Download as pdf or txt
Download as pdf or txt
You are on page 1of 22

See discussions, stats, and author profiles for this publication at: https://www.researchgate.

net/publication/325262366

Ashma'wi Asaukake

Preprint · May 2008

CITATIONS READS
0 20,549

1 author:

Usman Ahmed Adam


Kaduna State University
19 PUBLICATIONS 25 CITATIONS

SEE PROFILE

Some of the authors of this publication are also working on these related projects:

Assessment of the Management of Public Access Computers in Academic Libraries in Kaduna State, Nigeria View project

All content following this page was uploaded by Usman Ahmed Adam on 21 May 2018.

The user has requested enhancement of the downloaded file.


0

Fassara cikin

Na Sheikh Abdul-Bari Al-Ashama’wi

Fassarar
Usman Ahmed Adam
1

Sadaukarwa
Na sadaukar da wannan kokarin zuwa ga Mahaifi na Wanda son sa gareni yasa
yasani a hanyan karatu bai gusheba yana karfafe ni har Allah ya dauki ransa, Zuwa ga
Mahaifiya ta wacce son da take mani yasa taketa karfafe ni kan karatu tana ji dani
har gobe. Allah Ina rokon ka kasaka masu da dukkan Alheran ka, ka basu ladan
fassarawa da duk wanda kabashi ikon karantawa.

GABATARWA
Ina farawa da Sunana Allah mai rahama mai Jinkai, Dukkan godiya ta
tabbabta ga Allah mahaliccin kowa da komai, Tsira da Amincin Allah su
tabbata ga fiyayyen halitta Shugaban mu Ja goran mu mai shir yarda mu
Annabin mu Muhamadu (SAW), Tsira da Amincin Allah su tabbata ga
Matanshi da ’Ya’yanshi da Sahabbanshi da duk wanda yayi masu bi su har
zuwa ranar Sakamako.
Bayan haka bazan iya kiran wannan Fassara ba saboda nasan cewa bai isa
akirashi da wannan sunanba, amma zan iya kiranshi dan kokarin fassara, na
rubuta shine bias alkawari da nayiwa yaya ta kan cewa zamu karanta
wannan littafi da sauran littafan da ake karantasu azaure na fikhu, ganin
cewa Allah bai sa karatun ya doreba sai nayi Alkawarin zan fassara mata su
cikin harshen hausa a rubuce. Gashi Allah ya yarda na fara da Ahalari da
Ishmawi ina mai rokon sa yasa su zamo masu amfani gareni da ita da duk
wanda yasami ikon karantawa ya kuma bani ikon cigaba da Fassara sauran
har zuwa Lauwali da sani amin.
2

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI

Shehu Abdul-Bari Mutumin Ashmawi dan darikan rufaiyyah (Allah yai


mashi rahma) yace: wasu daga cikin Abokai na sun nemi in wallafa littafi
takaitacce Akan tafar kin fikihun Imam Malik (maz haban Malikia) Allah ya
Kara masa Yarda, Sai na amsa masu, ina mai kaunar Lada gun Allah.

BABIN ABUBUWAN DAKE WARWARE ALWALA

Kasani (Allah yai maka dace) Cewa: Abubuwan da suke warware Alwala
sun kasu kashi Biyu (2):-

1. HADASAI:
2. SABUBBAN HADASAI (Abubuwan da zasu iya haifar da hadasi)

1. Kaga HADASAI, Guda Biyar (5) ne, uku daga GABA sune: MAZIYI,
WADIYI da BAWALI (Fitsari) biyu daga BAYA Sune: BAYAN
GIDA da TUSA.
2. Sukuma SABABBAN HADASAI:
* BARCI: yakasu kashi hudu (4):-
- Barci mai tsawo mai nauyi Yana warware Alwala
- Barci Gajere mai nauyi shima Yana warware Alwala
- Barci gajere mare nauyi baya warware Alwala
- Barci mai tsawo mare nauyi an so sake mashi Alwala.

* Yana da ga cikin Sababban hadasi wanda suke warware Alwala:


1. Gushewar hankali, da hauka, suma ko, maye
2. Fita daga Addini (Ridda)
3. Kokwanto cikin samuwar hadasi
4. Shafan Azzakari da tafin hannu ko tafin yatsu koda da cindo ne
inyanaji indan wani abu ya shafeshi.
5. Shafa (Mace ko Namiji) yana da hukunci hudu.
- in yai nufin jindadi da shafan kuma yasami jin dadin zai sake
Alwala
- In yasami jin dadin batare da nufiba, zai sake Alwala
- In yashafa don yaji dadi saibai ji da dinba zai sake Alwala
- In bainufi jin dadi da shafanba kuma bai ji dadin ba dayashafa
bazai sake Alwalaba
3

Abubuwanda basa warware Alwala


Alwala bata warwarewa da:
- shafan dubura
- Shafan marena
- shafan farjin yarinya karama
- yin amai
- cin naman rakumi
- yin kaho
- yin Kyas Kyastu
- yin dariya acikin sallah (Sallar ta baci)
- ko in mace tashafi farjin ta ( ance inta shigarda yatsanta zata
sake Alwala)
Allah Shine mafi sani.

BABIN RUWAN DA YAHALATTA AYI ALWALA DASHI

Kasani (Allah yai maka dace) cewa: Ruwa ya kasu kashi biyu
1. Wanda ya hadu da wani abu
2. Da kuma wanda bai hadu da wani abu ba

2. Kaga ruwanda bai hadu da wani abu ba shine ruwa mai


tsarkakewa, wato sakakken ruwa Wanda ya halasta ayi Alwala dashi,
ruwan samane ko Wanda yabubbugo daga kasa.

1. Ruwan daya hadu dawani abu kuma daya daga ciki suffofin sa uku
suka canza ( Launi, Dandano, Ko Kanshi,) yakasu kashi biyu:

* Ruwanda yahadu da najasa:


- Ruwanda ya hadu da najasa ya kuma chanza bai in ganta ayi
Alwala dashiba.
- Ruwanda ya hadu da najasa amma bai canzaba in rowan bashi
da yawa najasar ma bata da yawa an karhanta Alwala dashi
abisa mashhurin zance.
* Ruwanda yahadu da abu mai tsarki:
- Ruwanda ya hadu da abu mai tsarki in za a iya raba abinda
ruwan; kamar ruwanda ya hadu da za’afaran, wardi ko kullu da abinda
yai kama dasu, Ruwan na da tsarki akansa amma bazai tsarkake wani ba,
za a iya amfani da shi cikin al’a du na yauda kullum kamar girki, kamu,
4

sha da abin da yai kama da haka, ba zai yiwu ayi amfani da shi cikin
Ibadu ba, Kamar Alwala ko wanin shi.
- Idan abin bazai yiwu a raba shi da ruwan ba, kamar gishiri ko
kanwa ko abinda yai kama dasu ko kuma ruwanda yake gudana a taskar
arsenic ko kibrit duk wannan Ruwan masu Tsarkakewa ne ga wanin su, za a
iya Alwala dashi.
Allah shine mafi sani.

BABIN FARILLAI, SUNNONI DA MUSTAHABBAN ALWALA

FARILLAN ALWALA GUDA BAKWAI (7) NE:


1. Niya lokacin wanke fuska,
2. Wanke fuska
3. Wanke hannuwa zuwa gwiwan hannu
4. Shafan dukkan kai
5. Wanke Kafafuwa zuwa idon sawu
6. Gaggawa
7. Cudanyawa
Sannan kuma ya wajaba agare ka lokacin wanke fuska ka tsatstsefe gashin
gemunka in gemun babu kauri yazama za’a iya ganin fata, in kuma yana da
kauri tsatstsefewa bai wajaba a gareka ba. Haka kuma ya Wajaba agare ka
lokacin wanke hannuwan ka ka tsefe yatsun ka, bisa mashahurin zance.

SUNNONIN ALWALA GUDA (8) NE:


1. Wanke hannuwa da farko zuwa idon hannu
2. Kuskure baki
3. Shakaruwa
4. Fyacewa
5. Dawo da shafan kai
6. Shafan kunnuwa (ciki da waje)
7. Sabonta ruwa don shafan kunnuwa
8. Jera tsakanin farillai.

MUSTAHABBAN ALWALA GUDA BAKWAI (7) NE:


1. Fadin Bisimillah wajen farawa
2. Waje mai tsarki
3. Karanta Ruwa bada iyakaba
4. Ajiye Kwarya ahannun dama in budadde ne ( in kuma ba budaddeba
ne sai a ajiye a hannun hagu kamar buta)
5. Wanke wa na biyu da na uku, in na farko ya cika,
5

6. Farawa da magabacinkai
7. Yin aswaki
Allah shine mafi sani.

BABIN FARILLAI, SUNNONI DA MUSTAHABBAN WANKA

FARILLAN WANKA GUDA BIYAR (5) NE


1. Niyya
2. Gama jiki da ruwa
3. Cuda dukkan jiki
4. Gaggawa
5. Tsatstsefe gashi
SUNNONIN WANKA GUDA HUDU (4) NE:
1. Wanke hannuwa zuwa idon sawu
2. Kuskure baki
3. Shaka ruwa
4. Shafan kunnuwa
MUSTAHABBAN WANKA GUDA SHIDANE (6):
1. Farawa da gusarda kazanta daga jiki.
2. Sannan cika wanke gabobin Alwala
3. Wanke saman jiki kafin kasa
4. Wanke kai so uku
5. Farawa da dama kafin hagu
6. Karancin ruwa tareda kyautata Wankewa.
Allah shine mafi sani..

BABIN TAIMAMA
FARILLAI SUNNONI DA MUSTAHABBAN TAIMAMA

FARILLAN TAIMAMA GUDA HUDU (4) NE:


1. Niyya ( mutun yai niyan halasta ma kansa sallah da Taimama do
taimama bata dauke hadasi bisa mashahurin zance)
2. Shafan dukkan fuska da hannuwa zuwa idon hannu
3. Bugun kasa na farko
4. Waje mai tsarki (shine duk wani abinda yake doron kasa na kura,
rairayi, dutse ko tsakuwa da abinda yayi kama da haka.
SUNNONIN TAIMAMA GUDA UKU (3) NE:
1. Jeranta shafa
2. Shafa daga idon hannu zuwa gwiwa
3. Sabunta bugun kasa do shafan hannaye
6

MUSTAHABBAN TAIMAMA GUDA UKU (3) NE:


1. Fadin bisimilla
2. Farawa da shafan mabayyanin hannun dama da hagu zuwa guiwa san
nan ciki zuwa karshen yatsu.
3. Da shafan hannun hagu kamar haka.
Allah shine mafi sani.

BABIN SHARUDDAN SALLAH.


SALLAH NADA SHARUDDAN WAJIBCI DA SHARUDDAN
INGANCI

SHARUDDAN WAJIBCIN SALLAH GUDA BIYAR (5) NE:


1. Musulunci
2. Balaga
3. Hankali
4. Shigan lokaci
5. Isan kiran manzon Allah (S.A.W)
SHARUDDAN INGANCIN SALLAH GUDA SHIDA (6) NE:
1. Tsarkin hadasi
2. Tsarkin habasi
3. Fuskantan gabas
4. Suturta Al-aura
5. Barin zance
6. Barin ayyuka masu yawa
Allah shine mafi sani.

BABIN FARALLAI, SUNNONI, MUSTAHABBAI DA


MAKARUHAN SALLAH

FARILLAN SALLAH GOMA SHA UKU (13) NE:


1. Niyya
2. Kabbaran harama
3. Tsayuwa domin kabbaran harma
4. Karatun Fatiha
5. Tsayuwa domin Karatun Fatiha
6. Ruku’u
7. Dagowa daga Ruku’u
8. Sujjada
9. Dagowa daga Sujjada
7

10.Zaman karshe gwargwadon fadin Assalamu Alaikum


11.Fadin Sallama (da kalman Assalamu Alaikum ba salamu alaikum ba)
12.Natsuwa
13.Daidaituwa
SUNNONIN SALLAH GUDA GOMA SHABIYU (12) NE:
1. Karatun Sura bayan Fatiha araka ta farko
2. Karatun Sura bayan Fatiha araka ta biyu
3. Tsayuwa domin karatun Surah
4. Asurtawa a inda ake asurtawa
5. Bayyanawa inda ake bayya nawa
6. Dukkan kabbara sunnace (ban da kabbaran harama ita faralice)
7. Fadin sami Allahu Liman Hamidahu ( ga liman ko mai Sallah
Shikadai)
8. Zaman tahiya ta farko
9. Abinda ya karu nazama akan gwargwadon fadin Assalamu Alaikum a
tahiya ta biyu
10.Mayarda sallama ga liman
11.Mayarda Sallama ga wanda yake hagu idan akwai wani
12.Sa Sutra ga liman ko mai Sallah shikadai in anji tsoron wuce wan
wani.
MUSTAHABBAN SALLAH GUDA GOMA (10) NE
1. Daga hannuwa lokacin kabbarar harama
2. Tsawaita karatu cikin Sallah Subahi
3. Tsawaita karatu cikin Sallar Azuhur
4. Takaita karatu cikin sallar La’asar
5. Takaita karatu cikin sallar Magariba
6. Tsakaita karatu cikin sallar Isha’I
7. Fadin Rabbana walakal Hamdu ga mai bin liman ko mai sallah shi
kadai
8. Yin Tasbihi a cikin ruku’u da adu’a cikin sujjada
9. Fadin Amin ga liman aboye
10.Karanta Al-kunuti, itace kamar haka:-
Allahumma Inna nasta iinuka wa nastag firuka wa nu’uminu bika
wa natawakkalu alaika, wa nasni alaikal Khaira kullahu, Nash kuruka
wala nakfiruka, wa nakhna’u laka wa nakhla’u wa natruku
mayyakfuruka, Allahumma Iyyaka na’abudu walaka nusalli wa
nasjudu wa ilaika nas’ah wa nahfidu narju Rahmataka wa nakhafu
azabakal Jidda inna azabaka bil kafirina mulhiku.
8

FASSARA DA HAUSA
(Ya Allah ga reka muke neman taimako, gunka muke niman ga’fara, munyi imani
dakai, kuma gareka muka dogara, muna maka yabo da duk wani alheri, muna gode
maka, bama kafirce maka, muna masu biyayya gareka masu kaskantar da kai, muna
barin duk wanda ya kafirce maka, Ya Allah kai muke bautama muna sallah muna
sujjada garela, kuma gareka muke muke taruwa muna kaunar rahmarka muna
tsoron azabarka kwarai, lallai azabarka mesaduwace ga kafirai.)

Asallan Asuba ne kawai ake karanta Alkunut a boye a raka ar karshe


kafin ai ruku’u.
Shiko karatun tahiya Sunnane ana karantawa kamar haka:
Attahiyyatu Lillahi Azzakiyatu Lillahi Addayibatus Salawatu
Lillahi, Assalamu alaika ayyuhan nabiyu warahmatul lahi wabar
katuhu. Assalamu alaina wa ala ibadillahis Salihina. Ash hadu Allah
ilaha illallahu wahdahu lasharika lahu wa ash hadu anna
Muhammadan abduu wa rasuluhu.

In kayi sallama anan ya yi, in kuma ka so zaka iya karawa da:


Ash hadu annal lazi ja’a bihi Muhammadu hakkun, wa annal
jannata hakkun wa annan nara hakkun wa annas sirada hakkun wa
annas sa’ata ah tiyatun la raiba fiha wa annallaha yab’asu man fil
kubur. Allahumma salli ala Muhammadin wa ala a’li muhammadin
war ham muhammadan wa a’la muhammadin wa ba’rik ala
muhammadin wa ala a’li muhammadin kama sallaita wa rahimta wa
barakta ala Ibrahima wa ala a’li Ibrahima fil a’lamina innaka
hamiidum majiid. Allahumma salli ala’ mala’ikatuka wal
mukarrabiina wa ala’ anbiya’I wal mursaliina wa ala’ ahli da’atika
ajmaiin, Allahummag firli wa liwalidayya wali a’immatina wali man
sabakana bil iimani magfiratan azman. Allahumma inni as aluka
min kulli kharin saalaka minhu Muhammadun nabiyyuka Sallal
la'hu alaihi wasallam, wa auzu bika min kulli sharrin istaa’zaka
minhu Muhammadun nabiyyuka sallahu alaihi wasallam.
Allahummag fir lana ma kaddamna ma akh kharna wama asrarna
wama a’alalna wama anta aalamu bihi minna, Rabbana a;tina
fiddunya hasana wa fil Akhirati hasana wa kina azabannar, wa
au’zu bika min fitnatil mahya wall mamati wa min fitnatil kabari wa
min fitnatil masiihid dajjali wa min aza’bin nari was u’ul masiir.
9

ABUBUWAN DA AKA KARHANTA A SALLAH


1. Addu’ah bayan kabbaran harama kafin fara karatu,
2. Addu’ah lokacin karatun fatiha ko sura’
3. Addu ‘ah acikin ruku’u
4. Addu’ah ba yan tahiyar farko,
5. Addu’ah bayan sallaman liman
6. Sujjada akan tufafi, shin fida da abinda yayi Kama da su na kayan jin
dadi, saba nin tabarma ba duk da barin sujjada akan tabarmar yafi
amma ba aki ayi sujjada akantaba, saidai sujjada akasa shi yafi.
7. Sujjada Akan nadin rawani ko gefen hannun rika ko akan riga.
8. karatu a cikin ruku’u ko sujjada ko Addu’ah da harshenda ba larafci
ba gamai ikon yi da larafci.
9. waige acikin sallah,
10.Damke ya'tsu ko mummotsasu
11.zama kan hannuwa
12.Rufe idanu
13.Dibiya kafa kan daya
14.Tunani kan harkokin duniya
15.Daukar wani abu da hannun riga ko baki
16.Wasa da gemu
17.An karhanta yin bissimilla da ta'awizi asallar farali bisa mashahurin
zance amma an ruwaito daga Imamu Malik cewa ya halatta, kamar yadda
aka ruwaito daga dan maslama cewa anso Karanta Bisimmillah. Sannan
dan Nafi’u yace wajibi ne karanta su.
Idan mai sallah yayi wani daga cikin wadannan abubuwan da aka
karhanta (makaruhai) sallar sa bata baciba.
Allah shine mafi sani.

BABIN ABUBUWAN DA AKASO KAFIN DA KUMA BAYAN


SALLAH

1. Anso ga baligi yai sallar nafila kafin sallar azuhur da bayanta, da kafin
Laasar, da bayan magariba, sannan anso yawaita nafiloli bayan
magariba, wadannan ba wajibai bane mustahabbaine.
2. haka nan kuma anso sallan walha da tarawihi.
3. Gaisuwan masallaci ( raka a’ biyu duk lokacin da mutun yashiga
masallaci)
4. anso sallan Shafaii ( Mafi karancinsa Raka a’ biyu) da rakaa’ daya
Wuturi bayan sa wannan Sunnane muakkada, “maikarfi”
10

5. haka ma anso ayi karatu cikin Shafai da Wuturi abayyane (akaranta a


rakaar farko ta shafa'i Fatiha da Sabbi, Rakaa tabiyu Fatiha da Kulya,
a kuma Wuturi Fatiha, Kulhuwalla'hu da falaki da nasi.
6. anso Sallah Raka atanil Fijir tawani ruwayan ance sunnane ( ana
karanta fatiha ne kawai acikinsu)
Allah shine mafi sani.

BABIN ABUBUWAN DA SUKE BATA SALLAH


Sallah tana baci da:
1. Dariya da ganganci ko da mantuwa
2. Da sujjadar rafkannuwa don barin ko karin Mustahabbi
3. Kara rakaa’ ko Sujjada ko abinda yayi kamada haka da gangar.
4. Ci ko sha
5. Magana da gangar saidai na gyaran sallah shima kadan don in tayi
yawa tana baci.
6. Huri da ganganci
7. Yin hadasi
8. Tuna sallar da tawuci1
9. Amai idan aka kirkireshi.
10.Karin Rakaa; Hudu a Sallah mai Rakaa’ Hudu ko Rakaa’ Uku a Sallah
mai Rakaa’ Uku ko Rakaa’ Biyu a Sallah mai Rakaa’ Biyu da
mantuwa (ninka adadin raka’an sallah)
11.Yin Sujjadan Rafkannuwa (Kabli ko Baadi) tareda liman in baasami
ko rakaa’ dayaba.2
12.Barin Sujjada kabli in anbar Sunnoni uku kuma lokaci yai tsawo.
Allah shine mafi sani.

BABIN SUJJADAN RAFKANWA


1. Ana Sujjadar Raka’ah Biyu Kafin Sallama idan aka rage Sunnah
Muakkada Sannan ana yin masu Tahiya da Sallama, in kuma karine
ana Sujjadar Bayan Sallama.
2. Idan akayi kari da ragi Alokaci daya ana Sujjada kafin Sallama
Saboda ragi na rinjayan kari.

 Rafkanwa acikin Sallah ta kasu kashi Uku (3):-


1. Rafkanwan Barin Farali ba ayi mata Sujjada in mutun yamanta da
farali dole yazo da abinda yamanta in bai tunaba har yai sallama
lokaci yakure sallan ta'baci. Sai yasake wata sallan.
11

2. Rafkanwar barin Mustahabbi kamar Al-kunuti ko fadin Rabbana


walakal Hamdu ko Kabbara daya da abinda ye kama dahaka ba a yi
masu Sujjada in kuma akayi masu Sujjada kafin sallama sallah tabaci
3. Rafkanwar Barin Sunnah kamar karatun Surah ko Kabbara biyu ko
Tahiya biyu ko zaman tahiyya ko abinda yayi kama da haka ana yi
masu sujjada ba'adi in karine, kabli in ragi ne. sannan Sujjada ba'adi
bata wucewa don mantuwa ko yaushe akatuna za abiya ko da bayan
Wata ne.
- In aka gabatar da sujjada Baadi kafin sallama ko aka jinkirta
Sujjada kabli bayan sallama sallar bata baciba bisa mashurin
zance.
- Wanda yamanta shin yayi sallah Raka'ah uku ne ko biyu ne zai
gina sallarsa bisa mafi karanci, wato shine biyu, sai yacika
sallarsa sannan yayi Sujjada bayan sallama.

BABI CIKIN LIMANCI


Yana daga cikin sharuddan limanci Liman yazama:
1. Namiji
2. Musulmi
3. Mai hankali
4. Baligi
5. Ya’san abinda sallah bata inganta saidashi na karatu da hukunci.
 Inkai koyi da Liman bayan haka sai yabayyana maka Kafiri ne ko
mace ne ko matamaza ne ko mahaukaci ne ko fasiki ne ko yaro ne
wanda bai balagaba ko yayi hadasi dagangar sannan yai maku sallar
Sallar ka ta baci, yazama dole kasake sallah,
 Anso lafiyar gabobi ga liman sannan anki limancin mai yan kakken
gaba ko shan inna ko mai yawan fitsari ko mai miki yaywa mai lafiya
limanci.
 An karhanta liman mai dandakakken gaba ko wanda ba aimashi
kaciyaba ko dandaudu ko wanda aka jahilci halinsa ko dan zina ko
bawa a sallar Farali amma in Sallar nafila ce ba aki limancin daya
gacikin wadanda ambatonsu yawuce ba.
 Limancin makaho yahalasta, hakama wanda ya saba mazahba ko
innini ko kuturu in kuturtan batai yawaba yanda zata cutar da mutane
ya halasta.
 Ya halasta ga maibin Liman ya hau wani abu wanda zai daukakashi
kan liman kamar hawar sama, amman bai halasta ga liman ya daukaka
kan masu binshiba saidai da wani abu kadan kamar tabarma ko abinda
12

ye kama da haka. In kuma liman din ko maibin liman ya nufin


daukakan girman kai sallansa tabaci.
Yana daga cikin sharuddan Maibin Liman yai niyyan koyi da Limaminsa
 Baashardantawa limanba yai niyan limanci saidai a halaye hudu
1. Sallan Jumaa’
2. Sallan Jam’i
3. Sallan tsoro.
4. Sallar mayewa
Wasu daga cikin malamai suka Kara da cewa liman yana niyya ne
saboda asami ladan falalar jama’ah saidai ansami sabani cikin wannan
Magana.
 Anso gabatarda Sarki a limanci sannan maigida. ana gabartar da mai
hayar-gida Kan maigidan. Sannan sai Wanda yafi sannin fiqhu Sannan
sai Wanda yafi sannin Hadisi Sannan sai Wanda yafi iya karatun Al-
qur’ani sannan sai mai yawan bauta sannan sai mai yawan shekaru a
musulinci sannan sai mai madaukakin dangi, Sannan sai mafi kyawun
halitta, sannan sai mafi kyawun dabi'u sannan sai mai kyan tufafi.
 Wanda yakeda hakki alimanci sai yagaza cika darajan limancin,
kamar maigida yazama mace ko bawa ko jahili anso ya wakilta
waninsa wanda yafishi.
Allah shine mafi sani.

BABIN SALLAR JUMA’AH


Sallar juma’ah Faralice akan kowane mutun, tanada sharuddan wajibci,
da rukunai, ladubbai, da kuma hanzari wadanda sukan halatta rashin
zuwa.

Sharuddan wajibcin Sallar Juma’ah bakwai (7) ne:


1. Musulunci
2. Balaga
3. Hankali
4. Mazantaka.
5. Yanci (Da)
6. Zaman Gari.
7. Lafiya.

Rukunan Sallar Juma’ah biyar (5) ne:


1. Masallacin Juma’a.
2. Mutane (Jama’a). (basuda iyaka a mazhabar malikiyya saidai suka
sance jama’ah Wanda zasu iya yin alkarya guda. Wasu daga cikin
13

malamai sun karfafa cewa Juma’ah ta halasta ga mutane goma


shabiyu (12) wadan da zasu tabbata har sallama.
3. Huduba ta farko (ita rukuni ce a bisa ingantaccen magana, da huduba
tabiyu bisa mashahurin zance. Dole Huduba ta kasance bayan
zawalin rana kafin sallah, Huduba bata da iyaka agurin malikiyya ya
zama dolene kawai tazama abinda ake cewa Huduba, sannan anso
tsarki cikin Huduba, ansami sabani ciki wajaban tsayiwa don
Huduba .
4. Liman: daga cikin suffofin sa yazama Wanda sallar juma’ah ta wajaba
akan sa ba wai matafiyi ko yaro ba ko waninsu cikin wadanda sallar
juma’ah bata wajaba akansuba.
 Anshardan ta cewa Wanda yayi Huduba shi zai bada sallah sai dai
inda hanzari Wanda zai hana shi kamar Ciwo, hauka ko abinda ye
kama da haka ya wajjaba a jira liman don hanzari wanda bazai dauki
lokaci bisa mafi ingancin zance.
5. Wajen zama. Yazama dole ayi sallar juma’ah a wajen da mutane ke da
zama gari ko kauye.

LADUBBAN JUMA’AH GUDA TAKWAS (8) NE


1. Wanka domin Juma’ah, Sunnah ce a wajen dukkan malamai, da
sharadin hada wankan da tafiya Masallaci, idan mutum yayi wanka sai
ya shagalta da cin abinci ko Barci, zai sake Wanka bisa mashahurin
zance.
2. Yin Asuwaki
3. Aske gashi Kai.
4. Yanke Kunba
5. Nisan tan abin da zai iya haifar da Iska mare dadi.(Kaman Tafarnuwa,
Albasa ko wanin su)
6. Sa Tufafi mai Kyau.
7. Sa Turare.
8. Tafiya zuwa Masallaci a kasa sai dai a kwai wani hanzari Wanda zai
sa ahau abin hawa.

HANZARI
Anyima Wanda Yasami Kansa Cikin Daya Daga Wadannan Yanayi
Rangwamin Zuwa Juma’ah:-
1. Ruwan sama mai yawa.
2. Tabo mai yawa.
3. Kuturta wacce zata cutar da mutane da warinta.
14

4. Ciwo ko Jinyar mai ciwo, kamar mata, Da, ko daya daga cikin
Mahaifa kuma ba wanda zai kula dasu kafin a dawo, Kamar yadda in
Ciwo yayi tsanani da daya daga cikin makusanta ko dan uwa shima
yakan zama hanzari, IMAMU MALIK yace : Idan ciwo yai tsanani
balaifi daya daga cikin yan’uwa ko makusanta ya kula da harkansa ko
da zai bar zuwa Juma’ah
5. In Mutun yaji tsoron Daurewa ko dukan azzalumi ko fashi.
6. Mai matsanan cin hali in yaji tsoron kar masu bashi su kamashi.
7. Makahon da bashi da Jagora.
 Ya haramta ga Wanda Juma’ah ta wjjaba a Kansa yai tafiya bayan
rana ta take, Hakanan Magana ko Na’fila ta haramta lokacin da liman
yake Huduba (hudubar farko ko takarshe) sai dai in yariga ya fara
nafilan kafin liman yashigo sai ya cikasa nafilan sa.
 Saye Da Siyarwa Ya haramta Bayan Kiran Sallah na Biyu, Sannan
kuma ana bata cinikin in yafaru.
 Anki barin aiki ranar Juma’ah
 Nafilan Liman lokacin kiran sallar Farko,
 Anki Zuwan Yarinya Budurwa Masallacin Juma’ah
 Hakanan kuma anki Tafiya Bayan fitowan Al-Fijir,
Allah Shine mafi sani.

BABIN SALLAR JANAZA


Sallar Janaza Faralin Kifaya ce (wani kan dauke ma wani) Tanada Rukunai
guda Hudu (4)
1. Niyya
2. Kabbara Hudu
3. Addu’ah tsakanin kabbarorin hudu
4. Sallama.
Ana addu’ah da abinda yasamu, sai dai Ibn Abi Zaid (acikin risala)
yafifita a karanta :-
Al-hamdu lillahil lazi amata wa ahya, wal Hamdu lillahil lazi yuhyil
mauta, lahul azmatu wal kibriya’u wal mulku wal kudratu was sana’u
wa huwa ala kulli shai in kadeer, Allahumma salli ala Muhammadin
wala a’li Muhammadin wa ba’rik ala Muhammadin wa ala a’li
Muhammadin kama Sallaita war-himta wa ba;rakta ala Ibrahima wa
ala a’li Ibrahima innaka hamidun majid, Alla’Humma innahu
Abduka wa bni Abdika wa bni Amatika Anta Khalaqtahu, wa
razaqtahu wa Anta amatta hu wa Anta Tuhyihi wa Anta Aalamu
bisirrihi wa ala’niyatihi, Ji’ina’ka Shufaa’ah lahu fa shafi’na fihi,
15

Allahumma inna nastajiruka bi habli jiwarika lahu innaka zul- wafa’I


wa zimmah, Allahumma Qihi min Fitnatil Qabari wa min Azabi
Jihannam,Allahummag-fir lahu war-hamhu waa-fu anhu wa a’fihi wa
akrim nuzulahu wa wassi’I madkhalahu wag-silhu bi ma’I wa salji wa
barad waqqihi minaz-zunubi wal khadaya kama yunaqqas-saubul
abyadu minad-danas wa abdilhu daran khairan min darihi wa ahla
khairan min ahlihi wa zaujan khairan min zaujihi, Allahumma inkana
muhsinan fazed fi ihsanihi wa inkan musi-an fataja’waz an sayyi a’tihi,
Allahumma innahu qad nazala bika wa Anta khairu manzulin bihi,
faqeerun ila rahmatika wa Anta ganiyyun an azabihi, Allahumma
sabbit indal mas-ala mandiqahu wala tabliihi fi qabarihi bima la
daqata lahu bihi wa alhiqhu bi nabiyyihi Muhammadin Sallal lahu
alaihi wa sallam, Allahumma la tah rimna ajarahu wala taftina ba
adahu,

FASSARA DA HAUSA
(Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya ke kashewa da rayawa, godiya ta tabbata
ga Allah wanda yake rayar da matattu, girma da daukaka da mulki da iko da yabo
duk sun tabbata gareshi, Shine mai iko akan kowa da komai, Ya Allah kai tsira ga
annabi Muhammadu (saw) da alayen annabi Muhammadu kayi albarka ga annabi
Muhammadu da alayen annabi Muhammadu kamar yadda kayi tsira kayi rahama
kayi albarka ga annabi Ibrahima da alayen annabi Ibrahima, Allah Kai abin
godewane kuma Kai me germane,Ya Allah mamacinnan bawankane, dan
bawankane, kuma dan baiwarkane, Kai kahalicceshi Ka azurtashi kuma Kai
kakarbi ransa kuma kaine zaka rayashi, Kafi kowa sannin abinda ya boye ko
yabayyana Munzo muna masu neman ceto gareka Ka bamu cetonsa, Ya Allah muna
kusanta da abinda yakusantaka da shi don kai mai Alkawari ne mai kuma cikawa
da Alkawane,Ya Allah Kakiyeshi daga Fitinar Kabari da azabar wutar Jihannama,
Ya Allah ka yafe mashi Kayi mashi rahama Kayi mashi ran gwami Ka kiyayeshi Ka
girmama masaukinshi Ka yalwata mashiganshi Allah Ka wankeshi da ruwa da
kankara da raba, Ka tsarkakeshi daga dukkan zunubai da kurakurai kamar yadda
ake wanke tufafi fari daga datti, Allah Kamusanya mashi gida wanda yafi nashi,
Ka musanya mashi iyalai wadanda sukafi nashi, ka musanya mashi mata wacce
tafi tashi, Ya Allah in ya kasance ma abocin ayyuka masu kyaune ka kara masa
akan ayyukansa in kuma ma abocin muna nan ayyukane Ka yafe mashi, Ya Allah
to gashi ya sauka gareka kaine fiyayyen mai ma sauki, Allah yana mabukaci zuwa
rahmanka Kai kuma Ka wadata da azabtar dashi, Ya Allah ka tserar dashi wajen
tanbaya, Allah kar Ka jarrabeshi da abinda ba zai iyaba, Ka sadashi da Annabinshi
Muhammadu (SAW) Ya Allah kar Ka haramta mana ladanshi kar Ka fitine mu
bayanshi.
16

Ka fadi haka bayan ko wace kabbara. Bayan kabbara ta hudu kace:


Allahummag-fir lihayyina wa mayyitina wa hadirina wa ga’ibina wa
sagirina wa kabirina wa zakarina wa unsana innaka taalamu
mutaqallabana wa maswana wag-fir lana wa liwa’lidina wali man
sabaqana bil iimani magfiratan azman, wa lil-muslimina wal-
muslima’ti wal-muminina wal-mumina’ti al-ahya’I minhum wal
amwati, allahumma man ahyaytahu minna fa ahyihi alal-iimani,
waman tawaffaitahu minna fatawaffahu alal-islami wa as-idna
biliqa-ika wa dayyibna lilmauti wa dayyibhulana, waj-al fihi
ra’hatana wa masiiratana.
Sannan sai kai Sallama.

FASSARA DA HAUSA
(Ya Allah kagafarta ma rayayyimmu ka jikan mamatanmu wadanda muke tare dasu
da wadanda bamu tare dasu, manyanmu da yaranmu mazanmu da matanmu, Allah
Ka san inda muka sanya gaba kasan makomanmu, Allah Ka yafe mana da iyayen
mu da wandada su ka riga mu iimani, ga fartawa mai wanke dukkan zunubai,
Allah ka ga fartawa musulmai maza da mata, mu’uminai maza da mata masu rai
da matattu. Ya Allah wanda karayashi a cikin mu Karayashi a akan imani wanda
kuma Ka dauki ranshi Ka daukeshi akan Musulunci, Ka azurtamu da saduwa
daKai, Ka da dada mutuwa garemu, ka da dada mu ga mutuwa, Ka sanya hutu da
jin dalin mu a cikinsa.)

Sannan in mamacin macece Sai kace: Al-lahumma Inna ha amatuka


sai kuma kaci gaba da lamirin mace kuma bazakace: Wa ab dil ha
Zaujan Khairan min Zaujiha ba (Ya Allah kasake maata miji wanda
yafi mijintaba) Saboda zata iya zama matan mijinta naduniya a Al-janna
don matan Al-janna an iyakance su ga mazansu ne kawai.
 In kahalar ci Sallan Janaza baka sani ba shin mamacin macece ko
namiji ne sai kace: Al-lahumma Innaha Nas matuka (ya Allah wannan
gawankace) Sai kawuce da fadan Lamirin mace.
 In kuma mamacin Yaro ne Bayan yabo ga Allah da salati ga Manzon
Allah (SAW) anso kace:-
Allahumma Innahu Abduka Wabni Abduka Anta Khalaqtahu
wa razaqtahu wa Anta amattahu wa Anta tuhyiihi, Allahumma aj-
alhu liwa’lidaihi salafan wa zukhran wa faradan wa ajran wa saqqil
bihi mawa’ziinahuma, wa aazim bihi ujurahuma, wala tahrimna wa
iyyahuma ajrahu, wala taftina wa iyyahuma ba adahu, Allahumma
alhiqhu bisali salafil-muminiin fi kafalati Ibrahima wa abdilhu
17

daran khairan min darihi wa ahlan khairan min ahlihi wa a’fihi min
fitnatil qabri, wa min azabi Jahannam.

FASSARA DA HAUSA
(Ya Allah Shi bawanka ne dan bawanka ne Kai Ka halicce shi Ka azurtashi
sannan Kai Ka matardashi Kai kuma zaka rayashi, Ya Allah Ka sanyashi (Bashi,
Asusu, Kundi, Lada) ga iyayenshi, Ka nauyaya mizaninsu dashi, ka girmama
ladansu, Allah kar ka haramtamasu ladanshi, muma kar ka haramtamana ladanshi,
kar Kafitnesu bayanshi muma kar Kafitnemu bayanshi, Ya Allah Ka sadashi da
ya’yan mu’minai cikin rainon Annabi Ibrahima, ka canza mashi gida wanda yafi
gidanshi, da iyalai wandanda suke fi nashi, Ka kiyayeshi da fitinan kabari, da
azaban Jahannama)

Zaka fadi haka bayan kowani kabbara amma bayan kabbara ta hudu
kace:- Allahummag-fir li as-lafina wa afradina wa liman sabaqana
bil’iimani, Allahumma man ahyaytahu minna fa ahyihi alal-iimani,
waman tawaffaitahu minna fa tawaffahu alal-islami, wag-fir lil-
muslimina wal-muslima’ti wal-muminiina wal-munina’ti, Al-ahya’I
minhum wal- amwa’ti.

FASSARA DA HAUSA
(Ya Allah kajikan wanda suka rigamu da wanda suka gabacemu da wanda suka
riga mu da imani. Ya Allah wanda Ka raya shi a cikin mu Ka rayashi akan iimani
wanda Ka dauki ranshi acikin mu Ka daukeshi kan muslunci, Ka ga fartama
musulmai maza da mata da mu’minai maza da mata masu rai da mutattunmu.)
Sannan sai ka sallame.
Allah Shine mafi sani.

BABIN AZUMI
Azumin Watan Ramalana ana farawa lokacin da watan Sha’aban ya cika
ko da ganin Adilai biyu ko mutane masu yawa wadanda bazai taba
yiyuwa su hadu akan karya ba, kuma ana barin azumin don cikan watan
kwana 30 ko ganin Adilai biyu ko Jama’ah masu yawa.
 Ana yin niyyar Azumin adaren farko ne badole bane ayi Niya kullum,
 Ana cika azumi har zuwa faduwar rana
 Yana daga cikin Sunna, Gaggauta Shan-ruwa da Jinkirta Sahur
 In ganin Wata ya tabbata bayan Al-Fijir Kame baki da ramuwa sun
wajaba.
18

 In mutun Yayi niyan Azumi kafin a ga wata niyar sa batayiba koda


ganin watan ya tabbata azuminsa bai yiba saidai zai kame baki sabo
da alfar man watan Azumi, ya rama azumin daga baya.
 Ba a Azumi ranar shakku don a lissafashi cikin watan Azumi amma za
a iya yi don Tadawwu’I (neman lada) ko in ya dace da randa mutun ya
sanyama kansa azumin nafila.
 Anso kamewa a farkon ranar shakku har zuwa rana ta daga in ba aji
tabbacin ganin watan ba sai a ci gaba da cin abinci.
 Azumi baya karyewa do zuwan amai sai dai in an kirkiri aman da gan
gar yazama wajibi a rama azumin.
 Mafarki ko yin kaho baya karya azumi sai dai anki yin Kaho ga mara
lafiya don tsoron ganin jiri don hakan zai iya bata Azumi.

YANA DAGA CIKIN SHARUDDAN IN GANCIN AZUMIN

1. Niyya kafin keto wan Al-fijir (A Azumin Farali ko Nafila). Niya


daya ta’isa ga duk wani Azumin daya wajjaba ayishi ajere kamar
Azumin Ramalan ,Kaffara (Kisa ko Zihari) ko Azumin da mutun ya
sama kansa, amma azuminda bai zama dole ayishi ajereba ko Azumin
keban taciyyar rana dolene ayi Niya kowani dare.
2. Yankewan Jinin Haila ko na biki, idan jinni ya tsaya kafin Al-fijir
dadan lokaci kadan Azumi ya wajjaba koda batai wankaba har saidai
Al-fijir ya fito.
 Ana sake niya in bibiyan Azumi yayanke don Ciwo, Jinin Haila, Jinin
Biki ko abinda ye kama da haka.
3. Hankali, Wanda Bashida hankali ko wanda ya suma Azuminsa bai in
gantaba awannan hali.
 Ya wajjaba ga mara hankali ya Rama azumin da yawuceshi cikin
halin Hauka koda bayan shekaru da yawane. Haka shima wanda ya
suma.
4. Barin Saduwa da mace, barin ci ko sha, wanda yayi daya daga cikin
wadannan da gangar ba tare da wani Tawili daya dogara akansaba ko
kuma rashin sani, ramako da kaffa'ra sun wajjaba akansa.1
 Kaffara shine: Cida Miskinai Sittin, Mudu ga kowani Miskini (mudu
irin na Manzon Allah (SAW) Wannan shine zabinda aka fifita in ba
hakaba Yanta Wuyayiya (Bawa ko Baiwa) Musulma in Kuma ba
hakaba Azumin Wata Biyu ajere.
 Idan wani abu ya kai Makoshi ba ta hanyan Bakiba kamar ta Hanci,
Kunne ko abinda yayi kama da haka ko da turaren wutane ramako ya
19

wajjaba kawai. Hakanan lokacin da aka hadiye yawu da za a’iya


zubardashi ramako ya wajjaba.
 In wani abu yawuce Makoshi na ruwan kuskure baki, ko aswaki haka
kuma abinda ya wuce ciki koda na ruwan allurane ko wanda yaci
abinci cikin kokonton fitowan al-fijir ramako kawai ta wajjaba.
 Babu Ramako ga abinda ya wuce makoshi na Kuda, Kura, gari,
Cimintin dauri ga mai san’antashi, Alluran da akayi tagaba ko
maganin da akashafa don ciwon ciki.
 Ya Halasta ga mai Azumi yayi aswaki da Rana ko ya kuskure baki
don kishi ko ya kai safe bai wankan Janababa.
 Mai ciki idan taji Tsoro, ta Fasa Azumi ba ciyarwa akanta, ta wata
ruwayan ance zata ciyar.
 Mai shayarwa idan ta ji tsoron halaka ga danta kuma bata sami
mairaino ba ko Dan yaki yarda da kowa ta fasa Azumi amma zata
biya.
 Tsoho mai shekaru dayawa zai ciyar idan ya sha Azumi.
 Idan mutun yayi Jinkirin Biyan Azumi har wani Azumin ya kewayo
zai bada Fidya duk sanda ya biya don Jinkiri.
 Ciyarwa acikin duk abinda ambatonsu ya wuce shine: ciyarda Mudu
Duk randa aka Rama Azumi.
 Anso ga mai Azumi ya kame Harshensa ya kuma gaggauta biyan
abinda ke Kansa na Azumi ajere.
 Anso Azumi ranar Arfa (ga Wanda baije hajiba asherakan),
 Anso azumin Kwana goma na Zul-Hajji, Al-Muharram, Rajab,
Sha’aban da kwana uku a kowani wata. (Imamu MALIK yaki asanya
azumin kwana ukun kowani wata suzama ranar sha’ uku, sha’hudu,
sha’biyar saboda ba ambaci ranakunba. Hakanan Imamu MALIK yaki
yaki Azumin kwana Shidan Shawwal do tsoron kar Jahilai su hadasu
cikin Azumin Ramalan)
 Anki dandanon gishiri ga mai azumi. Idan ya dandani gishiri ya tofar
bai wuce makoshiba ba komai akansa,
 Anki Magabatan Saduwa da mace, kamar Sumbanta, Runguma, Kallo
mai tsawo ko wasa da mace in an amincema faruwan abinda zai karya
Azumi, kamar fitar Maniyyi in kuma ba'a amincewa faruwan hakanba
abubuwanda aka fada sun Haramta. Amma idan mutun yayi maziyyi
don yin hakan zai rama Azumine kawai in kuma yayi maniiyi zai
rama yakuma yi kaffara.
 Anso tsayuwan dare cikin watan ramalan, sannan abin kwadaitarwa ne
sosai.
20

Don Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace:


Wanda ya tsaya cikin daren wantan Ramalana yana mai imani da
Allah mai neman Lada gun Allah, an gafarta masa zunubansa da suka
wuce. Anso kadai tuwa da tsayuwan dare in dai ba zai sa arufe masalla
taiba.1
Allah Shine mafi sani.

View publication stats

You might also like