Professional Documents
Culture Documents
Hanyoyin Daidaita Sahu. - .!!!
Hanyoyin Daidaita Sahu. - .!!!
As salaamu alaikum!!!
Malam Bala,
Gabatarwa
A Daidaita Sahu
Daidaita Sahu a Ilmance
Daidaita Sahu a Aikace
Rufewa
GABATARWA:
Shekaru kusan biyu da suka gabata naje Kano don ziyara kamar yadda
na saba. Kafin barin Abuja limamin unguwarmu ya bani wasu kudade in
sayo wani littafi da aka sa a masallaci don karantarwa cikin wasu ranaku.
Kasancewan babu wadatuwarsa yasa aka bani sautun in naje in sayo
kamar kwafi goma. Na samu sauki a kan yadda aka bani, a lokacin da
na samu kaina a shagon masu littafai kenan na Kasuwar Kurmi. Wanda na
tambaya da farko ya ce mani bai da littafin, sai dai in zan yi hakuri zai
nemo mani. Na ce ai ba matsala, muddin za a samu ina so kuma zan jira.
A karon farko ya shigo da guda shida don nuna mani ko ina son irin bugun.
Nan take na amince cewa ina so kuma ma ya karo makamantansu. Ya
ajiyesu ya koma.
A wani ziyara har wa yau da na kai Kano, na samu kaina a Kofar Na’isa,
bayan sallar Isha’I, yamma ta rufo bargonta a kan al’umma. Na tsallaka
bangaren kwanan Gandun Albasa kenan sai kawai naji wani a bayana
yana cewa: “. . . kiyayeka Ustaaz. . . Allah Ya sa kafi haka Ustaaz. . .!!!” na
waigo ban gane shi ba don ban san shi ba. Yana sanye da suwaitar bacci,
fara, da wando fari a zanzare, da hula hana sallah. Nace: “yauwa barka
ka dai. Yaya aiki?” ya amsa. Sai kawai na shantake da tsare mota don
samun wacce zata kai ni Hotoro, masaukina a wancan lokaci. Can sai naji
yace: “ustaaz”, na waigo nace: “barka dai, wani abu ne?” sai yace: “eh.
. .wallahi arzikin Naira goma kadai nake son kai mini.” Nan take na ciro
gudan Naira dari na bashi nace ya nemo canji don in bashi abinda yake
so. Tabbas na san akwai masu sayar da kayayyaki a bakin titi, nan
bayanmu, don haka ko juyawa in kalleshi ban yi ba. Sai da na tabbata
bana jin mostinsa a bayana, sai na waiga. Kwamfa! Ya kule kwanan
Gwandun Albasa, ko ganinsa ba a yi. Daga nan na bi bayansa, kuma ina
shan kwanan sai na hangoshi yana dawowa, a zatonsa na gaji da tsayuwa
na wuce, don yaci bulus. Yana hangoni shima sai ya shashance: “ah. .
ustaaz wallahi canji naje nema kuma ban samo ba. . .kai don Allah zan
samu canji nan wajenka?” yace ma wani dan kamasho. A takaice dai sai
hamsin biyu aka samu, na karbi daya na bar shi da guda dayan. Har na
dawo Abuja hankalina a tashe yake na abinda ya faru, don wani abu
daban na hango. Allah Ya sawwake.
A DAIDAITA SAHU:
Duk wata gwamnati da aka samar da ita a doron kasa wajibi ne ta lura
kuma ta kare ma al’umma tunaninta, kada ya gurbata. Don wannan
bangare shine abu mafi muhimmanci ga al’ummar gaba daya. Har wa
yau shine zai ba al’umma yi ma gwamnati adalci a kan tayi mai kyau ko
bata yi ba. Amma idan ya zama tunanin al’umma a gurbace yake, to ta
hanyar son zuciya, kowa zai iya fadin abinda ya ga dama a lokacin da ya
ga dama, a kuma inda ya ga dama, ba tare da ya kiyaye da mai zai je
ya kawo ba na sakamakon maganganu ko aikinsa. Da wannan na ga ya
zama wajibi ga wannan hukuma ta tsara yadda gwamnati zata canza ma
al’umma tunaninta dangane da:
Wassalaamu alaikum!!!