Professional Documents
Culture Documents
Tarihin Zuriyar Sharif Yahya Na-Tsakuwa Tare Da Yan' Uwansa
Tarihin Zuriyar Sharif Yahya Na-Tsakuwa Tare Da Yan' Uwansa
Tarihin Zuriyar Sharif Yahya Na-Tsakuwa Tare Da Yan' Uwansa
2022
Hamza Garba
Abdullahi Al-
Hassani
08095022295
7/13/2022
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
ISBN: 978-978-989-373-7
Phone number:
08095022295
09030333353
1
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
TARIHIN SHARIFAI
NA
ZURIYAR
SHARIF YAHYA NA-TSAKUWA
TARE DA YAN’UWANSA
NA
2
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
3
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
4
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
5
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
6
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
7
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
SASHI NA UKU
Daukacin zuriyar Aminatu (Uwar Na-Hakuri) yar’ Usman dan Ibrahim dan
Abubakar
1. Gidan sharifiya Maryam……………………………………………..…….……………257
(1) Bangaren Sharif Muhammad Duna………………………………………………257
8
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sadaukarwa
Bisa yarjewa ta Allah madaukakin Sarki, Na sadaukar da wannan littafi ga
kafatanin jikokan Annabi tare da masoyansa (SAW).
9
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
A karshe, ina rokon Allah da ya datar da wannan aiki izuwa mafi kolkoluwar
daraja, ya daukaka shi sannan kuma yasa ya amfane mu a duniya da kuma
lahira.
Jawabin Godiya
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki wanda ya bani ikon
rubuta wannan littafi da ya kunshi tarihin Sharifai tare da tarihin zuriyar
gidan Sharif Yahya Na-Tsakuwa hadi da yan’ uwansa dake zaune a
unguwar Dukawa cikin kwaryar birnin Jahar Kano Najeriya. Hakika, wannan
aiki yarjewa ce ta Allah (SWT) kuma muna Addu’ar Allah isa wannan aiki ya
amfanar da al’umma baki daya, Amin.
Bayan haka, yazama wajibi inyi godiya ta musamman ga marigayi Alh.
Sharif Isma’ila wanda kusan dukkan tarihin zuriyar gidan Sharif Yahya Na-
Tsakuwa, shi ne ya bada shi kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen kiyaye
tarihin gidan, muna Addu’ar Allah ya gafarta masa, Amin.
A karo na biyu, godiya ta musamman ga magabatanmu wadanda suka yi
bajinta wajen rubuta littafi na farko na zuriyar gidan Sharif Na-Tsakuwa
kamar, Sharif Nura Waziri Alkali Kabara, Sharif Isuhu Dukawa, Sharif
Hashimi Dukawa, Sharif Auwalu (Mai-Fata), Sharif Hassan Kabara, Sharif
Sule Dukawa, Sharif Bala Kabara, Sharif Kabiru Liman, Sharif Bashir Ibrahim
Liman, Sharif Alhaji Bala. Tare da wasu masu tarin yawa.
A karshe, muna mika godiya mara iyaka ga iyaye da yan’ uwa da kuma
dukkan wadanda suka bamu gudunmawa wajen hada wannan tarihi
kamar: Sharif Aliyu Sabi’u Sharifai,Sharif Aminu (Gayatul-Muradi), Sharif
Yammani, Sharif Aminu Bala, Sharif Usman (Na-Makka), Sharif Bashir,
Sharif Aminu Sunusi, Sharif Nura Umar, Sharif Muhammad Yakubu (Mai-
Afafa), Sharifiya Halima yar’ Muhammad Bell, Sharifiya Hassana jikar Sidi
Fari Amale (ta kan-tudu), Sharif Aminu, Sharif Uban na Malam Murtala,
Sharif Jadda jikan Sidi Liman, Sharif Khalifa Abba Liman, Sharif Khalifa
Kabiru Liman, Sharif Khalifa Musa Liman, Sharif Abdulkarim Aliyu Salihu,
Sharifiya Uwa ta Kaduna Jikar Amale, Sharifiya Rukayya Ibrahim, Sharif
Liman Kadawa, Sharif Salisu Baban Nasidi, Sharif Alhaji Malam Dan-Agundi,
Sharif Isuhu Musa Sharifai, Sharif Musatafa Malafa, Sharif Abba Abdulkarim
10
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Dayyabu, Sharif Salisu Chiromawa, Sharifiya Turai Liman, Sharif Baba Dan-
Liti, Sharif Baba Mai-Kudi, Sharif Abubakar Hashimi, Sharif Jibril Al-Hassani
Al-Ashtari, Sharif Salisu Kankarofi, Sharif Malam Sabo Kadawa/Chiromawai.
Manufa
Na rubuta wannan littafi domin ya samar da gamsashshen bayani na
abunda ya danganci Sharifai wato jikokan Annabi (SAW), kasantuwar
litattafai masu tarin yawa na nasabobi na Ahlulbait an rubuta su ne da
yaren Larabci inda wasu kuma da yaren Turanci, naga dacewar da in rubuta
littafi da yaren Hausa domin Al’ummarmu su san tarihin Sharifai tare da
samar da ilimi wanda zai bude kofar bincike da kuma fadadar tarihi.
Bugu da kari, akwai matsaloli da yawa wadanda al’umma tare da su kansu
sharifan ke fama dasu wadanda suka kunshi: inkarin Shariftakar
musamman idan sharifan sun kasance bakake ne, ko alakar Sharifai da
wuta ko kuma banbanci tsakanin Sharifi dan mace da kuma Sharifi dan
namiji, Dukkan wadannan mun kawo bayani na ilimi dangane dasu a cikin
wannan littafi hadi da musabbabin yaduwar su a sassan duniya har damu
nan kasar Hausa.
A wannan bigire, yana da kyau na soma da bada hakuri ko kuma neman
uzuri ga wanda yaga wani bayani bai masa dadi ba, hakika haka tarihi ya
gada bisa zuwa da mabanbantan ruwayoyi, kuma yana da kyau wajen
sanin cewa “banyi hakan domin kaskantar da wani ko wata zuriya bane,
kawai hakan ya faru ne bisa abunda bincike na ya tabbatar mini”.
A karshe, ya kai mai karatu kasani; “Na yiwa Allah alkawarin bazan rubuta
sonrai ba, bazan fitar da wani cikin nasabarsa ba, bazan shigar da wanda
baya cikin nasabar da ba tasa ba, bazan ruubuta sonrai ko son zuciya ba,
bazan kozanta wata zuriya ko kaskantar da wata zuriya ba kuma nayiwa
Allah alkawarin zanyi iya iyawata wajen rubuta abunda yake gaskiya”. Duk
abunda ya kasance kuskurene bayyananne cikin wannan littafi, to hakika
kuwa ina neman afuwa tare da neman gafarar ubangiji, abunda kuwa ya
zamto dai dai, ina godiya ga Allah bisa hakan.
Alhamdulillah.
11
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Shimfida
Wannan littafi ya kunshi bayani tundaga halittar duniya har izuwa samuwar
Sharifai a doron kasa. Mun zabi yin hakan domin wanzar da ilimi kuma
domin littafin ya kasance ya game dukkan wani tarihi na sharifan tun daga
halittar duniya har izuwa samuwarsu. Hakanan, ya kunshi ya’ya da kuma
jikokansu hadi da musabbabin yaduwarsu a bankasa domin wanzar da
bayanai game dasu tare da bude kofa ga masu nazartar tarihi da bincike, a
karshe, mun kammala shi da Tarihin Zuriyar Sharif Yahaya Na-Tsakuwa tare
da yan’ uwansa dake Unguwar Dukawa cikin birnin Jahar Kano. Muna
rokon Allah da ya tabbatar damu akan daidai ya kuma sanyamu cikin
wadanda zasu dace bisa wannan kuduri namu.
12
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
13
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Wannan Aya tana nuna yadda larabawa suka baiwa ilimin sanin nasaba
muhimmanci inda suke kiyayeta tare da kuma darajata har ta zamo musu
abun alfahari da kuma daukakar su cikin daukacin halittu.
Hakanan, har ila yau, mafi aksarin al’umma basu da masaniya akan
nasabarsu inda da yawa sukan gaza fadin sunan kakansu ko da kuwa na
farko ne, a cikin kabilun Hausawa zamu iya cewa, iya bangare uku ne kawai
suke kiyaye nasabarsu, kuma sune: Sharifai, Masarauta da kuma Malamai,
na hudun da suke raka musu baya sune Mawadata. Banda jerin wadannan,
kusan babu wanda zai iya jeranta kakansa har izuwa na biyar ko na bakwai
wanda hakan illa ne wajen kiyaye nasaba da kuma tarihi.
Addinin Musulunci ya bada fifiko wajen kiyaye nasaba inda yazo cikin
Hadisai da kuma Littafi mai girma (Alkur’ani) wajen nuna mana
muhimmancin ta da kuma amfanin ta. Nasaba tana karawa al’umma
kwarjini musamman gurin masu ilimi da kuma masu nazartar tarihi, tana
taimakawa wajen sadar da zumunci, hadin kai da kuma zaman lafiya, Duk
al’ummar da ta kiyaye nasabarta to kuwa ta kiyaye darajarta, mutuncinta
da kuma tarihinta.
Yazo a hadisi inda Manzon Allah (SAW) yake cewa “Ku sanar/kiyaye
Nasabar ku domin sadar da zumuncin ku”4.
Ta hanyar nasaba muke sanin junanmu da kuma alakar dake tsakanin mu
kuma sai ta hanyar ta kawai zamu iya sadar da shi zumuncin.
A cikin sahabban Annabi (SAW), Sayyadi Abubakar Al-Siddik yayi fice
matuka wajen sanin Nasabar ilahirin Larabawa domin sai da takai Manzon
Allah (SAW) yana cewa da shi ya gayawa Hassanu (Babban mawakin Annabi
SAW) nasabar larabawa, bayan shi akwai Abdullahi bin Usman, Mukramatu,
Amiru bin Darib, Akilu bin Abi-Dalib, Urwatu bin Uzainatu, Jubair bin Mud’in
daga bani Naufal5.
Bayansu an samu wadanda suka biyo bayansu irin su: Sharif Jamaluddeen
Ahmad bin Unubi, Abi-Nasir Sahal bin Abdullahi Al-Bukhari, Imam
Fakarruddeen Al-Razi, Ibn Asir Izzudeen Abu Hassan Aliyu bin Muhammad
bin Muhammad bin Abdulkarim Al-Shaibani Al-Asir, Aliyu bin Muhammad
14
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
15
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
16
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
17
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
“Lalle ne Allah yana umarnin ku, ku bayar da amanoni zuwa ga masu su.
Kuma idan kunyi hukunci a tsakanin mutane, kuyi hukunci da adalci. Lalle
ne Allah yana yin madallah da abinda yake yimuku wa’azi dashi. Lalle ne
Allah ya kasance maiji ne kuma mai gani” (4:58).
Hakanan a wata Ayar, Allah yana gaya mana cewa:
“yaku wadanda sukayi Imani, ku kasance masu tsayuwa da adalci, masu
shaida saboda Allah, kuma ko da akan ku ne, ko mahaifa da mafi kusantar
zumunta, ko da (wanda ake yi wa shaida) ya kasance mawadaci ko
matalauci, to kuwa Allah ne mafi chan chanta da lamarinsu. Saboda haka
kada ku bibiyi son zuciya harku karkata. Kuma idan kuka karkata da Magana
ko kuwa kuka kau dakai, to lalle ne Allah ya kasance masani ga abinda kuke
aikatawa” (4:155)
A wata ayar Allah yana gaya mana cewa “kuyi adalci koda kuwa akan
makusantanku ne”
Wadannan ayoyi sun bayyana mana tabbatar da gaskiya da kuma yin adalci
a kowane al’amari musammanma a bangare na nasaba. Hakika
“Mukaddima ta Ibn Kaldum” ta ishemu misali ta sigar da yake tsage gaskiya
akan asalin kabilun maghrib da kuma fayyace gaskiya ga kabilun da suke
jingina kansu da sharifai da gangan ba tare da yaji tsoro ko kuma zargin
masu zargi ba.
(5) Wadatuwa ga barin kwadayi da son zuciya: Ga wanda yake da ilimi
akan nasaba dolene ya wadatu ga barin son zuciya da kuma kwadayi
domin hakan na iya kaishi ga halaka.
Hakika nasaba zuwa ga Annabi abace wadda kowa yake so kuma yake
marari saidai samunta yarjewa ce ta Mahalicci, ya zama wajibi a guji sanya
dukkan wadanda basa ciki ko da kuwa sun nuna kwadayinsu da bukatarsu a
fili.
(6) Tabbatar da abunda ya inganta: Duk da cewa akwai sabani na malamai,
bincike da kuma bayanai na nasabobi masu yawa, zaifi dacewa wajen
tabbatar da abunda fakihai na nasaba suka tabbatar, amma babu laifi
wajen bayyana wani dalili ko wani bayani abun amincewa tare da hujja
gamsashishiya. Amma zaiyi wahala a aminta da sabon bincike ko wani
bayani wanda babu shi a baya kokuma kirkirarren labari akan wata
nasaba.
18
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(7) Kaucewa kokwanto ko zato: bayani na nasaba baya zama abin dogaro a
gina shi akan kokwanto ko kuma zato kokuma a kaddara wani abu
wanda babu tartibin bayani akansa. Ana gina dukkan wani bayani na
nasaba akan abunda aka tabbatar da afkuwarsa kuma kwalkoluwar
darajarsa shine ya kasance mashhuri ne.
Farkonn Halittar Allah Madaukakin Sarki
Allah yana gaya mana a cikin Alkur’ani cewa:
“Allah shine mahaliccin dukkan komai, kuma shine wakili akan
komai”12(39:62).
Dukkan wani abu da muke gani dama wanda bama gani hadi da mai rai da
mara rai Allah shine ya halicce shi kuma yake kula dashi.
Malamai sun karawa juna ilimi akan farkon abunda Allah ya fara halitta,
kaso na farko sun tafi akan cewa farkon abunda Allah ya fara halitta shine
Alkalami, sai girgije/gajimare sai kuma kurisiyyun sa. kuma wannan yayi
daidai da ra’ayin Ibn Jarir Al Tabari, Ibn Al Jauzi, da wasunsu. Sun kafa hujja
da hadisin da imam Ahmad, da Abu Dawud da kuma Imam Tirmizi suka
rawaito daga Ubaidullah ibn sabit cewa, Manzon Allah (SAW) yace “Farkon
abunda Allah ya fara halitta shine Alkalami, sannan yace dashi (Alkalamin),
da ya rubuta dukkan abunda zai afku a kowace sa’a har izuwa tashin
alkiyama”13.
A daya bangaren, mafi jamhurin malamai sun tafi akan cewa farkon abunda
Allah ya fara halitta shine Gadon Mulkinsa wato kursiyyu kenan. Wannan
yayi daidai da ra’ayin Imam Hafiz Abul A’la, da imam Hamdani da
wasunsu14.
Halittar Sama Da Kasa
Allah yana gaya mana a cikin Alkur’ani cewa:
“Lalle ne ubangijinku shine Allah, wanda ya halicci sama da kasa a cikin
kwana shida” (7:54).
Malamai sunyi sabani akan kwana shidan da Allah yake nufi, kaso na farko
sun tafi akan cewa kwanaki shidan irin kwanakin mune na duniya inda kaso
19
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
na biyun suka tafi akan cewa ba irin kwanakin mune na duniya ba. Mujahid,
Ad-Dahhak da kuma Ka’ab al Ahbar sun rawaito daga Ibn Abbas (RH) cewa
“ko wace kwana daya, daidai take da dubunnan shekaru15”.
Ibn Jareer ya rawaito daga Ad- Dahhak Ibn Muzahim da wasusunsu cewa
“sunayen wadannan kwana shidan sune: Abjad, Hawwaz, Hutti, Kalemun,
Sa’fas da kuma Qurasht16. Ya rawaito (Ibn Jareer) cewa mabiya Al- taurah
sunce Allah ya fara halitta ranar Lahadi, mabiya Injila kuma sukace ranar
Asabar inda mu Musulmai daga abunda mukaji daga Manzon Allah (SAW)
“Allah ya fara halittar sama da kasa ranar Asabar ne”17. Dangane da Abunda
Allah ya fara halitta (tsakanin sama da kasa), Suratul Fussilata (41:9-12) ta
tabbatar da cewa Allah sai da ya fara halittar kasa sannnan ya halicci sama
dogaro da cewa kasa itace ginshiki na samar da tushe”. Duk da cewa a kwai
malaman da suka kafa hujja da suratul Nazi’at (79:27-33) a matsayin hujja
kan cewa sai da Allah ya halicci sama sannan ya halicci kasa18.
Hadisi yazo inda yake fayyace mana aikin da kudurar Ubangiji tayi a kowace
rana, Imam Ahmad bin Hanbal ya rawaito Hadisin Abu Huraira inda yake
cewa:
Manzon Allah (SAW) ya riki hannuna kuma yace dani “Allah ya halicci kasa
ranar Asabar sannan ya halicci duwatsu ranar lahadi, ya halicci bushiyu
ranar litinin, ya halicci ababai marasa dadi ranar talata, ya halicci haske
ranar laraba, sannan ya shimfida/sanya ababan daya halitta ranar Alhamis,
sannan ya halicci Annabi Adamu da la’asar ranar Juma’a19. Shine (Annabi
Adamu) karshen halittar Allah a awar karshe ta ranar juma’a, tsakanin
la’asar zuwa dare/faduwar rana.
Halittar Mala’iku, Aljanu Da kuma Dan Adam
Ummul-Mu’minin Nana Aisha (RA) ta rawaito daga Manzon Allah (SAW)
cewa:
“Mala’iku an halicce su ne daga haske, Aljanu an haliccesu ne daga wuta,
shi kuma Adamu an halicce shi ne daga abunda Alkur’ani ya fada
(yunbu/kasa) 20.
20
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
21
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Hakan yana nuna mana cewa kafin wanzuwar dan Adam a ban kasa, Allah
ya halicci wasu al’ummatai inda daga bisani saboda saba masa da sukayi ya
halakar dasu ta hanyar turo musu Aljanu inda su kuma suke karfafa akansu
kuma suka karkashesu baki daya sannan kuma suka maye gurbinsu tare da
wanzuwa aban kasa.
A wata ruwayar daga Ad-Dahhak shikuma ya rawaita daga Abdullahi Ibn
Abbas yace, “yayinda Aljanu suka wanzar da barna aban kasa tare da zubar
da jini, sai Allah ya turo Iblis a garesu tare da runduna ta mala’iku suka
karkashesu (Aljanu) sannan suka koresu daga kasa izuwa koramai da kuma
tekuna25.
Shi iblis (shedan) yana daga cikin kabila ta Mala’iku wanda ake kiransu da
Jinnu, ana kiransu da Jinnu ne saboda sune suke kula da Aljannah26.
Abdullahi Ibn Abbas yace “sunan Ibliss na ainahi kafin ya sabawa
ubangijinsa shine Azazeel, a wata ruwayar kuma an ambata shi da suna
Harith kuma ya fitone daga wata kabila da ake ce mata Jinn27. Yayi kama da
mala’iku, saidai ba jinsunsu daya ba saboda shi daga wuta aka halicce shi su
kuma daga haske aka halicce su.
Bayan da Iblis ya sabi Ubangiji akan kin bin umarnin Allah na yiwa Annabi
adamu sujjada sai Allah ya la’ance shi kuma aka sakko dashi daga sama
izuwa ban kasa. A hadisin da Imam Ahmad yarawaito daga Jabir Ibn
Abdullahi yace: Manzon Allah (SAW) yace:
“Fadar/karagar Iblis tana kan ruwa, a kowace rana yana tura mabiyansa
cikin mutane don su haifar da sabani/husuma, wanda yafi kowa a cikinsu
(mabiyansa) shine wanda yafi kowanne a cikinsu haddasa
husuma/sabani”28.
Dangane Da Halittar Annabi Adam Allah Yana gaya mana cewa
“kuma a lokacin da ubangiji yace da mala’iku; lalle ne Ni mai sanya halifane
a cikin kasa, sai sukace(mala’iku); ashe zaka sanya a cikinta wanda zaiyi
barna a cikinta, kuma mu muna yimaka tasbihi tare da gode maka kuma
muna tsarkakewa a gareka, sai yace (Allah ya fada ga mala’iku); lalle Ni
nasan abunda baku sani ba”29.
22
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Katadah yana cewa mala’iku sunsan cewa yan’ Adam zasuyi barna da kuma
zubar da jini aban kasa saboda abunda suka lura dashi dangane da halayyar
Binn da kuma Jinn wanda suka wanzu aban kasa tun kafin Annabi
Adamu30.A wata Ayar Allah yana gaya mana:
“Kuma a lokacin da Ubangiji yace da mala’iku: lalle Ni mai halittar wani jiki
ne daga kekashashshen yunbu wanda ya chanja. To idan na daidaitashi
kuma na hura daga ruhina a cikinsa to ku fadi a gare shi kuna masu yin
sujjada”31. (15:28-29)
Hakika Dan-Adam ya samu karramawa wadda Allah baitaba yiwa wata
halitta irinsaba inda ya karammashi har sau hudu; ya halicce shi da
hannunsa, ya hura masa rai daga ruhinsa, ya umarci mala’iku suyi masa
sujjada sannan kuma ya sanar dashi iliman da bai sanar da kowanne daga
halittarsa ba32.
Bayan halittar Annabi Adam, Imam Al-Zuhri a cikin littafin sa Al-Dibakatul
Kubra ya kawo cewa Allah ya halicci Nana Hauwa’u (matar Annabi Adam)
daga kashin hakarkarin Annabi Adamu. Allah yana kuma gaya mana cewa:
“Yaku mutane, ku bi Ubangijinku da takawa wanda ya halittaku daga rai
guda (Annabi Adam), kuma ya halitta daga gareshi ma’auransa (Nana
Hauwa’u), kuma ya watsa daga garesu maza masu yawa da mata”33(4:1).
23
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Al Hafiz Abu Ya’la ya rawaito daga Aba-Huraira cewa, Manzon Allah (SAW)
yace:
“Allah ya halicci Annabi Adam daga kasa, sannan ya mayar dashi tabo, sai ya
barshi har yazama bakin tabo, sai ya halicce shi sannan ya tsarashi, sannan
ya barshi har sai da yazama ya bushe kamar tukunya (ta kasa)”35.
Bayan halittarsa, Allah ya sanya shi da ya zauna a gidan Aljanna kuma aka
haneshi da cin wata itaciya. Malamai sun tattauna akan itaciyar da aka hana
Annabi Adamu cinta inda akace bishiyar Inibi ce, shi kuma As-Sauri ya
rawaita daga Abu-Hussain shima (Abu-Hussain) daga Abu-Malik cewa
bishiyar itace “Bishiyar Dabino”, Amman Ibn Juraij ya rawaita daga Mujahid
cewa bishiyar itace “Bishiyar Baure”, kuma An bayyana cewa hakan ya faru
ne a cikin gidan Aljanna inda aka bayyana Aljannar a cewa “Jannatul
Ma’awa” ce, wasu kuma sukace Aljannar it ace Jannatul Khuld”36.
Shedan yazo musu yace dasu “An hana ku kuci wannan itaciya ne kawai
saboda idan kun cita zaku zama mala’iku ko kuma ku kasance
madauwama”, Nana Hauwa’u itace ta fara cin itaciyar kafin Annabi Adamu
sannan kuma ta roki Annabi Adamu da shima yaci itaciyar37. Al-Hakim ya
kawo a cikin Mustadrak inda aka rawaito daga Abdullahi Ibn Abbas cewa:
“Annabi Adam bai dauki lokaci mai tsayi a cikin gidan Aljannah ba inda
lokacin bai wuce tsakanin la’asar zuwa waduwar rana ba (wannan yana
nuna mana cewa gabaki daya daga shigarsa Aljanna zuwa fitarsa bai wuce
daga la’asar zuwa maghriba ba) 38. A hadisin Muslim, an rawaito daga Aba-
Huraira shi kuma daga Manzon Allah (SAW) cewa: “Ranar da tafi kowacce
cikin ranaku ita ce ranar Juma’a, a ranar ne aka halicci Annabi Adam, a
ranar ne aka sanya shi cikin gidan Aljannah kuma a ranar ne aka fitar dashi
daga cikin ta”39. Wannan hadisi ya kuma karawa maganar da Al-Hakim ya
rawaita karfi na cewa gabaki dayan rayuwar Annabi Adam bata wuce daga
la’asar zuwa waduwar ranaba a cikin gidan Aljannah.
Bayan fitowarsa daga Aljanna bisa dalilin cin itaciyar da aka haneshi da ita,
Allah ya saukar dashi aban kasa a gurin da yanzu yake a yankin Indiya tare
da matarsa Hauwa’u inda a nanne suka cigaba da rayuwa kuma suka
hayayyafa a wannan gurin.
24
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
25
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
kuma wasu wadanda suka fitar da tsatso masu yawa, Al-Yarz ya haifi
Khanookh wanda Kanukh shine Annabin Allah Idriss (AS) da kuma wasu
bangarorin da suka fitar da zuriya44.
Bayan annabi Shisu, Allah ya turo Idriss wanda shine farkon wanda Allah ya
aiko shi a matsayin Annabi a ban kasa bayan Annabi Adam kuma shine ya
fara rubutu da alkalami/biro, kuma ya fara zane akan kasa, Annabi Idriss ya
rayu tare da Annabi Adam tsawon shekara 308, Al Aufi ya rawaito daga
Abdullahi Ibn Abbas cewa “Annabi Idriss Allah ya dauke shi izuwa sama ta
shida kuma a nanne Allah ya karbi rayuwarsa amman a wata ruwaya wadda
Bukhari da Muslim suka rawaita, ta tabbatar da cewa a sama ta hudu Allah
ya ajiye Annabi Idriss ba sama ta shida ba kuma Mujahid dama wasu sun
tabbatar da hakan45.
Bayan tafiyar Idriss, Allah ya aiko Annabinsa Nuhu domin ya tabbatar da
Tauhidi cikin Al’umma, shi Annabi Nuhu dan gidan Lamak ne, shi kuma dan
Mattoshlak dan khanookh (wanda shinne Annabin Allah Idriss), dan Yard ko
Yarz dan Mahla’eel dan Qainan dan Anuus dan Sheesu dan Annabi Adamu
wanda shine uban halitta baki daya46. An haifeshi bayan rasuwar Annabi
Adamu da shekara dari da ashirin da shida (126), Ibn Jarir ya tabbatar da
hakan dama wasu daga cikin ragowar malamai, saidai wasu sunce an
haifeshi bayan Annabi Adamu da shekara dari da arba’in da shida 146 47.
A hadisin da Abu-Umamah ya rawaito daga manzon Allah (SAW) inda ake
tambayar Annabi tsakanin Annabi Nuhu da Annabi Adam, sai Manzon Allah
(SAW) ya bada amsar cewa “karni goma ne a tsakanin su”, A mafi
ingantacciyar Magana, ko wane karni daya akwai shekara dari a cikinsa,
hakan yana nuna mana cewa tsakanin Annabi Nuhu da kuma Annabi
Adamu shekara dubu ne tsakanin su48.
Annabi Nuhu yasha fama da mutanensa wajen tabbatar da tauhidi inda sai
da ya shekara 950 yana kiran mutanansa akan kadaituwar Allah guda daya
amma sukaki binsa cikinsu kuwa harda dansa. Annabi Nuhu daga karshe, ya
roki Allah akan ya halakar dasu inda Allah ya umarce shi da a cikin kowane
jinsi na dabbobi ya dauki namiji da mace da kuma wadanda sukayi immani
dashi cikin mutanensa a cikin jirgin ruwan daya kera. Allah ya turo musu da
26
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
ruwa inda yake bulbulowa ta kasa da kuma kwararsa ta sama wanda saida
dukkan Al’umma suka halaka illa kadai wadanda suke cikin jirgin Annabi
Nuhu wanda sune kawai suka tsira.
Bayan tafiya da sukayi ta tsayin lokaci a jirgin ruwa, da ruwa ya janye daga
tsandauri kuma ya kasance za’a iya tafiya a tsandauri tare da zama a ban-
kasa, sai suka sauka daga jirgin ruwan kuma sukayi masauki a wani yanki na
tsauni dake Aljazeera (wato bangaren Jazeeratul Arab kenan) 49. Daga cikin
mabiyansa (Annabi Nuhu) da suka sauka a wannan yanki na Al-Jazeera babu
wani da ya samar da zuriya a cikinsu illa Annabin Allah wato Annabi Nuhu
kenan50. Wannan kaulin yayi daidai da fadin Allah (SWT) inda yake gaya
mana cewa:
“Muka sanya zuriyarsa suna masu wanzuwa (Aban kasa)”51.
Dukkan wanda yake a wannnan duniyar kuma ko daga wane jinsi ya fito, to
kuwa ya fito ne daga daya cikin ya’yan Annabi Nuhu guda uku.
Yayan Annabi Nuhu
A zance mafi inganci ya’yan Annabi Nuhu susu hudu ne, amma wadanda
suka bishi kuma sukayi amanna dashi susu uku ne inda guda daga cikinsu
shine ya bijire masa kuma ya kafircewa kiransa wanda shine Allah yake gaya
Annabi Nuhu a cikin akur’ani cewa baya daga cikin Ahalinsa. Guda ukun da
sukayi amanna da Annabi Nuhu sune: Samu, Hamu, da kuma Yafus.
Malamai sunyi sabani akan sunan dan gidan Annabi Nuhu wanda bai bishi
ba, wasu daga cikinsu sunce sunan sa “Yam”, Imam Ibn Kasir da Imam
Tabari suna kan wannan ra’ayin. Shi kuma Imam Baidawi ya tafi akan cewa
sunan dansa wanda bai bishi ba “Kan’ana”52.
Yazo a cikin hadisin Manzon Allah (SAW) dangane da yayan Annabi Nuhu da
kuma zuru’o’insu a sassan duniya, yazo a cikin Hadisin Samra Bin Jundub
cewa, Manzon Allah (SAW) yace:
“Annabi Nuhu ya haifi ya’ya guda uku; Samu shine baban Larabawa, Hamu
shine baban Habashawa, shi kuma Yafus baban Rumawa”53.
27
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
28
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
29
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
kiransu izuwa ga bautar Allah Shi kadai, saboda kira ga Tauhidi Imam Al-
Zuhri ya kawo cewa “sai da aka kulle Annabi Ibrahim a kurkuku tsawon
shekarar bakwai sannan kuma aka jefa shi a cikin wuta inda Allah ya
kubutar da shi62. Abune sannanne cewa, Annabi Ibrahim yayi hijira daga
wannan gari izuwa Harran kokuma Hurran, daga nan kuma zuwa Falasdinu
wadda ya mayar da ita cibiyar yada da’awarsa. A cikin tafiyarsa ya ratsa ta
kasar masar wato Egypt kenan a yanzu inda ya hadu da wani sarki wanda ya
kasance mai matukar nuna isa da kuma iko hadi da zalunci, bayan da
wannan sarki ya samu labarin matar Annabi Ibrahim wato Sarah sai yayi
nufin mallaketa inda ita kuma Allah ya tsareta daga zaluncinsa. Bayan da
wannan sarki yaga falalar dake tattare da Sarah sai ya bata kyautar yarsa
wato Hajara domin ta dinga yi mata hidima63.
A lokacin da Annabi Ibrahim ya shekara 20 a Baitul Makdis sai Sarah tace
dashi, “Allah bai nufeni da samun haihuwa ba, don haka ka riki wannan
baiwa tawa (Hajara)”. Annabi Ibrahim ya auri Hajara kuma bayan wani
lokaci sai Allah ya Azurta ta da samun ciki wanda hakan ya janyo kishi daga
wajen Sarah domin ita Allah bai azurta ta da samun haihuwa ba, bayan
wani kankanin lokaci, Allah ya azurta Hajara da samun da Namiji wanda aka
sanya masa suna Isma’’il. Yazo cewa, An haifi Isma’il lokacin da Annabi
Ibrahim yake da shekara 86 a duniya64.
Bayan haihuwar Isma’il, Sarah ta bukaci Annabi Ibrahim daya dauke Hajara
ya mayar da ita wani gari na daban, Annabi Ibrahim ya taho da ita inda ya
dawo da ita kusa da ka’aba ya ajiyeta a karkashin wata bishiya (A garin
Makkah). A wannan lokaci babu kowa a Makkah kuma bai kasance guri
wanda fatake keyin zango a gurin ba, Annabi Ibrahim ya barsu a wannan
guri tare da guzurin ruwa da dabino, yayin da ruwan ya kare, sai Nana
Hajara ta soma neman ruwan da zata bawa Isma’il tare da dubawa ko zata
samu wanda zai temaka musu, ta dinga hawa dutsen Safa da kuma na
Marwa (domin neman ruwa ko hangen wanda zai temaka musu) wanda sai
da tayi hakan har sau bakwai, Yazo a cikin Hadisi inda Manzon Allah (SAW)
yace “wannan shine tushen ibadar da akeyi na tafiya tsakaknin su (Safa da
Marwa)65.
30
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Nana Hajara taji Murya daga sama ana yi mata Magana sannan kuma ta ga
Mala’ika yana haka rijiyar Zam-Zam da diga-digansa ko da fuka fukansa har
saida ruwa ya bulbulo, Bayan da ruwan ya bulbulo, sai tazo tana tare ruwan
wato tana gewayeshi inda Manzon Allah (SAW) yace “Allah yayiwa
Mahaifiyar Isma’il rahama, da ace bata dinga tare ruwan ba (Zam-Zam) da
zai dinga tafiyane har ya zamto mai gudanuwa ne aban kasa”66.
Bayan samuwar ruwan Zam-Zam sai wasu kabilu daga mutanen Yemen
sukazo wanda ake kiransu da “Jurhum” suma suka zauna bisa izinin Hajara a
wannan guri67. Isma’il ya girma cikinsu sannan kuma ya koyi Larabci daga
gurinsu harma ya auri daya daga kabilar Jurhum68. Bayan da Nana Hajara ta
rasu, Annabi Ibrahim ya kawo ziyara inda bai samu Isma’il ba, sai dai ya
tarar da matarsa kuma ya tambayeta game da halin rayuwarsu inda ita
kuma tayi masa korafi da cewa suna cikin kuncin rayuwa da kuma rashin
wadata, da yaji haka sai ya bata sallahun cewa idan mijinta ya dawo tace
dashi ya chanja dokin kofarsa, bayan daya dawo ta gaya masa sai ya fahimci
cewa mahaifinsa ne kuma ya gane sakon mahaifinsa inda ya sauwakewa
matarsa69.
A karo na biyu, (Isma’il) ya sake wani auren, inda ya auri yar Madad dan
Amru, jagoran kabilar Jurhum kuma shugaban su, Kuma Allah ya azurta
Isma’il da ya’ya goma sha biyu (12) daga wannan matar tasa yar’ Mudad
dan Amru, ya’yan sune: Nabid, Nabalud, Kaidar, Adba’il, Mibsham,
Mishma’u, Dauma, Misha, Haddad, Yutma, Yadur, Nufais da kuma
Kaiduman. Kuma wadannan ya’ya nasa sun haifar da kabilu masu yawa da
suka cigaba da zama a Makkah tsawon lokaci70.
Idan muka koma rayuwar Annabi Ibrahim a Falasdinu wato Baitul-Makdis,
zamuga cewa bayan samun Isma’il da kuma barinsu daga Kudus izuwa
Makkah, Allah ya azurta Sarah da samun ciki wadda itace matar Annabi
Ibrahim ta farko kuma ta haifi danta mai suna Ishak, Tsakanin haihuwar
Isma’il da kuma haihuwar Ishak shekara goma sha uku ne71. Kamar yadda
tarihi ya tabbatar, daukacin banu Isra’il sun fito ne ta tsatson Annabi Ishaq
dan Annabi Ibrahim.
31
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
SASHI NA BIYU
Bayani Akan Larabawa da kuma Rabe Raben Su.
Shekh Muhammad Furiy ya fadada al’ummar Larabawa izuwa kaso/gida
uku1.
(1) Larabawan farko
Sune Asalin Larabwa na chanda, wadanda bazai yiwu a samu cikakken
bayani filla filla game da tarihinsu ba, kamar irin su: Adawa, Samudawa,
Dasmiyawa, Judaisiyawa, da Amalikawa da dai sauransu.
(2) Larabawan Asali
Sune wadanda suka fito ta tsatson Ya’rib dan Yashjub dan Kahdan. Kuma
sune ake kira da Larabawan Kahdaniyyawa.
(3) Larabawan Adnan
32
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sune wadanda suka fito da tsatson Annabi Isma’il kuma ana kiransu da
Adnaniyyawa ko kuma ace musu Musta’ariba.
Ya kara da cewa, su wadannan Larabawan na Musta’ariba, Larabci ba shine
yaransu na Asali ba, koyansa sukayi duk da cewa sun mayar dashi yarensu
na Asali kuma kakansu shine Annabi Ibrahim (AS).
Ya’yan Annabi Isma’il
Annabi Isma’il dan Annabi Ibrahim ne kuma ya haifi ya’ya goma sha biyu da
matarsa ta biyu yar’ Mudad dan Amru wanda shine jagora kuma shugaban
kabilar Jurhum inda ta haifa masa ya’ya goma sha biyu sune: Nabid,
Nabalud, Kaidar, Adba’il, Mibsham, Mishma’u, Dauma, Misha, Haddad,
Yutma, Yadur, Nufais da kuma kaiduman2. Wadannan ya’ya nasa sun Haifar
da kabilu masu yawa da suka cigaba da zama a garin Makkah tsawon lokaci.
Sannan, rayuwarsu ta dogara akan kasuwanci zuwa kasar Yaman da ta
Sham da Misra sunnan suka yadu izuwa sassan tsibirin Larabawa da
wajensa sannan aka rufe shafinsu cikin dadewar zamani sai dai ya’yan
Na’bid da Kaidar3.
Hakika Na’bid da kaidar sune wadanda Allah ya daukaka cikin zuriyar
Annabi Isma’il da Annabi Ibrahim. Zuriyar Na’bid sun kafa babbar daula mai
karfi a lokacinsu kuma ta jagoranci kabilun dake gefensu. Sayyid Sulaiman
An – Nadawy bayan bincike na ban mamaki da yayi ya tabbatar da cewa,
sarakunan Gassanah da kuma mutanen Madinah musamman Ausu da
Kazraj basu fito daga zuriyar Kahdan ba, saidai asalin su ya’yan Nabid dan
Isma’il ne kuma sune suka wanzu a wannan yanki4.
Shi kuwa Kaidar dan Isma’il basu gushe suna hayayyafa ba a garin Makkah
har aka samu Adnan da dansa Mu’ad kuma daga kansa ne Larabawa suka
haddace nasabar su, Adnan shine kaka na ashirin da daya cikin Jerin
Nasabar Annabi (SAW) 5.
Hakika ya’yan Mu’ad da kabilun da suke cikinsa sun yawaita ne ta bangaren
dansa Nizar, wasu kuma sunce, Mu’ad bashi da wani da idan ba Nizar ba
kuma shi Nizar yana da ya’ya hudu wanda suka haifar da manyan kabilu
masu yawa, sune:
Iyad
Anmar
Rabi’ah
33
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Mudar
Wadannan biyun na karshe, Rabi’ah da Mudar sune gidajensu yafi bunkasa
har suka samar da kabilu masu yawa6. Daga bangaren Rabi’ah an samu:
Banu Asad dan Rabi’ah, da Anazah, da Abdulkais, da Ya’yan Wa’il (wato)
Bakru da Taghlib da Hanifah da sauran su.
Shi kuma Mudar, sai aka samu bangarori biyu masu girma: Kaisu Iylan dan
Mudar da kuma ya’yan Ilyasu dan Mudar.
Daga Kaisu Iylan aka samu: Banu Sulaim, Banu Hawazin, Banu Gadfan. Daga
Banu Gadfan kuma aka samu Zubyan, Aysha’u, da Ganiyyu dan A’asar.
A bangaren Ilyasu dan Mudar kuma an samu: Tamim dan Murrata, Huzail
dan Mudrikata, da ya’yan Asad, da Kuzaimata, da kabilun Kinanah dan
Kuzaimata.
Daga Kinanah kuma aka samu: Kuraishawa su ne ya’yan Fihri dan Maliki dan
Nadir dan Kinanah7.
Su kuma kuraishawa sun rarrabu izuwa kabilu daban daban, mafi shahara a
cikin su sune: Jumahin, Sahmin, Adiyyu, Makhzum, Taimu, Zuhra, da
Kabilun Kusayyu dan Kilab8.
Kabilun Kusayyu dan Kilab sune: Abdu-Dar dan Kusayyu, Asad dan Abdul-
Uzzah dan Kusayyu da Abdul Manaf dan Kusayyu.
A wani kaulin an kasafta kuraishawa izuwa gida 12 kawai sune: Banu Abdul-
Manaf, Banu Abdu-Dar bin kusayyu, Asad bin Adul’uzzah bin kusayyu,
Zuhrata bin Kilab, Makhzum bin Yakzata bin Murrata, Tamim bin Murrata,
Adiyyu bin Ka’ab, Mushim bin Musiyyu, Umar bin Lu’ayyu, banu Tamim bin
Galib, Al’haris bin Kusayyu, Muharib bin fihri9.
Abdul-Manaf dan Kusayyu ya rabu gida hudu sune: Abdul-Shams, Naufal,
Mudallib da kuma Hashimu10.
Daga gidan Hashim kuma Allah ya zabo Shugaban Mu Muhammad (SAW)
dan Abdullahi dan Abdulmutallib dan Hashimu.
Malamai sun fadada bayani akan rabe raben ya’yan Adnan da Kuma
guraben zaman su.
Lokacin da ya’yan Adnan suka yawaita sai suka rabu izuwa sassa daban
daban cikin garuruwan Larabawa suna bibiyar inda ruwa yake da ciyayi, sai
kabilun Abdul- Kais da kabilun Bakru dan Wa’il da kabilun Tamim sukayi
kaura zuwa Bahrain suka cigaba da rayuwa a chan. Banu Hanifah dan Sa’ab
34
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
dan Aliyu dan Bakru kuma suka tafi Yamamah inda suka sauka a cikin
kogon dutsen Yamamah.
Sauran dangin Bakru dan Wa’il kuma suka zauna suna yawo a cikin kasa
daga Yamamah zuwa Bahrain zuwa Saifu- Kazimah, zuwa gefen teku, zuwa
gefen Iraq da Ablah da Hait.
Taglib kuma suka sauka a tsibirin Furat, wasu daga cikin su kuma suka
cigaba da zama tare da ya’yan Bakru, Banu Tamim kuma suka zauna a
kauyukan Basra, Banu Sulaim kuma a kusa da Madinah daga dajin Wadil-
Kura zuwa Kaibara har zuwa gabashin Madinah wajen iyakar duwatsu har
inda ya dangane da Jarrah.
Banu Sakif kuma suka nufi Da’ifa, Hawazin kuma a gabashin Makkah wajen
Nahiyar Audas wadda take tsakanin Makkah da Basra. Banu Asad kuma
suka zauna a gabashin Taima’a gidajen Buhtar na kabilar Dai’i ne, tsakanin
su da Kufah tafiyar kwana biyar. Zubyan kuma suka zauna a kusa da
Taima’a har zuwa Hauran, sauran kabilun Kinanah kuma suka zauna a
Tihama, Kuraishawa kuma a Makkah da gefenta sai dai kuma a rarrabe
suke babu wani Abu dake hada su har sai da Kusayyu dan Kilab yazo ya
girma sannan yayi kokarin hada kansu, kuma ya samar da shugabanci da
ya daga darajar su da daukakar martabar su11
Gidan Abdul-Manaf.
Abdul Manaf shi dan Kusayyu ne kuma shine kaka na uku a jerin kakannin
Manzon Allah (SAW). Ya auri mata guda uku sune:
1. Atika bint Murrata Al- Hulaliyyah kuma itace ta Haifa masa;
(1) Mutallib ibn Abdul-Manaf. Takansa ne aka samu banu Mutallib
(2)Amr-Al-Ula/ Hashim Ibn Abdul-Manaf, shine kakan Banu Hashim kuma
daga gareshi suka fita
(3)Abd-shams/Qays Al-Ula Ibn Abdul Manaf, daga gareshi banu Abdul-
Shams suka fita
(4)Tumadir Bint Abdul-Manaf Al-Kuraishiyya
(5) Kilabah bint Abdul-Manaf Al-Kuraishiyyah
(6)Hayyah bint Abdul-Manaf Al-Kuraishiyyah
35
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
36
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
37
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
38
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sashi na uku
Gidan Annabta
A mafi ingantacciyar Magana, Shugabanmu kuma Manzon mu, Annabi
Muhammad (SAW), shine farko wanda Allah ya fara halitta a daukacin
halittarsa baki daya. Manzon Allah (SAW) ya kasance tare da ubangijinsa
tun lokacin da babu sama, babu kasa, babu Alkalami, babu kursiyyu,
hakanan babu komai illa kebantuwarsa da ubangijinsa (SAW). Mafi
jamhurin malamai sunyi ittifakin cewa Manzon Allah (SAW) shine farkon
halittar Allah kuma shine wanda ya dau shekaru dubunnai yana bautar
ubangijinsa tun kafin daukacin halitta susan yadda zasu yi bautar. Malamai
sun kuma fadada mana yadda lamarin yake, bisa cewa, farkon hasken
wanda Allah ya fara halitta shine hasken Manzon sa (SAW), sannan kuma
daga baya aka halicci hasken ragowar dukkan halittu.
39
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Hakika Allah madaukakin sarki ya tsarkake nasabar Annabi (SAW) tun daga
kan Annabi Adamu har izuwa kan mahaifansa (RA), Malamai masana tarihi
sun tabbatar mana da cewa, gabaki dayan iyayen Manzon Allah (SAW) babu
dai/guda a cikinsu wanda aka same shi da wani laifi ko ya sabawa ubangiji,
Daukacin halittar Allah, babu wani da ya azurta wajen kiyayewa tare da
tsarkakewa ta nasaba irin Annabi (SAW).
Yayin da haihuwarsa (SAW) ta gabato, Nana Aminatu ta samu bushara iri-iri
daga gurin Annabawa da kuma salihan bayi, ta dinga samun bushara daga
daukacin halittun Allah kuma ta dinga ganin abubuwa wadanda suka keta
Al’ada, lokacin da yazo duniya (SAW), ya kasance yana mai sujjada ga
Ubangijinsa kuma ya kasance a wanke abun tsarkakewa. Ya tabbata cewa,
lokacin da aka haifi Annabi (SAW) sai da daukacin dabbobi suka dinga
rigegeniya inda suka dinga yiwa junansu bushara akan haihuwar Annabin
karshen zamani wanda yakasance rahma ga daukacin halitta.
A mafi shaharar Magana, an haifi Manzon Allah ( SAW) ranar litinin 12 ga
watan rabi’ul Auwal, Duk da cewa akwai sabanin zance akan ranar
haihuwar, amma 12 ga rabi’ul Auwal shine mafi shaharar zance wajen
malaman tarihi. A wani kaulin, babban malaminnan kuma masanin taurari
da falaki Mahmud Basha ya ambata cewa an haifi Manzon Allah (SAW) a
unguwar Banu Hashim dake garin Makkah a safiyar ranar litinin 9 ga watan
Rabi’ul Auwal a shekarar giwa, wanda yayi daidai da cikar shekara 40 da
samun sarautar Kisra Anu-Shurwan, kuma yayi daidai da ashirin da biyu ga
watan Afrilu na shekara ta 571AD1.
Kakansa Abdulmutallib shine ya rada masa suna, kuma ya saka masa
“Muhammad”. Bayan Mahaifiyarsa (SAW), Suwaiba wadda kuyangar Abu
Lahab ce, itace ta fara shayar dashi a lokacin tana shayar da danta mai suna
Masruhu kuma kafin nan ta shayar da Hamza bin Abdulmutallib a bayansa
(SAW), (bayan ta shayar da Annabi) ta shayar da Abu Salamah dan Abdul-
Asad Al-Makhzumi2. Bayan suwaiba, itama Halima Al- Sa’adiyya yar Abu-
Zu’aib daga kabilar Banu Sa’ad ta shayar da Manzon Allah (SAW) wadda
mata ce ga Harisu dan Abdul-Uzza wanda ake masa alkunya da Abu Al-
Kabshata3.
40
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
41
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Hakika Abu Dalib ya rike amanar da aka dora masa harma da kari akan
kulawar daya bawa Manzon Allah (SAW). Kuma, yarjewa ce ta Allah da
kuma amincewar sa daya sanya rikon Manzon Allah (SAW) A hannun Abu
Dalib (RA).
Bayani Akan Nasabar Annabi (SAW).
Malamai sun kasa nasabar Annabi (SAW) izuwa kaso uku. Kaso na farko
daukacin malamai sun tabbatar da ingancinta kuma babu kokwanto akan
sahihancin ta, kaso na biyu kuma wasu na tabbatarwa wasu kuma na inkari
akanta inda kaso na uku kuma babu kokwanto wajen rashin ingancin ta.
Bangaren farko cikin Nasabar Annabi (SAW)
Shine: Muhammad (SAW) dan Abdullahi dan Abdulmutallib dan Hashimu
dan Abdul-Manaf (sunansa na ainahi Mughira) dan Kusayyu (sunansa na
ainahi Zaidu) dan Kilab dan Murrata dan Ka’ab dan Lu’ayyi dan Ghalib dan
Fihiri (shine akewa lakabi da kuraishu kuma gareshi ake danganta
kuraishawa) dan Malik dan Nadir (sunansa na ainahi Kaisu) dan kinanah dan
Khuzaimata dan Mudrikata (sunansa na ainahi Amir) dan Ilyas dan Nazar
dan Mu’ad dan Adnan (SAW) 9.
Bangare na biyu cikin Nasabar Annabi (SAW)
A bangare na biyu ana daukar nasabar sa (SAW) daga kan Adnan izuwa
Annabi Isma’il (AS). Ana jerantata kamar haka:
Adnan dan Adad dan Humaida’u dan Yasa’u dan Salman dan Aud dan
Buwar dan Kiwal dan Abi-Auwam dan Nashiyyu dan Hizar dan Tadlass dan
Tadlan dan Dalikh dan Kajim dan Najis dan Majiyyu dan Abkiyyu dan Abkar
dan Ubaidu dan Al-Du’a dan Hamid dan Muntin dan Butraz dan Bahraz dan
Yulkinu dan Argun dan Abku dan Risan dan Aisu dan Ikyadin dan Ibhami dan
Maksiru dan Bahisu dan Zaziku dan Shama dan Maziyyu dan Audu dan Iram
dan Kidar dan Ibrahim (AS) 10.
Shekh Mubarak Fury ya kawo wata nasabar data sha banban da wannan ta
farko, ya fara da:
42
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Adnan dan Addi dan Humaisi’u dan Salman dan Ausu dan Buza dan Kimwal
dan Ubayyu dan Auwam dan Nashid dan Hizza dan Baldasu dan Yadlaf dan
Tabikh dan Jahim dan Nahis dan Makh dan Iyadd dan Abkar dan Ubaidu dan
Du’a dan Hamdan dan Sunbur dan Yazrabiyyu dan Yuhzan dan Yulham dan
Ar’awah dan Iyad dan Dishan dan Aisar dan Afnad dan Ayham dan Mukassir
dan Nahis dan Zarih dan Sumayyu dan Mizzy dan Audah dan Iram dan
Kaidar dan Isma’il (AS) dan Ibrahim (AS) 11.
Bangare na uku cikin Nasabar Annabi (SAW)
Bangare na uku yana bayani ne daga kan Annabi Ibrahim izuwa kan Annabi
Adam (AS).
Ibrahim (AS) dan TariKh (Shi Azara Baffansa ne kuma bisa al’ada ta
Larabawa, suna kiran Baffa da sunan Abba) dan Nahur dan Saru’u dan
Falikh dan Abir dan Shalikh dan Arfakhshad dan Samu dan Nuhu (AS) dan
Lamikh dan Matushalukh dan Akhnukh dan Akmukh ance shine Idriss (AS)
dan Yarid dan Mahala’il dan kainan dan Anusha dan Shisu (AS) dan Adam
(AS).12
Siffofin Annabi (SAW).
Sayyadina Aliyu Allah ya kara yarda dashi yana daga cikin sahabban da suka
siffanta Manzon Allah (SAW), yana cewa:
“ Manzon Allah (SAW) ba zankalele bane kuma ba gajere ne durkusashshe
ba, shi dai matsakaici ne a cikin mutane kuma ba mai churkudadden gashi
bane a warware, sai dai gashin sa a hade yake kuma mai tsayi kuma ya
kwanta ( gashin nasa SAW), kuma ba mai kumburarriyar fuska bane, haka
nan ba siriri bane, kuma ba mai kiba ba, fuskar sa a kewaye take mai farin
launi mai hasken jar fata, kwayar idanun sa baka sidik ce, ga gazar gashin
gira, mai manyan gabobi ne madaidaita, yana da kyawun gashi siriri tun
daga kirjinsa har zuwa cibiyarsa, mai yalwar tafin hannu ne da kuma kaurin
yan yatsun hannu dana kafa, idan yana tafiya sai kayi zaton gangarowa
yake daga tudu, shine mafi gaskiyar mutane a wajen Magana, mafi cika
alkawari da yarjejeniyarsu, shine mafi taushin dabi’arsu da mutunta
zamantakewarsu, wanda ya hange shi bada tsammani ba sai kwarjininsa ya
43
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
kamashi, idan kayi mu’amala da shi sai kaso shi, shine mafi yalwar kirji cikin
mutane, masu siffanta shi suna cewa “ bamu taba ganin kamarsa ba
kafinsa hakanan bayansa (SAW)13.
Kamun kafa da Shi (SAW) Wajen Rokon Ruwa
Tun kafin aiko shi (SAW), ya kasance abun mamaki tare da Al’ajabi cikin
Al’amuransa da kuma rayuwarsa ga ilahirin Larabawa dama wadanda basu
ba. Duk abunda ya taba ko ya kusan ta, sai ya zamto mai albarka ta ban
mamaki kuma abin so da marmari ga daukacin halitta. Saboda Albarkarsa,
ya kasance kakanninsa da kuma baffanninsa basa jin dadin chin abinci sai
tare da shi kuma basa iya rayuwa idan basu jishi a kusa dasu ba.
Ibn Kasir ya rawaito daga Jalhamatu dan Arfadatu yace:
“na shiga garin Makkah a lokacin suna fama da fari da karancin ruwa, sai
kuraishawa suka ce, ya kai Abu-Dalib, lallai muna cikin Fari, iyalanmu suna
shan wahala ko zaka fito ka roka mana ruwa?, sai Abu-Dalib ya fito yana
dauke da wani karamin yaro (wato Annabi SAW kenan) kai kace ranace a
cikin duhu saboda haskensa, wani gajimare ya ayyana a samansa yana yi
masa inuwa, sai Abu-Dalib ya jingina bayan wannan yaro da jikin Ka’aba ya
tare Yaron da yan-yatsunsa, a lokacin sama tayi wasai babu wani alamar
hadari da gajimare, sai ruwa ya kece da zuba yayi ta kwarara har rafuka
suka cika, magudanai suka kawo , kasa tayi kore shar, albarka ta samu”14.
Akan hakane Abu-Dalib yake yiwa Annabi yabo da cewa:
“Mai cikar Hasken da ake yin kamun kafa dashi lokacin rokon ruwa, jagoran
marayu, garkuwar matan da basu da gata”15.
Wannan Alfarmar ta yadu har izuwa kan baffaninsa da kuma jikokansa
(SAW), ya kasance ana zuwa wajen Sayyadi Abbas domin ayi kamun kafa
dashi a samu ruwa, hakanan ya kasance a kasar Murtaniya idan aka rasa
ruwa, sai su futo da kananan yara jikokan Manzon Allah (SAW) su ajiyesu a
rana domin kamun kafa dasu akan Allah ya shayar dasu ruwa bisa daraja da
kuma Alfarmar dake tattare dasu 16.
Jarumtarsa (SAW)
44
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Aurensa (SAW)
Nana Khadija ta nemi auren Manzon Allah (SAW) bayan da ta yarda da
amanarsa da kuma amincinsa, a wannan lokaci, manya manyan masu mulki
da kuma masu kudi daga kuraishawa sun nemi aurenta amman taki yarda
inda daga karshe ta yaba da kyawawan halaye na Annabi (SAW) kuma ta
nemi amincewarsa akan aurenta, Nana Khadija ta samu amincewarsa
(SAW), Annabi Ya auri Nana Khadija tana da shekara 40 inda yake da
shekara 25 kuma ya bada tumaki guda 20 a matsayin sadakin ta18.
Nana Khadija itace ta Haifa masa Alkasim wanda da shine ake yiwa Annabi
alkunya dashi (Abul- Kasim), sannan Zainab, Rukayya, Ummu-Kulsum,
Fatima (shugabar Matan Aljannah) sai kuma Abdullahi. Inda cikon ya’yan
Annabi (SAW) wato Ibrahimul- Mu’azzam mariyatul Kibdiyya ce ta Haifa
masa shi.
Aiko shi da Annabta.
45
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Yayin da Annabi (SAW) ya cika shekara 40, sai Allah ya aiko shi a matsayin
Annabi kuma Manzo domin ya isar da sakon Allah na bauta masa shi kadai
da kuma wanzar da Adalci/Shari’a aban kasa. Allah ya aiko shi ga dukkanin
Al’umma (Mutum da Aljan) kuma daukacin halittu sun shaida cewa shi
Annabin Allah ne.
A wannan lokaci, duniya baki dayan ta na cikin duhun jahilci da kuma bakin
zalinci inda masu karfi su suke danne raunana da kuma tsananin rashin
wayewa. Kasantuwar tsayin lokaci ba’a turo wani Annabi ba bayan Annabi
Isa (kimanin Shekara 500 ke tsakaninsu) al’umma gabaki daya sun dena
bautar Allah sai yan kadan inda suka koma bautar gumaka, dabbobi, wuta,
ruwa da dai sauransu. Mata sun kasance ababan wulakantawa da kuma
kashewa inda idan aka haifa maka mace to kamar an wulakan taka ne ko an
kaskantar dakai, mata basu da gado kuma su kansu ababan mallaka ne,
babba cikin ya’ya shine zai mallake dukiya tare da auren wasu daga matan
mahaifinsa idan ya mutu, afkuwar yaki da gadonsa (gadar yaki daga manya
izuwa jikoki) hadi da asarar dukiyoyi da rayuka duk ba wani abu ne mai
wahala ba, dama wasu da yawa wadanda ke tattare da dabi’u da kuma
halayyar mutanen wannan lokaci.
Hakika, Manzon Allah (SAW) ya gamu da kalubale mai yawa lokacin daya
gayawa mutanen Makkah cewa Shi Manzon Allah ne kuma an turo shi ne
domin a bautawa Allah shi kadai tare da tabbatar da shari’ar Addinin
Musulunci. Duk da cewa, sunsan shi mai gaskiyane harma suna yi masa
lakabi da “Al’amin” kuma basu taba saminsa da kuskure ba ko wani abu da
yake bayuwa izuwa tawaya ko samun nakasu, amman a wannan lokaci sai
da suka musanta shi kuma suka ki aminta dashi sai yan kadan. Maimakon
suyi Imani, sai ya kasance sun bude kofa ta musguna masa, chutar da shi,
kin yin mu’amala da chinikayya da shi dama ahalinsa baki daya, yunkurin
kashe shi da kuma kashe mabiyansa dama wasu nau’ikan na chutarwa.
Sayyadi Abu-Dalib, bai gusheba yana bawa Annabi kariya har sai da Allah ya
karbi rayuwarsa kuma a wannan shekarar ne Allah ya karbi rayuwar Nana
Khadija, wannan shekarar tazama mai kunci matuka wajen Annabi (SAW)
inda ake kiranta da shekarar bakin ciki saboda rasa masoyansa kuma masu
taimakonsa da yayi.
46
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
47
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(5) Nana Zainab yar Khuzaima (RA): Yar kabilar Hilal dan Amir Sa’sa’ah ce
kuma ana mata lakabi da Ummul Masakin saboda tausaya musu da
tallafa musu da take yi, mijinta na farko shine Abdullahi dan Jahshi
wanda yayi shahada a Uhud, Manzon Allah (SAW) ya aureta shekara ta 4
hijiriyya kuma bayan tarewarta da wata 2 ko 3 sai ta rasu.
(6) Ummu Salamah itace Hindu yar Abu-Umayyah (RA): Mijinta na farko
shine Abu Salamah kuma ya aureta (SAW) a watan shauwal shekara ta 4
hijiriyya.
(7) Nana Zainab yar Jahshin dan Rabab (RA): yar kabilar banu Asad ce dan
Khuzaimah, mijinta na farko shine Zaidu dan Haris kuma ita yar gwaggon
Manzon Allah ce (SAW), Allah da kansa ya umarci Annabi da ya aureta
(Ahzab:37), ya aureta a watan Zul-Ka’ada shekara ta 5 hijiriyya.
(8) Nana Juwairiyya yar Harith (RA): Ya’ ce gurin shugaban Banul- Musdalak
daya daga cikin kabilun Kuza’a. An ribace ta ne a yakin Banul Musdalak
kuma ta kasance cikin rabon Sabit dan Kaisu dan Shammas sai ya nemi
ta fanshi kanta, sai manzon Allah ya biya fansarta kuma ya aureta a
watan Sha’aban shekara ta shida Hijiriyyah.
(9) Nana Ummu Habiba (RA): Sunanta na ainahi shine, Ramlatu yar Abu
Sufyan (RA), mijinta na farko shine Ubaidullah dan Jahshin kuma sunyi
hijira izuwa Habasha tare dashi daga bisani yayi riddah a habasha ya
koma addinin Kiristanci ita kuma ta zauna a musulunci kuma shi ya mutu
a chan Habasha. Sai manzon Allah (SAW) ya nemi aurenta a gurin
Najashi inda ya aurar da ita gareshi kuma ya aiko masa da ita (Madinah)
a shekara ta bakwai sai kuma ta tare.
(10) Safiyyatu yar Huyayyu dan Akhdab (RA): Tana daga cikin wadan da
aka kama a kaibar, sai Manzon Allah ya zabeta da kansa kuma ya yanta
ta kuma ya aureta a shekara ta 7 hijiriyyah
(11) Maimunatu yar Harith (RA): Yar uwar Lubabatu yar Harith ce
mahaifiyar Fadlu dan Abbas, Annabi ya aureta a watan Zul’Ka’ada
shekara ta bakwai lokacin ramuwar Umrah bayan ya kammala Umarar
sa a mafi ingantacciyar Magana.
Wadannan 11 sune iyayen Muminai, guda biyu daga cikin su sun rasu(Nana
Khadija da Nana Zainab Ummul Masakin) a tsawon rayuwar Annabi (SAW),
guda 9 kuma Annabi yayi wafati ya barsu a Madina.
48
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Akwai guda 2 wadan da Annabi (SAW) ya aure su amma bai tare dasu ba,
daya daga cikin su yar kabilar Banu Kilab ce , dayar kuma yar Kabilar Kinda
ce kuma ita akafi sani da sunan Juniyya.
Dangane da kuyangogi, yana da kuyangi guda 2, wato sadaka kenan.
(1) Mariyatul- Kibdiyya (RA): Wadda mukaukis ya bayar da kyautarta gareshi
(SAW) kuma itace ta haifa masa Ibrahimul- Mu’azzam wanda ya rasu tun
yana karami, ya rasu a Madina ranar 28 ko 29 ga watan shauwal, dai dai
da 27/1/632AD.
(2) Raihanatu Yar Zaid An Nadriyya ko Kuraiziyyah (RA): Tana daga cikin
wadanda aka kama a banu Kuraizah, sai ya zabeta da kansa.
Abu- Ubaidullah kuma ya kara ambatar wasu guda biyun daban da ya same
su a cikin sashen wadanda ya kama cikin yake yaken sa (SAW). Daya daga
cikin su itace: Jamila, dayar kuma matarsa Zainab yar Jahshin ce (RA) ta
bashi kyauta20.
Janhankali.
Yanada kyau musani cewa, daukacin auren da Manzon Allah (SAW) yayi,
tattare yake da manufofi, da kuma dalilai kuma uwa uba umarnin Allah ne.
idan mukayi kallo na tsanaki zamu ga cewa, daukacin auren da manzon
Allah (SAW) yayi, yayi sune a shekara goman karshe na rayuwarsa wanda
hakan yake nuna mana cewa akwai manufofi tattare da hakan. Bisa
zuzzurfan bincike, Manzon Allah (SAW) yayi wadanchan aure ne domin
masalahar addini dama mu musulmai baki daya kuma uwa uba, yin auren
ya kasance silar wanzuwar Addini a wanchan lokaci da kuma taimakawa
wajen bunkasar sa. Yana da kyau mu zayyano wasu dalilai dazasu iya zama
hujja ga mai nazari da kuma bibiyar tarihi.
Daga cikin kyawawan Al’adun Larabawa, akwai girmama siriki da jin
nauyinsa da mutunta shi domin itace babbar kofar hada dangantaka da
sauran kabilu, harma suna ganin yin rigima ko gaba da suruki abun kunya
ne kuma babban aibu ne daza a muzunta mutum ko kabila dashi, don haka
Manzon Allah (SAW) yayi nufin toshe Baraka ta wannan hanyar21.
Wannan yana nuna mana cewa, surukun taka da larabawa, na iya dakushe
gaba da kiyayya wadanda sukan iya bayuwa izuwa yaki da kuma zubar da
49
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
50
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
51
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Kuji tsoron mata (ku kiyaye su), kuji tsoron Allah akan lamarinsu, domin ku
rike su da amanar Allah, ku nemi halaccin farjojinsu da kalmar Allah, kuma
hakkinku ne akansu kada su shigo da wanda baku amince ba cikin gidajen
ku, idan suka aikata haka, zaku iya dukansu, amma ba duka mai fasa jikiba,
kuma hakkinsu ne akanku ku ciyar dasu ku tufatar dasu da abinda shari’a
tayi umarni.
Hakika na bar muku abunda idan kuka yi riko dashi ba zaku bata ba, shi ne
littafin Allah.
Yaku mutane! Lallai babu wani Annabi a bayana, kuma babu wata Al’umma
a bayanku don haka ku bautawa Ubangijinku ku yi sallolinku guda biyar, ku
azumci watan ku (Ramamdan) ku bayar da Zakkar dukiyoyinku cikin dadin
rai, ku ziyarci dakin Ubangijinku, sai ku shiga Aljannar Ubangijinku”
Lallai za’a tambayeku game dani, ko wace irin amsa zaku bayar? Sai suka
ce: “mun shaida lallai ka isar da sako, ka bayar da Amana ka yi nasiha ga
al’ummah”. Sai ya daga dan yatsansa (Annabi SAW) izuwa sama yana
nunawa mutane kuma yace: “ya Allah ka shaidah”. Sai da ya maimaita sau
uku”24.
Wanda yake daga murya yana isar da maganar Annabi (SAW) a wannan
rana a filin Arfah shine Rabi’atu dan Umayyatu dan Khalaf25.
Annabi (SAW) ya cigaba da koyar da sahabbansa yadda aikin Hajji yake har
ya karaso wajen yanka inda ya soke Rakumi sittin da uku (63) da hannunsa,
sai ya baiwa Aliyu dan Abi-Dalib (RA) ya soke sauran da suka rage guda
talatin da bakwai (37) cikon darin kenan26.
Bayan wacchan hudubar da Annabi (SAW) yayi ta ranar Arfa, ya kuma yin
wata ranar goma ga watan Zulhijjah, ranar Sallah kenan inda yake kan
Alfadararsa “Shahaba’a” Aliyu kuma yana isarwa da mutane alhali suna
tsaye wasu kuma suna zaune kuma ya sake maimaita wasu daga cikin
bayanen da yayi jiya, hakika Bukhari da Muslim sun rawaito daga Abu-
Bakhrata (RA) y ace Annabi (SAW) ya yi mana huduba a ranar suka (yanka)
ya ce:
52
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
“Lalle zamani yana juyawa kamar yadda yake tun ranar da Allah ya halicci
sammai da Kassai, shekara wata goma sha biyu ne, daga cikin su akwai
guda hudu masu Alfarma, uku a jere suke: Zul’ka’ada, Zul-Hajji, Muharram
da Rajab watan Kabilar Mudar da ke tsakanin Jumada da Sha’aban.
Wannan wane watane? Sai muka ce: Allah da Manzonsa su ne mafi sani, sai
yayi shiru sai da mukayi zaton zai ambace shi da wani suna da ba nasa ba,
sai yace: Ba Zulhijjah bane? Sai mukace: kwarai shi ne. wannan wace rana
ce? (Annabi SAW ya tambaya), sai muka ce: Allah da Manzonsa ne mafi
sani, sai yayi shiru har mukayi zaton zai ambaci wata rana da ban, sai yace:
Ba ranar suka da yanka ba ce? Muka ce: kwarai ita ce. Sai yace: Lallai
jininku da dukiyoyinku da mutuncinku haramun ne a tsakaninku, kamar
alfarmar wannan rana da kuke ciki, a wannan wata a wannan guri.
Lallai zaku hadu da Ubangijinku kuma zai tambaye ku ayyukan ku, ku
saurara! Lallai kada ku zama batattu a bayana, har sashenku ya yi fada
(rigima) da sashe.
Ku saurara! Shin na isar (da sako)? Sai suka ce (sahabban Annabi SAW):
kwarai ka ka isar. Sai yacez: Allah ka shaida! Lallai wanda ya halarta ya
isarwa wanda bai halarta ba, sau dayawa mai isarwa yafi kiyayewa fiye da
mai sauraro”27.
A wata ruwayar kuma ya ce (SAW):
“Ku sani duk wani azzalumi kansa yake zalunta, ku saurara! Kada azzalumi
yayi zalunci ga dansa ko mahaifinsa, ku sani: lallai shaidan ya yanke kaunar
a sake bauta masa a wannan gari har abada, sai dai zai samu biyayya daga
gareku cikin abubuwan da kuka raina daga ayyukanku, shi kuma zai gamsu
da hakan”28.
Alamomin Bankwana Na Annabi (SAW)
Yayinda Addini (na Musulunci) ya tumbatsa kuma ya isa izuwa garuruwa
masu nisa daga Jaziratul-Arab dama gefunanta hakanan Al’umma suka
tsayu akan bautar Allah shi kadai wato alamun cewa Addini ya gama cika
kuma sakon da aka Aiko Annabi (SAW) ya gama isa, sai hakan ya zamto sako
ga Annabi (SAW) cewa rayuwarsa ta duniya tazo karshe.
53
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
54
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
55
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
56
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sashi Na Hudu
Ahlul Baiti.
Ahlul baiti kalmace wadda ake amfani da ita wajen ayyana zuriya ko iyalan
wani mutum ko kuma zuriyarsa. A mafi shaharar zance cikin duniyar
musulunci, idan akace Ahlul-Baiti to ana nufin iyalan gidan Annabi (SAW).
Hakika malamai sun banbanta akan suwanene hakikanin Ahlul baiti inda
jamhurinsu suka tafi akan cewa sune wadanda Manzon Allah (SAW) ya
hanasu cin sadaka, wato sune, Ahli Akilu, Ahli Abbas, Ahli Ja’afar da kuma
Ahli Aliyyu (Allah ya kara yarda agaresu). An tambayi Zaidu Bin Arkam (RA)
suwanene Ahlul-baiti? Sai yace “sune wadanda aka haramtawa cin sadaka a
bayansa”, sai akace dashi su wanene kenan? Sai yace “Ahli Akilu, Abbas,
Ja’afar da kuma Aliyyu”1. Hakanan, an kara da matayen Manzon Allah
(SAW) a cikin Ahlul baiti cewa suma suna cikin Ahalinsa, amma a mazhabin
Imam Malikh (RA) ya kara da Sayyadu-Shuhada wato Hamza (RA) inda aka
ambata Sayyadi Abbas da Akilu da Ja’afar da Aliyu da kuma Hamza cewa
sune Ahalin gidan Annabi (SAW) wato Ahlul-Baiti kenan2.
Duk da cewa, sahabbai da kuma malamai sunfi fifita ya’yan Nana Fadima
cikin Ahlul-baiti dogaro da cewa, sune suka samu dacewa da shiga bargon
Manzon Allah (SAW), tare da samun Addu’arsa wadda su kadai suka
57
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
58
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
farkon wanda ya fara fadin falalarsu da kuma darajarsu, sannan hadisi sai
kuma fadin malamai. An rawaito cewa, Shehu Usman Dan-Fodio a cikin
Kanzul Aulad na tarihin Fulani yana cewa “Dukkan wanda ba tsatsonsu ba,
to komai matsayinsa da girmansa, bai kaisu ba”. Hakikanin saninsu da kuma
sanin matsayinsu baki daya sai ranar Alkiyama, saboda a wannan rana ce
kowane mutum ke neman tsira inda su kuma zasu tafi izuwa wajen kakansu
Annabi (SAW).
Falarsu ta farko shine fadin Allah:
“Lalle ne, Allah yana nufin tafiyar da datti daga gare ku yaku iyalan gidan
Manzon Allah (SAW), sannan kuma ya tsakake ku, tsarkake wa”5.
Imam Ahmad ya rawaito daga Abu sa’id Al-Kudri cewa wannan ayar ta
sauka ne akan mutum biyar,wato Annabi (SAW), da Sayyadi Aliyyu, da Nana
Fadima Al- Zahra’u, da Sayyadi Hassan da kuma Sayyadi Hussaini. Ibn Jarir
shima yace, an saukar da wannan Aya wadda acikinta akwai Sayyadi Aliyyu,
Nana Fadima, Hassan da kuma Hussain. Kuma dai sune Ahlul Kasa’i6.
Aya ta biyu
“Allah da Mala’ikunsa suna Salati ga Annabi, Ya ku wadanda kuka bada
Gaskiya, kuyi salati a gareshi”7.
Ka’ab dan Ujrata yace, lokacin da aka saukar da wannan aya, sai muka ce da
manzon Allah (SAW), lallai munsan yadda zamuyi maka sallama, amman ta
yaya zamuyi maka salati, Sai Manzon Allah (SAW) yace kuce “Allah kayi
salati ga Muhammad da Alayen Muhammad”……. Har izuwa karshe8.
Imam Dailami ya kawo cewa, Manzon Allah (SAW) yace, Ana tsare Addu’a
(A hanata karasawa wajen amsarta) har sai mutum yayi salati ga Annabi
tare da Iyalan gidansa, Imam Shafi’I, yana cewa “yaku iyalan Gidan Manzon
Allah (SAW), Soyayyar ku wajibi ce da Allah ya saukar da ita a cikin
Alkur’ani, ya isheku kolkoluwar daraja cewa, duk wanda baiyi muku salati
ba to kuwa bashi da Sallah (wato a cikin Sallah, musamman a tahiyar
karshe)9.
59
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Wannan yana daga cikin wajabci a mazahabar Imam Shafi’I, cewa, duk
wanda yayi Sallah baiyiwa Iyalan gidan Annabi Salati ba, to kuwa bashi da
Sallah. A wani bayanan a bayyana cewa, Imam shafi’i yana nuna cewa Sallar
ce bata cikaba ko kuma sallar ta tawaya saboda rashin yiwa Iyalan Gidan
Annabi salati10.
Aya ta Uku
Allah yana gaya mana cewa: “Salam Ala Ali Yasin”11.
Hakika masu tafsiri sun kawo daga gurin Ibn Abbas (RA) cewa, abunda ake
nufi da wannan Aya shine “Salam Ala Ali Muhammad” wato kuyi salati ga
Iyalan gidan Manzon Allah (SAW), hakanan, wannan yayi daidai da nufin
Imam Kalbi akan lafazin wannan Aya12.
Aya ta hudu
Allah yana gaya mana cewa “Wakifuhum Innahum Mas’ulun”13. (A tsayar
dasu domin su Ababan tambaya ne).
Dailami ya rawaito daga Abu Sa’id Al-Kudri cewa Manzon Allah (SAW) yace
“wannan Aya tana Magana ne akan daraja ko fifiko na sayyadina Ali”. A
wani kaulin, da kuma Ahlul-baiti. Allah madaukakin Sarki ya umarci manzon
Allah (SAW) cewa, da ya sanar da halitta cewa bazai tambaye su akan isar
da sako ba, sai “Soyayyar Makusanta”14. Malamai sun tabbatar mana da
cewa, makusantan nan sune Sayyadi Ali da Nana Fadima da Alhassan da
kuma Alhussaini15.
Aya ta biyar
Fadin Allah (SAW) “Wa’atasimu bi-habillahi Jami’an Wala Tafarraku” 16.
Imam Sa’alabi ya kawo a cikin tafsirin wannan Aya cewa: Imam Ja’afar Al-
Sadik yana cewa, “mune igiyar Allah” wadda Allah yake fada (Ayi ruko da ita
kuma kada a rarrabu) 17.
Aya ta shida
60
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
61
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
62
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ibn Hibban ya rawaito a cikin sahihai cewa Annabi (SAW) yace “Babu wani
dazaiji yana kin ko ya tsani ahalin gidana face sai Allah ya shigar dashi cikin
wuta
Al-Hakim ya rawaito cikin Hadisin Anas bin Malik (RA) cewa Annabi (SAW)
yace “Ubangijina yayi mini alkawari cewa muddin iyalan gidana suka shaida
cewa babu abun bautawa da gaskiya sai Allah kuma suka shaida da aminta
da abunda nazo da shi to baza ayi musu azababa
Ibn Jarir Al-Tabari daga tafsirin Ibn Abbas (RA) cewa, Ayar da Allah
madaukakin Sarki yake gayawa Manzonsa (SAW) cikin suratul Duha aya ta
biyar cewa “Wala saufa yu’udika rabbuka fatarda” (ubangijinka zai baka har
sai ka aminta ko ka yarda), Ibn Abbas yace “Annabi yana da Alfarmar da zai
ceci kafatanin iyalan gidansa inda babu wani wanda zai shiga wuta
Al-Bazzar, Abu-Nu’aimin, Abu-Ya’ala, Al-Ukili, Al-Tabarani da kuma Ibn
Shahin sun rawaito daga Ibn Mas’ud inda yace yaji Manzon Allah (SAW)
yace “Fadima ta tsare mutuncinta sai Allah ya kiyaye ko ya haramta
zuriyarta daga shiga wuta
Al-Daylami ya rawaito a cikin Hadisin Sayyadina Ali (RA) inda yace yaji
Manzon Allah (SAW) yace “Farkon wadanda zasuzo tafkina ranar alkiyama
sune iyalan gidana”
Al-Daylami ya rawaito Hadisin Abu-Sa’id (RA) inda Annabi (SAW) yace
“Iyalan gidana da mutanen Madina sune dukiyata, sune jikina, sune wajen
farincikina da kuma kariyata, ku karbi kyawawan ayyukansu kuma ku
gafarta musu akan kurakuren ayyukansu
Al-Daylami ya rawaito cikin Hadisin Sayyadina Ali (RA) inda Annabi (SAW)
yace “ku ladabtar da ya’ya yenku a bisa abubuwa guda uku, son Annabinku
da son Ahalin gidansa da kuma karatun Alkur’ani”
A wani Hadisin, Annabi (SAW) yace “Abunda zai tabbatar daku akan siradi
shine; son Ahalin gidana da kuma sahabbai”
Girmamawar Sahabbai Ga Iyalan Gidan Annabi (SAW)
63
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bayan wafatin Annabi (SAW) ba’a samu wasu mutane da suka girmama
sharifai kuma suka darajtasu kamar Sahabban Annabi (SAW), musamman
sayyadi Abubakar da Umar da Usman da kuma shi kansa Mahaifinsu wato
Imam Ali (RA). Sahabbai suna sonsu da kuma girmamasu sosai hadi ba basu
dukkan wani hakkinsu ba tare da musgunawa ba.
Hakika yazo cewa sayyadina Abubakar yana cewa “Wallahi kyautatawa
Iyalan gidan Annabi (SAW) yafi Kyautatawa nawa iyalan”.
An rawaito daga Ibn Mas’ud yace “soyayyar iyalan gidan Annabi (SAW) na
rana daya tafi ibadar shekara”) 27.
Aba-Huraira ya rawaito daga Annabi (SAW) cewa “mafi alkairinku, shine
mafi alkairi ga ahalina a bayana” 28.
Hakanan Sayyadina Umar ya kasance saboda son da yake musu, ya sanya
shi matsawa Sayyadina Ali sai ya bashi auren jikar Annabi (SAW) wato
Ummu-Kulsum” domin yaji Manzon Allah (SAW) yace “Dukkan wata Nasaba
da kuma surukunta zasu yanke ranar Alkiyama sai Kusaci da kuma
surukuntaka izuwa gare Ni”29. Duk da cewa Yar’sa mai alfarma tana auren
Annabi (SAW) amman saboda kwadayin kusaci da Annabi (SAW) ya sanya
shi neman auren Ummu-Kulsum.
Hakanan, Sayyadina Abubakakar yana daukan kayan amfanin da aka girbe
daga gonar Fadak ta Annabi (SAW) ya bawa Ahlulbaiti kuma haka wadanda
suka gaje shi suma suke aikatawa (wato Sayyadi Umar da Usman da kuma
Ali)
Halakcin yin Tawassulli da zuriyar Annabi wajen Addu’a
Kafin wafatin Annabi (SAW) ya kasance sahabbai suna zuwa domin ya rokar
musu Allah ko kuma kamun kafa da Annabi wajen rokon Allah akan ya biya
musu bukatarsu, yazo a hadisi inda makaho yazo wajen Annabi tare da
bukatuwa akan yanaso ganinsa ya dawo inda Annabi ya bashi addu’ar dazai
yi, kuma ya aikata wannan addu’a wadda kunshe take da tawassalli da
Annabi (SAW) inda Allah ya karbi addu’arsa kuma idonsa ya bude.
64
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bayan wafatin Annabi (SAW), ya kasance Sahabbai sukan nemi ayi musu
addu’a musamman wajen wanda suke ganin yana da wata falala domin
kamun kafa da shi akan Allah ya amshi rokonsu. Yazo cikin Hadisi sananne
kuma mashahuri cewa, a wani lokaci cikin Khalifancin Sayyadina Umar anyi
kamfar ruwa, wato damuna tayi tsaiko kuma al’umma sun bukaci ruwan
sama amman Allah bai nufi da ya saukar da ruwan a wannan lokaci ba, a
cikin wannan yanayi Sayyadina umar ya tashi inda ya tafi wajen Sayyadina
Abbas Baffan Annabi (SAW) kuma yayi kamun kafa da shi cikin fadinsa cewa
“Ya Allah mun kasance muna kamun kafa da Annabi (SAW) akan ka shayar
damu ruwa, sai ka shayar damu, ya Allah muna kamun kafa da Ammin
Annabinka (Abbas) Ya Allah ka shayar damu (Ruwan Sama)”30. Kuma bisa
wannan addu’ar, Allah madaukakin Sarki ya shayar dasu ruwan sama a
wannan lokaci.
Irin wannan kadiyyar ta faru a garin Fas dake kasar Morocco a yanzu cikin
shekaru da suka shude inda akayi kamfar ruwan sama mai tsanani har takai
al’umma sun fito suna rokon ruwa amman Allah bai shayar dasu ba, a
wannan yanayi ne babban malamin Fas Shekh Abdulkadir Al-Fasi ya umarce
su dasu fito da jikokan Annabi (SAW) wato sharifai kenan domin ayi
tawassali dasu wajen rokon Allah akan ya shayar dasu ruwan sama,
al’ummar Fas a wannan lokaci sun aikata hakan inda suka fito tare da
sharifai jikokin Mustafa (SAW) akayi Sallar rokon ruwa tare dasu (Sharifan)
kuma akayi tawassali dasu hadi da kamun kafa wajen rokon Allah da ya
shayar dasu, hakika a wannan lokaci Allah ya amsa addu’arsu inda ya shayar
dasu ruwan sama31.
Dogaro da fadin Annabi (SAW) cewa “Taurari amana ne ga al’ummar sama
hakanan, iyalan gidansa (SAW) amanane ga mutanen kasa”32 sharifai sun
kasance fitila gurin al’umma kuma muke kaddara cewa “Allah yana yi musu
duba na rahma bisa alfarma ta kakansu (SAW), kuma dogaro da wadanchan
hujjoji da muka zayyana, babu laifi wajen neman addu’ar Sharifai dogaro da
falala ta musamman da Allah ya kebance su da ita.
Rabe-raben nasabar sharifai.
65
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bisa bincike da kuma zuzzurfan nazari akan sharifai, zamu iya kakkasa
nasabobinsu izuwa rukunai daban daban musamman ta bangaren
amincewa da da’awarsu ko akasin haka. Dogaro da dulin lokaci da kuma
gushewar tarihi hadi da masu bincike dama tarwatsewarsu (Tarwatsewar
Sharifai a duniya) ya sanya rasa tarihi mai dimbin yawa na abunda ya
danganci su sharifan da kuma daukacin rayuwarsu. An samu al’ummatai da
yawa masu ikrarin jingina kansu da Annabi (SAW) ko kuma jingina wasu
waliyayy da cewa suna cikin Ahlul-Baiti bayan su wadanda ake yiwa da’awar
hakan, basu taba ikrarin hakan ba, kuma ba’a taba samun wasu manya ko
masana daga zamaninsu ko lokacinsu da suka nasabtasu da hakan ba,
hasalima sai bayan rasuwarsu ko kuma shudewar zamani sannan aka kirkiri
nasabtasu da Annabi (SAW). Wasu akan alakantasu da zuriyar Annabi (SAW)
bisa dalili na huldatayya ko chudanya dasu sharifan inda wasu kuma domin
soyayyar duniya suke yin da’awar hakan. Yanada muhimmanci sanin cewa
babu wata zuriya ko nasaba da yakamata a tashi haikan a kiyayeta kuma a
tsarkaketa irin zuriya da kuma nasabar Annabi (SAW) domin rashin yin
hakan na iya bayuwa ga wadanda basa ciki su shiga kuma su jawowa zuriyar
abun suka da kuma aibatawa musamman wajen kafirai da kuma munafikai.
Zamu iya kasa Darajojin Nasabar tasu kamar haka.
(1) Daraja ta farko: sune sharifan da sahihan magabata kuma fakihai a
bangaren nasaba suka tabbatar da nasabar su a cikin tarihi, suke da jerin
nasabar kakanninsu har izuwa ga Manzon Allah (SAW) babu katsewa,
suke da tarihinsu, suka shahara da ita nasabar (cewa su sharifai ne),
kuma suka kubuta daga kokwanton masana. Hakika wannan itace mafi
kwalkoluwar daraja ta bangaren Nasaba kuma Abar yadda hadi da
tabbatarwa.
(2) Daraja ta biyu: sune sharifan da suke da nasaba wadda bata yanke ba ko
bata katse ba, kuma a gurin da suke da zama an yarda cewa su sharifai
ne, suka kubuta da kokwanton masana, suna da tarihinsu amman
malamai fakihai masana nasaba basu tabbatar dasu cikin Tarihi ba kuma
hakan yana afkuwa ne musamman bisa dalili na yin hijira, ko rashin
marubuta tarihi da nazarinsa a gurin da suke ko kuma boye kansu da
sharifan suke a wanchan lokacin
66
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(3) Daraja ta uku: sune sharifan da basu da nasaba, malamai fakihai basu
tabbatar dasu ba a cikin tarihi (a cikin litattafan nasaba), suna da tarihin
zuriyarsu kuma sun shahara cewa su sharifai ne a garin da suke ko
yankin da suke kuma babu kokwanto akansu.
(4) Daraja ta hudu: sune sharifan da suke da nasaba amman akwai
yankewa, kakkatsewa ko kuma samuwar sunayen da babu su a cikin
nasaba tabbatacciya, malamai masana tarihi basu tabbatar dasu ba,
amman sun shahara da nasabar su a guri ko yankin da suke sannan
akwai sabani dangane da aminta da nasabarsu ko akasin haka.
(5) Daraja ta biyar: sharifan da basu da nasaba, basa cikin tarihin malamai
masana nasaba, basu shahara da nasabar ba, kuma akwai kokwanto ko
zato dangane da da’awarsu, sannan kuma basu da tarihin zuriyarsu.
A wannan bangare, zamufi rinjayarwa da kuma amincewa da sahihancin
bangare na daya dana biyu da kuma na uku, amman hakika na hudu dana
biyar suna bukatar zuzzurfan bincike kafin aminta dasu kokuma akasin
hakan.
A karshe, rashin samuwar nasaba bashine mataki na farko wajen yarda ko
kin yarda da zuriyar sharifai ba, saudayawa, cikakkun sharifai sukan rasa
nasabar su bisa dalili na mutuwa, yaki, yin hijira, wanzuwa ko zama cikin
al’ummatan da basa kiyaye tarihi, boye kansu da sukeyi dama dalilai masu
tarin yawa.
Janhankali
Hakika su Sharifai, mutanene wadanda Allah ya daukaka su kasantuwar sun
fito daga gidan Annabi (SAW) kuma suka samu soyayyar Allah ta dalilin son
da Annabi yake yiwa iyalan gidansa. Yana da kyau al’umma su sani cewa, su
Sharifai ba ma’asumai bane ba, don haka zasu iya aikata laifi ko kuma sabo,
amman, dolone a kiyaye alfarmar gidan Annabi (SAW) a gare su koda kuwa
angan su suna aikata wani laifi wanda ya sabawa shari’a. yana da kyau
musani cewa, tozarta Sharifi ko cinmutuncin sa tare da wulakanta shi, dai
dai yake da aibata gidan Annabi (SAW) domin shi dan Annabi ne, kuma ya
zama dole ga musulmai da su kare martabar gidan Annabi.
67
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Domin zama hujja, yana da muhimmanci na kawo kadiyyar data afku bayan
wafatin Annabi (SAW) a Madina, akwai wani babban malami daya dinga
kyamata da kuma jin haushin wani Sharifi jikan Annabi (SAW) bisa sauka
daga doron Shari’a da yayi, rannan ya shiga Masallacin Annabi ya kwanta
yana fuskantar Raudar Annabi (SAW) sai yayi mafarki da Annabi yana cewa
da shi “Ya kai wane (Annabi ya ambaci sunansa) mai ya kaika tsanar
ya’ya’na? sai nace: ina neman tsarin Allah, ya Annabin Allah ni ban tsane su
ba, kawai na tsani abunda naga suna aikatawa na sauka daga doron Sunna
ne, sai Yace dani, Shin ba’a samun mai futuna/maraji cikin nasaba? Sai nace
hakane ya rasulullah, sai yace dani: wannan dan nawa mai futuna ne 33.
Wannan yana nuna mana kiyaye alfarmar Sharifai koda kuwa sun kasance
sun sauka daga layin shari’a, domin cin mutuncinsu da kuma tozarta su
kamar aibata gidan Annabi (SAW) ne.
Musani cewa, dukkaninmu batattu ne sai da Annabi yazo sannan muka
shiriya kuma bamu da tabbacin zamu mutu akan shiriya sai dai fatan haka.
Musulmi na kawarai yazama dole ya dinga yiwa duk sharifin da ya sauka
daga doron Shari’a addu’a domin bayyanar da soyayyarsa ga Annabi, yazo
cewa lokacin da mahaifin Sayyadi Abubakar ya musulunta, cewa yayi, “wlh
musuluntar wasu daga zuriyar Annabi (SAW) yafi masa soyuwa daga
musuluntar mahaifansa”. Don haka, yazama wajibi musulmai suso
shiryuwar Sharifai sama da Shiryuwar nasu ya’yan da kuma makusantansu.
Idan mukayi duba na tsanaki, zamuga cewa, mafi yawan Sharifai ba
mawadata bane wanda hakan shine mafi kolkoluwar darajarsu, kamar
yadda yazo a cikin Sira ta annabi (SAW) inda Allah ya bashi zabin duniya da
kuma lahira amma sai ya zabi lahira akan duniya. Annabi (SAW) da kansa ya
rokarwa iyalan gidansa rayuwa wadda take mai albarka kuma tsaka tsaki,
yazo a hadisi inda Annabi yayi musu addu’a cewa:
“Allahuma Ij’al Rizka Ahli Muhammadan Kutan”34
“Allah ka sanya Arzikin Ahalin Annabi (SAW) iya abunda zai wadace su”
Kasantuwar daukakar neman duniya ga daukacin halitta, amma su kuma
Sharifai kakansu Annabi (SAW) yayi musu addu’a ta samun lahira da kuma
samun rayuwa irin wadda yayi, kuma su a garesu itace mafi kwalkoluwar
68
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
darajarsu tare da samun soyayyar ubangijin su. Hakan ba yana nuna cewa
baza’a samu Sharifi mai tarin arziki ba, samun dukiya falala ce daga Allah
kuma koda an samu ahalin Annabi da tarin dukiya, mafi aksari sukanyi
rayuwa mai matukar sauki tare da yabawa hadi da zama abun alfahari
wajen al’umma.
Sashi Na Biyar
Gidan Annabta (SAW)
Muhammad
Abu-Dalib (SAW) Abbas
69
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Muhammad
Aliyu Ishak Isma’il Mu’awiya
Alkasim
Abdurrahman Muhammad Ja’afar Yazid Aliyu
Abdullahi Abdullahi Saleh
\
Gidan Annabi (SAW)
Shugaban mu kuma Annabin mu (SAW) ya haifi ya’ya guda bakwai, guda 3
maza da kuma guda 4 mata. Mazan sune: Alkasim shine wanda ake yiwa
Annabi Alkunya dashi inda ake kiransa da Abul-Kasim (SAW), sai Abdullahi
da kuma Ibrahim Al-Mu’azzam. Matan sune: Rukayya, Ummu-Kulsum,
Zainab da kuma Fadima (Radiyallahu Anhum). kuma ita Nana Fadima ita
kadaice ta yada zuriya cikin ya’yan Annabi (SAW), haka nan dukkan wani
sharifi da yake a duniya indai yana jingina kanshi zuwa ga Annabi, to ya
fitane ta tsatson Nana Fadima (RA).
70
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sayyadina Ali a matsayin wanda ya zaba daya aureta, yazo cewa Sayyadina
Abubakar khalifan Annabi da kuma sayyadina Umar Amirul Mu’minina duk
sun nemi auren Nana fadima inda daga bisani kuma shima Sayyadina Ali ya
nema kuma Allah ya kaddara aurensa da ita1.
Sayyadina Ali ya auri Nana fadima a Madina tanada shekara goma sha
takwas (18) kuma ta Haifa masa sayyadina Hassan wanda shine babba
kuma na farko cikin jerin ya’yan sayyadina Ali da kuma Nana Fadima, an
haifeshi shekara ta uku bayan hijra inda Manzon Allah (SAW) dakansa ya
sanya masa suna Hassan, Na biyu cikin Jerin ya’yan Nana Fadima da kuma
Sayyadina Ali shine Sayyadi Hussain Al-Shahid wanda malamai sun tabbatar
da cewa tsakaninsa da sayyadina Hassan wata shida ne kuma an haifeshi
hijira tana da shekara hudu kuma Manzon Allah (SAW) yayi wafati
sayyadina Hassan yana da shekara 8 inda sayyadina Hussain yake da
shekara 72. Malamai sun kawo cewa, tsakanin haihuwar Imam Hassan da
kuma samun cikin Imam Hussain Allah ya kara yarda a garesu, kwana
Hamsin ne3, ta ukunsu itace Zainab Al-Kubra sai kuma ta hudunsu itace
Ummu-Kulsum wadda Amirul Mu’uminin wato sayyadina Umar ya aureta,
Wadannan sune gidan farko cikin jerin ya’yan sayyadina Ali kuma sune mafi
kolkoluwar daraja cikin daukacin sharifai ko Ahlul-Baiti kasantuwar sun
hada Nasaba ta kai tsaye da Annabi (SAW) kuma jinin Annabi yana
gudanuwa a jikinsu da kuma na tsatsonsu baki daya, ana kiransu da Sharifai
“Fadimai ko Fadimiyyin” cikin jerin Ahlul-Baiti3.
Bayan wafatin Annabi (SAW) da wata shida, Allah ya karbi rayuwar Nana
Fadima (RA) kuma hakan ya sanya sayyadina Ali auren wasu matan inda
sune suka Haifa masa ragowar ya’yansa. Malamai sun ayyana mana
sunayen matan da sayyadina Ali ya aura bayan rasuwar Nana fadima kuma
sune: Umama bint Abul-As (wadda itama jikar Annabi (SAW) ce, kuma itace
wadda tahau bayan Annabi lokacin da yake Sallah, Ummul-Banin Hizam
Amriyyatu daga bani Kilab, Laila bint Mas’ud Al-Taimiyyah, Asma’u bint
Umais Al-Kas’amiyyah, Sahba’u bint Rabi’ah daga banu Jasum bin Bakar,
Khaulatu bint Ja’afar Al-Hanafiyyah, Ummu-Sa’id bint Urwah bin Mas’ud,
Mihyatu bint Umra’ul Kaisu Al-Kalbiyyah. Sai dai, ba’a iya kididdige yawan
71
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
72
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
73
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
74
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
A wata ruwayar wadda Shekh Al-Abdili yazo da ita da kuma Shekh Aliyu bin
Muhammad Al-Alawi, sun kawo cewa “Imam Hassan ya haifi ya’ya goma
sha shida inda sha daya maza ne kuma 5 mata ne, mazan sune: Hassan,
Zaidu, Hussain, Dalha, Isma’il, Abdullahi, Hamza, Ya’kub, Abdurrahman,
Abubakar da kuma Umar, Hakanan masu nasaba sunce Abdullahi da ake
kawo shi shine Abubakar kuma an kara da Alkasim (cikin jerin ya’yan imam
Hassan) wanda kari ne sahihi wanda ya inganta, amma a bangaren matan
an samu sabanin sunaye inda aka fara gabatar da sunansu kamar haka:
Ummu-Hussain (Al-Kirkal) Ramlatu, Ummu-Hassan Fadima, Ummu-
Salamah, Ummu-Abdullahi amman an kara da sunan Rukayya ga wadanda
suke cewa (ya’yan nasa) su shida ne, a kaulin Shekh Aliyu bin Muhammad
Al-Alawi ya kawo sunayensu akamar haka: Fadima, da Ummul-Kair
(Ramlatu), da Ummu-Hassan, da Ummu-Salamah, da kuma Ummu-
Abdullahi10.
Daukacin malamai kuma fakihai cikin ilimin nasaba sun tabbatar da cewa
mutum uku ne kawai cikin ya’yan Imam Hassan suka fitar da zuriya kuma
sune: Imam Zaidu, Imam Hassan Al-Musannah da kuma yarsa fadima bint
Hassan11. Hakan yana nuna mana cewa biyu maza ne inda kuma guda dayar
mace ce, ita macen wato fadima bint Hassan mafi yawanci ba’a fiya kawota
ba saboda anyi auren zumunci ne tsakanin gidan Imam Hassan da kuma na
Imam Hussain inda ta auri dan gidan Imam Husaini wato Imam Aliyu Zainul-
Abidin kuma ta Haifa masa Muhammad Al-Bakir, da Abdullahi,da Hassan da
kuma Hussain Al-Akbar. Dililin auren da Fadima bint Hassan tayi a gidan
Imam Hussain ya jawo da yawa daga cikin malamai ke kaddara cewa Imam
Hassan Al-Musannah da kuma Imam Zaidu sune suka yada zuriyar Imam
Hassan dogaro da cewa anfi jingina ya’yan Fadima bint Hassan izuwa ga
Imam Hussain duk da cewa daukacin malaman nasaba sun aminta da
kasantuwar jinin Imam Hassan tattare dasu ta bangaren mahaifiyarsu.
Ummu-Abdullah
Imam
Ummu-Salamah Hassan bin
Imam Aliyu
Ummu-Hassan
75
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Abdurrahman
Abubakar
Alkasim
Abdullahi
Hassan Isma’il Fadima Ramlatu Hamza Hussain Ya’akub Umar Dalha Zaidu
Hassan
76
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
77
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
78
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
79
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(6) Idriss dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-Musannah dan Imam
Hassan: A mafi ingancin zance, Imam Idriss Al-Akbar ya haifi ya’ya
guda biyu, ta farkon itace Fadima yar gidan Imam Idriss kuma ya
haifeta ne a Madinatul Munauwara tun kafin ya taho izuwa magrib,
Bayan tahowar sa (Idriss) izuwa Maghrib yar’sa Fadima ta auri
Muhammad dan Yahya dan Abdullahi Al-Kamil kuma itace ta Haifa
masa (ta haifawa Muhammad dan yahya) ya’yansa wato Ahmad da
kuma Abdullahi25. Bayan saukarsa a Magrib ya auri baiwa yar Kabilar
Barbar ana kiranta da sunan “Kanzatu” wadda su (Mutanen Maghrib)
asalinsu ba Larabawa bane, Idriss ya rasu ya barta da ciki inda bayan
rasuwarsa da wata hudu ta Haifa masa da namiji inda aka sanya masa
sunan mahaifin sa wato Idriss kenan kuma ana yimasa lakabi da Idriss
Al-Asgar (Idriss Karami) 26. Idriss na biyu ya rayu anan cikin Magrib
wato kasar Morocco kenan a yanzu cikin Kabilar Barbar inda suka
girmama shi tare da shugabantar dashi kuma ya auri yar kabilar inda
ta Haifa masa ya’ya goma sha biyu, a wata ruwayar kuma ya haifi
ya’ya sama da haka27. Mafi ingancin zance da kuma shuhura wajen
Ijma’in malaman nasaba shine, Idriss Al-Asgar dan Idriss Al-Akbar ya
haifi ya’ya goma sha biyu kuma sune: Muhammad Al-Khalifa wanda
shine babban su kuma shine ya gaji sauratar mahaifinsu bayan
rasuwar sa, sai Ahmad, Abdullahi, Umar, Hamza, Dawud, Isa, Alkasim,
Yahya Aliyyu, Ja’afar, da kuma Idriss. Wasu daga cikin Malaman
Nasaba suna karawa da Kasir, Hassan, Husaain, Sulaiman, Ibrahim da
kuma Imran28.Amman a mafi ingancin zance, wadanchan sha-biyun
sune sukafi ingantuwa da kuma shuhura wajen Malaman Nasaba.
kowanne daga cikin ya’yan Idriss Al-Asgar dan Idriss Al-Akbar ya bar zuriya
kamar haka:
(1) Ya’yan Muhammad Al-Khalifa dan Idriss Al-Asghar: yazo cewa
Muhammad bin Idriss Al-Asghar ya haifi ya’ya guda uku sune: Aliyu
wanda ake ce masa “Haidara” kuma mahaifiyarsa itace Rukayyatu
bint Isma’il bin Amir bin Mus’ab Al-Azdi, da Abu Zakariyyah Yahya da
kuma Abu-Isma’il Ibrahim, wasu sunce yana da wani dan
80
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
81
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(9) Ya’yan Ahmad bin Idriss Al-Asgar: ya haifi dansa mai suna Kunun37
(10) Ya’yan Idriss dan Idriss Al-Asgar bin Idriss Al-Akbar: ya haifi
dansa mai suna Idriss shi kadai38
(11) Ya’yan Aliyu dan Idriss Al-Asgar: ya haifi Umar inda shi kuma
Umar ya haifi Muhammad da kuma Abdullahi39
(12) Ya’yan Ja’afar dan Idriss Al-Asgar: ya haifi Musa.40
Gidan Abdullahi Al-Kamil
Musa Al-Jauni
Sulaiman
Muhammad Nafsuzakiyya
Abdullahi
Yahya Sahibul- Daylam Al-Kamil
Ibrahim
Idriss Al-Akhbar
Fadima
Muhammad Imam
Idriss Al-
Abdullahi Umar Aliyu
Akbar
Idriss Idriss Imam
Yahya Idriss Al-
Asgar
Muhammad Yahya Ahmad
82
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Abdullahi
Sidi Maimun
Sidi Aliyu
Sidi Ahmad
Hussain Aliyu
Aliyu Hassan
Muhammad Aliyu
83 Ibrahim bin
Abdullahi
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Abdullahi Hassan
Muhammad
Ibrahim Ibrahim
Hassan Ahmad
Muhammad Sulaiman
Hassan Abdullahi
84
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Hassan
Muhammad
Yahya
Muhammad Hussain
85
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ibrahim
Aliyu Isma’il Al-Dibaj
Al-
Abdullahi Ibrahim Duba-Duba Gamar
Ahmad Muhammad
Ibrahim Muhammad
Muhamad Hassan
86
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Hussain Hassan
Abi-Dahir Abdul’azim
Aliyu
Muhammad Muhammad
Hassan
Al-
Aliyu Al-Abid Musalisu
Al-Hussain Hassan
Abdullahi
Aliyu
87
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Hassan
Muhammad
Aliyu Musa
Muhammad Alhassan
Ja’afar
Hassan
Ubaidullah
Abdullahi
Ubaidullah
88
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Muhammad Muhammad
Kamuludeen Abdullahi
Ahmad Muhammad
Abul-Hawal Tajuddeen
Ibrahim
Dawud
Ishak
Hassan
Sulaiman
Muhammad
Musa
Ishak
Muhammad
Katadah Zaidu
89
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Muhammad Aliyu
Hussain
90
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ansari yana tambayar sa akan nasabarsa sai jabir ya bashi labari kuma
yace dashi “Kakanka Manzon Allah (SAW) yace dani in isar da gaisuwar
sa a gareka”48. Muhammad Al-Bakir ya haifi da guda daya wato Ja’afar
Al-Sadik kuma shine ya yada zuriyar Muhammad Al-Bakir. Ja’afar Al-
Sadik ya haifi ya’ya bakwai inda a wata ruwayar kuma ya haifi sama da
bakwai amman wadanda suka yada zuriyar sa susu biyar ne kuma sune:
Musa Al-Kazim da Isma’il da Aliyu Al-Aridi da Muhammad Al-Ma’amun
ko kuma Muhammad Al-Dibaj da kuma Ishak. Shi Musa Al-Kazim ana
yimasa lakabi da Abu-Ibrahim ko Abu-Alhassan kuma ya haifi ya’ya goma
sha hudu sune: Hassan, Hussain, Aliyyu Al-Rida, Ibrahim Al-Murtada,
Zaidun-Nari, Abdullahi, Ubaidullah, Abbas, Hamza, Ja’afar, Haruna,
Isma’il, Ishak da kuma Muhammad Al-Abid, a wata ruwayar kuma ya
haifi ya’ya 59 inda mata susu 37 da kuma maza susu 2249.
(2) Abdullahi Al-Bahir dan Aliyu Zainul-Abidin: ya haifi dansa mai suna
Muhammad Al-Arkad, shima (Muhammad Al-Arkad) zuriyar sa sun fita
daga dansa guda daya wato Isma’il, inda Isma’il ya haifi Muhammad da
kuma Hussaini50.
(3) Umar Al-Asharaf dan Aliyu Zainul-Abidin: ana yi masa alkunya da Abu-
Ali ko kuma Abu-Hafsa. Daukacin zuriyar sa sun fita ne daga dansa mai
suna Aliyu Al-Asgar inda shi kuma (Aliyu) ya haifi ya’ya guda uku sune:
Alkasim, Umar Al-Shajri da kuma Abu-Muhammad Al-Hassan. Alkasim
zuriyar sa sun fita ne daga dansa Abi-Ja’afar Muhammad Al-Sufi. Shi
kuma Hassan ya haifi ya’ya guda uku sune: Abi-Hassan Aliyu Al-Askari,
Ja’afar Dibaj da kuma Abu-Ja’afar Muhammad. Shi Abu-Hassan Aliyu Al-
Askari ya haifi ya’ya guda uku sune: Abi Aliyu Ahmad sufi, Abi-Abdallah
Hussain, da kuma Abi Muhammad Al-Hassan. Umar Al-Shajri dan Aliyu
dan Umar Al-Ashraf, tsatsonsa sun fita ne daga dansa Abu-Abdullahi
Muhammad inda shi (Abu-Abdullahi Muhammad) ya haifi ya’ya guda
biyu sune: Umar da kuma Aliyyu51.
(4) Hussain Al-Asgar dan Aliyu Zainul-Abidin: ana yi masa alkunya da Abu-
Abdallah. Daukacin tsatson sa sun fita ne daga ya’yan sa guda biyar
sune: Abdullahi, Aliyu, Sulaiman, Ubaidullah Al-A’araji, da kuma Abu-
Muhammad Al-Hassan52.
91
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(5) Aliyu Al-Asgar dan Aliyu Zainul-Abidin: ana yi masa alkunya da Abul-
Hassan. Ya haifi dansa Hassan Al-Afdash kuma shine ya yada zuriyar sa,
shima (Hassan Al-Afdash) ya haifi ya’ya guda biyar sune: Aliyu, Umar,
Husaain, Hassan Al-Makhfuf da kuma Abdullahi Al-Shahid53
(6) Zaid Al-Shahid dan Aliyu Zainul-Abidin: ana yi masa alkunya da Abu Al-
Hassan. Zuriyar sa sun fita ne daga ya’yan sa guda uku sune: Hussain da
Isa da kuma Muhammad, Amma dansa (dan Imam Zaid Al-Shahid) Yahya
Al-Akbar ya mutu bai bar zuriya ba. Hussain ya haifi ya’ya uku sune:
Yahya, Hussain da kuma Aliyu. Muhammad dan Zaid Al-Shahid ya haifi
dansa guda daya shine: Abu-Abdallah Ja’afar Al-Sha’ir. Isa dan Zaid Al-
Shahid wanda ake yi masa Alkunya da Abu-Yahya ya haifi ya’ya guda
hudu wanda sune suka yada masa zuriya sune: Ahmad Al-Muktafi, Zaidu,
Muhammad da kuma Al-Hussain. Hakanan yazo cewa Zaidu Al-Shahid ya
haifi wata mace amma kuma ta mutu 54. Imam
Fadima
Hussain
Muhammad Ja’afar
Muhammad Muhammad
92
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ubaidullah Hussain Aliyu Ibrahim Muhammad Abdullahi Isma’Il Abbas Zaid Haruna Hamza
Bangaren Muhammad dan Hanafiyya kuma dan Imam Aliyyu bin Abi
Dalib
Ana yi masa alkunya da Abu-Alkasim. Wadanda suka fitar da zuriya daga
tsatson sa (tsatson Muhammad dan Hanafiyya) sune: Aliyu da kuma Ja’afar.
Amma dansa (Dan Muhammad Al-Hanafiyya) wanda ake kira da abu
Hisham wato Abdullahi Al-Akbar tsatson sa sun yanke ko sun kare, hakanan
Imam Tajuddeen yana cewa tsatson Muhammad dan Hanafiyya yan Kadan
ne matuka55.
Ja’afar dan Muhammad Al-Hanafiyya ya haifi dansa guda daya mai suna
Abdullahi inda shima Abdullahi ya haifi da guda daya mai suna Ja’afar Al-
Sani inda shima (Ja’afar Al-Sani) ya haifi Abdullahi.Shi kuma Aliyyu dan
Muhammad dan Hanafiyya ya haifi Aba-Muhammad Hassan.
Muhammad
dan
Abu-Hashim Abdullahi Hanafiyyah
Ja’afar
93
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Abdullahi
Ja’afar
Abdullahi Muhammad
Aliyu
Abu-Hassan Ahmad
Abu-Muhammad Al-Hassan
Alkasim Al-Hussain
Abbas dan
Imam
Abdullahi
Aliyyu
Al-Abbas Hassan
Ubaidullah Hassan
Hamza Abdullahi
Muhammd Hassan
94
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Yahya Muhammad
Umar
Al-
Muhammad Adraf
Ubaidullah
Ibrahim Isma’il
95
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Shi Isma’il bin Abdullahi bin Ja’afar bai wani haihu da yawa ba kusan ma
ance ya’ mace kawai ya bari (ita ta bar masa zuriya) 5.
Ishaq bin Abdullahi dan Ja’afar ya haifi ya’ya guda uku sune: Muhammad da
Ja’afar da kuma Alkasim.
Aliyu dan Abdullahi dan Ja’afar ya haifi Muhammad Al-Ra’is kuma shi kadai
ne ya fitar da zuriya a tsatson Aliyu. Muhammad Al-Ra’isi wanda ake yi
masa alkunya da Abu-Abdullahi ya haifi: Ibrahim, Abdullahi, Isa da kuma
Yahya.
Hamidu Musawir
Muhammad Al-Asgar
Ja’afar Alkasim
Muhammad Ja’afar
96
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Aliyu Abdullahi
Hassan Abdullahi
Muhammad
Muslim Ahmad
97
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Haris
Sayyadina
Ubaidullah Abbas bin
Kusam Abdulmutallib
Ummu-Hani
Mu’abbad
Fadlu
Kasir
98
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Aminatu
Safiyya
Sashi Na Shida
Dalilan Yaduwa Ahlul-Baiti a Sassan Duniya.
Hakika Allah madaukakin sarki yayi mana bayani a ayoyi da yawa akan
girman kadarin Ahlul-Baiti da kuma daukakar darajar su hadi da kaunar su
ga ilahirin al’umma, Hadisan Annabi (SAW) suma sun yi mana bayani akan
su da kuma tsoratar damu akan taba su da kuma saba musu. Yazo cikin
Hadisi inda Manzon Allah (SAW) yake gaya mana cewa
“Iyalan gida na (Ahlul-Baiti) kamar jirgin Annabi Nuhu ne (A.S) inda duk
wanda ya shiga jirgin to ya tsira kuma duk wanda yaki shiga to kuwa ya
halaka”1.
Wannan hadisin yana nuna mana muhimmancin su cikin Addini da kuma
girman su a gurin Allah. Annabi (SAW) yasan cewa za’aci zarafin ya’yansa da
kuma jikokansa bayan tafiyarsa, yazo a cikin Hadisi cewa Mala’ika Jibrill ya
gayawa Annabi (SAW) cewa Sayyadina Hussain Kashe za’ayi wanda hakan
matuka ya sanya Annabi bakin ciki da kuma juyayin hakan har sai da Annabi
ya zubar da hawaye akan hakan. Hakanan yazo cewa Annabi (SAW) ya tsaya
a Fakh wanda guri ne tsakanin Makkah da kuma Madina inda ya bawa
sahabbansa labarin cewa a wannan guri ne za’a kashe wasu daga iyalan
gidansa2.
Bayan wafatin Annabi (SAW) da kuma na kalifofinsa masu girma, Ahlul-Baiti
sun shiga dimuwa matuka bisa yakin da akayi a Karbala wanda shine ya
Janyo Kisan Imam Hussaini da kuma dayawa daga cikin Jikokan Annabi
(SAW) da kuma mabiyansu. Tun kafin yakin, Imam Hassan aka fara kashewa
99
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
ta hanyar bashi guba inda hakan yayi sanadiyyar ajalinsa. Bayan Kisan Imam
Hassan da kuma na Imam Hussain, Ahlul-Baiti sun shiga rayuwa ta
Azabtarwa da ake yi musu hadi da tozartawa, zaginsu da kuma cin
mutuncinsu, kullesu, basu guba, dama uwa uba kisansu da aka dingayi 3. A
wannan lokaci, ya kasance al’ada wajen zagin Imam Aliyu da kuma daukacin
Ahlul-Baiti a bayyane da kuma hawa mumbari domin zaginsu, ya kasance
ziyarar kabarin Imam Hussain laifi ne babba wajen hukuma wanda hakan ka
iya bayuwa ga kullewa, azabtarwa ko kuma kashewa4.
Sanannen Malamin nan kuma masani wajen Tarihi Imam Abu-Farrij Al-
Asfahani ya jero sunayen Ahlul-Baiti wadanda aka kashe tun daga farko
wanda hakan ya janyo dayawa daga cikinsu suka bar garinsu na haihuwa
wato Madina izuwa sassa daban daban na duniya. Bisa nazari da kuma
tarihi, sai da yazamto mafi yawancin sharifai sun bar Madina inda har yanzu
sharifai sunfi yawa a wasu sassan duniya sama da garinsu na asali wanda
hakan ya samo asali ne tun daga ficewarsu a wanchan lokaci da daular Banu
Umayyad da kuma ta banu Abbas ke shugabanci.
Imam Abu-Farrij Al-Asfahani ya jero sunayen Ahlul-Baiti wanda suka hada
da wadanda aka kashe da kuma wadanda aka kulle su a kurkuku tun daga
lokacin Manzon Allah (SAW) har izuwa lokacin da aka kammala rubuta
littafin5. Zamu kasasu izuwa sahu-sahu da kuma lokacin da aka kashesu.
Sahun farko na wadanda sukayi shahada cikin Ahlul-Baiti.
Wadanda aka fara kashewa cikin Ahlul-Baiti sune:
(1) Ja’afar bin Abi-Dalib: shine farkon wanda aka fara kashewa a cikin
Ahlulbayt bayan kafuwar addinin Musulunci (wato bayan aiko Annabi
SAW), ana yiwa Sayyadi Ja’afar alkunya da Abul-Masakin kuma ya
shahara da sunan Ja’afar Al-Dayyar, shine na uku cikin jerin ya’yan
mahaifinsa wato Sayyadi Abu-Dalib. An kashe Sayyadi Ja’afar a yakin
Mu’uta kuma ya zama kwamandan yakin kafin kashe shi. Kuma an kashe
shi kafin wafatin Annabi (SAW).
(2) Imam Aliyu bin Abi-Dalib: Allah madaukakin Sarki ya daga darajar Imam
Aliyyu ta bangarori da yawa, shine wanda Mahaifiyar sa ta haifeshi a
cikin dakin Allah mai alfarma wato Ka’aba kenan kuma ta sanya masa
100
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Haidara inda daga bisani kuma Mahaifinsa ya sanya masa suna Aliyyu
inda Annabi ya sanya masa suna Abul-Turab. Ya Auri Nana Fadima Al-
Zahra’u yar’ Manzon Allah (SAW) kuma ana yi masa alkunya da Abal-
Hasnain wato baban Hassan da kuma Hussain. Imam Aliyu shine wanda
Manzon Allah (SAW) yace “Duk wanda ya yarda cewa Ni (SAW)
Shugaban sa ne to Aliyu shima shugaban sa ne”. yayi kalifanci bisa
jajircewa da kuma tsayuwa akan gaskiya da kuma Adalci, ya kasance mai
sanyi da kuma hakuri ga kowa, hakanan mai matukar zafi ne kuma baya
son raini ko wargi wajen aiwatar da shari’a da kuma shugabanci, ana
siffanta shi da karfi kuma anjiyo shi a yakin Kaibar yana cewa “Nine
wanda Mahaifiyata ta sanya mini sunan Haidara”6. Kalmar Haidara ai
ma’anarta shine “Zaki”, Sayyadina Ali yakan Rusa runduna duk karfinta
kuma duk inda ya tunkara to saidai wasu su maye gurbin su. Mutum ne
mai matukar tsoron Allah tare da kiyaye dokokin sa kuma Allah ya
Azurta shi da ilimi inda khalifofin Annabi wanda suka gabace shi a
halifanci suma sukan nemi fatawa a gurinsa. Ya rasu a Kufa wato Irak
kenan a yanzu inda Abdurrahman Ibn Muljum ya Kashe shi yana Sallah a
masallaci a watan Ramadan7.
(3) Imam Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib: shine dan Nana Fadima da kuma
Sayyadina Ali na farko kuma Jikan Annabi (SAW). Ana yi masa alkunya da
Aba-Muhammad, shine wanda Manzon Allah (SAW) yayi ishara dashi
cewa “Zai sulhunta wasu rundunoni guda biyu na Musulmai masu fada
da juna” wato rundunar sayyadina Ali da kuma ta Sayyadina Mu’awiya,
yayin da ya karbi Halifanci sai ya sasanta tare da zama karkashin
shugabanci guda daya. Yazo cewa an hada baki da matarsa mai suna
Ja’adatu inda ta bashi guba kuma wannan gubar itace ta zamo ajalinsa 8.
Sahu na biyu cikn wadanda sukayi shahada a Ahlul-Baiti, Sune wadanda
aka kashe tare da Imam Hussain a Karbala
(1) Muslim bin Akilu bin Abi-Dalib: shine farkon wanda aka fara kashewa
cikin sahabban Imam Hussain kuma an kashe shine tun kafin a kashe
Imam Hussaini da yan kwanaki. Lokacin da wasiku suka yawaita kuma
kiran Imam Hussain ya daukaka ga mutanen Iraq akan yazo suyi masa
mubayi’a sai ya tura Muslim bin Akilu bin Abi-Dalib akan yaje gurinsu
101
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
102
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangare na Uku
Wannan bangare ya hadar da wadanda Al’umma suka kashe su dalili na
rigin-gimu ko wata hatsaniya ko kumama sabani daya afku, hakanan ya
hadar da wadanda shugabanni na wanchan lokaci suka kashe koma suka
kulle su a kurkuku har saida sukayi shahada, mafi aksarinsu an kashe sune a
lokacin daular Banu Umayyad. Jerin wadanda sukayi shahada a lokacin
sune:
(1) Abubakar bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(2) Aunu Al-Asghar bin Abdullahi bin Ja’afar bin Aliyu bin Abi-Dalib
(3) Abdullahi bin Aliyu bin Abi-Dalib
(4) Abdullahi bin Muhammad bin Aliyu bin Abi-Dalib
(5) Zaidu bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib: Imam zaidu yayi yaki
da gwamnatin Umayyad wato gwamnatin Hisham bin Abdulmalik a garin
kufa. Yusuf bin Umar Al-Sakafi ya bada kudi ga mutanen kufa inda suka
bari aka samu nasara akan Imam Zaidu kuma aka kashe shi10. Lokacin da
aka kashe Imam Zaidu Jarir bin Hizam yace yaga Annabi (SAW) a mafarki
yana cewa da mutane “Shin haka kuka aikata ga ya’ya’na/Iyalina”11.
(6) Yahya bin Zaidu bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib: yayi bore
ga gwamnatin Umayyad inda aka kashe mutanensa kuma aka rataye shi
a kofar garin Jurjan inda daga bisani aka tura da kansa (wato aka yanke
kansa) izuwa ga Nasir bin Sayyar inda shi kuma ya tura shi izuwa ga Al-
Walid bin Yazid12.
(7) Abdullahi bin Muhammad bin Aliyyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(8) Abdullahi bin Al-Miswar bin Aunu bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(9) Abdullahi bin Mu’awiyata bin Abdullahi bin Ja’afar bin Aliyu bin Abi-Dalib
(10) Ubaidullah bin Hussain bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
103
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(2) Hassan (Al-Musallisu) bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib: An
kamashi kuma an kulle shi a cikin kurkuku har sai da ya rasu a ciki.
(3) Ibrahim bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib: an kamashi kuma
an kullecshi a cikin kurkuku har sai da ya rasu.
(4) Aliyu bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib: Al-Hussain bin Nasir
yana cewa “Abu-Ja’afar Al-Mansur ya kulle su tsawon dare sittin basa iya
gane dare ko rana kuma basa sanin lokacin sallah yayi sai idan Aliyu bin
Hassan yayi tasbihi (Sannan suke gane cewa lokacin Sallah yayi). Allah ya
karbi rayuwar sa a cikin kurkuku.
(5) Muhammad Nafsuzzakiyya dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-
Musannah dan Imam Hassan dan Aliyu da kuma Nana Fadima
(6) Ibrahim dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-Musannah dan Imam
Hassan Al-Mujtaba
(7) Abdullahi Al-Ashtar dan Muhammad Nafsuzzakiyya dan Abdullahi Al-
Kamil dan Hassan Al-Musannah dan Hassan Al-Mujtaba
(8) Aliyu Al-Abid dan Hassan Al-Musallisu dan Hassan Al-Musannah dan
Hassan Al-Mujtaba
(9) Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(10) Abbas bin Hassan bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(11) Isma’il bin Ibrahim bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(Yazo cewa shine ake cewa Duba-Duba): An tambayi Abdurrahman bin
Mawali akan halin da suke ciki (Ahlul-Baiti a kurkuku) a lokacin da yake
tare dasu, sai yace “sun kasance cikin hakuri”, yayi ishara da Isma’il bin
Ibrahim bin Hassan bin Hassan inda yake cewa “Duk lokacin da aka
tsananta azaba a gareshi (A cikin Kurkuku) sai hakurinsa ya kuma
karuwa”13.
(12) Muhammad bin Ibrahim bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-
Dalib: An rawaito cewa Abu Ja’afar yazo (inda Muhammad bin Ibrahim
bin Hassan bin Hassan yake) sai ya kalle shi yace da shi: Kaine Dibaj Al-
Asfar? Sai ya amsa masa da cewa: A shine; sai yace (Abu Mansur)
Wallahi sai na kashe ka, kashewa wadda ban taba yiwa wani a cikin
Ahalin gidanku ba, Abu Mansur yasa an saka shi a cikin gini alhalin yana
raye (wato an gine shi a cikin gini)14
104
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(13) Aliyu bin Muhammad bin Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin Aliyu
bin Abi Dalib: Abu-Ja’afar ya kulle shi tare da iyalan sa a cikin kurkuku
har sai da ya mutu.
(14) Muhammad bin Abdullahi bin Amru bin Usman bin Affan: duk da
cewa nasabar sa tana danganuwa ne da Sayyadina Usman Khalifan
Manzon Allah (SAW) amman, a daya bangaren shima Ahlul-Baiti ne
domin Mahaifiyar sa Jikar Manzon Allah ce (SAW) kuma itace Fadima
bint Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib, bayan rasuwar Hassan Al-Musannah
sai Abdullahi bin Amru ya aureta kuma ta Haifa masa Muhammad.
Muhammad bin Abdullahi bin Amru bin Usman bin Affan ya’yan sa sune:
Kalid, Usman, Abdul’aziz, Ubaidullah da Alkasim. Abdullahi Al-Kamil bin
Hassan Al-Musannah bin Hassan Al-Mujtaba bin Imam Aliyu (RA) ya
kasance yana son sa (yan son Muhammad bin Abdullahi bin Amru)
hakanan shima yana son su15.
(15) Hussain bin Zaidu bin Aliyu
(16) Musa bin Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib: Ya
auri jikar sayyadina Abubakar ( Ummu-Salama bint Muhammad bin
Dalha bin Abdurrahman bin Abibakar)
(17) Aliyu bin Hassan bin Zaidu bin Aliyu bin Abi-Dalib: Abu-Ja’afar ya kulle
shi a kurkuku tare da mahaifin sa Hassan bin Zaid, bai gushe ba har sai
da ya mutu a kurkuku.
(18) Hamza bin Ishak bin Aliyu bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
Lokacin Hadi
Wadanda aka kashe sune:
(1) Aliyu bin Abbas bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib: Mahaifiyar
sa jikar Sayyadina Abubakar ce (Aisha bint Muhammad bin Abdullahi bin
Muhammad bin Abdurrahman bin Abubakar) Al-Hadi ya kama shi kuma
ya kulle shi a kurkuku har sai da Hussain bin Aliyu Sahib-Fakh ya nemar
masa afuwa, amman yayin da zai fita daga kurkuku sai aka saka masa
guba kuma ta kama shi inda daga shigar shi madina da kwana uku ya
rasu16
(2) Isa bin Zaid bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
Lokacin Musal Hadi
105
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
106
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(1) Muhammad bin Muhammad bin Zaidu bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu
bin Abi-Dalib
(2) Hassan bin Hussain bin Zaid bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(3) Hassan bin Ishak bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(4) Muhammad bin Hussain bin Hassan bin Aliyu bin Aliyu bin Hussain bin
Aliyu bin Abi-Dalib
(5) Aliyu bin Abdullahi bin Muhammad bin Abdullahi Bin Muhamad bin
Aliyu Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(6) Muhammad bin Ja’afar bin Muhammad bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu
bin Abi-Dalib
(7) Abdullahi bin Ja’afar bin Ibrahim bin Ja’afar bin Hassan bin Hassan bin
Aliyu bin Abi-Dalib
(8) Aliyu bin Musa bin Ja’afar bin Muhammad bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu
bin Abi-Dalib
(9) Muhammad bin Abdullahi bin Hassan bin Aliyu bin Aliyu bin Hussain bin
Aliyu bin Abi-Dalib
(10) Muhammad bin Ibrahim bin Isma’il bin Ibrahim bin Hassan bin
Hassan bin Imam Aliyu
(11) Muhammad bin Hussain bin Hassan bin Aliyu bin Aliyu Zainul-Abidin
bin Imam Ali
Lokacin Mu’utasim
Wadanda aka kashe sune:
(1) Muhammad bin Alkasim bin Aliyu bin Umar bin Aliyu bin Hussain bin
Aliyu bin Abi-Dalib
(2) Abdullahi bin Hussain bin Abdullahi bin Isma’il ibn Abdullahi Ja’afar ibn
Abi-Dalib
Lokacin Mutawakkil
Yazo cewa, Mutawakkil yana daya daga cikin wadanda suka kai matuka
wajen matsantawa Ahlul-Baiti tare da kashesu da kuma kulle su, sai da takai
cewa ya hana ziyartar Imam Hussain tare da hukunta duk wanda yayi
ziyarar sa. wadanda aka kashe sune:
107
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(1) Abu-Abdullahi Muhammad bin Saleh bin Abdulahi bin Musa bin
Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(2) Muhammad bin Ja’afar bin Hassan bin Umar bin Aliyu bin Hussain bin
Imam Ali
(3) Alkasim bin Abdullahi bin Hussain bin Aliyu bin Hussain ibn Aliyu bin Abi-
Dalib
(4) Ahmad bin Isa bin Zaid bin bin Aliyu bin Hussain bin Imam Ali
(5) Abdullahi bin Musa bin Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin
Abi-Dalib
Lokacin Musta’in
Wadanda aka kashe sune:
(1) Yahya bin Umar bin Hussain bin Zaid bin Aliyu ibn Hussain bin Aliyu bin
Abi-Dalib:
(2) Hussain bin Muhammad bin Hamza bin Abdullahi bin Hussain bin Aliyu
bin Hussain ibn Aliyu bin Abi-Dalib
(3) Muhammad bin Ja’afar bin Hassan bin Ja’afar bin Hassan bin Hassan ibn
Aliyu bin Abi-Dalib
Lokacin Mu’utaziin
Wadanda aka kashe sune:
(1) Isma’il bin Yusuf bin Ibrahim bin Musa bin Abdullahi bin Hassan bin
Hassan
(2) Hassan bin Yusuf bin Ibrahim Musa Abdullahi bin Hassan bin Hassan
(3) Ja’afar bin Isa bin Isma’il bin Ja’afar bin Ibrahim bin Muhammad bin
Aliyu bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(4) Isa bin Isma’il bin Ja’afar bin Ibrahim bin Muhammad bin Aliyu bin
Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(5) Ja’afar bin Muhammad bin Ja’afar bin Hassan bin Aliyu bin Umar bin
Aliyu bin Hussain bin Imam Ali
(6) Ibrahim bin Muhammad bin Abdullahi bin Ubaidullah bin Hassan bin
Abdulahi bin Abbas bin Aliyu
(7) Ahmad bin Muhammad bin Yahya bin Abdullahi bin Hassan Hassan bin
Aliyu bin Abi-Dalib
108
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(8) Ahmad bin Abdullahi bin Musa bin Muhammad bin Sulaiman bin Dawud
bin Hassan bin Hassan bin Imam Ali
Lokacin Muhtadi
Wadanda aka kashe sune:
(1) Aliyu bin Zaid bin Hussain bin Isa bin Zaid bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu
bin Abi-Dalib
(2) Ja’afar bin Ishak bin Musa bin Ja’afar bin Muhammad bin Aliyu bin
Hussain bin Aliyu
(3) Musa bin Abdullahi bin Musa bin Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin
Aliyu bin Abi-Dalib: Sa’id Al-Hajib ya kamashi tare da Dansa Idriss da
kuma dan dan-uwan sa Muhammad bin Yahya bin Abdullahi bin Musa
da kuma Aba-Dahir Ahmad bin Zaid bin Hussain bin Isa bin Zaid bin Aliyu
bin Hussain izuwa Irak. An bashi guba (Musa bin Abdullahi) kuma aka
yanke kansa aka kaiwa Mahdi18
(4) Isa bin Isma’il bin Ja’afar bin Ibrahim bin Muhammad bin Abdullahi bin
Abil-Kiram bin Muhammad bin Aliyu bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-
Dalib
(5) Muhammad bin Abdullahi bin Isma’il bin Muhammad bin Abdullahi bin
Abil-Kiram bin Muhammad bin Aliyu bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-
Dalib
(6) Aliyu bin Musa bin Muhammad bin Alkasin bin Hassan bin Zaid bin
Hassan bin Alliyu bin Abi-Dalib
(7) Aliyu bin Musa bin Isma’il bin Musa bin Ja’afar bin Muhammad bin Aliyu
bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(8) Ibrahim bin Musa bin Abdullahi bin Musa bin Abdullahi bin bin Hassan
bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(9) Abdullahi bin Muhammad bin Yusuf bin Ibrahinm bin Musa bin Abdullahi
bin Hassan
Dama wasunsu (cikin wadanda aka kashe)
Lokacin Mu’utamid
Wadanda aka kashe sune:
109
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(1) Ahmad bin Muhammad bin Abdullahi bin Ibrahim bin Hassan bin Isma’il
bin Ibrahim bin Hassan bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(2) Ahmad bin Muhammad bin Ja’afar bin Hassan bin Aliyu bin Umar bin
Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(3) Aliyu bin Ibrahim bin Hassan bin Aliyu bin Abdullahi bin Hussain bin Aliyu
(4) Hamza bin Hassan bin Muhammad bin Ja’afar bin Alkasim bin Ishak bin
Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(5) Muhammad bin Hussain bin Muhammad bin Abdurrahman bin Alkasim
bin Hassan bin Zaid Al-Akbar bin Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(6) Musa bin Musa bin Muhammad bin Sulaiman bin Dawud bin Hassan bin
Hassan bin Aliyu bin Abi-Dalib
(7) Hussain bin Ibrahim bin Aliyu bin Abdurrahman bin Alkasim bin Hassan
bin Zaid bin Hassan bin Aliyu
(8) Muhammad bin Abdullahi bin Zaid bin Abdullahi bin Zaid bin Abdullahi
bin Hassan bin Zaid bin Hassan
Dama wasunsu (cikin wadanda aka kashe)
Lokacin Mu’utadid
Wadanda aka kashe sune:
(1) Muhammad bin Abdullahi bin Muhammad bin Alkasim bin Hamza bin
Hassan bin Ubaidullahi bin Abbas bin Aliyu bin Abi-Dalib
(2) Muhammad bin Zaidu bin Muhammad bin Isma’il bin Hassan bin Zaidu
bin Hassan bin Imam Ali
Lokacin Muktafi
Wadanda aka kashe sune
(1) Muhammad bin Aliyu bin Ibrahim bin Muhammad bin Hassan bin Ja’afar
bin Ubaidullah bin Hussain bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(2) Aliyu bin Muhammad bin Aliyu bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abdullahi bin
Muhammad bin Aliyu bin Abi-Dalib
(3) Zaid bin Hussain bin Hussain bin Zaid bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin
Abi-Dalib
(4) Muhammad bin Hamza bin Ubaidullah bin Abbas bin ibn Hassan ibn
Ubaidullah bin Abbas bin Aliyu bin Abi-Dalib
110
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Lokacin Muktadir
Wadanda aka kashe sune:
(1) Abbas bin Ishak (shine ake cewa dashi Al-Halwas) bin Ibrahim bin Musa
bin Ja’afar bin Muhammad bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu bin Abi-Dalib
(2) Al-Muhsin bin Ja’afar bin Aliyu bin Muhammad bin Aliyu bin Musa bin
Ja’afar bin Muhammad bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu
(3) Hassan bin Muhammad bin bin Abdullahi Al-Ashtari bin Muhammad bin
Abdullahi bin Hassan bin Hassan bin Aliyu
(4) Abdullahi bin Muhammad bin Sulaiman bin Abdullahi bin Hassan bin
Hassan
(5) Aliyu bin Aliyu bin Abdurrahman bin Alkasim bin Zaid bin Hassan bin
Aliyu ibn Aliyu
(6) Alkasim bin Zaid bin Hassan bin Isa bin Aliyu bin Hassan bin Aliyu
(7) Muhammad bin Abdullahi bin Hassan bin Aliyu bin Ja’afar bin
Muhammad bin Aliyu bin Hussain bin Aliyu
(8) Muhammad bin Ahmad bin Abdullahi bin Musa bin Abdullahi bin Hassan
bin Hassan bin Aliyu
(9) Aliyu bin Musa bin Aliyu bin Aliyu bin Muhammad bin Aunu bin
Muhammad bin Aliyu bin Abi-Dalib
(10) Alkasim bin Ya’akub bin Ja’afar bin Ibrahim bin Muhammad bin Aliyu
bin Abdullahi bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(11) Ja’afar bin Salih bin Ibrahim bin Muhammad bin Aliyu bin Abdullahi
(12) Abdurrahman bin Muhammad bin Abdullahi bin Isa bin Ja’afar bin
Ibrahim bin Muhammad bin Abdullahi bin Ja’afar
(13) Ahmad bin Alkasim bin Muhammad bin Ja’afar bin Muhammad bin
Aliyu bin Aliyu bin Hussain
(14) Hussain bin Aliyu bin Muhammad bin Aliyu bin Isma’il bin Ja’afar bin
Muhammad bin Aliyu bin Hussain
(15) Muhammad bin Ahmad bin Hassan bin Aliyu bin Ibrahim bin Hassan
bin Hassan bin Aliyu
(16) Muhammad bin Ja’afar bin Muhammad bin Ibrahim bin Isma’il bin
Ibrahim bin Hassan bin Hassan bin Aliyu
111
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(17) Alkasim bin Ahmad bin Abdullahi bin Alkasim bin Ishak bin Abdullahi
bin Ja’afar bin Abi-Dalib
(18) Ja’afar bin Hussain bin Hassan Al-Afdas bin Aliyu bin Hussain
(19) Husssain bin Hussain bin Muhammad bin Sulaiman bin Dawud bin
Hassan bin Hassan bin Aliyu
(20) Ahmad bin Hassan bin Aliyu bin Ibrahim bin Umar bin Muhammad
bin Umar bin Aliyu bin Abi-Dalib
(21) Zaid bin Isa bin Abdullahi bin Abi-Muslim bin Abdullahi bin
Muhammad bin Akilu bin Abi-Dalib
(22) Aliyu bin Muhammad bin Abdullahi bin Aliyu bin Muhammad bin
Hamza bin Ishak bin Aliyu bin Abdullahi bin Ja’afar
Dama wasun su da dama sun rasa rayukansu a lokuta maban-banta inda
wasun su kuma suka rasa rayukan su a lokaci daya misalin wadanda sukayi
shahada tare da Imam Hussain a Karbala da kuma wadanda sukayi shahada
tare da Muhammad Nafsuzzakiyya, haka nan suma wadanda sukayi
shahada tare da Hussain Sahibu Fakh.
Wadannan Kisan da aka dinga yiwa Ahlul-Baiti shine Musabbabin yin Hijirar
su daga Madina Izuwa sassa daban daban na duniya musamman ma
yankinmu na Africa, domin da yawan kashe kashen da akayi, yan uwansu ne
wato Daular Abbasiyya sune suka dinga kashe su tare da yaran su da kuma
masu goya musu baya. Ya kasance ana yi musu kisa na wulakanci inda wasu
da ransu aka dinga bunne su ko kuma a saka su cikin gini da ransu ko kuma
a yanke musu hannu da kafafuwa, banda tsarewa da kullewa da ake yimusu
a cikin kurkuku, ya kasance ana dukan su duka mai tsanani inda dayawa
daga cikinsu sun mutu ta dalilin haka ga kuma Azaba da ake yimusu da zafi
ko kuwa da wuta19. Ya zamto al’ada idan an kashe su (Ahlul-Baiti) to sai a
yanke kawunan su domin a kaiwa shugabannin wanchan lokaci. Haka
sidiran ake daukansu ko a tafi dasu inda akaga dama domin kashe su ko
kulle su, Sau dayawa akan kama su tare da ya’yansu dama jikokan su domin
a kulle ko a kashe su, basu guba ya zamo abu mafi sauki domin rabasu da
duniya. Hakika , babu wata kabila ko dangi a duniya da suka fuskanci
kalubalen da Jikokan Manzon Allah (SAW) suka fuskanta, kuma wannan
shine musabbabin yin Hijirarsu izuwa gurare daban daban na duniya.
112
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sashi Na Bakwai
Hijirar Sharifai Izuwa Sassan Duniya
Wanda ya fara fita cikin zuriyar Annabi (SAW) izuwa wani guri ko wani yanki
shine Ja’afar bin Abi-Dalib, Sayyadi Ja’afar ya bar garin Makka izuwa nan
Africa domin yin Hijira bisa umarnin Manzon Allah (SAW) inda ya zauna a
kasar Habasha wadda take Ethopia a yanzu. A wannan kasa ne ya haifi
Dansa mai suna Muhammad kuma ya dauki lokaci mai tsawo a habasha
inda daga bisani kuma ya koma izuwa Madina.
A wasu ruwayoyin kuma, an tabbatar da zaman Sayyadah Zainab yar gidan
Imam Aliyu da kuma Sayyadah Sakina yar gidan Imam Hussain a Masar
bayan kisan da akayiwa Ahlul Baiti a Karbala (wato Egypt kenan a yanzu
kuma kamar yadda muka sani, kasar Egypt itama kasa ce daga kasashen
Africa). Duk dacewa akwai sabanin Malaman Tarihi amman wasu suna
tabbatar da cewa Sayyada Zainab yar Imam Aliyu da kuma Sayyadah Sakina
yar Imam Hussain sun rasu a Egypt inda wasu kuma suka rinjayar da cewa
sun rasu a Dimashk ko kuma Madina.
Bayan da rigingimu suka tsananta musamman ma a mulkin Abbasawa, sai
Ahlul-Baiti suka dinga yin Hijira daga Madina izuwa wasu garuruwan
wadanda zasu samu saukin rayuwa da kuma saukin gallazawar da yan’
uwansu Abbasawa suke yi musu. Tarihi ya tabbatar da cewa Imam
Muhammad Nafsuzzakiyya ya tura dansa Abdullahi Al-Ashtar izuwa kasar
indiya ko kuma Fakistan (A lokacin kasashen suna Hade ba’a raba su ba)
inda a wasu ruwayoyin kuma shi da kansa ne (Abdullahi Al-Ashtar) ya gudu
izuwa chan ko kuma aka gudu dashi izuwa chan.
Sharifai sun cigaba da fuskantar gallazawa, tozartawa da kuma
wulakantawa inda a ko dayaushe hukuncinsu bai wuce kashewa ba, ko
dauresu, ko basu guba ko kuma haka sidiran a dauke su a tafi dasu izuwa
113
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
114
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Farkon wanda ya fara tahowa wannan yanki namu na Africa (Africa mai
Nisa) yazo ya zauna kuma yayi aure yabar zuriya, shine Idriss Al-Akbar dan
Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-Musannah dan Hassan Al-Mujtaba dan
Imam Aliyu da kuma Nana Fadima Al-Zahra’u yar Annabi (SAW). Idriss ya
gudo daga Madina bayan afkuwar waki’ar Fakh inda a nanne aka kashe
Yan’uwansa, ya taho izuwa Africa yabar yar’sa guda daya wadda ya Haifa
mai suna Fadima4, yabar dukiyarsa da kuma matarsa domin tsira da
rayuwarsa.
Idriss ya taho ne da abokin tafiyarsa wanda ake kiransa da Rashid, shi
Rashidu asalinsa mutumin Africa ne wato Maghrib kuma ya rayu a Madina,
ya taho da Idriss nan Africa saboda ana neman sa za’a kashe shi5.
Idriss ya taho izuwa Magrib Hijira tana da shekara 169AH ranar Tarwiyyah
wato 8 ga watan Zulhijjah, domin tsoron Abunda zai faru dashi idan ya
zauna daga Musal Hadi wanda Kalifa ne na daular Abbasiyya, sunyo tafiya
Mai nisa har suka shigo Kasar Masar6. Bayan sun shigo cikin gari, sai suka ga
wani gida wanda sukayi mamakin kyawunsa da kuma ta’ajibi akan gidan
inda suka tsaya suna kallon gidan, mamallakin gidan yaga su Imam Idriss da
abokin tafiyarsa Rashid suna kallon gidan inda shi mai gidan yazo ya
tambayesu akan labarinsu kuma sukaki bayyana masa su suwaye akaron
farko saidai sun nemi masauki a gurinsa kuma ya amince inda ya saukesu a
cikin gidansa, bayan da ya saukesu sai suka bashi labarin cewa su daga
Madina suke kuma Rashidu ya sanar dashi cewa Idriss Jikan Manzon Allah
ne (SAW), hakan matuka ya sanya wanda ya saukesu farin ciki da kuma
murna inda yayi musu alkawarin basu mafaka tare da Amana7. Bayan
saukarsu, tuni labari ya jewa Aliyu bin Sulaiman Al-Hashimi wanda shine
shugaba kuma Jagora a Kasar Masar kuma shine Kalifan Abbasiyya a kasar
Masar. Aliyu bin Sulaiman ya kirawo wanda ya saukesu kuma ya gaya masa
labari yazo masa cewa, ya sauki wasu baki a gidansa inda ya gaya masa
hatsarin zamansu a Masar kuma ya shaida masa cewa “Khalifa ya rubuto
masa cewa yana neman zuriyar gidan Annabi (SAW) tare da binciken duk
inda suke, domin cewa, shi (Khalifa na Masar) baya son a Zubar da Jinin
gidan Annabta a kasarsa”, Shugaban na Masar ya bawa su Idriss kwana uku
domin su fice bisa tsoron kada labari ya jewa Khalifan Abbasiyya8.
115
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Idriss da abokin tafiyarsa Rashid sunbi ayarin fatake suka bar Masar (domin
kada a ganesu ko a gane fitarsu kuma abisu a cinmusu) inda suka nufi garin
Barkatu, sun yi zango a garin Barkatu na dan wani lokaci sannan suka nufi
garin Kairawan inda sukayi Zango a kairawan shima na wani dan lokaci 9.
Lokacin da zasu fita daga garin Kairawan, sai Rashidu ya sanyawa Imam
Idriss kaya kwatan kwacin na uban gida da yaronsa inda shi Rashid ya
kasance a matsayin ubangida shi kuma Imam Imam Idriss ya kasance a
matsayin yaronsa (yaron Rashid), badan komai ba sai don su badda kama
kuma su gujewa masu bin sahunsu10. Bayan fitarsu daga Kairawan, sai suka
shiga garin Tilmisana inda suka yi zango na dan wani lokaci sannan suka
shiga Danjatu suka wuce izuwa garin Sus Al-Aksa kuma suka karasa izuwa
Takaddama har cikin garin Danjata inda ya zauna na yan kwanaki sannan ya
karasa izuwa birnin Walila inda a nanne ya nemi masauki kuma ya sauka a
gurin, Ishak bin Abdulmajid Al-Auraba Al-Mu’utazili ya girmamasu ya
darajta su kuma ya basu duk wata gudunmawa da suke da bukata11. Imam
Idriss ya isa garin Walila hijira tana 172AH12. Wannan yana nuna mana cewa
Imam Idriss da Rashid sun dauki tsawon shekara uku suna tafiya cikin
tsaunuka, sahara da kwazazzabi domin tsira da rayuwar su.
Bayan da Imam Idriss ya zauna a garin Walila, sai Ishak bin Abdulmajid Al-
Auraba ya dinga yiwa mutanen garin bushara da zuwan Idriss da kuma
muhimmancinsa tare da janyo masa mutane domin yi masa mubayi’a,
daukacin Al’umma sunyi masa mubayi’a ranar Juma’a 14 ga watan
Ramadan hijira tana da 172AH domin ya tsayar musu da hukuncin Alkur’ani
da kuma Sunnar Manzon Allah (SAW) 13. Farkon Kabilun da suka fara yi masa
mubayi’a sune: Maknasat, Gamarah, Lamayah, Lawatah, Sidratah, Gayatah,
Nafzatah, wannan duk daga kabilun Auraba, Sannan kuma kabilun Zinatah
da wasu daga cikin kabilun Barbar kamar su: Ziwagah, da Wazwawah14.
Lokacin da komai ya kammalu (goyon bayan da ya samu da kuma
shugabantar dashi da suka yi) sai yayi azamar yaki domin tabbatar da
abunda Kakan sa (SAW) yayi na tabbatar da Tauhidi aban kasa inda ya dinga
bude garuruwa har sai da ya dangane da Tilmisanah15.
Yayin da labarin Imam Idriss ya fantsama sai Haruna Al-Rashid wanda shine
Khalifah na Abbasiyyah ya fara shirya hanyar da zai kawar da Imam Idriss
116
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
domin jin tsoro akan gawurtar da Imam Idriss yayi da kuma karfin da yake
karawa, sai Haruna Al-Rashid ya tura Sulaiman Ibn Jarir Al-Shammak da
nufin ya kashe Imam Idriss. Sulaiman Ibn Jarir yazo wajen Imam Idriss kuma
ya nemi kusaci dashi bisa nuna cewa shi masoyinsa ne (Masoyin Imam
Idriss), bisa kaddarar Ubangiji, Sulaiman ya samu kusaci wajen Imam Idriss
inda yayi amfani da damar da ya samu na gusawar Rashid daga gurin Imam
Idriss sannan ya gabatarwa da Imam Idriss da wani turare inda yace dashi
“Ya shugabana, wannan wani nau’i ne na turare sabo wanda na taho da shi
tunda daga Mashrik (Jaziratul Arab) bai dace da kowa ba sai kai”, Yayin da
Imam Idriss ya karbi turaren kuma ya shake shi sai ya wadi magashiyyan
bisa guba da aka zubawa turaren, yayin da Sulaiman Ibn Jarir Al-Shammak
yaga gubar ta kama Imam Idriss sai ya gudu da nufin komawa inda ya fito16.
Bayan da Rashid ya dawo kuma ya tarar da Abunda ya faru, sai suka
sukwani dawaki suka bi Sulaiman suka cimmasa kuma suka sare masa
hannun dama amman duk da haka ya samu ya tsere17. Bayan da Rashid ya
dawo, sai sukayi Jana’izar Imam Idriss kuma suka binne shi a Walila sannan
ya tara Jama’a yace dasu “Imam Idriss bai bar da ba sai kuyangarsa wadda
take dauke da ciki wato Kanzatu Al-Nafziyyah, idan zakuyi hakuri har ta
haihu kuma idan namiji ta haifa kuma ya girma to sai muyi masa mubayi’a”
nan take suka amsa masa da cewa “su basu da wani ra’ayi sai ra’ayinsa
kuma suka kara da cewa idan namiji ta haifa to sai suyi mubayi’a inkuwa
mace ta haifa to sai suyi nazarin hukuncin da zasu dauka (wato su zabi
shugaba a tsakaninsu)”18. Rashid yayi farinciki bisa kalaman su kuma yayi
musu Addu’a bisa hakan, inda ya cigaba (Rashid) da khalifancin Imam Idriss.
Yayin da watannin haihuwar Kanzatu suka cika sai Allah ya Azurtata da
samun da namiji mai kama da mahaifinsa sa’annan aka mayar masa da
sunan mahaifinsa wato Idriss inda ake kiran mahaifinsa Idriss Al-Akbar shi
kuma dan ake kiran sa da Idriss Al-Asghar (wato mahaifin shine Idriss Babba
shi kuma dan Idriss Karami) 19. Mahaifiyar Imam Idriss Al-Asghar wato
Kanzatu Al-Nafziyya, ta fito ne daga Kabilar Nafzatu wadda babbar kabila ce
a garin Darabulis kuma an kara da cewa ita Nafzatu tana daga cikin kabilar
Auraba inda su kuma Auraba suna daga cikin ya’yan Aurab dan Barnus20. An
117
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
haifi Imam Idris Al-Asgar ranar Litinin 3 ga watan Rajab hijira tana da 177AH
cikin shekarar da mahaifinsa ya rasu21.
A cikin shekara takwas da haihuwarsa, Imam Idriss Al-Asghar ya haddace
Alkur’ani, yasan Ilimin Fikhu, da Sunnah (wato Hadisi), da Nahwu, da Waka
wadda fusaha ce gurin Larabawa, da tarihin shugabanni da shugabanci, da
hawa doki dama wasu abubuwan, Yayin da ya cika shekara 11, sai Rahid ya
umarci da ayi masa mubayi’a inda daukacin kabilun wannan yanki suka yi
masa mubayi’a kuma suka shugabantar dashi akansu, anyi wannan
mubayi’a ne ranar Juma’a 17 ga watan Rabi’ul Auwal hijira tana da 188AH 22.
Rashid yasa anyi mubayi’a bisa abubuwa daya gani tattare da Idriss wanda
ya hada da hikima, hazaka, ilimi, iya zance, fusaha, hankali. A ranar da aka yi
masa mubayi’a, a ranar ya hau mumbari yayiwa mutane Kutba23. Yazo
cewa, bai dade da hawa mulki ba Allah yayiwa Rashid Rasuwa inda ya
cigaba da mulki kuma ya taimaki Addini kamar yadda mahaifinsa yayi. Idriss
Al-Asgahr (wato Idriss Karami) ya haifi ya’ya 12 anan Walila amma a wasu
ruwayoyin ance sun zarta hakan24.
Bayan Imam Idriss, a cikin sharifan da suka shigo Africa, na biyunsu shine
Muhammad bin Sulaiman bin Abdullahi Al-Kamil bin Hassan Al-Musannah
bin Hassan Al-Mujtaba bin Imam Aliyu da Nana Fadima Al-Zahra’u yar
Manzon Allah (SAW)25. Duk da cewa akwai kuskuren da ake tabbatarwa
cewa Sulaiman dan Abdullahi Al-Kamil shine ya zauna a Tilmisana, amma
bisa bincike da kuma maganganu na masana tarihi ya tabbatar da cewa
Sulaiman an kashe shi ne a yakin Fakh sai dai dansa Muhammad bin
Sulaiman shine ya shigo Africa kuma ya shigo ne bayan afkuwar Fakh
169AH/785M26. Shi ne na biyu a shigowa Africa bayan gudowar sa daga
Sham wato inda daular Abbasiyya ke mulki, sai ya Zauna a Sudan inda daga
bisani, ya samu labarin cewa Baffansa wato Idriss Al-Akbar yana Maghrib
inda ya bar Sudan ya karaso Maghrib27. Bayan da ya karaso, Imam Idriss Al-
Akbar ya bashi shugabancin Garin Tilmisana inda ananne ya rayu kuma ya
haifi zuriyarsa kuma aka tabbatar da cewa sai da ya haifi ya’ya 10 a
Tilmisana hakanan ya fadada zuriya a wannan gari. A cikin ya’yan sa guda
goma, guda hudu ne kawai suka fitar da zuriya, ragowar basu da zuriya,
wadanda suke da zuriyar sune: Abdulllahi, Hassan, Ahmad da kuma Idriss 28.
118
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
119
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
120
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ibn Mashish wanda babban Malamine kuma masani ne shima kashe shi
akayi a Morocco, dama wasu da dama daga cikin Sharifai36.
Karyewar dauloli da kuma rigingimu sun taka muhimmiyar rawa wajen
kwararar sharifai izuwa yankuna daban daban na Africa, ya kasance a
Maghrib kusan duk bayan wani lokaci sai an samu hambarar da wata
gwamnati izuwa wata ko kuma yake-yake wanda hakan yana haddasa
asarar rayuka da kumama dukiya mai yawa wanda duk wannan na daga
musabbabin Hijirar su.
Yada Ilimin Addinin Musulunci da kuma kasuwanci suna daga cikin jigon
yaduwar Sharifai a kasashen Africa musamman ma yankin mu na west
Africa. Da yawa daga cikin Sharifai sun shiga da’awa ta hanyar yada Ilimin
Addinin Musulunci kuma ta hakanne sharifai suka yawaita a sassa daban
daban na Africa dama duniya baki daya.
Shigowar turawan mulkin mallaka ya taka muhimmiyar rawa wajen
yaduwar sharifai dama al’ummatai masu yawa, tarihi ya tabbatar da
afkuwar rigingimu da kuma barnatar da dukiya hadi da asarar rayuka masu
dimbin yawa yayin mulkin Mallaka a Africa. A kasar Morocco an samu tashe
tashen hankula da kuma uwa uba kasar Algeria inda aka kiyasta cewa anyi
asarar rayuka sama da miliyan daya cikin yakin da aka dade anayi tare da
yin hijirar miliyoyin mutane da suka bar kasar. Daga cikin wadanda suka bar
kasar akwai sanannen sharifinnan na kasar Libya wato Shekh Muhammad
Ibn Ali Al-Sanusi Al-Hassani, dama wasu da dama, hakanan, kasar Libya
itama an gwabza fada tsakanin turawan mulkin Mallaka da kuma al’ummar
kasar wanda ya sabbaba asarar rayuka masu yawa, wadannan rigingimu sun
tilasta yin hijirar sharifai izuwa wasu yankunan domin tsira da rayuwarsu.
Shigowar Sharifan kasar Hausa (Nigeria)
Sharifai masu yawa sun shigo cikin kasar Hausa kuma daukacinsu sun shigo
ne ta kasashen Niger, Chad inda su kuma (Nigr da Chad) sun shigo musu ne
daga Algeria, Mali, Libya, da kuma Sudan. Ana kirdadon cewa, kasar Barno
itace ta fara samun sharifai kasantuwar itace ta fara samun Musulunci
sannan kuma kasar Katsina da kuma kano musamman bisa shurarta ta
fannin kasuwanci da kuma karbar baki. A bisa abunda ya inganta daga tarihi
121
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
kuma ya shahara, sharifan da suka fara shigowa cikin kwaryar Birnin Kano
sune:
1. Sharifan Tsangaya ta Gaya: Yazo cewa, farkon sharifan da suka fara zuwa
Kano, sun zone a karni na goma sha-daya (11c) wato sun shigo cikin
ayarin Kabilar Wangarawa wadanda suka jaddada ko kawo Musulunnci a
cikin birnin Kano, a cikin su akwai wanda ake kira da Mahmud kuma an
tabbatar da cewa yana daga cikin farkon sharifan da suka shigo kano
kuma sune sukayi rassa a garin Tsangaya ta garin Gaya (Sharifan Gaya)
da garin Kademi da kuma wasunsu daga cikin kwaryar Birnin Kano. kuma
sune jikokin Imam Sulaimanu dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-
Musannah dan Hassan Al-Mujtaba dan Imam Aliyu da kuma Fadima yar
Annabi (SAW).
2. Tsatson Yahya: Jikokan Imam Yahya wanda akafi sani da Sahibu-Daylam,
suma sun shigo kasar Hausa inda suka fara zama a kasar Borno sannan
kuma suka fantsama cikin garuruwan Hausawa. Kuma suma suna cikin
sharifan farko da suka yawaita cikin kasar Hausa.
3. Sharifan cikin garin Kano dake unguwar sharifai: Zasu iya zama na uku
ko sama da haka cikin wadanda suka shigo cikin Jahar Kano, sunyi
shuhura kuma sanannu ne tare da faffadar zuriya da kuma shugabanci.
4. Tsatson Sharifan Dukawa: Asalinsu Maghrib ne wato kasar Morocco, sun
shigo kasar Kano ne daga Nijar wajejen kasar Agadez kuma sun kafa
gari/Unguwar Sharifai dake Tammawa cikin karamar hukumar Gezawa
ta kasar Kano. Daga cikinsu akwai mashahurin dan kasuwar nan wato
Sharif Yahya Na-Tsakuwa wanda yayi fataucin fata a garin Tsakuwa dake
Kano da kuma Sidi-Fari Amale (Sarkin Sharifan Kano).
5. Tsatson Sharif Abdurrahman: sun zauna a Dala cikin birnin Kano, kuma
sun taimakawa Shekh Usman bin Fodio wajen gudanar da Jahadinsa a
kasar Hausa, hakanan, zuriyar wannan gida sune suke rike da sarautar
Sharkin Sharifai a garin Sokoto
6. Sharif Ahmad Al-Hassani: ya shigo daga Kasar Libya kuma ya zauna a
Dukurawa tare da barin zuriya inda daga bisani ya koma Kura kuma daga
tsatsonsa aka samu Sharif Zangina dake Lokoja.
122
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
123
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
124
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
125
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
126
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
alkiyama. Kuma an nakalto Sayyadi Umar (RA) yana cewa “inaso na haifi da
daga gareta (daga Ummu-Kulsum jikar Annabi) wanda Zai zamto nasabarsa
(nasabar dan nasa) tana danganuwa gare Shi (SAW)42. Wannan aure na
Sayyadi Umar (RA) yayi shi ne domin samun falala da kuma tabarraki na
Annabi (SAW) kuma domin shima ya samu kusaci da Annabi ranar alkiyama
saboda auren Jikarsa (SAW) da yayi, bugu da kari, domin ya haifi da wanda
yake dan gidan Annabi (SAW), wato zuriyarsa su zamto suna komawane
izuwa gidan masoyinsa (SAW).
Malamai masana halittar Mahaifa suna cewa “ana halittar ya’ya ko tsatso
daga Maniyyin mahaifi da kuma na mahaifiya, amma tsoka ana halittarta ne
daga gudan jinin Mahaifiya kuma mafi yawancin halitta ana yinta ne daga
bangaren mahaifiya a mafi yawanci (halittar yaro a cikin mahaifiyarsa anfi
yinta ne mafi yawanci daga uwa sama da Uba), idan har mutum zaiyi
nasaba da mahaifinsa da kuma bangaren mahaifinsa, to kuwa jinginuwa
izuwa bangaren Mahaifiya shine farko saboda halittarsa a cikin ciki,
mahaifiya itace ta bada gudunmawa mafi yawa43. Wadannan malamai sun
fayyace mana cewa, a halittar dan Adam kusan gudunmawar uba shine
dugon Maniyyi wanda sai dashi ne ake yin halitta, `amman daukacin halitta
a cikin Mahaifiya, uwa itace take bada gudunmawar komai hatta wajen
halittar tsokarsa, inkuwa hakane, to kuwa za’a iya yin gado daga zuriyar
uwa na halaye, girma, ilimi dama wasu abubuwa da dama sama da uba.
Malamai masu tarin yawa sun tabbatar mana da shariftaka ta ban garen
mace, Imam Shafi’i an rawaito yana cewa “Shariftaka ta bangaren uwa
tabbatarciyar abace” a wani kaulin kuma wanda ake danganta shi da imam
Shafi’i yace “Nasaba tana tabbatuwa ga dan mace”44, Imam Al-Kabisi yana
cewa “Uwar da ta kasance Sharifiya, to shariftaka tana tabbatuwa ga
ilahirin zuriyar ta kuma ya kara da cewa duk wanda mahaifiyarsa ta kasance
Sharifiya, to kuwa shariftaka ta inganta a gare shi da kuma ilahirin zuriyarsa
kuma za’a girmama shi da girmamawar da ake yiwa Sharifai kuma
tafikarwarsa zata kasance irin tafikarwarsu45 ”, Shekh Al-Ukbani da wasunsu
sun tabbatar da cewa “Sharifi dan mace da kuma shima zuriyarsa dukkansu
suma Sharifai ne”, shima Kadi Jalil Abul-Abbas Ibn Gumazi an nakalto shi
yace “wanda Sharifiya mace ta haifa shima Sharifi ne”46, Shi kuwa Shekh
127
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
128
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(3) Akwai Aulad Ibn Halima: sharifai ne tabbatattu, kuma jikokin Shekh
Abdussalam Ibn Mashish dake Morocco, shariftakarsu ta bangaren
Mace suka sameta
(4) Aulad Ibn Raisun: suma sharifai ne sanannu dake Morocco, kuma
shariftakar su ta bangaren mace suka sameta.
(5) Yazo cikin littafin Gayatul-Muhtami Fi-Mas’alatul Sharaf Min-Jihhatul
Umm na Sulaiman bin Kalid Al-Harraki cewa “Shekh Muhammad
Rashid Rida wanda babban malami ne a Egypt shima Sharifi ne ta
bangaren mahaifiyarsa52.
(6) Shekh Ahmad bin Ahmad Al-Fasi Al-Barisi wanda ya shahara da suan
ibn Zaruk, shima Sharifi ne ta bangaren uwa kamar yadda Sulaiman
bin Kalid al Harraki ya kawo53
Alakar sharifai da Wuta
Hakika tasarrufi da wuta, yarjewa ce da kuma horewa ta Allah madaukakin
sarki, Tasarrufi da wuta baya daga cikin sharadin zama sharifi, da yawa daga
cikin sharifai basa iya tasarrafi da wuta kuma hakan ba shine yake nuna
cewa su ba sharifai bane, kuma da yawa daga wadanda ba sharifan ba,
sukan samu yarjewar (A gurin Allah) yin tasarrafi da wuta kuma hakan ba
yana nuna cewa sun zama sharifai ba, sharifi shine wanda yake da
ingantacciyar Nasaba izuwa ga Annabi (SAW) ko da kuwa yana tasarrafi da
wuta ko kuma ba yayi.
Idan muka duba tarihi, zamuga cewa dayawa daga cikin kakannin Ahlul-Baiti
anyi musu izaya da wuta yayin da aka kama su a daular abbasiyya, idan da
ace yin tasarrafi da ita sharadi ne na shariftaka to da kuwa wutar da akayi
musu izaya da ita da bata cutar dasu ba.
Dangantakar Bakar Fata da Sharifai da Kuma Larabawa
Kamar kowace Al’umma, bakar fata tana daga cikin jinsin da Allah ya
daukaka kuma yayi musa baiwowi masu tarin yawa hadi da samun
shahararrun mutane a cikin su. Su kansu Larabawa, sun kasance a chakude
tsakaknin farare da kuma babake wanda hakan ya bayu da samun
Larababwa masu yawa kuma suke Usul amman kuma bakake a halitta. Ga
mai bincike da kuma nazari a fannoni na tarihi da kuma Ilimi, zai fihimci
129
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
cewa, idan muka cire Larabawa to kuwa babu wasu jinsin al’umma da Allah
ya daukakasu kuma ya darajta su kamar bakar fata. Insha Allahu, zamu
gabatar da bayani bisa daraja da kuma daukakar bakar fata cikin Al’umma.
130
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
131
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
132
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
133
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
134
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
cewa ai baki ne sosai wato “Adam Shadid Al-Udmah”. Indai kuwa hakane,
to babu wata hujja akan cewa babu sharifi baki domin kuwa, kakan nasu
(Sayyadina Ali) an tabbatar da cewa bakar fata ne.
Bayan iko na Ubangiji na ya halicci kalar da yaga dama, akwai dalili na
auratayya wanda shima ya taka Muhimmiyar rawa wajen kasantuwar
Sharifai zama bakake. Hakika yazo cikin Hadisi inda wani Balarabe yazo
gurin Annabi (SAW) da korafin cewa: Matarsa ta Haifa masa yaro wanda
yake baki alhalin cewa shi da matar tasa dukan su Larabawa ne kuma
farare, sai Annabi (SAW) ya tambaye shi akan wani kalar Rakumi da ake
samunsa cikin rakuma, sai wannan Balarabe ya bada Amsa cewa “Ana
samun wannan kalar rakumi ne idan a kakanninsa akwai mai irin wannan
yanayin”, sai Annabi (SAW) ya gaya masa cewa “Shima a cikin iyayensa ko
Kakanninsa akwai bakar fata shi isa matarsa ta haifa masa bakar fata”. In
kuwa hakane, to babu wata hujja ko dalili da za’ace babu sharifai ko kuma
bazai yiwu a samu sharifai bakake ba. Tarihi ya tabbatar da auratayya
tsakakanin Sharifai da kuma bakaken fata a Madina kuma dalilin wannan
auratayyar ta sanya aka samu sharifai masu yawa kuma bakaken fata a
Madina.
Sharifan da suke bakake kuma na kusa da Annabi (SAW) sune:
(1) Imam Aliyu bin Abi-Dalib (RA)
(2) Muhammad Nafsuzzakiyya dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan dan
Hassan
(3) Musa Al-Jauni dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan dan Hassan dan Imam
Aliyu
(4) Muhammad Al-Bakir: wasu suna cewa wankan tarwada ne
(5) Ja’afar Al-Sadik
(6) Musa Al-Kazim
(7) Hassan Al-Askari
(8) Muhammad Al-Jauwad
(9) Aliyu Al-Rida
(10) Aliyu Al-Hadi bin Muhammad Al-Jauwad
(11) Hassan Al-Kalis
135
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(12) Muhammad bin Idris Al-Asghar bin Idriss Al-Akbar bin Abdullahi Al-
Kamil bin Hassan Al-Musannah bin Hassan Al-Mujtaba bin Imam Aliyu:
yazo cewa shima wankan tarwada ne61.
(13) Yahya bin Abdullahi Al-Kamil bin Hassan Al-Musannah bin Hassan
Kamar yadda malaman tarihi da kuma masana Nasaba suka tabbatar da
zamowar su bakaken fata, babu wani dalili ko hujja da zata kore kasantuwar
sharifai kuma bakake a ko ina suke kuwa a fadin duniya. Ita shariftaka ba a
launin fata ko kyawu ko dukiya ko mulki take ba, ita shariftaka tana a
nasaba ne wato jinginuwa da gidan Annabi (SAW) ta hanyar haihuwa.
Ayoyin da sukazo cikin Alkur’ani da yaren bakaken Fata (wato Habasha)
(1) “Daha” = kalmar Daha itama yaren Habasha ce. Kuma ita “Daha”
kalmace da ake amfani da ita wajen kiran mutum (Ya wane) na kira
(2) “Yu’utikum Kiflaini” = Kalmar “Kiflaini” yaren Habasha ne. ita Kalmar
“Kiflaini tana nufin “Rarrauna”. Da yaren Habasha
(3) “Ina Ibrahim La Auwahun Halim” = Kalmar “Auwah” yaren Habasha ne.
Kalmar “Auwah” da yaren Habasha tana nufin “Mu’umini”
(4) “Inna Nashi’atallail” = itama yaren Habsha ce. Ita Kalmar “Nashi’a” da
yaren Habasha tana nufin “Idan ka tashi/Mike”.
Wadannan dama wasu da dama cikin Al-Kur’ani, na daga cikin girmamawar
da Allah ya yiwa bakaken Fata bisa zabar wani yare daga cikin su kuma ya
sanya shi cikin Alkur’ani. Domin Karin bayani zaka iya duba Littafin Imam
Jauzi “Tanwir Al-Gabish Fi-Fadlu Sudan Wal-Habash”.
Darajar da bakaken Fata suka samu a gaban Annabi (SAW).
A daukacin Al’Umma, babu wani jinsi da suka samu wannan falalar sai
bakaken fata. A hadisin da aka rawaita daga Ummul-Mu’uminina Nana
Aisha (RA) yazo cewa “bakaken fata wadanda suke mutanen Habasha sun
gudanar da wasanni (Na Al’ada) a gaban Annabi (SAW) a cikin Massallacinsa
mai Alfarma inda Sayyadi Umar yayi nufin hanasu amman Annabi (SAW) ya
dakatar da shi kuma yace da shi “Banu Arfadu suna cikin Aminci” kuma
Annabi (SAW) bai Hanasu ba62. Abu Amru ya kara da cewa “Banu Arfadatu
wani jinsi ne daga bakaken fata masu raye-raye63
136
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Yazo cewa, yayin da Annabi (SAW) ya shigo Madina (yayin Hijira) bakaken
Fata mutanen Habasha sune suka dinga wasanni saboda nuna murna da
kuma farinciki bisa zuwan Annabi (SAW) Madina64
Yazo a cikin Hadisi wanda aka rawaita daga Ibn Abbas inda Manzon Allah
(SAW) yake cewa “ku riki bakaken fata saboda mutum uku daga cikinsu yan
Aljannah ne (wato sune) Lukman Al-Hakim da Najashi da kuma Bilal bin
Rabah65
A wani hadisin na daban wanda aka rawaita daga Abu-Huraira (RA) Manzon
Allah (SAW) yace “Shugabanci naga Kuraishawa, hukunci naga Ansar
(Mutanen Madina) kiran Sallah kuma naga Bakake 66.
Sannan, Allah ya karrama jinsin bakar fata bisa turo Annabi wanda yake
bakar fata, yazo a cikin fadin Imam Ali (RA) cikin fadin Allah (SAW) “Daga
cikinsu (Annabawa) akwai wadanda muka baka labarinsu da kuma wadanda
bamu baka labarinsu ba” sai yace (Imam Ali) Allah ya aiko Annabi bakar fata
wanda yana daga cikin wadanda ba’a bawa Annabi (SAW) labarinsa ba, Ibn
Abi-Hatim ya fayyace lamarin inda yace Annabi da aka turowa Ashabil-
Ukdud bakar fata ne67(Al suyudi ).
137
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
138
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
139
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Muhammad shine babba cikin jerin ya’yan Imam Idriss kuma shine ya gaji
Mulkin Mahaifinsu bayan da yayi wafati anan Maghrib. Muhammad ya haifi
Aliyu da Yahya da kuma Ibrahim.
Aliyu wanda ake yimasa lakabi da Haidara dan Muhammad ne, dan Idriss na
biyu dan Idriss na farko dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-Musannah
dan Hassan Al-Mujtaba dan Nana Fadima Al-Zahra’u yar’ Annabi (SAW), ya
gaji Mulkin Maghrib bayan rasuwar Mahaifinsu (Bayan rasuwar Muhammad
bin Idriss) kuma yayi hukunci bisa jajircewa tare da adalci. Aliyu ya haifi
Imam Ahmad wanda suke yi masa lakabi da “Mizwar”, yazo cewa Kalmar
Mizwar a yaren kabilar Barbar yana nufin “Shugaban Shurafa’u/Sharifai
kuma mai kula ko lura ga dukkan al’amuransu (mai kula ko lura da Al-
Amuran jamhurin sharifai)1.
Ahmad-Mizwar shugaba ne mai matukar gudun duniya tare da tsoron Allah,
hakika yayi fice cikin jikokan Imam Idriss musamman ta fuskar gudun duniya
da kuma tsoron Allah hadi da kadaituwa wajen Ibada. Yayin da rigingimu
suka yawaita a lokacin da wasu daga al-Ummar Maghrib dake samun
shugabancin Musa Ibn Abi Al-Afiya suka soma yakar Ahlulbayt wajen kashe
su da kuma tozarta su, Imam Ahmad Mizwar ya fita yayi hijira inda yabar
cikin kwaryar birni ya tafi izuwa cikin surkukin tsaunuka domin cigaba da
rayuwarsa achan tare da bautar Allah kuma shine tushen sharifan da
akeyiwa lakabi da sharifan Jabalul-Alam2.
Sharifan Jabalul-Alam
Jabalul-Alam dutse ne dake kasar Morocco kuma a kusa da nanne Imam
Ahmad-Mizwar ya zauna kuma ya gudanar da rayuwarsa. Daga bisani
jikokansa (Jikokin Ahmad-Mizwar) sun dawo wannan dutse na Jabalul-Alam
inda suka cigaba da gudanar da rayuwarsu a wannan guri kuma bisa dalilin
zamansu a wannan guri ya sanya al’umma suke kiransu da sharifan Jabalul-
Alam.
Imam Abdussalam Al-Umrani Al-Kalidi ya kawo cikin littafinsa na Jawahirul-
Bahira Fi-Nasbussharif cewa “Imam Aliyu Haidara a mafi abunda yafi
shahara ya haifi dansa guda daya wato Imam Ahmad-Mizwar kuma shima
(Ahmad Mizwar) ya haifi dansa guda daya mai suna Sulaiman amma anfi
140
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
saninsa da “Salam” inda shi kuma (Salam) ya haifi dansa guda daya mai
suna Isa, shima (Isa) da guda daya ya Haifa wato Hurma kuma shima
(Hurma) ya haifi dansa daya mai suna Aliyu inda shima (Aliyu) ya haifi da
guda daya mai suna Abubakar. Abubakar shine ya yada wannan zuriya inda
ya haifi ya’ya guda bakwai kuma guda biyar cikin bakwai suka fitar da
wannan zuriya mai albarka. Wadanda suka fitar da zuriya cikan ya’yan
Abubakar susu biyar ne kuma sune: Mashish, Yunus, Aliyu, Abdullahi
(Malahi) da kuma Ahmad, wadanda basu bar zuriya ba sune: Fatuh da kuma
Maimun. Wadannan rukuni (susu bakwai) sune ake kiransu da Sharifan
Jabalul-Alam kuma sannannu ne cikin Nasaba da kuma rubutun malamai 3.
Hakika, wadannan Sharifai na Jabalul Alam sun samu tabbaci da gasgatawa
wajen ilahirin malamai masana nasaba tare da samun Shuhura, ma’abocin
littafinnan na “Al-Durrussani” yana cewa “Daukacin tsatson Imam Idriss
babu kamar Sharifan Jabalul Alam da kuma Sharifan Jaudiyyin wajen
Ingancin nasaba tare da Shuhurarta a cikin kafatanin su wanda dalilin
kasancewarsu hakan, Allah shi ne yabarwa kansa sani”4. Shekh Al-Kasar ya
kara da cewa “an kebanci ahalin Alam (wato an kebanci Sharifan Jabalul
Alam), sune tsatson Shekh Abdussalam ibn Mashish da wadanda suke da
hukunci irin nasu (wadanda suka fito tsatso daya da shi shekh Abdussalam)
daga yan’uwansa da kuma baffaninsa (wadanda dukkansu Sharifai ne daga
tsatso guda) da kari/dadi wanda waninsu bai samu irinsa ba cikin dukkan
wadanda sukayi shuhura cikin Sharifan Maghrib (hakan yana nuna mana
Allah ya daukaka su cikin ilahirin Sharifan Maghrib wajen yarda da cewa su
Sharifai ne tsatson Annabi SAW)”5. Wannan yana nuna mana cewa, sharifan
Jabalul Alam, sun samu wata falala daga ubangiji musamman ta fuskar
daukaka su da Allah yayi, ga Shuhura, ilimi, Malunta, Jahadi, kasuwanci da
kuma samun gwarazan waliyayy a cikinsu kamar Sidi Abdussalam Ibn
Mashish wanda shi ne babban Malamin Imam Abul-Hassan Al-Shazali kuma
a daukacin kasar Maghrib kusan shi ne waliyyin da yayi shuhura, a karshe,
sun samu kiyayewar Allah ta bangaren sahihancin nasabarsu da kuma
Shuhurarta. Wannan zuriya ta gidan su Sharif Yahya-Na-Tsakuwa tare da
yan’uwansa, tsatso ne daga Sharifan Jabalul Alam kuma sun fito ne takan
Yunus dan Abubakar dan Aliyu dan Hurma dan Isa dan Sulaiman (Salam)
dan Ahmad-Mizwar dan Aliyu dan Muhammad dan Idriss Al-Asghar dan
141
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Idriss Al-Akbar dan Abdullahi Al-Kamil dan Hassan Al-Musannah dan Hassan
Al-Mujtaba dan Imam Aliyu da Nana-Fadima Al-Zahra’u yar Annabi (SAW),
kuma sun fita ne ta bangaren Aulad Abdul-Wahid cikin tsatson Yunus dan
Abubakar Al-Alami Al-Idrissi Al-Hassani.
Rabe-Raben Sharifan Jabalul Alam
Kamar yadda bayani ya gabata, sharifan Jabalul-Alam rukuni ne na mutum
bakwai inda guda biyar ne suka fitar da zuriya daga cikinsu, kuma jikokin
Imam Ahmad Mizwar ne dan Aliyu dan Muhammad Al-Khalifa dan Imam
Idriss Al-Asgahr dan Imam Idriss Al-Akhbar dan Abdullahi Al-Kamil dan
Hassan Al-Musannah dan Hassan Al-Mujtaba dan Imam Aliyu da kuma Nana
Fadima Al-Zahra’u yar Annabi (SAW). Dalilin zamansu a wannan yanki ko jeji
da yake tattare da tsaunuka ya faru ne bisa yakarsu da akayi kuma aka
tasamma karar dasu wanda hakan ya tilastawa Imam Ahmad Mizwar barin
masarautarsu ya koma izuwa jeji domin cigaba da rayuwarsa6. Jikokansa
(Ahmad Mizwar) sune tushen dukkan wasu sharifai dake zaune a wannan
yanki na Jabalul Alam inda a nanne suka gudanar da rayuwarsu kuma suka
fitar da tsatso masu tarin yawa tare da albarka wanda ya hadar da Manyan
Waliyayy, Shugabanni, Mujahidai da kuma Attajirai. Dukkan wani sharifi da
yake Al-Alami to asalinsa shine wannan yanki na Jabalul-Alam dake kasar
Morocco. Sharifan Jabalul Alam sun rabu izuwa gida biyar kuma sune:
1. Jikokan Sidi Mashish bin Abibakar Al-Alami Al-Idrissi.
Sidi-Mashish yana daga cikin ya’yan Sidi-Abubakar bin Aliyu Al-Alami Al-
Idrissi Al-Hassani, kuma shine mahaifin babban waliyyin nan wanda ya
shahara na nahiyar Africa wato Sidi Abdussalam Ibn Mashish wanda shi
kuma (Sidi-Abdussalam Ibn Mashish) Malamin Imam Abul-Hassan Al-Shazali
ne mai Darikar Shazaliyya kuma a gurinsa (a gurin Sidi Mashish) ya karbi
darikar Kadiriyya. Wannan bangare ya samar da bangarori da yawa na daga
jikokan Annabi (SAW) kamar irin su:
Aulad Shantuf, Aulad Idriss bin Hammu, Aulad Baguri, Aulad Sidi Aliyu Al-
Sharif, Shurafa Al-Shafshafaniyyun, Aulad Ibn Abdulwahab, Aulad Maudan,
Aulad Mu’azzin, Aulad Ibn Alkasim bin Mabkus, Aulad Ibn Halima, Aulad Ibn
Al-Dalib, Aulad Ibn Al-Dayyib Al-Alamiyyin, Aulad Al-Fasi Al-Alamiyyun, Ahlu
142
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
143
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Aulad Al-Lihani, Aulad Shalwashi, Aulad Mizwari, Aulad Ibn Yunus, Aulad Al-
Arabi.12
Bisa ga abunda ya inganta a tarihi, Sidi Abdurrahman dan Sidi Yunus Al-
Alami takansa Aulad Rahmun suka fita, kuma ana kiransu da wannan sunan
ne (Rahmun) bisa yawaitar masu suna Abdurrahman ko maimaituwar sunan
Abdurrahman a cikin nasabarsu.
Shi kuma Abdullahi dan Sidi Yunus Al-Alami ya haifi dansa guda daya mai
suna Muhammad, kuma dukkan wanda nasabarsa take kaiwa izuwa kan
Abdullahi dan Sidi Yunus Al-Alami sai tabi takan Muhammad domin shine
dan Abdullahi tilo guda daya13. Alhamdulillahi, bisa amincewa ta Ubangiji,
wannan zuriya mai Albarka ta gidan Sharif Yahya Na-Tsakuwa tare da yan’
uwansa, nasabarsu tana kaiwa har izuwa kan Muhammad dan Abdullahi
dan Yunus dan Abibakar Al-Alami Al-Idrissi Al-Hassani.
Yaduwar Sharifan Jabalul Alam.
Bayan daukan dogon lokaci na wadannan sharifai da ake yimusu lakabi da
sharifan Jabalul-Alam a wannan tsauni (Tsaunin Jabalul Alam) wanda cikin
ikon Allah ya haifar da samun zuriya mai tarin yawa tare da zaman lafiya, sai
suka fara fita izuwa wasu yankuna da kuma gurare wadanda suka hadar da
cikin birane da kuma kauyuka. Wasu daga cikinsu sunyi hijira bisa radin
kansu inda wasu kuma domin kasuwanci, yada ilimin Addinin musulunci
kasantuwar tushen zuriyar shine ilimi da kuma Jihadi. Malaman tarihi sun
tabbatar da cewa wadannan sharifai na Jabalul Alam sun fita cikin ayari
inda suka nufi kasar Baitul-Makdis lokacin Salahuddin Al-Ayubi inda suka
taimaka masa wajen kwace birnin Kudus ko Masallacin Baitul MaKdis daga
hannun Yahudawa. Da yawa daga cikin wadannan sharifai sun fitone daga
inda suke domin yada ilimin addinin musulunci inda wasu kuma domin
kasuwanci. Zuriyarsu ta fadada a gurare da kasashe masu tarin yawa domin
akwaisu a Jordan, Makkah Madina, Falasdinu, Syria, Irak dama ragowar
kasashe masu yawa da suka hadar da na turawa da kuma na Larabawa.
Kasashen mu na Africa ya zamowa wannan zuriya kamar gida domin sun
shiga cikin kasashenmu na Africa masu tarin yawa irinsu Algeria, Tunusia,
144
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Libya, Mali, Murtania, Chad, Niger, Nigeria da Ghana dama wasu kasashen
namu na Africa.
Wasu ayari daga wannan zuriya sunbar Morocco wato Jabalul-Alam inda
suka dawo wani yanki da yanzu yake a kasar Algeria da ake kiransa da Jabal
Al-Sanus kuma wannan yanki yana nan a kasar Tilmisana dake Algeria a
yanzu. Bayan zamansu a wannan guri (Jabal Al-Sanusi) wasu ba’ari daga
cikinsu sunyiyo gaba inda suka shigo kasar Agadez/Agadas dake Jamhuriyar
Nijar a yanzu suka zauna a wannan yanki na tsawon lokaci. Bayan zamansu
a Agadas dake Nijar, wani jigo daga cikinsu mai suna Abubakar da dansa
mai suna Ibrahim sun shigo kasar Katsina kuma suka karaso kasar Kano inda
suka zauna a Tammawa wadda yanzu take a karamar Hukumar Gezawa
cikin kasar Kano suka zauna, daga bisani, Sharif Usman wanda suke yiwa
lakabi da “Sumu” (Sharif Usman danSharif Ibrahim ne) ya shigo cikin
kwaryar birnin Kano wato Unguwar Darma wadda ta dawo ake kiranta da
Dukawa Fuskar-Gabas inda ya gina Gida na iyali ya zauna, ya gudanar da
rayuwar sa a nan tare da barin zuriya da tsatso mai tarin yawa a wannan
unguwa. Ya tabbata cewa, akwai zuriyar wannan gida a kasar Nijar yankin
Agadez kasantuwar zama da kuma barin zuriya da wasu daga iyayen
wannan zuriya sukayi a wannan yanki14.
Abubakar shine wanda daukacin wannan zuriya suka fita ta tsatsonsa, kuma
shine farkon wanda ya taho kasar Hausa inda ya baro kasar Agadas sannan
ya fara yin zango a kasar Katsina sannan yayi zangonsa na biyu a garin
Tammawa dake kasar Gezawa cikin Kasar Kano. ya taho ne tare da dansa
mai suna Ibrahim inda suka shigo cikin kasar Kano wato garin Tammawa.
Kamar yadda tarihi ya tabbatar, shi wannan gari na “Tammawar Sharifai”
dake karamar hukumar Gezawa cikin Jahar Kano, Abubakar da dansa
Ibrahim sune farkon wadanda suka fara zama a wannan gari kuma suka
assasa tushensa, bisa dalilin zamansu a wannan gari yasa al’umma suke
kiran gurin da Tammawar-Sharifai, wato Tammin Sharifai kenan (Cikakkun
Sharifai) kuma har yanzu unguwar da suka zauna tana nan ana kiranta da
Unguwar “Sharifai” bisa dalilin zamansu a wannan guri. Kamar yadda na
145
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ibrahim Shine wanda suka taho tare da Mahaifinsa (Abubakar) daga garin
Agadez dake Jamhuriyar Nijar inda suka zauna a kasar Katsina sannan garin
Tammawar Sharifai sannan kuma a karshe suka zauna a Unguwar Darma
wadda ta dawo ake kiranta da Dukawa Fuskar Gabas cikin kwaryar birnin
Jahar Kano16.
146
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
idan mukayi hadani da gidan Sharif Yahya Na-Tsakuwa wanda asalin yadda
yake a baya, tun daga gaban gidan har abunda yake bayansa ya kuma
zagayo ya dawo, duk gida ne guda daya, hakanan gaban gidan inda shima
har yanzu mallakin zuriyar gidanne, idan muka tsallaka daya bangaren
zamuga cewa tun daga gidan Sharif Dan-Shila a yanzu da kuma abunda yake
bayansa, da gidan Sidi Liman (Gidan su Sharif Mai Doki) dukkansu bisa usuli
gidajen Sharif Yahya Na-Tsakuwa ne. Hakanan idan muka koma gidan Sharif
Sulaimanu wanda ake kiransa da Na-Hakuri, zamu ga cewa ya samu
yalwataccen gida matuka gaya (a cikin Sharifai/Chiromawa) musamman ta
fuskar Gabas da kuma abunda yayi bayan gidan har ya zagaya kan tudu
(Kan-tudu na bayan gidansa dake unguwar) kusan gabaki daya harabar
gurin mallakinsa ne domin har Kududdufi ne da shi da ake kiransa da
kududdufin Na-Hakuri. Suma bangaren Sidi-Fari Amale haka abun yake a
cikin unguwar Sharifai musamman ta bangaren yalwar muhalli da suke da
ita. Dukkan wanda ya bibiyi tarihin tsohuwar unguwar Darma wadda yanzu
wani ba’ari daga cikinta ya dawo Dukawa, Sharifai da kuma wani bangare
na kofar Wambai zai samu wannan tarihi musamman wajen ragowar
magabatan da suka rage. Hakika a yanzu, gidajen wadannan Sharifai
(Zuriyar Na-Tsakuwa da yan’ uwansa) ya ragu matuka gaya bisa dalilai
wadanda suka hada da siyar da muhallansu da suka dingayi hadi da kyauta
da suka dinga bayarwa
147
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bisa ga wannan alaka da kuma aminci dake tsakaninsu ya sanya Sarkin Kano
Abbas baiwa Sharif Na-Tsakuwa Sarautar Sarkin Sharifan Kano18. cikin
abunda bincike ya tabbatar, Sarkin Kano Abbas shine farkon wanda ya fara
kirkirar wannan Sarauta kuma kafinsa ba’a taba yintaba ko kuma Masarauta
bata taba nadi akan wannan mukami ba19. Sharif Na-Tsakuwa ya nemi
afuwar Sarki Abbas tare da cewa shi dan-kasuwa ne ko kuma bafatake
kuma bazai yiwu ya hada shugabancin Al’umma da kuma fatauci ba, amma
bisa ga hakan yana neman afuwar Sarki akan ya bada wannan matsayi ga
dan yar’uwarsa wato Sidi-Muhammad wanda akafi sani da Amale, wannan
roko na sharif ya samu amincewar Sarki inda sarkin Kano Abbas ya nada Sidi
Muhammad (Amale) a matsayin Sarkin Sharifan Kano20.
148
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
tare da sanar dashi cewa ya bashi Sarautar Sarkin Sharifan Kano, sai dai
shima ya nemi afuwar sarki inda yace masa shi dan kasuwa ne kuma bazai
iya hada shugabancin Al’umma da kuma kasuwanci ba, ya tabbata cewa
sarkin Kano Ado Bayero ya gayawa Sharif Ibrahim (Tripoli) cewa “Naji daga
gurin magabata na cewa irin wannan uzurin daka fada, irinsa kakanka ya
fada wanda hakan ya sanya shi kin karbar shugabancin Sharifai”21. Mutane
da yawa cikin wannan zuriya anyi musu tayin sarautar Sarkin Sharifai amma
Allah bai nufesu da sun karba ba, musamman bangaren Sidi-Fari Amale
kasantuwar sun taba rike wannan sarauta a baya.
Bayani akan Nasaba, ya’ya da kuma jikoki na wannan zuriya mai Albarka
Usman wanda suke yiwa lakabi da “Sumu” (dan Ibrahim) shi ne farkon
wanda aka fara haifa cikin kasar Hausa kuma dukkan wanda yake
nasabtuwa izuwa gare shi (Ibrahim) a Sharifan Dukawa dake cikin Kwaryar
Birnin Kano, to ya fito ne ta tsatson Usman “Sumu” dan Ibrahim dan
Abubakar, duk da cewa akwai ragowar yan’uwansu ko kuma wadanda suka
fito daga zuriya daya cikin garin Agadez dake Jamhuriyar Nijar amma
Usman Shi ne tushen daya samar da dukkan wanda yake nasabtuwa izuwa
ga wannan zuriya dake kasar Kano.
149
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
6. Idriss
5.Abdullahi
4. Hassan
7. Idriss Al-Asghar 3. Hassan 2.
Fadima
8. Muhammad Al-Khalifa 1. Muhammad
9. Aliyu (Haidara) Yahya
Abdurrahman
Muhammad
Aliyu
Muhammad
Sharif
Abubakar
Sharif
Ibrahim
Usman (Sumu)
Abbas
Salmah (Iyana)
Haruna
Abdullah
151
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Kamar yadda muka anbata a baya, Ibrahim haifa Usman wanda suke yi
masa lakabi da “Sumu” inda shi kuma (Usman) ya haifi ya’ya guda bakwai.
Sharif Abbas
Sharif
Sharif Muhammad Dan-Didi
Usman
Sharif Sulaiman Allo “Sumu”
152
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sharif Abbas dan Usman “Sumu” dan Ibrahim dan Abubakar
Abbas shine babba wajen mahaifinsu (Usman) kuma ya haifi da guda daya
inda shima ya haifi dansa guda daya amma dukkansu tsatsonsu ya yanke.
dan nasa shine
1. Sharif Malam Ibrahim (Ibrahim Bursa) dan Abbas dan Usman (Sumu) ya
haifi:
(1) Sharif Abdu Guro (Shine dan Ibrahim Bursa tilo guda daya). Sharif
Abdu-Guro bashi da Zuriya (Tsatsonsa ya yanke). Hakan yana nuna
mana cewa, daukacin tsatson Sharif Abbas dan Usman (Sumu) ya
yanke bisa yankewar tsatson Abdu-Guro domin shine dan Sharif
Ibrahim Bursa tilo guda daya
Gidan Sharif Muhammad Dan-didi dan Usman dan Ibrahim dan Abubakar
Sharif Muhammad Dan-Didi shine na biyu cikin jerin ya’yan Usman (Sumu)
kuma ya haifi ya’ya guda shida, guda uku sun bar zuriya, ragowar ukun basu
da zuriya, Ya’yan nasa sune:
1. Sharif Isyaku: Bashi da zuriya (Bai haihu ba)
2. Sharifiya Tambara
3. Sharifiya Hadiza
4. Sidi Umaru: Bashi da zuriya
5. Sharifiya Ta’isa: bata da zuriya
6. Sharifiya Aminatu
153
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
154
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
155
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
156
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(D)Sharif Murtala
(E) Sharif Labaran
(F) Sharif Gali
(G)Sharif Mustafa
(H)Sharif Mujtaba
(I) Sharif Fa’izu
(J) Sharif Naziru
(K) Sharif Rabi’u
(L) Sharif Hafizu
(M) Sharif Muhammad
(N)Sharifiya Rabi
(O)Sharifiya Nafisat
(P) Sharifiya Alawiyyah
(Q)Sharifiya Ummi
(R) Sharifiya Halima
(6) Sharif Isa dan yalwa: Bashi da zuriya
157
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
158
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(G)Sharif Yahya
(H)Sharif Muhammad-Inuwa
(I) Sharifiya Magajiya
(J) Sharifiyaa Aisha
(K) Sharifiya Umma
(L) Sharifiya Habiba
(2) Sharif Ibrahim (Uba) dan Idriss dan Aminatu ya haifi:
(A) Sharif Idriss (Baban gida)
(B) Sharif Abdulkadir (Bazallahi)
(C) Sharifiya Bilkisu (Mai Karama)
(D)Sharif Abdulbaki
(E) Sharif Abdulbari
(F) Sharif Fa’izu
(G)Sharif Mansur
(H)Sharifiya Salamatu
(3) Sharif Ahmad (Badayi) dan Idriss dan Aminatu ya haifi:
(A) Sharif Rabi’u
(B) Sharif Yusif
(C) Sharif Hussaini
(D)Sharifiya Ummu-Salamah (Ummi)
(E) Sharifiya Aminatu (Goggo)
(4) Sharif Rabi’u dan Idriss dan Aminatu ya haifi:
(A) Sharif Abdullahi (Baban gida)
(B) Sharif Aminu
(C) Sharif Abubkar
(D)Sharif Umar
(E) Sharif Usman
(F) Sharif Aliyu
(G)Sharif Mukhtar
(H)Sharif Usama
(I) Sharifiya Sa’adiyya
(J) Sharifiya Saudatu
(K) Sharifiya Maimunatu
(L) Sharifiya Maryam
159
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
160
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sharif Sulaimanu (Allo) dan Usman “Sumu” dan Ibrahim dan Abubakar
Bangaren Sharifiya Uwanin Soro yar’ Sulaimanu (Allo) dan Usman “Sumu”
161
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharif Abubakar (Habu) dan Sulaimanu (Allo) dan Usman “Sumu”
Sharif Abubakar dan Sulaiman Allo ne, kuma ya haifi yarsa mace guda daya,
itace:
1. Sharifiya Maimunatu.
Maimunatu Yar Abubakar ce kuma jikar Sulaimanu Allo dan Usman (Sumu)
dan Ibrahim dan Abubakar, kuma ta haifi mata guda uku sune:
(1) Sharifiya Sa’adatu
(2) Sharifiya Ummu-Kulsum (Wadda akafi sani da Ummu-Kattime)
(3) Sharifiya Rabi’atu: bata da Zuriya (Tsatsonta ya yanke)
162
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Shariifya Salma (Iyana) yar’ Usman “Sumu” dan Ibrahim dan Abubakar
163
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sidi Fari Amale (Sarkin Sharifan Kano) dan Salmah yar’ Usman “Sumu”
Sidi-Fari Amale cikakken sunansa shine Muhammad dan Jaishi dan Ja’afar,
wannan itace nasabarsa ta bangaren mahaifinsa24. Idan muka koma
bangaren mahaifiyarsa, sunanta Salmah (wato Salamatu) kuma sharifiya ce
wadda bisa ga abunda ya tabbata a tarihi, daukacin shariftakar gidan Sidi-
Fari Amale tare da ragowar yan’uwansa, sun sameta ne daga ita Sharifiya
Salmah. Sharifiya Salmah a bisa ingantacciyar Magana kuma sahihiya tare ta
tabbatarwa, ta fitone daga gidan mahaifin su Sharif Yahya Na-Tsakuwa.
Sunan mahaifinta Usman wanda suke kiransa da “Sumu” inda shi kuma dan
Ibrahim ne kuma dan Abubakar25.
164
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
ya tabbata cewa saboda yalwa, har sukuwa ake ta dawaki a cikin gidan
nasa.
A bisa abunda ya tabbata wajen iyaye, masana tarihi da kuma bincike, Sidi-
Fari Amale yayi Sarautar Sarkin Sharifai, kuma yayi wannan sarauta ne
tsakanin 1904 zuwa 191228. Duk da cewa akwai sabani cikin tarihi, amma
bincike da tarihi ta bangaren wadanda suka jibinci Masarauta da kuma
Magabata sun tabbatar da cewa Sarkin Kano Abbas shine ya kirkiri Sarautar
Sarkin Sharifai ta Kano wadda itace irinta ta farko a kasar Huasa. Sarkin
Kano Abbas ya bada ita ga Sharif Yahya Na-Tsakuwa inda shi kuma ya baiwa
dan yar’uwarsa (Salmah) wadda ita kuma Mahaifiya ce ga Sidi-Fari Amale.
Sidi-Fari Amale baiyi sarautarsa a cikin unguwar Darma wadda ta dawo
Sharifai ba, ya gudanar da Sarautarsa ne a fadar Sarki inda yake zuwa ake
gudanar da zaman fada tare dashi a matsayinsa na wakilin Sharifai29.
Ya tabbata cewa Sidi-Fari Amale bai rasu yana kan karagar sarautaba,
hasalima sauka yayi ko kuma murabus bisa radin kansa wanda hakan
yanada nasaba bisa sabani da aka samu tsakaninsa da masarautar Kano,
duk da cewa akwai zantukan al’umma mabanbanta bisa dalilin saukarsa,
amman abunda yafi inganta shine cewa “yayi hukunci ne inda masarauta
tace masa bata yadda da wannan hukuncin ba, wanda hakan matuka ya
hassalashi kuma ya sanya shi zuwa gaban maimartaba Sarki ya ajiye/tube
wannan rawani na sarauta da aka bashi”30. A bisa maganganun magabata,
sarki ya nemi da ya dawo ya cigaba da shugabanci amman bai dawoba31.
Bayan ajiye rawaninsa, Sidi-Fari Amale ya dawo gida ya zauna na wani dan
lokaci, sannan daga bisani ya ibi wasu daga cikin bayinsa tare da rakumansa
ya tafi ya ratsa kasar Agadez harma ya shiga Algeria inda a nanne aka
tabbatar da rasuwarsa32. La’alla, ya kasance cewa, tafiyarsa tanada nasaba
165
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
166
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
167
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
168
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
169
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
170
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(H)Sharifiya Abu
(I) Sharifiya Ummu-Hani
(9) Sharifiya Binta (Hajiya Sharifiya) yar Ibrahim (Halilu) ta haifi:
(A) Sharifiya Kubra
(B) Sharifiya Uwaliya
(C) Sharifiya Ta-Annabi
(D)Sharifiya Barira
(E) Sharif Kabiru (Hashimu)
(F) Sharif Balarabe
(G)Sharifiya Halima
(10) Sharif Aliyu dan Ibrahim (Halilu) ya haifi:
(A) Sharif Muhammad-Nasir (Malam)
(11) Sharifiya Asma’u yar Ibrahim (Halilu) ta haifi:
(A) Sharifiya Sadiya
(B) Sharif Abba
(C) Sharif Yusuf
(D)Sharifiya Binta
(E) Sharif Muhammad
(F) Sharif Ibrahim
(12) Sharifiya Rabi’atu yar Ibrahim (Halilu): Bata da zuriya
171
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
172
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
173
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
174
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
175
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
176
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
177
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
178
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharif Abbas (Dan-uwan Sidi Fari Amale) dan Salmah yar’ Sumu
Sharif Abbas dan-uwan Sidi-Fari Amale ne kuma dan Sharifiya Salmah ne,
ya haifi:
1. Sharif Muhammad (Baba Agun)
2. Sharifiya Hauwa’u (Sharifiya Uwaje)
3. Sharifiya Fadima: Bata da zuriya
179
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sharif Abubakar (Abba Jos) dan Hauwa’u (Uwaje) yar Abbas ya haifi:
(1) Sharif Al-Hassan (Alhaji Dan-Batu) dan Abubakar (Abba Jos) ya haifi:
(A) Sharif Dan-Lami dan Alhassan ya haifi: Walid
(B) Sharif Kabiru dan Alhassan ya haifi: Sabir, Momi, Lubabatu, Hafsa,
Sadik, Aminatu, Ahmad, Zainab, da kuma Muhammad
(C) Sharif Abba dan Alhassan ya haifi: Yasmin, Hussaina, Nura, Aisha,
Taslim, Fadwa, da kuma Ahmad
(D)Sharifiya Aminatu yar Alhassan ta haifi: Zahraddeen, Mubarak, Lalo,
Aminu, Sadik, Umar da kuma Hafsa
180
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sharifya Fadima Yar’ Usman “Sumu” dan Ibrahim dan Abubakar
Sharifiya Fadimatu yar Sharif Usman ce wato “Sumu” kuma an aurar da ita a
gidan Alhaji Muhammad Abba Mai-Kwarno dake nan Unguwar Dukawa
wadda yanzu ta dawo lambar Kofar Wambai, kuma a nanne ta haifi
ya’yanta. Sharifiya Fadimatu ta haifi:
1. Sharif Almustafa (Almu)
2. Sharif Ahmad (Mai-Mesa)
3. Sharif Yusif
4. Idriss
5. Sharif Ibrahim
6. Sharif Jibrin
7. Sharif Dan-Azumi: Bashi da zuriya
8. Sharifiya Iya: Bata da Zuriya
181
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
182
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
183
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
184
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
2. Sharif Inuwa dan Idriss dan Fadima yar Usman “Sumu” ta haifi:
(1) Sharif Adamu (Ado)
(2) Sharifiya Fadima (Binta)
(3) Sharifiya Rabi’atu
185
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
1. Sharifiya Aishatu (Baba Barewa) yar Jibril dan Fadima Kubundu ta haifi:
(1) Sharifiya Lami
(2) Sharif Habibu
(3) Sharif Mahmuda
Gidan Alhaji Sharif Yahya Na-Tsakuwa dan Usman dan Ibrahim dan
Abubakar
Sharif Yahya Na-Tsakuwa shine karami wajen mahaifinsu kuma shine wanda
Allah ya daukaka shi da dukiya mai tarin yawa tare da Shuhura da Ya’ya
hadi da mallakar bayi. Yazo cewa Allah madaukakin Sarki yana amsar
Addu’arsa idan yayita wadda hakan ta sanya mararin Addu’arsa ga salihai
hadi da jin tsoronta ga masu laifi. Yana daga cikin tarihinsa cewa mutum ne
mai girmama kowa tare da mutunta dan Adam inda yake rayuwa da
mutane daban daban wadanda ya hadar harda masu rangwamin hankali
tare da kuma basu hakkinsu. Lokacin da Allah ya karbi rayuwarsa, anyi koyi
da fadin Annabi (SAW) cewa “A ciri itace a saka akan kabari domin samun
gafarar Ubangiji ga mamaci”, yana daga cikin baiwar da Allah yayi masa
cewa yayin da aka dasa wannan ice a kabarinsa (kabarin Sharif Yahya Na-
Tsakuwa) sai wannan itace Allah cikin Ikonsa ya raya shi inda ya zama
bishiya kuma ya kasance cewa daukacin kabarinsa yana karkashin wannan
itaciyar. Hakika wannan baiwa ce ta Ubangiji tare da samun falala dogaro
da cewa mamaci zai dinga samun rahamar Ubangiji matukar wannan itace
da aka saka bai bushe ba. Sunyi zamani daya da Sarkin Kano Abbas, kuma
Allah ya karbi rayuwarsa kimanin sama da shekara 80 data gabata kuma an
binne shi a makabartar Kara dake Abbatuwa.
186
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ya kasance cewa, zuriyar wannan gida mai albarka suna rera baitoci na
waka a duk wani lokaci da wani abu na farin ciki ya faru musamman ma a
bikin aure. Kusan zan iya cewa, a zahiri, babu wasu gidajen Sharifai dake
kusa dasu da suke da wannan al’ada illa su kadai, sun rike wannan al’ada
tasu tsawon lokaci hatta kai cewa, dazarar al’ummar da suka sansu sunji
sautin wannan waken, za’a ayyana cewa “zuriyar gidan Sharifan Dukawa
ne”.
“Yaumi Al-Hashimi,”
“Yaumi Al-Zamzami”
Waka ce aka rera ta bisa tsari na tsarma Larabci da kuma Hausa, wadda
take dauke da nuna alfahari na Nasaba da kuma ni’ima ta wadata a
wanchan lokaci.
187
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Baiti na farko dana biyu suna nufin: wannan rana tamu ce mu da muke da
kaka Annabi (SAW) wanda yake bakurai she kuma muma, jinin kuraishawa.
Baiti na uku: Tabbas wannan ranar fa tamu ce, mu da muke da tsatso mafi
girma wanda Allah dakansa ya bashi kulawa da rijiyar Zamzam kuma muma
muke tsatso daga wannan dangi.
Baiti na hudu: Hakika kakannin mu sun ishe mana komai dama wadanda
suke bamu ba, na daga mutane da kuma bayin su, sannan kuma a farko da
karshe, muke da Annabi (SAW) wanda shi ne ganuwa na dukkanin halittar
Allah.
Baiti na biyar: wannan baitin kuma, yana bayani ne akan gidan Sharif Yahya
Na-Tsakuwa, kasantuwar a wannan zamani kusan ba kowane yake iya yin
bene ba, ya zamto abun alfahari a gurin zuriyar wannan gida cewa wadatar
su ta sanya gidansu akwai bene wanda wannan iko ne daga falalar Allah.
Baiti na Shida: yana yi mana bayani ne akan wanda yayi wannan aiki: wato
Sharif Muhammad Dan-Jiji shi ne yayi wannan bene a gidan Sharif Yahya
Na-Tsakuwa.
Sharif Na-Tsakuwa Ya haifi ya’ya guda goma sha takwas (18) sune:
1. Sharif Danjiji
2. Sharif Magaji
3. Sharif Alh Ibrahim
4. Sidi Liman (Ibrahim)
5. Sharif Alh Yaro: Bashi da zuriya (Bai Haihu ba)
6. Sharif Alh Usman (Tsoho Babba)
7. Sharif Ahmad
8. Sharif Abdu: Bashi da Zuriya (Bai Haihu ba).
188
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sharif Dan-Jiji dan Alhaji Sharif Yahya Na-Tsakuwa ne kuma shi ne babban
dansa, daga cikin halayensa, mutum ne mai tsoron Allah tare da gudun
duniya hadi da hakuri da son yan’uwa. Daga cikin abunda zamu iya tunawa
da shi, “mutum ne mai samun yarjewar Allah idan ya fadi Magana” sau
dayawa idan ya furta abu ko yayi wani zance, cikin ikon Allah sai Allah ya
tabbatar da wannan maganar tasa. A cikin tarihinsa akwai wani lokaci da ya
taba turawa da a siyo masa kunu a wajen wata mai sana’ar sai da kunu
anan unguwar Dukawa amman sai wannan mai saida kunun taki ta sayar
masa da kunun, hakan matuka ya bata masa rai inda ya tashi da kansa yaje
wajenta domin jin ba’asin kin siyar masa da kunun datayi, kasantuwar babu
wani dalili kuma akwai nau’I na wulakantawa sai yayi mata addu’ar cewa
“in Allah ya yarda wannan kunun nata babu mai siye”, mai bada labarin ta
tabbatar mana da cewa “wlh sai da wannan mai sayar da kunun tayi sati
babu mai siyen wannan kayayyaki nata, karshe ma wannan sana’ar tata sai
da lalace gabaki daya”34 .kuma wannan bayani duk wanda yake ya rayu da
Sharif Dan-Jiji ya san afkuwar wannan al’amari, kuma hakan yana nuna
mana tsabar biyayya ga Allah da kuma bin doron tafarkin Shari’a shine yakai
189
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
190
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
191
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(N)Sharifiya Hafiza
(O)Sharifiya Fiddausi
(P) Sharifiya Badriyyya
(Q)Sharifiya Aishatu
(R) Sharifiya Asiya
(S) Sharifiya Fadima
(T) Sharifiya Aminatu
(U)Sharifiya Husna
(V) Sharifiya Khadija
(W) Sharifiya Rukayyatu
(X) Sharifiya Shukra
(Y) Sharifiya Khausar
(4) Sharif Nasiru dan Fadima (Tasidi) ya haifi:
(A) Sharif Auwalu
(B) Sharif Sani
(C) Sharifiya Sharfa
(D)Sharif Mudallib
(E) Sharif Salisu
(F) Sharif Mikdar
(G)Sharif Abulkairi
(H)Sharif Saddik
(I) Sharif Umar
(J) Sharif Usman
(K) Sharifiya Surayya
(L) Sharifiya Aminatu
(M) Sharifiya Khadija
(N)Sharifiya Aishatu
(5) Sharif Sunusi dan Fadima (Tasidi) ya haifi:
(A) Sharif Abubakar (Saddik)
(B) Sharif Abdussamad
(C) Sharif Khalil
(D)Sharif Sulaiman
(E) Sharif Sabi’u
(F) Sharif Abdullahi
192
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(G)Sharifiya Aishatu
(H)Sharifiya Hajiya
(I) Sharifiya Mami
(J) Sharifiya Nusaiba
(K) Sharifiya Fiddausi
(L) Sharifiya Zainab
(6) Sharifiya Maimunatu yar Fadima (Tasidi) ta haifi:
(A) Sharif Sani
(B) Sharif Alkasim
(C) Sharif Abdul’aziz
(D)Sharif Haruna
(E) Sharif Saddik
(F) Sharifiya Safariyya
(G)Sharifiya Haulatu
(H)Sharifiya Salma
(I) Sharifiya Khadija
(J) Sharifiya Fadima (Lubabatu)
193
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
194
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
195
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
196
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharif Alhaji Ibrahim dan Sharif Yahya Na-Tsakuwa dan Usman “Sumu”
197
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(4) Sharif Asta (Hajja Duwala) yar Adamu dan Ibrahim ta haifi:
198
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(6) Sharifiya Hajara (Hajiyan Borno/Hajja Gana) yar Adamu dan Ibrahim
ta haifi:
199
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(1) Sharif Alhaji Hussaini Sarkin Dukawa dan Aminatu (Asabe) ya haifi:
(A) Sharif Muhammad Inuwa
(B) Sharif Salihu
(C) Sharifiya Aminatu
(D)Sharifiya Aishatu
(E) Sharifiya Khadija
(F) Sharifiya Zainab
(G)Sharifiya Hassana
(H)Sharif Hussaini
(I) Sharifiya Binta
(J) Sharifiya Sadiya
(K) Sharif Hassan
(L) Sharif Hussaini
(M) Sharifiya Ummi
(N)Sharifiya Bushra
(O)Sharifiya Bilkisu
(P) Sharif Usman
(2) Sharif Hassan dan Aminatu (Asabe): Bashi da zuriya
(3) Sharif Mu’azzamu dan Aminatu (Asabe) ya haifi:
(A) Sharifiya Khadija
(B) Sharifiya Safiya
(C) Sharf Muhammad Sani
(D)Sharif Ahmad
(E) Sharif Muhammad Jilani
(F) Sharifiya Hauwa’u
(G)Sharif Muhammad Samiru
(H)Sharif Umar
(I) Sharifiya Rukayyatu
(J) Sharifiya Binta
(K) Sharifiya Salamatu
(L) Sharif Muhammad Nura
(M) Sharifiya Harira
(N)Sharifiya Murjanatu
(O)Sharif Ja’afar
200
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
201
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Albarka) daga gurinsa aka same shi inda shi kuma daga gurin
magabatansa. Ya kasance dattijo mai Nutsuwa tare da fikira hadi da
kiyaye tarihi, yayi tafiye tafiye izuwa kasashe daban daban tare da
samun ilimi na daga fannin Addini da kuma zamntakewar rayuwa. Muna
Addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa ya kuma sada shi da kakansa
Annabi (SAW). Amin.
202
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
203
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
204
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
205
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(2) Sharifiya Hajara (Hajiyan Kadawa) yar Rakiya yar Ibrahim ta haifi:
206
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
207
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
208
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
209
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
210
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(G)Sharif Sadisu
(H)Sharif Hamisu: Bashi da zuriya (Tsatsonsa ya yanke)
2. Sharif Abbas Mai-Doki dan Sidi Liman, Jikan Na-Tsakuwa, Ya haifi:
(1) Sharifiya Aminatu yar Abbas (Mai-Doki) ta haifi:
(1) Sharifiya Sha’awanatu
(2) Sharifiya Nasara
(3) Sharif Umar
(4) Sharif Mustafa
(5) Sharifiya Saratu
(6) Sharifiya Hannatu
(2) Sharifiya Memuna yar Abbas (Mai-Doki) ta haifi:
(1) Sharif Saifullahi
(2) Sharifiya Fiddausi
(3) Sharifiya Zahra’u
(4) Sharifiya Rukayyatu
(5) Sharif Umar
(6) Sharifiya Habiba
(7) Sharifiya Ummukulsum
(8) Sharif Auwalu
(3) Sharifiya Binta yar Abbas (Mai-Doki) ta haifi:
(1) Sharif Badaru
(2) Sharif Jaddah
(3) Sharif Amir
(4) Sharifiya Rukayya
(5) Sharifiya Kairatu
(6) Sharif Mukhtar
(7) Sharif Abbas
(8) Sharif Ahmad
(4) Sharifiya Kursiyya yar Abbas (Mai-Doki) ta haifi:
(A) Sharif Inuwa
(B) Sharifiya Rufaidah
(C) Sharifiya Aishatu
(D)Sharifiya Khadija
(E) Sharifiya Ummu-Ruman
211
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
212
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
213
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
214
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
215
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(G)Sharif Sulaiman
216
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
217
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
218
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
219
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
220
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
221
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
222
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
223
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(D)Sharifiya Fatima
(E) Sharif Salim
(F) Sharifiya Zainab
(G)Sharifiya Rukayya
224
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
225
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
226
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
227
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
228
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
229
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
230
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharif Ahmadu dan Sharif Yahya Na-Tsakuwa dam Usman “Sumu”
231
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(4) Sharif Sani (Sabo) dan Fadima (Sidi) yar Ahmadu ya haifi:
232
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
233
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharif Alhaji Haruna dan Sharif Yahya Na-Tsakuwa dan Usman “Sumu”
234
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(2) Sharifiya Bilkisu (Jiyan) yar Auwalu dan Haruna, (Anyi auren zumunci
tsakanin Sharif Sunusi dan Sharif Sani Mai-Aku dan Sharif Yahya Na-
Tsakuwa da kuma Sharifiya Bilkisu yar Sharif Auwalu dan Sharif Yahya
Na-Tsakuwa) ta haifi:
235
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
236
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
237
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
238
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(G)Sharifiya Usaina
(H)Sharifiya Khadija
(I) Sharifiya Kairiyya
(2) Sharif Salisu (Malan) dan Fadima (Uwani) yar Haruna ya haifi:
239
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(D)Sharif Ahmad
(E) Sharif Muhammad (Mamman)
(F) Sharif Mahmud
(4) Sharifiya Amina (Lami) yar Fadima (Uwani) yar Haruna ta haifi:
240
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
241
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharif Alhaji Sani (Baba Mai-Aku) dan Sharif Yahya Na-Tsakuwa dan Usman
“Sumu” dan Ibrahim dan Abubakar
242
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
243
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
244
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
245
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
246
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
7. Sharifiya Aishatu (Lami). Yar Alhaji Sani ce (Baba mai Aku), ta haifi:
(1) Sharifiya Binta
(2) Sharifiya Aisha
(3) Sharif Muhammad
(4) Sharif Hussaini
(5) Sharif Mujtaba
247
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
248
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharifiya Maimunatu yar’ Sharif Yahya Na-Tsakuwa dan Usman “Sumu”
Ta auri sharif Abubakar (Mai-Kantai) dan Sidi-Fari Amale, kuma sun haifi:
1. Sharif Hajji
2. Sharif Shu’aibu
3. Sharifiya Zainabu (Jabu)
249
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
250
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
251
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
252
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Bangaren Sharifiya Binta yar’ Sharif Yahya Na-Tsakuwa dan Usman “Sumu”
253
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sharifiya Aminatu (Uwar Na-Hakuri) yar’ Usman “Sumu” dan Ibrahim dan A bubakar
Aminatu wadda akafi sani da “Uwar Na-Hakuri”, ya’ ce gurin Sharif Usman
“Sumu”, kuma kamar yadda ya tabbata a tarihi, itace mahaifiyar Na-Hakuri
da yan’ Uwansa. Bayan data kai munzalin aure, mahaifinta Usman Sumu ya
aurar da ita anan gidan Majema dake bakin titin Dukawa dake cikin kwaryar
birnin Jahar Kano. ya tabbata cewa a gidan da tayi aure tanada abokanan
zama (Kishiyoyinta) kuma bisa hakan ya sanya cewa, zamu tattara bayanan
wannan bangare na Aminatu izuwa ga ya’yan da ita ta Haifa domin cewa
254
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
nasabarsu itace wadda take kaiwa ga zuriyar gidan iyayen Sharif Yahya Na-
Tsakuwa.
Sharifiya Aminatu yar’ Usman dan Ibrahim dan Abubakar dan Dawud dan
Abi-Abdurrahman Al-Barra’I dan Sulaiman Musa dan Sulaiman dan Ukairu
dan Muhammad dan Usman dan Ibrahim dan Shekh Ja’afar Al-Sanusi dan
Muhammad dan Sa’ad dan Muhammad dan Makhluf dan Muhammad dan
Muhammad dan Hammad dan Abdurrahman dan Abdulwahid dan Hammad
dan Muhammad dan Abdullahi dan Yunus dan Abibakar dan Aliyu dan
Hurma dan Isa dan Sulaiman (Salam) dan Ahmad (Mizwar) dan Aliyu
(Haidara) dan Muhammad Al-Khalifa dan Idriss Al-Asghar dan Idriss Al-
Akhbar dan Abdullahi Al-Khamil dan Hassan Al-Musannah dan Hassan Al-
Mujtaba dan Imam Aliyu da kuma Nana-Fadima Al-Zahra’u yar Annabi
(SAW).
8. Sharif Adamu
255
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Abubakar
Abbas
Muhammad
Usman
Sulaiman (Allo) “Sumu” Ibrahim
Fadima (Kubundu)
256
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Aminatu (Kundun)
Adamu
Gidan Sharifiya Maryam yar’ Aminatu (Uwar Na-Hakuri) yar’ Usman “Sumu”
Bangaren Sharif Muhammad (Duna) dan Maryam yar’ Aminatu (Uwar Na-
Hakuri) ya haifi:
1. Sharifiya Maryam (Hajiya Jummai) ita kadai ya haifa (Muhammad
Duna)
kuma ta haifi:
(1) Sharif Hassan:Bashi da zuriya
(2) Sharif Hussaini: Bashi da zuriya
(3) Sharifiya Usaina: Bata da zuriya
(4) Sharif Hassan: Bashi da zuriya
(5) Sharif Abdullahi (Sabo Sarki)
257
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sulaimanu (Na-Hakuri) dan Aminatu (Uwar Na-Hakuri) yar Usman “Sumu”
258
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
259
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
260
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sharifiya Aminatu (Kundun) yar Sulaimanu Na-Hakuri ce, sun koma garin
Fataskum inda a wannan gari ne suka yada daukacin Zuriyarsu.
261
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
262
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
263
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
264
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sharif Abdurraziki dan Aminatu (Uwar Na-Hakuri) yar’ Usman “Sumu”
265
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
266
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
267
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
268
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
269
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
270
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
5. Sharifiya Binta
6. Sharif Habibu
7. Sharifiya Safiyya
8. Sharif Malam Nasiru
9. Sharifiya Khadija (Gaji): Bata da zuriya
10.Sharif Aliyyu
11.Sharif Abubakar: Bashi da zuriya
271
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
272
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
273
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
274
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
275
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
276
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Gidan Sharif Yakubu (Bauchi) dan Aminatu (Uwar Na-Hakuri) yar Usman “Sumu”
277
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
1. Sharif Rabi’u
2. Sharifiya Hajiya Gambo
3. Sharifiya Hajiya Azumi
4. Sharif Sani: Bashi da zuriya (Tsatsonsa ya yanke)
5. Sharif Hassan : Bashi da zuriya (Tsatsonsa ya yanke)
6. Sharif Hussaini: Bashi da zuriya (Tsatsonsa ya yanke)
278
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
1. Sharifiya Hadiza (Dije) yar Alh Rabi’u dan Yakubu Bauchi, ta haifi:
(1) Sharif Baban Zage
(2) Sharif Magaji
(3) Sharif Mubarak
(4) Sharif Ghali
(5) Sharif Abdurrazak
(6) Sharif Aliyu
2. Sharif Sule dan Alh Rabi’u dan Yakubu Bauchi ya haifi:
(1) Sharif Mujittafa
(2) Sharif Kabiru
(3) Sharif Najiyullahi
(4) Sharif Hadiyatullahi
(5) Sharifiya Maryam
(6) Sharif Mujittafa
(7) Sharifiya Fatima
(8) Sharifiya Aisha
(9) Sharifiya Kadija
(10) Sharif Ahmad
(11) Sharif Muhammad
(12) Sharif Mustafa
3. Sharif Sani dan Alh. Rabi’u dan Yakubu Bauchi ya haifi:
(1) Sharif Abba
(2) Sharif Isyaku
(3) Sharif Yusif
(4) Sharif Sanusi
(5) Sharif Najib
(6) Sharif Naziru
(7) Sharif Sale
(8) Sharif Ya’u
(9) Sharif Adamu
(10) Sharif Hadi
(11) Sharif Hadi
(12) Sharif Sani
(13) Sharif Mutawakkilu
279
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
280
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
11.Sharifiya Aisha (A’i) yar Alh Rabi’u dan Yakubu Bauchi ya haifi
(1) Sharifiya Marwanatu
281
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
282
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
2. Sharifiya Habiba
Bangaren Sharifiya Gambo yar Yakubu Bauchi dan Aminatu (Uwar Na-
Hakuri) ta haifi:
1. Sharif Habibu
2. Sharifiya Aminatu
3. Sharif Idriss (Idi): Bashi da zuriya (Tsatsonsa ya yanke)
283
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
284
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
285
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
286
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
7. Sharif Isma’il
8. Sharif Kabiru
9. Sharifiya Aminatu
10.Sharif Muhammad: Bashi da zuriya
287
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Ta auri sharif Ibrahim (Halilu) dan Sidi-Fari Amale kuma daukacin zuriyarta
suna komawa ne gidan sharif Halilu kuma ta Haifa masa ya’ya guda hudu
sune:
1. Sharif Abbas (Gambo)
2. Sharif Muhammad Al-Kabir (Baba Dan-Ladi)
3. Sharif Hassan
4. Sharifiya Binta (Anyalo/Hajiya Sharifiya)
288
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
289
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
290
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
291
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
292
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
293
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
294
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
295
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
296
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
297
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
298
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
(29) Dr. Rashid: Dar Al-Uloum :2016 bayanin Dr. Rashid Kous
(30) Imam Ahmad: Musnad na Imam Ahmad
(31) Tirmuzi: Sunanu Turmuzi
(32) Al-Sulmi: Al-Ashraf Ala Ba’adu man bifas min mashahirul
Ashraf na Muhammad Al-Dalib bin Alhaj Sulmi
(33) Sharif Isma’il: sharifi kuma cikakken masanin tarihi, Allah ya
bashi kaifin hadda tare da kiyaye tarihi, kuma dukkan tarihin gidan
Sharif Yahya Na-Tsakuwa shi ne ya bada shi tare da taimakon
ragowar yan’uwansa.
(34) Sharif Salisu kankarofi: babban malami kuma masanin tarihi,
shi ne wanda ya fara karfar Nasabar gidan Sharif Yahya Na-Tsakuwa
a hannun Sharif Isma’ila domin taskancewa da kuma rubuta littafin
Sharifai
(35) Sharif Jibril Al-Ashtari Al-Hassani: mai rike da mukamin Dan-
Masanin Sharifai na Nigeria kuma masani akan tarihin Shariai da
Nasabobinsu, shi ne nabiyu a karbar tarihi da kuma nasabar gidan
Sharif Yahya Na-Tsakuwa domin taskancewa..
(36) Al-Ummar garin Tammawa: sune wandanda naje (Mawallafin
littafi) domin bincike tare ta tabbatar da tarihin gidan sharif Yahya
Na-Tsakuwa kuma Alhamdulillah, binciken yayi dai dai da abunda
tarihin gidan Na Tsakuwa ya tabbatar cewa “zuriyar gidan na
tsakuwa sune tushen kafuwar unguwar Sharifai dake tammawa
kuma dalilin zamansu yasa ake kiran unguwar da Sharifai. Wadanda
na samu damar zantawa dasu sune: Malam Shu’aibu wanda yake
limamin unguwar Sharifai dake tammawa kuma mai bada karatu a
masallacin, da Mukhtari Aliyu wanda dattijo ne a garin, da Malam
Muhammad Rayyanu shima dattijo ne a garin, da kuma Alhaji Garba
Jali wanda shi ne Sarkin Fulanin Tammawa bangaren Tammawar
Fulani kusa da Unguwar Sharifai.
(37) Sharif Nura Waziri Alkali: Masani akan tarihin Sharifai kuma
makusanci ga Masarautar Kano tare da tarihinta
(38) Sharifiya Jummai yar Sharif Inuwa jikar Sharif Ibrahim dan
Sharif Yahya Na-Tsakuwa, itace wadda sharif Dan-Jiji ya aika ta siyo
masa kunu kuma ta shaida dukkan abunda ya faru tare da
299
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
300
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
16 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 54 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir
17 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 55 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir
18 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn ASIR 56 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir
19 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 57 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir
20 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 58 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Kasir
21 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 59 Furiy, Ibn Asir
22 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 60 Furiy
23 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 61 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir
24 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 62 Furiy
25 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 63 Furiy
26 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 64 Furiy
27 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 65 Furiy, Ibn Asir
28 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 66 Furiy, Ibn Asir
29 Kur’an 67 Furiy, Ibn Asir
30 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 68 Furiy, Ibn Asir
31 Kur’an 69 Furiy, Ibn Asir
32 Ibn Kasir, Al-Zuhri, Ibn Asir 70 Furiy, Ibn Asir
33 Kur’an 71 Furiy, Ibn Asir
34 Ibn Kasir, Al-Zuhri 72 Furiy, Ibn Asir
35 Ibn Kasir 73 Furiy, Ibn Asir
36 Ibn Kasir 74
37 Ibn Kasir 75
38 Ibn Kasir 76
Sashi Na-Biyu
1 Furiy 8 Furiy
2 Furiy 9 Al-Lahwi
3 Furiy 10 Furiy
4 Furiy 11 Furiy
5 Furiy 12 Kalidi
6 Furiy 13 Furiy
7 Furiy 14 Furiy
301
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sashi Na Uku
1 Furiy 23 Furiy
2 Furiy 24 Furiy
3 Furiy 25 Furiy
4 Furiy 26 Furiy
5 Furiy 27 Furiy
6 Furiy 28 Furiy
7 Furiy 29 Furiy
8 Furiy 30 Furiy
9 Furiy 31 Furiy
10 Unubi 32 Furiy
11 Furiy 33 Furiy
12 Furiy 34 Furiy
13 Furiy 35 Furiy
14 Furiy 36 Furiy
15 Furiy 37 Furiy
16 Lecture Na Barrister Dan-Almajiri 38 Furiy
Kano
17 Furiy 39 Furiy
18 Furiy 40 Furiy
19 Furiy 41 Furiy
20 Furiy 42 Furiy
21 Furiy 43 Furiy
22 Furiy 44 Furiy
Sashi Na Hudu
1 Al-Lahwi 18 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
2 Al-Lahwi 19 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
3 Nabahani, 20 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
4 Nabahani, Al-Zayyani 21 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
5 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi 22 Audio Lecture Barrister Dan-
Almajiri
6 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi 23 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
7 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi 24 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
8 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi 25 Nabahani, Al-Zayyani, Al-Lahwi
302
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
Sashi Na Biyar
1 Al-Lahwi:34 31 Razi
2 Al-Lahwi:38, Al-Alawi:12-13 32 Razi, Al-Kalidi,
3 Bukhari:1, Al-Lahwi 33 Al-A’araji, Razi, AL-Zur’aini
4 Al-Lahwi:39 34 Razi, Al-Kalidi
5 Unubi:101, Al-Alawi 35
6 Unubi, Bukhari, Al-Alawi 36 Razi
7 Al-Alawi:12-13, Al-Lahwi:38 37 Kalidi
8 Al-Ayyashi:22, Al-Zayyani:46, Al- 38 Razi
Lahwi:111
9 Razi:3 39 Kalidi
10 Unubi:107, Al-Alawi 40 Kallidi
11 Bukhari:4-5, Razi:3-4 41 Samarkandi:34
12 Unubi, Bukhari, Al-Alawi 42 Samarkandi:35, unubi:317
13 Samarkandi:38-39, Unubi 43 Samarkandi:36
14 Samarkandi, Unubi, Al-Alawi, 44 Unubi:333
Bukhari
15 Samarkandi, Unubi, Al-Alawi, 45 Bukhari:30,
Bukhari Razi:7393,Samarkandi:44:45
16 Samarkandi, Bukhari, Razi 46 Samarkandi:45, Bukhari, Unubi
17 Al-Zayyani:49, 47 Unubi:339
18 Samarkandi:24 48 Unubi:339
19 Samarkandi:24 49 Al-Alawi:106
20 Samarkandi:25 50 Samarkandi:80-81
303
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
21 Samarkandi:25 51 Samarkandi:88-89
22 Unubi:372 52 Samarkandi:90-97
23 Unubi:572 53 Sanarkandi:97-102
24 Al-Zayyani:54 54 Samarkandi:87
25 Unubi:372 55 Samarkandi:102
26 Unubi,Bukhari, Al-Alawi, Razi, 56 Samarkandi:103
Samarkand
27 Al-Lahwi, Al-Shaibani 57 Samarkandi:104
28 Al-Shaibani:107 58 Samarkandi:108
29 Al-Kalidi 59 Samarkandi:
30 Al-Kalidi 60 Samarkandi:109
Sashi Na Shida
1 Nabahani, Al-Lahwi 11 Al-Asfahani:139
2 Al-Asfahani:366 12 Al-Asfahani
3 Al-Asfahani 13 Al-Asfahani:184
4 Al-Asfahani 14 Al-Asfahani:185
5 Al-Asfahani 15 Al-Asfahani:182
6 Al-Asfahani:40 16 Al-Asfahani
7 Al-Asfahani 17 Al-Asfahani:386
8 Al-Asfahani 18 Al-Asfahani
9 Al-Asfahani:98 19 Al-Asfahani
10 Google Search, Wekepedia 20
Sashi Na Bakwai
1 Al-Asfahani:366 35 Al-Abidi:107
2 Google Search, Wekepedia 36 Google Search Al-Fasi na Libya
3 Samarkandi,Bukhari, Unubi, Al-Alawi 37 Al-Harraki:31,132
4 Unubi, Al-Alawi:62 38 Dr.Rashid-Dar-Al-Aloum
5 Al-Lahwi, Al-Alawi, Bukhari, Razi, 39 Al-Harraki, Musnad Imam Ahmad
6 Al-Lahwi 40 Sunan Tirmizi
304
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
7 Al-Lahwi 41 Nabahani
8 Al-Lahwi 42 Al-Harraki:177
9 Al-Lahwi 43 Al-Harraki:171
10 Al-Lahwi 44 Al-Harraki:208, Al-Lahwi:84
11 Al-Lahwi 45 Al-Harraki:116, Al-Saba’i
12 Al-Lahwi 46 Al-Harraki:117
13 Al-Lahwi 47 Al-Harraki:118
14 Al-Lahwi 48 Al-Harraki:116
15 Al-Lahwi 49 Al-Harraki:117
16 Al-Lahwi 50 Al-Harraki
17 Al-Lahwi 51 Al-Harraki:173
18 Al-Lahwi 52 Al-Harraki:259
19 Al-Lahwi 53 Al-Harraki:257
20 Al-Lahwi 54 Al-Zuhri:9
21 Al-Lahwi 55 Al-Jauzi
22 Al-Lahwi 56 Al-Jauzi
23 Al-Lahwi 57 Al-Jauzi
24 Al-Lahwi 58 Al-Jauzi:86
25 Al-Abidi:50 59 Al-Jauzi
26 Al-Abidi:49-50 60 Al-Asfahani
27 Al-Abidi:50 61 Al-Lahwi:276
28 Al-Abidi:50 62 Al-Jauzi:77, Al-Suyudi:83
29 Al-Abidi:51 63 Al-Suyudi
30 Al-Abidi:54 64 Al-Jauzi
31 Al-Abidi:55 65 Al-Suyudi:68
32 Al-Abidi:57-60 66 Al-Suyudi:71
33 Al-Abidi:61 67 Al-Suyudi:78
34 Al-Abidi:65-66 68
305
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
306
Tarihin Sharif Yahaya Na Tsakuwa Hamza G. Abdullahi
307