheart." Yana kaiwa nan ya shige d'akinsu ya rufe. Ita kanta
Zeezee ta kasa k'arisa lunch d'in se juya fork d'in kawai take a cikin plate d'in.
Bayan da yaran suka gama ci ta tattara gun sannan ta wuce d'aki ta samu Al'ameen.
Ko juyawa ya kalli wa ya shigo beyi ba sanin ita ce definately. Ciki ta k'arisa
tare sa zama daga side na kansa ta gefen pillownsa "Sweetheart?" Ta kira sa a
hankali. Shiru yayi kaman baze amsa ba chan yace, "yes Princess." Without turning
to look at her.
"Sweetheart mesa baka k'arisa cinye lunch naka ba ka tashi?"
"Na k'oshi" ya amsa a takaice.
"Definitely not, I know you too well saboda abinda Afreen ta fad'a ka k'oshi?"
"Me tace ma?"
"Talk regarding Adeel."
"Nop not at all kawai na k'oshi ne and I want to rest now." Har yanzu be juya sun
had'a ido ba. "Please stop backing me ka juyi muyi magana."
"Princess can't we discuss it later? Ina so inyi bacci yanzu."
"You are simply avoiding me Sweetheart, I just want you to know that I am not
having an affair with Adeel, for God's sake why will I cheat on a perfect husband
like you?" Tayi maganan tare da cusa hannunta cikin gashinsa tana sosa mai cikin a
hankali in a soothing manner. Shi abu d'aya yakeson ji yanzu sun had'u da Adeel
kuma ta bashi number'nta yes or no.
"Yes I did met Adeel jiya a jifatu." Mumunar fad'i gabansa yayi da k'yar ya iya
fad'in "and you did gave him your phone number?"
"Swe-"
"Please yes or no?" Ya tambaya still not minding to look at her.
"Yes Sweetheart I did gave Adeel my phone number."
"Its okay abinda nakeson ji kenan, if you may excuse me inason in d'an huta
please kaina namin ciwo." Hannunsa yasa ya zare nata dake cikin gashin kansa.

Kansa ta d'aga ta aza akan cinyarta. Ganin yana k'ok'arin sauk'ewa tayi sauri
tace, "please don't Sweetheart let me hold you." Baya ya juya mata ba tare da yace
komi ba, hannun nata ta sake miyarwa a hankali cikin gashin kansa tana massaging
masa scalp nasa a hankali. "Sweetheart I am not cheating on you, ba komai a tsakani
na da Adeel taya zan koma son Adeel bayan zuciyana na gunka? Taya zan koma son
Adeel bayan torturing d'ina da yayi ya nuna min hatred a fili? Why will I love the
man that made my life a living hell and forget about the man who showered me with
love and care, raised my standards and is ready to sacrifice the whole world to me?
Taya zanyi haka Sweetheart? Believe me when I say this wallahi ba komai tsakani na
da Adeel na bashi number na ne saboda Ruky Mama..." nan ta kwashe labarin komi ta
bashi "I am not lying to you Sweetheart I will never lie to you." Se anan ya juyo
yana fuskantar ta kansa akan cinyarta har yanzu "then why didn't you tell me all
these Princess? Inda Afreen bata d'auko maganan ba shikenan kenan bakida niyyan
gaya min? Didn't we promise never to hide things away from each other again?"
"We did and I'm sorry for breaking that promise, I thought it of no use."
"It is of every single use Princess, Adeel was your first love and also your ex
husband ba yadda za'ayi inji you guys are in contact and expect me not to go mad or
angry. I love you remember?"
"I know and I am sorry, am really sorry please stop being mad wallahi ba komai
tsakani na da Adeel I just consider him as a muslim brother and nothing more you
are the love of my life Sweetheart kai ne ginshik'in rayuwa na."
"I know Princess kinsan why I was mad?"
"Saboda ka d'au something is going on between Adeel and I?"
"Noo" ya fad'a tare da kad'a kai. "I will never believe in such a thing saboda I
trust you 100% kuma nasan you'll never betray my trust or will you?"
"I will never do that Sweetheart thanks for trusting me, toh meya 6ata maka rai
tunda kace haka?"
"For hiding it away from me."
"Bazan sake ba I'm sorry kaji? Do you believe me now?" Kai ya gyad'a mata tare da
murmusawa kad'an. "Can I go for a kiss then?" Kai ya kad'a mata "no."
"Sweetheart are you still mad?" Ta tambaya tamkar zatayi kuka murmushi ya mata
sannan yayi bending kanta da kansa ya shiga kissing nata after a while yayi
releasing nata. "No keeping secrets away from each other okay?"
"Okay Sweetheart may I join you mu kwanta tare? I miss your arms around me."
Sauk'e kansa yayi daga kan cinyanta yayi ya koma kan pillow, anan ta samu ta
tsokala kanta a d'an space dake gefen nasa, cusa jikinta tayi a nasa shi kuwa ya
rungumeta gagam har sukayi bacci.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!?? ZAIMEEN flames??????*


Beeenovels.blogspot.com ????

?????? ??????
??❣??
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*????
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee??_*

*March, 2017*
8⃣3⃣

****
Se Maghrib suka tashi, da mumunan ciwon ciki Zeezee ta tashi ta juma batayi
menstral cramp irin wannan ba tun bayan haihuwar Afreen se yanzu. "Princess is
there a problem?" Ya tambayeta ganin yadda take ta yamitsa fuska.
"Sweetheart menstral cramp." Ta fad'a da k'yar.
"Yau kuma?"
"Argghh!" Ta kama sa by his arm tana matse hannunsa cike da azaban da takeji.
"Sannu kinji? Zaki iya jira inyi Sallah?" Kai ta gyad'a mar zallah sannan ya miqe
nan da nan yayi alwala shida Khaleefah suka wuce masallaci, Afreen kam dan wasan da
tayi se bacci kawai take if not idan idon ta biyu tare suke zuwa Masjid d'in. Suna
dawowa Khaleefah ya tsaya a parlour yana kallon cartoon network.

Al'ameen na shiga d'aki ya tarar da Zeezee miqe a kan tiles tanata juyi.
Jallabiyansa ya cire yayi hanging ya k'arisa kanta da sauri, "Princess cikin ne?"
"Ka dawo sannu da zuwa."
"Cikin ne har yanzu?" Nan ma kai ta gyad'a. "Sannu kinji zaki iya miqewa?" Da
sauri ta kad'a kai "ka barni anan kawai yafi dad'i."
"Anan sanyi ze shiga jikinki Princess yi hak'uri ki bari in mai dake kan gadon."
With a single nod ya d'agata ya miyar da ita kan gadon "ina zuwa." Anan ya fice
dawowansa ya taho mata da pain killer da ruwa "gashi sha kinji?" Da taimakonsa ta
had'iye ta koma ta kwanta.
"Sannu Princess get well soon."
"Uhumm thank you, I will."
"Shh! Princess date naki besan ranan zuwa ba se da ya bari ranan da zanzo bayan
yasan missing naki da nayi." Murmushin dole ta k'irk'iro "we have to wait for just
few days nan da 3-4 days ze d'auke and we'll have ourselves to our satisfaction."
"Get well soon okay? I love you."
"I love you more, Sweetheart please ka aika Saje ya siyo wa yaran dinner ban jin
zan iya tashi."
"Meh amfanin Da dansu? I'll cook dinner for all of us."
"Awww you are so sweet amman karka yi dani ni bazan ci ba."
"Da yunwa kikeson ki kwana min? No way ko kad'an ne zaki ta6a."
"Me zaka mana cooking toh?"
"Zaki iya cin louisiana?"
"It won't be b- arrgghh!!" ta sake matse mai hannu "Sweetheart cikina."
"Sorry, dai-dai ina ke miki ciwon?"
"Mara na." Ta mai pointing, kayan nata ya d'aga a hankali tare da aza hannunsa
akan bare stomach nata ta gun marar nata ya shiga massaging mata a hankali. Hakan
ba k'aramin easing pain d'in yake mata ba, har bacci-bacci ta soma ji unknowingly.
"Sweetheart you are so sweet, thank you."
"Anything for my Princess sannu kinji? How are you feeling now?"
"Much better compared to d'azu I love you." Massaging mata ya cigaba dayi har
seda ya tabbata tayi bacci. K'ure AC'n yayi to 16 degrees sannan ya ja blanket ya
rufeta dashi. Pecking forehead nata yayi a hankali "I love you Princess Allah baki
lafiya" daga fad'in haka ya ja mata k'ofan ya rufe. A parlour ya tarar da Khaleefah
se kallon sa yake hankali a kwance yana cin pop corn.
"Da da where is Mammy am hungry."
"Mammy is sick Lil Man."
"Omg! Wishing her a speedy recovery."
"In shaa Allah Lil Man where is Princess?"
"A minute back she was sleeping, but naji k'aranta a bathroom ta tashi kenan."
"Good, kana jin yunwa kace?"
"Yes Da da and Mammy is sick how are we gonna do?"
"We are going to be the ones to cook."
"We?" Ya tambaya bewildering.
"Yes, Da da, you and Princess."
"Yeyy!" Take ya miqe "what are we going to cook then?"
"louisiana!!"
"Damn! I love louisiana."
"I know and that's why we are making it. Go and check on Princess seku zo kusa
aprons naku okay?"
"Right away Da da!"

In a minute suka sami Da da a kitchen nan ya sanya musu aprons nasu. Flour ya
auna yayi mixing da mixer sannan yasa Khaleefah fasa musu egg nan Afreen tace itama
se tayi gashi ba iyawan tayi ba, a takaice seda tayi asaran k'wai har guda biyar
sannan ta samu ta fasa d'aya ya shiga cikin saucer. Buhun flour d'in ta nufa ita a
dole zata d'aga garin haka ta juye duka a k'asa. "Omg! Princess what have you
done?"
"Da da ba ni bane Khaleefah ne."
"Thanks God Da da nada ido and he saw who poured it down."
"Leave there in mun gama zamu tattara." Kaca-kaca sukayi da kitchen d'in wane
kitchen d'in bori duk dan had'a louisiana, wasa da flour daya zuben suka shigayi
inda sukayi kaca-kaca da fuskokinsu dakuma jikinsu gabad'aya flour tako ina har
cikin gashin kansu ba babba ba yaro, Al'ameen acikin yaransa wane agemates nasu
haka yake miyar da kansa wasa suka ta sha se k'aran shewa da dariya kawai ke tashi
a gidan. Atlast suka samu suka had'a suka sa a oven sukayi zaman jiran shi a dining
space inda Afreen keta basu labarin classmates nata da teacher, shikam Khaleefah
toshe kunnensa yayi don tsiya wai muryan Afreen baya mishi dad'i. Itako ta matso
kusa dashi ta kama kunnensa tana mai ihu a ciki. Atlast sunka galabaita sosai se
yunwa sukeji, barin ma Afreen data k'arisar da energy'n ta tana basu labari ji take
kaman ta ci louisianan a d'anye tsabagen yunwa. Oven na making sound ita da
Khaleefah suka ruga a guje kitchen suna jiran Da da yazo ya cire, bin pan d'in suke
da kallo a yayinda k'amsnin girkin ya mamaye masu hanci a kan dining table Al'ameen
ya ajiye nan suma suka zazzauna akan kujerun su. Kowa da plate nashi a gaba yana
jiran ayi serving nasa, ganin Al'ameen ze soma serving Khaleefah Afreen tasa ihu
tsakaninta da Allah ita bata yarda da hakan ba. Da mamaki Al'ameen ya tsaya kallon
wannan lil Princess tasan gaskiyan Zeezee ne Afreem needs to be scolded atimes if
not abin nata zezo ya wuce gona da iri. "Afreen why are you shouting like that?
Ain't you aware that Mammy is sick and sleeping?"
"Ni o'o no way Da da I go first."
"First in what?"
"Serve me before you do Khaleefah."
"Princess keda Khaleefah waye babba?"
"Ni o'o nine first."
"Da da just serve her first its all thesame." Cewar Khaleefah.
"Then say thank you to Khaleefah."
"But why?" Tayi maganan as if zatayi kuka. Shi ya gane komi yanzu k'iriniyar
Zeezee kap Afreen ta d'auko ba wanda ta rage. "Because Da da said so, now tell him
thank you."
"O'o."
"Shikenan Toh Princess bazata ci louisiana ba." Wani ihun ta sake sawa at the
peak of her voice wannan karan seda ta tasar da Zeezee daga bacci. Ai ta fad'a
sorry'n nan tak'i tama fi tsoron Zeezee akan Al'ameen saboda ta lura Da dan su bame
fad'a bane. Suna cikin ci suka ga Zeezee ta fito fuskanta jik'e da ruwa da alama
tayi brushing ne.
"Mammy!" Khaleefah da Afreen suka kirata lokaci d'aya sounding delighted. Miqewa
Al'ameen yayi ya doso inda take tare da pecking nata lightly on the lips "how are
you feeling Sweetheart?"
"Alhamdulillah da sauk'i your you are my remedy. Omg! Sweetheart me haka a
fuskanka? And your hair also? Flour?" Murmushi ya sakar mata;
"muje kici abinci."
"Louisiana'n kuka had'a?"
"Yes Mammy, I, Da da and Khaleefah." Afreen ta amsa.
"Wow I have such wonderful chefs ashe." Kujera yaja mata ta zauna.
"Omg! Afreen look at your hair sekace ba this week aka miki kitson ba? And you
too Khaleefah your hair is all messy, Sweetheart nasan kun gama min asaran flour.
Am I right?"
"Uhmmmm!" Al'ameen yaja nishi yana bin yaransa da suke faman mai murmushi da
kallo. "Akwai turum a store don't worry Mammy." Ya sanar da ita.
"Owww se a store meaning kun k'arar da buhun dake kitchen d'in kenan? Na shiga
uku!" Nan da nan Al'ameen yayi serving nata as if beji me tace ba yace' "eat okay?"
"Mammy how are you feeling?" Khaleefah ya tambayeta trying to change the topic
yasan soon zatace zata yimai aski abinda baya so kenan.
"Alhamdulillah my lil Soldier thank you okay?"
"Mammy ijit true you are sick?"
"I was but am okay now."
"Better, if not Dr will inject you on your bom bom." Dariya duka suka sa sannan
Zeezee takai bite d'aya baki. "Wwow! Yummy so spicy haka kuka iya girki dama?"
"Yes Mammy ni nayi duka" cewar Afreen, wani banzan kallo Khaleefah ya bita dashi
"ke me kika iya ko seperating yolk ma baki iya ba."
"F*ck you" tace masa.
"Ahhh!" Khaleefah ya saki baki wide in shock bashi kad'ai ba harta Da da da
Mammy. "Afreen! What did you just say?" Zeezee ta tambayeta unbelievably. Ganin
zata sake nanata abinda ta fad'an Al'ameen yayi sauri yayi covering lips nata da
hannunsa. "Shush! Princess don't ever say that again, its not good only ugly girls
say it." Hannunsa ta cire da k'arfi daga bakinta "thats not tlue I heard our Anty
shaying it the other day and she is beautiful."
"No she is not don't ever say it again." Zeezee tayi scolding nata "now say sorry
to Khaleefah idan kika sake fad'an abinda kika fad'a sena... sena..." tama rasa me
zatace.
"Idan na sake cewa f*ck you?" Nan ma da sauri Al'ameen ya sake covering mata baki
"Afreen no don't say it again, only bad people say so, and you're a good girl
right? A beautiful girl am I right?" Al'ameen ya tambayeta
"Yes Da da nafi Khaleefah kyau ba?" Shiru Al'ameen yayi "right?" Ta sake fad'a.
Ido Al'ameen yama Khaleefah sannan yace, "yes Khaleefah mumuna ma kece kakkyawa ai
that is idan kika dena fad'an abinda kika fad'an kenan."
"Fad'an me Da da."
"That bad thing you said just a couple of minutes ago."
"What?"
"The F word Princess."
"Oh you mean f-" da sauri ya sake covering mata baki. "Promise Da da you won't
say it again? Ko mu tafi Washington banda ke?"
"O'o."
"Then be a good girl and apologize to your brother."
"Okay Khaleefah am sorry."
"Ita okay naughty girl."
"Da da see he is calling me a naughty girl."
"Oh come on why Khaleefah? Now tell Princess you are sorry."
"Damn Da da! Zata sake raina ni."
"Tell her you're sorry for calling her a naughty girl." Baki ya murgud'a mata
sannan yace "sorry" briefly.
"He didn't call me Princess Da da."
"Call her Princess okay My Soldier?"
"Da da do I have to ni she is not my Princess." Duk anan kallonsu kawai Zeezee ke
tana cin abincinta a hankali lamarin Al'ameen da kids nasa se ido.
"Then who is your Princess if not Afreen?"
"My wife" ya fad'a confidently. Kad'an ya rage Zeezee bata fito da abinda ke
bakinta ba don dariya har tunanin aure Khaleefah yake ahh lallai.
"Khaleefah you are still very young, it'll take you decades kafin time d'in chan
before then Afreen is your Princess shiyasa Mammy ta haifa maka ita so you can be
her last standing soldier."
"Ni bana so I will find my Princess some other day just as how the Prince inside
the sleeping beauty story found his Princess."
"Da da so am not a Princess?"
"Who said so? you are a Princess bakiga har magic wand kinada ba? Khaleefah call
her a Princess ko kuma bazan sake training men d'ina da kai ba."
"Alright alright Princess shikenan?"
"Yeyy!" Se anan suka samu suka k'arisa dinner'n. Nan Zeezee ta shiga tattara
plates d'in "no Sweetheart kibari zan tattara baki da lafiya" fad'in Al'ameen.
"Oh please don't bother nan da kitchen d'in." Tana shiga kitchen nata taga yadda
Da da dakuma yaransa suka yi mata turning d'inshi upside down sekace kitchen na
bori. K'ara ta saki "OMG! Sweetheart!!!" Jin haka Al'ameen da yaran sukayi d'akin
Khaleefah da sauri suka 6oye a chan suna yiwa Zeezee dariya. Kuka ne kawai bata
yiba bata san ta ina zata soma handling kitchen d'in ba like ba abinda yake right
place nasa komi sun hargitsa. Ajiye plates d'in tayi cikin sink ta fito ta shiga
neman su "Sweetheart kai da carbon copies nakan nan ku fito where are you guys? You
guys owe me an explanation, ina kuke ne wai?" Nemansu ta shiga yi se chan ta samesu
a d'akin Khaleefah tana bud'e k'ofan Afreen ta shiga shooting nata da bubble gun na
Khaleefah kuma da water gun.

*MIEMIEBEE. Team #YGC!??*


ZAIMEEN flames??????
Beeenovels.blogsot.com ??

?????? ??????
??❣??
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*????
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee??_*

*March, 2017*
8⃣4⃣

"OMG! Khaleefah stop it, Afreen! Zan muku bulala fah, stop it!" ai kaman cewa
tayi ku cigaba jik'ata sukayi jak'ab suna masu mata dariya, duk anan Al'ameen na
zaune akan gado yana kallonsu harma da videotaping nasu. Se chan ganin Princess
tasa tana iya kamuwa da mura yace dasu, "kids cut it out ko kun manta Mammy is
sick?"
"Ahhh!" Suka bud'e baki wide open tare da dropping guns nasu "we are sorry
Mammy."
"We are not done yet" tace dasu furiously "and even you too Sweetheart."
"Ni kuma me nayi Princess? Zo abinki come please."
"Nak'i" tayi maganan tana kakkarwa don sanyi wane zatayi kuka.
"Oh don't cry please Darling, yi hak'uri kizo ga towel inyi draining naki. Kids
say sorry to Mammy."
"We are very sorry Mammy" suka fad'a a tare, tare da kama kunnuwansu. Kaman
bazata musu magana ba tace, "its okay"
"Zo kinji Princess?" Kaman baza ta je d'inba sekuma ta shiga takawa wajen nasa.
Bata san me ba se ta ji su Afreen sun shiga yin dariya kona me oho. Seda ta isa gab
da Al'ameen kawai taga ya ciro water gun a bayansa ya shiga jik'ata dashi seda yayi
draining tas sannan ya barta. Khaleefah da Afreen don dariya har fad'i sukayi a
k'asa suna buga kan rug. Immobile Zeezee ta tsaya gun shima Al'ameen dariyan yake
mata. In between gritted teeth tace, "harda kai ko? Thank you" tana kaiwa nan ta
fice a zuciye not minding the calls Al'ameen ke ta mata sending.
"Kids Mammy is angry."
"She really is, Da da please karka barta tamin aski."
"LOL don't worry."
"Its your job to make her happy once more Da da." Cewar Afreen.
"Tam kunsan me nake so daku?" Atare suka kad'a kai suna sauraronsu. "I'll go and
calm Mammy down ku kuma ku shiga bathroom and wait for me, pull out your clothes ku
jirani a bath tub zanzo in muku wanka."
"Da da together with Afreen?" Khaleefah yayi maganan unbelievably yana pointing
na Afreen.
"Yes Khaleefah I'll bath you both together acikin jacuzzi."
"No way Da da taya zata ganni naked?"
"Sena gani" cewar Afreen tana yi mai gwalo.
"Khaleefah you both are still kids what's there?"
"O'o am still her big bro ni bazata ganni naked ba."
"LOL okay Lil Man we'll do it this way wear your pants then."
"Yauwa much better."
"Nima Da da baze ga min nono ba" Afreen tayi maganan harda 'yar kukanta. Dariya
sosai Al'ameen ya tsaya yi ina ma nonon bale ace baza a gani ba.
"Princess you are just 3 years old."
"Ni o'o."
"Okay Khaleefah baze gani ba toh yanzu do as I ask ku jirani cikin bathtub I'll
be right back Khaleefah banda wasa da ruwa Afreen banda neman tsokana."
"Okay Da da" suka amsa a tare suna pulling kayansu.
"I love you both."
"We love you too" daga nan ya fice yaje ya samu Zeezee zaune gaban dressing
mirror tana sanye da towel iyaka tsakiyan cinyanta. Drier ne a hannunta tana drying
gashinta da suka jik'a, tana ganin wanda ya shigo ta kawar da kanta, a nitse
shikuwa ya k'arisa gaban mirror'n a hankali ya kama hannunta ready to seize it.
"Sake min hannu" ta fad'a in a serious tone. K'in jinta yayi seda ya k'wace
drier d'in nan ta gwada tashi and da sauri ya miyar da ita. "Ka dena ta6ani bana
so."
"Am sorry kinji?" Ya fad'a a hankali tare da baza gashin nata akan bayanta ya
d'aga piece kad'an a hannunsa yana drying mata, duk anan bata ce masa komi ba.
Shiru ne kuma ya ziyarce su both har seda ya gama mata drying d'in, ribbon data
miqa hannu zata d'auka ya rigata nan ma bata ce komi ba tasan duk neman sata magana
yake, a hankali ya shiga kama mata gashin ya nannad'e yadda take yi. Yana gamawa ta
miqe zata fice hannunta ya rik'o da sauri restraining her, ko kallonsa bata yi ba
ita har yanzu bata sauk'o ba taya zasu jik'a ta haka su tsaya suna mata dariya.
Yatsan sa yasa a ha6arta tare da d'ago face nata still tak'i ta kallesa "Princess
are you still mad? Am sorry your Soldier is sorry." Ganin batada niyyan mai magana
yayi owning lips nasa ai kuwa tak'i basa had'in kai sealing lips nata tayi gagam
not letting him any access. Murmushi ya saki yasani abu d'aya zeyi mata ya kashe
mata jiki sede beyi a take ba seda ya bari ita da kanta ta fara gajiya sannan yayi
working magic nasa Zeezee batasan lokacinda tayi gasping ba, anan yayi using
opportunity'n yayi owning nata gabad'aya it was a gentle yet strong and
compassionate kiss, bayan d'an lokaci kad'an ya saketa tare da hugging nata duk
yadda takeson ignoring nasa ta kasa he is wayy hot. Hugging nasa tayi back a
hankali, hakan ba k'aramin sanya sa farin ciki yayi ba "I'm sorry kinji? The kids
wanted to play and I can't turn them down as a father I'm sorry kinji? Forgive your
soldier."
"Ya wuce."
"Kin sauk'o? You are no more mad? Or do I have to go down on my knees?"
"I won't let you do that not even for the world, after this logical and magical
kiss of yours how can I still stay mad?"
"Am glad zaki kwanta inje inyi ma su Khaleefah wanka? Suna jira na tun d'azu."
"Muje tare."
"No you are sick sleep okay I'll handle them."
"Am feeling much better muje." Hannunta ya rik'o har suka k'arisa bathroom d'in
inda suka tarar da Khaleefah da Afreen suna ta wasa abinsu, sun cike bathtub da
ruwan kumfa Afreen tana yiwa Khaleefah spike hairstyle sun tsayar da gashin kansa
duka, so takeaway da wanda yace ba za a gansa naked ba da wacce tace baza a gane
mata nono ba duk sun manta sun tu6e suna wasa.

"Wasa de wasa deh" fad'in Zeezee.


"Mammy! Da da!" Sukayi exclaiming a tare. A nitse suka k'ariso wajen kids nasu
"yeyy! Mammy will be the one to bath me" cewar Afreen.
"And Da da will be the one to bath me too." Cewar Khaleefah. Nan da nan Zeezee da
Al'ameen suka shiga wanke yaransu sunayi suna having fun har suka gama sukayi
wrapping nasu a towel Zeezee ta wuce da Afreen d'akinta tashiryata tsaf tasa mata
pajamas nata sannan ta karanta mata bed time stories. In a swift Afreen tayi bacci
bayan ta tofe ta da addu'a taja mata blanket ta rufeta tare da pecking nata a
forehead ta kashe mata wuta ta fice. Shima Al'ameen haka yayiwa Khaleefah kusan a
tare suka fito daga d'akunan. "She is fast asleep" ta sanar dashi.
"So is he."
"Muma muje mu kwanta."
"Go first Princess I'll have to take care of the kitchen sannan inyi wanka nima."
"Kabari mana gobe idan me aiki tazo muje kayi wankan."
"No don't worry hurry kije ki kwanta will join you in a bit."
"Muje and finish it up together kasan bazan iya bacci ba if your arms aren't
wrapped around me."
"Aww! Are you sure?"
"Yes Sweetheart" tare suka wuce kitchen d'in Zeezee kanma bata san daga ina zata
fara ba bin steps na Al'ameen take har suka kimtsa suka miyar da komi back to it's
rightful place sannan Zeezee ta share Al'ameen yayi mopping suka fito duk a gaje
suka nufi d'akinsu ta jira Al'ameen ya fito daga wanka suka kwanta.

***
In three days time suka wuce Abuja awaiting their flight to Washington D.C Afreen
and Khaleefah couldn't keep calm, the following day jirginsu ya tashi Afreen harda
sakin fitsari a panties dan yadda cikinta ya rud'e da jirgi ze tashi, ita kanma wai
ta fasa tafiyan a sauk'eta zata gun Granny. Flight nasu na Bauchi to Abuja ma
dalilin daya sa bata rikice musu ba was because she was fast asleep har suka isa
bata sani ba. Nan kam tayi kuka da ba don private jet na Al'ameen suke tafiyan ciki
ba da mutane sunyi musu dariya suce ga 'yar k'auye.
Safe and sound Allah ya isar dasu Washington inda suka sauk'a a
The Dupont Circle hotels and suites.

***
Life couldn't be better for this happy family, ba aikinsu a kullum banda fita
leisure points suna exploring Washington and enjoying each other's company kaman
wasa har suka shafe wata d'aya basu sani ba.
Yau bayan Zeezee ta kwantar da Khaleefah da Afreen wajajen k'arfe 10pm Al'ameen
ya shigo as always taje ta taresa suka k'ariso d'aki suna hira kaman yadda suka
saba, alokacin da Al'ameen ya shiga bayi don watsa ruwa wayan Zeezee ya shiga ruri
tana dubawa taga unknown number, without hesitation ta d'aga tare da yin sallama.
"Wa'alaikumus salam " meshi ya amsa.
"Adeel?" Ta tambaya.
"Na'am Zeezee ya kike?" Tana kallon k'ofan bayin cike da fargaba ta amsa da
"lafiya ya gida?"
"Lafiya k'alau yasu Khaleefah and..."
"Afreen" ta sanar dashi "we are all good." Mamakin ina ya samu new line nata take
seta tuna ko maybe agun Lubiee ya amsa. "Masha Allah dama na kira ne in sanar dake
k'aruwan da muka samu, Ruky ta sauk'a lafiya d'azu da yamma ta samu 'yan biyu duka
mata."
"Wow! Masha Allah, kai na muku murna Allah ya raya ya d'ayyiba itama zan kira ta
nayi mata barka amman ka gaisheta kafin nan bana 9ja but idan na dawo zanzo yi mata
barka."
"Toh Zeezee we are grateful ki gaishe da Maj-Gen."
"Ze ji in shaa Allah Daddy'n twins." Yana murmushi sosai yace, "yauwa take
care." Ta ajiye wayan bada jimawa ba Al'ameen ya fito all wet yana sanye da towel a
waist nasa, packs and muscles sun bayyano mehn! so wow!
"Unless kanason tayar min da vibes you'll come over here Sweetheart." Murmushi
ya saki mata daga nesan tare da kashe mata ido "wai da gan-gan kake hakan ko
Sweetheart kasan bana iya ignoring wannan sexy body'n naka."
"Then don't look" ya fad'a mockingly.
"Haka ma zaka ce?" Itama kayan nata ta tu6'e ta rage skirt da bra zallah.
"Oh come on ki miyar please nayi wanka yanzu ban son sake yin wani." Banza da shi
tayi tamkar bada ita yake magana ba seda taga ya soma takowa inda take sannan ta
d'aga kai ka "kuma wallahi nan gani nan bari."
"Haba Princess" yayi maganan finally tare da zama a gefenta yana neman ta6ata.
"Uhn-uhn fa don't touch me."
"Toh Yi hak'uri am here kince nazo nazo toh."
"Banaso go back from where you came from." Pinning nata yayi a kan gadon tare da
rufe kansu da bargo.****

_An hour later..._


Kanta na akan chest nasa tana shafa kan packs nasa tace, "kaga ina son sanar da
kai abu ma ka mantar dani." Shima wasa da gashin kanta yake yace, "ni d'in kenan am
too hot har nake iya saki forgetting abu." Bugi ta kai masa a hankali "ai kaine ka
kasa ignoring d'ina saboda am too hot."
"Ni de."
"Whatever naji am hot accept it or not."
"Princess who said you are not hot? Of course you are just that I am hotter."
"D'agani nama fasa kwanciya anan zanje na samu su Afreen a parlour." Da sauri ya
jata baya "you know you are the hottest right? Thats why I couldn't resist you, you
always turn me up even when am not in the mood." Dad'i sosai taji ta koma ta kwanta
"I love you."
"I love you more Princess."
"Yauwa shiganka bayi Adeel ya kirani."
"Ohh really?" Ya fad'a ba yabo ba fallasa.
"Yes matar sa ta haihu sun samu a set of twins duka mata."
"Masha Allah, Allah ya raya ya d'ayyiba idan Allah ya mayar damu 9ja se muyi musu
barka."
"Really Sweetheart?"
"Yes Princess ko bakiya son inje?"
"Who am I to say so? Daman inaso muje tare amman am afraid ban san ya zan fara
fad'a maka ba."
"Oh come on Princess banason inji kina cewa kina tsoron sanar dani wani abin am
here for you always."
"And I appreciate that thanks okay?"
"Tashi muyi wanka."
"Ni se Asubah zanyi bacci nakeji."
"Alright mu bari se Asuban Toh goodnight Princess."
"Dreams about me Sweetheart." Pecking forehead nata yayi, "I'll" ahaka har bacci
yayi taking over control nasu.

*MIEMIEBEE. team #YGC!??*


ZAIMEEN flames??????
Beeenovels.blogspot.com ??

?????? ??????
??❣??
❣❣
•°•★•°• •°•★•°•
°• •° °• •°
°•° °•°
*‘YAR GATA CE!*????
•°•★•°•
°• •°
°•°
*_written by miemiebee??_*

*March, 2017*
8⃣5⃣

_Last chappy in dedication to each and every reader❤❤_

In 3 days more return flight nasu to 9ja ya tashi. Afreen harda kuka ita wai
bazata koma 9ja ba, Al'ameen kansa yaso su dad'a prolonging zaman nasu achan amman
kuma zasuyi resuming school soon enough.
Wannan karan Afreen bata tsula fitsari ba amman de tayi kuka kam. Safe and
sound Allah ya dawo dasu a hankali suka sake settling. 2 days da dawowansu suka
shirya dukansu as a family suka fita unguwa gidan Adeel. Zeezee na shiga gidan
events of maltreatment da Adeel yayi mata ya soma dancing akanta da sauri ta kawar
da tunanin suka k'arisa ciki. Gidan se k'amshin turaren wuta yake, seda mutane
kad'an-kad'an da suka zo yin barka. A parlour suka zauna Afreen se neman yin 6arna
take amman Zeezee ta rik'eta gagam. In some few minutes Ruky ta fito rik'e da
d'ayan baby'n haka Adeel ma. Amsan na hanun Ruky tayi Adeel kuwa ya miqa wa
Al'ameen na gunsa. Afreen da Khaleefah wane su cinye babies d'in they couldn't keep
calm. Gaisawa sukayi cike da mutunci sannan su Al'ameen sukayi congratulating nasu.
"Mammy are the babies ours?" Afreen ta tambaya tana neman cirewa baby'n dake
hannun Zeezee hula.
"No na Uncle da Aunty ne."
"Mu ina namu?"
"Suna nan zuwa in shaa Allah Princess."
"No I want them now, we are going home with them right Khaleefah?"
"Namu ne da zamu tafi dasu?" Yace da ita tare da hissing. Wane Al'ameen yasan
_f*ck you_ Afreen zata ce yayi sauri yayi covering lips nata " don't say that
Princess if you do baza muje kasuwa mu siyo miki babies ba."
"Toh nayi shilu zaka saya min?"
"Yes Sweetheart."
"Sure Da da?"
"Absolutely." Se anan tad'an ji sanyi.
"Toh zamu tafi Ruky, se kuma ranan suna yara masha Allah kamanninsu hak ba kuma
marabansu da Adeel."
"Haka Khaleefah ma ai ba marabansa da Da danshi har ma Afreen even though ita da
akwai jinin ki sosai a jikinta." Cewar Ruky tana wasa da bakin mayafinta.
"Ai next idan na tashi haihuwa me kamanni na zan haifo haka kawai muta haifan
masu kamanninsu." Dariya dukansu suka sa.
"We'll get going" cewar Al'ameen yana k'ok'arin mik'ewa.
"Har ka gaji da rik'e matar taka kenan Maj-Gen" fad'in Adeel. Bewildering Zeezee
da Al'ameen suka tsaya kallon Adeel.
"Sorry?" Apologized Al'ameen.
"Ban fad'a muku ba ko? Na hanun kannan de takwaran matarka ce Zainab na hannun
Zeezee kuma takwaran Ruky Ruqayya."
"Adeel are you serious?" Zeezee ta tambaya sounding delighted.
"Yes Zeezee."
"Kai ban yarda ba, haka wai Ruky?"
"Gashi kuwa ya fad'a miki."
"Kai ban san da wani bakin zan muku godiya ba wallahi, so am this special to
you, nagode sosai Allah ya raya ya d'ayyiba nida Ya Al'ameen are so grateful Allah
yabar zumunci."
"Ameen" duka suka amsa.
"Mungode Adeel Allah yabar zumunci, ba zancen tafiya ai bari na koma in zauna
tunda me sunan Princess d'na aka sa." Dariya duka sa saki "Kai gaskia you guys took
me by suprise yanzu har kumin takwara bazaku sanar dani ba in taho da akwati naba?
Khaleefah kaga nikam nayi maka kamu."
Baki ya zumburo lallai ma Mammy ta raina shi dayawa baby'n take expecting nasa ya
aura?
"Kayi shiru ko bakaso ne? Idan ka bari na sake haifan na miji fa mashi zan
baiwa."
"Eh ki bashi ni tamin baby dayawa." Habaa wani dariyan suka sake sawa. "Ya
Al'ameen bani me suna na kaga" da wasa da wasa har suka d'ibe kusan awa basu sani
ba tsabagen yadda hira tayi dad'i. Yaran ba a iya banbance su ko Ruky bata soma iya
banbance suba da numbering da tayi musu a tafin k'afa take gane su. Zeezee de dad'i
kashe ta takwaran ta har biyu yanzu.

Sun zo tafiya Afreen ta 6arke da rigima ita wallahi se an basu baby d'aya ba
yadda Al'ameen beyi ba don ganar da ita fa baby'n bawai an haifa musu bane nasu
Adeel ne amman tak'i jinsa se kuka take da k'yar Zeezee ta d'agata suka fice, nan
ma da suka koma gida basu tsira ba, kuka tayita musu har seda bacci ya kwasheta.
Al'ameen na miqe akan gado Zeezee kuwa tana tsifan kai a k'asa a gefen sa Al'ameen
ya kalleta yace;
"Toh Princess seki san nayi fa Afreen nason siblings twins kuma."
"Toh ai daga kaine, shoot me sharply kaga in ban sambad'o twins d'in ba."
"LOL haka ne?"
"Eh mana."
"Yafa kamata ace akwai ajiya na achan Princess, Afreen is 3 years 2 months old
amman ko alaman ciki babu tattare dake."
"Karka damu Sweetheart soon enough I'll be carrying your baby again."
"I can't wait to be a Daddy for the third time." Murmushi kad'ai ta sakar masa
tana me cigaba da tsifan ta. "In tayaki?"
"Ai ka gaji Sweetheart d'azu fa kayi wa Afreen."
"When it comes to my family bana gajiya hauro nan kizo mu tsefe miki."
"Are you sure?"
"Oh come on Princess." Cike da jin dad'i ta miqe ta fad'a jikinsa tare da kissing
nasa lightly "I love you my soldier." Wink ya mata sannan ya kwantar da kanta akan
cinyansa ya shiga tsefe mata har bacci ya isketa a wajen.

****
Life moved on, a sunan 'yan biyun Ruky kaya sosai Zeezee ta kai mata barin ma na
yara, Ruky da Adeel se godiya tun daga rana me kaman na ranan suka k'ulla
everlasting zumunci basu ta6ayin 3 weeks basu ziyarci gidajen juna ba da wasa da
wasa Ruky da Zeezee suka zame tight friends haka Adeel da Al'ameen ma tamkar yaya
da k'ani haka suka zame, komi idan Adeel zeyi seya nemi shawara gun Al'ameen.
Afreen ko sede ranan da basu je gidansu Ruky ba kokuwa Ruky bata zo gidan su ba
seta ta da bori ita a bata babies d'in duka bama guda d'aya ba duka take so yanzu.

•*•*•*•*•* 4 months later...*•*•*•*•*•


For a week or so kenan Zeezee ke feeling weakness da kuma nausea hakan yasa yau
da kanta tayi dropping kids nata a school daga chan ta wuce asibiti inda akayi mata
gwaji bayan results ya fito Dr tayi congratulating nata game da k'aruwan data samu.
Ciki ne d'auke da ita. Zeezee can't wait ta sanar da Al'ameen nata she is pregnant
again. Scanning aka yo mata inda aka gano cikin ma na 'yan biyu ne ba d'aya ba and
they are one month old. Dad'i akan dad'i kenan ga ciki gashi kuma na 'yan biyu?
What else can she ask for? Printing out photo scan d'in tayi ta koma gida sounding
excited and thrilled. Mama ta soma kira ta sanar da ita sannan Lubiee se Ruky Mama
after asking them to promise her bazasu sanar da kowa ba batason Al'ameen yaji
labarin a waje tafison ta fad'a mai da kanta. Bata ta6a nunawa Al'ameen batada
lafiya ba bale wai tace mishi taje asibiti. A ranan da ze dawo tayi aiki sosai ta
had'a kan dining ta watsa musu roses kan gado sannan ita da yaranta sukayi wanka
tsaf suka shirya in white dukansu. Not long enough Al'ameen ya iso nan su Afreen
suka je suka tarosa, suna shigowa ya sauk'e yaran yayi hugging matarshi rabonsu 3
months kenan. Bayi ta rakasa ya watsa ruwa sannan suka fito suka ci abinci bayan
sun k'are yaran duk suka nufi d'akunan su dan duba tsaraban da Da da ya kawo musu.
Anan Zeezee da Soldier'n ta suka samu kansu suma. "Muje d'aki Sweetheart I have a
suprise for you."
"My Princess bata gajiya da suprising d'ina kullum and guess what? I love your
suprises."
"Tashi muje toh" d'akin suka nufa inda ta wuce wardrobe ta ciro photos d'in ta
miqa mai. Ya kalla yafi sau goma amman ya kasa gane mene abin saboda gudan jini
suke har yanzu basu cika halitta ba, ba kai balle k'afa da har zesa ya gane mutane
ne.
"Princess what is this?" Ya tambaya at last.
"Me kake gani a wajen?"
"Dots guda biyu." Dariya tasa sosai da yace dots guda biyu.
"LOL toh dots guda biyun nan baby twins naka ne."
"Excuse me?" Ya fad'a unbelievably.
"Yes am one month pregnant and it's a twins gasu nan ga d'aya ga d'aya." Ta nuna
mishi. Watsi da photos d'in yayi ya d'agata sama yana juyi da ita a yayinda take
faman dariya se chan ya sauk'eta yayi mata brushing light kiss on the lips.
"Princess are you serious?"
"Yes Sweetheart just a week back nima nayi confirming I can't tell you how happy
I am."
"Not as I am, I can't wait to finally meet our twins my carbon copies of course."
"Whick kind you carbon copy? In shaa Allah dani zasuyi kama nayi imani da hakan."
"LOL zamu ga toh, Princess thank you ashe de ni d'innan sharp shooter ne."
"Come on nide na iya maintaining abinda ka bani."
"Owww haka ne? are the kids aware?"
"Nop kai nakeso ka sanar dasu."
"Yau akwai shopping ki shirya yanzun zamu fita."
"Kai Sweetheart I love you, I love you, very very much" kisses ta shiga showering
masa a face har seda ta gaji "and I love you more and more and more and more...
till infinity."
"What do you think our twins sex are Sweetheart?"
"Either of thesame sex they are or different sex I just love our kids Princess I
can't wait to shower them with love, care and compassion."
"I know you will Sweetheart you are such a great Dad, you are my inspiration and
role model I have no one to look upto except for you."
"Allah ya inganta ya sauk'e ki lafiya Princess you are the best Mother every
child would want to have, Allah ya cigaba da baki ikon tarbiyyar mana da yaran mu
ya kuma biyaki da gidan Al~jannah, ya cigaba da kai rahama kabarin iyayenmu ameen.
My love for you shall never die may we live long to witness our grandchildren's
marriages." Tana hawaye tana dariya duk don murna da farin ciki ta amsa da "ameen
Sweetheart I love you morethan I can ever let you know." Face nata yayi cupping da
both hands nasa tare da kissing away tears natan, "cry nomore Princess today is one
of the best day of our lives kinsan wani abu?" Da sauri ta kad'a kai "twins d'innan
ba a 9ja za'a haife su ba, a favorite country naki zamuje ki sambad'o mana su
achan." Hannayenta ta zagaye a wuyansa "really Sweetheart? Zamu sake komawa
Washington?" Ta tambaya sounding thrilled.
"Over and over and over again har se randa kikace min Sweetheart Washington ya
fita miki a rai."
"Awww I love you" daga fad'in haka tayi owning lips nasa kissing him with all
that she got.

_Some minutes afterwards..._


"Kids where are you?" Shouted Al'ameen "ku fito ko nida Mammy mu tafi?" Daga
cikin d'akin Afreen tayi shouting "nooo!!!!" Da gudu ita da Khaleefah suka fito
suka tsaya gab a gaban Zeezee da Al'ameen da sukayi inter wining fingers nasu.
"Da da, Mammy where are we going?" Khaleefah yayi tambayan.
"Shopping lil Man."
"Yeyyy! I love shopping" cewar Afreen "what are we going to shop?"
"Babies wear, items, and everything."
"Wow! But we don't have any baby Da da."
"We do Princess right here " ya dafe cikin Zeezee. "Mammy is pregnant akwai twins
namu acikin Mammy twins irin na Aunty Ruky guda biyu kyawawa kaman ki."
"Really Da da?" ta fad'a sounding delighted tana daka tsalle "kunje kun siyo a
market kuma?"
"Yes Princess ba kika ce kina so ba?"
"Yes I do."
"Muma mun siyo nan da lokaci kad'an Mammy zata haifo mana su."
"Yeyyyy!!!! Nima zan zama big sister'n su."
"Sure why not?"
"Da da are you serious that Mammy is pregnant?" Asked Khaleefah.
"Yes lil man."
"Mammy are you?"
"I am My lil Soldier you are soon going to be a big brother again you and
Princess."
"Yeyyy!!!" Da gudu ya fad'a jikinta ta d'aga shi sama Afreen ma ta fad'a jikin
Da da shima ya d'agata sama. "Are we ready to shop for our twinsets?"
"Yesss we are!" suka fad'a at the peak of their voices suna murna. Fitowa duka
sukayi Khaleefah da Afreen suka ruga a guje cikin mota suka wuce third sit inda
suka saba zama, nan Al'ameen ya rufo k'ofa tare da rik'o hannun Princess nasa "I
love you my price possession, my one and only Princess."
"I love you more my heart race and beat I am yours forever." Owning lips nata
yayi giving her the kiss of her life sun ma mance a waje suke. Dan gulma tun daga
mota Afreen ta hangesu, da sauri ta ta6a Khaleefah.
"Khaleefah! Khaleefah! look at what Da da and Mammy are doing." Rufe mata ido
yake sonyi kaman yadda ya saba aiko ta k'wace kanta da iya k'arfin muryanta ta
dannawa lovebirds kira; "Mammy!!! Da da!!!"
Murmushi both parents suka saki sannan suka sake juna a hankali, smiling to each
other suka miyar da kallonsu kan Afreen dake musu waving hand ta window tana
murmushi. "I love you" tayi shouting.
"We love you too our Princess" suka fad'a a tare "and you too our last standing
Soldier" tare da blowing musu kisses "and my twinsets." Al'ameen yayi adding yana
mata murmushi na sosai from the bottom of his heart. ❤❤❤❤

*•*•*••*••*•*•**•*•*••*•*•*•*•*•*•*•*•*
*TAMMAT BI HAMDULILLAH!!!*
*•*••*•*•*•*••*••*•*••*•••*•*••*•*•*•*•*

ANAN NI MIEMIEBEE KE AJIYE ALK'ALAMINA NI MA. DA FATAN NA ISAR DA SAQON DA NASO


ISARWA GA DUKKAN WANDA YA/TA KARANTA WANNAN LABARI, INDA NAYI KUSKURE KO NA FAD'I
BA DAI-DAI BA ALLAH YA YAFE MIN, AMEEN.

Littafafan marubuciya;
1.) NA YARDA DA KE
2.) NA FI TSANAN KA
3.) HEEDAYAH
4.) KAMAR KUMBO KAMAR KORENSA...
5.) BEHIND OUR LOVE
6.) TANA TARE DA NI...
7.) 'YAR GATA CE!

????????????
*ACKNOWLEDGEMENT;*
_FIRST OF ALL MIEMIEBEE WOULD LIKE TO THANK *YOU* FOR READING A PIECE OF HER
WRITE UP. A BIG THANK YOU TO EACH AND EVERY OF MY SUPPORTER/FAN THAT MADE IT
THROUGH OUT THIS JOURNEY OF #YGC?? IT WAS WITH Y'all SUPPORTS, LOVE AND CARE THAT
MADE ME PASSED EVEN THROUGH THE DARKEST OF DAYS AND ALL THE CHALLENGES I
ENCOUNTERED DURING #YGC AND FOR THAT MIEMIEBEE IS SAYING HATS OFF TO Y'all. I
REMAIN LOYAL.

A big shoutout to these classical and unique group members of;


MIEMIEBEE NOVELS group 1&2.
MIEMIEBEE FANS club 1,2 & 3.
YAR GATA CE FANS club 1 & 2
MY BLOG READERS and to each and any other group that loved and cared for me and
YGC. MIEMIEBEE na alfahari daku from the bottom of her heart.❤

MAY WE ALL MEET IN ALJANNATUL FIRSAUS YEAH AND EVEN THE HATERS TOO??.

*Don't forget to follow me on wattpad @miemiebee* OR stay tuned on my mobile


blog beeenovels.blogspot.com

WITH THIS, AM SAYING, *MA'ASSALAMA* CANT WAIT TO SEE Y'ALL IN MY UPCOMING


ENGLISH NOVEL _THE BAD BOY GAME #TBBG_ TAG AND SAVE IT, BE ON WATTPAD AND TIGHT
YOUR SEATBELTS, THERE WILL BE CASTS AND EVEN SHORT VIDEOS THERE SO DON'T MISS OUT.
ROCKING WATTPAD LIKE WE BEEN SENT FOR IT! #TBBG WILL HIT YOUR SCREEN BUT NOT TOO
SOON.??*

#OneLove from Miemiebee??


Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira)

You might also like