Yan Arabic CMPLT

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 269

🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡

🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 YAN ARABIC🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*DEDICATE*
_to_ _All_ _Arabic_ / _Islamic_ _students_
󨐽񆠽񆠽񆠽񆠽񆠽񆠽񆠊
Ina k'ara godiya ga Allah subhanahu wataa'la daya k'ara bani damar fara rubuta
wannan littafi nawa na ya'n Arabic ina fatan dikkan Abinda yake dai-dai Allah ya
bani ikon rubutawa amin👏.

📚📚📚📚📚📚📚📚📚
Ina d'aliban Islamic / Arabic midium wannan littafi sadaukarwa ne gareku kuyi
yanda kuke so dashi Allah yasa ku kasance cikin farin ciki aduk inda kuke a fad'in
duniya.
📚📚📚📚📚📚📚📚📚

ZAMANI WRITERS ASSOCIATION


(we are here to educate,motivite and entertain our reader's)
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

0⃣0⃣1⃣ 0⃣0⃣1⃣

Cin cirundan d'alibai ne nake hanga a can nesa dani wanda suka hau layi- layi amma
yawansu baya bada damar a gane a layi suke,dik girma irin na filin dake bayan
I.C .T na wannan makaranta d'aliban k'ok'arin cikeshi sukeyi, kasance war d'alibai
ne mabanbanta courses wasu hira suke wasu kuwa gajiya tasa ko hiranma basayi gasu
dai tsaye suna jiran layi yazo Kansu ko wanne hannunsa rik'e da credentials d'insa
kana ganunsu dai kasan masu neman Admission ne.
Yawancin matan a zazzaune suke wasu a tsugunne .

Can gefan titi motar tai parking ya juyo ya kalleta da D'an mirmishi a kan
fuskansa yace" To Nahnah Khadeejah ga skul d'inku kuma wad'an nan tarin jamaa'r da
kike gani dikka masu neman Admission ne kamar ki don haka yanzu cikinsu zaki shiga
saiki Tambayi ya'n Department d'inku kema kibi layi"

Dafe baki tai cike da tsoro tace "yanzu yaya dik wannan tarin muta nan kar b'ar
Admission letter zasuyi to ta yaya zan samu karb'a ayau"?

Mir mishi ya k'ara yi yace" To ai dik ba course d'aya kuke ba kowa department
d'insa daban don haka in kin je zaki ga kowa data windows d'in da zaki ga masu
basu"

"Tom yaya saina dawo" ta bud'e murfin motar tana fita,


Kud'i ya d'auko 2k ya mik'o mata"ungo wannan ki rik'e a hannunki don neman wani
kud'in ko in kin fara jin yunwa don zaku iya kai yamma"

Karb'a tai tana fad'in "Tom yaya na gode"

A hankali ta k'ara so wajan k'irjinta nata dukan uku uku don ita jama ar yawansu
yana bata tsoro ,gefan dataga matan suna zaune ta k'arasa da sallama abakinta "
‫ "السالم عليكم‬wasu daga cikinsu sun amsa mata yayin da wasu suke bidirin gabansu wasu
kuma binta sukai da kallo irin kallon nan da mata kewa y'ar uwarsu mace musamman
idan tai babban wanka,😜

Gyaran murya tai cikin sanyin miryanta tace"Don Allah ina Tambaya ne"
"OK Allah yasa mun sani"
"Don Allah *YA'N* *ARABIC* nake nema"
"To gaskiya sai dai ki matsa can gaba kad'an kiyi Tambaya nan dik babu su"
Gaba ta k'ara kad'an ta k'ara Tambaya nan wata dake zaune agefe tace "gamu nan "
K'ara sawa tai kusa da ita ta zauna tare da mik'a mata hannu sukai musabaha tace"
nima *YA'R* *ARABIC*ce zan amshi Admission letter ne"
Kallonta tai sosai tace"Ok kice y'ar uwace kinga duk way'an nan ma department
d'inmu d'aya" ta fad'a tana nuna sauran y'an Matan dake gefe,dik mik'a musu hannu
tai sukai musabaha"
Nan suka ci gaba da zama suna jiran a fara raba musu letter n.

Khadeeja Alk'adi yusuf haifaffiyar garin sakkoto ce y'a ta goma sha bakwai
acikin gidansu kuma ita ce autarsu,
Mahaifinsu Alk'adi Yusuf tsohon Alkali ne a babbar kotun Shari ar musulunci ta
garin sakkoto Dattijo ne me cikar kamala da addini yana da mata biyu da ya'ya' goma
sha bakwai maza goma sha biyu mata biyar,
Babban D'ansa Namiji ne Yaya babba kenan sai na biyunma na miji ne yaya Sani
sai ta uku mace Aunty sai ta hudun Aunty Amina ta biyar ma mace ce Aunty jamila
bayan Aunty jamila saida aka haifi maza hud'u sannan aka k'ara haifar mace agidan
wato juwairiyya daga nan aka k'ara maza shida sannan aka haifi auta Wato Nahnah
khadeejah, y'ar gata ce sosai agidansu don dikkan yayyanta mata an musu aure
mazanma duk sunyi aure mutum hud'u ne kawai basuyi ba wato yaya nura , yaya
usman ,yaya kabir da yaya sadiq , duk suna karatu basu kammala ba gidansu Nahnah
khadijah gida ne na y'an boko kuma suna da ilmin addini sosai mahaifinsu ya yabar
aiki tun bayan haihuwar Nahnah khadeejah ba dad'ewa kasan cewar ya tsufa sosai
yanzu yana zaune ne agida cikin kulawar y'ayansa da jikoki,
Zuri arsu suna da yawa sosai don mahaifinsu ma agidansu su ashirin ne don haka
su d'un y'an dangi ne sosai in suna taro su kad'ai ma suna cika gida ko busuyi
gayya ba.

Yaya Haroon d'a na tara agidansu mutum ne me barkwanci da yawan wasa yana da
tsana nin son y'an uwansa me zimunci ne matuk'a bai iya siwa kansa abu ba tare daya
saiwa wani daga cikin y'an uwansa ba, yana son Nahnah matuk'a dikkan hidimarta
akansa yake ya dauke komai haka Nahnah kulum bakinta yana kiran Yaya haroon sun
shak'u sun saba dikda kowa na gidan sonta yake kasancewarta k'arama kuma mace
acikinsu, wata shahararriyar makaranta tahfeez/ Arabic primary and secondary skl
dake garin sakkoto ita Yaya Haroon yasa Nahnah ai kuwa kafin ta kammala primary
ta iya larabci sosai ta yi hadda da yawa ,bayan ta kammala primary ta zarce jenior
acikin makarantar, a lokacin yaya Haroon ya sami canjin aiki k'ark'ashin federal a
kano nan da nan ya had'a kayansa yai shirin tahowa kano kuka gun Nahnah kamar ranta
zai fita shi kansa sai da yai kwallar rabuwa da Nahnah ya d'au hanyar kano.

Haka rayuwa taci gaba da tafiya koda yaushe in Yaya Haroon yazo Hutu in zai
koma sai yayi fama da kukan Nahnah, yaya Haroon yai dacan zuwa kano don ya sami
matar aure har sun dai daita Kansu iyayensa sunzo daga sakkoto ansa ranar aure
anyi komai.

Taku ce
Layuza kabir Adam
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸YA'N ARABIC🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡

NA
LAYUZA KABIR ADAM

DEDICATED
TO ALL ARABIC/ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*💻ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣0⃣2⃣ 0⃣0⃣2⃣

Tunda NahNah taji yaya Haroon zaiyi aure ta shiga murna tana fad'in"shike nan zan
koma kano gidan Yaya tunda aure zaiyi" kowa ta fad'awa sai dai yayi dariya don sun
San Baffa da son y'ay'a bazai iya bada Khadeejahnsa ba yanda kullum zansan sa na
kanta kullum nasihar sa ga y'ay'ansa su rik'e mai Nahnah koda bayan ransa kada su
bari tai kukan rashin uba,

Bayan wata hud'u akai bikin Haroon ya


Tare da amaryarsa a garin Kano cikin unguwar hotoro agidansa daya siya k'aton
gaske,

Bayan bikinsu da wata guda ya kawo amaryarsa sakkoto donta gaisa da danginsa
suga juna,
Murna wajan Nahnah ba'a magana taga yaya da matarsa aikuwa Hafsa ma tanata
murna yau taga Nahnah kullum bakin Haroon naga Nahnah, kwanansu Biyar sukai shirin
tafiya ai kuwa Nahnah tace ina ai k'afarta k'afar yayanta tun suna zaton abin wasa
ne har abin ya fara basu mamaki,k'am ta rik'eshi tana kuka harda shishshik'a yaya
Usman uban y'an masifa ya fuzgota yana fad'in " Dalla malama rufe mana baki hauka
mukeyi za a barki ki tafi kano"

K'ara take cikin tsananin kuka tace" wayyo Allah na yaya Haroon don Allah karka
tafi ka barni inka barni mutuwa zanyi wayyo yaya nah"

Baffa ne ya dogaro sandarsa ya fito daga sashinsha yana fad'in "wai auta wane
irin kuka ne kikeyi haka sai kace wanda aka cirewa ido ko kukan Harunanne"?
Yana k'arasa fitowa yaga yanda Nahnah ke turje turje tana ihu, rik'o hannunta
yai cikin sigar rarrashi yace"yi shiru auta ta kinji rabu dasu anayin Hutu zansa
Bashir ya kaiki"
"Ni banso Banson makarantar ni yaya nah zanbi kano"
Jim Baffa yai ya kalli Haroon yaga yanda shima duk idonsa yai jawur harga Allah
badan yasan Baffa bazai tab'a iya bashi Nahnah ba daya rok'i alfarmar tafiya da
ita,
Muryar Baffa ce ta katse mai tunaninsa"Haruna zo ina son magana dakai kaida
matarka"
Ciki suka koma bangaran Baffan yayin da yaya usman ya ciccib'i Nahnah zuwa
cikin d'aki ya rufeta tanata dukan k'ofar tana ihu,
Bayan sun zauna Baffa yai gyaran murya ya fara magana"Haruna ka sani ni bana
bada aran d'ana bare inyi kyautarsa tun tuni y'an uwanka maza da mata na nesa da
kusa sukemin nacin d'aukar khadeejah amma bantab'a amsawa wani ba akan idonka ko
kwana uku Khadeejah bata tab'ayi gidan wani ba cikinku amma yau na d'auki amanar
Khadeejah na dank'a muku kaida matarka koda bayan raina Khadeejah ta kuce Ku
rik'emin ita amana Ku zama iyayenta Ku share hawayenta kunji"
Tsananin farin ciki ne yasa Haroon kasa magana illa zuwa da yai ya rik'e
k'afafun Mahaifinnasa yana d'ora kansa a cinyoyinsa,
Hafsa cikin jin kunya tace"Mun gode Baffa Allah ya bamu ikon rik'e amanar daka
bamu"
"Ameen Hafsa Allah yai muku albarka" nan ya taro dikkan jama'ar gidan ya shaida
musu kyautar da yaiwa yaya Haroon aikuwa kowa ya cika da mamaki yanda akasan
k'aunar dake tsakaninsa da Nahnah, nan dai kowa yai musu fatan alkairi, Nahnah ko
daketa kuka a d'aki harta gaji tai bacci bata San meke faruwa ba,dole Yaya Haroon
ya d'aga tafiyansu sai nan da kwana biyu.

Makarantar su Yaje ya nema mata transfer don lokacin j.s.s two take,
Bayan ta farka a bacci ake shaida mata Tare zasu tafi da Yaya Haroon Baffa ya bar
mai ita ai kuwa kamar tayi me don murna, nan da nan ta shiga shirya kayanta.

Kwana d'aya Transfer d'in ta fito don haka washe gari suka d'au hanyar kano,
shike nan Nahnah khadeejah ta zama ya'r kano,

Tunda suka dawo yaya Haroon ya shiga nema mata makarantar da zata ci gaba
wadda tai dai-dai da irin karatunta, Tambaya yake akan wace makaranta ce ta Arabic
wadda take da karatu da tsari nan wani ya bashi shawara akan ya kaita "TAHIR GIRL'S
ISLAMIC/ARABIC SENIOR SECONDARY SCHOOL GYAD'I-GYAD'I KANO"

Ai kuwa nan da nan ya nema mata gurbin karatu a Tahir kasancewar lokacin za'a
fara jarabawar shiga babbar secondary wato senior nan yai mata registration itama
ta zana.

Zaman Nahnah a
gidan Yaya Haroon ba k'aramin dad'i yake w Hafsa ba don Nahnah yarinyar kirki ce
ga son aiki bata da ganda ko kad'an,kullum tana waya da y'an gidansu a wayan
yayanta don haka bata da kewansu.

Ahaka Nahnah Khadeejah ta gama secondary skul d'inta cike da tarin nasarori
kasancewarta yarinya zak'akura ita ta rik'e head students har tai Candy duk wani
quiz da za'a fita a skul d'in ita ke jagoranta.

Satin Nahnah biyu da candy akayo musu waya jikin Baffansu yai tsanani an bashi
gado a asibiti ba shiri suka d'au hanyan sokoto,
Tunda suka sauka garin suka ga yanayin jikin nasa hankalinsu ya tashi matuk'a
don baima San Wanda ke kansa ba ko kad'an, kwanansu biyu agarin Allah ya karb'i ran
Baffah Sunyi kuka matuk'a na rashin gwarzon uba musammam Nahnah da take jin tafi
dikkan y'an uwan nata k'aunarsa, to koma dai yaya ne ya tafi ya barsu sai fatan
dacewa.

Saida sukai sati biyu a sokoto suka dawo bayan an raba musu gadonsu kamar yanda
yabar wasiyya kar suja lokaci wajan raba masa gado wannan shine abinda musulunci ya
bada dama.
Shirye shiryen shiga makarantar gaba da secondary Yaya Haroon yake ta mata
kamar yanda ta zab'a tana son yin (SA'ADATU RIMI COLLEGE OF EDUCATION KANO) tun
tana secondary tai alk'awarin yin wannan makarantar la'akari datai da duk malamin
daya zo musu (TEACHING PRACTICES) indai daga (sa'adatu Rimi) yake sai taga
k'warewarsa da nagartasa fannin koyarwa daban take data sauran malaman don haka
taci d'amarar yin wannan makaranta.

Taku ce
Layuza kabir Adam
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 YA'N ARABIC 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

📚📚📚📚📚📚📚📚
DEDICATED TO ALL
ARABIC/ ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*💻ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣0⃣3⃣ 0⃣0⃣3⃣

Nahnah Khadeejah dika shekarunta goma sha tara doguwa ce ba sosai can ba tana
da jiki dai-dai misali bata da siranta bata da k'iba baka ce amma irin black
beauty d'innan tanada manyan ido Wanda suke d'auke da gashin ido gazar-gazar tana
da cikar gashin gira sannan idanuwan ta lumshashshu ne kamar tana jin bacci
tanada sanyin murya amma tana da tsiwa in an tab'ota tanada wuyan sabo da
mutane don haka wasu ke ganin girman kanta, wannan kenan.

Yau zuwan datai ka'rb'an Admission letter d'inta a skul d'in dik ya gajiyar da
ita jin jikinta take yana mata ciwo kasancewar yaune zuwanta na farko cikin skul
d'in don dik wani abu yaya Haroon ke mata yau d'inne yace ya dace ta fara zuwa
skul d'in tana ganin yanda komai ke tafiya don ta gane kan skul d'in kafin su fara
lectures, don haka tunda ta dawo ta shige d'akinta ta kwanta kan gado tana matse
gajiyan, jif taji mubashshir ya fad'o kanta yana fad'in " Aunty oyo yo na dawo a
islamiyya kema kin dawo daga unguwar"
Shafa kansa tai tace"Na dawo mubashshir sai dai a gajiye nake tib'is jeka cire
uniform d'inka"
Tashi yai yai waje yana k'walawa k'aninsa mukarram kira Wanda yake d'an shekara
d'aya.

Bayan sallar magriba suna zaune a parlour ita da Aunty Hafsa da Mubashshir da
mukarram suna cin abinci ta kalli Hafsa tace "Aunty gaskiya skul d'innan akwai
d'alibai da yawa kinga mutane kamar k'asa"

Mirmishi tai tace " ai kad'anma kika gansu sai kun fara lecture zakiga al'umma
lokacin kowa yazo"
Jin jina kai tai tana d'okin ace yau gata a cikin hole tana d'aukan lecture ta
zama ya'n matan high institution, a lokacin tasan bakinta bazai rufu ba 😀.

Duk wani Abu daya kamata na departmental sunyi I.D card ya rage musu yau
zasu amsa,
Kasancewar ranar Alhamis ne tana azimi gashi ana k'walla rana don haka jikinta
duk ba k'wari ta shirya cikin doguwar riga ja me adon fari don haka tai roiling
kanta da farin mayafin kashka k'arami tasa takalmi fari tare da rataya jakanta ta
fito parlour tana yiwa Aunty Hafsa sallama.

Keke napep ta hau ya kaita har cikin skul d'in ba laifi yau jama'ar kad'anne ,
a hankali take tafiya cikin nutsuwa har ta isa wajan da ake amsar I.D card d'in
maza ne a zazzaune suna hira irin ta rik'ak'k'un samari da suke ji da Samar taka,
ta gefansu ta ratsa zata wuce d'aya daga cikinsu ya taso yasha gabanta yana
fad'in"Y'an mata ji mana"
Fuskewa tai kamar bataji me yake fad'i ba ta zagaye ta gefansa zata wuce ya k'ara
shan gabanta " Dake fa ake magana kina jin mutane sai kace y'ar k'auye"
D'ago da idanunta tai cike da tsiwa tace"kai Malam ban hanya "
"In aka k'ifa me zaki iya? Ke sai kace wata y'ar k'auye ana miki magana kina
fuskewa ahaka kamar kin waye"
Cike da gajiya da batunsa da rainin wayonsa ta k'ara rab'e jikinta ta gefe ta
wuce, d'aga murya yai yana fad'in " sokuwa kin samu ma an kulaki zakiyiwa mutane
hauka."
Bata kulashi ba ita dai taci gaba da tafiyanta ranta a b'ace.

Bata dad'e ba ta amshi I.D card d'in tare da time table ta fito bakin titi tana
neman abin hawa,
K'irrrrr taji daga bayanta anja birki tare da tada k'ura a hanzarce ta juya
don taga waye,

Kallon motan tai sosai don ta gane fuskar wannan saurayinne yamutsa fuska
tai tare da kauda kai tana D'an k'aramin tsaki, Figar motan yai har zuwa kusa da
ita ya zuge glass d'in tare da lek'o da kai yace "ya'r k'auyen banda kawai."

Ko kallonsa batai ba balle a gane da ita yake.

Yau kam Sam bataji dad'in zuwa makarantar ba dik ranta a b'ace yake zuciyanta
sai tafasa take,
Har dare bata da walwala aranta take fad'in Allah ka sakamin b'acin ran da
wannan bawan naka yasani aciki, ahaka bacci yai gaba da ita.

Bayan sati d'aya suka fara lecture sosai take jin dad'in karatunta don tana
fahimtar komai yanda ya dace,
Yau kwanansu hud'u da fara lectures d'in suna zaune cikin hole tsit kakeji don
lecturer d'in dake ciki bashi da sauk'i ko k'ank'ani motsi inka fiye yi zai iya
koranka waje gashi da kwarjini,
Imla'i wato (dictation) yake ta musu duk sun duk'ufa rubutu suke, wasu samari
suka zo jikin window suka tsaya suna ta surutu duk suka fara jan hankalin d'aliban
ai kuwa a zafa fe yai wajansu da saurin bakinsa ya fara musu bala'i yana koransu
daga jikin windows d'in k'unk'ni suke suna fad'in (mufa ba ya'an secondary bane da
za'a rik'ai mana irin wannan Koran hasalima mu degree mukeyi cikin skul d'dinnan ba
n.c.e ba har za'a shiga rayuwarmu."
D'aya daga cikinsu yace "kai jibesu yanda d'aliban nasa sukai wani tsit kamar
ana musu hiran mutuwa da gani sabon yanka ne"
Dariya suka sa gaba d'aya cike da shak'iyanci d'aya yace "kai kasani ko hiran
mutuwar yake musu sukai tsit haka tunda dai kana jinfa larabci sukeyi."
"Hhhhhhhhhhhhhhh"
Duk suka sa dariyan tashin mutunci,
A hankali ta d'ago kanta ta dubi samarin dake tata iskancinsu 'rasssss .. Taji
gabanta ya fad'i ganin wannan saurayin ne daya mata wulakanci ranar nan da sauri
tai k'asa da kanta don karya ganta. . haniyar su ta k'ara ji suna tafiya sabida
korar karan da lecturer d'in yaci gaba da yimusu.

Bayan ya dawo cikin ajin yaci gaba da k'orafi kan rashin tarbiyar wasu d'aliban
Sam basa ganin malaman da ba nasu ba da mutunci,
Haka dai yaci gaba da mitarsa ya hak'ura.

Wajan karfe d'aya sun fito lecture sukai hanyan masallacin mata don yin sallah
ita da wata Hafsa wadda tun zuwanta suke zama gu d'aya sabida sunan Aunty Hafsa
yasa Nahnah taji ta shiga ranta har suka d'an saba kad'an,
Suna tafe suna d'an hira daga bayanta taji ana fad'in "Ya'n mata ina zuwa cikin
wannan ranar"?

Daf taji gabanta ya fad'i don taso ta gane miryan waye "waike wace irin
bak'auyi yace ahaka ana kallonki wayaiyiya dake kinyi kwalliya irinta manyan mata
amma duk d'abiunki irin na k'auyawa, ai yanzu y'an mata sun daina wannan jan ajin
ana kwankwasawa suke bud'ewa, kin san kuwa irin yanda manyan yaran makarantar nan
suke yayina duk macan da kika cewa UK tasan ni amma ke tun rannan ana miki
magana kina wani basarwa"
Duk maganar da yakeyi ba wadda tasa idonta cikin nasa yana gefan Khadeejah
Yanata zubarsa suko tafiyansu suke abinsu har suka isa k'ofan masallacin sukai
shigewansu abinsu basu bi ta kansa ba,
Sosa kai yai cike da takaici ya juya ya koma inda abokansa ke jiransa.

Bayan sunyi sallar sun fito Hafsah ta dubi Khadeejah tace"wai a ina kika samo
wannan tab'ab'b'an ya ishi mutane da zuba haka."

Tab'e baki tai cike da basarwa tace"oho ni banma sanshi ba kawai shirme ne
irin na mazan da basu San abinda ya kawo su makaranta ba."

" To Allah ya kyauta"

Daga nan suka bar zancen suka shiga wata lecture d'in.

Taku ce
Layuza kabir Adam
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 YA'N ARABIC 🌸

NA
LAYUZA KABIR ADAM

DEDICATED TO ALL
ARABIC/ ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*💻ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣0⃣4⃣ 0⃣0⃣4⃣

Cikin k'warin giwa da nutsuwa Khadeejah ke tafiyar da komai d'inta acikin skul
d'in Sam bata shiga cikin shirgin kowa inba Hafsa Usman ba tana naxartar rayuwar
kowa ne ta gane inda yasa gaba, tana so ta gane iya kamun kan ko wace mace cikin
class d'in nasu ne duk da masha Allah d'aliban Arabic d'alibai ne masu cike da
Nutsuwa da kamun kai da matuk'ar wahla kaga d'alibar dake karantar Arabic/ Islamic
tana wani abu na rashin d'a'a ko ballagazanci da maza.

Yauma kamar kullum ta shirya tsaf cikin atanfa d'inkin Riga da sket tai
d'aurin d'ankwalin fanka ya tashi sosai gwanin birgewa mayafinta na cumar tasa ta
d'au jakanta ta fito a parlour ta tarar da Yaya Haroon ta zauna suka gaisa
yace"Nahnah ya karatun kina jin dad'insa dai ko?"
Mirmishi tai tace " Yaya wlh Alhamdulillah komai yana tafiya dai-dai."

"Madallah bari in kaiki don yau ba da wuri zan fita ba zamu je wata gaisuwa daga
office d'inmu."

Suna tafe suna hira har suka k'araso skul d'in dake ma a new block's zasuyi
lecture d'in yasa ya ajiyeta a bakin gate tunda ba nisa zatai ba ya d'auko 1k ya
bata godiya tai ta fito.

Cike da nutsuwarta take tafiya harta k'arasa block d'in tasa k'afa ciki tana
k'ok'arin zama taji lecturer d'in yace " ‫" انت‬
A nutse ta juyo ta dubeshi taji ya k'ara fad'in " ‫"لماذا تاكرت؟‬
K'asa tai da kanta don ganin duk idon d'aliban ya dawo kanta ganin batai
magana ba yasa yace " ‫"تالي االهنا‬
A hankali ta k'araso gaban Allon jikinta harya fara rawa yace" ‫ اخرجي‬." rau rau
tai da idonta harya kawo ruwa ta had'a hannayenta waje d'aya alamar ban hak'uri 👏
tace" "‫افوان يا عستاذ‬
Ganin yanda jikinta ke rawa yasa ya kauda kai tare da nuna mata hanya da
sauri ta koma ta zauna a gunta tana ajiyan zuciya,
Lecture ya cigaba da yi musu cike da k'warewa irinta malamin daya son harkar
education.

Bayan sun fito Hafsahm ta dubeta tana murmushi tace " Khadee haka kike dama
da tsoro? daga ance meyasa kika makara sai jikinki ya d'au rawa."
Gyad'a kai tai tace " hhhhmmmm Bazaki gane ba Hafsa ba maganarsa ce ta
tsorata niba idon mazan nan yasa jikina rawa jifa yanda duk suka zuba min
idanuwansu"
To meye ai dakewa zakiyi kamar biki gansu ba."
" Ke wlh nifa kinga cikin maza na taso agidanmu amma ni Allah yasa min k'in
had'a sabga da wani namiji daba na danginmu ba."
Dariya sosai taba Hafsa don haka sai da tai me isarta sannan tace"To tunda
kikazo high institutions ai kinzo gidan maza kuma dole ki alak'a dasu."
Had'e rai tai tace " kai dai Hafsa kema kallon kitse nakewa rogo nai zaton ke
d'in me kamewa ce amma meye naji kina fad'a haka?"

Kallonta Hafsa tai sosai kafin tace " Ke nifa ba abinda kike zargi nake nufi ba
inaso in nuna miki ne dole ko yaya sai kinyi alak'a da maza akan harkar karatu
kamar group discussion, group Assagment da ire ire ransu kinga dole maza da mata
ake hadawa."

Kai kawai ta d'aga bata k'ara magana ba suka nufi cafeteria.

Suna zaune shagon me wainar fulawa suna jira a soya musu Hafsa ta cewa
Khadeejah "Deejah ina zuwa bari in kai photo copy can wajan kafin asoya mana."
"Ok to sai kin dawo."

Wayanta ta d'auko tana ta bud'e data don ta duba sok'onnin da aka turo mata tunda
ba Wanda zatai hira dashi,
Kasancewar shagon cike yake da mata wasu nacin abinci wasu na hira suna jiran a
soya musu,
Wata budurwa ce ta shigo shagon da shadda koriya ajikinta tasa blue d'in hijabi
duk ya tattare ya tashi sabida tsufan da yayi ga takalmin soso ruwan hoda fuskar
nan tata ko yar powder babu kwata-kwata dai abin ba birgewa waje ta samu ta zauna
hannunta d'auke da robar taliya da manja data siyo agaggauce ta cinye tasha ruwanta
ta mik'e ta fice,
Tana fita wasu y'an mata suka bushe da dariya d'ayar ta kalli sauran k'awayenta
tace "Kai Rahma umar irin wannan d'aukan wanka da kikai ai sai a d'auka meenat
event zakije biki"
Wata ma ta amshe " A 'a wlh wannan ba Rahma bace tafi dacewa da Iklima salis."
Bushewa sukai da dariya sunata shak'iyan cinsu wadda aka kira da Rahma ta
yatsina fuska tace" kai ai wlh wasu matan suna bada gayu don Allah jibi yanda ta
wani zo skul abirkice saikace wadda akaiwa rasuwa, kina high kina zuwa skul da wani
shiga irinta mahaukata mitsssss taja tsaki."
Dariya suka k'ara yi Ilkima tace "ai wlh wanna in yar department d'inmu ce ko
kulata bazan rink'ayi ba don bata kai ko matsayin in dubeta ba."

Wata dariyan sauran suka saki suna mata tafi wata cikinsu tace" To waiku ina
ruwanku da ita maybe ma ba y'ar skul d'innan bace wata k'ilama irin masu masarar
nan na bakin gate yunwa ta kamata shine ta shigo ta rage zafi da y'ar taliyarta."
"Ke inji uban wa? to wlh d'aliba ce kina ganinta da Jakarta kawai irin y'an
Arabic d'innan ne masu jawa skul d'inmu zagi, bazaki tab'a ganin y'an Arabic da
kwalliya ba waisu ustazai."

Karo na farko Khadeejah ta d'ago kanta ta dubesu da maganar da sukeyi najin sun
fara zagin department d'inta har zata tanka sai kuma kawai tai shiru,
Wayanta ce ta fara Ring ta d'aga cike da murna da shagwab'a ganin Yaya ja'afar
ne yayansu dake aikin soja
" Hello broth"
Daga d'aya bangaran ya amsa
Tace " morning"
"Morning sis"
" how are you"
"Fine broth "

Salon yanda take maganar da shagwab'a yasa duk hankalinsu ya dawo kanta
Nan suka fara kallon kallo da ido suka fara gulmanta dukda dik da English suke
maganar duk sunajin me take fad'i sun San bada saurayi take wayanba yayanta ne amma
hakan bai hanasu gulmanta ba.
Bayan ta gama ta ajiye wayan tana kallon Hafsa data dawo yanzu fuskanta d'auke
da mirmishi tace" Hafsa k'ila yau kafin agama lecture zan gudu gida yayana yace min
ya taho daga Lagos zai kawo mana ziyara daga nan ya wuce Garinmu"
Mirmishi Hafsa tai tace" kuma shine zaki gudu gida ai lokacin da zamu tashi har
kije ma be zama lalle ya sauka ba, kuma wlh kin San malamin Islamic d'innan da zai
mana a k'arshe yace duk Wanda bai attending lecture d'insaba zai sami matsala
dashi"

Jim tai kafin tace" To bari injira"

Ta window d'in shagon wata ta lek'o tace " Umm mema sunanku um Y'AN ARABIC."

Atare Hafsa da Khadeejah suka d'ago suna dubanta tai mirmishi tace"Wlh ban San
sunayenku bane muna department d'aya daku daman wucewa zanyi na hango Ku nan."
"Khadeejah tai dariya tace "To ki zaga yo mana Y'AR ARABIC tunda muma bamu San
sunanki ba."
Zagayowa tai tazo ta sami gu ta zauna tana fad'in "Wlh sai zagaye nake ni kad'ai
wadda muke zama da ita yau bata zoba shiyasa ban San zuwa wajan da ban San kowa
duk skul d'in ta isheni fa"
"Kinji duka fa satin mu biyu acikin skul d'in da fara lecture ai sai a hankali
za'a saba ke meye sunanki?"

"Saudah Sadeeq suna na"


"Ok ni kuma Hafsa wannan d'in kuma Khadeejah Alk'adi Yusuf."

Tsalam sukaji bakin Iklima cikinsu " Hy friends don Allah wane department kuke?"

Kallon ta Hafsa tai tace"Mu Y'AN ARABIC ne muna department under Islamic."
Da mamaki suke kallonsu don abin ya d'aure musu kai duk cikin su ukun babu
wata me k'ask'antacciyar shiga duk Kansu cikin ado suke abinda sha'awa,
A sanyaye Rahma tace tana duban Khadeejah " Amma baiwar Allah dama ke d'in y'ar
Arabic ce kina ji munata aibata Y'AN ARABIC biki tanka mana ba."
Cike da b'acin rai Khadeejah tace 'In tanka ince muku meye tunda naga alamar
sana'arku ce yi da mutane tunda wannan baiwar Allah ta shigo ta fita kuke zancanta
K'arshe ma kuka b'ige da jingina ta da department d'in ARABIC sabida gurb'ataccen
tunaninku ya Baku Y'AN ARABIC basa kwalliya, tunda an fad'a muku don mutum yana
karantar addini an haramta mai ado wannan rashin kyakykyawan tunanin ne."

Tsit sukai duk kunya ta kamasu gudun kar aga kashinsu yasa d'aya daga cikinsu
k'arfin halin fad'in " Ke malama karki fad'a mana magana mana naga zantukanki sina
yin gautsi ."

Had'iyan yawu tai taci gaba " ai bamu muka ce Y'AN ARABIC d'in suna zuwa skul da
k'azanta ba muma ji mukai ana fad'i don haka karkiga laifinmu."

" To tunda ji kikai ana fad'a daga yau duk Wanda kukaji yana zancan Y'AN ARABIC
basa kwalliya to ki k'aryata shi don waccan ma da kuke gulmanta ba department
d'inmu take ba, a k'arshe ina me Baku shawara da Ku guji zancan mutum bayan idonsa
domin haramunne Allah ya haramta hakan."

Mik'ewa tai tana kallon su Hafsa "Ku tashi mu tafi don saura minti Goma mushiga
lecture in mun fito mazo mu amshi Wainar karmu makara."

Har sunje bakin k'ofa ta juyo tana fad'in "y'an uwa sai anjima ."

Bata saurari amsarsu ba ta bar gun.

Taku ce
Layuza kabir Adam
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

*🌸YA'N* *ARABIC* 🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDICATED TO ALL
ARABIC/ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS
ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣0⃣5⃣ 0⃣0⃣5⃣

Akan hanyarsu ta zuwa lecture d'in kowa bai tankawa d'an uwansa ba, kai tsaye suka
shige cikin lecture theater d'in suka maida hankali gun d'aukan darasin.

Tsawon awa guda suka fito Hafsa ta dubi Nahnah tana cewa"mu wuce mu karb'i
wainar mu ko ?"

Ba tare data ce komai ba kawai gyad'a kai tail suka wuce ,


Suna zaune zasu fara cin wainar Hafsa ta kalli Nahnah tana d'an murmishi tace
" khadeejah daman kin iya fad'a haka ina miki kallon me sanyi da yawa,"

Cikin basarwa tace "fad'an me kuma nayi Hafsah"


"Au har kin manta rikicinku da mutanan nan na d'azu ai naji dad'i da kika gyasa
musu magana"

" lalle ke har kinsa wannan abin a gurbin fad'a ai gaskiya kawai na fad'a musu
kan kuskuransu"

Hafsah ta bud'e baki da zummar Kara magana ta katseta ta hanyar cewa " mubar
wannan batun oya muci abinci donni harna manta ma dasu banda kin tuna"

Cike da zumud'i ta nufi hanyar gida bayan kammala lectures d'insu don tasan yanzu
Yayanta ya k'araso tunda daman ya fad's mata bazai wuce awa uku zuwa Hud'u bai
sauka ba, don haka da k'arfin gwiya ta shiga gidan ai kuwa muryansa ta fara juyowa
suna hira da yaya Haroon da gudu ta k'arasa parlour tana fad'in " Yaya Oyo yo sannu
da zuwa marhaban bika "
Dariya yai tare da rik'o hannunta yana fad'in " Nahnah duk wannan sannu da zuwan
nawa ne lalle kin cancanci tsara ba me tarin yawa"

Dariya ta k'arayi ta zauna tanaiwa Yaya Haroon barka da gida sannan ta k'ara
kallonsa tace "yaya sannu da hanya gaskiya ka tafiyu ya aikin?"

Mirmishi yai yace"um bari kawai y'ar k'anwata sai a hankali ta skul d'in? Um wai
yau saiga autar Baffa a high institution abin kamar wasa"
Yaya Haroon ne yai dariya tare da fad'in " kaga Nahnah an zama manya ko "

Yaya nura ya k'ara dariya yana jinjina girman data k'ara,

Aunty Hafsa ce ta fito hannunta d'auke da k'aton faranti da Sauri Nahnah ta


tashi ta k'arb'i kayan tana "Sannu Aunty ya gidan ya aiki"
Had'e rai tai cikin sigan wasa tace " bazan amsa ai da biki san da niba kina ta
Nura ko"

Caraf yaya Nura ya amshe "a'a Aunty ba ruwana bani na rik'eta ba fa"

Ita dai Bata tanka ba tai cikin d'akin fuskanta d'auke da mirmishi,
Ruwa ta watsa ta d'auro alwala don magriba tayi tazo tai sallah sannan ta fito
parlour inda su yaya suke cin abinci ta zauna tare da d'aukan flate itama ta zuba
ta fara cin nata.

Bayan sallar isha'i duka suna zaune a parlour sinata hira yaya Nura ya jawo
trolley back d'insa yana fad'in Nahnah bari in baki tsara banki irin ta y'an matan
jami'a,

Cikin zumud'i ta matso gabansa tana cewa "yauwa my broth na gode sosai fa"

Dariya yai "ke tun kafin abaki har kin fara godiya "

Ita dai a zumid'ance take kallon jakan taga me zai d'auko,

Zuge jakan yai ya fara ciro wasu dogayan riguna y'an ubansu guda biyar sannan
takalma k'afa uku da jakunkunan su sai wasu jakun kunan irin wanda d'alibi yake
buk'ata masu kyau ya tura mata gabanta yana fad'in
"To gashi amma Allah yasa rigunanma suyi miki dai-dai don naga kin k'ara
tsayi"
Tsananin Murna bayyane kan fuskarta take d'aga kayan tana fad'in "masha Allah
broth amma ka burgeni na gode Allah ya k'ara muku bud'i da wadata ya yalwata
arzik'inku"

Da mirmishi kan fuskarsu suke amsawa da Ameen don a kullum burinsu bai wuce
ganin farin cikin autar tasu ba ko don amanar da Baffansu ya bar musu.

Da sassafe yaya Nura yai shirin d'aukar hanyar sakkoto bayan ya cika wa Nahnah
jakanta da kud'i yace don tana buk'atar kud'i a irin wannan lokacin.

A haka Nahnah taci gaba da tafiyar da karatun ta cike da nutsuwa sai abu guda da
yake cin ranta yake dagula mata lissafi shine UK ya matsantawa rayuwanta da yawa
duk inda ta shiga sai ya bita kuma daya ganta ba maganar arzikin da zai furta mata
sai masu ciwo arai.

Yau ma kamar kullum ta shigo cikin skul d'in sanye da doguwar riga yellow an
mata aiki sa stones red color masu d'aukan ido don haka tai amfani da red d'in
mayafi wajen yin rolling d'in kanta k'afanta sanye da takalmi red da jaka red,
kallo d'aya zakai mata ka Tabbatar da ainihin kyan da tayi masha Allah.

Tafiya take cike da nutsuwa da kamun kai irin na d'aliban da addini ya ratsa
su.

hon d'in motan dake bayanta ne ya isheta don haka ta juya don ganin waye yake son
rikita mata kwanya haka,
Caraf idonta ya fad'a cikin na UK yana mata wannan banzan kallon nashi me cike
da izza da jin kai, a hankali tai k'asa da idonta tare da Kau da kai gefe tana jin
wani b'acin rai aranta.

Tsawon tafiyar da tai daga bakin gate d'in zuwa inda zatai lecture UK bai
fasa bin bayanta ba tare da sakar mata hon d'in motar Wanda hakan yai sanadiyar jan
hankalin dukkan wanda ke bin hanyar kanta.

Sanin halinsa da d'aukacin d'aliban sukai yasa hakan bai zama bak'on abu agunsu
ba, sun sanshi d'alibi ne mai d'aukar magana da maida mace ba abakin komai ba,kai
tsaye sun san tsokananta yake yana son watsa ta.

Jiki babu k'wari ta k'arasa hole d'in tana shiga ta zauna zuciyanta na bugawa
don b'acin rai, ko sallama batai wa d'aliban dake zaune gefanta ba wanda wannan ba
d'abi arta bace kai bama d'abiar duk wani d'alibin Arabic bane.

Tun shigowarta suka fahimci akwai damuwa tare da ita amma ba Wanda ya tanka mata
kasancewar Malam ya fara darasi.

Babu abinda ta tsinta cikin lecture d'in har malamin ya fita, ahankali taji
Hafsah ta dafa kafad'anta tana fad'in
"Khadeejah ya akayi ne na ganki so silent?"

Sharrrr hawaye ya fara bin kumatunta don dama kad'an take jira tai kuka,

"Subhanallah Khadeejah meke faruwa haka ko baki da lfy ne?"

Kuka sosai take kamar wadda akaiwa mutuwa, abinda ya tayar da hankalin Hafsah
matuk'a ta shiga rik'e hannunta tana jijjigata, abinda yaja duka hankalin matan
dake ajin suka shiga Tambayar lafiya meya faru.
Ganin mutane sun cika kanta yasa tai k'ok'arin tsaida kukanta ta share hawayen,
Nasiha suka rink'a mata akan kome ke damunta ta barwa Allah ta daina kuka haka,
gyad'a Kai kawai tai ba tare da ta furta komai ba.

Kusan 5 minutes suna zaune gun ita da Hafsah ta sauke ajiyan zuciya tare da
furta" Hafsah me na tsarewa wannan mutumin yake takura rayuwata me namishi?"

Kallon ta Hafsah tai cikin rashin fahimta tace "Waye ne Khadeejah?"

"Mutumin nan daya takura min a skul d'innan,_ yau tun daga bakin gate yake bina
da horn har bakin hole d'in nan, Hafsah biki ga yanda mutane ke kallona ba kamar
nayi lefi. . ."

Ta k'arashe maganar tana matse k'wallan da ya k'ara taruwa a idonta.

Shiru na d'an lokaci ya shiga tsakaninsu daga bisani Hafsah tace " kiyi hak'uri
Khadeejah ki cire wannan mutumin aranki, duk abinda zai miki karki sa damuwansa
cikin zuciyarki,irinsu suna da yawa marasa mutunci kinga maybe ma shi yanzu ya
manta ya miki hakan ke ya barki da damuwa."

"Hafsah biki San yanda na tsani kallo ba, duk yanda muke da mutum ban so ya fiye
kallo na amma yau mutumin nan yaja min tarin idanuwan jama'a akaina kamar nayi
lefi."

Ruk'o hannunta Hafsah tai tana fad'in " Tashi mu tafi kiyi hak'uri ki bar batun
nan kinji."

**********************
Kwanaki da yawa sun shud'e yayin da karatun su Nahnah yai nisa
sun fara shirin fara exam na first semester N.C.E one, ta maida hankalinta sosai
kan karatun ta don ita bamai wasa bace kan harkar karatun ta.

Damuwanta d'aya ne UK a kullum k'ara matsawa rayuwarta yake ba sassauci duk wani
motsin Hafsah akan idonsa yake, abin haushin kuma ba wai fa yana sonta bane a'a
kawai kullum burinsa ya ganta ya musgunawa rayuwarta da bak'ak'en kalamai wai yana
fad'in tunda ya nuna da farko yana ra'ayinta ta watsa mai k'asa a ido ta watsashi
to shima sai ya rama da babban wulak'anci agareta.

Yau zasu fara da exam d'in Education 111 Wanda za'a shiga k'arfe goma.

Tun k'arfe Tara saura kwata tazo skul d'in kai tsaye (‫ )المكتبة‬library ta wuce don
taci gaba da duba hand out nata.

30 minutes ta samu cikin ‫ مكتبة‬d'in ta fito zuwa inda zasuyi exam d'in don ta sami
waje me kyau,

Ta kusa daf da lecture Theater d'in taji ana bin bayanta kamar za'a taka mata
takalmi da sauri ta tsaya cak ba tare data wai waya ba don jikinta ya bata ko waye,
ilai kuwa muryanshi ya daki dodon kunnanta " ke villager girl yau kuma saurin me
kikeyi haka, ho har college d"in ta fara bugarki naga an daina yangar da yauk'in"

Tsit bata bashi amsa ba yaci gaba " ke ko muguwar gidahuma ce a haka dai gashi
jiki ya karb'i gayu amma cikin kan sai duhun jahilci taf, sai anyi batu kuce wai Ku
y'an ARABIC ustazai, me ake da macan Arabic medium babu komai a tare da ita sai
duhun kai da rashin wayewa, duk gayu da iya kwalliya irin na macan Arabic inka
latsata ba wayewa, banza tsami kawai ware ki bawa mutane waje."

A kasalance ta d'aga k'afarta ta tafi zuciyanta kamar zata fito idonta duk ya
kawo ruwa.

Wannan shine abinda kullum ke faruwa inta had'u da UK Wanda ita har mamaki abin
ke bata na yanda baya fashin rana wajen bibiyarta.

Haka ta k'arasa cikin ajin jiki a mace, ganin Hafsah tana mata mirmishi yasa ta
saki ranta ta k'arasa kusanta ta zauna suka gaisa.

Tsawon satittika suka d'auka suna exams d'in wanda Nahnah taketa zumud'in su
gama ta had'a kayanta zuwa Gida sakkoto birnin shehu.

Kwanasu d'aya tak da gamawa ta shilla sai gida cike da d'okin ganin iyaye da y'an
uwa.

Tunda ta dira a sakkoto Dangi suka baibayeta kowa murna yake yana fad'in " Nahnah
an girma an zama emmata"
Ita dai mirmishi kawai takeyi aranta tana fad'in babu abinda ya kai mahaifa
dad'in in kana mahaifarka sai kaji kamar kafi kowa.

Bata sami kanta ba sai dare tai wanka tai sallah bayan taci abinci ta haye gadon
ummanta cike da nishad'i.

Hira sosai sukai da ummanta har wajan sha biyu kana sukai bacci.

Zuwanta sakkoto ziyara take sosai daga gidan wannan zuwa na wancan gidan
yayyinta mata da maza da duk dangin mahaifanta.

Kasancewar hutun nasu duka na sati uku ne yasa kwanta goma sha takwas ta
d'auko hanyar kano tare da kaya nik'i nik'i Wanda yayyanta suka harhad'a mata da
y'an uwa.

Bayan sallar magriba ta iso gidan cike da gajiya, gaisawa kawai sukai da Aunty
Hafsah ta ajiye jakanta ta fad'a toilet tai wanka ta d'auro alwala, bayan ta idar
da sallar tai addu'oi ta fito parlour inda ta samu Yaya Haroon ya dawo nan ta
zauna suka gaisa cike da murna yana tambayarta ya ta barosu ta amsa " da duk
lafiyansu qlau"

Nan ta zauna sukaci abincin dare suka shiga hira har zuwa wani lokacin sannan kowa
yai niyar kwanciya.

************************
Rayuwa ta lula yayin da karatu yai nisa gasu Nahnah, yanzu suna satin
k'arshe na cinye second semester d'insu , Wanda tun dawo warsu hutu bata k'ara
ganin UK ba, hakan ya haifar mata da kwamciyar hankali don babu me shigar mata
rayuwa yanzu.
Bayan kwana biyu, tana zaune ita da Hafsah da ummy usman suna d'an hira sama sama
tare da duba littafan dake hannunsu suna nazari aciki,
Shewan samari taji a gabansu suna ihu tare da tafa hannunwa d'aya cikinsu na
fad'in "kai gaskiya nayi missing skul d'innan tun ranar final exam ban ko bi ta
hanyarta ba"

"To gidan ubanka ce skul d'in da in ka gama saika ci gaba da zuwa"


Wani ya fad'i yana yamutsa fuska,

"Kai dole ya shigo mana tunda ya bar babyn sa acikinta duk da ma dai suna
had'uwa a wajen shan eh . . .. "

Dariya suka d'auka duka suna tafawa.

"Kai Kai kai UK kaga waccen lady d'in kamar Bak'auyiyarka nan Y'ar Arabic."

A tare duka sika d'aga kai suna kallon inda yake nuna musu daga bisani suka shek'e
da dariya suna fad'i " villager villager girl"

Yar taji gaban ta ya fad'i tai saurin yin k'asa da idonta.

A hankali ya tako zuwa gabanta yana tafa hannu tare da fad'in " Gidahuma daman
kina nan ni harna manta dake ma, ana nan dai da duhun kan irin naku na y'an Arabic
ko? Jibi banza meye to na sunkuyar da kai kamar bak'auyiyar amarya? Dalla d'ago
kiji me zance miki."

Daga gefansa wani yace "anya UK ba son yarinyar nan kake ba inba haka ba meye na
shiga rayuwarta haka?"

Da sauri UK ya dafe kai yana fad'in " AA ka cuceni ka gama dani ka wulak'anta
ni ka tozarta ni wallahi Allah ya isa tsakani na da kai, kama rasa da wa zaka
had'ani saida wannan Y'ar Arabic d'in me tarin duhun kai da k'auyanci, wadda ko
Kalmar Love bata iya furtawa ba balle tayi shi, wlh da inyi love da Y'ar Arabic
k'ara in mutu banyi aure ba, meta sani da zata min meta iya mutttsssss, AA kasan
dai ni mijin wayayyiyar mace me aji ne wadda zan shiga da ita ko ina ta fiddani
kunya."

Dariya sosai sauran abokan keyi na yanda ya daddage yake masifa har idonsa ya
canja da b'acin rai.

Tsaki yaja ya bar gun sauran suka bishi.

"Khadeejah don Allah me kikaiwa wannan mutumin haka, Tun tuni nake ce miki mukai
k'ararsa ga hukumar makaranta kika ce abarshi zai daina gashi nan yanzu ya bar
skull d'inma bai fasa shigowa yimiki hauka ba."

D'agowa tai tana mirmishin yak'e Wanda yafi kuka ciwo ,


" Hafsah nifa ban jin haushinsa yanzu nasan jahilci da rashin sanin addini ke
damunsa, yaje yayi duniya ce wata rana zai daina."

Ummy tace "ni kin san abinda yafi b'ata min rai dashi da yake cewa me macan Arabic
ta sani a harkar love me zata iyayi, Allah ina rok'on ka daka had'a shi da y'ar
Arabic a gidan auransa naga yanda za'ayi."

"Don Allah muyi abinda ke gabanmu mu bar wannan zancan haka."


Taku ce y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YAN* *ARABIC* 🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDICATED TO ALL
ARABIC/ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣0⃣6⃣ 0⃣0⃣6⃣

Tsawon wata goma Nahnah bata k'ara ganin UK ba Wanda hakan ya tabbatar mata da ya
kammala skul d'in gaba d'aya,kuma tasan a wannan lokaci yana hidimar k'asa tunda
shi a b'angaran degree yake, hakan ya k'ara kwantar da hanlalinta harta manta shi
cikin rayuwarta.

A lokacin suna N.c.e 2 ne shima sunyi nisa don har sun fara shirin zuwa Teaching
practice (T.P) da sunyi exam d'in second semester d'in zasu tafi Wanda zasu cinye
tsawon semester guda baza su dawo ba sai wata second semester N.C.E 3.

**************
Alhj Usman katsina shahararran D'an kasuwa me wasa da y'ay'an nera, mutum me
karamci da girmama talaka bashi da girman kai ko kad'an yana da tsananin kyauta da
son mutane, yana da gaskiya matuk'a a harkar kasuwancin sa, matsalansa d'aya ce
masifar son ya'ya' baya son abinda zai sami d'ansa ko kad'an duk yanda kuke dashi
to matuk'ar ka shiga harkar ya'ya'n sa to zaku raba gari abinda d'ansa ke so shi
yake so ba tare daya kula da munin abun ba.

Wannan son ya samo asali ne daga rasuwar matar sa uwar ya'ya'nsa Wanda ta rasu
tun yaran suna k'anana su uku a haihuwar autar ta rasu awa d'aya da haihuwar,
Tausayi da k'aunar ya'ya'n ta taka rawar gani wajen sangarta su.
Yakai tsawon shekara bakwai bayan rasuwar baiyi aure ba ya tara ma'aikata sama
da goma agidan suke kula da yaran nashi cikin kulawa da aminci, yayin da shi kuma
yake cika musu lalitarsu da kud'i don ya gamsu da kulawar da sukewa y'ay'an nashi.

Umar shine Babba Wanda yaci sunan kakansa suna kiransa da Daddy, sai ummu sulaim ,
sannan Ruk'ayya auta wadda taci sunan mamanta me rasuwa, suna ce mata sweety Wanda
Abbanta yake kiranta har sunan ya bita.

Iya nacin da akewa Alhj. Usman akan yayi aure bai yi ba saida Sweety ta shekara
bakwai sannan Allah ya had'ashi da Aunty Murjanatu wadda ta tab'a yin aure shekarta
d'aya ta fito ya ganta ya aura kan sharad'in kulawa da y'ay'ansa cikin amana da
aminci.

Zuwa yanzu tana da y'ay'a biyu a gidan duk maza zaid da haris.

Umar wato 'Daddy' a yanzu yana can kwara state yana N.Y.N.C.E d'insa Wanda ya
rage mai wata d'aya ya gama, kuma anan gidansu Abban sa ya gama yimai shirinsa tsaf
don tafiya k'asar India yin wani course na shekara biyu akan fannin karatunsa.

Ummu sulaim kuwa an Mata aure bada dad'ewa ba har yanzu tana kan karatunta a
bayero.

Sai sweety itama yanzu tana shekararta ta biyu a northwest.

Yaya haroon abokin kasuwancin Alhj Usman ne yana karb'ar shinkafa a gunsu ya raba
a wajan aikinsu da sauran store store, Jinin su ya had'u matuk'a Alhj yana son yaya
Haroon sabida ya kula da amanarsa, wani sa'in har gida yake kiransa su tattauna a
maimakon office d'insa.

Rashin lafiya ne ya kama Alhj Usman sakamakon yana da ciwon sugar har aka kwantar
dashi a asibiti, kwanansa d'aya a asibitin yaya haroon yace Aunty Hafsah da Nahnah
su shirya ya kaisu su dubashi.

Bayan sunyi sallar magriba ya d'aukesu suka tafi,


Kasancewarsa babban mutum yasa Asibitin cika da jama'a masu dubiya, a haka dai
suka ratsa cikin d'akin,
Alh Usman yana hango Yaya Haroon ya fara mik'a hannunsa yana kirmishi irin na
mara lafiya, a hankali yaya ya k'ara yasa Hannunshi cikin nasa suka gaisa yana
tambayarshi ya k'arfin jikin, cikin jin ciwo ya amsa, nan su Aunty Hafsah da Nahna
ma suka gaidashi suka mai ya me jiki sannan Duk suka gaida da mutanan d'akin.

Tun shigarsu d'akin Nahnah ta kula da Sweety dake gefan gadon tana share
hawaye, tausayinta ya kamata tasan me take ji tasan k'aunar mahaifi, tasan tsoron
Sweety kar mahaifinsu ya rasu, tana wannan tunanin wayanta tai k'ara alamar ana
kiranta, fita tai daga d'akin don ta samin damar d'agawa,

Tana nan tsaye tana wayan taga fitowar sweety daga d'akin taje can nesa ta zauna
tare da kifa kanta tana kuka sosai.
Bayan ta katse wayan ta zubawa sweety ido tana cike da tausayi, samun kanta tai
da k'arasawa wajanta,a hankali takai hannunta ta dafa bayanta tare da mata sallama,
da sauri ta d'ago kanta tana share idonta, tsugunnawa tai tana magana k'asa k'asa "
kiyi hak'uri ki bar mai kuka, addu'anki yake buk'ata,asannu Allah zai bashi lafiya
kinji."

Gyad'a kai sweety tai tana goge idonta tace"na gode"

"Ba komai naga ne tunda muka shiga d'akin kike kuka zaki karyar mai da zuciya, ki
tamai addu'a,kinga ai jikin nashi ma da sauk'i tunda ance jiya baima San Wanda ke
kansa ba."

Gyad'a kai kawai take don nuna gamsuwa da maganar Nahnah,

Ruk'o hannunta tai tare da cewa"shike nan insha Allah na bar kuka, taso mu koma
d'akin."

Suna shiga yaya Haroon yace" Nahnah mu tafi daman ke muke jira"

Sallama sukai da mutanan d'akin suna k'ara addu'a ga Mara lafiyan.

Tunda Nahna ta dawo gida bata da sukuni duk tausayin Sweety ya kamata duk da
bata Santa ba bata tab'a ganinta ba amma tasan y'ace ga Mara lafiyar, abinda kawai
take tunowa sanda tana sakkoto kafin Baffa ya rasu in bashi da lafiya haka take
zama taita kuka.

*BAYAN* *KWANA* *BIYU*

Ranar jumma'a ne Nahna bata je skul ba don basu da lecture, bayan an sakko
masallaci suna zaune suna cin abinci dasu Ashraf suna shirmansu tana ta dariya,
yaya ya shigo gidan da Sauri yaran sukaje suka tare shi, cikin fara'a tace "Yaya
sannu da zuwa "

"Yauwa sannu Nahna, ina Auntyn tak . . . . ?

"Gani ma na fito, sannu da zuwa,Allah yasa lafiya naganka yanzu?"

Zama yayi yana shafa kansa yace "lafiya qlau wlh, ina sone mu koma dubo Alh
Usman amma ina son ku d'an masa girki ne don naji yace min yana son fatan alkama da
yakuwa da gyad'a, don haka ina son Ku shirya mai zuwa nan da k'arfe hud'u don Allah
sai muje."

Nahna ce ta mik'e tana fad'in "Aunty bari inje in fara had'a kayan girkin"

"Yawwa Nahnah ki had'a harda na darenmu kawai basai mun k'ara yin wani
abincinba kinga"

"Tom Aunty" ta fad'a tana shigewa kitchen d'in.

Yaya kuma ya mik'e yace " Hafsah kawomin abinci inci in d'an kwanta kafin la'asar
d'in".

K'arfe hud'u da rabi suka fito Nahna ta bud'e motan tasa Abincin abaya itama
ta shiga tare dasu Ashraf.
Yau asibitin da sauk'in jama'a y'an dubiya don d'akin daga Aunty murja sai Ummu
sulaim da sweety da wata tsohuwa wadda da gani kasan Maman Alh ce,

Bayan sun gaggaisa da mutan d'akin sukai gaida Alh tare da mai sannu,duk da ma
jikin nashi yau Alhamdulillah yayi sauk'i sosai yana zaune jingine da filow, sweety
ce ta taso da fara'arta ta rik'e hannun Nahnah tana fad'in "k'awata sannu da zuwa"
Mirmishi Nahna tai tace "um munzo ya mai jikin"

"Me jiki Alhamdulillah, Dad itace fa wadda nake fad'a ma ranar da suka zo taga
ina kuka taita rarrashina tana min nasiha".

Da mirmishi kan fuskarsa yace" Ayya sannu kinji y'ar nan, ai tun shekaran jiya
sweety kemin zancenki."

Juyawa yai yana kallon Yaya Haroon yace"Haroon wannan fa ko k'anwar kace?"

Cikin mirmishi Yaya yace "eh autarmu ce Alh aguna take ai"

"Madallah yarinya me hankali,Allah yai miki albarka kinji, ya sunanki?"

Cikin jin kunya Nahna tace "Khadeejah"

" sannu khadeejah"

Nan suka ci gaba da d'an tab'a hira , yaya Haroon yace "Alh, ga faten alkama an
maka ko zaka iya ci"

Cikin fara'a Alh usman yace" Tom na gode Haroon sannunku da k'ok'ari"

Aunty murjah ta mik'e ta d'uko plate da spoon ta zuba mai D'an kad'an don tasan ba
wani ci zaiyi da yawa ba.

Abu kamar wasa ya cinye yace a k'ara mai da yawa ta k'ara mai nan ma ya cinye
tsaf yai gyatsa da godiyar Allah.

Mamaki kowa yai na cin abincin da yai don tunda ya kwanta bai cin wani abin
arzik'i.

Kallon yaya Haroon yai yace "Haroon wannan girkin yamin dad'i sosai na gode da
kai da me girkin duk Allah yai muku albarka."

Cikin jin dad'i Yaya yace"ameen Alh, khadeejah kinji girkin ki yaiwa Alh
dad'i"

Cike da kunya Nahnah ta sunkuyar da kai.

Hajiya Babbah (Babar Alhajin) kallon Sweety tai tace " kinga yarinya me hankali
ta iya girki banda me sai uwar kwalliya da kinibe kika iya."

Turo baki sweety tai tana k'un k'uni na damunta da Hajiyan take.

Shikam Alh kallon Nahna yake da mamakin ta yanda ta iya girki haka kamar babbar
mace gashi da gani nutsuwa ta ratsa yarinyar, lokaci d'aya yaji k'aunar yarinyar ta
shiga ransa.
Y'ar mutan ja'oji ce
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YAN* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / __ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

_HAPPY_ _SALLAH_ _TO_ _ALLS_ _MUSULUM_ _UMMAH_


🎉🎉🎉🎉🎉🎉🎉🎉

0⃣7⃣ 0⃣7⃣

Zumunci ne sosai ya k'ullu tsakanin Nahnah da sweety, kullum sai Nahnah tayiwa Alh
usman Faten alkama ta kai mai asibitin, anan sike zama suyita hira da sweety har
aka sallameshi.

Koda yaushe sweety cikin kiran Nahna take suyi waya tai ta fad'amata"Nahna wlh
kina birgeni kinada hankali. Abbanmu ma kullum sai ya yabeki nutsuwarki da iya
girkinki,Daman a unguwarmu gidanku yake da kullum agidanku zan rink'a yini,"
Haka kullum take fad'i ita kam Nahna sai dai tayi dariya kawai.

Sweety irin emmatan nan ne masu iyayi da surutu, akwai jin kai da iya tsara
kwalliya,bata son harka da tsamaye inka duba duk Wanda sweety ke harka dashi tofa
gaye ne in mace ce sai babbar yarinya wadda ta amsa sunan had'ad'd'iya me aji,amma
duk da haka in kikayi mata taji kin shiga ranta to zatai k'awance da Kai.

Yau ranar Saturday ne sweety taiwa Nahna waya kan zata to gidansu, don haka da
wuri Nahna ta tashi ta shirya mata kayan motsa baki sannan tai wanka tai kwalliya
cikin d'inkin doguwar riga na material fari da adon bak'i tasa d'an kwali bak'i
akanta,kasancewar bata iya zama ba d'an kwali akanta koda cikin gida take, bayan
ta kintsa gidan taiwa su Ashraf wanka suma ta shiryasu ciki kwalliya.

Tana zaune tana chart da wayarta kiran Sweety ya shigo, da murmishi kan fuskarta
ta d'auka" Assalamu Alaikum"

"Hello my Nahna gani a akan layin naku kizo ki tafi dani."

"To gani nan d'an jirani kad'an."

D'akin Aunty ta shiga ta shaida mata zata je ta taho da sweety a k'ofar layin,
Sannan ta koma d'akin ta d'auko mayafinta ta kama hannun ashraf suka fito.

A hankali cike da nutsuwa take taka k'afanta tana tafiya.

Sweety kuwa tana zaune cikin motanta take hango tahowan Nahnah, d'an mirmishi tai
aranta take fad'in"Gaskiya Khadeejah aji ce tanada nutsuwa komai nata cikin sanyi
yake natural ce.

Nahnah tana tafiya a hankali tazo gota motan Sweety taji ance
" my Nahna"

Da sauri ta kalli gun, mirmishi tayi tana fad'in"daman kece cikin motan?"

"Tom zagayo mana mu k"arasa" sweety ta fad'a tana bud'e Mata murfin motan.

Tafiya kad'ance ta sadasu da gidan tunda daman duk cikin layin suke,fitowa Nahna
tai ta bud'e d'an madaidaicin gate d'in nasu yayinda Sweety ta shigo da motan tai
parking d'inta suka k'arasa cikin gidan.

Da sallama suka shiga parlourn Aunty ta amsa musu fuskanta d'auke da fara'a
tanaiwa Sweety sannu da zuwa,itama cikin girmamawa ta gaida Auntyn sannan ta zauna
suma su Ashraf suka gaidata.

cikin fara'a Nahnah tace sannu da zuwa,yau dai gaki gidanmu ko.

Hararan wasa ta wurga mata tace"eh ni nazo gidanku saura kuma kema kizo gidanmu
wani week d'in."

Mirmishi kawai Nahnah tai ta shige kitchen don kawo mata abubuwan motsa baki.

Hira sosai suke don Aunty ta basu waje sannan yaran ma duk sun shiga d'akinsu,
don sun saba indai anyi bak'i basa zama gun parlour.

Sweety kasancewarta wayayyiya yasa ta saki jikinta ta sha lemon da aka kawo mata
tare da cincin.

Ganin lokacin d'ora girkin rana yayi yasa Aunty fitowa da niyar shiga kitchen
tunda mai girkin tanada Bak'uwa, da sauri Nahna tace

" Aunty me zakiyi a kitchen? badai girki zaki d'ora ba."

"Eh yau na huttasheki kinada bak'uwa ki kula da ita kawai."


"A'a Aunty ki barshi zanyi sweety ba matsala bace zansa mata kujera a kitchen
d'in inayi muna hira ko tawan"

Ta fad'a tana kallon sweety,

Ita d'inma dariya tayi tace"Eh Aunty ki barshi zan tayata sai
In koya nima."

" y'ar dariya Aunty tai tace" To kuyi ba damuwa,ke Nahna saiki tambayeta abinda
take sonci Ku dafa."

"OK Aunty ba matsala."

Tare suka shiga kitchen d'in da sweety tana aikin suna hira yayinda take d'an
taimaka mata da irin yankan su albasa da b'are magi, girkin ba mai Wahla sosai bane
don sweety ca tai danbun cuos cuos take so, don haka nan da nan suka gama had'a
komai, zuwa awa guda har ta zubashi a cikin food flask.

Har zasu fito a kitchen d'in Nahna tace"sweety ko kina shan lemon kwakwa muyi?"

"Yawwa tawan kamar kin san shine best d'ina cikin drink's, amma kina ganin bashi
da wahla bazai gajiyar dake ba."

"Hhhhhmmm,kedai je parlour ki huta ko ki shiga d'akina don na lura kin gaji


sosai."

"A'a ban gaji ba ni wallahi dad'in aikinma nakeji ,daman ina Girki a gidanmu don
ina son inga na iya abubuwan girki da yawa.

"Hhhmmm karki damu zaki iya kinji k'awa ta, yanzu dai zo muyi lemon da sauri mu
gama.

Nan da nan suka shirya leman suka jefa k'ank'ara,lokacin k'arfe biyu tayi,don
haka suka shige d'aki don yin Sallah,suna shiga d'akin Sweety ta fad'a gadon ta
kwanta tana fad'in " Wasshhhh,my besty na gaji sosai wlh, ashe haka masuyin aiki
suke jin gajiya in sun gama".

D'an dariya Nahnah tai tace"kefa kika ce dad'in aikin kikeji,shiyasa tunda farko
nace ki zauna".

"Hhhhhmmmm wlh da mukeyin aikin ban gaji ba sai yanzu".

Jinjina kai Nahnah tai tana mamakin D'an aikin da Sweety tayi amma har zatace ta
gaji,gaskiya wasu y'ay'an masu kud'in sai a hankali.

A fili dariya tayi tace " To ko ruwan zafi zan had'a miki ki d'an gasa jikinki
sai kiji dai dai".

" To d'an had'amin, don naji bayana har ya rik'e".

Ruwa me d'umi ta had'a mata sannan ta fito ta mik'a mata towel.

Bayan ta shiga wankan Nahna ta tada sallah,

Tsawon 10 minutes Sweety ta fito d'aure da towel tana tsamtsame jikinta, Cikin
kirmishi Nahnah ta kalleta tace "Ki bud'e Woodrow ki zab'i kaya ko".
"A'a ki d'auko min da kanki, don ban san inyi wanka in maida kayan dana cire ne
da bazanma canja ba".

Mik'ewa Nahna tai ta d'auko mata wata doguwar riga me matuk'ar kyau,

"Woww Nahnah wannan riganfa yayimin kyau sosai wlh,inada irinshi amma nawa ba
kalan wannan bane, nawa copy color ne, wannan Orange colour d'in yafi kyau
gaskiya".

"Hmmmm in kina so ki rik'e na baki duka".

D'an zaro ido tai tace" da gaske ki barmin"?

"Eh da gaske mana Sweety".

"Kai gaskiya Nahnah kinada kirki sosai wlh, na gode kinji, kuma kin San wani Abu
wlh don ina k'aunanki ne fa har nace miki tayi kyau don ni bana kulawa da abinda
mutum yake dashi balle in yaba mai kin San rainin hankalin mutane yanzu saisu
rainaka, ke kuwa me hankali ce baki da matsala don haka kika shiga raina sosai, na
gode kinji Nahnah".

Mirmishi ta k'arayi tace "sweety nice da godiya kinji".

A haka suka gama shiryawa suka fito don cin abinci, bajewa sweety tai kamar a
gidansu take ta kwashi girkin nan ta kora da lemo.

Sai daf da magriba ta tafi tana k'ara fad'awa Nahnah tana jiranta itama ta kawo
mata ziyara, ita dai mirmishi kawai take.

Tun daga lokacin Zumuncinsu ya k'ara k'arfi, duk da Nahnah bata tab'a zuwa
gidansu sweety ba amma tabbas tasan y'ar hamshak'i ce daga yanda yaya yake bata
labari zuwa yanayin d'abiunta ta shaida hakan,gashi tana ganin yanda take hawa
motoci na kece raini, hakan yasa Nahnah baya baya don tsira da mutuncinta, dukda
yawan zuwa gidansu da sweety take ita kam tak'i zuwa nasu gidan, kullum in ta
dameta da mita sai tace tai hak'uri zata zo.

**********
Yau Nahnah ta kaiwa sweety ziyara inda taga abinda ya girmi tunaninta don
gidane na alfarma agun, ko motoci sun kai 15 a gidan, abinda ya k'ara bata mamaki
yawon maa'katan dake gidan haka suka rink'a zuwa suna gaidata kamar wata matar
sarki, haka Auntyn su Sweety taketa ina taka saka da ita, da sauran k'annenta su
haris, na yanda Nahnah taso awa biyu zuwa uku zatai a gidan ta tafi amma Sweety ta
k'ek'ashe k'asa tace saita yini don itama in taje gidansu yini cur takeyi,
Haka badan taso ba ta zauna.

Kiran Abbansu sweety tai tayi a waya tana fad'a mishi Nahnah tazo ya dawo da wuri
su gaisa.

Suna zaune a parlour sunata hira wata y'ar aiki ta shigo da kayan fruit yankakku
tazo ta ajiye gaban Nahnah ta juya zata fita wata uwar tsawa sweety ta buga
mata"keee jaka mahaukaciya, haka ake ajiye abu gaban mutane".

Jiki na rawa ta dawo ta k'ara gyarawa bowel d"in zama kan center table d'in.

Wani kallo Nahnah tabi Sweety dashi na rashin jin dad'in abinda tayi, ta kalli
y'ar aikin tace "jeki abinki".
Bayan fitar ta sweety tace"Nahnah ya naga kin canja fuska haka?.

" gaskiya banji dad'in abinda kikai mata ba, ai d'an Adam ba abin wulak'antawa
bane, dukda tana aiki k'ark'ashinku kinci zarafinta wlh".

Ta k'arashe maganar cikin yanayin b'acin rai,

"Hhhmmm Nahnah biki san way'annan y'an aikinba,basu da nutsuwa ko kad'an".

"Duk rashin nutsuwarsu basu can canci dizgi irin haka ba, tunda har Allah ya
karrama d'an Adam ya dace muma mu karrama kanmu mu girmama junanmu, gaskiya sweety
in har kina son mu shirya dake karki k'ara irin haka ba kyau irin hakan kinji".

Jin jina kai tai tare da fad'in "shikenan na daina Nahnah".

Cike da mirmishin farin ciki tace"yawwa my Sweety na gode da fahimtata da kikai".

Daga nan suka shiga wani zancen har Abbah ya dawo suka gaisa da Nahnah yaita sa
mata albarka don shima zuciyansa na matuk'ar k'aunar Nahnah.

Da yamma Sweety ta dawo da ita gida a motanta, tare da tarin kayan kwalliya da
turaruka Wanda ta had'a mata,sannan Auntynsu ta bata tirmin atamfa da wani less
d'an ubansu da mayafi, sannan Abbah ya bata 20k Wanda tak'i amsa Sweety kuwa tasa
mata cikin jakanta bata Sani ba, saida tazo gida ta gani. ta d'auka ta
kaiwa Yaya Haroon wai ya mayarwa Abban sweety ita bazata amsa ba, yaya yace " a'a
ba haka za'aiba don Alh, baya son yayiwa mutum kyauta yak'i karb'a".

Don haka ya kirashi a waya yamai godiya, sannan ya bawa Aunty Hafsa kud'in yace ta
ajiyewa Nahnah in tana buk'atan siyan wani saita bata.

Nahnah tai shiru can tace" yaya ba abinda zan buk'ata dasu,ka d'auki " 15k,ka
bawa Aunty 5k".

Mirmishi yaya yai yana jin dad'in hankali da nutsuwa irinta Nahnah khadijah
autar Baffah.😀

K'irgo 5k Yayi ya mik'awa Aunty Hafsa,sannan ya k'ara k'irgo wata 5k d'in ya


mik'awa Nahnah yace "to rik'e wannan a hannunki, karkice komai daga haka".

Badan zatai wani abu dasu ba amsa.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji.
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*
_DEDICATED_ _TO_ _ALL_
_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣8⃣ 0⃣8⃣

Haka rayuwa taci gaba da garawa, lokaci yai nisa, Nahnah sun cinye semester sunyi
exam har sunje tak'aitaccen hutu sun wuce T.P, nan wata secondary skul ta maza dake
bayan gidansu taje, duk da taso zuwa ta bawa makarantarsu ta bada gudummawa, amma
yaya ya bata shawaran taje wannan d'in,tunda itama Arabic skl ce, bata ja kan
maganar yaya don haka kai tsaye ta zab'i wannan d'in, duk da tarin tsoron koyar da
mazan da takeyi.

Ga duk Wanda yasan yanayin koyar da d'alibai maza zataga yasha bamban dana
mata, duk iya shegen d'aliba mace tanayiwa malami ne bayan idonshi kama daga sawa
malami suna yimai izgila, gwada irin tafiyarshi ko yanayin koyarwarshi, kaikwayen
maganarsa da duk irin wannan iskanci d'aliba mace tanaiwa malami ne bayan idonsa,
amma d'alibi namiji inka bari ta had'oka dashi zaka ga tijara mabanbanta.

Kashi ne da wulak'anta babba ga malami yaje koyarwa bai san me zai koyar da
d'alibi bai San ina ya nufa ba, ma'ana dai ya zama garmaho yaita Kame kame gaban
d'alibai, wannan ba k'aramin kaskanci take jawa malami gaban d'alibi ba.

Duk irin wannan matsalolin malamansu sun nusar dasu kafin tafiyarsu, don haka
Nahna tun kan tafiyarta (T.P) ta shiryawa kanta rayuwar da zatai don kaucewa duk
wata matsala.

S.S 1 aka bata da J.S 2 zata rink'a musu Qur'an da tajweed, sannan tai musu
Hadith da musd'alahul Hadith,
Sukuma J.S 2 tai musu Qur'an da fiqihu,

Duka course ne masu zafi wajen koyarwa, don haka ta dage wajen bincike (‫ )بحث‬don
harkar koyarwa tana buk'atar malami ya Zama kullum cikin bincike, musamman data
lura da wani abu tun ranar da sukaje za'a k'addamar dasu gaban d'alibai, malami na
farko yaje zai gabatar da kansa ya farayi da Hausa taga wani gani gani da sukeyi
mai suna dariya, To na biyu da yake malamin English ne sai yai da turanci, haka
akaitayi wani yai da Hausa wani da turanci, don haka tasa aranta da Arabic d'inta
zatayi duk kuwa da taga d'aya namijin d'an Department d'insu ne na Arabic amma yai
da turanci don a tunaninsa zaifi birgewa, ita kam ana zuwa kanta, bayan tai sallama
tai gaisuwa ga malamai ta fara gabatar da kanta cikin harshen larabci, Wanda yaja
hankalin d'alibai da malaman, kai tsaye kowa ya gane wace ita da kuma girmama
harshen da take koya kuma zata koyar, tun anan ta gane abubuwa da dama don haka ta
dage wajan karrama larabci.

Tana jin dad'in koyarwar sosai,don bata fuskantar wata matsala bangaren karatu
tsakaninta da d'aliban, sai dai abinda ba'a rasa ba.

D'alibai zama dasu saida taka tsantsan musamman maza, wani sa'in tana musu karatu
tana ji zasu rink'a gulmar wasu malaman suna zaginsu, ita kanta tasan bata tsira ba
dukda girmamata da sukeyi, amma wani lokacin tana kula da d'an iskancin da sukeyi
tasan da ita suke.

Tunda ta fara zuwa da hijab take zuwa, yau kam tai sha'awar saka mayafi, tai
kwalliyanta tasa mayafinta na kirki, Tana shiga skul d'in daga bakin gate taga
yanda d'aliban ke kallonta,amma bata damu ba ta wuce staff room d'insu, lokacin
shigarta aji yanayi ta tashi zuwa ajin, amma tana shiga sai taga d'aliban sun juya
suna kallon wani d'alibi tare damai dariya, suna magana k'asa k'asa, kasancewar
bamai shiga sabgar d'alibi bace damusu shishshigi cikin lamuransu yasa bata tsaya
tambayarsu meke faruwa ba ta shiga yin abinda taje yi.

Tun daga ranar ta fuskanci data shiga ajin zataga suna kallon Hasheem suna
dariya da k'us k'us, don haka ta gano wani abu,amma saita basa.

Wata rana an tashi tana tsaye bakin gate tana jiran wata malama dasuke T.P d'in
tare yar layinsu ce, daga bayanta taji hiran da suke Wanda su Sam basu ma lura da
ita ba, don gun a cakud'e yake d'alibai,

"Kai Yusuf wlh Allah da gaske Hasheem son malama khadeejah yake, don gashi yace
yanzu har kasa bacci yake sabida tunaninta".

"He heeeeee jimin d'an iska kai yanzu malamar taka kake so"?

"To bazai sota ba akwai haramci aciki ne"

"Hheee heeee, ba haramci amma akwai iskanci, d'alibi yace yana son malamarsa"

"Wlh ba wani iskanci, ko a girme dai nasan Hasheem ya girmeta kawai don dai
karatu yamai gardama ne,amma ko yanzu yaje k'ofar gidansu zance fitowa zatai"

"Hhhmmm wlh ni ko abinda ke birgeni da malamar dad'in muryarta, kanaji fa in tana


mana karatu Qur'ani kamar balarabiya, kawai sai inji wani shauk'i ya kamani,ga
idanuwanta kalan love shiyasa nake surutu in tana karatu data d'ago tamin kallon
nan na kai shiru sai inga kamar kallon k'auna ne".

Ihu sosai sukasa suna k'yalk"gala dariya,

"Kai dallah kuzo mu wuce wannan gayan bazai fito ba".

Haka suka wuce suna ci gaba da hiram ba tare da sun San da ita a gunba.

Kunya, fargaba, b'acin rai suka bai baye Nahna taji inama bata tsaya gunba, wane
b'acin raine wannan ace d'alibinka yace yana sonka,🤔 inama batazo wannan
makarantar ba inama inama.

Tanata wannan nazarin Malama ummi ta taho suka tafi, Sam bata malama ummi bata
lura da yanayin da take ciki ba,don haka taketa janta da hira, ita kam sai dai tace
um da um um, a haka har suka k'arasa layin nasu kowa ya shige gida.
Tun daga ranar tsakanin Nahnah da d'alibanta sai d'aure fuska yanda take sakar
musu tayi musu karatu cikin raha duk ta rage, don haka sukasha Jinin jikinsu suka
kama Kansu, ahaka har suka cinye watannin da zasuyi a T.P suka fara shirye shiryen
komawa skl su k'arasa semester guda data rage musu.

****************
B'an garan dangantakarsu da sweaty sai abinda yai gaba don yanzu sun
k'ara k'ullewa sun zama Aminan juna, sweety tana cin ribar zama da Nahnah sosai
don Nahnah bata barin sweety tayi wani abu ba dai dai ba saita nuna mata rashin
dacewar hakan, zamanta da ita gashi tana k'ara fahimtar da ita kan abinda ya shafi
addini musamman b'angaran fiqihu, don haka sweety take k'ara ganin girman Nahna da
k'imarta.

*************
B'angaran samari kuwa Nahna bamai ra'ayinsu bace, bata bawa ko wane
saurayi dama akanta don haka duk layinsu suke mata kallon me girman kan tsiya, har
wasu na fad'in kwad'ayi da son abin duniya ke sata wulak'antasu ,shiyasa ma ko
k'awaye bata dasu sai y'ay'an masu kud'i irinsu sweety take kulawa.

Duka zantuttukansu basa damunta, ita dai bata shiga sabgarsu, don tasan ita bamai
kwad'ayi bace kamar yanda suke fad'a yayanta ya tsare mata komai na rayuwa, dukda
bai zama me kud'i ba amma me tarin rufin asiri ne.

*TAB* ' *D'I* *JAN* 🤔.


Rana ta farko da Nahna ta gane UK yayan sweety ne taji ba dad'i matuk'a don
bata so wani abu ya k'ara had'ata da UK koda kuwa hanya ce, tasa aranta tunda yabar
skl d'insu tsawon shekara biyu to bazasu k'ara had'uwa ba, amma me yau taji abunda
ya kawar mata da farin cikinta kai tsaye.

Tun had'uwar Nahna da sweety takejin labarin Broth Dady a bakin ta, kullum
hiranta saita saka da broth d'inta don shak'uwace me tsanani a tsakanin Sweety da
D'an uwanta ko Auntynta ummu sulaim da take mace basu shak'u da itaba kamar broth
Dady,Don haka tasanshi sosai a bakin sweety, kasancewar yana k'asar waje yaje yin
course na shekara biyu yasa basu tab'a had'uwa na, ko a photo bata tab'a ganinsa ba
don ita bamai bincike bace a wayar mutane dukda yanda suke da sweety bata tab'a
d'aukan wayanta ta kalli pic's ba musamman data lura komai na wayanta akwai cord
akai, sannan tasha cemata zata had'a had'ata dashi a waya su gaisa amma saita nok'e
don bata son tura kai inda Allah bai kaita ba, sannan bata tab'a shiga main parlour
d'insu ba, kullum ta k'aramin parlour take shiga ta wuce d'akin sweety, hakan yasa
bata tab'a cin karo da pic d'insa ba.

Yau kam tana zuwa gidan don dubata batada da lafiya su haris sukace mata sweety
na babban parlour, don haka ta tsaya ta kirata a waya tace tana k'aramin parlour
tana jiranta, kai tsaye ta fito tana fad'in
"daman zakizo da gaske, ke kamar bak'uwa sai ki rink'a wani abu"

Murmishi Nahna tai batace komai ba suka shiga parlourn, inda Nahna taga abinda ya
girmi rayuwarta wato kansa girmansa abin Jan hankali ne balle tsaruwarsa,

Basarwa Nanha tai ta samu waje ta zauna tana gaida Aunty murja da Abbansu suka
amsa, tace yamai jiki suka amsa da sauk'i, Abbah yace" kinga tun d'azu ake fama
taci abinci tak'i don haka ma na dawo daga office amma tak'ici"

Kallonta Nahna tai tad'an harareta tace "ke sai kace wata yarinya aita fama dake
kici abinci kik'i bari in tafi gidama tun kafin ki b'ata min rai".

Da sauri ta rik'e hannunta tana marai recewa "kai my Nahna don Allah karki tafi
ni abincin ne banso ko zakimin wannan abin da kikai min agidanku rannan".

"Um zan miki taso muje kitchen d'in naku".

Dariya tasa tana fad'in " yawwa dear na gode, Abbah bari yanzu zakaga naci
abincin da yawa".

Suna zuwa kitchen d'in tacewa sweety "d'auko eggs guda biyar ki d'ebo dankalin
Hausa guda biyu madai daita ki kawo taruhu guda biyu manya da albasa babba guda
d'aya da magi".

Kafin minti ashirin harta gama, palourn suka dawo ta zauna ta cinye tsaf tasha
magani,nan Abbah yai tasawa Nahna albarka yana ta mata godiya, itakam Nahna har
kunya ta kamata tacewa sweety "mu koma d'akinki"

Tashin datai zasu fita idonta ya fad'a kan k'aton pic d'in dake mak'ale a saman
k'ofar fita, dam taji gabanta ya fad'i don bazata tab'a manta wannan fuskarba har
abada kuwa.

Jitai kanta na juyawa da k'yar ta k'arasa d'akin, zuciyarta cike da tunanin me


had'in UK da gidan nan harda akasa pic d'insa a gidan.

Sweety ta kula da canjawar Nahna don haka tace " yadai dear naga kinyi wani
iri?"

Basarwa tai tace "a'a ba wani abu kaina naji yad'an Sara min amma normal ne".

Hira suke d'an tab'awa Nanah ta soko zancan "Sweety naga pic d'in wani a k'ofan
fita a parlour d'inku wane ne"

" wai bikisan waye ba? Broth Dady nefa, bari in nuna miki a wayana ki gani,
daman tun zamanmu biki tab'a ganin pic d'insa cikin wayana ba? ai broth d'ina
babban yaro ne hands some guy"

Mik'o mata wayan tai tana fad'in "kalli kiga duka wannan folder d'in pic d'insa
ne, ina zuwa bari in d'an watsa ruwa ko jikin ya k'aramin k'arfi".

Ina! Ai Nahnah batama jin me sweety ke fad'i don hankalinta duka ya koma kan
photon.. . . .
Takuce
Y'ar mutan Ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣9⃣ 0⃣9⃣

Nahna sosai hankalinta ya tashi, taji lokaci guda ranta ya b'aci tai danasanin
mu'amala da Sweety, domin da tasan k'anwar UK ce da batai gangancin k'awance da ita
ba, pic's d'inshi sun kai 70 cikin folder d'in, wani shi d'aya wani shida ita wani
da duk y'an gidan nasu, wani da friend d'insa, gasu nan dai tari guda bata iya ko
kallan goma ciki ba ta runtse idonta tana karanta "Innalillahi wa'inna ilaihi
ra'jiun"

A hankali nutsuwa tazo mata ta daidaita tunaninta jin sweety na k'ok'arin fiowa
a toilet d'in,
" My Nahna kinga broth d'ina ko,had'ad'd'an gaye ne fa, babban yaro Wanda
duniya ke yayi, baya harka da tsamaye komai nashi a tsari yake, classes guy ne fa".

Saida takai aya Nahna cikin basarwa irin tata tace" ya Allah! dear wannan irin
yabo haka kin dage kinata wasa D'an uwanki haka ".

Sosai sweety ta kalli Nahna sannan ta zauna bisa stool tana pacing d'inta tace"
Khadeejah ! Ina son broth d'ina, ina ji dashi matuk'a,kamar yanda yake matuk'ar
sona, broth d'ina ya girmemin sosai amma hakan baisa ya nuna son girmanshi akaina,
bashida abokin hira kamarni, dukkan abinda nake so yana sonshi, don haka nakeyinsa
matuk'a, b'angaran had'uwa yaya na k'arshe ne, aji ne shi, tun ina k'arama yake
koya min yanda yakeso inyi rayuwa ta gayu ,yana son inyi mu'amala da gayu don bai
son k'aramar harka, hhhhhmmm bari kawai Nahna ina ji da broth".

" hhhhmmm Sweety me broth".

Juyawa tai taci gaba da shirya kanta gaban mudubin tana fad'in " Khadeejah dama
dama dama zaki amincewa buk'atata ki yarda da soyayyar d'an uwana, tun tuni nake
sha'awar had'aki da shi matsayin masoya, Nahna ina sonki ina son ki auri broth
d'ina don Allah".

Cikin wani tashin hankali Nahna ta dubi Sweety idanuwanta duka a waje tace "
a'a bari sweety banson wannan maganar, don Allah karma ki soma wlh, babu wata
alak'a tsakanina dashi ta arzik'i balle har aure, gaskiya ban son irin haka karki
k'ara min irin wannan maganar".

Mik'ewa tsaye tai fuskanta babu alaman rahma don ranta a b'ace yake ta d'auki
jakanta tace " zan wuce gida Allah ya k'ara miki lafiya me d'orewa".

Mamaki ne k'arara akan fuskan sweety don ita bataga abunda ya d'agawa Nahna
hankali haka ba,

Rik'eta tai da k'arfi tana fad'in " haba khadeejah me yai zafi haka cikin zance na
harda ya d'aga miki hankali haka,cool down Nahna mana. . ."

Tattaro nutsuwarta tai ta d'an sassauta fuskanta tare da fad'in" ba wani abu
sweety kawai banson wani maganan soyayya ne yanzu cikin rayuwa ta".

Ajiyan zuciya me k'arfi sweety ta saki " To don Allah kiyi hak'uri ban son ranki
zai b'aci ba amma insha Allah bazan k'ara miki maganan nan ba kinji".

"OK ba damuwa, zan wuce gida ".

Bata jira me zata k'ara cewa ba tasa kai ta fice, ba tare data jirata ba don tai
mata rakiya.

*********
Zuciya a cushe Nahna taje gida, don tsohon tsimin da UK ya dasa mata a
zuciya yau kam ya tashi, duk duniya babu mutumin daya wulak'antata ya tozartata
sama da UK , ya cusgunawa rayuwarta matuk'a ya b'ata mata rai ganin UK bai tab'a
zama alkairi a gareta, duk sa'in da zasu had'u saiya wulak'antata ganan mutane,
shin yaushe ne zuciyarta zata daina ganin bak'in UK, amma wai har Sweety take
k'ok'arin had'ata dashi, to ko maza sun k'are me zatai dashi mutumin dabai San
darajar d'an Adam ba.

Haka ta yini ranar zuciyarta a damule har Aunty Hafsa ta ganota, amma data
tambayeta meya faru sai tace kanta ne ke ciwo daga haka ta wuce d'akinta ta kwanta.

*********
Can gidansu sweety kuwa ta cika da mamaki matuk'a don bata tab'a ganin Nahna
cikin makamancin yanayin ba, ta San Nahna Me sanyi ce da taushin hali ba abu
k'arami kesa kaga fishinta ba,amma daga cewa zata had'ata da broth d'inta sai ta
b'ata rai haka.
************
Bangaran Abbah kuwa bayan fitar Sweety da Nahna daga parlour ya dubi
Aunty Murjah yace " murjah wani abu ne yake min yawo arai dangane da yarinyar nan
Khadeejah, tun randa na fara ganinta a asibiti naji yarinyar ta burgeni matuk'a
nutsuwarta, kamun kanta, yarinyar tanada hankali sosai, don haka murjah nake ganin
da zan samu yanda nake so da na had'ata da Daddy na, ko me kike gani".

Dogon numfashi Taja tana tunanin felek'e irin na Dady,donshi d'an k'yale k'yale
ne komai bai son inba Wanda mutane zasuce yes ba, don haka tana tunanin bazai
amince da tayin Abbansa ba. .. . . .

Katseta yai da fad'in "ya kikai shiru murjah ko da Matsala ne"?

"A'a Alh. daman ina tunanin Dady ne, baka tunanin zaik'i amincewa? Kuma itama
yarinyar baka tunanin ko tanada Wanda take so?"

Shafa kansa yai a hankali yana wani d'an tunani zuwa jimawa yace" duka wannan
matsalar baza'a rasa ba amma babbar matsalar ace yarinyar nada Wanda zata aura,
amma donta Dady ko baiso sai ya aureta hak'ik'a amma zanyi dogon nazari tukun,don
matuk'a ina k'aunar yarinyar nan wlh zanso ta zama cikin zuri'ata da yardar Allah".

Ajiyan zuciya tai tace "To Allah ya tabbatar da abinda yake alkairi".

********

Da gasken gaske Abbah kejin wannan had'in da yakesonyi cikin zuciyarsa duk da yasan
waye d'anshi, yasan Dady da abinda yake so, yasan Nahna bazata zamo daga cikin
zab'insa ba tunda ita ba babbar yarinya bace me yafa mayafi iya wuya, ita ba y'ar
shahararran me kud'i bace yar masu rufin asiri ce kuma masu wadatar zuci, amma
bazai karaya ba yanzu dagewa zaiyi da k'ulla alak'a fiye da da tsakaninsa da Yaya
Haroon har yakai ga gaci, don yana hango alkairi matuk'a tsakanin d'ansa da Nahna
tunda yasan d'ansa ba wani nutsuwa ce dashi ba amma yasan da yardar Allah Nahna
zata zamo fitila gareshi.

******
Bayan kwana biyu Sweety tanata kiran wayar Nahna amma duk sai tajita a kashe
tana son ta k'ara bata hak'uri duk da tana ganin rashin takamaiman abinda yasa
Nahna fishi amma dai itace sila don haka ya dace ta nemeta, gashi wayanta bata
shiga don haka ta shirya zuwa gidansu ta k'ara bata hak'uri.

Taku ce
Yar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸
*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

AYIMIN AFUWA READERS 🙏,WLH TYPING NE BA DAD'I INA SON YIN POSTING KULLUM AMMA BA
DAMA SABIDA YANAYIN ABUBUWA😀
KUDAI GANE KAWAI READERS.

INA GODIYA DA K'WARIN GWIWARKU GARENI Y'AN GROUP D'IN Y'AN ARABIC ,KARKU DAMU
ZAKURINKA JINA AKA-AKAI INSHA ALLAH.

0⃣1⃣0⃣ 0⃣1⃣0⃣

A yanda Sweety taga Nahna ta tareta ba wani damuwa akan fuskanta, cikin fara'a da
murna kamar yanda ta saba kullum,bayan sun gaisa da Aunty Hafsa suka shige d'akin
ta.

"Nahna manya, kin tafi da fishi kuma kin kashe wayanki don karma in kira ko".

"Hhhhmmm ban kashe waya don keba, kawai ina son in huta 2 day's shine na
ajiyeta".

Kallonta tai sosai tana d'an mirmishi tace "To nidai zuwa nai in k'ara bada
hak'uri don Allah, ban San maganata zata b'ata ranki ba".

"Karki damu ya wuce, daman ni batun soyayya ne kawai banso".

" hhhhhmmm Nikam sai nake ganin kamar da matsala akan wannan ra'ayin naki, don kuwa
farin cikin rayuwa baya cika saida soyayya".
Cikin basar da zancen tace " kin tsareni da surutu ko ya jiki ban k'ara miki ba,
ina fatan dai kin warke sosai".

"Tunda kika ga na fito ai na warke".

Cikin tsokana Nahna tace " a'a kefa k'afar yawo ce ko biki warke ba in ya motsa
miki sai kin fito".

Dukan wasa ta kaimata tana cewa "ji sharri nice k'afar yawon, wlh in ba skl ba da
nan gidan da gidan Aunty sulaim sai inyi wata nawa banje ko inaba, ko friends
d'ina suke zuwa gidanmu in sun matsu, sun gama k'orafinsu kaina sun gaji, ke d'inma
don ta dabance yasa kullum nake zuwa gidanku tunda ko ba komai za'a k'aramin
karatu".

"Tom na gode emmata da zuwa gidanmu da akeyi".

Dariya sukai , sannan suka shiga wani hiran.

B'angare guda na raina kuwa na riga da na gama tsara rayuwata dangane da mu'amalata
da sweety da ma gidansu gaba d'aya, dole zan rage alak'ar dake tsakaninmu, zan
janye musu sosai kuwa, sabida naji tana fad'in shekara biyu zaiyi a can k'asar kuma
yanzu yayi shekara d'aya da watanni, don haka kafin ya dawo mun raba. hanya ma
dasu tunda dama sweety ke shigemin ita ta dage ta k'ulla k'awance dani tun ina
yakicewa har muka shak'u, sabida haka zan sake sabon taku, don nasan duk randa UK
ya dawo ya ganni a gidansu to Allah kad'ai yasan kuma tozarcin da zaimin, don haka
kafin akai ga jallin ma k'ara inyi gefe.

Itakuwa b'angaran sweety tana kan bakarta na son had'a wannan soyayya, tunda dai
Nahna ta nuna mata bawai d'an uwan nata ne bata soba a'a soyayyarce duka bata
miradin farawa a yanzu, to zatabi duk hanyar da zatabi ta rink'a tausar Nahnan a
hankali har ta janye ra'ayinta daga nan saita dawo mata da zancen d'an uwan nata.

*********
Kwatsam Yaya yaji kiran Alh usman yana shaida mai ya shirya wannan shekaran yana
cikin way'anda ya biyawa aikin hajji,

Wayyo Allah ina yaya zayyi don murna, ba shiri sai gashi yayo gida ya taremu
da wannan abin farin cikin, nan muma muka rink'a murna dasa albarka, nan muka shiga
sanar da y'an uwanmu na sakkoto suma sukaita murna dasa albarka. Har gida mukaje
mukaiwa Abban sweety godiya na wannan alheri dayaimana.

Shirye-shirye duk sun gama kankama na tafiyan yaya don muna sa ran ko wace rana
za'a iya kiransu.

Duk wani guziri dame gida ke barwa gidansa in zaiyi tafiya irin wannan ta aikin
hajji Abban sweety shi ya mana mai makon yaya, kama daga kan kayan abinci kayan
masarufi har zuwa kan kud'in da zai bar mana Wanda zamu rik'e hannunmu, duk iya
yanda yaya yai wajan nuna mai ya barshi yana da isassun kud'in da zai barmana komai
amma Alh,usman d'in ya nuna ba komai ai duk cikin neman lada yake.

Yaya bai son me zai k'ara ajiye mana ba don komai ya wadacemu don haka kawai ya
bar mana ATM CARD d'insa duk sanda wani abu ya taso mu ciri kud'i cikin account
d'insa.

Bayan kwana biyu su yaya suka tashi zuwa k'asa me tsarki, ya barmu da tarin
kewarsa.
Wanda tafiyar sunkai su ashirin k'ark'ashin jagoranci Abban sweety kama daga y'an
uwansa na matarsa da ma'aikatansa da kuma shi, wanda duk shekara dama shi ba fashi,
iyalan gidansa kuwa babu Wanda bai tab'a zuwa ba don sweety ma tacemin sai biyu
taje aikin hajji ummara ma sau biyu.

Tun tafiyar yaya sai gidan yai mana fayau don yaya mutum ne mai sauke hak'k'in
iyalinsa, koda yaushe in yana gida zai kasance tare damu ana hira da wasa da
dariya, wata rana yajani mu had'ewa Aunty Hafsa kai muyita tsokanarta,wata rana
kuma ni da ita muke had'e mai kai mu tsokaneshi iya son ranmu, yaya yaci abinci
kwano d'aya damu ya nemu shawararmu kan al'amuransa na office dana kasuwa, ba Aunty
Hafsa da take matarsa ba harni da nake k'anwarsa nayi kewarsa matuk'a hakama
yaransa su Asharaf kullum cikin maganar Daddynsu suke, ahaka har muka saba da
kewarsa.

Ana saura kwana uku sallah aka kawo mana sanmu na layya daga gidansu sweety don
harshi abbansu ya d'auki nauyi kawo mana,amma duk da haka yaya ya siya mana k'aton
rago mai makon sa da rago da yake yankawa.

Ranar sallah bayan mun dawo idi mahaucin dake mana fid'a yazo ya yanka mana sanmu
da rago muka rabashi gida uku muka shigar da kaso d'aya gida, sannan kaso d'aya
muka rarraba kyauta zuwa gidan abokan yaya da dangin Aunty Hafsa, kaso d'aya mukai
sadaka ga marasa k'arfi kamar yanda addini ya tanadar.

Duk yanda sweety take son inje gidansu nak'i, tsakanina da ita sai waya wayarma
wani sa'in kashewa nake don karta dameni, in tazo gidanmu kuma zai amshe da fara'a
kamar da, wani lokacin kuma in tace zata zo sai ince bana gidan duk don dai
janyewa daga gareta.

Bayan sati d'aya da sallah su yaya suka dawo gida Nigeria, mukai murna kamar me da
dawowarsa,kamar yanda shima yai farin ciki da ganinmu cikin k'oshin lafiya da
kwanciyar hankali.

kwana uku da dawowar yaya ba tare daya huta gajiya ba muka shirya muka d'au hanyar
garinmu sakkoto sabida yawon kiran da suke mai da masu cewa zasu zo mai sannu da
zuwa, ganin zai wahalar da yan uwansa ciki harda iyayensa mata yasa yaga k'ara shi
yaje musu,don yasan zumunci irin na family d'insu kowa k'ok'ari zaiyi yaga yazo,
don haka k'ara shi yaje su ganshi.
Mota guda aka d'aukar mana daga tasha sabida yaya bazai iya dogon tuk'i ba sabida
akwai gajiya tare dashi, ta d'ebemu da kayanmu da tarin tsarabar da yaya yaiwa
dangi, don saida ma yaje kasuwar haji camp ya k'aro kaya da tarin yawa don tsarabar
saudiya bazata ishi arabawa danginmu ba don yawonsu.

Mun isa sakkoto yamma lis cike da gajiyan mota, y'an uwa da abokan arzik'i aka
taremu cikin farin ciki da murnar ganinmu, bayan mun gama gaggaisawa da kowa muka
nufi b'angaran umma na inda nanne masaukinmu da Aunty Hafsa shi kuma yaya ya nufi
b'angaran samarin gidan don yai wanka ya huta, muma wankan mukai sannan mukai
sallah aka kawo mana abinci da fura mukayi k'at.

Bayan sallar isha'i yaya ya shigo parlour ya samemu d'an zama yai cike da
gajiya yana cewa "Umma zuwa zanyi in kwanta don jikina ba k'wari wlh".

Cikin nuna kulawa ummana tace " Ayya sannu Haruna ai kayi k'ok'ari daga dawowa
ka d'auko hanya haka, Mu munata shirin zuwa maka barka".

" ai umma in nace zan barku Ku taho wahalar zatai yawa,amma yanzu da nazo duk
saimu gaisa da kowa, in mukai sati guda sai mu koma kinga hakan yafi ai".

"Haka ne kam sannu kaji, tashi kaje ka kwanta ka huta, Allah ya tashemu lafiya".

Mik'ewa yai yana mana sallama ya fita zuwa sashin mahaifiyarshi umma Babba itama
yai mata sallama sannan ya wuce shashinsu.

Washe gari da safe bayan mun karya kumallo munyi wanka . yaya ya fito da tsarabarsu
ya warewa iyayenmu mata nasu sannan y'an uwanshi maza da mata sannan ya ware na
sauran family duk Wanda yazo sai abashi abinda ya samu.

Ranar gidan yini akai bak'i na zuwa yiwa yaya sannu da zuwa har dare.

Tsawon kwanakin da mukai babu inda mukaje ,sai mu da ake zuwarwa, haka har muka
cinye sati guda mukayo kano.

Taku ce
Y'ar mutan Ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*
_DEDICATED_ _TO_ _ALL_
_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation@gmail.com

0⃣1⃣1⃣ 0⃣1⃣1⃣

Tun bayan dawowar yaya Haroon daga saudiya sai alak'arsu ta k'ara k'arfi da
Alh.Usman domin Alh, ya bud'awa yaya sosai a harkar kasuwancinsu, a da kaya yaya ke
ansa agunsa ya ringa rabawa ma'aikatan wajan aikinsu, in anyi salary su bada,Yanzu
kam abin yafi gaban nan domin yanzu ya bashi damar sa han nunshi sosai harkarn
kasuwancinsa, duk wasu kaya in sun shigo mai sai ya bawa yaya jagorancin rarrabasu
zuwa store store, don haka ya zama yaya shima yanzu baya samun zama, daya tashi
gurun aiki zai shiga sabgogin kasuwancinsa, don haka yanzu sai bayan sallar isha
yake shigowa, wata rana ma sai wajan goma, sosai muka k'ara samun ci gaba aharkar
rayuwa, har mota yaya ya siya sabuwa ya aje mana tsohuwar tashi a gida tare da
driver duk inda zamu ya kaimu.

Ban garan karatu na kullum k'arewa yake don shirye shiryen final exam muke nan da
sati biyu.

A b'angaran Sweety kuwa duk yanda nake k'ok'ari wajan yakice ta ita tak'i barin
hakan, kullum tana gidanmu ni kuwa na daina zuwa nasu, tayi Iya k'orafinta harta
gaji ta bari.

************
_BAYAN_ _WATA_ _GUDA_

Yaya zaune tare da Alh, usman a katafaran parlourn sa na ganawa da bak'i, gyaran
murya yai ya fara magana,

" Haroon dalilin nemanka na yau ya banbanta Dana kullum, domin yau magana ce me
tarin mahimmanci zamuyi da Kai, wadda bata shafi kasuwanci ba, ina fatan samun
nasara".

Sosai yaya haroon ya maida dukkan hankalinsa ga Alh, Usman don jin abinda yake
fad'i.

" haroon kan maganar k'anwarka Khadeejah ne, hak'ik'a tun ranar dana fara ganin
khadeejah na tabbatar da ingancinta nasan lalle yarinya ce daban da y'an matan
wannan zamanin, nutsuwarta, kamun kanta tare da tarbiyarta duka abin birgewane ga
kowane mutum dayasan kansa, tun a lokacin na fara wani tunanin game da ita, na fara
sha'awar kasancewarta surukata, haroon don Allah alfarma nake nema a gareka ka
taimaka ka bani Khadeejah na had'ata aure da Daddy".

Dammmmm yaya yaji gabansa ya fad'i, don bai san mema zaicewa Alh, usman ba, don
haka yai shiru kamar me tunani.

Muryan Alh,usman ce ta ratsa kunnuwansa yana fad'in " Haroon taimako na zakayi
alfarma nake nema gareka nasan khadeejah tafi k'arfin auran miji irin Daddy don
khadeejah matar kamilallun maza ce amma ka taimka kayi wani abu akai".

Cikin sark'ewar murya Yaya yace " To Alh, zanyi shawara da ita Nanan don a sani
na dai nasan Nahna bata kula ko wane saurayi don haka bata soyayya, to Amma wani
abu guda akwai alk'awari dana d'aukarwa Mahaifina tun sanda ya bani kyautar Nahnah
kan cewa bazan mata dole ba a cikin rayuwarta, don haka Alh,yanzu zanjewa khadeejah
da maganar nan a matsayin shawara ba dole ba, zanji ta bakinta abinda tace zanzo
maka dashi".

Shiru Alh, yayi zuwa can yaja ajiyar zuciya tare da fad'in " Shikenan Haroon
ina sauraranka,Amma don Allah kayimin k'ok'ari kaji".

"Insha Allah zanyi k'ok'ari"


Jiki ba k'wari yaya yai mai sallama ya fito.

Tafiya yake a mota amma duka nutsuwarsa bata tare dashi tunani ne barkatai cikin
ransa, yama rasa ta ina zai fara don a zahiri bai son abinda zaiwa Nahna dole a
cikinsa, Tun had'uwarsa da Alh, usman baifi sau biyu ya tab'a ganin Daddy ba, amma
ganin da yai mai ya tabbatar irin sangartattun y'ay'an masu kud'innan ne, hak'ik'a
baya son abinda zaisa Nahna cikin matsala ko kad'an don amanar Mahaifinsa ce,
A haka ya k'arasa gida jiki ba k'wari ko kad'an.

Tun shiganshi gidan Aunty Hafsah ta lura da yanayinsa don haka suna shiga d'aki
ta dafa kafad'ansa tana fad'in "Abban Ashraf meke faruwa na ganka haka"?

D'an mirmishi ya k'ak'alo yana Shafa gefan kumatunta yace " me kika gani Hafsa?"

" naga rashin nutsuwa da walwala a tare da kai ?"

"Karki damu zamuyi magana anjima yanzu had'amin ruwan wanka tukun?"

Cikin tsarguwa tace "Allah yasa naji alkairi wlh har gabana ya fara bugawa"

"Karki damu bari zuwa anjima d'in".

Ina k'ule kan gadona inata zuba karatu don exam d'inmu tayi nisa yanzu kullum ina
kan karatu ko zaman parlour banayi Iya kacina cin abinci nake komawa d'aki, sallah
kad'ai ce take shiga tsakanina da littafina, yau kam dake ina hutun sallah ko
kad'an ban motsaba, ina jin shigowar yaya amma ban fita ba sai yaje sallar magriba
ya dawo zanje masa sannu da zuwa.

Jin shigowarsa shida su Asharaf daga sallah yasa na fito parlourn,


" yaya sannu da zuwa ya aiki"?
"Yawwa sannu Nahnah ya gida ya karatu"?

"Alhmdll karatu yazo k'arshe ai yaya".

"Masha Allah , in angama kuma sai a koma degree ko sai kin huta"?

"A'a yaya k'ara in wuce kai tsaye don wannan tsyawa hutun shi kenan sai abu ya
shiririce".

"To Allah ya taimaka Nahna autar Baffah".


Ya k'arashe da D'an mirmishi.

Dariya itama tayi kawai tana tuno Baffanta cikin ranta.

Bayan sunci abinci akai sallar isha nan kowa ya tashi don himmar sallah,

Koda Yaya ya dawo daga masallaci yau bai zauna hira ba a parlourn d'akinsa ya
wuce kai tsaye inda Aunty Hafsah ta bishi, ganin ba kowa a parlourn yasa su Ashraf
shigowa d'akin suna fad'in Aunty zamu kwanta,

"nace da wuri haka me yasa yau bazakuyi kallo ba "?

"Abba ya shiga d'akinsa momy ma ta kwanta"

"OK to bari a kashe kayan kallon"?

Fita tai taje ta kulle duka k'ofofin gidan ta kashe kayan kallo sannan tazo ta
shirya su Asharf d'in suka kwanta kan gadonsu.

Tunda ta koma gadonta ta kwanta take tunani aranta, duk yanda akai yau akwai
damuwa tare da Yaya ta lura duka d'an wasan da yakeyi k'arfin hali yake, ko dake
jiki da jini k'ila baya jin dadi ne.

Watsar da tunanin tai ta shiga karatunta.

A d'aki kuwa Yaya yake shaidawa Aunty Hafsah duk yanda sukai da Abban sweety, itama
shiru tai tana tunani zuwa can tace" Da farko dai ina son karka tunkari Nahna da
wannan maganar har zuwa ta kammala exam's d'inta don yanzu babu buk'atar a kawomata
rud'ani cikin zuciya, sannan shawara ta gaba inka samu Nahna kan batun nan ka bita
da rarrashi, sabida inka bata umarni tabi kai tsaye zata ga rashin adalcinka
gareta, shima Abban sweetyn ka bishi a sannu karka nuna mai kai tsaye had'in bai
ranka domin zaiga rashin kyautarwa gareshi tunda shi yana iya iyinsa wajan ganin ya
kyautata maka, sannan babban muhimmun abu shine muyita addu'a Muna neman alkairin
Allah cikin lamarin".

Cike da gamsuwa da maganar Aunty Hafsah yaya ya gyad'a kai yace " Naji dad'in
shawararrki Hafsah Allah ya shige mana gaba".

Amsawa tai da ameen zuciyarta cike da sak'e sak'e.

******************
Tsawon sati guda yaya bai Sanar da Nahna halin da ake ciki ba, ya bari sai ranar
datai last exam d'inta zai zauna da ita.

Ranar Laraba itace ranar da zasu gama exam, duk sinyi shirye shiryen graduation
d'insu,
Ranar suna fitowa a final paper d'insu kowa ka gani bakinsa bai rufuwa wasu na
fad'in Alhamdullillah, wasu ko Allahu Akhbar kawai suke fad'i, sab'anin wasu da
zakaga suna fitowa zasu hau ihu Mara dalili, Wanda (Y'AN ARABIC) suka sha banban da
sauran.

Kai tsaye Open theater suka wuce inda zasu gabatar da '‫ 'برناميج‬wato programs na
larabci tare da masrihiyya, wajan ya cika yayi mak'il da alumna inda zakaga duka
( y'an Arabic) mata sanye da ankonso na Atamfa sai mazan sanye da shadda iri d'aya
gwanin sha'awa da birgewa,

Nahna sanye da kayan sarakuna an mata ado da alkyabba da takalmi irin na


sarakai, kasancewarta matar sarki cikin drama d'in, fadawane keta bin bayanta suna
mata kirari irin yanda akewa sarakai, a hankali take takowa yayin da masu video da
masu d'aukan pictures sukai Ca a kanta, cikin kunnanta taji muryan Ashraf da
Khaleel suna fad'in
" Aunty Nahna Aunty Nahan"

D'ago idanuwanta tai ta dubi sashin da suke tare da sakar musu mirmishi,

Tana zuwa ta fara gabatar da kanta cikin harshe mad'aukaki (Arabic) bayan tai
sallama ta mik'a gaisuwa ga prover's ga dikkan malamai tare da dukkan Wanda yake
wajan,sannan kai tsaye ta shiga gabatar da shirin, inda hankalin dukkan Wanda yake
wajan ya dawo kanta.

Yanda take sarrafa harshen larabci tamkar harshenta shine abinda ya burge kowa
gashi sin d'in da aka d'orata a kai ya dace da ita,
Bayan gama drama d'in aka shiga muhawar tsakanin maza da mata inda mata ke kare
mahimmancin ilimin y'a mace su kuma maza suke kare rashin muhummancinsa duka cikin
harshen Larabci,

Sannan aka fara sako k'asidun da suka yiwa Kansu na rabuwa da juna, da Wanda
sukaiwa prover's da malamansu.

Abufa yayi abu inda akaita d'aukan pictures ana video,

Basu tashiba sai bayan la'asar inda kowa ya kama hanyar gida da mutanansa,
Sweety taiwa Nahna hotuna kamar me tare da video don duk motsin datai saita
d'auketa har abin ya fara bawa Nahna dariya.

Yau kam cike take da tarin farin ciki wanda fuskarta take bayyana hakan.

Bayan sallar isha'i suna zaune a parlour su Ashraf Aunty Hafsah sunata bawa yaya
labarin abubuwan da akai a skl d'in su Nahna shikam ya biye musu yanata fad'in
Masha Allah, madallah,
Zuwa can ya kira Nahna cikin murya me cike da kulawa yace " Nahna daman ina son
muyi wata magana dake me mahimmanci don haka da safe kafin na wuce office zan ganki
kinji. . . . . . . "
Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation.@gmail.com

Wannan page d'in naki ne (Fauzidadi) na bakishi kyauta kiyi yanda kikaso dashi,
sabida kulawarki ga wannan novel, na jinjina miki yanda bakya gajiya da
adanaminshi.
👍🏾👍🏾👍🏾👍🏾👍🏾👍🏾👍🏾

0⃣1⃣2⃣ 0⃣1⃣2⃣

Damm Nahna taji gabanta ya fad'i, dukda bata San me yaya zai fad'a mata ba amma
tasan me muhummanci ne,ga yanayin data gani a fuskar sa, a hankali tace To yaya
Allah ya kaimu safiyar, mik'ewa tai cikin sanyi tai musu saida safe ta shige
d'akinta .

Haka ta kwanta cike da tunanin cikin ranta har bacci me nauyi ya d'auketa.
Bayan sallar asuba tana zaune kan sallaya tana karanta azkar har k'arfe shida ta
shafa addu'a ta mik'e tana k'ok'arin ninke prayer mat d'in taji muryan yaya a
k'ofar d'akin yana mata magana, da sauri ta aje tai waje, zaune ta sameshi kan
kafet ya mik'e k'afansa yana jan casbaha, a hankali ta k'arasa gareshi ta zauna
tare da gaisheshi ya amsa fuskanshi d'auke da fara'a ,

" Nahna ya gajiyan taro kuma "

" Alhamdulilah yaya "

" To masha Allah"

Shiru ne ya biyo baya na D'an lokaci daga bisani ya nisa yace


" Nahna kiban duka hankalinki nan, magana ce me mahimmanci matuk'a zamuyi dake "

Dammmm taji gabanta ya k'ara fad'uwa,

" Nahna nasan kinsan Alh Usman kinsan alak'ar dake tsakaninmu dasu, Nahna kin
Sani cewa ina tare da shi ne sabida kasuwanci dake tsakaninmu Wanda zuwa yanzu
zumunci ne me k,arfi Tsakaninmu."

Numfashi yaja yana k'ara gyara zamansa,

Zuwa lokacin duk Nahna ta matsu taji me zai fad'i,

" Nahna wato wata magana ce Alh Usman yazomin da ita me girma , yana son ya had'a
zuri'a damu, yazomin da zancan yana son in kin amince yahad'aki aure da d'ansa,
Amma Nahna ba dole za'a miki ba amincewarki nake buk'ata, don Nahna ko k'arshen
alak'ata da Alh usman kenan in biki aminceba,wlh bazan aurar dake ga d'ansa ba,kije
kiyi shawara Nahna in kinga bakya ra'ayi ki sanar dani kinji, abinda yasa ma nai
miki maganar don naga baki kula kowa ne ma'a babu soyayyar wani a zuciyarki ko?"

Ya k'arashe maganar da kallonta.

Cikin kid'ima ta gyad'a kai tare da fad'in "eh yaya zanyi shawara ".

" To jeki ina sauraranki daga yau zuwa kwana biyu,amma fa karkiyi abinda zaki
cutu kinji Nahna".

Tashi tai tana tafe tana had'a hanya ko gani batayi sosai don tsananin tashin
hankalin daya ziyarceta, tana shiga d'akin ta fad'a kan gado tare da fad'in

"innalillahi wa'inna ilaihi ra'jiun, shin wace Masifa ce ke tunkaro rayuwarta,wane


sabon tashin hankali ne wannan ,wai shin dama har yanzu UK bai fita cikin rayuwar
taba , don tsananin masifa yanzu baya k'asarma amma har saida yabi k'wak'wk'wafin
rayuwarta ya had'a da mahaifinsa da sunan yana son auranta kawai don ya cuzguna
rayuwarta,wayyo Allah yanzu ina zatasa ranta ,kai wlh Sam babu abinda zatayi da UK
matsayin mijin aure, baya cikin tsarin mazan da zata iya aura harta kai tai rayuwar
aure dashi,".

Maganganu kawai taketayi cikin ranta tama rasa me zatai kawai saita fashe da
matsanancin kuka Mara sauti.

Tsawon lokaci tana kuka me cin rai har bacci yai gaba da ita ,bacci Mara dad'i
me cike da tunane tunane.
Bayan awa guda ta farka idonta yai mata nauyi sosai a hankali ta maidasu ta rufe
bayan minti biyu ta k'ara bud'esu tana tunano abinda ya faru da ita ,sai taji
gabanta ya fad'i rasss nan da nan idonta ya k'ara Kawo ruwa ,ta mik'e a hankali ta
shige toilet tai wanka ta fito sanye da towel tana tafe tana Jan k'afa,k'arasowa
tai gaban mirror ta shafa mai tare da d'auko riga doguwa tasa ba tare data tsaya
yin wani kwalliyaba, don zuciyarta ba d'adi Sam, maimakon ta fita parlour don
karyawa saita koma ta kwanta kan gadon tana dafe kanta dakemata tsananin ciwo.

Tunani take kala kala cikin ranta ta rasa ma ina zata tsaya ne . . .
Muryan Aunty Hafsah ta jiyo tana dafata
" Yadai Nahna tunanin me kike haka inata kiranki biki jiba,ko baki da lfy ne?"

Da k'yar ta tashi zaune tana mutsika ido tace " kaina kemin ciwo wlh Aunty, ban
jinki ba sam"

"Ayya sannu tashi muje kici abinci kisha magani"

Badon taso ba ta fita, ba kowa parlour don Yaya ya fita office su Asharaf kuma
suna skl, ta Shiga kitchen ta d'ebo abincin kad'an tare da ruwan shayi ta fito,
cin abincin kawai take ba tare don tana jin dad'insa ba , Aunty Hafsa na gefe tana
kula da duk motsinta.

Bayan ta gama Aunty ta mik'a mata magani tasha tana runtse ido, tace

"Aunty ya naga duk kinyi komai harda wanke wanke biki bari na fito ba "

" ba komai naga kina bacci ne yasa kawai nayi nasan akwai gajiya tare dake sosai
, ga bashin baccin karatun exams da kika tarawa idonki".

Lumshe idonta tai kawai bata ce komai ba.

Cikin rashin jin dad'in ganin halin da take ciki Aunty tace " Nahna yayanki
yamiki maganar d'an gidan Alh usman ko?"

Gyad'a kai kawai tai, Aunty taci gaba. " Nahna ki tsaida hankalinki kiyi
shawara bawai dole za'a miki ba in kinga biki amince ba ki fad'i kawai kinji"

"To Aunty "

Daga haka tai shiru don bata son magana ko kad'an,


Ganin tai shiru yasa Aunty tace kije ki kwanta ki huta Nahna"

Mik'ewa tai ta shige d'aki ta fad'a kan gado zuciyarta ba dad'i .

Tsawon kwana biyun da yaya ya bata tayi tana sauraran taji ya kirata ya tambayeta
meta yanke taji shiru , har kwana hud'u bai kirata ba.

Yau da dare tana kwance kan gado tanata sak'e sak'e aranta wai idan yaya ya kirata
me zata ce, kullum dai addu'a take tana neman mafita gun Allah, shin wai dagaske
UK sonta yake ko kuwa iskanci ne , ita dai tasan farkon ganinta dashi ya nuna mata
samartaka daga baya kuma data nuna mai bata ra'ayi ya shiga gasa mata azaba da
wulak'antata gaban mutane kuma yanzu yazo da wani zance kodai wulak'ancin da yai
matane bai isheshiba zai aureta yaci gaba dayi mata, koma dai mene ne ai tana
fad'awa Allah wani tunani ne ya fad'o mata arai, saita saki wani d'an mirmishi
tana jinjina kai.

Kuyi hak'uri da wannan don Allah👏👏.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation.@gmail.com

0⃣1⃣3⃣ 0⃣1⃣3⃣

Misalin k'arfe sha biyu na rana ina kitchen ina had'a abincin rana naji anata
knocking k'ofa a hankali nace

" waye "

" Autar Baffa yayanki ne usman"

Tsalle na buga tare da bud'e k'ofan parlourn ina fad'in


" yaya Usman oyoyo"
Shigowa yai ciki yana dariya yace " wash na d'auko gajiya auta ina mutan gidan
ko basa nan?"

" eh Aunty taje Unguwa yaya yana office Yara suna skl saini kad'ai, yaya ya Hanya
".

" Alhamdulillah Nahna kin ganni ba zato ko? Wlh Sakkoto na nufa mun sami Hutu,
kuma sai muka biyo ta kano yiwa wani abokin aikinmu ta'aziya ,nace to bari in biyo
mu gaisa".

" kai amma yaya naji dad'in zuwanka wlh, nima ina ganin cikin satin sama zanzo
sakkoton".

"Um su Nahna graduate an girma sai aure kuma ko?"

Mirmishi kawai tai ta tashi ta shiga kitchen don kawo mai ruwa da lemo.

Bayan ta kawo mai ta zauna sunata hira yaya usman yace


" ki shirya kawai mu wuce tare "

Da sauri ta d'ago tare da fad'in "kai anya yaya zai bari kuwa?"

"Me zai hana ya barki tunda daman kina shirin zuwa"

"To ai kai yau zaka juya kuma ni sai nan da sati zan tafi kaga bai San da tafiyar
tawa ba yau "

" OK bari in fad'a mai ma nazo"

Wayansa ya d'auka ya kira number d'in yaya Haroon bugu d'aya ya d'auka

"Hello Usman ya kake "?

" yaya lfy qlau ya gida ya iyali?"

"Duk kowa lafiya , ya wajan aikin naku?"

"Alhamdulilah, gani ma na shigo garin naku,nazo gidan sai Nahna kad'ai"

" ah da gaske usman?"

"Hhhmm Allah da gaske"

"OK ina Office amma zanzo gidan yanzu hafsa kuma tana Unguwa, amma ai ba yau zaka
wuceba ko?"

"Eh to da dai naso wucewa yau d'in amma zan bari zuwa gobe."

"OK to ina hanyar dawowa."

"Tom sai kazo Allah ya kawoka lafiya."

Hira sukaci gaba dayi da Nahna yana bata labarin ya samu mata k'anwar friend d'insa
a nan kano take don haka insha Allah da wuri za'ayi bai so a wuce 7 month.

Murna sosai Nahna tai tana tambayar sunanta yace " Amrah"
Nan yake k'ara bata labarin yana sa ran zai samu transfer zuwa Kano nan da 2 month
don haka zai sai gida a Kano ya zauna kusa dasu.

Haba murna kamar me gun Nahna ta mik'a mai hannu suka kashe cik'e da k'aunar juna
irinta D'an uwa da y'ar uwarsa.

Ana kiran sallar azahar yaya haroon ya dawo,nan suka rungume juna da yaya usman
suka gaisa da cike da k'aunar juna sannan suka d'aura alwala suka wuce
masallaci ,kafin su dawo Nahna ta shirya musu abinci tare da had'ad'd'an zobo.

D'aki itama ta shiga tai sallah tana zaune tana addu'a taji shigowarsu shafawa tai
ta mik'e don ta had'a musu abincin.

A tare a flate d'aya ta had'a musu abincin duka sukeci suna hirar zumunci cike da
nishad'i,nan yaya usman yake bawa yaya labarin ya samu mata zaiyi aure sannan zai
samu transfer zuwa Kano don haka yace ya fara nema mai gida nan kusa zai siya,
shima yaya murna yai ya godewa Allah sannan yace zai shaidawa wani abikinsa me
saida filaye da gidaje ya samo mai.

Anan ma yaya usman yake cewa yaya ya bar Nahna su wuce tare yaji tana cewa zataje
wani week d'in, yai Jim sannan yace to ta had'a kayanta su wuce amma sati biyu
zatai ta dawo.

Bayan la'asar yara suka dawo daga skl nan sukaita murna dunga Auncle d'insu, basu
jimaba Aunty Hafsa ta dawo itama da fara'arta suka gaisa da Yaya usman sunata
barkwanci.

Da dare da wuri na kwanta bayan na gama parking kayana cikin trolley back,
Aunty ta lek'o taga ina bacci ta koma take shaidawa yaya nayi bacci, jawomin k'ofa
datai yasa na farka jin tana cewa yaya nai bacci yasa na gane nemana yake, dammm
naji gabana ya fad'i don nasan kan dai wannan maganar ne. . .

K'asa k'asa nakejin muryan yaya Haroon yana magana tsam nai da raina ina
sauraran me yake fad'awa yaya usman.

" wato usman uban gidana Alh Usman ne yazomin da wata buk'ata kan Nahna wai yana
son in bashi auranta ga D'ansa, to tun a ranar na fad'amai bazan tab'a yiwa Nahna
doleba, amma zan shawarceta kan batun inji ra'ayinta, to nai mata maganar tsawon
kwana biyar na bata lokaci tai tunani ta yanke shawara , amma sai bayan nai mata
maganar kuma nake dana Sani don na lura tun lokacin kamar batada kuzari,ina tsoron
kar in takurata, bisa ga alk'awarin dana d'aukarwa kaina da kuma mahaifinmu kan
rik'e amanarta da kuma kaucewa duk abinda zaisata cikin had'ari."

Cikin mirmishi yaya usman yace " To yanzu Yaya Haroon shike nan Nahna bazatai
aure ba don gudun damuwarta, ina tunanin zuwa yanzu ya dace ace ko Nahna ba'a mata
aure ba ace dai tanada wani tsayayye amma fa ga yanda Aunty Hafsa ta shaidamin
Nahna ko saurayi batayi duk nacin mutum akanta hak'ura yake ya barta, kaga ai dama
wannan da zaka tsaida mata shi a mijin aure tunda ba tab'a yin saurayi taiba shi
d'in bazai sha wahala wajan jawo hankalinta ba , sannan Abu na gama kaga dai irin
tarin Alherin mutuminnan a gareka bai kyautuba karon farko daya zoma da buk'ata ka
watsa mishi k'asa a ido, kuma me sonka aishi zaiyi sha'awar had'a zuri'a da kai."

"Wato usman duk alherin da Alh Usman yaimin bazan manta dashi ba domin kuwa d'an
halak bai manta alheri,ammafa hakan bazai sa inyiwa Nahna dole akan auran d'ansa ba
koda kuwa hakan zai Kawo k'arshen mua'malarmu dashi,sannan wani abu Nahna fa bata
tab'a ganin yaronba inba a hoto ba, koni bai wuce in K'irga ganina dashiba,kuma a
ganina na farko dashi na gane irin sangartattun y'ay'an masu kud'in nan ne, duka
shine abinda ya fara kashemin jiki dashi."

"A'a yaya karka karaya ka kira Nahna dai kaji meta Yanke shawara kafin mu wuce
gobe , sannan maganar sangartacce ne wannan D'abi'ace ta mafi yawon y'ay'an masu
kud'i matuk'ar dai yaron baya shan giya baya Neman mata to ba matsala bace
auransa."

Jin jina kai yaya yai sannan ya d'ora


" a gaskiya Umar baya daya cikin lefukan nan Don na tab'a tambayar sectare d'in
Alh yace baya d'aya ciki sai dai kawai ji da kai da nuna Isa tare da sangarta,
sannan zan k'ara bawa Nahna dama harta dawo Daga Sakkoto sannan inji ra'ayinta,don
bansan takurata ko kad'an sannan kafin nan zanta k'ara nufar Allah da lamarin yai
mata zab'in miji mafi alkairi".

Wani gumi naji yana tsatstsafomin tun daga kaina har k'afata don a hirarsu na gane
Yaya yana son had'in nan sai dai yafi k'aunar farin cikina fiye da komai, don haka
nasa araina daga yau nai d'amarar sadaukar da burina zan amincewa auran uk kodan mu
sakawa Abbansa Alherin da yake mana duk da nasan babu komai cikin auran Uk sai
hak'uri da karb'ar k'addara amma zan jurewa hakan,kuma zanci gaba da kaiwa Allah
kukana nasan bazai bari in wulak'antaba.

Sai kuma naji wasu hawaye masu zafi suna bin gefan kuncina ,Tunowa danai burina ya
karye nason auran miji ma'abocin addini,don nasan Uk bai San komaiba cikin addini
zanyi jahadi zan sadaukar da soyayyta ga Wanda ya tsaneni yake musgunamin Wanda
bai San darajar d'an Adam ko kad'an . . . a haka bacci ya d'aukeni bayan nasha kuka
na gode Allah.

**************
Da safe kafin in tashi har Aunty ta gama had'a break fast ta shirya Yara sun tafi
skl Wanda duk aikina ne, ganin ina bacci yasa duk tayi hakan.

Bayan na fito a wanka a gaggauce nasa Kaya don ina toilet inata kiran yaya Usman
inyi sauri in shirya da wuri yake so mu wuce , don haka ko kwalliya ban tsaya yiba
na fita parlour.

A zaune na samesu suna jirana mu karya bayan na gaishesu na zauna muka karya,
bayan mun gama yaya Usman ya dubeni yana fad'in "To maza d'auko jakarki mu wuce
banso muyi rana "

Mik'ewa nai zuwa d'aki na yafo mayafina na d'auki jakata ta hannu na jawo trolley
d'ita na fito,
Aunty ce cikin wasa take fad'in " To su Nahna yau sai Sakkoto birnin Shehu in
anje a gaida Mama da umma a gaida duka mutan gidan".

Cike da fara'a nace " Tom Aunty duk zasuji insha Allah ,in su Ashraf sun dawo
kice musu mun tafi bamuyi sallama ba."

"Tom zan fad'i musu Allah ya kaiku lafiya".

Yaya Haroon ne ya kaimu tasha muka d'auki shatar mota k'arama don Yaya usman bai
son matsuwa .

Tunda muka d'au hanya muke hira daga bisani yaya usman ya jefomin maganar da sukai
da yaya jiya yana nusar dani kan In tsaida hankakina gu d'aya koda zan d'ora degree
d'ina hakan bazaisa in k'iyin aureba, sannan yaci gaba da nusar dani kan iniwa yaya
biyayya don duk cikin y'an uwana ba Wanda yai hidima dani tun daga k'uruciya har
zuwa yanzu, koshi da muka fito ciki d'aya baimin ko rabin abinda yaya yakeminba,tun
kuwa mahaifinmu na raye har izuwa yanzu.

Shiru nai ina sauraran sa duk jikina ya mutu murus.

Haka yaita min nasiha da jan hankali kar in watsawa yaya k'asa a ido , a haka
bacci ya d'aukeni nidai don jikina ya mutu da nasihar har mukaje Sakkoto ban
tashiba saida naji motar ta tsaya a k'ofar gidanmu.

Taku ce
y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation.@gmail.com

*Ina* *taya* *d'an* *uwa* *Abokin* **aiki* *d'aya* *daga* *cikin* *jagorori* *na
gidan *marubuta* *murnar* *auransa* ( _Jameel_ _Nafseen_ ) *Allah* *ya* *bada**
*zaman* *lfy*, *ya* kawo *zuri'a* *ta* *gari* .
❤❤❤❤❤❤❤

0⃣1⃣4⃣ 0⃣1⃣4⃣
Kwana na biyu a sakkwato Dangin Baffanmu sukayo Kano don zuwa nemawa yaya Usman
auran Amrah agidansu dake badawa bisa jagorancin Yaya Haroon, anyi komai an gama
sun bada kud'in aure dasa rana an tsaida lokacin bikin wata biyar, za'a had'a da
bikin safwan d'an gidan Babban yayanmu zata auri yar gidan Auntynmu juwaira.

Naji dad'in hutuna a garinmu nai ziyarar dangi sosai duka gidan yayyena mata
naje nai musu kwana d'ai-d'ai.

Saura kwana biyu in dawo da dare ina kwance d'akin ummana ina chart naji muryan
ummana ta zauna kusa dani tana fad'in " Khadeejah tashi zaune muyi magana "

Dammmm naji gabana ya fad'i, a nutse na mik'e zaune ina kallonta nace "umma inaji"

Gyaran murya tai sannan ta fara magana " Khadeejah wata magana naji daga gun
usman, jiya kawunku na k'ofar fada yazo da maganar yaronsa Hisham yace yana sonki
da aure in ba'aimiki miji a Kano ba, to amma yana fad'a usman yai tsalan yace wai
yayanki yaimiki miji d'an uban gidansa ne yakesonki har kun gama shirya kanku, shin
wannan zancen haka yake?"

Jinai kamar an tsoma ni cikin tafashashshen ruwan zafi yanda zufa ta wankeni, da
k'yar na fizgo numfashina tare da Kalmar "ehh"

Shiru umma tai tana naxarina na d'an lokaci, sannan cikin hikima irin tasu ta
manya ta shigamin tambayoyi Wanda naita fad'i mata yanda abin yake Daga k'arshe
nace " Umma nidai na amincewa yaya inna koma zan sanar dashi na amine da auran
Umar".

"Sunan yaron umar ne ?"

"Eh Umar sunansa amma Daddy suke kiransa"

Tsakanin d'a da mahaifi sai Allah duk sai naga jikin ummana yai sanyi, tai shiru
tana naxarin maganata don a zancena ta fuskanci abubuwa da yawa, jin muryanta nai
tana fad'in
" Khadeejah kina son sa"

Dammmm na k'arajin gabana ya fad'i don ba komai cikin raina sai tsantsar tsanar Uk
da k'in d'abiunsa, amma taya zan sanar da mahaifiyata bana son sa kuma inje in cewa
yaya na amincewa,shin banbar zuciyar mahaifiyata cikin damuwa ba kuwa. . . .

"Khadeejah tunanin me kikeyi ne inata miki magana ?"

A dibirbirce nace " um um umma dadai ban sonshi amma yanzu na fara. . . "

Gani nai ta saki wani hikimtaccen murmishi irin nasu na manya tace "Nahna
Khadeejah ina horonki daki zama yarinya ta gari,me Neman zab'in Allah a dukkan
lamuranki,kici gaba da biyayya ga yayanki, kana ina haneki dayin soyayya domin
wanin Allah,duk Wanda zakiso ki shoshi domin Allah,kada wani abin duniya ya rud'eki
a soyayya, kud'i ko kyau mulki ko nasaba kada susaki a k'aunar wani bawa duka son
da aka ginashi badon Allah k'arshensa tozarci ne da rashin alfanu kinji ko Autar
Baffah".

Jinjina kai nai jikina amace nace " insha Allah umma zaki sameni me biyayya ga
dukkan nasiharki".

"Allah yai miki albarka Khadeejah ya tsare rayuwarki daga dukkan abin k'i, Allah ya
d'oraki Akan mak'iyanki yabaki galaba a duk lamuranki".

" Ameen ameen ummana "


Kawai nake fad'i don tsantsan dad'in addu'ar ummana da naji,wayyo Allah uwa uwa
uwa dabance Allah ya sakawa iyayenmu da alkairi.

Bayan fitar ummana a d'akin na kwanta tare da lumshe ido zuciyata cike da tunani
Kala kala harma na rasa Wanda zanyi ciki, kawai dai nasan naji dad'in hiran da
mukai da ummana da adduo'in da taitamin Wanda najisu har cikin zuciyata.

Kamar yanda yaya ya umarceni sati biyu cif nayi na d'auko hanyar Kano cike da kewan
dangina.

Sai yamma na isa gida a gajiye tik'is ina shiga su Ashraf sukayo kaina da murna,
Aunty Hafsah ma ta tareni da "sannu da zuwa mutanan sakkwato ya hanya"

Cikin gajiya na amsa da "yawwa sannu da gida Aunty na sameku lafiya?"

"Lafiya qlau Nahna k'arasa d'aki ki huta, kafin mu gaisa".

" Tom Aunty"

Ina Shiga d'aki na cire kaya na tare da fad'awa toilet na watsa ruwa me d'umi na
d'auro alwala don in maida sallar la'asar data kufcemin.

Saida nai sallar magriba sannan na fito parlour a lokacin yaya ya dawo nan na zauna
muka gaisa cike da d'okin ganin juna,sunata tambayata yana barosu ya gajiyan
hanya.

Bayan munci abinci munyu sallar isha'i nan na fito da tsarabar kowa na bashi
mukaita hira har bacci ya fara d'aukana,na mik'e tare da musu sallama na shige
d'aki.

Washe gari da safe ya kama asabar ban fito da wuri ba don kowa na gidan bacci
yake, tunda yara ba skl yaya ba office, har k'arfe goma banji motsin Aunty ba don
haka na fito na shiga kitchen don had'amana break fast, banyi wani abu me wahla ba
kunu kawai na dama na soya doya.

Har nagama na wanke kwanukan dana b'ata,na share parlour tare da mofin ko ina,
anan naji motsin Aunty a d'akinta alamar sun tashi,don haka na koma d'aki na tashi
su Ashraf nai musu wanka Nima nayi muka fito don karyawa anan na tadda su yaya
suma sun fito,muka gaisa naje kitchen duk na fito mana da kayan abincin ni INA
had'awa Yara Aunty tana had'awa Yaya,bayan mun gama karyawa yaya ya kirani d'akinsa
nasan dalilin kiran, don haka ba tare da dogon tunani ba naje na zauna ina fad'in
"yaya gani"

"Tom zauna sosai mana Nahna,kan wannan maganar dai da mukayi dakene kafin
tafiyarki,na baki lokaci sosai don kiyi tunani da kuma shawara me kyau, don haka
Nahna ina sauraranki me kika yanke?"

Saida nai jim sannan na numfasa nace "Yaya na amince"

Kallona sosai yayi don ya gano gaskiyar abinda na fad'a ko akasin haka amma be
fahimci komaiba taredani.
" Nahna kin tabbatar da abinda kika fad'i har cikin ranki haka yake ,bana son ki
cutar da kanki don wani dalili, farin cikinki nakeso ba nawa ba,Nahna shin har
ranki kin amince da auran Umar duk kuwa da biki tab'a ganinsaba ?"

Karo na biyu na k'ara fad'in "eh Yaya na amince kuma insha Allah bazaku sameni me
baku kunyaba."

"To Nahna na gode Allah yaimiki albarka ya faranta miki."

A hankali na amsa da "ameen"

"Tashi kije to autar Baffah"

Mik'ewa nai ina mirmishin yak'e. Idona har dishi dishi yakemin.

Kitchen na wuce na shiga aiki Mara dalili don in sami kwanciyar hankali,inda
Allah ya taimakeni Aunty ta wuce d'aki gun yaya don indai yana gida daman bata
komai shigewa suke d'aki abinsu, saisu Ashraf ne keta damuna da surutu,nikam banko
bi takansu abubuwa kawai nake cikin rashin kuzari.

Haka naita aikin badan inajin dad'insa, tuwon shinkafa miyar agushi nayi tare da
lemon kwakwa na zuzzuba a coolers na ajiye don nasan sai wajan ma la'asar za'aci,
lokacin Dana Shiva d'aki sallar azahar kawai nai nasawa su Ashraf uniform d'in
islamiyya, nace suje akwai Abinci na zuba musu a plate a parlour, suna fita na
fad'a gado na hau aikin nawa wato tunani, kusan awa guda ina sak'awa da kunewa da
tunanin irin rayuwar danasa kaina aciki, nasan babu abinda zan tsinta cikin auran
UK sai tsiya da zunzurutun wulak'anci Wanda nafi tsana a rayuwata, To waima wane
yasa na furta Kalmar amincewa ne ,me yasa idona ya rufe naiwa kaina ganganci? Ya
Allah Allah ka fitar dani cikin k'anginnan kasadar dani ga dukkan allkairanka. . .
da wannan tunanin bacci yai gaba dani Wanda ban farka ba said a naji ana kiran
sallar la'asar na mik'e zuwa toilet na dauro alwala nai sallah,sannan na fito
parlour mukaci abinci.

Takanas yaya yaje gida ya sanar da Abban sweety amincewa danai, farin ciki
kamar zai kar sa yaita godiya ga Allah yana k'ara godewa yaya,nan yake sanar da
yaya zuwa yan watanni Uk zai dawo k'asar Bayan ya dawo sai akawo kud'in aure dasa
rana, yaya ya amince shima ya sanar dashi Nahna zata d'ora degree d'inta ,ba
damuwa yace yana k'ara godiya.

Da dare Abban sweety ya kira Auntynsu da sweety yake sanar dasu yanda sukai da
yayana ,wata irin k'ara sweety tasa cike da tsananin farin ciki tace " Wayyo Allah
yau ranar farin cikin a kenan, mafarkina ya zama gaskiya, wlh Abbah na dad'e ina
wannan fatan har maganar na tab'a yiwa Nahna tace bata so Ashe dai Nahna Rabon
gidanmu ce Alhamdulillah."

Murmushi kawai Abban yake yace " murjah ke bikice komai ba"

Dariya tai tana fad'in " nayi far in ciki Alh Allah ya Santa Alkairi yasa
abokiyar arzik'ice, yanzu ya d'an gidan nawa an sanar dashi ne ?"

Jim Abbah yai kana yace " a'a ban sanar dashi ba tukum, ina wani shiri ne , don
jiyama munyi Waya yake cemin 5-6 months insha Allah zasu gama".

"To Allah ya tabbatar da alkairi yasa damu za'ayi"

"Ameen ameen murjah, sai muyita addu'a Allah ya dai daita tsakaninsu yasawa kowa
soyayyar d'an uwansa don wannan shine damuwata".

" karka damu Alh, insha Allah a sannu zasu so junansu".

Nan dai sukaita hira har sweety ta fara batun yanda zasusha shagalin bikin, su
Abbah sai dariya suke mata na d'okin da takeyi.

A b'angarena kuwa kullum sai tunani da damuwa na rasa ya zanyi da raina, Allah
yana gani ban k'aunar Uk na tsaneshi kamar yanda ya tsaneni, shin ahaka za'ayi
zaman auran? Kuma babbar damuwata ma shine shin Uk ne yasa Abbansa ya nema mai
aurena don yaaci gaba da wulak'antani da yagani, ko kuwa ma bai San da maganar ba
shima kawai jinta yai Daga sama, in kuwa haka ne ya zasu kwashe dashi,nasan
wulak'ancinsa zai iya cewa ma ni nasa had'amu, ire iren tunanin da suke hanani
sukuni kenan, ganin banda mafita yasa na maida dukkan lamarin ga Allah tare da
Neman zab'insa in wannan had'in alkairine Allah yasa min nutsuwa a raina in babu
alkairi Allah ka Kawo silar rugujewarsa cikin sauk'i.

Kamar yanda yake a k'aida bayan yin graduation a school d'inmu zamuje
entrepreneurship 'koyon Sana'a ' domin dogaro da kai to haka muma muka sai form
muka cike tare da mayarwa.

Ranar Monday muka fara zuwa entrepreneur acikin school d'in, ni na cike catering
wato koyon girki da snacks drinks da sauran duk abinda ya danganci girki,domin ina
k'ara Neman k'warewa sosai kan harkar snacks da cake.
Hafsa k'awata kuwa b'angaran makeup and saloon ta zab'a, Wanda zamuyi tsawon sati
takwas.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation.@gmail.com

0⃣1⃣5⃣ 0⃣1⃣5⃣

Hak'ik'a na samu k'arin wayewa a fannin girke girke a entrepreneur d'in da muke ,
sannan fannin mu'amala na k'ara had'uwa da mutane iri-iri Kasancewar department ne
mabanbanta aka had'a agun, nayi sabbin k'awaye dukda ba d'abi'a tace ba kwashe
kwashen k'awaye,amma wani dole ka kulashi don yanda zaita tura kansa gareka,
hakama malaman da suke koya mana girkin sun sanni sosai a gun har yasa suka ban
jagorancin captain a gun sabida hazak'ata don sau d'aya in aka koya abu na d'auke
shi don dama ba yabon kaiba ni gwanace wajan girki Aunty Hafsah ta horar dani da
girki sosai.

Tsawon satittikan da mukai na samu ci gaba sosai abin sai godiyar Allah,haka
b'angaran make up wani sa'in in mun tashi a gunmu da wuri su Hafsa busu tashi ba
nakan shiga gunsu in zauna anan ma na d'an koyi kwalliya irin wadda ake yayi, tare
da gyaran gashi.

Cikin nasara muka gama entrepreneurship d'inmu , aka bamu shaidar kammalawa
"certificate".

Duk wani abu daya dace muyi a school d'inmu munyi mun had'a duk Slip's d'inmu dasu
semester form zuwa duk wasu takardu da ake buk'ata munyi bucking result.

Sati shida dayin bucking d'inmu result d'ina ya fito tare da tarin nasarori ,ranar
Dana amshin result d'ina na shaidar N.C.E ina zuwa gida na zube nai sujudishshikur
ga ubangijina na gode mai tare da naiman agajinsa a karatuna na gaba da zan d'ora.

Aunty cike da farin ciki ta d'auki Waya ta kira Yaya, ai kuwa ba'afi 30 minutes
ba sai gashi a gidan fuskarshi d'auke da fara'a yazo yakarb'i result d'in yana
dubawa ,ai kuwa hak'oransa tar a waje ya dube ni yana fad'in " Alhamdulillah, Allah
kaine abin godiya Autar Baffah ta fito da kyakyawan sakamako ,Allah ya sanya
alkairi, yayi miki jagoranci a karatun da zaki d'ora"

"Ameen ameen yaya" abinda kawai naketa maimaitawa kenan zuciyata da fuskata cike
da tsantsan farin ciki.

Da dare ina kwance d'aki ina charts saiga kiran sweety ya shigomin, saida nai d'an
mirmishi sannan na d'auka, bako sallama ta faramin k'orafi,

"Lalle Nahna kin kyauta kin nuna min ni d'in ba komai bace a gunki biki d'aukeni
yanda na d'aukekiba ,wai Nahna har ki karb'i result d'inki amma ki Kasa fad'amin
sai a status d'inki naga kinsa, ba komai na gode".

K'it naji ta kashe wayan, mirmishi na kuma sannan na bita ,harta kusa katsewa
sannan ta d'auka,

" haba tawan kinsan ke d'in ta dabance a guna, Abubuwa ne kawai sukai min yawa
shiyasa ban samu kiranki ba kiyi hak'uri kinji my sweety ".

Sai sannan naji ta d'anyi dariya sannan ta faramin murna tana min fatan alkairi,
nan muka d'an tab'a hira sannan mukai sallama.

Tun a washe gari Yaya yaje ya siyamin form d'in degree, yana kawomin naje cafe na
cike tare da tura musu, ba'a d'au lokaciba muka gama komai na fara lecture inda
suka bani level 2.

Yanzu banda wani ishashshen lokacin zama a gida kullum in na fita tun safe sai
yamma lis, don haka na manta da duk wani Abu sai karatuna kawai nasa agaba.

Fannin addu'a kuwa ban gaza ba kullum nai sallah saina rok'i ubangiji ya
tabbatarmin da alkairi cikin wannan had'in.

Addu'ar da nake yasa naji hankalina yana k'ara kwanciya, yanzu banjin tashin
hankalinnan da nakeji inna tuna batun auran.

Kwanaki sukaita wucewa bikin Yaya usman ya matso don yanzu saura wata guda cif,
munata shirin biki harda sweety don tunda na fad'a mata zancen bikin tace ai
tafiyar da ita za'ayita itama zata garinmu,don haka duk ankon bikin da aka turo
mana sakkwato tare yaya ya siya mana, ashe itama acan tasa Abbansu yai mana sabbin
d'inkuna har kala hud'u hud'u Kaya masu tsada, tare da takalma da jaka harda
mayafai.

Naso ace tun saura Sati d'aya bikinnan zan tafi amma school bazai bari ba, gashin
kwana biyar za'ai Ana programs na bikin inata tunanin ya zan b'ullowa tafiyar, haka
dai ina gani zan tauye wasu lectures d'in nawa don ba k'aramin shiri dangi sukaiwa
bikin nan ba , bikin mutum uku ba wasa ba , don haka ma yanda aka tsara duka
gidanmu za 'ayi komai , suma su Aunty juwaira gida zasu taho da gidansu yaya Babbah
don hankali ya tsaya waje guda.

Kwatsam labarin tafiya yajin aiki ya taso daga makarantun gaba Da secondary a k'asa
baki d'aya, Wanda babu ranar komawa har sai Baba ta gani, duk son karatuna naji
dad'in wannan yajin aikin don ko ba komai zanyi shagalin biki hankali kwance.
Nan na fara tunanin tafiya a washegarin ranar,don lokacin ya kama bikin saura kwana
biyar a fara, amma matsalata guda Sweety inna tafi nace sa taho dasu Aunty Hafsa
baza taji dad'iba, kuma in nace mu tafi tare inaga kamar Abbanta bazai bartaba taje
tai kusan sati biyu, ina zaune ina neman mafita saiga kiranta a wayana, ina d'auka
ta fara magana
" Nahna kinji wai yau an tafi straight ko"

"Eh wlh yanzu nakeji a radio, ai naji dad'i kinga zamuyi sabgoginmu hankali
kwance, badan ma Abba bazai barki ba ai da tun gobe zamuyi gaba"

" Haba dai me yasa bazai barniba ai ba wani matsala, in dai goben kike so mu
wuce saimu tafi"

"OK to Allah ya kaimu mu tafi bari in shirya trolley back d'ina"

"A'a karki had'a bari in kira Abba yanzu in fad'a mai gobe zamu tafi sai inzo
gidan naku yanzu mu had'a kayan waje d'aya don Akwai wasu kayanki anan da Abbah ya
d'inka mana".

" OK to ina jiranki"

Bayan na kashe wayan nai shiru ina tunani araina wai shin haka rayuwar Y'ay'an masu
kud'i take sakaka ba tsaro ba tsangwama? Daga jin magana sai tafiya🤔,

Koni da garinmu zani yanzu fargabar sanar da Yaya tafiyar nan tun gobe nakeyi,
duk da nasan bazai hanani ba, amma ita daga fad'a mata har tace to.

Fitowa nai parlour ina kiran sunan Aunty , ta amsa daga d'akinta tana fad'in
"Nahna gani cikin d'aki"

"Aunty kinji wai an tafi straight duka k'asa yau"

"Haba da gaske"

"Wlh da gaske Aunty yanzu nakejin a radio kuma saiga sweety ta kirani yanzu tana
k'ara fad'amin , shinema nake cemata da Abbanta zai barta da mun wuce gobe wai
tace eh zai barta"

Dariya Aunty tai tana fad'in" was yaga areni muje biki"

Mirmishi nai ina cewa " ai Aunty rayuwar gidansu sweety ba tsaro wlh, yanzufa da
yamman nan zatazo mu had'a Kaya,nida ko fad'a a'a Yaya banyiba"

"Ai ba matsala kinsan bazai hanaki ba ,kawai dai ki kirashi awaya ki sanar dashi
kafin ya dawo ma"

Wayana na d'auka na kira number Yaya duka biyu ya d'auka


"Nahna ya dai "?

" um yaya barka da yamma ya aiki"

"Barka dai Nahna aiki gashi munata fama"


"Yaya daman yanzu ne nakejin an tafi yajin aiki k'asa baki d'aya shine nakeson gobe
in tafi sakkwato inyi gaba"

"Hhhhmmm Nahna naga dai bikin nan kina d'okinsa, amma kuma Sweety ta rigaki fad'i
don muna tare da Abbansu yanzu ta kirashi take fad'in zaku tafi goben"

Dariya nai ina fad'in "um sweety zumud'i"

Shima y'ay'an dariya ya d'anyi yace "To shikenan sai a had'a Kaya Allah ya kaimu
goben"

"Ameen yaya sai ka dawo "

Ba'a jima ba saiga sweety da jakunkuna da Kaya nik'i nik'i kallonta na tsaya yi
ina dariya " Sweety wannan uban kayanfa kamar zamuyi tafiyar wata biyu, duka fa
sati biyu zamuyi "

"Oh Nahna biki tareni ba kin tsaya min tsiya"

" To sannu da zuwa sweety nah, Kawo kayan in tayaki"

D'akina muka wuce nan take firfitomin da kayan da Abbansu ya siyamana, nai shiru
ina wani tunani can nace "mun gode Allah ya saka da alkairi, amma Sweety Allah yasa
ba takurashi kikai dole ya siya mana ba."

"Ah haba wannan y'an kayan zakice na takurashi kedai kawai tashi mu shiryasu"

Komai mun had'a da muke buk'ata manyan trolley back biyu da k'arama d'aya don
Kaya muka dija kamar me.

Sai Bayan magriba sweety ta tafi gida da shirin gobe da wuri zamu wuce don kar
muyi dare.

Bayan yaya ya dawo yakirani parlour na zauna ya fara magana kamar haka "Nahna
gobe insha Allah zaku wuce ko,Abban sweety yawa driver d'insa na office magana
zaizo k'arfe Tara ya d'aukeku shi zai kaiku, sannan sweety inaso ki kula sosai in
kunje kinga bake kad'aibace zaki tafi da bak'uwa, kuma yanzu kinga duk zuri'ar
gidan Alh Usman sun zama surukai garemu, don haka ki kula da ita mu fita kunya kar
tana ta murna zataje garinmu kuma ta gano wani abin da zai b'ata ranta, dukda ba
alfahari ba nasan zuri'ar gidanmu ba baya bane wajan karrama bak'o amma duk da
haka ita a k'ara mata akan Wanda akewa, naiwa su umma Waya na fad'a musu da ita
zakuzo don haka a tanadeta."

"Tom yaya Allah ya kaimu goben, kuma insha Allah za'a kula sosai"

"Yawwa Nahna daman nasan baki da matsala, Jeki ki kwanta Allah ya kaimu goben".
K'arfe Tara driver d'insu sweety yai parking k'ofar gidanmu tare da ita a tsaitsaye
ta shigo suka gaisa da Aunty Hafsah muka fita da kayanmu mukai musu sallama, nan
driver ya cilla mota muka d'au hanya.

Taku ce
Y'ar mutan Ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *YA'N* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

💻 *ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝 .
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation.@gmail.com

0⃣1⃣6⃣ 0⃣1⃣6⃣

Sanda muka shiga gidanmu da murna aka taremu tare da d'ibar mana Kayanmu zuwa
masauki kowa na mana sannu da zuwa.

Kai tsaye alwala mukai muka maida sallan dake kanmu, bayan mun idar na tashi na
fito parlour nan na tarar an shirya mana kayan abinci iri da kala na koma d'akin na
cewa Sweety " taso mu ci abinci don ji nake cikina ba komai"

Bayan mun fito parlour nan muka gaisa da umma da Mama suka k'arai mana sannu da
hanya, nan na had'a mana abincin muka fara ci, kasancewar Sweety batada bak'unta
yasa ta saki jiki take kwasar loma😜.

D'aya daga cikin jikokin gidanmu Wanda suke zaune a gidanmu ne ya shigo yana fad'in
" Aunty Nahna wai direban daya Kawo Ku ya gama cin abincin zai wuce"

"To jekace ya shigo su gaisa dasu Mama ko"

Jim kad'an ya shigo suka gaisa yai mana sallama zai wuce nan mukaita mai Allah ya
kikaye hanya, yana amsawa da Amin ya fice.

Wayata na d'auko na kira number d'in Zainab amarya bugu d'aya ta d'auka tana
fad'in "k'aramar uwa yanzu nake shirin kiranki ancemin kunzo"

"Waya fad'a miki munzo"

"Allah da gaske yanzu khairat tacemin kunzo wai taga me motar daya kawoku ma"

"Eh kuwa gamu har mun huta munci abinci"

"To me yasa buku sauka gidanmu ba don Allah Nahna?"

"Lalle ma ga gidan tsohona kawai sai in sauka gidanku, kawai dai zuwa safe in mun
huta zamu shigo".

" Allah k'aramar uwa ban yardaba nidai yanzu ma zanzo in tafi daku ai dai biki
kukazo ba wajan tsofaffin nan ba ".

" hhhmmm ai kuwa bazamu gidanku ba,kuma tsofaffin sune kanku idawa,da bazarsu kuke
rawa".

Dariya Zainab tai kawai ta kashe wayan.

Dake tsakanin Zainab da Nahna ba wani nisa don haka ma suka taso kamar k'awaye,
basa b'oyewa juna sirrinsu, amma dukda hakan Zainab tana bawa Nahna girmanta na
matsayin k'anwar mahaifiyarta.

Sweety kuwa ta samu su mama sunata hira suna bata labarin garin sakkwato da
tarihin kafuwarsa, dake ita d'in gwanar son labari ce ta mik'e k'afa tana kwasan
zance.

Sai wajan k'arfe sha d'ayan dare suka kwanta, sweety tana fad'awa Nahna itafa gari
na wayewa zata fita taga gari,Nahna dai sai mirmishi.

Washe gari muna sallar asuba muka koma bacci ,wajan k'arfe Takwas muna tsaka da
bacci don ko niyar tashi bamuyiba najiyo muryar Zainab a kaina tana fad'in
"k'aramar uwa wai ko tashi bukuyiba har zuwa yanzu,gaskiya Ku tashi haka".

Juyi mukai a tare don karad'in Zainab ba kad'an bane,cikin bacci nace " haba Zee
tun yanzu har kin bar gidanku kinzo ki damemu ko"
"Haba Aunty nah don Allah ki tashi,wlh ina son ganinki matuk'a nai kewarki"

Badan nasoba na tashi zaune ina mita,

Sweety ma tashi tai tana mitstsika ido don dukanmu da bacci tare damu,

Zainab ta kalli sweety tana mirmishi tace "sorry bak'uwarmu na tasheki da


karad'ina ko"

Itama mirmishin tai tana mik'ewa tsaye tace " karki damu amarya ai lokacin tashi a
bacci ma yayi".

Kai tsaye sweety ta shige toilet tai wanka tare dayin brush, tana fitowa nima na
shiga, hira sosai Zainab kewa sweety dake itama uwar magana ce nan sukaita zuba,
bayan na fito ban wani tsaya doguwar kwalliyaba kawai mai na shafa na d'an goga
powder tare da lips stick, nasa doguwan rigan atamfa, na dubi sweety da Take kallon
wani pic d'inmu tun muna yara a wayar Zainab, nace "Taso maje muyi breakfast in
kika biyewa wannan amaryar bazata barki ki huta ba da magana".

Dariya tai tana fad'in " gaskiya Nahna wannan pic d'in yayi kyau zan turashi
wayana in ajiyewa y'ay'anki,suka mamansu sanda tana y'ar shekara shida jibi y'ar
lukuta dake ".

Mirmishi kawai nai araina ina cewa Zainab ta kwafsamin data bar Sweety ganin wannan
tsohon hoton.

A zahiri kuwa rik'o hannunta nai ina fad'in " don Allah ki taso muje mu karya"

Lafiyayyan abinci na samu y'an tsofaffin sun shirya mana, duk da yanzu an kawo musu
masu aiki sabida yanayin girma gashi y'ay'ansu sun kawo k'arfin da zasu iya d'aukar
musu ma'aikata koda sunfi goma , amma hakan bai hanasu shiga kitchen ba da Kansu
suka shirya mana komai, kunun alkamane da had'ad'd'an shayin zob'o a d'aya flask
d'in,sannan ga lafiyayyan k'osai, gefe kuma ga soyayyr doya da kwai, d'aya kwanan
dana bud'e farfesun kayan cikin ragone yaji kayan K'amshi, nan muka zauna muka
b'arji dad'i mukai k'at, bayan mun gama Zainab ta jamu muka fice zuwa inda akemata
gyaran jiki,nan muma samu rabonmu aka D'an mitstsika mana dilka.

Bamu muka dawo gidanba sai yamma lis don ba k'aramin yawo mukai ba daga gidan
gyaran jiki muka wuce kasuwa kuma.

Bayan munyi sallar magriba ne muka had'a kayanmu muka wuce gidansu Zainab sai randa
za'a sata a lalle kuma zamu dawo gidan tunda anan za'ai taron bikin.

Kwananmu Hud'u yau a sakkwato duk mun zagaya gidajan y'an uwa dake kusa min gaisa
Wanda suke nesa kuma nace ma had'u in sunzo biki.

Ana gobe za'a fara bikin mukaje gidan k'unshi aka tsantsara mana ja da bak'i
sannan muka wuce saloon akai mana gyaran kai, Sweety ta had'u da k'awayen Zainab
sun d'inke kamar sunsan juna dake Zainab ma akwai harkar girma dason fafa, don't
haka k'awayenta suka zama wayayyu irin sweety nan suka d'inke abinsu ni kuwa bamai
son hayaniya bace don haka ko hira suka b'arke da ita sai dai inyi mirmishi kawai
ina binsu da ido.

Gidan Yaya Sani anan aka ware amarya da k'awayenta zasu zauna, dake cikin layinmu
gidan,nan muka had'a kayanmu muka kai can,dana k'awayenta da zasu rink'a kwana.

Yau kam za'asa amarya a lalle,gidanmu ya cika yai dam k'am dangi na kusa dana nesa
duk sun hallara bikin mutum uku ai ba wasa ba, bayan La'asar su Yaya suma suka dira
nan mukaita murnar ganin juna,Aunty Hafsah tanata tsokanata wai Nazi Sakkwato na
manta dasu,nikam sai mirmishi kawai nakeyi.

K'arfe biyar jama'a sun cika damk'am a filin da za'ai kamun amarya da ango, nan
muma muka fito cikin ado, kowa ya ganmu yace masha Allah,
Yanayin Al'adun garinmu ya birge Sweety nan fa ta bawa wani yaro jikan gidanmu
camera d'in data taho da ita yai tai mata video d'in abubuwa.

Sai magriba aka tashi,abin gwanin birgewa.

Washe gari akayi dinner,ni kaina na jinjinawa kaina irin kyan danayi,sosai
akamin makeup, gashi ankon bikin ya amsheni nasha gwargwaron ashobe, hakama Sweety
tai kyau matuk'a,musamman dake gwanar makeup ce a fuska itama.

Bayan an dawo daga dinner d'in muna zaune anata hira kundan y'am matan amarya da
raba dare suna hira, hira muke kamar ba gobe naji sweety ta dafoni tana mirmishi
tace "Nahna kinga na d'aura pic d'inmu a status wani ya ganki ya zuzuce".

Mirmishi nai ina fad'in " Sweety ke ko bakida dama".

"Da gaske fa nake, amma nace mishi an miki miji,lokaci kad'an za'ayi bikinki".

Caraf wata k'awar Zainab tace " da gaske an mata miji don Allah?".

"Wlh da gaske an Mata miji , yayana zata aura insha Allah".

Ihu y'an d'akin suka d'auka Iklima na fad'in " Ah lalle sweety Ashe shiyasa agun
dinner d'in nan kiketa tareta kar wani ya saceta,Ashe yayanki kikewa gadi,amma
gaskiya yayanki ya dace wlh da samun one in towns "

Sunata shak'iyancinsu nidai mirmishi kawai nakeyi,don nasan ko nace zan tanka
bansan me zanceba, a haka sukai suka gaji sukai shiru.

Tsawon kwana uku ana gabatar da programs d'in bikin,ana hud'un aka d'aura
aure,washe gari lahadi dandazon maza sukayo kano inda aka d'aura Auran Yaya usman
da amaryarsa Amrah.

A yanda aka tsara ranar Litinin mata goma zasu taho kano domin d'aukar Amaryar
Yaya usman akaita gidanta,kamar yanda yake a al'adance dangin miji ke zuwa karb'ar
Amarya.
Don Haka tun aranar Lahdin da yamma aka kai Zainab gidanta,daga nan muka fara
shirin had'a kayanmu.

Washe gari k'arfe goma na safe motoci biyu na abokan yaya suka d'auko mu zuwa
kano .

Kai tsaye gidanmu suka wuce damu,bayan mun sauka munyi salla tare dacin abincin da
yaya yai mana odanshin daga hotel dake shi tun jiya da suka taho d'aurin aure bai
sake biyosu ba ya zauna, bayan mun huta masu wanka sun k'arayi, k'arfe biyar duka
muka tafi d'aukan amarya Amrah, inda muka samu kyakkyawan tarb'a daga
danginta,kunsan kano garin karrama bak'o ce, 😜 bayan y'an nasihohi da aka k'ara
yiwa marya kamar yanda yake a al'adance aka bamu ita tare da sauran danginta muka
wuce da ita zuwa gidanta dake unguwarmu,nesa da layinmu kad'an don anan yaya ya
samo mai gida ya siya.

Tunda muka sada Amarya da d'akinta bamu dad'eba muka dawo gidanmu,muka barta da
danginta.

Da darema yaya bai bari anyi girki ba don yasan kowa a gajiye yake, take away ya
k'ara yimana,inda y'an tsofaffin ciki sukaita k'orafin sudai basucin wani Abu
daddare inba tuwo ba,kumam dariya kawai mukaita musu.

Duk yanda sweety taso wucewa gida aranar hanata nai,nace ta bari sai da safe zan
rakata har gida,jin haka yasa ta zauna.

Gari na wayewa muka shirya breakfast muka sallami bak'inmu, bayan duk sunci abinci
sukai wanka, ba'a jimaba Yaya usman ya k'araso gidan namu , nan aka gaggaisa ya
k'arai musu godiya,sannan yace " driver da zai maidasu sakkwato yazo".

Babbar mota ce yaya ya d'auka musu don karsu takura,nan suka wuce munata d'agawa
juna hannu cike da kewan juna.

Bacci duka muka koma sai wajan sha d'aya muka farka nan mukai wanka muka shirya, na
had'awa sweety duka kayanta da tarin tsarabar da iyayenmu suka had'a mata da kayan
gyaran biki, nan muka fito Aunty nata mata godiya,yaya ne ya d'aukemu don yace
"tuwan girma miyarsa nama,yanda Mahaifinta ya bamu ita har zuwa sakkwato dole ya
mik'ata da hannunsa tare da mai godiya".

Munyi sa'a kuwa da mukaje Abban na gida bai fitaba wai mura ce ke damunsa,nan ya
taremu da murnarsa,sweety y'ar shagwab'a da murnarta ta fad'a kan Abbanta tana
fad'in " Miss you my Sweet Dad".

Dariya yai yana shafa kanta yace "ya gajiyan hanya data biki,sweetyn Abbah?".

Cikin murnar ganinsa take fad'in " ai Abbah gajiya akwaita, don mun war-wasa".

Dariya yai yana dawo da hankalinsa kanmu, cike da jin kunya da girmamawa na
gaisheshi,ya amsamin cikin sakin fuska da fara'a,yana tambayana gajiyan biki, nidai
duk sai najini a takure,don haka kawai mirmishi nai na sunkuyar da kaina, nan
Auntynsu ta shigo muka gaisa itama tana mana bangajiya,

Hira Yaya suka shigayi da Abbah don haka muka wuce d'akinta,muma hira muka Fara
Wanda duk ta bikice, kusan awa guda Yaya yace in fito mu wuce,nan naitai mata
godiya da irin karar da tai mana, ta rakoni bakin motar mukai sallama yayama
yanata k'ara mata godiya da Allah ya huce gajiya.

Taku ce
Y'ar mutan Ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽


Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽


Zamaniwriterassociation.@gmail.com

KYAN TAFIYA DAWOWA,YAU DAI ALLAH YA NUFA NA DAWO 💃😀


GROUP D'IN Y'AN ARABIC FAN'S KULLUM K'ORAFI SUKE DA TSIMAYI,TO YAU GANI NA
DAWO,MUNA TARE A KODA YAUSHE🤝

0⃣1⃣7⃣ 0⃣1⃣7⃣

Tsawon kwana biyu muna matse gajiyan biki, ban koma gidan ya Usman ba saida yaita
k'orafi ranar da yamma yazo har gidan yace in shirya muje, nan na shirya na shirya
su Ashraf muka tafi tare.

Muna shiga gidan yaya Usman ya fara k'walawa Amaryarsa kira, " precious fito
ga Auta nan naje na d'auko miki ita".

Daga kitchen ta fito tana mirmishi tace " ai da har nayi fishi da ita, nan nan
kusa amma ta kasa zuwa".

Y'ar dariya mai nace "Haba my Aunty kar kiyi fishi da k'anwarki mana, gajiyan
biki ne ya hanani fitowa,amma gashi nazo yanzu".

" OK OK to nayi miki uziri amma yau bazaki fita gidan nan ba sai k'arfe goma
na dare".

Nidai mirmishi kawai nai na zauna,nan muka gaisa ta kawo mana kayan motsa
baki,munata hira harda yaya,ana sallar magriba ya tafi masallaci muma mukai sallah,
bayan min idar nace Aunty Bari mu wuce gida yaya bai son muna magriba a waje".

Daga bayana naji muryan yaya usman yana cewa "ba inda zaku sai munci abinci kunyi
sallar isha'i saimu rakaku".

Komawa nai na zauna ina fad'in "to Yaya".

Abinci ta had'o mana mukaci harda yayan sannan yace ta shirya inya dawo sallar
isha'i su rakamu gida, ai kuwa taita murna zata fita waje, ni dariya ma ta bani
nace
"kwana uku kawai da kawoki shine kike son fita".

" hhhhmmm Nahna ji nake kamar nai wata a gidan nan".

Bayan munyi sallar isha'i yaya ya shigo muka fito, a k'afa yace muje ma motsa k'afa
yai parking motarsa,muna tafe muna d'an hira har muka k'araso gida, a k'ofar gida
muka had'u da yaya ya dawo daga masallaci cikin fara'a yace "a'a amarya harda ke
akai rakiyar, to sannu da zuwa".

A cikin gidama Aunty Hafsa da fara'arta ta tari amarya suka gaisa cikin girmama
juna ta gaida yaya ma tanata jin kunya wai ita ga wan miji.

Nanma hira akaitayi basu bar gidanba sai tara da rabi.

Bayan mako biyu ne aka sasanta da gomnati da ASSU dan haka aka janye strike,nan
muka fara shirin komawa school on Monday.

Tunda muka koma school karatunmu ya k'ara d'aukan zafi,na k'ara maida
hankali sosai ga karatuna.

Lokacin da yaya Usman ya gama cin angwancinsa zai koma bakin aiki yazo ya
samu yaya na yana Neman alfarmar inje gidansa in rink'a kwana da Amrah don tace
tsoro takeji bazata iya kwana ita kad'aiba, nan yaya ya amince,yace ai ba damuwa.

Ranar daya koma bayan sallar magriba na d'auki kayana da zanyi amfani dashi da
safe in zani school da kayan baccina,na wuce gidan yaya usman.

A yanda na sameta kamar Mara ladies tana kwance kan kujera,na k'arasa da Sauri
ina fad'in " Aunty Amrah bakida lafiya ne?".
Lumshe ido tai tana fad'in "lafiyata qlau Nahna kawai ina kewan habeebina
ne".

Y'ar dariya nai nace " kai Aunty nah daga tafiyarsa yau har kin fara kewansa?".

D'an zaro ido tai tace "hhhhmmm khadijah kinsan kuwa me ake nufi da aure? bazaki
gane girman so da k'aunba sai kinyi aure,wlh yau ji nake kamar inyi me Nahna nai
kuka nai kuka harna gaji,ji nake kamar yai wata guda da tafiya don tsananin kewansa
na yini gudan nan".

Cikin mamaki nake kallonta don sai nake ganin kamar Wannan son da Takewa Yaya
usman yayi yawa,ban tunanin zan iya son namiji haka a rayuwata,kai ina bazan iyaba
gaskiya.

A hankali na dafata cikin sigar rarrashi ganin k'walla ta fara kwanciya a


Idonta " kiyi hak'uri Aunty na insha Allah kamar yaune zakiga ya dawo tunda yace
sati biyu zaiyi ya dawo,kuma kinga yacema transfer yake nema zuwa kano insha Allah
nan kusa zai samu ya dawo gida gaba d'aya aita shan k'auna".

Mirmishi tai tace "na gode Khadijah, amma nasan yau da k'yar zan iya bacci wlh".

Nidai a zahiri rarrashinta naitayi amma a zuciyata ina mamakin mata irin
wad'annan masu zazzafan so ga maza.

Da lokacin kwanciya yai tace mu kwanta a bedroom d'inta nace " a'a bari dai in
kwanta a Wannan d'akin tunda shima da gado".

"Meyasa bazaki kwanta anaba ?".

Girgiza kai nai ina fad'in " gadon da mijinki yake kwanciya bai dace in kwanta
akaiba,bama niba kowa ma bai dace ya kwanta kan gadon da kuke kwanciyaba".

Jin jina kai tayi tace "To muje can d'in mu kwanta,daman bama kwanciya Wannan
d'akin".

Mun kwanta muna d'an hira tanata ban labarin Lokacin tana school da rayuwar
boarding school d'insu, nikam sai dariya nake ina jin jina rayuwa irinta boarding
school, wayanta tai ringing da sauri naga ta tashi zaune tana dafe k'irji tace "
wayyo my hubby".

Mirmishi nai kawai nai addu'a na shafa tare da juya baya na lumshe idona ina son
bacci ya d'aukeni don jin yanda take magana da yaya kamar wata y'ar Baby.

Amrah irin matan nan ne masu soyayya matuk'a in tana tare da yaya sai tai ta
baka kunya don idonta rufewa yake taita mai soyayya.

A hankali naji ta dafoni tana fad'in "Khadijah ga yayanki zakuyi magana".

K'arb'a nai nai sallama muka gaisa nake tambayarshi sun sauna lafiya,ya amsa
da eh can yace " Autan Baffah ki kula da Auntynki kinji kirink'a bata hak'uri
kinga dik ta tayar da hankalinta kinji".

"To yaya ba damuwa zan rink'a kula da ita sosai insha Allah karka damu".
Bayan ta karb'i wayan taci gaba da shagwab'anta tana sakar mai wasu zafafan
kalamai,nikam duk jinai kunya ta rufeni nai tsit ban k'ara ko motsiba.

Da safe tana bacci na tashi na shirya abin breakfast naci na shirya zuwa school,
saida zan fita na tasheta " Aunty ki tashi ki rufe gidan ni zan wuce school ".

Da sauri ta tashi tana fad'in " Khadijah bikiyi breakfast ba zaki tafi,wlh bacci
ne ya d'aukeni da nauyi,bari in d'ora miki ko ruwan tea ne kisha".

Mirmishi nai nace "Ai na shirya komai ma har naci nasa miki naki a cooler".

" Ayya sannu da k'ok'ari Nahna na gode ".

Har k'ofar gida ta rakoni ta rufe gidan.

Da yamma dana taso na wuce gida, sai dare na k'ara komawa gidan Yaya Usman.

Ya zama kullum haka nake da magriba in tafi gidan yaya Usman da safe in wuce
school in na tashi kuma in wuce gida,har tsawon sati uku Yaya dawo ya kwana Biyar
ya k'ara komawa,

*****************
Haka rayuwa taci gaba da garawa komai yana wucewa, kwanaki sunja sosai Wanda
ya rage kwana uku UK ya dawo daga karatunsa, tunda labarin nan ya ziyarceni naji
hankalina ya tashi matuk'a na rasa inda zan tsoma raina,sabida nasan lokacin aurena
yazo kenan da Babban mak'iyina.

Kowa dake tare dani ya lura da canjin dana shiga duk walwalata ta kau,don haka
Aunty Hafsah ta Sani a gaba da nasiha da maganganu masu dad'i taita ban shawara kan
in k'ara dagewa da addu'a, anan na d'anji nutsuwa tazomin.

Ana jibi zai dawo Sweaty tazo gidanmu ganin irin yanda yanayina ya canja yasa
ta fara min magana cikin sanyi " Nahna Duk kin canja damuwa ta bayyana tare dake
kuma nasan don dawowar Broth ne,amma don Allah ina Neman alfarmarki daki kwantar da
hankalinki waje guda kamar yanda kikai a baya,ni inaji a jikina tarayyarki da Broth
d'ina alkairi ne garemu gaba d'aya,don Allah karkiyi abinda za'a gane hankalinki
bai tare da yayana har ai k'ok'arin fasa auran nan naku,kinji my sweet Nahna".

Matse k'wallar idona nai nace "sweety bana fatan a samu matsala ta
b'angarena domin zanzama y'ar halak ga Yaya na, kawai dai ina tunanin irin rayuwar
da zanyi tare da d'an uwanki ne bisa dolan da za'ai mishi akaina,nasan bazan tsinci
komai cikin auransa ba sai tsana da tsangwama".

" a'a ki daina fad'in haka My Nahna insha Allah zakiyi alfahari da auran Broth
d'ina zaki sameshi me adalci a gareki kiyi hak'uri ki kwantar da hankalinki kiyita
addu'a kinji".

Share idona nai nace "To ba komai insha Allah zan kwantar da hankalina ki
tayani da addu'a Allah ya daidaita tsakaninmu".
Haka dai taita k'ara kwantar min da hankali,har wajan magriba ta tafi.

Da dare ina kwance d'aki a gidan Yaya Usman ba bacci nakeba kawai tunani
nakeyi, Aunty Amrah na toilet tana wanka,bayan ta gama duk abinda zatai ta rufo
Wancan d'akin ta kashe duk kayan wuta ta shigo d'akin da sallama,a hankali na amsa
mata tazo ta zauna bakin gadon tare dafani tace " Khadijah wai don Allah make
faruwa dake ne? Kullum damuwarki k'aruea take Amma inna tambayeki sai kice Norma
ne,Khadijah yanzu bankai matsayin da zan San damuwarki ba kenan,koda ban kasance
matar yayanki ba ni yanzu na d'aukeki matsayin k'awata kuma y'ar uwa ta, bazan
b'oye miki damuwata ba,don haka Khadijah ki fad'amin meke damunki in na shawara ne
in baki shawara in na addu'a ne in tayaki da addu'a ".

Tashi nai na zauna ina share hawayena nace " Aunty Amrah aure za'amin da mijin
daya tsaneni bai ko son kallona, akan lefin da bansan nai mai ba haka nan tun fara
ganina dashi ya kafawa rayuwata ido ya tsangwameni gashi yanzu aure zai shiga
tsakaninmu".

"Nahna kina nufin auran dole za'ai miki? Duk gatanki duk yanda yayyanki suke sonki
suke ji dake?".

" a'a Aunty Amrah ni a b'angarena ba auran dole za'aiminba,shine dai za'a mai
dole a gidansu don mahaifinsa ne ke son had'amu.. ."

Nan dai na kwashe komai na fad'a mata tun farkon had'uwarmu a school har
alak'ar dake tsakanin mahaifinsa da yaya usman da k'awancan dake tsakanina da
k'anwarsa, da k'ullin da mahaifinsa yake son k'ullawa a tsakaninmu.

Jim tayi zuwa can tace "Nahna gaskiya dole ki shiga damuwa amma Wannan matsala
ce mai saurin warwarewa indai zaki bada had'in kai wlh a sannu Zai soki so ma irin
na mutuwa,amma sai kinyi hak'uri kin sawa ranki cewa bautar Allah zakiyi a cikin
gidan auranki, Nahna shi namiji agun mace ba komai bane matuk'ar ta iya zama dashi
tasan yanda zatayi mu'amala dashi tasan lagonsa da hanyoyin kyautata masa wlh a
sannu zai zama a tafin hannunta,sai yanda tai dashi, Khadijah ki kwantar da
hankalinki ki k'ara addu'a tunda har da bakinki kince kinyi ta istahara kuma duk
sanda kikai kina jin yana Jin tsanarsa ta ragu a ranki to kinga gashi har yakai
yanzu kinajin zaki iya zama dashi kuma bakya k'yamarsa kamar da kinga ai addu'a tai
tasiri kenan,don haka yanzu ma bacci bai kama kiba tashi zakiyi kiyi alwala kiyita
kai kukanki ga Allah, nima bari inyi alwala in tayaki rok'on uban gijinmu".

A zahiri maganganun Aunty Amrah sunmin dad'i don haka na tashi muka d'auro
Al'wala mukai sallah raka'a hud'u mukaita addu'a har bacci ya fara fizgar Aunty
Amrah taje ta kwanta,ni kuwa saida dare ya raba naje na kwanta inajin zuciyata
wasai,( tunasarwa garemu y'an uwa aduk sanda matsala ko damuwa tai mana yawa to
Addu'a kad'ai itace mafita)

" da asuba ma wasai na tashi nai sallah ban koma ba na d'auko k'ur'ani naita
karatu bayan nayi azkar ban kwanta ba sai wajan shida da rabi kasancewar ranar bamu
da Lecture sai k'arfe goma.

****************
Ranar Laraba k'arfe hud'u na yamma UK ya sauka a filin jirgin malam Aminu kano
inda ya sami tarar Abbansa da K'annansa,cike da murna suka tareshi kowa na nuna
farin cikin sa na ganin sa, nan suka d'unguma zuwa gida, nanma ya tarar an shirya
gidan Ka flowers masu tsananin kyau anyi decorations tin daga bakin gate har zuwa
cikin harabar gidan, zahirin farin cikin sa bai b'oyuwa don ganin yanda aka
k'awata gidansu don tararshi kamar wani ango.
Kai tsaye Sweaty tai mai iso zuwa d'akinsa da aka k'awata maishi nanma da
flowers ga kamshin turare air freshener tako Ina, ruwan wankama sweety ce ta
had'amai yaje yai wanka,tsawon awa guda ya d'auka yana kimtsawa kafin ya fito
harabar gidan inda duka family d'in gidan suka had'u suna jiransa, yana fitowa suka
shiga gabatar mai da kayan abinci Abubuwan motsa baki kala kala harma ya rasa me
zaici aciki sai dai ya cakuli Wannan ya fincini wancan, yanaci sunata mai hira
kowa na nuna kulawansa akansa,har akai sallar magriba suka wuce masque shida Dad.

Ranar dai har k'arfe sha d'ayan dare Daddy (UK) yana tsakiyan danginsa suna hira
yana basu lbrn karatunsa.

Da safe k'arfe bakwai saiga kiran waya daga sweaty ina gani naji gabana ya
fad'i cikin kasala na d'aga wayan, "Hello Aunty nah kin tashi koni na tasheki?".

" hhhhmmm Sweaty na tashi tun d'azu harma nai shirin school ".

" OK kin tashi lfy ya gida?".

"Lfy qlau yasu Abbah da Aunty murjah?".

" kowa lafiya qlau yake amma biki tambayi Broth d'ina ba kuma dai kinsan ya dawo".

Jim nai inajin fad'uwar gaba nace " hhhhmmm ni ban San ya dawo ba tunda biki
fad'aminba".

"OK ya dawo to tun jiyama nata kiranki wayanki a kashe in sanar dake ".

" hhhmm To ya dawo lfy?".

"Um lafiya qlau ya dawo yaushe zakizo mai sannu da zuwa?".

" hmm bari zamuyi maganar yanzu zan wuce school ne".
Nai saurin yanke zancan don ban San me zance mataba

"OK to a dawo lafiya Aunty Nah".

Muna kashe wayan na sauke wata nannauyar ajiyar zuciya, tare da d'aukan jakata
naiwa Aunty Amrah sallama.

******
Bayan kwana biyu da dawowar UK da dare yana zaune parlour shida Sweety
sunata hira tana nuna mai hotuna a wayanta,a hankali yazo kan folder d'in hotunansu
na bikinsu yaya usman a sakkwato,yana kalla a hankali yace " sweety a ina kukai
wannan pictures d'in ?".

"Lab Broth a sakkwato ne fa".

" meya kaiki sakkwato ke kuma?".

"Broth bikin yayan friend d'ina nefa mukaje".

" yanzu Abbah ya barki tafiya biki har sakkwato,don sangarta".

"A'a broth akwai alak'a sosai tsakaninmu da ita,kuma yayanta da take gunsa mutumin
Dad ne suna harkar kasuwanci sosai".
" um hmm" kad'ai ya fad'a yaci gaba da kallon pictures d'in,

Yazo kan pic d'in amarya Zainab da angonta a gun dinner ya saki mirmishi yana
fad'in " wannan ne angon ya wani dankama hula kamar bawa, ni ran aurena ma k'ananan
kaya zansa, nasan zagi kawai zansha gun jama'a nikuma maganar kowa baya damuna ".

Cikin zumud'i sweaty tace " oh my Broth don Allah ka kusa yin aure? Ai k'ara
kasa hankali wlh kayi,na matsu naga auranka".

Kallon ta yai dalala cike da mamaki yace " sabida me kuka matsu nayi aure, nawa
nake da za'a matsu inyi aure 30 years kawai shine za'a sa idona akan inyi aure,
haka fa Dad ya matsamin tun kafin in dawo kullum sai yamin maganar aure aure Ku
kamar wasu y'an k'yauye kawai ayi aure ayi aure shine burinku lalle kuwa zaku dad'e
Baku ga auran ba ".

Rik'o hannunsa tai cikin sigar rarrashi take cewa" cool down my Broth mana meye
na d'aukan zafi haka daga maganar aure,shine nan tunda baka so anbar maganar daga
yau".

Komawa yai ya jin Gina da kujerar yana fesar da iska me zafi,

" Sisy kinaji ko wato ban San in matse rayuwa inyi aure tun yanzu daga aure kuma
shikenan sai a fara haihuwa a gidanka shikenan kuma an shiga wani zance na daban,
Haba ina impossible ace guy kamar ni a fara kirana baba kuma Abba Haba baxai yuyu
ba,gaskiya ba yanzu ba zuwa nan dai da 5 years haka".

Kallon sa k'ir sweety keyi can tace " yanzu Broth duk tarin baby's d'in da
nake gani tare dakai daman duk ba sonsu kakeyiba?".

" hhhhmmm gaskiya ke yarinya ce kawai don kina ganina da emmmata kuma duk saisu
zama ina sonsu? Lalle da sauranki, To duk yaran da kike gani girls friends d'ina ne
kawai,guda d'aya ce kawai cikin su Fadlah y'ar k'asar nan ce da muka had'u da ita a
can take nacemin sai munyi aure,to itama bawai auran nata zanyiba amma duk dai
tsarinta yaimin don ta had'u babbar girl ce ko ina tayi gata educated gata so
beautiful, gata gentle babyn tayi kawai don ba aure zanyiba da ita zan aura".

Dammm gaban sweaty ya buga don tasan za'a sha wahla matuk'a kafin a daidaita
dashi akan Khadijah, jitai duk zaman ta gun ya isheta don haka ta mik'e tsam tana
fad'in "broth bari in kwanta na gaji".

" OK good night " kawai yace bai d'ago ya kalleta ba.

Tana shiga d'aki ta fad'a gado zuciyanta fal tunani.

Shikuwa Nan ya zauna yana tunanin me yasa akeso yai aurene,to yama gano
dabara daman so yake ya juya inda ya fito don shi bai tunanin zuwa yanzu zai iya
zama a Nigeria zaman waje yafi komai dad'i a gunsa kayi rayyuwarka bamai sama
ido, don haka bari gari ya waye ma yajewa Abbansu da wannan maganar.

❤❤❤

Readers mu masoyanku ne tunda munayi don ku, amma Ku duk yanda kuka rik'emu babu
damuwa,Masoya da mak'iya duk muna alfahari daku😅
❤❤❤

Taku ce
Y'ar mutan j'aoji.
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

📚 📚📚📚📚📚📚📚

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
JINJINA GAREKI MY NASMAT INA TAYAKI MURNAN KAMMALA NOVEL D'INKI (Y'AR GWAGWARMAYA)
HAK'IK'A MUN ILIMANTU MUN FAD'AKANTU KANA MUN NISHAD'ANTU DASHI,ALLAH YA K'ARA
BASIRA SIS NASMAT
UP
UP
UP
ZAMANAWA KUNAYI MUNA JIN DAD'I 💃
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

0⃣1⃣8⃣ 0⃣1⃣8⃣

Da sanyin safiya Daddy(UK) ya tadda mahaifinsa a turakarsa zaune yana kallon


labarai a BBC, waje ya samu ya zauna cikin girmamawa ya gaisheshi,cike da fara'a ya
amsa mai yana k'ara tambayarshi ya sauran gajiya,ya amsa da babu tare da k'ara
tank'washe k'afa ya fara magana cikin nutsuwa da lankwasa kai " Abbah daman wata
magana na k'ara zuwa da ita,amma ina fatan samun had'in kanka kamar yanda ka saba
bamu had'in kai a dukkan wasu lamuranmu".
Gaba d'aya Alhj Usman ya tattaro hankalinsa ga d'an nasa yana cewa "OK ina jinka
Babana fad'i abinda ke tafe dakai".

" To Abbah daman kan karatuna ne,a school d'inmu sun bamu scholarship mu goma
a matsayin way'anda mukafi kowa k'ok'ari a wannan shekarar cikin duk school d'in,
kan cewar mu zauna dasu mu k'ara wata goma sha biyar mu k'ara wani course, duka
kan business don zasu bud'e company a nan gida Nigeria k'ark'ashin school d'in to
suna son mu kasance ma'aikata na farko da zamu fara aiki companyn kuma y"an Nigeria
d'in suke so, daga bisani in mun gama course d'in sai ai bikin yayemu sannan mu
taho tare dasu a bud'e company mu kasance wakilansu anan Nigeria".
Shiru yai yana tsimayin abinda Abban nasa zaice,
Tsawon lokaci bai magana ba daga bisani ya nisa yana fad'in "Daddy nah naji
dukkan batunka kuma nayi matuk'ar murna daka kasance cikin zakarun shekara a school
d'inku, wannan babban abin farin ciki ne a garemu baki d'aya, sannan naji dad'in
course d'in da zaka k'arayi kan business don karatu ko wane iri ne baya yawa, amma
wani hanzari ba gudu ba Daddy nah akwai abu me matuk'ar mahimmanci a gabanka kafin
wannan, Wanda shine zai shiga tsakaninka da wannan k'udirin naka".

Da sauri UK ya d'ago ido cikin fargaba yana duban mahaifin nasa bakinsa har
rawa yake yana furta " Abbah Abbah meye abinda zai shiga tsaka nina da wannan
babban cigaban da zan k'ara samu?".

Cikin rashin damuwa Abban nasa yace " Aure, Aure nake so kayi Daddy nah, auran
nan shi kad'aine cikar mutuncinka shine Zaisa ka k'ara nutsuwa kayi cikakken
hankali Abbah nah".

A kid'ime yake fad'in " Aure Abbah? Aure fa kake cewa,haba Abbah har nawa nake
da aure zai min shigar sauri haka Abbah, wlh Abbah babu aure a tsarina nan kusa,don
Allah kamin afuwa ka bar maganar nan ka barni in koma in k'ara samo ci gabana. . .
"

Ganin duk yanda ya kid'ime yasa Abban nasa sassauta murya cikin sanyin rai ya
fara magana " Daddy nah meya kid'ima ka haka? Maganar auran kawai shine ka tada
hankali, haba mana Baba na shin ka manta aure shine cikar mutuncin ko wane d'an
Adam ka manta aure sunnar manzon Allah ne, mu ba auran mukai muka haifeku ba? to
haka nakeso kaima kayi auran ka haifamin jikoki,ina son ganin iri daga gareka Abbah
nah,ina so ace nima yau ga Baba nah ya zama babban mutum, ka kwantar da hankalinki
kaji indai don rik'on company ne zan baka guda cikin company nah ka rik'e shi
kyauta ma in kana so,nidai burina kayi auran kaji Daddy nah".

Girgiza kai ya shigayi yana had'a hannaye alamar neman agaji yana fad'in "help me
my hero help me,kamin rai wlh ban shirya ba ni yaro ne Abbah ban kaiba wlh,ina zan
kai mace ni yanzu da k'uriciyata".

Cikin takaici Abban yace " kai d'inne yaro ko ? Shekara talatin harda d'aya kake
kiran kanka yaro saiba iya shege, duk y'an matan da kake kulawa daman ba auransu ka
shirya ba yaudararsu kawai kakeyi ko, to yau anzo k'arshen shirmanka, don haka kasa
aranka Aure ba fashi matuk'ar ina numfashi".

"Wlh Allah Abbah duk y'an matan nan wlh duk friends d'ina ne ni ban tab'a cewa
ko waccansu zan aureta ba, kawai su suke haukansu,Abbah ka taimakeni ".

Gyaran murya yai kana ya daidaita zamansa yana cewa " Abbana kwantar da
hankalinka ka fahimceni,ni na riga da na zab'a maka matar da zaka aura domin na
yaba hankalinta da tunaninta,yarinyar tanada nutsuwa da kamun kai irin matar da
kowane namiji ma'abocin hankali yake fatan samu to irinta na sama maka babana, gata
na gaba da zanmaka a rayuwa kenan tunda na baka ishashshen ilimi Wanda duk inda ka
shiga dashi ka wuce raini,to gashi na zab'a maka mace ta gari abokiyar rufin
asirinka,ina Neman had'in kanka Babana akan auran kaji".

Tunda Alhj Usman ya fara Wannan maganar UK ya shiga comma ta d'an lokaci duk sai
yaji kansa baya aiki brain d'insa ta tsaya cak,

"Ko baka jinane inata magana kai shiru".


Maganar Abban nasa ya katseshi,

Da sauri ya d'ago idonshi cike da hawayan tashin hankali ya rarrafa ya rik'o


k'afafun sa ya fara magana," kaimin rai mahaifina ka taimaki rayuwata ka ceci
farin cikina don Allah nine fa Daddynka Abbah nah baka tab'a yimin abinda bana soba
baka tab'a yimin dole ba a rayuwa,komai da nakeso shi kakemin amma gashi yau
zakamin auran dole, auran dole fa mata akeyiwa Abbah, matan ma marasa gata amma
Abbah ni namiji D'an gata za'a yiwa auran dole,kamin rai Abbah na".

Cikin tarin takaici yace "tashi kaje d'akinka Daddy naga kanka ba dad'i naga
tunaninka ya tsaya cak, jeka inka samu nutsuwa ka dawo muyi magana amma tabbas ba
fashi indai ina Raye da izinin Allahu sai anyi Wannan auran".

Cikin layi da tangad'i ya wuce d'akinsa,kwanciya yai kan fadonsa idanuwansa na


nuna mai komai biyu biyu, a haka bai san iya adadin tsawon lokacin daya d'auka ba a
kwance anan".

*******
Tsawon kwana biyu gidan ba dad'i don Sam Alhj Usman ya d'aure fuskarshi yak'i
barin kowa yazo mai da wata magana akan wannan lamarin,don Aunty murjah tana ta
zuwa da zancan amma sai ya d'aure fuska yace tabar mai wajan bai son wata magana
data shafi Daddy.

Shikuwa b'angaran UK yana ta fishi ko abinci bai fitowa yaci sai dai Sweety ta
kai mai d'aki,duk ya rame yayi fici fici dashi, shi tunaninsa yanda Abbansu yake
bala'in son su yasan in yaga ya shiga damuwa zai janye k'udirinsa,amma abin mamaki
sai yaga har tsawon kwana takwas Abban bai nemeshi ba,kuma basu had'uba ko sau
d'aya don tun daga ranar da akai case d'in bai fito daga d'akinsaba ko salla ma sai
dai ya had'ata yayi don dama ba wani damuwa yayi yayita akan lokaci ba balle har
yashiga jam'i.

Sweety kuwa duk k'aunar da takewa d'an uwanta bata damu da halin daya shigaba
tasan in yayi fishinsa na d'an lokaci zai bari, don kuwa wlh a zahiri da
bad'ininta take son wannan auran.

Abbah fa abin ya fara damunsa don rashin ganin d'an nasa yana damunsa,har sama da
sati yana k'ulle a d'aki, gashi Aunty murjah tana fad'a mai kullum Daddy fa ramar
tashi tayi yawa sai ya nuna mata bai damu ba amma cikin ransa yana jin babu dad'i
amma dai dole ya daure a wannan karon ya fiddaa damuwar Daddy daga ransa.

****
Yau ummu sulaim tazo gida tana zuwa taci karo da halin da D'an uwanta yake ciki
hankalinta ya tashi matuk'a nan taita kwantar mai da hankali " Haba Broth sai kace
mace zaka zauna cikin damuwa haka, kaga yanda duk kamanninka suka canja,don Allah
ka kwantar da hankalinka ka gane gatan da Abbah keson yi maka, kasan dai
mahaifinmu bazai tab'a cutar damuba, don haka kasa a ranka zakayi mai biyayya sai
Allah ya sanyaya zuciyarka".

Cikin kalan tausayi yace "kin San kuwa illar da Abbah yake son yimin, yanzu fa
zab'armu akai mu goma za'a k'ara mana wani course akan business sannan a bud'e mana
company a nan Nigeria, don Allah duk ba d'aukakarmu bace,amma sabida wannan auran
daya k'udura a ransa yace bazan koma ba,wlh tun kafin inga Wannan yarinyar na
tsaneta ban ko son ganinta balle ta shiga rayuwata,duka nawa nake da za'a
durk'usarmin da rayuwata ".

Ita dai ummu sulaim rarrasinsa tai tayi tana nusar dashi akan yiwa Abbansu
biyayya,sannan tace zata zauna har dare in Abbansu ya dawo zata lallameshi ta
rok'a mai ya taimaka koda an d'aura auran ya barshi ya koma yayi course d'insa,don
dai wata goma sha biyar kamar yaune.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร
(Me laya kiyayi me zamani)

A
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

0⃣1⃣9⃣ 0⃣1⃣9⃣

Lokacin da Abbah ya dawo bayan ya huta yaci abinci, Ummu sulaim tazo suka gaisa
bayan sun d'an tab'a hira ta gyara zama cikin nutsuwa ta fara magana "Abbah daman
kan maganar Broth ne,yau da nazo na sameshi cikin yanayi Mara dad'i,Wanda hakan Sam
baimin dad'i, Nai mai nasiha kuma na nuna mishi mahimmancin biyayyarsa gareka da
alherin da zai riska anan gaba da wannan auran,amma Abbah abinda shi broth yafi
damunsa da d'aga mai hankali yamin bayanin course d'in da yake son k'arawa da
alherin da zai riska a gaba inyai wannan course d'in,shine nace Abbah me zai hana
amai alfarma koda auran ne a d'aura sai ya tafi yabarta anan tunda itama Khadijan
karatunta takeyi,kamar yaune zaije ya dawo, a taimaka Abbah a duba Wannan maganar
".

Alhj Usman Wanda tun fara maganarta yake naxarinta ya gyaran murya a hankali ya
fara magana " Ummu sulaim wato dai inna fahimceki son kai zaki nuna ko? Sabida
farin cikin d'an uwanki sai in maida kaina k'aramin mutum idon mutane, mun gama
magana yana dawowa za'ayi bikin sai kuma ince musu zai koma amma a d'aura aure
subar y'arsu a gida ko? Har tsawon wata ba d'aya ba ba uku ba wata har sha biyar".

"A'a Abbah ba haka nake nufi ba,ina nufin in an d'aura auran saita tare da ta
rink'a karatun ta cikin d'akinta tunda yarinyar tanada nutsuwa babu wani kokonta
akanta ko".

Girgiza kai yai tare da fad'in " hhhhmmm ummu sulaim ke yanzu in k'anwarkice zaki
so akaita gidan miji ta zauna tsawon wannan lokaci ita k'adai a gida kuma daga
auran ya tafi ya barta,har yaushe suka zauna suka fahimci juna balle so ya shiga
tsakaninsu um?".

Ummu sulaim da duk dabararta ta k'are tai shiru tana nazarin abinda zata k'ara
k'ullawa, Aunty Murjah wadda duk ta gama jin hirar tasu tana tsaye tana harhad'a
kayan dayaci abinci, ta fita ta dawo sannan ta sami waje ta zauna tana fad'in "Alhj
bari dai insa baki a zancen nan dukda dai ka gargad'eni da k'ara shiga zancen, nace
Alhj in da zaka sassauta ka sauko da sai ai abinda kowa ransa zai d'anyi sauk'i
kuma a sassautawa Daddy,kayi hak'uri a d'aura auran ayi biki da duk abinda akeyi na
hidimar aure sai ta tare anan gidan a wancan part d'in da ba kowa,shi kuma sai ya
tafi d'in kamar yaune zakaga ya dawo,in tana kusa damu ina ganin bazata shiga
damuwa ba tunda ga sweety saisu rink'a kwana tare".

Shiru yai yana jinjina maganar ta, kana daga bisani yace " ke ummu sulaim jeki
ki kirashi ".

Ta mik'e cikin jin dad'i ta tafi kiransa, yana kwance rigingine idonshi
lumshe,ta shigo tana fad'in " broth broth taso Abbah na kiranka an dai daita".

Da k'yar ya mik'e ya fito zuwa gun Abban,bayan ya zauna Abbah ya dubeshi yaga
irin ramar da yai ya fita hayyacinsa,yaji ba dad'i amma sai ya dake yace "Wato
Daddy sabida sunnar ma'aiki kake wannan nunk'ufurcin ko,to hakan ma yayi dai
dai,yanzu dai Auntynka da y'ar uwarka,sun nema ma alfarma, kan wannan maganar,don
haka yanzu za'ayi bikin da komai da komai sai ta tare anan gidan in yaso saika
tafi in Allah ya kaimu lokacin dawowar taka yayi sai Ku tare a gidanku"

Cikin in ina ya fara fad'in "Abbah nifa auran ne bana so gaba d''aya ni duka
banson maganar auran,don Allah kayi hak'uri ka k'yaleni da batun auran nan wlh ko
an d'aura auran nan bazan tab'a son matar ba don tasa an illata ni an
lankwashemin rayuwa haka kawai ni . . .

Tassss Tasss kakeji ya d'aukeshi da mari, " don ubanka ko zaka mutu sai an d'aura
wannan auran,kuma ma tafiyar na fasa barinka,bazaka ba kuma in dai ina raye da
izinin Allah sai anyi auran nan".

Kuka wiy wiy UK yake da idonsa, yana rok'on Abban nasu amma yasa k'afa ya
mangareshi, ya wuce cikin d'akinsa.

Aunty murjah da Ummu sulaim Wanda duk suka mik'e tsaye cikin tashin hankali,
Sweety ta shigo tana share hawaye ganin yanda d'an uwan nata yake kuka kamar
k'aramin yaro, ta rik'oshi tana fad'in "Kayi hak'uri broth ka daina yiwa Abbah
gaddama don Allah, taso ka koma d'akinka".

Itada ummu sulaim suka kamashi zuwa d'akinsa,ita kuma Aunty murjah tabi Abbah
d'aki donta k'ara rarrashinsa amma tana shiga ya nuna mata k'ofa don bai son ganin
kowa tare dashi.

A d'akin UK kuwa kuka yake rizga kamar anmai mutuwa,y'an uwan duk sunyi tsilli
tsilli suma sai sharar k'walla suke an rasa me bakin magana, a haka mijin ummu
sulaim yazo d'aukanta yai mata waya, ta fito su tafi, badan taso ba ta mik'e tana
fad'in " Broth ka kwantar da hankalinka kaji zan k'ara dawowa mu tattauna da Abbah
inya huce,sweety ki kawo mai copy yasha yasha paracetamol kada kansa yai ciwo,
Daddyn Aslam yazo zamu tafi".

Haka sweety taci gaba da rarrashinsa tana fad'a mai kalaman kwantar da hankali
ahaka bacci ya d'aukeshi sannan ta tashi ta for tafi d'akin ta jiki ba k'wari.

*****
Bayan kwana biyu Alhj usman ya sami yaya da zancan sa ranar aure da kai kud'in
auran,nan yaya yace zaiyi waya da y'an gidan can sakkwato abinda sukace zai sanar
dashi.

****
B'angaran UK kuwa ba sassauci ya k'ara sawa kansa tsangwama, duk yana tunanin
Abbah zai gaji ya sauko,ya hak'ura shi duk mamaki ma ya kamashi akan y'ar wani
Abbah zai takura d'ansa,wannan wace irin yarinya ce meye had'in iyayenta da Abbansa
har ya k'wallafa rai akan aura mai ita,kai duk yanda akai mahaifinta Babban k'usa
ne maybe abokin kasuwancin sane kuma yasan tabbas yafi Abbah kud'i da ido a k'asa,
don haka kawai yasa a ransa Abbah wani jarin yake son d'aurawa a kansa don haka wlh
bazai yarda ba Sam".

******
Yaya haroon yaiwa Babban yayansu waya ya shaida mai za'a zo kawo kud'in auran Nahna
dasa rana don haka su shirya ,nan ya amsa da ba komai duk sanda sukazo a shirye
suke, da tararsu.

Da dare ya kira Alhj Usman ya shaida mai yanda sukai da yayansa,ba b'ata lokaci
yace to zai sanar da Abokinsa da Y'an uwansa guda biyu saisu had'u su uku suje.

Ranar lahadi da safe wakilan Alhj Usman suka d'au hanyar sakkwato bisa jagorancin
yaya Usman Wanda direban Alhj Usman usman yajasu.

Tarb'a ta musamman suka samu a gun mutanan sakkwato ina kasa ina ka aje sukai ta
musu , bayan sunci Abincin da aka kawo musu sunsha sunyi k'at daga nan suka fara
tattaunawa kan mak'asudun zuwansu,cikin girma da mutunta juna akai komai nan suka
tsaida Ranar aure wata uku suka bada kud'in aure dana sa rana 100k, haka suka taho
cikin farin ciki da nisad'i na tarar da suka samu.

9⃣
Taku ce
9⃣9⃣ mutan ja'oji9⃣
Y'ar 9⃣
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร
(Me laya kiyayi me zamani)

0⃣2⃣0⃣
0⃣2⃣0⃣ 0⃣2⃣0⃣

Gab da sallar magriba suka shigo gidan don haka Allah alwala kawai sukai suka wuce
masallaci tare da Alhj Usman d'in donshi yaya sauka yai tun a hanya ya wuce
gidansa.
Bayan sun fito a masallaci suka yada zango a turakar Abban nan da nan aka
cikasu da abinci da lemuka,bayan duk sun gama cin abincin yayan Alhj Usman ya fara
sanar dashi duk yanda sukai da irin yarar da suka samu a gun surukan nasu,nan
abokinsa ya d'ora da fad'in " Ai Alhj Usman kayi dace da surukai masu mutunci da
addini, domin kuwa sun mana tarb'a ta k'warai,mun dai daita auran nan da wata uku
cif insha Allah ".

Cikin jin dad'in duk maganganunsu ya fara magana " hak'ik'a naji dad'in albishir
d'inku, daman nasan tabbas duk inda Nahna Khadijah ta fito babban gida ne,dukda
bansan dangintaba bayan yayanta,amma sweety ta sanar dani lokacin da sukaje biki ta
shaida min karamcin zuri'arsu Khadijah to gashi yau na k'ara tabbatar da hakan daga
bakinku, tabbas na sani komin dad'ewa wata rana Daddy zaiyi alfahari da auran
Khadijah ".

Nan sukaita tattaunawa Baffah yace " Usman ina Daddyn yake inmai albishir da
samun gidan surukai manyan mutane".

Jinjina kai Abbah yai kana yace "Baffah ai Daddy baya son wannan auran dole nake
mai. . ."
Nan ya zayyane musu komai daga farko har k'arshe,

Duk kuma sai jikin su yai sanyi Baffah yace " ka sasauta mai dai Usman kabi a
sannu kaita mai nasiha,da kansa zai fahimci alkairin abin,sannan maganar komawa da
zaiyi kayi tuni kan maganar dai karkace zaka hanashi kaji ko".

"To Baffah za'ayi yanda kace insha Allah".

" yawwa sannan ka turomin shi gobe ko jibi zan k'aramai nasiha da Jan hankali".

"To ba damuwa zan turo shi Baffah Allah yaja da rai ya k'ara girma".

Nan yaita yi musu godiya sannan ya kira driver yasa ya maida kowanne gidansa.

******
A can gidansu Nahna kuwa bayan yaya ya koma gida yai sallar magriba ya kira Nahna
da Aunty Hafsah bayan duk sun zauna ya fara magana " Nahna yau munje sakkwato da
wakilan Alhj Usman don nemawa D'ansu auran ki,to duk abinda ya dace anyi , su yaya
Babbah da wakilansa sun tsaida ranar aure nan da wata uku in Allah ya rayamu, don
haka ke Hafsah sai Ku fara shirya duk abinda ya kamata ki samu Amrah ku yi list tun
daga furniture har kayan kitchen duk dai abinda ya dace na gida kuyi list".

Cikin sanyin jiki tace


"To Allah ya sanya alkairi,yasa muna raye za'ayi".

Ni kuwa a lokacin ban San takamaimai halin da nake ciki ba,kawai dai nasan ban
gane sauran zantuttukan da yaya kemin Wanda duk akan hak'uri ne da juriyar zama da
miji, amma kalma d'aya bazan ita maimaitawa ba cikin nasiharsa, tsawon lokaci yana
min maganganu masu dad'i Wanda daga bisani yace " Nahna tashi kije ki k'ara
hak'uri kinji,Allah yai miki albarka".

Hakan ma banji ba saida ya sake maimaitawa na gane me yace,don haka na tashi na


shige d'aki kaina na bala'in sarawa.

Tunda na shiga na kwanta kan gado ban San tsawon lokacin da na d'auka kwance ba
sai da naji Aunty Hafsah na tab'a ni na firgigi ina kallonta, " Nahna bacci kike ne
haka anyi sallar isha'i tun d'azu bikiyi ba,ga Amrah tana ta kiran kwayarki taji
har Tara tayi biki jeba, tashi maza ki tafi kar hanya ta k'ara duhu".

Tashi nai jikina ba k'arfi na d'auki hijab d'ina nasa tare da d'aukan duk
abinda zanyi amfani dashi da safe na zuwa school na d'au wayata na fito parlour,
nan na samesu zaune nai musu saida safe na wuce".

A hanya ma ina tafe tanata kirana ban d'auba tunda naga na kusa da gidan, sanda
na k'arasa nai knocking cikin tsoro tazo tana fad'in "waye nace " nice Aunty
Amrah".
da sauri ta bud'e k'ofan tana k'aremin kallo tace "lafiyanki Nahna? Inata kira
shiru gashi biki shigo da wuri ba yau".

Wucewa nai cikin gidan na aje kayana a saman kujera sannan na gaisheta,ta amsa
tanata bina da kallo, sallar isha'i nai tare da shafa'i da wutiri,na dad'e kan
sallaya ina kai kukana ga ubangiji akan ya daidaita tsakanina da UK don yanzu kam
na tabbatar da shine abokin rayuwata, araina ina tabbatar da tasirin addu'ar da
nakeyi don yanzu Sam banjin tsanar sa kamar da a zuciyata sai dai kuma tsananin
tsoron abinda zan riska a zamana dashi, ban gajiya ba naci gaba da kai kukana ga
rabbil izzati,nakai k'arfe goma sha biyu kan abin sallar sannan na tashi,

Aunty Amrah na kwance kan gado tanata zuba soyayyarta da mijinta a waya, ko
kayan jikina ban k'ok'arin cirewa ba na haye gadon,addu'a nayi na tofa, ina rufe
idona naji maganarta " Nahna "

Ban amsaba sai bud'e ido danai ina kallonta,ta d'ora ". Nahna Aunty Hafsah ta
kirani kina sallah ta sanar dani an tsaida ranar auranki wata uku nan gaba, na
tabbatar wannan maganar ce ta sauyaki yau duka na ganki wata iri,a kullum Nahna
ina k'ara fad'a miki k'iyayyar UK gareki bamai zuwa ko ina bace,tabbas akwai abinda
Allah yake nufi da lamarinku tun daga had'uwarku har yanzu da Allah zai k'ara
had'aku a matsayin ma'aurata,ki kwantar da hankalinki,in kina nuna damuwarki ga
lamarin nan zaki tayar da hankalin y'an uwanki,kuma kin shaidamin kina son farin
cikin yayyanki sama da farin cikinki koba haka ba?".

Gyad'a mata kai nai ina k'ak'alo mirmishin yak'e nace " karki damu Aunty Amrah
insha Allah zaku sameni yanda kuke so,matsala dai daga gareni akan wannan auran
baza'a tab'a samu ba".

"Yawwa Sistanmu haka nake son ji daga bakinki,muyi bacci dare yayi".

******
A gidan Alhj usman kuwa UK ya sami labarin Neman da Baffah yake mai,dukda bai
San ankai kud'in auransa har ansa masa ranaba tabbas amma yasan bazai wuce dalilin
auran nan bane ake nemansa, washe gari da yamma ya shirya ya tafi gidan
Baffah,yanda yakejin jikinsa ba k'arfi yasa ya nemi driver yakaishi.

Tunda suka gaisa da Baffah yake binsa da kallo da irin ramar da yayi,nan yai
gyaran murya ya fara magana" Daddy mun tattauna da mahaifinka ya shaida min
gaddamar da kake yi mishi bisa umarnin daya baka,shin Daddy kana son ka haifi
y'ay'a suyima biyayya?shin kana tunin zaka shiga aljanna in har ka mutu a wannan
hanyar ta sab'awa mahaifinka? Daddy ka Sani koni Hajiya bani na ganta nace ina
soba,mahaifina ne ya zab'armin ita a matsayin matar da zan aura,kuma na aureta a
gaba naga alkairin hakan don haka ba umarni ba ina baka shawara da kayiwa
mahaifinka biyayya zakaga alkairi a gaba kaji ko Daddy?.

Duk jikinsa a mace murus ya d'aga kai alamar gamsuwa da maganar,


Nan Baffah ya d'ora da fad'in " kaga munje Sakkwato mun kai kud'in aure dasa
rana,an tsaida lokaci wata uku masu zuwa,
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

*ALLAH* *KA* *SHIGA* *LAMARINMU* , *ALLAH* *KARKA* *BAR* *WANI* *BAWANKA* *YA*
*CUTAR* *DA* *RAYUWARMU* 👏

0⃣2⃣1⃣
0⃣2⃣1⃣ 0⃣2⃣1⃣

Kamar saukar ruwan zafi haka yaji batun Baffah,wato ma har ansa mai rana wata uku
wayyo Allah ina mq ya mutu ya huta da ganin bak'ar ranar nan,

Baffah baiyi k'asa a gwiwa ba yaci gaba damai nasiha cikin salon kwantar da
hankali " Daddy Kaga sabida gaddamar da kaiwa mahaifinka har yace ya fasa ma
barinka ka koma,don haka yanzu inka koma gida kaje ka sameshi ka bashi hak'uri kace
ka amince da auran,yayi hak'uri ya barka ka koma ka samo ci gaba, ka kaskantar da
kanka ka nemi gafarar mahaifinka kaji domin ka b'ata masa rai matuk'a da gaske,
kuma albishir d'in da zanma kayi dace da mace y'ar babban gida,idan nace y'ar
babban gida ina nufin gidan Addini da Tarbiya, na tabbatar inka auri yarinyar nan
zakai alfahari a gaba har ka godewa mahaifinka da yaima wannan gatan, ka tashi
kaje gida ka baiwa mahaifinka hak'uri kaji ko".

Jiki ba sanyi yawa Baffah sallama ya fito driver yaja suka wuce gida.

Kai tsaye d'akinsa ya wuce ya kwanta bisa gadonsa yana fidda wata k'walla me
zafi a gefen iidonsa.

Sai da dare ya fito zuwa d'akin Abbansa ya sameshi zaune yana kallon
labarai,waje ya samu ya zauna jiki a sanyaye ya gaida shi,cikin rashin kulawa ya
amsa mai ba tare da ya ko kalleshiba, jim yai a zaune duk jiki ba laka, can dai ya
numfasa ya fara " Abbah don Allah kayi hak'uri ka yafemin,nayi nadamar gaddamar da
nai maka,yanzu na fahimci abinda kake nufi na yarda da auran nan bisa umarninka".

Kallonsa sosai Alhj Usman yai yana nazarinsa tsawon y'an mintina yace " Daddy
kayi abinda banyi tsammanin zakayi minba ka bijiremin a lokacin da nake Neman
had'in kanka, Daddy na soka matsayin d'a mafi soyuwa gareni na nuna ma dukka nin
gata da ake nunawa ko wane d'a,naso farin cikin ka dukkan muradinka shine nawa,
babu abinda na rageka dashi Daddy amma Nazo da buk'ata ta karo na farko gareka amma
ka watsamin k'asa a ido,kasa k'afa kai facali da buk'ata ta ko ".

Cikin nadama da k'asa dakai yake fad'in " ka gafarceni Daddy yanzu na amince
zanma biyayya, fata na d'aya in an d'aura auran nan ka barni in koma in samu ci
gaba Abbah ".

" daman nasani Daddy nasan don buk'atar Kane yasa kace ka amince badan farin
cikina ba,amma dukda haka ina jan kunnanka daka zama d'a abin alfaharin iyayensa,
kuma in amma d'aura auran saika kwana biyu yarinyar ta saba dakai naga rik'on
ludayinka sannan zaka Taci, badanma yarinyar karatu take anan makarantar daga gama
Sa'adatu rimi ai da tare zaku tafi ma can k'asar,amma dukda haka inta sami Hutu ta
rink'a zuwa maka hutu, tashi kaje Allah yai maka albarka ".
Jiki a sabule ya tashi ya fad'a d'akinsa,yana zama gefen gado dafe da kansa
tai sallama ta shigo d'akin,d'agowa yai yaw kalleta ba tare daya amsa
sallamarba,itama bata damu daya amsa ba ta sami waje ta zauna, daf dashi ta rik'o
hannunsa tana fad'in " broth yada Irin wannan tagumin haka,don Allah ka sararawa
kanka, kar wani ciwon ya kamaka, Broth matar da Abbah ya zab'a maka abin alfaharin
kowane namiji ce, tanada rik'o da addini matuk'a".

Cikin zafin rai yace "sisy na samu Abbah na fad'a mai na amincewa auran nan
amma wlh inna bar k'asar nan banda ranar dawowa,don k'iyayyar auran nan a can
k'asan raina take, sweety bani labarin wace yarinya Abbah zai auramin har kuke
zuzuta ta haka y'ar wace ce meye matsayin mahaifinta a k'asar nan meye matsayin
karatunta,yaya wayewarta take ?".

Dimm sweety taji gabanta ya fad'i don Duk abinda UK ya lissafo tasan babu
abinda Nahna take dashi banda ilimi, amma cikin k'arfin gwiwa ya dakewa tace ina
zuwa Broth bari in d'auko wayata in nuna maka pic d'inta, daga haka tasa kai ta
fice zuwa d'akinta cikin minti biyu ta dawo da wayarta,wajan data tashi ta koma ta
zauna ta fara mai magana cikin kwanciyar hankali " broth sunanta Nahna khadijah
y'ar asalin garin Sakkwato ce, mahaifinta ba Kowa bane face tsohon alk'alin
musulunci a garinsu Allah yamai rasuwa tunda dad'ewa, tana zaune hannun yayanta
wanda aiki ya kawoshi kano, yanzu haka suna huld'ar kasuwanci da Abbanmu,
danginta duka ma'abota addini ne kuma duk suna karatun boko masu rufin asiri
ne matuk'a domin kuwa sunfi k'arfin komai na buk'atar rayuwa, amma baza ace musu
masu kud'i ba, zuria'ace abin shawa'a da birgewa, don haka ma Nahna ta kasance
mai kyakkyawar d'abi'a, matsayin karatunta N.C.E ne y'ar Arabic ce Nahna inda
yanzu take degree d'inta a Sa'adatu Rimi college of education, tana karanta
Shari'a low, tun farkon karatunta Islamic Arabic take karanta har izuwa yanzu
atakaice dai Nahna *y'ar* *Arabic* ce, itace wadda nacema naje sakkwato bikin
Yayanta, a halin yanzu banda wata babbar k'awa data wuce ta".

Cikin takaici ya dakatar da ita da hannunsa yana girgiza kai tare da fad'in
"yanzu Duk cikin labarin yarinyar nan sweety meye abun birgewa,meye abun Jan
hankali, wane Abu zan fad'awa friend d'ina guda d'aya in sun tambayene labarin
matar daza'a aura min, maza da sauri fitomin da pic d'inta in gani in k'arasa
d'iban takaici".

Cikin sarewar gwiwa sweety ta shiga lalibo pic d'in Nahna cikin wayarta tana
nuna mai,

A firgice yake kallon pic d'in yana nunashi da yatsa " wannan itace yarinyar
da ake k'ok'arin lik'amin,gidahuma da ita me halin y'an k'auye, *Y'ar*
*Arabic* ??? Yarinyar da inuwarmu bata had'uwa na tsaneta tun tuni,sabida rashin
wayewarta,a farkon kallona da ita taimin kama da wayayyiya amma ina latsata na gane
ba komai tare da ita sai hauka da k'auyanci, wlh an cuceni an gama dani,na shiga
uku ni yanzu wannan yarinyar zan gani matsayin matata? To wlh Allah inma ita ta
bibiyi rayuwata tabi Duk hanyar databi tasa wanta ya lik'awa Abbah ita don na
aureta to wlh ta tafka kuskure ta halaka kanta, me zanyi da auran *Y'ar* *Arabic*?
Hhhmmm lalle yarinyar nan tasa kanta a bala'i wlh saina azabtar da ita matuk'a,
wato game d"in da muka buga a college ne bai isheta ba shine ta bibiyi rayuwata
tsawon wannan lokacin ".
Rik'o hannunsa sweety tai cikin kuka tana fad'in " haba broth me kake fad'a
haka,don Allah karka cutar da y'ar mutane ,wlh ita batama sanka ba in banda a
photo. . .

"Waye yace miki haka waye yace bata sanni ba k'arya take miki wlh pretend ne
tasanni tsaf ita tasan abunda ta k'ullo amma ki barni da ita,zan maganinta".

" broth wlh Nahna mutuniyar kirki ce, kuma wlh itama Sam bata son auran nan kamar
yanda baka so,kawai biyayya takeyi,broth don Allah ka rik'eta amana wlh ina sonta
sosai mutuniyar kirkice Nahna ".

Dariyar mugunta yai yana fad'in " tashi kije ki kwanta dare yayi kibar kukan
nan".
Kamar bazata tashi ba amma ganin ya had'e girar Sama yasa ta mik'e ta fice ranta
d'auke da nauyi.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣2⃣2⃣
0⃣2⃣2⃣ 0⃣2⃣2⃣

Tunani ne ya cika zuciyar Sweety, shin wai dama akwai sanayya tsakanin Nahna da
broth d'inta, amma kuma ai Nahna bata tab'a nuna mata tasan shi ba,koda ta ganshi a
photo ai bata nuna sanayya tsakaninsu ba,amma dai Gobe Duk yanda ake ciki zata nemi
Nahna taji komai, tana wannan tunanin har bacci ya d'auketa.

A gidansu Nahna kuwa koda yaushe mik'a lamarinta ga Allah take, bata dogon
bacci kullum tashi take cikin dare tana kai kukanta gun me share mata hawaye, don
haka koda yaushe take jin zuciyarta na mata sanyi,kamar ba wani abu gabanta, Sam
take jin tsanar UK da tsanar auransa na fita cikin ranta,Duk da baza tace ta fara
son abin aranta ba amma baza tace tana k'insa kamar farko ba.
Da yamma lik'is Sweety tazo gidansu Nahna bayan sun gaisa da Aunty suka shige
d'aki,cikin fara'a sa tsokana ta dubi Nahna " Aunty nah zance ko amarya zance?".

Mirmishi Nahna tayi tace "ko d'aya karki fad'a,in bazaki kice Nahna ba kice
Khadijah".

" a'a ni yanzu wannan sunan yamin nauyi a baki ai sai mutane suga rashin
kyautawa ta ina fad'ar sunan matar yayana".

Dukanta tai a baya tana fad'in "ai kuwa Duk abinda zakice in dai ba Nahna ba ko
Khadijah bazan amsa ba ".

Dariya sweety tai kana ta gyara zama kan gadon tana fad'in " kai gaskiya Nahna
kina da zurfin ciki na bala'i wlh,yanzu Duk tsawon zamanmu dake ace biki tab'a
nuna min kin san Broth ba koda wasa,ashe akwai sanayya tsakaninku,to shi ya
fad'amin kun Dan juna a college ba kad'anba don zumunc kukai sosai ".

Zaro ido Nahna tayi ba tare data tuna ba ta fara fad'in " kai sweety UK d'in ne
yace miki munyi zumunci?to wlh tsawon sani na dashi a college ba wani Abu na
arzik'i daya tab'a had'a mu in banda tsantsar tsanar juna da tsangwama da
yakemin,Duk inda nake UK sai ya bibiyeni yaje ya tozar tani ya wulak'anta ni gaban
tarin jama'a,har randa na daina ganinsa a skul d'in".

Ruk'o hannunta sweety tai ganin yanda yanayinta ya sauya lokaci guda tace "kiyi
hak'uri Nahna amma don Allah ina son ki fad'amin tsakani da Allah komai dake
tsakaninki da Broth tin farkon saninki dashi".

Nahna bata b'oyewa Sweety komai ba ta sanar da ita tun farkon had'uwarsu,idonta
yana tara k'walla ta k'arasa zancen , hannu sweety tasa tana sharewa Nahna ido "
kiyi hak'uri Nahna don Allah karki k'ullaci Broth a zuciyarki,karki k'ulla ceshi
hakan zai hanaku jin dad'in zaman aure,matuk'ar kina tuna Irin haka bazaki tab'a
ganin farinsa ba zaki rink'a jin tsanarsa a ranki, nasani Nahna Ke me ilimi ce
sanin addininki yana miki amfani,don haka nasan auranku zaiyi albarka Duk abunda
yaya zaiyi gareki don Allah ki daure Nahna komai lokaci ne wata rana ba zaiyi ba
kinji Nahna, hak'ika Duk wanda yaji wannan labarin yasan akwai wani abu da Allah
ya b'oye gareku shiyasa harya had'aku a baya cikin rashin fahimta yanzu kuma ya
had'a Ku matsayin ma'aurata,tabbas akwai wani Abu da Allah ya b'oye tsakaninku kiyi
hak'uri kinji don Allah ".

Mirmishi Nahna ta k'ak'alo tana Gobe k'wallan idonta tace " karki damu sweety
Duk wannan na san yana cikin k'addarata, auren UK babbar k'addara ce gareni wanda
sanin tsakanina dashi yasa hankalina ya tashi amma dana kai kukana game sharemin
hawaye sai naji Duk hankali na ya kwanta, ni yanzu banda wata matsala da wannan
auren domin na rok'i ubangiji zab'i kuma da alkairi don haka karki damu,insha
Allah ni dai daga gareni babu wata matsala kan auren nan matsalar tana ga d'an
uwanki".

"Insha Allah shima ba wata matsala zaku zauna kuyi rayuwarku cikin kwanciyar
hankali harku Tara mana baby's ma ".
Ta k'arshe tana dariya,girgiza kai kawai Nahna tai tana mirmushi don bata da abin
fad'a, sun dad'e suna hira har aka fara kiran sallah nan sukai sallah sannan sweety
ta wuce gida.
************
Kwanaki ba jira suke ba,don gashi yau an cinye wata Guda dasa ranar Nahna da UK
wanda yanzu ya rage wata biyu, sweety ta matsawa Nahna su fitar da anko amma fir
tak'i tace ita bata da sha'awar yin anko a bikinta, ganin ta kafe yasa sweety yiwa
Aunty Hafsah maganar, nan tace karta damu zata mata magana ta shirya suje Gobe su
fitar.

Da dare Nahna na zaune parlour tana koyawa su Ashraf Assignments kasancewar yaya
usman na gari bazata kwana gidansa ba, Aunty tazo ta zauna gefenta tana fad'in
"wannan assignment d'in bai k'areba ne har yanzu?".

" a'a mun gama yanzu Aunty bayani nake musu dai , wani abin za'a miki ".

" a'a magana nakeso muyi,Kai Ashraf had'a books d'in na kai d'aki".

Bayan yaran sun shiga d'aki Aunty ta dubi Nahna sosai tace "Nahna ki shirya Gobe
kuje kasuwa da Sweety zaku fitar da anko,sabida Kinga rannan ma Su Aunty sukayo
waya suna tambayar bamu fitar da anko ba har yanzu, Kinga saiku fitar harda namu
na yini ko".

Kallon Aunty tai kamar zatai kuka tace "Aunty wlh ban sha'awar anko gun bikin nan
kawai a barshi ".

" Nahna kina so ki nunawa duniya baki son auran nan kenan,kullum sai kice mana
bakida matsala da aurannan amma yanzu kuma zaki fara tsiro da zancen kin yin anko
tun a matakin farko,don haka ki shirya gobe kuje ".

" Tom Aunty Allah ya kaimu " bazata iya yiwa Aunty gaddama ba don haka tace haka
taja bakinta tai shiru".

*****
A gidansu sweety tana zaune gaban Abbansu tana fad'a mai zancen siyo ankon da
zasuyi " Abbah ka bamu kud'i mu fitar da anko kasan miji Ke bada kud'in anko".

Cikin jin dad'i da nishad'i Abban yace "karki damu ga ATM kuje dashi Duk abunda
kuka siya ba matsala Ku ciri kud'i".

D'auka tai tana fad'in " yawwa Abbana, don hidima fa nakeso muyi da bikin nan
bikin babban yaya ba wasa ba ".

Aunty murjah ce tace " in kunje Nahna sai Ku fitar mana da less me kyau na yinin
bikin na manya anunawa dangi".

"Tom ba matsala Aunty kuma zamu zab'o muku cancad'ed'e "

*******
Washe gari misalin k'arfe goma sweety tazo gidansu Nahna ba b'ata lokaci suka
tafi,suna zaune a gidan baya yayin da Driver Ke driving nasu, Sweety keta hira ita
kam Nahna sai dai tai mirmishi kota d'an tanka kad'an don batajin hira ko kad'an
yau d'in Duk da kasancewarta daman bamai yawon hira ba, a k'ofar Mudatex sukayi
parking tacewa driver ya jirasu zuwa awa d'aya.

Kai tsaye suka shiga wajan kasancewar daman sweety batada wajan siyayya a kantin
kwari inba Mudassir and brothers ba, nan taita gaggaisawa da y'an shagon Duk sun
Santa sunata fad'in hjy Ruk'ayya sannu da zuwa,nan ta sami waje ta zauna ta nunawa
Nahna wajan zama itama, yaron wajan ya iso suka gaisa sweety tace " Allah yasa an
kawo kaya,don ban son gama gari ".

Dariya yai yace" hjy Ruk'ayya mu wuce Sama akwai kaya ko fito dasu ma daga sito
ba'ayiba,muje ki zab'a son ranki".

Sosai ta baje take zab'ar kala yayinda yaron gun Ke taya zab'ar kala,ita kuwa
Nahna ta zama y'ar kallo sai mirmishi kawai takeyi wanda daman shine d'abi'arta
koda yaushe zaka riski fuskarta da mirmishi,koda bazatayi magana ba,

Wani had'ad'd'an less suka zab'a me kyau matsayin ba dinner,sannan suk'a k'ara
zab'i wani less kuma na dangin su sweety na mother's day, ta kalli Nahna tace "
Nahna naku fa na yinin wane kala zaku zab'a ?"

Jim Nahna tayi tana tunanin gaskiya bazata d'orawa danginta wahala ba don wannan
less d'in tanaji suna cewa Duk 1 yard 2500, tayaya zata fitar dashi matsayin ankon
yini don dai dai ruwa dai dai tsaki,su danginsu zasu iya siya ko na nawa ne amma
ita danginta masu k'aramin k'arfi ne don haka bari ta nemi me sauk'i,

Jin sweety ta k'ara magana yasa ta D'an d"aga ido tana kallon kayan gun kana tace
" gaskiya bari mu zab'i atamfa mu don nasan zasufi sonta,tunda Kinga muna da
tsofaffi da yawa a danginmu kuma su sunfi ganewa atamfa".

Ta fad'a cikin dariya, itama sweety dariyan tayi,tace "To mu zab'i wadda kike
ganin zata yiwa Kowa kyau,

Nan suka fitar da wata me kyau kud'inta 3500 tirmi d'aya, tun a shagon sweety uwar
azarb'ab'i ta d'auki hotunan ankon ta d'ora a dp da status d'inta.

Koda suka dawo gida Sweety ta fito da kayan tana nunawa Aunty Hafsah ta jin jina
musu sun zab'o anko me kyau,nan itama ta d'auki hoton less d'in dinner d'in da
atamfar yini ta turawa mutanan sakkwato.

Da dare Aunty Amrah tazo gidan don ganin ankon tunda Yaya usman yana gari Nahna
ba zuwa gidan zatayi ba, nan Yaya Haroon ya cewa Aunty Amrah ta shirya cikin satin
zasu shiga kasuwa ayo Duk siyayyan kayan d'aki dana kitchen.

Yayyena maza da mata da iyayenmu mata Duk sun turo da gudun mawarsu ta account
d'in yaya,Kud'i ne ba na wasa ba aka Tara don yayyena suna ji dani matuk'a
kasancewata auta cikinsu, ga rashin mahaifi don sun san babu me yimin saisu, kuma
uwa uba ance musu gidan masu abin hannu zan shiga dole su k'ara k'aimi wajan
k'awata min gidan don gudun raini da wulak'ancin dangin miji da jama'ar gari.

Kwana uku a jere suna shiga kasuwa an siyo min furniture Irin wanda ake yayi gado
7by7 Mbf guda d'aya sannan normal set d"aya , kujeru ma set biyu akai min da
k'atuwar TV d'ina da firji ga kayan kitchen komai yaji. Haka aka had'asu Duk aka
rufe yaya ya kai gidan abokinsa jikin gidanmu ajiya sabida akwai k'aton gareji a
gidan basa amfani dashi nan aka had'a Duk aka k'ulle.

A nan na k'ara tabbatarwa kaina ni y'ar gata ce gaba da baya ganin Irin uban
siyayyan da akai min.

A can gidansu sweety ma shiri sukeyi sosai don Aunty murjah da ummu sulaim kasuwa
suke shiga koda yaushe had'a lefe na ajin k'arshe Abbah ya bud'e bakin aljihu so
yake ayi abin harkar girma, b'angaren ma da zasu zauna Duk da daman ba kowa a part
d'in k'alau yake amma Abbah ya kawo ma'aikata suna k'ara tsara gun an k'ara fito
dashi yanda baka zato.

*******
Biki ya rage sati hud'u aka kawo lefe,subhanallah zo kuga kayan arzik'i abin
ba'a cewa komai fa don Abbah basuyi la'akari da cewa Nahna ba y'ar kowa bace balle
ayi mata kaya kad'an,a'a sakin jiki akai aka sa mata suttura masu matuk'ar tsada da
kyau, English wear's akwati biyu aka cika dashi had'ad'd'u na gaske, lokacin da
Yaya Haroon yaga kayan ya kira Alh Usman a waya yake cemai wannan uban kaya ina
Nahna zata kaisu,mirmishi kawai yai yace duk abunda akaiwa Nahna na aure ta kai
amata nutsuwarta kamun kanta tarbiyarta da iliminta Duk sun kai a kashe mata ko
nawa ne, nan Yaya ya k'ara godiya ya kashe wayan.

K'awaye da y'an unguwa tako ina suka rink'a tururuwar zuwa kallon lefe kowa
yazo yace alasan barka,

A b'angaran UK kuwa mamaki yake yanda yaga Duk danginsa rawar k'afa suke da auran
nan wanda shi shirin sa ma kawai yakeyi na tafiyarsa, bai damu da wani shiri ba,
don baya tunanin zayyi wani event ko d'aya don bai san me zai cewa abokansa ba in
sukaji zai aure kuma ma abin bak'in cikin ace wai y'ar Arabic Mara wayewa zai aura
masu yawo da hijabi kullum.

Ita kuwa sweety ta dage events sosai takeso ayi yayin da ta rasa had'in kan
Amarya da ango ita Nahna tace Sam bata sha'awar wasu bidio'i a bikinta,tafi so ayi
walima kawai aka d'aura aure, yayin dashi angon ya kafe babu wanda zai gayyata
balls azo aga Irin matar tasa, don haka babu wani event ko d'aya da za'a yi, jin
hakane yasa tai k'wafa tana nazarin hanyar da zata b'ullo musu.

Da dare sweety ta shiga d'akin UK baya nan sai wayarsa ajiye kan kago,mirmishi
tai ta d'auki wayan kai tsaye ta shiga contacts d'insa ta fara tura I.V d'in bikin
tai marking baki d'aya cikin sauri ta ajiye wayan ta fice,

Bayan kusan 20 minutes ta jishi yanata k'wala mata kira,lokacin tana gaban Abbah
suna hira a dake ta amsa harya shigo parloun kome ya tuna saiya juya ya tsaya
bakin k'ofa yana cewa tazo, cikin basarwa taje tace "gani broth"
Cike da masifa da b'acin rai yace " Sweety waye ya d'aukarmin waya ta d'azu"

Nunawa tai Sam bata san zancen ba nan ya hau masifa yana fad'in "ni za'a
rainawa hankali a d'auki wayata kawai a turomin abinda banda niyar turawa don q
wulak'anta ni".

Daga bayanshi ya muryan Abbah yana fad'in " kaida waye ne Baba na,waya tab'amin
kai?"

Dummmm yaji gabansa ya fad'i,toshi yanzu zai cewa Abbah katin auransa aka turawa
abokansa ne kome,kawai Sai yw basar yace "wlh Abbah ban san wanda ya d'auki wayata
yamin shirme a ciki ba,kuma tabbas nasan bazai wuce wannan yarinyarba amma gashi
tana min musu wai ba ita bace".

Hak'uri Abbah ya shiga bashi yana fad'in koma waye yayi hak'uri yabar zancen,
cikin fishi ya koma d'akinsa,ya zauna bakin gado dafe da kanshi, tsaki kawai yake
ta ja, don yanda wayanshi taketa ringing yasan abokansa ne suke fama kira don
tabbatar da sak'on daya shigo musu,da bak'in ciki ma ya ishe shi saiya kashe wayan
baki d'aya ya koma ya kwanta kansa na sarawa kamar zai fashe.

Da safe bayan ya kunna wayansa, tarin sak'on ni ne suketa shigo wa abokai nata
masa k'orafi kan zaiyyi aure amma bai sanar dasu da wuriba ciki harda manyan
abokansa aminansa, baiyi mamaki ba saida ya bud'e Datan shi ya chiga net nan yaga
inda aketa cacca karsa tako ina,rasa abinda zai fad'a musu yayi don haka kawai ya
shiga bada hak'uri kan cewa auran ne yazo mai ba zata shima bai shirya wa hakan
ba,a haka ya samu ya rufe bakinsu, amma tarin takaicinsa dayaji kowanne na cewa
zaizo,dana k'asar da way'anda ba y'an k'asar ba,ya tabbatar kashinsa ya bushe,
asirinsa ya tonu kenan,kamar yace musu basai sunzo ba amma yasan hakanma wani
watsa kansa zai k'arayi,don haka yanzu kuma dole ya nemi mafita ta gaba kuma, don
haka ya kira number d'in abokin sa mashkur yace da yamma su had'u zasuyi magana.

*****
Da yamma suna zaune a balcony kan kujerun roba shida mashkur bayan sun d'an
tab'a hiran abokai ,ya gyara zama yana cewa" Wato kanaji ko Mashkur wannan auran da
kukemin k'orafin buku sani ba sai yanzu daya rage 2 weeks wlh banda shirin yinsa
nan kusa, Abbah ne lik'amin shi kai kasan banda wani tsarin yin aure shekaru
kusa,to babban abin takaicin ma abokina zaka iya tuna lokacin da muke SA'ADATU
RIMI Lavel 4 wata yarinya y'ar Arabic dana matsawa na tsaneta wata yarinya nan
kamar wayayyi ya amma lokal ce ka tunata?"

Jim Mashkur yayi can yace "ohhhh wlh na tunata tabbas na tunata wata y'ar black
beauty ko y'ar Arabic na tunata meya faru?"

Yawun takaici UK ya had'iye kana yace "Mashkur wai wannan yarinyar fa Abbah zai
aura min".

Da sauri ya k'ara kallon shi " haba dai UK meya had'a ka kuma da wannan
yarinyar?"

Yak'e yai wanda yafi kuka ciwo nan ya fayyace mai komai, shuru Mashkur yayi
kamar ruwa ya cinyeshi can ya nisa yace "Yanzu dai me faruwa ta faru sai asan
yanda za'a gyara gaba domin duk abunda za'a yi a kare mutunci shi za'a yi inba
haka ba abokai su rainaka".

" eh nima hakan nake nufi don kasanni ban san harkar k'aranta, ko abunda za'a
rainani,don haka ka bani shawarar yanda zanyi".

"Ai mafita gudace yanzu a k'awata bikin sosai a shirya programs zafafa ita kuma
amaryar taka tunda ustaziya ce kaja mata kunne ka gargad'eta kan ta fidda ka
kunya Kar aje gaban abokai za'ai harkar wayewa tazo tana sissinne Kai".

Jin jina kai UK ya shiga yi nuna gamsuwa da shwarar Mashkur nan sukaita
shawarwari sannan Mashkur yai mai sallama ya wuce gida.

Abunda kuma ya k'ara hargitsa shi budurwarshi fadlah ta kirashi a waya tana
rizgar kuka ta sami labarin auransa, rarrashinta ya shiga yi yana nuna Mata ba
lefinshi bane Abbansa zai mai amma Sam tak'i yarda tana fad'in Ya cuceta Ya
yaudareta kullum tana cewa suyi aure amma yana fad'a mata shi bai shirya aure ba
shekaru kusa amma gashi don yaga sun rabu zaiyi aure, ganin zata b'ata mai rai yasa
ya kashe wayan.
Takuce
y'ar mutan ja'oji
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣2⃣3⃣
0⃣2⃣3⃣ 0⃣2⃣3⃣

Duk yanda UK yaso ya kaucewa kula Sweety yaga bazai yiyu ba,tunda indai yana fishi
da ita ta yaya zai samu yanda za'a fitar dashi kunya, haka badan yaso ba ya kirata
yana fad'a mata taje ta shirya duk wasu programs wanda zasu nuna girmansa gun
abokansa,don bai san harkar raini,
Wani bala'in dad'i ne ya rufe sweety harma ta kasa b'oyewa,cike da farin ciki
ta mik'e tana fad'in Tom yawwa my broth haka nake sonka,
Wani kallo ya watsa mata sannan ya tsaidata" naga kin fara wani rawar kai Kar
kiyi tunanin ko na fara son auran ne wlh ko d'aya balle kije ki sami abin fad'a,
kawai haukan da kikayi min ne na turawa friends d'ina invitation yasa ba yanda
zanyi Kar suzo su rainani ko suyi tunanin banda kud'in da zan shirya wasu events
ne,don haka zan kankarowa kaina k'ima, kuma gobe ki shirya ki rakani gun yarinyar
don zan gargad'eta matuk'a wlh ta kunyatani gaban mutane ta k'arawa kanta lefi
saina maidata tamkar baiwa a gidana, fice kiban waje".

Jiki ba k'wari Sweety ta fice tana tausayin Nahna har cikin ranta, dole a
lokacin ta shirya ta wuce gidansu Nahna.

Tana zuwa ta sami bata nan tana gidan yaya usman Aunty Amrah tayi kiranta, zama
tayi suka gaisa da Aunty Hafsah suna d'an tab'a hira tace "Aunty daman Broth ne
yace gobe zaizo gun Nahna suyi magana kan sheduls na bikin sabida abokansa da
yawa zasu zo dana India dana sauran k'asashe da sukayi karatu tare,to so yake a
k'awata abin sosai,to shine kafin yazo nazo in rarrasheta kar yazo tace bata so
ayi,Kinga yanda nake fama da ita kan ko dinner ta bari ayi tak'i,to yanzu tunda shi
ya amince don Allah Aunty ki k'ara rarrashinta,ta amince".

Gyara zama Aunty tayi kana tace " ba komai zan k'ara tank'wasarta,insha Allah
bazata bada matsala ba,yanzu kije can gidan Amran Ku had'u saiki fara mata
maganar".

Sallama taiwa Aunty ta wuce gidan yaya usman d'in,


*****
A gidan yaya usman d'inma samu tai sunata fafatawa da Aunty Amrah me gyaran
jiki tazo tana cewa bata so, ganin idon sweety yasa tai shuru me gyaran jikin ta
fara dirjeta,dake matar y'ar Sudan ce A unguwar su Amrah take ita tai mata na
bikinta,don haka gudunmawarta ta d'auko matar ta biyata tayiwa Nahna,

Sun d'au tsawon lokaci a d'aki tana dirje mata jiki tare da turarata da wasu
asirtattun turarika, yayin da Sweety da Aunty Amrah suke parlour suna tattaunawa
kan yanda za'a tsara bikin, nan suka k'ara tsara sabon IV ,
Ranar Alhamis za'ayi kamu ayi lecturer, ranar Friday za'a d'aura aure k'arfe
biyu bayan sallar jumma'a ,da dare za'a fita dinner, ranar asabar za'ayi culture
day,karfe biyu zuwa h'udu sannan a fita lunching hud'u zuwa bakwai, ranar lahadi
ayi mother's day,wanda su Sweety zasuyi nasu a Annour event su kuma su Nahna suyi
Nasu a gida sai k'arfe bakwai akai amarya bayan an kaita kuma k'arfe tara a k'ara
fita friends night wanda iya abokan angone kawai da k'awayen amarya zallah,zasuje
nan Sweety ta k'ara typing d'insa cikin wayanta tayi mai editing sosai ta watsashi
a yanar gizo,sannan ta wuce ta kai printing press su fitar Mata shi,ranar dai basu
zauna da Nahna ba don harta wuce gida ba'a k'arasa gyaran jikin ba, Aunty Amrah
tace ta bar komai gunta zata sanar da ita sak'on duka,

Yau kam Nahna taga abinda ya girmeta,aranta take tunanin wane Irin gyaran jiki
ne wannan ace ko ina na jikinka sai an dirje,tun tana jin kunya harta daure amma
wani gun ca take ta barta ta goga da kanta.

Sai yamma lis aka gama,tana fitowa kamshi na binta,Ta zauna parlour tanata yiwa
Amrah k'orafin Duk an wahalar da ita,dariya Amrah tayi tace "kuma daga yau har
ranar da za'a kaiki gidan Umar ana miki wannan gyaran jikin, me gyaran jikin ce ta
fito,ta bud'e jakarta ta fiddo wasu kullin ledoji ta bud'esu tana kallon Nahna
tace " wannan ki rink'a sha da madara wannan kisha da Zuma wannan kiyi turaren
tsugunno,cikin rashin fahimta tace "na meye wannan din kuma?"

Dariya Aunty Amrah tayi tacewa me gyaran jikin " Barta zan mata bayani a d'aki
naga kamar kunya takeji".

Mirmishi kawai Nahna tayi ta mik'e tsaye tana fad'in "bari in wuce gida maman
biyu".

" he lalle ma Nahna bakinki ya bud'e,kema kwana nawa ne zaki zama maman biyun
".

Da sauri Nahna ta rufe ido tana Neman mayafinta ta gudu,ruk'o hannunta tai tace
"zauna zamuyi magana kafin ki wuce"

Wuce wa tai ta raka me gyaran jiki k'ofar gida sannan ta dawo, ta zauna tana
fuskantar Nahna sosai ta fara " Nahna sweety tazo da magana zakuyi amma Baku sami
zama ba taban sak'o ki shirya in Allah ya kaimu gobe Umar zaizo Ku gaisa, sannan
yace a shirya events sabida abokansa zasu zo,don haka mun tsara nida sweety,
kamar yanda kika ce ran Alhamis kinaso ayi lecture da kamu to hakan za'ayi,amma
batun walima da zakiyi bayan d'aurin aure da yamma ta tashi dinner za'ayi da
dare,asabar ayi culture show da yamma ayi lunch dangin amarya Dana ango duka waje
d'aya sai Lahadi ayi mother's day akai amarya,bayan an kaiki kuma zaku fita friend
night sabida abokansa da zasu zo,ina fatan baza ki bamu kunya ba Nahna don in kika
Bijire zai fara ganin kin fara mai gaddama tin kafin kuyi aure,ki nuna mai Ke me
biyayya ce bisa umarninsa".

Nahna jitai kamar zata kurma ihu,abikinta duk za'ayi wannan bidi'oin,wlh ita an
gama da ita,me ake da auran me bud'e d'd'en ido wanda boko tai mai tsiro, amma
kasancewar bamai bijirewa na samanta bace yasa bata tanka ba ta tashi tace "Babu
komai Aunty Amrah bari inje gida kafin akira magriba".

A gida ma dai maganar d'aya ce nan Aunty Hafsah taci gaba da bata baki,akan ta
tausasa zuciyar ta ayi komai a gama, nan ma bata tanka ba sai gyad'a Kai da tayi
alamar amincewa.

*******
Washe gari ma dame gyaran jikin tazo Aunty Amrah ta kirata a waya tazo, na yau kam
anfi dirzarta, har ta gaji da k'orafi, tai shiru turaruka kuwa kala kala aka
rink'a turara mata na tsugunno dana jiki, da yamma yauma aka gama,nan taji tanata
jin jiri Aunty Amrah ta kawo mata milk me sanyi tasha,nan ta kwanta kan kujera tana
hutawa, Aunty Amrah kuwa na kitchen tanata aikinta.

******
Sweety da UK motarsu ta tsaya k'ofar gidansu Nahna, wani mugun kallo UK yake bin
gidan dashi yana ayyanawa aransa duka gidan baifi kaso d'aya cikin goma na
gidansu ba, dukda tsarin ginin gidan yayi kyau amma yayi k'ank'anta abunda yaketa
rayawa a ransa kenan,har sweety data shiga gidan kiran Nahna ta dawo ta bud'e
k'ofar motar ta shiga tana fad'in " broth bata nan tana gidan d'aya wanta nan k'asa
ne ba nisa mu k'arasa can d'in".

Tsaki yaja kawai ya juya kan motar yana bin hanyar data nuna mai,suna tsayawa
k'ofar gidan yaya usman ya k'ara kallon gidan ya saki wani tsaki duk gidajan kamar
na sadaka wasu kananu dasu wai yar wannan zuri'ar akeso ya aura muttsss nan ya kuma
sakin wani dogon tsakin,ita dai sweety bata tanka mai ba ta fice a motar.

Bayan ta shiga sun gaisa da Aunty Amrah suka gaisa da Nahna tace "Aunty nah
muna tare fa da Broth a waje, dummmmmm taji gabanta ya fad'i amma saita karanto
sunan Allah cikin ranta, Amrah tace " sweety ai munyi zaton sai dare zaizo"

"Hhhmmm ai Broth baya fita da dare Duk yawonsa iya rana ne zuwa yamma".

Ita dai Nahna na zaune bata tanka ba, saida Aunty Amrah taje ta bud'e sitting
room ta dawo tace " Sweety kice ya shigo ciki"

Yin duniya sweety tayi yak'i shigowa yace ba zama yazoyi ba,kawai tace ta fito
karta b'ata mai lokaci don baiga wajan zama ba a wannan d'an gidan, rasa yanda
zatayi tayi kawai saita juya cikin gidan tana fad'in " Kinga yanzu yanzu aka
kirashi a waya yayi bak'o a gida kuma daga nesa yake,shine yace tunda yazo kawai ta
fito su gaisa ya dawo wani lokacin".

Aunty Amrah tace "ayya,ba damuwa ai Nahna ki fita Ku gaisa to".

Mik'ewa tai a sanyaye tasa hijabinta ta fice, koda ta fita k'ofar gida ta hango
motarsa fake a gefe dukda ba sanin motar taiba amma tasan shine tunda motar kad'ai
ta gani a layin, tsaye tayi bata k'arasa ba,amma datai wani tunani saita k'arasa
gaban motar b'angaran driver ta tsaya, saida ta d'au tsawon lokaci sannan ya zuge
glass d'in motar yana Mata wani kallo na rainin hankali, gefe ta kauda kanta tana
fad'in " ina yini"

Taki yaja yana kauda kai gefe yace "bashi nazo jiba kuma karki yi farin ciki
kiyi zaton ko zance nazo,Sam har abada bazan tab'a zuwa zance gun y'ar Arabic
ba,har abada,wato don la'in ba maita da k'aunar da kokemin kin kasa jurewa shine da
kika daina ganina a school saida kika bibiyi gidanmu kika zo kika cinye kurwar
Abbana da maitarki,harya tura minke wai in aureki,to wlh ki sani zaki gamu da
uk'uba ta da kanki zaki bar gidana wlh,ki shirya zaman rashin y'anci don kin jamin
an ruguzamin tsarin rayuwata,an tauyeni wlh saikin d'and'ana kud'arki,waima in rasa
wa zan aura sai y'ar Arabic, jibi wani tafkeken hijabi da kika saka waike
ustaziyya, ni wlh an gama dani,kuma ina so ki karkad'e kunnuwanki da kyau ki jini,
domin in kika kuskure koda da wasa kika watsani cikin friends d'ina wlh kin k'arawa
kanki bala'i,Kinga dai yanda aka shirya bikin nasan wai ina son bikinba sai don in
fita kunyar abokaina,don haka in akazo gaban jama'a kika nuna wa duniya Ke gidahuma
ce wlh zaki shiga hannuna, don haka ki bud'e kunne kiji ki k'ara ji friends d'ina
zasu zo daga k'asashe daban daban in kika nuna gaban su Ke y'ar Arabic ce ustaziyya
hhhhmmmm".

Wani takaicine ya mamaye zuciyar Nahna amma saita rink'a kiran "innalillahi
wa inna ilaihi ra'jiun" cikin ranta nan nutsuwa ta sauka a zuciyar ta,takalleshi
karo na farko ta kauda kanta tana wani mirmishi na gefen baki tace "duka naji
zancen ka,inka gama zan wuce ciki".

Baice mata komai ba ya zuge glass d'in sa yana bawa motar key,
Ganin haka tai wucewarta gida, tana shiga sweety tai musu sallama ta fita,Sam
bata bari Aunty Amrah ta fahimci wani b'acin rai tare da itaba, bayan kusan 10
minutes itama ta wuce gida,tana danne duk b'acin ranta.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣2⃣4⃣
0⃣2⃣4⃣ 0⃣2⃣4⃣

Saura kwana hud'u a fara biki y'an sakkwato suka fara zuwa mota biyu, washe garin
zuwansu akaje akayi Jere(kafi),tunda suka dawo kowa tofa albarka cin bakin sa yake
kan tsaruwar gidan Duk da gidan a cikin gidan su yake,kamar yanda mahaifinsa ya
fad'a sai ya dawo daga India zamu tare a gidanmu, an k'ara tsara part d'in sosai
gashi kayan sun amshi gun,duk zancen da suke ina jinsu araina ina addu'ar Allah
yasa in riski farin ciki a cikin gidan ba wai had'uwar gidan ba.
Shirye shirye fa sun kankama don yau laraba gobe Alhamis za'ayi kamu da lecture,
yau tun safe bamu zauna ba,k'awayena da y'an uwana duk muna tare gidan me k'unshi
wanda muka fita tun bakwai na safe amma har ya zuwa yanzu k'arfe biyar ba'a gamawa
mutum uku cikin mu ba wai duk da hakan ma masu kunshin su uku ne a gidan, duk y'an
uwana wanda suke sa'annina da k'awayena ban bar kowa ba,sabida ina jin yanda ake
k'orafi duk sanda biki ya taso cikin k'awaye ko y'an uwa in amarya ta x
Zab'e wasu ta bar wasu cikin duk hidimarta shi yasa na d'auki aniyar yin iya bakin
k'ok'ari na wajan ganin ban b'atawa kowa ba,

Waya ta dake kan cinyata ta d'auki ringing na kalla fuskana d'auke da mirmishi na
d'aga wayan" Hello Amarya kin dawo gida ne?"

"Um um sweety wlh har yanzu muna can".

" kai Ku nawa ne haka?"

"Hhhmmm mun kai mu ashirinfa ko ma munfi,amma da yawa an gama don kusan mutum
goma sun koma gida saimu sha d'aya yanzu anan".

" ok Kinga muma yanzu muka dawo daka gun k'unshin Kinga duk y'an uwanmu na katsina
sunzo, yanzu kan maganar kayan da za'a bada gift ne gobe gun lecture, yanzu masu
aikin suka kirani sun gama komai shine nace ina za'a kai a ajiye miki tunda bakya
gida".

Shiru nai can nace " Gaskiya gidanmu ba wajan ajiyar kaya Sweety don cike yake da
mutane,kuma gidan yaya usman ma cike yake,ina ganin kawai ki ajiye a gidanku
sweety goben sai ku wuce dasu gun".

"OK to ba damuwa Aunty nah,ya maganar gyaran kan goben fa da wuri zamuje kar mu
shiga lokacin kamu".

" hhhmmm zamu b'ata fa in kina cemin Aunty kawai kicemin Nahna na yafimin dad'i".

" ni dai bazan ceba,ki dai shirya da wuri goben".

Mirmishi nai kawai na kashe wayan.

Bamu muka tafi gidaba sai bayan sallar magriba, a gajiye muke matuk'a ga yunwa
damuka tara tun Karin safe sai lemo da biscuit kawai da mukasha, gidan namu babu
masakar tsinke don jama'a ana tai mana sannu na sami gefen kujera na zauna ina
fad'in "Wash Allah".

Gwaggo na dake zaune kan kujerar tace " sannu Khadijah tun safe sai yanzu dole
Ku gaji ai".

D'an mirmishi nai nakai dubana fa Aunty Amrah data shigo parlourn d'auke da
abinci tana ajiyewa mutanan d'akin a gaban su, nace "maman biyu bamu key d'in
gidanki mu tafi yanzu don Duk a gajiye muke wlh".

D'auko min key d'in tayi tana rad'amin Abu a kunne ".

Girgiza kai na fara ina fad'in " wlh ba ruwa na nifa na fice daga parlourn da
sauri ina dariya".

Babbar kula aka cika mana da abinci duka wanda zamu kwana dasu gidan yaya usman
suka taso muka wuce.

Kusan raba dare mukai hira da y'an uwana da Aminiyata Hafsah wadda ta had'o
kayanta ta dawo gidanmu har agama biki,

Da safe bayan munci abinci mun gyara gidan me gyaran jikin nan sarkin naci tazo
wai tunda yau jiya ba'ayiba yau ba inda zanje sai anyi,badan naso ba na zauna aka
fara min,
Wayata aka kawo min da take ta k'ara nasan sweety ce koda ban gani ba,ina
d'agawa tace "Amarya gamu k'ofar gidan yaya usman ".

" Ku shigo mana".

Bayan sun gaggaisa da jama'a ta lek'o da kanta d'akin da ake min gyaran tana
d'an mirmishi tace "y'ar Sudan a gyaramin ita da kyau yanda d'an uwana zai gigice
inya ganta".

Hararanta nayi ina mirmishi nace " jirani 10 minutes za'a gama"

Bayan kusan minti a shirin na fito inata zuba k'amshin turaren da ake turaramin
jiki wanda ya gama kama fata ta, duban y'an matan nayi ina fad'in " dawa dawa ne
basuyi gyaran Kai ba?".

Da yawansu ko wacce da gyaran kanta tazo k'alilanne zasuyi

"To kunsan yanda za'ayi munyi magana da maman Amira me saloon ta cikin layinmu
zan kawo mata costumers kuma kunga ni sweety taje ta biya kud'i a sabon gari tayi
bucking, don haka Kar maman Amira taga rashin kyautawarmu taga mun gujeta don haka
Ku kuje gunta tai muku in na dawo zan bata kud'in ita Hafsah sai muje da ita can
karna barta nan cikinku bata san kowa ba zata takura koya kuka gani".

" eh hakan yayi saikun dawo ".

Bayan mun shiga shiga mota Sweety na driving sai Ramla cousin sister d'inta na
zaune gefenta nida Hafsah muna zaune baya, ta cikin madubi ta kalleni tana mirmishi
tace " Amarya gaskiya kina birgeni wlh yanda kike ji da family naki,komai baki son
b'ata musu rai family dinku sunada zumunci matuk'a wlh".

Y'ar dariya nai ina fad'in " kinga kuwa tun jiya su Aziza suke tambayarki kina
ina yanzu kuma da kika zo suna can gidan mu buku had'u ba sai zuwa jimawa ".

Dariya tai sosai tace " kai Aziza y'ar is ce wlh harna tuno bidirinmu a sakkwato
in muna chart inna tuna mata ces din gidan lalle muyita dariya,inaji da Aziza Duk
cikin y'an matan family d'inku nafi ji da ita don Kuna matuk'ar kama wlh dukda
kamanninku duk d'aya ne amma kamarku da Aziza ta b'aci shiyasa nakeji da ita".

Hira mukaci gaba dayi har muka k'arasa cikin kasuwar sabon gari, gefen shagon
saloon d'in mukai parking bayan ta rufe ko ina na motar muka shige shagon, mutum
biyu ne ciki me shagon da yarinyar ta ba b'ata lokaci aka fara min yarinyar kuma ta
fara yiwa Ramla.

Kasancewar su k'wararru a harkar gyaran kai yasa ba'a d'au wani lokaci ba aka
kammala mana dukanmu muka taho gida.
K'arfe uku aka fara tafiya wajan kamu da lecture wanda za'ayi a sani Abacha an
shirya gun sosai son lecturer d'inmu ce zatayi lecture d'in akan zaman aure yanda
nake son malamar yasa muka saba da ita sosai babba ce a hukumar hisbah, ina jin
lecture's d'inta a gidan radio don haka na k'udurta a raina ita zata min lecture
d'in aure na.
Sosai nayi kyau cikin wata rantsattsiyar lifaya y'ar asalin na nad'ata ta zauna
das a jikina fuskata d'auke da k'ayatacciyar kwalliya ta amare,kasancewar malama
zarah bata son b'ata lokaci a duk lamuranta yasa ta gargad'emu da kada mu b'ata
lokaci gun zuwa ai kuwa k'arfe hud'u hole d'in ya cika damk'am da jama'a, hud'u da
y'an mintuna ta iso wajan ita da malama khadijah me tafsiri,
Kamu aka fara yi, wanda yake bisa ala'da dangina suka min kamu da turare me
k'amshi daga nan fa Mlm Zarah ta fara suburbud'a lecture akan abunda ya taramu a
gun, Allah yaiwa Mlm Zarah kaifin harshe da iya jan ra'ayin wanda takewa magana don
ya maida hankali ya saurareta da kyau hakan yasa dukkan hole d'in baka jin
maganar kowa sai girgiza kai kawai da akeyi (wa'azi ya fara ratsa mata,😜)

Tofa zance fa Mlm Zarah take saki kasancewar Duk hole d'in ba namiji duk mata ne
yasa ta k'ara k'aimi wajan sanar da mata sirrikan rik'e miji gam a tafin hannu,
wani abin ma inta fad'a kunya saita rufeni Allah yasa naja lifaya ta na rufe
fuskata, tofa nan ta fara kwararo batu kan azabar da Allah ya tanadarwa matan da
suke muzguna ran mazajensu,zo kuga jikin mata yayi qlau Duk jiki ya mutu, tana
fad'in girman aure da matsayinsa cikin musulunci da yanda ya dace mace ta girmama
mijinta, ban k'ara karaya ba saida naji ta waiwayo kan batun biyayya kan macen data
auri mijin da bata so, dole ne ayiwa miji biyayya koda kuwa ba'a sonshi, haba Duk
sai jikina ya k'ara mutuwa,
Lecture na awa d'aya da rabi tayi tai dagargaza sannan Mlm Khadijah me
tafsiri ta tashi ita kuma,ta fara bada wasu sirrika da kissosi nan fa tafi da
kabbara suka b'arke a gun, har Irin tafiyar daya dace mace tayi a gaban mijinta
saida ta nuna haba wa nanfa na k'ara tsumuwa inaji araina anya duk zan iya wannan
abubuwan da suke fad'i kuwa.
Minti talatin Mlm Khadijah me tafsiri tayi, sukai sallama tare da addu'a suka
rufe taro, kayan rabo kuwa daman kowa an bashi nashi tun mutum zai shigo ake dank'a
mai jakarsa a hannunsa ya shigo hole d'in da ita maganin mutum yace bai samu ba.

Su kuwa malaman gift na alfarma aka shirya musu sosai farantai manya aka
shishshirya musu kayan snacks dasu naman kaji aciki lemo da ruwa ma katan biyu biyu
aka sa musu tare dasa musu kud'i dubun ashirin matsayin su zuba mai a mota wanda
Ummu sulaim ce yayar sweety ta basu kud'in aka rakasu har mota anata musu godiya
tare da amsar number wayoyinsu kowa na cewa zata gayyacesu lecture.

Haka ma tunda muka dawo gida labarin wannan lecture ake musamman y'an matan da iya
shege zasu tuno wani abun su kwashe da dariya suna fad'in " Nahna da fatan dai
lecture d'in nan ta shiga kanki kije ki girgiza Umar".

Mirmishi kawai nake ban tankawa ko waccen suba na wuce toilet na gasa jikina da
ruwa me zafi sannan na d'auro alwala nazo nai sallar magriba na maida isha'i don
har an fara kiraye kirayen sallar ishan, yau ban tayasu hiran da suke ba don a
gajiye sosai nake don haka gado na haye na lumshe ido bacci nasan d'aukata,amma
kafin minti biyu wayata ta fara ringing kamar bazan bud'e idon ba haka na daure na
bud'e ina kallon kan wayar bak'uwar number ce banyi tunanin komai ba na danna
tare da sata a kunne na sanyin muryata ya had'u da baccin da nakeji ya k'arasa
muryar yin sanyi matuk'a, sallama nayi tare da saurarawa don jin waye, shuru naji
anyi na y'an dak'ik'u sannan naji anyi magana cikin gadara da isa " ki fito k'ofar
gida ina jiranki kuma karki b'ata min lokaci".

UK ne na fad'a cikin raina don har abada muryarsa bazata tab'a b'acemin ba to me
zan masa me ya kawo shi guna yanzu kuma?
Banda amsar bawa kaina don haka na mik'e jiki ba k'arfi nasa zumbulelen hijabi kan
kayan baccin dake jikina,tambaya ta suka farayi ina zani ban kalli ko waccen su ba
nace " ina zuwa kirana ake a waje yanzu zan dawo ". Nasa kai nai waje . . .

Taku ce
y'ar mutan Ja'oji

🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

ALLAH KAI MANA MAGANIN ABINDA YAKE DAMUN MU ALLAH KA SHIGA CIKIN LAMARINMU👏

0⃣2⃣6⃣
0⃣2⃣6⃣ 0⃣2⃣6⃣

Jin Hannun Hafsah a kafad'ata yasa na juya ina dubanta,mirmishi tai min tana
fad'in "Angon yazo ko? Kinga ya dace mu wuce yanzu gashi har 8 ta wuce ".

Jin abinda Hafsah tace yasa me kwalliyar yin dariya tana fad'in " Amarya Bari
mu kwarara miki turare dukda naji sirrin humrah tare dake gaskiya daga ji me gyaran
jikinki tayi amfani da zafafan turaruka wajen gyara ki".

Hafsah ce ta tanka mata ni kuwa ban iya cewa komai ba har zuwa sanda ta d'auko
kwalbar turare ta fara min feshi kamar ance ta k'arar dashi a jikina, net ta d'auko
me taken one million Stone shima ta feshi shi da turaren sannan ta yafa min akaina
wanda hakan ya bawa fuskata damar d'an sakayawa shima net d'in babbane sosai ya
zuba ta baya,ta gaba kuma fuskata da k'irjina kawai ya rufe,

A hankali nake takawa kasancewar takalmin yamin tsini da yawa,gefena Hafsah


d'aya gefen me kwalliyar ce ta rik'emin hannuna,tun kafin mu k'aroso bakin motar
abokinsa dake driving ya dannan pin nan take mirfin motar ya bud'e, fitowa Angon
yayi cike da fara'a d'auke da fuskanshi hannayensa biyu yasa ya ruk'o hannayena
yana lek'a fuskana ya d'ago yana mirmishi me kwalliyar tace " Angon kasha k'amshi
ga amaryarka nan nai Mata bridal makeup don k'ara fito maka da ita".
Alamar jinjina yai mata tare dasa hannunsa a aljihu ya ciro kud'i yana mik'a
mata yace "ga tukwicinka nan don wannan kwalliyar ta cancanci tukwici bayan an biya
kud'in ta ".

Dariya tai tana mai godiya ta juya ta koma, shi kuma yana rik'e da hannayena ya
sakani cikin motar, Hafsah gaba ta zauna bayan ya rufe motar Hafsah ta juyo a
hankali tana fad'in " Ango barka da dare ya taro"?.

Cikin d'an sakin fuska ya amsa mata,kafin ta kuma magana Abokin Angon yace cikin
tsokana "wato Sabida ni ba ango bane shine baza'a gaisheni ba ko k'awar Amarya".

D'an mirmishi tayi tana fad'in" Ah Afuwan ba haka bane kaima zamu gaisa mana,ya
taro ya fama da jama'a".

Nan ya amsa cikin tsokana ya juyo gareni yana fad'in " Amarya ansha k'amshi
ya taro".

Kaina a k'asa gabana nata fad'uwa, ina k'ok'arin amsa mai Yai caraf ya amshe "
Kai dalla rik'e gaisuwarka bama buk'ata, wayon kaji daddad'ar muryar mata ta ne to
na amsa Mata".

Dariya Abdushshakur yai yana tada motar ya cilla ta kan titi cikin gwanancewa,

K'amshin turarena daya cika motar taf ya shak'a tare da lumshe ido kasancewar
sa me matuk'ar son k'amshi, yana bud'e ido suka had'a ido da Abdushshakur ta
madubi ya kashe mai ido yana fad'in yadai my friend ko har ka. . . ." da sauri ya
rufe baki yana dariya,

Hararansa yai yana cewa "wlh ka lalace dasa iso friend ban sanka da haka ba
fa".

K'ara matsowa kusa dani yai sosai jikinmu na gugar juna yake yima Abdushshakur
gwalo tare da fad'in ka daina kallon mu fa Malam". Bakinsa yasa dai dai kunnena
yana magana cikin rad'a" Ke karfa kiyi wani tunani cikin ranki game ne kawai zamu
buga kuma wlh kika bari aka miki game over zamu had'u,k'ara kiyi iya yinki ki
fiddani kunya kinji na fad'a miki ".

"Hhhhmmmm daman nasan za'a rina ni nasan ba saduda yayi ba kafiya kuma irinta
UK amma ba komai Allah yana tare dani ai".

Music me dad'i Abdushshakur ya kunna cikin motar tare da k'aro Sanyin A.C
nan motar ta wani shika da nishad'i,tunda muka shiga banyi k'ok'arin d'ago fuskata
ba yanda take a lullub'e haka na saddata k'asa har muka isa MEENA EVENT CENTER
nan motar mu tai parking a compound d'in gun duk sauran abokansa suna waje don
jiran isowarmu, motar sweety ma tana wajan tana ganin isowaemu ta shiga ciki domin
fito da sauran y'an matan da zasu shigar da Amarya da ango,
Duka y'an matan anko ne a jikin su yayin da mazan suke da shiga mabanbanciya,
muna zaune cikin mota sweety ta shirya gun ko wace mace da namiji kusa da ita,yayin
da gaba aka jera plower's baby's guda shida,
Ana mana izinin fitowa ya danna pin Motar ta bud'e shi ya fara fita sannan ya
kamo hannu na ya fito dani muka tako a nutse hannuwanmu suna sak'e cikin na juna,
muka shiga tsakiya gabanmu y'an yara bayanmu emmata da samari muna k'arasawa kusa
da hall d'in aka saki kid'an police Band cikin taushi dasa jiki ya motsa, nan fa
y'an yaran suka fara takawa cikin rausaya Kai haka ma emmatan da samarin , muna
shiga ciki fa waje ya rud'e da ihun zuwan amarya da ango, a tsakiyan fili muka fara
tsayawa nan aka shiga mana b'arin kud'i waje ya rude da rawa da lik'i, min dad'e
tsaye m.c ya buk'aci kowa ya koma ya zauna a mazauninsa abar Amarya da Ango kad'ai
a tsakiyan filin,
Nan kowa ya koma mazauninsa muka rage mu kad'ai tsakiyan filin ai kuwa ziciyata
taci gaba da bugawa da sauri sauri ganin yanda ya k'ara matsowa kusa dani sosai,
m.c ne ya buk'aci Ango daya bud'e fuskar amarya,ai kuwa cikin wani salo yasa
hannuwansa biyu ya d'age net d'in dake rufe da fuskata k'asa sosai na k'ara yi
da kaina ya d'ago da fuskana fuskanshi d'auke da mirmishi ahankali na lumshe
idanuwa,nan wani annuri da asirtaccen kyau ya k'ara bayyana tare dani, yarrrrr
yaji a jikinsa yana tunanin anya wannan y'ar Arabic ce kuwa,sosai ya zuba min ido
don tabbatarwa a zahiri dai yana hango kamannina a fuskana amma wannan tsananin
kyanfa daman haka wannan yarinyar take da kyau kodai makeup d'in nan ce tasa tai
wannan tsananin kyan. . .

Ihu da tafin daya cika wajan ne ya dawo dashi tunanin daya shiga ai kuwa yaji
wata bala'in kunya ta kamashi amma duniyanci Irin nasa da nuna shi wayayyene yasa
kawai ya bud'e babbar rigarsa ya sakani a ciki tare da hugging d'ina yana dariya,
nan duk friends d'insa na gida Dana k'etare sukayo kanmu da sabon lik'i suna b'arin
manyan kud'i don nuna kara ga abokin nasu, ganin yanda mazan suka kewaye mu naji
wani sabon fargaba da ta k'ara lullub'eni ai kuwa ban san sanda na kifa kaina bisa
k'irjinsa ba tare da kewaye hannuwana jikinsa,wani k'ara rungumeni yai yana shafa
bayana tare da kashe wa abokansa ido cikin shak'iyanci ai kuwa waje ya k'ara
rud'ewa da ihu m.c ya samu abinyi fad'a yake yana k'ara fad'a"gaskiya wad'annan
ma'aurata sun dace da juna Allah ya kawo zuri'a ta gari Allah yasa wata Tara masu
zuwa muzo shagalin suna". Masu video fa hotuna suka shiga aikinsu na d'auke d'auke.

Mun d'au tsawon lokaci sannan m.c ya bamu damar zuwa mu zauna nan ya ruk'o
hannu na muka tafi gun zamanmu muka zauna a high table,anan na k'are mai kallo
shima kayansa kalan nawa ne light blue shadda d'inkin babbar riga da y'ar ciki
babbar rigar irinta samarin Zamani y'ar k'arama dai dai jikinsa, idonsa sanye da
farin glass kamar yanda ala'adarsa take,sai wata hula zanna me tsadar gaske da
akewa lak'abi da minister kalan kayan nashi, hannunsa sanye da agogon vansar
chairman world, sai k'afarsa sanye da bak'in takalmi south, duk a cikin abunda
bai kai minti d'aya ba nai mai wannan kallon.

Nan akaci gaba da gudanar da event d'in cikin aji da nishad'i,zuwa d'an lokaci
aka fara raba abinci ganin duk hankalin jama'a ya bar Kansu yasa ya sunkoyo sosai
yana min magana cikin kune "Hhhhmmmm yarinya taga faffad'an k'irji shine harda wani
lafewa a ciki to k'walelanki wannan k'irjin na matar zab'in raina ce ba matar tushe
ba ".

Ganin masu Neman abinyi sun fara d'aukanmu a hoto yasa ya janye jikinsa yana
wani mirmishi, Wanda nima mirmishin ne d'auke a fuskata wanda ban san name ne ba.

Sai misalin k'arfe sha d'aya aka tashi, yanzuma motar Abdushshakur muka hau
Hafsah a gaba kamar yanda muka zo,
Bayan sun ajiye mu k'ofar gida ina shirin fita a motar ya rik'o hannuna yana
magana k'asa k'asa " yau kin fidda kanki kunya sai kuma Sunday shima kiyi k'ok'ari
kinji ko".

Ganin Abdushshakur na kallonmu yasa na gyd'a mai cike da gajiya wanda zakai
tunanin shagwab'a ce.

Koda na shiga cikin gida tsokana ta akai tayi wai mun kasa hak'ura zuwa jibi
gaban jama'a muke rungume juna, mirmishi kawai nakeyi ba tare dana tankawa kowa ba.

Washe gari asabar akai culture day tun k'arfe biyu ake gudanar da wasannin
gargajiya da al'adu a filin wasa na Ahmad Musa sannan zuwa k'arfe hud'u aka wuce
lunch sai bayan sallar magriba aka dawo.

Yau lahadi kuma akeyin Mothers day yau kam mu ba fita zamuyi ba a gida muke
yinin mu inda muka yini masu kid'an k'warya suna cashewa, tunda naga anyi sallar
la'asar fa jikina ya fara mutuwa naji zuciyata ta narke duk y'ar walwalar dake tare
dani ta kau na koma jugum,

Ina jin kiran sweety a waya kuwa tana fad'awa Aziza ta fad'a a cikin gida ana
sallar magriba fa za'azo d'aukan amarya nan jikina ya k'ara sanyi hawaye suka fara
bin kuncina duk k'awayena ma sai jikin su ya mutu da sauran y'an matan, kayan
takaici da rawar kai Irin na abokan UK wai tun kafin akira magriba suka fara zuwa
d'aukan amarya ance sunzo da wuri wai sai ca sukai eh duk nuk'u nuk'u da fad'an da
za'a yiwa amarya ayi mata kafin suyi salla su fito don ana idar da sallah zasu d'au
amarya.
Nan fa na rikice da kuka wiwi na k'udundune cikin d'akin Aunty Hafsah ina
matsanancin kuka me shiga rai, Iyayena suna zaune tare dani suna k'ara min nasiha
kan hak'uri hak'uri dai nikam kuka kawai nake Aunty Hafsah ta shigo d'akin tana
fad'in "Nahna tashi kiyi wanka kiyi salla Kinga an fara kiranvsallar".
Mik'ewa nai cikin jan hanci na shiga toilet wanda daman an gama had'amin ruwan
wankan,ina wankan ina kuka saida naji ana min magana in fito haka na hak'ura na
fito tare da d'auro alwala, ina sallar ma ina kuka haka naita addu'a a sujjadata
ta k'arshe ina rok'on Allah yasa min albarka a cikin rayuwar aurena,
Ban wani sa komai ba humra kawai na goga a jikina nasa kaya aka fito dani ina
fitowa Yaya Haroon na shigowa ya koro yara da suke bin motocin da suka d'auki y'an
kai amaryar, fad'awa nai jikinsa ina kuka ya rungumoni yana bubbuga bayana shima
duk zuciyarsa ta karye, cikin sanyin jiki yace " Kiyi shuru Autah kinji ki daina
kuka haka Allah yai miki albarka Allah ya baki zuri'a me albarka Allah yasa farin
ciki cikin rayuwar ki ".

Muryarsa ce ta fara rawa don haka yai shuru tare da jawoni zuwa waje da kansa ya
sakani cikin motar yana shirin juyawa na ruk'o hannunsa ina fad'in " Yaya na ka
yafemin ja yafemin don Allah ".
Janye hannunsa yai cikin nawa yana shafa kaina tare da d'an mirmishin yak'e ya
juya da sauri jin idonsa ya ciko da k'walla".

Duk wanda ke wajan saida ransa ya sosu haka umma maman su yaya Haroon ta shigo ta
zauna gefena yayin da k'anwar mama ba na ta zauna d'aya b'angaren Hafsa Aminiyata
kuma ta shiga gaban motar aka cilla damu,shike nan na bar gidanmu wayyo Allah na.

Muna sauka a mota na shak'i k'amshin iskar gidansu sweety naji wani fad'uwar
gaba,yanzu shikenan nan ne fa gidanmu, cikin kunnena Umma tace " maza yita addu'a
kinji Khadijah Ke malama ce yi addu'a ki shiga da bisimillah kinji".

Cikin raina naita addu'oi ina neman tsari da dukkan fitinar da take gidan tare
da neman Alkairan gidan tare dani, bisa al'ada cikin gidan aka shigar dani wajan
iyayensa, parlourn cike yake da manyan mata masu aji da izza kallo d'aya zaka musu
kasan ko wanne yana ji da kansa a nera, bayan gaisuwa ga juna umna ta fara mik'a
amanata garesu " To Y'an uwa ga Nahna Khadijah nan mun kawo muku ita ta zama y'ar
ku,Khadijah dai duk wanda yasanta yarinya ce bame fitina bace ko cikin y'an
uwanta halayyarta daban take,amma yanayin rayuwa koda zaku ga wani abin k'i daga
gareta Ku mata fad'a Ku nusar da ita tunda yarinya ce k'arama, mun baku Khadijah
bisa amana kamar yanda muke kyautata zaton zata sami Duk wani kula daga gareku
kamar tana tare damu".

Wata mata ce cikin isa da nuna ita wata ce ta fara magana" OK duk munji baya
nanki kuma muna fatan Allah ya bamu ikon rik'onta ,amma dai Ku cigaba da yiimata
fad'a don kun san rayuwar ta data Daddy ba d'aya bane ,maybe zai iya yin wani Abu
taga kamar yai mata ba dai daiba so dole tayi hak'uri dashi tunda tsarin rayuwar sa
duk cikin manya yayi ta,to Allah ya tsara madai itace matar sa amma mun so k'warya
tabi k'warya. .
Da sauri wata matar ta katseta da fad'in "Haba Aunty iyami wannan ba girmanki
bane meya kawo kad'an nan maganganun haba bai dace ba wlh,gaskiya biki kyauta ba ai
yanzu Duk mun zama d'aya tsakaninmu dasu Khadijah tunda aure ya shiga tsakani".
Kafin itama ta k'arasa abinda zata ce Aunty murjah ta fito tana fad'in " Ku
shigo da ita Abbansu yace a k'araso mai da ita su gaisa".
Son jin gulma dame za'a fad'a yasa Aunty iyami mik'ewa ita da wata magulmarciyar
irinta suka bi bayanmu zuwa b'angaran Abbah wanda zuwa lokacin Duk raina ya gama
b'aci matuk'a da maganar Aunty iyami ta k'arshe don haka na rik'e sunanta tsam
cikin raina don nasan zaman da zanyi da ita.

A gun Abbah kuwa tarb'a muka samu sosai don da fara'arsa ya taremu yana cewa
kowa ya zauna akan kujera ganin su umma na zama a k'asa,nikam a k'asan na zauna ina
k'ara duk'un k'une kaina, "zo matso kusa dani Khadijah karki zauna a can "

A hankali na tashi na k'arasa gabansa na zube ina gaisheshi cikin muryar


kuka,dafa kaina yayi yana cewa "Yi shuru bar kunan haka y'ata y'ar albarka ban son
ganin hawayenki".

Gaisawa sukai dasu Umma yanata tambayarsu ya taro ya hidima , su kuwa cikin jin
dadin irin karbar daya musu suke amsawa, nan ya shiga musu godiya sosai ya k'aramin
nasiha sosai " Khadijah kiyi hak'uri da dabiun Daddy kinji Nasan Ke yarinya ce
kamilalliya me ilimi don haka naita addu'a ina kwadayin Allah yasa ki zama
abokiyar zamansa don nasan zanyi alfaharin auranki da Daddy,dukkan y'an matan
dake rubibin sonsa nasan suk shirme ne ba wacce take sonsa domin Allah, amma ke
kuwa nasan zaki zauna dashi cikin ta ilimi zaki rink'a nusar dashi abubuwa da yawa
kiyi hak'uri kinji Khadijah ".

Wani bak'in ciki ne ya turnuk'e su Aunty iyami da jin kalamansa don sun san
gugar zana yake musu suda y'ay'ansu da suke kwad'ayin auran UK,

Mun jima zaune Abbah nata Nasiha daga bisani ya zaro key d'in mota ya mik'awa
Aunty Murjah yace " murjah ga kyautar y'arki nan dana tanadar mata duk randa aka
kawo ta gidan sabida zuwa school ".

Cikin fara'a Aunty murjah tace to Abbansu Khadijah ta gode kuma muma mun tayata
godiya Allah ya k'ara bud'i".

Su Umma ma Godiya sukaita yi suna jinjina k'aunar da nasan Allah nan kemin tare da
karamcinsa gareni".

Haka muka baro gun Abbah zuwa part d'ina muka bar masu bak'in ciki natayin
k'us ,

Zuwa minti talatin duk manya y'an kawo amarya sun watse sai y'an mata kawai da
za'a fita friends night dasu, sweety ce ta shigo parlourn tana zuwa tazo kusa dani
tare da rank'afawa ta lek'o fuskana tana d'an mirmishi tace "Shike nan Aunty nah ta
dawo gidanmu ta zama y'ar gidanmu har abada".
Hararanta nai ina kauda kaina gefe,
Matar dake bayan ta ce ta ajiye d'an akwatin kit d'in dake hannunta tana cewa"
Ruk'ayya a fara kwalliyar nan yanzu don lokaci na tafiya".

Sweety tace "Aunty nah game kwalliya tazo zata miki Kinga 9 za'a tafi gashi
7:30 yanzu".

D'aki muka shiga na na sake d'auro alwala don nafiso ana gama min na nai sallah
kafin mu tafi,araina inata bak'in cikin ace wai sabida boko da wayewa dataiwa
mutane yawa daren da aka kawo amarya d'akin ta kuma ace wai a k'ara fita wani fatin
na daban,

Yau d'in ma kwalliya sosai akai min bayan an gama kafin nasa kaya nai sallar
isha'i don zuwa lokacin an dad'e ma da yin sallar duk y'an Matan ma sun k'ara
shiryawa, yau farin gown d'in nasa asalin bride gown na y'an k'asar India itama ta
amsheni sosai kaina ba gwaggaro bane yau mayafin rigar aka samin saman kai yayin da
akamin gyaran gashi Irin ba y'an India sai wani ribbon da aka samin a gaban gashi
kamar Irin na sarauta,yau fuskata a waje take,hannayena duka cike da awarwaraye
Irin dai yanda y'an India keyi kallo d'aya zaka min kasan tsaf kwalliyar amaren
India akaimin don har wannan d'an abin da suke sawa a goshinsu kamar d'an kunne aka
samin,

Ihu parlourn ya d'auka lokacin da na fito daga d'akin kowa fad'i yake har nafi
ranar dinner kyau.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

ALLAH KAI MANA MAGANIN ABINDA YAKE DAMUN MU ALLAH KA SHIGA CIKIN LAMARINMU👏

0⃣2⃣7⃣
0⃣2⃣7⃣ 0⃣2⃣7⃣

Ina tsaye duk kunya ma ta baibayeni na rasa me zance musu da shakiyancin da suke
tamin, sweety ta shigo cikin shirinta tsaf tana fad'in " yawwa to duk kowa ya fito
ya motoci na jiranmu mu wuce".

Fita suka farayi d'aya bayan d'aya ina tsaye ta k'ara so gareni tana rik'e
hannuna tace "amarya Kyan da kikai yau ya zarce na kullum,ki jira angonki yanzu da
kansa zai shigo Ku tafi".

Ta k'arashe maganar tana mirmishin tsokana, jin takun takalmansa mukai yana
shigowa parlourn a tsakiya yaja ya tsaya hard'e da hannayensa a k'irji cikin
shigar suite farare k'al har takalman dake k'afansa farare ne haka ma fatan
tsadaddan ogogon dake hannunsa, sai gashin kansa bak'ik'irin kwance luf luf kana
kallon sa zaka gano tsantsan kyan da yayi, cike da nuna isa yacewa sweety" jeki ku
jiramu gamu nan fitowa ".

Tana fita ya k'ara taku biyu zuwa uku yaja ya tsaya yana fad'in "ki kula sosai
yauma karkiyi abinda zaki bani kunya kinji ko".

Kai kawai na gyad'a mai ba tare dana d'ago ba, shima kauda kai yai daga kallo na
ya juya zuwa k'ofa yana fad'in "zo mu tafi"

A hankali na taka nabi bayan sa har zuwa k'ofar fita daga part d'in sannan ya
dakata ya tsaya har ba k'ara so kusa dashi yasa hannunshi ya ruk'o nawa k'am a haka
muka k'arasa fita inda muka tarar da motar da zamu tafi a cikin ta sauran motocin
kuwa duk sunyi layi daga cikin gate d'in har zuwa waje,da sauri d'aya cikin
abokansa ya bud'e mana k'ofar muka shiga sannan yaja muka shiga cikin rukunan
moticin ,
Tunda muka shiga bai tanka minba saima d'auko wayansa da yayi yana danne
dannansa a ciki, ni kuwa kaina yana k'asa ina wasa da yatsun hannu wana,a haka muka
k'arasa gun motocin duk suka tsaya saida aka sanar sa m.c zuwanmu sannan muka fito
yasa hannunsa ya rab'oni jikinsa yayin sa sauran abokansa kowanne ya tsaya tare da
mace d'aya muka jera a haka har zuwa cikin Hall d'in yayin da wani kid'a me taushi
yake tashi haka sukai mana rakiya har zuwa mazaunin mu, bayan y'an matan sun gama
cashewa a fili aka basu damar komawa mazauninsu, nan aka cigaba da gudanar da
program d'in cikin wayewa irinta rik'akkun y'an boko, dama m.c din ya bawa ango da
amarya su fito filin rawa su nuna farin cikin su, a nutse muka sakko filin yayin
daya nanuk'eni gefen kafad'arsa,wak'a me tsuma rai aka sakar mana ta turanci me
d'auke da dadad'an kalaman soyayya ga kid'inta me taushi, duk yanda m.c d'in ya
dage kan na rausaya na kasa shi kuwa gogan rausayarwa sa yake cike da iya wa, ganin
ina neman kwafsa mai nak'iyin rawar yasa ya rik'o kuguna da hannayensa biyu yana
juyi dani kamar y'ar baby, tafi abokansa Ke masa ganin yanda ya wani basar yana
jujjuyani a jikinsa, sosai kunya ta lullub'eni k'asa nai da kaina inajin wani
fad'awar gaba, lik'i ne ta ko ina ya b'arke a wajan jinai an farke min rafar kud'i
akaina kamar ba'a sonsu,a hankali na d'ago ido don gani wace wannan wadda batayiwa
angon sai ni kad'ai shima dai dai lokacin yakai kallonsa gareta yanda naga suk
sunyi shock a lokaci guda yasa na k'ara kallonsu sosai a hankali naji yace "tnx
fadlah " mirmishi kawai tai ta basar tare da juyawa ta bar wajan, binta yai da
kallo yana mamakin yanda tazo wajan don bayyi zato ba ko kad'an wai fadlah zata zo
kano bikinsa,ganin kallon da yake mata yasa na juya zan koma mazaunina da sauri
ya ruk'oni muka jera zuwa mazaunin namu,bayan anyi ciye ciye akaci gaba da cashiya
inda abokansa suke ta rawa suna ihu irin na wayayyun samari y'an boko, gab da za'a
tashi aka buk'aci mu fito mu yanka cake, k'awataccen cake ne me d'auke da sunayanmu
nida shi, hannuna da nasa ya had'a bayan sun kirga 3 muka yanka nan akaita yi
mana tafi m.c yace amarya ta yanka ta bawa angon ta a baki,tab d'in babbar magana
kenan nanfa k'irjina ya fara lugude ina jin kamar bazan iyaba,amma dana tuna
warning d'insa akaina na kada in kuskura in bashi kunya sai na tattaro nutsuwa na
daidaita kaina,a hankali na yanko cake d'in nakai bakinsa ai kuwa caraf ya had'a
tare da hannun nawa yasa abakinsa yana tsotsa nan da nan hannun nawa ya fara rawa,
saida ya had'iye cake d'in sannan shima aka bashi damar ya yanko ya bani,kai rashin
kunya tanaga namiji wai daya yanko cake d'in sai yasa a bakinsa ya rik'e da
hak'orinsa sannan ya kamo fuskata zuwa tashi fuskar yana kai bakinsa ga nawa da ido
yaimin alama dana bud'e bakina,runtse idona nai ina d'an bud'e bakin nawa turamin
cake d'in yai cikin bakina yana hade baku nan namu waje guda, innalillahi kawai
nake furtawa cikin raina jikina yana rawa, da k'yar na hadiye cake d'in kwalla tana
taruwa a idona ta b'acin ran rashin kunyar da yake tsulawa a gun yana sani jin
kamar k'asa ta tsage in shige,
Zuwa lokacin ihu ya gama karad'e Hall d'in gaba d'aya tafi kawai Ke tashi da ihun
mutane,su anasu ganin ya gama wayewa k'arshe wannan abin da yakeyi, wanda ni kuwa
anawa sashin nake ganin zunzurutun rashin kunya ne da wayewa irinta nasara, abinda
yayi da wasa ko don nuna wayewarshi ga abokansa sai ya juye mai ya koma sabon
yanayii tare dashi don har ya fara manta inda yake tsaye k'ok'ari yake ya wuce
makad'i da rawa Allah ya taimakeni Mus'ab ya gane halin da abokin nasa ya fara
shiga don haka yai m.c magana kan ya bawa angon da amarya damar komawa mazauninsu,
jiki a sanyaye ya ruk'o hannuna zuwa mazaunin namu,Duk kansa yai mai nauyi, yama
rasa tunanin da zaiyi,kawai sai ya lumshe ido, dake hankalin kowa naga filin rawa
sai ba'a lura da yanda yanayinsa ya canja ba, a sannu tunanin sa ya fara dawowa
wani mugun tsaki yaja tare da furzar da iska tunawa da yayi wai bakinsa ne cikin na
wannan y'ar Arabic d'in, har yake neman watsa kansa a gabanta, mutttssssss ya k'ara
Jan tsaki tunawa da yayi da matsayinsa da nawa matsayin,ni kuwa zuwa lokacin duk
jikina ya K'ara yin sanyi jin tsakin da yaketa ja ,daman gashi dik a takure nake.

Haka aka tashi a taron dukka ni dashi da abinda muke sak'awa cikin zukatanmu,
bayan mun fito yacewa abokansa suyi k'ok'ari su maida dukkan y'an matan nan
gidajansu, sannan ya amsa key d'in motarsa yace zai ja mu koma ba wanda zai shigar
masa mota yanzu,dariya suke ta masa nan wani abokansa ya matso yana rad'a mai gulma
kan zuwan fadla da kukan da tayi sanda taga bakinsa cikin nawa, da kyar suka
rarrasheta ta tafi, d'age kafad'a yayi yana jan tsaki yace " damuwanta ne wannan
ai ban gayyaceta ba" nan motan yayi yana d'agawa sauran hannu muka wuce gida.

Muna zuwa part d'in mu muka wuce ba wanda ya tankawa wani shi yai d'akinsa nima
na shiga wanda aka fara kaini cikinsa matsayin nawa, kai tsaye kayan jikina na cire
tare da shigewa toilet nai wanka na d'auro alwala nazo naita jero salloli ina
rok'on ubangiji ya samin juriya da hak'uri kan Duk yanayin da zan tsinci kaina
ciki a zaman aurena, sannan na rok'i Allah ya sanya dukkan alkairai cikin rayuwar
auranmu,na dad'e bisa prayer mat ina kaiwa Allah kukana, har tsakiyan dare sannan
bacci ya fara fuzgata,banko cire rigar danai sallarba na haye gado da addu'a bakina
ba jimawa bacci me nauyi yai gaba dani.

Kiran sallar asuba ya farkar dani da kyar na iya bud'e idona don baccin dake
cikin sa,ga tarin gajiyar biki, haka na daure nayo alwala nai salla azkar ma inayi
bacci na jana haka nai na koma gado,wanda ban farkaba sai takwas, ina farkawa naji
yana bud'e gidan zai fita bud'e labulen window d'in nayi ina kallonshi haryaje
parking space ya shiga mota ina tsaye naga ya tada motar ya fice, toilet na shiga
na had'a ruwa me zafi na gasa jikina sannan nayo wanka, wasai na jini yanzu duk
gajiyan ta bar jikina,banyi wani dogon kwalliya ba powder da lipstick kawai nasa
Sai turaran Humra dana jik'a jikina dashi, na d'auko riga da siket na atamfa na
saka tare da kama kaina da ribbon na d'aure,ban d'aura d'an kwali ba sai mayafi
dana yafa na fito parlor, kewaye gidan na farayi ina kallon yanda tsarin part d'in
yake kasancewar nasan ni kad'ai ce a gun baya nan,

parlour biyu duk ansa kujeru, set d'aya orange and copy, set d'aya pink and
purple, sai d'akuna biyu suma Duk ansa kaya,a babban parlourn ansa min
dank'akemiyar Plasma t.v a gefe guda ansa show glass ta turaren wuta wanda aka
cika ta taf da designed na kwalabe aji iya aji sai standard flowers a jere a gefen
show glass d'in yayin da akasa wani had'ad'd'an santer table me matuk'ar a
tsakiyar jerin kujerun, cen gefe dining area ne wanda aka saka had'ad'd'an dining
table me zagaye da kujeru guda shida,daga gefe kuma fridge ne tsaye ash colour,
gefen dining area d'in wata show glass ce ta kwance me hawa biyu duk an jera wasu
zafafan glasses cups kalan fari tas Dame kalan ruwan garai sai masu flowers duk
ajiki, a gefe guda kuma jikin dining area d'in duka k'ofar shiga kitchen ne,wanda
yake k'aton gaske me d'auke da d'an madaidaicin stor a ciki,wanda aka cika su taf
da kayan abinci, cikin kitchen d'in a kewaye yake da loga sama da k'asa duk anyi
min jeren kayan kitchen sai cooker gas me had'e da oven da electronic ajiki, can
jikin stor d'in ansa de freezer bud'e ta nayi naga kayan miya da nama acikinta
na maida na rufe tare da jingina jikinta ina tunanin meya kamata in shirya na
breakfast, Dukda nasan bai zama dole yaci abinda zan girkaba amma dai hak'k'insa ne
in dafa mai,wannan tunanin ya bani k'warin gwiwar fara had'a mana breakfast me
kafiya, kasancewar akwai dukkan kayan amfani fa na'urorin girki kala kala a gun
yasa nan da nan na gama had'a komai na zuba a cikin wasu zafafan Warmer's
lafiyayyu, nazo na jerasu jan dining table sannan na koma na gyara kitchen d'in duk
abinda nai amfani dashi saida na gyara na goge ya zama kamar ba'ai komai ba a
kitchen d'in, turare gidan na k'ara yi da turaren wuta sannan na koma d'aki na
k'ara gyara kaina,hijabi na d'auko cikin kayana wanda ya shiga da atamfar
jikina,na fito zuwa cikin gidan,a bakin parlour na had'u da sweety da sauran y'an
biki da basu tafi ba suna bawa ma'aikatan gidan umarnin inda zasu gyara, tsalle tai
ta rungumeni tana fad'in "oyoyo Aunty Nah wlh tun d'azu nake tunanin inje in duboki
amma ina tunanin ko buku tashi a bacci ba". D'an hararenta nai ina fad'in "ba
wani nan kawai kin manta dani ne cikin gidanku,amma bacci me zamuyi tayi har yanzu
around 11" y'ar dariya tai tanamin rad'a a kunne " nasan ko ansha amarci jiya"
duka nakai mata ina fad'in "Allah ya shiryeki Ke kam ni ban hanya in wuce". Dariya
ta farayi ta ruk'o hannuna " zo in rakaki ciki nasan surukanki kika zo gaidawa"
ban kulata ba na fara gaisawa da y'an wajan sannan muka shiga ciki,babu wasu mutane
da yawa,y'an uwansu ne na katsina sai tsirarun na nan garin,tsugunnawa nai na fara
gaishesu, nan suka shiga ansawa cikin sakin fuska suna tambayata ya bak'unta,kaina
a k'asa naji fitowar Aunty Murja daga d'aki tana cewa "a'a amarya kin fito ai na
aika muku da abin breakfast akace k'ofar a rufe buku tashi ba". Cikin
tsananin kunya nace "Aunty ai nayi mana breakfast d'in ma" haba Khadeejah me
yasa kika wahalar da kanki ga gajiyar biki tare dake aida biki yi ba ma kin huta
sosai, mirmishi kawai nake kaina a k'asa tace "taso muje ki gaida Abban naku"
mik'ewa nai ciki da nutsuwata nabi bayanta zuwa sashin Abban,da sallama muka shiga
na tsaya daga bakin parlourn tace " k'araso mana " a zaune muka same shi kan rug
yana cin abinci da fara'a kan fuskanshi yace yace "Khadeejah har kin fito" cikin
girmamawa sosai na gaisheshi ya amsa yana tambaya ta ya gajiyan taro, d'an mirmishi
nai nace "A khan fulfill ah " yace " Murjah Allah yasa dai y'ar taki taci Abinci
ko?". "Eh Alh, an aika musu ma k'ofar a rufe basu tashi ba,sai yanzu take
cemin ai tayi musu ma ". "Masha Allah, Allah yai muku albarka ya
Baku zuri'a d'ayyiba kiyi hak'uri da rayuwar aure kinji Khadijah kisa a ranki
jihadi zakiyi aljannarki zaki nema kinji" gyad'a kai kawai nakeyi nan yaci gaba
da yimin nasiha sosai , Aunty murjah ce taje ta d'auko key tana mik'o min tace "
Khadeejah ga mukullin motarki jiya ban baki ba sabida jama'a Kar ki yar".
Karb'a nayi ina fad'in "Na gode Allah ya saka da alkairi Allah ya k'ara girma".
Ameen Ameen suketa amsawa, sallamar sace tasa suka kalli k'ofar ni kuwa banko
d'ago ba kaina yana ak'asa, nan ya sami waje kusa da Abban ya zauna ko kallon
inda nake baiyi ba yace " Abbah barka da safiya, Aunty kin tashi lfy " tare suka
amsa da "lafiya qlau ya gajiya " cikin basarwa yace "Normal". Kallon sa
sosai Abbah yai yace "d'azu naga fitarka ina kaje da safe haka?" "Ah naje raka
friend's d'ina ne airport zasu koma". " ok an gode musu Allah ya saka da
alkairi". Inji Abbah mik'ewa yai yana fad'in "Abbah bari in k'arasa in huta " a'a
zauna muyi magana ". Komawa yai y zauna badan yaso hakan ba, "Daddy nah ga matarka
nan amana ce a gareka Amanar Allah kuma amanata ka rik'e ta da amana ka bata
dukkan kulawar data kamata karka sa aranka ni na aura maka ita,ka rink'a ji har
cikin zuciyarka cewa kai ka ganta kaji kana so ka aureta,in har kayi hakan ya gama
min komai a duniya,kuma zanci gaba da alfahari da kai dukkan wani hak'k'in uba akan
d'ansa ka sauke min nawa in har ka kula da Khadeejah, marainiya ce ka zame mata
miki ma gurbin miji kuma ka zame mata gurbin uba a sanda buk'atar hakan ta taso
kaji Baba nah". " ok Abbah ba damuwa " juyowa yai gareni yace "Khadeejah kiyi
biyayya ga umarnin mijinki matuk'ar bai sab'awa umarnin ubangiji ba kinji". "
insha Allah Abbah ". " yawwa Allah yai muku albarka ku tashi Kuje ".
Jira nai ya fara mik'ewa ya fita sannan nabi bayan sa, a balcony mukaci karo
da sweety nace "To wuce muje ". Dariya tai tace " yanzu mijinki yace wai inzo in
had'a mai abin breakfast nace kin shirya mai ai,don haka kije ki had'a mai zan
biyoki a baya in na k'arasa abinda nakeyi ".
Kallonta nai cikin had'e rai nace " ba komai na gode tun yanzu kin fara guduna
don kin ganni a cikin gidanku".
Rik'oni tai da sauri tana fad'in "Sorry Aunty nah wlh yunwa nakeji ban karya
ba ".
" yawwa Daidai kenan Kinga saimu karya tare ai nima banci komai ba".
Badan taso ba ta bini muka tafi, muna shiga na taddashi kan dining harya had'a
abinda zaici ya fara kwasar gara, kallon sweety nai nace "jeki zubo mana muci anan
kinji" wata dariyar rainin hankali tai tace "ashe kuwa bazamuci ba,karki bada kanki
don Allah muje kawai dining d'in muyi fuska muci kayanmu" ruk'oni tai muka k'arasa
kan dining table d'in ta zauna tana fad'in "Aunty nah had'a mana don Har k'amshi ya
cikamin hanci".

Cikin nutsuwata wadda ta had'u da sanyin da jikina yai na bud'e baki ina
fad'in " Barka da safiya" yi yai kamar ba dashi nakeba saida na k'ara maimaitawa
sannan yace "yawwa" kawai fara had'a wa sweety nai sannan na D'an d'ibi chiefs da
ruwan tea rabin cup , shuru wajan sai k'aran cokula kawai kakeji, sweety jin shurun
yai yawa tace "Aunty nah wlh kunna na fa ya fara motsi,wannan girkin ai sai kisa
mutum ya fad'o akan kujera".
Cikin hararan wasa nace " hhhhmmmm tsokana ko".

"Da gaske ba tsokana ba girkin yazo da wani salo fa ". Mirmishi kawai nai don
Duk a takure nake, zata k'ara yin magana yace " kai sis mana kin cikawa mutane
kunne,kinsan dai ban son ina cin abinci ana surutu ko,son a tofe abinci da yawu
kawai ". Dariya tai tace " na manta amin afuwa big broth ".
Daga nan bata k'ara magana ba,ni na fara tashi na komai parlour na zauna ,bayan
y'an mintuna ta biyo bayana, shi kuwa k'arawa ma yai yaci gaba daci, araina nake
mamakin wane Irin cine dashi haka tun kafin mu faraci yake ci har min gama yana
aikawa".
Kamar sweety tasan tunanin da nake cikin raina naji ta matso kusa dani tana min
rad'a " Aunty na saifa kinyi da gaske don wlh mijinki babban container ne dashi a
cikinsa mugun ci gareshi baya wasa da nik'a".

Mirmishi nai a hankali nace " hhhmmm ba ruwana in yajiki"

Dariya tai tace "to shike nan tunda bakya so na rink'a baki sirrin. . .".
K'arar wayarta ce ta katse abinda zatace ta d'aga tana fad'in " ok gani nan
zuwa".
Mik'ewa tai tace " Aunty na bari inje ana nemana Kinga muna da sauran bak'i amma
in duk suka tafi zan dawo anjima".
Kai kawai na d'aga mata,
Tana fita na tashi na shige d'aki na cire hijab d'in jikina ina kwanciya kan
gado, wayata na d'auka na kira number din Aunty Hafsa bugu biyu ta d'auka tana
fad'in "Amarya yanzu nake zacenki ai "
Cikin muryan kamar zanyi kuka nace "Um um Aunty kin manta dani dai".
Dariya tace " Haba wa zai manta da y'ar sa,koda biki kirani ba anjima zan
kiraki, ya gidan ya bakunta".
Nan muka gaisa ina tambayarta yaya tace yana waje , nace su umma fa tace duk
gasu nan,Basu wayar tai muka rink'a gaisawa dasu nace ta bawa su Aunty
juwairiyyya, tana karb'a nace "Aunty wai bazakuzo ba har yanzu " dariya tai tace mu
kan Bazamuzo ba amma da ga y'an matan nan suna shiryawa duk zasuzo"
"Yawwa Aunty don Allah kice suzo yanzu fa".
Nan mukai sallama na kashe wayan ina murna yanzu zan rabu da zaman kad'aici.

Taku ce
y'ar mutan ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

‫ من الشيطان الرجيم‬،‫أعوذ باالله السميع العليم‬.

0⃣2⃣8⃣
0⃣2⃣8⃣ 0⃣2⃣8⃣

K'arfe d'aya ina kan prayer mat na idar da sallar ina addu'a naji ana knocking
door mik'ewa nai naje don bud'ewa hayaniyar da naji na tabbatar y'an gidanmu ne,da
sauri na bud'e ina murna,cikin farin ciki na rungumesu muka k'araso cikin
parlourn, bayan mun gaisa bajewa mukai muka shiga hira ana shafta Azeeza tace "
Ke ina fatan kin d'ora mana watu don bamuci na rana ba muka taho"
Dariya nai nace "he lalle ma ni zan muku girki wlh tashi Ku shiga kitchen d'in
da kanku Ku girka abinda kuke so don a gajiye nake matuk'a" Zainab ce ta kalleni
wai "lalle ansha amarci dole a kasa girki amma ai kinwa mijinki yaci" "ah donme
bazanwaciki ina ba yaci kune dai bazan muku ba".

Mik'ewa sukai zuwa kitchen suna nemawa Kansu abinda zasu girka, nida Asma'u da
Zainab suka barmu zaune,muna hira Asma'u tace " wlh Nahna bikiga yanda kikayi
kyau ba, kin dace da gidan sosai ".
Mirmishi kawai nai Zainab ta d'ora " To mamana ta shigo sahun mu y'arki ta
rigaki sanin dad'in aure".
Dungureta nai nace " Y'ar duniya Ke kikasan wani dad'in aure ni ba ruwana ".
Hira muke sosai suna k'ara fad'a min yanayin zaman aure kasancewar su sunyi sun san
yanda zaman yake, sosai na bud'e kunne ina k'ara kwasar dabarun zama da miji,
kusan awa da rabi suka gama girkin shinkafa da miyar kaji sukai da couslow,
bayan sun gama naje na d'auki wasu sabbin cooler na zuba mai abincin, ina fitowa
daga kitchen d'in shi kuma yana fitowa daga d'akinsa,kallo d'aya nai mai nasan
bacci yasha,don da alama ma alwala yayo zaiyi sallah gaisheshi sukai ya amsa ba
yabo ba fallasa, ya fice , d'aya palourn naje na shirya mai abincin sannan na dawo
muka fara cin abincin, bayan mun gama muka gyara gidan tare da kitchen din, nan
muka k'ara bud'e shafin hira tunda daman suma sunyi sallar azahar d'in su, sai da
akayi la'asar sannan muka tashi don gabatar da sallah daga nan kuma suka fara
shirin komawa gida number d'in sweety na kira nace tazo suyi sallama dasu azeeza
mutuniyarta,nan tazo suka gaisa tace bari taiwa driver magana ya fito da mota ya
maidasu, tana fita na bud'e musu duk akwatinan lefe na nace su zab'i Duk abinda
suke so,ganin sun tsaya filako,yasa na shiga fitar musu da kaina kayan kwalliya ko
wacce na cika mata Leda dasu underwears,saida sukace ya isa , sweety ce ta shigo
tana cewa su fito driver ya fitar da mota, haka na rakasu suka tafi duk jikina ba
dad'i don Gobe zasu wuce nasan ni damu k'ara had'u wa kuma wata hidimar ta taso a
sakkwaton, bayan na koma k'ara gyara gidan nai nasa mai turare,sannan na shiga
wanka ,bayan na fito na shirya cikin wata doguwar riga kalar popul me jikin roba
duk jikinta stones ne nasa d'an k'aramin mayafi kalanta nai rolling,lokacin
k'arfe biyar da rabi ina fitowa na ganshi ya fito daga k'aramin parlourn kaina a
k'asa nace "sannu da zuwa" bai kalli inda nake ba yace " wa kika ajiyewa wancan
abincin sauran mutane,ko ance miki ina cin abincin da mutane da yawa sukayi
shi,niba k'azami bane don haka kije ki fiddashi cikin parlourn ".

Wani bak'in ciki naji ya turnik'eni amma saina hadiye na wuce, fito da cooler
d'in nayi na fara k'ok'arin d'ora mai wani abin,Abu mai sauk'i nake son girka mai
amma ina tunanin maganar sweety ta d'azu da take cewa cine dashi sosai baya wasa da
cikinsa,don haka na duba cikin kayan abincin namu naga akwai garin doya don haka
nan da nan na d'ora ruwan zafi kafin meye ya tafasa nan da nan na tuka sakwara na
kira sweety a waya nace don Allah ina zan sami farar Leda zan kwashe sakwara tace
bari ta kawomin, D'an lokaci Sai gata da ita tace," na fad'awa Aunty ma yanzu babu
Leda a part d'inku gashi can ta bawa driver ya siyo muku".
Karb'a nai na fara bud'e ta ina cewa "don Allah ya za'ayi da abincin nan Kinga
baici ba Kar abarshi ya lalace"

" OK kawo in kaiwa ma'aikatan nan zasu ci "

Tana fita na kwashe sakwaran a Leda na jera cikin wasu warmares d'in masu
d'aukan hankali don ba k'arya an zubamin foodflast da yawa kuma masu matuk'ar kyau,
miyan agushi na shirya lafiyayyiya da taji naman kan rago,naso in had'a lemo amma
lokaci ya tafi don har an fara salla a masallatai, Nima da azama na juye miyan na
had'a zuwa dining area, da sauri sauri na shige toilet na d'auro alwala, na tada
sallah, ina idarwa naji shigowansa don haka ban tsaya doguwar addu'a ba na shafa na
fita,amma saina tadda baya parlor d'in don haka na koma na k'ara gyara wa na feshe
jikina da turare na k'ara shafa powder da lipstick, na fito yanzuma baya nan
kitchen na wuce na wanke tukwanan da y'an kwanikan dana b'ata, ina goge hannuna da
kitchen towel naji maganarsa a bayana "Ke haka ake ajiyewa mutum abinci ba serving
spon koda hannunki zan d'ibi miyan"
Dafe kai nayi don gaba d'aya sauri saurin da nake yasa na sha'afa bansa
serving spoon d'in ba, amma saina nace "kayi hak'uri don Allah wlh na sha'afa ne"
tsaki kawai yaja ya fita a kitchen d'in a ransa yana k'unk'uni shi rabon ma daya
shiga kitchen harya manta don komai yimai ake,amma daga yin aure jiya shine har yau
ya fara shiga wai kuma a haka ake cemai komai nashi zai canja tunda yai aure wai
zai sami kulawar dabai tab'a samu ba mutttsss yaja dogon tsaki yana zama kan
kujerun da sukai wa dining d'in k'awanya".

A hankali na k'araso inda yake na fara zuba mai abincin Wanda k'amshi ya gama
cika gidan tako ina, wani yawu ya had'iya nan da nan yaji yunwar da yakeji ta
k'aru, don haka ina gama ziba mai yaja flat d'in ya fara ci,mik'ewa nai zan bar
wajan yace "Ke dawo ki zauna,

Ba musu na dawo na zauna kaina a k'asa ina jinsa yanata loma abinsa, wayata
dake aje gefen kujera ce taketa k'ara amma banko yi alamar tashi in d'auko ba saida
yace "Ke wai bake ake kiraba kika barwa mutane abu na cika musu kune"

A sannu na tashi na d'auko wayar na dawo mazaunina, zuwa lokacin ma har wayar ta
katse number d'in Aminyata Hafsah ne da sauri nabi kiran tana shiga ta d'auka da
sallama muka gaisa kamar yanda yake mafi yawan lokaci in nida ita ne ko a zahiri ko
waya bamu fiye yin magana da Hausa ba don haka yanzuma cikin harshen larabci muke
magana tanata tsokanata, mun kai minti hud'u sannan mukai sallama, ina kashe wayan
naji ya saki wani mugun tsaki,da sauri na d'ago na kalleshi naga ya k'ara tsare
gira don haka na maida kaina ga wayata na nemo number d'in sweety tana d'auka nace
"kizo muci abinci mana "
Dariya tai tana fad'in "wane ni nazo cin abinci da daddare oga na kusa kedai
kuci kawai ki kulamin da cikin d'an uwana".
Kwafa nai nace " wato ni ba y'ar uwakki bace ko na gode"
"A'a wlh ba haka nake nufi ba Aunty nah ki gane kawai ai yanzu banda sama dake
sorry kinji".
" To indai kina son in hak'ura kizo muci abinci tunda ai nasan yanda kike son
sakwara ".
" hhhmmmm kin san me na gaji sosai ban son tashi Amma zan turo yanzu a
karb'amin".
Lokaci kad'an d'aya daga cikin y'an Aikin gidan tazo ta amsa Mata abincin, a
lokacin ne shima ya gama ci na kwashe kwanikan zuwa kitchen don ni kam bazanci ba
sai nayi sallar isha'i,ina fitowa zan wuce d'aki naji kiransa a bayana,"Ke zo nan"
Dawo wa nai Nazo na zauna k'asan kafet dake malale tsakiyan kujerun wanda shi
yake zaune saman kujeran, nakai wani lokaci a zaune kafin ya d'ago kansa ya
kalleni lokaci d'aya ya kauda kan nasa sannan ya fara magana "ina son in sanar dake
duk wasu dokoki na, da farko ki sani niba k'azami bane banson k'azanta ko kad'an,
sannan ba abincin kowa nakeci ba ni karma kiyi bak'i suyi girki kice zaki ajiyemin
bana buk'ata in kuwa kikai hakan zan gane kuma zan d'au mataki,Abu ba gaba indai
kika kawo min abinci bazaki tashi ba saina gama ci tsaf na tashi sabida bazai yuyu
ki ajiyemin abinci ki tafi ba kuma nazo buk'atar k'arawa ko wani Abu kuma saina
kiraki ba,d'akina ina buk'ar a rink'a gyaramin shi sau biyu a rana da safe da
yamma, duka k'anan kayan da nake amfani dasu Ke zaki rink'a wankewa sabida kowa na
fad'a min nai aure zan huta don haka dole in huta Duk da banga wani abin hutawa
cikin auran ba, nayi niyar gasa miki aya a hannun na shishahigin da kikaiwa
rayuwata da rashin kunyar da kika dad'e kinamin a school yanzu anzo inda zan rama
kin kawo kanki da kanki,amma sakamakon diddani kunya da kikai gun friend d'ina a
events duka zan miki sassauci akan abinda na tsara a kanki,karki Bari na kamaki da
wani kuskure cikin umarni na"

Cikin sanyin miryata nace "Insha Allah zan kiyaye "


" Jeki " kawai ya fad'a yana kauda kansa gefe ,
Mik'ewa nai na wuce ina fad'in "Saida safe "
Bai amsa ba sai juyowa da yai yabi bayana da kallo har nashige d'aki,
Ajiyar zuciya ya sauke bayan wucewata yana sak'e sak'e a ransa" To wai meyasa ma
nake son sassautawa yarinyar nan inda naci burin azabtar da ita amma me yasa
zuciyata Ke tankwasani kan na kyaleta? Tsaki yaja ya tashi ya shige d'akinsa ina
sak'awa da warwarewa.

Ni kuwa ina shiga d'aki salla na fara k'ok'arin yi


wadda naji har an fara kira a masallatai.

*********
A can gidanmu kuwa washe gari duk yan garinmu suka tafi,amma banda mama na da
umma da yayyyena mata guda biyu,sabida basuzo sunga d'akina ba,don haka da dare
yaya Haroon ya kawosu ai kuwa murna kamar zan tashi Sama bayan na cika musu gabansu
da lemuka nazo na zauna tsakiyansu inata fara'a da murna , nan yaya Ya k'aramin
nasiha haka ma su mama suka k'aramin nasiha da hak'uri akan zaman aure, nidai
sauraransu nake ina mamakin kowa dai nasiha da ban hak'uri basu son yanzu ni
banjin wata damuwa ko d'aya kan wannan auran ba don addu'ar da nakeyi da rok'on
Allah ya ansamin ya samin sassauci sa nutsuwa sosai a cikin zuciya ta,

Yaya ne yace inwa su umma rakiya gun Aunty murjah da Abbah su gaisa, d'aki naje
na d'auko hijab d'ina muka tafi.

Sosai suka sami tara daga Aunty murjah da Abbah cikin mutunci da girmamawa suka
gaisa jin yaya Haroon na waje yasa aka kirashi ya shigo ciki shima suka gaisa Abbah
ba ruwanshi a waye yake abinsa don haka baya surukuta ya saki jiki yaketa hira
yana k'ara yi musu godiya,kallona yai yace "Khadeejah sun gaisa da Mijin naki
kuwa ?".
Cikin jin kunya nace " a'a Abbah da suka zo ya fita amma yanzu ban sani ba koya
shigo".

"To maza jeki duba inya dawo ki kirashi su gaisa ai ba dad'i suzo basu gaisa ba
kuma".

Mik'ewa nai zuwa part d'in namu ai kuwa ina shiga na ganshi tsaye yana kunna
T.V matsowa nai kusa dashi nai k'asa da murya " Abbah yace kazo parlourn sa zaku
gaisa dasu maman mu ".
" OK " kawai yace na juya kafin na fita part d'in harya biyo bayana kusan atare
muka shiga,Abinda ba halinsa ba wai jin kunyar wani mutum amma yau sai ya tsinci
kansa da kunyar su Umma don haka ya sunkuyar da kai k'asa yana gaishesu amsawa
sukai cikin girma,wanda hakan ya faranta ran Abbah matuk'a. Nan dinma dai had'a mu
akai aka k'ara mana fad'a kan rayuwar aure,sannan sukai musu sallama Abbah ya bawa
Aunty murjah kud'i masu yawan gaske ta basu,sukak'i k'arb'a Sam saida taita musu
magiya sannan suka karb'a tare da godiya na rakosu bakin motarsu muna sallama nan
wani hawaye ya b'allemin harda shashshek'an kuka sweety ce ta rik'oni tana ban
hak'uri suka tafi.

Haka ta rakoni part d'in tanata rarrashina a haka ya shigo ya samemu ta gefen ido
ya kalleni ya kauda kai gefe har zai shige d'akinsa sai ya tsaya yana cewa"kukan fa
?".
Sweety ce tace "Wai don su maman su sun tafi gobe zasu wuce sakkwato".
" shine abin kuka, jeki zamu rufe k'ofar"

Mik'ewa tai tana cemin "saida safe Aunty na".


Tana fita ya bita ya rufe k'ofar sannan ya kashe kayan kallon ya wucewarsa
d'akinsa bai k'ara tanka min ba, ganin zaman bazaiminba yasa na kashe Haske na
shige Nima d'akina na sa kayan bacci na kwanta.

*******
Haka rayuwar tamu ta kasance zaman kadaran kada han har tsawon kwana bakwai
kullum zan gyara mai d'akinsa safe da yamma sannan koda yaushe innai girki in
zaici saina zauna ya gama ci zan bar wajan, yau ya kama lahadi kuma ina son gobe
Monday in koma school don lectures da yawa sun wuceni,don haka bayan na gama had'a
abin breakfast na gyara ko ina nai wanka na shirya cikin wasu riga da siket y'an
kanti masu laushi wanda suka kama jikina matuk'a na gyara gashina nasa mai ribbon
kalan kayan ja sannan na d'auko flat takalmi shima ja nasa bansa dogon d'an kunneba
sai barima dana mak'alawa kunnan bak'a, na feshe jikina da turare me sanyin
k'amshi, fitowa nai zuwa d'akinsa nai knocking saida yaban izinin shiga,na tura
k'ofan na shiga tsaye yake dagashi sai d'an k'aramin towel d'aure a kugunsa, da
sauri na kauda idona daga kallon sa ina fad'in "Ina kwana"
" lafiya qlau"
Bayan haka duka mukai shuru can nace "um daman zan gyara d'akin ne nai tunanin ko
ka shirya ne".
Tafiya ya farayi zuwa hanyar toilet d'in yana fad'in" ki gyara mana".
Ya shige toilet d'in, yana shiga na fara gyara d'akin na canja bedsheets d'in
nasa sabo na share d'akin na kunna turaren wuta a lokacin ya fito daga wankan yana
tsayawa gaban dressing mirror na fad'a toilet d'in na had'a inner wears d'in sa na
wanke sannan na wanke toilet d'in na fesa freshener na fito, harya sa kayansa ya
gama shiryawa yana tsaye yana d'aura agogo na wuce shi saida naje bakin k'ofa
sannan nace mai "food is ready " "OK" yace kawai ,

D'akina na koma na k'ara goga Humrah na kalli kaina a madubi naga komai dai
dai, ina fitowa shima yana fitowa son haka a tare muka k'arasa dining table d'in,
na had'a mai break d'in kunun gyad'a ne da awaran kwai sai ferfesun kifi wanda
yasha kayan k'amshin miya, cup k'arami na d'auka nima na zuba kunun na fara sha
sab'anin da da kullum sai ya gama ya tashi nake cin nawa, nayi mamakin yanda naga
yana shan kunun gyad'an haka don saida na k'ara mai sau biyu cup uku yasha sauran
abubuwan nema bai wani tab'a ba, bayan ya gama yana goge baki da tishu na kalleshi
kad'an tare da rage muryata sosai nace "Am don Allah ina son komawa school gobe ".
Kamar bazai magana ya mik'e saida yai taku biyu zuwa uku sannan ya amsa " ba
matsala"

Daga haka ya fice daga gidan,


Ni kuwa nan da nan na tashi na had'a wanke wanke nayi,na tsaftace kitchen d'in
sannan na tafi wajan su sweety duk da bata nan tana school muka gaisa da Aunty
murjah na zauna muka d'anyi hira a nan take fad'a min Abbah yace za'a bani y'ar
aiki guda d'aya ta dinga taimakamin ,mirmishi nai nace " Aunty wane aiki ne dani da
har za'a kawo min y'ar aiki,wlh ba komai duk zan iya,kicewa Abbah ya barta kawai".
"A'a ko wanke wanke ai ta rink'a miki da moping".
Nace " To Aunty mu bari zuwa gaba in Aikin ya fara min yawa zanyi magana ".

Nan nake shaida mata ma gobe zan fara koma school, taimin fatan alkairi mun D'an
jima muna hira sannan na koma part d'ina,

Yau da wuri na fara Aikin girkin dare don Danbun cous cous nake sonyi kuma da
yawa nake sonyi sabida har Abbah nake son kaiwa don nasan mutuminsa sannan ina son
inyi lemon kwakwa.

Aikina nake cikin nishad'i na kunna wak'ar mu ta graduation Na N.C.E d'in mu


wak'ar larabci ce ta bugu sosai ina son wak'ar duk lokacin da nake cikin nishad'i
ta kan tayani ko in ina cikin kad'aici sai in kunta,yanzunma dagani sai d'an wando
3qurter da riga y'ar figigi mara hannu kasancewar zafi ta busa, ina aikina ina bin
kasidar nan da nan na gama aikin kafin sallar magriba harna kammala na zuba a
Warmer's sannan na zubawa Abbah a wani kalan cooler d'in na d'auko juk babba na
zuba mai lemon kwakwa d'in na d'auko kwandon sa abinci nasa aciki na d'auko wani
farin bowel me ruwan garai na zuba mai had'in coleslow d'in da nayi Duk na jera
sannan nashiga d'aki don yin wanka.

Wanka na shiga nayi tare da d'auro alwalan magriba sannan na fara kwalliya sosai
yau nai kwalliyar na saka dogon wandon jeans wanda yake pencil sosai nasa wata body
hug me roba k'aramin hannu gareta iya cinyar hannu ta kamani sosai k'irjina yayi
d'am a ciki kasancewar dukda nake siririya Allah ya wadatani da dukiyar fulani da
hips wanda suke da jan hankali don haka ko wane irin kaya suke karbar jikina,
doguwar riga after dress na d'auko nasa tare da hijab nai sallar magriba ina idarwa
bayan nai addi'oi na fito na d'auki abincin Abbah zan kai mai a k'ofar parlour
mukai karo da sauri na matsa ina fad'in "sannu ban kula bane" cikin tsare gida
yace " ina zaki?" " Abbah zan kaiwa abinci".
"Haka yace miki baici abinci ba". " a'a danbun cous cous nayi ne naga yana
sonshi shine na dibar mishi". "Ki sauri ni dawo malama ina buk'atar abinci yanzu".
" To " nace na wuce ina k'ara saurin tafiya ta, koda naje part d'in nasu sweety na
bawa abincin nace don Allah ta k'arasawa da Abba shi".
Tana ta min tsiya banko saurareta ba na juya na fice,
Sanda naje na sameshi dagashi sai gajeran wando da singlet na maza yana zaune a
dining area d'in hijabin jikina na cire tare da After dress d'in na k'arasa
gareshi yana d'agowa yaji wani Abu ya cakeshi a k'irji duk dashi bai zama me yawon
sha'awa ba sannan yana iya kallon mace ako wace Irin shiga bata rikitashi ba
kasancewar yana rayuwa cikin indai wa da turawa wanda basu damu da sitirce
al'aurarsu ba amma yanzu kallon da yai mata sai yaji wani abu ya tsirga mai dukda
abinda ya gani d'in ba bak'onsa bane a garin data baro, ya fad'a duniyar tunani
harna kammala zuba abincin naga ya lula tunani,bance komai ba na koma na zauna
saida naga abincin na shan iska baici ba nai k'asa da murya sosai nace "Abincin fa
yana hucewa ". Da sauri ya kauda kansa yana basarwa yaja abincin ya fara ci,daga
yanda naga yanaci yana kurb'ar lemon tare da lumshe ido na gane yaji dadinsa sosai,
satar kallon juna muke kusan sau biyar muna had'a ido hakan yasa duk ma naji kunya
ta kamani don na kula idon nasa akan k'irjina yake yawo,cikin wata murya daban
san sanda nayi ta ba na marairaice fuska" Don Allah inje d'aki "
Yi yai kamar baiji abinda nace ba yaci gaba dacin abincinsa, k'ara maimaitawa nai
badan yaso hakan ba yace "jeki " yana fad'a nai sauri na tashi don duk na takura,
gado na fad'a ina wani tunani araina mirmishi ya sub'ucemin na jijjiga kai ina
k'ara yarda da shawaran da zuciyata take bani.

B'angaran uban gayyar kuwa da kyar ya k'arasa cin abincin ya tashi ya shiga
d'akinsa tunani fal ransa anya kuwa bai fara jawa kansa raini ya bari yarinyar nan
ta kamashi yana kallon ta haka,lalle ya kamata ya k'ara tsare gida sosai yasan
makircin mata iri iri in suna son ka fad'a tarkonsu amma ita kam bata isa ya fad'a
nata tarkon ba,wai meye ma abin birgewa ga wannan k'aramar yarinyar kuma y'ar
Arabic me k'arancin wayewa mutttssss yaja tsaki yana dayawa kawai k'ara ya fara
shirin komawa India nan da sati biyu don baiga amfanin zaman sa a nan ba tunda dai
an tilastashi yayi auran to ai shima sai abashi damar shi kuma don haka gobe
zaijewa da Abbah maganar nan gaskiya.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣2⃣9⃣
0⃣2⃣9⃣ 0⃣2⃣9⃣

Yau Monday tunda nai sallar asuba ban koma bacci ba na shiga kitchen na had'a
kayan breakfast,shayin zobo na had'a wanda yaji na'a,lemon grass,da kayan k'amshi
danginsu citta da kanumfari,sannan na soya gurasan larabawa,nai D'an yam balls
kad'an, bayan na gama nai wanke wanke a gurguje na gyara gidan tsaf, wanka ma a
gurguje nai nayo kwalliya ta me sauk'i kasancewar yanzu nasan hakkin dake kaina
dole in canja salona ta kowace fuska dukda daman bawai ina shigar banza bane ko yin
wani Abu na shashanci amma dai dole in k'ara takatsantsan matuk'a yanzu,na shirya
cikin atamfa ta blue me yarfen ganye milk nasa hijab dina me hannu milk wanda yazo
min har kusa da idon sahu akwatinan lefe na na bud'e na d'auko takalmi da jaka Duk
milk, nasa kallo d'aya zakai min ka gano sabuwar amaryace, lokacin dana fito daga
d'akin bakwai da minti ishirin nasan bai tashi a bacci ba amma sabida kare hakki
saina tura k'ofan a hankali na shiga, kwance yake kan gadon yana bacci hannayensa
rungumu a k'irjinsa tsayawa nai na y'an seconds ina tunanin abinyi naga ya fara
motsawa da sauri na juya zan fita cikin muryar bacci naji yana cewa " Ke Mene?"
Ban jiyo ba na amsa mai "em daman nai tunanin ka tashi ne zan gyara d'akin
kafin na wuce school".

"Kije kawai in kin dawo kya gyara"


Yana fad'a ya juya yaci gaba da baccinsa.
Ni kuwa dining na nufa na d'anyi break Sama Sama don bana iya cin Abu da yawa da
sassafe haka, kud'i nasa a jakata masu nauyi don yin transport da sauran buk'atun
school.

Nayi nisa da gidan ina tafiyata a nutse saura k'iris in k'asara titi naji horn
d'in mota a bayana ban juya ba illa k'ara matsawa da nai gefe sosai don nai
tunanin ko hanya motar Ke nema amma sainaga ma ta matso kusa dani sosai ta tsaya
cak nima na tsaya ina mamakin waye wannan, muryar Abbah ce tasa na d'ago kaina ina
kallon motar "zo ki shiga mu tafi Khadeejah" naji yace ba musu na bud'e murfin
motar na shiga tare da gaishe da Abban da drivern dake jansa, cikin b'acin rai
Abbah Ke magana "Khadeejah ya akai kika fito school Ke kad'ai ina Mijin naki ya
barki fitowa a k'afa".
Cikin ladabi na k'ara sunkuyar da kaina nace " Abbah bacci yake ne be tashi ba".
"Shashancin banza kenan wannan bacci yafi iyalinshi mahimmanci kenan,ni jiya
Murjah Ke fad'a min yau zaki koma school abinda yasa ban miki maganar ba nai
tunanin kun shirya komai da mijinki,amma dake shi shashasha ne ya barki zakije ki
hau motar haya duk motocin dake cikin gidan sun zama ba amfani kenan,ko yanzu ma
driver Ke cemin gaki nan a gabanmu don yaga fitarki a k'afa yana goge mota lokacin,
amma zan had'u da Daddyn zai gamu da fishi na matuk'a da gaske, kema daga yau karki
k'ara yunk'urin fita ba mota ko ina zakije don haka ma dole ya fara koya miki mota
kwanan nan kema ki fara hawa motar ki".

Nidai tunda ya fara magana ban ce komai ba sai wasa da nake da yatsun
hannuna,haka muka kai har school d'in Abbah nata fad'a sai driver daketa bashi
hak'uri, motar na tsayawa nace " Abbah na gode a dawo lfy".

Kud'i ya miko min wai nasai wani abu nace a'a amma dole yasa na amsa .

Ina shiga aji na tadda hall ya cika taf amma lecturer bai zoba, nan fa
K'awaye na sukaita shewan ga Amarya ga Amarya nikam mirmishi kawai nake ina mik'a
musu hannu muna gaisawa nan akaita k'ara min Allah ya sanya alkairi way'anda ma
basu sami damar zuwa ba sukaita ban hak'uri suna fad'a min uzurinsu nikam ca nake
ba komai wlh addu'ar suma ta wadatar, a haka lecturer ya shigo shima saida yamin
Allah ya sanya alkairi dake ba wani yawa ne damu ba yasa duk malamanmu sun sanmu
kuma an basu I.V din d'aurin aure,
Wajan k'arfe d'aya muna masallaci zamuyi salla Naji kira a wayata da bak'uwar
number bayan na d'aga sai naji muryar Abbah nan yake tambaya ta karfe nawa zan
tashi nace mai sai wajan 5 yace to driver zaizo d'auka na in na fito bakin gate in
duba zan ganshi, godiya sosai nai mishi.

Lokacin da muka tashi ina fita bakin gate naga motar Abbah data kawoni na
jira nan na shiga drivern yaja muka tafi,sanda mukaje gida biyar da rabi a gaggauce
na cire kayana na shiga kitchen faran shinkafa na d'ora na nik'a kayan miya a
blender nan da nan na d'ora miya ma sannan na d'auko fruits na wanke na fara
gyarawa don had'a fruits lasad, ban koma d'aki ba saida naga na kammala aikina
duka na kwashe a flasks na saka fruits d'ina a fridge don yayi sanyi, lokacin
k'arfe bakwai don har an shiga salla da sauri nai wanka nai salla nasa wata riga
iya gwiwa me d'an k'aramin hannu nasa hula akaina tare da goga humra a duk jikina,
zuwa lokacin nasan Me gidan ya shigo ai kuwa ina fita na ganshi kan kujera a
kwance, ina k'ara sawa kusa dashi ya d'ago ya kalleni nace "sannu da zuwa ".

Kamar yanda ya saba ba yabo ba fallasa ya amsa min, dining dining d'in naje na
shirya mai abincin sannan na d'an tako ina cemai" na had'a abincin "
Cikin isa Irin tashi ya taso ya zauna ya faraci ina zaune gefenshi ina karanta
hand out d'ina, harya gama na kwashe kwanukan na gyara wajan,bayan nai sallar
isha'i naci abinci ban zauna parlourn ba na koma d'aki nai shirin kwanciya don
karatu nake sonyi sosai wanda akayi bana nan.

B'angaren Uk kuwa bayan yayi sallar isha'i a d'akinsa don ba ko yaushe yake bin
jam'i kasancewar addini ba waje ya samu sosai a zuciyarsa ba,sallolinsa dai gaba
d'aya ba wadda take wuceshi ko baije masallaci ba zaiyi a gida amma bayan kamsa
salawat d'in nan fa bai k'ara nafila ko raka'a d'aya,balle azimin tad'auwa'i,
addu'oi duk ba nashi bane, yana kwance kiran Abbah ya shigo wayarsa yana nemansa,
tashi yai yasa rigarsa ya fice.
Daga yanda yaga fuskar Abbah yasan da matsala don haka jiki a sanyaye ya k'arasa
ya zauna yana mai barka da dare, a ciki ciki ya amsa ya maida hankalinsa ga abinda
yake a computer d'in dake gabansa saida ya kusan minti uku sannan ya kashe ya juyo
gareshi, ya k'ara had'e rai sosai sannan ya fara magana " Daddy ka kyauta matuk'a
da tozarcin da kai min yau kaji ".
Da sauri ya d'ago ya kallin Abban yana fad'in " Abbah me nayi ?"
" ni kake tambaya ma me kayi ko yayi kyau".
"Don Allah Abbah kayi hak'uri ka fad'a min Abinda ya faru wlh ban san me nayi ba"
K'wafa Abban yai yace "Ka tozarta ni duk motocin dake cikin gidan nan ace wai
Khadeejah bak'uwa a cikin gidan nan yau duka kwananta takwas a gidan nan amma ta
fuskanci wulakanci daga gareka, y'ar mutane ka Bari ta tafi makaranta a mortar
haya, tsakaninka da Allah Daddy tsawan rayuwar ka zaka iya tuna lokacin daka hau
motar haya? Amma sai matarka mutuncinka data cancanci Suturtawa daga gareka itace
zaka barta fita titi ta hau mota ga tarin motoci a gida,ko Dan ka nunamin ka isa
kayi yanda kaso".

Girgiza kai ya shigayi yana fad'in "Abbah lokacin data fita bacci fa
nakeyi,kuma maimakon ta sami driver ya kaita shine ta tafi da kanta".
" OK bacci yafi uzirin matarka kenan yafi karatunta mutunci ko? To umarni nake
baka ba shawara ba daga yau karka kuskura in k'ara ganin matarka a wata mota inba
taka ba kuma fita ko wace irice Kaine me kaita,sannan daga nan zuwa kwana biyu ina
son ka fara koya mata mota koda ka koma indai in uziri ya taso mata ta tafi a
motar ta kaji na fad'a maka tashi kaban waje ".

Tashi yai ya fita ransa a mugu mugun b'ace da wannan hukuncin na Abbah, yana
shiga d'akinsa yai cilli da rigarsa ya fad'a gado yana huci da firzar da wata iska
me zafi,wai nufin Abbah shine driver na wannan yarinyar wai auran Dolan ma akai mai
bai isa ba kuma sai an bishi da dokoki masu zafi haka,gaskiya an takura shi wlh shi
wannan yarinyar ta zama masifa a cikin rayuwar shi ,anya bazai nemi hanyar korar
yarinyar nan daga gidansu ba ko zai samu ya wataya,saida ya gama kuncinsa da b'acin
rai ya shige toilet ya watsa ruwa don yaji sauk'in zafin da ransa Ke masa.
Yana kwance ya kasa bacci yana nazari kan wane Irin k'auna Abbanshi kewa Nahna
haka har yake fifita lamuranta akan na kowa,dame ta siye zuciyar mahaifinsa haka,in
yai tunanin sai dai kawai yaja mugun tsaki ya juya,a hankali kuma zuciyar shi kuma
ta fara mai lissafin Irin k'ok'arin yarinyar wajan yin duk abinda ya umarceta da
wanda ma bai umarceta ba,kamar dai yau ko sau d'aya baiyi zaton a wannan safiyar
zata iya yimai girki ba kafin ta fita amma daya tashi yana tunanin inda zai sami
abinda zaici yana fitowa parlour yaga ta shirya mai komai a table gashi ta gyara ko
ina har tana k'ok'arin gyara mai d'akinsa badan yace ta tafi ba amma gashi ma a
dawowar da tayi da yamman nan hartai girki ta gyara mai d'aki ta wanke mai toilet,
gaskiya in haka ne fa tana k'ok'ari, mutttssss kuma yakuma jan tsaki wani sashin na
zuciyarsa na fad'a mai to meye amfaninta daman in batai wad'an nan ayyukanba tunda
daman ta saba da wahala tun agidansu.
Haka yaita sak'awa da kuncewa har bacci yai gaba dashi ransa ba dad'i.
Taku ce
Y'ar mutan Ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

*Allah* *ka* *zab'a* *mana* *shugabanni* *na* *gari* , *Allah* *karka* *barmu*
*da* *zab'in* *kanmu* .👏

0⃣3⃣0⃣
0⃣3⃣0⃣ 0⃣3⃣0⃣

Yauma daga sallar asuba ban koma ba na shiga kitchen na fara ayyukana bayan na
gyara gidan ko ina na shirya cikin doguwar riga y'ar k'asar Sudan bak'a mai
yalwataccen k'asa nai rolling da yalwataccen mayafinta wasu sabbin takalmi da jaka
na fiddo cikin kayana orange color kasancewar aikin jikin rigar shima orange
ne,dole in kula wajan canja shiga don duk lokacin da mace tai aure idon kowa akanta
yake don aga yanda kamannin ta zasu canja da yanayin sutturarta,musamman y'an
makaranta(duk da ba yabon kaiba y'an department d'in Arabic sa ido bai damesu ba
abinda Ke gaban su kawai sukeyi)

Nazo k'ofar d'akin nasa naji motsin alamar ya tashi don haka na tsaya nai
knocking,ya bada izinin shiga,da sallama na shiga ya amsa fuska d'aure tamau cikin
sanyin muryata na gaisheshi bai d'ago ba ya amsa,nace "Em daman zan gyara d'akin
ne".
Tashi yai ya shige toilet daman dagashi sai towel d'in wanka, tsaf na gyara d'akin
nasa turare sannan na wuce nai break, ina mik'ewa yana fitowa cikin shiri 'kauda
kai yai gefe yana fad'in" In kin shirya wuce mu tafi".
Cikin D'an dibirbircewa nace "Tom bari in d'auko jakata"
bai tanka ba ya juya ya fice nima da hanzari na shiga na d'auko jakan na fito
tare da kulle k'ofar, harya tada motar na bud'e na shiga, cikin fishi naga yaja
motar da gudun gaske ya fice nidai kaina naga takardar dake hannuna ina karantawa,
kafin me sai ganinmu nai a gate d'in school d'in don bala'in gudun da yake yi har
ciki ya shiga dani yaja burki da k'arfi ya tsaya,cikin mutuwar jiki nace "Na gode"
na bud'e mirfin motar zan fita yai magana da izzarshi "Ke k'arfe nawa zaki tashi"
4:00 insha Allah "
Waya ya mikomin "sa number d'in ki anan" karb'a nai nasa mai ina mik'a mai zan
fita ya k'ara tsaida ni "tsaya" naja na k'ara zama, kira naji cikin wayana ina
d'aukowa yace "kiyi saving in kin tashi ki kirani da ita".

1k ya mik'omin rannan nashi kamar yaji sak'on mutuwa, nidai kaina na kawar ina
cewa " ka barshi akwai kud'i a hannuna ".
" wannan ba damuwata bace in zaki amsa ki amsa karki b'ata min lokaci ".
Karb'a nai ina godiya na fice a raina ina mamakin bak'in hali Irin nashi
mutum koda yaushe k'unci kuma a haka y'ar uwarsa Ke fad'in dad'in zama
gareshi ,ina wannan tunanin na k'arasa Hall d'in da zamuyi lecture a ciki.

B'angaren sa kuwa cikin bacin rai ya koma gida lokacin ya duba agogo ko takwas
har sa'ilin batayi ba aka tasheshi a bacci sabida wannan yarinyar tsaki yaja ya
wuce dining ya cika cikinsa sannan ya koma d'aki yama rasa abinyi ga bacci Sam ya
bar idon nashi daya d'an k'ara matsewa,gashi ba wajan zuwa gareshi ba duk abin dai
ba dad'i,haka dai ya d'au wayansa ya shiga net don rage kad'aici.

Ni kuwa lecture ta nai a nutse saida muka shiga period d'in k'arshe ne ya rage
saura minti goma mu fito na kirashi nace mun tashi don bansan Sai mun fito in tsaya
jiran sa.
Ai kuwa ko bayan fitowarmu saida nai kusan wata minti goman sannan ya kirani
yace min yana gate,Allah yasa daman kusa da gate d'in mukai lecture din don haka ba
b'ata lokaci na k'arasa da sallama na bud'e na shiga ciki ciki ya amsa nace mai "
Barka da yamma ".

" yawwa " kawai yace ya tada motar.

************
Haka rayuwar mu taci gaba da gudana kadaran kadahan ranakun da nake zuwa school
hud'u don bama lecture Friday duka rana kun nan shi yake kaini ya dawo dani,sannan
weak end da yamma mu fita ya koya min mota duka wannan lokacin ba abinda ya canja
daga zamanmu yanda muke dai haka muke Sai dai ni bana wasa wajan yin duk abinda
nasan hakkinsa ne dake kaina,sai dai b'angaren Abbah yana k'ok'ari matuk'a wajan
son faranta raina don haka nima duk sanda nake da lokaci banje school ba ina zama
in shirya mai abinda nasan yana sonci kamar su danbu,dashishin alkama,zob'o,kwad'an
zogale kona rama duk ire iren abinciccikanmu na gargajiya don haka kullum cikin
kyautatamin shima yakeyi.

A haka muka kai wata guda cif da auranmu,lokacin UK ya fara damun Abbah da
maganar tafiyar sa don a cewarsa duka abokansu da aka zab'e su tare zasuyi course
d'in wai Duk sun fara don haka Abbah badan yaso ba yace yaje ya fara shiri sati
biyu masu zuwa sai Ya tafi,Ba haka yaso Abbaan yace ba,yaso ace kwana biyu kawai ya
bashi amma har sati biyu, haka ya hak'ura yabi umarnin Abban,

Ranar da Dare Abbah ya Kira ni a waya inzo yana kirana, ba b'ata lokaci naje
anan yake shaida min miji na zai koma indai nan da sati biyu kamar yanda na shaida
da tafiyar don haka ya k'ara ban baki yana nunamin mahimmancin Abinda zaije yi
badan hakanba yace bazai barshi ya koma d'in ba, Nikam mirmishi kawai nai nace "Ai
ba komai Abbah, Allah ya kaimu lokacin kamar yaune zai dawo fatanmu Allah ya bada
sa'a ".

Sosai Abbah yaji dad'in maganar tawa yaita samin albarka.

Bayan na dawo part d'in mu naketa tunanin tafiyar tashi araina daga baya na
watsar naci gaba da abinda Ke gabana .
A cikin kwana kin na k'ara azama wajan kyautata masa kuma ina k'ok'arin kyautata
alak'a tsakanina dashi, duk da shima na lura a kwanakin ya d'an rage had'e giran da
yakeyi in yana zaune zai d'an sassauta fuskanshi ko in sweety ta shigo muna hira
yakan d'an jefa baki kad'an inma abin dariya mukai zai d'an murmusa, amma fa har
lokacin bai min zancen tafiyar ba haka Nima ban nuna mai na sani ba.

Ya rage saura kwana biyar tafiyan ranar lahadi Abbah yace ya kaini gida shima
ya gaisa da yaya na yai musu sallama, ai kuwa ina zaune bayan na gama duk ayyukana
nazo ina karyawa ya shigo yana kallona ya kalli agogo sannan ya k'ara dubana
yace " Ke ki gama duk abinda kike nan da 15 minutes zakije gidanku Ku gaisa,sannan
zan musu sallama kin san 5 day's ya rage in koma India ".

A nutse na dubeshi ido da ido ina kurban copy d'in dake hannu na na gyad'a Kai
tare da fad'in" Tom" kawai, Juyawa yai ya shige d'akinsa, ni kuwa yana shiga na
daka tsallen murna na kwashe kayan danai amfani dasu zuwa kitchen na wankesu, nan
da nan sannan na k'ara kintsawa don dama a shirye nake kayan jikina kawai na canja
don daga doguwar riga zuwa wani lafiyayyan less dinkin riga da zani na d'aura
d'an kwali na d'as nasa mayafi da jaka da takalmi duka kalan adon less d'in, bansa
turare ba sanin haramcin hakan sai dai humra me dad'in k'amshi dana shafa, lokacin
dana fito parlourn sha biyu dai dai na tsaya k'ofar d'akin nasa ina knocking daga
ciki naji yace "ki jirani ina zuwa"

Ina zaune kan kujera kusan minti uku sannan ya fito cikin shigarshi ta gado
wato k'ananan kaya kallo d'aya nai mai na kauda ido ina fad'a cikin raina "wai
mutumin da zaije gidan surukai ne yai wannan shigar shi koda yaushe bashi da shiga
sai wannan, amma insha Allah a sannu saina canja salon wannan shigar tashi don a
duniya ni ina son inga namiji da manyan kaya da Babbar riga hakan na
birgeni . . . . ."
"In kin gama kallon ko tunanin ki wuce muje " maganar shi ta dawo dani cikin
salona na basarwa na kauda ido tare da mik'ewa nai nai gaba ya biyoni a baya yana
kulle k'ofar ".

A compound d'in muka had'u da sweety nace mata gida zani tazo muje tana dariya
tace "um um sai wani zuwan in zakije zamu tare".
Marairaice murya nai nace " Haba don Allah kizo muje"
Rad'a tai min a kunne tana dariya "Ke wake bin miji da mata unguwa inje in katse
muku hanzari in hanaku soyewa a mota "
Dukan kafad'anta nai tare da hararanta na wuce na barta tanata min dariya.

Muna tafe cikin motan zama irin na kurame saida ya gaji ne ma ya kunna
wak'a yana bi tare da kad'a Kai, ni kuwa kaina na jingina jikin mirfin motan idona
a lumshe ina jin wani nishad'i da ban san kona mene ba, a haka danja ta tsaidamu
na bud'e idona naga me tallan chocolate yana mik'owa ko zamu siya,kallonsa nai ina
marairaice mirya nace "pls zan sai Abu".
Gyad'a min kai kurim yai, na sauke glass d'in ina cewa yaron ka bani kwali biyu
yana k'ok'arin mik'owa yace " K'ara mata kwali biyar da sauri na kalleshi nace
"bafa wani Abu zanyi dashi ba yara zan kaiwa, kwali biyar yai yawa 12 peaces ne a
kwali d'aya".
Kafad'a ya d'age yana fad'in in tai musu yawa Ke kyasha daga haka ya mik'awa
yaron kud'i yana karb'ar ledan da yake mik'omin kan cinyata yaja motan don
lokacin har an bada hannu.

Motan na tsayawa k'ofar gidanmu naji farin ciki ya lullub'eni na bud'e mirfin
cikin zumid'i na zan fice yace " Ke in kin shiga kice zan shigo mu gaisa".

Ina bud'e gate d'in naci karo da yaya na yana goge motarsa kasancewar weak end
baya fita,da sauri na k'arasa gabansa cikin farin ciki ina cewa "yaya"
Shima cikin farin cikin yace "Nahna Oyo yoooo" duka dariya mukasa na zube k'asa
ina gaisheshi ya amsa cikin fara'a yana tambaya ta ya gida yame gidan "Ai yaya tare
ma muke dashi yana waje ".
" OK to shiga gamu nan shigo wa dashi ".

Da sauri na k'arasa ciki da sallama ina kwalawa su Ashra kira ai kuwa da gudu
suka fito suna rungumeni nan Aunty ma ta fito da murnarta tana min sannu da zuwa,
bayan mun gaisa naji sallamar yaya sun shigo,Sai sannan nake ce mata "Aunty tare fa
muke dashi gasu nan shigowa da yaya". Da sauri ta tai d'aki don d'auko hijabin ta,
K'arasowa sukai parlourn ni kuwa inata faman wasa dasu Ashraf d'ina suna ban
labari,anan Aunty ta fito tana mai sannu da zuwa bayan ta zauna suka gaisa cikin
girmama juna ta mik'e tana fad'in " Bari a kawo ma ruwa ".

Mik'ewa shima yai yana " a'a wlh ki barshi tafiya ma zanyi".

Yaya yace "A haba Daddy ka zauna mana kasha ko D'an ruwan ne daga zuwa sai
tafiya".
Mirmishi yai yana mik'ewa Ashraf kud'i yace" ba komai yaya wani lokacin inna
dawo na sha".
Yaya yacewa Aunty " Tafiyar tashi ce fa ta taso wannan satin zai wuce ".

" Au Daddy tafiyar ce tazo,To Allah ya kiyaye hanya ya bada sa'a ".
Amsawa yake da "amin amin " ya fita yaya yabi bayan sa.
Bayan sun fita muka d'an fara hira da Aunty sai ga yayan ya shigo yana cewa
"jeki zai wuce "
Mik'ewa nai cikin jin kunya na fita, a bakin mota na sameshi yace " In anyi
sallar magriba a zanzo in d'auke ki "
"To Allah ya kiyaye saika dawo".
Juyawa yai ya shiga motan na shiga cikin gida.

Yinin ranar muna tare da Aunty tanata k'ara koyar dani dabarun zaman aure da
yanda ake kula da miji .

Bayan sallar la'asar na tafi gidan yaya Haroon muka rungume juna da Aunty Amrah
wadda naga cikinta harya d'an fito, itama dai k'ara min darasi take kan dai rayuwar
sai gab da magriba na koma gida na koma gida, ina salla naci abinci banfi minti
biyar da gamawa ba ya kirani a waya in fito yazo,anan ma saida yaya ya fita suka
k'ara yin sallama yana mai fatan alkairi muka wuce.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣1⃣
0⃣3⃣1⃣ 0⃣3⃣1⃣

A hanya muka tsaya yai take away, sannan muka wuce gida, muna shiga ana sallar
isha'i don haka kai tsaye toilet na wuce nai wanka sannan na d'auro alwala nai
salla,ina kan sallayan ya lek'o d'akin karo na farko kenan daya tab'a zuwa " In
kin idar ki Samar min abinda zanci don wannan abincin dana siya yai yaji da yawa"

Kafin ya k'arasa ma na mike ina nade abin sallar na saka riga y'ar k'arama
iya gwiwata na fice " a zaune na hangoshi a k'aramin parlourn yana kallon ball,don
haka da azama na shige kitchen d'in na fara k'ok'arin dafa mai ko jelof Na taliya
ne.

Cikin 30 minutes na dafa mishi taliyan tasha kifi sai k'amshi take,lokacin
danake zuba mai kuwa har yawunsa ya tsinke don shi akwai son dad'i, ina zaune
gefenshi harya gama na tashi na had'a kayan ina cemai "saida safe " d'agowa yai
ya kalleni tsaf sannan yace "OK"

Ni kuwa ina shiga d'aki handouts na d'auko nai karatuna Sama Sama don ina jin
bacci, nan da nan kuwa bacci ya d'auke ni.

Yauma kamar kullum da asuba na tashi nai duk abinda zanyi na had'a break fast
sannan nai wanka,ina shiga d'akinsa naga ya shiga wanka kafin ya fito na gama
gyaran d'akin bayan ya fito na gaisheshi ya amsa na wuce toilet d'in na wanke.

A dining na sameshi muka karya,amma yau sai naga baici abincin da yawa ba, haka
ma muna tafiya a mota naga sai d'an yatsina yake kamar bai jin dad'i, munje zai
saukeni naga ya d'an matse cikin sa yana rufe ido ,tsayawa nai ina kallon sa yana
bud'e ido muka had'a ido a sanyaye nace " baka da lafiya ne"
Girgiza min Kai yai alamar a'a nai Jim sannan na fice ina cemai "na gode "

Tunda muka fito a lecture nake kiransa ganin ban ganshi inda ya saba jirana ba
in yazo, kusan kira biyar sannan ya d'aga wani iri naji muryansa " ki d'an jira na
turo driver yazo ya daukeki".
Bayan ya kashe wayan saiga driver ya duk jikina a mace na shiga motan ina
tunanin baida lfy daman naga alama tun safe amma yace ba komai .

Koda mukaje gida da azama na shiga parlourn a kwance na sameshi kan rugs yanata
juyi dafe da k'irjinsa ban san sanda na ruk'o shi ba ina fad'in " meya sameka don
Allah sannu ".
Damk'e hannuna yai yana cemin " Bani ruwa insha pls"
Da sauri na tashi na cire hijab d'ina na d'auko mai ruwan ina zuba mai a cup na
d'aga kansa ina bashi a baki, saida ya shanye na dire cup d'in ina cewa " bari in
kira sweety muje asibiti ko " girgiza kai yai yace cikin muryar Wahala "karki kira
min kowa nasha magani zuwa anjima zai daina "
Haka mukaita zama ciwo baya baya sai gaba don rik'e k'irjinsa yai yana juyi
cikin wahla yake fad'in " my god my god help me "
Ni kuwa sai salati nake ina mai sannu can naji ya fara kakarin amai da sauri
na tafi d'aki na d'auko varf nasa mai nan yaita aman bayan ya gama na d'auko mai
ruwa ya kuskure baki sannan naje na zubar,sanda na dawo naga ya fara samun relief
don haka na zauna gefansa inata tunanin kodai in kira sweety amma ina tsoran Kar
yace na tara mai jama'a, bacci ne ya fara daukansa Sama Sama na shiga d'aki don in
watsa ruwa sabida zafin da akeyi sosai, da sauri sauri nai wankan na fito Nasa riga
da skirt na Atamfa ina k'ok'arin fitowa naji kakarinsa da gudu na k'arasa na
sameshi ya damk'e ciki yana wani kakkafewa salati nasa na fice da gudu zuwa part
dinsu sweety, ina shiga na sami Aunty murja a kitchen tana ganina haka ta fara
tambaya ta lfy, cikin tashin hankali nace mata "shine baida lafiya Aunty "
Salati ta fara tana biyo bayana,sanda muka shiga harya fice hankalinsa kamar ya
suma juyawa tai da gudu ta kira ma'aikatan gidan maza da driver tace d'auko hijab
d'inki mu tafi asibiti cikin kidima na d'auko suka d'aga shi zuwa mota a lokacin ma
Aunty ta d'auko mayafinta ta fito"

Asibitin da suke ganin likita mukaje da gaggawa doctor sukai kansa don sun
san Case d'insa, anan Aunty Murjah ta kira Abbah ta fad'a mai ta kira sweety don
itama tana gidan ummu sulaim.
Zuwa lokacin idona yak'i tsaida hawaye wani Irin tausayinshi nakeyi ganin yanda
yake jijjiga gadon da yake kwance sabida bala'in ciwon ciki, allura akai mai amma
kamar ba'ayi ba,
Hannayena na cikin nasa inata mai addu'a ina tofa mai, a lokacin Abbah ya shigo
ya shigo da sauri yana fad'in "Daddy sannu sannu kaji a garin yaya me kaci ciwonka
ya tashi haka"
A lokacin nema su sweety suka shigo tare da ummu sulaim suna kar'asowa bakin
gadon duk hankalinsu a tashe, ganin Irin hawayen dake gudu a idona yasa sweety
dafani tana cewa "ki daina kuka Nahna zuwa anjima zai dawo normal, ulcer d'in sace
ta tashi daman ciwonsa ne duk sanda yaci yaji ko yayane yana tashi ".

Cikin shashshek'a nace " Take away yai jiya da zamu dawo gida,kuma yacemin da
yaji daman ".
Abbah shima cayai" kiyi shuru haka ki daina kukan kinji"

A lokacin ya k'ara wani juyi tare da k'ara damk'o hannuna yana Wani Irin
kakari, kowa addu'a yake mai cikin tausayawa, doctor d'in ne ya shigo da alluran
bacci yace kowa ya fita amma ganin irin rik'on da yai min yasa yace ni in tsaya,
alluran akai mai wanda baifi minti biyar ba bacci me nauyi ya d'auke shi,dukda haka
hannuna na cikin nasa,sai a sannan na sami nutsuwa naja kujera bakin gadon na
zauna,lokacin har anyi sallar magriba,kasancewar period d'ina yayi ban tashi nai
sallar ba ni, su Abbah suka k'ara shigo wa yace "yayi bacci ko " nace "eh Abbah"
Duk sannan su sweety suka shigo tace "Doctor yace sai zuwa safiya za'a
sallamemu insha Allah yana farkawa zai dawo normal".

Muna nan zaune aka kawo Abinci daga gida akai akai naci nace " a'a sai dai
zuwa anjima"

Sai k'arfe goma sukai shirin tafiya ummu sulaim ma Mijin ta yazo d'aukanta,Abbah
yace Sai in zauna gun mijina,ga d'aya nan daga ma'aikatan gidan namiji za'a barshi
ya kwana a receptions kozan buk'aci wani abu sannan za'a je a kawo mana duk abinda
zamu buk'ata,
Sweety naiwa alaman tazo nai mata rad'a in zata had'o mana kaya ta d'auko min
pants d'ina da pard tace to ba damuwa.

Bayan fitansu doctor d'in ya k'ara shigowa yace " in rage mai rigan dake jikinsa
yaga yanata gumi sannan yace inya farka in bashi malt da d'an abinci kad'an" sanna
ya d'aura mai drip ya fice .

Driver ne Ya dawo ya kawo min jaka da duk abinda zamu buk'ata,toilet naje na
gyara jikina.
Bayan na gama duk abinda zanyi na dawo bakin gadon na zauna ina k'arewa
fuskanshi kallo, kana kallonshi zaka gano tsantsan wahalar da yake ciki,wajan nakai
k'arfe d'aya na dare zaune sannan bacci ya d'aukeni.

Juyi yai cikin wahala yana yatsina fuska yaji hannunsa d'aure da robar k'arin
ruwa, bin robar yai da kallo na y'an sakanni sannan yai k'asa da idonsa,kallo ya
bita dashi ganin yanda take bacci a takure kan kujera bakin gadon, ga hawaye
bushashshe duk a gefen idonta,lumshe ido yai yana tunanin yanda ta rud'e taketa
kuka dataga yanda jikinsa ya tsananta, yana a haka yanata tunani har bacci ya k'ara
d'aukanshi.

Wajan k'arfe uku na farka sannan naga ruwan saura kad'an don haka na zauna ina
jira ya k'are,baifi 10 minutes ba ya k'are na zare mai robar ,bud'e idonsa yai
cikin yanayin bacci yana kallona nace mai "sannu ya jikin naka"
Lumshe ido yai yana amsawa cikin wahalalliyar murya,nace " in had'a na abinci"
Girgiza kai yai alamar a'a nace "ka daure ko maltina kasha doctor yace a baka
wani Abu kaci "
Rufe idonsa yai muryanshi can k'asa yace" bari sai anjima"
Daga haka bai k'ara cewa komai ba,ina tsaye kansa kusan minti goma naji yana
sauke numfashi alamar ya koma bacci,don haka na koma Nima na zauna anjima kad'an
bacci ya k'ara d'aukana.

Ban k'ara farkawa ba sai asuba ina tashi toilet d'in na shige nai wanka na gyara
jikina bayan na fito nasa kayana da Hijab d'ina tunda bana salla sai azkar nai,
inata zaune ina kallonsa naga bai ko motsawa ba sai wajan k'arfe bakwai saura
sannan ya farka matsawa kusa dashi nai ina mai sannu sannan nace "bari in had'a ma
ruwan wanka ko"
D'aga kai yayi, na shige toilet d'in kasancewar da heater a ciki na sirka mai
ruwa me zafi,na fito ina fad'a mai na had'a, mik'ewa yai yana rik'e da k'arfen
gadon ya daddafa ya shige toilet d'in.
Bayan ya fito na ciro mai jallabiyar da aka kawo mai,yasa na k'ara mai
sannu,maltina na juye mai a cup na mik'a mai, ya amsa cikin sanyin jiki ya kafa
kai yana sha kad'an kad'an,a sannan sweety ta k'wank'wansa k'ofar naje na bud'e
mata muka sakarwa juna murmushi na matsa ta shigo gaisawa mukai tana tambayar ne
jiki nace "da sauk'i " zama tai kan gadon kusa dashi tana tambayanshi ya jiki " ya
amsa cikin d'an sakin fuska ,kallona tai tace "Aunty na muna ta kiran wayoyinku
duk ba'a d'aga ba"
D'an bud'e ido nai nace "Ai Duk suna gida wayoyin "
"OK to ga abinci nan Abbah yace kuci sosai kafin yazo ,wanka kawai zayyi yanzu
zaizo".

Tashi nai na d'auki flat na zuba mai chiefs nasa spoon,na kawo mai ,karb'a yai
ya fara ci naga ya d'ago kai yana kallona can naji yace " Ke bazakici ba"
"Um sai anjima banson karyawa da safe haka "
Bai k'ara magana ba sai sweety ce tace "amma ai Kinga kin kwana bakici abinci ba
na tabbata yanda muka barki jiya bikici komai ba"
Kauda zancen nai ta hanyar cewa ta bani aron phone d'inta ,mik'omin tai nan nasa
number d'in yaya na bugu d'aya ya d'auka nake fad'a mai asibiti muka kwana Daddy
baida lfy'
Jajantawa yai sannan yace inya fito office anjima zai shigo ya dubashi .
Bayan na kashe naga ya zuba min ido kamar zaice wani Abu kuma naji yai shiru,
Muna zaune a haka sweety na d'an janmu da hira kad'an kad'an, a sannan Abbah ya
shigo tare da Aunty murjah da sauri na tashi kan kujerar da nake zaune ina mai
sannu da zuwa, amsawa yake tare da fad'in "a'a Daddy na jiki yai sauk'i
Alhamdulillah,sannu kaji " shima cikin y'ar fara'a ya amsa suka gaisa da Aunty
murjah ma,tsugunnawa nai na gaishesu cikin ladabi suka amsa suna tambayata me
jiki na amsa da sauk'i, A sannan doctor ya k'ara shigowa ya dubashi yace za'a
k'ara mai allura wajan k'arfe goma sai a bamu sallama tunda ya dawo normal.
Bayan fitan doctor Daddy ya gyara kwanciya yana cewa "Abbah yarinyar nan fa
bataci abinci ba na mata magana wai ba yanzu ba"
Juyowa Abbah yai yana fad'in " Haba Khadeejah ya zaki zauna da yunwa haka Kinga
jiyama fa k'inci kikai kema Kar ulcer d'in ta kamaki fa,Sweety zuba mata taci
kinji"
"OK Abbah bari ma in zuba mana muci tare don Nima banyi break d'inb"

Nidai cakula kawai nake don duk kunyar Abbah ta hanani sakewa duk yanda yake
k'ok'arin Jana a jiki amma na kasa sakewa in daina jin kunyarsa,kula da hakan da
yai yasa shi fita waje nan na samu na d'anci da yawa na mik'e.

Anjima kad'an suka shigo tare da yaya na,


Bayan sun gaisa da me jikin yamai sannu sannan Nima na matsa kusa dashi ina
gaisheshi rik'o hannuna yai yana tambayata me jikin na amsa da sauk'i, ya d'an
jima a tsaye yai sallama damu ya wuce office,
K'arfe goma doctor yazo ya k'ara mai allura tare da bashi magunguna kuma ya
k'ara gargad'insa da cin yaji komai k'ank'antarsa,don ulcer d'insa bata son yaji ko
kad'an,sannan ya sallamemu, sweety taja mu da Aunty murjah zuwa gida Abbah kuma
ya wuce kasuwa.

Kwanaki biyun da yai jinya duka cikin kulawata yake sosai nake bashi kulawa,shi
kuma ma yanda na lura har wani k'ara shagwab'emin yake kodan yaga hankalina ya
tashi da ciwon nashi ne oho, abin yana baka'in d'auremin kai yanda nake ganin sauyi
tare dashi in yaimin wani abun har tunanin nake araina kodai UK ya fara sona ne
kamar yanda na yarda tabbas zuciyata ta fara kamuwa da son sa sabida lokaci lokaci
ina zama inyi tunaninsa har inyi mirmishi,hak'ik'a addu'ar da nakeyi koda yaushe
cikin zamana dashi ta fad'a akaina tunda gashi zuciyata ta fara kamuwa da
k'aunarsa,duk da shima kamar canji ya fara samuwa cikin kwana uku kacal,
Yau Alhamis in Allah ya kaimu gobe juma'a k'arfe tara na dare jirginsu zai
tashi,yau d'in da wuri yai shirin fita don yaji k'arfin jikinsa sosai yana son
yaje yaiwa y'an uwa sallama,ina tsaye a dining ina serving d'insa na zuba mai kunun
gyad'a na d'an juyo na kalleshi naga yana kallona,k'asa nai da murya nace "in
k'ara maka koya isa"
Kallona yai ido cikin ido yace "me kika maidani ne,wannan uban kunun kuma kina
maganar ki k'ara min"
D'an mirmishi nai kawai na bud'e gwangwanin madara na zuba ina juyamai duk
abunda nake idonsa na kaina, harna juya na bud'e flask na zuba mai lafiyayyan
k'osai dayasha albasa,bayan yaja ya fara ci naga ya lumshe ido alaman yamai dad'i
d'an mirmishi nai na d'aga wayana na kira Hafsa a waya ina tambayarta ya lecture,
dariya tai tace "ai Ke ango ya b'oyeki,ya jikin nasa"
"Hhhmmm da sauk'i me jiki, kinsan gobe in Allah ya kaimu zai tafi to ina
d'an . . . ."
Rufe bakina nai sanda na tuna a inda nake maganar Kar nai sub'utul kalam, Aunty
ummy wata y'ar department d'inmu matar aure ce da y'ay'anta biyu muna shiri da ita
sosai,ita ta amshi wayar tana cewa "Sis yi zamanki ki kula da mijinki kinji duk
abinda akai in kin dawo zamu nuna miki ki zauna ki nemi lada"
y'ar dariya nai nace "To Maman boy zan kula sosai "
"Yawwa sis ki dage fa kinji "
Dariya kawai nai na kashe wayan, sweety na k'ara kira tana d'agawa nace "nayi
mutuminki kunun gyad'a gashi kina school"
"Don Allah da gaske Aunty na,don Allah ki samin a flask in na dawo zan sha"
"OK zan ajiyemiki har ki dawo yana jiranki "
Bayan na kashe wayan naga yana turomin cup d'in gabana "kina neman kai da
kununa to ban yarda ba ki k'aramin one cup kuma ki barmin sauran cikin flask d'in
in na dawo zansha "
Dariya nake gintsewa na yanda yake cewa da cup d'aya ya isheshi amma gashi yanzu
yana neman k'ari "
Saida ya kuma shan cup guda sannan ya mik'e yana fad'in "zanje inyi sallama da
y'an uwa kafin in dawo ki k'ara yimin Irin d'an waken jiya "
Mik'ewa Nima nai ina cewa "To a dawo lfy,insha Allah kafin ka dawo an maka"
Juyawa yai ya fice,ni kuwa daman aiki ne dani sosai,
Don haka na shige kitchen na fara had'a snacks kala kala don nai mai tsaraban
tafiya. . . . .. . ..

https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣2⃣
0⃣3⃣2⃣ 0⃣3⃣2⃣

Sosai na zage naita aikina,kasancewar akwai isassun na'urori don haka cikin sauk'i
nai komai na gama,d'an waken ne ban mishi ba sai bayan la'asar sosai don nasan zai
iya kai magriba bai dawo ba don karya huce, hai wanka na tsaf na shirya cikin riga
da wando sak'ar Pakistan na gyara kaina na jera mai ribbons k'anana masu kyau ban
d'aura d'an kwali ba,nasa d'an kunne da sark'a suma na k'asar Pakistan d'in,sannan
na bad'e jikina da sanyayyan turare,nan da nan na fito d'as dani kamar y'ar k'asar,
k'ara gyara gidan nai sosai na turarashi da turare,ina zaune a k'aramin parlour ina
jiran akira sallar magriba Aunty Hafsa ta kirani tace min da k'aninta nan Isma'il
ta bashi sak'ona ya kawo min yace yazo yana k'ofar gate in aiko biyeni 'amin,nai
mata godiya tare da kashe wayan, Hijab d'ina nasa na fita na sami d'aya cikin
ma'aikatan gidan na fad'a mishi akwai bak'o a baking gate don Allah su amso min
sak'o a gunsa, ina nan tsaye naga an bud'e gate d'in gidan mota ta shigo, ta cikin
glass na ganshi muka had'a ido, bayan yai parking na tsinci kaina da k'arasawa
gefen mirfin motar ina bud'ewa tare damai sannu da zuwa, D'an sakin fuskarsa yai
yana amsawa a sannan ne wanda na aika ya kawomin watan k'atuwar leda na karb'a ina
mai godiya, bin ledar yai da kallo bayan ya fito daga cikin motar,gaba nai shi
Kuma yana biyeni har zuwa part d'in namu,ina Shiga na ajiye ledar ina cire hijab
d'in dake jikina, nai baking standard fridge dake palourn na d'auko mishi robar
ruwa me sanyi tare da glass cup,tsugunnawa nai gaban kujerar da yake na zuba mai
ruwan ina mik'a mai,yana karb'a yace "tnx"
Bayan ya shanye ya mik'omin cup d'in tare da mik'ewa ya shige d'akinsa, binsa
nai d'akin, ya juyo yana kallona ganin na biyoshi ban damu ba na shige toilet na
had'a mai ruwan wanka da turaruka masu k'amshi na wanka, na fito ina cemai "ga
ruwan wanka na had'a ma"

"OK tnx" ya fad'i yana k'ok'arin cire kayansa.

Bayan fitowansa daga wanka ya zauna bakin gado yana tunani a ransa shin wai
yarinyar nan me take nufi da wannan hidimar wai duk mata daman aikinsu kenan a
gidan miji, kai haba gaskiya bazai zama haka ba,kawai dai maybe itace me hidimar,ya
dad'e zaune yana tunanin abubuwa masu yawa game da ita,ya gano wasu qualities tare
da ita tanada kirki da girmama babba,tanada tausayi da k'ok'rin faranta ran wanda
take tare dashi koda hakan zai bak'anta mata,ya dad'e zaune yana tunanin ganin
hakan bazai masa ba yasa ya tashi ya wuce toilet d'in.

Ni kuwa na gama shirya table tsaf ina jiran fitowansa,inata zaune ina jiransa
har aka kira salla na wuce d'aki don gabatar da sallah.

Ina tsaye bakin mirror ina fesa turare ya turo kofan yana fad'in "Azo a bani
abinci ina jin yunwa sosai"

K'asa k'asa nai da idona ina dubansa nace "OK ina zuwa kad'an "

Ya juya ya fita yana tunanin aransa,wasa wasa fa yarinyar nan ta iya dressing
ba tun yanzu ba tun had'uwarsu ta farko ya kula da iya adonta don dai kawai tana
b'oyewa ne amma yanzu daya Ke zaune da ita yake ganinsa a zahiri,

Bayan na gama zuba mai d'an waken na zuba maihad'ad'd'an kunun ayan danayi
wanda yasha madaran ruwa sosai da dabino da kwakwa,
Kurb'a d'aya yaiwa kunun ayan ya kad'a kai cikin gamsuwa da d'and'anon da yayi
masa, bayan ya gama cinye na gabansa kawai naga yaja wanda Ke fagana yaci gaba
daci ,d'agowa nai na kalleshi amma shi ko ajikinsa,ganin haka yasa na tsiyayi kunun
ayan inasha tare da tunanin shi kullum in ina zuba mai abinci sai yace ya isa, kuma
inya gama sai ya k'ara, daman ni d'an wake ba cimata bace don wanda ba zuba dinma
ina fara ci ya gundureni sai gashi shi ya d'auke yana sank'amewa, banda ma shi da
abinsa d'an wake ai bai dace da abincin dare ba,ina wannan tunanin naji
maganansa" ki shirya in anyi sallar isha'i zamu je unguwa" daga haka ya mik'e,
Ni kuwa a raina nake tunanin To ina kuma zamuje,Hhhmmm lalle UK ya fara sauk'i.

Kwalliya na canja bayan nai sallar isha na shirya cikin doguwar riga y'ar k'asar
dubai wanda k'irjinta zuwa cinya yake cike taf da adon stones masu d'aukan ido,
ruwan powder ce nai rolling kaina da Vail fari kalan stones d'in rigar, nasa
takalmi da fari da pors fara,ina fitowa parlourn shima yana fitowa daga d'akin
sanye da t-shet blue a jikinsa da trouser baki k'afansa sanye da takalma sau ciki
bak'ak'e, kallo d'aya nai mai na kauda kai, gaba yai tare damin nuni da hannu
alamar muje , saida na kulle ko ina sannan na biyo bayansa a lokacin har yaiwa
motan key, bud'e gaban nai na shige motan da sallama d'auke a bakina kamar nutse
d'abi'a ta take kullum zan shiga motan tasa sai nai mai sallama wata rana ya
amsa wata rana ya fuske,

Mun hau titi sosai ya kunna music yana ji tare da kai ba tare daya tanka ba,ni
kuwa idona naga titi ina d'an kalle kalle na, gani nai munyi parking motar bakin
wani zazzafan Stor bayan ya gyara tsayuwan motan muka jera muna takawa a
nutse
Cikin store d'in muka shiga kai tsaye yaja kwandon sa kaya ya turo gabana, muna
tafe yana zab'ar abubuwa yana sawa ciki ,abunda ya d'auremin kai yanda yake zab'ar
abubuwan mata kama daga turaruka,pard, powder sabulai da sauran abubuwan buk'atar
mata, daga nan mukai b'angaren abubuwan ciye ciye da sannan kayan amfanin gida
cika bayan mota mukai da kaya wanda duk kusan nawa ne shi abunda ya d'auka kad'an
ne, duka shi ya zab'i komai don yace in d'auki abunda nakeso bace um um dan haka
yaita jidar min da kansa, daga nan mukai wajan shan ice cream muna zaune kan kijeru
ya bada akai mana oder d'in kayan shaye Shaye,muna zaune nan bame cewa da wani
uffan hankalinsa naga wayansa wanda ni kuma nake wasa da d'an cokalin shan ice
cream d'in,sai dai lokaci zuwa lokaci yakan d'ago mu had'a ido, mun D'an dad'e
yace in tashi mu tafi.

Sannu a hankali muke takowa zamu fita a gun wani Alhaji ya shigo yana waya
hankalinsa kuma naga wani b'angaren wanda hakan yasa bai kula ba ya bangajeni
abunda ya haddasa min yin baya zan fad'i da sauri ya tallafoni zuwa jikinsa yana
min sannu shima mutumin tsayawa yai yana min sannu tare da ban hak'uri,wata Irin
gigitacciyar tsawa mukaji ya karad'e gun,ya gade rai matuk'a yana hararan mutumin
"kai wane Irin bagidajen mutum ne Mara lissafi kawai kazo ka bangaje min mata ta
kamar baka gani haba wannan ai sakarcine mutttssss"
Binsa mutumin yai da kallo yana jin wani b'acin rai shi za'a fad'awa wannan
kalmomin ma don haka cikin fishi yake fad'in "Kai kasan ni waye kake fad'amin
wannan Kalmar ni kake cewa sakarai lalle zaka gane kuranka,tunda kai jaki ne ban
Sani ba na bige ta kuma na bata hak'uri shine zaka zageni ,har meye jikin matar
taka zaka zageni kanta in ta shiga cikin mata ma baza' a ganeta ba.. . .

Kau kakeji ya d'auke mutumin da mari yana huci kafin me shima mutumin ya rama
wani wawan naushi ya kaiwa mutumin a baki nan da nan jini ya b'ata mutumin wanda
zuwa lokacin mutane sun cika gun suna bada hak'uri, ni kuwa jikina banda rawa ba
abunda yake na rik'e hannayensa ina " don Allah ka barshi kazo mu tafi gida" ganin
mutumin ya tunkaromu da k'arfinsa yana kwacewa daga ruk'on da mutune suke mai
ruk'umk'umeshi nai ina kuka don shima k'ara tunkarar mutumin yake yana danna mai
zagi.

Security d'in wajan ne suka k'araso suna tambayar ba'asi wani da akai komai a
kan idonsa yake larabta musu nan dai sukaita bawa kowa hak'uri sukaja mutumin suka
fita dashi muma muka fita zuwa gun motar mu.
Tunda muka d'au hanya yake sauke ajiyar zuciya me cike da tsantsar b'acin
rai, ni kuwa sai matse D'an guntun hawayena nake yi, a haka muka isa gidan baiko
bi takan kayan ba ya fice ya barni a motar, taimakon ma'aikatan gidan na naima
sukaita kwaso min kayan zuwa parlour bayan sun gama nai musu godiya tare da rufe
k'ofan nai cikin d'akina, zama nai bakin gado ina tunanin abunda ya faru lalle
rashin hak'urin UK ya b'aci jibi yanda lokaci guda ya koma kamar wani horo
jijiyoyin kansa Duk suka tashi, idonsa yai jajur kamar gauta,

To wai ma duk akaina ya shiga wannan yanayin, gaskiya ya kamata inje in


bashi hak'uri don yanda yake furzar da iska bana tunanin zaima iya yin bacci yau
d'in nan gaskiya gara inje in bashi kahuri tunda dai Duk akaina ne hakan ta daru,
daga wannan tunanin na mik'e zuwa toilet don shirin bacci .

Shi kuwa a can d'akinsa yana kwance kan gado dafe da kansa ya sakko da
k'afafunsa k'asan gadon don ko takalmansa bai cire ba,ya dad'e ba'a b'ata masa rai
Irin haka ba an zageshi an wulak'antashi gaban mutane, yayi mari an rama,hannu
yasa ya shafo began fuskarsa yana tab'o inda aka mareshi d'in, wai duk akan wannan
yarinyar aka mai wannan wulak'ancin shi dama ya Sani bai fita da ita ba,kodake
gaskiya dole ya kare hakkinta tunda dai sunanta matarsa. . . . .

A hankali na turo k'ofar cikin shigar riga da wando na Jean's kaiba ba


d'an kwali na gyara gashina tsaf sai d'aukan ido yake ,d'an bud'e ido yai ya kalli
ni ya maida ya rufe a ransa yana jin wani Abu na mintsininshi duk da shi bai fiye
yawon sha'awa ba kuma fidda tairaicin mace bai sashi jin wani Abu amma bai san me
yasa ba cikin kwana biyun nan yarinyar nan take fuzgarshi kodan ita d'in halalinsa
ce . .
A hankali na k'araso bakin gadon na tsugunna ina zare mai takalman dake k'afarsa
nakaisu ma'ajiyarsu na dawo tare da zama gefanshi, na k'ara sanyaya muryata na fara
magana " Don Allah kayi hak'uri kaji naga ranka ya b'aci da yawa kuma duk nice
sabadi kayi kahuri kaji"

Shiru yai bai magana ba kuma bai bud'e idon ba, na k'ara narkar da muryata kamar
zanyi kuka" in ka tafi kana cikin fishi da b'acin rai hak'ik'a banci nasara ba,
Kaga mutumin nan maybe shi yama manta amma Kai ya barka cikin b'acin rai,zaka bar
gida gobe kamata yai ace yanzu kana cikin nishad'i da tunanin rabuwa da gida ba
tunanin wancan banzan mutumin ba,don Allah ka fiddashi cikin ranka kaji"
Bud'e idon yai a hankali ya furta "karki damu "

"To yanzu me kake buk'ata in kawo ma"

"Ba wani Abu jeki kwanta"

Shiru nai kamar bazan tashi ba can dai na mik'e har nakai bakin kof'a naji yace
"an shigo da kayan nan kuwa ?"

Kaina na gyad'a alamar eh


" OK ki ciromin duk abinda yake nawa ciki "

Fita nai na dudduba kayan ba wasu abubuwa bane masu yawa nashin , dana koma
zaune na sameshi yana b'alle rigan jikinshi tsugunnawa nai ina mik'a mai ya amsa
ya aje bakin gadon yana fad'in "ki d'an had'amin ruwan wanka pls"
"OK "

Bayan na had'a mai ya shiga ni kuma na koma kitchen na d'ebo abubuwan dana
shirya mai, d'anbun nama ne da cake, dunout,meat pai ,coconut biscuit
Yana fitowa yabi kayan da kallo sannan ya wuce gaban mirror ya goge jikinsa
tare da shafa mai da turare yazo ya zira rigan bacci,duka kaina na k'asa ina wasa
da hannuwana, zuwa yai ya zauna gefan gadon baicemin komai ya fara duba wayansa,
k'oka'rtawa nai nace "um daman snacks ne na maka ko zaka tafi dasu sabida shan tea
".

Sosai ya kalleni yana mamakin to me zaiyi da wad'an nan abubuwan acan kuma shida
yake odar d'in abinci bashi da wata matsalan abinci ko abinsha, amma wani saahin
na zuciyarshi yaji dad'i don koba komai ta nuna kulawarta gareshi kuma yana son a
nuna an damu dashi, kawai sai ya tsinci kansa dayin murmushi yace " Tnx sannu da
k'ok'ari"

Nima mirmishin nai nace " ba komai hak'k'inane "


Cikin ransa yace wai duk wannan ma cikin hidamar aure ne,lalle mata sunga ta
Kansu,amma a zahiri sai yace "ki had'aminsu cikin wannan k'aramin truly back d'in
tunda duk anyi raffing Nasu"

Tashi nai na d'auko jakan nasa ledan ko wanne na jera bayan na gama na d'ora
kan jerin jakunkunan dayai parking a gefe, sannan na juyo ina cemai "To saida safe
in Allah ya kaimu"
"Tnx good night"

Bayan fita na ya dad'e za'une yana nazarin da tunanin d'abiun na.

Haka Nima a can d'akina bayan nasa kayan bacci kawai juyi nai tayi a gadon ina
jin farin cikin da ban san dalili ba kuma ina jin daman mu kasance tare har wayewar
gari, gaskiya zuciyata ta fara zurfi cikin soyayyar mijina wanda Ke zaune dani a
dole kuma don biyayyar mahaifinsa,har yanzu bai d'aukeni matarsa ba ma balle ya
fara sona cikin ransa . . wani mirmishi ne ya sub'icemin dana tuno kalmarshi ta
d'azu "kai wane Irin bagidajen mutum ne Mara lissafi kawai kazo ka bangajemin mata
ta "

Tsintar kaina nai da sakin wata y'ar k'arar murna tare da rungume filo ina
jin araina lalle mijina ya fara sona kamar yanda Allah ya fara jarrabata da
k'aunarsa cikin y'an kwanaki, juyi kawai nake kan gadon ina hasashshen duk randa
Allah ya tabbatar da soyayya tsakaninmu zanyi yak'i da wasu d'abiunsa masu yawa
wanda basa cikin d'abiar cikakkan musulmi lalle zan dage da addu'a Allah ya sanya
soyayyta cikin ziciyar mijina tunda dai yanzu shine majinginata don haka zanyi
adduar samun farin ciki cikin rayuwarmu.

*Amin* *uzuri* *amin* *afuwa* *ina* *busy* *nayi* *bikin* *babbar* *k'awa* ,
*Aminya* *ina* *matse* *gajiya* *kwana* *biyu* , *muna* *Neman* *addu'arku* *na*
*Neman* *alkairi* *da* *zaman* *lfy* *ckn* *auransu* *sa* *samun* *zuri'a*
*d'ayyiba* .👏👏👏

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣3⃣
0⃣3⃣3⃣ 0⃣3⃣3⃣

Bayan sallar asuba nai azkar ina zaune kan sallaya ina addu'a na maida hankalina
sosai ga rok'on ubangiji na ya tsaremin mijina daga fitinar dukkan wata mace Allah
ya tsaremin mutuncinsa da addininsa Allah ya bashi sa'ar wannan tafiya,na d'au
tsawon lokaci ina addu'oi na Shafa tare da tashi na fita kitchen don nema mana
abun break fast, k'osai nai mai kwai tare da kunu sannan nai farfesun kayan kan
sa, wanka nai d'an gaske cikin riga da siket English Wear masu jikin roba inda
rigan take da bud'ad'd'e har k'irjina na iya fitowa sai skate d'in shima yayi
tytn nawa sosai,wata hula na saka wanda gabanta yake kamar ribbon duk ansa stones
kalan kayan itama red color na wadata jikina sosai da turaren humra ina fitowa
parlourn na sameshi tsaye yana waya ya juya baya yana kallon k'ofa, takuna ne yasa
ya juyo ya dubeni a sannan kuma ya kashe wayan tare damin wani kallo da bazance ga
fassararsa ba,d'an duk'awa nai ina fad'in "barka da safiya "
Saida ya zauna kan kujeran sannan ya amsamin da cewa "kin tashi lfy"
"Lfy qlau Alhamdulillah"
Na amsa ina nufar table don had'amai abinci, biyo bayana yai ya zauna yana cemin
'ki zubamin sosai don yau da yunwa na tashi"
"Um hmmm " Nace ina k'ara zuba mai ,
Bayan na gama had'a mai komai na koma na zauna ina kallon shirin da akeyi a
tashar m.b.c 3 daga inda nake ina iya kallon dai TV d'in tana saitin dining area
d'in, bayan kamar 20 minutes naga ya mik'e yana cewa "bari naje na dawo ina zuwa "
"To a dawo lfy Allah ya kiyaye ganga"
"A'a ai bama nisa zanyi ba zanje gun Abba ne"

Mirmishi nai araina ina cewa wato inba nisa za'ai ba ba'a addu'a kenan
hhmmmm , rakashi nai har bakin k'ofa bayan ya fita na rufe k'ofan tare da wucewa
d'akinsa na gyara maishi tsaf ina tunani araina shike nan yau me d'akin bazai kwana
ciki ba sai wata nahiyar kuma nan da nan naji wata irin kewansa ta kamani tun
kafin ya tafi d'inma, had'a dukkan unders nashi nai na wanke su tas tare da
turare d'akin da turaren wuta d'an mai duguri, ina shigowa d'akina naji ringing
wayana kafin na d'auka ma ta katse dubawa nai naga 3 miss call a ciki a sannan wani
kiran ya shigo na d'aga da sallama cikin k'ara sanyaya muryata "Ina kika shiga
inata kira shiru"
"Ayya kayi hak'uri ina gyaran d'akinka ne wayan kuma tana bedroom dina "
"OK kizo Abba na kiranki"
"Tom ganinan "

Hijab na d'auka babba nasaka har k'asa me hannu na rufo part d'in,

Shi kuwa bayan shiganshi gun Abba bayan sun gaisa Abban Ke k'ara tambayarsa
ya shirin tafiya y'ar dariya yai yace " Abba shiri kam an gama komai"
Yace "jiya da dare naso in ganka kuma Salis yacemin kun fita "
"Eh mun d'anje store ne nai mata d'an siyayya kuma bamu shigo da wuri ba"

Mirmishi yai cike dajin dad'in ganin sauyi cikin rayuwar tasu,kana ya nisa
yace "Tom daman na kiraka ne don inji me kake buk'ata kuma in baka kud'i ka zubawa
ita Khadijan a account nata wanda dai zata jima tana amfani dasu "

"Abba ai akwai kud'i sosai a guna kasan sun turomana fa da kud'i don muyi hidiman
tafiyan dasu kuma account d'ina ma akwai nauyi sosai,na ware wasu kud'i sosai daman
yanzu zan bata ta rik'e a hannunta kuma duk wata zan rik'a tura mata kud'i
account"

Jinjina kai Abban yake cike da tsantsar jin dad'i yace "masha Allah hakan yayi
Daddy nah Allah yai maka albarka ya saka maka bisa biyayyan da kai min Allah ya
baka zuri'a ta gari".

" ameen ameen " kawai yaketa fad'i


"tom ka kiramin khadijan tazo yanzu ina son ganinta "
Shine kiran dayamin yanzu.
Da sallama na shiga parlourn na k'ara sa k'asan kujerar Abba na zauna kaina a
k'asa nace "Abba barka da safiya an tashi lfy "

"Lfy qlau Nana Khadeejah ya gidan "


"Lfy lau Abba"

"Masha Allah hakan nakeso najinaji, to ya shirye shiryen tafiyan me gidan kuma "
ya fad'a cikin mirmishi
Cikin jin kunya sosai nace "Alhamdulillah Abba"
"Madallah ,gobe iyanzu dai Daddy yayi nisa damu ko"
Wannan karon shiya amsa yana y'ar dariya yace "Abbah ai iyanzu baku fara
missing d'ina ba sai zuwa kwana biyu ko"
"A'a komu bamuyi kewarka ba ai matar ka zatai yi "

Ba kunya wai ya lek'o fuskata yana cewa " Nahna wai zuwa 24 hours kin fara missing
d'ina"?

Nidai kaina na k'asa duk kunya ta rufeni ina mamakin rayuwar Irin ta gidan
cike da tsantsan boko ba ruwansu da wani jin kunyar d'a ko suruki, mirmishi kawai
nake ina wasa da hannayena,

Nan Abba yai gyaran murya ya koma serious ya fara magana "Abunda yasa na kiraki
Daman don na k'ara jan hankalinku kan hak'uri da juna da yanayin rayuwa musamman
yanzu da zakuyi nesa da juna kuma wata rayuwar zaku k'ara shiga dole sai kun
k'ara hak'uri musamman Ke da kike mace Khadeejah dole sai kin kai zuciya nesa kin
k'ara ninka hak'urinki kinji, kusa aranku kunyi nesa da juna bukuyi nesa ba abun
nufi Ku rink'a jin Kuna tare koda yaushe, ki rik'e amanar auranki kaima ka rik'e
amanar matar ka,Ku mutunta junanku ko Kuna nesa ko Kuna kusa,Allah yai muku albarka
biyayyar da kuke mana Allah ya baku masu yi muku "

Duka amsawa mukai da "ameen"

"Khadeejah in kinada wata matsala ki sanar mana yanzu kinji "

"A'a Abba ba komai wlh "


"To shikenan indai kinada wata damuwa dai kamar koda yaushe ina fad'a miki ki
sanar dani kai tsaye karki damu ni gurbin Mahaifi nake a gareki kinji"

Gyad'a kai nake alamar gamsuwa da maganar, nan dai yaita mana nasiha daga nan
suka shiga hira zuwa jimawa kad'an yace "Toku tashi kuje Ku k'arasa shiryawa ko"

Mik'ewa mukai a tare muna mai sallama.

Muna shiga part d'inmu na cire Hijab d'in na d'ora kan kujera zan wuce kitchen
don yin wanke wanke, aikina nake a sannu Sannu naji alamar mutum a bayana d'an
juyawa nai ai kuwa na ganshi tsaye ya hard'e hannuwanshi a k'irji ya tokara
k'afanshi jikin k'ofa d'auraye hannuwana nai na k'araso kusa dashi a tausashe nace
" Kana buk'atar wani Abu ne "?

D'an mirmishi yai kawai ya ruk'o hannuna zuwa d'akinsa,karo na farko daya tab'a
rik'e hannuna a cikin gidan ,
Bakin gado ya zaunar dani ta bude bed site ya d'auko wasu bandir na kudi y'an
dubu dubu Guda biyu wato 200k ya ajiyesu kan cinyata yana fad'in " ki rik'e
wannan a hannunki sabida school da sauran buk'atu,komai na abinci akwai in nama da
kayan miya ko kifi sun k'are bance ki siya da wannan kud'in ba ki fad'awa Abba in
za'a kawo na gida za'a kawo miki kinji".

Gyad'a kai nai jikina duk yai sanyi idona harya fara kawo ruwa, ya kalli cikin
idona yana girgiza kai "kuka kuma meye abun kuka kiyi shiru kinji "
D'aga kai nai ina had'iye kukan dakeson kufcemin,
"Jeki k'arasa aikin naki "
Mik'ewa nai na fita na shiga d'aki na ajiye kud'in sannan na k'arasa aikin duk
jikina ba laka"

Sanda na dawo parlour na sameshi kwance kan kujera yana kallo zan wuce
bedroom d'ina ya kirani "zoki zauna nan ki tayani kallon wannan film d'in "
K'arasowa nai inda ya nuna min kusa dashi na zauna ina jin wani banbarakwai
kulawan dabai tab'a nunamin ba yau yake nunamin kodan zai tafi ne oho, tun ban
fahimtar film d'in harna fara gane kansa donni ba masoyiyar kallon Indian film bane
amma sai naji film d'in harya fara min dad'i tun ina zaune gefen kujerar tasa harna
zame na d'an kwanta hakan yasa ya matsamin na kwanta sosai muna kallon ne tare
da tattauna abunda Ke faruwa a film d'in in wajan dariyane muyi Har awa biyu cif
ya k'are a sannan ne kuma aka kira sallar azahar na mik'e ina fad'in "bari in
sallah in shiga kitchen me kakeso inma na lunch"
Shima mik'ewa yai yana mik'a yace "wasssshhh"
Y'ar dariya nai cikin dabara nace "kace wasshhh ni kuma bari in k'ara sa ma da
La'ila ha illallah,Muhammadurrasulillah s.w.a, sai in samu ladan naka ko a raba
mana tare".

Girgiza kai yai tare da fad'in " a'a baza kiyimin wayo ba bari in fad'i abuna
da kaina,la'ilaha illallah Muhammadurrasillah"

D'an shagwab'e fuska nai nace "au ka k'wace Ladanka ko tom nima yanzu zan sami
wani tunda zan dafa maka abinci "
D'akinsa ya shige yana y'ar dariya Nima na wuce nawa.

Bayan na shiga toilet na d'aura alwala harna shinfid'a prayer mat sai nai wani
tunani don haka na fita zuwa bedroom d'in sa a hankali na tura k'ofan tasa a
tsaye na sameshi ya shinfid'a prayer mat yana saka jallabiya alamar dai anan d'akin
zaiyi sallar kamar yanda nai tunanin d'an mirmishi nai nace "em daman nazo ne nasan
yanzu zaka tafi masallaci kuma ban Sani ba ko bazaka shigo da wuriba shine zan
tambayeka me zan dafa maka "
Kunya yaji ta kamashi sai yaji bazai iya yin sallar a d'akinba don haka ya
tsugunna ya nad'e mat d'in ya na fad'in "kimin sakwara da miyan agushi "
"OK ba damuwa"ina fad'a na juya na fita shima yabiyo bayana ya wuce masallacin,
araina nake tunanin ko meyasa bai son yin salla cikin jam'i oho,
Ban tsaya doguwar addu'a ba nai kitchen d'in nan na fara had'a girkin cikin
k'warewa da tsafta,awa biyu cif na shirya table d'in sannan na wuce d'aki na
sakeyin wanka na shirya cikin doguwar riga na material d'in kin play k'irjin ya
matseni sosai wanda hakan ya bawa k'irjina daman yin d'as cikin rigar, shima a
lokacin ya sake watsa ruwa yasa trouser 3 quarter da singlet ya fito dukkanmu
mirmishi muka sakarwa junanmu na zuba mai sakwaran leda biyu yace in k'ara d'aya
na k'ara sannan na zuba miyan a d'an bowl na miya wanda tasha ganda da kifi ,na
tsiyayo mai lemon kwakwa wanda yasha Madara da flavor, Bayan na zuba mai ya kalleni
yana cewa " maza sa spoon muci tare "
D'an dubansa nai amma ban tanka ba na d'auki spoon d'in na fara ci, leda
d'aya naci na k'oshi shi kuwa saida yaci leda uku da rabi yasha lemon kofi
uku,kallonsa nai muka had'a ido da sauri na kauda kaina ina d'an mirmishi "
kallona kikeyi ko Kinga inada ci sosai , kin san ni bana wasa da cikina fa "
"Hhhhhmmmm niba haka nake nufi ba fa"

Mik'ewa yai yana fad'in "kyama fad'i gaskiya".


Nidai mirmishi kawai nakeyi.

Misalin k'arfe bakwai motocin gidan suka jeru tare da mutan gidan harda Aunty
ummu sulaim don yimai rakiya wanda mota guda tana d'aukene da kayansa kuma ita zamu
shiga Nidashi, ina sanye da doguwar riga bak'a me adon Brown mayafinta ne nad'e a
kaina takalmina ma brown ne sau ciki, ina tsaye bakin k'ofa rik'e da wayoyinsa
sanda yake gyara igiyan takalminsa, ya d'ago muka had'a ido wasu hawaye danaketa
k'ok'arin b'oyewa ne suka silalo hannuna ya rik'e d'aya hannun yana rufe k'ofan
part d'in namu,saida muka shiga bayan motan muka zauna driver yaja yabi bayan
motocin su Abbah ya rik'o hannuna cikin nasa yana magana a hankali " Kar kiyi kuka
kinji Khadeejah ki kwantar da hankalinki kamar yaune zanje na dawo shekara d'aya da
y'an watanni ba yawa garesu ba kuma kinaji Abbah yace kina samun hutu zakuzo min
sannan Nima zanzo in mun sami time ko yaya ne , karki damu kinji ,ki maida hankali
sosai kan karatunki,Kinga lokacin ma da zan dawo gaba d'aya kin kammala duk
karatun nak ko"?
Gyad'a kai nai ina shashshek'a, wani tausayi ne ya lullub'eshi besan meyasa
yakejin wani bak'on yanayi tare dashi ba kwana biyu tausayin ta keji maimakon da
da yake bala'in jin haushinta, jin kukan ya tsananta yasa ya kamo fuskata daf da
tashi "ki fad'amin meye matsalar in dai akwai wata damuwa ki sanar dani ,ni wannan
kukan ne banso ki daina plss" unexpected naji harshensa kan fuskata yana lashe
hawayen dake fita a idona, limshe idon nai da sauri inajin gabana na wani
fad'uwa ,hannuna na damk'e sosai cikin nasa yake lasan fuskan nawa wanda lokaci
guda hawayen ya tsaya sai fad'uwar gaba , jawoni yai jikinsa sosai ya Sani cikin
k'irjinsa ina shanshanar k'amshin sa, wata nutsuwa naji tana saukar min don wannan
shine karon farko a rayuwata dana tsinci kaina kwance jikin namiji haka,pitting
bayana yake alaman rarrashi yana fad'amin magana me sanyi "kiyi shiru ki fad'amin
meye matsalan meke saki kuka haka ki sanar dani kinji"
Tsintar kaina nai da fad'in "kayimin alk'awarin zaka rik'e amanar aurena,zaka
rink'a tunani a kowace rana,sannan zaka kauda idonka daga kowace mace". Duka cikin
miryan kuka da shagwab'a nake wannan maganar,
Mamakin magana ta yake yanajin salon danai maganar har cikin k'wak'walwarsa,
cikin kunnena ya zura bakinsa yana cewa " I'm promise promise. . . . .
Dai dai lokacin motar ta tsaya da sauri na tashi a jikinsa ina gyara rigata
mirmishi yai yana kallona sannan ya bud'e mirfin muka fita.
Bamu dad'e a airport d'inba aka fara kiran fasinjoji nan naji gabana ya k'ara
fad'uwa yana lura dani don haka ya gyad'a min kai alamar k'arfafa gwiwa, sallama ya
farayi da kowa ya tsugunna gaban Abba yana mai sallama ya shafa kansa yana samai
albarka, haka ma Aunty murja tai mai sannan ya rik'o hannuna Aunty sulaim da Sweety
yai musu sallama ya rik'o su salis ma ya rungumesu jikinsa,a sannan ya k'araso
gabana ya rik'e dukkan hannuwana yana kallon cikin idona wanda suka k'ara cika da
hawaye duk yanda naso maidasu sunk'i tsayawa rungumoni yai jikinsa ya matseni
sosai yana pitting bayana muna a haka tsawon lokaci muka k'arajin kiran da akewa
fasinjoji a hankali ya zameni a jikinsa yana kissing d'ina ya juya yana jan y'ar
k'araman jakansa,ina tsaye ina binsa da kallo naji an rik'o hannuna a hankali na
juya sweety ce ta gyad'a min kai tare da rik'o hannuna muka tafi gun motocinmu
wanda tuni su Abban har sun wuce.

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA
LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣4⃣
0⃣3⃣4⃣ 0⃣3⃣4⃣

Ban Sani ba ashe haka kewa Ke damun zuciyar d'an Adam, cikin kwana uku kacal da
tafiyarsa amma duk kewanshi ta addabi rayuwata ko ina na gidan ji nake yamin fad'i
musamman in lokacin cin abincinsa yai wanda daman nan ne muke duk wata hurd'a me
tsayi wai ashe zama kawai waje d'aya koba jituwa a tsakani yana sanya kewa in an
rabu? Tabbas ban san da hakan ba sai yanzu, nidai nasan ba wani abu me girma bane
tsakanina da shi wata rana ma saimu kwana mu yini magana sau biyar bata shiga
tsakaninmu ba banda cikin kwanakin yafiyarsa da suka gabato, amma duk da haka
duk inda wani abu ke had'amu in na zauna gun banjin dad'in raina,ko d'akinsa in
na shiga sai Inji k'walla ta taru a idona, uwa uba da zan tafi school na saba ya
kaini ya d'aukoni koda wata kalma bazata shiga tsakaninmu ba amma zamana kawai
kusa dashi muna tafiya a haka ma dad'i kemin, gashi yau din Abba yace min in fara
anfani da motata zuwa school d'in tunda daman hannuna ya fad'a,

Fargaba da tunani suka dameni amma haka na daure na naita addu'oi kafin
shigata motar har na shiga na tada inata addu'oin neman tsari daga sharrin k'arfe,
tafiya nake a nutse cikin yanayi na y'an koyo har Allah ya sadani da school
d'in, da Hafsah Aminiya na had'u tana ganina nai parking ta k'araso tana dariya
tare da rik'e baki "ah lalle Har hannu ya fad'a kenan masha Allah, Allah ya tsare
dukkan sharri"
Fitowa nai bayan na rufe motan muka jera ina bata labarin fargabar danakeji
harna k'araso, dariya take tana fad'in 'aima kinyi k'ok'ari Allah ya tsare Sharrin
k'arfe"
"Ameen Ameen tawan"
Muna hira a haka muka k'arasa ga hall d'in bamu.

Koda aka tashi duk way'anda suke y'an hanyarmu tare muka tafi dasu nace Duk su
shiga in rage musu hanya,ai kuwa nan sukaita godiya kunsan d'an makaranta komai
girmansa yana son rage hanya 😃

****
Duka sweety ta tarkato ta dawo part d'ina da zama komai tare muke koda batada
da lecture in zan tafi school zata tashi miyi break tare mu gyara ko ina sannan in
tafi in barta, gashi tana matuk'ar k'ok'ari wajan kyautata mu'amala tsakaninmu duk
da muna rayuwa ne Irin ta k'awaye amma hakan bai hana tana bani girmana.

******
Can k'asar india kuwa Uk ya shiga rubibi kasancewar yai jinkirin dawowa yasa duk
abubuwa sunyi nisa bashi don haka yaita k'ok'arin daidaita komai har tsawon kwana
biyar sannan ya sami nutsuwa, kuma sai a ranar ya sami sukunin saka layinsa nacan
cikin wayanshi, da dare bayan yai sallar magriba ya d'auko wayan ya kira Abba,cikin
farin ciki suka gaisa Abban yake tambayarsa meyasa baisa layinsa ba har wannan
kwanakin yanata nemansa ,fad'a mai uzurinsa yai amma dukda hakan dai Abban yai mai
fad'an yasan yanzu yanada mata kuma tana buk'atar kulawarsa kuma zataso taji
kiranshi tun tuni don haka ya hanzarta ya kirata, amsawa yai dato sukai sallama,
bin wayar yai da kallo yana nazarin maganganun Abban nashi, gaskiya bai kyautaba a
yanda ya tafi yabar yarinyar tana cikin damuwa ya dace ya nemeta da wuri dukda yana
yawon tunata koda yana busy lokaci lokaci tana fad'omai a rai amma baiyi yunk'urin
nemanta ba,kodake ba laifinsa bane busy ya shige da yawa.

Duba lokaci yai yasan yanzu a Nigeria yamma ce bari ya bari sai can bayan yai
sallar isha'i kamar k'arfe sha d'aya ma gomansu lokacin anyi magriba a Nigeria
d'in don haka ya jawo laptop d'in sa yaci gaba da gudanar da sak'k'onin cikin ta.

*****
Bayan sallar magriba muna zaune parlor da sweety muna kallo dukda rabin
hankali na baga kallon yake ba,wani Irin yanayi nakeji Mara dad'i cikin zuciyata,
yau kwana biyar da tafiyarsa amma yaci ace ko yaya ya kirani amma shine harya manta
dani kodake daman nasan wannan kulawan da yaita bani ba har zuci bane kawai don
zaiyi nisa ne,nasani banda gurbi a zuciyar sa tun tuni, nima gajeran tunani ne yasa
na fara wannan hasashshen yanzu gashi can ya koma inda ya saba ganin wayayyan mata
taya ma zai tuna dani,naso inji labarinsa ko gun sweety ne amma bazan iya
tambayarta ba tunda itama batamin maganar shi ba ko kad'an, inaga kotai tunanin ya
kirani ne shiyasa batamin batun ba. . . .
Mik'o min wayata tai da taketa ringing a d'aki banjiba sai ita tajiyo shine
taje ta d'auko min, bani tai tana d'an dariya tace "Aunty nah ga Broth na kira
tabbatas wannan number d'insa ce "

Karb'an wayan nai wanda zuwa lokacin har wayan ta tsinke nabi number d'in da
kallo a zahiri ta k'asar wajace kuma nasan shi kad'ai nake dashi a waje k'ara kira
akai na d'aga jikina a mace tare kuma dajin wata Irin fad'uwar gaba,daga can naji
muryanshi na fad'in "hello"
Saida ya sake mainaitawa sannan na tattaro nutsuwa da k'warin gwiwa nasawa kaina
na masa da fad'in " Assalamu Alaika"

"Wslm " yace yana d'an mirmishi daga d'aya b'angaren


K'ara tausasa muryata nai nace "Barka da dare ka wuni lfy,ya aiki ya karatu"?

"Duka Alhamdulillah,ya kk ya school"

"Alhamdulillah"

" Kin jini shiru kwana biyar ko ina busy ne sosai sai yau na sami nutsuwa "
"Um hmm Allah ya taimaka ya bada abunda akaje Neman"

Har cikin ransa yaji dad'in addu'ar ya amsa da "amin na gode"

"Um hmmmm"

Shiru mukai na D'an lokaci sannan yace "Akwai wata matsala "?

" a'a ba komai "

"OK sai anjima ko "


"Allah ya tashemu lafiya"

Daga can ya katse kiran nabi wayan da kallo ina d'an mirmishi, maganar Sweety
naji wanda nama manta da ita a gun "Tom Aunty na tunani ya k'are anji lafiyar miji
ko"
Dariya nai kawai na kauda kai,zama tai gefena tana fad'in "ai ina kula dake
kwana biyu yanda kike shiga tunani kuma nasan dan bai kiraki bane don haka ma ban
miki maganar ba karki samin kuka"

"Hhhhhmmmm kin ma maidani wata kala daga magana sai kuka "
Kiran salla ne ya tashemu muka shiga d'aki donyin sallan,

Yau kam nayi baccin farin cikin wanda Har naso makara,haka na yini ranar ba wata
damuwa Har mamakin kaina nake yanda zuciyata take k'ara fad'awa tarkon k'aunar
wanda banko son kallonsa ada mutum na farko daya takura rayuwata kuma na tsani
d'abi'unsa amma gashi k'addarar aure ta gifta tsakanin mu har gashi na fad'a
k'aunarsa ikon Allah kenan wanda yafi gaban komai.

Bayan kwana biyu ya k'ara kirana da dare muka gaisa nan ma dai ba wata doguwar
hira mukai ba yai min sallama,
Tun daga ranar ya zama duk kwana biyu zai kirani mu gaisa ya tambayeni koda wata
matsala nace mai babu, duk yanda Allah ya jarrabeni da masifar k'aunar sa ban bada
kaina don koshi ban nuna mai na matuk'ar damuwa da rashinsa balle wanda Ke kusa
dani mutum bazai gane inda na nufa ba,kuma hakan bai sani na fasa addu'a da rok'on
Allah alkairi cikin rayuwar auranmu ba.

A b'angaren UK kuwa fadlah ta sakoshi gaba da nata makaman yak'in kullum da


salon da take zuwar mai, kasancewar har ita aka d'iba cikin masu k'ara yin course
d'in kuma gidajan da aka kama musu dukka jere suke cikin wani katafaran estate
akayi sa'a kuma gidan sa da nata suna jere da juna don haka ko yaushe tana biye
dashi cikin school ko a gida, Fadlah nada girman da bai iya wulak'antata don tana
cikin matan dayasa aransa inda zai aure a kusa ita zai aura,amma gashi yanzuma da
akai mai auran k'addara ta kasa hak'ura dashi kullum fad'a mai take ita ta amince
zata zauna dashi a matsayin matar sa ta biyu, ya nuna mata ta hak'ura da batun aure
kawai suci gaba da zumunci da mutunci don shi yanzu inma yai mata alk'awarin aure
yai k'arya damanshi tsarin rayuwar sa mace d'aya ce zai aura donshi d'an boko ne
to amma tunda gashi anmai auran dole to ya k'arb'i k'addararsa bai jin zai zama
cikin maza masu tara iyali wannan wanda Basu wayeba, ganin kullum batada aiki sai
mai naci damai kuka yasa ya rarrasheta yace ta bari dai yaga yanda gaba zatai amma
yanzu suyi abunda ya kaisu kawai randa suka dawo gida Nigeria sa nemi mafita,amma a
ranshi yasan bawai auran ta zaiyi ba gaskiya.

Kwanaki suna ta tafiya har yai wata guda da tafiya kuma a sannan muka fara exam
wanda ta d'auke mu wata guda itama duka hutun sati biyu muka samu don haka ma
wannan hutun bai cikin wanda zanwa mijina ziyara sai hutun mu na gaba da zamuyi
tsawon sati shida a gida shine Abba yace muna yi zan tafi India .

Mun koma school nan naci gaba da karatuna cikin kwanciyar hankali sai dai
yanzu abunda ya fara damuna sai UK yai sati guda bai kirani a waya ba, kuma inma
ya kira Sama Sama zamu gaisa ya kashe tun ina daurewa har abun ya fara damuna
matuk'a . . .

Manège manège

Taku ce
y'ar mutan ja'oji
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *Y'AN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣5⃣
0⃣3⃣5⃣ 0⃣3⃣5⃣

Sosai nasa abun a raina har hakan ta fara bayana kowa ya fara gane halin da nake
ciki,yin duniya sweety tayi in fad'a mata matsala ta amma sai dai inyi mirmishi
ince ba komai tasan zurfin cikina amma duk da haka ta alak'anta hakan ne ga
rayuwar aurena,taso gane matsala ne tsakanina da mijina amma batai shishshiga ba
taja bakinta tai tsit, ko a school haka abokan karatuna zasuyita tambayata ko
banda lfy amma amsar dai d'aya ce ba komai, a haka wata rana Aunty ummy tace min
zata kawomin ziyara kasancewar yanzu muna huld'a da ita sosai fiye da da don
yanzu duk inda zaka ganmu da Hafsa Aminiya zaka ganmu da Aunty ummy kasancewar
tanada matuk'ar k'ok'ari yasa tamu tazo d'aya don muna k'aruwa da juna matuk'a
asalinta babanta balaraben chadi ne mamanta kuma fulanin nijar ne don haka kana
kallonta zaka gane ba bahashiya bace amma zama cikin hausawa da auran miji bahaushe
yasa ta rikid'e a magana da mu'mala tunda tace min zata kawomin ziyara naketa
murna don zama da ita akwai k'aruwa sosai ko a harkar karatu ko a harkar yau da
gobe, ran asabar ne zuwan nata don haka ina tashi nai ayyukana tsaf nai wanka na
gama komai kasancewar sweety ranar bata nan ana bikin k'awarta tun sassafe ta fita,
wajan sha d'aya na kira wayanta nace "Aunty ummy shiru baki zo ba"
Dariya tai tace ina shirya oga ne tare zamu fito ya saukeni amma nan da 30
minutes insha Allah ina gidanki"
Sallama nai mata ina cewa saita k'araso.
Tashi nai na shiga kitchen ina tunanin in fara rage aiki kafin tazo don haka na
d'ora tuwo don nasan masoyinta a duniya tuwon shinkafa miyar d'anyan kub'ewa kuma
ta fad'a min shi zan mata, inata aikina wajan awa guda har na gama tuwon na kwashe
zan d'ora miya naji knocking da sauri na k'arasa ina fad'in " sai yanzu Maman boy
gaskiya kin makara " na fad'a tare da bud'e k'ofan dariya tai bayan ta shigo tace
bazaki ganeba Kedai Khadeejah, tsayawa nai kallonta ganinta ita kad'ai nace 'ina
Farha da my boy na ganki Ke kad'ai"

Sai da ta zauna kan d'aya daga kujerun parlourn sannan tace "Abban su ya wuce
dasu gun mamanshi wai tace kwana biyu basuje mata week end ba"

"Haba amma shine harda yarona za'a tafi inata murna yau yarona za'a kawo min
ziyara"

"Ke bar wannan yaron naki rigimamme ai nan da 4 days zan yayeshi don bazanyi
Ramadan dashi ba tunda daman ba shan nono yake sosai ba "

Wuce wa kitchen nai ina cewa"a'a yarona bai kai yaye ba sai dai in kuma k'ani
aka samo mai"

Ruwa da lemo na kawo mata sannan na zauna muka gaisa sosai bayan ta d'an sha
ruwan tace "Wane k'ani kuma ai nida wata haihuwa sai nan da shekara uku ko hud'u
insha Allah kafin nan boy ya shiga school banda wata matsala amma ai konikan danai
tsakanin Farha da boy ta b'aci don haka yanzu nake Neman tsari da konika"

Dariya nai kawai ina mamakin yanda take gudun haihuwa kusa kusa,
Hira muke sosai na saki jiki daga hiran karatu yanayin duniya har muka gangaro
kan rayuwar aure, to an tab'o inda kemin k'aik'ayi duk da ban cikin mata masu
rashin sirri amma wani abun dole kesa kai magana, tana lura da yanayin da nake
kwana biyu wanda shine sanadin zuwan ta ma tunda tayi tayi a school taji damuwata
nak'i,yanzu kuwa cikin hikima ta sako zancen yanda zan fad'i mata komai kafin ma
ta tambaya, labarin mijinta ta fara bani "wato Khadeejah rayuwar aure sai hak'uri
mazan yanzu sun girmi karatun me karatu, shiyasa zan iya kashe ko nawa ne kan
namiji zan iya sadaukar da dukkan lokaci na ga namiji matuk'ar hakan zai zaunar
dani daram cikin ransa, wato Khadeejah akwai wani lokaci da Abban boy ya tafi
canada rimi rimi fa muka rabu tunda ya tafi kullum zamuyi waya muyi chart amma
daga baya Duk saina ga canji ya fara bayyana inna kirashi sai ya gama hidimar sa
zai nemeni kuma inya kira ba wani k'wakk'waran uzuri tsawon lokaci muke a haka na
d'au fishi dashi na daina nemansa nima duk sanda ya kira ma sai naso zan d'aga
wayan,ban Sani ba ashe dama na bashi tayin abunda yaso,wata yarinya ce take d'auke
mai hankali a can tai kanai kanai cikin rayuwarsa janyewar da nai dashi nai fishi
sai ta bashi damar sakewa da ita, sai daga baya nai tunani naiwa kaina fad'a nai
na shiga nemansa ba dare ba rana na mak'ale masa koda yaushe naita kiransa a waya
in yana aiki ya bani uzuri daga na kintaci ya tashi aiki zan ta kiransa saimu raba
dare a waya koda yaushe bashi da lokacin kowa sai nawa duk sauran lokacin shi daba
na aiki ba to nawa ne wani sa'in ma ko wanka zai yi sai ince yasamin video call
zan rink'a tayashi wankan, a dole yarin yar nan ta fita cikin rayuwar sa don kota
zo gunsa muna waya zaice ta tafi zai nemeta in da safe kuma aiki bazai bashi damar
neman ta, a haka na shawo kan matsala ta cikin sauk'i,Kinga danaci gaba da d'aukan
fishi shikenan na barwa wata banzar mijina tun suna soyayya ta iya baki da baki
harta koma ta jiki da jiki shikenan ni an cuceni ko".

Jin jina kai nai ina nazarin kalaman Aunty ummy wanda kai tsaye zuciyata ta ban
amsa da cewa lalle Irin halin da UK yake ciki kenan a India ba makawa nan da nan
hawaye ya kuncewa idona, ni ban tab'a d'an d'ana zumarshi ba wata banza na can tana
k'wak'ubemin miji, lafad'a ta Aunty ummy ta dafo tana fad'in "Khadeejah meya faru
kuma naga kina kuka?"

Cikin sheshshek'an kuka nace "Maman boy kusan fa cikin wannan halin nake ciki
yanzu Umar bai kirana a waya sai yai sama da sati bai neman ba kuma yana kira bama
wata magana daga gaisuwa zai kashe,ina jin tsoron ko dai nima wata mace ki janye
mai hankali "

Girgiza kai tayi "a'a Kar kiyi wannan zaton Khadeejah ko nima ban zargi mijina
ba sai da na sami k'wakk'waran hujja daga abokin aikinsa, don haka karki fara
zargin sa ba kyau kin Sani maybe shi ko aiki ne yasha kansa,ko wani dalili kuma
mafa ni ina ganin kamar da sakacinki Khadeejah Ke kike bari ya kashe wayan maybe
shiru kawai kikeyi bayan kun gaisa bakya fad'a mishi Irin halin da kike ciki na Ke
wansa da buk'atar sa kk?"

D'an zaro ido nai nace" Aunty ummy yanzu sai nace mai ina buk'atar sa koma?"

Wani kallo naga tabini dashi na rashin fahimta sannan ta rik'o hannuna tana
fad'in " Khadeejah kina son kicemin baki buk'atar mijinki baki muradin ganinshi
kusa dake bakya marmarin sake had'a shin fid'a dashi akoda yaushe? "

Jim nai araina ina tunanin kodai ma in sanarwa Aunty ummy asalin yanda zaman mu
da Uk yake ko in shaida mata ma bamu tab'a had'a makwanci ba maybe in samu mafita
gareta,kai na sake girgizawa cikin raina nace bana cikin mata masu fad'in sirrin
auransu wannan haramun ne matuk'a duk halin da zan shiga bazan tab'a fad'awa wani
wannan sirrin ba,

Girgiza kafad'a tai cikin yanayin bani kwarin gwiwa tace "Khadeejah ki tashi
tsaye ki damk'i zuciyar mijinki da gangar jikinsa karki bari kawaici da Kunya Susa
miki waigi tsakaninki da farin cikin ki lalle ne in har kina son samun mijinki a
tafin hannunki sai kin zama karuwa y'ar bariki me zafafan kalamai da zafafan aiki
amma na soyayya sannan zaki cimma burinki, ina baki shawara Khadeejah yanda
mijinki yai doguwar rayuwa cikin masu bud'ad'd'an ido to ganinki za'a rink'a yi a
kulle biki san komai ba musamman keda kike *Y'AR* *ARABIC* da yawa mutane wani
kallo sukewa macen da take y'ar Arabic me ilimin addini gani suke bata iya soyayya
ba bata iya komai ba kunya da kawaici kamun kai da nutsuwar mu mu Y'AN ARABIC ita
kesa ake mana wani kallo na daban,abunda ba'a Sani ba mu fitsara ce ba fidda
tsiya bamu iya ba amma a bed munfi duk wata da take jin kanta wayayyiya fanni
soyayya mu d'in na daban ne domin mu soyayya mukeyi me y'anci Irin wanda musulunci
ya koyar kuma take tafiya da kowane Irin Zamani, Khadeejah mufa d'alibai ne masu
karantar Islamic tome za'a layance mana duk mutumin fa da yake karanta rayuwar
gidan manzan Allah (s.w.a) babu wata rayuwa da zata bashi matsala kota dameshi,
ya karanta yaji yanda ake zama da miji yanda ma ake zama dako wane irin mutum, duk
duniya fa babu wani mutum daya kai manzan Allah iya soyayya da rayuwar aure shi
yasan yanda ake kula mace a ririta ta tayima abunda bata san tana yinba, shi yasan
yanda ake faranta ran juna kuma shi yake koyar da matansa yanda zasu kula dashi
suyi Abunda ransa zai fari,agidan manzan Allah aka saukar da duk wata soyayya
shauk'i da nishad'i to mu kuma d'aliban Arabic meye bamu karanta ciki ba meye bamu
Sani ba,daman anfanin ka nemi Sani kan rayuwar manzan Allah ai don kayi koyi da
ita ne to mukam mun koya mun san komai kuma mun gode Allah don haka Khadeejah
kiyi amfani da 'sak'afa islamiyya' (wayewa ta musulunci" da 'sak'asa ilmiyya'
(wayewa ta ilimi) ki daidai ta rayuwar ki da mijinki rayuwar zata fimiki dad'i,
don wlh Allah duk rayuwar da babu namiji cikin ta rayuwa ce Mara dad'i mara armashi
Khadeejah ki mori rayuwar ki kiji dad'i kuma ki sami aljannarki".

Sosai maganganun Aunty ummy suka shige ni kuma sukai tasiri a jikina da zuciyata
lokaci guda naji wani Irin k'warin gwiwa ta saukar min, godiya nai mata sosai
sannan muka shiga kitchen mukai miya a tare muka had'a kunun aya bayan munyi
sallar azahar mukaci abincin nan mukaci gaba da hiran mu wanda nake k'aruwa da
ita matuk'ar k'aruwa har bayan sallar la'asar sannan Abban boy yazo ya d'auketa nai
mata rakiya gate da kayan shafa na mata cikin leda inata k'ara mata godiya.

Bayan na idar da sallar magriba ina zaune kan abun sallar tunanin duka
maganganun mu na d'azu da Aunty Ummy nake tabbas saina cire duk wata kunya dake
tare dani da kawaici na nemawa kaina y'an ci don haka daga yau insha Allah zan fara
dukkan wani k'alubale na shirya karb'ar sa, ina nan zaune har akai isha'i na tashi
anyi tare da shafa'i da wutiri nai addu'oina naje na watsa ruwa a lokacin ne sweety
ta shigo a gajiye tik'is itama wankan tai ko abinci bata nema ba tanayin salla ta
kwanta, parlour na dawo na kwanta kan kujera sannan na fara lalubar number d'in sa
a hankali na danna kira harta katse ba'a d'aga ba ban karaya ba na sake kira shima
tana gab da tsinkewa ya d'aga duummmm naji gabana ya fad'i amma saina kira sunan
Allah wanda shi zai bani k'warin gwiwa, "Assalamu Alaika " na fad'a cikin wata
murya
" wslm , ya kk ya Guda"
" lfy qlau muke kaifa"

"Nima lfy ta qlau"


"Masha Allah, ya karatu"

"Gashi munata yi"

"Tom Allah ya taimaka "

"Ameen"

Shiru ya ratsa na d'an sa'anni na rasa me zance,amma dana tuna meke gabana
saina k'ara k'asa da muryata sosai kamar me rad'a nace" Saura ne wata nawa ka
dawo "

Wani iri yaji tambayar wadda har taso bashi dariya amma sai ya basar yace "wata
na nawa ne da tafiya yanzu "

Jim nai ina tunani can nace "um yanzu watan ka fa hud'u yanzu "
"OK Kinga basai na fad'a ba saiki k'irga ki gani saura wata nawa yanzu tunda dai
wata goma sha biyar zamuyi"

Shagwab'e murya nai kamar zanyi kuka nace " nidai Allah watannin nan basa sauri
nifa duk na matsu ma muyi hutu in kawo ma ziyara "

Tofa ya fad'a a ransa me yarinyar nan Ke nufi ne, d'an mirmishi yai yace " kina
son zuwa inda nake ne?"

Kamar y'ar k'aramar yarinya nace "um ina son ganinka fa kullum sai naita
tunaninka inji kamar ma inzo in ganka"
Wani bak'on yanayi yaji ya ziyarce shi, don salon yanda maganar Ke ratsashi har
ya fara shiga cikin jikinsa, jin danai yai shiru yasa nace " mijinaaaaaaa"

Wawwwww ya furta cikin ransa yau kuma shi ake kira wannan sunan,
Ni kuwa rasa sunan da zan fad'a mai ne yasa na kirashi da wannan sunan don dai ba
girma ba ladabi in kirashi da sunanshi na gaskiya Umar,kuma bazan iya cemai UK ba
wannan sunan abokai ne, broth kuwa sunan da y'an uwansa Ke cemai ne,Sai Daddy shi
kuma sunan da Abban sa da sauran dangi Ke fad'a mai ne ni kuwa nafi son in kirashi
da sunan da wani bai tab'a fad'a mai ba,ai kuwa da gaske sunan ya bigeshi ,amma
basarwa Irin tasa yasa ya basar d'in yana fad'in "um ina jinki "

"Baka kewanmu ne kai "


" hhhmmm inayi mana me kika gani "
"A'a naji baka cewa ma kana son zuwa ka ganmu ne"

"Inna fad'a ma baza tai amfani ba tunda nasan ba zuwan zanyi ba ko,nida gida
sai nayi wata goma "
"Hhhmmm haka ne tom ni zan kawo ma ziyara nanda wata uku insha Allah, wannan
karon semester d'in mu wata uku ce yanzu munci wata d'aya da komawa nanda wata
biyu zamu fara exam muna gamawa insha Allah zanzo Abba ma yace har dashi zamuzo "

D'an mirmishi yai yace "To ina jiranku sai kunzo "

"Um hmmmm, daman nace um"

Jin nai shiru yasa yace "fad'i mana ina jinki ko akwai wata matsala "

"Um um daman ina son ince ne don Allah me yasa yanzu baka kirana "

Shiru yai don bashi da amsa tunda shima dai bayace ga shi ba,

"Naji kai shiru ko laifi nai maka "


"A'a ba wani lefi kawai aikine yake min yawa kin san course d'in namu akwai
wuya"

"Oh to Allah ya taimaka ya bada sa'a,Allah yasa kafi kowa cinyewa "

Har ransa yaji dad'in wannan addu'ar don haka cikin sakin fuska yace "ameen na
gode"

"Um tom zanyi bacci sai da safe "

"OK Allah ya tashemu lfy,ina sweety koke kad'ai ce "

"A'a tare muke kwana ai kullum tare muke yanzu dai tai bacci"
"OK sai da safe to"

Kashe wayan nai cikin fara'a nai wani juyi har cikin raina yau nakejin farin
ciki wayan Sama da 10 minutes mukai yau wanda duka bama wuce 2 minutes a wayan
namu, k'udurtawa nai araina gobe sai munyi 20 minutes insha Allah.

Tashi nai na koma d'aki na kwanta cikin nishad'i da farin ciki nai addu'a tare
da lumshe idanuwa na.

Shi kuwa UK bayan kashe wayan binta yai da kallo yana wani mirmishi wanda bai
san dalilin yinsa ba, d'ago ido yai suka had'a ido da fadlah dake zaune ta zabga
uban tagumi tana kallon sa idonta duk ya tara hawaye,duk sai ya diririce don har ga
Allah shi yama manta tana zaune kiran farko dai yasan tana gun suna searching wani
abu cikin Laptop nashi don ko a lokacin ma yanata mata magana kan taje ta kwanta
dare yayi sosai amma tak'i don haka kiran daya shigo yana kallon wayan yak'i
d'agawa yace tashi kije gidanki, tak'i tashi tana lek'en wayan har kiran ya katse
da kiran ma ya k'ara shigowa yai ta mata masifa tak'i ganin kiran yana neman
katsewa yasa ya d'aga sai kuma yanzu daya gama ya waigo sannan ma ya tuna da ita,
d'an tsare gira yai yace "Fadlah jeki gidan ki dare yayi sosai,ban son kina kai
tsawon dare haka,kin san zargi zai iya shiga zuciyoyin mutanan dake tare damu in
suna ganin kina dare a nan "

Had'iye b'acin ran dake taso mata tai tace "Don matar ka ta kiraka shine
kake korata ko choice?"

"A'a wane Irin don mata ta ta kirani ai tun kafin a kirani nake cemiki kije ki
kwanta,yanzu dubi ogogo fa k'arfe nawa yanzu?"

K'ara karkace kai tai cikin yanayin wai a tausaya mata tace "choice don Allah
kayi wani Abu mana cikin rayuwar mu kasan fa yanda nake sonka ko . . . .
Dakatar da ita yai yace "naji koma dai meye kije zamuyi magana da safe "

Daga haka ya mik'e zuwa bedroom d'in wanda yake k'waya d'aya tal ya rufe k'ofa,
gado ya haye yana shafa sumar kansa yana Neman mafita tsakanin shi da fadlah don a
zahirin gaskiya shi bai san yanda zai da ita ba wlh,jin k'aran rufe k'ofa yasa ya
gane ta fita don haka ya tashi ya fita ya rufe parlour sosai ya kashe duk kayan
wuta yazo ta kwanta.

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣6⃣
0⃣3⃣6⃣ 0⃣3⃣6⃣

Yau lahadi ina tashi da safe tuwona na jiya kawai na d'umama naci na fara k'ok'arin
had'a kayan da zanyi dashishin alkama da miyar taushe, don yau na shirya yiwa Abba
shi kwana biyu ban mai girki ba, kuma matsayin abincin rana nake son mai don yau
nasan ba inda zashi yana gida, sweety tanata baccin gajiyan biki banyi k'ok'arin
tashinta ba na shiga aikina sosai har wajan sha biyu na gama har had'amai zob'o
wanda nasa sugar kad'an don yanayin jikin sa, bayan na zuzzuba Duk cikin warmers na
zuba zab'on cikin wani k'aton juk, sanda na shiga zanyi sanka na sami sweety zaune
bakin mirror tana Kwalliya, y'ar dariya nai nace "yau dai bazaki baccin dare da
wuri ba sai yanzu zaki tashi "

Mirmishi tai tace "tun 11 fa na tashi waya nake da Hubby na kuma ina gamawa na
fad'a wanka"
"Ok bari nima inyi wankan "
Na fad'i ina shigewa toilet,

Saida nai sallar azahar sannan na d'auki abincin na wuce wajan Abban sweety ta
rik'omin juk d'in, sanda muka shiga Parlourn nashi yana zaune yana waya zama mukai
muna jira ya gama ni ina d'an nesa dashi yayin da sweety ta zauna jikin sa kamar
yanda ta saba kullum tana manne dashi, bayan ya gama wayar ya juyo da kalkonsa
gareni cikin tsokana yace "Khadeejah wannan k'anwar taki bazata girma ba ya kamata
ki fara shirin mata aure ko zata san ta girma ta daina wannan tab'atar"

Y'ar dariya nai nace "Abba ai tace in tana tare dakai jinta take y'ar yarinya "

Dariya yai yana shafo kanta yace "me aka kawo min ne a wannan kulan"

D'an mirmishi nai na gaisheshi ya amsa cikin kulawa sannan sweety ma ta


gaisheshi ya amsa yana cewa a bud'e min inga me aka kawo "

Tasowa nai ba bud'e mai abincin ya gani shak'a yai yana dariya yace "Tom sweety
jeki ce Murjah ta bar had'a abincin gashi Khadeejah ta kawo min"

Fita tai can ta dawo da Aunty murjah d'auke da flat da spoon, gaisheta nai itama
ta amsa cikin fara'a tace " Khadeejah kice kin fansheni kenan "

Mirmishi kawai nakeyi kaina a k'asa ganin an zuba mai abincin zai fara ci yasa
na mik'e ina cewa sweety "bari naje parlour"

Itama mik'ewa tai ta biyoni d'akinta mukaje muka zauna munata hira , ranar a
part d'in su muka yini sai wajan k'arfe shida da rabi muka koma part d'ina muna
zuwa mukai sallar magriba mukaci abincin da mukazo dashi da daga gun Aunty murjah.

Yanda na gama tsarawa daman ina yin sallar isha'i zan kirashi ,don haka kafin
nai sallar nai wanka ina idar da sallar na koma d'aya d'akina nabar sweety itama
tana kwance tana waya da saurayinta,
Bugu d'aya biyu uku ya d'auka yana d'agawa yace "Bari insa credit zan kiraki
"

" um um inada credit sosai a ciki".

"OK Ashe hajiya ce Ke ko"

D'an k'ayataccen mirmishi nai nace "Barka da dare "

"Ya kk"

"Lfy qlau ya school"

"Um muna fama "

"Tom Allah ya taimaka"

"Ameen ya school d'in naki Ke"

"Alhamdulillah school tai zafi "

"Meyasa tai zafi "


"Sabida mun fara had'a kayanmu daga cikin ta"

"OK yaushe zaku gama ne"

"Da saura amma ba sosai ba yanzu dai da muncinye sauran wannan semester d'aya ce
ta rage mana kuma itama bame tsayi bace"

"Allah ya kaimu "

"Ameen"

Shiru muka d'anyi can nace " um kasan me?"

"Um um sai kin fad'a"

"Don Allah in kayi salla in ka gama yiwa su Abba da kanka addu'a ka rink'a
rok'amin Allah yasa na fito da first class"

Jim yai yana tunanin shi yaushe ma rabon sa daya tsaya yai wata addu'a inya idar
da salla ai shi yana idarwa tashi yake don bai jin yanada wata buk'ata da zata d
Sashi damuwa ya tsaya yaita addu'a, (hhhhhhmmmm lalle kunji fa tunanin mutumin Ku
uk)

Jin danai yai shiru yasa nace " kona d'ora ma nauyi"

"Um um kawai ina tunanin kema kina son ki fita da first class ne"

Y'ar dariya nai ta jan hankali nace "eh mana ina so, tunda kaima ka fita dashi
Kaga sai muyi anko ko"

" hhhmmm haka ne zan rink'a miki addu'a insha Allah "

"Yawwwwa My na gode,kasan me?"

"Um um fad'i inji "

"Idan fa miji yanawa matar sa addu'a ko to da wuri Allah Ke karb'a, ko addu'a ta


alkairi kota akasin haka, don Allah ina rok'on ka duk lefin danai maka ka yafemin
Kar kayimin addu'ar da zata kaini wuta"

"Karki damu kinji "

"Yawwa na gode sosai "

"Hhhmmm"

"Ya naji kace hmmmm"

" ba komai kawai wani tunani nayi "

"A kaina kayi tunani"

"A'a ba akanki bane"


"Ummm hmmm"

Haka naita jansa da hira har kusan rabin awa sannan mukai sallama, nai juyi kan
gadon ina mirmishi tare da rungume pillow na dad'e ina tunani sannan na taso na
fito,ina shiga d'akin sweety tace "ina kika shige ne Aunty Nah"
"Hhhmmm ina wancan d'akin ne"

Daga haka na haye gadon ina addu'ar bacci.

Haka rayuwa taci gaba da tafiya tsakaninmu kullum zamuyi waya na kusan 30 minutes
kuma kullum nike kira ko yace min in kashe sai ink'i ince mai inada kud'i, sai dai
kawai yayi dariya yace hajiya wai wake samiki kati,nima dariyan nake nace mai
kud'in da yake samin ne a account da wanda Abba Ke bani nake sa credit d'in dashi.
A haka muka k'ara shak'uwa da juna har ya rage yau saura kwana uku a kama azumin
Ramadan munata shirye shiryen shiga wata me alfarma.

Yauma kamar kullum da dare muna waya nai k'asa da muryana nace "Mijinaaa!"

"Um mata ta"


Ya amsa karon farko da nake kiransa da sunan ya tab'a amsawa ,
Wani bala'in dad'i naji ya lullub'eni nai mirmishi nace " ina son ka bani pic
d'in ka inga yanda ka koma"

Dariya yace "me zakiyi da pic d'ina?"

"Um ina son in ganka ne mana"

"In kina son ki ganni ki duba pic's d'in weeding d'inmu mana kita kallo na"

Shagwab'e murya nai nace "um um nidai na yanzu nakeso ka turo min"

Wani yarrrrr yaji ajikinsa shima k'asa yai da murya cikin nashi salon da yake
sace zuciyoyin mata yace" To bud'e Datan ki in turo miki ta WathApp ko"

"OK bari in bud'e"

Kashe wayan yai ni kuma na bud'e data na, bayan kusan 5 minutes naga pic's sun
fara shigowa kusan guda goma ,bayan sun gama bud'ewa na zubawa wani guda d'aya ido
ina kallon yanda yai kyau sosai a pic d'in d'an mirmishi nai araina nace " hhhmmm
gaskiya ba k'arya mijina ya iya d'aukan wanka na Dad'e a duniya banga namiji daya
iya dressing kamar mace Irin saba,duk da duk y'an uwansa sun fishi kyau nesa ba
kusa ba amma kuma duk yafisu farar fata don shi fari ne sosai da sosai gashi yanada
yawan gashi a fuskar shi wanda sajensa ya kewaye duk fuskar shi harda quarter
million yake dashi, wanda hakan yasa shi yin kyau wanda a zahiri in magana ake ta
kyawawan maza bazai zamo sahun farko ba sai dai a sahu na biyu kona uku amma farar
fata da wadatar saje da iya tsantsar gayu yasa yake tafiya da hankalin mata da
yawa,ciki kuwa harda ni tunda gashi nima yanzu ya janye hankali na gaba d'aya.

Bayan na gama kalla na darje kallon abuna sannan na sake kiran wayar yana
d'agawa yace "nai zaton ma Kunyi bacci fa"

"Hhmmm ya za'i nai bacci kawai na tsaya kallon ka ne handsome guy, ka k'ara
girma kayi kyau sosai "

"Allah ko?"
"Um da gaske"

"Ok to nima turomin naki ingani ko kin k'ara girma kema"

"Um um ni ina nan yanda nake"


"Ban yadda ba turomin in gani"

"Nayi missing duk pics d'ina fa yanzu"

"To ki d'auka yanzu ki turomin"

"Ummm yanzu fa night Wear ne a jikina ka bari gobe zan turo maka in na d'auka "

"Um um ban yarda da wannan wayon ba ni yanzu nake son ki turomin"

"Tom bari in d'auka ma"

"OK ina jira kuma in kika turomin wani ba na yanzu ba zan gane"

Mirmishi kawai nai na kashe wayan, tashi nai naje gaban mudubi na kalli
kaina,naga komai normal sanye nake da riga wanda iya kacinta cinya kasan cewar
ana tsananin zafi, bata da hannu sa D'an siriri kuma wuyanta bud'ad'd'e ne don
haka saman k'irji na Duk a waje suke, zanin Dana d'aura kan rigar na ajiye a gefe,
d'aukan wayan nai na fara buga selfie har biyar sannan na tura mai suna shiga naga
ya bud'e bayan kamar 3 minutes na sake kiran sa nace "Sun shigo ko?"
"Um"
Kawai naji yace nima shiru nai jin yai shiru,jin shirun yai yawa yasa na sake
magana "ya naji kayi shiru ko bacci kakeji ?"

Cikin wata dasashshiyar murya naji "da wannan rigar kike kwanciya kuma tare da
sweety?"

"Um um nifa yanzu ina bedroom d'ina ita kuma tana d'ayan d'akin,kuma in zanje
d'ayan d'akin ina d'aura zani".

" ok, kin cemin biki k'ara girma ba kuma ni naga kin k'ara girman".

Jin yanda muryanshi take a shak'e nasan yana cikin wani yanayi don haka na k'ara
mak'ale muryata yanda zata k'ara Jan hankalin sa nace " kowa fa haka yake cewa na
rame amma kai kace na k'ara girma"

"Um ai ba duka jikin naki ne yake k'ara girma ba wasu wajajan ne ya k'ara
girma".

" hhhmmm tom ina ne ya k'ara girman"

A'a bazan fad'a ba amma nidai naga inda ya girma"

Bubbuga k'afata na fara yi kamar yana kallo na cikin shagwab'a nace "Allah Allah
nidai ka fad'a min ko inma kuka".

Y'ar dariya yai yace " zan fad'a miki sai gobe,Kinga yanzu dare yayi sosai biki
barni nai bacci ba".

"Tom gobe ko ina kira shi zaka fara fad'a min kaji ".

" OK karki damu,good night "

"Sweet dream"

Kashe wayan nai ina jin wani dad'i yana ratsani na lumshe idona ina godiya ga
Allah lalle yanzu na fara tabbatar da soyayya ta cikin zuciyar mijina".
Manage

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣7⃣
0⃣3⃣7⃣ 0⃣3⃣7⃣

Kasancewar yau Monday yasa ban sami sukuni ba a school muka yini ina dawowa da
ciwon kai na dawo don haka ina wanka nai sallar magriba abinci ma Sama Sama naci
nasha magani, anayin isha'i na kwanta ba jimawa bacci ya d'aukeni.

B'angaren uk kuwa yau duk da kewan ta ya yini lokaci lokaci hakan shiga cikin
gallery d'in sa ya kalli pic's d'in sannan yayi mirmishi don haka yau yake Allah
Allah lokacin kiran yayi ya k'ara cewa ta turo sabon pic kuma da kayan bacci yasha
kallo ya more, amma abun mamaki dai dai lokacin da kiran ya sab'a shigowa yayi har
ya wuce da kusan awa Guda don haka ya fara shiga damuwa meya faru yau bata kirashi
ba har yanzu,zaman jira yake tayi har sama da awa biyu yaga kiran bai shigo
ba,yanke shawarar kiran yai,amma abun mamaki kira kusan sau hud'u yai amma ba'a
d'aga ba,shi kuma har ga Allah yau a matse yake da son yin muryar, sake kira yai
shuru don haka ya kira wayan sweety bugu d'aya ta d'aga tana gaishe shima bai tsaya
amsawa ba yace "Ina Khadeejah me take inata kiran wayar ta bata d'aga ba"
" tayi bacci wlh yau tunda wuri kanta ne yake ciwo ".

Ji yai zuciyar sa ba dad'i a dak'ile yace " shike nan ki mata sannu"

Ni kuwa ban san abunda ake ba don sosai nake jin dad'in baccin, wanda ban farka
sai kusa da asuba shima fitsari ne ya farkar dani, ganin kuma an kusa asuba yasa na
d'auro alwala nazo na fara nafilfili har aka kira sallar asuba,bayan nayi na zauna
nai azkar har wajan k'arfe shida da rabi sannan na tashi na fara shirin had'a
abunda zamuyi break dashi bayan na d'ora girkin na wuce toilet donyin wanka ina
cewa sweety data tashi yanzu "ki kula mana da girkin zan shiga wanka".

Saida mukazo yin break sannan sweety Ke fad'amin Broth d'in ta jiya nata kira
na ina bacci, D'an zaro ido nai nace" nifa nama manta da wayan wlh don jiyan nan na
gaji, kuma araina nake cewa in lokacin yin wayan mu yayi zan tashi"

Dariya tai tace "um kullum sai a shige d'akin aita soyewa in nace ina kika shige
sai kice wani abu kike, baki san na ganoki ba tun tuni".

D'an mirmishi nai kawai na tashi zuwa d'aki don d'auko wayan tawa, tarar da
tarin Miss call d'in shi sannan ba naga message d'in sa bud'ewa nai ina karanta
abinda ya k'unsa,

_Hi_ _my_ _wife_ _ya_ _kk_ _ya_ _jikin_ _naki_ , _na_ _kira_ _biki_ _d'aga_
_ba_ _sweety_ _tace_ _kanki_ _na_ _ciwo_ , _sannu_ _Allah_ _ya_ _baki_ _lfy_ ,

Mirmishi nai bayan na gama karantawa sai na tsinci kaina da kiran wayar
tashi, tana shiga ya d'aga " kin warke kenan, ya jikin naki "

"Hhhmmm na warke da sauk'i sosai,ka tashi lfy?"

"Na tashi ina lecture ne ma yanzu amma inna fito zamuyi waya"

"Ok bye".

Koda naje school inata tsammanin kiransa amma bai kira ba sai dare,nan
mukasha k'aunar mu don yau abun yafi na kullum dagewa yai sai na turo pic d'ina na
lokacin, nak'i sai da naga kamar zai fishi sannan nace tom bari na turo ina kashe
wayan nai sauri na sakko da akwatin kayan baccina wanda yake shak'e da had'add'u
kuma fitinan nun kayan bacci, wata riga da wando na Ciro wanda rigar iya kacinta
k'asan breast d'ina kuma kan breast d'in ne kawai a rife shima d'in ana iya ganin
sa kasancewar rigar roba ce ta d'ame sosai ta fitar da komai ana gani,saman
albarkatun k'irjin nan duk suna waje, sumamman dake ina da fara period don haka
suk sun k'ara cika sosai sunyi kyau,kuma daman Masha Allah don Allah yamin baiwar
breast cikakku kuma tsayayyu wadatattu, wandon rigar shima iya kacinsa cinyata,kuma
ya d'ameni sosai mazaunaina sun zauna d'am a cikinsa , da sauri sauri nai komai na
d'auki wayan nai pic guda biyu na tura mai,ina turawa ya kira da sauri sauri naji
yace" sunyi kad'an maza k'ara ko guda goma ne ki turomin yanzun"

Sake d'aukan wasu nai tayi tako ina na tura mai,

Kafin in kira ma ya kirani da d'ayan wayar sa, nace "ya naga ka kira da wannan
layin"

"Um sabida d'ayan ina kallon ki ne ciki muna waya ina kallonki"

Cikin wata iskantacciyar murya ta narka maza nace "ahhhh nidai gaskiya kunya fa
nakeji "

"Kunyar me?"
" kana kalleni kuma muna waya"

" hhhmmm to Mene ne don na kalleki ba mata ta bace"

"D'an mirmishi nai bance komai ba"

Lokaci guda muryanshi ta narke ta dashe tai can k'asa, gaba d'aya yaji
hankalin sa ya tashi musamman inya kalli albarkatun kirj'in sai yaji kamar ana
tsikaranshi, jiyai yana sha'awan shafawa a hankali yakai hannu kan screen d'in
wayan ya shafi saman breaks d'in yana wani lumshe ido, tare da k'ank'ame jikinsa,

"Kayi shiru kuma"

"Dole inyi shiru tunda kin turomin abunda zai rufe min baki amma kinsan me?"

"Um um saika fad'a"

Muna gama wayan nan ki cire kayan nan ban san kowa ya ganki dashi"

Cikin taokana nace" ba wanda fa zai ganni sweety ce kawai a nan "

"Sweety mijin kice zaki ce ita kad'ai ce wannan shigar ni kad'ai zan ringa
ganinta,muna gama waya ki cire su kinji ko"

"Um ba matsala amma don fa ka goge pic d'in Kar wani ya gani "
"Waye zai gani aini ba wanda ke karban wayana, kuma ko mutum ya ansa bai isa
yaga folder d'in ba don kykkyawan ajiya nai musu sabida su dunga d'ebe min kewa"

"Hmmmmmm pic daman yana d'ebe kewa"

"Eh mana ni yana d'ebe min,wanda kika turomin rannan ma su naketa lalla ga na
yau ma sun d'aga min hankali "

"Wayyo Allah me nai na d'aga ma hankali mijina"

"Gashi kin d'auki pic tsirara kin turomin yana neman hanani bacci"

Wata y'ar k'arar kissa na saki nace "wayyo don Allah ka bar fad'i tunda haka ne
ma bari ni in goge ka daina kallona a haka"

"A'a wlh karki sake ki gogemin,nifa ma da wasa nake miki ina son Irin
wannan shigan sosai kinyi kyau Allah".

Dad'i naji na narke murya " Tom zanyi bacci".

"Um um baza kiyi ba ban gaji da hiran ba fa"

Sake gyara kwanciya nai nace "Tom ka bani lbr me dad'i kaji "

"Ni labarin da zan baki ko kin d'aga min hankali yanzu ji nake kamar ma in taho
gida"

"A'a wane irin ka dawo na kusa fa zuwa gunka"

"Tom ki shirya duk lokacin da kikazo ko hhhmmm"

Mirmishi kawai nai ina k'ara rungume pillow d'in don yanayin da yake magana duk
motsani yakeyi, maganganu yake ta sakar min masu tsuma zuciya,wata Kalmar inya
fad'a min saina runtse idona, kasa magana nake duk abinda yace sai dai ince um ko
um um don ko idona na kasa bud'ewa sabida na shiga cikin shauk'i,bamu tab'a yin
waya kamar ta yauba mun manta dare ne ma munyi soyayya mun cinye lokaci, saida naji
yana magana har bana iya gane abunda yake fad'i,nan kuma fa tunanin ya fara zuwar
min Kar muje muyita tayar wa da juna hankali kuma ya kasa control d'in kanshi ya
fad'a wani hali, saurin yin ta'awizi nai na kauda tunanin araina, saida muka
shafe sama da 2 hours sannan muka rabu, juyi naita yi a gadon ina jin yanayin na
dad'uwa gareni, kusan awa guda na sake shafewa a saman gadon cikin shauk'i sannan
na tashi na shige toilet na d'auro alwala, tsawon lokaci ina rok'on ubangiji ya
tsaremin mutuncin mijina ya kauda idonshi daga ko wace mace.

Bani na bar kan prayer mat d'in ba sai k'arfe biyu na dare na koma can d'akin,
sweety nata kwasar bacci nima idona cike yake taf da bacci na haye gadon tare da
addu'ar kwanciya bacci kafin wani D'an lokaci baccin ya jani.

Gobe Talata insha Allah ilahirin musulmin duniya ke sa ran ganin wata jama'a
nata shirye shirye haka muma a namu b'angaren duk gidan cike yake da kayan masarufi
wanda Abba yai order d'in su zai rabawa talakawa, ga y'an aiki da aka k'aro sosai
sabida girkin Abincin sadaka da akeyi ana kaiwa masallatai, ji nake kamar inyi me
don murna sai kace yau ne zan fara azumtar azimin ramadan,duk da nasan k'ark'ari in
an fara dani inyi d'aya ko biyu ya yanke min don ina gab da up.

Yauma haka muka raba dare muna waya sannan muka rabu, washe gari kuwa cikin
ikon Allah watan azumi ya bayya don haka kowa ya k'uduri niyar d'aukan azumi a
daran ranar.

Alhamdulillah mun shiga cikin ramadan don gashi yau Alhamis har ankai
d'aya,muna baje part d'in su sweety kamar yanda Abba yace Anan zamu rink'a shan
ruwa gaba d'aya a babban parlourn su,muna nan har aka kira sallar isha'i anan mukai
alwala muka fita harabar gidan don bin jam'i mu sami Asham kasancewar masallacin
na jikin gidan don haka matan unguwar da yawa suke shigowa bin salla a nan, sanda
muka hau sahu za'a tada sallar nan wani Irin nishad'i nakeji kamar yanda yake ga
duk cikakken musulmi in dai watan Ramadan ya kama to zaka zuciyar mutum tai wasai
nishad'i na saukar mai, hakan yau nakejin zuciyata cike fal da nishad'inishad'i

Tsawon lokaci aka idar da sallar kai tsaye part d'ina na wuce na d'auki
wayata yaya na haroon na kira muka gaisa na mai barka da shan ruwa sannan muka
gaisa da Aunty Hafsah, gida sakkwato ma nika iyayenmu duk nai musu barka da shan
ruwa na kira yayyaena sannan na kira Aunty Amrah itama mun dad'e muna hira bayan
mun gama toilet na shige nai wanka nai shirin bacci sannan na kira wayan ogan
muryanshi cikin yanayin bacci yake amsa sallamar da nake mai" precious ya kk"

"Lfy qlau ya ibada"

Jan numfashi yai sannan yace " mun kai azumi da k'yar shiyasa ina shan ruwa na
kwanta yanzuma kiran kine ya tashe ni".

Cikin mamaki nace " wai ko sallar isha'i baka samu ba balle Asham ?".

Cikin rashin damuwa yace "wlh banyi ba sabida nasha wahla sosai ina shan ruwa
bacci ya dauke ni".

" Ayya shed'an ne don karka samu ladan Sallar Asham na ranar farko na wata me
alfarma shine ya sa maka bacci, amma daurewa zaka rink'ayi ka bari sai kayi
sallar sannan ka kwanta kafin lokacin wayanmu yayi ko"

"Eh hakan zan runk'ayi precious amma fa ke sai naji kamar ma bikiyi azumin ba
muryan ki fes da ita "

D'an mirmishi nai "hhhmmmm nayi mana ai yanzu ana goman farko azumi bai bada
wahla kowa yana zumud'in sa, kuma ni azumi baya ban wahla sam "

D'an zaro ido yai yana fad'in " Ke kinsan wahalar azumi kuwa amma kice baya baki
wahla lalle ma"

Mamakin d'abiun sa nake mutum ne shi bamai kula da al'amuran addini ba,iya
salloli biyar d'inma da aka wajabta mai ba ko yaushe yake yinsu cikin jam'i ba
matsayin sa na namiji, yafi k'aunar yinsu cikin gida kuma harga Allah na tabbata
ba komai ya Sani na daga cikin k'aidojin sallar ba,amma in yana bin liman yau da
gobe zai fahimci komai ya k'ara ganin yanda ma sallar take, batun nafilfili kuwa
daman ba'a magana don innace ma yanayi nai k'arya, to gashi kuma anzo batun babbar
ibada me tarin falala da girma kuma ya fara gazawa daga yin d'aya ya fara fad'in
yasha wahla harya kasa yin sallar isha'i, lalle rayuwar mijina tana buk'atar
tallafi da kulawa ta fannin addini".

Muryanshi ce ta katse min tunanin dana tafi " meya faru naji kinyi shiru?".

"Hhhmmm ba komai ,Kaga mu kuwa bamu dad'e dayin sallar ba munbi jam'i a
masallaci wani irin nishad'i da farin ciki nakeyi yau d'in nan,kaima bari in barka
kayi sallar inka idar mayi wayan ko, kamin addu'a don Allah kaji ".

" ok to ba damuwa bani y'an mintina kad'an ma"

"A'a na baka awa guda ma kayi sallolinka kai addu'a oinka ka rok'a mana rahma da
dacewa wajan ubangiji".

" OK"

Bayan mun kashe wayan na kwanta lamo bisa gadon ina nazarin rayuwar
mijina,lokacin da Allah ya fara karkato min da hankalin sa gareni nake da damar
fahimtar dashi addini lokacin ne kuma yai nesa dani amma a hakan ma bazanyi k'asa a
gwiwa ba zanyi iya yina cikin hikima Irin tawa in rink'a nusar dashi addini sannan
zuwa ranar da Allah zai dawo dashi gida zan mik'e tsaye don bazan zauna ina kallon
mijina cikin duhun jahilci ba alhalin inada ilimin da zan tallafeshi dashi, duk sai
naji jikina ba fad'i zuciyata tamin rashin sukuni, tunowa danai da tsohon burina
nason Allah ya bani miji ma'abocin addini matuk'a nasha hasasho rayuwata ta gidan
aure tare da miji malami ina d'aukan darasi a wajan sa, amma sai gashi Allah yamin
canji da burina kuma na tabbata wannan shine alkairi na tunda kullum zab'i nake
bashi kan miji ba gari mafi alkairi sai gashi yamin zab'in kuma nasan akwai abunda
Allah Ke nufi da hakan,don haka zanci gaba da rungumar k'addarata sosai kuma na
k'ara godewa ubangiji na da bai barni da zab'in kaina ba, don ko yanda nakejin so
da k'aunar sa na dad'a shiga raina na tabbatar akwai hikimar ubangiji a cikin haka,
tunani kala kala naita yi har wajan 30 minutes naji kiran sa, da wani salon na
k'ara zuwar mai wanda shima ya rink'a narke min tamkar wani D'an jinjiri,kamar ko
yaushe mun dad'e cikin birnin masoya sannan muka rabu, alwala na d'auro nazo na
tada salla don na k'ara d'aura d'amara kan yiwa mijina addu'a musamman cikin wannan
watan,ina rok'on ubangiji ya k'ara tabbatar da alkairi cikin auranmu sannan ya
sanya sona da k'aunata cikin zuciyar sa kamar yanda nasa ya d'arsu cikin nawa.
Yau kam kamar yanda na tabbatar banda rabon yin azumi hakan kuwa don muna
tashi yin sahur na tadda bak'ona yazo don haka ma banyi ba na koma bacci na bakina
d'auke da zikiri.

Bayan munsha ruwa gun Abba mun d"an tab'a hira na mik'e tunda nasan bazanyi
salla ba part d'ina na wuce na kira wayan mijina kam da d'an k'arfinsa naji shi
bayan mun gaisawa nai mai barka da shan ruwa nake tambayarsa su sunyi salla tuni ko
dariya yai yace "Tun tuni ma mun manta munyi salla yau banyi bacci ba saida nai
salla kuma yanzu fa nake shirin na d'anyi bacci ko na awa guda ne kafin muyi
wayan"

"Um yau na kiraka da wuri ko"

"Kun idar da sallar ne kuma"

"A'a yanzu ma dai naji an fara raka'ar farko "

"OK to je kiyi Kar a wuceki"

D'an mirmishi nai cikin yin k'asa da murya nace "ni yau bazanyi ba"

"Meyasa baza kiyi ba".

Shiru nai ina d'an mirmishi k'asa k'asa ,


Ya sake cewa " ko kin gaji yau?"

"Hhhmmm ai gajiya bata hana salla ko"

D'an mirmishi yai don ya gano inda ta nufa kuma cikin tsokana yace
"Ohh Ashe yau Ke gandiya ce "

Mirginawa nai akan gadon ina dariya k'asa k'asa nace "waye yacema ni gandiya ce ,ai
yara ne suke shan azumi ni kuwa babba ce ko"

Dariya yai sosai sannan yace "eh yara suna shan azumi sannan ma mata irinki suna
sha kamar yanda kema yau daga yin d'aya kika b'ule".

Wayyo Allah kunya kamar yana kallona na runtse idona cikin tsananin kunya da
shagwab'a na fara fad'in" Allah Allah nidai ka daina ban so "

Dariyar sa yake son ransa yace "meye bakya so gaskiya fa na fad'a Ke d'in yau ba
magana zanwa Abba ma waya in fad'a mai karma ya k'ara damuwa kizo gunsa shan ruwa
don kina shan abunki da rana"

"Wayyo Allah ka bari so kake ka kasheni da kunya ko nidai Allah ban so ".
Sheshshek'ar kukan wasa na farayi araina ina tunanin rayuwa irinta gidan zai fa
iya sanarwa Abba wai wlh dana shiga uku,

Wutar duk da take aiki a jikinsa ce ta d'auke don kukan kissar da nakeyi ya
tab'a ko ina na jikinsa, nan da nan yaji an fara mintsinin shi, muryarshi ya k'ara
narkewa yace " yi shiru yi shiru my precious wasa fa nake miki, bazan fad'a mai ba
,ai nasan ko wace mace ma tanayi ko ".

" um kowa yanayi bani kad'ai bace".

K'ara kyalk'ylewa yai da dariya sosai yace "a'a wlh badai kowa da kowa yana yiba
iya Ku iku mata ne kukeyi mu bamayi maza ".
Ya k'arashe maganar yana k'ara k'yalk'yala dariya.

Jin dariyan tashi tak'i k'arewa yasa na kashe wayan ina turo baki, kira ya
k'arayi nak'i d'auka sau uku yana kira sai da ya turo tex yana rok'ona in d'aga ya
daina dariyan,
D'an mirmishi nai sanda kiran ya sake shigowa na d'aga jinsa nai ya kashe murya
sosai cikin salon shagwab'anshi yace " precious "

"Um" kawai nace

Jin yanda na amsa Kawai naji ya k'ara k'yalk'yalewa da dariya, maimakon inji
haushi kawai nima sai na saki dariyan ina cewa " wai dariyan me kake min Allah ka
daina" na k'arashe Nima ina dariyan, sai yai mai isarsa sannan ta tsagaita yana
cewa "kin san meke bani dariya ?".

" um na sani mana ni kakewa dariya "

"A'a wlh bake nakewa ba wani labari zan baki "

"Tom bani ina ji"

"Kina ji lokacin da muna secondary school ne akwai wata yarinya a ajinmu sunan ta
Deborah muna soyayya da ita a lokacin, bata san mata suna wannan abun ba ranar mun
fito break muna zaune reception muna cin abinci da ita munata soyewar mu sai aka
koma class tana tashi zamu tafi kawai sai naga jini a gun data tashi da sauri
nace" Mene ne wannan a k'asanki"

Cikin kid'imewa take kallon jinin daya b'ata kujerar data zauna ai kuwa tasa
hannu aka ta fara ihu nima na rikice don lokacin ban san meye ba, na rik'e ta
tana kuka nima ina kuka don tunani na wani abune ya fashe a jikinta jinin Ke fita
haka, muna wannan halin wata Auntyn mu tazo wucewa ganin halin da muke ciki yasa ta
tsaya tana tambayar mu meya faru a tare muka shiga nuna mata inda jinin ya b'ata
munayi muna kuka, fahimtar datai bamu san meye ba yasa,tamo hannunta tace ni in
wuce class taje da ita staff room ni kuwa dana tafi aji na kasa komai haka na
kwantar da kaina kan des inata d'an kuka na ina tunanin shikenan Deborah ta wani
ciwon ya sameta maybe ma mutuwa zatai haka na k'arasa zamana a class har aka tashi
bata dawo aji ba, kamar had'in baki ranar muna zuwa islamiyya lokacin bamu fara
gudun islamiyya ba sai wata yarinya a ajinmu taiwa ya sayyadi tambaya kan wani
karatu da yake mana a lokacin na manta dai tambayar datai mai amma nasan kan abun
ne,to a ranar ne naji bayani kan abun don yanda yaketa mata bayani sosai na rik'e
abun a raina, to a ranar nasan meye wannan jinin, shiyasa duk randa na tuna shirmen
da mukai da Deborah sai naci dariya na k'oshi".

Ya k'arasa maganar yana wata dariyar ,nima dariya sosai nace "lalle ansha kunya
kenan,kuma data zo school washe gari bataji kunyar ka ba?".

" Ke su arna meya damesu da wata kunya,da tazo ma ni na k'ara mata bayani akan
abun, kin san me nifa duk a karatun da ake mana a islamiyya babu abunda ya tab'a
zama akaina Irin wannan shima kuma don anyi karatun ne a lokacin nake buk'atar
Neman Sani akan sa,sabida inaji da Deborah fargabata Kar inje wani ciwon ne ya
sameta".
Wani haushi ne naji ya turnik'eni danaji yace yanaji da Deborah d'in sa don
haka na had'e raina nace "um wato kanaji da ita ko, lalle kuwa".

" hhhmmm Ke nifa ban tab'a jin yarinyar data ratsa raina Irin Deborah ba don
yarinyar akwai masifar brain ga aji komai nata me aji ne shiyasa nakeji da ita".

Jinai wani kishi ya taso min ya tsaya a k'irjina,don haka cikin dasashshiyar
murya nace"Tom bari in kwanta ko"

"Ban gane ki kwanta ba tun yanzu,meya faru naji muryanki ta canja".

" ba komai "

Sai a sannan ya gano tabargazarda yayi don haka ya sassauta muryanshi yace
"precious Kar kisa wani abu aranki fa, tsohon zance fa nake miki ni yanzu ma wlh
ban san duniyar da Deborah take ba,don muna gama secondary suka koma garin su".

Sai a sannan naji d'an sanyi ya ratsani na saki raina mukaci gaba da hiranmu
cikin nishad'i.

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣8⃣
0⃣3⃣8⃣ 0⃣3⃣8⃣

Haka akaci gaba da gudanar da ibadar azumin Ramada cikin kwanciyar hankali , har
yau ankai goma, Abba yayi matuk'ar k'ok'ari don kayan Abinci ya had'a bana wasa ba
ya aika dasu can gidan mu sakkwato yace inji mijina, haka akaita rabawa y'an uwa
na kusa da nesa tare da abokan arzik'i, sannan yasa turaman atamfaofi da yawa yace
nasu umma da mama sauran na y'an uwa, Haka ma anan kano Ya aikawa yaya haroon kayan
abinci bana wasa ba haka ma yaya Usman sannan yasa turaman atamfofi na Aunty Hafsa
da Aunty Amrah suma su Yayan harda shaddodi, gaskiya Abba yayi k'ok'ari, waya tako
ina aka rink'a kirana anamin godiya wai sunga kaya inji mijina sun gode, nikam sai
dai inyi mirmishi kawai.

A daran ranar Abban ya kiramu nida sweety bayan munyi sallar Asham ya bamu
kud'i wai na kayan sallar mu ne in zamu k'aro, ga Atamfofi da shaddodi yace mu
d'auki iya yanda muke so, godiya nikam nai tayi yace "ba komai ai hakki nane"

Bayan kwana biyu ma saiga transfer kud'i daga Uk 100k wai inyi hidimar salla nace
Abba ya mana komai, amma yace babu ruwan sa da kud'in Abba wannan kyautar shi ce
tsakaninmu wannan kuma hakkin sane ya dole yayi min, nikam godiya nai tayi ina mai
addu'a, a ranar nake tambayarsa zanje in yiwa su yaya na barka da shan ruwa, yace
to ba matsala, washe gari da safe kuwa na tafi gida bayan na tsaya na saiwa su
Ashraf wasu tsada tsadan kaya riga da wando wando masu masifar kyau da tsada
kowanne kala biyu, sanda naje gidan kuwa murna kamar sayi me, bayan mun gaggaisa
na sami nutsuwa nan na fito da kayan na basu sukaita murna, a gida nasha ruwa naje
nawa su yaya usman ma barka da shan ruwa sai bayan sallar Asham sannan na koma gida
a mota ta dake da ita na tafi.

Kwanaki nata gudu azumi nayin nisa yayinda muka k'ara k'aimi wajan bautar
Allah da addu'oi,kullum in zanyi addu'a ta saina rok'i ubangiji shiriyar sa ga
mijina da kuma k'ara neman alkairi cikin zamanmu, wanda kullum kuwa ina ganin canji
na k'aruwa a zamantakewar mu.

A haka muka kammala azumi mukayi sallar idi cikin kwanciyar hankali da farin
ciki, bisa umarnin da Abba ya bashi yace inje sakkwato inyi kwana hud'u don in
gaida iyaye da y'an uwa,hakan yamin dad'i matuk'a ranar da na sanar da yaya nah
Haroon yace ai suma sunyi shirin tafiya harda yaya usman da matarsa don haka muka
rankaya ranar biyu ga salla mukai gida sakkwato, nayi tsaraba sosai kasancewar
shine zuwa na farko tun bayan aurena,gashi Abba ya cikani da kud'i haka shima Uk ya
turomin 50k yace inyi tsaraba, na zaga dangi sosai cikin kwana hud'un nan kuma Duk
inda naje zan musu alkairi, badan naso ba na dawo son su yaya acan na barsu tunda
mu muna tsakiyar semester don hutun sati d'aya kawai aka bamu, randa na dawo washe
gari aka koma school amma banje ba sabida gajiya ga gyare gyare Dana d'anyi.

*************
Haka rayuwa taci gaba da gudana yai da dad'i gobe babu,amma nikam a fanni na
sai dai nace masha Allah don yanzu anzo matakin ma da na daina kiran uk a waya sai
dai shi ya kirani wata irin kulawa nake samu daga gareshi,abunda na tabbatar
addu'ar da nakeyi dare da rana Allah yana amsamin tunda gashi kullum gari ya waye
da sabon salon k'aunar da zan samu daga gareshi,yanzu bama sai iya dare ba koda
rana yaso jin muryata zai kirani sai dai bama wani dad'ewa da dare ne dai sai mun
manta ma a waya muke sannan muke hak'ura mu rabu da juna.

**************
Yana kwance saman d'an madaidaicin Royal bed d'insa bayan gama wayar
su,tunanin yake cikin ransa shin wai meke damun sa ne kan wannan yarinyar, shikam
abun har mamaki yake bashi yana rasa yaushe kuma ta ina ya fad'a tarkon k'aunar
ta,shida yasan wayar gari kawai yayi ya ganshi tsamo tsamo cikin tafkin k'auna
wanda har yake shiga damuwa in baiji muryar taba, yanzu Nazo matakin da yake kasa
rintsawa sabida tunani da begenta,duk dare in sukai waya tafiya take ta barshi da
begenta, gashi shi bamai yawon sha'awa bane amma dayaji muryan ta sai yaji hankalin
sa ya fara gushewa nan da nan za'a sakar mai da notinan sa yaita mata sambatu yana
fad'in abunda bai san ma yana fad'a ba, wani sa'in in suka gama waya ma sai yai
wanka don jinsa yake sharkaf ya jik'e, amma fa dake d'an duniya ne har yanzu yak'i
barin hanyar da wani zai gane tsananin su,cikin abokansa tunda sun san ba son auran
yake ba shiyasa yanzu ma bai bari su fahimci ya fad'a tarkon k'auna ba, yanzu
Fadlah ma Sama Sama yake da ita, ko gidanshi yanzu bai bari tana shigowa sosai inma
ta shigo bai wani sakar mata fuska, ta tambayeshi ta tambayeshi kan ya fad'a mata
lefinta amma amsar d'aya ce yace ba komai,

Yau ina kwance banjin dad'i kwata kwata ko school banje ba, kiran wayar
sa ya shigo wayata na d'aga muryata can k'asa me cike da alamar rashin lafiya
tattare dani, "Mata ta "

"Na'am miji na,barka da dare "


Na amsa mai,
"Ya naji muryanki wani iri ko gajiya ne"

"Um um wlh banjin dad'i ne tun safe"

"Oh my God meke damun ki"

D'an jan numfashi nai nace " mura da ciwon kai ne kawai"

Da sauri yace " Wane Irin kawai mura da ciwon kai ba kawai bane ai, kinsha magani
amma"

Shagwab'e murya nai nace " um um ni banson magani "

Marairecewa yai kamar zai kuka yace " ki taimaka min kisha magani kinji Baby
nah, Kar zazzab'i kuma ya kamaki daga mura".
"Bubbuga k'afa na farayi ina D'an kukan shagwab'a nake fad'in" nidai ban so
ban son magani da akwai d'aci fa".

"K'ara k'asa yai da muryanshi yace" Khadeeeeejahhh"

Wani shockkkkk naji ya kamani jin yanda yaja sunan nawa nace "um mijinahhhh"

"Kina son farin cikina?"


" farin cikin ka shine nawa ai "

"Tom in dai haka ne ki daure don Allah kisha maganin kinji zakifi jin k'warin
jikin ki Kinga saimu fi jin dad'in yin wayar ko".

" Tom amma fa kad'an zan sha kaji"

D'an mirmishi yai yace "eh na yarda kisha kad'an d'in ma"

"Tom ka jirani minti biyu zanje insha". Bayan na fad'a na kashe wayan na tashi
zuwa parlour don samo maganin, a nan na tadda sweety tana kallo tace " yadai
Aunty na me kike buk'ata"

Zama nai gefen ta ina fad'in "wlh Yayan ki ne ya takurani sai nasha magani
shiyasa na fito insha D'an kad'an"

Dariya tasa tana fad'in "ai daman nasan shi zai saki kisha amma tun d'azu nake
miki magiya kisha don Allah kink'i yanzu kyasha don dole ai"

Tashi nai zuwa fridge na d'auko ruwa ina cewa "baki da amsa yanzu don cikin
lokacin mijina nake amma ki bari anjima zamu had'u"

Tanata tsokana ta ban kulata ba nasha maganin da k'yar na koma d'akin,

Duk yanda nakejin kaina kamar zai fashe haka na daure nake k'arfafa kaina mukaci
gaba da wayan,bamu dad'e ba mukai sallama.

***********
Tafiya sosai lokaci yayi wanda yanzu ya rage saura sati guda mu kammala exams
d'in mu da muka fara sati biyu daya wuce, duka yanzu hankalina naga shirye shiryen
tafiya India ga mijina, shiri sosai nakeyi , gyaran jiki kusan kwana goma aka
fara min wata k'wararriyar mata Maman boy ta had'a ni da ita take min gyaran jiki
kasancewar da wuri muke gama exam son kullum d'aya mukeyi don haka ana tashi gidan
matar nake wucewa, iya kwana goman da aka fara gyaran na canja matuk'a nayi wani
haske amma ba Irin d'au d'in nan ba,kasancewata bak'a yasa sai fatata tai wani
brown color taita shek'i da d'aukan ido,ga wani k'amshi na musamman wanda Duk inda
na motsa sai kaji k'anshin,ko fitsari nai maimakon zarnin fitsarin sai dai k'amshin
miski da wani asirtaccen k'amshi Ke tashi, batun tsimi kuwa ya riga ya zama ruwan
sha na, shiri nakewa can jikina matuk'a don nasan yanda muka afka k'aunar junan mu
yanzu babu abunda zai hana mu cure mu zama abu guda yanzu, don haka nake mai
tanadin kaina na musamman, gashi me gyaran jikin nawa ma tanata tsumani da nata
tanadin, bayan wanda nakeyi da kaina,kamar yanda duk wani wanda yasan matan
sakkwato ya sansu da gyara da tsimi.

Tunda Abba yace mai mun kusa zuwa mai ziyara ya k'ara rikid'ewa da rigima,
ranar muna waya yake tambayata wai ranar yaushe zamu taho na k'ank'ance murya
cikin tsokana nace "kai dai daga nan zuwa sati guda kaita tsammanin mu don nima
ban san ranar da zamu taho ba amma dai an gama komai na shirin tafiyar".

" wlh ko precious duk na matsu kizo don na gaji da zaman gauran cin nan da matata
da komai ina kwana cikin yunwa"
Y'ar dariya nai "Meyasa kake kwana da yunwa baka samun abinci ne?"

Na fad'a kamar ban san inda ya nufa ba,


Cikin muryan shauk'i yace "Bana yunwar Abinci bana yunwar ruwa yunwarki kawai
nakeyi"

"Ummmm daman ana yunwar mutum ne"

"Hhhmmm ko ba'ayi nidai ina yunwar ki dare da rana kullum burina inga ranar da
zan kauda wannan yunwar tare dani".

" hhhhmmmm karka damu saura k'iris mu had'u duk yunwa da k'ishin ruwar ka zan
kauda ma dasu kaji miji na gari".

"Yawwwa my precious kinyi alk'awari ko?"

"Hhhmmm karka damu kaji"

"Tom wlh ki shirya banda raki banda ragwanta "

Mirmishi kawai nai ban k'ara cewa komai ba, haka yaci gaba da jifana da kalamai
masu sanyi da dad'i har sama da awa biyu,muka rabu.
Rana bata k'arya inji masu iya magana gashi yau ya rage kwana d'aya tal jirginmu
ya tashi zuwa India, ina zaune gaban akwatina wanda na gama cikashi tsaf da kayan
da zan buk'ata na tsawon sati shida, d'ayan akawatin kuwa kayan shafa ne da
turaruka dangin su Humra kwalakca dasu lobelia, Duk wani abun k'amshi wanda ya amsa
sunanshi me k'amshi da mata ke amfani dashi na tanadeshi, banyi gigin d'aukan wasu
kayan maganin mata ba,nasan iya abunda nai amfani dashi yanzu ajikina ya isa min
aiki har tsawon watanni, duk da bawai wani tarkacen shirme nasha ba wanda nasan zai
tafi da tsarina dai dai nai amfani dasu, kayan fruit kuwa daman mutane nane namusu
shan kaca suma, tunani nake meye ban had'a ba na tabbatar komai ya zama ready,
kaina yasha kitson gana wanda aka mai d'iba na iyawa kasancewar inada cikar gashi
sosai yasa kitson ya zauna akaina kamar an dasa hula jelar gashin kuwa tana zube a
kafad'una yar yar da ita, sai hannuwana da k'afafu sun sha k'unshi ha da bak'i
koda nake bak'ar fata hakan bai hana bak'in kunshi yimin matuk'ar kyau don bak'ina
me kyaune kuma ba can sosai bane bak'in.

Sweety ce ta shigo tana fad'amin kiran Abba, nasa hijab d'ina nabi
bayanta, a saman cafet na sameshi zaune bayan na gaisheshi ya amsa cikin fara'a
"Khadeejah ya shirye shiryen"

Cikin d'an jin kunya nace " Alhamdulillah "

"Tom daman na kiraki ne in shaida miki yanzu agent d'in jirgin da zamu bi yake
sanar dani an samu sauyin yanayin tashin jirgin daga karfe hud'u na yamma zuwa tara
na safe don haka saiki zama cikin shiri suk inda takwas tai ace kina ready kinji"

Kaina a k'asa cikin jin nauyi nace "To Abba Allah ya kaimu "

Ya amsa da "Amin"
Sannan yace Inje inci gaba da shiri da nake.

Bayan na gama Duk abunda nake nazo kwanciya na d'auki waya ta tarin Miss
call d'inshi na tarar ban san ya akaiba wayan ta shiga silent ga Miss call nan
kusan goma, nabishi yak'i d'agawa inata kira amma fir yak'i d'agawa na tabbata
fishi yai mirmishi nai araina ina tunanin daya san gobe zamu dirar mai dabai
k'irk'iri fishi ba don Abba yak'i sanar mai takamai mai ranar da zamu zo kawai dai
yace ya zama cikin shirin ganin mu cikin satin, don so yake yai surprise
d'insa,ganin yak'i d'agawa yasa na kashe wayan na sata a charge kawai dana duba
ogogo k'arfe sha biyu saura don haka na d'aura alwala na fara nafilfili har zuwa
d'aya saura sannan na kwanta.

*Munyi* *zab'e* *mun* *zab'i* *zab'inmu* , *Amma* *Allah* *zab'inka* *muke*


*nema* *Allah* *kai* *mana* *zab'i* *na* *gari* *karka* *barmu* *da* *zab'in*
*ranmu* *Allah* *ka* *bamu* *shugabanni* *na* *gari.*👏👏👏

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣3⃣9⃣
0⃣3⃣9⃣ 0⃣3⃣9⃣

*ALLAH* *KA* *IYA* *MANA* *DA* *IYAWAR* *KA* , *ALLAH* *KAGA* *HALIN* *DA*
*JIHATA* *TAKE* *CIKI* , *ALLAH* *KARKA* *BAR* *AZZALUMAI* *SUYI* *TASIRI*
*AKANMU* .
👏👏👏👏👏👏👏

Tunda nai sallar asuba na shiga kitchen don samin abunda zanyi break kafin mu wuce,
na d'ora kenan sweety ta shigo kitchen tace" Aunty na jeki fara shiri bari inyi
girkin"

Wucewa nai bedroom na cire kaya na shige toilet, wanka na silla iya wanka kamar
wanda na kwana goma banyi ba, bayan na fito nazo na jik'a jikina da turaruka masu
d'aukan magana, a nutse nake shirina, ba wata doguwar Kwalliya nai ba powder na
shafawa fuskata wadda tai wani fayau tai kyau sabida gyaran jikin Dana sha,sannan
na shafa Lipstick fari na k'ara gyara gashin idona da maskara sannan nasa brush
na gyara cikakkiyar girata na saita kamar naja gira, wata y'ar bala'in doguwar
riga nasa bak'a kirar Dubai me tarin duwatsu a gaban k'irjin wanda yake daidai
jikina Sai k'asanta da yake a bud'e sosai nasa hills takalmi shima bak'i nai
rolling kaina da mayafin rigar, y'ar jaka bak'a na d'auka a hannuna na fito
parlour lokacin bakwai harta wuce, samun sweety nai tanata gyaran gidan harta
gama had'a mana break fast d'in, da fara'a kan fuskata nace " wayyo y'ar uwa ns
barki da aiki ko"

Mirmishi tai duk jikinta a sanyaye tace "Har kin shirya ga break d'in can na
jiranki bari inyi sauri inyi wanka kafin ki gama".
D'aki ta shige da gudugudu ni kuma na k'arasa dining na fara had'a abunda zanci.

********
K'arfe takwas da rabi muna filin tashi da saukar jiragen Mlm Aminu kano, Yan
rakiyarmu Aunty murjah,sweety, salis da Autansu Hisham, naso yaya na yazo amma
yace tunda nazo dai munyi sallama shikenan basai sunmin rakiya ba, duk muna
zazzaune muna jiran a fara kiran fasinjoji, nida sweety muna d'an hira tana fad'a
min zatayi kewana tsawon kwanakin da zanyi ,nima nace mata zanyi kewarta,y'ar
dariya tai tace " kina tare da mijinki yaushe zakiyi wani kewana" duka nakai mata a
kafad'a ina dan dariya nace "Ke ko hhhmmm"

A lokacin aka fara kiran fasinjojin nan muka mik'e Abba yai musu sallama nima
sallama nakewa Aunty murjah sannan na rik'o hannun sweety nace "Sis sai na dawo?"

Rungume ni tai tana min rad'a a kunne"kiyi k'ok'ari ki dawo mana da baby "

Janyewa nai da sauri ina hararanta Abba yace " muje Khadeejah".

Jawo jakata nai nabi bayansa ina d'aga musu hannu.

Muna shiga Abban ya gamu da abokinsa da yayansa bayan mun gaisa yace in zauna
kusa dasu shi kuma ya zauna tare da abokin Nasa, bayan jirgi ya lulu bakina
d'auke da addu'a karon farko dana fara shiga jirgi a rayuwata,amma ban nuna komai
tare dani ba,muka shiga hira da Yayan nasa masu D'an karen surutu nidai harna gaji
naja bakina nai shiru.

******
Dai dai k'ofar wani d'an k'aramin gida motar data d'auko mu daga filin jirgi
bayan driver yayi parking muka fito muna fitar da jakunkunanmu.

Sau biyu Abba yana k'wank'wasa k'ofar akazo aka bud'e, tsayawa kawai yai
cikin wani matsanancin farin ciki ya kama baki yana fad'in "Abba nah"

Dariya Abban yai yace "na'am Daddy nah "

Jakan hannun Abban ya amsa yana wucewa gaba muka bishi duk farin ciki ya
cikashi Abba ya zauna kan kujera ni kuwa k'asa kan kafet na samu na zauna da sauri
Abba yace "A'a tashi ki zauna Sama mana Khadeejah nace ki daina irin haka "

Girgiza kai nai cike dajin kunya nace "a'a Abba nan ma yayi "

Dawowa yai d'auke da lemo da ruwa kan plat ya ajiye yana zaunawa yace "Abba
Kunyi surprise d'ina wlh, Sannun Ku da zuwa ya hanya"

Cikin fara'a da murna suka gaisa da Abban, ni kuwa cikin kunya na gaidashi ya
amsa yana tsareni da idanuwan sa yace " Sannunki da hanya,ki tashi ki hau kujera
mana kika zauna k'asa"

Girgiza kai nai kawai bance komai ba, sai Abba daya ajiye cup d'in d'aya sha
lemo ne yace"Ai bazata zauna ba,kullum haka muke fama da ita tak'i sakin jikinta".

Kad'a kai kawai yai yana D'an mirmishi, idon sa k'yar akaina, duba agogo yai
yace "Abba bari inyi muku order na abinci "
"Mirmishi Abban yai yace ai naga ma lokacin sallar azahar yayi ko?"

Duba ogogon nai naga k'arfe biyu na ranar su,

Abba yace "Muje masallaci muyi salla sai muci abincin ko?"

Mik'ewa yai ya shiga d'akin yai alwala sannan ya sako doguwar riga kan tree
quarter d'in wandon dake jikinsa,Abba ma shiga d'akin yai kasancewar d'aki d'aya ne
kawai a gidan kuma a ciki toilet d'in yake,sai palour da D'an k'aramin kitchen,
bayan fitarsu masallaci na tashi na shiga d'akin nima don Yin sallar, ina zaune
kan prayer mat ina addu'a ya shigo d'akin jingina yai da jikin k'ofa ya hard'e
hannayensa yana kallona, sarai ina kallon shi ta gefan idona,nai kamar ban ganshiba
naci gaba da addu'a ta,a hankali ya tako zuwa gabana ya tsugunna tana lek'a idona,
shafawa a hankali na kalleshi da sauri nai k'asa da idona sabida wani kwarjini
daya min,rik'o hannuna yai yana D'an mirmishi yace "Ki taso ga abinci can na
jiranki, " To nace idona na kallon gefe.

Sanda muka fito parlourn har Abba ya fara cin abincin da aka kawo daga gidan
abinci da sukai order,
Cikin jin kunya na samu gefe na zauna,da kansa ya d'auki plat ya zuba min tare
da turowa gabana, jan abinci nai gabana ina D'an tsakura don duk kunya ta rufeni,
ba jimawa Abba ya mik'e yace "Daddy bari in tafi masaukina inaga sai zuwa gobe kuma
zan dawo kuma insha Allah jibi zan juya".

Cikin marairecewa yace " Ah haba Abba wai da gaske kwana biyun zakai?"

D'an dariya yai yace "To ai dama nace ma rakiya nayowa Khadeejah insha Allah
kuwa jibi zan juya kasan dai tarin sabgogin dake gabana".

Shima mik'ewa yai yace " To Abba bari in rakaka".

Saurin dakatar dashi yai yana fad'in "a'a zauna abunka ma had'u gobe".

Dagewa yai sai ya raka Abban, don ce mai yau shima zai D'an tsaya yayi siyayya
don haka ya barshi,suka tafi tare yana cemin " To Khadeejah sai gobe ko".

Kaina a k'asa nace "To Abba Allah ya kaimu".

Fita sukai suka sami motan haya suka hau zuwa hotel d'in da Abba zai sauka, saida
suka gama komai ya shigar mai da y'ar jakarsa d'akin sannan yamai sallama ya
taho,kasuwa ya wuce kai tsaye don yin siyayyar abubuwan ciye ciye dana buk'ata.

Ni kuwa bayan fitar su na saki jiki naci abincin sannan na gyara gun naje
kitchen na wanke plats din na ajiyesu inda naga sauran, dawowa nai ina tunanin
wanka zanyi ko in jira ya dawo tukun, wani tunani nai don haka da sauri na tashi na
shige toilet d'in da sauri sauri nai wankan, na fito cikin sauri na bud'e jakata
na Ciro kaya nasa bayan na goge jikina da turaruka, Sama Sama nai Kwalliya na dawo
parlourn na zauna ina kunna T.V....

K'aran k'ararrawa naji alamun son shigowa, k'ara dannawa akai ,a hankali na tashi
naje na bud'e k'ofan,yana tsaye hannunsa d'auke da ledoji, hannu na mik'a zan amsa
ina mai sannu da zuwa,girgiza kai yai yana dariya yace " a'a bazan baki kayaba daga
zuwanki rufo k'ofar dai , rufo k'ofan nai na biyo bayansa, a tsakiyan parlourn ya
ajiye kayan a sanda na k'araso a hankali ya bud'e hannayensa alaman in shiga
ciki,rufe idona nai da hannayena da suka sha rantsatstsan k'unshi, taku uku yai ya
k'araso gareni gaba d'aya naji ya sanyani cikin jikinsa . . . . .

Ayi hak'uri da wannan zamu had'u gobe da yardar Allah.

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣4⃣0⃣
0⃣4⃣0⃣ 0⃣4⃣0⃣

Mirmishi nai kawai kaina a k'asa, rik'o hannayena yai cikin miryan rad'a yake
fad'in " nayi farin ciki da zuwanki my Khadeejah, Abba nah ya faranta min rai
matuk'a, amma ke gashi kin kasa nuna min farin cikin ki".

D'ago idanuwa nai na yarfa wani asirtaccen kallo wanda shi kad'ai ya isa ya
tabbatar mai da farin cikin dake tare dani,cikin muryan shagwab'a nace" kaima kasan
nayi farin ciki sosai ai".

Baki na ya zubawa ido a hankali yakai lab'b'ansa saman nawa yana gogawa
laushi da taushin da leb'e na ke dashi ya k'ara bashi damar lasar su, lumshe idona
na k'ara yi ina jin wani farin ciki yana saukar min yanda da gaske nake hangon
tsantsan k'aunata cikin k'wayar idonsa, ganin abin yak'i k'arewa yasa a hankali na
kamo hannunsa ina D'an janyewa, bud'e idonsa yai yana mirmishi nima mayar mai da
mirmishin, "me yasa kikayi wanka biki jirani na dawo ba, kin manta tsarin da mukai
wa junan mu duk randa muka had'u komai namu zai zama d'aya, cinmu shanmu kwanciyar
mu da duk wani motsinmu ko?"

Juya idona nai farrr ina D'an zaro shi nace "a'a ai ba tun yau za'a fara ba, ni
bakuwa cefa".

Dariya ma abun ya bashi yace " wlh ba wani bakuwa kwanakinmu a k'iyaste suke don
haka zamuyi amfani da damar mu mu morewa juna" ya k'arasa cikin y'ar dariya yana
lek'a fuskata ,kauda kaina nai gefe ina mirmishi na mik'e ina fad'in " bari insa
kayan nan a kitchen ko"

Shima mik'ewan yayi yana fad'in "eh fito dasu daga ledan akwai fruits a ciki"

Duddubawa nai na ajiye komai a mazauninsa cikin kitchen d'in duk da ba wani
babba ne ba kuma ba wani kayan amfani sosai a ciki daga tukwane biyu sai food flast
set d'aya tea flast d'aya sai flats 12 Peace's da cups,spoons da dai D'an sauran
robobin amfani, D'an dariya nai cikin raina nace "hhhmmm kitchen d'in maza kenan"

Bayan na fito na sameshi tsaye yana balle rigansa,a hankali na k'araso gabanshi
ina tayashi b'allewa, kallona yake cikin mirmishi yace "zanyi wanka nima" gaba na
wuce zuwa toilet d'in na had'a mishi ruwa a k'ofan da zan fito shi kuma zai shigo
yasa hannayenshi ya rik'o ni yana kashe min ido, shagwab'e fuska nai nace " Kayi
wankan ka fito tukun"

Shima shagwab'ewan yai yana nok'e kafad'a yace "um um ni kizo ki tayani "

K'ara yin ciki yake dani zuwa toilet d'in na fara bubbuga k'afa ina tuttureshi,
jijjiga jikin da nake ya k'ara bashi daman morewa kallon wajen da yafi d'aukan
hankalinsa matuk'a, ganin danai ya zubawa k'irjina ido yasa dabara ta fad'o min
nace "To duba ruwan kaga ya maka dai dai sai in tayaka"

Mirmishi yai yace "yawwa ko k'ofa Baby nah"


Ya juya zuwa bathtub d'in, ina ganin ya juya na juya nima da gudu na fice ina
rufomai k'ofan ina dariya,
Bin k'ofan yai da kallo yana mirmishi yace "lalle yarinyar nan wato wayo taimin
kenan hhhmmm".

Ni kuwa d'akin na k'ara gyarawa sosai na d'auko turare cikin kayana na feshe d'akin
dashi,sannan na duba cikin kayanshi naga wani bedsheets d'in na d'auko nasa shi na
cire wancan d'in, kaya na d'auko mai mara nauyi na ajiye, duba agogo nai naga
k'arfe hud'u don haka yana fitowa naga ya tunkaroni yana gyad'a kai alaman zan
kamaki, D'an dariya nai nace"bari inyi alwala lokacin salla yayi"
Nima banyi ba ai muje muyi, ja baya nai nace "To yi ka fito sai inyi "

Damko hannuna yai yace "lalle yarinyar nan wai guduna ma kikeyi ne kome? To muje
tare zamuyi"

Binsa nai ina D'an dariya k'asa k'asa, muna shiga toilet d'in na D'an sha mur na
nufi sink na fara alwalan duk tab'a nin da yake nak'i sa abun a jikina,ganin da
yai na basar ya cafkoni gaba d'aya yana had'a ni sa bango yai min wata matsa har
saida na saki y'ar k'ara nace "wasshhh my hubby zaka ballani"

Bakinsa ya zura cikin nawa da zafi zafi ya shiga kissing d'ina tako ina,tun ina
kauda kai har jikina ya saki na fara mayar mai da martani a take nutsuwa ta fara
barin jikin mu,tun ina maida mai martani a sanyaye nima na shiga mai da sauri
sauri,jin hannunsa yana yawo cikin rigata zuwa k'asa yasa na fara tuno fa a
toilet muke kuma alwala ma na shigoyi, bakina na zare cikin nasa ina rad'a mai
cikin kunne "lokacin salla zai fita fa"

Idonsa a lumshe yace "To madam ai kece kika jawo duk kin rud'ani"

Cikin jin kunya na murmusa ina ficewa a toilet d'in nace "kayi alwalan inka fito
nima sai inyi"

Bayan na fita na jingina jikin bango ina maida numfashi, lalle yau babu
makawa zan murzu don yanda naga maita k'ara ra idon sa, ina nan tsaye ya fito ban
bari ko ido mun had'a ba na shige toilet d'in nima.

***********
Bayan sallar isha'i muna zaune kan kujera Guda yanata faman nanik'ata mirmishi
kawai nake ina yanka mana fruits a hankali yakesa hannu yana d'auka zuwa bakin
sa,cikin yanayi me jan hanlali na zuba mai ido,shima idonsa ya sanya cikin nawa
yana min kallon tambaya ,D'an turo baki nai nace" Meyasa jiya inata kiranka kak'i
d'agawa jiya"

"Nima meyasa inata kiran ki kika k'i d'agawa"

"To inafa gun Abba ne dana dawo naga kiran kuma na bika ka shareni,kasa na kwana
cikin tunani da kewan ka".

K'ara matsoni yai jikin sa yana min magana k'asa k'asa da sauri na runtse
idona ina girgiza kai don kunyar da maganar tasa naji, tun daga haka ban k'ara
magana ba na shiga cin fruits d'ina, shima mirmishi yake yanata tsunkulata, nak'i
kulashi, muna nan zaune muna kallo wanda rabin kallon kawai tsokana ne yakemin,har
k'arfe goma na fara hamma kallona yai yace" Bacci kikeji?"

D'aga kai nai alamar eh,ya mik'e a hankali tare da rik'o ni kashe kayan kallon
yai da haske muka shiga d'akin kauda kai nai nace " bari inyi wanka"

Wata y'ar dariya yai a hankali yace "ah kinsha k'arya kin Sani ai indai wankan ne
tare zamuyi"

Kauda kai nai ina k'ok'arin shige wa ,tsalle d'aya yai ya cafkoni a tare mukasa
dariya, nai kalan tausayi ina fad'in "don Allah ka barni inyi,sai kayi nifa kunya
nakeji Allah"

Cikin kashe ido yace " kunya? Kunyar wa kikeji kuma mijinki ko wa? Wai daman duk
abunda ake fad'a min a waya bai kai zuci ba?"

K'asa nai da idona cikin kalan shagwab'a nace "To to ai wannan bana kallon
idonka"

Wata dariya ma abun ya bashi yace "To yanzu ma ki daina kallon idon nawa sai
kimin duk abunda kike cewa zaki min".

Yana fad'in haka ya ruk'oni zuwa toilet d'in, nikam jingina kawai nai jikin
k'ofa ina kallonsa ya had'a ruwan wankan saida naga ya fara k'ok'arin cire kayan
jikinsa sannan na kauda idona, ban san ya gama cirewa ba saida naji hannayensa
jikina yana fara zaremin dukkan sutturar dake jikina,runtse ido na nai ina jinsa
har ya kammala ya had'e ni da jikinsa,subhanallah ya Allah, na furta cikin
raina,jin fatarmu had'e waje guda, gaba d'aya ya had'e jikin mu, magana fa ta k'are
tunda na tsinci kaina cikin zallar fatar jikinsa babu wani abu da yai shamaki
tsakanin mu, ban tabbatar da hakan ba saida naji hannayensa na yawo cikin dukkan
jikina yana sakarmin wani Irin sautin nishi cikin kunnena,lokaci guda jikinmu ya
hau rawa k'afafun mu suka fara karkarwa,bud'e bakin danai zan mai magana yai caraf
ya zira min bakinsa cikin nawa,halin da nake ciki yasa ban ankara ba na cafke da
sauri, duk yanda nake tunanin abun ya wuce haka ban san ya akai ba ban san na iya
ba ban san kuma zan iyaba,yanda na shiga maida mai martanin salon soyayyar, abubuwa
sosai nake mishi shima yake maida min martani hankalin mu yayi nisa bamu gane komai
ba,a hankali ya d'aga ni muka fita a toilet d'in kai tsaye gado ya d'ora ni yabi
bayana, hhhhhhmmmm wasa yai nisa game d'in gudu yake matuk'a ban san haka k'arshen
wasan yake ba saida game d'in zai yi over nan na gane kurena na fara k'ok'arin
k'watar kaina amma ina babu wannan zancen don zuwa lokacin bai san ma inda
hankalinsa yake ba, nan fa na fara kukan wahala,ina rok'on sa iya rok'o amma
mutumin nan ko jina bayayi kamar ma k'ara mai k'aimi nake wani irin surutai yake
wanda daji kasan bai cikin hayyacin sa, ban k'ara sanin inda hankali na yake ba
sai da sanyin asuba ya busa naji sanyi yana ratsa jikina, a hankali na bud'e idona
k'wak'walwata na son tariyo min abunda ya faru, runtse idona nai sanda na fara
tuno daren mu na jiya, kusan 30 minutes da farkawata amma idona a rufe, tunanin
danai Kar lokacin salla ya wuce yasa na mik'e a hankali,wata y'ar k'ara na saki
sanda naji k'afafuna sun amsa, kallon jikina nai da sauri na koma na zauna a bakin
gadon ina neman abunda zan rufe jikina dashi amma babu ganin baccin sa yake hankali
kwance yasa na mik'e a hankali ina kakkare jikina da hannayena, ruwa me zafi na
had'a na gasa jikina dashi na dad'e cikin toilet d'in sannan na d'auro alwala na
fito d'aure da towel,cikin sand'a na bud'e jakata na zaro doguwar riga nasa da
hijab na tada sallah, har na idar bai motsa ba ni kuwa bana tunanin ma zan iya
tashin sa ko zai kai k'arfe goman safe, inata azkar,can yai juyi yana lalubo inda
nake yaji wayam da sauri ya bud'e idon ya hango ni kan sallaya,tashi yai ya zauna
bakin gadon yana D'an sakin mirmishi, ni kuwa tunda naga ya tashi na maida kaina
k'asa kamar banma san me yake ba, ganin hanlali na naga sallaya yasa ya mik'e ya
shige toilet ina ganin ya shige na tashi na nad'e zanin gadon na shimfid'a wani
na koma na kwanta,koda ya fito banma nuna idona biyu ba harya idar da sallar yazo
bakin gadon ya zauna yana rik'o hannuna" my precious bacci kika koma?"
Shiru nai kamar banjinsa,ina jin yasa hannu yanata shafar wuyana,maganar sa yake
shi d'aya " Khadeejah kin biyani kin gamai min komai a rayuwa,kin sanyamin farin
ciki cikin rayuwata kin shayar dani zumar da ban san da ita a duniya ba" tsawon
lokaci yana surutansa ya tashi yana gyara min kwanciyar ya fita parlour.

Wajan k'arfe goma na farka na tashi da k'yar ina salati ba kowa a dakin don haka
na wuce toilet na k'ara gasa jikina da zafafan ruwa, bayan na fito na shirya cikin
riga da siket na wani material me laushi launin ruwan bula,nai light make up ina
d'aura D'an kwali na ya shigo ta baya ya rungumoni yana sinsina wuyana,rufe idona
nai cikin sanyin muryata nace"barka da safiya"

Juyo dani yai gabansa yana kallona yace "my wife ya jikin naki "

Ban iya amsawa ba sai D'an mirmishi danai idona a rufe ya rungumeni yana fad'in "
na gode mata ta na gode Allah ya yai miki albarka na gode kinji,kin bani abunda
wani bai tab'a bani ba Allah ya saka miki da gidan aljanna ya faranta ranki kamar
yanda kika faranta nawa, zo muje Abba yazo".

Wata bala' kunya ce ta kamani, kawai naji kamar in na fita Abba zai san halin da
nake ciki,ko daga yanayin tafiya ta ma,haka na daure nabi bayan shi ina takawa a
hankali, Muna had'a ido da Abba ya sakar min mirmishi kamar ko yaushe, ni kuwa sai
naji kunyar sa da nakeji ta da ta k'aru da kaso mafi yawa, da sauri na tsugunna
k'asa kaina a k'asa na fara fad'in "Abba barka da safiya"

"Barka dai Nahna Khadeejah ya bak'unta,ya jikin yanzu Daddy yake cemin kwana
kikai da zazzab'i ko"

"Kai na gyad'a cikin ninkuwar kunya nace " Da sauk'i Abba "
"Sannu kinji yanayin canjin k'asa ne, yace min ma ko abinci biki ciba maza daure
gashi nan ya muku order kici ko yayan ne,kai Daddy maza zubo mata ko farfesun ne
taci ".

Dan bowl ya d'auko ya zuba min farfesun hanta sannan ya had'a min ruwan tea, a
kunyace naci na D'an sha ruwan tea d'in,bayan na gama na yun k'ura zan tashi don
kai kwanikan kitchen, nan fa k'afa ta rik'e na famo ciwo da sauri ya maidani ya
zaunar yana cewa " sannu koma ki zauna bari in kai kitchen ".

Komawa nai na zauna ina lumshe ido,don ni kad'ai nasan zafin da naji,

Abba ne yace " harda ciwon k'afa kuma Khadeejah?"

Da sauri na girgiza kai ina fad'in "a'a jiya ne da dare na buge da kujerar nan".

Abba kan bai kawo komai cikin zuciyar sa ba don shi anashi tunani ai tun kafin ya
taho an wuce wajan,tunda yaga yanda muka d'in Ke muka shirya kafin tahowar shi
cikin tausayawa yace " OK sannu kinji Allah ya sauwake ki ringa kula kinji".

Gyad'a kai nai kawai, hira suke kan karatun UK d'in nikam shiru kawai nai ina
sauraransu, can Abba yace zaije wajan wani abokin kasuwan cinsa ya dawo tunda sai
k'arfe hud'u jirginsu zai tashi, UK yace zai rakashi yace a'a ya tsaya guna tunda
banjin dad'i da sauri nace " a'a Abba kuje nima bacci zanyi".

Gaba Abba yai ina mai adawo lafiya, shi kuma ya tsugunna gabana ya rik'o fuskata
yana fad'in " ki kula da kanki kinji my wife don Allah Kar kiyi abinda zaki wahala,
ki kwanta kiyi bacci sosai ".

" um hmmm,adawo lafiya" kawai nace ya mik'e ya fita tare da rufemin k'ofar.

Ajiyar zuciya na sauke Dana ga fitar sa,don dama da biyu nace yaje don nasan
inya zauna takurani kawai zaiyi, kan kujera na hau na kwanta don baccin dake
d'aukan idona.

Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣4⃣1⃣
0⃣4⃣1⃣ 0⃣4⃣1⃣

Bacci nai sosai kusan awa biyu na farka, lokacin sha biyu da rabi ta wuce don haka
na wuce toilet na k'ara had'a ruwan zafi na gasa jikina don baccin da nai dai naji
duk jikin ya k'ara min tsami yayi nauyi, alwala na dauro na fito na gabatar da
sallar azahar don lokacin dana fito d'aya tayi, yunwa naji inaji na tashi na wuce
kitchen nemawar kaina abinci,ba wani abun arzik'i me nauyi a kitchen d'in daga
kayan fruits sai ragowar ferfesun safe da soyayyar doya da k'wai, D'an tsaki naja
na koma d'aki ,d'aya jakar dana taho da ita ya kayan snacks d'in danai mai na fito
dasu wrapping nai danan na warware na d'auki meat pai guda biyu da cake naje na
had'a ruwan tea nasha, bayan na gama na wanke kwanikan da suke a b'ace na k'ara
gyara ko ina,sannan na koma parlourn na zauna , wayata na d'auko ina tunani ya
kamata in kira y'an gida fa amma kuma bani da layin k'asar don haka na mayar na
ajiye ina tunani inya dawo sai in amshi layinsa in kira su, ganin zaman kad'ai cin
ya isheni yasa na kunna T.V wadda ta d'aukemin kewa har lokacin sallar la'asar
yayi na mik'e da niyar inje d'aki inyi salla naji ana knocking a zatona shine amma
ina bud'ewa sai naga wata budurwar tsaye tana sanye da riga da wando na Pakistan ta
yafa mayafin kayan hannun ta rik'e da wata y'ar k'aramar jaka k'afarta kuma sanye
da wani dogon takalmi kamar zai huda k'asa, akwai alamun wayewa da budewar ido
tare da ita,duka a kallo d'aya na gano komai dake jikinta harda yanayinta,gani nai
tana bina da wani kallo na tuhuma,D'an sassauta fuskata nai alaman fara'a, cikin
harcen nasara kamar yanda naga tafi dacewa dashi nai mata magana ina tambayarta me
take buk'ata,yatsina fuska tai cikin izza tace"ina neman me gidan ne?"

D'an mirmishi nai nace"baya nan yaje unguwa tare da Abban sa".

K'ada kai tai cikin yauk'i tace" ok ba damuwa"


Ta juya ta koma ni kuma na maida k'ofan na rufe ina sak'e sak'e cikin raina, kai
tsaye na wuce toilet na d'aura alwala tare dayin salla, na dad'e zaune kan abun
sallar ina rok'on ubangiji yaci gaba da tsaremin mutuncin mijina da addinin sa.

Wajan k'arfe hud'u da rabi naji ana sake knocking tashi nai naje ina tunanin ko
ina suka zauna tun tafiyarsu ga Abba yace k'arfe hud'u jirginsu zai tashi ko ya
fasa tafiyane,

Ina bud'e k'ofan ya had'a ni da k'ofan cikin shagwab'e wan murya yace "washhhh my
wife nayi missing naki tsawon yinin nan ga gajiya matuk'a tare dani".

Mirmishi d'auke akan fuskata nace " sannu da zuwa "

Rufe k'ofan yayi ina manne jikinsa sai sinsina k'amshin jikina yake daga gashi na
zuwa wuyana, tare muka zauna kan kujerar ina k'ara mai sannu da zuwa,na mik'e nace
"bari in kawo ma ruwa ko".

Bina yai da ido yana lumshe su annuri bayyane akan fuskarsa,da kaina nasa mai cup
d'in a bakin sa ina bashi ruwan,bayan ya shanye na janye cup d'in ina D'an mirmishi
nace" da gani ka gaji da yawa yau,ina Abba ".

D'an dariya yai yace " Ai Abba jirginsu ya lula yaso mu dawo kuyi sallama to
lokaci ya k'ure kawai sai na kaishi masaukin sa ya d'auki kayan sa, don ya kaiwa
abokan kasuwancin sa da yawa ziyara".

Marairecewa nai kamar zanyi kuka "Amma gaskiya banji dad'i ba wlh,Abba tafiya ba
sallama"

Cikin D'an dariyarshi ya kamoni jikinsa yana magana k'asa k'asa kamar wanda bai
so wani yaji shi yace" kiyi hak'uri kinji beauty nah, ni bamma tambayi jikin naki
ba da sauk'i ko?"

Ya fad'a yana kashe ido, kauda kai nayi,gefe ina D'an mirmishi, hannu yasa yana
juyo da fuskata duk yanda yaso kallon k'wayar idona nak'i bashi dama don haka ya
shiga yimin cakulkuli dariya na fara kyalkyalawa ina zilzillewa,saman cafet muka
zubo duka muna dariya, daga cakulkuli ya shiga tab'e tab'e kuma, lumshe ido nake
don jin dad'in abubuwan da yakemin mun lulu sosai cikin shauk'i da romance juna
karaf na tuno da bak'ar gagarumar wahlar da nasha daren jiya zumbar na fara
k'ok'arin k'wace jikina ya k'ara kwakubeni cikin sanyin murya nace " plss plss "

Rungumeni ya k'ara yi yana shinshinar wuyana, idonsa a lumshe yake min


gamana"kiyi hak'uri karki barni babu abunda zan miki kawai ina son samun nutsuwa
ne"

Jin abunda yace yasa na k'ara sakin jiki mukaita yamutsa juna, tsawon lokaci
sannan ya mik'e yana d'aga ni yace"muje ki taimaka min inyi wanka"

Muna shiga toilet d'in ya rufe k'ofan tsayawa yai gabana yace "tare muyi fa"

Nidai idona a rufe na gyad'a mai kai jinai ya fara zaremin kayan jikina nidai
banko yi k'ok'arin hanashi ba,ya gama shima ya cire nasa jina kawai nai cikin
ruwan wankan daya tara, da dai harnayi shiru banso na biye mai amma dana tuno y'an
cin aurena nazo nema sai kawai na biyemai mukaita shafar juna muna mulmula juna,
mun dad'e munata abubuwa sannan mukai wankan muka fito, yana zaune kan dressing
mirror yana goge jikinsa ni kuma ina tsaye ina dubo kayan da zansa ya tako a
hankali bayana ya tsaya ina juyowa na fad'a k'irjin sa ya manneni D'an turo baki
nai nace "um nidai ka barni in shirya duk ka lugugutani"

Mirmishi yai yace " ki shirya in anyi magriba zamu fita muyi siyayya" ya fad'a
yana shafo albarkatun k'irjina cikin kunnena yake magana "Baby na ina son wannan
sunamin kyau a ido kuma sunamin dad'i a hannuna"

Hannu nasa na rufe idona ina D'an dariya k'asa k'asa, ya dad'e yana shafasu ya
hak'ura ya sakeni yasa kaya sannan nima nasa kayan muka fito parlour, nan ma dai
bai barni ba haka yaita lalubani da shafani, har lokacin magriba yai muka tashi don
yin salla, wani Abu daya sani damuwa nace ya jamu salla amma daga yanda naga
tashi sallar naga bata gama cika ba,kawai dai basarwa nai ina tunanin Neman mai
mafita, shiryawa nai cikin doguwar riga shi kuma cikin k'ananan kaya muka fita .

*Manage* *plsss*
*manage* *plsss*
Taku ce
layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*Y'AN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣4⃣2⃣
0⃣4⃣2⃣ 0⃣4⃣2⃣

Wani lafiyayyen mall muka shiga babu abin buk'ata da babu a ciki kama daga kayan
amfanin gida kayan gyaran gida kayan sawa kayan kitchen kayan ciye ciye,kai Duk
wani abun buk'ata akwaishi a mall,don ba k'aramin girma ne dashi ba, kai tsaye
wajan kayan sawa naga ya jani mun nufa, wasu y'an iskan kaya ya rink'a juda wanda
dasu za'a iya cewa k'ara babu,ga wasu azababbun night gown, sai da na rik'e
hannunsa ina fad'in "wannan kayan fa haka dear"

D'an mirmishi yai kana ya gyad'a kai yana fad'in " duk naki ne ina sha'awarsu
jikin mata ta".

Gyad'a kai kawai nai ina kallon yanda ya d'iba kamar baya son kudin,daga nan
muka tafi b'angaran kayan shafa nan ma turaruka masu kyau da tsada ya d'ibar min,
da kalan mayukan da nake amfani dasu, sannan muka nufi b'angaren kayan amfanin gida
da kayan abunci,nan yace in d'ibi abunda nake ganin zai mana amfani,daman ni kuwa
so nake in rink'a mana girki da kaina don haka na tsaya na dibi kayan Girki sosai,
har kutunya ma na d'auka da sauran kayan amfanin kitchen.

Bayan mun dawo gida ban zauna ba sai da na ajiye komai a muhallin daya dace
sannan na k'araso inda yake kwance kan kujera yana kallo,zama nai gefen sa ina
d'an lek'a fuskar shi,mirmishi yai kamo hannuna yana murzawa a hankali yace
"kinje kinata aiki kin barni ni kad'ai ko "
Langab'e kai nai nace "ai na gama yanzu kuma in mukai sallah sai mu zauna
tare har safe ko"

Mik'ewa yai a hankali ya kamoni muka tashi ya mannani a jikinsa muka wuce
d'aki, ina k'ok'arin wucewa toilet ya kamoni idonsa k'asa k'asa kallo d'aya nai mai
na gano tsantsan jarabar dake tare dashi, d'an far nai da idona nace" Salla fa"

"Um mu farayin wanka sai muyi alwalan muna yin sallah mu kwanta don Allah a
buk'ace nake"

D'an zaro ido bai nace "ban warke bafa "

Baice komai ba ya rik'oni zuwa toilet, ya Allah kawai na furta lokacin da naji
yanda yake wasa da sassan jikina kamar me, duk abunda yamin sai najishi har cikin
kaina don Allah ya Sani jikina akwai saurin karb'ar sak'o, a
Idanuwa na a lumshe na tallafo kansa INA shafa sumar sa cikin salon tafiyar
tsutsa,muryata a sark'e nake magana" Reality muyi wankan mana"
D'an bud'e shanyayyun nashi idanuwan yai ya zubawa fuskata su yana tabbatar da
asirtattcen kyawun da Allah yai min, a hankali ya busomin iskar bakinsa saman
idona, k'ara lumshesu nai ina d'an sakin wata siririyar ajiyar ziciya ,cikin
kunnuwana yake rad'a min "My Khady mata ni'ima ne tabbas ban San da hakan ba sai
yanzu,ina jina tamkar jinjiri bani da wata damuwa, kawai burina in ta jina cikin
jikin ki ina d'an d'ana daga ni'imar ki,my beauty komai naki daban ne da sauran
mata jiya na tabbatar babu wani namiji daya tab'a jin abunda naji,naji abunuwa naji
abu naji abunda dad'insa ya kusa tafiya da numfashi na,my Khady kinada wata
matattarar ajiyar dad'i ajikin ki Wanda na san koke biki San inda yake ba ni
kad'ai na gano abuna"

Wata kykyawar runguma ya k'ara min cikin jikinsa,dukkan wata gab'a ta jikinsa
rawa take a lokacin ina jin yanda jikinsa ke kakkarwa don tsananin buk'atar dake
tare dashi, ni kuwa zuciyata sai bugawa take don har ga Allah nasan na amince mai
ya k'ara kusantata a yau zan D'an d'ana kud'ata don ni kad'ai nasan ciwon da nakeji
don dai inada dauriya ne amma dako tafiya bazan iya me nisa ba, ban ida tunanin ba
naji ya d'aukeni cak zuwa d'akin bisa gado yai mana masauki yanda ya kwantar dani
haka ya bini yamin runfa idonsa cikin nawa, D'an kauda idona nai gefe ya had'e
fuskokin mu yana sauke min numfashinsa a fuskata,Wanda hakan ya k'ara saukar min da
wata irin kasala fiye data farko, a hankali yasa hannunshi yana shafa k'irjina
zuwa wuyana,tabbas bazan iya kasa maida mai da martani ba don nima tuni hankali na
ya fara gushewa, maida mai martani na shigayi Wanda hakan ya k'ara zafafashi kusan
fita a hayyacin sa yake Neman yi a hankali yake magana Wanda badan kusancin dake
tsakaninmu ba bazan tab'a jin me yake cewa ba " my wife ina buk'atarki matuk'a
kuma nasan biki warke ba,nasan kina jin ciwo ya zanyi Khady nah"

Na rasa mafita ya zanyi dashi ya zanyi da radadin danakeji ya kuma zanyi da


buk'atar mijina,Na Sani fa jiya bawai gama shigata yayi ba yayi dai iya yinsa ne ya
bari yau kuma ya zata kasance tsakaninmu, wani dogon numfashi naja sanda naji bakin
sa ga breast d'ina kamar yana feeding kansa, lalle duniyar aure daban take yau
gashi sak'o da lungu na babu inda Mijina bai lek'a ya shiga ba a jikina, "ki
taimaka min ki tallafeni matata plss and plsss"

Mik'a mai ragamar nai yayi iya yinsa,har ya gamsu Wanda zuwa lokacin ni kuwa na
azabtu matuk'a don ni zan ma iya cewa yau yafi jiya wahla,ko hannuna kasa d'aga wa
nai don azaba,yana kwance gefe yana dai daita nutsuwar sa, ni kuwa ina shan
zugi,saida ya samu k'arfi ya dawo jikinsa sannan ya kawo hannunsa a hankali ya
jawoni jikinsa yana shafa kaina cikin sigar rarrashi, nai lamo a jikinsa ina fidda
y'ar kwallar azaba,ya shafo fuskata jin hawaye nabin idona yasa ya shiga rarrashina
yana d'an pitting bayana,"sannu sannu khadeeja sannu kinji Allah yai miki
albarka,Allah ya tabbatar dake matsayin shugabar matana na gidan Aljanna,Allah ya
sakawa Abbana da alkairi ,Allah ya sakawa iyayenmu duka da alkairi,Khady kin biyani
bazan gaji da fad'a miki ba ,kin gama min komai a rayuwa ,kin sadaukar da farin
cikin ki gareni, Ashe ganganci naso yiwa kaina danai k'ok'arin bijirewa Abbana Ashe
Abbana shi yasan me yagano yasan nagartar dake tare da mace y'ar Arabic me ilimin
addini, nayi wauta naso tafka babbar asarar da bazan maye gurbinta ba, haka yaci
gaba da zantukansa, nidai idona na lumshe bacci nason d'auka ta amma dana tuno
bamuyi sallar isha'i ba sai na fara k'ok'arin tashi,yai saurin rik'eni "me kike so
ina zaki?" Ya jeromin tambayar " bamuyi salla bafa kuma ina jin bacci nason
kamani".

"A'a kiyi baccin ki bari in kin tashi sai kiyi ko cikin dare".

Girgiza mai kai nai nace " A'a in nai bacci ban farka ba kuma fa in na mutu a
baccin me zancewa Allah, dame zan cike gurbin sallar?"

Shiru yai can yace "To zaki iya tashi kona d'aukeki".
" A'a zan iya ma"

Tashi yai dani a jikinsa muka mik'e a hankali na fara takawa na runtse idona
cikin azaba ina yarfe hannu, d'agani yai yana fad'in"sorry sorry kinji nasan
bazaki iya tafiya ba daman kiyi hak'uri "

Ruwa me zafi ya had'a min na shiga wayyo naga azaba jinai kamar na kurma ihu
amma da ruwan ya fara shiga jikina sai naji dad'insa. Sau uku yana canja min ruwan
ina shiga Sai naji dama dama nan mukai wankan tare sai naga ya tsaya zai d'aura
alwala,a kaikaice na kalleshi nace "alwalan zaka sake kuma?"

"A'a ai daman banyiba". nace " wadda kayi ma a cikin wankan ai ta isa ".

Jim yai can yace" yanzu zan iya yin sallar da alwalan cikin wanka?"

Gyad'a mai Kaine nace "Alwalar cikin wankan tsarki ya halatta ayi sallah da ita
matuk'ar bayan anyi ta ba'a tab'a al'aura ba".

Lek'o fuskata yai yana d'an kashe ido yace " To ya sayyada aini ban Sani ba ko
na tab'a,ko kinga na tab'a?".

Kauda kai nai nace " Tunda kana kokwanto ka sake yin wata a gaba a tara".

Y'ar dariya yace "Wayyo mata ta malamata y'ar Arabic gaskiya dole mu rink'a zama
ana nusar dani wasu abubuwan fa".

Nidai shuru nai ina kallonsa ya gama alwalar ya d'aura towel muka fito ina
takawa a hankali ina d'ingishi na isa gaban Waldrop na ciro doguwar riga nasa
shima yasa kaya mukai salla, muna idarwa ya mik'e da sauri na kalleshi yace "
yah me kike so"
Nace " A'a naga muna idarwa ka tashi ne bakai addu'a ba".

Komawa yai ya zauna yana mirmishi yace "To muyi addu'ar".

D'aga hannu nai ina addu'o'ina cikin zuciyata shikam sai ca yake " Amin Amin"

Ina shafawa shima ya shafa muka mik'e a tare" da sauri ya isa Waldrop d'in ya
zaro rigar bacci d'aya cikin kayan da muka siyo, yazo gabana a hankali ya zare min
hijab d'in sannan yasa hannu yana son ciremin doguwar rigar da sauri na rik'e ina
girgiza kai don bayan rigar babu komai a jikina,ganin na hanashi cirewa yasa ya
mik'omin rigar yana cewa"To kisa da kanki nima bari in shirya"

daga haka ya juya ya d'auko shima tashi rigar baccin ko a jikinsa yai zir a
gabana yasa, nikam runtse ido nai nace "Reality kaje parlour zansa kaji b"

Dariya yai ya juya ya fita, yana fita nai sauri nasa rigar wadda iya kacinta
cinyata kuma net ce don haka komai nawa a bayyane yake,d'an yalolon pant d'in nata
nasa me zaren d'aurewa,na goga humra a jikina nasawa Lip's d'ina lipstick fari me
k'amshi ,janye zanin gadon nai ina k'ok'arin nemo wani ya shigo hannunsa d'auke da
fresh milk me sanyi daSauri ya k'ara so ya karb'i zanin gadon yakai toilet yazo ya
shimfid'a wani sannan ya fesha freshner akai,ina zaune kan stool yazo ya zauna
gefen gadon ya tsiyayomin mikl d'in ya mik'amin akarb'a nai ina d'an kurb'a a
hankali shima yana sha,idonsa akan k'irjina da suke tsaye tsaf ta cikin rigar yake
k'are musu kallo,ina kallon sa yanda yake musu wani kallon maita yana lumshe
ido,ajiye cup d'in nai ina mik'a Wanda da gayya na turo k'irjin aikuwa d'if yaji
wutar sa ta d'auke,ya mik'e da sauri shima yana fad'in "yah akai ?"

Cikin yanga ga jan hankali nake k'arasawa bakin gadon nace "Bacci "

"OK ok kwanta ina zuwa nima"

Fita yai da cup d'in ya dawo tare da kashe glop d'in d'akin ya hayo gadon yana
sane ya wani fad'o kaina, y'ar k'ara na saki ina tureshi. . . ...

Taku ce

Y'ar mutan ja'oji


https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*'YAN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

*MY* *BLOOD* *SISTER* *ALLAH* *YA* *BADA* *ZAMAN* *LFY* , *YA* *SANYA* *ALKAIRI* ,
*ALLAH* *YA* *HAD'AKI* *DA* *DUK* *KAN* *ALKAIRAN* *DAKE* *CIKIN* *GIDAN* *AURE*
*YA* *KAD'E* *FITINA* , *ALLAH* *YA* *BAKI* *ZURI'A* *D'AYYIBA*.👏👏👏

0⃣4⃣3⃣
0⃣4⃣3⃣ 0⃣4⃣3⃣
Washe gari da wuri na tashi na had'a mana lafiyayyen breakfast bayan na gama na
gyara gidan ina k'ok'arin shiga wanka ya farka idonsa k'yar a kaina,lumshe ido nai
ina d'an asirtaccen murmushi nace" Barka da tashi"

Kashemin ido d'aya yai baice komai ba ya mik'e zuwa inda nake tsaye d'aure da
d'an guntun towel ya kamoni zuwa toilet d'in yana magana can k'asa k'asa " kin
barni ina bacci ni kad'ai shiyasa ma duk banji dad'in baccin ba,kuma zaki shige
wanka ki barni ko".

Bance komai ba illa mirmishi dake fita kan fuskata,na had'a mana ruwan wankan
muka cud'a jikin mu tas,tare muka shirya muka fito parlour don yin break, rabi
soyewa rabi cin abunci haka muka kammala ya samin d'ayan layinshi na k'asar a
wayata , nan na fara kiran ya'n gidanmu muka gaisa cikin nishad'i sannan na kira
y'an Sakkwato suma mun dad'e muna hira daga nan na kira sweety mukasha hirarmu
tanata tsokanata nidai dariya kawai nake, ganin dayai hiran tamu tak'i k'arewa
yasa ya shiga min cakulkuli yana tattab'ani dariya nasa ina fad'in "wayyo ka bari
don Allah ka bari".

Muryan sweety naji tana " oh kina kusa da mijinki kika kirani to sai anjima asha
soyayya lafiya"
K'it ta kashe wayan kafin inyi k'ok'arin bata amsa,amshe wayar yai daga hannuna ya
ajiye tare da wani shigewa jikina yana sunsunata kamar wani mage, haka na biye mai
muka shifa soyewarmu,amma ban bari abun yai nisa ba don nasa araina saina huta
kafin muk'a lek'awa babbar Head quarter😄.

************
Wasu irin kwanaki muke shud'ewa masu cike da tarin so da k'auna,azababbiyar
soyayya ce a tsakaninmu wadda bamu San da ita a duniya ba,shak'uwa me tarin yawa
ce ta shiga zuk'atanmu,har ya zamana bama tunanin kowa da komai sai junanmu,mun
zama wasu Chen gum babu abunda ke rabamu,komai tare mukeyi wanka girki cin abunci
bacci hira, duk motainmu tare ne, ganin danai bashida niyar komawa skl yasa na
lallab'ashi nace yayi hak'uri ya koma ai muna tare kar aita wuceshi,da k'yar ya
koma,amma kullum nike kaishi da safe muna tafe ina driven yana faman mammatsani da
shafani intamai magiyar ya bari kar in kifar damu amma sai dai yai dariya yaci gaba
da shafa cinyata, inna kaishima kafin ya fita a motar saiya tsotseni tas, a hakan
ma daya samu sarari zai kirani a waya yaita min shagwab'a wai kewana ta isheshi shi
ya rasa yandama zaiyi, haka zanta lallb'ashi ya kashe wayan jimawa kad'an kuma zai
k'ara kira ni abunma har dariya yake ban,kuma da lokacin tashinsa yayi zanje in
daukoshi , wata irin azababbiyar k'auna yake nunamin wadda ban tab'a zaton samunta
a duniya ba daga gurin ko wane irin namiji ba balle ma Uk, wani abu kuma yanzu
sai yai kwana uku bai kusanceni ba ammafa duk sassan jikina suna shan matsa abunda
na lura yafi buk'atar wasanni fiye da sex don baya tab'a barin hannun sa ya huta in
muna tare yaita shafani kenan da latsani kenan, har jikina ya saba da tab'etab'ensa
,breast d'ina kuwa tun suna min zugi da rad'ad'i har sun fara sabawa don kullum
suna cikin bakinsa yana faman tsotsonsu.

***************
Yau da daddare muna kwance kan cafet ina wasa da hannunsa yatsun hannuna nake
kalla cikin nashi, yatsunsa farare tas nawa kuwa chocolate color mirmishi nai na
d'ago na kalli idonsa nace " Reality kalli hannuwan mu"

Kalla yai yana mirmishi yace "me sukayi?"


Nace " kallesu mafi da bak'i"

Mirmishi yai ya kamo hannun nawa yana magana k'asa k'asa "fatarki ai tafi tawa
kyau ga laushi ga santsi,ada kam ina ganin bak'ar mace bata birgeni kona kulata to
bawai har zuciba,amma yanzu na gano ni'imar dake tattare da b'akar mace na gano
sirrin hakan,dukda abokaina da yawa way'anda suke harka da mata sunsha fad'amin
zak'in da bak'ar mace ke dashi in naga suna neman mata bak'ar fata sai inji na
k'ara tsanar su don ban hango abunda bak'ar mace ke dashi ba, amma a zahiri ko a
bad'ini yanzu zan tsaya gaban kowa in fad'i sirrin bak'ar mace ,zan fad'i alkairan
dake tare da mace y'ar Arabic me d'abiun musulunci da koyi da addini, wato
Khadeejah nayi nadamar furicina nayi nadamar gujin mace y'ar Arabic, Ashe ba mace
me bayyana surarta bace ta iya rayuwa ashe wayayyun matan da nake kalla nake
tunanin suke da abin bayarwa nake tunanin suna rayuwar aure su suka iya soyayya
Ashe duk shirmamman tunani nakeyi, yanzu kam na gano sirrin nasan inda kayan dad'i
suke,na tabbatar ni'ima soyayya nishad'i kulawa da kayan dad'i duk suna tare da
mace ma'abociyar addini irinki,Wlh wlh wlh Allah khadeejah yanzu bana kallon ko
wace kalar mace a matsayin mace inba keba,bana hango komai tare da wata mace sai a
gunki,bazan gaji da godewa Abbana ba da gatan da yai min na bani d'aya tamkar da
dubu Khadeejah y'ar Arabic me abun dad'i da gard'i gami da zak'i"

Saurin tura harshena cikin bakinsa nai ina tsotsar bakin sa, tare damai wasu
salo masu tafiya da tunanin namiji, cikin k'warewa shima ya amshe muka shiga
tsotsan bakunan mu,nishi me tattare da dad'i muke saukewa da sauri sauri a
hankali yakai hannunsa inda yafi k'arfi ya shiga matsasu cikin k'warewa, jin ya
fara tab'omin ma tattar dad'i yasa na fara turomai k'irjin ina bashi damar
shafarsu cikin iyawa, a yanzu na tabbatar nima ina cikin mata mabuk'ata don wani
sa'in har mama kin kaina nake, yanda nake zak'ewa a harkar, jin danai duk sassan
jikina na amsawa yasa nasa hannayena biyu na kunce igiyar y'ar ficikar rigar dake
jikina,na shanuna suka bayyana lokaci guda don daman babu bra a jikina, na kamo
kansa ina saita bakinsa a saitunsu ai kuwa da k'arfi ya amshe ya fara lasar su
yana tsotsa, mik'amai nake k'arayi ina shafa sumar kansa zuwa bayan sa, munfa lula
mun mik'a can, mun d'au lokaci muna romancing junanmu mun fice hayyacinmu cikin
k'warewa na shiga sucking nashi nan fa na k'ara kunnamai wuta duk ya
firgice,sambatu kawai yakemin yana wasu surutai Wanda suke sirrin mune.

Bayan mun koma d'aki wajan sha biyu da rabi munyi wanka muna kwance
mak'ale da juna yanata shafa kaina tare dasamin albarka Wanda ya zame mai jiki
yanzu kullum cikin samin albarka yake tunda ya fuskanci inajin dad'in hakan,lumshe
idona nai Wanda bacci ya cikasu tun inajin me yake harna Lula,jin sauke numfashina
yasa ya gyaramin kwanciya sosai a jikinsa ya rufemu.

*************

Bayan mun idar da sallar asuba ina zaune kan prayer mat ina karatun Qur'an Wanda
aladatace kullum,shikuwa yana kwance kan gadon yai rufda ciki yana kallona cikin
burgewa da sha'awa,a ransa yake tunanin inama shima Allah yai mai wannan baiwar
yaji yanata karanto al'qur'an rai rai cikin murya me zak'i irin wannan, kullum in
ina karanta Qur'an haka yake zama yaita kallona cike da sha'awa da birgewa,gashi
wani babban abun k'awatarwar yanda nake karantoshi daka ,don koda yaushe ban son
haddata tai rauni, shi yasa nafijin dad'in bitar haddata, d'ago kai nai a hankali
don jin kamar ana kallona, ai kuwa karaf idanuwanmu suka sark'e a tare muka sakarwa
juna mirmishi, ina kai aya nai addu'a na shafa tare da mik'ewa na cire kayan
sallar ya rage dagani sai pant da da half vest na fad'a gadon ina D'an
mintsininshi don tsokana, cafkoni yai yana y'ar dariya yace"zo ban son Allah ki
koya min karatun Qur'ani in rink'a yin irin yanda kikeyi, mirmishin jin dad'i nai
don na hau mataki na biyu kenan tunda yanzu na samu nasara a fannin salla,dabarar
da nai kuwa kullum muna tare sai in kunna tashar danasan ana yawan yin program
akan salla Wanda ana bayani da baki ana kuma practical, inna kunna duk sai in
maida hankalina kai yaita tsokanata amma sai in k'irk'irowa kaina mutuwar jikin
dole,inya matsamin sai ince" Reality rayuwarmu na cikin had'ari don bamu iya komai
cikin addini ba,musamman salla yanzu dubi kaga yanda ake nuna salla a zahiri amma
da yawa ba haka mukeba Ashe duk ibadar da mukema cikin jahilci muke,"

Dayaji na fara wannan maganar shima jikinsa yake sanyi, to anan nake cin
galabrsa,in takuramai dole mu maida hankali ga kallon yanda ake sallar,a haka har
na fara ganin canji matuk'a tare dashi, don kaso saba'in cikin kurakuran da yake a
salla hamsin ya ragu, to yanzu kuma gashi da kansa yai maganar son koyon Qur'ani.

Jinai an birkitoni da sauri na dawo daga duniyar tunanin dana fad'a, D'an
mirmishi na sakarmai nace"Karka damu daga yauma inka shirya saimu fara"

Tashi yai ya zauna sosai ya koma serious sannan ya kamoni nima na zauna,cikin
nutsuwa ya fara magana "Khadeejah da gaske nake wlh, na sani ban San komai ba daga
addini na ko salla ta yanzu ne na San na farayinta dai dai, na guji islamiyya tun
k'uruciya na maida neman ilimin addini a matsayin k'auyanci,bana tunanin k'ara
sanin komai kan addinina, amma yanzu tarayyata dake sai naji ina sha'awar k'ara
sanin addinina,kina buegeni My deejah zanso in aikata aikin da zai shigar dani
aljanna kodan muyi rayuwa dake har a lahira don ke na gama kyautata miki zaton
alkairi na tabbata ke y'ar aljanna ce tunda kina yin ayyukan da zasu sadar dake da
aljannar, don haka Khadeejah ki bani daga iliminki ki rink'a k'ara min sani akan
addini kinji".

Cike da jin dad'i nace " Reality insha Allah zamuyi rayuwa tare a cikin aljanna
matuk'ar ka bani damar shiganta tunda aljannata tana gareka inka bud'a min zan
shiga,sannan zamu rink'a k'aruwa da juna daga abunda Allah ya sanar dani duk da ba
wani abu na Sani ba nima har yanzu neman Sani nake, amma insha Allah zamu rink'a
ware wani lokaci muna k'arar da junanmu".

Kamoni yai jikin sa yana shafa kaina tare da samin albarka,yana k'ara fad'a min
irin ribar dayake riska cikin rayuwar auran mu.

*************

Tun daga ranar ya zamana kullum mukai sallar asuba sai munyi karatu in k'ara mai
Qur'ani da Fiqihu kuma na turamai App na Qur'ani cikin wayar sa ga video audio duk
Wanda yaso, amma ko sau d'aya bana tab'a d'arsa wani abu a raina ko na kawo wani
abu da zaisa inji a raina nafi mijina Sani ko wani abun sai dad'i da nishad'i da
nakeji na sauyawar sa ta sanadiyyata.

****************
Yau da safe bayan na kaishi skl na dawo inata d'an aikace aikacena naji ana
knocking tunanin na tsayayi to Waye kuma tunda nasan tun zuwana garin sati kusan
uku sau d'aya aka tab'a knocking d'in k'ofar inba UK ba,jin k'arar tak'i k'arewa
yasa naje ina lek'awa ta D'an abunda ake hango na waje, mace na gani ya juya baya
ban iya hango fuskarta jim nai kamar bazan bud'e ba sai dai kawai nai addu'a na
bud'e, jiyowa tai cikin yauk'i da d'aukar kai tana kallona sannan ta bud'e baki da
k'yar tace "Am ina neman hubbey nah, ina fatan yana ciki".

Cikin mamaki na k'ara kallon ta nan na tuno itace wadda tazo kwana na d'aya da
zuwa k'asar, basarwa nai na tattaro jarumtata nace " amma ina tunanin kinyi makuwa
ne don wanna gidan namiji d'aya ne a cikinsa kuma mallakinane me gidan, sai dai
inaga ki k'ara sa ga block d'in gaba maybe ki dace".

Kallon kinma rainamin wayo taimin sannan ta kad'a ido cikin isa tace "ina nufin
Umar Usman umar katsina ( UK )ai shine mamalakkin wannan gidan ko?.

" gyad'a kai nai cikin halin ko in kula nace" Eh haka ne amma yanzu kiyi hak'uri
yana hutawa ne bai buk'atar ganin kowa sai ni kije zuwa dare kya dawo in ya zama
dole ku had'u yau d'in "

Ina gama fad'i na maida k'ofar na rufe ,

Cikin zafin zuciya Fadlah ta tun karo k'ofar da niyar hankad'awa amma wata
zuciyar tace "Bari karki bada kanki sai kace wawiya bari da sannu ki rama"
Juyawa tai zuwa nata gidan cikin b'acin rai,ta Sani sarai UK na skl a wannan
lokacin daman ta rasa yanda zatai ne yasa ta biyo ta wannan hanyar don ta hanashi
zaman lfy da matar da yake ikirarin yanzu a kanta zai iya b'atawa kowa rai,don tun
randa suka zo k'asar ta san sunzo kuma data nunamai tasan da zuwan namu kai tsaye
ya jamata kunne kan karta kuskura ta taka ko k'ofar gidan sa don bai son abunda
zai b'ata ran matar sa, abunda yai mata ciwo kenan gashi yanzu ko kad'an bai bari
su had'u ko a skl tsare gida yake gashi Allah ya jarrabi zuciyarta da tsananin
kaunarsa da sonsa.

K'wafa tai tana k'ara fad'in zata k'ara sasu a tarko na gaba,don ta fahimci y'ar
Arabic d'in da yake zagi da kushewa yanzu ta zama babban reshe cikin zuciyar sa.

Ni kuwa k'unci b'acin rai da kishi duk sun cikamin zuciyata nan da nan shed'an ya
fara k'iyostomin wasu abubuwa cikin raina,na fara tunanin kodai mijina Neman mata
yake ko yarinyarsa ce dai wannan tunda zuwanta biyu gidan yanzu kuma daga ganin
yanayin yarinyar ma batada wata ishashahiyar Tarbiya, zugi zuciyata ta
shigayi,haka na zauna ina sak'awa da kuncewa har wajan awa guda, naga zaman
bazaimin ba na tashi na shiga ayyukana,inajin yanata kirana a waya nai mirsisi
nak'i d'agawa , abuncin rana na shirya Sakwara nai tunda daman munada garin
sakwarar na tuk'a tare da miyar agushi da taji ishashshan kifi da ganda, na had'a
lemon kwakwa dayasha Madara nasa a fridge. Lokacin dana duba agogo naga baifi saura
30 minutes ya fito a lecture ba kai tsaye wanka na shige a gaggauce na shirya cikin
doguwar riga k'irar dubai nai Rolling kaina da D'an madaidaicin mayafi nasa
takalmi kalan kayan na fito tare da key d'in motar na rife gidan.

Sanda na shiga skl d'in sun jima da fitowa a lecture d'in ina parking naga ya
tunkaro motar fuskar sa d'auke da fara'a, kamar yanda na saba kafin ya k'araso na
bud'e mai motar yana shiga ya kamo hannayena yana fad'in "Kin tayar min da hankali
matata wlh har zuciyata ta fara bugawa bai tunanin ko wani abune ya sameki naga
inata kiran wayarki baki d'aga ba ,gashi bikizo d'auka na ba harna fara tunanin in
hau motan friend d'ina ya saukeni sai kuma gaki".
Danne fishina nai na k'ak'alo mirmishin k'arfin hali nace " Sorry dear aikine ya
rik'eni ina kitchen banga kiran ba saida na fito kuma kafin in shirya lokaci ya
tafi ".

Ajiyar zuciya ya sauke yana rungumeni yace " Har hankalina ya kwanta,amma da kam
zuciyata ta fara shiga rud'u".

Dakewa nai nace "oh Reality d'an cikani mu k'arasa gida tukun".

Janyewa yai yana mirmishi yace " amma kodm d'an kiss bikiyimin ba"

D'an kissing d'inshi nai na tada motar muka fita a skl d'in hannunsa na jikina
".

Koda mukaje gida danne zuciyata nai tayi don nafison inyi kishi me aji na Wanda
tasan me takeyi,don haka kamar yanda na saba mai komai haka na taimaka mai yai
wanka mukai salla koda mukazo cin abunci yanda muka saba haka nai mai,amma me wai
duk wannan daurewar da nake ina sawa zuciyata k'warin gwiwa ya fuskanci akwai wani
abu a k'ark'ashin raina don haka ya kamoni jikinsa tare dayin k'asa da murya yace "
My khadeey wai meke faruwa ko bakida lfy ne naga kamar yanayinki ya d'an canja".

K'ak'alo mirmishi nai nace "a'a ba komai lfy ta qlau kawai dai ajizancine irin
na D'an Adam".

Shafa kaina yai yana fad'in " indai bakyajin dad'i dai ki sanar dani muje kiga
doctor ".

Bance komai ba sai d'an mirmishi na kamo gemun sa ina d'an wasa dashi.

Da yamma yace muje mu d'an zaga gari ko zan dawo normal, kallon sa nai nace "
Bafa komai dear ba abunda ke damuna".

Dagewa yai shidai mu fita inga k'ara ganin gari,ban soba don zuciyata banjin
dad'inta haka na daure na shirya muka fice, shike driving d'in muna tafe muna d'an
hiranmu, wajan shan iska ya kaimu muka samu gefe guda kusa da wani ruwa muka
zauna, wajan yamin dad'i yanda k'amshin furannin ke tashi a wajan ga wata iska me
sanyi dake ratsa mutum ga ruwa nata gudu ta cikin duwatsu,hakan yasa naji duk wani
bak'in cikina ya yaye nishad'i ya mamaye zuciyata, hiranmu muke irinta Masoya cike
da shauk'i muna shan ice cream, kujera d'aya muke zaune don haka ne muke manne da
juna, yana tsokanata yakai ice cream d'in bakin sa ashe cokalin bai saitu ba ya
b'ata mai suk gashin bakinsa har gemu,dariya nake sosai ina tafa‹ hannu,cikin wasa
yasha mur yana fad'in "kin sa na b'ata bakina kuma kina min dariya ko zan kamaki".

Cikin dariya na kamo camera d'in wayata na shiga buga mana selfie ina dariya,
ganin dariyar tawa tak'i k'arewa yasa ya kamoni ya matseni cikin jikin sa, cikin
tun tsira da'riya nake fad'in " tsaya tsaya in goge maka kaji na daina ".
Sassauta rik'on da yai min yai a hankali nasa harshena na shiga lashe suk inda
ice cream d'in ya tab'a,lumshe ido ya shigayi yana wani k'ara rik'eni,d'an janyewa
nai ganin ya fara tafiya wata nahiyar don nasan ya manta ba a gida muke ba.

Fadhal wacce take zaune can nesa damu tana kallon duk abunda mukeyi zuciyar ta
ta gama kumbura,don tun fitarmu daga gida akan idon ta ta fito zata unguwa taga
tashin motar mu haka kawai taji ziciyarta ta raya mata tabi sahunmu don haka a
hankali taita binmu har gun,koda mukaje tai nesa inda bazamu gantaba amma ita tana
kallon duk motsinmu, abunda muke yasa take ganin ma kamar ma da gayya muke don haka
zuciyarta ta rink'a k'issima mata taje ta shak'oni kawai wata zuciyar kuma tace
zuwa zaki ki wargatsa wannan farin cikin da suke ciki ki haddasa fitina a tsakanin
su,da wannan shawarar tai amfani ta mik'e kai tsaye tayo gurinmu.

Nuna mai pic's d'in nake shima yanata dariya kawai mukaga mace tazo ta zauna a
kujerar dake daura da tamu ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana kad'asu cikin
wata lank'washashahiyar murya tace " my hubbey ashe kana nan kana shan iska,yanzu
na k'araso wajan kawai naji k'amshin turarenka,nan zuciyata ta tabbatar min kana
gun ina wara idanuwa kuwa na hangoka".

Tamke fuska yai matuk'a yace "Ke fadlah wai wace irin mace ce me zuciyar
tunkiyoyi,me ya kawoki nan eh".

Kad'a ido tai cikin iya duniya tace " Ah kasan mun saba zuwa wajan nan dakai ko
wace yammaci,to kwana biyun ma da k'arfen k'afa tazo maka in kewarka ta dameni sai
inzo in d'ansha iska d'azu da safe ma naje gida Neman ka don idona yana tsananin
son kallonka a lokacin amma waccan tace min wai kana bacci ta hanani ganin ka ,
yau kuma sai gashi mun had'u,gaskiya my heart nayi missing d'inka sosai fa,ka gane
kawai ta fad'a tana kashe mai ido ".

Mik'ewa yai cikin zafin nama zai kwasheta da mari yana fad'in" ke ni zaki
rainawa hankali,yaushe muka tab'a zuwa nan dake don uwarki,banza mayya na fad'a
miki bazan aurekiba bazan iya auranki ba,inada mata ta data fiki komai kuma dukkan
zuciyata tata ce,babu wani sauran wajan wata mace a cikin ta".

Kamoshi nai ganin yanda yake balbala masifa na kashe murya cikin salona "haba
Reality me yasa kake tada jijiyoyin ka akan d'an wannan maganar,don Allah karka
wahalarmin da kanka kasa b'acin rai aranka,kan abunda bai kai ya kawo ba, cool
down my man, muje gida kawai don ina buk'atar hutawa a jikin ka kaji shimfid'ata
mayafina farin cikina".

Na k'arasa ina manna mishi kiss a leb'ansa naja hannunsa mukai parking lot don
d'aukan motar mu, muna tafiya ina jiyo muryan ta tanata bala'i tana fad'in " Banza
munafikin mata,sau nawa kake fad'awa duniya babu abunda zakai da mace kalar wannan
kai mijin wayayyiyar mace ne,kullum fad'a kake auran dole akaima amma don
munafirci shine yanzu a gabanta kake fad'in itace zab'inka".

Fizge hannunsa yai zai koma nai saurin rik'oshi fuskata a d'aure nace "kome tace
kai kaja tunda kana mu'amala da ita don haka bakada bakin cewa komai yanzu, ni ka
maidani gida in zaka dawo sai ka dawo".

Ina fad'a na bud'e mirfin motar na shige, jiki a sanyaye ya bud'e shima ya
shigo, bayan yayi wa motar key mun d'au hanya sosai ya sako hannun shi zai kama
nawa na janye ina kauda idona zuwa kallon titi, kallona yai yaga yanda na k'ara
tsare gida nan jikinsa ya k'ara yin sanyi cikin sanyayyar murya yace " kar kiyi
fishi dani zuciyata karki yarda da maganar wannan mahaukaciyar yarinyar".

Katseshi nai da sauri ta hanyar d'aga hannun nace "ka bar wannan maganar don
Allah bana buk'atar jinta ko kad'an don na riga na gama jin komai daga bakinta
kuma".

Jan bakinsa yai yai shiru yana tunanin irin hukunci da zai d'auka akan fadlah
data had'a mai wannan gwaramar.

Taku ce
Layuza kabir Adam
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร*_

https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*'YAN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

0⃣4⃣4⃣
0⃣4⃣4⃣ 0⃣4⃣4⃣
A haka muka k'arasa gida kowa zuciya ba dad'i, Allah yasa muna shigama ana kiran
magriba don haka hankalinmu ya koma gayin salla,yana fita masallaci na tada tawa a
cikin sallar nake kaiwa Allah kuka kan ya tsare kuma ya kare min mijina ya
tsareshi daga sharrin masharratan mata,harya dawo ina zaune kan prayer mat d'in ina
y'an addu'o'i na,ganin yazo ya Sani a gaba yasa na shafa na tashi, fuska ba
walwala,cire kayan sallar nai na d'auko wata figigiyar riga nasa,kai tsaye na wuce
kitchen na had'a mana abuncin dana girka kafin mu fita, bayan na gama jera komai na
shigo d'akin taddashi nai kwance ya dafe kansa yana tunanin, a d'an dake nace " na
shirya abinci".

Shiru bai ce komai ba,ganin ina tsaye shiru kawai na juya zan fita, cikin
sanyin murya yace "Deejahhh ".

Ban amsa ba kuma ban juyoba,sai dai tsayawa danai cak, a hankali naji ya taso
yana taho wa, had'a ni yai da jikinsa yana k'ok'arin juyo dani,a hankali na lumshe
idona don ban sonma k'wayar idona ta shiga cikin tashi, zubawa fuskata ido yai yana
nazarin canjawa ta lokaci guda,

" my Deejahhh don Allah ki tsaya ki saurreni,ki tsaya na fad'a miki tsakanina da
yarinyar nan kinji".

D'an zamewa nai ina kauda idona nace "ka bar wannan maganar fa ta riga ta
wuce,muje muci abinci kawai".
Ina fad'a na rik'o hannunsa zuwa parlourn.

Abincina nakeci hankali kwance shi kuwa sai juya cokalin yake yana d'iba sama
sama,fuskarsa cike taf da damuwa

Nasan shi sarai bai wasa da cikinsa ko kad'an don haka yau yanda naga yana cin
abuncin sai yaso ya karyamin zuciya,amma wani tunanin danai saina dake,tashi kawai
nai naje na wanke bakina na dawo har lokacin bai wani ci abun kirki ba, zama nai na
jawo abincin gabana nasa spoon d'in na fara bashi da kaina, kamar wani lusarin
yaro haka yake k'arb'ar abincin yanaci,saida na tabbatar yaje gejin dayake k'oshi
sannan na ajiye na bashi lemon yasha.

Kayan na had'a nakai kitchen, ya san saina wankesu tas zan fito don haka yabiyo
bayana, kamar yanda muka saba ina wankewa yana kifemin su, harna gama na gyara
wajan, lokacin sallar isha'i yayi don muna fitowa na wuce toilet na d'aura alwala,
shi kam kuskure bakinsa yai don yanada alwalar sa yayi masallaci ni kuma na tada
tawa.

Ranar haka muka kwana kowa da tunanin dake ransa,amma duk da haka bamu nisanci
junaba a gado,duk da ba wai yanda muka saba nanike juna mukai ba,amma kawunanmu na
jere kan pillow d'aya muna shak'ar numfashin juna.

******

Duk fa yanda UK yaso tada zancan nan nak'i bashi dama,koya d'auko maganar sai
ince ya wuce yabar zancen,duk hankalinsa yak'i kwanciya ko school ya daina shiga
in nace mai school sai yace bazaijeba, nikuwa in shareshi abuna, amma duk abunda
yake na hak'k'insa zan mai ko a gado ya nemeni zan bashi had'in kai sosai musha
k'aunar mu,ammafa da safe ba fara'a, wato shiruma amsa ce, hukuncin shiru yafi
komai hukuntawa, shi anashi b'angaran yafiso in tsaya muyi maganar baki da baki
ya fad'a min ko wace Fadlah don yasan maganganun datai a gabana zai samin zargin ko
nemanta yake Wanda shi yafi d'aga hankalinsa.

Kwana biyar muka d'auka cikin wannan yanayin, Wanda harya fad'a sabida rashin
nutsuwa rashin ganin fara'a ta walwalata kad'ai yasa shi rama,yama rasa ya zaiyi da
ransa, ban tab'a tunanin a zahiri haka mijina ke sona ba sai yanzu na tabbatar
kuma na gasgata don haka yau kam na d'au aniyar kwantar mai da hankali duk da
tsananin kishin fadlah na zuciyata.

Bayan sallar isha ya shigo jiki a sab'ule hannayena d'auke da ledoji,ya zubesu
tsakiyar parlour, ina zaune kan kujera two seater hankalina nakan T.V ,jikina
sanye da riga da wando kalan peak da fari na roba sun kama jikina tsam rabin
albarkatun k'irjina a waje suke ga mazaunaina sun matse cikin wandon wanda yake iya
gwiwata rigar ma hannunta iya dantsena yake, kaina babu hula sai gashina dana
fakeshi nasa masa ribbon fari.

D'an d'ago da kaina nai na kalleshi fuskata ba yabo ba fallasa,nace mai


"welcome dear".

K'arasowa yai kusa dani ya duk'o tare da kissing d'in lips d'ina yana shafa
gefan fuskata yace" sannu da hutawa my Deejah sarauniyar mata".

D'an mirmishi kawai nai na mik'e ina fad'in "bari in baka lemo".

Ina tafiya ina kad'a mazaunaina don nasan idonsa na kaina,


Wata ajiyar zuciya ya sauke yana lasar lips d'in shi, tare da tunanin kalar
baiwar jiki da Allah yai min,

Dawowa nai d'auke da Ruwa da lemo tare da glass cup akan flat zama nai kan
hannun kujerar da yake kai na tsiya yamai lemon ina mik'a mai, idonsa akan k'irjina
ya amsa cup d'in yanawa albarkatun k'irjina wani mayen kallo ganin yana neman zuba
min lemon ajiki yasa cikin muryan shagwab'a nace " Wai kallon na mene haka
Reality ?".

Lumshe idonsa yai yana D'an kurb'ar lemon, kad'an yasha ya mik'omin nasa hannu
zan amsa ya damk'e hannun nawa cikin nashi yana busamin wata iska kan k'irjina,wata
gwauruwar ajiyar zuciya na sauke ina fad'in "Yah ".

Hannunsa d'aya yasa ya fara shafo saman k'rjin nawa, yarr yarrr tsikan jikina
ta tashi cup d'in dake hannunmu ban San ya akaiba kawai naji lemon ya zube a jikina
y'ar k'ara nasa ina duba yanda lemon ya b'atamin kaya " wayyo Allah, Reality ji
ka b'atamin kwalliya na ,Allah Allah ni bazan yaddaba ni ka biyani kayana".

Had'e hannayan sa yai alamar ban hak'uri yana marairaice fuska "pls pls my
Deejah kece fa kika rikitani nama rasa me zanyi har cup d'in ya fad'i a jikin ki,
pls kiyi hak'uri kinji my heart👏 ".

Turo bakina gaba nai cikin salon shagwab'a nace " To to nidai na ciremin kayan
kayi min wanka,sannan ka wanke min kayana".

Jiki na rawa yaji banza ta fad'i ya fara fad'in "To indai wannan ne karki damu
duka zanyi kinji beauty nah".
Mik'ar dani tsaye yai ya fara k'ok'arin ciremin rigar, ni kuwa na wani saki
jiki kamar yarinya, bayan ya cire rigar ya zagaya ya b'alle min bra d'in wowww nan
fa kayan kallo suka bayyana,mai makon yaci gaba da aikinsa sai kawai naga yasa
hannayensa biyu kan tweens d'ina yana musu shafar y'ay'an kyanwa,🐯

Bank'arewa nai na fara bubbuga k'afa Wanda hakan ya baya Boob's d'ina damar yin
tsalle suma🙊, luuu ya shagala da kallon su yana wani had'iyar yawu,ina sane naci
gaba da tsallena ina yarfe hannu,
Ya ilahi ya furta lokacin da duk wani na'ura ta jikinsa ke had'a shock, idanuwana
dake rufe na bud'e jin ya fizgoni jikinsa ya shiga shafa ni tako ina jikinsa na
rawa, Kai namiji ma dai in ya shiga wannan level d'in zama mara hankali yake sam😃,
Tuttureshi nake ina fad'in "nidai kaje kamin wanka na, ba haka nace kayi ba ".

Bai saurareniba yaci gaba da bidirinsa musamman a kan Na shanuna,jin dayai


bakina yak'i mutuwa sai rigima nake mai,ya cafke harshena yai mai kyakyawon
ladabtarwa,ai kuwa nai lif ina amsar hukunci 🙊😂.

To nidai ban San ya akaiba kawai na ganmu kwance kan 3 seater muna ta bitar
karatu, hannayensa yasa ya zame 3 quarter wandon dake jikina, sai a sannan na tuna
ashefa yau in up ne,don haka na rik'e hannayensa daga k'ok'arin da suke na zame
D'an pant d'in, cikin muryar data ladaftu da zafafan darusa nace " Pls banida
tsarki fa".

Bai yarda ba saida yasa hannu ya tab'o sannan ya maida hankalinsa ga sauran
sassan jikina, had'in kan da bai zato ba ya samu don saida na tsotseshi tass na
fitar mai da . . . . . .😜 , sannan muka saki juna muna maida numfashi me d'auke da
dad'i da gajiya.

Sai bayan mintina goma sannan ya mik'e ya kamani mukai toilet, wanka yamin
tass shima yayi sannan ya mik'omin pad d'ita nasa,muka fito, duk a gajiye muke
nasa y'ar yaloluwar night gown na haye gado,shi kuwa fita yai parlour ya kashe duk
kayan wuta,sannan ya dawo ya kashe na d'akin ya fad'o kan gadon yana fad'in "kai
wannan yarinyar ta galabaitar dani fa,mirmishi nai ina juya bayana ya kamoni
jikinsa yana dariya,a hankali yake shafa bayana zuwa gashina, ajiyar zuciya me cike
fom da tsantsar son juna muke saukewa, a cikin wata cool voice yake fad'in " Nahna
Khadeejah ki yafemin kinji,wlh Allah duk maganganun da fadlah ta fad'a kawai sharri
tai min,ban tab'a koda rik'e hannun tab'a da sunan in kusanceta , nasan dai Best
friend d'ina ce kafin muyi aure dake,amma tunda mukai aure babu jituwa tsakanina
da ita,na fad'a mata bazan aure ta ba amma ita ta kafe, nan dai ya kwashe komai
tsakaninsa da Fadlah ya zayyane su cikin kunnuwana, D'an mirmishi nai nace " karka
damu my heart komai ya wuce kaji".

Albarka yaita samin har bacci ya d'aukemu.


Tun daga ranar kuma sai komai ya koma normal, muka ci gaba da shimfid'a
soyayyarmu me tsayawa a rai, a haka kwana kin hutuna suka taho k'arewa nan kuma
damuwa ta fara damun mu na rabuwa da juna,don tabbas zuciyoyinmu da jukkunan mu
zasu d'an d'ana rashi, duk kwanakin nan haka muke yinsu cikin rashin sukuni,
ganin damuwar da muke ciki nace mai zan k'ara sati guda ya zama sati bakwai kenan,
murna kamar zaiyi me nan ya kira Abban sa ya fad'a masa zan k'ara sati d'aya Abban
fad'a ya hau yana fad'in "karatunta fa ya zaka rik'e yarinya bayan ta koma school"

Marairece murya yai yace "Abba itace fa tace zata k'ara satin kuma tace kota
koma school a satin farko lecture bata kankama ba".

Jin haka yasa Abban yace to ba komai.


***********
Siyayya sosai Yakemin ta tsaraba har ca nake tayi ya bari ya bari amma yak'i.

To duk da k'arin satin da muka samu gashi dai yau ya rage kwana biyu cal in
tafi,da safe muna kwance kan gado ya hanani motsawa ko nan da can ya rukunkumeni a
jikinsa yanata lallatsani, a hankali nace " mijina zanyi kewarka wadda ban san
adadinta ba,zan shiga wani hali na rashin ka tare dani".

Shafo fuskata yai yana magana Wanda sai kai da gaskema zaka ji me yake fad'i "
My Deejah duk yanda zakiyi kewana bai kai yanda zanyi nakiba,tun yanzu zuciyata ta
gama raunana,wlh Allah ina ji araina zan hak'ura da wannan course d'in in biki mu
koma gida muci gaba da rayuwar mu tare".

Girgiza kaina nai idona na zubda hawaye nace "a'a karka fad'i haka Reality, kaga
kaci rabi fa muyi hak'uri kamar yaune zaka k'arasa wata bakwai d'in nan ka dawo
gida".

" ina jin wannan wata bakwai d'in kamar shekara bakwai a zuciyata,tabbas nan da
wata uku zanzo gida insha Allah ".

"Tom my ina sauraranka ina maraba da zuwanka kaji".

Haka mukaita musayar kalmomin da zamu kwantarwa da junan mu hankali, a ranar


dai haka muka yini service har saida naji na gaji bazan iya k'arawa ba,don haka
naita binsa da wasanni.

Da dare ma fita muka k'arayi yai min wasu siyayyar muna zagaye cikin mall d'in
ne sai gamu gaban kayan baby haka kawai naji zuciyata ta kwad'aita da d'iban kayan
don haka na shiga jidarsu kamar kamar me,yana can yana d'aukarwa sweety kaya ya
zagayo ya ganni na cika kwando da kayan yara zuba min ido yai cikin mamaki ya
jawoni jikinsa yana D'an mirmishi ya d'ora hab'ansa a saman kafad'ata " Deejah me
zakiyi da kayan Baby haka".

D'an farrr nai da idona nace "Kasani ko kaina nake d'ibarwa".

Nan da nan naga yanayin fuskarsa ya canja ya shiga girgiza kai " a'a mukam baby
ba yanzu ba wlh sai mun huta sosai,ko na dawo Nigeria sai mun sami kamar one year
sannan zamu fara k'ok'arin samun Baby ko".

Wani dammmmm naji gabana ya fad'i, innalillahi wa inna ilaihi ra'jiun, wai daman
wannan ak'idar UK ke da ita,lalle akwai gagarumar matsala a gabana,don gaskiya ni
Allah ya halicci zuciyata da tsananin son yara,ina son haihuwa fisabilillah,don ko
yanzu akace inada ciki zanyi farin ciki in godewa Allah, kai gaskiya duk randa
Allah ya dawo da UK Nigeria saina yak'eshi akan wannan mummunar ak'idar".

Juyo dani yai ina kallon sa yace " ya naga kinyi shiru Baby nah".

Jarumta da dakiya na k'ak'alowa kaina na D'an saki mirmishi ina fad'in "Ah ba
komai fatanmu dai Allah ya bamu masu albarka".

" yawwa mata ta,kinga yanda muke soyayyar nan muke farantawa juna rai da kin
samu ciki komai zai tsaya shike nan sai kiga kin waniyi kalan tsufa duk haka mata
suke yanzu".
D'an mirmishi nai ina basarwa nace"wannan fa siyayyar ta Aunty Amrah ce ita taban
sautu in siyo mata kayan Baby ".
" cikin jin dad'i da gamsuwa yake girgiza kai yana fad'in "OK OK Bari ma a k'ara
mata".

Nan ya shiga jibga wasu akan Wanda na d'iba.

Ni kuwa jikina k'ara mutuwa yai don ban tab'a zaton haka daga UK ba,dukda bai
tab'a nuna min daman yana sha'awar Baby ba amma baitab'a cemin bai soba,gaskiya
wlh banji dad'in wannan Maganar ba.

************
Daren da zan bar k'asar nan dare ne me cike da Abubuwan masu yawa,dare ne me tarihi
a rayuwarmu, dare ne Wanda muka ko kasa rintsawa a cikinsa, yanda mu kaga rana haka
mukaga daran nan,mun gurji juna mun mun kashe arna rundina rundina,wani abu daya
tafi da tunanina ya tsayamin a rai yanda a kusan karo na biyar sanda zamuyi
releasing abunda ban tab'a jiba nadaga dad'i shi naji haka ma UK wani kuka yakeyi
yana wani gurnanin dad'i Wanda ya rink'a dukan gadon da hannayensa biyu yana wani
salati cikin shauk'i da gigita, lalle wannan abu bazai fita a rainaba naji dad'in
da ban tab'a zaton akwai shi a cikin sex ba, haka muka kwana hawaye na fita a
idanuwansa Wanda na rasa name ne.

Bayan munyi sallar asuba yau ko karatun bamuyiba ya jawoni muka hau gado duk da
yanzu ba wani abun mukaiba muna dai manne da juna har kusan k'arfe bakwai da rabi
sannan muka tashi mukai wanka,daga nan na d'an samar mana abunda zamuci Sam bamu
wanici abun arzik'i ba don ziciyoyinmu ba dad'i, k'arfe goma jirginmu zai tashi don
haka a gaggauce muka k'ara sa abunda zamuyi,ya fito min da tarin jakunkunana yasa a
mota, tunda muka shiga motar naga ya tadata na fara kuka,jiyowa yai ya d'an kalleni
bai ce komai ba ya maida hankalinsa ga tuk'in da yake rannan nasa a jagule,muna
shiga filin jirgi na k'ara tsananta kukana, bayan ya samu yayi parking ya kamo
hannuwana yana d'an matsawa tare da cije lips d'in shi girgiza min kai yake alamar
rarrashi amma bakin sa ya kasa furta komai,ganin da yai kukan nawa yak'i tsayawa
yasa ya bud'e motar ya rik'oni muka fito a hankali yace " Cool down mana pls
dear".

A hankali nake tsagaita kukan nawa inda matafiya suke zama ya zaunar dani,sannan
ya fito min da jakun kunan kayana, muna zaune hannuwana sark'e cikin nasa yana
d'an matsawa a hankali, shima ajiyar zuciya yake saukewa a hankali muna nan zaune
aka fara kiran fasinja da sauri na fad'a jikinsa ina sakin wani marayan kuka,
bubbuga bayana yake a hankali yana fad'in "kiyi hak'uri kinji insha Allah very soon
ina nan tafe nima".

Ganin fasinjoji nata shiga jirgi yasa ya kama hannayena zuwa gaba dai dai inda
ya dace ya tsaya anan ya tsaya yana janyeni daga jikin sa, hannu yake d'aga min
yana wani mirmishin yak'e kawai sai naga hawaye na tsiyaya daga idonsa a haka muka
rabu idanuwan mu na zubda hawaye.
Taku ce
Layuza kabir Adam
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌸' *YAN* *ARABIC*🌸

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ _and_ _entertain_ _our_ _Reader's_

0⃣4⃣5⃣
0⃣4⃣5⃣ 0⃣4⃣5⃣

Ko acikin jirgin idona bai bar zubda hawaye ba,zuciya cinkushe da rashin
sukuni,wata dattijuwar balarabiya da take zaune gefena ganin datai idanuwa sun
kasa tsaida hawayan ta kamo hannuna cikin hard'ad'd'an larabcinta na gargaliyya
take bani hak'uri wai inyi shiru, jan hanci nai tare da share hawaye na ina gyad'a
mata kai alamar na bari.

Tsawon awannin da mukai cikin jirgin ina duniyar tunanin da kewa.

Ina fitowa cikin jirgin na hango sweety tanata mirmishi tare da d'ago min
hannu, cikin tsananin farin ciki na k'ara sa muka rungume juna, kallona ta tsaya yi
tana dariya tace "Aunty na kece kuwa anya banyi b'atan kaiba".

Dungure mata kai nai nima cikin dariya nace " a'a bani bace sai ki duba cikin
jama'ar wajan ko zaki ganni".

Dariya mukasa baki d'aya ta kamo min kayana drivern daya zo da ita ya k'araso
ya d'ibar mana kayan yasa a mota, bayan mun shiga ta zuba min ido cikin tsokana
"wlh Allah bikiga yanda kikai wani masifar kyau ba Aunty nah,Allah Wanda bai miki
farin sani ba bazai ganeki da wuriba".

" kai don Allah ki daina ni banga wani canjawa danai ba".

Mirmishi tai tana fad'in "zakiji maganganun mutane zaki tabbatar da magana ta".
Nidai dariya kawai nake,a haka muka k'arasa gida Aunty murjah muka samu tsaye
ta taremu cikin farin ciki, don haka kai tsaye sashin su na wuce,muka gaisa cikin
farin ciki Aunty murjah take min sannu da zuwa,ruwa da lemo sweety ta kawo min
nasha, nan Abba ya fito shima cikin fara'a yakemin sannu da zuwa,cikin jin kunya na
sauka kan kujerar nake gaidashi zama yai yana amsa min da dariya kan fuskar sa ca
yake " Sannu da hanya mutanan India ,ya kika barosu".

"Lfy qlau Abbah na sameku lfy".

" lfy qlau Khadeejah ga sweety nan tai kewarki kullum maganar ki".

Dariya nai ina kallon ta ta d'age min gira,


Mun d'an tab'a hira Abba yace "jeki ki huta Khadeejah anjima kyazo muyi hirar
jeki huta kiyi salla kici abinci".

Mik'ewa nai sweety ta biyo bayana tana cewa y'an aikin gidan su kwaso min kayana,
ina shiga na tadda sashin a gyare tsaf sai k'amshi ke tashi, jiyowa nai inaiwa
sweety alamar jinjina nace " sannu da aiki sweetyn mu"

Dariya tai tace "bari a kawo miki abinci kafin ki fito a wankan".

Kai tsaye na shige toilet d'in nai wanka na d'auro alwala, bayan na fito nasa
simple doguwar riga nai salla sannan na dawo parlourn na tarar an shirya min abinci
kala kala zama nai nad'an tsakuri kad'an naci don baccin da nakeji ya kama
idona,sabida kwana bana samun wani bacci,ina hawa gadon kuwa bacci yai gaba dani.

Cikin bacci narink'a jin ringing d'in wayata da k'yar na bud'e ido na jawo
wayar ganin sunan Wanda ke kan wayar yasa da sauri nai picking d'in kiran,
" Baby nah"

Shagwab'e murya nai kamar zan kuka nace "ummmmm Reality nah'

" ina kika shiga nake ta nemanki baki d'aga ba".

"Bacci nake fa,ya kk ya kewana".

" gani nan ba yanda nake Khadeejah kin tafi da sukuni da walwalata tunda na dawo
daga rakaki ina kwance zazzab'i ya rufeni sai yanzu na samu ya sauka na tashi nai
salla, kin samesu lfy yasu Abba ".

" duk lfynsu qlau,amma honey kaci abunci kasha magani".

"Khadeejah ban San Abincin ko kad'an maganin wannan zazzab'in kuma bani da
maganinsa yana gareki kin tafi dashi".

" kayi hak'uri kaji don Allah kaci abunci ko kad'an ne kaji inba haka ba ciwo
zaima yawa ga damuwa,wlh nima jina nake wata iri ban jin dad'in jikina da
zuciyata,kewarka duk ta dabaibayeni".

"Hhhhmmmm baby ke ki nama iya fad'a wlh ni yanzu banma San halin da nake ciki ba
Sam babu walwala tare dani cikin yini guda na fice hayyacina balle tsayin watanni
ya zanyi".

Rarrashin sa na shigayi ina mai kalamai masu dad'i har ya sake mukayi hira sosai
cikin so da k'auna ".

************
Washe gari sai ga Aunty Hafsa da yara murna kamar nace me, na rungumota ina
fad'in" Oyo yo my Aunty itama cikin farin ciki ta ruk'oni muka zauna tana rik'e da
baki tace "a'a Nanah wannan kyau haka har ina,lalle India ta amsheki".

Dariya nai nace " kai Aunty kema haka zakice ni kan banga wani canji ba".

"Ai ke bazaki gani ba,amma masha Allah".

Gaisawa mukai cikin farin ciki,su Ashraf ma suka gaisheni na kamo su jikina ina
fad'in" wayyo yarana sun girma fa,Aunty me kike basu haka ".

Dariya tai tace " hhhhmmmm tsayi ne irin naku suka d'ebo gashi nan sunata yi".

Dariya nai nasa su a jikina "ai mun muki wayo Aunty yara sunyo family d'in
su,Aunty ina Aunty Amrah".

" hhhmmm Khadeejah Amrah ai tai nauyi ta daina fita don yanzu kwana biyu ma
nak'uda take a tsatstsaye wancan satin ma sai da mukaje Asibiti".

"Ayya kice ta kusa sauka,Allah ya raba lfy".

Ameen ya Allah, ai badan wancan cikinma ya lalace ba ai da tuni yaro ya fara


zama,wlh tana shan wahalar cikin nan sosai, gashi Usman sam ya hana ta tafi gida
shi ba a gari yake ba amma yace bazata wankan jego ba wai k'auyanci ne,shine yasa
aka kawo innar ta take zaune da ita".

" wayyo harta ban tausayi wlh".

"Hhhmmm kema haka zaki kawo mana Baby soon".

Zaro ido nai ina cewa " Aunty rufamin asiri don Allah ".

"Hhhmmm kyama fad'a".

Tashi nai na kawo musu lemo da ruwa, duk inda nai Aunty bina take da ido tana
fad'in " masha Allah Nahna kin canja sosai wlh ".

Nidai sai dai inyi dariya kawai,hira sosai muke da Aunty Tace bari ta shiga su
gaisa da Aunty murjah, hijab d'ina nasa na rakata , tarb'a ta kirki ta mata kamar
yanda suka saba,bayan sun gaisa suka d'an tab'a hira sannan muka taso,Aunty murjah
tace " Khadeejah karfa ki wahalar da kanki ga girki nan an had'a daku anan ".

"Tom Aunty mun gode Allah ya saka da alkairi".

Da muka dawo shashi na na fitowa da Aunty tarin tsarabar dana zo da ita nace
ta tayani fitarwa kowa, kallona tai tace " kamar wadda kikaje saudiya wannan
tsaraba haka".
"Hhhhmmmm Aunty wlh nai nai ya barta yak'i haka yaita min siyayya kamar me".

D'an mirmishi tai tace " zama yai dad'i kenan ".

Dariya kawai nai na shiga fiffitar da kayan, Yaya na na fitarwa tsaraba sama
data kowa sannan Aunty Hafsa don akoda yaushe su nake kallo gurbin iyayena, sannan
na d'aukarwa Abba riga da wando na Pakistan tunda naga yana sosu, Aunty murjah ma
doguwar riga guda biyu sai turaruka ,su khamees ma Riga da wando su biyun,mutinyata
sweety kuwa siyayya bata wasa ba daman muka mata, sai Aunty Amrah ma na ware mata
nata,kowa dai na ware mai abunda ya dace dashi , wata jaka na zuge na zazzage kayan
ciki Aunty tabini da ido ganin uban yawan kayan yasa ta kalleni tace " Nahna har
an fara siyan kayan Baby hhhhmmmm mun kusa samun Baby kenan".

Kunya ce ta rufeni nace "a'a wlh Aunty kanti muka shiga naga kayan sun min kyau
shine na siyo in anyi haihuwa sai in rink'a barka dasu,kuma kinga ga Aunty Amrah ma
akan hanya ".

Mirmishi kawai tai tabar zancan can k'asan ranta kuma tana fad'in" Ai daman da
ganin wannan kyan ai nasan An samu".

Bayan munyi sallar azahar sweety ta shigo me aiki na binta d'auke da kulolin
abinci, D'an hararanta nai nace " ko lek'oni bikiyi ba tun safe da kika fita ".

Dafe kai tai tana dan mirmishi" wlh Auntyna yai d'in ne sai a slow ina jin wani
iri ne,da dare ai muna tare sorry ".

" OK sannu ".

Juyawa tai ta fita na d'auko mana babban tray na had'a mana abincin harsu Ashraf,
muna ci na kalli Aunty nace " Aunty harna tuno gida wlh yanzu kuwa mutum yaita
cin abinci shi kad'ai ".

Dariya tai kawai taci gaba dacin abincinta.

Bayan sallar la'asar Aunty na shirin tafiya yaya ya kirata a waya wai tai sauri
ta wuce asibiti Amrah nacan ".

Da sauri ta lalibo mayafinta tana cewa " Nahna bari in wuce asibiti su Amrah sun
koma,bari nabar yaran nan driver zaizo ya d'auke su ".

Ganin yanda Aunty ta rikice nima duk sai hankalinsa ya tashi, fitowa mukai tare
naga direbobin gidan duk zaune guda d'aya na kira nace yakai Aunty Private
hospital sabon gari.

Tunda ta tafi minti kad'an nake kiran Aunty a waya tace to inta addu'a dai,duk
jikina ya k'ara sanyi.

Bayan magriba akazo aka d'auki su Ashraf, har sallar isha'i shiru,ina zaune a
d'aki bayan idar da sallata ina azkar naji ringing wayata da sauri nakai ido kan
wayar sunan yaya na dana gani yasa na d'auka da gudu gudu gabana na fad'uwa ina
d'aga wa nace " yaya ta haihu?.

"Alhamdulillah Nahna Amrah ta haihu an sami Namiji".

"Alhamdulillah masha Allah, yaya amma duk suna lafiya ko".


" eh lafiyar su qlau ana gyarasu tukun".

Muna kashe wayar na kira Yaya Usman ina fad'in "Yaya congrat Allah ya raya mana
Baby boy yai mai albarka".

Cikin tsananin farin ciki yake cewa " Ameen Ameen sweet sis yanzu yaya Haroon
yake fad'a min ta sauka an samu Baffa ".

" wayyo Allah Baffana kasa yaya Allah ya raya mana yasa yai halin me sunan".

"Ameen Nahna insha Allah gobe ina hanya ma".

" To Allah ya kawoka lfy ".

Bayan na kashe na kira Honey nah bugu d'aya ya d'aga "my beauty one".

" na'am honey Aunty Amrah ta haihu ta Haifa mana d'a namiji sunan sa Yusuf sunan
Baffan mu ".

" Alhamdulillah Allah ya raya Baby daman ke yake jira ya fito ko".

Dariya nai "eh mana Ashe tun wancan satin take labor Allah yayi ina gida zata
haihu, Honey kamar in tafi yanzu wlh".

" A'a kiyi hak'uri da safe sai kije kinji ".

" Tom Allah ya kaimu ruhina,daga nan muka shiga hira ".

*************
Washe gari kuwa k'arfe goma na gama komai na shiga na gaida Abba nake sanar
mai haihuwar Barka yai yace in naje inyi musu barka,Aunty murjah ma tace in yiwa
su Aunty barka kafin tazo, ita kuwa sweety daman ta tafi school.

A mota ta na tafi cike da d'oki ina addu'ar Allah yasa in samu yaya na a gida
duk da munyi waya yace bai fita ba.

Ina tsayawa k'ofar gidan mu naga yaya na fitowa da motarshi,da sauri nai parking na
fito shima ya ganni don haka ya fito cike da farin ciki k'arasawa nai fara'a kan
fuskata ina fad'in "yaya da ban k'araso yanzuba kenan tafiya zakayi bamu had'u ba.

Dariya yai yana rik'o hannuna yace " To Allah yayi zamu had'u yanzu ko mu k'ara
sa gidan.

Sosai yaya na ya nuna farin cikin ganina bayan mun gaisa yake k'ara tambayata
hanya da India na amsa mai da duk Alhamdulillah, sama sama muka tab'a hira sabida
zai fita ana jiran sa,yai min godiyar tsaraba ya tafi, mota ta naje na k'ara
gyarawa parking sannan na d'auko jakar kayan Babyn da nazo dashi, nunawa Aunty nai
kaya set goma dana zab'owa Baby boy d'in masu masifaffan kyau ,Aunty taita min
godiya,nan na tayata k'arasa aikin gidan tai wanka muka fito zuwa gidan mejegon
dake tun jiya da daran aka sallamesu.

Da d'an ihuna na shiga gidan ina fad'in "Ina Baffa na ayi sauri a mik'omin
shi".

Dariya duk akasa don gidan cike yake da dangin Aunty Amrah,

Masha Allah na fad'i lokacin dana d'auki yaron,sak kamannin sa na y'an gidanmu ne
har bak'ar fatar manyan ido da cikar gashi kana ganinsa kaga tsatson Alk'adi Yusuf
na rungumeshi jikina ina fad'in" Yaro yayo kaman Danginsa yayo takwaran sa sak,
Dariya Aunty Hafsa tai tace "wlh ana haifar sa nace kamar Ashraf yana jinjiri babu
abunda ya rabasu".

Wata mata dake gefe tace " Ai gaskiya Khadeejah kunada k'arfin jini Ku duk
danginku kaman ninku d'aya ".

Dariya nai " Aimu y'an baiwa ne"


Duk aka d'au dariya nan muka gaggaisa da y'an d'akin mukai wa juna barka, matsawa
nai jikin Aunty Amrah ina tsokanan ta cikin raha "Aunty na yadai akwai wahala ne
abar naga duk kinyi wani kala".

D'an gyad'a kai tai irin zaki Sani d'innnan tana mirmishi, k'asa tai sosai da
murya yanda bamai jin me muke fad'a tace " Tace Wlh zaki d'and'ana yarinya in za'a
samu akwai dad'i amma wajan haifowa sai kin kusa mutuwa kima shirya ".

Zaro ido nai nace "kice ba sauk'i?".

Cikin dariyar mugunta tace " wlh ba sauk'i I ciwon arne,balle kinje in had'u da
miji kinsha dad'i Allah yasa kin d'auko ciki ".

Da sauri na rufe bakinta mukasa dariya gaba d'aya, kallon mu duk sukai don basu
San me mukewa dariyar ba, sai na fuske ina jawo jakar kayan dana kawo na mik'awa
Auntyn ta , ana bud'e wa aka shiga yaba kyan kayan guda goma zafafa dasu,nan aka
shiga godiya sai kuma hira ta b'arke,ita kam Aunty Hafsa tashi tai ta shiga kitchen
don yin aiki da d'ora girki tunda gidan bak'i nata zuwa, janye Aunty Amrah tai tace
zatai bacci ta shige d'aki binta nai muka zauna muna hira tana k'ara ban labari kan
ciki da wahalarsa uwa uba ciwon nak'uda,jin haka duk sai jikina ya mutu ta kalleni
tana dariya tace " kin shiga yana yi ko,kinsha dad'i a India zaki gane kuranki a
Nigeria in haihuwa tazo".

Kasancewar babu kunya tsananin da Aunty Amrah ba kamar Aunty Hafsa ba don ita
gurbin uwata na d'auketa tunda ta rik'e ni tun daga yarinta,ita kuwa Aunty Amrah
kusan sa'a muke da ita shi yasa ban damuwa hirarmu muke kwasa irinta mata,
D'an janye ido nai ina fad'in "Allah Aunty Amrah ba komai fa cikin satin da zan
taho nai wanka ".

Dariya tai tace " Tunda kikai wankan baku k'ara had'uwa ba kenan?"
Kallonta nai ina d'an mirmishi nace "um um ,ai satin duka muna manne ma ".

Dariyar mugunta tai tace " Allah yasa kin samu cikin satin ma".

Gabana ne ya fad'i, sai kawai na murmusa, Cikin raina kuwa ina tunanin yanzu ace
inada ciki ya zamu kaya da umar mutumin daya nuna min kai tsaye bai son haihuwa
yanzu,shida yake tunanin shekara biyu nan gaba sannan in samu ciki, lalle in ciki
ya samu a yanzu zaman mu ya shiga garari ban San makomata a gunsa ba .

D'an tab'oni tai tace "ke har kin fara tunanin nak'udar ne".

Dariyar yak'e kawai nai na bar hirar.

Sai yamma lis muka bar gidan nida Aunty Hafsa gida muka koma bayan nai sallar
magriba naci abinci sannan na wuce gida.

******
Shirye shiryen suna aka shiga ba zama,dake Baban boy ma ya dawo sai farin ciki yake
da samun Babyn sa,yanda naga yana rawar k'afa da farin cikin wannan haihuwar sai
abun ya birgeni, nace jibi yanda yaya Usman ke murna Allah ya bashi d'a amma mijina
yana neman tsari da ita yana rok'on Allah ya nesanta mai rabo a kusa, duk sai naji
damuwa ta lullub'eni, na fara nemawa kaina mafita tunda wuri don wlh Allah inya
dawo yacemin zai min abunda zai hanani haihuwa sai dai in ya daina kusanta ta.

********
Ana i gobe suna y'an garinmu suka zo da yawan su,kowa da alkairin sa don a dangin
mu in dai akaiwa Baffa takwara to yaron zai sha hidima matuk'a haka Ashraf yasha
wannan gatan, duk da da wuya kaga wani d'an gidanmu me aure mace ko na miji in dai
mutum nada y'aya maza sai ka samu me sunan Baffan mu, haka sauran gidajan dangi
suke wa Baffanmu takwara tun yana raye har zuwa yanzu.

➖➖➖➖
D'inkuna nai mana nida Aunty Hafsa da Aunty Amrah kala biyu biyu wani tsadaddan
less ne na mana da Atamfa supar duk iri d'aya na bayar akai mana d'inki don kowa
nasan measurements d'inta, sannan nasai mana mayafin da zai hau da less d'in.

Yaya na da yaya Usman ma,duniyar yadi ba shiga na sai musu yadi goma goma kala
d'aya na bayar awajan a musu d'inkin babbar riga da y'ar ciki ,haka na siyawa su
Ashraf suma na bada a d'inka musu,
Banda matsalar kud'i yanzu kudin da suke account d'ina sun shallake tunanina don
kullum mijina da Abban sa cikin samin kud'i suke,don haka naga banda wata matsala
sai dai inta yiwa y'an uwana hidima dasu.

Bayan zuwan y'an Sakkwato da dare muna zaune gidan mu anata hidima nan aka shiga
fiffito da kayan barkar da za'a kai gidan su Amrah kamar yanda al'ada take kowa ya
bada abunda yazo dashi wasu rigunan baby wasu turmin atamfa wasu Shadda, ni kuwa
Pampas ma me d'ari na siya na sai set d'in kayan wanka na k'ara rigunan baby guda
biyar na saka turmin atamfa da shadda yadi goma, don wancan kayan dana kai bai
cikin kayan danginmu nawane daban danai niya, wannan kuwa daman nasan dole kowa a
cikin dangi zai bada abunda Allah ya hore mai, akwatina aka cika da kayan barkar
da safe iyayen mu da yayyan mu zasu kai, kowa yaga hidimar danai sai yamin godiya
dasa albarka,nikam mirmishi kawai nake don banga amfanin samun da bazakayiwa
danginka ba.
Ranar suna kamar yanda yaro yaci Suna Yusuf za'a rink'a kiransa Baffah munso mu
samai lak'ani na y'an gayu me ma'ana amma Yaya Usman k'emagadai yace Baffah yakeso
a rink'a kiran yaron don zaifiji aransa cewa sunan Baffan namu yaci da gaske, haka
kuwa kowa ya d'auka Baffah Baffah, anyi sha'ani anyi bidiri sosai suna yai
armashi mun cakare mun d'au wanka anga munsha anko da matan yayyane na sai kuma
matan yayyanmu na can Sakkwato suka hau k'ananun maganganu da nuna facalanci mu
kuwa ko kulawa bamuyi ba don mun tara jama'a hidimar su ce a gaban mu,ga dangin
mijina Aunty ummu sulaim da Aunty murjah ga sweety, sannan ga friends d'ina duk na
gayyata, haka akasha bikin suna aka watse, duk a gajiye nake nai wanka na fito a
d'akin Aunty Hafsah wayata nata ringing Aunty ta mik'omin tana fad'in "Tun d'azu
mijin ki ke kira kin zamanki a toilet".

Karb'a nai ina mirmishi na kara wayan a kunnena " Jin kalmar farko daya fad'a
yasa na fara bubbuga k'afa zanyi kuka, "Don Allah son Allah honey kai nefa kace
kwana biyu zanyi yaufa akai sunan,gashi duk dangi na nan ana tare kace in tafi
gida yanzu,kuma fa dare ma yayi k'arfe tara fa my heart".

K'ara cije Lip's d'insa yai daga can b'angaran yace " Deejah nah tunda akai
haihuwar nan kin rage bani kulawa kullum kina gida da rana bama samun waya da dare
kuma kiyi saurin bacci wai kin gaji, kin dan halin da nake ciki kuwa?"
Zama nai gefan gadon jin yanda muryan sa ta canja, Allah yasa na kowa a d'akin na
k'ara k'asa da murya "Kayi hak'uri kaji mijina zuciya ta nasan kana daurewa ka
k'ara insha Allah wata rana muna tare babu abunda zai rabamu kullum kullum ina
cikin jikin ka ina wasa da abuna ko?"

Numfashi yaja yana matse k'afarsa yace "Deejah nah! Ina cikin halin da nake
neman d'aukin ki kinsan dai halin da nake ciki kin San me nake buk'ata a irin
wannan yana yin, gashi kina cikin mutane babu damar ki kwantar min da hankali
yanda nake buk'ata shi yasa nace ki koma gida ki kula dani".

Rik'e kaina nai ina tunani shin ina zan kwanta ni kad'ai in kula da mijina muyi
waya wadda yake so muyi in fad'a mishi duk kalan kalmomin da yake so in fad'a mai
da zasu rage mai tsananin sha'awar dake tare dashi,k'ara d'aga ido nai na kalli
agogo lokacin tara da minti hud'u a hankali nace " Ina zuwa ka ban y'an mintina
kad'an kaji ".

Kashe wayan nai na tashi na bud'e jakata doguwar riga nasa na yafa mayafinta ko
mai ban tsaya shafawa ba na d'auki key d'in mota ta da wayoyina na fito parlour
Wanda yake damk'am da jama'a , kowa bina yai da kallo na k'ok'aro mirmishi ina zama
gefan kujera yayin da Aunty Hafsa ta cillo min tambaya " ina zaki naga kin d'auko
key?"

Dafe kai ne irin da matsala d'innan nace "gida zanje yanzu Umar ya kirani wai
akwai wata takar da a d'akin sa in dubata akwai cord ajiki in tura mai zaiyi amfani
dashi a skl d'in su kuma yanzu ake so ya tura,shine zanje in duba in tura mai in
dawo".

Caraf Aunty juwairiyya tace " a'a auta in kin tafi bazaki biyo dare ki dawo ba
kiyi kwanciyar ki da safe sai ki dawo muyi sallama in zamu wuce,yaushe zaki tafi
yanzu kuma ki zauna duba takarda har ki tura mai ki dawo ai sai bayan goma".

Kowa ya d'auka eh eh in kwanciyata kawai innaje".

Mik'ewa nai ina musu sallama na fice.


Na d'au hanya sosai naji kiran ya k'ara shigowa hannu nasa na d'aga wayan tare da
sata hand free "hello shimfid'ata me kike ne har yanzu ".

" kayi hak'uri gani akan hanyar komawa gida ne ina driven ".

Cikin mamaki da zumud'i yace "da gaske kike don Allah ko tsokanata ?".

",Allah da gaske bari in k'ara sa tukun".

Kashe wayan yai yana juyi kan gadon nasa a fili ya furta " Allah na gode ma
daka azurtani da mace irin Khadeejah, hankali nutsuwa biyayya soyayya duka nata
ne,Khadeejah me ajiye farin cikinta ne ta d'auki nawa ko zai k'untata mata,nasan
yanzu tana cikin dangi tana nishad'in ta amma sabida farin cikina ta koma
gida,Allah kaiwa Khadeejah albarka duniya da lahira".

Ina shiga gidan naga sweety ta fito yiwa saurayin ta rakiya bakin motar sa,
bayan ta sallameshi ta k'araso inda nake da tambayar "Aunty nah lfy na ganki kin
dawo yau".

Bayanin da naiwa y'an gidan mu shi nai mata, jim tai tana fad'in" Ayya gaskiya
broth ya had'aki da aiki,bari in canja kaya in shigo tace min tana wucewa ciki,

Ina shiga d'akina na fad'a na cire kayana tare dasa rigar baccina sai da
nasawa k'ofar key sannan na hau gadon ina kiran wayar sa ringing d'in farko ya
d'aga " My Deejah"

"Na'am reality nazo gida harnai shirin bacci ma"

"Sannu kinji Allah yai miki albarka, gobe da safe saiki koma kiyiwa su Mama
sallama ko".

" eh haka za'ai"

"Kiyi hak'uri kinji wlh na rasa yanda zanyi ne yasa na takura ki,marata ciwo
kamar zata fashe".

" sannu kaji Honey da muna tare da tuni ina jikinka ina wasa da ita ko".

"Washh Allah don Allah kizo gareni yanzu".

" ba yanda zanyi ne mijina nima a buk'ace nake da kai duk jikina kewanka yake
harma tweens d'in ka duk suna buk'atar ka. . . .".

Kalmomi masu zafi nake fad'a mai Wanda suka k'arasa rikitashi daga nan na shiga
fad'a mishi Wanda suka kwantar mai da hankali, har k'arfe biyun dare sannan muka
kwanta.

K'arfe bakwai na shirya na koma gida wasuma ko tashi a bacci basu bai sai gani
na sukai, nima bayan na karya bacci me nauyi ya d'auke ni, ban farka ba sai sha
d'aya, wajan k'arfe biyu motocin da zasu d'aukesu suka zo ba b'ata lokaci mukai
sallama dasu suka d'au hanya.
************
Rayuwa ta mik'a na koma school inda muke ta karatu ba kama hannun yaro, b'angaran
rayuta da mijina kuwa Masha Allah don sosai yake nuna min kulawa,kullum k'ara
k'aunar junan mu muke cike da kulawa.

Wani abu d'aya daya fara shigar min rayuwa shine yanda naga jini namin wasa
wani sa'in sai in ganshi kad'an yazo wani sa'in kuma ya d'auke a haka naketa bin
sa in yazo in aje ibada inya tafi inyi tsarki, ban jin wani canji a jikina amma
kuma ciwon kai ba'a magana kullum dashi nake kwana nake yini,harya zame min jiki
tun inashan magani na daina kawai na alak'anta hakan da tsananin karatu don yanzu
da mukai nisa karatun yafi zafi, yanzu wata na biyu da sati biyu da dawowa daga
India banyi wani cikakken jini ba sai d'is d'is dinnan da nake gani don haka yau
kam nace zanje ganin likita bisa takuramin da umar yai kan inje inga likita kar
wata cuta ta shigeni,k'arfe wajan Tara ba isa asibitin bayan yin duk abunda ya dace
na isa ga likita ina sanar mai matsala turani yai amin tes kusan guda hud'u yace
in dawo Washe gari amin scanning a marata,haka na dawo gida ina addu'ar Allah yasa
ba wata babbar cuta bace ta kamani, haka na kwana ba dad'i Washe gari kuwa daga
makaranta ina fitowa lecture ta farko na tafi asibitin, anyi scanning sukace awa
biyu in jirasu, school na koma awa biyun na koma,kai tsaye likita ya tabbatar min
ina d'auke da cikin sati goma,amma cikin wasa yakeyi in ba'ai da gaske ba zai b'are
ne tunda ina zubar da wannan jinin kad'an lokaci lokaci, bayanin yanda zan kula da
kaina da cikin yamin sannan ya rubutamin wasu uban magunguna harda ba k'arin jini.

Da k'yar na k'ara sa ga mota ta ina shiga na dafe kaina duk ilahirin jikina rawa
yake gabana na fad'uwa ban San halin da nake ciki ba, tunani nake ya zanyi in
wannan labarin yaje ga kunnan umar me zai biyo baya yaya rayuwar Abunda zan aura
zata kasance tunda uban bai so bai marmarin samun d'a yanzu,to shinma cikin zai
zaunane tunda likita yace min rawa yake bai zama lalle yai k'wari ba,innalillahi wa
inna ilaihi ra'jiun ina mafita ga rayuwata ni Khadeejah shafa fatar cikin cikina
nai ina jin wata nutsuwa na saukar min in har Allah ya bani d'a ko y'a a wannan
rayuwar ya gama min komai kawai sai dai in nemi lahira.

_Shin_ _ya_ _zata_ _kaya_ _ne_ _da_ _wannan_ _cikin_ ?🤔

Y'an uwa mu had'u bayan salla insha Allah, ibadar da zamu shiga ibada ce wadda me
rabo ke riskarta,muna rok'on uban giji ya datar damu ya samu cikin y'antattun bayin
sa🙏
Taku ce
Layuza kabir Adam
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🌸🌸🌸🌸
🌸 *'YAN ARABIC* 🌸

NA

LAYUZA KABIR ADAM

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*

📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

Masha Allah fan's ina fatan munyi salla lafiya,Allah ya karb'i ibadun mu ya
maimaita mana👏

0⃣4⃣6⃣
0⃣4⃣6⃣ 0⃣4⃣6⃣

Da k'yar na kai kaina gida don banma bi ta kan wata skl ba, key nasa na bud'e pat
d'ina na shiga duk kayan hannuna na watsar na fad'a kujera na kwanta dafe da
kaina,zuciyata ta cushe nama rasa wane tunani ne zanyi, Meye mafita meye madafa
gareni,me zanyi dariya ko kuka, tabbas ya dace inyi dariyar rabauta da samun ciki
don baiwa ce me girma gareni,kuma tabbas ya dace inyi kukan makoma a wajan mijina
sa'ilin da yai karo da wannan zancan, tunda bai so bai marmari, sama da awa guda
ina kokawa da zuciyata wajan samowa kaina mafita amma hakan bai yuyu ba,daga bisani
Allah ya taimakeni bacci me nauyi yai gaba dani Wanda ya d'aukeni har tsawon awa
uku,sanda na farka k'arfe biyu a kasalance na tashi na daddafa zuwa toilet wanka
nai tare da d'auro Alwala, Sallar azahar nai nan na zauna ina godiya ga Allah bisa
kyautar dayamin sannan nakai kukana gun sa don ya share min hawayena ya dasawa
mijina k'aunar haihuwa ya samai farin ciki a lokacin da wannan labarin zai
riskeshi.

Yau kam haka na yini sukuku ba wani kuzari y'an class d'in mu suka kirani jin
shiru ban dawoba nace musu banjin dad'i na wuce gida, lokacin da sweety ma ta shigo
ta taddani zaune na rafka tagumi tace yadai D'an sakin fuska nai nace mata ba komai
kawai kaina ke damuna da ciwo tace to insha magani nace mata nasha kawai, haka
nakai har dare ba sukuni,ko UK daya kirani ina yin sallama ya fuskanci da damuwa
tambaya ta ya shigayi meye damuwata ,shima cemai nai gajiyan skl ce ta samin ciwon
kai kuma nasha magani bacci ma nakeji, sallama yamin yace in bacci na kawai da safe
ma had'u,daman hakan nafi buk'ata don haka na kashe wayan na kwanta zuciyata cike
da tunani.
Da safe dana tashi na d'anji sassaucin zuciyata don haka na lallab'a na tafi
skl, ban wani sakeba haka dai ganinan har k'awayena na fadin in koma gida tunda
banjin dad'i nace musu kawai ba komai zan iya, ana tashi kuwa daga skl d'in na biya
pharmacy nasai magungunan da likitan ya rubutamin sannan nayo gida.

Tunda na fara shan magungunan sai naji jikina yamin dad'i na Sami k'arfi sannan
ciwon kanma na dainaji, tunfa daga nan kuma sai lafiya ta wadaceni sosai don haka
na tabbatar magungunan sun karb'eni k'ara dagewa nai da shansu ban wasa ko kad'an,
zancan damuwa kuwa na yakicewa zuciyata na fidda abun a raina, na k'udurtawa kaina
bazan tab'a fad'awa mijina inada ciki ba,kowa ma bazan fad'a mai ba, sai randa ya
fito kowa ya gani, a lokacin kuma zan shirya karb'ar duk wani hukunci daga me
cikin wato uk.

Maida kai nai sosai a karatuna don semester d'in mu ta k'arshe ce, kuma babu
sauk'i a exam's na tabbata, b'angare d'aya ina k'ara godewa Allah daya wadatani da
lfy duk irin wannan laulayin na masu ciki banayi ciwon kanma tunda na fara shan
magungunan nan ya kama gabansa,har wani kuzari nakeji a jikina koda yaushe, hakan
yasa na k'ara sakewa da mijina koda yaushe d'inke muke muna k'ara narkewa cikin
k'aunar juna, shirin da yake na zuwa kawo mana ziyara ya rushe dalilin matsesu da
akai skl ana turasu camfanoni da yawa yanzu basa zama ma cikin skl d'in don haka
koda ya nemi excuse ma basu bashi ba,lokacin da yake fad'amin kamar zai kuka cike
da b'acin rai yake, dukda nima naji ba dad'i don ina buk'atar mijina amma sai na
riski kaina da farin ciki don koba komai hakan zai k'ara b'oyar min da cikina,duk
da yanzu ya haura wata uku amma ko kad'an bai wani fara fitowa ba,amma amma inajin
motsinsa kad'an kad'an kuma Ina yawon zuwa ganin likita yana tabbatar min da
lafiyarsa, maida kai nai naita bashi hak'uri da nuna mai damuwa ta don karya
fahimci wani abu har kuka nai wai na gama shrin taransa,daga baya shi ya juya da
rarrashina haka muka gama nunawa juna damuwar mu muka hak'ura,nace mai ba komai ai
saura k'iris ma ya dawo duka bai wuce wata biyar ba su dawo gaba d'aya.

**********BAYAN WATA BUYU

Biki ne ya taso mana a gida Sakkwato na y'ar yayan mune, na shiryawa bikin nan don
na dad'e banje sakkwato ba,don haka naketa d'oki dukda kwana uku kawai zanyi in
dawo sabida Satin zamu fara final exam's, Su sweety kuwa tuni ma sukai graduation
Tafiya service kawai ya rage musu,don haka muka shirya tafiyan har ita, nai rawar
gani sosai a bikin nan sabida duk gidan mu daman Aunty ce mijinta baida wani
k'arfi kuma ga girma ya kamashi don tsoho ne ,don haka lokacin da muke waya da
Mamana take fad'amin zancan take sanar dani yayyan mune mazama sukaiwa Amaryar
kayan d'aki don Babanta bai dashi,tausayin sune ya kamani nacewa Mamana zan kira
Auntyn A waya inji me suke buk'ata, ai kuwa na kirata bayan mun gaisa nake
tambayarta ya shirin biki tace Alhamdulillah anatayi,na rasa ma me zan tambayeta
suke buk'ata Auntyn mu tanada y'ay'a manya duk mata Wanda duk suke gidan miji
k'ananan ne maza, don haka y'ar ta ta uku itace ma sa'ata shiyasa muka d'auketa
tamkar uwa,jin nauyin tambayarta halin da suke ciki nake don haka nace ta bawa
Amaryar wayar muyi magana,Bayan mun gaisa nace "Ummy ya shirin biki ina fatan an
gama da komai ko".

Jim tai sannan tace " Eh Aunty Nahna wlh su Yaya Babba duk sun min kayan d'aki
komai na d'aki sunmin ".

" OK to b'angaran kitchen fa?"

Shiru tai na d'an lokaci sannan tace "suma d'in su Aunty juwairiyya sunata
k'ok'ari wlh yanzu gas ne ya rage da sauran d'an abunda ba'a rasaba".

" ok ba damuwa ki turomin account number d'inki zan miki transfer kud'i sai asai
abunda ba'a k'arasa ba".

Godiya tai tamin nidai na kashe wayan ina tunanin nawa ya dace in tura
musu,k'arar shigowan account number d'in ne yasa na d'auki wayan tunanin in tura
musu 100k nai don haka nai musu transfer d'in dubu d'arin ai kuwa yana shiga ta
kirani da murna tana godiya sannan ta bawa Auntyn itama taitamin godiya.

******
Ranar Alhamis muka d'au hanya ni sweety Aunty Hafsa da yara Sai Aunty Amrah, mota
Babba Abban su sweety ya bayar akaimu,don haka tafiya mukai cikin nutsuwa kuma
cikin d'an lokaci muka isa, kamar yanda muka saba a gidan mu muka sauka, tara me
kyau muka samu daga y'an tsofaffin iyayen mu da sauran jikoki da masu aikin gidan
bayan mun huta munci abunci tare da salla muka wuce gidan bikin tunda ranar aka
fara bikin, tofa tunda muka shiga cikin dangi kowa ke tofa albarkacin bakinsa
akaina,wai na canja nai k'iba nai wani asirtaccan kyau tabbas ba makawa ciki
gareni, haka suketa fad'i nidai mirmishi kawai nake ina kauda zancan

Haka akai kamu ranar akasa amarya a lalle,da dare gida mukayo duka anan muka
kwana,washe gari kuma Amarya tai yinita da k'awayenta Wanda shima ya k'ayatar dukda
ba wata k'arya akaiba dai dai gwargwado akai komai,washe gari kuwa ranar Asabar
aka d'aura Aure akai yini tare da kai Amarya,to Aranar Asabar d'in ne kuma har naji
gidan bikin ya isheni yanda naji zancan inada ciki ya karad'e danginmu kaf kowa ca
yake zaizo kano suna in Allah ya saukeni lfy,abun ya wuce inyi musu tunda harda
iyayena cikin masu zancan, gashi sunata tambayar Aunty Hafsah amma itama sai tace
tana kyautata zaton hakan dukda ban sanar mataba,wata mata dake gun take fadin
"Toku banda abinku ai da ganin Khadeejah babu tambaya kunsan ciki gareta gashinan
dukta d'anyace alamu k'arara sun nuna, kila irin cikin y'an gidanku zatayo b'oyayye
tunda duk kanku sai cikinku yakai kusan watannin bakwai cikin na takwas yake
fitowa".
kunyace matuk'a ta rufeni da kalaman ta don haka na tashi tsam na bar gun,ina
tskaicin mutane masu surutu haka.

Daran Asabar d'in muna kwance d'akin da muka sauka su Aunty Hafsah da Aunty
Amrah duk sunyi bacci saini da sweety ni ina waya da mijina ita kuma tana chatting,
bayan na kashe wayan sweety ta zubamin ido tana kallon na,ganin tak'i kauda kai
nace " emmata yada kallo haka".

D'an mirmishi tai ta tashi zaune tana fadin "Aunty nah ashe yardar dake tsakanin
mu bai kai insan kinada ciki ba har sai a sakkwato zanji".

D'an zaro ido nai cikin basarwa nace" Au wai ke yarda kikai da wannan maganar?
Lalle sun ruftaki yasin taya zan samu ciki mijina na India ni ina Nigeria kawau
surutun sune fa".

"A'a don mijinki na India ai kinje wajan sa munsan a can aka samu ai".

Dariya sosai nai sannan nace " yanzu watana nawa da dawowa daga India sweety ,ki
lissafa inda na sami cikin tun a can aida tuni yanzu ya fito kowa ya ganshi zuwa
yanzu au yaci ace ya girma ko".

Tsam tai da ranta tana tunanin can tace "gaskiya kam nima saida nai wannan
tunanin kuma gashi ni banga kina laulayin da masu ciki keyiba,kinga babu yanda
za'ai ai ciki ba laulayi".
Dunk'ule hannu na nai alaman jinjina nace " yawwa y'ar uwa kema kin gano
Ashe,kawai wai da anga mutum yai kyau yayi k'iba sai a jawomai ciki,surutu ne bai
ishesu ba sai suje suyitayi au".
Da haka na bagarar Da ita muka shiga wani zancan,

Washe gari da sassafe driver daya kawomu yazo d'aukan mu,muka d'auko hanya.

*****
Tun daga nan zancan cikina ya dasu a danginmu kowa ya sani, ita kuwa sweety tun
acan tabar zancan don ta yarda da abunda na fad'a mata.

Kwanan mu uku da dawowa na dawo daga skl a gajiye ina zaune kan kujerar ina
hutawa sweety ta shiga kitchen kawo min abunci, wayata ce tai ringing ina d'agawa
naga sunan Aunty Hafsa,d'agawa nai da sallama ina fad'in "Aunty nah ya gidan".

" lfy qlau Nahna ya exam d'in ?".

"Alhamdulillah Aunty yanzuma na dawo gidan wlh".

" To Allah ya bada sa'a, daman wata magana nake son muyi ".

" Tom Aunty ina sauraranki".

"Cikin ki wata nawa ne Nahna ".

Dammm naji gabana ya fad'i ina k'ok'arin mata musu ta dakatar dani " ban son
musu Nahna fad'a min kawai wata nawa ne banga abun b'oye b'oye bafa".

Cikin tsananin jin kunya nace "Aunty wata biyar ne ".

" yawwa daman nima hakan nake tunani zan sanar da yayan ki ne daman ".

" wayyo Allah Aunty don Allah karki fad'a mai wlh Allah kunya nakeji kibar
maganar kawai iya mu".

Dariya tai kawai tace "To na barta kinji, amma ki rink'a kula da kanki ki
rink'a cin abunci masu kyau sosai".

Dabarun kula da kaina taita bani da nai maita godiya muka kashe wayan.

Ina d'agowa idona caraf cikin na Sweety tana tsaye rik'e da flat d'in abinci
kallo take min me cike da tuhuma hakan ya tabbatar min taji hiran mu da Aunty tunda
a free nasata, cikin yanayin damuwa tace "Ban kai nasan kina da ciki ba Nahna
matsayi na bai kai mu raba farin ciki dake ba".

Tana kaiwa nan ta shige d'aki,ni kuwa zama nai jigum ina nazarin maganar ta,ita
sweety bata San me yasa nake b'oye zancan cikin nan ba,amma dukda haka nasan baza
taji dad'i ba, mik'ewa nai na bita d'akin turus nai ganin tana ta had'a kayanta
waje guda,da sauri na k'arasa gareta tare da dafa bayan ta,bata jiyo ta kalleni ba
illa k'ara tsuke fuska datai, cikin sigar rarrashi na fara magana" haba sis me yasa
zakiyi fishi dani me yasa kike had'a kayanki? Kina nufin barin b'angaran nan zakiyi
ki kome".

Muryanta na rawa tace "me yasa bazan koma part d'in muba me yasa zanci gaba da
zama inda ba'a nemana, tun tuni na gane ni kad'ai ce nake son zama dake Nake iya
raba damuwa ta da farin cikina tare dake, sirrina duka ina sanar miki amma ke
akasin haka ne,koda yaushe b'oyemin sirrinki kikeyi me yasa? Yanzu ina tunanin ina
cikin sahun mutane na farko da zansan kinada ciki amma lokacin danaji hakan ma daga
bakin family d'in ki sai kika musa min kika b'oye min, me nai miki Nahna?".

Rasa abunda zance mata nai don haka na k'ara k'ank'ame hannun ta cikin nawa a
hankali nake matsa hannun nata alaman rarrashi,a sannu na fara magana yanda zata
fahimceni tsaf na kwashe dalilin b'oye cikin na fad'a mata,na sanar da ita ra'ayin
yayan nata akan ciki da haihuwa, idon ta cikin nawa cike da tausayi tace " na
fahimceki Aunty nah kuma na gamsu da hujjarki,amma kuma randa ya sani ya zakiyi
kuma kina sane yaya zai dawo k'asar nan kafin wata hud'u zaizo ya riski ciki jikin
ki,kuma yanzu zakita zama ne da ciki Abban bai sani ba,tabbas bazaiji dad'i ba
randa duk yaji kin b'oye mai duk da kema da taki hujjar".

"Sweety ban san yanda zanyi ba wlh,ina son mijina ina son zama da mijina,sannan
ina tsananin son cikina Allah ya jarrabeni da son haihuwa bazan iya yiwa Umar
biyayya kan gujewa haihuwa ba,kuma tabbas zuwa yanzu zuciya ta taf take da k'aunar
mijina da son zama dashi, damuwa ta ban san ya zaman mu zai kasance ba duk randa
yasan wannan maganar".

Dafa kafada ta tai tace " ki kwantar da hankalinki Aunty nah insha Allah duk
randa broth ya samu labarin cikin nan ko ya ganshi da idonsa zai kasance cikin
farin ciki zaiyi murna, yanzu abunda nakeso dake zan sanar da Abba kinada ciki don
inyaji bazaiji dad'i ba,amma zan fad'a masa karya sanar da Broth sabida biki fad'a
mai ba har yanzu sabida kina son surprise d'insa ne duk randa ya dawo k'asar nan,
nasan indai na fad'a mishi haka bazai tab'a mai maganar ba,duk dai dabaran da zanyi
zanyi in sanar da Abban kinji "

Gyad'a kai nai cikin rashin gamsuwa don nidai tabbas nasan indai Maganar nan ta
shiga cikin gidan su sweety to kamar yaji ne.

Haka dai na tashi zuwa d'aki jiki ba dad'i zuciyata cike da wasi wasi.

Taku ce
'Yar mutan Ja'oji🙋
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?

🍡🍡🍡 🍡🍡🍡
🌸🌸 🌸🌸🌸🌸
*'YAN ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*

*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

DEDECATED TO ALL
ARABIC /ISLAMIC STUDENTS
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI WRITERS ASSOCIOTION*


📝
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀ ร

*Ina* *barar* *addu'arku* *y'an* *uwa*

0⃣4⃣7⃣
0⃣4⃣7⃣ 0⃣4⃣7⃣

Bayan sallar isha'i Abba na zaune a parlourn sa news yake dubawa sweety tai
sallama ta shiga fuskarta d'auke da fara'a,amsa mata yai shima cikin fara'ar yace
"sweety nah duk yanda akai akwai labari me dad'i "

Kusa dashi taje ta zauna yana dariya tace "Abba nazo da labari me dad'i kam,amma
sai ka bani goron albishir".

Kamo hannun ta yai yana gyara zama yace" Tom na amince maza fad'a min albishir
d'in zan baki goro me tsoka ".

" Tom amma Abba ina son kamin wani alk'awari kafin in sanar dakai".

"Kai Sweety nah wai wannan wane irin labari ne me dad'i haka da aketa jan
sa".

Dariya tayi tace " Abba kamin alk'awarin in dai na fad'a maka bazaka fad'awa
Broth ba".

Da sauri ya kalleta yace "wane abun farin ciki da zaki sanar min kuma kice bakya
son d'an uwanki ya Sani,me yasa".

" Abba akwai lokacin da aka tsara zai sani din amma ba yanzu ba ".

" ok to fad'a min ina sauraranki maza".

Gyara zama ta k'ara yi sannan tace "Abba zaka samu jika ta b'angaran broth da
Aunty Khadeejah soon".

Da sauri ya kalleta yace " yimin bayani sosai in fahimta mana"

"Abba Ina nufin Aunty Khadeejah tanada ciki na 5 months tun dawowar ta daga
India".

Cikin tsananin farin ciki yace " Alhamdulillah, Allah abun godiya ,amma ya akai
ban sani ba tuntuni sai yanzu".

"Yawwa Abba anzo inda nakeson azo d'in,kaga nima ban sani ba sai yau Aunty
Khadeejah tayi surprise d'in mune, mu duka shiyasa ta b'oye mana bama muba har
family nata duk yanzu ne suka San da wannan zancan ,amma ta rok'eni kar mu bari don
Allah broth ya sani sabida tana son ranar dawowar sa ya zama shine abunda zata
tareshi dashi na gitf,tana son sai a ranar daya dawo zai sani kaima tace inna fad'a
maka don Allah ince ma karka fad'a mishi haka tace in fad'awa Aunty murjah".

Dariya Abba yake cike da farin ciki yana godiya ga Allah, Abunka da d'an boko
sai ya d'au zancan yiwa UK surprise shima a abun burgewa da k'ayatarwa a duk sa'ar
da UK d'in ya shigo k'asar, suna cikin haka Aunty murja ta shigo ganin farin ciki
k'arara shimfid'e kan fuskar Abba yasa itama fad'ad'a fara'arta tana zama gefansa
take cewa " Alhaji na meya samu ne irin wannan bayyanannan farin ciki haka".

Rik'o hannun ta yai yana fad'in "Abun murna da farin ciki ne suka riskemu murjah
ashe Khadeejah ciki gareta tun dawowar ta daga India yanzu cikin watansa biyar ".

Fad'ad'a fara'arta itama tayi tace " kai an gode Allah masha Allah, amma shine
sweety keda ita buku tab'a fad'awa kowa ba har zuwa wannan lokacin".

"A'a Aunty nima yau na samu zancan akwai dalilin dayasa ta b'oye".

Nan ta fad'a mata dalilin itama tace


" to ai shike nan indai duk suna cikin k'oshin lfy itada cikin,amma Alhj in Allah
ya kaimu gobe sai muje asibiti likita ya dubata sosai sannan ai mata awo ko".

"Eh hakan yayi murja yanzu kije ki fad'a mata ta zama cikin shirin sannan saiki
d'an k'ara mata bayanin yanda abun yake ki wayar mata da kai ko".

Mik'eqa Aunty murjah tai cikin farin ciki tana fad'in " ai mu yanzufa ba zama
Daddy zai haifo jika ".

Duk dariya sukai ,sweety tabi bayan ta suka fita,shi kuwa Abba bin bayan su yai
da kallo yanata fara'a.

Ina kwance d'aki don har nai shirin bacci ina jiran kiran mijina don wayar ma na
hannuna,jinai sweety na magana a bakin k'ofa " Aunty na har an tafi tsinkar furen
ne ".

Y'ar dariya nai nace 'kema kin sani ai yanzu lokacin me zuciyata ne, ki shigo
mana kika tsaya ".

Shigowa d'akin tai tana fad'in " A'a ai naga a irin wannan lokacin bakya buk'atar
kowa kusa dake".

Dukan wasa nakai mata ta matsa tana dariya tace " kizo Aunty murjah na parlour
tana son magana dake ".

Zaro ido nai nace " don Allah da gaske ,innalillahi,me kika ce mata?kar dai har
kin sanar dasu ".

Cikin basarwa sweety tace " Ah to me za'a jira,kedai kawai kizo muje sauri
take".

Jikina har rawa yake na lalubo hijab nasa nabi bayan sweety, a zaune na tadda
Aunty murjah 😂😭fuskarta cike taf da fara'a take kallona,k'arasa nai na zauna k'asan
cafet ina gaidata ,da fara'ar ta take amsa min tace "Yau munji abun farin ciki
munwa Allah godiya,amma kuma bamu samu labari da wuri ba,har k'awar ko abokin na
shirin zuwa dukda sweety ta fad'a mana plan d'inki, yanzu ki shirya gobe in Allah
ya kaimu zamuje kiga likita ya tabbatar da lafiyarku sannan ki fara zuwa awon ciki
kinji".
Kunya kamar k'asa ta bud'e in shige haka na zama kaina k'asa nama kasa amsa mata
,nan taita min bayanin yanda zan kula da cikina da kaina, daga nan taimin sallama
ta tafi ,tana fita sweety ta kyalkyale da dariya tace " To kunyar tamene Aunty na
tunda an riga an samo mana d'an India ".

Hararanta nai nace " zamu had'u wlh ,ni duk kinsa kunya ta dabaibayeni wlh ni
yanzu da wane ido ma zan kalli Abba ".

Cikin dariyar tsokana tace " da wannan idon da kike kallon kowa,ke shifa Abba
yana can dad'i ya cikashi sai hamdala yake".

Hararanta kawai nai na tashi na shige d'aki don jiyo Ringing d'in waya na da
nake.

Misalin k'arfe takwas na shirya tsaf don kar Aunty tazo tana jirana,ina zaune
gaban mirror sanye da hijab d'ina ina fesa turare sweety ta shigo tace in fito
Aunty tana parking lot tana jirana, y'ar jakata na d'auka tare da zura takalmina na
fice ina rufe d'akin.

Tun daga nesa na gango driver harya saita kan motar yana kallon gate k'arasawa
nai na bud'e baya inda Aunty murjah ke zaune na zauna ina gaidata kaina a k'asa
amsawa tai tana dariya tace " ya jiki jikin " cikin tsananin kunya nace
"Alhamdulillah"

Gaisuwar da driver kemin tasa na d'aga kai ina amsa mai sannan yaja motar muka
tafi.

********
Duk iya bincike da dube duben daya kamata likita yayi yamin ya tabbatar da
lafiyata data abunda ke cikina sannan ya k'ara bani shawarwarin kula da kaina da
abincin daya dace me ciki ta rink'a ci, sannan muka baro asibitin.

Tun daga wannan ranar yau sati guda kenan ban bari mun had'u da Abba ba don ko
sashin su nak'i shiga tsananin kunyar had'uwa da Abba nake,shikuwa Abba kullum
cikin yimin siye siye yake na kayan k'walama in ya kawo zai bawa sweety kosu Kamis
su kawo min,ina son zuwa inyi godiya amma na kasa, innace sweety tace mai na gode
sai taita min dariya wai inje da kaina, haka in taje wajan Abba zata ita bashi
labarin kunyarsa da nakeji ban son had'uwa dashi, shima dariyan yake kawai yace
Khadeejah kenan.

Yau sweety taje gidan ummu sulaim ta sanar da ita zancan cikin itama murna tai
tayi wayar ta ta d'auka tana fad'in "bari inyiwa broth murna an kusa zama Abba".
Da sauri sweety ta rik'o hannun ta tana fad'in " Rufamin asiri ".

Kallon tuhuma take mata ,nan sweety ta warware mata komai kan matsalar k'in
haihuwa da UK keyi da kuma rashin sanin da zaman cikin, da b'oyewa su Abban su
gaskiyar zanzan da sukai , hawaye ummu sulaim take tace " Ashe muna murna broth ya
shiryu ashe da sauran sa,yanzu meye abun k'i cikin haihuwa don Allah wasu nacan
nata nemanta ido rufe shi ambashi yana gudu, wlh Allah sweety kullum a gidan nan
rok'on ubangiji muke ya ban cikin kullum burinmu in yiwa fu'ad k'ani ko k'anwa
Abban fu'ad Allah ya jarrabeshi da son yara gashi ni bame yawan haihuwa ba,amma
shi broth baima tab'a haifa ba amma har yake neman tsari da ita saboda ak'idar boko
ak'idar banza".

Jinjina kai sweety tai tace " dukda haka broth ya shiryu matuk'a ya gyara
d'abi'unsa zamansa da Nahna ,wannan muguwar ak'idar tasa ce kawai ta rage kuma
insha Allah ina kyautata zaton in ya dawo yaga cikin zai hak'ura ".

Haka sukaita tattauna matsalolin Uk suna mai addu'ar k'ara shiryuwa.

Tsawon sati biyu naga b'oye b'oye bazai kaini ba don haka na shirya na tafi gaida
Abba da magriba kayan sallar isha'i sanne in sanar dashi ranar nayi graduation a
ranar dukda ya sani don har kud'i sosai ya aikomin inyi hidimar graduation d'in
dashi,

Da sallama na shiga parlourn nasa ya amsa min cikin sakin fuska yana fad'in "
k'araso mana Khadeejah shigo"

A nutse na k'arasa k'asan rug na zauna kaina a k'asa nace "Abba barka da dare ".

" yawwa barka dai Khadeejah,ya exams yau dai an gama ko".

Gyad'a kai nai ina d'an mirmishi, yace "To Allah ya fito da kyakykyawan
sakamako,dukda nasan yarinyar tawa akwai himma da k'ok'ari Allah ya dafa miki".

Cikin jin dad'in addu'ar tasa nake amsawa da " Ameen Abba na gode,Allah yaja da
rai ya k'ara lfy ".

" Ameen Khadeejah, ya kuma jikin naki,ina fatan babu wata matsala a tare dake".

To anzo wajan fa nan na k'ara k'asa da kai kamar zan nutse, y'ar dariya Yai yace
"ki daina damun kanki fa Khadeejah koda yaushe ina fad'a miki ki d'aumeni mahaifi
ba suruki ba ki daina jin kunya ta, duk damuwarki ki rink'a sanar min kinji".

Gyad'a kai kawai nake kamar k'adangaruwa,haka yaita jana da hira nikam sai dai
inyi mirmishi kawai,dayaga dai na takura sai yace " Tashi kije ki kwanta ki huta
don nasan yau kunsha hidima, kamar jira nake tsam na tashi inai mai sallama na
fita.

Sai ya zama na tun daga ranar na rage kunyar had'uwa da Abba na koma kamar kullum
duk kwana biyu zanje in gaidashi mu danyi hira.
***************
Wata rana da dare ina kwance muna waya da Ruhina yace "my wife kwana biyu fa
biki turomin pic d'in kiba,ko rowar jikin akemin ".

Dariya nai me cike da k'issa da jan hankali nace" ka tab'a ganin anwa me abu
rowar abunsa, nida Ruhina da jikina duka naka ne kayi yanda kaso".

Cikin jin dad'i da kalamaina yace "yawwa wify to aturomin yanzu in gani kuma
tun daga sama har k'asa ".

Ba tare da damuwa ba na fara d'aukan pic d'ina cikin kayan baccin dake jikina yar
ficici dasu na tura mai,

Yana kalla mirmishi yake tayi can ya kirani " Ke me kike ci kikai k'iba haka,
ko inafa yai b'ulb'ul dashi".

Sai a sannan ma na tuna da yanayin jikina daya sauya don cikina har yanzu bai
wani fito sosai yanda za'a gane kai tsayeba,amma nai k'iba ta jikina don Boob's
d'ina sun cika matuk'a su K'ara girma,haka ma hip's d'ina ya k'ara bud'ewa yai
girma,jikina ma duk ya murje yai k'iba madaidaiciya,
Cikin basarwa nace "Hhhmmmm hutu ne kawai ba zuwa school ba karatu brain d'ita
tayi fresh banda wata matsala".

Dariya yai yace " lalle kuwa kina hutawa don gashi nan ko ina ya nuna har an
tsokane min ido da tws d'ina".

Dariya kawai nai ina janye hankalin sa daga maganar k'ibar muka fad'a duniyar
k'auna.

*********
Rayuwa na tafiya yanzu cikina ya shiga wata bakwai kenan, kuma a yanzu ne ya
fito sosai ya zauna a jikina, zuwa yanzu ba k'aramin shiri Abba kewa cikin ba
sabida yace baya buk'atar Daddy ya dawo yasai komai na taran Babyn,don haka ya bawa
Aunty murjah A.T.M card d'insa yace muje nida ita da sweety mu siyo duk wani abu da
ake buk'ata na tarar Baby,ca nai bazan bisu ba suje su biyu ni kunya nakeji wlh,
sukai sukai nak'i don haka Aunty murjah ta kira Aunty ummu sulaim tace ta shirya
zasu siyayyar haihuwa suka had'u su uku suka tafi.

Kaya suka jido bana wasa ba fa kamar bada kud'i ake siyaba ,duk wani abu na
buk'atar baby sun siyo kayan wanka kayan shafa,kayan sawa komai fa basu bari
ba,haka suka lodesu gaban Abba yaita dariya dajin dad'i bayan dukya gama gani yasa
aka kawosu pat d'ina d'aki guda a gefe aka zuba kayan aciki,nidai binsu kawai nake
da kallo irin dukiyar da aka kashe, sai bayan sun koma pat d'in su na shiga d'akin
ina duba kayan fuskata d'auke da fara'a ina yaba k'aunar da wannan family sukemin,
zuwa nai na d'auko akwatin kayan babyn da nazo dasu daga India na had'a a d'akin,
sannan na rufo k'ofar ina addu'a a raina Allah ya rabani da cikin nan lfy.

*Taku* *ce*
*y'ar* *mutan ja'oji*🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITER'S* *ASSOCIATION*

📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ _and_ _entertain_ _our_ _Reader's_

*Allah* *kasan* *damuwar* *dake* *k'asan* *rai* *Allah* *kai* *mana* *maganin*
*ta* 👏👏👏

0⃣4⃣8⃣
0⃣4⃣8⃣ 0⃣4⃣8⃣

Yanzu kuma duka hankali na ya koma ga tarar dawowar mijina wanda nake k'arfin hali
kawai don zuciyata taf take da fargabar abunda ka iya zuwa ya dawo,sati hud'u ci ya
rage zai dawo Wanda lokacin ciki na yana wata takwas cif, yanzu bama samun wani
sukuni dashi sabida course d'in nasu ya k'are sai project suke had'awa da shirin
tahowa gida, anan Nigeria kuwa company d'in su an gama komai an bud'e jiran
dawowarsu kawai ake su fara aiki,don haka yanzu koda yaushe yana busy,sai muyi
kwana biyu bamuyi waya ba sabida lokacin da zai gama uzurinsa ya dawo gida ni tuni
nai nisa a bacci ma.

B'angaran Abba kuwa yasa an tada ginin katafaran gidan mu,dake kusa danasu don
filin dake jikin gidan k'aton gaske yasa ake mana gini na d'aukan zance, tunda yai
alk'awarin daman inya dawo a gidan mu zamu tare, nikam bana murna ma da sabon gidan
da za'a karb'i ra'ayina abarni cikin gidan nafi son haka balle yanzu ga ciki zanfi
son zama cikin mutane.

**********
Kwanaki sunyi gudu sosai harya rage yanzu kwana goma cif UK ya dawo gida
Nigeria,kowa murna yake amma nikam yak'e kawai nake,dalilin yawon fad'uwar gaba ma
yasa duk na rame na fige sai hanci zirit da idanuwa,ga cikina ya fito sosai yai
girma, gidan mu kuwa an gama komai har furniture's duk an saka zuwa kitchen
material komai an kammala,sai batun y'an aiki Abba ya tuntub'eni kan za'a samomin
masu aiki ko inadasu ta b'angarena, har zance a'a bana buk'atar masu aiki mata,sai
kuma nai tunanin yanzu haihuwa zanyi ina buk'atar mataimaki, ga gidan ni kad'ai zan
samu mutane kusa dani amma dai ni ba wani son me aiki nakeba ,sai kuma nace eh zan
duba gudawa nawa za'a samo,Abba yace a samo mata guda uku biyu masu aiki d'aya me
rainon Babyn da za'a haifa, sannan a samo maza guda uku suma me gadi dame kula da
gida filawowi da sauran su ,sannan me wanki da guda da zuwa d'an aike haka, cikin
gamsuwa nace tom Abba za'a samo.

Bayan ba dawo part d'ina na kira yaya na bayan mun gaisa nake tambayarsa ko
za'a samu masu buk'atar aiki a can gida sakkwato, yace min zai kira au yaji,aikuwa
bayan kamar awa guda ya kirani ya sanar dani akwai masu so da yawa daga maza har
mata a irin mutanan unguwar mu masu k'ara min k'arfi.

Da safe na sanar da Abba an samu acan sakkwato,yace tom ba matsala zai aika
driver yaje ya taho dasu,naji dad'in hakan sabida nasan duk ma'aikatan dake aiki
k'arkashin Abba ba k'ara min alheri suke samu ba ga albashi me tsoka,koba komai
nima y'an garinmu sa samu daga gareni.

**********
Kayan gyaran jiki sosai Aunty ta aikomin sannan ta aiko me gyaran tamin gyaran
fata,bana wani d'okin don cikin jikina ma ya isheni ga fargaba,don haka ban wani
bada had'in kai a gyaran ba fatana kawai Allah ya daidaita mu idan ya dawo.

Bayan kwana biyu Abba ya tura driver sakkwato yaje ya debo ma'aikatan,don daman
sun zama cikin shiri,

Ina son garina da mutanan cikinsa shiyasa lokacin da aka kawosu naita musu
barka na rasa inda zan ajesu,babu k'yama ko wani Abu na sake cikin matan munata
hira su kuwa mazan bayan sun shigo mun gaisa aka kaisu sukaci abunci sukai salla,
can gidan aka kaisu aka nuna musu d'akin su,k'aton d'akine daka shiga gate me
d'auke da k'ananun katifu uku, kowa da tasa daga ciki harda toilet d'in su, biyu
manya ne don duk da iyalansu ma sai d'aya ne saurayi don haka shine me wanki da
guda da zuwa aike,d'aya me gadi d'aya me kula da filowa da sharan gida.

Bayan y'an tambayoyi danaiwa matan na fuskanci suna cikin talauci, d'aya
dattijuwa ce da yar autar yarta budurwa tacemin shekararta goma 16 sai d'ayar
bazawara ce da bazata wuce shekaru talatinba, b'angaran ma'aikatan gidan su aka
kaisu son sai ana gobe zai dawo zamu tare a gidan.

*********
Rana bata k'arya inji y'an Hausa,yau kam gamu cikin gidanmu mun tare Wanda
gobe kuma me gidan zai sauka gida Nigeria, kwana nai kan sallaya ina kaiwa Allah
kukana kan ya daidaita tsakanina da mijina idan ya dawo har asuba sannan nai sallar
asuba na kwanta, bacci sosai ne ya d'auke ni Wanda ya kaini har k'arfe goma da
addu'a na tashi a baking,l ganin time yasa nai saurin tashi nai toilet wanka nai na
fito ban wani tsaya shafe shafe ba na zura doguwar riga nai parlour, samun su
karima nai har sun gyara gidan tsaf sun koma b'angaransu dake can farkon gidan.

Kitchen na shiga don samawa cikina abun tab'awa kasancewar jiya munyi kayayaki
sosai na tarar me gidan yasa na d'iba ciki naci, sannan na fito zuwa part d'in masu
aikin, sumun su nai har sunyi wanka sun k'ara gyara part d'in nasu batun abunci
daman da kitchen d'insu a ciki ansa musu duk kayan girki zasu rink'a yin nasu da
masu aikin maza, cikin sauri suka shiga gaida ni na samu waje na zauna muka gaisa,
nan nace karima da Binta suzo muje su tayani aiki su bar Baba ta huta ita.

Munata aikin abinci amma hankali na bai tare dasu ko sweety data shigo ta amsa
ragamar aikin tanata min tsiya da tsokana nako kasa amsa mata sai dai yak'e
nake,ji nake kamar zuciyata zata faso k'irjina ta fito don fargaba, a haka wajan
sallar azahar aka gama komai aka shirya su a wasu k'ayatattun warmas masu d'aukan
ido,tsaf muka shirya dining table d'in duk girmansa saida muka cikashi da kala
kalan abinci da kayan mak'ulashe, k'arfe hud'u zai shigo gida don haka bayan mun
gama komai sun k'ara gyaramin gidan suka koma part d'in su.

Wanka nai nazo na zauna bakin gado gabana na k'ara tsananta fad'awa jikina
harya fara rawa, ambaton Allah nai tayi sannan nutsuwa ta saukar min, cikin rashin
kuzari na kimtsa tsaf cikin wata doguwar riga y'ar k'asar dubai pink color ce an
mata adon stone silver, kyau iya kyau rigan nadashi, jikina na wanke tsaf da turare
masu d'aukan hankali, bansa d'an kwali akaina ba gashi na da yasha gyara na k'ara
tajewa na shafeshi damai sannan na sake shi ya zuba baya, na d'auko plate d'in
takalmi kalan kayan nasa a kafata don ban yawo ko cikin d'akina ne ba takalmi
sabida sanyin tile's, kasancewar cikin sanyi nake yin komai yasa na d'au lokaci
don Dana duba agogo ya muna min uku da kwata, na tabbata zuwa 30 minutes zai iya
shigowa gida, don su sweety ita da Abba dasu yaran tuni suka k'arasa Airport don
tararsa,

Parlour na dawo na zauna ina tunani kala kala cikin raina, can naji tsayuwar
motoci a harabar gidan da sauri naje jikin window d'in da zai sadani da kallon duk
abunda ke wakana a k'asan harabar, shine ya fito daga motar sanye da k'ananun
kaya jikinsa kalan brown Wanda suka amsheshi sosai k'afansa sanye da brown takalmi
sau ciki,haka ma fatan agogon hannunsa take brown, kallo d'aya zaka mai ko daga
nesa ne ka tabbatar da tsantsar kyawun da yayi hakama fatar jikinsa tai frees
alamun ana hutawa. Gaisawa yake da ma'aikatan da suka taso suna gaida shi,yayin
dasu Abba da duk y'an rakiyar tashi sukai mai sallama suka juya zuwa gida Abba yace
abarshi ya huta zuwa jimawa sa k'ara gaisawa.

Yanda yake taka k'afafunsa yana tunkaro cikin gidan haka k'arin bugun
zuciyata ke tsananta, gumi ya gama lullib'e ilahirin jikina,k'afafuna da hannayena
wani bala'in karkarwa suke, na jingina kaina jikin window d'in ina ambaton Allah da
neman d'aukinsa.

A babban parlourn k'asa ya dakatar da ma'aikatan da suka biyo shi da


jakunkunansa, tsayawa yai yana k'arewa parlourn kallo fuskar sa d'auke da mirmishi
kallo yake yaga ta inda zan bayyana jin shiru yasashi sakin wani k'ayataccan
mirmishi ina k'iyasto dad'in da zai kwasa yanzu ba anjima ba,juyawa yai ya rufe
k'ofan parlourn ya fara taka k'afafunsa zuwa matakal da zata sa dashi da saman
benan, cikin wani cool voice yake fad'in "my pretty! my angle! my heart! my
sweetness! My heartbeat fito mana in ganki idanuwa da ruhina duka sun matsu su
ganki don Allah yi sauri ki fito ina marmarin jinki a cikin k'irjina, zo inji
d'uminki, fad'a yake yana lallek'a d'akunan harya k'araso d'akin da nake ganina
tsaye na juya baya yasa shi k'arasowa da sassarfa yana fad'in" badai fishi kuma
ake dani ba don na dad'e ban hayo saman ba, wata wawuyar runguma yamin ta bayan
yana kwantar da fuskar sa akan wuyana tare da sakin wata nauyayyar ajiyar zuciya,
matseni ya k'arayi a jikinsa yana jin wani nishad'i na saukar mai, a hankali ya
juyo dani idonsa a lumshe yana k'ok'arin sanyani cikin k'irjinsa jin abu ya tokare
shi yasa bud'e idonsa yana kai kallon sa ga cikina, k'ara bud'e idonsa yai sosai
don yaji kamar gizo abunda ya gani idonsa kemai d'an janye ni baya yai yana kai
hannunsa kan cikin ya danna jin tauri yasa shi d'agowa da sauri yana kallona Wanda
zuwa lokacin har hawaye ya gama jik'a fuskata jikina kuwa kamar mazari haka yake
rawa idonsa ya zuba sosai cikin nawa yana son tunano meyema wannan a jikina, don
shi duk tunanin sa ya tsaya,tsawon lokaci muna tsaye a haka,a hankali kuma ya zame
jikinsa a jikina ya zauna bakin gadon dafe da kansa, ni kuwa banma sami sukunin
zaman ba ina dai tsaye jikina nata mazari kamar nayi sata an kamani, can sama da
mintina goma ya d'ago da idonsa da suka kad'a ya saukesu a kaina, cikin k'arfin
hali ya fizgo maganar dake son fitowa daga bakinsa, "Khadeejah meye wannan a jikin
ki"?.

Sunkuyar da kaina k'asa nai don banda amsar bashi,muryarsa naji tsakiyar kaina
yana k'ara tambaya ta Karo na biyu, nanma ba amsa shiru nai,wata razananniyar tsawa
naji ya sakar min karo na uku yana tambaya ta meye wannan a jikina, jinai cikina ya
murd'a abunda ke cikina ya dunk'ule ya tare waje guda sanadiyar haka naji fitsari
ya fara bin k'afafuna, cikin sark'ak'k'iyar murya na fara fad'in" Kayi hak'uri don
Allah ka yafemin wlh ban san ya zaka d'au lamarin ba shiyasa ban sanar dakai ba
tun tuni".

Hannu ya d'aga min yana mik'ewa tsaye cikin tsananin b'acin rai yace "ba wannan
na tambayeki ba ca nai ki fad'a min meye wannan a jikin ki".

Cikin tsananin kuka nace " Ciki ne".

"Ciki ? wa yai miki shi".

Cikin firgici na d'ago idona a kansa ina kallon sa, kafin daga bisani naji
zuciyata ta soye kukan ma ya d'auke k'af nace " Me kake nufi ne umar me kake nufi?
Kana tambaya ta wayamin ciki akwai Wanda zaimin ciki ne bayan kai,to kai kamin shi
cikinka ne dana taho dashi daga India Wanda na same shi satin da zan baro India,
inka so ka yarda".

Zuba min ido yai cikin tsananin b'acin rai yana gyad'a kai yace" naji naji amma
meye dalilin da kika b'oyemin tun sanda kika san da zamansa a jikin ki,Khadeejah
tun yaushe nake fad'a miki ban shirya fara tara y'ay'a ba sau nawa na sanar dake
haihuwa bata cikin tsarina a shekara uku ma nan gaba, na sanar dake ban so ban so,
ban shirya tsufa yanzu ba,banso ban marmari,amma don ha'inci irin naki sai kika
b'oyemin tun sanda za'a iya zubar dashi,yanzu a lissafe nasan yafi wata takwas
yanzu duk dabarata nasan sai kin haife wannan cikin, tom kinyi kuskure na farko a
cikin rayuwar ki ,saida kika bari na aminta dake sannan zaki haince ni,to kije ki
haifeshi ki raini abunki".

Daga haka yasa kai ya fice yabar d'akin.

Taku ce
Y'ar mutan ja'oji🙋

🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

0⃣4⃣9⃣
0⃣4⃣9⃣ 0⃣4⃣9⃣

Da kyar yakai kansa d'akin dake daura da nata dafe da kansa ya fad'a bisa
faffad'an gadon yana runtse ido tare da furzar da iska me zafi,cije lips d'in sa
yai yana fad'in "why why? Khadeejah zaki min haka,me yasa zaki yaudareni,me yasa
zaki b'oyemin? Kin san yanda na dawo da k'ishin ruwan ki kuwa,kinsa yanda zuciyata
kemin rad'ad'i kuwa,na tara buk'ata ta watanni takwas ina zumud'i da marmarin
k'arasowa gareki ki biya min buk'ata ta amma gashi daga dawo wata naci karo da
bak'in ciki da b'acin rai, naci karo da abunda ya canja tunani, kin yaudare ni
Khadeejah, kin kutso min abunda ban tsarashi a tsarin rayuwata ba a kusa,zan janye
miki in barki da cikin in zai baki farin ciki da kwanciyar hankali tunda shi kika
zab'a akaina".

Surutai yai tayi marasa tushe yana bubbuga kai jikin katifa,wanda b'acin rai
ya saukar mai da wani mahaukacin ciwon kai, kwanciya yai lif bisa gadon bai san
takamaimai ma halin dayake ciki ba tsawon lokaci yana a haka.

Bin bayansa nai da kallo harya bar d'akin na saki wani kuka me cin rai,
nadama da dana sanin auran sa nake a wannan rana,na gama kyautata zaton d'abi'unsa
sun dai daita ashe da sauran rina a kaba, dukda dai nasa ni kuma na tabbata daman
hakan zai faru amma bansan wannan maganganu zasu fito daga bakin sa ba, ba komai
kamar yanda ya fad'a inje in kula da cikina tunda shi na zab'a to zanci gaba da
kula da shi har Allah ya rabamu lafiya kuma Allah ya rayamin abunda zan haifa.
Tashi nai na d'auro Alwala don kaiwa Allah kukana da neman sassauci yanda
zuciyata ke rad'ad'i da k'unci.

Har sallar magriba ina zaune kan prayer mat inaiwa Allah tasbihi da zikiri,ina
kai kukana gareshi da neman d'aukin sa cikin wannan cakwakiya data taso min.

Bayan sallar isha'i na fito zuwa parlourn k'asa cin karo nai da dukkan kayan
Abincin dana jera ba'a tab'a komai ba,hakan ya tabbatar min baici komai ba
kenan,tunani nake a raina,tabbas nasan mijina bai wasa da cikin sa kuma duk yanda
akai yanzu yana cikin yunwa,yanzu kenan haka zan barshi ya kwana da yunwa ga
abincikan dana b'ata lokaci wajan had'a su, zasu zama asara kenan fa, kasancewar
zuciyata tai sanyi yasa na taka a hankali na koma saman, k'ofar d'akin sa na nufa
knocking na farayi a hankali kusan sau biyar na k'wank'wansa ba'a tanka ba ci gaba
da knocking d'in nai har na fidda ran za'a amsa min sai kuma naji yace"waye " cikin
wata dashashshiyar murya me cike da tsantsar b'acin rai.

Tausasa lafazi nai a sannu nace " Nice,daman zan fad'a ma abinci na dining fa".

Had'e rai ya k'ara yi sosai ciki ciki yace " bana buk'ata kije kawai" .

Wani k'ululun bak'in ciki ne ya tasomin yake k'ok'arin mamaye d'an sassaucin
dana samu, cikin mutuwar jiki na juya zuwa d'akina ina ambatan sunan Allah. Sabida
ni akoda yaushe sunan Allah bai gushe min ko cikin tsanani ko sauk'i, koda na koma
d'akina kwanciya nai ina share hawayen dake ziraromin.tabbas nasan zan fuskanci
haka daga UK don haka dole in koyi dauriya in sawa raina har ranar da Allah zai
kawomin mafita kan lamarin.

**********
Juyi kawai yake kan gadon cike da tarin damuwa, zuciya a kuntace rai ba dad'i,
ga wata yunwa na sakutar cikinsa ji yake kamar yaci babu,ya daure ya daure amma fa
abun ya faskara ganin zai halaka donshi mutum ne bame wasa da cikin saba yasa ya
mik'e ya fito k'ofar d'akin ta ya kalla yana sakin tsaki, a sannu ya sauko zuwa
k'asa kai tsaye ya haye kujeran dake dining d'in bubbud'e warmers d'in ya farayi
k'amshi ya cika hancin sa,nan da nan yaji wata kahaukaciyar yunwa ta k'ara taso
mai.da sauri yai serving d'in kansa ya fara cin abincin ba kad'an bafa yaci iya ci
tare da shan drinks d'in masu d'an karan dad'i,mik'ewa yana mik'a tare da fad'in
'Alhamdulillah ".

**********
Haka na kwana ba ishashshan bacci don haka ina sallar asuba na koma bacci me
nauyin gaske ya d'auke ni Wanda bansan adadin lokacin dana d'auka yinsa ba. Kawai
cikin kaina naji hayaniya anamin ihu aka, da ambaton Allah na tashi ina gani dishi
dishi ,tsaye na ganshi rik'e da k'ofan d'akin yanata wani uban muzurai" ke malama
dake nake ina abincin break d'ina kika kwanta bacci har k'arfe tara".

Da sauri na kalli agogo saina fara k'ok'arin sakkowa a gadon ina daddafawa tare
da rik'e mara irin dai na masu tsohon ciki. Wani wawan tsaki naji yaja tare da
sakin k'ofan d'akin ya juya,jiki a sanyaye na k'arasa sauka zuwa toilet nai
fitsari ko wanka ban tsaya yiba na wanke fuskata na fito,sauka nai zuwa kitchen
d'in k'asa na fara k'ok'arin had'a me saukakken abun karin kumallon, doya da k'wai
na soya tare da daga ruwan tea daya sha kayan k'anshi, sai sauran parfesun jiya na
d'umamashi, zuwa nai na kwashe duka kayan dining table d'in anan naga uban abincin
daya d'iba,girgiza kai kawai nai na kwashe kayan tas nakai kitchen sannan na
gyarashi na jera mai girkin.
K'ararrawar d'akin masu aiki na danna,bayan Lami ta shigo nace tayi wanke
wanke ta gyara kitchen d'in, sannan na koma d'akina.

Wanka nai na tsara kwalliya bame tsauri ba sannan na shirya cikin wata doguwar
riga mara nauyi don yanzu babu kayan da nake jin dadin su kamar dogayan riguna,
turare na feshi jikina dashi sannan na fito zuwa d'akin nasa inata knocking ba'a
amsa ba nai tunanin kulawa ne bazai ba dana lek'a k'asa ta tsakiyan k'arfinan da
akaiwa corridor d'in ado dashi saina hangoshi yanata uban kwasar girki.
d'akin na shiga na fara gyara mai dukda dai komai k'arfin hali nakeyi,sabida
yanayin jikin nawa,na wanke mai toilet tas tunda daman ba wani datti bane ,sannan
nasa mai freshener na d'akin ya d'au k'amshi, ina k'ok'arin fita ya turo k'ofar
ya shigo,matsawa gefe nai na bashi hanya,baiko kalleni ba ya wuce risinawa nai
kamar yanda na saba na gaisheshi ciki ciki ya amsa min ya wuce bakin gadon ya zauna
yana saka safa da takalma, jinai zuciyata ta karye hawaye ya kunshe min,a sannu na
k'arasa gabanshi na tsugunna tare da rik'o k'afafunsa cikin shashshekan kuka nake
fad'in "Ka yafe min mijina ka yafewa laifina,insha Allah bazan sakema laifi
makamancin wannan ba,wannan d'in ma bansani ba rabo ne ya ratsa bansan na samu
wannan cikin ba".

D'aga min hannu yai cikin razanarwa " karki raina min hankali mana ,don kin
maidani gara zakice tsautsayi ne, in rabo ne me yasa da kikaga cikin ta bayyana
biki sanar min ba tunda wuri insa a zubdashi,ai na fad'a miki ban son haihuwa yanzu
ban shirya zama baba ba yanzu,d'an yaro dani anmin aure cikin shekarun k'uriciya
na hak'ura na amsa kuma ma sai ciki sai haihuwa, shi kenan mutum ya zama tsoho,
wlh impossible, badai dani ba".

Yana kaiwa nan ya janye k'afar sa yabar d'akin.

Niko nace( oh🤔 me hali baya fasa halinsa,anata murna UK ya shiryu ya gyara
d'abi'unsa ashe da sauran rina a kaba)

Bin bayan sa nai da kallo ina share hawaye na,cikin zuciya ta nake rok'on
Allah ya dafamin ya kawo min agajin sa cikin lamarin nan.

Yana fita kai tsaye gidan su ya shiga don jiya yana cikin damuwa Sam bai
samu damar komawa sun k'ara gaisawa dasu ba.

Yanda Abba yai tunanin ganin sa cikin tsananin farin ciki ba haka ya ganshi
ba,don fuskar nan tashi d'aure tamau yai sallama cikin parlourn Abban ya shiga,
binsa yai da ido yana mirmishi yace "Babana ka samu fitowa ".

Zama yai sosai gaban Abban yana d'an kalato fara'a ya risna ya gaida shi,cikin
farin ciki yake amsa mai tare da tambayar sa ya hanya ya gajiya kuma.

Cikin d'an yak'e yace " Abba gajiya ta gudu sai abunda ba'a rasa ba".

"To masha Allah, ina fatan dai komai lfy ko".

" eh Abba,ina Aunty murjah ?".

" Taje kawo min abinci ,amma kuma Daddy ya naga fuskar ka kamar da matsala".

D'an shafo gashin sa yai yana d'an tsakin gefan baki yace "A'a Abba ba komai
kawai kaina kemin ciwo tunda na tashi a bacci amma na sami magani ma a gidan
nasha".

"To Allah ya sauwak'e gajiya ce kawai kuma daka sani ka kwanta ka huta sosai
zuwa azahar sai ka fito".

Zaiyi magana Aunty murjah ta shigo d'auke da kayan Abinci fuskar ta kuwa cike
da fara'a tace" A'a mutanan k'asar Hindu har ka fito ".

Cikin mirmishin yak'e yake gaisheta bayan ta sauke kayan abincin, zama tai
tana amsa mai da tambayar sa ya gajiyan hanya,sannan ta had'awa Abba abincin suna
d'an hira kad'an kad'an .
" Daddy matso muci Abincin mana".

Girgiza kai yai yana fad'in "Wlh Abba a k'oshe nake sosai yanzu na gama break
fast".

Dariya Aunty murjah tai " Haba Abba kaima dai tsokana kakeyi yaushe zaici
abincin mu ,bayan kasan y'ata ta cika mai ciki da kayan dad'i ".

Dariya sukai ita da Abba amma shi kam d'an mirmishi yai yana shafa kansa.

Jimawa kad'an Aunty murjah ta tashi ta basu waje don su D'an tattauna, Abba
nacin Abinci suna hira yana mai tambayoyi kan karatun nasu da company nin da suka
bud'e.

Yaso cinye maganar cikin nan Amma abun bazai cinyu ba,don haka ya k'ara gyara
zama yace " Abba kasan sama Khadeejah nada ciki".

Fara'ar Abba ce ta yalwata yace "Eh na sani mana Daddy nah, amma nima bai wuce
Wata biyu dana sami labarin ba,nai farin ciki kuma na godewa Allah me kyauta da
k'ari don shine Abun godiya".

"Amma Abba meyasa kaima da kake tare dasu gida d'aya baka sani da wuri ba sai
wata biyu da suka wuce".

Cikin dariya yace " An fad'a min uzirin dayasa ba'a sanarwa kowa da wuri ba ".

" To Abba Amma meyasa baka sanar dani ba tun ina can".

"A'a ba ruwa na ance min karna sanar dakai don sai dama na d'au alk'awarin
bazan sanar dakai ba sannan aka fad'a min ciki,don ance ana son yin surprise d'inka
ne,shine gift d'inka ".

D'an cizan gefan bakin sa yai cikin taikaci yana tunanin rainin hankalin da
yasa ta b'oye mai ma .

Dafo kafad'ar sa Abba yai yana d'an bugawa a hankali " Karka damu my boi ai
babban abun farin cikin samun cikin fatan mu Allah ya rabasu lfy,komai abun buk'ata
na riga da na gamai musu, yanzu haihuwa kad'ai muke jira Allah ya baku masu
albarka,kar kasawa kanka damuwa kan rashin sanin da cikin kaga yanzu daka sani ai
farin ciki ninki ninki kenan abunda baka Sani dashi ba unexpected ka ganshi sai
godiyar Allah ko ".

Cikin ransa yake mamaki wato Abba zahirin farin ciki yake da wannan cikin harya
gama mai hidima ko.

Jin Abban ya dafoshi yasa yai saurin k'irk'irar mirmishi,yace " zo muje ka
rakani unguwa in kan ya daina ciwon".
"Ok ba damuwa Abba".

Mik'ewa sukai suka fita zuciyar UK cike taf da tunani da b'acin rai.

Bayan na idar da sallar azahar ina zaune kam prayer mat ina addu'a, naji knocking
d'in sweety a bakin k'ofa "Aunty nah in shigo ko in koma ".

Shafawa nai ina fad'in" Me zai hanaki shigowa sis ".

Turo k'ofan tai ta shigo taja stool ta zauna idonta cikin nawa ,zama nai nima
bakin gado ina fad'in " sai yanzu kika shigo tun safe".

Y'ar dariya tai tace "wlh Aunty na bacci nai sosai sai around 12 na tashi Aunty
tace min broth d'in ma ya shiga yana tambaya ta ".

" hmmm y'ar hutu sannun ki".

"Hhhhhhhh ba wani y'ar Hutu kawai dare na raba ina aiki a system wlh. Amma sai
naga idonki kamar kinyi kuka ".

K'ok'arin danne damuwa ta nai nace " ah haba wane kuka zanyi kuma,kawai ban sami
ishashshan bacci ba,kin San wannan babyn naki tunda ya girma bai barina baccin
kirki".

Zuba min ido tai tana son fahimtar gaskiyar zance na, "Amma Aunty nah . .".

Shiru tai kuma kawai


Nace " ya kikai shiru ?".

Mirmishi tai tana girgiza kai "A'a kawai dai ina son kiyi hak'uri da duk
abunda zaki gani daga broth, kar kisa wani Abu a ranki kinga hawan jini baida dad'i
game ciki kuma damuwa ke kawo shi.

" karki damu sis ba komai kinji".

Jinjina kai tai daga nan muka shiga hira.

*********
Yau kwanan sa biyar da dawowa babu abunda ya canja tsakanin mu, zan mai girki
yaci in gyara mai d'aki, iya kaci inna gaisheshi ya amsa a ciki ciki daga nan kuma
ba wata kalma da zata k'ara had'a mu.

Duk yanda nakeson dannewa abun ya faskara kullum bana bacci amma ban gajiya da
kaiwa Allah kukana, abun yana ban mamaki da d'aure min kai ace d'an Adam Allah yai
mai kyautar d'a guda amma ya rink'a nuna k'iyayyar abun a zahiri, abunda yake
k'ara sani cikin damuwa shin haka zan haifi d'an ya taso babu soyayyar uba,wannan
ke k'ara samin damuwa matuk'a.

********
Cikin dare yana kwance kan katafaran gadon sa me cike da ni'ima amma babu wani
walwala a tare dashi, buk'atar daya tara ta tsawon lokaci ce ke taso mai, juyi
kawai yake yana damk'e marar sa data d'aure mai tamau,tun saukar shi garin yake jin
wutar sha'awar shi na ruruwa gashi Khadeejah tasa waigi tsakanin shi da ita,ta
b'ata mai ta ha'ince shi, yanzu badan wannan cikin ba da yanzu ya kauda k'ishin
dake damun sa,da tuni yanzu suna kwance jikin juna suna shan soyayyar su tabbas da
yasan da labarin cikin nan tun yana karami babu abunda zai hana yasa a nik'eshi.

Tabbas yana son Khadeejah so mai tsanani yana jinta can cikin k'asan
ransa,amma wannan b'acin ran ya danne komai yanzu in banda haushin ta babu abunda
yakeji. Ko son kallon ta bai yi,don in ya ganta ma b'acin rai ke taso mai, ya zama
dole ya nemawa kansa mafita,bai k'aunar auran mace sama da d'aya a rayuwar sa,amma
yanzu tunda Khadeejah ta zab'awa kanta haihuwa to zai barta da haihuwar zaije ya
nemo matar wuce sa'a wadda bazata tara mai yara a gida ba,kawai don soyayya zai
aureta,don shi baiyi aure don ya haihu ba.

*Taku* *ce*
*Y'ar* *mutan* *ja'oji* ✍
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

*ALLAH* *KAI* *KAD'AI* *KASAN* *DAMUWAR* *DAKE* *K'ASAN* *ZUCIYA* , *ALLAH* *KA*
*KAWAR* *MANA* *DA* *DUKKAN* *DAMUWAR* *MU* 🙏🙏🙏

0⃣5⃣0⃣
0⃣5⃣0⃣ 0⃣5⃣0⃣

Damuwar da nake ciki ta wuce zuciya har ta fara bayyana a zahirina,duk yanda nake
k'ok'arin b'oyewa abun ya wuce haka,yau tsawon sati biyu da dawowar sa amma kullum
cikin bak'in ciki nake yini ina kwana babu sassauci tsakanin mu, duk iya hakkin sa
dake kaina ina iya k'ok'arin saukewa amma shi ya gagara sauke nawa ko guda d'aya.
Yau kam na tashi jikina ba dad'i gashi wancan satin ban samu naje awo ba,don
haka yau nace mai ina son zuwa ganin likita in kujerar da yake zaune ta ban amsa to
shima ya bani,haka nq gama magana ta na tashi na fita. Banda inaiwa Allah na
biyayya da babu abunda zai hanani fita a wannan ranar don ni kad'ai nasan ciwon da
nakeji a tare dani, a daddafe nake har yamma sweety ta shigo kallo d'aya tai min ta
gane halin da nake ciki, bayan ta zauna ta rik'o hannu na" Aunty na ya dai na
ganki a haka ko baki da lfy "

D'an cije bakina nai cikin son basarwa nace " kawai kin san yanayin jikin namu
sai a hankali".

Cikin nuna tausawa tace "Ayya sannu Allah dai ya rabaku lfy,ai an kusa insha
Allah".

Mirmishi nai ina cije ciwon da nakeji, a hankali take jana da hira da son kawar
min da damuwar data gani kwance kan fuskata, ni d'in ma cikin k'arfin hali nake
b'iye mata har aka kira magriba ta wuce gida nima na tashi don yin salla.

Bayan sallar isha'i na samu da kyar naci abinci ba kwanta don wani zazzab'i ne
me zafi ya rufeni, sosai nake kakkarwa har hak'ora na na had'ewa cikin ikon Allah a
haka wahalallan bacci ya d'auke ni ,duka duka na awa guda nai na farka da wani
sabon ciwon mara tun ina juyi kan gado harna sakko k'asan rug inata murk'ususu da
ambaton Allah, tsawon awa biyu na d'auka ciwon ba sassauci a sannu na d'aga kai
ina kallon agogo duka duka lokacin k'arfe d'aya na dare, koda ban tab'a haihuwa ba
amma inaji a raina wannan yai kama da ciwon nak'uda nake yi, amma ya zanyi ko in
kira sweety a waya ne ko dai Aunty Hafsa zan kira ,na rasa me yakamata inyi nasan a
wannan halin ko na kira UK bai zama lalle ya kula dani ba, don haka kawai na mik'a
kamarina ga Allah nasan ya isar mini, Hukunci na ubangiji wajan k'arfe biyu wani
wahallan baccin ya sake d'aukata ina jingine jikin gado shikam ban San iya lokacin
dana d'auka yin saba,nadai san bawai dad'in sa nakeji ba, cikin mafarki naji ciwo
na k'ara sand'ata inayi sannu sannu harna farka tofa tun daga lokacin ganga ganga
ya taso min ba sauk'i yi nake inaji kamar raina ne zai fita kiran sunan Allah nake
ina neman d'aukin sa.
A kunnena aka fara kiran sallar Asuba har aka shiga masallaci a lokacin
k'arfi na ya gama k'arewa numfashi ma da k'yar nake fiddawa, ina kwance kamar kaya.

UK ya dawo sallar asuba har zai wuce d'akin sa sai ya tuna yau k'arfe shida zai
fita don katsina yake son zuwa ya gaida su kuma a yau yake son zuwa ya dawo don
haka bari ya sanar dani in had'a mishi break da wuri.
Yana turo k'ofan ya ganni kwance yai zaton ma bacci nakeyi a k'asan amma me
sai yaga jini na bina da sauri ya k'araso cikin d'akin yana fad'in "Ke Khadeejah
Khadeejah ".

Idona na rufe ruf alamar ma ban cikin hayyacina a firgice ya k'araso ya d'aga
ni yana jijjigani da kiran sunana, amma ba amsa tsoro ne ya kamashi yace "
innalillahi kar dai rasuwa tai" ki yai gaban sa ya fad'i kwantar da ita yai ya fice
a guje zuwa d'akin sa ya d'auko wayar sa bayan ya dawo d'akin ya k'ara d'agoni
jikin sa yana kakkarwa ya fara lalubo number d'in mutan gidan su duk Wanda ya kira
tak'i shiga sai da yai tayi sannan ta Abba ta shiga yana d'awaya yace "Abba
Khadeejah Khadeejah Abba kuzo don Allah".
Cikin d'imuwa Abba yace " ba lafiya ne UK to gamu nan zuwa".

Aje wayar yai yana hura min iska a hanci na,wani numfashi naja ina ambaton
Allah dishi dishi nake kallon sa murya can k'asa nace " Reality Kaine?".

"Nine Khadeejah nine sannu kinji ".

" ka yafemin laifin da nai maka mutuwa zanyi ka yafe min".


". Kiyi shiru ki daina cewa komai Khadeejah kinji".

A haka su Aunty murja da sweety suka fara knocking " Aunty Ku shigo k'ofar a
bud'e take ".

Da sauri duk suka turo k'ofar ganin jinin dake bina yasa Aunty sakin wani salati
tana fad'in" garin yaya ka barta haka da ciwo Daddy".

Girgiza kai yake yana fad'in "Aunty nima yanzu na risketa a wannan halin,muje
asibiti ".

Ciccib'ota yai da gudu gudu suka fito inda Abba yake cikin mota harya kunnnata su
kawai yake jira don ko takan driver bai biba, baya yasata shida sweety Aunty ta
zauna gaba, tafiya suke kowa cikin tashin hankali bamai magana,tafiya bamai yawa ba
ta sadasu da family hospital d'in su, cikin gaggawa aka karb'eta zuwa maternity.

Zaman awa uku cif sukai ba wani k'ok'k'waran bayani duk likitan daya fito sai
dai yace musu su k'ara Mata addu'a ta kusa. su yaya haroon da suka zo tun d'azu
suma suna zaune sunyi jigum jigum kowa bakinsa d'auke da addu'a.

Tunda nake ban tab'a tunanin ciwon nakuda yakai haka ba,duk da inajin yanda ake
fad'ar sa,kuma ansha yin nakuda a gabana amma yau danaji ciwon a jikina na tabbatar
iyayen mu sunyi jihadi wajan haihuwar mu,ciwo ne wanda bashida misali,rok'on
ubangiji nake ya karb'i raina in huta,don k'arfina ya k'are, ko hannuna ban iya
d'agawa duk iya rarrashin da nurse's d'in nan da suke min kan inyi nishi abun ya
faskara na kasa, UK kuwa da yake kaina rik'e da hannayena zuwa lokacin yai kuka ya
k'oshi likitocin sunyi sunyi ya fita yak'i, don har mari ya kusa tsinkawa wata
nurse data Dame shi kan ya fita,ca yake ai mata ta tace kad'ai a d'akin babu inda
zanje Ku kashe min mata ta".

A hankali nake mai alamar ya sunkuyo inmai magana,cikin muryata dabata fita nace
"Kayi hak'uri zan mutu kana fishi dani,don Allah ka yafemin ko ban haihuba na
mutu ka yafemin ka rink'a bina da addu'a. . . . in kuma na haihu don Allah kayi
hak'uri ka nunawa abunda na haifa gata ka kaunaceshi,bana so d'ana ya tashi da
rashin soyayya mahaifi da maraicin uwa kuma,ka yafemin kaji mi . . .

Ban k'arasa ba idanuwa na suka rufe,


Wata gigitacciyar k'ara ya saki yana fad'in" Karki tafi don Allah Khadeejah
karki mutu ki barni wlh ina sonki ban gaji da zama dake ba,ki taimaka min Khadeejah
ki tashi wayyo Allah mata ta".

Kukan sa ya k'ara jawo hankalin jama'ar dake waje har y'an gidan mu suka
k'araso wajan d'akin a rude ta window suke lek'awa suna tambayar mene ne amma
gunjin kuka kawai hakan yasa suma sakin kuka don tunanin su kawai na rasu ,
likitocin da suka shigo d'akin suka k'ara dubani nan suka tabbatar musu da raina
suma nayi,kuma ya kamata a gaggauta yin aiki a cire min cikin.

Da k'yar Abba ya lalkab'ashi ya sami nutsuwar yin signing kan takardar cs d'in
da za'a min.hankalin y'an uwa ya k'ara tashi wasu na kuka wasu na salati,shi kuwa
gogan cikin firgici yake fad'in " don Allah kuyi kuyi mata aikin nan Ku cire mata
wannan cikin mata ta nake buk'ata don Allah karku bari ta mutu, kin gama Khadeejah
bazaki k'ara haihuawar nan ba kin gama ta batada amfani".

Ganin yana neman zaucewa yasa Abba kamoshi zuwa kafad'ar sa yana bubbuga bayan
sa"cool down my man kayi shiru haka kaita mata addu'a zata tashi insha Allah, zata
tashi bazata tafi ta barka ba kaji ".
Cikin shashshek'ar kuka yake fad'in" Abba ka sani fa ka sani a irin haka mamy ta
rasu muka rasa ta a gun haihuwa mamy ta rasu ga Khadeejah ma zata mutu wajan
haihuwa ".

K'wallar data taru a gefen idon sa ya share da hannun yana jijjiga kai don shima
Abba cikin rud'ani yake,haka mamy tai haihuwar sweet taita zubda jini harta
rasu,don haka yake jin mutuwar ta ta dawo mai sabuwa A yau duk ya rud'e shima.

Duk abunda ya kamata anyi aiki kawai za'a shiga da ita yanzu.yanda aka turo
ta kwance akan keken zuwa d'akin operation d'in ya k'ara saka y'an uwa cikin
rud'ani sunata d'aga mata hannu da fatan dacewa.

UK dai kuka yak'i k'arewa kamar k'aramin yaro rik'o hannunsa Abba yai suka
shiga masallaci dasu yaya haroon don yin sallar azahar, ko bayan da suka idar ca
yai mai ya zauna nan suyita nafilfili do rok'on Allah yasa ayi mata a sa'a.

Likitocin kuwa nata k'ok'arin su wajan ganin komai ya tafi dai dai, sunyi
nasarar ciro mata 'ya mace masha Allah nan nurses suka fito da ita don a gyara ta
su kuma likitocin na k'orarin mata d'inki.

Su Abba yaya haroon yaya usman da uban gayyar na masallaci tun sallar azahar
basu fito ba,don haka koda aka fito da Babyn basa gun su Aunty murjah ne sukai
ribibin karb'arta suna godiya ga Allah duk da duk hankalinsu naga son ganin halin
da za'a fito da uwar hakan bai hanasu farin ciki da nuna godiyar su ga Allah ba.

Bayan sallar la'asar su Abba suka fito a masallaci suna k'arasowa ana fito da
ita daga d'akin zuwa d'akin hutu itada matacciya ba maraba,don haka jiki a sanyaye
sukabi bayan su, bayan an d'ora ta bisa gadon likitan dake tsaye ya tsawatar kan
banda magana ko motsi me k'arfi a d'akin insha Allah zuwa magriba zata iya
farfad'owa.

Nan akai ta kiran y'an uwa da abokan arziki ana sanar dasu haihuwar, kowa dai
ya sami sukuni zuwa yanzu amma banda UK fatan shi dai yaga matar sa ta farka.

Sweety na gefe rungume da baby da take nannad'e cikin farin over role da towel
sai baccin ta take,zubawa Babyn ido tai tana d'an mirmishi tace "Aunty hafsa kinga
Babyn nan kamar su d'aya sak fa da broth komai nata ".

Mirmishi Aunty Hafsah tai tace "gaskiya kam kunwa yarinya ta wayo babu abunda ta
d'auko nata duk gidan ku tayo".

Murna fal kan fuskar sweety ta k'ara rungume Babyn a jikin ta tana jin k'aunar
ta na ratsata.

******
Duk yanda ake zaton zan farka da wuri ban farfad'o ba sai cikin dare cikin ikon
Allah kuma sai na farka cikin hankali na bakina d'auke da salati, Aunty murjah da
Aunty Hafsah da suke tare dani suka yo kaina suna fad'in " Khadeejah kin tashi
sannu sannu kinji ".
Lumshe idona da yai min nauyi nai ina son tunano abunda ya faru dani amma na kasa
tuno komai,don haka nabar idon a lumshe ina son samun nutsuwa, UK dake zaune a
parlourn yaji kamar suna ambatan sunana hakan ya tabbatar mai na farka, da sauri ya
turo k'ofan ya shigo tare da k'arasowa gaban gadon yana kamo hannun wana yace "
Khadeejah, kin farka ko Khadeejah ta".

Ina jinsa amma naki bud'e idona yaita magana nai shiru a haka bacci ya k'ara
d'auka na, jin sauke numfashi na ya tabbatar mai na koma baccin.

"Auntyn data farka meta fara cewa?".

Aunty murjah tace " Wlh da salati ta farka kuma ta bud'e idon kuma ta rufe".

Girgiza kai yai yana kallon fuskata data fad'a fayau ta rame tsakankanin
lokacin,wani tausayi ne ya kamashi ya dafe kansa dake mai ciwo, Aunty Hafsah tace
"Umar kaje ka huta ka samu bacci kona awa biyu".

Mik'ewa yai yana fad'in" To Aunty bari in kwanta kan kujerar parlourn ko zan samu
hutu".

Ban farka ba kuma sai bayan sallar asuba wannan Karon ma da salatin na farka amma
kuma yanzu ina gane komai da tunano komai da Irin wuyar dana sha duk lokaci guda
suka dawo min a k'wak'walwa, runtse idona nai Ina girgiza kai, da sannu suke ta
jeramin a lokacin kuma UK daya kira likita suka shigo tare . k'ara duddubani yai
yana min tambayoyi don

tabbatar ina cikin hankali na "Khadeejah ina Babyn da aka ciro miki?".

Shafa cikin nai idona a rufe na tuna ashe fa anmin aiki an ciro baby da sauri
nace " Ina Babyn nawa don Allah Ku bani inga mena Haifa?".

Mirmishi likitan yai yanaiwa Aunty Hafsah alama data mik'o Babyn, saita min Babyn
yai a fuskata yace " ga baby girl d'in ki me kama da Abban ta "

Zuba mata ido nai na tsawon lokaci sannan na lumshe idona a raina nake tasbihi
ga ubangiji na gode mai bisa wannan Babban ni'ima da yai min.

Ganin na lumshe idona yasa likitan mik'a musu yarinyar yana fad'in
"Alhamdulillah ta dawo hankalin ta,zuwa ko wane lokaci in tai tusa kotai gyatsa sai
Ku bata ruwan tea tasha".

Dafo kafad'ar UK yai yana dariya yace" My friend kuka ya k'are ga madam ta dawo
normal ".

Shima UK dariyan yai yana d'an shafa kansa.

***********
Bayan sallar asuba wajan k'arfe shida naji shigowan UK cikin d'akin yanaiwa su
Aunty sallama zaije gida yai wanka,Aunty tace " Daddy ka samu in kaje kai wankan
kaci abinci ka kwanta ka huta ko zuwa azahar ne saika dawo ".

Amsawa yai da to ya k'araso bakin gadon ya lek'a fuskata yana fadin" wannan
allurar tanada k'arfi sosai baccin bai bar kantaba har yanzu".

Aunty murjah ce ta amsa mai da "Eh ai sai a hankali zata sake ta, kuma baccin ma
shi yafi mata kaga zata k'ara samun nutsuwa sosai ".

Gyad'a kai cikin gamsuwa sannan ya k'arasa gadon da Babyn ke kwance yana kallon
ta fuskar sa d'auke da mirmishi ya d'an shafa gefan kumatun ta, ya juya ya fice.

Bayan fitar sa inajin su Aunty nata hiran irin firgicin daya shiga lokacin da
nake labour da yanda yake ta kuka yana fad'in karna mutu na barshi, jin maganganun
su ya k'ara sani cikin mamaki dukda ina cikin halin ciwo amma nima na tabbatar da
tashin hankalin daya shiga don yanda ya kafe a labour room d'in nan yanata
rirrikeni da tofa min addu'o'i har sautin kukan da yake nake jiyowa cikin kunne
na,to wai daman UK bai daina sona ba kome,nikam na fidda raima da k'aunar shi
gareni nai tunanin ko ina haihuwa ma ya sakeni amma sai naga wata kulawa yake ban
ta musamman, tun asubar jiya har zuwa yau,kai anya kuwa babu wata k'ullalliya daya
shirya min don haka bazan tab'a yarda da shiba,kuma zanyi taka tsantsan da yarinya
ta don yanda ya nuna bai son haihuwar nan babu wani abu dazai canja mai ra'ayi.

_To_ _UK_ _bari_ _mu_ _jira_ _muga_ _me_ _kake_ _k'ullawa_ _kamar_ _yanda_
_Khadeejah_ _ta_ _fad'a_ 👀👀👀

*Taku* *ce*
*Y'ar* *mutan* *ja'oji* 🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

*Allah kaimin maganin damuta ka kawo min mafita cikin* *lamarina ,Allah ka shiga
tsakanin mu da mak'iyan mu* 🙏🙏🙏

0⃣5⃣1⃣
0⃣5⃣1⃣ 0⃣5⃣1⃣

Allah ya taimake ni wajan k'arfe goma iska ta fita a cikina don haka suka ban ruwan
tea nasha nan na d'an ji k'arfin jikina, kafin me kuwa asibitin cike yake da
jama'ar mu, y'an katsina ma da akai musu waya tun jiya wasu sun d'auko hanya
yau,tunda akace musu aiki akamin duk hankali su yak'i kwanciya.

UK kuwa tunda ya wuce gida zuciyar sa ke cike da nauyi da kuma farin cikin daya
rasa wane iri ne, zai shiga gate suka had'u da Abban bayan ya fito a mota sun gaisa
yake k'ara mai barka da tambayar me jiki,amsawa yai cike da mirmishi akan fuskar
sa, ganin da Abba yai idonsa jajir ya tabbatar akwai tarin bacci akansa,don haka
yace yaje ya kwanta ya d'an sami hutu, gyad'a kai yai ya wuce ciki.

Yana shiga parlourn ya taddashi tsaf masu su lami sun gyareshe tas duk inda ya
b'aci, daga nan sama ya haye zuwa d'akin sa ya watsa ruwa bayan ya fito kuma ya
fuskanci tarin yunwar daya tara,don haka ya wuce kitchen ruwan tea kawai ya had'a
da bread yasha a tsatstsaye sabida wani zazzafan bacci daya kama idanuwan sa, yana
gamawa kuwa ya kwanta nan parlour ya kunna a.c .

*********
A can asibiti kuwa y'an barka sunk'i Yankewa wannan ya shigo wannan ya fita kama
daga kan mutanan mu zuwa mutanan gidan su UK, kowa yazo sai yai maganar tsananin
kamar da Babyn nan keyi da Baban ta, babu wani abu data d'auko nawa banda girman
ido,inajin sweety da Aunty ummu sulaim nata mana tsiya wai yanda yayan family d'in
mu ke kama damu haka suma babyn su ke kama da family d'in ta,tunda tayo Abban ta
don ita sweety ma dagewa tai kai da k'afa bada UK take kama ba da ita take
kama,Abban su na zuwa ta kalleshi cikin yanayin shagwab'ar ta tana fad'in "Abba don
Allah Baby dawa take kama in ba niba".

Dariya yai yace " Tabbas kuwa baby da maman ta sweety take kama kobo da kobo".
Kowa dariya ya farayi, Abba kuwa zubawa Babyn ido yai fuskar sa d'auke da
mirmishi aran sa yake fad'in "Alhamdulillah Allah abin godiya,muna godiya gareka da
wannan babbar kyauta da kai mana,Allah ka rayata ka albarkace ta tsawon rayuwar
ta".

Ya dad'e asibitin saida su yaya sukazo sannan suka fita tare da zasu tafi,
yacewa Aunty murjah itama ta shirya taje gida daga nan akwai sak'o duk ta had'o
tazo dasu.

Bayan sallar Azahar Aunty murja taje gida,d'akin ya rage daga ni sai sweety da
Aunty Amrah sai k'awata Hafsah, don su Aunty Hafsah kuma da y'an gidan su da Aunty
ummu sulaim suna can parlour, Babyn dake hannun Hafsa ta fara kuka,inaji na lumshe
idona kamar ina bacci, sweety tace " Aunty na Baby na na kuka a tashi a bata nono
kika wani rufe ido".

Dariya su hafsa sukai ni kuwa nai kamar ma banji ba, sunata tsiyar su nai musu
shiru, ga Babyn taki barin kukan sweety ta d'auko ruwan zamzam take bata,inajin
yanda take lasan ruwan tan tan,sabida ansa dabino a ciki, wani irin sukuni da
nishad'i nakeji a zuciyata,tabbas zuciyata daga jiya zuwa yau babu inda babu farin
ciki a ciki, har tsoro nakeji yanda k'aunar y'ata take a cikin zuciyata tun kafin
tazo duniya don haka nake rok'on Allah ya tallafa min wajan tarbiyar abunda zan
haifa ,kar tsananin so da k'auna yasa na gaza wajan tarbiya, yanzu haka ji nake
kamar in bud'e ido inganta rungume a k'irjina amma ba dama don tunda na dawo
hankali na su Aunty ke cewa in sata a jikina amma tsananin kunya da kawaici bazai
barni ba,dukda ina buk'atar hakan, jin kukan da Babyn ta k'ara tsanyawa yasa na
d'an bud'e idon anan Aunty Amrah tace "Nahna karfa ki tsaya wani jin kunya ki d'au
hakkin yarinyar nan,wlh nono take buk'ata gashi nan sai lasan harshe take .
Mirmishi nai nace " Hafsa tallafa min na tashi".

Kamani tai na tashi na jingina jikin gadon a hankaki bayan na kara filo,saida na
daidaita zamana sannan sweety ta d'oro min ita kan cinyata, tallafota nai jikin
k'irjina na zuba mata ido ina kallon yanda taketa lasan baki tana harba hannu ga
idanuwan ta bud'e tar masha Allah, ganin na tsaya kallon ta ban shirin bata nonon
yasa Aunty Amrah matsowa kusa dani tace "bafa kallon ta zaki tsaya yiba zuge zif ki
bata tasha".

d'an marairaicewa nai nace " wlh nifa zafi nake tsoro".

Dariya sukasa gaba d'aya na d'ago ina kallon su tare da turo baki nace"ke sweety
zoki d'auke ta bazan bayar ba".

Itama matsowa tai gaban gadon tana danne sauran dariyar tace "yi hak'uri Aunty na
d'an bata kad'an kinji babu zafi ko Aunty Amrah". Ta k'arashe maganar da kallon ta.

Ganin yanda suke ta ban baki yasa na zuge zif d'in rigata a hankali cike da
fargaba da kunyar karon farko da zan fara bud'e rigata haka gaban jama'a, a sannu
nasa mata a bakinta ai kuwa ta cafke da sauri ta fara tsotsa,can na runtse idona na
cije baki inajin zafin yanda take tsotsa.

Aunty Amrah ce ta kawo bakin ta kunne na tana min rad'a" ke raguwa ce Allah,
Katon gardi ma yasha balle y'ar Babyn nan".

da sauri na kauda kai gefe ina fad'in "um um nidai baya sha ".

Dariya tasa tana gyaramin kan Babyn sosai a jikina,ta juya ta d'auki Baffa dake
kuka.
A dai dai nan aka turo k'ofar d'akin duk hankalin mu ya koma ga k'ofar, sanye yake
da k'ananun kaya farare tas takalmin k'afar sa ma fari tas yayi kyau shar dashi,
jingina yai jikin k'ofar fuskar shi d'auke da mirmishi, kallo d'aya nai mai na
maida kaina, gaisheshi suka farayi ya amsa fuskar shi d'auke da mirmishi, suna mai
barka sai washe baki yake yana amsa musu,da d'ai d'ai suka fita sweety na tsokanar
shi " broth kama daina yarda da masu cewa kamarku d'aya da Baby na,don dazu da Abba
yazo yace bada kowa take kamaba illa dani".

Dariya yai yace "To sweety ai in tai kama dake to nima zata iya kama dani ko"?.
Gyad'a kai tana dariya tace'kumafa haka ne broth".

Mik'a mai hannu tai suka tafa sannan itama ta fita.

A hankali ya k'araso bakin gadon da muke yazo tsaya a kaina yana zuba min
idanuwan sa,wani kallon k'urulla yake min wanda ni kuma wata kunya da ban san
dalilin taba ta rufeni,ga wani takaicin sa kuma a sashin zuciyata,don na d'au
aniyar koya sauko ya hak'ura ni kuma saina gasa mai aya a hannu,

Jinai ya sako hannunsa yana shafa kan Babyn sannan a hankali ya


furta"Congratulation my khady, Alhamdulillah jiki ya fara kyau,ga Babyn ma cikin
k'oshin lfy ,amm ki rink'a lura sosai kinga c .s akai miki sai kin kula don mu samu
ya had'e da wuri ".

Shiru namai kamar banjin sa, bai gajiba ya d'ora da fad'in


" sannu kinji Khadeejah kinsha wahala matuk'a kin d'aga min hankali, gani nake
kamar ranki zai fita yanda numfashi ke fita a lokacin nan,wlh na tsorata matuk'a,
yanzu Khadeejah duk a haka mata ke haihuwa su tara yaya amma wasu sai ki gansu ma
da yaya goma har sama da haka, hhhmmmm sannu kinji".
Still ban d'ago balle in amsa,sai k'ok'arin rufe rigata dana fara don naga ta
koma bacci,hannun nasa zan zuge zif d'in amma sabida a rank'wafe nake hannun bai
kaiba,matsowa yai sosai ya zuge min zif d'in sannan ya zauna kan kujeran dake gaban
gadon tare da d'aukan Babyn, zamewa nai na kwanta tare da lumshe idona.

Tunda yasa Babyn a jikin sa ya zuba mata ido yana k'ara tabbatar da tsantsan
kamar dake tsakanin su,banda kwayar idonta baby abunda yake jikinta ba irin nasa
ba, d'aga ta yai yasa ta a k'irjin sa yana wani lumshe ido,wata tsantsan k'aunar ta
yakeji yana saukar mai a cikin k'irjin sa, hannayen sa yasa ya k'ara rungume ta a
jikin sa,idanuwan sa a lumshe, tsawon mintina goma sha biyar yana a haka duk wata
gab'a ta jikin sa tai sanyi,wai daman wannan halittar ce a cikin Khadeejah amma har
yake ikirarin baya so,daman haka d'a yake da dad'in kalla da dad'in d'auka, yanzu
wannan Babyn tasa ce mallakin sa,hhhhhmmm Lalle yaso ya tafka wauta a rayuwa,
yanzu wannan tsananin son nata da yaji yana ratsa zuciyar sa da gangar jikin sa
duka haka iyaye sukeji akan yayan su,masha Allah, hak'ik'a Allah abun godiya ne".

K'ara sauko da ita daga k'irjin sa yai yasa ta akan cinyar sa,ya kama yatsun
hannunta yana kalla sannan ya cire safar k'ofar ta ya duba yatsun k'afar ma,
jijjiga kai yai yana fad'in "tsarki ya tabbata ga ubangiji halitta".

Nikam tunda na rufe idona ina dan tunani daga haka bacci ya d'auke ni, ban k'ara
sanin me yake ba.

Zaman awa guda cif yai a d'akin shi d'aya yana kuncewa da sak'awa,bak'in da akai
yasa ya tashi ya fita,ni kuwa banma san me akeba, sai bayan na tashi sweety ke
cemin ai ya dad'e bai fito a d'akin ba ta shigo taga na barshi shi d'aya zaune ni
inata bacci,mirmishi kawai na mata na kauda zancan.

**************
Kwanakin mu hud'u yau a asibin masha Allah jikin nawa yanata yin kyau,don yanzu
da kaina zan tashi in zazzagaya a haraban asibitin kuma koda yaushe in za'amin
dressing wajan suna fad'in banida k'anjiki don yana had'ewa yanda nakeso.
Koda yaushe safe da dare UK na asibitin nan wata zafaffiyar k'auna ke nunawa
Babyn nan,gaban kowa bai jin kunya ko hannun wa take in yazo zaiwa sweety inkiya ta
karb'a mai ita, kuma inya amsheta haka zaita rungume ta yana mata kiss har hira
zakaji yana tayi da ita kamar tana jinsa,wani sa'in ma fita yake da ita harabar
asibitin sab'e a kafad'ar sa yana zagaye da ita. Y'an uwana da sukazo daga sakkwato
kullum suna zuwa su yini ana da dare yaya in yazo ya wuce dasu gida don Aunty
Hafsah da sweety ne suke kwana dani, tsakanina da UK ba sauyi in yazo zaita jana
da surutu da hira yana nuna min wata kulawa ta musamman amma in ba' a gaban mutane
bane kallo bai isheni ba,in na saurareshi to bamu kad'ai bane a cikin d'akin da
mutane amma donni dashi duk maganar da zaiyi kurma nake komawa, abun na damun sa
matuk'a ya ban hak'uri yamin magiya ya rarrasheni amma a banza,koda yaushe ca yake
yayi nadama in yafe mai,amma ko zuciyata tai sanyi naji kamar in bar komai in share
sai inji na kasa inna tuno maganganun da yake fad'a min duk sai inji wani takaici
na taso min.

************
Randa mukai kwana biyar aka sallamemu, muka dawo gida Goggona da zata zauna
dani har nayi arba'in aka ware mata d'aki guda a k'asa don haka nima na dawo
k'asan gaba d'aya da zama.
Shirye shiryen suna aka fara dukda Abba yaso a d'aga sunan zuwa satin sama zuwa
lokacin na k'asa yin k'wari sosai,amma su Aunty murjah sukace k'ara ayi kawai, in
huta gaba d'aya.

Ana gobe suna Me k'unshi da kitso sukazo gida yimin me kitso nayi me k'unshi
nayi nan danan suka gama min nai shar dani,gidan ya cika damk'am da jama'a don duk
mutanan mu na sakkwato sunzo hakama b'angaran UK y'an uwan su na katsina da yawa
sunzo amma su suna gidan su su sweety dukda katanga d'aya muke don haka ba sukuni
duk gidajan.

Kayan barkar da Abba yai mana nida Babyn masha Allah, haka UK da yamma ya shigo
da nashi akwatinan da yai mana set guda abun sai son barka,kowa Allah sa albarka
yake gwanin birgewa.

Da dare ina zaune tsakiyan y'an uwana munata hira yayin da wasu kecan
b'angaran masu aiki sunata aikin hidiman suna, wayata dake gefe ce tai ringing na
kai kallona ga screen d'in wayan Hubbey na gani na yawo akai,yinai kamar bazan
d'auka ba sai kuma dai na d'auka bance kala ba saida yai sallama na amsa yace
"Khadeejah ina son ganin Baby na a kawo min ita yanzu".

Zanyi magana naji harya datse kiran, Tabbas nasan umarni ya bani kuma sab'a
umarnin sa dai dai yake da sab'awa ubangiji na, kallon Fatima y'ar Auntyn mu nai
da Babyn ke hannun ta nace " kinga wai Abban ta yace akaita ko zaki mik'a mai ita
sama".

Da sauri Aunty tace "A'a ita da tazo yau tasan kan gidan kune da zata
mik'ata,tashi a ki kaita da kanki mana".

Marairaicewa nai da fad'in" Aunty nifa bazan iya hawa upstairs da ita ba".

"To tashi ta rakaki da ita".

Mik'ewa nai na gyara d'aurin zanina sannan nai gaba fatima ta biyo bayana da
babyn.
A hankali nake taka steps d'in ina hutawa don ban son abunda zanyi in sami
matsala a d'inki na, muna zuwa step d'in k'arshe fatima ta tsaya tana mik'omin
ita,d'an mirmishi nai na karb'eta na wuce zuwa d'akin nasa da sallama na tura
k'ofan na tsaya,

" shigo mana ". ya fad'a da siririyar murya, a sannu na shiga tsakiyan d'akin
na tsaya, yana zaune bakin gado ya zubamin ido, ni kuwa na kauda kai gafe ciki
ciki nace " gata ".

Tasowa yai a hankali ya k'araso gaba na tare dasa hannunshi ya karb'e ta,ganin da
yai na juya ina shirin fita yasa ya rik'oni,da sauri na kalleshi shima idon sa tsaf
cikin nawa, kauda kaina gefe nai ina fad'in" meya faru kuma".

"Ki tsaya ina son muyi magana ne".

" amma ai ca kai kawai in kawoma ita".

"Eh na sani, amma don Allah kiban d'an lokaci muyi magana".

Bazan iya bijirewa umarnin saba don haka na juyo na tsaya kaina a gefe, kamo
hannu na yai zuwa bakin gadon muka zauna,ganin yanda ya matseni sosai yasa na d'an
matsa ,mirmishi kawai yai idon sa akan Babyn yana wasa da hannunta, ita kuwa
idonta tsaf kansa,ta gefan ido nake kallon sa,yanda yake mata wasa yana kissing
d'in ta.

Kusan mintina uku,sannan ya d'ago kansa gareni yana zama serious yace "
Khadeejah! Shin yanzu Khadeejah bazaki iya afuwa gareni ba,bazaki sassauta min ba
Khadeejah, nayi nadama nayi nadamar furuci na, ban san haka haihuwa keda dad'i ba
Khadeejah saida Babyn nan tazo duniya duk bayan second's k'aunar ta k'ara tsanan ta
take a zuciyata, don Allah kimin afuwa kinji ".

K'asa nai da kaina kawai don ban son mai rashin kunya domin nasan hukuncin hakan
wajan ubangiji na,zafin zuciya bazai sani in fad'awa halaka,haka kuma ban shirya
saukowa ba don haka shiru shine mafi alkairi daga magana.

Rik'o hannuna yai sosai cikin nasa yana k'ara matsowa jikina yace " k'unshin nan
yai kyau sosai,da ina nan akayi zan bawa me k'unshin kyauta ta musamman. . .
shafawa hannuwan yai tayi yana yaba k'unshin.
" shike nan tunda baza kiyi magana ba, daman kan batun sunan da za'a sawa Baby
ne,shin kinada sunan da kike so a samata ?".

Girgiza kai nai kawai,yace "babu?".

Nace " Eh ".

" To daman tunda aka haifeta araina naso saka mata sunan mama na wato
Ruk'ayya,hakan yayi miki".

Gyad'a kai nai ina fad'in "Eh yayi,Allah ya raya min ita ".

Cikin mamakin furucina ya kalleni nad'an sakwanni sannan yace " Allah ya raya
miki ko ya raya mana".

Ban kalleshi ba na mik'e tsaye da fad'in "Bari na sauka nabar jama'a".

Bina yai da ido harna fice abuna

Girgiza kansa ya shigayi yana mamakin wannan shiru shirun dana koya a gareshi,
shi wlh yanzu bashida matsala face ita, haihuwar ce daman bai so kuma yanzu yaji
yana k'auna k'arshen ransa to menene kuma matsalar tunda daman akan ta suka sami
sab'ani yanzu ai komai sai ya daidaita su had'u suyi rainan y'ar su cikin so da
k'auna. Ya dad'e yana sak'awa da kwancewa daga baya ya zame ya kwanta yana kwantar
da Babyn a k'irjin sa,a haka bacci ya d'auke shi.

Tunda na sakko k'asa mukaci gaba da hira da jama'ata amma rabin hankali na duk
yanaga y'ata,musamman danaga lokaci yayi tsayi har awa guda da saukowa ta, nan
duk idona ya koma ga stair's d'in ina jiran sakkowar sa amma har awa biyu lokacin
na kalli agogo sha d'aya dai dai tun k'arfe tara kuma nakai mai ita, tabbas kunya
da kawaici au kad'ai ne sukai min Katanga da tashi zuwa d'auko abata, sabida ko dai
dai da minti guda banso in wulga idona ban ganta ba kusa dani.duk da bazan nuna
hakan a zahiri wani ya fahimta ba amma zuciyata zata kasa sukuni kuwa.

Sha biyu dai dai kowa ya tashi daga hira don kwanciya,amma nikam ko baccin ma
banji,Goggo ce tace " To yau dai da alama jinjira wajan Baban ta zata kwana tunda
gashi har yanzu bai sakko da ita ba".

Yaya jummai tace "hhhhhhhh komai dare zaki ga ya kawo ta wuyar ta ta buk'aci
nono ai, k'ilama bacci ne ya d'auke su amma data farka zata nemi uwar ta ai".
Daga haka naga kowa na k'ok'arin kwanciya, tashi nima nai zuwa d'akin jegon mu
zuciyata ba dad'i, toilet na wuce na gyara jikina nai brush na fito sannan nai
shirin bacci cikin doguwar rigar bacci me laushi wadda ta sauka har k'asa ,batada
hannu sai d'an siriri,gabanta duk botir ne ajere har zuwa wajan ciki, d'an turare
na goga na haye gadon da addu'a kan bakina.

Tunda na kwanta ko sau d'aya bacci baizo idona ba,yayin danaga sauran jama'ar
d'akin sun bud'e baki sunata bacci harda minshari abinsu.

Duk motsin agogo na kan idona har wajan k'arfe biyu saura ji nake kamar in tashi
inje in d'auko abata.
Can nakejin kamar sautin kukan ta na k'ara kasa kunne sosai kafin in tabbatar
naji an bud'e k'ofar fatima ta shigo idonta cike da bacci take fad'in" Aunty kinga
kizo Baby ta tashi gata can hannun Abban ta,muna kwance a parlour kukan ta ya
tadani yace in kiraki".

Tashi nai nabi bayan ta muka fita,ina fita parlourn naji yanda take tsanyara
kuka har cikin raina,da d'an sauri na na k'arasa ya mik'o min ita yana fad'in
"yanzu ta farka kuma da kuka,bacci ne ya d'aukemu tun bayan fitar ki".

Ban tsaya sauraran surutun da yake ba na juya zuwa d'aki don kukan da take har
tsakiyar raina nakeji.

Da sauri na d'auko ruwan zamzam d'in ta nai bisimilla ina samata fidar a baki ta
fara shan ruwan da sauri saurin ta, daga nan na b'alle botir d'in Rigar na fara
bata nonon cafka tai ta fara sha na lumshe idona ina k'ara rungume ta a
jikina,wani sanyi na ratsa zuciya ta,ji nake kamar tai shekara bata wajena,ta dad'e
tana shan nonon na canja mata wani shima saida na Tabbar ta k'oshi sannan nasata a
kafad'a ina shafa bayan ta can naji tai gyatsa ,sauko ta nai na cire mata rigar
jikin ta har pampas d'in na canja mata wasu, zuwa lokacin harta koma baccin, bayan
na kwanta na sata jikina inajin wata nutsuwa na ratsani daga nan bacci me nauyi ya
d'auke ni.

*TAKU* *CE* *Y'AR* *MUTAN* *JA'OJI*✍


🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _lentertain_ _our_ _Readers_

0⃣5⃣2⃣
0⃣5⃣2⃣ 0⃣5⃣2⃣

Tun sassafe gida ya fara kacamewa da hayaniya, hidima kowa keyi, nikam ina d'aki
cikin adona me sauk'i na atamfa super riga da zani,sai babyn da akaiwa wanka itama
cikin kayan sanyi don da sanyin safiya garin.
Sweety ce ta shigo da gud'a tana fad'in "Broth ya biyani,ya gama min komai
wlh,yayiwa sweet mom d'ina takwara kuma nima yayi min,shiyasa tunda akai haihuwan
nake tambayar sa me sunan Babyn yak'i fad'a min nace zan bada ai mata calander ne
yace ya bada ayi komai duk don yana son surprise d'ina,tnx tnx my broth".

D'aukan Babyn tai ta rungume ta tsam" Allah ya raya mana ke namecy yayi miki
Albarka".

Kowa dariya kawai ke mata, ta jiyu tana kallona da kashe ido cikin tsokana
tace"Em Aunty na naga wannan gidan naku baku bani d'aki ba sabida ba'a buk'ata
ta,amma yanzu kam dole zanya kaina d'aki don inyi rainon sweet daughter ".

Dariya nai ina fad'in" hakan shi zaifi min dad'i wlh,ki kwaso kayan ki kawai".

Y'ar dariya tai tace tom "Tom yanzu me zamu rink'a kiran ta".

Kafin nai magana Aunty Amrah tace " Ai zab'i na gareki maman Baby ".

Farrr tai da ido cikin tsananin farin ciki da nishad'i tace " em mu rink'a kiran
ta little ko Aunty na ".

Mirmishi nai ina fad'in" banida zab'i fa sweety duk yanda kukai".

Sauran y'an d'akin suka amsa mata da yayi, don haka ta juya cike da farin ciki
ta fice.

Taro yai taro zuwa azahar gidan nan namu babu wajan aje k'afa aji dad'i, jama'a
damk'am ,kowa barka barka,anyi hidima anyi yanke yanke ,anci ansha an raban
kayayyaki ,sosai ga calendar, stickers memo,key holder abubuwa sosai aka raba, Duk
hidiman da ake Abba shima yana can parlourn sa da mutanan sa suna waleema,haka
uban gayyar,abokan sa kamar mata haka aka rink'a taron nan dasu,masu hotuna da
video tako ina d'auka suke,abun yayi,ni kuwa sabida d'inki na ban wani zirga
zirga,ina zaune main parlour yanda kowa yazo zai ganni sai dai in zan canja kaya
nake tashi, pic's ma da k'yar naje aka yiyyi dani, na sake da UK anata mana hotuna
ina fara'a ta kamar ba komai tsakanin mu,Babyn sa kuwa yana manne da ita, har sai
da wani abokin sa ya tsokaneshi "Oh abokina nan kaita kukan an had'a ka da y'ar
Arabic an gama dakai,to sai gashi daga aure kai bilulun da ita harda ciki da
haihuwa".

Dariya yai yana kallon sauran abokan nasa yace " Wato guys wlh ina baku shawara
kuyi azama kuje ku nemo *y'an* *Arabic* d'in nan wlh sunfi ribar aure,duk wata
ni'ima an tattarata garesu,nutsuwa da kwanciya hankali tana ga mijin daya auri
ma'abociyar addini ga sanin sirrin so da iya sarrafa soyayya nan da nan ake
kwancewa mutum k'ulli. . . . 😍

K'arashewa yai da dariya yana tafa hannu.

Suma duk dariyan suka sa wani cikin obakan yace "d'an iska yanzu ai saika daina
yimusu gani gani tunda ka latsa kaji bauwar dake tare dasu,ni daman shiyasa nafi
son auran mace maabociyar addini wlh,ba ruwana da wani kyanta ko wayewa,don haka
don Allah ka fad'awa Khadeejah ta lalubomin cikin k'awayen ta nima inbi sahun mijin
*'YAN ARABIC*😂".

Duk Kansu dariya suke wasu na mama kin yanda duk d'abi'un UK ya canja tun bayan
auransa .

Bamu muka sami kanmu ba sai bayan sallar magriba gidan ya sarara sai masu k'ara
kwana Wanda suma sunfi jiya yawa.

Ruwa me zafi sosai na samu nai wanka na gasa jikina,sannan na had'a tea me kauri
nasha,daga nan naji dama dama, Babyn ma wanka aka mata da ruwan zafin don sabida
yawan d'auka jikin ta zai mata ciwo,amma da aka gasata da ruwan zafi zataji dad'i.

Da wuri bacci ya d'aukeni ban tsaya sauraran su da hira ba.

*********
Washe gari tashi ba sai wajan Tara,bayan nai wanka Goggo tasa aka shigomin da
kayan abunci naci nai nak Alhamdulillah, sai a sannan aka shigomin da Little Ruky
an shirya ta tun tuni cikin jan kaya masha Allah tai kyau tsaf da ita sai tsotson
yatsa take,a hankali na janye yatsan a bakin ta nasa mata nono ,idona akanta ina
k'ara jin son ta na shiga zuciyata, naji an turo k'ofan an shigo, d'ago kai nai don
ganin waye,ganin sa tsaye ya harde Hannaye yasa na maida kaina k'asa, k'arasowa yai
bakin gadon ya tsugunna tare da rik'o hannu na cikin nasa d'aya hannun kuma yana
shafa kan Babyn,tsawon mintina muna a haka daga bisani ya nisa kana yace"my deejah
barka da safiya". Tunda ni ban samu matsayin a gaidani ba.

Kunya kuma naji ta kamani amma saina basar ciki ciki nace "ina kwana".
Bai amsa ba illa kafeni da yayi da idanuwa,sannan yasa hannu ya d'auki little
ya zauna bakin gadon yana mata wasa.

Minti biyar ya waiwayoni tare da tattara dukkan hankalin sa ya fara magana"


Khadeejah tafiya ce ta taso min da asuba aka kirani, wai ana neman mu a Lagos kan
company d'in mu,ina tunanin one week zamuyi mu dawo insha Allah, yanzu haka ana
jirana k'arfe 11 jirgin mu zai tashi,ki kulamin da mama na da kanki, kiyi hak'uri
dani ki yafemin laifukana".

Shiru yai na d'an lokaci sannan ya d'ora " akwai kud'i a d'aki na,duk abunda
zakiyi kije ki d'auka, sannan idan bak'in mu zasu tafi ki sallame su.

Mik'ewa yai da Babyn a hannunsa yana yin hanyar waje,tunanin shi zan biyo shi
yaga ba niyya,saiya tausasa murya yace "zo muje ki dawo da ita".

Ba musu na tashi nabi bayan sa,a parlour ya tsaya yaiwa jamaar da sukai saura
basu tafiba sallama,suka bishi da addu'ar Allah ya kiyaye hanya.

Ni kuwa a kunyace na ratsasu na wuce.


Driver na hangomu ya tada mota, baya ya shiga ya zauna sannan ya rungume ta
jikinsa tare da kissing d'in ta,miko min ita yai idonsa k'ir cikin nawa,yana jira
yaga me zance. K'asa nai da kaina a hankali na furta " Allah ya kiyaye hanya ya
bada abunda akaje nema".

Cike dajin dad'i ya amsa"ameen ameen dear,ki kulamin da kanki da mamana ".

Gyad'a kai kawai nai na juya shima driver ya tashi motar suka tafi.

Dana koma cikin y'an uwana hira muka bud'e yayin da masu aiki keta faman aikin
naman hakika.

*******
Washe gari kowa ya koma inda ya fito ya rage gidan dagani sai goggona da
Aslamiyya y'ar Auntyn mu da zatai hutu anan.duk sai naji gidan yamin wayam,donma
Goggo me hira ce tana bamu labaran dariya dana mutanan da.

****
Bayan kwana biyar da suna UK ya kirani a waya sama sama muka gaisa ya tambayi
y'ar sa nace mai tanan qlau daga haka na kashe wayan.

Munci gaba da wanka tsawon sati hud'u na murje nai kyau dani Little Ruky ma tai
b'ulb'ul Masha Allah da ita,ga wayo tayi don yarinyar akwai wayo kullum idonta
k'yar tana kallon kowa. Zuwa lokacin ya zama UK bashida wani aikin in yana gida sai
na kula da ita,don yanzu inya dawo sai intai kuka kawai nake ganin ta ya kawomin
ita inbata nono ya koma da ita,ganin irin kulawar da yake bata yasa zuciyata yin
sanyi don dama akan ta ne gabar,amma dukda haka fa ban sakar mai kamar farko,sai
dai yanzu zamuyi hira kad'an kad'an fuskata ba walwala sosai .shi kam hakan ma
yamai dad'i yasan a sannu zamu dawo normal kamar da.

D'inki na ya warke ras jikina ya had'e yanda ake buk'ata,gashi daman banyi
dogon jini ba duka sati biyu ya d'auke min don haka na dage na fara gyara kaina da
kayayyakin da aka had'omin daga sakkwato, Goggo ma batai sanya ba wajan bani wasu
sirrika daya kamata me jego ta kiyaye bayan d'aukewar jinin bik'i,Masha Allah ni
akan kaina inaji na zam zam duk da daman bawai na bud'e bane tunda bada kaina na
haihu ba.

Watan mu biyu cif Goggo ta fara shirin tafiya gida,don daman mun dagene ta zauna
mana har zuwa yanzu,amma tun muna ar'bain taso tafiya. Siyayya sosai UK yai mata
na tsaraba hakama Abban su ya bada kud'i akai Mata siyayyan tsaraba,duk na shiga
damuwa sabida ba k'aramin shakuwa da sabo bane ya k'ara shiga tsakanin mu, gashi
d'aki guda muke kwana a k'asa ko yaushe muna tare, naso nabita ma muyi yawon
ar'bain yayyena maza da basu gantaba in kai musu ita amma danaiwa UK maganar yace
gaskiya bazan tafimai da yarinya har sakkwato ba tana wata biyu in bari inta k'ara
k'wari da kansa ma zai kaimu, banso ba haka na hak'ura.

Daran da Goggo zata tafi mun raba dare muna hira har bayan sha biyu muka kwanta
.

Kiran sallar farko naji ana mana knocking door, da mamaki nace " waye?".
Cikin muryar bacci naji yace "Khadeejah bud'e nine".

Tashi nai ina mutstsika ido na bud'e don nai tunanin ca zai in mik'o mai little
don haka na d'auke ta nasa a kafad'a na fita,tsaye na ganshi yanata safa da marwa
tsayawa nai a bayansa ina fad'in" lfy?".

K'arasowa kusa dani yai yana fad'in "lfy qlau ina Goggo?".

Nace " bacci take".

Yace "ki tasheta ki had'a kayanki kema yaya yai min waya yanzu wai an mai waya
daga gida umma batada lfy zakuje ku dubata gobe zaku dawo".

Zaro ido nai ina fad'in "innalillahi wa innailaihi ra'jiun,meya sameta kodai
rasuwa tai kuka b'oyemin ?".

Rik'o hannu na yai ganin jikina nata rawa ya karb'i little tare da zaunar dani
kan kujerar dake gefe na," ki kwantar da hankalin ki Nahna,umma tana nan da ranta
wlh kawai ciwon ciki ne yaya yace min to har an kwantar da ita ma a asibitin tun
jiya da yamma cikin dare aka mai waya,to suna son zuwa yau don haka yace zasu biyo
su dau Goggo tunda daman yau d'in zata wuce,yace inba damuwa kema in barki Ku tafi
tare,ki kwantar da hankalin ki yanzu kije ki shirya ana fitowa masallaci zasu biyo
ku tafi".

Share hawayen daya gangaro min nai ina mik'ewa zuwa d'aki .

Tashin Goggo nake cikin kuka ta farka da salati take take tambaya ta meye ina
matse ido nake sanar mata meke faruwa, salati ta d'auka da mik'ewa tana gyara
d'aurin zani tace "Allah ubangiji ya jishshemu alkairi, wannan ciwon ciki kwana
biyu ya matsawa Yaya,yi maza ki had'a kayanki bari inyo wanka da alwala".

K'aramin akwati na d'auko na had'a kayana set uku dana little a ciki duk abunda
zamu buk'ata na had'a, idona yak'i yabar zibda hawaye don gabana ya tsananta
fad'uwa kawai ji nake kamar b'oyemin ake kodai ummata ta rasu ne.

Goggo na fitowa aka kira asubahi da sauri nima naje nai wanka tare da d'auro
alwala,a lokacin UK ya kwankwasa k'ofa naje ya mik'o min little zai wuce masallaci,
Goggo na mik'awa ita na tada salla,ita kuma ta had'a ruwan wanka ta mata.

Wajan k'arfe shida su yaya sukazo shida yaya usman ne, nida Goggo muka shiga
bayan motar UK yanata d'aga mana hannu ya koma, ganin yanda naga jikin su yaya
amace lis yasa ni k'ara firgita, cikin share hawaye nace " yaya wai meya sami
umman ne".

"Cikin sanyin murya yaya usman ya amsa min " wlh ciwon ciki ne ,wai harya
tab'a Mata hanji yauma za'a mata aiki".

"Ya Allah ya bata lfy yasa ayi a sa'a" Goggo ta amsa da "Ameen".

*******
Lokacin da muka shiga sakkwato kai tsaye asibitin muka nufa.yanda muka tatar da
y'an uwan mu cirko cirko yasa jikin mu k'ara mutuwa, da sauri na k'arasa ina
tambayar su jikin nata sukace an shiga da ita aikin tun tuni,zaman awa guda mukai
kafin aka fito da ita,duk kanta mukayo amma aka dakatar damu da cewa ko d'akin kar
Wanda ya shiga don tana buk'atar hutu.

Har dare muna zaune muna zaman jiran farfad'owar umma amma shiru,sai cikin dare
ta farka amma kuma ba cikin hankalin ta ba,k'arshe ma sai ta fara suma hankali tace
muka kira doctor yazo kanta, allurai yai mata nan bacci ya k'ara d'aukan ta, mukam
duk hankalin mu a tashe har gari ya waye.

Tsawon yinin ranar nan haka mukayishi cike da tashin hankali don jikin umma fa
ba sauk'i saina Allah, kuka nayi shi harna gaji,kawai tunani nake in umma ta rasu
shike nan banda uwa banda uba,sai gatan y'an uwa.
wajan yamma Allah ya taimaka jikin yai sauk'i harta fara dawowa hankalin
ta,cikin yanayin tsananin rashin lfy ta mik'omin hannu na k'arasa jikin gadon ina
share hawaye nace "sannu umma,Allah ga baki lfy ".

Can k'asan bakinta tace " Ameen Auta, ina miki wasiyya da yiwa y'an uwanki
biyayya, musamman Haroon ki kula dashi da rayuwar sa,baki da sama dashi duk duniya,
sannan kibi mijinki, kibishi iya iyawarki,sannan ki kula da tarbiyar abunda kika
haifa kinji ".

Gyad'a kai kawai nake ina share hawayan daya keta gudu a idona. Haka sauran y'an
uwan mu ke zuwa bakin gadon suna mata sannu duk da ka taketa amsa musu don maganar
ta rik'e ,daga haka kuma sai bacci ya k'ara d'aukan ta, duk sai muka d'an sami
nutsuwa, har mukaje mukayi sallar magriba da aketa kira.

Gab da sallar isha'i ta k'ara farkawa da shak'uwa me k'arfi tanayi k'irjin ta


har sama sama yakeyi duk likitocin nan suna kanta, sun koramu waje, bayan mintinan
da basu wace sha biyar ba rai yai halin sa,Aunty salma dake jingine jikin window
d'in taga sunja zani sun rufe mata jiki har fuska bayan duk sun cire injinan dake
aiki ajikinta,wata k'ara data saki ya samu ankara da gudu mukai jikin window Wanda
dai dai nan likitocin suka fito suna bamu hak'uri.

*Taku ce*
*Y'ar mutan ja'oji*🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_
0⃣5⃣3⃣
0⃣5⃣3⃣ 0⃣5⃣3⃣

Jina da ganina ne ya d'auke na wasu mintina zuwa can ya dawo min tare da hargitsi
da firgici,ganin duk wata halitta data jib'anci ahalin mu zubar hawaye take,nan
take na k'ara tabbatar da mahaifiyar mu ta rasu kenan.kuka Wanda ya amsa sunan kuka
shine ya kawomin ziyara, na kifa kaina jikin bango ina kuka me cike da ban tausayi
da maraici, wato rashin iyaye babu babba ba yaro ba mace ba namiji duk wanda aka
tab'a sai ya koka. Ganin yanda muka cika asibitin da koke koken mu yasa aka
hanzarta bamu gawar zuwa gida, daga nan aka shiga sanar da y'an uwa jana'izar da
safe in Allah ya kaimu.

Nikam ban ma cikin nutsuwar da zan sanar da wani don duka a firgici nake ,ina
zaune gaban gawar addu'o'i naketa mata idona na zubda hawaye,Allah sarki Mama
abokiyar zama ta gari maman su yaya Haroon ta fice hayyacin ta don suma ma tai da
taji labarin rasuwar,sabida shakuwar dake tsakanin su ta wuce misaltuwa busiyi
zaman kishi da juna ba tun farkon zaman su har tsufan su.

Haka muka kwana tsam a zaune muna ta yi mata addu'a da karatun Qur'ani,tare
da rok'a mata gafarar ubangiji.

*******
Tashin hankalin rashi be k'ara gigita wanda yai rashi irin idan an d'aga gawa za'a
fita da ita,duk dakiya da k'arfin imanin mutum in aka d'aga gawa sai ya girgiza,
k'arfe bakwai dai dai aka d'aga gawar umma cikin makara zuwa k'ofar gida,don
sallatar ta,gidan ya hargitse da koke koken jama'a yayin da nikam idona ya kafe
k'am ba hawaye don zuciya ta ta wani bushe idona ya k'afe sai wani k'una da
nakeji kamar ana suya cikin k'irji na yanda nake a jingine jikin bango ina bin kowa
da kallo duk da fahimtar komai nake ba amma kunnuwa na naga k'ofar gida inda nake
jiyo saurin muryar liman yanata kabbara, a haka kuma hayaniyar tashin ababan hawa
ya karad'e tabbacin an idar za'a tafi kaita makwancin ta.runtse idanuwa na nai ina
taune lips d'ina tare da dafe kai cikin raina nake wa Allah tasbihi don neman
sassauci a wannan yanayin da k'unci yai wa zuciya k'awanya.

Misalin k'arfe tara ina kwance kan gadon umma na kuka nake mara sauti me cike da
k'una, a bayana naji muryar sweety da Aunty murjah suna gaisawa da mutanan d'akin
tare dayi musu gaisuwa,juyowa nai da kumburarrun idanuwa na na bud'e su da k'yar a
Kansu.
K'arasowa sweety tai bakin gadon tana dafani tace "Sannu Aunty nah,sannu Allah
ya jikan umma ya gafar ta Mata zunuban ta".

Mik'ewa nai da k'yar na zauna idona na zubda hawaye , gaisawa mukai da Aunty tana
k'ara min gaisuwa, sweety ma tamin gaisuwa tare da zama kusa dani,a hankali tace "
tare muke dasu Aunty Amrah harda Abba da broth,tun daren yaya Haroon ya sanar da
Abba mun nemi tickets wanda zamu sami jana'izar amma bamu samu ba,saina yanzu ".

Jijjiga kai nai ina share hawaye nace " Wlh ni nama manta ban sanar da kowa
ba,wayar tawa ma ban san inda take ba".
"Eh ai munata kira ba'a d'aga ba".

Su Aunty Hafsa ne suka shigo d'akin itada Aunty Amrah idanuwan su taf da hawaye
suka zauna muka gaisa tare da yiwa juna gaisuwa.

Wajan k'arfe goma Abba da UK suka shigo gidan don yin gaisuwa wa mata,da k'yar
na mik'e na fita zuwa parlourn mama inda suke mata gaisuwa, k'arasawa nai na
tsugunna ina gaida Abba " cikin tausayawa yake amsamin tare da min gaisuwa, shi
kuwa UK idanuwan sa akaina ya kasa furta min ko kala sai kallon tausayi da yake
bina dashi kawai, ni kuwa kaina yana k'asa banma san me yake ba,mik'ewa Abba yai
shima yabi bayan sa suka koma k'ofar gida.

*****
Bayan sallar la'asar Abba ya aiko inzo,a bakin gate na same shi dasu yaya haroon
a tsaye k'asawa nai ina k'ok'arin taugunnawa yace "A'a yashi tashi Khadeejah,
daman sallama zan miki zamu wuce don jirgi zamu k'ara bi kuma biyar zai
tashi,amma nida murja ne zamu wuce Rukayya da Daddy na suna nan zuwa jibi sai su
taho, kiyi hak'uri kinji Khadeejah ki rage kukan haka addu'a take buk'ata yanzu,ita
tata tai kyau tunda ta rasu ta sanadiyar ciwon ciki kinga tayi shahada,fatan mu
Allah ya karb'i shahadar ta".

D'aga kai kawai nakeyi kamar k'adangaruwa don ba baki da nayi niyar yin magana
kuka ke k'wace min.

Bayan munyi sallama yace in turo Aunty murjah su wuce.

Dana isa na sanar da ita taje taiwa mama da y'an uwa na sallama, sweety ta
rakata gun Abba a k'ofar gida yaya usman ne zai kaisu airport a motan shi.

Da dare ina zaune ina baiwa little nono Goggo ta shigo tana mik'omin waya ta wadda
kota kanta banbi ba,k'arb'a nai ina duba tarin miss call d'in dake kanta ban
tsaya duba kona su waye ba na ajiye ta gefena,ina dafe kaina da yake tsananin min
ciwo kamar zai tsage, wayar sweety tai ringing kasancewar tana salla kuma wayan sai
ruri take tana k'ara min ciwon kan yasa na jawo wayar ba tare dana duba me kiran
ba nai picking call d'in ina sata a kunne nace"Tana salla ne".

"Khadeejah".

Naji ya furta a taushashe, shiru nai karo na biyu ya k'ara maimaita suna na anan
na amsa da " na'am ".

Yace " Khadeejah kiyi hak'uri kinji,bamu samu keb'ewa nai miki gaisuwa ba, Allah
taji kan umma yai mata rahma,Allah ta karb'i shahadar ta".

A can k'asan bakina na amsa da "ameen".

Shiru duk mukai nad'an lokaci daga bisani yace " Ina little? ".

" gata tana bacci".

"Ok ki shafa min kanta,sai da safe".

" ummmhmmm".
Kawai nace na kashe wayan,don yau d'in nan magana masifar wahla take min. Lalle
rashin iyaye masifa ne,wato yanzu sai nakejin har rasuwar Baffa tana dawo min
sabuwa fill, duk da ban girma a cikin gidan mu tsakiyar iyaye naba hakan bai hana
shakuwa me k'arfi a tsakani na dasu ba. Shiyasa yanzu nakejin ko sauran y'an uwana
da suke gari d'aya gida d'aya dasu basu kaini jin mutuwar ba.Tabbas ina son
mahaifana so na hak'ik'a kamar yanda zuciyoyin su suka ginu suma da
k'aunata.tsakanin d'a da mahaifi sai Allah kawai.

******
Washe gari ma haka akaci gaba da amsar gaisuwa har dare, sai wajan k'arfe tara
hankali na yakai ga neman little don tunda akai rasuwar tana gun Goggo sai tai kuka
take kawo min ita in bata nono, tunda tasan bana cikin nutsuwa ta nima me rarrashi
na nake nema.

D'an kalle kalle nai kozan hango ta hannun wani amma ban ganta ba,gashi kuma na
hango Goggo a tsakar gida tana salla, komawa nai na kwanta don bazan iya tambayarta
wani tana inaba koda qlau ne balle ina cikin wannan halin.

********
UK ne tsaye cikin d'akin da akai mai masauki yana ta jijjiga little dake ta d'an
kuka tana son yin bacci, tunda yai sallar isha'i ya kira sweety ta kawo mai ita
yake ta fama,don tunda yazo bai ganta ba ko sau d'aya.

Yaya haroon ne ya shigo yana ajiye mai flask d'in abincin daya shigo mai
dashi,ya d'an lek'a fuskar little yana fad'in "Ta hanaka zama ko,aima naga ta rufe
ido ko bacci zatai?".

Mirmishi yai yana fad'in" eh daman in zatai bacci sai tai rigima,yanzuma baccin
zatai".

Gyad'a kai yaya yai yana fita daga d'akin, a ransa yake sak'a tun jiyan fa dasu
UK suka zo baiga sun had'u ko sau d'aya da Nahna ba,gaskiya ya kamata su had'u ai.
Wayar sa ya ciro cikin Aljihu yana lalubo number can ya sa a kunnan sa yana fad'in
"ki sameni d'akin Sadeeq yanzu".
Daga haka ya kashe wayan.

Ni kuwa jin kiran da yayan kemin yasa na mike a hankali na jawo hijab d'ina dake
gefe na nasa tare da fita, a tsaye bakin d'akin na sameshi,ina zuwa kusa dashi na
fara hawaye,rik'o hannu yai yana fad'in" muyi hak'uri mu duka Nahna, lokacin umma
yayi dole bazata k'ara ko second guda ba,addu'ar mu take nema a halin yanzu kinji
ki tsagaita da kukan nan haka kinji ".

D'aga kai nai alamar gamsuwa .can ya cika hannun nawa yana fad'in " ki shiga
d'akin umar na ciki ki amso Babyn don kuka take ".

Gyad'a kai nai kawai tare da nufar d'akin, sallama d'auke a baki na, a bazatta
yajiyo muryar tawa don haka cikin taraddadi ya amsa,na bud'e na shiga tare da
jingina jikina jikin k'ofar.
Zuba min ido yai can ya numfasa tare da kwantar da little a gefan gadon ya taso
zuwa gareni, sosai ya matso jikina har muna gogar juna,zubawa fuskata ido yai wadda
ta fad'a fiyau yana sauke numfashi akan ta,ni kuwa idanuwa na a lumshe suke sai
hawayen dake fita cikin su suna bin kunci na.
A hankali yasa harshen sa yana lashe min hawayen tare da rik'o hannuna guda cikin
nasa yana murzawa alaman rarrashi, duk yanda yake sid'an hawayen bai sa sun tsaya
ba illama k'ara yawa da suke, zuciya tace naji tanata wani bugawa da sauri sauri
wanda har jikina shima ya fara rawa,k'ara Matsoni yai sosai ya rungume ni a jikin
sa yana k'ara lasan fuskata, sannan a hankali yasa bakin sa cikin kunne na yana
fadin " sorry my wife ki bar kukan haka kini,sorry plsss and plsss". Ya k'ara
tsantsameni a jikin sa yana hura min iska a kunne da saman fuskata. ni kam na kasa
hanashi abunda yake wanda ban san dalilin hanawan ba,a hankali nutsuwa ta ziyarceni
hawayen idon nawa ya tsaya, shi kuwa zuwa lokacin harya fara manta lallashi na
yakeyi ma. kwankwasa k'ofan da akai yasa ya sakeni da sauri ya koma bakin gadon ya
zauna yana min nuni da ido wai in bud'e, ban musa ba na bud'e k'ofar,yaro na gani
dan yaya Babba yake tambaya wai yaya Sadeeq na ciki ana neman sa,ban iya amsa mai
da baki ba sai kai dana girgiza mai kawai ya juya ya tafi,na rufo k'ofan tare da
juyowa ina kallon gefe nace "kawo ta mu koma daman yaya haroon ne yace inzo in
karb'eta tana kuka".

Bai cemin uffan ba sai zuba min ido da yai cike da tsantsar tausayi na.
Ganin tsaiwar tai yawa yasa na k'ara magana Karo na biyu cike da k'osawa
" ka kawota muje mu kwanta dare yayi fa".

D'auko ta yai ya nifoni yana zuwa ya k'ara had'e ni da jikinsa murya a sanyaye
yace "Tunda nazo bamu samu had'uwa ba,Ya hak'uri".

" Alhamdulillah ".


Na fad'a ina mik'a hannu na zan amsheta,bai hanani ba ya sakar min ita yana
fad'in" sai da safe,insha Allah gobe in anyi addu'ar sadakar uku zamu wuce".

"To Allah ta kaimu da rai da lfy".

Amsawa yai da " ameen" yana bud'e min k'ofar na fice.

Da baya da baya ya koma ya kwanta akan gadon yana dafe kansa tare da lumshe
idanuwa,tunano tsawon lokacin daya d'auka rabon sa daya rungume ta haka yake yi,
tun randa ta baro India yanzu wata goma sha d'aya kenan an tunkari shekara,
gaskiya ba k'ara min dakewa yake ba da jurewa,tunma kafin ta haihu suna cikin
rikicin nan take tsaka da buk'atar ta amma wannan turtsetsan cikin bazaima bari ya
kusan ceta ba,gashi ba jituwa ko kad'an a lokacin, yanzu kuma tunda ta haihu ba
fuskaba magana ma sai da niya take amsa mai,kwana biyu nema ta d'an fara sassaura
mai akai rasuwar nan, kuma koba haka ba yana tsoron daga fara ganin y'ar fuska ya
fito da zalamar sa tace ma don haka yake binta da bata hak'uri, shiyasa zaici gaba
da daurewa da cijewa da shan k'wayoyin kwantar da sha'awa,har Allah ya k'ara
sassauta zuciyar ta ta sake su dawo normal.

Ni kuwa tunda na koma ciki naiwa Little shirin bacci na kwanta ina lallab'ata
tai bacci a haka nima baccin yai gaba dani.

******
Washe gari sadak'ar uku su Aunty ummu sulaim suka zo ita da mijin ta, suma by air
suke, don haka ana sallar azahar sukace zasu koma ,tare dasu sweety da uk , duk sun
shigo sunwa kowa sallama, na fito yi musu rakiya bakin gate nan na sami mijin ummu
sulaim da UK tsaye,muka k'arasa mijin sulaim ya k'ara min gaisuwa tare da min
sallama, yaya Haroon zai kaisu airport, duk sun shiga motar sai shi dake tsaye
jikin murfin motar hannun sa rik'e da little yana kallo na, matsowa kusa dani yai
sosai yana mik'o min ita,sannan a hankali yake min magana" ki k'ara hakuri akan
wanda nasan ki dashi,kiyi tayi musu addu'a Allah ya gafar ta musu, ki rage damuwa a
ranki kinji?".

Gyad'a kai nai idona na cikowa da k'walla,juyawa nai bayan na karb'i yarinyar
nan na d'aga musu hannu na wuce cikin cikin gida.

******
Tsawon kwanaki bakwai muna karb'ar gaisuwa, zuwa lokacin zuciyoyin mu duk sun
rage rad'ad'i, a cikin wannan kwanakin tun bayan tafiyar su UK kullum sai yayi min
waya safe da dare yana k'ara ban hak'uri da kwantar min da hankali, duk da ba wata
doguwar hira muke ba amma hakan yana min dad'i tunda ya nuna kulawar sa gare ni.

Washe garin bakwai d'in kuma muka d'auko hanyar gida dasu yaya da matan su.
Tunda muka fito a gidan kuka na ta dawo sabo shi kenan yanzu duk sanda nazo
sakkwato bazan k'ara ganin umma na ba😭.

A mota dai bamai rarrashi na don suma duk dakewa kawai suke,amma duk zuciyoyin
su babu dad'i.

La'asar likis muka shigo gari,kai tsaye ni suka fara saukewa sannan suka wuce
gida.

Tunda na shiga gidan duk ma'aikatan suka yo kaina suna min barka da zuwa tare da
d'aukar akwatin kayana.

A gajiye nake likis don haka a daddafe na zauna a parlour muka gaisa dasu sukai
min gaisuwa na tashi na hau sama na barwa su lami little, share d'akin nai na canja
zanin gado sannan na fad'a toilet nai wanka da ruwa me sanyi don tsananin zafin da
akeyi, lokacin har anyi sallar magriba don haka nai sallata tare da nafila na dad'e
zaune ina addu'a, sannan na shafa.
kaya me sauk'i nasa riga iya gwiwa mara hannu, sannan na d'an goga humra nai
parking gashi na nasa hijab na sauko k'asa ,samu nai har lami ta dafa min cous
cous da miyan jajjage,
Karb'ar little nai zuwa sama nai mata wanka itama,jin an fara kiran sallar
isha'i yasa na kwantar da ita na tada salla, bayan na idar na d'ora shafa'i da
wutiri.

Tana ta wasan ta da kafafuwan ta kasancewar tana ganin haske batai kuka ba,don
haka nake sallata cikin nutsuwa da kwanciyar hankali,ina wutiri naji an bud'e
k'ofar an shigo, kai tsaye ya wuce kan gadon tare da kwanciya ya saka little
jikinsa yana binta da kisses, surutu yake ta mata"mama na nai mussing naki over,
kullum na kwanta sai nai mafarkin ki da maman ki, ashe yau kuna hanya maman ki bata
fad'a min yau zaku dawo ba, kema kinyi missing d'ina ko sweetheart? "

Kamar tasan me yake sai kallon sa take tana wantsala hannu,yanda yake mata wasa
da kumatun ta yasa taketa wangale baki don ta fara dariya, shima darinyan yake
kamar me hira da wani Babba, cillata sama yake yana mata y'ar wak'a"mamana Ruhina
mamana sahibata maman Abban ta me kama da Abban ta".

Bayan na idar nai addu'o'i na na shafa,Mirmishi ya ya sub'uce min jin shirmen


wakar da yake, amma sai na basar na tashi ina cire dogon hijab d'in dake jikina
wanda har sharan k'asa yake yi, bayan na ajiyeshi na tsugunna ina nannad'e prayer
mat d'in tare da fad'in "Sannu da zuwa".

Tashi zaune yai yana bina da kallo don rigar dake jikina ta shan iska ta
bayyana sashin jikina, cikin kulawa yace " Khadeejah sannunku da hanya,ashe kuna
tafe yau ban sani ba ai da na shigo muku take away ".

Girgiza kai na nai ina fad'in" ba komai ai su lami sun dafamin abinci ma tun
yamma muka shigo ai".

"Ok sannu da hanya,ya k'arin hak'uri".

" Alhamdulillah".

"Allah yajik'an iyayen mu ya kyautata makwancin su".

Cikin sanyin murya na amsa da " Ameen ya Rabbi".

Wayar sace tai k'ara yana dubawa yaga Abban sane,ya d'aga da sallama daga can
Abban yace "Daddy muna gidan naku munzo k'ara yiwa Khadeejah gaisuwa ".

Da sauri ya mik'e yana fad'in" To Abba gamu saukowa yanzu".

Kallona yai yana mik'ewa yace "Abba yana k'asa yazo k'ara miki gaisuwa".

Yana fad'a yafita same da little a kafad'ar sa.

Zani na d'auko na d'ora kan rigar jikina sannan na saka hijab d'ina na fita.

A main parlour na iskesu shida Aunty murja ,cikin jin nauyin Abban na k'arasa na
zauna ina gaida shi" Abba barka da dare".

Cikin sakin fuska kamar ko yaushe ya amsa "yauwa Khadeejah ya hanya".

Amsawa nai kaina k'asa , sannan na gaida Aunty murja itama,nan suka k'ara min
gaisuwa, Abba yace " Ai ban San kun dawo ba sai a masallaci me gadin Ku ke shaida
min kin dawo gab da magriba, dana kira Daddy kuma yace shima bai shigo gidan ba bai
san kin dawo ba".

"Eh wlh muna shigowa ana salla ".

" To Khadeejah yanzu babu abunda yai saura tsakanin ki da mahaifan ki illa
addu'a, itace kad'ai yanzu zaki rink'a musu don muna k'aunar ki gare su kinji ko ".

Gyad'a kai nake tayi,yaci gaba damin nasiha tare dayin addu'a ga iyaye na,naji
dad'in hakan nan naita masa godiya, ya mik'e da Ruky a jikin sa yana kallon UK yace
" Daddy kaga uwar gidana taji ruwan sakkwato tai bul bul da ita,gashi sai naga ta
k'ara wayo masha Allah ".

Dariya UK da Aunty murja sukai nikam sai mirmishi nai kaina a k'asa, Aunty murja
tace " ai daman yarinyar nan da wayon ta tazo tar take ido a tsakar ka".

Dariya su Abba sukasa yace "A'a murjah yada kishi haka,nafa lura kishi kike da
little Ruk'ayya".

Nan sukaita barkwancin su nikam kaina na k'asa inata mirmishi, ya mik'awa UK ita
sukai mana sallama,mukai musu rakiya bakin gate.

A tare muka juyo ina gaba yana bin bayana har cikin parlourn, hanyar dining
nayi sab'anin shi da yai sama.

*Taku ce*
*Y'ar mutan ja'oji*
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

0⃣5⃣4⃣
0⃣5⃣4⃣ 0⃣5⃣4⃣

Sama sama naci abinci na tashi tare da kashe kayan wuta na wuce saman, d'akina na
shige kai tsaye na k'ara watsa ruwa sannan nai brush na fito,kayan bacci nasa wanda
rigar duka iya cinyata ne,kuma net ce bansa bra ba sai pant danai amfani dashi
kalan rigar na goga humra a duk sassan jikina, glop d'in na kashe tare da hayewa
gado bakina d'auke da addu'a, bacci ya fara d'auka ta na lumshe ido ina k'ara
karanto adduoi cikin baki na, don nasan little sai ta farka zai kawo min ita.

A can d'aki UK yai shirin bacci tsaf ya feshe jikin sa da turare, zama yai bakin
gado yana dafe kansa,a ransa yake tunanin wai kaida matar ka a cikin gida d'aya
amma kana cikin buk'atar kasancewa da ita ba dama, yanzu yanda yake jin wani
feelings na taso mai babu abunda yake buk'ata irin yajishi cikin jikin ta,gaskiya
ya tabbata yayi kuskure a rayuwar sa, ya tafka shi da yawa,duk yanda matar sa kemai
biyayya da k'aunar shi amma saida yai mata lefin daya k'ure tunanin ta har ya
haifar mata tsanar sa da tsanar zama kusa dashi,don yanda yake ganin idanuwan ta a
duk sa'in daya rab'eta babu sauran nuna armashi ko d'oki tare da ita.
Yanzu yasan yana zuwar mata da buk'atar shi plan d'in sa ya rushe so yake su
gama dai daitawa su dawo normal yanda zasuyi komai cikin shaukin juna bawai yai
kid'an sa yai rawar saba.

Juyawa yai ga little daya ji tanata motsi kwanciya yai kusa da ita yana shafa
kanta zuwa bayan ta, baccin ta koma ya d'ora ta a k'irjin sa yana shafa kanta a
zuciyar sa yake jin wani tsananin so da k'aunar yarinyar na ratsa zuciya sa,ji
yake kullum in gari ya waye da k'arin k'aunar ta yake tashi, ya dad'e yana tunani
har bacci yai gaba dashi,wanda baifi y'an mintina da fara baccin ba ta fara
wantsala k'afa tana mutsu mutsun kuka.
Tashi yai tare da ita a jikin sa ya nufo d'aki na.

Cikin bacci naji an lalubo min Boob's d'ina ,motsawa nai kad'an ina gyara
kwanciya zuwa can naji an fara tsotsa, bud'e idona nai cikin mayan bacci naji
motsin ta jikina tanata cilla k'afa alamar kuka don bataji dad'in kwanciyar ba
da tanda kan boobs d'in bai shiga bakin taba sosai.
K'ok'arin tashi na farayi na ganshi zaune kan gadon ya zuba min ido, hannu
nakai na kunna haske,muna had'a ido ya kauda kai gefe cikin basarwa yace " inata
tashin ki ki bata nono baccin yai miki nauyi ki gyarata sosai yunwa take ji".

Sata nai a jikina ina k'ara kwanciya ban k'ara tanka mishi ba, kusan minti biyu
ya mik'e tare da kashe mana hasken ya fita.

Ajiyar zuciya na sauke ina wani tunani a raina,don yanda naga yanayin sa nasan
Tabbas cikin buk'ata yake,amma ya gagara bayyana min,shin bana cikin fishin
ubangiji kuwa, ina zaune da raina da lafiyata mijina na cikin shawa'a amma na kasa
biya mai buk'atar sa, koda yake ai baice min yana nemana na hanashi kaina ba,da
ilimi na babu yanda za'a yi in hora mijina ta wannan hanyar, ko yanzu ya dawo zan
bashi kaina,amma muddun bai nema ba bazan kai kaina gare shiba, dukda kuwa nima ina
jin feelings tare dani.

********
Kwanan mu uku da dawowa da dare ina zaune a parlourn mu na sama ,yau kwalliya
nakeji don haka na shirya cikin wasu y'an iskan riga da mini siket red color wanda
suka kamani matuk'a,ga rigan me wuyan V ce kuma ta kama jikina kasancewar roba
ce, k'irjina da yanzu suka k'ara cika taf duk da daman ni ne cikar k'irji ce , to
ya had'u da shayarwa,sun ciki sosai har sun burtso ta tsakitan yankan wuyan
rigan, kaina na gyara nai park d'in sa cikin wani babban ribbon shima red, nasa
barima red a kunne na, plate shou na sanya k'afata.
Little ma na shirya ta cikin y'ar riga pink calor na goga mata powder a duk
jikin ta kasancewar lokacin zafi ne, na kwantar da ita kan kujera tanata wasa da
hannun ta,ni kam kallo nake a tashan Arewa 24 ina kallon wani shiri daya ja
hankali na.

A hankali naji hucin numfashi a gefen wuyana,da sauri na juyo muka had'a ido har
hancin mu na had'uwa, kauda kaina nai da sauri ina fad'in "sannu da zuwa".

Bai amsa ba illa k'ara matso da fuskar sa da yai jikin tawa sosai numfashin mu
ke sauka a tare, na lumshe idona ina k'asa da kaina,hannun sa yasa ya d'ago da
fuskata yana son saka idon sa cikin nawa amma nak'i bashi dama.

A hankali cikin kunne na yace " kin samin yarinya a kan kujera kuma kin juya mata
baya sai ta zamo ta fad'i ko".

Juyawa nai na kalleta naga ma bacci ya d'auke ta, d'an mirmishi nai nace
"k'ara ta koyi kwanciya akai ai".

" a a nidai ki daina sata kuma ki juya mata baya".

Lumshe ido nai tare da k'asa sosai da murya ta nace "Insha Allah an daina daga
yau ".

Shafo fuskata yai yana mirmishi yace " good girl,kiyi min wannan kyakykyawan
mirmishin da ake min rowan sa yanzu".

Ban San sanda mirmishin ya sub'ice min akan fuskata ba d'an kauda kaina gefe
nai cike da kunya,gashi ya tokare ni yamin rumfa aka ya hanani sakat, ganin da
yai ina k'ok'arin mik'ewa yasa ya d'an matsa baya kad'an, ina mik'ewa ya jawoni
jikin sa cike yana gogo min gemun sa a wuyana abu na farko daya san yana motsoni,a
hankali yake furta" kinyi kyau matuk'a my Angle I'm missing u my beauty, kin
gijemin tsawon lokaci, ina cike matuk'a da buk'atar ki amma ke ko ajikin ki ko?".

Idona a lumshe nace "muje kaci abunci".


" um um ni banjin yunwar abinci yunwar ki nakeji kinji don Allah ki bani kanki
don Allah ".

Again idona yana lumshe nasa bakina cikin kunnen sa daya rank'wafo wuyana yanata
kissing " um naji dukda haka dai kaci abinci ka huta tukun ".

" bai ce komai ba yaci gaba da shafani yanata sinsina k'amshina tsawon minti
hud'u ,murya a sark'e yace " My wife ina cikin yunwar ki matuk'a, amma muje inci
abincin ".

A slow ya cikani ya juya ya d'auki little ina bin bayansa muka sauka k'asa.

Saida na gama shirya mai abincin sannan na mik'a hannu zan amsheta,mak'e
kafad'a yai yana wani kashe ido yace " barta taji d'umin kijina, baccin nata ma yai
nisa".

D'an mirmishi nai duk jikina a mace sabida ya saukar min da kasala kawai basarwa
nai, na d'an rausayar da kai gefe ina fad'in " Bazakaji dad'in cin abincin bafa a
haka ,kuma itama bazata sake tai baccin ba don naga har yanzu baka gama iya rik'e
taba".
Na k'arashe cikin tsokana.
D'an zaro ido yai cikin mamaki yace "nine ban iya d'aukan taba,lalle yarinya
wuyanki yai k'wari to koke ai shaida ce yanda na iya rik'e mutum a hannu na, kuma
tun ina d'an yaro nake rainon sweety na iya goyata ma balle d'auka".

D'an dariya nai cike da jan hankali nace " ka gane zuwa zan in mata Shirin bacci
ne".

"Ok ungota".

Inasa hannu zan amsheta ya rik'e hannun nawa yanamin wata magana cikin sigar
rikita me sauraran ta" in kin shirya ta kema ki shirya tara ta gani nan zuwa
gareki kinji ".

Yanda na rank'wafo yasa Boob's d'ina fitowa sosai ta tagan rigar,shafosu yai
yana k'ara min magana k'asa k'asa.

Nikam ganin inasa hannu ya hanani d'aukan ta ya rik'e hannu yasa nai magana
cikin muryar shagwab'a " To ka kawo ta,kuma ma fa ni banida tsarki ina up".

Wata zabura yai yana mik'ewa tsaye yasa little akafad'an sa da hannu d'aya
kuma ya rik'oni jikin sa,ban aune ba kawai naji hannun sa cikin siket d'ina har
cikin pant nawa,zaro ido nai ina k'ok'arin yin baya nace "ya haka ".
Miryanshi a dishashe yace " zan duba ne in gani don in tabbatar ".

Turo baki nai nace " nifa wasa nakeyi,don Allah kaci abincin yana yin sanyi
fa".

Janye little d'in nai a kafad'ar sa na juya zuwa stair's, sai da na taka step
uku sannan na juya don jikina ya bani yana kallo na ai kuwa idona karaf cikin
nashi yana tsaye ya hard'e hannaye ya k'irji ya zuba min ido, gwalo nai na haye
saman ya d'an girgiza kai yana mirmishi tare da cije lips d'in sa,komawa yai kan
kujerar ya zauna yana jin wani nishad'i na ratsashi yau ya shirya sosai da sahibar
sa dukda bai kai ga gaci ba amma yau kam akwai alamun nasara sosai da ganin
mirmishin dake sauka kan fuskar ta.
Da azama ya fara cin abincin duk ya zak'u.😜

Ni kuwa ina shiga d'aki na cirewa little kayan jikin ya na samata na


bacci,sannan nima na shige toilet nai brush sabida ban dad'e dayin wanka ba, fitowa
nai nasa night gown na feshe jikina da turare na goga ko ina, har bayan kunne na
zuwa wayana dasu tsakanin boobs d'ina, amma ban shafa a jikin suba sabida nasan duk
jikin su babu inda UK baya tsotsa🙈,gashi nima tun daga salon farko daya min duk
jikina ya amshi sak'onnin shi.

Bayan na gama na k'ara saka air freshener a d'akin ya d'au kamshi kashe hasken
dakin nai na haye gado ina tofa addu'a adukkan sassan jikina da jikin little
sannan na tattofe gabas da yamma na jawota jikina ina sakin wani miskilin
mirmishin nai don nasan yana jin shiru zai biyo ni .

Shi kuwa UK yana gama cin abincin ya mik'e cike da d'oki ya wuce d'akin sa
wanka yai a gaggauce ya fito ya zauna gaban mudubi yana gyara jikinsa kamar wani
mace ya goggoga turaruka a duk jikinsa sannan ya d'auko d'an boxer yasa zama yai
bakin gado yana tunanin shigowar ta,har zuwa yai bakin gadon daya sawa little a
d'akin sabida inya d'auko ta wani lokacin in tai bacci ciki yake zurata.
K'ara gyara mata gadon yai yana fad'a a ransa "my daughter yau a cikin gadon ki
zaki kwana Abban ki zai more yau".
Sai kuma ya saki mirmishi, yana kallon agogo k'ara minti goma yai tabbas in
bata shigo ba binta zaiyi.

Ina kwance tunani kala kala a raina naji an turo k'ofan an shigo tare da
mayarwa a rufe,k'ara lumshe idona nai irin na masu baccin nan, kusan minti guda
yana tsaye yasa hannu ya kunna glop tare da takowa a hankali zuwa bakin gadon ya
zuba mana ido na d'an seconds sannan a hankali yasa hannu ya zare ta a jikina yana
rungume ta a k'irjin sa tare da kissing d'in duk jikinta ya k'arasa zuwa bakin
gadon ta yana jawoshi jikin gadon mu ,sanyata yai a ciki yana tofa mata addu'a,
zuwa yai kashe glop d'in ya hayo gadon a hankali yasa hannunshi ya kunna lamp ya
jawoni jikin sa yana sauke wata ajiyar zuciya,duk bidirin da yake idona na rufe ni
ban yarda ba me bacci, a hankali naji yana shafa gashi na dana sake shi ban samai
ribbon ba, sanya bakin sa yai cikin kunne na yanamin rad'a " my heartbeat nasan
fa idon ki biyu kina jina kawai jamin aji akeyi,nidai kaina bisa wuyana a karb'i
tubana".

Inajin sa amma banko motsa ba,shima shiru yana yawo da hannun sa a sassn jiki na,
inda kullum hangen sa yake yakai hannu yana shafosu cikin wani irin salo tare da
d'an matsasu,ban San sanda na runtse ido ba ina d'an bank'arewa, a hankali ya zare
rigan dake jiki na,had'uwar k'irjin mu waje guda ya haifar mana da balaeen shock a
tare muka sauke ajiyan zuciya,ya k'ara matseni a jikin sa, nima na kwantar da kaina
akan fuskar sa hancin mu na gogar na juna,harshen sa yasa yana lasan lips
d'ina,bud'e bakina nai nima ina jawo harshen sa da nawa muka shiga tsotsan bakin
juna,hannayen sa biyu yasa yana wani irin wasa da k'irjina tare da kada kansu,
Tabbas har cikin kwanyata nake karb'ar sakonnin sa,wani numfashi na sauke a
galabaice ina k'ara sarrafa harshena cikin bakin sa, duk mun gigice mun gigita
kanmu,mun lula can wata nahiya, wato mijina yai masifar sanin lagona don in har zai
gogamin gemun sa a fuskata zuwa wuyana yai wasa da k'irjina to nikam ya gama kunna
min wuta,ban aune ba naji kan abuna cikin bakin sa yana wani irin tsotsan su, tare
da lailaya d'ayan da wata siririyar k'ara na saki ina zare mai boxers d'in dake
jikin sa,cikin wani irin gigitaccan shauk'i ya juyani k'asan sa muka can duniyar
sama.

Tsawon watannin da muka d'auka bamu had'u da juna ba muke k'ok'arin fanshewa a
wannan daran,don damunyi Rleax muke k'ara tsokano juna da sabbin wasanni, mun raba
dare har muna k'ok'arin cinye daran wajan rayashi da aikin kashe arna🙊.

Bayan mun tabbatar wa kanmu mun gamsu ,ya jawoni jikinsa yana shafa bayana ni
kuwa na wani saki jiki inata mai shagwab'a da k'orafin ya hanani bacci,wata
shu'umar dariya ya saki cikin kunne na yana fad'in, " um um Baby kece fa kika
hanamu rintsawa ni tun a second round naso hak'ura amma kika rik'e min abuna tsam
a jikin ki, ina janyewa kina k'ara matseni,ai dajin kukan dad'in da kike nasan kin
fini ma buk'atuwa kawai halin mata ne yasa ake wani basarwa amma aini yau naga
k'wa. . .
Kafin ya k'arasa nai saurin toshe bakin sa da tafin hannuna ina bubbuga mai
k'afafuwa na dake sak'ale cikin nashi tare da kukan shagwab'a "um um Allah Allah
nidai bana so ni ka bari, Allah kaine ka hanani sakat ".

Hannunn nawa ya zare daga bakin sa yana dariya sosai,bugun sa na shigayi a


k'irji tare da tuttureshi daga jikina, amma ya rik'e k'am yana dariya tare da
mak'ale kafafuna da nake bubbuga masa a nasa, ganin yanda yake dariya gashi yak'i
bari na in bar jikin sa yasa na sakin kukan sakal ci harda wangale baki kamar
k'aramar yarinya, saurin rufemin bakin yai yana d'an zaro ido yace" Rufamin asiri
don Allah, tsakiyar dare ne fa,kar jama'a su juyoki, yi hak'uri ni duk wasa nake
miki kawai tsokana ne,amma nasan ke bikiyi kewana ba ko kad'an tunda dai ni me lefi
ne gareki, nine kawai nai missing d'inki kuma na cika da sha'awarki har yasa naketa
rounds ban gaji ba,amma ke kam kawai taimakona kike badan ma na tab'o shocking
point d'in kiba nasan da bakida lokaci na".

Ya k'arshe yana had'iye dariyar datake cinsa, ina k'ok'arin magana little ta
fara k'ishin k'ishin d'in kuka,da sauri ya lalubo boxers d'in sa yasa ya d'auko
ta, yana mik'o min,mak'ale kafad'a nai na tashi na lalubo zanin da nake salla a
gefan drawer na d'aura na wuce toilet, saida nai tsarki na d'aura Alwala don
bazan shayar da ita da najasa a jikina ba,gudun sharrin shed'anu, sannan na fito na
karb'eta tanata cilla kuka,haske na kunna na bata ruwa kafin nono don da ruwa nake
fara rarrashin ta in tana kuka sabida zuciyan ta tai sanyi kafin in shayar da ita

d'an kallon sa nai ta gefen ido bayan na zauna kan kujerar dake gefan gadon
nace " d'an janye mana wannan bedsheet d'in kabar plen d'in ".
Cikin tsokana yace " sabida me za'a canja shi yanzu".

Cikin dakewa nace "sabida ka b'atashi ".

Mik'ewa yai yana mirmishi ya janye shi yana fad'in" mun b'atashi dai a tare ".

Ban tanka mai ba nidai na kwanta ina bawa little nono ,shi kuma ya shige
toilet da wancan bedsheet d'in a hannun sa.

Lumshe ido nai ina tunanin tsananin jarumtar dana nuna yau d'in nan,dukda nima
nasan na azabtu da rashin mijina tsawon lokaci, gashi bayan na gama jinin haihuwa
nai amfani da kayan gyara sosai,kuma daman ran suna inajin wasu y'an class d'in mu
matan aure suna hiran wai in mace tai haihuwan fari karan ta na farko da miji
yafi komai dad'i, don ita kanta mace a sannan ne take gane cikakkan d'and'anon
mijin ta, cike da gamsuwa da zancen nan nasu na lumshe ido,tabbas koba haka bane
nikam haka yake gareni, don zan iya cewa duk rayuwar da mukai a India muka gurje
juna ban tab'a gamsuwa irin na yau ba,duk da naji a jikina amma dad'in ya lullub'e
wahalar🙈.

Fitowa yai d'aure da towel jikin sa na d'igar ruwa alaman wanka yayi, ya zauna
bakin gadon yana goga min ruwa a kafafu na,janye su nai cikin muryar baccin daya
fara fizgata nace " ban so ka bari fa".
Hayowa gadon yai yana fad'in "karki bacci ki tashi kiyi wanka,kece fa a India
kike cemin ba'a son mutum yai bacci da janaba a jikin sa".

D'an bud'e idona nai ina fad'in" ai nayi tsarki kuma na d'aura alwala, na sami
kariya daga shaid'an, abunda ba'a so mutum ya kwanta bai baiko yi tsarki ba".

"Hhhmmmm kedai kawai kice bacci ya kamaki bazaki iya tashi ba, kuma mafa uku
tayi kina fara baccin asuba zatayi".

juya mai baya nai nace" um zan sami kona awa guda ne".

Shima ya matso muka kwanta.

******
Washe gari cike da nishad'i mu duka muka tashi, sai wani shishshige min yake ya
hanani sakat ko motsi nai yana bayana, a wajan break ma sani yai a cinya yana bani
a baki, Allah sarki little ko tasan Abban ta na angwancewa yau sai baccin ta
takeyi, ba rigima, wajan sha d'aya bayan mun gama break ya d'auke ni tsam muka haye
sama, d'akin sa ya wuce dani ya shiga jagwalgwala ni,wannan karon kam nok'ewa nai
ina d'an tuttureshi ya danneni a gadon yana cafke bakina ,sosai muke tsotse bakin
juna,can ya sararamin na sauke ajiyan zuciya da cewa "ka d'aga ni inje wajan
yarinya ta karta farka tai kuka".

Kashe min ido d'aya yai yana magana can k'asan bakin sa" wannan yarinyar kin
b'aci da rashin kunya y'ar fari amma bakya kauda ido akanta".

D'an turo baki nai nace "k'ara ni agaban mutane bana nunawa wani fa".

Hannu na dake cikin nasa ya matse yana fad'in" waye wanin to dawa kike?".

Dariya nai na mik'e tsaye ina zare hannu na cikin nasa,saida naje bakin
k'ofa nace "kai ne me nunawa gaban mutane baka kunyar y'ar fari".
Nai mai gwalo na fice da gudu.

Dariya kawai yai yana girgiza kai ya maida bayan sa ya kwantar akan gadon.

Gaba d'aya weekend d'in nan cike da soyayya muka yi shi, soyayya ma kuwa me
tsayawa cikin rai, haka yau Monday daya tafi office bini bini ya kirani awaya yana
tambayata ya nake ya yarinyar sa yanzu ma ina idar da sallar azahar ya kirani yana
tambaya ta ya muke.
Nikam mirmishi nai nace " gamu duka cikin kewan ka ga little ma tanata rigima
".
"Sorry dear anayin sallar la'asar zan taho gida kinji ki shafa min ita ki
mata kiss matsayin nawa in na dawo zan maida miki ".

Cikin salon jan hankali nai yar dariya ,nace " ok ba damuwa muna jiran ka,Allah ya
dawo mana dakai lfy,ya kiyaye ka".

Cikin jin dad'in addu'ar ya amsa da "Ameen ameen ".

*****
Da dare yace mu shirya muje shopping, ai kuwa ba k'aramar siyayya yai mana
ba,musamman little yai mata siyayyan kayan wasa sosai harda kayan wasan ma da sai
takai shekara uku bata fara wasa dashi ba, keke mota mashin na yara komai
rankacaf,muka ciko mota dasu.
Da mukazo gida d'akin k'asa da duk sauran kayan wasanta yake ciki,muka zuba ya
zauna ya k'ara gyara mata d'akin ni kuwa,sama na haye na barshi don yin shirin
bacci.

*****
Sosai muka k'ara shiryawa da mijina duk wata damuwa dake tsakanin mu ta kau,mun
k'ara d'inke kanmu.

*Taku ce*
*Y'ar mutan ja'oji*🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

~Fan's ayi hak'uri da jinkirin da *Y'AN ARABIC YAI INSHA ALLAH YA DAWO BA WASA HAR
IZUWA K'ARSHENSA*~🙋

_*Wannan page na sadaukar dashi ga dukkan y'an uwa Marubuta,musamman y'an


k'ungiyata ta* *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*_

_*Tare da dukkan Marubuta na groups d'in*_


_*MARUBUTA*_
*_TASKAR MARUBUTA_*
*LAYUZA KABIR NOVELS GROUP*
*UMMUN YUSRAH FANS*
*ZAMANI WRITERS FANS*
*YAK'I DA RASHIN GASKIYA GROUP*
*Y'AR MUTAN ARKILLA NOVEL*
*AUNTY MAIMUNA O'G NOVELLAS*
*TASKAR LITTATFAN HAUSA NA BILLYN ABDUL*
*Y'AR MUTAN J'AOJI NOVEL GROUP*
_*Marubutan dake cikin dukkan way'an nan groups d'in dana lissafo ina gaisheku
kyauta, yawanku yayi yawa dana lissafoku d'aya da d'aya😅Har abada ana kyawun tare🤝
Allah ya tsareku ya kareku da dukkan sharrin masharranta,Allah ya k'ara bud'e
k'wak'walanku ya k'ara muku hazaka da basira*_

0⃣5⃣5⃣
0⃣5⃣5⃣ 0⃣5⃣5⃣

___________________________Rayuwa me cike da walwala muke gudanarwa, cikin


satittikan da suka biyo baya, hankulan mu sun kwanta,fahimtar juna ta k'ara shiga
tsakanin mu,musamman yanda UK ke nuna matuk'ar kulawa ga little sai nutsuwa ta
k'ara kamani na tabbatar yayi nadamar abunda yai akan cikinta.

*******
Yau kam tun safe da muka tashi jikin little ba dad'i, zazzabi take sosai don na
bata magani amma yak'i sauka,don haka yana office na kirashi a waya ina shaida masa
yanayin jikin nata,cikin tashin hankali yace" maza ki shirya gani nan zuwa mu kaita
asibiti".

Daga haka ya katse wayar da sauri ya mik'e yana had'a takardun gaban
sa,masinjansa ya kira ya mai bayanin zai je gida daughter d'insa ba lfy.
Ya mai fatan samun lafiya yana rufo k'ofan office d'in.

**********
Cikin hanzari na canja kayan jikina tare dasa Hijab, parlour na fito na d'auki
waya ta,k'ok'arin kiran sweety na fara yi a waya don in shaida mata, ringing d'in
farko ta d'aga tana fad'in "Aunty nah yanzu nake k'ok'arin zagayowa ai".

Cikin sanyi muryata data karye nace " Kinga zazzabin little yayi zafi wlh yanzu
zamu kai ta asibiti ma".

"Subhanallah, bari inzo muje tare".

Sweety ta fad'a a rikice.

Ina zaune na zuba tagumi idona a kan yarinyar da numfashin ta ke fita a wahalce
saboda tsananin zazzabin dake jikin ta, addu'o'i ne d'auke a bakina ina rok'on
ubangiji ta bata lafiya.

Aunty murja da sweety sukai sallama tare da shigowa, cikin raunin murya na amsa
musu.

Hannu Aunty tasa ta amshe ta tare da tab'a wuyan ta,da sauri ta kalleni jin
tsananin zafin dake jikin yarinyar tace " Khadeejah garin ya ya kika zauna da ita
haka? ai zafin jikin yai yawa,ba'a son a bar yaro da zazzabi tsawon awanni".

Ji nai wani hawaye ya gangaro min nasa hannu ina sharewa nace "Ai ganin na bata
magani ne yasa nake tunanin zai sauka a d'an lokaci kad'an,amma kinga sai k'ara
hawanta ma yake yi".

Zatai magana UK ya turo k'ofar parlourn da sauri ya shigo, k'arasowa yai yana
cewa " Ai kawai taso mu wuce asibitin don ban ma rufe motar ba".

Tare da sweety muka tafi Aunty ta koma gida tana mana fatan samun sauk'i.

Sai da muka hau titi sosai sannan ya sa hannunsa a jikinta, girgiza kai yai
tare da cewa " Gaskiya ya kamata da yawa zazzab'in nan, kinyi sakaci wlh,zazzabi
jikin yarinya tun k'arfe takwas har k'arfe d'aya bai sauka ba,amma ki kasa kirana
ki fad'a min ".

Nidai ban ce komai ba inata matsar ido,don zuciyata ta gama karyewa,duk dakiyar
da nake ta k'are".

**********
Cikin hanzari likitan da muka samu ya fara dubata, tsawon minti ashirin ya bamu
gado don yace zazzabin yai zafi in akai sake sai ta fara jijjjiga, nan da nan ya
bani umarnin in cire mata duk kayan jikin ta na barta da pampas kawai, umarnin sa
nabi duk da ina tunanin sanyin dake ciki d'akin.

Wata Norse ce tazo ta d'an bowl da ruwa a ciki da farin towel ta goge mata
jikin,cikin ikon Allah kuwa sai zafin ya d'an ragu,allura akai mata sannan aka jona
mata drip don likitan ta tabbatar mana tana buk'atar ruwa a jikinta.

*******
Zuwa dare sai gashi numfashin ya dawo ya dai daita, kuma zazzabin ya sauka sai
kad'an,su Aunty Hafsa da Aunty Amrah sunzo tun yamma sai bayan magriba suka
tafi,Aunty murja da Abbah ma sunzo sun dad'e bayan sallar isha'i suka tafi.

Tare da sweety muka kwana,duk yanda UK ya rikice yace asibitin zai kwana shima,
Abbah hanashi yai,yace "inka zauna lafiya zaka bata? kaje gida kai ta mata addu'ar
samun lafiya shine mafita".

A haka muka samu ya tafi bayan ya kawo mana duk abunda zamu buk'ata".

*********
Kwanan mu biyu a asibitin tana samun kulawa matuk'a, a kwana na uku kuma sai
ta fara jijjiga tana suma,abunda ya matuk'ar k'ara d'aga gankulan mu, UK da sweety
kuka kariris, nikam zuciyata ta k'ek'ashe sai k'unar zuci don ma inata yawon
ambaton Allah ne nake jin sauk'i sauk'i.

Babban likitan yara dake asibitin ne yazo da kansa ya duba ta,ganin yanda take
jijjiga yasa aka canja mana d'aki, don k'ara samun kulawa ta musamman, tsawon yini
da daran nan a tsaye mukayi shi, a ranar har Aunty murjah bata tafi gida ba,tare
damu ta kwana, k'arfe shida na safe ran little yabar jikin ta.

Ina zaune kan prayer mat ina lazimi da kaiwa Allah kuka na kan ya bata lfy, naji
sweety ta saki wata k'ara tana rik'e Norse d'in da take sanar mata ta rasu,don shi
likitan tunda yaga numfashin na ta ya fita gaba d'aya ya juya ya fita bai ce
komai ba.
Runtse idanuwa na nai ina jin zuciyata tana wani mugun buguwa da tsananin
k'arfi,cikin sark'ewar murya nace "Innalillahi wa'inna ilaihi ra'jiun,Allah kasa
cikin mafarki nake,Allah karka tabbatar min da abunda kunnawana suke . . . . . ."
ban k'arasa ba naji UK da Aunty da suke reception sunje karb'o sun shigo da gudu
suna salati.

Jikin gadon Aunty ta k'arasa tana d'ago gawar little Wanda ta tabbatar da ta
rasu, salati kawai take da fad'in "Allahu Akhabar,Allah kasata cikin yaran cikin
aljanna, kasa me taryar muce".

Wannan lafazi na Aunty ya tabbatar min da babu little ta tafi kenan.

Siririn kuka na saki bakina d'auke da " innalillahi wa'inna ilaihi ra'jiun".

UK kuwa tamkar k'aramin yaro haka ya tsugunna yana rusar kuka da gunji.

Sweety ce tai k'arfin halin tsaida kukan ta ta kira Abbah ta sanar mai,sannan ta
kira Yaya Haroon shima ta sanar mai.

Kafin k'arfe bakwai suka bamu gawar tun zuwan Abba muka wuce gida,dukkan mu babu
wanda ke cikin nutsuwar sa.

******
A gida muka tarar da su yaya Haroon duk sun zo, zuwa lokacin kuwa sabida ambaton
Allah da nake tayi zuciyata ta rage rud'un da take ciki.

Cikin tausayawa yaya ya ruk'o Hannuna yana fad'in "Sannu Nahna kiyi hak'uri
kinji, Allah daya baki Rukayya kuma ya amshi abarsa ya fiki son ta,shi zai k'ara
miki wasu ".

D'aga mai kai nai kawai na wuce na zauna kan kujera don idona dishi dishi yake
min.

Cikin d'an lokaci Aunty murja tai mata wanka,Yaya Usman ya shirya ta cikin
likkafanin ta, Auntyn ummu sulaim ce ta mik'omin ita lokacin da aka gama shirya
ta aka nannad'e ta cikin bargo,tace " Yi mata addu'a ".

Girgiza kai nai ina share hawayen daketa zubomin na kasa magana, ganin haka yasa
Abbah dake tsaye yasa hannu ya karb'eta su yaya suka rufa mai baya suka fita.

Kowa matsar ido yake inka d'auke sweety dake rizgar kuka iya k'arfin ta.

Nikam mik'ewa nai na dafe bango tare da yaye labulen ina kallo sahu biyu da suke
sallatar gawar, idona nakan UK dake sahun gaba yanafa kuka idon sa rufe.

Lokacin dana ga Abba ya rungume gawar a k'irjin sa sun nufi mota,na saki wani
rikitaccen kuka da fad'in " wayyo little d'ina!!!! Wayyo Allah na ka bani hak'urin
rashin ta"

Babu wanda ya dakatar dani daga kukan da nake don duk zuciyoyin su cike suke da
tausayi na".
********
Har azahar UK na kuka riris, tun kowa bai rarrashin sa har suka shiga bashi hak'uri
damai nasiha, suna nuna mai Allah daya bashi kuma ya karb'e ya fishi buk'atar ta.
Da haka dai ya samu yai shiru,amma zuciyar sa cike take taf da k'unci.

*******
Sai bayan sallar isha'i ya sami gani na,ina zaune cikin d'aki nai salla ya shigo,
idonsa k'yar a kaina,ni kuwa kallo d'aya nai mai nai k'asa da kaina don wasu hawaye
da suka taho min.

Tsawon mintina biyu yana tsaye idonsa a kan gadon ta dake gefen namu,duk yanda
ya so jurewa kasawa yai, hawayen da yake rik'e wa ne suka shiga zarya kan
fuskarsa, tun yana yi a zuci har ya fito fili,ya tako a sannu ya dafa kafad'ata,ban
yi k'ok'arin d'ago kaina ba don nima kukan nake ban son ya gano halin da nake ciki
ya k'ara karaya.

Cikin sark'ewar muryar shi data gaji da kuka ya ke fad'in " Nahna kin ga yanda
rayuwa ta mana ko,sai da muka shak'u da yarinyarmu tai wayo ta saba damu sannan
mutuwa ta raba mu da ita, yau duka watan Little uku da sati uku Allah ya karb'e ta
ba . . . . ".

Da sauri na toshe mai baki jin zai yi sab'o,girgiza kai ba shiga yi ina rik'e
kuka na nace" kayi shiru kar kai sab'o,mu zama masu tawakkali sannan mun sani komai
dad'ewa daman Allah zai karb'e ta koda kuwa zata shekara dubu ne a duniya, kullu
nafseen za'ik'atul maut, dukkan me rai zai d'an d'ani mutuwa,tabbas Allah ne ya
bamu ita kuma ya fimu son ta,muyi hak'uri dukkan mu muna hanyar mutuwa m. . . . ."
Kuka yaci k'arfina don haka na datse maganar da ina tsoshe bakina.

Hannuna yake ta murzawa alamar rarrashi shima yana had'iye kukan sa.

A haka Ummu sulaim ta shigo d'akin ta same mu,nasiha ta k'ara mana sannan ta kama
hannun UK tana fad'in " Broth kaje waje mak'ota sun zo maka gaisuwa".

Sai da taga ya fita sannan ta juyo gareni tace"ki dawo parlour kibar zaman
kad'aici shike sa kike yawon kuka".

Ba musu na tashi na biyo bayan ta zuwa Parlourn.

*******
Wajan k'arfe tara su Aunty Amrah sukai mana sallama zasu tafi,amma yaya haroon
yace Aunty Hafsah ta zauna wajena don ta d'an ragemin kewa,zuwa kwana uku kar
abarni ni kad'ai.

Tare muka kwana da Aunty Hafsah da sweety a d'akina,ina kallo suna ta bacci amma
nikam ko kyas na gagara yi,don zazzab'i ne yamin ruf sabida Nonuwa na da suka cika
taf suke min tsiko, na sha paracetamol ma amma dake sun kumbura sun cicciko sosai
sai azabar ciwo suke min,ga kewar little da ta addabeni da nayi juyi sai inga kamar
tana gefe na,kunnuwa na har jiyo min sautin kukan ta suke, a haka ina wannan halin
har aka kira asuba,da k'yar na dafa naje toilet na d'auro alwala sallar ma a
daddafe nayi ta don yanda jikina ke rawar d'arin zazzab'i.

Auntyn hafsa ce ta farka itama taje tai alwalar sannan ta fito ta tashi
sweety, ganina kwance kan abun sallar ya tabbatar mata nayi tawa tuni tai zaton ma
bacci na koma don haka ta shimfid'a wata sallayar ta tada salla.
Duk yanda naso daurewa abun ya gagara don haka na sanar wa sweety ta kira family
doctor d'in su ya rubutomin maganin da zai rage min zugin, ba b'ata lokaci ta
kirashi kuwa Yace zai kira UK yazo ya amsa a asibitin.

A rikice ya shigo d'akin yana fad'in "meya faru yanzu doctor ya kirani in zo in
amsa miki magani".

Ban iya bashi amsa ba,sai Aunty Hafsah ce tace mai " Ciwon nono ne kasan dama
dole zai yi ciwo,amma insha Allah tana samun magani zai dai na".

Cikin tausayawa ya k'araso bakin gadon yana fad'in " muje asibitin tare kawai ya
duba ki sosai zaifi".

Ba musu na mik'e da taimakon sweety naje toilet na kintsa,sannan muka wuce


asibitin.

********
Allura doctor d'in yamin tare da bani magunguna,muka dawo gida.duk yanda nake
daurewa sai da ya kaini ga kwanciya ruf har ranar da akai sadakar uku ne naji dama
dama,amma daka ganni zaka tabbatar da ina jin jiki, jiki ba dad'i zuciya ba dad'i.

********
Duk wata walwala ta kau daga cikin rayuwar mu musamman UK ya hana kansa sukuni
kullum cikin zancan little yake da kewar rashin ta,kayan ta yake sawa a gaba yai ta
kuka,hakan yasa na tattara duk wani abu nata na kai su d'akin kayan ta dake k'asa
na rufe.
Nikam kullum dake ina yawaita addu'a da neman sassauci a zuciyata sai Allah yasa
min dangana,ya zama na ma nike bashi hak'uri ina nusar dashi, amma duk da haka
zuciyar sa ta kasa dangana,babu wata rana da zata fito ta fad'i bai yi zancan
little ba,sai a yanzu yake k'ara jin wani tsananin son ta a zuciyarsa,yana rayawa a
ranshi daman haka yaya suke a zuk'atan iyayen su,ashe a duniya zai so d'a har haka
cikin ransa, tabbas Allah ya jarrabeshi da tsananin soyayyat little gashi ta rasu
ma abun ba sauk'i.

********
Wata guda da rasuwar little ne muka sami labarin sati na sama mu fita camp daga
hukumar N.Y.S.C sabida tsaikon da muka samu na strike d'in dukkan universities
d'in mu yasa tun wata biyu baya bamu shiga camp ba.

Tunda na sanar mai ya shiga damuwa kan wadda yake ciki,amma naita rarrashin sa
har Allah ya kawo ranar tafiyar muka wuce jigawa dake daman nan aka turamu.

Ko yaushe na sami sukuni zamuyi waya ina k'ara kwantar mai da hankali don ni
yanzu ma bala'in tausayi yake ban dukkan lamuran sa cikin sanyi yake yi,bashi da
wai kuzari.
*********
A haka cikin ikon Allah mukai wata biyu muka yo gida,daga nan kuma akai posting
d'in ko wannan mu inda zai yi hidimar k'asar sa,Allah yasa daman ni ina da
catipicat na aure UK ya kai musu anyi duk yanda akai aka barni a garina, cikin
ikon Allah muka fara hidimar k'asar mu.

~Bayan wata takwas~ ~A gurguje pls~🙏


************

Zuwa lokacin UK ya k'ara ficewa hankalinsa, ba iya rashin little ba kawai yanzu
burinsa dare da rana ya bud'e ido ya ganni da ciki,amma Allah bai kawo ba,gashi
kuma ya jarrabi zuciyar sa da tsananin son haihuwa a lokacin dalilin da yasa dukkan
nutsuwar sa da kuzarin sa suka kau,daman shi mutum ne mesa abu a ransa, a hakan ma
ina iya bakin k'ok'arina wajan kwantar mai da hankali,tun bansa damuwa a raina har
nima Abun ya far damuna, nan na shiga addu'ar Allah ya dubemu ya azurtamu ya bani
ciki kodan kwanciyar hankalin mijina.
Da naga abun nasa ya ci tura sai na fad'awa Abba halin da muke ciki na damuwar
sa na rashin little da son samun wani gudan jinin, sosai Abbah ya mai nasiha tare
da nuna mai cewa shi Allah ba'a mai tilas yanda yaso haka zai aiwatar.
Nasihar Abba tasa kwana biyu ya d'an rage damuwa,nima sai naji dad'i don
rashin walwalarsa na damuna matuk'a da gaske.

********
Yau kam tunda na dawo gida na shige kitchen don da kwad'ayin danbun shinkafa na
tashi,aiki sosai nake a kitchen dagani sai d'an gajeran wando iya kacinsa cinyata
sai y'ar riga mara nauyi,na juya baya ina wanke cabej naji numfashin mutum a
bayana,da d'an sauri na juyo don tabbatarwa kawai sai naji yasa hannu ya rungumeni
a jikinsa, ajiyar zuciya na sauke tare da lumshe ido,cikin sansanyar murya nace
"Heartbeat kaso tsoratani fa".

Kansa ya sanya kan wuyana yana goga min k'asumbarsa a dukkan wuyana da
kafad'una, muryansa can k'asa yace" masha Allah tunda dai ban tsorata ruhuni ba,
kusa dai tsoratata nai ko?".

Hannu nasa ina shafo gefan fuskar shi tare da mirmishi nace" Ka dawo da wuri
Honey Allah yasa lafiya dai".

Kusan minti guda bai ce min k'ala ba,sai aikin shinshina wuyana da yake kamar
magen data samu wajan laushi,duka hannayensa na zagaye dani yana k'ara sani cikin
jikinsa, ganin yai shiru nima sai nai shiru ina wasa da yatsuna kan hannunsa dake
zagaye dani,can ya sauke min wata malalaciyar ajiyar zuciya a cikin kunne wadda
tasa har tsikan jikina duka ta tashi wani yarrrrrrr tun daga k'wak'walwa ta har
k'asan k'afata,na k'ara lumshe ido ina cije baki, can k'asa k'asa da murya yace
"my life!".

Ban iya bud'e baki na amsa ba illa cewa kawai da nai" ummmmm"

"Yau duka banyi wani abun kirki ba a office, tunda na fita nake jin wani tsananin
feelings tare dani,duk yanda nake ta daurewa zuwa lokacin tashi na yayi na
kasa,dauriyata ta k'are zuwa yanzu shiyasa na taho gida ga halalina gudun karna
fad'a ga halaka".

Jiyo dani yai gabansa muna fuskantar juna,idanuwanmu sarke cikin na juna muna
sakarwa junan mu wani lafiyayyan kallo me narka zuciya, kwantar da kaina nai bisa
k'irjinsa ina cusa duka hannayena cikin gashinsa nace " mijina baka da wani wajan
hutawa bayan jikina,bakada gonar yin shuka bayan ni,nice shimfid'arka wajan sauke
gajiyarka,kuma mayafinka me tare maka dukkan sanyi da k'ura,ka kawo buk'atar ka
inda za'a sauke maka sannan ka samu tarin lada,ina maraba da kai ako wane lokaci
domin a shirye nake kuma a buk'ace nake da kai mijina".

Zame jikina nai a hankali na k'arasa ga gas na kashe sannan na rufe cabej d'in
da nake wankewa,na wanke hannuwana tass sannan na jiyo gareshi.

Yana sak'ale da hannayensa a k'irji yana kallona fuskar sa d'auke da dukkan


annuri,mirmishi na sakar masa tare da d'age gira nace "Bisimillah yallab'ai mu
k'arasa ga turaka".

Bud'e hannayen yai na shige jikins a haka muke tafiya har zuwa upstairs sannan
ya d'aukeni muka haura saman ina sak'ale jikinsa kamar y'ar Baby.🤪

Taku ce
Y'ar mutan Ja'oji🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

💔💔💔💔💔
*_wannan shafin sadaukarwa ne gareka Abu khatheer my Honey,my Heartbeat, my
soulmate, my hubby,my Reality, my my my my ,kuma Baby na d'an lelena🙈,cikin bacci
da ido biyu tunanin ka nake, dukkan motsina da kai a ciki,Allah ya baka lfy yasa
kaffara ne🙏,Allah ya tabbatar da dukkan alkairan sa garemu, ya . . . . . .🙈 kudai
kawai kuce Ameen_*
😅😅💃💃
0⃣5⃣6⃣
0⃣5⃣6⃣ 0⃣5⃣6⃣

Dukkan wata gajiya sai da na kauda mai ita a wannan lokacin, kulawa sosai na bashi
tare da soyayya mai shiga cikin rai, bayan nutsuwa ta kama zuk'atan mu ya kwantar
dani bisa k'irjin sa yana shafa bayana, a hankali cikin gajiyayyiyar murya yace
"Heartbeat! Yanayin dana tsinci kaina yau a ciki Allah yasa rabo ne ya keta,Allah
yasa kin samu ciki a wannan yammacin, wlh Allah my khady haihuwa nake so, so nake
na bud'e ido na ganki d'auke da wani cikina, ina ma ki zama daga cikin mata masu
haihuwa duk shekara,kafin shekara biyar inga yara hud'u na yawo cikin gidan nan
matsayin nawa halal d'ina masu amsa sunan su da nawa".

Cikin salon kwantar da hankali na shafo sangalalin hannayensa har zuwa


yatsunsa,ina k'ara tura fuskata cikin k'irjin sa,tare da sauke wasu tagwayen
numfashi masu tafe da tsantsar k'issa da jan hankali na fara magana" karka damu
Reality insha Allah very soon zamu samu,Allah shike kyauta ya k'ara ya kuma
k'arawa,yana sane damu zai bamu ne,na farko ma ai bamuyi tsammani ba ya bamu wannan
ma baya mantuwa yana sane tsaf damu".

Shafo gashina yai idonsa rufe ya sauke ajiyar zuciya tare da fad'in "Khadeejah!
Allah ya min baiwa a lokacin da yasan ya dace yayi min amma sai na butulce mai, na
nuna cewa nifa kawai an min kutse ne a lokacin, sam ban yi murna ba da nai arba
da kyautar da yayi mini,k'arshe ma sai na b'ige da muzguna miki tare da d'ora miki
alhakin abun, ranar da little tazo duniya naji bak'on yanayi tare dani,lokaci guda
Allah ya sanya min soyayyar ta cikin k'irjina, har nake mamaki da tambayar kaina
dama haka muma iyayen mu suke k'aunar mu? haka daman dukkan iyaye kejin son yayan
su a zuk'atan su?watanni uku da satika da little tai aduniya sun zomin da nishad'i
da farin ciki, lokacin da zuciyata ta shagala ga k'aunar sanyin idaniya ta a
lokacin kuma Allah ya nuna ikonsa garemu, tabbas nasan Allah ya hukuntani ne
gwargwadon butulcin da nai mai,domin shi Allah baya zaluntar bawansa sai dai bawa
ya zalunci kansa,Khadeejah nai tunanin kwanaki kad'an da rasuwar little zaki k'ara
samun wani cikin amma sai gashi har an tafi shekara, Allah dai yasa ba rabon mu
kenan a duniya ba".

D'igar hawayen sa danaji akan hannayena dake gefan fuskarsa shi yasani d'ago
kaina naga yanda hawaye ke bin kuncinsa da gudu gudu, yatsuna biyu nasa ina share
mai hawayen tare da k'ara sanyaya muryata nace"haba my heart, ya zaka min haka kana
son in shiga cikin damuwa kenan,kana son nima in k'i kwantar da hankali na, don
Allah ka daina zubda hawayen ka Allah yana sane damu insha Allah zai bamu wani
rabon,gaggawa muke shi kuma Ubangiji bai son aikin gaggawa".

Harshe nasa a hankali na fara lashe hawayen nasa, a sannu na d'ora lips d'ina
kan nasa ina gogawa tare da zira harshena cikin bakinsa ina wasa dashi.

Cikin sanyin jikinsa ya shiga karb'ar sak'onnina tare da k'ara sakani cikin
jikinsa sosai, tsawon lokaci ina rarrashin sa tako wace siga tare damai kalaman
kwantar da hankali, har naga ya fara dariya, sannan na tashi daga jikinsa ina
d'aura towel hannu na mik'a mai shima ya mik'e, ina mik'a mishi wani towel d'in
amma sai yak'i k'arb'a, kawai jinai ya kunce min nawa tare da shigewa ciki,
marairaice fuska nai ina d'an biga k'afa tare dasa hannu ina tuttureshi nace" nidai
ka barni inje in wanka kagafa har hud'u tayi tun biyu fa".

Kashe min ido yai yana dariyar tsokana yace" to muje mana muyi wankan,ai bance
zan k'ara komai ba yanzu sai Zuwa dare kuma".

Ja nai da baya na fizge towel d'in da gudu na shige toilet. Bina yai da kallo
yana dariya tare da d'aukan dayan towel d'in ya d'aura ya biyo bayana.
Ko juyowa banyi ba naci gaba da had'a ruwan wankan tare dasa turarukan wanka
sannan na cire towel d'in sak'ale nai tsalle d'aya na shige cikin Bathtub d'in,
yanda nai shima haka yai ya shigo ciki tare da mak'alewa jikina yana fad'in ayi
min wankan duk na gaji bazan iya yiba".

Ban tanka mai ba sai cud'ashi dana shiga yi yanata wani shagwab'emin da
narkewa ,nima wankan nai sannan muka canja ruwa don yin wankan tsarki.

Bayan fitowarmu a gaggauce muka sanya kaya don lokacin har hud'u ra rabi ta
kusa,salla ya jamu mukai,bayan mun idar nasa riga mara nauyi iya k'aurina,shima
3quarter yasa da singlet,jansa nai zuwa kitchen ya tayani mukaci gaba aikin tare,
munayi muna soyewarmu,har muka gama, shi yaje ya shirya dining table ni kuma na
gyara kitchen d'in.

Sai bayan sallar magriba mukai dinner, yace in shirya muje gidan abokinsa da yai
aure,cikin murna nai d'aki da gudu na shirya cikin riga da siket na wani had'ad'an
boyel less milk da filawa ja,nai amfani da jan Vail da takalmin duk kalan
ja ,sosai nai kyau, ina tsaye gaban mudubi ina k'ara gyara d'an kwalina ya turo
k'ofan sanye da k'ananan kaya ta cikin mirror na kalleshi muka sakarwa juna
mirmishi, yana tsaye jikin k'ofar hard'e da hannayensa yace "Babyna kinyi kyau
sosai fa".

Farrrr nai da idanuwa ina takowa zuwa gareshi cikin rausaya da rangwad'a,gaban
sa na tsaya ina k'ara gyara mai wuyan rigar nace" Kayan nan suna maka kyau
matuk'a, amma nai zaton manyan kaya zaka sa fa".

Mirmishi d'auke kan fuskar sa yace" Su kike so in saka?".

Gyad'a Kaine tare da rausayar dashi.


Rik'o hannuna yai yana fad'in "To muje d'aki ki zab'o min wanda kike so in
saka".

Wajan closet d'in sa na nufa na zab'o mai wata narkakkiyar shadda


Milk color wadda aka yiwa aiki da bak'in zare,d'in ki boda ne, sannan na zab'o
mai bak'in takalmi da hula bak'a, bayan na gama shirya shi wani bayyanan nan kyau
naga yayi min,kasancewar sa bamai yawon saka manyan kaya ba yasa duk sanda ya
saka sai kaga kamar bashi ba,cikar kamala da haiba duk sai su bayyana a gareshi,
lumshe ido nai bayan na sakar mai wani hot kiss nace"kayi kyau har ba'a magana
Zaujee,manyan kaya sun fi kowane kaya maka kyau".

Shafo fuskata yai da fad'in "Sabida ke nake d'inka wa Baby na,amma nikam da basu
wani birgeni, saka sun da nake yanzu sai nima nake jin dad'in su a jikina".

Waya ta na d'auka na fara buga mana slf ta ko ina.

*********
Kyakykyawar tarb'a muka samu daga wajan Muktar da matar sa laila, mun dad'e gidan
muna hira muktar nata tsokanar UK wai duk ya zama kalan ustazai yanzu,har maganar
sa ma ta canja,shi dai dariya yai yace " zama da ustazai ne maida ni haka".
Sai k'arfe goma muka baro gidan.
Muna shigowa shirin bacci kawai mukai ina jin sa yanata tsokana ta nai mai
shiru don bacci ya kama idona.

~A gurguce plsss~👇🏼

Cikin hukuncin Allah muka gama hidimar k'asar mu cikin nasara,daga nan na samu
nutsuwa ban zuwa ko ina ko yaushe cikin hidiman mijina nake.

A wannan tsakanin ne bikin sweety ya taso in da akasa rana wata biyu kawai bisa
rok'on da mijin yai tayi kan ayi a wata biyun.

Tun daga lokacin bama samun zama mune kasuwa mune manyan Mall mall.

______________ Rana bata k'arya yau ya rage kwanaki goma bikin sweety Kuma yaune
aka k'arb'i lefe kaya na alfarma tun safe bamu zauna ba munata hidimar jama'a,y'an
uwa da suka zo karb'ar lefen,sai dare gidan ya sarara kowa ya tafi,y'an aiki duk
sun gyara ko ina,
Aunty murjah ma tana b'angaran Abba yasa muka k'ara baje kaya ni da sweety tana
ganin kayan, nikam inata tsokanar ta ita dai duk jikin ta a mace yake,sallamar UK
parlour d'in yasa muka kalli k'ofan a tare, muna had'a ido ya sakar min harara y'ar
dariya nai ina mik'ewa gareshi tare da mai sannu da zuwa,"A'a ni kam ba ruwana
dake yau gaba d'aya kin manta dani ina ta kiran wayar ki ma bikiyi picking ba".

Marairaicewa nai ina fadin "hubby nah wake mantawa da zuciyar sa,dukkan abunda
nakeyi ruhina na tare da kai gangar jikin ce kawai anan ".

Lakuce min hanci yai yana fad'in" um dad'in baki dai da wayo za'a min kawai".

Kad'a ido nai tare da rik'o hannun sa nace "zoka zauna ka kalli kaya kafin in
had'ama abunda zaka ci".

Nan na barshi tare da sweety na wuce kitchen da azama na fara shirya mai plate
daman na riga na ajiye mai abincin daran da naiwa Abba, tuwon semo da miyar
d'anyan kub'ewa da taji tantakwashi.

Center table na jawo mai gaban sa na shirya mai abincin akai,bayan ya fara ci
na shiga d'ad'd'aga mai kayan yana kalla,jinjina kai kawai yake yana yabawa tare da
addu'ar fatan zaman lafiya ga ango da amarya.

Sai wajan sha d'aya muka zagayo gidan mu,kai tsaye toilet muka wuce mukai wanka
tare da alwalan kwanciya don neman kariya daga shed'anin mutum da aljan.

Muna kwance hira muke tab'awa kad'an kad'an yana matsa min jikina dake min ciwo
sabida gajiyan yau,cikin tsokana yace" wato ko ki tambayeni ma yau ina na tsaya
sai taran dare kika ganni".

Cikin rashin damuwa da batun nace"Ai nasan don kasan muna hidimar mutane ne baka
shigo da wuri ba,don koda ka dawo ma a hidimce zaka ganni,lokacin daka shigo ma ban
dad'e da gamawa Abba abinci ba".

"Hhhmmmm yarinya shi yasa nima nai tafiya ta tad'i don nasan in na shigo ma gidan
da wuri bakya nan".

Da sauri na tashi daga jikin sa cikin fargaba nace " me kace?".

Cikin dakewa da basarwa yace"Naje gun k'anwar ki ne tace ma in gaida ki sosai".

Jinai wani mashi ya soki zuciya ta da k'arfi,amma cikin y'an seconds nai tunanin
wace ce ni,mace me aji nake,don haka na d'an murmusa tare da fad'in "hhhhhmmm ina
amswa sosai nima ina gaishe ta sosai".

Kaina na maida jikin sa na kwantar, zuciyata na wani irin bugu.

Mamaki ne ya kamashi ganin yanda na dake duk da yasan tsananin kishin da nake
dashi,a zahiri yaga firgici tare dani amma kuma sai furucina ya nuna ban damu ba,
cikin son k'ara jan zancan yace" biki tambayeni wace ba kuma ya sunan ta sannan a
ina take ba".

K'ok'ari nai na fizgo kalmomi daga bakina nace" hhhmmmm ai wannan duk ba
hurumina bane,in ma kuma ina da hurimi dasu nasan in lokaci yai zanji ai".

Daga yanda nake furta maganar yasan nazo wuya kawai b'oyewa nake k'ok'arin
yi. Amma kuma sai yaji ba dad'i da ban nuna zafin kishi kansa ba,

D'ago ni yai zaune shima ya zauna tare da fad'in "Da wasa nake miki my life
karki d'auka da gaske fa".

Kallon k'yar namai tare da fad'in" Ko da gaske kake ba abun damuwa bane ko
b'oye b'oye, na dad'e ina fad'a maka ban marmarin rayuwa da kishiya a rayuwa
ta,amma in har akwai zama da kishiya cikin rayuwar aure na to zan zauna da ita
tsakani da Allah kuma in amsa kaddara ta hannu biyu, kuma ai zuwa yanzu daman ya
dace ka fara neman aure ko don samun Baby kaga sai damuwar ka ta tafi akan son
haihu. . .".

Da sauri ya rufe min baki yana jawoni jikin sa sosai, tsawon minti guda sannan
yace " Wlh Allah da wasa nake miki Khadeejah, kin sani nasha fad'a miki ban ra'ayin
tara mata matsayin nawa,sam sam banda wannan ra'ayin balle har kike cewa wai kodan
in sami Baby, kina nufin har anzo matakin da zan miki kishiya don biki k'ara
haihuwa ba? to kima cire wannan daga ranki wlh duk abunda nake nema nadaga yaya
fata na su zamo daga gareki, kodan samar musu da kyakykyawar rayuwa me cike da
nutsuwa da tarbiya, ni da wasa nake mu bar wannan maganar ma don Allah ".

Yana gama fad'a ya koma ya kwanta tare dani a jikin sa, nidai lumshe ido kawai
nai zuciyata ba dad'i duk da kalaman da yai yanzu sun Dan samun nutsuwa da
kwanciyar hankali amma sai nake jin zuciyata cikin kishi sosai".

A haka bacci yai gaba damu,Wanda bamu farka ba sai asuba, bayan mun idar da salla
munyi azkar wanda shi ya ke karantawa da fassaran hausa don bai haddace su duka
ba,shiyasa na bashi littafin yake amfani dashi.

Tsawon 30 minutes muka shafa na jiyo ina gaisheshi kamar kullum ya amsa min
cike da kulawa sannan ya k'ara k'asa da murya sosai yace" my life kiyi hak'uri da
maganar da nai miki jiya Allah wasa ne kawai nake miki".

Mirmishi bayyane kan fuskata nace "lah nifa har nama manta da wannan issue
karka damu nasan raha ne kawai ka ke yi".

Shafa kaina yai cikin nutsuwa yace" masha Allah, Allah yai miki albarka mata
ta".

Cikin jin dad'in Addu'arsa na amsa"ameen ameen my zaujee,Allah ya kare min kai
daga dukkan abun k'i ya faranta rayuwar ka duniya da lahira".

********************
Abun fa yazo, don yau ne Alhamis za'a saka Sweety a lalle, tun safe ban gida duk da
gidan nawa cike yake taf da k'awaye da y'an uwan su,duka d'akunan k'asa da parlour
sun baje suna bidirin su, shigowa ta daga wajan saloon kenan na zauna tsakiyar su
muke gaisawa da d'an hira,wasu da yawan su na san su,wasu kam yau na fara ganin
su,dukkannin su y'an mata ne sai mutum biyu da na gani da yara hannun su,da kuma
wata shukra ita bazawara ce, raha sosai muke dasu ana hira, na kira lami nace su
kasance a part d'in sabida kula da hidiman bak'i da gyara waje, cike da girmamawa
ta amsa da fad'in "To uwar d'akina an gama insha Allah".

Daga bayana naji an saki wani siririn tsaki,juyawa nai idona ya fad'a kan Zee
yarinyar Aunty uwani,wanda tun shigowa ta ma ban kula da ita a wajan ba,d'auke kai
nai daga gareta ina cewa Lami " shi kenan jeki".

Ta mik'e ta tafi,nima tashi nai ina ce musu barin


in d'an watsa ruwa.

******Tunda na shiga d'aki nake tunanin wannan karon zan koyawa zee
hankali,sabida duk sanda muka had'u wajan wani taro nasu ko a kano ko a katsina sai
taita min tsaki tana hararana ta gefan ido, tun ban gane me nai mata ba,har na fara
fuskantar tsakanin ta da UK don da ta ganshi zata fara wani rausaya da rangwad'a
tai ta shige mai,babu Wanda ya sanar dani da kaina na fahimci hakan,don haka nasa a
raina zan daina koda kulata bare ta rink'a min kallon banza.

************k'arfe biyar aka fara gudanar da kamu a wani babban fili na Abba dake
cikin layin namu can k'asa.

An shirya wajan da kayan al'adar hausawa komai yayi gwanin birgewa, yayin da aka
d'auko makad'an k'warya na gidan sarki suke cashewa.
shigata nai cikin wani sari riga da siket da mayafin sa, har da sark'a da D'an
kunne kalan sa don akwati guda UK yai min na kayan fitar biki kamar yanda yai wa
kansa ma,kuma duk yawanci kayan namu kalansu d'aya ne, nai kyau badan san kai ba
sai dan sanin cewar nayi kyau d'in. duk in da na ratsa za'a ce kai kinyi kyau,
mirmishi kawai nake nace "na gode".

Ina lura da Zee da hararar da take wurga min tunda na shigo wajan,kallon arziki
bata isheni ba,don haka sabgar gabana kawai nake yi.kasancewar wajan ba maza sai
yara kawai yasa muka cashe abun mu,amarya ta fito na balle bandir d'in kud'i inata
mata lik'i itama bud'e pos d'in ta tai ta fiddo kud'i ta shiga maida min
martani,ganin haka yasa Aunty ummu sulaim itama tazo tanata mana lik'i ai kuwa
sai akai rubdugu cikin filin ana mana watsin kud'i, masa kid'an kwarya fa sun ga
abun nema sai suka sake dagewa da sakin sabon kid'a.
Zee ji tai kamar zata mutu don takaici,haushi taje ji in taga family d'in su na
nan nan dani kowa sona yake wanda na tabbatar kyautatawar da nake musu ce tasa
suke k'ara k'aunata,ita kam takaicinta yanda nake ba y'ar boko ba ba wata me
bud'ad'd'an ido ba amma na iya zama da mutane da siye zuk'atan su,(bata san ba anan
take ba,iya zama da mutane baiwa ce,kuma hankali da nutsuwa ke sa ka fahimci kowa
ka iya zama dashi gwargwadon halin sa)

Tai nisa cikin tunani hassada da kyashi taji an dafa bayan ta,juyowa tai taga
waye wata cousin sis d'in ta ce wadda halin su yazo kusan iri d'aya, tace"sis ya
kike zaune anan duk son ki da rawa ga jama'a nata cashewa ?".

Yatsina fuska tai cikin takaici tace "A'a filin ba irin namu bane,naga kucakai
sun cika wajan".

Dariya Khairy tai yace" Hhhhhhhh nasan kuma da wa kike,wlh karki sa damuwar
wannan yarinyar ta hanaki walwala wajan bikin da kika ci burin rak'ashewa".

D'an tsaki tai tace "ke ni wlh fa ko son kallon ta bana yi sam yarinyar nan bata
min ba,ai Broz ya tafka asara wlh duk ajinsa ya k'are ga wannan yarinyar".

Rashin abun yi yasa suka ita gulmar su,nikam inata rak'ashewata da walwala
banma San suna yi ba.

Sai magriba aka tashi daga kamun.

***********duka gidan nawa muka rankayo da su,ni dai bayan na tabbatar nasa su lami
sun ajiye musu duk abun buk'ata sama na haye don yin salla.

Wanka na fara yi sannan na d'auro alwala bayan nai sallar na d'an shafa creem
tare da perfumes d'ina, riga da sket English wear nasa wanda suka zauna jikina
d'as na sanya hula kan kitson da aka yarfa min tamkar na barebari,don tabarakallah
gashi a kaina kam ba'a magana, ganin har lokacin UK bai shigo ba yasa na k'ara
sakkowa k'asa, nan na same su sun baje a parlour suna cin abunci wasu na hira,wasu
na danna waya,tsallakawa nai kusa da Ikee na zauna ina tsokanar ta" manya gatan
wasa ke baki cin abincin ne?".

Y'ar dariya tai da fad'in "Auntyn mu wlh banjin yunwa ne kawai a gajiye nake
jina".

" Ayya sannu,to ko ruwa za'a had'a miki me d'an d'umi kiyi wanka,maybe gajiyar
zaman mota ne".

Lumshe ido tai tace "Eh yanzu zan yi wankan in kwanta,waya nake son in gama".

Dariya nai da fad'in" hhhhhmmm ashe soyewa ake yi nazo na zauna,bari in canja
waje to".

Dariya duk akasa,nan muka shiga hira da labarin yanda kamun yau ya kasance.

Da gudu gudu Sweety ta shigo parlourn tana fad'in "Aunty na Aunty na".

Cikin kulawa nace " ya akai Amarya?".

"Zo sirri ne abun taso mu matsa kar way'annan yaran su jimu".

Dariya wasu suka sa yayin da wata cousin sis d'in tace" Eh lalle yarinya nuna
mana zakiyi kin girma za'a miki aure shi yasa kike kiran mu yara".
Gwalo tai mata da fad'in "Eh d'in fa ba yaran bane ku,amma banda Shukrah da Aysha
da Ummy su sun girma amma duk ku d'in nan yara ne".

Ni kaina dariya nai ina mik'ewa don jin sirrin me zamu yi, caraff cikin kunnena
naji yo wani lafiyayyan tsaki Wanda babu tantama nasan daga bakin wa yake don haka
ko juyawa banyi ba sai Sweety ce tace " Wai ke Zee meke damun ki yau duk na ganki a
wani cunkushe ?".

Harara ta watsa mata da fad'in "ba case d'in Ki bane wannan".

Tab'e baki Sweety tai ta rik'o hannu na muka haye sama.

Cikin damuwa ta kalleni bayan mun zauna tace " Aunty nah Allah wannan abun da
kika bani nasha yana bani matsala fa".

Cikin dariya nace "Matsalan me ?".


Marairaicewa tai da fad'in" Ni gaskiya bazan k'ara shan komai ba Allah, kinji
yanda nake jik'ewa kamar me period, gashi sai injini in feelings ko yaushe, har ji
nake kamar ana tsankwalina wlh".

Dariya nai sosai nace "To ai shine gyaran mana Sweety, ko yaushe an fi son mace a
jita da danshin ni'ima ba abushe k'amas ba,kin ga kayan nan tun daga gun Sis
Nasmat y'ar mutan ark'illa sokkoto nasa aka aikoshi,don ko yaushe ina jin yanda
y'an group ke zuzuta kyan kayanta,koni danai amfani dasu na tabbatar da ingancin
su, don haka karki damu kiyi ta amfani dasu,Allah zaki zama sarauniyar mata a
zuciyar Angonki,domin gyara shine mace,ke Sister in low ce dana bud'e miki zancan
kin gane".
Na k'arashe maganar da dariya, turo baki tai da fad'in" A'a ni kam basai an
bud'e min ba,Wanda ma ake min bita kullum sun isheni,kin kaini group d'in matan
aure ma kullum sai lecture suke kin suna karar min da ruwan kai na".

Tare mukasa dariya dai dai lokacin UK ya shigo yana fad'in "Gulma dai ta kusa
k'arewa daga ran lahadi, kullum sai Ku k'ule d'aki kuyi ta gulma".

Dariya mukai ita da Sweety ta mik'e tai downstairs,k'arasowa yai ya zauna kusa
dani yana matsa cinyata yace" kun bar bak'in Ku a k'asa kunzo kunata gulma,wai me
kike fad'a mata ne kullum yanzu na ganku tare kuskus kukeyi".

Kashe mai ido nai nace "Abun sirri ne tsakanin mu oga".

Matse min hannu yai har nai y'ar k'ara yace" Akwai wani sirrin da za'ai da wani
bayan wanda akeyi dani,ni dai Allah yasa ba bata labarin ihun da nake cikin dare
ake ba,don Ku mata in za'ai wa yarinya aure sai kuyi ta fad'a mata sirrin ku wai
don itama ta rink'a yin haka a gidan mijinta".
Serious na koma ina kallon shi nace "kana tunanin ina cikin mata masu bayyanar
da sirrin Auransu? Duk duniya babu wani mutum da zan iya shearing sirrinka dashi
duk kuwa yanda muke dashi,rashin ilimi kesa mace bayyanar da sirrin kwanciyar
auranta ga wata, ban ce ma mata in sun had'u basa wannan hiran ba amma gaskiya
yawanci bita ne mu keyi tare da k'ara wayarwar da junan mu kai kan rayuwar aure da
matsalolin cikinta".

Numfashi ya saukr yana fad'in" Yawwa hakan ai yafi, amma ka gama shagali cikin
dare da safe a bawa k'awa labari ai an tsiraita ka".

Dariya nai kawai ina kauda zancan ta hanyar fad'in "In had'a maka abunci?".

" A'a bari nai wanka tukun".


D'aki muka wuce don na had'a mai ruwan wankan.

______________Washe gari jumma'a da yamma akai fulani show da dare akai dinner,
Ranar asabar kuma akai yini wanda shima a gida akai filin Abba, da dare muna zaune
tare da amare UK ya shigo parlourn daga bakin kofa ya tsaya yana kira na,yaron
Aysha ne a hannu na,ina zuwa ya amsheshi tare da fad'in "Ki kawo min jakan ban
dana baki ajiya me ita yazo".

Nace " OK " tare da juyawa zuwa sama.

Gefen kujerar da ba kowa ya samu ya zauna yana wa yaron wasa yace "Aysha Naeem
sa'an little ne ko?".

Amsa mai Aysha tai da fad'in" Eh little ma ta bashi sati biyu".

Gyad'a kai yai da fad'in "Da tana raye da tuni itama fa taba tafiya,yanzu
shekara guda da wata uku kenan da rasuwar ta".

Sakkowata ne ya dakatar dashi ya k'arb'i jakan tare da mikomi yaron ya fita.

Ban san hiran da sukai ba ni dai bayan na zauna dai naji zee ta kalli Ikee tana
tab'e baki da fad'in" Wato sis in baki labari wata ce a group chart d'in mu tai
aure tsawon lokaci bata haihuwa ba,bayan wasu shekaru ta haihu sai d'an nata ya
rasu kuma gashi mijin nata yanzu bala'in son haihuwa yake, kuma ita ta zama juya
don haka mijin harya fara tunanin k'arin aure amma dalilin an shanye shi ya kasa
furtawa,wai shine take neman shawara ya zatai,don tasan duk randa aikin da ta ke
yi a kansa ya karye tana cikin tasku".

Dariya Ikee tai tace "yo shi aikin asiri duk yanda ta kai ga sabun tashi wata
rana zai karye k'ara ma ta barshi yai auran sa tun da wuri ".

Dariya Zee tai tare da mik'a mata hannu suka tafa tace" ai kuwa bari in bata
shawarar nan taki".
Kamar gaske ta kunna waya ta shiga dannawa kamar tana typing wani abu.

Ni dai ko yarinya ce nasan dani Zee take,amma ko a fuska ban nuna na fuskanci
zancen ta ba,sai Aysha tai k'ok'arin sa musu baki a zanjan nasu da fad'in "To banda
abunku ai haihuwa Allah ne ke bada ita,kuma wlh yanzu ma ba kowane namiji ke son
haihuwa a kufe a kufe ba".

Tanka musu da Aysha tai ya basu damar jan zancan sukaita yada magana, nikam
tunda suke kallo basu ishe ni ba,k'arshe ma tashi nai na bar wajan, d'aki na shiga
zuciyata cike da b'acin rai har hawaye suka fara zubomin,sunan Allah nai ta ambata
sannan na sami nutsuwa, ina zaune a haka UK ya shigo kallo d'aya yamin ya gane da
damuwa a raina bayan ya gama shirin baccin sa tsaf ya hayo gadon yana fad'in" Naga
yau sarauta ake ji ko shiryani ma ba'aiba sai ni na shirya kaina".

Cikin k'ok'arin kauda komai daga raina nace"Gajiya ce kawai tare dani ba sarauta
ba".

"Wlh kin ga nima cikin gajiyar nake sosai, ai gobe dai da an d'aura aure biki ya
k'are".

Zan yi magana wayar sa ta fara Ringing jim yai bayan yaga me kiran naga ya
tamke fuska ya d'aga" Hello ina jin ki ".
Ban san me aka ce ba daga d'aya b'angaran naji yace " ke ina taki?".

"OK ina zuwa".

Tsaki ya ja bayan ya gama wayan,ban kalleshi ba nace" ya da tsaki kuma?".

"Wannan yarinyar ce Zee wai in bata aran charger tasa tata yanzu ta k'iyi".

Dummm nai can nace " OK bari in. Bata tawa".

Ina fad'a na mik'e tare da d'ora hijab kan night gown d'in dake jikina.

Tun daga step na biyu na hango idon ta kan hanyar tai tunanin shine,muna had'a
ido ta wani d'aure fuska nikam mirmishi na wadata fuskata dashi nace "wace ke neman
charger cikin Ku gashi".
Ina fad'a na mik'awa Sweety na juya".

*_Taku ce_*
*_y'ar mutan Ja'oji_*🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

*Allah ka dafa mana cikin lamuranmu ka share hawayen mu,ka amsa addu'o'in mu ka
tsare mu sharrin mak'iya da mahassadan mu*🙏🙏🙏

~second to the last~

0⃣5⃣7⃣
0⃣5⃣7⃣ 0⃣5⃣7⃣
Bayan na shiga d'akin ban ce mai komai ba na cire hijab d'in tare da hayewa
gado,ina hawa wayar sa na k'ara yin ringing ban kalli me yake bama balle in san
halin da yake ciki,sai lumshe ido na kawai da nai, ina jin sa yana ta sakin tsaki
har wayar ta tsinke,kashe ta yai gaba d'aya ya ajiye kan bed site,tare da matsowa
jikina yana juyo dani,"Gimbiya ya dai? ko duk gajiyan ne,bari in miki massaging ".

D'an mirmishi kawai nai ban dai ce mai komai ba,ya shiga mammatsamin jiki yana
min tausa, tsawon minti biyar naji yana magana" Wify!".
D'an bud'e idona nai na sauke a kansa ina jiran jin me zai ce" Allah yarinyar
nan bata da hankali ko kad'an ".

Cikin nuna alamun ban san da waya yake ba nace" wa fa?".

K'ara jawoni jikinsa yai sosai yana fad'in " Zee mana,wlh bata da nutsuwa, ya
za'ayi mutum na tare da matarsa a rink'a ta kiran wayarsa haka? Ba'a san halin da
mutum ke ciki ba ayi ta damun sa da kira ana yanke mai hanzari"

Tab'e baki nai cikin halin irin ban damu ba nace"Ita kasan uzirin da yasa ta
kira ka ne?".

Wani tsakin ya ja tare da fad'in "Babu wani uziri sai shirme, in da can tana
haukan ta ai yanzu tasan ina da aure,tun daga lokacin da nai aure ya dace ta rabu
dani,nasha fad'a mata ban da ra'ayin ajiye mace sama da d'aya a rayuwa ta,tunma ban
san dad'in auran ba,balle yanzu da nasan sugar d'in da ke cikin sa".

Ya kar'asa da sakar min wani sweet kiss.

Bud'e idona nai sosai cikin nasa tare da fara magana" Ashe daman son ka take?
na dad'e da son gano hakan ban gasgata ba sai yanzu daka furta da kanka, amma me
yasa bazaka amincewa buk'atar ta ba, tunda jininka ce ita,kaga sai kuyi auren
zumunci".

Kafin in rufe baki ya buge min shi, ai kuwa na shagwab'e fuska zan yi kuka,
shiru yayi ba tsawon mintina biyu sannan ya ce " karki k'ara had'ani da wata mace
da sunan soyayya bayan ke,ban so kinji na fad'a miki".

Ajiyar zuciya na sauke kawai tare da shigewa jikin sa har bacci ya d'auke mu.

********
Washe gari akai d'aurin Aure k'arfe biyar na yamma aka kai amarya gidan mijinta.

Ranar litinin dukkan jama'a kowa ya koma gidan sa.

_A gurguje plsss_
___________________
Bayan wata goma a lokacin ne na samu lecturing a makarantar Koyon shari'a da
harshen larabci a nan kano wato legal, abokin Abba ne ya samu Provost a makarantar
shine Abba ya nema mana lecturing ni da Sweety a nan,ai kuwa dake yana da ido nan
da nan muka sami gurbi,ita sweety English take d'auka ni kuma b'angaran Islamic.

Zuwa lokacin Sweety na d'auke da tsohon cikinta haihuwa yau ko gobe, ni kam
harna hak'ura na mik'awa Allah lamarin sa,don na fidda ran ma zan k'ara samun
haihuwa.

A tsakanin ne kuma lafiya tak'i wadata gare ni,kullum cikin zazzab'i nake da
ciwon kai dare da rana,UK yayi yayi in je asibiti nak'i har wajan sati biyu.

Yau juma'a ko tashi na kasa yi don tsananin zazzab'i, don haka har yayi shirin
fita office ya hak'ura ya taimaka min na shirya muka wuce asibiti.
Bincike sosai doctors su kai min nan suka gano ina d'auke da k'aramin cikin wata
biyu,kasancewar ni an samin drip ina bacci result d'in ya fito ya sa ban san
wainar da ake soyawa ba.

UK ya kasa gasgata me doctor ya ce mai don unexpected yaji zancan, k'ara sa kunne
yai yana cewa doctor d'in "doctor me kace ne k'ara maimata min pls"

Cikin dariya doctor ya ce " congratulation Umar Usman Katsina,madam tana d'auke
da Unborn Baby na sati takwas,Allah ta raba su lafiya".

Ji yai wani shock ya kamashi k'wak'walwar sa ta tsaya da aiki na d'an sekonni


zuwa can ta dawo aiki,cike da tsananin farin ciki ya cire takalman sa yana
tsugunnawa tare da yin sujjada ga Allah don nuna tsantsan farin cikin sa
(Sujudushshukur) tsawon mintina yana durk'ufe yana godewa Allah gaba d'aya hawaye
ya k'i tsaiwa a idon sa.

Ganin shiru shiru bai d'ago ba yasa doctor d'ago shi ya na bubbuga bayan sa
Tare da fad'in " ba kuka za kai ba Umar, wannan abun farin ciki ne dariya ya dace
kowa ya gani a kan fuskar ka".

Mirmishi ne ya yawaita kan fuskar tashi yace"Wannan kukan farin ciki ne Doctor
yau ban san me zan yi in nuna godiya ta ga Allah ba,amma tabbas a yau nasan na fi
kowa farin ciki da walwala ".

Wayar sa ya ciro a aljihu ya fara danna number d'in Abba, kira d'aya Abba ya
d'auka da fad'in" Daddy ya dai?".

Cikin zumud'i yace "Abba gamu a hospital Nahna ba lfy,Doctor ya dubata ya


tabbatar da ciki gare ta na wata biyu".

" Alhamdulillah Alhamdulillah, Allah kai ka cancanta mu godewa, Allah ya Kara


mata lafiya kuma ya raba su lafiya,bari na na fad'awa murja maza tazo wajan Ku
yanzu, ina fatan dai jikin nata bai tsanani ba?".

Yanda Abba ke magana cikin farin ciki haka ma UK d'in.

"Eh Abba jikin nata da sauk'i gashi an sa mata ruwa bacci ma take yi".

" To ka kula sosai ga murja nan zuwa ".

Yana yanke kiran ya kira Sweety ta sanar mata,itama ihun murna tasa tana fad'in
da ta gama lecture da yamma zata shigo".

Bayan ya yanke kiran ya kira Ummu Sumail itama ya fad'a mata Nahna na da
ciki,itama murna tai sosai tai fatan Allah ya raba lafiya.

Lokacin da ya danna kiran Yaya Haroon sai da ta fara Ringing sannan kunya ta kama
shi,yana jin Yaya yai sallama ya rage murya tare da gaisheshi sai kuma yai shiru,
Yaya Haroon ya ce" Daddy ya gida ya iyalin".

Cikin jin kunya yace "Alhamdulillah Khadeejan ce ma bata jin dad'i yanzu ma muna
asibiti".

Cikin damuwa yace " Subhanallah me ya sameta?".

"Um um Zazzab'i ne da ciwon kai".

" To bari in kira Hafsah tazo taga jikin nata,amma dai da sauk'i ko?".

"Eh da sauk'i Yaya gata tana bacci dai yanzu".

" To Allah ya k'ara sauk'i da dare zan shigo in dubata insha Allah ".

Ba jimawa sai ga driver ya kawo Aunty murjah, itama bata jima ba Aunty Hafsa
tazo,har lokacin ban farka ba.

Sai bayan sallar azahar na farka,na d'an ji dama dama,su Aunty nata min sannu ni
dai amsawa musu nake amma ina mamakin yanda naga fara'a sosai kan fuskar su,
taimaka min Aunty Hafsah tai na wanke bakina na d'an sha kunun Gyad'ar da aka
kawo,a lokacin doctor yazo ya k'ara dubani sannan yace zamu iya komawa gida bayan
ya rubuta mana magungun da zan iya amfani dasu.

Ya juya zai fita UK ya shigo nan ya ke sanar dashi ya ya sallame mu,suka k'ara
musabaha,ya k'araso d'akin " kallon farko da naiwa fuskar sa naga yanayin da banyi
tunanin gani a tare da shi ba,don na san ko ciwon kai kawai na keyi ya shiga damuwa
kenan duk ya rikici amma yanzu gani kwance kan a gadon asibiti na ga fuskar sa
d'auke da fara'ar da na dad'e banga irinta tare dashi ba.

Katsemin tunanin yayi ta hanyar min magana "Ya jikin naki?ban San kin tashi ba
ai,ina masallaci".

D'an yamutsa fuska nai da fad'in" da sauk'i ".

" Masha Allah, Aunty mu wuce gida ko?".

Gyad'a kai Aunty murjah tai tana fad'in"Ai masha Allah jikin nata,in mun je sai
tai wanka da ruwa me d'umi zata k'ara jin k'arfi".

Aunty Hafsah tace gida zata wuce tunda dai jikin nawa Alhamdulillah zuwa gobe
zata k'ara dawowa ta duba ni, don haka sai da muka biya ya sauketa a gida sannan
muka wuce .

Wani haushi naji ya turnik'eni yanda naga fara'a sosai kan fuskar UK, wato ni ina
jin jiki amma ko a jikin sa ko sau d'aya banga alamun damuwa da tausayi na kan
fuskar shi ba,sai wata dariya yake ma, gate d'in Su sweety muka tsaya Aunty ta
sauka sannan muka shiga namu,yana tsayawa na bud'e murfin zan fita da sauri ya
dakatar dani ta hanyar rik'oni cikin fishi na fizge nai wucewata,da mamaki ya tsaya
kallona sannan ya rufe motar da sauri ya biyo ni.

A falon k'asa muka had'e ya rik'oni jikin sa sosai yana fad'in "Meya faru ne My
Happiness?".

Turo baki nai nace " Don Allah cikani inje in huta na gaji".

Bai k'ara magana ba ya d'aukeni cak mukai sama,bai dire ni ba sai cikin d'aki,
bakin gado na kwanta shi kuma ya shige toilet ya had'a min ruwan wanka me
zafi,lokacin daya fito har bacci ya fara fizgata don alluran bata cika ni ba,kaya
ya fara cire min inata tuttureshi da turo baki,shi dai sai dariyar sa yake annuri
na k'ara fad'ad'a kan fuskar sa,abunda kW k'ara kular dani ina tunanin ya daina
damuwa da ciwo na.

Sosai ya gasa min jikina ya min wanka, sannan yace in d'aura alwala don rama
sallar azahar.

Da kansa ya samo doguwar riga cikin closet d'ina ya samin sannan ya shimfida min
prayer mat nai salla.

Kafin na idar ya sauka k'asa wajan su Lami ya amsomin faten patato da su kayi
min.

Haka ya sani a gaba yana bani a baki,ba dan naji dad'in saba da bazan ciba sai
turo baki nake,abunda ke k'ara sashi dariya, sai da na cinye tass sannan ya b'allo
min magungunan ina tirjewa haka ya sani jikin sa da lallashi na samu na sha.

Sai bayan da ya dawo sallar la'asar sannan ya zo ya zauna kusa dani cike da
annuri ya rik'o hannayena yana magana k'asa k'asa "Sweety wai na ga kina ta had'e
rai ne ko jikin ne?".

kauda kaina nai ina k'ara turo bakin.

Sani yai sosai cikin jikin sa yana min magana masu dad'i da tambaya dalilin
fishin da nake, cikin shagwaba nace" ba kai ne ba".

"Ayya ni kuma my Happiness me nayi?".

" Kaine kana ganin banda lafiya amma ka ke ta wani farin ciki sam ma baka damu da
halin da nake ciki ba".

Wata irin Runguma yayi min cike da tsananin shauk'i murya can k'asa yace "Nahna
Khadeejah! Allah ya amsa addu'ar mu kukan mu ya k'are, Doctor ya tabbatar min kina
d'auke da ciki na wata biyu yanzu".

Da sauri nai baya daga jikin sa ina kallon sa kallon son tabbatarwa,d'age min
gira hak'oran sa duk bayyane cike da dariyar farin ciki yake k'ara tabbatar
min,wani farin ciki wanda ban san iya girmansa ba ya ziyarceni na rasa in da zansa
raina,kawai sai na sa hannayena na rufe fuskata ina sakin wani mirmishi me cike da
kunya.

Cikin dariya ya jawoni jikin sa,yana fad'in" ba maganar kunya fa Baby,bud'e


idonki mu cashe mu godewa Allah ".

Hawaye na zuba kan fuskata nace " Taso muyi sallah mu godewa Allah ".

Salla mukai raka'a biyu mun dad'e muna addu'o'i da nuna godiyar mu ga Allah tare
da fatan Allah ya saikeni lfy.

Account d'ina na duba naga uban kud'in da ke ciki nan da nan naiwa Yayan mu
Babba dake Sakkwato Transfer na kud'i dake yana aiki da gidan marayu nace don Allah
ya cire a siyawa marayu abunci sadaka.

Can yamma Sai ga Sweety tana takawa da k'yar ta shigo tare da sakin gud'a,
dariya nasa ina tashi daga kwancan da nake nace " Maman biyu sannu fa,kink'i daina
fita ko? Kina son nakuda ta kamaki a waje".

Da k'yar ta zauna tana dariya tace"To k'orafi dai ya k'are yau na dau hutu a
school sai kuma Allah ya rabamu,don haka nazo in dubaki da babyn mu wannan abun
farinci ai ba zama".

Bayan mun gaisa take k'ara taya ni murna ni kam dariya kawai nai, tace "a bani
abinci inci" nasa Lami ta kawo mata abincin,munata hira har sallar magriba sannan
Salis yazo ya d'auke ta.

**********
Wannan cikin nawa me laulayi ne matuk'a,kullum ina sallar asuba sai nai amai ba
kad'an ba,haka nan da zazzab'i nake kwana, ga tsirfa ba komai nake iya ci ba, duk
abunda aka dafa to haramiyata ne,sai dai furta nake sha wani sa'in yogurt kawai,ko
kunun aya, da dare kuwa kullum Tsire ne abinci na da Malta.

Allah sarki UK yanzu bashi da wani sukuni sai na kula dani,da zazzab'in na ya
hauni zai sani jikin sa ni ina bacci shi yana gadi na,duk kuwa abunda nace ina so
jikin sa na rawa zai nemo min shi,har mamakin kulawar da ya ke bani nake.

Allah yasa sau biyu kad'ai na ke da lecture a sati don haka school bata takura
ni,dana shiga nai musu lecture nake tahowa gida.

********
Cikin ikon Allah Sweety ta sauka y'a mace,murna kamar me waje na lokacin da
naje barka na ga Baby kamar little d'ita kasancewar y'ar kamar mamanta tai, kullum
muna zaryar gidan me jego har ranar suna aka rad'awa yarinya Rukayya, bisa
alk'awarin da Salis yai mata in ta haifi mace sunan Mamanta kuma sunan ta zai sa
mata, ai kuwa tace yarinya da little za'a rink'a kiranta, tunda daman sunan guda
ne,har raina nayi farin ciki Sweety tai mana Kara.

********
Ban fara samun gamsarshiyar lafiya ba sai da cikina ya shiga wata biyar.
Yanzu kam ba amai ba tsirfar cin abunci sai ma wani tsananin ci dana koya,da
na ci anjima zanji an min yasa.

B'angaran UK kam hak'uri ya sawa kansa,sabida Sam yanzu ban yarda dashi,naji ba
abunda na tsana irin sex sam ban jin wani feelings tare dani,da ya shiga damuwa
amma daya nemi shawarar doctor kan lamarin yace "ai wasu matan haka suke ko wane
ciki da salon da zai zo mata,sai yayi hakuri kawai".

Babu yanda ya iya haka ya hak'ura ya zuba min ido, nasan sarai yana damuwa amma
ya zan yi? Ko na tursasa kaina banjin wani dad'i Sam,amma dai a haka nake d'an
takura kaina wani sa'in in barshi ya rage zafi.
**********
Duk siyayyar haihuwa komai sabo mukai don tunda naga na rufa shekara bayan
rasuwar little ban samu ciki ba duk na fidda komai nata na bayar,sannan gashi a
wannan karan scanning ya nuna namiji zan haifa,amma dake ba tabbas bane hakan ya
kasance yasa ban wani karkata ga iya kayan mazan ba.

Lokacin da cikina ya shiga wata tara duk wani shiri mun gama ranar kawai muke
jira, kullum bana rabo da tofa ayoyin Qur'ani cikin ruwa ina sha, sannan addu'oin
dake sassauta ciwon nak'uda,don ban tab'a manta uwar wahalar da nasha haihuwar
little, haka daga gida ko yaushe Aunty Hafsah itama cikin aiko min y'an dabaru take
na neman sassaucin nak'uda.

_Ta ku ce_
~Y'ar mutan Ja'oji~🙋
🍡🍡🍡🍡🍡🍡
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*'YAN* *ARABIC*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🍡🍡🍡🍡🍡🍡

*NA*
*LAYUZA* *KABIR* *ADAM*

_DEDICATED_ _TO_ _ALL_


_ARABIC_ / _ISLAMIC_ _STUDENTS_
📚📚📚📚📚📚📚📚

*ZAMANI* *WRITERS* *ASSOCIATION*


📝
_We_ _are_ _here_ _to_ _educate_ , _motivate_ ,and _entertain_ _our_ _Readers_

_*Alhamdulillah komai yai farko zai yi k'arshe,yau dai na huta da k'orafin Fan's
dana Hussain 80k sarkin posting kan rashin typing,wannan sadaukarwar taka ce kai da
dukkan fan's*_❤❤❤❤

_Mu had'u cikin sabbin novels d'ina masu fitowa insha Allah_

👉🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚

5⃣8⃣6⃣0⃣
6⃣0⃣ 5⃣8⃣ 5⃣8⃣6⃣0⃣
5⃣8⃣➡
5⃣8⃣6⃣0⃣
5⃣8⃣6⃣0⃣ 6⃣0⃣
Ranar da d'alibai suka gama exam zasu tafi hutun sati shida na second semester nai
aikin exam na gaji matuk'a, don duk exams d'in d'alibai dake hannu da sai da nai
mark na kai su ga Exams officer, a gajiye tik'is na tuk'o mota ta zuwa gida,lokacin
har an fara kiran sallar magriba, wanka nai tare da d'auro alwala nai sallah kiran
wayar kitchen ne nace su lami su shirya min dining ban jin zan iya wani aiki yau
don baya na a rik'e yake,don haka na zauna k'asan cafet tare da mimmik'e k'afafu
na,idona lumshe suke ina jin jikin nawa sam ba dad'i, sautin muryar sa na jiyo
kamar yanda ya saba in dai ya dawo bai same ni falon k'asa ba to tun daga step
d'in farko zai fara kirana har sai na fito na tare shi,yau kam ban jin zan iya
tashi don haka mirmishi kawai nake na zubawa k'ofa ido, da saurin sa ya turo k'ofar
yana fad'in "wai ina my angle d'in ta mak'ale ne."

Tsayawa yayi yana kallona fuskar shi cike da tausayi don da ganin zaman da nai
ya san bana dad'i bane,jiki sanyaye ya k'araso ya zauna dirshen gabana,y'ar dariya
bai da fad'in "oga Wannan zaman y'an borin fa?."

Yak'e kawai yayi da fad'in " ya dai na ganki zaune haka ko jikin ne?."

Rik'o hannun sa nai da fad'in "gajiya ce kawai wlh yau nai aiki over matse
kaina nai na kammala duk aikin dake gabana".

A hankali ya shiga matsa min k'afa da fad'in" Ayya sannu kinji Baby na,kinga
shi yasa nace miki da na iya Islamic duk ni zan rink'a miki makin exams wlh ki
huta,to ko na karb'a ban San me zan maka ba."

"Hhhhhmmm ina godiya da kulawa,amma yunwa nake ji na kasa sauka ki dining d'in
na shirya."

Da sauri ya mik'e yana rage kayan jikin sa,sannan ya sauka k'asa, kayan abunci ya
hayo dasu suka saman har d'aki, da sauri sauri ya sakamin tuwon da miyar danyan
kub'ewa,ai kuwa ba sauraro na fara zubawa cikina,sai da na cinye malmala biyu
sannan na sha kunun aya nai hamdala.
Sai a lokacin ya fito daga wanka tare da alwalar sallar isha'i, kayan ya had'a ya
matsar gefe, da nufin in ya dawo salla shima ya ci anan.

Bayan fitar sa masallaci na yunk'ura da k'yar nai toilet don d'aura alwala
nima,amma sai naga bakon yanayi tare dani,gabana ne ya fad'i don alamun nak'uda na
kusa kenan, tsarki kawai nai na fito ruwan zamzam d'ina na d'auka na k'ara tofa
wasu addu'o'in na sha, duk sai naji jikina ya mutu har hawaye ya fara zubomin don
na san ciwon nak'uda bai min da wasa ba.

Ina nan zaune cike da tunani kala kala ya dawo,ganin yanayi duk sai ya damu
yace"Ko dai baki da lafiya ne muje asibiti?. "

Girgiza kaina nai ina k'ok'arin b'oye damuwa ta nace"A'a nace ma fa gajiya ne
kawai,kaci abincin sai ka min tausa zan ji dad'i. "

Cikin hanzari ya jawo kulan abincin ya zuba ya fara ci,sama sama ya ci ya


tashi, dawowa yai ya d'aga ni zuwa gadon ya kwantar dani kamar yanda ya saba
matsamin jiki haka yai ta min massaging d'in, ai kuwa naji dad'i har wani lumshe
ido nake, a haka bacci me dad'i yai gaba dani,bai bar yi ba sai da ya tabbatar nai
nisa cikin baccin sannan ya tashi ya gyara d'akin ya sauka da duk kwanikan, sannan
ya had'o min kayan shayin da yasan duk dare ina farkawa sha.

Ya dad'e zaune yana kallon yanda nake bacci tabbas duk wanda ya kalleni ya san ba
wai jin dad'in baccin nake ba,duk tausayi ne ya k'ara kamashi, yana k'yamar halin
daya aikata da a baya, ina cikin irin wannan halin amma ya rink'a wulak'antani da
hantara ta,duk irin wannan wahalar nasha a baya amma babu mai taimaka min,wani
hawayen tarin nadama ne suka gangaro mai ya goge tare da fad'in "Allah ka yafe min,
ka amsa tubana,Allah ka raba wannan baiwa taka da cikin nan lafiya."

*************
Misalin k'arfe sha biyu na farka don jin wani azababban fitsari da k'yar na k'arasa
toilet nayi, ina dawowa ko minti biyar banyi ba naji wani,Cikin k'osawa na k'ara
zuwa nai,amma ina dawowa zan kwanta naji bayana ya rik'e k'am,duk dabarar da zanyi
in kwanta kwanciya ta gagara,ga bacci sosai a idona,na rasa ya zanyi kawai sai nasa
kuka,cikin shagwab'a na fara bubbuga bayan sa ina kiran sa, da saurin ya tashi yana
kunna hasken d'akin yace"Subhanallah, meya faru Nahna?."

Kuka sosai na sanya mai kuma nak'i magana,gaba d'aya rikicewa yayi ya rik'oni
yana fad'in "pls fad'a min mene ne don Allah? Ko baki da lafiya?."

Gyad'a mai kai nai da sauri ya sauka a kan gadon ya sami jallabiya yasaka,nima
kaya ya d'auko ya samin inata kuka don sosai naji bayana da mara sun rik'e min,
kuma ma dai harda shagwab'a naga yanda jikinsa ke rawa duk gigice( k'ara kiyi
k'ara'i Khadeejah ai a fari biki haka ba😜)
Bai wani tsaya d'aukan wani abuba ya sauko dani k'asa, da sauri ya fita yaje ya
fito da mota yai parking d'in ta kusa kusa,ciccib'oni yai cikin azama ya sani a
motar,muka fice.

**********
Doctor na dubani tace haihuwa ce amma dai da saura,nan suka bamu gado,kad'an
kad'an ciwon ke lafawa amma in ya motsa ba labari,nace UK ya kira Abba ko Aunty
murja amma yace Aa bai buk'atar kowa ya kula dani bayan shi.

Awa uku da zuwan mu asibitin nak'uda ta kankama dole likitoci suka koreshi daga
labour room d'in, fitar sa da minti biyar Allah ya rabani da cikin, kukan jinjiri
ne kawai ya ankarar dashi na sauka,da sauri ya k'araso bakin k'ofar yana kasa
kunne,ai kuwa cikin kunnan sa yaji doctor tace"Alhamdulillah ta sauka."

Da sauri ya juya yana d'aga hannayensa sama yace "Alhamdulillah Alhamdulillah


Alhamdulillah"

Nurse ta bud'e k'ofa ta fito tana mai albishir d'in samin Baby boy,cikin
tsananin farin ciki yace "Kina da babbar kyauta na wannan albishir d'in, kuyi
amfani da komai naku, a samin a bill don bamu zo da komai ba".

Juyawa tai ciki tana dariyar ganin irin rikicewar da yayi.

Ni kam ina haihuwa naji kamar an zare min wani katon dutse sakayau naji na koma
sai dai rashin k'arfin jiki.

Bayan sun Shiryamu ni da Baby aka kaimu d'akin hutu, zuwa lokacin har an kira
asuba, a masallaci asibitin yai salla ya dad'e a sujjada yana nuna godiyar sa ga
Allah.
Har lokacin bai kira kowa ya fad'a mai ba, yana son yin surprise d'in su.

K'arfe bakwai likitocin suka sallamemu bayan an gama tabbatar da bamu da wata
matsala ni da Baby boy d'in, duk bill d'in da aka cajeshi transfer yai musu haka
itama nurse d'in da tai mai albishir ya tura mata kyautar 20k

Yana d'auke da Babyn muka k'arasa mota ya bud'e min na shiga sannan ya dora min
babyn a cinyata ya zagaya ya shiga,bakin nan nashi kamar gonar audiga haka muka
tafi gida yana ta samin albarka tare da min sannu,nikam mirmishi kawai nake ina
rungume yarona a jikina wani sukuni na ratsani.

Sai da muka kusa k'arasa wa gida ya dau waya ya kira Aunty murjah Tana d'auka
yace "Aunty don Allah shigi gidan mu."

Bai tsaya jin me zata ce ba ya katse wayar, ita kuwa kallon Abba tai da take
had'awa break fast tace"To Khadeejah ina ga haihuwa tazo don Daddy ne kirana wai
inje".

Da sauri Abba yace "Maza jeki ina jin nak'uda take".

Mayafi kawai ta d'auko a d'aki ta fito tana shiga muma motar mu na shigowa, da
sauri ta juyo ganin mun shigo a mota,

Sam bata gane me ke faruwa ba don haka ta k'araso bakin motar dai dai lokacin ya
bud'e ya fito cikin dariya yake fad'in "Aunty kinyi sabon ango fa".

Bata gama dawowa daga mamakin furucin sa ba taga na bud'e mirfin motar ina mik'a
Mata jinjirin, da sauri ta karb'eshi cikin mamaki tace " ya akai haka Daddy?."

Dariya sosai yake yace "muje daga ciki Aunty kisha labari."

Ba musu ta juya muka wuce ciki.

A falo muka zauna Aunty nata jero tambayoyi,cikin tsananin murna ya sanar da ita
komai,ai kuwa Aunty me zatai in ba hamdala ba,ta zubawa yaron ido tana dariya tace
"masha Allah wannan karon dai Daddy Khadeejah tama wayo,don sak wannan fuskar ta
ta ce".

Turo baki yai kamar wani k'aramin yaro yace" Eh wlh Aunty nima haka na gani, amma
ai dai fatata ya d'auko ".

Dariya mukai gaba d'aya Aunty ta tashi da sauri ta mik'a mai yaron tace" Bari
maza a had'a ruwa me zafi ki gasa jikin ki,sannan a samar miki abunci ki ci".

Kai tsaye ta wuce Babban kitchen inda ta tadda su lami nata k'ok'arin gyarawa da
shirya min duk kayan da zan yi girkin break fast suma basu san wainar da ake toya
ba,sai da ta fad'a musu,gud'a Lami ta saki da fad'in "masha Allah kaga haihuwa me
dad'i, to bari maza a dafa mata abu me nauyi ta ci".

D'aki na guda dake k'asa wanda nai jegon Little anan ma wannan karon muka had'a
duk kayan mu na haihuwa don haka muka yada zango anan.
Ruwa me zafi Aunty ta had'a min na gasa jikina na zauna a ciki kasancewar an min
d'inki, na fito na shirya tsaf dani cikin riga da zani na atamfa,kafin nan Aunty ta
sanar da duk Wanda ya dace ta sanarwa.

Shayi me kauri ta had'a min nasha kafin abunci ya kammala, shi kuwa Baby boy an
canja mai kaya zuwa na sanyi masu kyau.

*********
Zuwa wani lokaci gida ya cika da y'an uwa da abokan arzik'i y'an barka.

Ni kam bacci ne sosai ya d'auke ni don haka suka dawo falo da Jinjirin suka
barni.

Wannan haihuwar ma Goggo ce tazo min daga Gida sakkwato take kula damu,Aunty
Hafsah da Aunty Amrah kullum sai dai suzo su yini su tafi.

Bayan haihuwa da kwana uk UK ya sameni kan maganar sunan da nake son a sawa
yaro,nace " zab'i ai na gareka Ogah".

Cikin jin dad'i yace"Za muyiwa Baffa takwara hakan yayi?."

Jim nai cike da farin ciki bace"Um yayi amma ni a son raina kafin nayiwa
Baffana takwara sai na fara yiwa Yaya Haroon."

Dariya yayi tare da fad'in "Yanzu dai kin fi son ayiwa yaya kenan?."

Daga mai kai nai cike da farin ciki, ai kuwa take ya d'auki yaron yamai hud'uba
da Haroon.

Har k'arshen zuciyata naji wannan dad'in don fatana kullum kenan.

Nan da nan dangi kowa ya san sunan yaro Haroon,yaya ma yai murna sosai da samun
takwara,ranar da mukai kwana biyar yayo nana akwati cike da kaya na takwaran sa.

Ana gobe suna kuwa gida ya cika mak'il da y'an suna,mutanan katsina dana
sakkwato.

Wannan karon ma Abba yayi hidima matuk'a da gaske, ranar suna an yi komai cikin
tsari da wadata, yaro Haroon zamu rink'a kiran sa da Raees.

Bayan kwana biyu da suna gida yai dif kowa ya koma in da ya fito daga ni sai
Goggo dake ka damu.

wannan karon sati biyu biki ya d'auke min don haka ba sauk'i na shiga gyara kaina
don ni kaina na san nai kewar mijina, yanzu ni da kaina nake ji a jikina ina
buk'atar sa.

Ranar da nai sati uku da haihuwa Ranar Alhamis da yamma Goggo taje gidan yaya
Usaman dubashi bai jin dad'i sai ni kad'ai a gidan ina zaune a falo d'auke da Raees
ina bashi nono UK ya shigo, muna had'a ido muka sakarwa juna mirmishi ya k'araso
kusa dani ya zauna jikin mu na had'uwa hannu yasa yanawa Raees wasa.

A hankali nace "Sannu da zuwa."

Dagowa yai yana lumshe ido yace" yawwa sannu princess, wannan shigar fa? Ana
tsokano mutum fa wlh, kuma dana matso ace jego ake".

Wata y'ar dariya nai me cike da k'issa nace"Ai jego ya k'are oga kawai muna jira
mu k'ara murmurewa ne".

D'an zaro ido yai da fad'in "don Allah da gaske?."

Dage mai gira nai ina y'ar dariya, jawoni jikin sa yai yana k'asa da murya yace
"Plsss princess a taimaka min wlh marata ciwo take, daurewa kawai nake yi fa."

Komawa serious nai nace"Sati uku fa da haihuwa Honey bamu koma normal ba kuma
kasan an min d'inki ."

"Eyya my wife kefa kika fad'a min tun rannan d'inkin ya warke rass, Don Allah ko
kad'an ne a taimaka min."

Ban aune ba naji bakin sa cikin nawa,nai k'ok'arin janyewa ko don kasancewar a
falo muke amma ya k'i bani wannan damar,kusan minti biyar naji abun nasa na son
mik'awa cikin hikima na janye ina fad'in "Falo fa muke don Allah in wani ya zo fa."

Idonsa da suka fara yin ja ya lumshe ya na sauke ajiyar zuciya,hannu yasa ya


d'aga Raees a kan cinyata ya wuce gaba dashi yana fad'in "Zoki had'a min ruwan
wanka."

Jimmm nai can dai na mik'e nabi bayan sa zuwa saman.

Ina shiga na tadda har ya kwantar da yaron ya fara k'ok'arin cire kayan sa, ban
tankashi ba na wuce toilet d'in,ruwan wankan na had'a mai sannan na d'auko towel na
fito lokacin ya rage daga shi sai boxer mik'a mishi towel d'in nai ina alaman ya
karb'a ya d'aura, hannun ya mik'o kamar zai amsa kawai naji ya jawoni jikin sa,a
tare muka sauke wata ajiyar zuciya a lokacin da k'irjinmu suka had'e waje guda,wasu
salo masu rikita jiki da zuciya ya shiga aika min wanda sukai sanadiyar tsumar dani
na shiga maida martani cikin zak'uwa da d'oki, Sam na manta condition d'in da nake
don bukace nake da mijina,mun manta mun shagala mun lula can wata duniya bamu gane
komai sai kanmu kawai,bamu dawo hankalin mu sai da komai ya lafa nutsuwa ta zo
mana,asan nan na tuna cewa fa jego nake duka satina uku da haihuwa,wani takaici ne
ya kamani sai ji nai hawaye na zubo min,kaina da ke hannun sa ya bada damar zubar
hawayen a tsintsiyar hannun nasa, d'ago guskata yai yana fad'in "kuka? Kuka kikeyi
Nahna?."
Wannan maganar tasa na saki sautin kukana,kamar wadda akaiwa wani laifin.
Da sauri ya tashi zaune yana rarrashina damin kalamai masu dad'i da nunamin
illar da kin amincewa dashi zata jawo mana,da haka dai na samu na hadiye kukan na
tashi zuwa toilet nai wanka,b'angaran kayana dake d'akin naje na d'auko wata
doguwar rigar atamfa na saka,duk yana kwance yana kallona, ni kam fuskata d'aure
tamau na k'araso gaban gadon na d'auki Raees dake bacci, ban ce mai kala ba na juya
na fice.

Wani mirmishi ya saki yana fad'in "Oh! Mata masu duniya,jimin yarinyar nan yanda
ta zak'e lokacin da take neman dad'i sai yanzu kuma ta gamsu take ta wani tsare
gira."

Mik'ewa yai fuskar sa cike da annuri ya shige toilet shima yai wankan tare da
d'auro alwala don lokacin salla ya kusa."

Ni kam jiki sanyaye na sauko k'asa, ina shiga d'aki na samu Goggo har ta dawo tana
tsaye ta d'auro alwala, duk duburburcewa nai na fara fad'in "Goggo kin dawo? Sannu
da zuwa ya jikin yaya Usman d'in."
Cikin nuna bata San me nake ba tace "Eh na dawo tun d'azu ai,jikin nasa da
sauk'i."

"Ina sama ina gyara sif ai ban ji shigowar ki ba ai."

Ita dai Goggo bata tanka min ba ta tada sallarta don ta ga alamun rashin gaskiya
kiri kiri tare dani.

Nima zama nai na bawa Raees nono don yana ta motsin nema, sai da na tabbatar ya
koshi sannan na ajiye shi naje nai sallar nima.

*********
Satin mu biyar cif Goggo ta tafi, don taga rawar k'afar UK tai yawa,ni ni kam tun
ranar nan ban k'ara yarda mun keb'e ba,don sai na k'ara gyara sosai gashi ina jin
tsoron d'inkin da akamin ance in bai gama warkewa ba aka matsa da Abu yana bada
matsala duk da ni nawa ya warke rass amma dai sai na k'ara takatsantsan.

Yau kam tunda Ya dawo da rawar jiki ya dawo Ina kallon na basar, duk kayan
buk'atar mu ya maidasu sama ina jinsa yana ta fad'in zaman k'asa ya k'are ai tunda
Goggo ta tafi,ko tanka mishi banba don yau sarauta nake ji,ko wanka ma shi yaiwa
Raees ya mai shirin bacci ya sashi cikin gadon sa,duk ina zaune ina kallon TV,
shima sai dai ya gama shiryawa sannan ya zo gare ni"Madam yau mulkin ne ya motsa
ne? Basarwa nai kamar banji shi ba sai da ya k'ara maimaitawa sannan na yatsine
fuska da fad'in "me ka gani fa?."

Mirmishi yai kawai ya kashe kayan kallon tare da d'auka na cak bai dire ni sai
cikin Bathtub daya cika da ruwa, y'ar k'ara na saki da fad'in " ni ban son wankan
ka cire ni."

Bai saurareni ba ya raba ni da duk kayan jikina, tass ya wanke ni yana yi ya


jagwagwalani,tun daga toilet zancan ya fara canjawa duk yanda naso basarwa abun
yaci tura haka na mik'a wuya kawai.

**********
Tun daka lokacin kuma sai muka zama mannau d'in junan mu ko yaushe aikin mu
faranta ran junan mu,ni yanzu har mamakin kaina nake yanda wani sa'in har nake fin
UK zumudi da d'oki kan harka,don shi wani lokacin in yai wasannin sama dani sai ya
gamsu amma ni sai anje magaryar tuk'ewa nake tsaida birki,shi kansa yanzu tsokana
ta yake wai na zama inji ban gajiya da aiki,daya fad'i haka sai dai in murgud'e
baki in ce "kai ka koya min ba fika iyawa"."

Watana hud'u da haihuwa hutun dana d'auka ya k'are, na koma Lecture, duk sanda
nake da lecture gida nake barin Raees wajan Aunty murja don ya saba da ita
sosai,tunda ko yaushe yana gidan dama.

Wani irin so da UK ke nunawa yaron har tsoro yake ban araina nake addu'ar Allah
yasa shima ba rasuwa zai ba, har fad'a nake mai kan ya rage nuna Wannan soyayyar da
yake mai yayan yanzu ba'a nuna musu irin wannan son a zahiru sai su tab'are.
duk sanda na fad'i haka kicin kicin yake da fuska yace" Haihuwar da sai da yaita
zubda hawaye yana magiya ga Allah sannan ya k'ara bashi kuma shine bazai so abunsa
ba."
Shiru nake mai in naji ya fara wannan mitar.

Shi kanshi yaron yanzu bai yarda da kowa in Ubansa na gida yata mik'a mai hannu
kenan yana tsalle,yai ta gwarancin sa wai ya san Babansa.

********
Watan Raees biyar cif na fara jin canji tare dani don wata kasala da yawon
kwad'ayi ke damuna, ban kawo komai cikin raina ba,sai da zazzab'i ya sakoni gaba
sannan naje ganin likita, gwajin farko aka tabbatar ciki gareni har na wata uku,a
tsorace na kalli doctor d'in don ta tabbatar min da abunda kunne na yaji,mik'omin
result d'in tai tana min congratulation, jiki ba k'arfi na k'arb'a na taho gida
tuk'in ma a sanyaye na ke yinsa.

lokacin da aka kawomin Raees daga gun Aunty murja tausayin sa ne ya kamani
ganin duka yaron watansa biyar gani da cikin wata uku kenan ko shekara bai cika ba
za'a mai k'ani ko k'anwa,shiru nai tare da zabga uban tagumi duk na rasa ma wane
tunanin zanyi.

****Da dare da UK ya dawo bayan yaci abunci yake tambaya ta me da naje asibiti me
suka ce min,result d'in na mik'a mai kawai,kalla yai sosai yace "ban fahimta ba, yi
min bayani."

K'walla cike da idona nace "ka duba sosai wai fa haka suka ce ciki gareni har
wata uku."

Da sauri ya kalleni yana fad'in "Wai da gaske ko wasa?."

Hawaye na yaci gaba da zuba nace "wane wasa wlh da gaske,kaga kenan tun Raees na
da wata biyu ka jibga min aiki."

Wata irin dariya naga yana yi har da nunani yama kasa magana k'arshe kawai sai
ji nai ya rungumoni tsamtsan jikin sa yana fad'in "Alhamdulillah, Allah kai ne abun
godiya,cikin shekara guda zaka min kyauta Yaya biyu,Na gode My Khady na gode
kinji,daman ni tunda na ga kin gyare a son abun nan nasan kin k'aro k'ok'ari da
fasaha baza kiyi sanya wajan cafewa ba."

Tureshi na shiga yi tare da kukan shagwab'a, shi kam dariyar sa kawai yake kwasa
yana ta tsokanata,harda cewa"kin San me?Wlh rannan danaga Hafeez wani abokina da
mukai school tare da yaran sa maza guda uku duk Kansu d'aya nake tambayar sa y'an
uku ne yace min a'a kawai babu tazara ne tsakanin haihuwar su,wlh sun birgeni kinga
nima in Allah ya taimake ni haka zaki rink'a min."

K'ok'arin mik'ewa na farayi daga jikin sa ya rik'e kam da cewa"Fad'a min meye
matsalar ki don Allah, wai haihuwan ne baki so kome?."

"A'a ni bance ban son haihuwa ba,wa zai ce bai son haihuwa kawai ni tausayin
yarona nake ji."

Serious ya koma ya gyaramin zama sosai yace "Kullum ke kike fad'a min Allah baya
d'aurawa bawa abunda bazai iya ba,kuma kin sani yanda muka rink'a rok'on Allah
kafin haihuwar Raees sai da little ta shekara uku da rasuwa muka sami Raees yanzu
bakya ganin babbar baiwa ce ya mana ya share hawayen mu ya bamu ya k'ara mana da
wuri, sannan dukkan wasu dalilai da suke sa ayi tsarin iyali a musulunci ko a
likitance babu dalilin da zai sa mu muyi shi, ke kika fad'a min musulunci ya yarda
ayi tsarin iyali ne don tsira da lafiyar uwa ko yaro, ko gudun lalacewar tarbiyar
yara ta rashin samun uwa ta gari ko uba na gari, rashin abun kula da cin sauran
yaran da aka haifa balle a sake haifo wani,tsoro firgici na rashin tsaron rayuka
duka way'annan dalilan sharia ta bada damar a jinkirta haihuwa har sai zuk'ata sun
nutsu,kuma a hakan ma in Allah ya kawo a k'arb'a ayi mishi godiya,to mu gashi Allah
ya mana arzikin da zamu iya kula da Yaya sama da d'ari in ya bamu,sannan muna da
nagartar da zamu tarbiyantar dasu al'umma ta amfana, muna cikin nutsuwar tsaro da
kwanciyar hankali,uwa uba ke da Allah ya bawa kina da isashshiyar lafiya, sannan
Raees Allah ya bashi wadatacciyar lafiya wannan cikin bazai shafi lafiyar sa ba,ki
kwantar da hankalin ki kinji. "

Share hawayena nai nace "Na gode Mijina da wannan tunatarwar,dama ajizanci ne
na d'an Adam yasa na damu, na gode Allah da ya bani miji me tunasar dani."

"A'a madam wannan duk cikin koyarwar ki gare ni ne,dama kuma ai tunasarwa mumini
kawai take amfanarwa ,Allah ya bamu zuri'a D'ayyiba."

********
Haka naci gaba da rainan cikina cikin sassaucin ubangiji, b'angaran Raees banda
matsala don yanzu ya fara cin abunci kuma muna bashi magungunan sa kuzari duk da
kasancewar sa me kuzarin dama.

Ba kowa ya lura da cikin ba sai da ya fara fitowa, masu min dariya nayi masu
barka na yi.

Ban yaye Raees ba sai dai cikina yayi wata bakwai lokacin shi yana da wata
Tara,kuma bai wani sami matsala ba ko kad'an, don yana samun kulawa sosai,ko yaushe
daga safiya zuwa yamma duk wajan su Aunty Murja yake yini sai Abbansa ya dawo ya ke
shiga ya karb'o shi.

________________
Watan cikina tara da y'an kwanaki Allah ya sauke ni lafiya,Wannan karon ma namiji
Allah ya bani,an kuma don shi d'in ma kamannina sak ya d'auko har bak'ar fatata.

Murna wajan UK kamar wannan karon aka tab'a mai haihuwar, hidima sosai ya shiga
yi damu,haka ma Abba yai rawar gani daga gidan mu ma kamar ko yaushe y'an uwana sun
yi min iya k'arfin su,yaro yaci Sunan Abba wato Usman ana kiran sa da Nurain, an yi
taron suna an watse cikin murna da farin ciki.

Haka naci gaba da rainan yarana cikin kulawa da k'aunar su,sun taso gwanin
sha'awa musamman dake Nurain me jikin girma ne irin na Abbansa sai nan da nan watan
sa uku ya fara zama wanda a lokacin kuma Raees ya ke gudun sa ko ina, masha Allah.

**********
Haka rayuwa taci gaba da gudana mana cikin Wadata da annushuwa,ban nemi komai na
rasa ba na rayuwa,mijina ya na matuk'ar sona da yayana kullum burin sa ya faranta
ranmu,in ya dawo duka lokacin sa yake bawa yaransa har sai ya shiryasu sunyi bacci
sannan ya dawo gareni kuma.

**********
Watan Nurain Goma cif na yaye shi sabida tafiyar aikin hajji da ta yaso mana,ni da
UK da Abba da Aunty Murjah, nima na tattara kud'ad'ena na biyawa yayana abin
alfaharu na,don banda wani abu da zan sakawa yaya Haroon dashi a duniya yayi min
komai na rayuwa,lokacin dana sanar dashi har dashi tafiyar nan farin ciki yasa har
k'walla yayi,nan ya kira y'an uwa ya shiga sanar dasu,kowa addu'a yai tamin da sa
albarka,ni kam a raina nake fad'in "To in ban yiwa yaya ba wa zanwa? Kud'in da suke
account d'ina sunyi yawa matuk'a, ga Wanda UK ke samin ga kud'in albashina,ban
siyan ko abun k'wandala a ciki kullum mijina cikin yimin hidima yake."

Zulk'ida na kamawa mune jirgi na uku zuwa k'asar Saudi,kuka rurus nake lokacin da
na ganni cikin masallacin manzan Allah, nai godiya gare shi da ni'imar da yayi min.

Munyi aikin hajjinmu cikin kula da shauki,sosai na dage da yiwa iyayena addu'ar
samun rahmar Allah a wannan waje me girman daraja da nake.

Bayan salla babba da kwana goma muka dawo gida Nigeria cike da kewar k'asa me
tsarki.

*************
Dawowar mu da ga saudiya da wata biyu wani cikin ya bayyana gareni, godiya nai
ga Allah daya bani wannan n'iima,lokacin Nurain yana da shekara da wata
biyu,tafiyar sa ko ina,UK ma murna ya sha ya gode Allah.

~Bayan shekara biyar~👇🏼


___________________
Lokacin muna da Yaya Biyar Raees,Nurain,Yusuf (Baffa) Umar(junior) sai k'aramar su
Little(Ruk'ayya)

Lokacin Raees na da shekara bakwai,Nurain shida,Baffa,Hud'u junior biyu sai Auta


me wata takwas.

Yarana Masha Allah Gwanin sha'awa kowa ya kallesu sai ya k'ara kuma ya tanka,don
haka kullum cikin tofesu da addu'a na ke,ba dare ba rana,sun taso cikin Tarbiya da
girmama junan su,haka jama'ar gari kowa Aunty kowa uncle, ko basu San mutum ba in
sunsan ya girmesu basa fad'ar sunan shi, haka tsakanin su suke b'oyewa junan su
suna.

Yare uku dam su ke ji,larabci English Hausa, duk Wanda suke yi baza kace suna jin
wani yaran bayan sa ba,don makarantar ma da suke boko da Arabic ce, ban yarda sun
karkata da iya boko ba,don haka Qur'an ma hadda sukeyi duk da karancin shekarun
su,don haka suka zamo taurari ko cikin yaran family.kuma kula da yarana Sam bai
shafi aikin koyarwa ta ba,komai ina bashi lokacin sa da yin komai cikin tsari.

_______________
Duk ran jumma'a Abban su sha biyu yake tashi aiki,suma kuma sha biyun suke dawowa
daga makaranta don haka suna dawowa kowa yake shiryawa su tafi masallaci, kafin su
dawo na shirya abunci don tare muke cin abinci da yaranmu in har suna gida.

Yau ma na shirya tsaf cikin riga da zani na atamfa wanda sukai min das a jiki
suka amsheni, Little ma na shiryata cikin kwalliyar ta gwanin sha'awa na saka ta
cikin keken ta don ta barni nai komai a nutse.

Ina tsugunne ina jera cups dintda zamuyi amfani dasu na fara jiyo
hayaniya,mirmishi nai na san sun dawo,sallamar Baffa ce ta katseni ya shigo cikin
nutsuwa "Assalamu Alaiki ya ummy"

Kafin na amsa sauran ma suka shigo duk da sallama kamar yanda yayi,amsa musu
nake fuskata d'auke da mirmishi ina binsu da kallon sha'awa don dukkansu sanye
suke da shadda fara tas babbar riga da y'ar ciki,ga hulunan su zanna akawunan
su,duk k'ok'arin cire rigunan suke nace "Wai ina Abban na ganku ku kad'ai?."

Junior ne yace"Yana tsaye da Baba me gadi."

Kafin nace wani abu ya shigo shima cikin irin shigar yaran tsaf da babbar riga,
"Ga Abba ya shigo madam ni ake jira ko?".

Fakar idon yaran nai na kashe mai ido guda tare da k'yasa mai alamar yayi
kyau,dariya yayi kawai yana amsawa a sirrance.

Bajewa mukai muna kwasar garar girki baka jin komai sa k'arar k'ashi😜, bayan mun
gama kowa yai hamdala sannan Raees ya taimaka min na gyara wajan,shi kuwa oga ya
d'auki little sai wasa suke mata shi da junior, Baffa da Nurain kuma suna harhada
kayan su da suka cire suna ninkewa.

Bayan duk mun dawo mun zauna hira muke da yaran mu wanda a haka ne muke gane
damuwar moka da kuma burin da kowa ke dashi,Baffa ne yai gyaran murya da fad'in"
Abba ni inna girma fa lauya nake son zama."

Da sauri Nurain yace"A'a wallahi na riga ka ko yaya."

Ya k'arasa da kallon Raees,shi kam dariya yayi da d'aga musu kai,nima dariyar nai
nace"Kullum dai sai anyi wannan muhawarar fatana kullum Allah ya baku ilimi me
amfani wanda Alumma zasu amfana dashi musulunci yayi alfahari da Ku."

Amsawa sukai da amin, UK ya juya ga Junior yana fad'in "Namesake fa mema kace
kana son zama inka girma?."

Cikin murna da zak'uwa yace"Abba ni Sarki zan zama."

Dariya mukasa gaba d'ayan mu don daman mun San k'arshen zancan nashi.

_*Alhamdulillahil lazi bi ni'imatihi tatummassalihin*_

_*Anan na kawo k'arshen wannan littafi nawa me suna 'YAN ARABIC abunda nai dai dai
a ciki Allah ya bani ladan sa,abunda na kuskure ina rok'on ubangiji ya yafe min*_

_*Dukkan abunda kuka ga nai dai dai wannan daga Allah ne,Abunda kuka ga kuskure
wannan daga gareni ne,kumin afuwa Ajizanci ne irin na d'an Adam*_🙏🙏

_*Na gode da jimirin bina da kukayi tsawon lokaci cikin wannan rubutu na gode
muku ba adadi kuma masoyana ina musu fatan Alkairi a duk inda suke a duniya,nima
ina sonku sama da yanda kuke sona,ana tare har abada*_🤝🤝🤝

~Ku kasance dani cikin littattafaina masu fitowa~

*MAKOMAR KOWA*
*'YA'YANA MATA SUNE SANYIN IDANIYATA*

~Domin k'orafi,gyara ko shawara ga number ta~👇🏼


*07067270055*

*25/9/2019*

You might also like