Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 317

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (001)

........A matuƙar razane Iffah ta shiga girgiza Tajwar Eshaan jikinta na rawa, gaba
ɗaya ta daburce jin jikinsa ya saki ma gaba ɗaya a kanta, hannu ta kai saitin
hancinsa, ƙirjinta ya sake girgiza tamkar zuciyarta zata ɓallo daga cikinsa ta
faɗi. Cikin fita hayyaci ta cigaba da ɗan girgiza kafaɗunsa dake jikinta da faɗin,
“Karka min haka, dan ALLAH ka tashi, ka tashi ka faɗamin, ka faɗamin wanene kai,
wanene Ajmaal? Minene alaƙarka da shi? Idan ka mutu nima wlhy mutuwa zanyi... wayyo
Ummu wayyo Babiy na shiga ukuna....” kuka ta fashe da shi mai tsuma rai tana mai
ɗaura goshinta kan nasa da cigaba da ambaton “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un!
Shike nan ni Fhareedah, shike nan na kasheshi Ummu, Ummu na kashshi na shiga
ukunaaaaa!!”.
A tare Miran Jasim da Miran Arshaan dake shigowa suka ɗauki salati, yayinda
Malikat Bushirat da kalaman Iffah sukai matuƙar cakar ƙirjinta tamkar saukar mashi
juwa ke neman zubar da ita a ƙasa, cikin sauri Daneen Ammarah dake bayanta ta
riƙota itama jikinta na rawar. Jasrah dake bayansu kam tuni tayi kukan kura akan
Iffah da ruɗani ya hanata sanin shigowarsu duk da salatin da su Miran Jasim ke
faman jerawa har yanzu. A birkice ta janyo Iffah baya ta shaƙeta, faɗi take itama
sai ta kasheta, sai ta rabata da numfashinta. Ganin Jasrah na neman yin kisa da
gaske Daneen Ammarah tai saurin zaunar da Malikat Bushirat a kujera ta nufesu. Da
ƙyar ta iya ɓangare Iffah da taimakon Miran Arshaan da sai da yaga Daneen Ammarah
ta zaburo sannan shima ya zabura. Yaraf Iffah ta zube ƙasa tana jan numfashi da
ƙyar, yayinda Jasrah ke cigaba da zabura cikin kuka akan ita sai fa ta kashe Iffah.
Ƙoƙarin tanƙwarata Miran Arshaan yake yi amma sai ta sake kufce masa. A wannan
karon kam da ƙyar Daneen Ammarah ta ɓanɓare Jasrah ta hanyar sauke mata mari itama.
Ɗifff kowa ya ɗauke wuta a ɗakin sai kakarin wahalar da Iffah keyi, dai-dai
nan kuma Sayeed Aashiq Ali ya iso da likitoci, kasanwarsa uba a gare su a tsawace
ya basu umarnin duk su fice. A kaikaice Miran Jasim da Miran Arshaan suka dalla
masa harara kafin su fice, Daneen Ammarah ta taimakawa Malikat Bushirat da bata
tofa ko kanzil ba har yanzu, Miran Arshaan kuma ya kama Jasrah. Iffah kasa tashi
tayi dan da gaske ta shaƙu, dole sai da aka taimaka mata itama. Da ƙyar aka iya
ɓanɓare hannun dake cikin na Tajwar Eshaan har yanzu tana kuka kamar ranta zai
fita. Sashenta aka maidata, tare da sake zagaye sashen Shahan-shan ɗin da tsaro na
musamman. Likitansa da wasu ƙwararrun likitoci biyu dake a kansa domin ceto
rayuwarsa tuni bincikensu ya gano musu dafin macizai da guba da ya sha. Sun sami
nasarar kashe kaifin dafin macizan, sai dai sun tabbatar da gubar ta fara ma
jikinsa illa, idan kuma ba'a gaggauta yin wani abu ba zai iya rasa ransa duk da a
yanzu ma dai sai abinda ALLAH yayi.
Hankalin su Malikat Bushirat da gaba ɗaya ta gama fita a hayyacinta ya sake
tashi, dan gani suke ma Tajwar Eshaan ya rasu ne likitocin na ɓoyewa ne kawai.
Saboda duk wanda ya ga a halin da aka samesa bazai taba sakankancewa zai rayu ba.
Malikat Haseena tsohuwa mai ƙarfin hali da jarumta, duk da yanayin da nata jikin
yake bata gaza nuna ƙoƙarin ta ba.
Da taimakon Daneen Ammarah aka maida Iffah dake matsanancin kuka tamkar wadda
ta zautu sashenta, suna shiga ta riƙo kafaɗunta cikin tashin hankali tana mai
girgiza ta, “Ibnati kice min ba haka bane kar zuciyata ta buga, dan ALLAH ki faɗa
mana gaskiya miya samesa, minene ya faru?”.
Babu alamar Iffah zata kare kanta, sai ma wani irin karkarwa da jikinta ya
farayi hawaye na rige-rigen sakkowa a kumatunta. Sai ma kawai ta tafi luuu ta zube
ƙasa....

★A firgice Iffah ta farka daga barcin da likita ya sakata na dole. Dan tun
bayan shafa mata ruwa ta farfaɗo yanda take kuka da surutai sai tai kamar wadda ta
zautu. Daneen Ammarah da ke kallon al'amarin nata matsayin ruɗani ne suka saka
doctor danƙara mata allurar barci gudun kar wani abu ya samu brain ɗin ta. Saurin
riƙota tai cikin muryarta data sha kuka ta shaƙe take faɗin, “Ibnati kwantar da
hankalinki...”
“Mamy hankalina bazai taɓa kwanciya ba. Dan ALLAH a wane hali yake? Ya rasa
ransa ko? Ku kaini na sake ganinsa karki ce a'a dan ALLAH Mamy”. Duk wanda ya ga
yanda Iffah ke jero waɗan nan tambayoyi yasan har yanzu a birkice take, dan tuni
hawaye sun sake ma fuskarta kaca-kaca. Riƙota Daneen Ammarah tai ta rungume itama
tana nata hawayen...
A tsawace Jasrah data faɗo musu babu zato ta bama jami'an dake a bakin ƙofar
izinin shigowa ɗakin. Daneen Ammarah tai saurin dakatar da ita itama a ɗan zafafe.
“Jasrah!! Ki dawo cikin hankalinki, idan kin manta bara na tuna miki. Ita ɗin
Zawjata-almilk ce, ba hadimar daular ruman ba, ba ɗakin barcinta ba koda falonta
haramunne shigarsu.....”
Itama Jasrah cikin rufewar idon ta tari numfashin Daneen Ammarah “Nima idan
kin manta bara na tunatar dake Daneen Ammarah. Ada wannan abar ke amsa sunan da
kike tunanin zai bata waccan darajar da kariya, a yanzu ko sunanta ƴar ta'adda, mai
kisan kai, kisan kan ma na Shahan-shan.....”
“Kin tabbatar da ita ta aikata?”.
Ta katseta itama a fusace.. “Mikike buƙatar ji bayan wanda kunnuwanmu sukaji? Da
wanda idanunmu suka gani?”.
Rikici ne yake neman ɓarkewa a tsakaninsu, kowanne na ƙoƙarin ganin ya
tabbatar da gaskiyarsa akan Iffah. Abune da bai taɓa faruwa ba, dan akwai girmamawa
tsakaninsu musamman kasancewar shekarun Daneen Ammarah sama dana Jasrah. A yanda
suke a fusace su duka ya sake hargitsa kan Iffah da gaba ɗaya ta daina gane komai,
sai ma hajijiya da ke neman son sake zubar da ita a ƙasa tai nasarar jingina da
bango.....

★....

A ɓangaren al'ummar ƙasar ruman kam dake faman zanga-zanga jin abinda ke faruwa
hankali ya rabu gida biyu, wasu sun yarda harda shiga jimami. Wasu ko na kallon
abin ta fiskar yaudara ne kawai Tajwar Eshaan ɗin na son ƙetare ƙasar ne saboda
baya son yin murabus. Wasu kuma sun kasance ƴan babu manufa ne kawai. Ƙasa ta ɗauki
ka-ce-na-ce tako'ina har wani bayajin zancen wani, haka ma kafofin yaɗa labarai da
social media.
Duk yanda suka so jin bakin likitocin da suka dubashin hakan bai yiwu ba,
sai dai an sami hatsabibin da ya haɗa guntun bidiyon cewar Shahan-shan babu lafiya
kai babu ma alamar yana raye. Wannan video shi yay rugugin amsa kuwa cikin ƙankanin
lokaci a kowace kafar ƴaɗa labarai na ƙasar. Duk da ɗan jaridan abinda yay kuskure
ne sai wannan bidiyo ya zama tamkar alkairi, dan kuwa ya sauya labarin Tajwar
Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed daga azzalumin da bai son yayi murabus zuwa abin
tausayi da fara tunanin anya kuwa babu wani abu a ƙasa da mutane ya kamata su
sani?. Cikin ƙankanin lokaci bakin ƴan jarida da masu rajin faɗa aji suka fara
fashin baƙi akan al'amarin, daga sauran talakawan ƙasa ma kowa nata faɗin
al'barkacin bakinsa, wasu ɓangarori na mutane kuma suka fara binsa da addu'ar fatan
alkairi da samun lafiya..
★★.....

Al'amarin fa tamkar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Tabbas a yanda su Miran
Jasim sukai shiri na gaske akan Iffah bata da wata mafita ta kowanne mahanga, sun
kuma tsaya tsayin daka wajen nuna ƙarfin iko da tabbatar da Miran Jasim matsayin
magajin kujerar Tajwar Eshaan har lokacin da ALLAH zai bashi lafiya shine zai
cigaba da jan ragamar mulkin sarautar Shahan-shan. Wannan damar dake a hanunsu
sukai amfani wajen damawa aka miƙa Iffah zuwa cikin kurkukun masarauta. A gefe kuma
masarautar ta ɗauki ɗumi fiye da na sanda ake zanga-zanga kan murabus ɗin Tajwar
Eshaan. Kowa faɗin albarkacin bakinsa yake, masu goyon bayan Iffah da ganin ta
ƙarasa musu abinda suke burin gani, da masu zaginta da ganin gangancinta, da masu
yima su Malikat Haseena ALLAH ya ƙara a cewarsu sun fifita lamarin Iffah fiye da
Zawjata-almilk na baya da suka rasa ransu. Surutai dai kala-kala sai wanda kunnenka
yaso ji. Dan har zuwa dare babu alamar masarautar zata lafa sai ma fita gari da
maganar ta farayi har wasu kafafen yaɗa labarai sun fara tsegunta zancen a
kaikaice.....

★...........★

Zuwa safiya daular ruman ta gama cika tako ina da sarakuna na jihohi dan labari
ya gama karaɗe ko'ina. Dole amintaccen likitan Tajwar Eshaan da suka kwana kansa ya
tattauna da manema labarai dan kwantar da hankalin mutane bisa umarnin Malikat
Haseenat. Ya tabbatar da Tajwar Eshaan ɗin na raye, an kuma sami nasarar daƙile
dafin macizan da aka shayar da shi a cikin madarar da bincikensu ya tabbatar musu.
Sai dai zai cigaba da karɓar magani zuwa wasu ƴan kwanakin da zasu iya ji daga
garesa. Hankali ya ɗan kwanta kaɗan, nanfa aka shiga jera masa addu'oin samun
lafiya tamkar ba suke zanga-zanga yay murabus ba.
Sai dai kuma ga wasu hankalinsu ya sake tashi ne. Dan Wannan sauyi da aka
samu saɓanin abinda sukai hasashen faruwa ya matuƙar tada hankalinsu. Saboda tun da
Malikat Haseena ta bada umarnin sanar da ƴan ƙasa halin da Tajwar Eshaan ɗin ke
ciki Miran Jasim da Miran Arshaan suka kasa zaune suka kasa tsaye. Sunbi wasu
hanyoyi ta ƙarƙashin ƙasa domin daƙile fitar zancen ga al'ummar ƙasar ta ruman sai
dai hakan ya gagara, dan Malikat Haseenat ta tsaya tsayin daka tare da rufe idonta
wajen ƙin ganin komai sai ƙoƙarin wanke Shahan-shan ɗin ga talakawansa...

★★......

“Dole ne mu gaggauta sake salo muma, dan a wannan gaɓar idan har muka bar
shaiɗanin yaron nan ya tsallake to mufa bazamu tsallake ba”.
Miran Jasim ne mai maganar hankali tashe yana faman kai kawo. Cikin gamsuwa
Miran Arshaan ya amsashi da faɗin, “Kafin hakan dole ne mu fara kauda yarinyar nan.
Dan barinta itama tamkar kashe maciji ne bamu sare kansa ba. Dan na tabbata zuwa
yanzu ta dawo hankalinta kamar yanda Barbushi ya tabbatar mana abinda yay mata
bazai jima a jikinta ba. Kaga kuwa a ƙalla yanzu muna da kusan awanni takwas da
faruwar komai, na kula kuma tsohuwar can son dawo da martabar jikanta take yi kawai
ta amfani da wannan ciwon”.
“Haka ne, kaima kayi magana mai ƙyau. Amma kasheta a wannan gaɓar bazai yiwu
ba, dan in har muka aikata hakan zai ƙara tabbatar ma mutane abinda tsohuwar ke son
a duba, kuma zai sake ɗaukaka darajar jikan nata dan na kula hankulansu ya fara
dawowa kansa duk da ƙoƙarin da mukai na munana shi a zukatansu. Na rasa mi wannan
matsiyacin yaron ya taka haka? Haka shima fa ubansa ya dinga wajiga rayukanmu”.
Ƙwafa Miran Arshaan yayi mai haɗe da cije lips. Cikin takaici da nuna jin zafi
yace, “Lokaci yayi da zamuyi yaƙi na gaske wajen shafe babin duk wanda yay ƙoƙarin
cigaba da kasancewa a gaban nasarar mu. Ba Eshaan kawai ba, hatta tsohuwar can da
uwarsa lokacin kasancewar su larihi yayi”.
Wani banzan murmushi Miran Jasim ya saki yana mai kallon Miran Arshaan
ɗin, a zuciyarsa kam faɗi yake (Har da kai a cikin wannan lissafin Akhi. Dan bazan
taɓa hawa karagar mulki da wani maƙiyi shaƙiƙi ba) a zahiri kam sai ya ɗan bubbuga
kafaɗar ɗan uwan nasa murmushi kwance a fuskarsa. “Shiyyasa bazan taɓa daina
alfahari da kai ba”.
Murmushi shima Miran Arshaan ɗin yayi, a tashi zuciyar yana ayyana (Kwanaki
kawai zakai na ɗan-ɗanar mulkin da ka kwashe tsahon rayuwarka kanayi, dan bazan
taɓa bari ka wuce kwanan wata ɗaya ba. Ni kaɗai na dace da cancantar zama magajin
daular ruman) a zahiri kam kaɗa kansa yayi har da ɗan risinar da kai alamar
girmamawa yana murmushi.........

Hummmm. barkanmu da sake dawowa filin daga ƴan uwa. Barkanmu da salla kuma. Ya
ibada? ALLAH ya sa muna cikin bayin da aka ƴanta, ya yafe mana kurakuranmu. Ya biya
mana buƙatunmu na alkairi. UBANGIJI ka sadamu da rahamominka marasa yankewa. Fatan
alkairi a gareku baki ɗaya🥰😍😘🙏.

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA


09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (002)

........Murmushi ta saki mai sanyi bayan gama sauraren dogon bayanin nasu, ta ɗan
muskuta zamanta na ƙasaita cike da ƙarfin hali da sake bayyanar rauninta na tsufa
da halin rashin ƙarfin jiki da jiyyar kwana biyu ta haddasa mata. Malikat Haseenat
kenan tare da manyan masu faɗa ajin masarauta da suka buƙaci zama da ita akan
lamarin Iffah da suke buƙatar shiga kotu domin yanke mata hukunci dai-dai da abinda
ta aikata bisa tunzurawar Miran Arshaan da Miran Jasim. Cikin dattakonta da ƙasaita
ta sake jan numfashi a karo na biyu idanunta akan su Miran Jasim, sai kuma ta ɗan
kaudasu tana jinjina kai.
“Bazan hana ko dakatarwa ba akan gurfanar da mai laifi irin Zawjata-almilk.
Sai dai a nawa adalcin ina bada ƙwarin gwiwa da shawara ga masu zaman shari'ar bin
komai a sannu da yin ƙwaƙwƙwaran bincike. Sashen Shahan-shan dai zagaye yake da
ƙyamarori, hakama madarar da aka tabbatar ya sha tana buƙatar musan daga ina ta
fito, shi kansa dafin data zuba waya samar mata da shi har ya shigo cikin
masarautar nan?. Abu na ƙarshe shine bata tsaro na musamman da saka idanu a dukkan
abinda zata ci. Dan in har wani abu ya sami yarinyar nan batare da gaskiya ta fito
ba a tabbata hukunci zai koma hannuna, kuma zan iya zartar da shi akan kowa. Idan
nace kowa ina nufin kowa ma koda nice a karan kaina”.
Babu wanda ya iya tari a falon sai jinjina kawuna kawai suke. Yayinda
Malikat Haseenat bata sake tofa komai ba sai ma ƙoƙarin barin falon da tai ta
hanyar gara wheelchair ɗinta da remote ɗin jikinta (nace kaga ƴan gatan duniya
lols😉). Da kallo suma kawai suka bita babu alamar wani zai ce har lokacin. Sai dai
zukatan wasu tamkar zasu kama da wuta dan baƙin cikinta, ji suke kamar subi dare
wajen mata yankan rago su zubar da jinin banza. Wasu ko gamsuwa sukai da bayanin
nata, dan dama sunbi wannan ayarin ne kawai saboda rashin ƙarfin cewarsu, amma da
za'a basu zaɓi sunfi buƙatar ayi haƙuri ma har Shahan-shan ya ƙarasa samun lafiyar
da kowa ke fata.....

★★★.....

Kusan a tare suka iso falon kowa ransa a dagule. Sai faman huci suke kamar
wasu zakuna. Tamkar basuga juna ba suka fara kaikawo kamar masu safa da marwa.
Sunyi haka ya kai sau hur-huɗu kafin Miran Arshaan ya dakata cikin ƙunar zuciya ya
furta, “A wannan gaɓar maciji muka kashe bamu sare kansa ba. Kauda wannan yaron a
bayan rayuwar wannan tsohuwar sunansa BAYA DA ƘURA....”
“...Idan har barin wadda rayuwa ta zame mata saura ƙiris a zahirance zai
amsa suna baya da ƙura to cigaba da numfashin waccan yarinyar sunansa BAYA DA
TARNAƘI”. Miran Jasim ya katsesa a zafafe shima. Tsaye sukai sunama juna kallon
kallo. Kafin Miran Arshaan ya katse shirun ta hanyar faɗin, “Tsuntsayen biyu jifa
iri ɗaya suke buƙata. Inba haka ba a cikin ƙarfin iko za'a tabbatar da ƙarfafa mai
rauni”.
“Na tabbatar da hakan ta hanyar gani da ido, kunnena kuma sun jiye min
tabbacin AKWAI WATA A ƘASA bayan tatsuniyar gizo da ƙoƙi”.
“Miye mafita?!”.
Cewar Miran Arshaan cikin tarar numfashin Miran Jasim. Miran Jasim ɗin ya kafesa
da idanu yana sakin wani murmushi. “A wannan gaɓar jifar tsuntsu huɗu da dutsi ɗaya
ne ba biyu ba”.
Jimmm Miran Arshaan yay yana kallonsa, dan a saninsa da hasashensa tsuntsayen
da ya kamata su jefa uku ne kawai ba huɗun ba. Sai dai kafin yace komai Miran Jasim
ɗin ya katsesa da sake faɗin, “Tabbas huɗu ne, sai dai zamu fara kauda ukun kafin
cikon na huɗun, dan haka dole ne a gobe mu ziyarci Barbushi”.
Miran Arshaan zai yi magana sai kuma ya haɗiye, batare da ya ƙara tofa komai
ba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Asuba ta gari”.
Da wani mugun kallo Miran Jasim ya bisa, yayinda shima Miran Arshaan ɗin ya
fice yana taunar lips tabbacin da nasa ƙudirin shima.

(Nace “Hummm”).

★★.....

Yau kwanakinta uku cif a cikin ɗakin da aka garkameta mai tsananin duhu da bata
iya banbance dare da rana, sai ɗan hasken da kan leko ta window dake can sama
karami na hasken rana ko wutar lantarki. Ta matuƙar zama wujiga-wujiga da fita a
hayyacinta dalilin ƙin cin abincin da ake kawo mata sau ɗaya a kowane yini, sai
madara. Tun a ranar farko ta gama fahimtar akwai babban ƙuli da ya kamata ta fara
fahimta kafin zuwan wannan lokacin. Zuwa yanzu ta gama fahimtar su Miran Jasim
sunyi amfani da ita ne, sunyi amfani da ita duk da itama da wannan ƙudirin a ranta.
Sai dai kuma cika baki ne kawai, ta fahimci a hakanne a randa ƙaddarar dake tafiya
da rayuwarta ta yanzu ta tabbata. Dole ta kira hakan da ƙaddara, dan inba ƙaddara
ba babu ta yanda zata iya cutar da waninta mai bautar ALLAH da hanunta. Ƙwarai da
gaske tanajin zafi, matuƙar zafi na rasa ƴan uwanta guda biyu a dalilin auren
Shahan-shan. Hakan kuma shine ya zama sanadin komai na jin kangarewar zuciya da
ƙudirin da babu tabbacin iya aiwatar da shi. Komai ya nema canja mata a lokacin da
tai tozali da fuskarsa, bata san dalili ba ta dingajin kamar shi bazai iya
kasancewa mai cutarwa ba, ta dinga jin dole akwai abinda yake ɓoye da ya kamata ta
sani, sai dai a lokacin data gama shirinta tsaf akan hakan ƙaddara ta sake sauyata,
komai ya nema rushewa a zuciyarta batare da riƙe wata makama mai ƙwaƙwarar hujja ba
ta yanke hukunci ga wanda bata da wata hujja ko shaida akansa, wanda maimakon ya
bada umarnin ɗaukar mataki a kanta ya nuna mata hanyar kuɓuta ta hanyar bata
umarnin zubar da madarar da bata san yanda akai takaita gareshi ba. Amma kash, da
alama ƙoƙarinsa na kubtar da ita bai tabbata ba. Dan gashi maƙiyansu da alamu suka
nuna shirinsu bana yau bane sun gama cin nasara, nasara biyu a lokaci ɗaya,
kaudashi da kaudata itama batare da ta san mi taci burin son sani ba. Sai ma sake
tsunduma a duhuwa tayi. Dole ta kira gaɓar da suna duhuwa, dan tanada tambayoyi
masu ɗunbin yawa akan kanta ma. Mafi girma a ciki sune taya Ajmaal ya zama Shahan-
shan? Wake halaka matansa idan har ya kasance ba shi bane? Miyasa bai iya cewa
komai bayan shine keda hakkin cewar? Da gaske ta rasa iyayensu suma da ɗan uwanta
tilo daya rage kokuwa duk cikin shirin su Miran Arshaan ne?.... Shi kansa Sir
Fawzan tana da bukatar sanin wani abu a kansa. Sai dai ta yaya? Ta wace hanya? Duk
yanzu bata sani ba. Zafafan hawayen da a kwana ukun nan bata taɓa gwada sharewa ba
suka sake zubowa masu zafi. Ta lumshe raunanan idanunta murmushi mai ciwo na suɓuce
mata. Fuskarsa take kallo a kan allon zuciyarta a lokacin da yake sakar mata
murmushin da har abada bazai taɓa zama mai gogewa ba a tarihinta. Siririyar dariya
da tafin dake shiga kunnenta a bazata ya saka ɓacewar murmushin kan fuskar tata da
buɗe lumsassun idanun nata lokaci guda..
Kanta ne ya sara da ƙarfi, da sauri ta maida su ta rumtse sakamakon hasken
daya ratsasu mai kaifi, yau kwananta uku tana a cikin duhu, dolene karfin idanunta
ya samu rauni a lokacin da aka samar da haske cikinsu. Duk yanda taso sake buɗewa
ta kasa, dan har cikin kwakwalwarta taji shigar kaifin hasken na bazata. Ta cije
lips a hankali tana mai ƙoƙarin ganin ta riƙe hawayenta da son danne tasirin
raɗaɗin dariyar izgilancin da bata san daga wanda take fita ba. Sai dai zuciyarta
na bata Miran Jasim ko Miran Arshaan ne. Bata da ƙarfin tashi daga kwancen da take,
dan haka tai jarumtar sake buɗe idanun nata sannu a hankali a karo na biyu,
zuciyarta na ambaton (Hasbinallahu wani'imal wakil). Da ƙyar ta iya tsaidasu akan
Miran Jasim dake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya bisa kujerar da basai tayi wani tunani ba
da ita aka shigo masa. Raɗaɗi idanun ke mata, gasu a kumbure jajur amma haka tai
jarumtar cigaba da tsaidasu a kansa harya gaji dan kansa daga dariyar yay shiru..
_“Zawgatu al-ibn! (Daughter in-law) proud of you. Kin zama ta daban a cikin
dubun da bazan so na manta ba. Duk da nima dai nasan ban cancanci ki manta ni ba ta
sauƙi, na san na cancanci zama abin alfaharinki a yanzu. Cikin sauƙi na cika miki
burinki, gaskiya na cancanci karɓar tukuyci na musamman. Koda yake kwantar da
hankalinki bama sai kin bani komai ba, zamanki anan ma babban tukuyci ne. Zan sake
faɗa “Ina al'fahari da ke”. Yay wata ƴar dariya mai ƙona zuciya dake shiga har
ƙarƙashin zuciyar Iffah, amma kasancewar ta jarumar gaske mai ƙarfin zuciya sai
batako motsa ba, raunanan idanunta kuma har lokacin suna a kansa duk da raɗaɗin
azabar shigar haske dake ratsasu har yanzu. Dan kansa ya tsagaita da dariyar tare
da gyara zamansa yana binta da wani shegen kallon ƙurulla har yana lasar lips ɗinsa
kaɗan.
“Bana son ki kalleni da irin kallon da nake da yaƙinin shine a allon
zuciyarki Zawgatu al-ibn!. Ina son ki dai fahimci ni ɗin mutum ne mai son kansa,
zan kuma iya kauda koda yatsan hannuna ne in har zai iya zame min cikas domin samun
cikar burina”. Yay wata ƴar dariya a zahiri, a can ƙasan ransa kam kallon da Iffahr
ke masa ko ƙiftawa babu yay masa tsaye a kan allon zuciya, amma kasancewar sa gwani
sai ya shanye babu alamun hakan a kan fuskarsa. Sai ma miƙewa yay cike da kasaita,
a gabanta yaje ya tsugunna tare da kai hannunsa fari sol zai shafa fuskarta. Cikin
wata irin zabura da ƙarfin da Iffah bata san yay ragowa a jikinta ba taja da baya
tana watsa masa wani mummunan kallo har hucinta na bayyana akan hancinta. Murmushin
gefen baki yay da lumshe idanu, sai kuma ya janye hannun nasa cikin ɗage kafaɗa da
son basarwa. Idanun ya sake lumshewa da buɗewa a kanta yana shu'umin murmushin dake
sukar zuciyar Iffah matuƙa. “Hakan ma ya burgeni Zawgatu al-ibn”.
Harara ta watsa masa kai kace idanun zasu faɗo, cikin kaushin muryar da ke
fita da ƙyar ta fara magana a karo na farko cike da gargaɗi. “Kai fagalalle ka
rubuta ka ajiye, a duk ranar da koda ɗan yatsan ka yay kuskuran taɓa jikina ni
Fhareedah bint Zayyan na maka alƙawarin karyasa, karaya irin wadda har kabar duniya
tabonta bazai goge a idanunka da zuciyarka ba. Iffah babban goro ce sai magogin
ƙarfe”.
Tabbas maganarta ta matuƙar sukarsa, ta kuma zauna daram bisa zuciyarsa
tamkar rubutu akan dutse, amma a zahiri sai ya murmusa harda lasar lips a karo na
biyu. “Immm bazance kinyi ƙarya ba kam, nima shaida ne ke ɗin babban goro ce, kuma
tabbas sai ni magogin ƙarfe. Ina miki albishir daga yau ki fara takaba da irga
kwanakin zamowarki babban goro ta magogin ƙarfe ni Shahan-shan na ƙasar ruman
Tajwar Jasim ibn Abdul-majeed Aliy! Nayi alkawarin sai na maidake karuwar da zata
zama a ƙololuwar abin kwatance a duniya duka bama ƙasar ruman kawai ba. Daga yanzu
kisa a ranki ƙaddararki ta fara a hannuna hhhh!!!”.
“hhahhaha!!!”.
Itama Iffah ta fara dariyar kamar yanda yake yi, sai dai tata cike da ƙarfin
haline kawai. Tsagaitawa yayi da tasa yana kallonta cike da mamakin da yake ƙoƙarin
dannewa, sai dai kuma fuskarsa na ƙoƙarin fallasa shi. Ganin bata da alamar
tsagaita dariyar tata ya miƙe cikin zafin rai....
“Alfahari da ƙaddara akan Fareedah rauni ne ai Aam! Dan ƙaddarar itace hasken
fitilar nasarar Iffah. Ƙyaƙyƙyawan mafarki Uncle”. Ta ƙare maganar da cigaba da
dariyar da tafi ta farko saka ƙuna a zuciya.
Miran Jasim dake tsaye cak shi bai fitaba shi bai dawo ba yay wani irin cizar
lips, sai kuma ya fice cikin zafin nama dan har ƙarƙashin ruhinsa dariyar Iffah ke
shigarsa.. Sai da ta daina jin takun sawunsa gaba ɗaya da kulleta da aka sakeyi
sannan ta tsagaita itama, a maimakon dariyar sai ta fashe da kuka mai tsuma zuciya.
Ta tabbatar duk abinda Miran Jasim ya faɗa zai aikata mafiyinsa, sai dai ba tana
kuka bane akan kanta, tana kuka ne a maimakon talakawan ƙasarta da Tajwar Eshaan
bin Haysam Abdul-majeed. Tana kuka ne akan tsananin buƙatar son sanin zahirinsa da
baɗininsa da su Miran Jasim suka zaburar da ita. Sai dai tasan guri ya ƙure, ƙurewa
irin ta numfashi da ƙarewar rayuwa. Koda ace shi ya rayu ita bazata rayu ba, koda
ace wasun sa na buƙatar ta rayu ita bata buƙatar rayuwar a halin yanzu.........✍️

(ALLAH sarki Iffah 😭🙏).

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN


MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (03)

......Kamar yanada Malikat Haseenat ta faɗa an sake tsaurara tsaro a ɗakin da Iffah
take, bana dakaru kawai ba harda tarin jami'an tsaron da Shahan-shan kawai suke
bama tsaro tako ina yayinda ta kasance cikin masu iya bibiyar komai kai tsaye. Shi
kansa abincin da ake kai mata a yanzu ya kasance na musamman dake samun saka ido,
dan a rana ta biyar da yunwa ta nema mata illa sai dai likita ya shiga ya dubata.
Dan dole ta koma cin abincin sai dai bata wuce lauma uku ko kurɓa uku na madara
take ta ajiyewa..

....A ɓangaren masu faɗa ajin masarauta ana ta cigaba da tattara bayanan da suka
kamata ta hanyar bincike. Sai dai tsaiko na farko da aka fara samu shine rasa cctv
footage na sashen Tajwar Eshaan da ga asubahin randa al'amarin zai faru har zuwa
lokacin isar su Daneen Ammarah da su Miran Jasim sashen. Sai wayar Iffah da itama
aka nema ƙasa da sama aka rasa da lap-top ɗinta. Wannan al'amari ma ya kawo ka-ce-
na-ce bana wasa ba har takai jami'an tsaro cafke mai kula da ɗakin tsaron aka
garƙame. Amma kuma juyin duniya yace bai san yanda akai ba. Hakama hadiman sashen
Iffah kaf ɗinsu an tattare, suma kuma sun rantse sun kuma basu san yanda akai wayar
Iffah da lap-top ɗin sukai ɓatan dabo ba. Ba kuma suga wani ya shigo sashen ba.
Waɗan nan abubuwa na rashin makamar tabbatar da Iffah akan laifin da kowa keda
yaƙinin ta aikata ya kawo rabuwar kai da rikici babban akan mata hukunci. Yayinda
su Miran Jasim suka sha jinin jikinsu, dan haka suka zama ɓangaren masu nuna kawai
a kashe Iffahn. Ɗayan sashen kuma da suka haɗa da zuri'ar Sayeed Khairul-Bashar
suka bore akan bincike na har sai an tabbatar a kuma ji dalilinta dan in ma har ta
aikata to dole akwai saka hannun wasu a masarautar.

Rikici ne bana wasa ba, dan har takai anyi wani zaman a karo na biyu amma sam
babu masalaha daga kowane ɓangare. Ɓangaren kuma dake ganin kashe Iffahn shi yafi
sauƙi sune ɓangare mafi ƙarfi dan da yawansu na jikin Tajwar Eshaan ɗin ne. Malikat
Haseenat ce kawai ke nuna a dai cigaba da bincike kar a aikata aikin dana sani.
Hakama Daneen Ammarah sam zuciyarta taƙi aminta Iffah zata aikata bisa raɗin kanta,
idan ma har ita ta aikata ɗin kenan tunda har yanzu babu wata shaida dake nuna
itace ɗin ta bashi madarar dan bayan ita suma masu dafa masa abinci da amintacen
hadiminsa duk suna a rufe. Ƙulle-ƙullen su Miran Arshaan ne yasa dukan zargin yafi
ƙarfi akan Iffah. A yanzu haka kuma sunyi kane-kane wajen sake rura al'amarin da
nuna ɗaukar zafi fiye da kowa musamman Miran Jasim daya kasance mai riƙe da
masarautar har zuwa samun lafiyar Tajwar Eshaan da ake fata...

★★.... ★.....

Har cikar kwanakin mako babu wani cikakken masalaha akan al'amarin, sai ma
ɗaukar zafi da kowane ɓangare suka sake yi. Iffah kuma taƙi taɓuwa bisa jajircewar
Malikat Haseenat na sai fa anyi bincike. Wannan kafiya ta saka Miran Jasim da Miran
Arshaan kasa zaune da tsaye. Barbushi kuma ya tabbatar musu in har fa Malikat
Haseenat na numfashi bazasu taɓa samun yanda suke so cikin sauƙi ba. Dan haka ya
basu zaɓi biyu. Kodai su gaggauta kasheta da hanunsu, ko kuma suyi ƙoƙarin tunzura
Malikat Bushirat dayin amfani da ita kamar yanda sukayi da Iffah ta kawar musu da
ita. Hankalinsu ya tashi, dan kashe Malikat Haseenat abu ne ba ƙarami ba musamman a
wannan gaɓar da take taka wata rawa mai banbanci da tasu duk da tafisu kusanci da
Tajwar Eshaan. Duk yanda suka tattauna da aunawa sun gafa wannan hanyar mai wahala
ce a gare su, dan haka suka zaɓi nufar sashen Malikat Bushirat ɗin domin fuskantar
ta kai tsaye. Fatansu zaman ya zame musu jifan tsuntsu biyu da dutsi ɗaya, dan
tunda aka fara rikicin nan Malikat Bushirat taƙi tofa komai ma, ta tattare
hankalinta kacokan akan ganin lafiyar Tajwar Eshaan da aka hana kowa gani a
masarautar sai ita da Malikat Haseenat har zuwa yau da ake cika kwanaki tara da
faruwar komai.......

★... MALIKAT BUSHIRAT ★...

Yanda take magana cikin fitar ɗacin sauti tana kaikawo a fusace zai tabbatar maka
ranta a ɓace yake ƙololuwa. Malikat Bushirat kenan da tun faruwar al'amarin nan
babu wanda zaice yaji bakinta duk wannan sa toka sa ƙatsin da akeyi. A yanzu babban
burinta bai wuce samun lafiyar tilon ɗan nata ba, batun hukunta wadda ta zama
sanadin komai wato Iffah kuwa duk faɗi tashin da ake komai tana sane, sai dai bata
shirya saka baki ba a yanzu acewarta akwai lokaci. A tsahon kwanakin nan dukkan
wani motsin masarautar ruman a cikin kunenta yake fiye da masu kai kawon. Hauhawa
da bunƙasar ɓacin ranta na yanzu kam yana da alaƙa ne da tattaunawar ta da su Miran
Jasim, zaman nasu kuma kacokan ya alaƙantu ne ga hana hukunta Iffah da Malikat
Haseenat tayi kai tsaye har sai anyi binciken da ta sharɗanta.

Irin wannan fusatar ga Malikat Bushirat shine fatansu, dan haka suka dubi juna
cikin son danne murmushin kan fuskokinsu. Zama suka gyara tare da sake buɗe sabon
shafin abinda suka faro. Miran Arshaan ya sake marairaice fuska mai cike da
tsantsar damuwa yana mai duban Malikat Bushirat..

“... Ni a ganina ɓacin rai ko damuwa bashi ne zai zame mana mafita ba. Mu zauna
mu tattauna yanda abinda ya dace kafin lokaci ya ƙure. Ban san miyasa Mammah ta
ɗauka al'amarin nan da rashin muhimmanci ba. A yanda nake ji a zuciyata da tuni
labarin wata akeyi ba yarinyar nan ba. Dan banga dalilin da zaisa ace wai sai anyi
bincike za'ai mata hukunci bayan komai data aikata a bayyane yake, wannan tamkar
muna nuna rashin muhimmancin ran yaronmu ne ma ai.....”

“Gaskiya kam Arshaan Akhi”. Miran Jasim ya tari numfashinsa da sauri, cikin nuna
ɓacin rai shima ya cigaba da faɗin, “Ni kaina komai na kasa fahimta musamman akan
ra'ayin Mammah. Sai nake ganin bata damu bane? Ko kuwa tafi son yarinyar sama da
gudan jininta? Inba hakaba minene na waɗan nan sharaɗin marasa tushe? Bayan komai a
bayyane yake. To gashi tace sai anyi bincike, amma dai-dai da cctv footage an nema
an rasa tabbacin komai shiri ne. Inada yaƙinin komai sai dai yarinyar nan ta shirya
kafin ta shigo masarautar nan. Dan binciken mu ya nuna ta aurensa ne dama domin
ɗaukar fansar ƴan uwanta guda biyu, shiyyasa ta kwantar da kai ta shiga jikinsu
musamman Mammah da Akia Ammarah da a yanzu suke nuna goyon bayansu kan cigaba da
rayuwarta sai kace sun manta matsayin wanda taso halakawa a gare su...”

Maganganunsu sake hargitsa Malikat Bushirat suke da tunzurata. Tuni jin zafin
Malikat Haseenat da tsanar Daneen Ammarah ya sake bunƙasa a ranta. Dama kullum
Jasrah cikin munana Daneen Ammarah ɗin take a wajenta yanzu bisa huɗubar Miran
Arshaan, dan tafi kawo mata zancen duk motsinsu a masarautar fiye da kowa, musamman
daya kasance ra'ayinsu ya babanta da nasu akan hukunta Iffah. Yanda take sake
kumbura jira suke kawai suji tace wani abu, amma kasancewar ta mace mai bahagon
hali dama fahimta ko uffan da suke so bata tofa ba, sai cika take dai tana
batsewarta ita ɗaya. Duk yanda suka cigaba da fanfatan kuma batace ɗin ba har
lokacin samun damar ganin Tajwar Eshaan yay a gareta, dan tunda abin ya faru suma
ɗin basu samu ganinsa ba kasancewar akwai doka mai haɗe da babban tsaro akan ganin
nasa ga duk wanda ya kwana ya tashi a daular ta ruman, su kansu bisa tsayawar
Malikat Bushirat ɗinne da itama sau ɗaya take da hurumin ganinsa a rana zasu ganshi
yau ɗin.

Duk wani motsi da shiga da fitar jama'a a ƙarƙashin saka idon masu tsaron
sashen yake a yanzun. Tako ina ka waiga cctv camaras ne. Su kansu ma'aikatan cikin
sanya ido suke a kowane motsin tsakaninsu dan a yanzu kowa bai yarda da kowa ba
ake. Sun sami tarba daga ƙwararren likitansa daya kasa ya tsare, yana hakane kuma
bisa umarnin Malikat Bushirat ɗin. Cikin girmamawa ya gaidasu, batare da damuwa da
yanda suka amsa masa cike da isa da ƙasaita ba ya jagorancesu zuwa ɗakin da aka
warewa Tajwar Eshaan ɗin domin jiyya. Ɗakine tamkar asibiti, dan komai zaka samesa
na aiki ingantattu da kowace ƙasa zata iya alfahari da shi. Dan ƙasar ruman na ɗaya
daga cikin ƙasashe masu ƙwararrun likitoci da duniya ke alfahari da su tako wane
fanni. Hakan yasa hatta shi kansa Shahan-shan dan yana ciwo bai ƙetare ƙasar
haihuwarsa, kai sai ma dai su azo tasu ƙasar neman lafiyar saboda ingancin su....
Zaune yake a gadon marasa lafiyar bayansa jingine da tausasan filo da jikin
gado da aka ɗago, duk da ya ɗanyi rama ƙyawun haibarsa da kwarjini na manne da
cikar kamalar fuskarsa. Yayi fayau da shi da ƙara hasken daya bayyana bakin
kwantacciyar sumar kansa data kumatunsa zuwa haɓa, light blue ɗin kayan jiyyar da
suma suka ƙara fitar hasken fatar tasa tar-tar ga mai kallo sun masa ƙyau kamar ya
saka ne domin ado. Sai manyan idanunsa da har yanzu fatarsu ke a ɗan kumbure alamar
dai yana cikin halin jinya. Duk da jin an shigo bai motsa ba idanunsa nakan lap-top
ɗin da yake sarrafawa cike da nutsuwa da ƙasaita.

Daga Miran Arshaan har Miran Jasim sukai turus alamar mamaki, dan sam zukatansu
basu ayyana musu samunsa a haka ba musamman yanda likitansa yaƙi cewa komai game da
zungurar da ƴan jarida ke masa akan son sanin halin da Tajwar Eshaan ɗin yake a
yanzu. Saboda tun washe garin da suka tattauna da ƴan jarida basu sake cewa komai
ba akan yanayin jikin nasa. Malikat Bushirat da hankalinta gaba ɗaya ke akan gudan
jinin nata ta ƙarasa garesa fuskarta ƙawace da murmushi. Sai da taja kujera ta
zauna a gefensa kaɗan ya ɗan ɗago saboda shigar ƙamshin turarenta cikin
hancinsa.....✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔. (04)

.......Kai tsaye ya sauke kumburarrun fararen idanunsa dake a ɗan shanye kanta.
“Barkan ki Ammie”. Ya faɗa a hankali fuskarsa da ɗan murmushi kaɗan tamkar an masa
dole.
“Barka My Niger”.
Ta amsashi tata fuskar na sake faɗaɗa da murmushin tsantsar kulawa da soyayyar da
take masa. Idanunsa ya lumshe ya sake buɗewa a kanta, dai-dai ta juya gasu Miran
Jasim dake tsaye tamkar gunkinan da aka ajiye domin tarihi. Shima a karon farko ya
ɗan juya nasa idanun zuwa garesu. Mara gaskiya ko'a ruwa gumi yake, haka kawai sai
kaifafan idanun nasa da rauninsu ke a bayyane sukai tasiri garesu. Da ƙyar suka iya
ƙoƙarin danne tsarguwarsu da bugun da zukatansu keyi a ƙirazansu. Kasancewarsa
mutum mai kaifin tunani da saurin karantar yanayi tuni ya karancesu tsaf, ya
risinar da idanun yana ƙoƙarin haɗiye murmushin dake neman suɓuce masa. Cike da
basar da yanayin nasu ya marabcesu da sannu da zuwa. Sun saita kansu da ƙyar wajen
amsawa fuskokinsu na ƙoƙarin bayyana damuwarsu mai ɗauke da tsantsar kulawa da
takaici.
Malikat Bushirat da gaba ɗaya hankalinta ke kan Tajwar Eshaan ba fahimtar
yanayin nasu tai ba ta sake juyowa garesu tana murmushi mai faɗi da amsa gaisuwar
ya jiki da sukai masa sai dai bai amsa ba ya basar kamar bai jiba.
“Ai jinkin nasa Alhamdullah, duk da dai doctors ɗin sunce sai sun masa aiki nan
da wasu kwanaki. A yanzu haka suna kan bashi magani dafin gubar na tattare kanta
waje guda dan ta macizan dai anci nasarar daƙileta.”
Zancen nata ya matuƙar dukansu a zuciya, sai dai ta wani gefen ya sakasu a
farin ciki. Amma sai suka danne komai wajen nuna jimami da tsantsar takaici da
damuwa. Tare da aibanta Iffah da tabbatar da sai sun saka dukan zuri'arta a nadama
Bama ita kawai ba. Babban burinsu kawai ALLAH ya basa lafiya ya koma karagar mulki.
Kalamansu sun sake tunzura fushin malikat Bushirat a bayyane, sai dai kuma batace
komai ba kamar yanda shima Tajwar Eshaan ɗin bai tanka ba, hasalima tun fara zancen
nasu ya ɗan kai dubansa ga likitansa dake a ɗakin shima, dan ƙa'idar zaman nasu a
ɗakin sai da shi. Da idanu ya masa magana. Doctor Afif ya jinjina kansa da takowa
gaban gadon ya janye ɗan tabir ɗin da aka saƙala ta samansa ya ɗaura lap-top ɗin da
yake sarrafawa. Gefe ya maida shi ya kife fuskar laptop ɗin. Daga haka ya kwantar
masa da gadon kaɗan da remote, shi kuma ya ɗan gyara kwanciyarsa ya maida idanunsa
ya lumshe. Bai sake buɗesu ba balle ya tanka duk maganganunsu, duk da kuwa yana
jinsu sarai....

★★.... ★....

“Anya kuwa matsiyacin yaron nan ba akwai abinda yake ɓoyewa ba kuwa?”.
Miran Arshaan ne ya faɗa cikin tashin hankali da kaikawo. Barowarsu daga sashen
Tajwar Eshaan kenan, Malikat Bushirat ta nufi sashenta suma suka nufi na Miran
Jasim dan akwai tazara a tsakaninsu da ita.
Miran Jasim da shima irin abinda ke ran Miran Arshaan ɗin ne a zuciyarsa ya
taune lips da masifar ƙarfi. “Akhi nima inajin hakan a raina, sai dai na kasa ɗaura
dukan motsinsa a mizanin daya dace. Kaima kasan yaron nan hatsabibin kansa ne fiye
da mahaifinsa, dole ne mu koma wajen Barbushi zuwa safiyar gobe dan muna buƙatar
ganawa ta gaggawa da shi”.
“Wannan shine dai-dai. Amma tilas tafiyarmu ta kasance tare da babban shiri,
dan muna buƙatar gusar da yarintar can itama kafin mudawo garesa”.
“Babu damuwa, dan yanda nake jina ko a yanzu akace nikam a shirye nake. Amma
asubancin ma yayi”.

Kamar yanda suka faɗa hakance ta kasance. Sai dai a daren sun gana da ɗaya daga
cikin Doctors ɗin dake kula da Tajwar Eshaan ɗin, sun kuma jima suna tattaunawa da
babu wanda yasan akan minene. Da safen suka sami damar sake shiga duba Tajwar
Eshaan bisa jagorancin Malikat Bushirat da suka sake maƙalewa, sai dai sun samu ma
yana barci. Dole sukai sallama da Malikat Bushirat ɗin dan ita a sashen take yini
ma yanzu. Duk da sun so jin abinda ke bakinta basu sami damar ba. Dan mace ce mai
zurfin cikin tsiya da zamu iya cewa Tajwar Eshaan ya gada a gareta ga
miskilanci......

★★...... ★.....

A safiyar basu sami damar barin masarautar ba zuwa ga Barbushi kamar yanda
sukaso saboda zuwan baƙi. Sarakunan ƙasar ruman gaba ɗaya ne suka sake zuwa domin
ƙara duba jikin Tajwar Eshaan. Inda wannan dubiya ta bama al'ummar ƙasar ruman
damar sanin yanayin jikin Shahan-shan ɗin. Dan Alhamdullah har fitowa yay falon da
akai musu masauki. Yayi zaman kusan mintuna talatin da su, lokacin da yake miƙewa
domin komawa kunnensa ya riski matsananciyar hayaniyar da ke ɗan tashi sama-sama
kamar daga wajen masarautar. Da farko baiyi mamaki ba, dan tunanisa har yanzu
waccan zanga-zangar ba'a dainata ba. Sai dai ya ɗan dakata daga yunƙurin barin
falon ya kai dubansa Sayeed Fayzul-haq daya jagorancin shigowar sarakunan garesa.
Cikin sauri ya matso garesa kansa a risine cike da girmamawa.
“Amincin da kariyar UBANGIJI su cigaba da gadinka ya adalin shugabanmu ko ana
bukatar wani abu ne?”.
Shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya nisa a hankali tare da ɗan lumshe
idanunsa ya sake buɗewa a kansa. A kan lips ɗinsa ya furta, “Akwai abinda ke faruwa
ne bayan wanda na sani?”.
“A sani na dai babu wani sabon abu, sai dai idan akan waccan hayaniyar ne ƴan
jarida ne ke cike da nacin son sanin yanayin jikinka kamar yanda al'ummar ƙasar
ruman ke ƙulafuci suma. Duk da kullum cikin jeren zuwa suke ƙofar masarauta dama,
amma yau ganin baƙi suke tunanin zasu sami abinda suke so shine suka taru fiye da
kullum. Shine jami'ai ke ƙoƙarin hana dukkan hanƙoramsu ta hanyar sake tsaurara
tsaro”.
“A tara taron manema labarai zanyi magana da su zuwa gobe Insha ALLAH”.
A firgice, a razane, a kuma ɗimauce Sayeed Fayzul-haq ya ɗago batare da ya
farga da abinda yay ɗin ba. Dan wata irin saukar tarnatsa kalaman Tajwar Eshaan ɗin
da suka fita a bazata sukai a cikin kunensa. Tabbas bashi kaɗai ba ga duk wanda
zaiji dolene al'amarin ya firgitar da shi, dan abune da bai taɓa faruwa ba kai
tsaye kamar haka a ƙasar ruman. Koda Shahan-shan nada buƙatar ganawa da manema
labarai sai dai ya wakilta waninsa bisa umarninsa ya tattauna da su da yawunsa.
Amma duk da Tajwar Eshaan ɗin bai fito yace shine zai tattauna da su ɗin ba a yanzu
Sayeed Fayzul-haq ya girgiza ƙwarai matuƙa.
A cikin abinda bai wuce awa guda ba wannan saƙo na Tajwar Eshaan ya shiga
karaɗe lungu da saƙo na ƙasar ruman da kewaye. Ko'ina ka leƙa zancen da ake kenan
Tajwar Eshaan zai zauna da manema labarai a safiyar gobe insha ALLAHU. Kowa burinsa
gari ya waye kawai, ba ƴan jaridar ba ba talakawan ba, hatta da manyan ƙasar ma
masu manufofi daban-daban sun shiga jerin masu jiran.

A daren shugabannin ƴan jarida na ƙasar ruman suka buƙaci zama na gaggawa, dan
dolene su tattauna abinda ya dace kasancewar akwai tambayoyi fal zukatan al'ummar
ƙasar ruman da ke son a amsa musu, kuma daga bakin Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-
majeed suke buƙatar ji duk da basu da tabbacin samu saboda abune mai matuƙar
wahalar gaske kowa ya sani......

★•••• ★•••••

Hankali a tashe suka iso ga Barbushi. Duk da tsalawar dare da na duhuwar jejin
babu alamar tsoron abin cutarwar tattare da su saboda bushewar zukata. Hasalima su
ba abinda zai basu tsoro anan bane damuwarsu. Wanda ya wuni basu tsoro da zama
cikin wasi-wasi na rashin makamar riƙewa ne matsalarsu. Boka Barbushi da ƙazanta da
dattin kafirci yay ma fuskarsa da gangar jikinsa ƙawanya ya tuntsire da wata irin
mahaukaciyar dariya da sai da ta ƙular da Miran Arshaan da Miran Jasim. Sai dai
basu nuna ba balle damar cewa wani abu. Sai da yay mai isarsa kafin ya tsagaita da
maida hankalinsa garesu. Basu da matsala akan faɗin abinda ya kawosu, dan sunyi
imanin ya san komai hatta gaibu (wa'iyazubillah 😭🙏), sakamakon idan sun zo wajensa
tun kan su faɗi abinda ya kawosun shike zayyane musu. A yanzun ma dai yana rufe
bakinsa daga dariyar tasa ya fara zayyano musu....
“Sarƙa-sarƙar sarƙaƙiya ce mai cike da mugun ƙullin dake ɗaure da kowa. Babu
mai iya gane tushen farawarta balle kamo bakin zaren ƙarshenta kasanwar anyi komai
a cikin duhun da idanun kowa bazai gani ba ko wanene shi a hatsabibanci. Ina mai
tabbatar muku shi ɗin hatsabibi ne ƙwarai da gaske. Kuma tabbas a yanzu ne aka fara
wasan hhhhhhhh!!!! Hahahahahahaha!!!!...”
Yanda mummunar daiyarsa ke amsa kuwwa a jejin haka sautin bugun zukatan Miran
Jasim da Miran Arshaan ke bada nasu sautin a ƙirazansu. Hatta yawun dake gudana da
kai kawo a bakunansu zuwa maƙoshi ya ƙame ƙaf. Hargitsatstsun idanunsu kawai suka
iya zubawa boka Barbushi da ke kwasar dariya har yanzu. Cikin ƙarfin hali da tsawa-
tsawa na fitar hayyaci Miran Jasim yay ƙoƙarin dakatar da shi a kausashe..
“Koma mi ya taka ko yake taƙama da shi mu bai damemu ba. Muna son a ƙarasa
mana rayuwarsa a wannan dare, haka itama yarinyar ta hanyar uwarsa Malikat
Bushirat, asirinta ya tonu duniya duk ta shaida itace ta kashe yarinyar kaga sai ya
gana da ƴan jaridar da hujja. A haddasa babban rikici tsakaninsu da talakawan ƙasar
nan harma da tsohuwar can da rayuwarta ta zame mana ƙadagaren bakin tulu. Mu kuma
zamuyi amfani da wannan rikicin wajen kawar da Eshaan ɗin ta hanyar aikin da
likitoci zasu masa, sai kawai ace bugun zuciya ne dalilin abinda ke faruwa..”
“Hhahahaha!!! Hhhhh!!!” Barbushi ya shiga kwasar dariyar wulaƙanci sa mai
tsananin bada amsa kuwa. “Ina son mugunta da mugu hhhhh!!. Ina son naga ana mugunta
HHhH!!. Koba komai ƴan wuta sun sami ƙaruwa hhhhh!! (Wa'iyazubillah. Ya rabbi badan
halinmu ba ka karemu daga nema a wajen waninka, ka tsaremu daga shirka da
mushirikai🙏😭).
Duk da kalamansa na ƙarshe basu ji ko gezau ba akan ƙudirinsu, duk da kuwa
sunyi imanin UBANGIJI ya halicci (WUTA DA ALJANNA) babu kokwanton zai cikasu kuma
kamar yanda ya alƙarwanta, sai dai son cikar burin duniya na ƙanƙanin lokaci ya
rufe zukatansu da idanunsu, sun jima matuƙa tare da shi sai gabanin asubahi suka
koma masarauta ta ɓarauniyar hanyar kamar yanda suka fita....

*_WASHE GARI_*

Ƙarfe goma na safe ƴan jarida da taron al'ummar ƙasar ruman sun cika ƙofar
masarautar Ruman cika mai ban mamaki kai kace Tajwar Eshaan ɗin zai fito ne ƙuru-
ƙuru su gansa kamar yanda suka jima suna bege a rayuwarsu. Dole aka baza jami'an
tsaro saboda gudun abinda zaije ya dawo.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_


ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (05)

........Tun a jiyan Doctor Afif yaso fahimtar da Tajwar Eshaan haƙuri da wannan
zama saboda jikinsa har yanzu bawai ya kasance yanda ake bukata bane ba. Hasalima
ana shirye-shiryen masa aikin da ya rage ne daga nan zuwa kwana biyu. Kallonsa
kawai Tajwar Eshaan yay har ya kammala masa bayanin cike da girmamawa kai a
rissine. Bai ce da shi komai ba tsahon lokaci, sai daga baya ya ɗan girgiza kansa
kawai iya amsar kenan. Dole doctor Afif ɗin ya haƙura gudun shiga hurumin daba nasa
ba.

Kamar yanda ya saba komansa kafin faruwar al'amarin haka ya gudanar a yau
ma duk da rashin ƙarfin jiki dana ciwon dake sukarsa kaɗan-kaɗan. Sai dai
kasancewar jarumin jarumai gwanin juriya da shanye kowane irin al'amari cike da
ƙarfin hali ya shirya cikin ƙasaitaccen shirinsa mai firgitar da duk wanda ya ɗaura
idanunsa a kansa shi ɗin wanene. Shirine da ya bayyanar da tsantsar ƙyawun da ALLAH
ya bashi da cikar kamalar mulki mai tafiya da kwarjinin kasancewar sa cikakken
mutum mai matuƙar zama barazana ga kowa. Ƙamshinsa matuƙar narka da zuciyar mai
shaƙa yake a kowane motsinsa. Ya cika ɗawusun da al'ummar ƙasar sa ke kiransa wajen
iya ado da zauna masa a jiki koma ya zarce. Dan tabbas ko'a cikin dubu baya boyuwa
da lalube ma cankosa ake kasancewarsa ɗaya ƙwallin ƙwal Shahan-shan Eshaan Ibn
Haysam Abdul-majeed da babu wani mai irin matsayinsa a ƙasar ruman da kewaye kaf.
A lokaci ɗaya gaba ɗayan masarautar ta ɗauki tsitt kasancewar fitowarsa a
zahirinsa cikin takun dake tabbatar ma ga duk wanda bai san wannan fuska a zahiri
ba shi ɗinne dai da suke cike da ƙishirwar son gani. Cikin karkarwar jiki data
zukata hadimai ke faman zubewa bisa kafafunsu zukatansu na neman wantsalowa ta
bakunansu duk da a kallo ɗaya da suke masa basa sake iya daga kai yin gigin kallo
na biyu. Baga hadiman kawai ba hatta da masu faɗa ajin masarautar ma wutar
kawunansu gaba ɗaya ta gama ɗaukewa dan al'ajabi. Domin kuwa tun fitowarsa
hadimansu ƴan leƙen asiri har ci da goshi suke wajen isar da tsegumi ga iyayen
gidan nasu kan fitowar Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed yau a zahirinsa
ga kowa babu shamaki.....

★A yanda dokin ya cika bargar da haniniya da fisge-fisge ya matuƙar tada


hankalin masu kula da su. Iya kokari yi suke na ganin sun dakatar da shi daga
ballewa saboda saninsa amma hakan ya gagara. Da yay wata irin mahaukaciyar girgiza
sai ga zaratan mazan su biyar a ƙasa wanwar. Darewa a ka dingayi duk inda ya keta a
cikin masarautar, yayinda hankalin mafi yawan hadimai ya tashi sanin babu mai iya
dakatar da shi sai mai shi......

Cak ya tsaya daga yunƙurin shiga motar da aka tanada domin zuwansa falon da
zaiyi zaman tattaunawa da yan jaridar duk da kuwa a cikin masarautar ne. Ko'a cikin
barci yaji takun waɗan nan kofatan bazai iya manta mai su ba. A zabure jami'ai Da
Gazi dake zagaye da shi suka zabura domin dakatar da ingarman farin doki da ko ga
mai kallo ya san ya wuce tara irin ta gaba-da-gaba. Amma domin kare shugabansu a
gare su tunkararsa dole ne koda tasu lafiyar bazata samu kariya ba. Ai girgiza ɗaya
yay ya zubar da kusan uku da suka tunkaresa, wasu na ƙoƙarin sake tunkararsa yay
wata irin turjiya, ya kwafuci ƙasa ya sake ƙwafuta yay girgiza mai haɗe da haniniya
sai gashi gaban Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed.
Dole kowa ya dakata wajen ya ɗauki shiru na wucin gadi duk suna kallon ikon
ALLAH. A hankali ya kai tattausan hannunsa a fuskar dokin ya shafa, haniniya ya
sakeyi da ƙwafutar ƙasa ya girgiza jikinsa. Wannan al'amari ya matuƙar ƙayatar ga
duk wanda ke wajen, duk da kuwa ba'a yau suka saba ganin irin haka ga dokin ba a
duk lokacin da ya kasance tare da Tajwar Eshaan ɗin..
Cikin muryarsa mai tausasawa da tarin nutsuwa ya kema dokin magana yana
shafasa a hankali fuskarsa da ƴar sakewa kaɗan sai dai ba murmushi ya ke ba.
Hasalima sai mai lurane zai fahimci sassaucin fuskar tasa a zahiri. Ya kwashe
tsahon mintuna huɗu da dokin, hakan ya bama duk wanda ke a wajen damar cigaba da
satar kallonsa, wanda kuma aka kaima gulma na ƙoƙarin tururuwar fitowa da leƙe a
maƙe. Cike da ƙasaitarsa ya damƙa dokin a hannun Sayeed Fayzul-haq, shi kuma ya
shige motar da ke buɗe har yanzu. Da sauri hadimin ya maida ya rufe murfin kansa a
rissine. Da ga haka motocin suka nufi inda za'ai zaman.

★Isar da saƙon shigowarsa katafaren falon ya saka duk wani mahaluki mai
numfashi yin ƙasa da kansa. Daddaɗan ƙamshinsa shine abu mafi ɗaukar hankali a
garesu da saka nutsuwar zuciya. Yayinda takun sawayensa masu tabbatar da ƙasaitarsa
ke ɗauka da sauka da bugun zukatansu. A zahiri da baɗininsu cike suke da ɗokin
kasancewa a tare da shi koda bazasuga fuskar tasa ba. Duk da kasancewar sa Shahan-
shan mafi ƙarancin shekaru a cikin duk Shahan-shan da suka gabata a daular ruman
kwarjininsa na razanar da su, dan ko makaho ya laluba zai bada amsar Tajwar Eshaan
Ibn Haysam Abdul-majeed cikin jerin jaruman maza zaratan gaske koda basu ganin
ainahin zahirinsa kuwa.
A hankali ya kai zaune saman kujerar da aka tanada dominsa cikin nutsuwarsa
da sanyin da rashin ƙarfin jiki ya haddasa masa. Kallo ya dinga binsu da shi cike
da nazarinsu kafin ya lumshe idanu da buɗewa yana jan ƙaramar iska ya fesar. Su
Miran Jasim da ke biye da shi bayan an kai musu labarin fitowarsa babu shamakin da
ke ɓoye zahirinsa suma duk zaman sukayi ransu yana ƙuna matuƙa, wasu kam ransu fari
ƙal da abinda Tajwar Eshaan ɗin yayi. Kasancewar sun tsara abin a yanda sukazo bisa
jagorancin wakilai ɗai-ɗai daga kowace jiha sai zaman ya kasance a tsare. Ko sau
ɗaya a cikinsu babu wanda ya gwada iya ɗaga kansa ɗan kwarjininsa ya gama mamayesu
tun kan su gansa, sai dai tabbatar da kammalawar zamansa ya sakasu sake gurfana
gaishesa. An amsa musu da yawun Shahan-shan batare da shi yako motsa ba daga zaman
ƙasaitar da yayi har sai da falon yay shiru.
Umarnin da aka basu na shiryawa ya saka su miƙewa musamman masu gyara
camaras da tabbatar da abin ɗaukar maganarsu ya zauna yanda ya kamata a inda aka
jerasu reras gabansa kaɗan. Kaɗan ya rage zukatan wasu su wantsalo da gasken gaske.
Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed a zahirinsa, wannan fuskar da suka jima da
mafarki da kulafucin son gani a bayyane ce a zahiri babu shamaki yau. Duk da kowa
yay masa kallo ɗaya baya sake maimaitawa a ransu ayyanawa suke dole ya dinga
kasancewa a ɓoye kam duk da cewa hakan al'adarsu ce, dan zasu iya cewa shine na
farko a tarihi cikin duk Shahan-shan da suka gabata daya bayyana fuskarsa a zahiri.
Abune da bai taɓa faruwa ba. Mafi yawancin al'ummar ƙasar ruman ƙyawawane duniya ma
ta shaida hakan, sai dai fa a yau kam sunga inda ƙyawu yake na zahiri, ƙyawu irin
wanda ko'a ƙasar ruman ɗin zasu ambacesa da ƙyawu ɗan gaske da ba'a iya ɗauke ido a
kallo ɗaya ga mai shi...
Wannan firgici ba'a iya falon kawai ya kasance ba. A duk lungu da saƙo na
ƙasar ruman ne dan tunda aka ɗora Camara ga Tajwar Eshaan komai ya koma live ga
masu kallo da saurare kamar yanda ya bada umarni..
A karan farko ya motsa pink lips ɗinsa da kyar ya fara magana a hankali.
“Inama duk wanda ya kasance anan fatan alkairi da godiyar amsa wannan gayyatar.
Tare da duk al'ummar ƙasata baki ɗaya. Kakannina, Iyayena yau ga ɗanku. Yayuna ga
ƙaninku, ƙannena ga Yayanku, ƴaƴana ga Abbun ku ba'a matsayin shugaban ku kawai ba.
Zaune nake anan da suna Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ba Shahan-shan ka ɗai ba.
Zaune nake domin baku haƙuri, zaune nake anan domin roƙonku alfarmar zama lafiya,
zaune nake anan domin baku damar bin hanyar data dace kubi dan ganin kun miƙani a
duk inda kuka aminta da a tuhumeni bisa duk laifukan da kuke kallon nayisu gareku.
Na yarda kuma na amince zan zama mai amsawa in har na aikata koda zai kasance
ƙarshen numfashina kenan. Bakuma zan zargeku ba. Kuje, kuje daga yau na baku damar
yanke hukunci, zan kasance mai jiranku. Zan kuma kasance mai biyayya ga shari'a,
zan kuma damƙa wannan mulkin ga duk wanda kuke buƙata na biku da fatan alherin ya
kasance alkairi ga ƙasar ruman baki ɗaya a bayana. Fatan alheri a gareku baki ɗaya,
da roƙon afuwar gazawata akan ku. Nagode nagode da fatan alherin da kuka min a baya
da ma wanda wasunku ke min har a yau👏”.

Tabbas da akwai camara da zata iya ɗaukar ƙasar ruman baki ɗayanta a wannan
lokaci da ansha kallon mamaki, da ansha kallon yanda komai ya tsaya cak tamkar ana
juya ƙasar da na'urar remote. Kalmomi ne da gaba ɗaya bazasu gaza ɗari da hamsin
ba, amma sun shiga al'umma fiye da zamansu guda dubu. Sunzo a wata siga da babu
wanda ya taɓa zato ko tsammanin fitarsu daga bakin da suka fita. Abu na gaba
mamakin ganin fuskar wanda ya ambatasu ga wasu mutane da ruɗani ya riska. Dole su
kira al'amarin da ruɗani kasancewar sanin wannan fuskar a fuskar da basu taɓa zato
ko tsammani ba.
Motsin gaɓɓai basu fara bayyana ba a zahiri sai da ƙyaƙyƙyawar fuskarsa ta
gushe daga allunan talabijin ɗinsu. A take amon sautika ya fara tashi a sigar
furuci daban-daban wanda ya hargitse ƙasar baki ɗaya tako ina, har zuwa dare kuma
babu alamar lafawarsa, dan tako ina sharhine ke kai kawo ga masu fashin baƙi akan
kalaman Tajwar Eshaan ɗin, ata wani gefen kuwa wasu videos masu ban mamaki suke
faman kaikawo a yanar gizo daga talakawan ƙasar game da fuskar da suka gani yau
matsayin Shahan-shan ɗinsu. Sai dai abin farin cikin kowane furuci kan fitane da
alkairansa batare da sun san shi ɗin wanene ba. Yayinda wasu kuma ke nuna irin
shock da suka tsinci kansu na ganin fuskar a matsayin Shahan-shan ɗinsu.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (06)

........Sir Fawzan na ɗaya da ga cikin waɗanda suka tsinta kansu a wannan razanin.
Hakama Azaan da Fhakir da suka kasance yaransa da duk inda ya saka ƙafa a ɓoyayyen
yanayinsa suna biye batare da sun san ainahin wanene shi ɗin ba. Ire-irensu nada
yawa da Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya mu'amulanta ta fuskoki daban-daban
na alkairinsa da bibiyar al'amarin al'ummar ƙasar tasa batare da sun sani ba sai a
yau da ya bayyana kansa a zahirinsa garesu.....

★★.....

A cikin masarauta wannan al'amari daya jagoranci motsin ƙasar a yau ya matuƙar
sakasu a rudani da firgici, dan da gasken gaske Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-
majeed ya musu duka irin na bayan ƙeya na cikin duhuwar da ko zaka tsinke wuyanka
dan waige bazaka iya hango wanda zai maka ba sai bayan yayi idan yaso. Hankula da
damar gaske sun tashi, irin tashin da sukejin ko wuta aka nuna musu zasu iya
jagorantar jefa Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin a yau.
Shi mai mulki ne, mulkin kuma shine abin baƙin cikin mafi yawansu. Su da shi
duk suna gwagwarmaya ne akan waɗanda yake mulka ne. Sai dai su ƙoƙarin wargaza
kansu suke yi masa bore domin cikar burikansu, shi kuma son dunkulesu yake domin
sauke nauyinsu da ALLAH ya daura masa duk da kasancewarsa mai shekarun da har yanzu
basu cimma arba'in ba a duniya...

Abinda zai sake birgeka ga wannan bawan ALLAH tun da ya gama fuskantar
al'ummar sa babu wanda ya sake jin wani motsinsa a wannan dare sai likitocin da ke
zagaye da shi, wanda a yau zasu masa aikin da ya rage insha ALLAHU kamar yanda ya
buƙata......

★★..... ★......
Duk jarumtarta da juriya a wannan gaɓar sai da nakasun ƙaddara ya kaita ƙasa.
Ƙarancin cin abincinta da tsantsar damuwar da suka zame mata abokan rayuwa sun mata
illa matuƙa. Ta fita a hayyacinta sosai tamkar ba Iffahr nan ba ƴar gayu mai bakin
da kadata sai wanda ya gawurta. Duk da ƙarfinta ya ƙare, rashin yaƙinin cigaba da
rayuwa bai sa ta sallama ba akan burin maida fansar ta ga su Miran Jasim. Babban
burin da take fata a yanzu koda bayan ranta shine al'ummar ƙasar ruman su kasance
masu tsananta bincike wajen sanin ainahin Tajwar Eshaan bin Haysam Abdul-majeed a
zahirinsa da baɗininsa. Duhuwar ƙaddara da bin makauniyar hanya sun haska mata wasu
muhimman abubuwa a wannan tafiyar, sai dai kash ita tata tazo ƙarshe, labarinta ya
zama tarihi a gaɓar daya kamata ace itace mai rubuta tarihin abinda ya kasance
burinta da sadakarwata.
Ta saki wani murmushi mai wahalar fassara ga wanda ya santa sakamakon
ƙamshin turaren data ɗauka tsahon mintuna tana shaƙa a dinɗaɗɗen ɗakin kurkukun da
take da yaƙinin yafi na kowa matsi da tsauri, sannan ita kaɗai ce mutum mai
numfashi a wajen sai ko dakarun da ke zagaye da ita da sunan tsaro....

(Kowanene Iffahn ta shin shino haka kuma? Ta hanyar turarensa, da alama dai
wanda ta sani ne ko take hasashe🚶).

Batai yunƙurin buɗe idanunta ba kamar yanda bata motsa ba. Ɗakin ya cigaba da
zama shiru babu alamar wanda ke tare da itan zai tanka har tsahon wasu mintuna data
fara jin gundira da kasancewar koma waye a tare da itan. Sai dai kuma da alama
akwai wani farin ciki, dake kokawa da gargaɗin ba haka bane a tattare da yaƙininta.
Kunya da tunanin idon da zata iya kallonsa in har ma shi ɗinne yasa taji bazata iya
ɗagawa ta tabbatar ba. Duk da duhun ɗakin hasken dake leƙowa ta mitsitsin windown
da wutar lantarkin waje ta hasko ya taimaka wajen ganin wanda ke zaunen. Sanye yake
da kaya baƙaƙe hatta da yatsun hanunsa a cikin safar hannu suke. Fuskarsa kam na
sakaye da norse mask daya sakaya ainahinsa, sai baƙin gilashi daya ɓoye idanunsa.
Ga mutum mai hangen nesa da ilimin saurin ɗaukar haske kan abu zai kira kowanene da
mace, dan ƙira da dirin jiki sam basuyi kama dana namiji ba duk da akwai maza masu
ƙarancin girma ta ɗa namiji. Babu alamar damuwa da rashin ɗagowar Iffahr da ta tasa
gaba ta na kallo, haka suke sake shanye adadin wasu mintunan babu alamar nuna
gundira duk da kuwa tsakkiyar dare ne da shiru ɗin masarautar zai iya tabbatar maka
da haka kai tsaye. Da alamar jiran cikar lokaci aka kai duba ga agogon dake a
tsintsiyar hannu, batare da cewa komai ba akai saurin ɗaga yatsu biyu ga wanda ke
baya tsaye da babu tantama shikam namiji ne. Cikin gyaɗa kawai ya zaro syringe dake
jikinsa mai ɗauke da ruwan allura ya nufi Iffah da har yanzu bata ɗago ba, babu ma
alamar zata ɗago ɗin. Zabura tayi da ƙoƙarin son sakin ƙara sakamakon jin saukar
ƙarfen allura ta kusa da gefen wuyanta da ke tsakani da kafaɗa. Abinda aka manne
bakinta da shi ya hana fitar ƙarar, cikin abinda kuma bai wuce mintuna uku ba sun
fice dai-dai da shaƙar wani ɓoyayyen ƙamshi daya bambanta dana farkon data fara
shaƙa data gama hasashen mai shi. Sai dai na yanzu ya sake tabbatar mata da an
yaudareta da ƙamshin ne kawai ba Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ɗin
bane......

Kammala theatre ɗin Tajwar Eshaan dai-dai da fiddo Iffah da mintuna kaɗan
baya aka farga da halin da take a ciki ta dalilin jami'an dake zagayata a kowane
dare domin tabbatar da lafiyarta bisa umarnin Malikat Haseenat. Da farko su sunma
zata ta mutu ne, ruɗewarsu da kururuwarsu taja hankalin jami'an dake zagaye da
sauran ɗakunan masu laifin dan waɗanda ke zagaye da Iffar har su huɗe duk suna zube
alamar akwai abinda aka shaƙa musu suma. Sunyi gaggawar sanar da halin da take a
ciki, cikin ƙankanin lokaci ƙwararren likitan dake a clinic ɗin masarautar ya isa
gareta, sai dai a take ya fahimci abin babban al'amari ne, dan haka shima ya
tabbatar da dubata bazai yiwu ba anan. Kai tsaye Malikat Haseenat ta bada umarni
ɗaukarta zuwa clinic ɗin.
An isa da Iffah clinic hankali tashe, yayinda likitoci suka rufu a kanta,
sai dai abin mamaki iya bincike har na kusan awanni biyar basu gano komai ba, gata
kuma a sanƙare babu inda ke motsi a jikinta sai bugun zuciyarta da na fitar
numfashi kawai. Hatta abincin da aka kai mata a daren ranar dana safiyar duk anyi
bincike kansa babu komai da aka zuba wanda zargin kowa ya karkata akai. Tofa wannan
al'amari yazo da wani sabon hargitsi da yafi na lokacin Tajwar Eshaan, dan fa a
wannan karon zukatan jama'ar masarautar ma kansu da bakunansu sun fara karkata da
wani abu daban mai nuni da (anya kuwa babu wata a ƙasa?).
Wannan kalma tayi wata irin amsa kuwa ga mafi rinjayen al'ummar cikin
masarautar da zuwa yanzu komai yaje ga kowa. Dama gasu a cikin wata ɗimuwar da
aketa faman ka-ce-na-ce da babu alamar zai ƙare anan kusa...

(🤔nifa gaskiya🥱, tom🤫 bara dai nayi shiru🤭).

★★.....

An sake wayar gari dai cikin tashin hankalin yanayin da Iffahr ke ciki wanda
hankulan mutane suka rabu biyu. Dan duk yanda ake ƙunshe maganar a iya masarauta a
washe garin sai da tai amsa kuwwa matuƙa a kafafen ƴa labarai dama na social media
fiye da tsammani. Anan ne fa kowa ya shiga ƙara tofa albarkacin bakinsa. Malikat
Haseenat tsohuwar alkairi, duk da abinda Iffah ta aikata ga jikanta ta kasance a
jerin farko na masu zuwa su dubata bisa jagorancin Daneen Ammarah. Hankalinta ya
matuƙar tashi, a take tausayin nan nata da zinariyar zuciya suka motsa ta nema
ganawa da likitocin dake tsaye akan Iffahr. Sunyi zaman tattaunawa na kusan awa
ɗaya, ƴan son suji mi zaman ya ƙunsa tuni sun baza hadimansu ƴan leƙen asiri, sai
dai kuma basu sami damar jin mi'aka tattauna ɗin ba, sai labarin zuwan ƙwararren
likitan da ake da yaƙinin yana da ilimi akan al'amarin na Iffah daga ƙetare domin
dubata tunda su likitocin na nan sun kasa fahimtar komai, dan hatta da likitoci uku
ƙwararru da suka zo daga baya suma basu iya yin komai ba a kai. Cikin ƙanƙanin
lokaci aka fara shirye-shirye zuwan doctor, abinka da masu ƙasa cikin abinda bai
gaza awanni goma sha biyar ba komai ya kammala doctor ya iso.
A wannan karon Daneen Ammarah ce tsaye kan komai, hakan sai ya bama Miran
Jasim da Miran Arshaan damar kafa wasu ƴan ƙananun magana ga su Jasrah dangin
Malikat Bushirat, acewarsu Daneen Ammarah ta nuna damuwa akan bare wadda ta shirya
halaka musu jininsu, har takai wasu ma na danganta halin da Tajwar Eshaan ɗin ke
ciki da ita har ma da Malikat Haseenat da wasu maganganun kan koma cikin kunenta
amma tai kunnen uwar shegu....

★★★.......

Ƙwararrun likitoci kuma manya ne suka rufu kan Iffah na tsahon lokaci. A
ranar dai basu cema kowa komai dan gane da al'amarin nata ba, sai dai Daneen
Ammarah nata ƙoƙarin ganin ta kwantar da hankalin Malikat Haseenat dake kiransu
akai-akai dan hankalin tsohuwar da gaske a tashe yake, tashin hankalin da kowa ya
gagara bama fassarar dalilinsa a gareta. Duk da a wannan ranar basu sami damar sake
ganinta ba hankalinsu ya ɗan kwanta da ganin jikin Tajwar Eshaan yayi ƙyau shi kuma
Alhamdullah, dan zuwa dare a bisa jagorancin likitansa doctor Afif sun sami shiga
ɗakin da yake. Duk da bai furta da baki ba alamu sun nuna yayi farin ciki da ganin
Daneen Ammarah ɗin, haka itama har da hawayenta na farin ciki ta kumayi sujudar
shukur na nuna godiyar ta ga ALLAH. Baiyi magana akan Iffah ba, itama kuma batai
masa ba duk da tanada tabbacin komai dake faruwa a masarautar yana zuwa masa
kasanwar tun a safiyar yau ɗin ya farka kuma likitoci sun tabbatar da nasarar da
aka samu kan aikin da akai masan a daren na jiya.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*


*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (07)

........Kwanaki biyu kenan ana jiran tsammanin farfaɗowarta amma shiru kake ji, tun
likitocin na iya controlling ruɗanin su Daneen Ammarah su ma har karayarsu ta fara
bayyana. Dukkan wasu salon dabaru irin nasu na ƙwararrun likitoci sunyi amma babu
wani canji tattare da Iffah duk da bincikensu na baɗini ya tabbatar musu nasara.
Zuwa dare da ke neman ƙulle adadin cikon kwanaki na uku ruɗanin likitocin ya sake
bayyana da shi kansa uban ginsamin duk da basarwar tasa a yau dai sai da ya
magantu. Dan cikin tashin hankali lokacin da Daneen Ammarah ta ziyarcesa take sanar
masa har da kukanta, saboda ita a nata tunanin ma yanzu ko bai ma san a halin da
Iffah ke ciki ba ne dai shiyyasa baiyi mata magana a kanta ba, itama kuma bata masa
ba. Shiru kamar bazai tanka ba duk da hawayen da take faman sharewa na tsikarar
zuciyarsa.
“Calm dawn Mamy”.
Ya faɗa cikin sanyinsa da ƙyar kai kacema ba daga bakinsa kalmomin uku suka fita
ba.
Daneen Ammarah da ke sharar hawaye ta shiga girgiza kanta kukan na sake ƙwace
mata, “Abni ta ina hankali zai kwanta da wannan yanayin, ina tausayin yarinyar nan
matuƙa. Ina tsoron wani ya sake samun damar cuta mata ta hanyar yahudawan nan da
bamu da tabbacin riƙe amanarmu da ke hannunsu. Tana da ƙyawawan halaye ɓoyayyu da
sai mai lura da nutsuwar fuskantar ta zai iya ganinsu a bayyane. Ita ɗin tamkar
lu'u-lu'u ce a cikin zinare, Abni bana so mu rasata a gaɓar da ta cancanci a kalla
a nuna tamkar jinjirin wata da kowa burinsa shine ganinsa. Bana son wasu suyi
amfani da wannan damar wajen salwantar mana da ita a wannan gaɓar da idanunmu ba
zasu kasance kanta na tsawon kowanne daƙiƙa ba....”
Kansa ya ɗan kauda gefe kaɗan tare da lumshe idanunsa da wani irin salon
ƙasaita irin na gawurtattun sarakunan da jinin mulki ke kaikawo a jininsu. A zahiri
kam babu alamar wani yanayi a fuskarsa da zai iya bada wata ƙofar da wani zai iya
fahimtar baɗininsa, hakama fuskarsa bata canja da ga yanda take ba. Babu alamar zai
ce kamar yanda Daneen Ammarah tafi buƙata da ga garesa har tsahon wasu mintuna da
ta gama fidda rai....
“Mamy bana son kuka”.
Ya sake faɗa a fisge a yanayin motsa pink lips ɗinsa kaɗan tare da dai-daita
buɗe lumsassun idanunsa a kanta yana mai riƙo yatsun hannunta uku na tsakkiya
kasancewar tana zaune ne a kujerar gaban gadon jiyyar tasa gab. Kai Daneen Ammarah
ta jinjina masa cike da rauni tana ƙarasa share hawayenta. Yanada abin faɗa fiye da
wanda ya faɗa a bakinsa amma furtawarce mafi girman aiki a garesa. Sai kawai ya
zaɓi ɗan yin luuu da idanunsa tamkar zai lumshe sai kuma ya buɗe tare da motsa
kumatunsa kaɗan alamar murmushi. Duk da a iyakar lips ɗinsa ya tsaya hakan bai hana
Daneen Ammarah maida masa murtani ba cike da jin ƙaunarsa matsayinsa na ɗan ɗan
uwanta mafi soyuwa a ranta kuma shugabanta.
Ƙwayoyin idanunsa ya juya ga Doctor da ke daga gefe, tazbihi kawai yake ma
UBANGIJI da girmama jini irin na masu mulki da ƙasaitar Shahan-shan ɗin na su, har
zuciyarsa na raya masa anya kuwa akwai wani sarki mai mulki da ƙasaitarsa zata iya
kamo ƙafar ta Shahan-shan ɗin nasu Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed?. Rashin
mai tayasa ya sashi haɗiye tarin gulmar dake ran nasa ya saci kallonsa ta ƙasan
ido, sai akai sa'a dai-dai saukar idon Tajwar Eshaan ɗin a kansa. Da sauri ya maida
nasa ya rissinar yana mai jin kaifi da tasirin na Shahan-shan ɗin a kansa.
“ALLAH ya ƙara lafiya da tsohon rai mai albarka ko ana buƙatar wani abu ne?”.
Ya faɗa cikin rawar harshe da kaifafan idanun Tajwar Eshaan suka haddasa masa.
Kallon nasa ya cigaba da yi har na wasu tsahon sakanni da suka kusa ƙulla mintuna
biyu kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya faɗi abinda ya ke ta juyawa a ransa tun
ɗazun.
“Zata iya kasancewa tare da mu anan?”.
Cikin gyaɗa kai da sake risinar da shi Doctor Afif yay saurin faɗin, “Idan
hakan shine buƙatar adalin sarki shugaban sarakunan ƙasar ruman da al'ummar cikinta
ya tabbata abu mafi sauƙin zartarwa a bisa umarninsa”.
Kansa kawai ya ɗauke ba tare da ya sake magana ba har doctor ya fice.
Daneen Ammarah da fuskarta ke faɗaɗa da murmushi ta buɗe baki zatai magana, sai
hakan yay dai-dai da ɗagowarsa gareta, har cikin rai yaji daɗin ganin murmushin a
fuskarta, amma bazaka taɓa gane hakan a tashi fuskarba. Ya dai ɗan sake ƙasa-ƙasa
da idanunsa masu yalwar cikar gashi da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta...
“Kinyi farin ciki?”.
“Sosai sosai kuwa sweetheart. ALLAH ya albarkaci rayuwarka, ya cigaba da tsare
min kai ga duk wani abin ƙi. Ya yalwata zuciyarka da imanin da baya yankewa da
tsoron ALLAH. ALLAH ya ƙara maka lafiya adalin shugabanmu abin alfaharin ƙasar
ruman da al'ummar cikinta....”
“Mammyy!”.
Ya faɗa da wani irin sanyi-sanyi da ke son bayyana shagwaɓarsa a fili duk da
fuskarsa ta shanye komai ta ɓoye. Karan farko Daneen Ammarah ta saki ƴar siririyar
dariya dan ganin Baby Eshaan ɗin ta na baya a zahiri. (Su baby Eshaan anji jiki😜
🏃)...

★Cikin ƙankanin lokaci aka cika umarninsa ta hanyar saka gado a ɗakin dake
jikin katafaren ɗakin jiyyar tasa da gilashi kawai ya rabasu da nashin da ya
kasance na musamman a sashe na musamman tare da dukkanin kayan aikin kula da duk
motsin mai jiyya da abinda irin tata jiyyar take buƙata. Yana zaune a irin zaman da
yafi yi a gadon jiyyar tasa ƙafafu a miƙe an rufesu da farin lallausan duvet har
zuwa ƙugunsa, bayansa jingine da filon daya zauna dai-dai yanda ake buƙatarsa da
taimakon ɗaga gadon da akai irin na mai jiyya. Duk da yanayi na mai jiyya da
fuskarsa ta nuna tana nan tar-tar da ita da hasken nan nasa mai ɗaukar ido kamar
madara, hakama kwantaccen gashin daya zagaye fuskarsa baƙi siɗik na kwance a fuskar
kai kace wani hamshaƙin gyara yake samu. Duk da kasancewarsa a asibiti mayataccen
ƙamshinsa da nasa ne shi kaɗai babu wani mahaluki mai irinsa ya gama manne ɗakin da
duk wani abu da ake sarrafawa. Alkur'ani ne a hannunsa yana karatu dan haka bai ko
motsa ba har aka kammala gyara gadon da za'a ajiye Iffah itama aka gungurota a
gado. Da taimakon likitoci biyu mata aka ɗagata daga gadon da suka turota suka
maidata a gadon da aka kafa. Sharɓan take kwance idanu a rufe, ƙyaƙyƙyawar fuskarta
ma'abociyar tsiwa da rashin barin sai ta kwana tayi wani fayau. Ta rame ga idon duk
wanda ya santa duk da bata cikin hayyacinta, damma bargon da aka lulluɓeta da shi
ya ɓoye ramar da tayi ta jiki. Har suka kammala komai suka fice bai motsa idanunsa
da ga kan Alkur'anin ba, karatunsa yake a nutse cikin zuciya da tattara dukan
hankalinsa kacokan.
Sai da ya kai inda yake buƙatar kaiwar sannan ya dakata yana mai lumshe
idanunsa da sakin jerarrun ajiyar zuciya, dan a duk sanda ya kusanci Alkur'ani ta
hanyar karantasa ya kanjisa cikin wata tarin nutsuwa da mulki ko dukiya ko wata
ɗaukakar duniya bata bama ɗan adam. Yakan shagaltu da wani sirri da mai karanta
Alkur'ani ne kawai ke iya samunsa a duniya. Sannan dukan damuwa da nauyin zuciyarsa
kan kwaranye ya dinga jinsa tamkar wani sabon mutum sabuwar haihuwa. Bayan jan
tsahon mintinan da suka sake tabbatar da gamsuwar nutsuwar da gangar jikinsa da
zuciyarsa ke buƙata ya sake sauke ajiyar zuciya da buɗe lumsassun idanun nasa inda
zuciyarsa ke fisgarsa da umarnin da bazai iya bijirewa ba. Duk da gilashin da ya
raba sun tsaf yake iya hangota kwance samɓal, illahirin jikinta da zahirinsa ke a
bayyane zagaye da na'urori kala-kala da suka kasance sirrin aikin likitoci. Idanun
ya sake lumshewa ya buɗe akan fuskarta dake fayau sai hasken data ƙara mai tsananin
ɗaukar idon mai kallo. Tabbas akwai abin faɗa a lips ɗinsa, sai dai ƙasaita da
ƙarfin jinin iko mai yawo a jijiyoyin jikinsa ya jagorancesa ga haɗiyesu kawai dan
barin kaza cikin gashinta kamar yafi alkairi ga mai kiyo.

★.... ★★.... ★.....

Tun isowar labarin abinda ya faru da Iffah a wancan daren take jin ranta
fes, sai dai zuciyarta na son sanin wanda ya aikata koma miye dan ta tabbatar
masoyinsu ne. Cikin zumuɗi tai yunƙurin kiran number ƴar uwarta domin ta sanar mata
amma ta gagara samunta. Hakan bai mata daɗi ba, amma dai bata damu sosai ba dan
tasan itama komai zaije gareta. Da wannan farin cikin ta kwana a wannan ranar har
zuwa jiya da Iffah bata dawo hayyacinta ba.

A yanzu kam cikin harzuƙa da ɓacin rai take neman Malikat Bushirat ɗin
dalilin labarin sake zuwan Daneen Ammarah sashen Tajwar Eshaan a yau, amma babu
alamar zata sameta, tana a cikin wannan ɓacin ran labarin maida Iffah sashen Tajwar
Eshaan ya sake riskarta. Cikin tashin hankali ta wancakalar da wayar tayo waje,
batare da jiran driver ba ta nufi sashen Malikat Bushirat ɗin..

Hadima Banou dake tafe a ɗan gaggauce dan cika umarnin aiken da Malikat
Haseenat tai mata tabi Jasrah da ke fitowa a mota rai ɓace da kallo. A hankali ta
lashe laɓɓanta tana mai haɗiyar yawu. Ta jima tana kawaici akan cikin nan na Jasrah
saboda shakkar Iffah, amma a yau kam ga dama ta samu. Sake haɗiye tsinkakken
yawunta tayi tana gyara tsaiwa. Gabb sukai karo da Jasrah da alamu suka nuna idonta
rufe suke da ɓacin rai, itako Hadima Banou duk da tayi ne ta biyu sai ta zube ƙasa
cikin rawar jiki tana neman afuwa da rantsuwar bata lura da tahowarta ba har da
ƙoƙarin dafa ƙafafun ta, Sake ɓaci ran Jasrah yayi, cikin rufewar idon ta ɗaga
hannu ta sauke mata lafiyayyen marin da ya saka sauran hadiman dake ɗan kai kawo
shiga razani. Maruwa dai kam Hadima Banou ta maru, dan har sai da tayi ƴar a
dunguren da duk wanda ke a wajen yaji tausayinta. Amma a gareta hakan ma nasara ce
dan ta samu abinda take so. Fuuu Jasrah ta tsallaketa ta wuce zuwa cikin sashen
Malikat Bushirat rai a ɓacin, sai dai cikin girmamawa hadiman ƴar uwar tata suka
sanar mata saƙon data bari na bata buƙatar ganin kowa. Watsa musu mummunan kallo
tai taja tsaki da shigewarta.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (08)

........Fitowarta kenan da ga toilet da alamun wanka tayo dai-dai da shigowar


Jasrah ɗakin. Malikat Bushirat ta zuba mata ƙyawawan idanunta kawai cike da mamakin
ganin yanda ta ingizo ƙofar gashi ko sallama batai ba. Jasrah da gaba ɗaya idonta
ke lulluɓe da tsantsar ɓacin rai ga dunƙulewa da ɗan cikinta yay waje guda ya ƙulle
mata mara ta zube a kan gado yarab. Malikat Bushirat da har lokacin ke binta da
kallo ta ƙaraso gareta da sassarfa tana ambaton sunanta. Bata iya ta amsa mata ba
har ta ɗagota jikinta.
“Jasrah! Are you ok?”.
Ina Jasrah bata iya ta amsata ba saboda yanda mararta ta ƙulle tamau. Hankalin
Malikat Bushirat yay ƙololuwar tashi ganin tana jan numfashi da ƙyar. Dole ta
shimfiɗeta tai amfani da telephone wajen kiran clinic. Cikin ƙanƙanin lokaci
doctor... ta iso, kamar an saita tana shigowa jini na ɓallema Jasrah..

★★

Wannan hali da Jasrah ta tsinci kanta a ciki ya ɗauke hankalin Malikat


Bushirat da ga sanin halin da ake ciki akan komawar Iffah sashen Tajwar Eshaan ɗin.
Dan kamar wasa jini ya ɓalle mata har sai da cikin jikinta da sukai matuƙar
ƙwallafawa rai ita da mijinta (Miran Arshaan) gaba ɗaya ya fita har itama ana neman
rasata dan itama hadima Banou ɗin taso taɓata ALLAH dai ya sa tana da sauran kwana
a gaba tasha da ƙyar sai dai a ranar kam a asibitin cikin masarautar ta kwana.
Rasa cikin nan ya matuƙar ƙona ran Miran Arshaan da ita kanta Jasrahn da sai
a washe gari ta dawo hankalinta har take faɗa musu dalilin shigarta wannan hali
saboda likita tace musu ɓacin ran da take ciki ne ya janyo ɓarin. Sabuwar tsanar
Iffah ce ta baibayesu tare da ɗaukar alwashin a sashen Shahan-shan ɗin da su
malikat Haseenat ɗin suka kaita sai sun bita sun halakar da ita. Ita kanta malikat
Haseenat ɗin sun ƙullaceta matuƙa dan a ganinsu ita ce sanadin komai. (basu san ita
bama tasan anai ba😏).

Bayan lafawar halin da Jasrah k ciki ba ƙaramin ɓacin rai Malikat Bushirat ta
nuna ba akan jin an maida Iffah sashen Tajwar Eshaan bisa wai umarninsa, sai dai
sam bata yarda ba acewarta Malikat Haseenat da Daneen Ammarah ne suka saka shi yin
hakan. A wannan gaɓar dai kai tsaye kowa ya fahimci fushin nata gaba ɗaya ya
dangana ne ga Malikat Haseenat. Dan a take ta saka a rufe mata likitocin da suke
duba Iffah, acewarta sai sun faɗa mata wanda ya sakasu yin shirin. Iya gaskiyarsu
sun rantse mata akan su babu ruwansu umarni kawai aka basu. abinda kuma ya samu
Iffah gaskiya ne kuma bincikensu ne ya basu da iliminsu. Bata nuna alamun zata
saurarensu ba ma balle yarda da abinda suke faɗa ɗin, sai ma sabon bincike data
saka akan zaman Iffah kurkuku. Sai dai me hatta jami'an da Malikat Haseenat tasa
suke tsaron Iffah sunƙi faɗar kowane sirri, hakan sai ya sake hargitsa mata lissafi
ga kuma su Miran Arshaan na tunzurata a gefe da sake munana tsohuwa Malikat
Haseenat da komai dake faruwa tana ji amma ko tari taƙiyi balle ta nuna tama san da
abinda Malikat Bushirat ɗin keyi. Ta dai aika Yumma (ƙanwarta da take tare da ita)
taje ta duba Jasrah a randa tai ɓari...

★★..... ★.....

A hankali ya janye idanunsa da ga kallon inda taken cike da basarwa yana amsa
sallamar Doctor Afif da ya shigo ɗakin akan lips. Dr Afif ya ƙaraso cikin ɗakin
yana mai rissinawa ya gaishesa, da idanu ya amsa masa kawai alamar ƴan izzar na
kusa. Shima Dr Afif ɗin bai damu ba, dan a ɗan zaman jiyyar nan har ya fara haddace
magana da idon nan. Gaban gadon ya ƙarasa yana sake rissinawa a cikin girmamawa ya
miƙa masa file ɗin hannunsa.
“Wannan shine file ɗin dukkanin bayanan nata da likitocin suka tattara. Sai
dai suna kan sake bincike akan rashin farfaɗowar tata kan lokaci da ya kamata ace
tayi tun kwanaki biyu da suka wuce”.
File ɗin ya amsa batare da yace komai ba, ya ɗan dudduba, sai kuma ya ɗago
idanunsa ya sake zubasu kan Dr Afif ɗin. Sai da yaja wasu sakanni kafin ya iya
furta abinda ke bakinsa da ƙyar. “Kai mi ka fahimta akan hakan?”.
Tsaiwa Dr Afif ya gyara yana mai sake rissinar da kansa. “ALLAH ya ƙara
maka lafiya da tsohon rai mai albarka ni ina ganin ko za'a sake neman wani
ƙwararren likitanne akan al'amurin nata da ya fi waɗan nan ɗin ƙwarewa. A yanda
suka san aikinsu bai kamata ma ace sun gagara gano wani ƙwaƙwƙwaran abu guda ɗaya
ba har zuwa yanzun, dan dole akwai abinda akai mata, dan bazai yiwu ace ta kasance
a wannan halin babu ƙwaƙwƙwaran dalili ba”.
Ɗan murmushi Tajwar Eshaan ya saki a karo na farko, batare da ya cema doctor
komai akan bayaninsa ba ya ziro fararen ƙafafunsa zuwa ƙasa. Slippers ɗin dake
ajiye gaban gadon ya saka, murya a dake ya furta, “Zan ganta”. Da sauri Dr Afif yay
gaba yana faɗin, “Bismillah ranka ya daɗe”.
Gaba ɗaya suka fito a ɗakin da yake tasa jiyyar, shi yana gaba doctor na
biye da shi, duk da a jikin ɗakin da yaken ne koma ace ɗakinne kawai aka raba da
glass sai ya zam ƙofar shigar sai kayi kamar ɗan taku biyar zuwa shida ne. Anan ɗin
ma ƙofar ta gilashi ce, doctor ya buɗe masa yana ɗan ja baya. Sai da ya fara shiga.
Tsaye yay a bakin gadon batare da ya zauna a kujerar da Doctor ya gyara masa ba.
Sai da ya fara kai dubansa kan na'urorin dake aiki a jikin nata, gadai bugun
zuciyarta normal na'urar ta nuna, sai dai nunfashinta baya tare da ita a zahirance.
Ɗauke idanun yay da ga na'urorin ya maida a kanta. Lumsassun idanunsa ya tsura
mata. Har yanzu tana kwance a yanda yake hangota daga ɗakin jiyyarsa tun ɗazun,
tayi wani irin fayau da ita ga uban haske data ƙara. Ƙoƙarin saita yanayinsa da ke
neman fallasa kan fuskarsa yayi, batare da yace komai ba cike da basarwa yay wani
irin shegen murmushin takaici mai nunin ma'anoni daban-daban da ya saka Doctor Afif
yin suman tsaye dan mamaki. Shi baima san Dr Afif ɗin nayi ba, sai ma idanunsan da
ya ɗan lumshe yana haɗiye murmushin ya taka a sannu gaban gadon sosai tamkar ba shi
ba. Yatsunsa guda biyu ya kai kan jijiyar kanta da tai ruɗu-ruɗu kusan na minti
ɗaya, kafin ya janye ransa a dagule ya dubi Doctor Afif. “A cire mata duk wata
na'urar jikinta”.
A ɗan firgice Dr Afif ya waro manyan idanunsa. Har lips ɗinsa na rawa wajen
faɗin, “Ranka ya daɗe na'urorin mam sune ke taimakamana ganin ɗan sauran abinda ya
rage yana aiki a tattare da ita. Cirewar zata iya zama haɗari a gareta. A gafarceni
idan na shiga hurumin da ba nawa ba”. Kamar ma bai fahimci bayanin doctor ɗin ba ya
sake furta, “Nace a cire”.
Sake daburcewa Dr Afif yay, sai dai bashi da damar cigaba da jayayya duk da
ya san bazai yuwu Iffah ta cigaba da rayuwa ba in har babu waɗannan na'urorin.
Wayarsa ya ciro a aljihu yay kiran wata nurse da ke aiki a clinic ɗin masarautar,
cikin ƙanƙanin lokaci sai gata tazo. Razana tai da ganin mai gayya mai aiki a
ɗakin, tuni ta zube gwuyawunta a ƙasa tana kwasar gaisuwa cikin tsumar jiki. Da
hannu yay ma Doctor nuni tai aikinta kawai batare da ko ya dubi sashen da take na.
Cikin sauri Dr Afif ya ce ta miƙe, shine ya shiga nuna mata yanda zatai komai.
Hannunta na ɗan rawa dan kasancewarsa a ɗakun kwarjininsa ya cika ko'ina. Abune
kuma da zatace bai taɓa faruwa ba a rayuwarta duk da itama ɗin dai jinin gidan ce.
Ta gama janye komai da ga jikin Iffah'r bisa umarnin Dr Afif batare da ya nemo
Doctor ɗin da ke kula da ita ba. Shiko gogan na tsaye kamar wani soja idanunsa a
kan duk yanda suke komai har aka kammala. Fita nurse ɗin tayi, shima doctor ya koma
gefe yana son ganin ikon ALLAH.
Kanta ya ɗan rissino a hankali ya kama duvet ɗin gadon ya sake gyara
mata, batare da ya dubi Doctor Afif ba ya nufi ƙofar fita yana faɗin, “Ina buƙatar
ganin Sayyid Fayzul-haq yanzu nan”.
“Umarninka shine abin jirana”. Doctor ya faɗa da sauri yana buɗe masa ƙofa.

★A mintinan da basu ƙarasa goma ba Sayyid Fayzul-haq ya iso. Cike da


girmamawa ya miƙa gaisuwa. Kai kawai ya ɗaga masa batare da ya janye idanunsa da ga
kan system ɗin gabansa da yake sarrafawa ba, dan tun shigowarsa ɗakin ita yay zaman
sarrafawa. Ɗakin ya cigaba da ɗaukar shiru na tsawon wasu mintuna kamar bashi yasa
ai kirasa ba. Sai da ya mula dan kansa kafin ya buɗe baki da ƙyar batare da ya bar
abinda yake ɗin ba. “Ina buƙatar ruwan zam-zam, da waɗan nan abubuwan”. Yay maganar
yana masa nuni da takardar da ke gefensa batare da ya ɗago ɗin ba dai. “An gama,
umarninka shine abin jirana. ALLAH ya ƙara maka lafiya da rayuwa mai albarka”.
Sayeed ya faɗa yana matsawa kansa a rissine ya ɗauka takardar. Sai kuma yay masa
sallama duk da yasan ba amsa zai samu ba ya fice da hanzarinsa domin gaggauta cika
umarnin shugabansa.
Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa dukkan abinda ya buƙata aka kawosu..

Ya hana duk likitocin sake taɓata a wannan yinin, sai ma Daneen Ammarah da ya
saka aka nemo masa. Tasha mamakin magungunan da ya nuna mata da ganin an cire duk
wata na'urar da ke tare da Iffah'r, sai dai yanda ya tsuke fuska babu alamar wasa
ya sata shanye duk abinda ke a ranta ta ɗauka abinda ya batan bisa umarnisa. Dan
duk da kasancewarsa ɗan ɗan uwanta a yanzu shi ɗin shugaba ne, akwai gaɓar da kuma
yake tafiyar da wasu al'amuran a tsakaninsu matsayin shugaba ɗin. Hakan baya
damunta, dan kowa ya san ALLAH ne ya bashi, ba dan kuma ya kasƙantar da su a kansa
bane ya fifitashi da jarabawar mulkin.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (09)

.........Yanda ya umarcetan haka tayi akan Iffah, dan dole ta kasance a tare da ita
har zuwa lokacin da ya bukaci ta kai tare da itan. Komai dake faruwa kuma akan
idanunsa ne, sai bayan wucewar Daneen Ammarah da kusan mintuna talatin ya ɗauka
Alkur'aninsa ya fito cike da takun nan nasa na izza da ƙasaita ya nufi ɗakin. Zama
yay a kujerar da ke gaban gadon shanyayyun idanunsa a kanta, ya mata kallo na wasu
mintuna tamkar mai nazari kafin ya fesar da ɗan huci ya ɗauke kansa. Alkur'anin ya
buɗe yana mai ƙara tabbatar da nutsuwarsa gaba ɗaya garesa sannan ya fara raira
karatu cikin daddaɗar muryarsa da bama kowane harafi hakkinsa cikin ƙwararren
larabci yanda ya kamata.
Ya ɗauki tsahon lokaci yana karatun, kafin ya tsagaita ya rufe ya ajiye.
Kujerar da yake zaunen ya sake matsarwa gab-gab da gadon, tamkar wanda baya so ya
kai hanunsa kan bargon ya ɗan yaye kaɗan. Kauda idanunsa yay da ga kallon inda suka
sauka ya maida a fuskarta, ɗan bakin tsiwar nan duk ya bushe. Ya ɗan ja wasu
sakanni a kallon nata, sai kuma ya kaudar yana sake tsuke fuska ya fara karanto
addu'oi yana tofa mata. Haka ya kasance tare da ita har gabannin asubahi, dan sai
da katafaren agogon masarautar ya buga cikar ƙarfe uku dai-dai sannan ya bar ɗakin
ya koma nasa. Dole ya kai kwance dan shima ba jikin nasa ya gama komawa normal
bane, a yanzu hakan ma jiri-jirin da ya fara ji yana rinjayarsa ne ya sakashi
haƙura ya dawo nan ɗin.......

★★... WASHE GARI ★★....

Ƙoƙarin rufe system ɗin gabansa yake dai-dai da shigowarta da sallama doctor
Afif na take mata baya kasancewar hadimanta basu da hurin biyota har nan. A kallo
ɗaya zaka fahimci ɓacin ran da ke shimfiɗe kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Doctor Afif ya
gyara mata kujerar da ke gaban gadon jiyyar Tajwar Eshaan ɗin, sai da ta zauna ya
juya ya fice tare da zuge musu ƙofar gilashin duk da wajene da bana shiga kowa da
kowa ba.
A hankali ya ɗan risinar da idanunsa alamar girmamawarsa gareta, sai kuma ya
motsa lips ɗinsa a tausashe ya furta “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki ya Ammie-
na”.
Duk da ɓacin ran da ke zagaye da zuciyarta hakan bai hanata ɗan sakin murmushi
ba, ta kai hannunta kan nasa ta riƙo, itama cikin sauƙaƙa harshe da nuna kulawa ta
amsa. “Tare da kai Bin Haysam Abdul-majeed. Ya ƙarfin jikinka?”.
Suna mafi soyuwa da yakan so ji da ga bakin mahaifiyarsa, sai dai kuma a duk
sanda ya jisa da ƙarfin izzar harshenta ya kan saurin gane ɓacin ranta a bayyane.
Ganin damuwarta kam shine abu mafi ƙona zuciyarsa dan shi karan kansa bai san irin
tarin ƙaunar da yake ma mahaifiyar tasa ba. Kaɗan ya gyara kishingiɗar da yay har
lokacin idanunsa na kanta, ya juya yatsunsa da ke riƙe da nata ya maida nasa a
ciki, a sannu yake tausa mata gaɓɓansu da kulawa da lallashi batare da ya sake cewa
komai ba. Tsahon mintuna suna a haka har ta fara sauke ajiyar zuciya alamar saukar
fushin nata. Ganin ta koma kamar yanda yafi buƙatar ganinta ya ɗan sake mata
murmushi.
“Nafi buƙatar ganin murmushin akan ƙyaƙyƙyawar fuskar Ammie-na a kowace
daƙiƙa ta numfashi na. Akasinsa kan ƙona zuciyata fiye da yanda wuta ke narkar da
kitse.”
Kalamansa koda a taƙaice suke zinarai ne a zuciyarta, shi ɗin yafi hasken
diamond walwali da ƙyalli a cikin idanunta a duk sanda take dubansa, ta so abubuwa
da yawa kafinsa ciki harda mahaifinsa sai dai shi tamkar shafine dake shafe dukanin
fejin sauran fejikan baya a littafin rayuwarta. Kafin ka buɗe a bangonta shine, a
shafin farko da shi take shimfiɗa, tsakkiya da ƙarshe shine mafi girma a ababen
yabonta da ƙaunarta. Ta sake sakin murmushi zuciyarta na sake risina da ga fushin
da ta baro sashenta a ciki.
Malikat Bushirat wata irin mace ce da gane halinta sai wanda ya santa, tana
da abubuwan ban mamaki ta na da kuma na ban tsoro harma dana ban sha'awa da suka
kasance mafi rinjaye a yimata ado. Hamshaƙiyace ta gasken gaske dan ko'a cikin
manyan matan dole a kirata *_ZAKANYA UWAR ZAKIN ƘASAR RUMAN_*. A yanzun ma halin
dattakon nata ta nuna, ta hanyar shanye dukan tarin abubuwan bakin nata ta cigaba
da bama ɗanta magajin mijinta mai amsa suna shugaban sarakunan ƙasarta kulawa har
zuwa lokacin data gamsu zata iya magana da shi babu fushi a harshenta. Ta
tsatstsaresa da idanunta masu kaifi irin na uwa, yayinda shi nashi ke a rissine
gareta risina irin ta ɗa a gaban mahaifiya.
“Na kasa gane komai da ga Mammah dangane da al'amarin yarinyar, a sanina
ita ke fara hukunta duk wanda ya zaɓi cutar da kai koda da mummunar magana ne, kuma
koda ni da na haifeka ce. Amma a wannan lokaci sai ta zaɓi bama mai son kawar da
numfashinka kariya batare da fahimtar da ni kaina hujjarta akan hakan ba. Shin taya
ake tunanin zan iya haɗa numfashi a ƙarƙashin runfa ɗaya da wadda ta shirya
kawarmin da abinda bani da madadinsa ko samin madadinsan ba har abada? Taya ake
tunanin zan iya kawaicin barinta da cigaba da kallonta a matsayin Zawgatu al-ibn
duk da yunƙurinta na son ganinta ta tarwatsani da tai? Idan har igiyar aurenka da
ke kanta ne katangar da ake iya min nuni da ita bango gareta ina son ka rusheta, ka
yanketa, yankewa ta har abada ibn Haysam Abdul-majeed. Dan hakan shine kawai zai
iya bani nutsuwa na manta da komai”.
Da ɗan ƙarfi ya matse idanunsa yana mai sakin numfashi a harɗe, sai dai
mai kallo da ido bai isa fassara kamilar fuskarsa ma'abociyar annuri da kwarjini ba
hatta ita dake amsa sunan mahaifiya a garesa.....
“Yanke hukunci cikin fushi da rashin haƙuri akan bincike ba itace ɗabi'ar
shugaba nagartacce ba”. Daneen Ammarah ce dake tsaye mai maganar tana ƙoƙarin
shigowa ɗakin, da alama ta ji dukkan kalaman Malikat Bushirat ɗin. Bai motsa ba,
hakama bai buɗe idanun nasa ba harta ƙarasa shigowa garesu, sai dai ya sauke wata
irin ɓoyayyar bahaguwar ajiyar zuciya acan cikin maƙoshinsa. Jin shiru ya ratsa
ɗakin ya sashi buɗe idanun sannu-sannu. Dukansu cikin ɓacin rai suke kallon juna
kowa najin ya isa yana kuma da ƙarfin iko akan yaƙin. Abune da babu wanda zai ce ya
taɓa gani a tsakaninsu sai a wannan lokaci, ciki kuwa harda shi kansa. Daneen
Ammarah ta sake katse yanayin nasu ta hanyar ɗora hannunta a kafaɗar malikat
Bushirat da alamu suka nuna ta gama kaiwa maƙura a fusata..
“Úht!”.
(sunan data kan kirata da shi wani lokacin)
“Ban sanki da garaje ba, ban sanki da kasa fahimta ba, ban sanki da munana
zato ba. Ban sanki da dagiya ba. Ina roƙonki ki danne, ki jure, ki zama mai ƙarfafa
gwiwar mai ƙarfin da ba ƙarfin akafi son ya gwada ba kai tsaye, saboda amsa sunansa
na shugaba. Bazan musa miki sunan Fareedah matsayin mai laifi ba, amma zan so ki
kasance a yanda na sanki wajen tabbatar da gaskiya akan kowane ne kafin zartar da
hukunci. Muma ba burinmu hana a hukunta ta ba, ko fifitata sama da gudan jininmu
kuma shugabanmu ba, so muke kawai abi tsarin da ya dace da dokar shari'a da muke
fata bayan ita za'a iya tono waɗan da ma suke aikata ɓarnar baya mai barinma gudan
jininmu baƙin fenti da tabo a rayuwarsa da rayuwar mulkinsa. Ki fahimci Mammah ba
fifita Fareedah take sama da abinda ta cancanci fuskanta bane, kariya take bata
matsayinta na tamkar makamin da zai iya zama zaren da zai jamu ga duk ɓoyayyun masu
laifin da muke fatan kamawa a cikin hannayenmu. Shin baki ji a ranki wanda suke
aikata ta'asar baya nada nasaba da na yanzu ba? Baki ji a ranki yanke mata hukunci
a kallonta ita kaɗai mai laifin tamkar basu ƙwarin gwiwar cigaba da aikatawar bane
koda kuwa a yanzu basu da hannu kan abinda yarinyar ta aikata? Shin baki tunawa shi
shugaba ne ba mai azaba ba?. Da yawan mutane gani suke sakacinsa da ƙin bama abu
muhimmanci koda mai muhimmancin ne halayyarsa, sai dai yanda yake yi shine cikar
zama cikakken duk wani shugaba. Shugaba da shanyewa aka sansa koda ɗacin na ƙona
makoshinsa, da haɗiyewa aka sansa koda raɗaɗin na azabtar da hanjinsa, da ɓoyewa
aka sansa koda girman al'amarin yafi girman zuciyarsa, da nazarta aka sansa koda
ƙarfin yafi ƙarfin ɗaukar ƙwaƙwalwarsa. Ba ko yaushe yake ihu ba, ba ko yaushe ake
gane ainahinsa ba, ba ko yaushe ake iya karantar zuciyarsa ba koda a ƙwayoyin
idanunsa ne.....” ta ɗan ja numfashi ta fesar a hankali da cigaba da faɗin, “Idan
har mu a karan kammu zamu kasa fahimtar kammu taya wanɗanda ke zagaye da mu zasu
fahimcemu?. Idan har uwa zata iya shanye wa da daurewa akan halayyar ƴaƴanta da duk
girman adadinsu bazasu haura ashirin ba mai zaisa shugaba mai mulkin ƙasa baki ɗaya
kamar ruman za'a so ganin zahirinsa a dole dan kawai farin cikin wani ɓangare ko
munanama wani ɓangare? Tayi laifi an yanke mata hukunci, daga baya gaskiya ta
bayyana bata da laifi ko tursasata akayi ko wani dalili da zai iya wanketa koda ace
ba shine yay hukuncin ba, to shi ne za'a kalla da tabon gazawa? Wa za'a munana? Wa
za'a aibanta? Wa za'a munanama kima da mutunci? Amasar itace shugaban nan dai Umm-
Jasrah. Dan ALLAH na roƙeki ki kwantar da hankalinki kar wasu su dinga amfani da
fusata fushinki domin cikar nasu burin, ki cigaba da zama a yanda na sanki inba
hakaba wasu zasuyi amfani da hannayenki wajen shafama kanki da kanki fentin da babu
wani ruwan da zai wankeki ya wanke wanda ake son amfani da soyayyarsa a zuciyarki.
Bayan ke uwa ce, kema ɗin shugaba ce.....”
Har cikin rai da ɓargo zantukan Daneen Ammarah sun matuƙar ratsata, sai
dai basu ruguje kaso ashirin cikin ɗari ɗin matsayin da take kallon Iffah da shi ba
har a yanzun, amma taji ta kuma amince zama mai haƙurin bin matakin da ya dace ɗin
wajen hukuntata, hakanne kawai zai bata salama kasancewar ta wadda bata ɗaukar
ƙiyayya da sauƙi ga duk wanda ya nuna mata, hakama soyayya. (Hakan kuskure ne
Malikat Bushirat, karka zafafa ƙiyayya, kar kuma ka zafafa soyayya dan wataran duk
zasu iya canja kansu a gurbin juna), sai kuma ƙudirinta na biyu babu gudu babu ja
da baya zata tabbatar da shi koda babu yardar kowa a daular ruman har shi kansa
Tajwar Eshaan ɗin........✍️
(Nace, “Humm”)

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (10)

........Daneen Ammarah da dama sanin fushin malikat Bushirat ɗin kan al'amarin ya
sata tada hankalinta ganin an kusanto da Iffah ga Tajwar Eshaan tai ɗan murmushi,
tasan kalamanta sunyi tasiri, sai dai ba tasirin da zai iya ruguje abinda take son
ganin ta ruguje ɗin ba (Wato ƙiyayyar Iffah a zuciyar Malikat Bushirat a yanzun).
Kanta ta ɗan rausayar tare da kallon Tajwar Eshaan da yay kamar babu shi a ɗakin,
dan idanunsa ma a lumshe suke kamar wanda barci ya ɗaukesa. Juyawa tai ta fice a
binta itama zuciyarta cike da ƙudirin tsayuwar daka domin tabbatar da gaskiya da
kuɓutar da yarinyar da takejinta har cikin ƙasan zuciyarta.
Idanun ya buɗe kaɗan ya bita da kallo tamkar yanda itama Malikat Bushirat ɗin
data gagara iya cewa komai ta bita da kallon..

*_“Hummm!! Bazan iya hakuri ba sai na tofa”_*


“Idan nace Humm fa ina nufin Humm da gasken gaske. Idan har Iffah ta rayu yaya
kuke tunanin a yanzu salon zamanta zai kasance da uwar mijin nata mai tsananin
ƙarfin iko? haka koda an tabbatar da jagororin abinda ya faru ta dalilin nata. Masu
karatu akwaifa cakwakiya, dan yanzu salon zai fara a ƙarƙashin abu uku ne, da zaku
iya canko min su dana baku babbar ƙyauta😉😁🥱”.

★.... TA-ƘURYA ★.....

“Na daɗe da faɗa miki wannan yarinyar hatsabibiya ce kar ki sakaci da rauninta
na kasancewa mai ƙarancin shekaru ko ƙanƙanta sama da ƙarfin ikon ki ta-ƙurya?. A
duniyar cikar buri raina abokin karo kuskure ne kuma ganganci ne da kan iya rusa
duk wani ginin da aka faro komai tsahon shekarunsa.....”
Ta-ƙurya da ke gurfane gaban Uwa cikin jin raɗaɗi a zuciya ta ɗago idanunta da
launinsu ya koma jazur, cikin rufewar idon irin na mai ɓacin rai da manta wake a
gabansa ta ce, “Mina gaza Uwa?! Minene ban bi ba a dukkanin sharuɗan ki a shekarun
nan? Miyasa matsala bata kasance abokiyar gogayya ta ba sai a lokacin da zan girbi
shukar dana ɓata tsahon shekaru wajen yimata barruwa? Miyasa? Miyasa?. Na ce miyasa
hakan ne?!. Miyasa sai da na yarda na rasa komai domin samun abinda nake kallo
komai a gareni sannan zaki hana mini? Ke ce kika ce karna taɓa kokwanto bazaki taɓa
barin zubar waɗan nan hawayen da a yanzu suke kwaranya akan fuskanta ba da ga
gareni. (Wa'iyazubillah 😭🙏). Miyasa? Miyasa a yanzu sabanin hakan nake gani?
Yarinya ƙarama da bata wuce na murjeta da tsinin takalmina ba ta shigo rayuwata da
barazanar yin kutse akan nasarata. Idan tafi ƙarfinki ne ki faɗa min danni batafi
ƙarfi na ba, babu wata uwa data haifi ƴa ko ɗan dazai zama barazana akan cikar
burina, in ko uwar ta haifosa har kuma ya kwatanta zan shafe babin zuri'arsa kaf da
babu wani abinda za'a kalla a tuna su kuma. A yanzu kam zanyi yaƙin da hannayena
dan bana buƙatar k......”
“K!! Ta-ƙurya ki dawo cikin hankalinki, kalleni da ƙyau ki san a gaban wa
kike? Uwar mugu nake bata sakarai ba. Banyi lalacewar da ke zaki ci tuwo a kaina ba
koda kuwa tuwun na ƙasa ne mai sauƙin wawaso. Idan kuma zaki gwada ga fili ga mai
doki”..
Cikin nuna halin ko gezau ta-ƙurya taja tsaki mai tsananin sauti dai-dai
lokacin da Uwa ke ɓacewa daga idanunta rai a ɓace. Ta rakata da harara tana mai
miƙewa da ga durƙuson da tai. Waya ta fusga cikin tsananin fusata ta hau danne-
danne tana kai kawo a katafaren ɗakin...

🙆Tofa al'amarin babba ne tsakanin ta-ƙurya da uwa ta ta😱. Mu dai ƴan kallo
ne😜.

★★..... ★.....

Alhamdullah a daren yau likitoci suka sami nasarar dawowar Iffah dake cika
kwanaki huɗu hayyacinta, zuwa safiya kam sai dai ace Alhamdullah duk da bawai tana
a cikin ƙarfin jikinta bane ko warkewa sarai kamar yanda take a baya. Daneen
Ammarah har da kukanta na farin ciki, bata ɓata lokaci ba wajen sanar ma Malikat
Haseenat. (Alhamdullah) ta dinga jerawa itama tare da jin nutsuwa na saukar mata,
dan tunda yarinyar nan ta tsinta kanta a halin nan hankalinta ya gagara kwanciya.
Malikat Bushirat duk da labarin farkawar Iffah ya zo har kunenta ta hanyar
doctor Afif batace komai ba hakama bata leƙa dubata ba, sai ma yazam a safiyar
ranar har zuwa yamma bata leƙa sashen Tajwar Eshaan ɗin ba gaba ɗaya, ta dai kira
waya domin jin cigaban lafiyar jikinsa. Shi ɗin ma dai bai shiga duba Iffahn ba sai
yamma duk da kuwa jiyan ma a gaban idonsa ta farfaɗo, Sannan har yanzu jikinsa babu
ƙarfi shima, dan da gaske gubar da suka haɗa da dafin macizan ta so masa illa
ƙwarai da gaske tunda gashi ma har sai da akai masa aiki dalilin taɓa wani sashe na
jikinsa data so tayi saboda ƙarfinta.

Duk da ɗakunan jiyyar tasu na maƙwaftaka da juna a yau bamai iya ganin wani
sakamako labulolin da aka zuge suka toshe gilashin da ya raba sun, koda babu
labulen gilashin mai ƙarfine da babu mai jin maganar wani koda za'ayi da ƙarfi ne,
sai dai zaka iya hango mutum fes. Har zuwa yanzu dai kayan jiyya ne a jikinsa sai
dai a kullum yakan canja da wasu sabbi sau fiye da biyu, ya ɗan rame saboda yanda
ciwon ya bugesa. Sai hakan ya sake fiddo hasken fatarsa mai launin tar-tar a cikin
idanun mai kallo. Cikin jarumtarsa da ƙarfin hali yake tafe doctor Afif biye da shi
a baya tare da Sayeed Fayzul-haq dake tsaye da ga bakin ƙofa dan zuwansa kenan.
Cikin sauri Sayeed ya danna maɓallin ƙofar gilashin ta zuge kanta a hankali. Baya
ya ɗan ja yana mai rissinar da kansa ga shugaban nasa mai matsayin gaske a garesa
da bazaya iya musaltuwa ba. Izzarsa da ƙasaita na tattare da shi, dan tamkar itace
jinin dake zagayawa a maimakon jininsa, ya ɗan ja iska ya fesar na wasu sakkani
kafin ya cigaba da takawa a sannu ya shiga bakinsa ɗauke da sallama can ƙasan
maƙoshi. ..
Daneen Ammarah da ke zaune a gefenta tana ƙoƙarin bata shayi mai zafin gaske
da Doctor ya bada umarnin bata ce ta ɗan waigo najin motsi, numfashi ta ɗan ja
ƙaɗan tana mai sauke idanunta a kansa. Sai kuma ta miƙe dai-dai Iffah tana damƙe
kofin shayin cikin hannunta duk da zafinsa da takeji sakamakon jin Daneen Ammarah
ta ambaci “Abni”. Sosai zuciyarta ke harbawa da ƙarfin gaske, kusan tare da ɗaga
sawunsa da saukewa cike da izzar da raunin ciwo bai rageta a gareshi ba sam. A
tsumen da fuskarsa take ya tabbatar ma Daneen Ammarah a Shahan-shan ɗin sa ya shigo
ba ɗanta ba, dan haka ta ɗan ja gefe a yanayin girmama darajar da ALLAH ya basa.
Cikin sauri Sayeed Fayzul-haq ya gyara masa kujera yana mai ja baya kusa da Doctor
ya rissinar da kansa. Duk abin nan dake faruwa yana tsaye kaifafan idanunsa masu
matuƙar tasiri da tabbatar da girman da ALLAH ya bashi na mulki badan yafi saura ba
na a kanta, kallo yake mata irin na ƙasan ido mai hana wanda akema sukuni koda bai
san wanda ke masa ba. Sai da ya gaji dan kansa sannan ya kai zaune sannu a hankali
ga kujerar da aka gyara masan...
Iffah ta kasa sake iya motsi duk da azabar zafin shayin da raɗaɗin da ke ratsa
mata hannu, sauƙinta ma ta ɗora shi ne bisa lallausan duvet ɗin da ƙafafunta ke
ciki har zuwa cinyarta. So take kawai taji ta ɓata, ɓata irin wanda ta daɗe tana
jin labarin masu layar zana nayi, ta kasa tantance ainahin abinda ke razanar da
kasancewar sa gareta, shin tsoro ne ko matsananciyar kunyar kai ne?. Inama inama,
inama daga halin data tsinci kanta bata sake farkawa ba balle su haɗu, inama an
cigaba da barinta ta dawwama a kurkukun da bazata sake ganinsa ya ganta ba har
abada. Tabbas har yanzu tana jin zafi, zafi mai haɗe da raɗaɗin rasa ƴan uwanta
guda biyu, sai dai saɓanin yanda ta ɗauka abun a da akwai banbanci da yanda take
kallonsa a yanzu...
Sake maida idanun nasa da ya ɗan kauda daga kanta yayi, sai dai yanzu a kan
kofin shayin da take faman damƙa ya sauke su, ya ɗanyi sama da su zuwa ƙirjinta da
girman rigar asibitin ta sakaya, sake sama yay zuwa kan fuskarta da ke nuna ainahin
yanayinta. Lumshesu yay da sake buɗewa cikin salon shanyesu matuƙa mai son nuna
kasala a bayyane, sai dai tsaf ya shanye komai daga kan fuskarsa ya haɗiyema ransa
yana mai furzar da iska kaɗan tare da gyaran muryar da ta sakata zabura alamar
hakan yazo mata a bazata. Dubansa ya maida ga Daneen Ammarah da itama gyaran muryar
tasa ya sakata ɗagawa kamar su doctor, sai dai maimakon shi bakinsa ya ce wani abu
sai Sayeed Fayzul-haq ne yay saurin faɗin, “Ranki ya daɗe, adalin shugaba mai
musanya sharri da alkairi na miƙo gaisuwar yaya jiki ga Zawjata-almilk. ALLAH ya
ƙara mata lafiya da rayuwa mai albarka.”
Daneen Ammarah ta ɗan nisa kaɗan da jinjina kanta tana mai gyara tsaiwa.
“Zawjata-almilk na godiya da wannan karamci, tana mai fatan alkairi da addu'ar
samun lafiya ga Shahan-shan shima”.
Iffah da ke saurarensu cikin tsinkewar zuciya ta ɗan ɗago ido kaɗan da
niyyar duban sa dan rashin gamsuwa da zancen Sayeed Fayzul-haq a maimakonsa, tasan
bazai barta ba, dolene ta samu hukunci dai-dai da laifinta. Sake tsinkewa zuciyarta
tai sakamakon shigar idanunta cikin nasa da ke mata kallon ƙasa-ƙasa da ta gagara
iya bashi fassara, sai kawai taji jikinta ya fara ƙyarma. Bata san ta ya ba, bata
san ya akai ba taji an riƙe kofin shayin hanunta da ke faman tangal-tangal zai kife
a jikinta. A raunane, a kuma birkice ta sake ɗago manyan idanunta da ciwo ya sakasu
raunana haɗe da kumburowa. Damar sarƙesu ya sake samu cikin shanyayyun nasa masu
kaifi, sai kawai ta saki kuka, kuka irin wanda ta jima da son tayi, kuka irin wanda
take buƙatar mai lallashi, kuka irin mai nuna tsananin bukatuwar ɗumin mahaifa ko
shaƙiƙan ƴan uwa da zasu rungumeka su lallasheka. Cigaba yay da kallonta kawai
shima zafin shayin na ratsa masa hannun da har ya fara gumi ga raɗaɗi na shigarsa.
Baya son ji dan yana matuƙar sukarsa, sai dai bazai hanata ba dan yafi son tayisa
har iya iyawar jin ta gamsu a karan kanta. Takoyi ɗin fiye ma da yanda yake buƙata,
dan sai da ta kai har ya fara cije lips ɗinsa a tsakkiyar haƙora. Sai dai ƙasaita,
izza da tsananin miskilanci mai samun jagorancin gudanar jinin mulki da ke tare da
shi ya hanashi cewa da ita komai, koman da koda kuwa abinda ya shafi laifinta ne
harta fara jan numfashi a suƙe mai alamar ƙoƙarin haɗiyewa........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*


*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (11)

.........Doctor dai da Sayeed Fayzul-haq kawunansu a ƙasa mamaki na ratsa su, dan
ba abinda sukai zaton gani ba kenan musamman idan akai la'akari da laifin Zawjata-
almilk ɗin. Daneen Ammarah kam idanunta ta lumshe tana mai sakin murmushi da addu'a
mai girma a ƙasan zuciyarta. Duk da tasan gane ainahin abinda ke cikin zuciyar
wannan gwarzon nasu abune mai wahala, mutum ne miskili da ya gajesa wajen uwa da
uba. Ga zurfin cikin tsiya uwa uba jinin mulki dake yawo a jikinsa. Sai dai hakan
baya nufin taƙi son tabbatuwar abinda take fata ɗin....
“Wannan ya huce a canjashi da wani Mamy”. Ya faɗa a can ƙasan maƙoshi yana
miƙewa tamkar bashi ne yay maganar ba. Da alama Daneen Ammarah ta fahimci abinda
yake nufin, dan kallo ta bisa da shi mai tattare da ɗan murmushi har ya fice Sayeed
Fayzul-haq da Doctor suka take masa baya.
“Muna godiya da wannan karamci”. Ta faɗa dai-dai zai fice a ɗakin.
A yanzun ma Sayeed ne ya amsa mata da tausasawa, yayinda shi ya fice abinsa.
Daneen Ammarah ta sake sakin murmushi da zaunawa a gefen Iffah, kofin shayin ta
amshe tana ƴar dariya. “Haba Ibnati, irin wannan rawar jiki haka! Ki kwantar da
hankalinki insha ALLAHU babu abinda zai faru sai alkairi. Abni adalin shugaba ne
mai son kwatanta adalci wa kowa koda kuma maƙiyinsa ne”.
Kalmar ƙarshe da ƙarfi ta zabiri Iffah. Sai kawai ta sake fashewa da kuka tana
mai jujjuya kanta lips ɗin ta na rawa. “Mamy nayi kuskure, kuskure irin wanda bazan
iya yafema kaina b.....”
“Ya isa haka”.
Daneen Ammarah ta faɗa tana mai ɗora mata yatsa akan baki alamar tai shiru. Shirun
kuwa tai sai dai hawayen basu bar zuba ba, ga jikinta na ɗan tsuma har sai da ta
rungume ta cike da lallashi..

*_★.. TA-ƘURYA ..★_*

Da ƙyar take shaƙar numfashi da fesarwa sakamakon warin da ƙarin harma da


tsamin dake tashi a cikin kogon dutsen mai tsananin saka hautsinawar ciki. Cikin
son danne aman da ke ta yunƙuro mata ta sake gyara mayafin dake jikinta ta ƙarashe
zancenta da, “Ruƙuƙi mai cika aiki na yarda da dukkan al'amarin ka tunda ƙawata ta
bani labarinka. Na yarda zaka iya ƙarashemin abinda uwa ta fara, na yarda zan
ƙarasa samun cikar burina a gareka, ina son a kawar min da duk wanda yace zai min
karan tsaye ko wanene shi a duniyar nan.....” (Wa'iyazubillah. Ya rabbi ka hanamu
ɓata akan son zukatanmu😭👏)
Wata irin basamudiyar dariya Boka Ruƙuƙi ya kece da ita, hakan ya bama
hamami da ɗoyin bakinsa damar sake busowa a cikin hancin ta ƙurya da takejin
cikinta na hautsinawa, tun a shigowarta kogon dutsen sihirtaccen ƙamshin turarenta
mai narka zuciyar mai shaƙa tuni warin kogon dutsen ɗakin boka Ruƙuƙi ya disashe
sa. Amma ta jure ta danne domin samun cikar burinta ya shafe kowanne ƙalubale da
zai iya shafarta.
Boka Ruƙuƙi ya gimtse fuska bayan ya gama kwasar dariyar tamkar bashi ba. Ya
ƙara juya jajayen idanunsa da ke sake fidda munin fuskarsa yana mai girgiza ƙaton
kansa. “Duk ƙasar ruman babu wani boka mai ƙarasa miki aikin da uwa ta fara. Ki
ɓace, ki ɓace gareni butulu inba hakaba zan ruguza duk wanda tai jajircewar gina
miki. Uwa uwar kowa ce mai share kukan masu kuka, butulu ki ɓace gareni, maza ki
ɓace!!!!”.
Ba ƙaramar gigitata tsawar tayi ba, tuni ta manta da matsayinta ta fito a
matuƙar kiɗime har tana gware da dutsi ALLAH dai ya taimaketa kan bai fashe ba.
Tana gama fitowa ta fara kwara amai, amai matuƙa tamkar zata amaryar da ƴan
hanjinta. Kasancewar daji ne ga kuma dare ya tsala daga inda amintacen hadiminta ke
jiranta ya dinga jiyo kakarin amanta. So yake yazo ya taimaka mata sai dai yana
matuƙar jin tsoro, jin dai ta cigaba dayi yay ƙundunbalar nufarta cikin matuƙar
sassarfa hannunsa ɗauke da gorar ruwa. Ƙasa ya zube duk da duhuwar da wajen ke da
shi, cikin rawar jiki yake jera mata sannu da miƙa mata gorar ruwan. Amsa tai dan
tana matuƙar buƙata, ta ɓalle murfin ta shiga sheƙama fuskarta batare da ta damu da
yanda yake jiƙa har jikinta da tsadaddun kayanta ba. Sai da ta kusa juyesa tas
kafin ta kuskure baki da sauran ta tsillar da robar tana sakin numfashi da ɗaɗɗaya.
Batare da tace da hadimin ko ci kanka ba ta nufi motar da suka zo bayan ta maida
norse mask ɗin fuskarta batare data bar hadimin ya ga ainahinta ba. Da gudu ya miƙe
ya rigata isa, shi ya buɗe mata murfin har sai da ta shiga sannan ya nufi mazaunin
driver...
Daga nesa da masarautar ya tsaya a inda suka ɗauka motar, Ta-ƙurya dake a
bayan motar ta jawo dukkan kayan ɓadda kamarta ta maida a jikinta, haka shima
hadimin nata sannan suka fita a motar. Kamar yanda suka fita ta ɓarauniyar hanya da
taimakon hadimintan haka suka koma cikin masarautar. Ta sauke bahaguwar ajiyar
zuciya lokacin da take zubewa a saman ƙawataccen gadonta. Har yanzu kanta juya mata
yake, har yanzu warin da ta shaƙo ya gagara barin hancinta. Ga matsanancin tashin
hankali, taya ita kam zata lallashi uwa, bayan ɓacin rai ya rufe idanunta ta
faffaɗa mata maganganu marasa da ɗi. Ta ina zata fara? Matsaloli sake yawa suke a
rayuwarta....

★★.... ★....

Samun lafiyar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ta saka razanin a


zukatan wasu a cikin masarautar matuƙa. Dan da gasken gaske ba haka suka so ba. Ga
soyayyar mutanen ƙasa tako ina bisa ɓoyayyun alkairansa da suka gano sanadin ganin
fuskar a zahirin Shahan-shan ɗin su yanzu. A yanzu kam babu inda zakaje kaji ana
zaginsa sai abinda ba'a rasa ba kasancewar duniya duk masoyanka sai ka samu maƙiya,
hakama duk maƙiyanka sai ka samu masoya.
Shari'ar farko da yay shirin fara gabatarwa itace kawo dai-daito tsakanin
iyayensa. Sai dai kuma sam hakan yaƙi yiwuwa saboda Malikat Bushirat ta matuƙar
ɗaukar zafi. Dan gaba ɗaya tana kallon Malikat Haseenat ne a mai son kanta da
fifita bare sama da gudan jininta. Harzuƙar tata na hauhawa ne bisa jagorancin rura
wutar da su Miran Jasim keyi ta bayan fage. Yayinda ita kuma Malikat Haseenat tai
biris kamar ma bata san mike faruwa ba. Ta kuma tsaya tsayin daka wajen bama Iffah
kariya da ƙara tsaurara tsaro na hana bama kowa hanyar iya cutar da ita. Al'amarin
na ƙara rikitar da kowa dan an kasa gane bakin zaren takun saƙar tasu akan Iffah
balle manufar kowanne.
A randa doctor ya sallami Iffah dole aka maidata kurkuku, dan rikici neman
tashi yayi a zaman fada tunanin wasu haka shine take-taken Tajwar Eshaan ɗin. Shi
dai komai baice musu ba har suka gama cece kucensu. Sai a washe gari ya bada
umarnin tsaida ranar da za'ai zaman shari'a. Dan a zahiri ba su Miran Arshaan bane
kawai ke tada jijiyar wuya kan ganin anyi shari'ar, har Malikat Bushirat zungurarsa
take yi matuƙa akan al'amarin. Acewarta in har bai gurfanar da Iffah ba ita zata
ɗauka duk matakin da ya dace a kanta...

★....

*21/4/2022* Rana ce data kasance na zaman shari'a tsakanin Iffah da ahalin


Tajwar Eshaan akan yunƙurin halaka ɗan su. Ƴan jarida sun so halartar wannan
shari'a ƙwarai da gaske, hakama jama'ar gari. Sai dai hakan bata faru ba sakamakon
cewar Shahan-shan wannan shari'a ce ta cikin gida. Ba haka su Miran Jasim suka so
ba, sai dai basu ce komai ba dan kar nuna zaƙewarsu yay yawa ya harbosu dan sun san
hatsabibi ne. A yanzun ma suna cikin taka tsantsan ne a duk wani motsinsu.
Kasancewar shari'ar cikin gida ce kamar yanda Shahan-shan ya faɗa da kansa
anyi zaman gudanar da ita ne a falonsa na biyu. Zaman ya kasance a iyakar waɗanda
ya shafa, sai manyan masu faɗa aji a ɓangaren shari'a. Falon yay tsit kowa ya nutsu
kawunansu a rissine duk da kasancewar duk iyayensa ne a wajen da kuma yayunsa, sai
dai girman da ALLAH ya ɗaura masa na shugabancin da har suma suka kasance a
ƙarƙashin sa ya tilasta musu biyayyar da girmama wannan girman koda basa so. A
sannu ya ke binsu da ido ɗaya bayan ɗaya har idanunsa ya sauka a kanta ƙyam.
(Miyasa kika fi yarda da zaɓa mana haka a lokacin da zaɓin ya fi rinjayen kasancewa
a zaɓin wasu?) Ya ayyana a zuciyarsa cikin ɗan jansu idanunsa luuu, lumshesu yay
tare da ɗan matsesu, sai kuma ya buɗe yana mai kauda kansa. Kusan tsahon mintuna
biyu yaja isaka ya fesar yana mai ɗanyin gyaran murya da sake saita kansa.
A nutse Sayeed Hanifud-Din ya fara da, “Alhmdullih kamar yanda na sani kuka
sani yau ranar 21/4/2022 zamu fara sauraren wannan ƙara. Muna roƙon UBANGIJI ya
bada ikon kamanta zartar da hukuncin adalci wajen bama mai hakki hakkinsa batare da
san zuciya ba”.
A tare aka amsa da amin har lokacin kawunansu dai a ƙasa. Ƙoƙarin hana idanunsa
da ke fusga gareta yay. Sayeed Hanifud-Din ya cigaba da faɗin, Muna buƙatar sake ji
da ga bakin masu ƙara. Muna fatan abinda ke a zukatansu ne zai fita a harsunansu,
kuskuren hakan na nufin ɗaukar mataki takowace fuska da shari'a a ta koyar damu”.
Kawuna suka shiga gyaɗawa da ambaton (Insha ALLAHU) alamar tabbatar da
abinda ya bukata ne zai tabbatan. Miran Arshaan ya sake rissinar da kansa da gyara
zama na tsantsar nutsuwa da duba ladabi. “Ni sunana Miran Arshaan ibn Abdul-majeed
Aliy. Zan kasance mai wakiltar ahalina dangane da guba da Zawjata-almilk ta zuba ga
ɗanmu a yunƙurinta na kasheshi ranar 21/2/2022. Muna roƙon adalin shugabanmu mai
albarka daya yanke mata hukunci dai-dai da laifinta dan ya zama izina ga ƴan baya.
Ngd.”
Babu wanda ya motsa a falon, tsahon mintuna biyu Shahan-shan ya nisa yana
mai ɗauke dubansa ga Miran Arshaan ya maida ga sauran ahalinsa. A karon farko ya
motsa lips ɗinsa a hankali, “Ko masu ƙara nada sauran wani ƙarin bayanin bayan
wannan?”.
Kawunansu suka shiga girgiza wa alamar a'a. Komai baice ba ya ɗauke kansa ya
maida ga Iffah da tun da aka shigo da su a falon bata ɗago ta kalla kowa ba. “Ko
wadda ake tuhuma tana da ja akan abinda ake tuhumarta da shi? Ko abin
cewa?”.........✍️

Miran Jasim Miran Arshaan kuyi takanku aradu ba ruwana

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (12)

.......Iffah da ke ƙoƙarin danne kukanta ta girgiza kanta alamar a'a. Idanunsa dake
mata kallon ƙasa-ƙasa ya ɗauke ya maida ga Sayeed Hanifud-Din dake riƙe da takardar
tuhume-tuhumen da akema Iffah. Miƙewa Sayeed.. yayi yana mai risinawar girmamawa ga
Shahan-shan. Kafin ya sake gyara tsaiwarsa ya maida kan Iffah. “Ranki ya daɗe
wannan kotu mai adalci na son ji daga bakinki dangane da waɗan nan laifuka da ake
zargin kin aikata su. Shin kin aikata da gaske? Ko kuwa dai abin ba haka
bane......”
“Ba haka bane? Kenan ma ƙazafi mukai mata bayan da bakinta ta furt.....”
Jasrah ce mai maganar rai ɓace. Sai dai muƙut ta haɗiye batare da ta ƙarasa faɗar
ba sakamakon kallon da Tajwar Eshaan yay mata, dan a yanzu sarkinta ne shi ba ɗan
yayarta ba. Idanun nasa ya juya kan Sayeed.. alamar ya cigaba. Sayeed ya sake
rissinar da kansa da ɗan rankwafawa sannan ya sake maida hankalinsa ga Iffah.
Tayi matuƙar jarumta da ƙoƙarin danne hawayen domin hanasu cigaba da zuba.
Sai dai tanajin raɗaɗinsu a ƙarƙashin zuciyarta, har hucinsu na rige-rigen fita da
numfashinta. Ta sani basai Jasrah tace komai ba, su dukansu zafinta sukeji, dan
dukansu taga hakan a fuskokinsu, Daneen Ammarah ce mai ɗan sassauci, bakuma tada
abinda za tace a kanta itakam.....
“Kotu na sauraren Zawjata-almilk”.
Sayeed Hanifud-Din ya faɗa a girmame duk da kuwa ya haifeta. Murmushin da ya bama
kowa mamaki Iffah ta saki, tare da ɗago fuskarta a karo na farko yanda zata iya
duban kowa. Sai dai bata aminta ta haɗa idonta da kowan ba. Tsaiwarta ta gyara
idonta na kallon sashen su Miran Jasim ƙasa-ƙasa, murmushi ta sake saki a karo na
biyu dan ganin yanda duk suka shiga yanayin firgici sai mazurai suke, duk da suna
ƙoƙarin dannewa kuma. (Ku kwantar da hankalinku ai ba'a zo wajen ba) ta faɗa a
zuciyarta tana ɗauke kanta. A zahiri kam natsuwarta ta sake tabbatarwa tana
fuskantar kotu da ƙyau. “Ni Fareedah bint Zayyan zan fara da bada haƙuri kafin
cewar da kowa ke buƙata da ga baki na. Nasan ko ba'a kawoni nan an gurfanar ba na
can-can-ci acema bana numfashi a dalilin taɓa rayuwar mutum mai girman iko kamar
Shahan-shan. Basai na wahal da Shari'a ba tabbas nice da kaina na bashi madarar da
ya sha mai ɗauke da dafin macizai....”
Babu wanda bai zaro idanu ba a mutanen falon dan mamakin ƙarfin halinta.
Shiko uban gayyar da furucin nata yazo masa a bazata kafeta kawai yay da idanu
zuciyarsa na matuƙar mamakin ƙarfin halin takife ɗin yarinyar...
Cikin ɗan taɓe baki Iffah ta ɗage kafaɗu tamkar bataga yanayin da duk suka
shigaba ta cigaba da faɗin. “Sai dai ba bashi madarar bace ya kamata ya zama abin
mamaki ga wannan kotu mai adalci, sannan kuma ba itace ya dace ta zama abin tuhuma
ba ko burin ganin an hukunta nin da kowa ke faman haƙilo da kai kawo sai kace
kunajin tsoron numfashina barazanace gareku. Ni inda nice ku, tushen samuwar
madarar zan maida hankali sani. Amma duk da haka ina so mai girma Shugabana da ku
ahalinsa ku duƙufa wajen bincikowa, ba kuma dan inajin tsoro ko shakkar hukuncin da
za'a min bane. Ba kuma dan zan kasa kama sunan wani bane wajen bayyana yanda akai
madarar tazo hannuna ba. Ku da kanku nake son ku gano kafin ku sami dukkan amsoshin
da kuke buƙata daga gareni dan ko numfashina zai tsaya sai na fesar da su ne tun
daga tushe, ku kanku masu kisan Zawjata-almilk na baya sai ku shirya ranar tonon
silili na tunkaro ku in har numfashina na harbawa daga gangar jikinna. Da ga ƙarshe
ina roƙon wannan kotu mai adalci data sallami amintaccen hadimin shugabana tare da
masu dafa masa abinci dan basu da laifin komai, su kuma masu ganin sun binne Iffah
ne su shirya akwai sauran wasan dan ko filin ba'a share ba. Dan sai sun biya fansar
jinin ƴan uwana uku da na iyayena koda zasu sami nasarar shafe nawa babin a doron
wannan ƙasar”.
(Fitinanniyar yarinyar nan zata sa su binne ni a tsakkiyar ƙasata) ya faɗa a
zuciyarsa yana mai lumshe idanunsa da ke bin lips ɗinta da kallon ƙasa-ƙasa,
murmushi da ke neman suɓuce masa ya haɗiye a zahiri acan ƙasan zuciyarsa kuwa yinsa
yake. Wanda bai sani ba sai ya ɗauka idanun nasa a lumshe suke, ga fuskarsa cike da
barazana mai saka ruɗani ga duk wanda zai iya dubansa saboda yanda ya ɗaureta
tamau.....
Kusan kowa sai da ya ɗauke numfashi a falon. Zukatansu kam na wata irin
duka kamar ganguna, kalaman Iffah basu da banbanci da saukar nakiya a tsakkiyar
kasuwar da bazaka iya banbance akan kanka ta fashe ba ko makwafcinka dan tsabar
ruɗani. Cikin rashin yarda da kai aka shiga kallon kallo, kowa tsoron fara tankawa
yake ko yin ƙwaƙwƙwaran motsin da zargi zai iya sauka a kansa. (Kun san mai kaza a
aljihu fa baya jimirin asss). Malikat Ashwaq ta ɗan juya idanunta cikin ɓacin rai
zatai magana da sauri Ameera Danish-Ara ta danne mata yatsun hannu tana mai haɗiyar
yawu da ƙarfi. Shiru tai ta haɗiye abinda yake shirin suɓuce mata. Hakama Malikat
Bushirat duk da kalaman Iffah sun daketa da ƙayatar da ita sai take jin kamar wani
makircine yarinyar ke son ƙullawa domin kufcewa hukunci. Itama yunƙurawar tai zatai
magana Daneen Ammarah ta girgiza mata kai da sauri.
Sayeed Hanifud-Din da gaba ɗaya shima yay mutuwar tsaye da waɗan nan
kalamai na Zawjata-almilk da babu ɗar ko shakku na tsoro a idanunta duk da raunin
dake tattare da yanayinta, jiki a sanyaye ya maida dubansa ga Shahan-shan. Babu
alamar zaice wani abu har tsawon wasu mintuna da tashin hankalin duk wani wanda ke
a falon ke sake bayyana. Sai da ya mula dan kansa yay gyaran murya. Cike da nutsuwa
da ƙasaitar data zama ado ga sanyinsa ya ɗan sake dubanta da kallon da ke tada mata
tsigar jiki a duk sanda ya yinsa. (Kinfa kife fuska tunda kin ɓallo min ruwa) a
zahiri kam sai ya sake gyara gilashin fuskarsa kaɗan. “A bisa baƙon al'amarin da ya
shigo a wannan shari'a bisa furucin wadda ake tuhuma, zamu ɗage wannan zama har
zuwa nan da kwanaki uku. Za'a sake tsaurara tsaro ga wadda ake tuhuma fiye da da.
Roƙon sakin wasu bai karɓu ba. Idan kuma da mai buƙatar cewa wani abu kotu na
saurarensa”.
Shiru kowa ya kasa cewa komai, da alama wasu sun tsargu da tunanin cewar
tasu zata iya zama talala musamman a sanin kaifin basira da sukaima Shahan-shan ɗin
nasu. Hannun da yaga an ɗaga ya bi da kallo har ya sauke idanunsa kan kakar tasa,
hakama duk wanda ke'a falon kallon nata yake. Malikat Haseenat ta jinjina kanta
cike da dattako bayan kotu ta bata izinin maganar data nuna bukatar yi. A ladabce
tai ƙasa da idanunta. “Muna godiya da wannan adalci na adalin shugabanmu, muna kuma
roƙo a bisa adalcin wannan kotu ta bamu belin wadda ake tuhuma kodan kare lafiyarta
da ranta da za'a iya nema a koda yaushe a dalilin furucin ta, babu yanda za'ai masu
waɗan nan laifukan da ta ankarar su koma gefe su naɗe hannun zaman jiran a
bankaɗosu batare da yunƙurin cuta mata ba”.
Nanma shiru kamar bazai amsa ba, bayan shuɗewar wasu mintuna kuma sai ya
motsa. “Kotu ta gamsu da roƙon, sai dai bazata iya bada belin wadda ake tuhuma ba
har sai an samo wani haske koda ƙanƙani ne da ga abinda ta faɗa ɗin. Za'a iya sake
nema a zama na gaba”.
Daga haka ya miƙe abinsa cike da ƙasaita yana takun nan nasa na izza da
bajinta. Dole kowa yay ƙasa da kansa har sai da ya fice sannan kowa ya ɗago. Iffah
da ke jin ana kallonta ta ɗan ɗago kanta, ilai kuwa idanun Miran Arshaan da Miran
Jasim ta gani na kallonta kamar zasu faɗo. Wani irin shegen makirin murmushi da ya
nema wantsalo zukatansu waje ta saki tana mai kanne musu ido ɗaya da musu wani irin
salo da yatsunta uku ta ɗauke kanta. Dan jam'ian dake tsare da ita sun zo tafiya da
ita za'a maidata kurkuku.

(Wannan ƴa ta Babiy dai to sai ta sa anyi farfesunta a daular ruman 🥲🚶)

★★★......

Har karo suke da juna yayin tafiya tsabar fita a hayyaci. Da ƙyar suka iya
ƙarasa kai kansu falon Miran Jasim da ya zamar musu mahaɗar tattauna matsalolin su.
“Tabbas kasheta zanyi, da hannuna kuma zan kashe matsiyaciyar yarinyar nan a
yau”.
“Da hakan mizai hana kaje kace masa kai ne kawai ka bada madarar”. Miran
Jasim ya faɗa cikin tsananin ɓacin rai yana wurgama Miran Arshaan da yay maganar
farko harara. Shima a harzuƙe ya dubesa. “To mi kake so muyi ko jira? Kai a
tunaninka wannan yarinyar mai kama da agwagwar ƙwa-ƙwa ta ƙi bayyana sunanmu ne
danta rufa asirinmu? To ka dawo hankalinka idan ma ya suɓuce maka ne. Dan tarko ta
kafa mana, tarko na talala garesa da bama mu ba hatta iyayen da suka haifemu sai
munyi dana sanin zuwansu wannan masarautar. Ban taɓa sanin tsagerancin ƴar iskar
yarinyar nan ya kai haka ba.”
Miran Jasim ya saki murmushi yana dafa kafaɗar Miran Arshaan. “Akwai abinda
ta taka ne, amma zamu sauke mata shi ta yanda ya dace. Zamu tabbatar mata da mu
iyayen iyayenta ne a wannan fanin na makirci. Ina son ka kwantar da hankalinka
Akhi, ba ita ba, hatta shi mai yanke hukuncin anzo gaɓar da.....hhhhhh”. Ya ƙare da
ƙyalkyalewa da dariya batare da ya ƙarasa ba........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (13)

..........Cikin kallon kai mahaukaci ne Miran Arshaan yaja guntun tsaki. “Na
kwantar da hankali fa kace? A gaɓar da nake hango cikar 99days ɗina kake tunanin
kwanciyar hankali a gareni. Jasim kanka kawai ka sani a hatsabibanci, dan haka kar
kai sakaci da ɗan hakkin da ka raina, dan shike zama RAINA KAMA KAGA GAYYA. Da
ganin idon wannan tsinanmiyar yarinyar kai ka san akwai abinda ta taka. Nama fara
zargin shegen yaron nan ba yana tare da ita bane kuwa?”.
Kalaman Miran Arshaan sun sanyaya jikin Miran Jasim da alama, dama can
ƙarfin haline kawai. Yaja numfashi mai nauyi yana jinjina kansa. “Hakane Arshaan,
amma ina son ka fahimta kasheta ma kai tsaye ba abune mai sauƙi ba. Dan bazasu taɓa
iya sakaci da bata kariya ba kamar yanda munafukan tsohuwar can ta ambata. Damar da
ke garemu kawai a yanzu shine komawa wajen Barbushi. Shine ya kamata ya mana wannan
aikin”.
Jiki a saɓule Miran Arshaan ya jinjina masa kai shima alamar gamsuwa.....

★★★.......

Duk yanda yake yaƙi da murmushin a karo na babu adadi ya gagara nasarar
dakatar da shi bayyana a kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa. Akan dole dai ya sakeshi tare da
lumshe idanunsa. “Fitinanniya”. Ya faɗa a hankali da sake nutsa kansa cikin
lallausar kujerar da yake zaune.
*_(Kai malam baka san darajar mutane bane?....)_* Kalaman da suka zama na
farko a haɗuwar farkon da bazai taɓa iya mantawa ba domin rubutattu ne a sashen da
baya goge muhimman abubuwa suka dawo masa kamar yanzu take furtasu. *_(Ka kusan
bige yaro amma tsabar kanka ba'a dai-dai yake ba shine koka fito kaga yaya yake ma
saboda ku masu kuɗin nan ɗaukar talaka kuke baida banbanci da titin da kuke gurza
tayoyin banzayen motocinku da kuka saya da kuɗinmu”). (“Anƙi a bakun, wlhy duk sai
kun fito kun dubashi kun bama kakarsa haƙuri zan baku key ɗin nan, inba hakaba sai
dai mu kwana anan.”)._*
“Zaki iya”.
Ya faɗa a hankali da ƙara sakin ɗan wani murmushin da kauda fuska kai kace
bayan shi akwai wani a ɗakin. Ƙoƙarin ture komai yake sai dai hakan kamar da wahala
dan komai kokawar sake maimaita kansa yake tamkar a yau ne ranar ke faruwa (Idan
hanunka ya sake gigin taɓa koda hijjab ɗin jikina ne sai na karyashi, Sannan koda
Shahan-shan ne yay wannan aikin bai isa barin wajen nan ba balle kai shashasha
driver”) (“Daga yau ko daga nesa kuka hangoni to ku canja hanya koda a jirgi kuke
kuwa”). Idanunsa ya lumshe da kai hannu ya shafi tattausar baƙar sumar kansa. Sai
kuma ya miƙe cike da ƙasaita yana mai ɗan sakin murmushin gefen baki da faɗin,
“Drama queen”.

(☺️
Da alama su Shanshani an shiga lambun fulawoyi🥱🚶)

★★...... ★....

“Mammah wlhy yarinyar nan ta fara bani tsoro nikam”. Daneen Ammarah ta faɗa da
alamar tsoron da gaske a kan fuskarta. Murmushi Malikat Haseenat tayi har haƙoranta
na bayyana. Sai kuma ta dubi Daneen Ammarah ɗin da ƙyau cikin ido. “Banda abin
Ammarah minene abin tsoron anan to?...”
“Mammah akwai wlhy, ki dubi fa furucin da yarinyar nan keyi, ni gaba ɗaya
komai ma neman ƙwacemin yakeyi. Ga shi tun ɗazu nake neman sister (Daneen Waheeda.
Ƴar uwarta dake aure a yankin larabawa) amma wayan yaƙi shiga.”
Sosai Malikat Haseenat ta tsareta da idanu, sai kuma ta ɗan muskuta kamar mai
son bada gargaɗi “Badai sanar mata zakiyi ba? Kirki ma fara wannan gamgancin, kin
san dai halinta ko, fitinanniya ce ta gaske. Bata haɗa al'amarin duk wani jininta
da kowa ba. Kuma kin san yanda ta nuna adawarta akan auran yarinyar nan da janta da
mukai jikinmu tun farko saboda ƙin bata haɗin kai taƙi zuwa ko dubashi duk da
labarin abinda ya samesa babu inda bai karaɗe ba”.
A sanyaye Daneen Ammarah ta jinjina kanta. “Hakane kuma Mamma, kiyi haƙuri
wlhy abinne duk ya ɗaure mun kai. Ita waccan (Malikat Bushirat) da zamu iya
tattaunawa kuma an riga an birkita al'amarin ta da zuga gaba ɗaya. Amma gaskiya
furucin yarinyar nan ya matuƙar gigitani. Mita sani haka akan abinda kowa bai sani
ba? Ta yaya ma ta sani ɗin bayan bata da alaƙa da wannan masarautar a lokacin da
abubuwan ke faruwa. Anya kuwa Iffah ba aljana bace Mamma”.
Dariya sosai Malikat Haseenat keyi, sai da tai mai isarta ta tsagaita tana
mai duban Daneen Ammarah da tai kasaƙe tana kallonta. “Babu wani aljana Ammarah.
Mutumce kamar kowa. Kuma duk abinda kike tunanin ta sani ɗin a ɗan zaman nan nata
ta fahimceshi. Ni kaina na san yarinyar hatsabibiya ce, sannan akwai wani ɓoyayyen
al'amari tattare da ita mai girman gaske da ita kanta bana tunanin tasan akwaishi
tare da ita”.
“Mamma kema fa kin fara bani tsoro”.
“To ko nima na zama aljanar?”. Malikat Haseenat ta faɗa cike da zolaya tana
murmushi.
“Wayyo Mamma ni dai bance ba kar kisa jikanki ya tsireni a tsakkiyar
masarautar sa. Kinga tafiyata”.
Da kallo kawai Malikat Haseenat ta bita tana murmushi. Tana matuƙar ƙaunar
ɗiyar tata da tausayinta. Ammarah itace ɗiya mafi soyuwa a ranta. Dan ta haɗa
abubuwa da yawa da ƴan uwanta basu da shi. Ga kuma ƙaddarar da ta sameta wadda har
yanzu sun kasa fahimtar tushenta, duk da dai zuciyarsu na karkata musu wani abu
daya shuɗe a rayuwarsu mara daɗin tunawa. Taja siririn tsaki da kauda al'amarin a
ranta cike da ƙunar zuciya......

★★.....

Dariya take sosai mai haɗe da kuka. Dariyar na zuwa mata ne a dalilin tuno
fuskokin Miran Jasim da Miran Arshaan a ɗazun, harma da na waɗanda bata san dalilin
razanar tasu ba game da furucin nata. Kuka kuwa tana yinsa ne da sanin ko mi zatayi
a yanzu ta dai riga ta rasa ahalinta, rasawa ta har abada. Sai dai koba komai tana
jinta sakayau a yau, kai koda ace su Miran Jasim sun halakata a wannan daren
bazatai baƙin ciki ba. Dan wannan ruɗanin da ta saka a zukatan manyan masu faɗa
ajin masarautar zai zama rikici ne na har abada da zai cigaba da hanasu farin ciki.
Sannan zai fargar da al'ummar ƙasar ruman son sanin wanene Tajwar Eshaan Ibn Haysam
Abdul-majeed da banbance abinda suke son sanin gaskiyarsa. Shima zai sakashi ya
maganantu ga al'ummar tasa ko da babu haka a cikin kundin tsarin mulkin nasa. Zai
saka tsoro kuma ga masu kashe masa matan da zai sake iya aura anan gaba. Ta jefa
tsuntsu biyu da dutse ɗaya kenan, kuma harga ALLAH ta sako zance masu kashe masa
mata ne badan tasan komai akan hakan ba, sai dai zuciyarta na zargin su Miran Jasim
ɗin ma anan, dan tunda suka iya shirya kashe Tajwar Eshaan ɗin lallai zasu iya
halaka matansa dan su goga masa baƙin fenti ko wani dalilinsu da ban. “Na barku da
wannan a halin daular ruman”.
Ta faɗa tana sake ƙyalƙyalewa da dariya a karo na babu adadi tun maidota ɗakin
kurkukun. Masifaffen kamshin da ya daki hancinta da kai saƙo cikin ƙwaƙwalwarta kai
tsaye ya sata haɗiye dariyar. Shiru tai zuciyarta dake ƙoƙarin ƙaryata ƙwaƙwalwar
tata na kaikawo da sauri-sauri. Tabbas alamar tsayuwar mutum take ji a ɗakin, sai
dai yaushe ya shigo? Ta ina kuma? Shine abu mafi ban mamaki. Cikin ƙoƙarin son
kauda abinda brain ɗin ta ke son tabbatar mata duk da zuciyarta na ƙaryata wa ta
ɗago kanta data tura cikin cinyoyi. Zabura ta ɗanyi idanunta na sake fitowa waje,
sai kuma ta shiga waige-waige. Shi ɗinne dai a zaune, zama irin na ƙasaita da iko a
cikin sabon ɗakin nata na kurku da aka canja mata a yau. Ga wani kwarjini da cikar
haiba zagaye da ƙyaƙykyawar fuskarsa dake bayyana shekarunsa. Ko maƙiyinsa ya
kallesa yasan ya iya tsara ado, adon da koda a ƙaramar sutura yayisa sai ya nuna
kansa....
Ƙafarsa dake kan ɗaya ya sauke, hakan ya sakata dawowa hayyacinta tai saurin
kauda kanta tana cure fuska waje guda ita a dole ba kallonsa take ba. Shima cikin
nasa salon basarwar ya kauda nasa idanun dake mata kallon ƙasa-ƙasa yana mai miƙewa
gaba ɗayansa. Hannayensa biyu duka ya zuba aljihu tare da yin ɗan taku ɗaya zuwa
biyu tamkar namijin tantabarar da ke son birge matarsa, sai kuma ya juyo a sannu
gareta ya sake sauke kaifafan idanun nasa a kanta. Cikin yanayin son lumshesu da
sake buɗewa ya motsa lips ɗinsa cikin sautin ƙasan maƙoshi ya furta, “Wacece ke? Mi
kike buƙata? Waya turoki a gareni ko ga ahalina? Dukiya? Mulki? Ko yin suna?”.
Tabbas kalamansa sun mata zafi, sai dai kwarjininsa da wata kima da take
kallonsa da shi a cikin idanunta sun hanata koda motsi. Shiru kusan na minti ɗaya
taƙi ta tanka, sai can kamar wadda aka zaburar taja nannauyan numfashi da sake suƙe
fuska tana mai fisgo jarumtarta a zahirance ta saki sassanyan murmushi. Da ƙyar ta
iya riƙe rauninta wajen bashi amsa tana mai haɗiye murmushin. “Ni ba kowa bace.
Bana buƙatar komai ga wani na sai UBANGIJI na. Farin cikin dunƙulallen ahalina
zinare ko lu'u-lu'u da duk dukiyar da ƙasar ruman ke taƙama da ita bazai iya
sayensa ba. Mulki baya cikin lissafina dan bai taɓa ko birge ni ba. Da suna nake
buƙata akwai hanyar da tafi wannan da zan bi nayi duniya ta sanni ba ƙasata ba
kawai ta ruman. Ni na turo kaina domin rama cuta ga macuci koda ace ya kasance
k.....” Sai kuma ta haɗiye tana mai kauda kanta da ga kallon da yake mata. Jin babu
alamar zai daina kallon nata ya sata sake juyowa garesa fuskarta a tsuke kamar
yanda tasa take. Suɓul ɗan ƙarfin gwiwar da take da ya suɓuce kamar yanda takejin
saurin kuzarinta na ida sabulewa da ga gangar jikinta shima. Idanu ta zuba masa a
karo na biyu tamkar wata gaula ko shasha. A yanda take kallonsa da ƙamewarta ya
sakashi cigaba da zuba mata idanun shima, sai dai duk da kallon nata ke ɗaukar wata
siga da ban, shi tayar masa da tsigar jiki yake a sigar da shi tashi zuciyar ke
amsa. Cikin son kauda abinda ke son masa kutsen ya fara takawa sannu-sannu kamar
mai sanɗa har zuwa gabanta..
Ta tafi kam, tafiyar da mai kallo zai iya kira suman zaune dan tsayuwarsa
gab da ita baisa ta motsa ba. Sannu a hankali ya tokare hannunsa ga ƙarfen ɗan
gadon da ke a ɗakin, tare da rissinowa gareta fuskarsu gab-gab da juna ya zuƙa
numfashinta ya fesa mata nasa da ya maidota hayyacinta, tsinin hancinsa kan nata
tamkar zai haɗe lips ɗinsu da ya dai-daita, ƙyawawan idanunsa da suka ɗan canja
launinsu tare da shanyewa kamar mai jin barci ƙyam akan nata da wani irin sassanyan
kallo data kasa fassarawa.
“Ko giwa ta faɗi tafi ƙarfin wawaso. Kina da kauɗi! Gaki da hayaƙi. Kar ki
kaini bango na aikata abinda zuciyata ke raya min faaaa..”.........✍️

_🙄😏Mufa a daina shige mana ba wannan ya kawomu daular ruman ba, dan duk abun
mutum sai mun masa hukunci ehe😌🚶. (Dangin Iffah'r mu koya kukace🥱)_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (14)

........Zabura tai saboda yanda yaja (faaa) ɗin ƙarshe da wani salon busa mata
numfashinsa mai ɗumi. Tare da waro idanunta waje tai baya gaba ɗayanta ta zube
ruguf a gadon idanunta na kif-kif na shiga ruɗani. Sai kuma ta tura bakin gaba da
ɓata fuska tamkar mai shirin fashewa da kuka. Idanunsa da ke a kanta ya sake
shanyewa, a yanayin son basar da salon nata ya ɗan ƙara kusanta fuskokin su tamkar
zai rungumeta har lips ɗinsu na gogar juna. A yanzun kam bata da zaɓin da ya wuce
rumtse idanun da masifar ƙarfi, ƙoƙarin danne tsumar da jikinta keyi tayi ta hanyar
son damƙo bedsheet ɗin gadon sai ta damƙo tattausan hanunsa. Da sauri ta janye nata
zata yarfar ya sarƙe yatsunta cikin nasa ya matse da ƙarfin da har sai da tai
zaburar da jikinsu ya manne da juna, cikin rawar baki da rashin sanin abin faɗa ta
fara magana a sarƙe.
“D... Dan ALLAH k.. kafin ka kashe ni ka faɗa min game da Ajmaal. Ka
faɗamin game da Iyayena da aka ce ka kashe?”. Ta faɗa maimakon amsa masa tashi
maganar tana mai sauke ajiyar zuciya da sauri-sauri saboda kusancin nasu ya yayi
yawa. Ga ƙamshin mayen turarensa wani irin harmutsa mata lissafi yake har gashin
jikinta na mimmiƙewa alamar tashin tsigar jiki.
Lips ɗinsa ya motsa kaɗan tamkar zaiyi magana sai kawai jin saukar duminsu
tai a kan nata, da masifar ƙarfi ta matse idonta da ƙanƙame illahirin jikinta da ya
ɗauka karkarwa. Miya rage mata ita kam, kawai ta saki ihun da sai ya girgiza
masarautar ko wani zai tai maketa daga ɗaurin goron da Shahan-shan ya mata, wannan
salon nasa ya girmi kanta bazata iya ɗauka ba. Hannun tai ƙoƙarin janyewa a karo na
biyu da lips ɗinta da ya ɗan ciza mai makon sumbatar da tai zato tamkar wadda ta
ɗosana kan wuta tana mai fisgar numfashinta shima a sarƙe.
Sosai abun ya so bashi dariya amma ya haɗiye kayansa yana ɗan janye jikinsa
baya, dan ya fahimci zata ma iya sume masa. Aiko wata wawuyar ajiyar zuciya ta
sauke ta miƙe zaune zumbur, cikin son kame rawar da jikinta keyi ta dunƙule kanta
waje ɗaya. Ƙoƙarin haɗiye murmushin da ke neman suɓuce masa a zuciya yayi, a
fuskarsa kam babu alamar hakan sai ma sake tsuke ta da yay fiye da farko. Jikinsa
ya ɗan ja baya ya koma a kujerar da ya tashi ya sake zama yana mai harɗe hannayensa
a ƙirjinsa da ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya ya zuba mata idanu kawai. Tsahon kusan
mintuna uku suna a haka kafin shi ya katse shirun ta hanyar gyaran murya.
“Su waye su?”.
Kaɗan ta ɗago tare da buɗe idanunta. A yanda taci karo da fuskarsa sai taji wani
irin shakkarsa da kwarjinin sa ya sake baibaye numfashinta. Yana zaune a kame
tamkar daɗa duniya tun shigowarsa bai motsa a yanda yake ba. Wani kallo data kasa
bama fassara ya jefa mata ya kauda idanun. Itama sai ta ja iska ta karasa risinar
da nata tana ɗan kallonsa ƙasa-ƙasa.
“Saninsu kai tsaye da ga gareni ba shine ya dace ba *_Sultan_*, taka tsantsan
da rayuwarka da sanya ido kan wanda duk suke zagaye da kai shine mai muhimmanci.
Idan ni banci nasara a yau ba, su zasu iya ci watarana, duk da nima ba haƙura nai
ba zan sake gwada sa'a ta a karo na biyu”. Ta ƙare maganar a salon juya manyan
idanunta da yamutse fuskarta dake tsuke tana laɓe baki idanunta dake cike da hawaye
a kansa. Sai kuma ta janye su ganin yanda ya tsareta da nasa.
Bai iya ya motsa ba, kallonta kawai yake da ƙoƙarin danne abinda ke taso masa
a kanta tun daga yatsan ƙafarsa har zuwa cikin tsakkiyar kansa. (Yarinyar nan ko)
ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam tsaf ya shanye komai daga kan fuskarsa ya
haɗiyema ransa yana mai furzar da iska kaɗan tare da sake yin gyaran muryar da ta
sakata sake ɗagowa dole, sai dai bata jure kallon nasa ba ta maida kanta ta
rissinar. Shima ɗauke nasa yay daga kanta tare da miƙewa, ta ƙasan ido tabi takun
sawayensa mai cike da izza da nutsuwa da kallo, sai da ya kai ƙofar fita gab ya
dakata sai dai bai juyo ba, “Na baki dama ta biyu, in har kikaci nasarar kaudani a
karo na biyu daga nan zuwa shekara ɗaya tukuycinki zama sarauniyar daular ruman
bisa karagar mulkin Shahan-shan. Idan kika gaza hukuncinki zama uwar yarana biyar a
ƙarƙashin ƙarfin iko ba soyayya ba....”
“Bana yarda aci riba kaina bisa ƙarfin mulkin mallaka koda anfi ƙarfi na.
Taya zakaci riba biyu a shekara ɗaya duk a kaina, Iffah ba tsuntsuwar da ake
ajiyewa a gida domin ado bace”.
Wani ɗan murmushin gefen baki yaso suɓuce masa amma sai bai bar hakan ba. A
ransa ya furta (Ƴar barazana ce yarinyar nan) a zahiri kam sai yay ƙoƙarin
ficewarsa maimakon bata amsa. Dan kansa har ya fara ciwo. In ba da iyayensa da
Malikat Haseenat ba bayaji ya taɓa magana mai tsaho da wani a rayuwarsa kamar ta
yau, shi kansa mamakin ma hakan yake, a rayuwarsa babu abu mafi bashi wahala kamar
yin magana mai tsawo, shiyyasa yafi yarda da yaren kurma koda a fada ne...
“Banfa yarda ba.... Soyayya kuwa ni bama ta taɓa zama abinda nake kallo da
muhimmanci ba da har zanyi kwaɗayin yima wani bayan ta ahalina”
Ya tsinkayi furucin nata yana ƙoƙarin ficewa. Yanzu kam sai da yay murmushin a
zuciyarsa da sake jinjina ƙarfin halinta. Bai kuma juya ɗin ba yay tafiyarsa. Ta
ɓarauniyar hanyar da ya fito ya koma sashensa, dan dama fita ce ta ɓadda kama.
Turus ya ɗanyi da ganin Malikat Haseenat da bai zaton gani a irin wannan lokacin
ba, kuma a falonsa da bazai iya tuna sanda ta shigo shi na ƙarshe ba. Basar da
yanda take binsa da kallon tuhumar da ya gani a idanunta yay ya ƙarasa takowa
gareta. Sai da ya kai zaune ya riƙo hanunta ya sumbata. Sannan ya furta “Idan
amintacciya na buƙatar ganin gudan jininta shin ba umarni kawai zata bada ba ya isa
gareta”.
Murmushi ta saki a karo na farko, itama cikin nata salon girmamawar garesa duk
da matsayinta kanta ta ɗan rausayar. “Idan uwa ta girmama ɗanta da ke amsa sunan
shugabanta laifi ne Hafidi?”.
Kansa ya girgiza yana ɗan murmushi a karo na farko. Ta san iya amsar kenan
daga garesa. Dan haka cikin rashin nuna damuwa ta cigaba da faɗin, “Fita ce ta
sirri, dan idanuna sun kasa rintsawa a wannan daren a dalilin furucin Zawjata-
almilk”.
Idanunsa ya ɗan motsa, kamar bazaice komai ba sai kuma ya nisa, “Jadda-ti miye
abin hana barci a ciki? Faɗin akwai wanda ta ambata bayan mun san da su? ko kuwa
furtawarta kasancewar bamu taɓa ji da ga bakin wani ba?. Shirmenta da son kare
kanta da ga laifinta ne kawai ya sata furtawa itama, nasan tana da hujja kan wani
ba.....”
“Ina bazai yiwu ba Eshaan. Na jima da fahimtar wannan yarinyar nada wasu
ɓoyayyun al'amura tattare da ita, sannan tana da ɗabi'ar zama kaifi.....”
(Mai hatsarin gaske ma kuwa, dan tafi duk yanda kike tunaninta Jaddah) ya
ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai ya ɗan yamutsa fuska kaɗan, dan kansa ke ciwo.
Can ƙasan maƙoshi ya ce, “Yanzu mi kike son ayi?”.
“Karmu matsa mata da son sanin da wa sukai wannan aikin. Kamar yanda tace
mu bincika da kammu muyi ƙoƙarin hakan, dan akwai wata hikima a zancen ta na bamu
damar mu bincika ɗin”.
“Yanda kikace haka za'ayi Jadda-ti. Sai dai kuma idan bamuyi bincike ba taya
za'a yanke mata hukunci? Ni fa ƙara aka kawo min, dolene na hukunta mai laifi ko na
wankesa akan gaskiyarsa”.
Murmushi tayi mai ma'anoni da yawa da ita tasan dalilin kayanta. Taja numfashi
ta fesar da ƙara damƙe hannunsa cikin nata. “Wannan sune siffofin adalin shugaba.
Sai dai inaji a jikina a kwanaki ukun nan daka bada wani abu zai iya faruwa, dan
duk masu hannu a ciki a yanzu hankalinsu ba'a kwance yake ba sam. Suna can neman
hanyar ɗaukar mataki a kanta kafin cikar kwanaki uku harma da mu kammu”.
Idanu ya tsira mata da mamakin jin kalamanta. Amma sai bai iya cewa komai
ba. Itama bata sake cewar ba ta sumbaci hannunsa tana mai lumshe idanun da buɗewa
alamar sallamar kenan. Shima nasan ya lumshe tare da rissinar da kansa ya buɗe a
hankali fuskarsa da ɗan yanayin murmushi sai dai bayin yake ba. Sai dai ta kurema
ganinsa sannan ya janye idanunsa da ke binta da kallo. Ya maida bayansa jikin
kujera ya maida idanun ya lumshe...
Duk yanda yake son hana tasirin kaikawonta a zuciya hakan ya gagara.
Ƙarfin halinta, tsaurin ido da kauɗin zance na matuƙar zaburar da shi. Koda a
tsoracan take sak take a zahirinta. Ba mata ba mazan ƙasar ruman gaba ɗaya shakkar
masa magana suke kansu tsaye, amma ita tar idonta da muryarta ke fita garesa. Itace
ta farko dake iya kallon cikin idonsa ta faɗi magana bayan mahaifinsa, amma ko
Malikat Bushirat da Malikat Haseenat bejin tunda ya mallaki hankalin kansa sun taɓa
hakan musamman a yanzu da yake matsayin Shahan-shan, suna masa magana da taushin
harshe da kuma kimantawa, duk da kasancewar sa ɗa garesu. Amma ita duk da akwai
girmamawar tattare da fitar sautinta garesa kai tsaye take babu alamar shakku, bata
kuma iya ɓoye abinda ke ranta koda a inda tasan anfi ƙarfi ta ne.
“Fitinanniya”.
Ya furta a hankali kan tausasan lips ɗinsa yana mai miƙewa da wani irin makirin
murmushi a kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa..........✍️

_wanga Shahan-shan ya fara bani olo_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (15)

........“Wlhy gaba ɗaya kaina ya kulle Akia, shin yarinyar nan wani ƙulli ne take
son yi dan ta kuɓutar da kanta saboda tasan babban burin kowa sanin mai kashe matan
Abni ne? ko kuwa gaskiya take faɗa? Idan gaskiya take faɗa taya akai tasani mu a
tsahon shekaru muka gagara ganowa? Anya kuwa shigowar yarinyar nan cikin masarautar
nan tun farko bada wata ƙullalliya ba?”.
Shiru babu alamar Malikat Bushirat zatace wani abu, hakan bai damu Jasrah ba ta
cigaba da faɗin, “Al'amarin Mammah ya cigaba da bani tsoro a wannan gaɓar. Anya ba
akwai abinda take ɓoye mana ba daya kamata mu sani?”.
A karo na farko Malikat Bushirat ta ɗago ta dubi Jasrah. Sai kuma ta miƙe
cikin yanayin ƴar zabira. “Kamar mi kike tunani?”.
“Abubuwa da yawa Akia. Ciki harda halayyarta ta yanzu dake bayyanar da ita a
mara gaskiya. Zuciyata na rayamun abubuwa da yawa fiye da yanda kike zato. Abin
tambayar anan miyasa take goyawa yarinyar nan baya? Miyasa take son bata kariya?
Bayan gudan jininta ta shirya halakawa? Ki duba kiga yanda taƙi bamu goyon baya
akan shari'ar nan ita da Ammarah. Yarinyar nan ita aka fara kaiwa sashen Abni, kuma
ita ta kaita, batai ko ciwon kai ba aka kai wata daga baya ta rasa ranta. Mi hakan
ke nufi? Kaɗan daga cikin zarge-zargena kenan”.
Kai kawai Malikat Bushirat ke jinjinawa alamar gamsuwa da bayanin Jasrah, dan
itama wannan tunanin ya jima yana mata kaikawo a zuciya. Taƙi fiddashi ne saboda
tuna halayen Malikat Haseenat ɗin masu yawa kafin yau, amma yanzu kam zuciyarta na
mata rawa akan a bubuwa da yawan gaske......

★★.... ★.....

Barbushi dake kwasar dariya bayan gama sauraren Miran Jasim da Miran Arshaan
ya tsagaita dan kansa ya tamke fuskar tamau kamar bashi ne yayi ba. “Ƙwarai kuna a
tsaka mai wuya, tsakar da in har bakinta ya buɗe ta furta ƙarshenku yazo. Abu ɗaya
zamuyi akanta, idan mun taki sa'a kun tsira. Idan akasin hakan ya kasance ku zargi
kanku....”
Komai basu iya sunce ba, dan zuciyarsu ta fara saka musu shakku akan
gazawar Barbushi. Inba gazawa ba taya ƴar yarinya ƙarama zai dinga nuna kamar ta
gagaresa. Bayan a da ya musu ayyuka manya da har a yanzu suke taka rawa da bazarsa.
Ransu ɓace suka baro wajen nasa, zukatansu na matsanancin ƙuna, kowa kuma da abinda
yake tattaunawa da ransa akan matakin ɗauka. Dan ko ana ha maza ha mata bazasu bar
Iffah ta cigaba da numfashi ba a wannan gaɓar. Kai hatta da uban gayyar za'ai
ƙurun-ƙus a wuce wajen dan sun gaji da gafara sa basuga ƙaho ba. In ba hakaba
yarinyar nan zata ɓallo musu aiki....

★★... TA-ƘURYA ★★...

Tun zaman shari'ar nan ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ta rasa makamar kamawa. A
lissafi bayan boka Ruƙuƙi ta ziyarci manyan bokaye a ƙalla huɗu amma amsa guda suke
bata bazasu iya mata aiki ba ta koma ga UWA. Tsabar takaici har kuka tayi, kuka
irin wanda ake kira kuka data ɗauka tsahon shekarun da bazata iya tuna sanda tayi
makamancin sa ba ma. Jin tsanar Iffah take fiye da komai yanzu a duniya. A kwanaki
biyun nan da suka gabata bayan zaman shari'a ta yanke shawarar gwada kasheta amma
duk hanyar da tabi sai ta sameta a toshe. Wannan ne ya sake ƙona mata rai da sake
jin raɗaɗi mafi girma.
(Ki ajiye komai ki sake komawa ga uwa, karki bari wahalarki ta wuce a banza)
shawarar aminiyarta ta sake dawo mata a karo na babu adadi. Jagwab takai zaune,
cikin don danne hawayen dake ƙoƙarin zubo mata tace, “Mike shirin faruwa da ni ne
haka? Shirin dana ɗauka shekaru kusan arba'in inayi ne wata mitsitsiyar halitta
zata zama sanadin rushemin, micece ita? Mi take takama da shi?” hawayen da take
dannewar suka zubo saboda radaɗin da take ji. Bata da sauran zaɓi a yanzu face sake
nemo UWA. Zumbur ta miƙe tamkar wadda aka tsikara. Ta lalubo kayan surkullen da
take kiranyen uwa da su, da ƙyar ta gano robar da hayaƙi ke ciki ta bulbula a
burner, take ɗakin ya harmutse har baka iya ganin komai, ita kanta numfashinta har
wani fisgar yake tsabar ƙarfin hayaƙin. Idanunta ta rumtse tare da zubewa bisa
gwiwunta ta fara hurwa na kiranye cikin yaren surkulle. Amma tsahon lokaci babu
alamar uwa, har hayaƙin ya Kore, bata gajiya ba ta cigaba tana mai sake ninka
rauninta (Wa'iyazubillah).
Ta share tsahon awa guda tana abu ɗaya babu uwa babu alamar ta. Sai ranta ya
ƙara sosuwa, ta dunƙule kanta waje ɗaya tana mai jin hawaye nason zubo mata. Amma
ta hana hakan saboda taurin zuciya. Har karfe biyu na dare da masarautar ta nitsa
bakajin motsin komai alamar anyi barci, in ma da wanda bai barcinba ya kasance a
killace ƙarƙashin inuwar karamin motsi. Waya ta ɗauka tai danne-danne ta kai kunne,
a bugu ɗaya aka amsa mata. Kafin ace komai da ga can cikin bada umarni ta furta,
“Ki sashi ya jirani a garden”. Daga haka ta yanke kiran. A gurguje tai shiri cikin
ɓadda kama ta fice, bazaka taɓa ɗauka mace bace, ta canja kammani cikin kayan
jami'an dake aiki bada tsaro a masarautar. Dan haka babu wanda ya maida hankali
kanta harta isa babban garden ɗin masarautar dake a ɓangaren kudanci. Wajen nada
ƙarancin haske, sai kukan tsuntsaye da ake kiwo jefi-jefi. Da sauri ya fito da ga
maboyarsa, ya zube a gabanta yana miƙa gaisuwa. Nuni tai masa ya miƙe batare da ta
amsa masa ba. Mikewar yay, kansa a rissine, dan haramunne a garesa kallonta.
Sai da ta gama ƙare masa kallo sama da ƙasa ta mika masa anvelope ɗin
hannunta. “Daga daren yau zuwa safiyar gobe ina buƙatar jin kuka, ina buƙatar naji
kukan mutuwar Zawjata-almilk. Idan aka samu kuskure kuwa kukan mutuwarka ahalinka
zasuyi. A jefata a babban ruwan swimming pool na garden ɗin gabashi”.
“Umarninki shine abin jirana da cikawa”. Ya faɗa da sauri cikin matuƙar
girmamawa. Bata sake tankawa ba ta juya tabar wajen. Sai da ta ɓacema ganinsa ya
iya ɗago kansa dake a risine yana sakin nannauyar ajiyar zuciya. Ba yau ya fara
mata aiki ba, sai dai a shi kansa har yanzu bazai iya sanin ainahin wacece ba. Dan
a koda yaushe cikin ɓadda kama take bashi umarni ko ta saka amintacciyar ta ta
bashi, sai dai a duk lokacin da ita ta bashi da kanta ya san ba aiki bane ƙarami.
Anvelope ɗin ya buɗe, ya wani zaro idanu da ganin makudan kuɗin da ke ciki miƙaƙƙu
sababbi ƙal sai ƙamshin sabunta suke. Fuskarsa washe da murmushi ya sumbaci kuɗin,
ransa fes da samunsu. Duk da dai yasan bazai cisu a banza ba, dan wannan aikin
bazai taɓa zama mai sauƙi ba a garesa kasancewar matsanancin tsaron da kurkukun da
Zawjata-almilk ke ciki, amma kodan waɗan nan taurarin dolene ya cika umarni.......

★★......

Ya kai mintuna goma yana kallon yanda masu tsaron kurkukun ke kaiwa da komowa,
kowanne kuma da makami tare da shi. Ga haske ƙal tamkar rana dan ko allura ka yar
ka duka ka ɗauka abinka batare da ka nema ba. Bugawar ƙaton agogon masarautar da
ake iya gani tako wace kusurwar daular ta ruman ya sashi jan numfashi a sarƙe.
Karfe uku dai-dai kenan, awa ɗaya garesa kacal na kammala wannan aikin. Dan huɗu
nayi zaka fara jin motsin hadimai na tashi domin fara ayyukansu, musamman masu
share-share da goge-goge. Zaman ɗammarar ƙugunsa ya gyara da ƙyau, hakama hular
kansa kalar kayan jikinsa na ainahin amintattun jami'an dake cikin sashen Tajwar
Eshaan. Ya ƙara saita kansa da ƙyau cikin dakewa ya tunkaresu hannunsa ɗauke da
babbar jaka. Duk da sanin matsayin masu waɗan nan kayan a gidan gaba ɗaya sukai
masa ca. Bai nuna razana ba duk da zuciyarsa na faman dukan dari-ɗari ne. Cikin
sake matse kansa ya sara musu alamar girmamawa yana mai miƙa musu I'd card ɗinsa.
“Umarnine da ga shugaba, zan sada kayan nan ga Zawjata-almilk domin sakasu a
gobe idan zata fita, na kwashe na dattin dake tare da ita”.
Kallonsa suke kawai suna sake kallon katin domin tantance shi ɗinne a
hoton kokuwa. Sai dai hoton ya ɗanyi duhu, duk da kuma hasken wajen dai rana bazata
taɓa zama ɗaya da hasken lantarki ba. A dake ya sake faɗin, “Ba tantancewar kaɗai
ake buƙata ba. Ya kamata ku kira sashen shugaba domin tabbatarwa, wannan shine
cikar aikin masu tsaro”.
Kalamansa sun ɗanyi tasiri garesu, sai dai duk da haka wani ya tubure akan
sai ya fara zuwa ya tabbatar bawai kiran waya ba. Dan ko ƙuda an tabbatar musu su
kasance masu himma wajen hanashi gittawa zuwa inda Iffah take sai da ƙwaƙwƙwaran
dalili. Tsabar ƙarfin hali na hadimin nan, babu ko nuna gezau ya bada goyon baya.
Hakan ya ƙara saka sauran jin sun yarda da shi, sai dai wancan ɗin babu alamar
hakan. Sai ma tabbatar musu da yay su cigaba da tsaresa zaije ya dawo”.
Tsahon mintuna goma da tafiyarsa sai gashi ya dawo, batare da yace komai ba
yay masa nuni da ya shiga. Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya saki da ɗan kashe ido
wa jami'in da a yanzu yake ta faman sinne kai kamar wani munafuki. Sauran basu
damuba dan su dama sun aminta tun dazun, dan haka ya wuce hankali kwance.

Tana tsaka da ɓarawon barcin da ya sace ta bayan ta idar da sallar da take


tsaiwar yi duk dare domin miƙa kukanta ga UBANGIJI taji kamar numfashinta na fita a
fisge, firgigit ta farka da ƙoƙarin kai hannunta saman hancinta, sai dai aikin gama
ya gama dan ya riga ya shaƙa mata abinda ke cikin handkherciff ɗin. Duk yanda taso
sake yunƙurawa hakan ya gagara sai ma jikinta dake saki baki ɗaya. Daga haka bata
sake sanin inda kanta yake ba.
Jikinsa na ɗan ɓari ya sakata a babbar jakar hanun nasa tare da zuge zip
ɗin. Bai tsaya ɓata lokaci ba ya saɓeta kasancewarsa ƙaƙƙarfan mutum babu alamar da
zai tabbatar maka mutum ya ɗakko. Gashi dama Iffah ta rame sosai duk da dama ba
wata mai jiki bace can. Sai dai kuma duk da hakan ƙarfin haline kawai irin na masu
busashshiyar zuciya dan sumar da itan da yay jikinta duk ya saki ta sake nauyi. Sai
da yay musu sallama da sanar da su ya kwaso kayan dattin wajenta ne bisa umarnin
Tajwar Eshaan sannan ya wuce.........✍️

Hummm

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (16)

........Kamar yanda al'adar take duk wani hadimi da karfe huɗu tayi zai fara
gudanar da aikinsa in har yana cikin hadimai masu kula da tsaftar masarautar.
Musamman ma masu shara da tsaftace irinsu garden barga da sauransu. Yauma hakance
ta kasance, hadiman duk sun tashi domin kama ayyukansu, kowa ƙoƙarinsa ya kammala
kafin sallar asubahi. Swimming pool ɗin garden ɗin gabashi dake kamar ta bayan
sashen Shahan-shan gab, babban swimming ne da masu aikin tsaftace ruwan cikinsa
suka kasance har su huɗu, kowace kusurwa da mai gyarawa. Sukan saka raga domin tace
duk wani datti daya shiga ciki, tare da sake ingantashi ya fita fes yana bada kalar
blue mai ɗaukar ido ko daga nesa. Aikinsu suka fara a nutse, tare da yima juna
magana jefi-jefi, can wanda ke a bangon yamma ya zabura tare da ƙwala ƙarar da tai
amsa kuwwa zuwa kunnen duk hadiman dake aikinsu suma gab da wajen. A take ƴan
uwansa sukayi kansa suna tambayar lafiya. Jikinsa na rawar karkarwa yay musu nuni
da cikin swimming pool, kallonsu suka maida wajen zukatansu na dukan tara-tara, dan
basu mance tsautsayin da ya taɓa faruwa ba da har yay sanadin rasa ran Miran Nayyar
(ƙani ga Marigayi Tajwar Haysam). A tare suma suka zabura jikkunansu na sake shiga
mazarin rawa.
“Tabbas mutum ne mun shiga uku!!”.
Wani ya faɗa a cikin sauran hadiman da ihun wancan ya jawo hankalinsu. Sake
daburcewa duk sukayi, an rasa wanda zai yi hoɓɓosan kai agaji ko neman agajin,
gashi motsin da suke gani anayi a cikin ruwan ya fara lafawa alamar wanda ke cikin
yana sake ƙasa. Wani da yazo kusan a ƙarshe-ƙarshe ne ya zabura zai afka, da sauri
wani ya rikoshi yana girgiza kansa. “Wannan bashine mafita ba, ayi azamar sanar da
jami'ai gudun kar mu aikata kuskure tunda bamu san wanene ba. Duk wanda ya kai
shekara arba'in da biyar baya anan yasan miya faru a dalilin irin wannan kuskuran”.
Sun gamsu da jawabinsa, duk da wasu labari kawai sukaji dan sannan girmansu bai kai
ba, wasu ma ba'a haifesu ba.

Cikin ƙanƙanin lokaci jami'ai suka iso wajen, hakama mazan masarautar dake
ƙoƙarin tafiya masallaci sallar asubahi. Rashin sanin wanene a ciki yasa shugaban
jami'an ya hana a shiga kai tsaye, sai dai tuni an gama dasa na'urorin da zasu iya
fiddo koma wanene. (Dan tun rasa Miran Nayyar da masarautar tayi Tajwar Abdul-
majeed ya tanadar da na'urorin domin tsaro). Tayi ƙasa sosai ga swimming pool ɗin
da girma sosai, cikinsa kuma anyi style kamar wani sashe-sashe da suffar ado. Hakan
yasa akaja lokaci mai tsawo kafin a samu nasarar samota, zuwa lokacin har an idar
da sallar asuba.
Kasancewar tsirarun mutane da Tajwar Eshaan ne kawai suka sami damar yin
sallar asubahin ya bada mamaki har Tajwar Eshaan ɗin yasa akai tambayar ko wani abu
na faruwa ne haka?. Waɗanda suke a masallacin duk basu sani ba, dan haka suka
tabbatar da babu komai, sai dai ko makarace ta kawo hakan. Baiji ya gamsu ba, amma
sai bai musa ba ya miƙe ya fito Sayeed Fayzul-haq da ya zama kamar amintaccensa
yanzu biye da shi. A falo Sayeed ya dakata, shi kuma ya nufi bedroom domin shiryawa
ya shiga grm. Dai-dai nan kiran waya ya shigo ta landline. Tsayawa yay cak, dan duk
kiran da zai iya shiga a wannan wayar direct dole mai muhimmanci ne da shi ya
shafa, kuma kai tsaye ake bukatar magana da shi. Tana gab da tsinkewa ya juyo,
idanunsa ya sauke akan sayeed, cike da ƙasaita yay masa nuni da wayar alamar ya
ɗaga. Cikin bin umarni sayeed ya ɗaga wayar, shiru kusan na minti ɗaya ya janye a
ɗan zabure yana kife wayar. “ALLAH ya ƙarama shugaban sarakuna da al'ummar ƙasar
ruman baki ɗaya lafiya da tsohon rai mai albarka. Kirane da ga shugaban jami'an
tsaro. An samu accident ne a cikin swimming pool ɗin babban garden, mace ce kuma,
ana kyautata zaton bata cikin hadimai, gashi tana buƙatar taimakon gaggawa da basu
da hurumin taɓata su”.
Ƙirjinsa ne yay wata irin mummunar bugawa, mafarkinsa na gabanin asubahi da
har yasa shi ƴar makara ya shiga maimaita kansa a kwanyarsa. Ƙoƙarin basarwa yay
kamar yanda ya saba, sai dai zuciyarsa taƙi bashi goyon bayan bada umarnin waninsa
yaje. Har ya daga ƙafarsa da niyyar cigaba da tafiya hakan ya gagara, idonsa ya
rumtse da ɗan ƙarfi ya buɗe, batare da yace uffan ba ya nufi ɓoyayyar hanyar da
zata sadashi da babban garden ɗin. Sosai mamaki ya kama Sayeed Fayzul-haq, sai dai
bashi da hurumin tambaya dan haka ya take masa baya da sassarfa...

★Cikin rawar jiki hadiman wajen suka shiga zubewa bisa gwiwunsu ganin mai
ruman ɗin ne fa da kansa. Yayinda jami'an suma duk suka risinar da kawuna. Taku
yake a nutse cike da ƙasaitar da ke tabbatar da kasancewarsa bajimin namiji da ko a
cikin jaruman gwarazo ne. A ƙirjinsa bugu yake kamar zai hantsilo waje, a zahirinsa
kuwa babu mai iya fahimtar komai koda daga fuskarsa ne. A hankali matan da ke
zagaye da ita suka dare, dan sune suka sanar cewar Zawjata-almilk ce, shugaban
jami'ai ya faɗa a rufe ne saboda shakkar isar da saƙon kai tsaye ga Shahan-shan
ɗin. Suma kawunansu duk a rissine suke, cikin rawar murya ɗaya daga cikin matan
data kasance amintacciyar hadima mai ƴanci dake da alhakin kaiwa da komowar duk
wani abinda ya shafi Shahan-shan da matansa ko makusancinsa (kamar jakadiya a ƙasar
hausa) ta ƙarasa zubewa cikin gurfana,
“ALLAH ya huci zuciyar shugaban sarakunan ƙasar ruman da al'ummar cikinta.
Umarninka muke jira domin taɓa Zawjata-almilk, dan rayuwarta zata iya
salwanta.....”
Idanunsa da ke ma Iffah kallon ƙasa-ƙasa ya ɗan lumshe, cikin jarumtar
son danne zillon da zuciyar ke masa ya ɗaga ƙafarsa da ƙyar yay taku ɗaya biyu da
ya sake saka matan darewa cikin rawar jiki mamaki na neman halakasu ganin gadan-
gadan Iffah ya nufa. Dai-dai yana ƙarasawa ɗaya da ga cikin jami'an wajen da yay
wata irin zabura ya sunkuto ɗaya daga kujerun dake a wajen ya dire masa, da sauri
aka ɗaura hiramin sayeed Fayzul-haq daya fincike a kansa. A hankali ya kai zaune
shanyayyun idanunsa na sake tar-tar a kanta cikin ɗan hasken da garin ya fara. An
lulluɓe jikinta da mayafi kasanwar kayanta dake jiƙe zai iya bayyana ainahinta,
kallon kusan sakanni biyar yaja numfashi ya fesar yana mai kai yatsunsa biyu saman
hancinta, babu alamar numfashi, ɗaukewa yay ya maida a jijiyar wuyanta, nan ma bata
harbawa, cikin jarumta da zaburo da sanyin da ke sauka a jijiyoyin jikinsa ya ɗan
ɗaga mayafin ya ciro hanunta. A kan tattausan nasa ya ɗaura yana mai ɗaura yatsansa
akan jijiyar tsintsiyar hannun ya lumshe ido. Da sauri ya buɗe sai dai ga mai kallo
bazai taɓa fahimta ba. Dan a nitse yake sarrafa hannunsa dake motsi kawai a jikin
nasa. Shugaban jami'ai da Sayeed Fayzul-haq dake ɗan satar kallonsa kasancewar duk
wani hadimi da sauran jami'an tun zamansa a kujerar duk sun juya bayansu suka ɗan
waro ido ganin ya kusanta ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da ta Iffah har hancinansu na gogar
juna. Ya lumshe idanu tare da sauke tausasan lips ɗinsa kan nata, ai dole suma suka
sake rissinar da kawunansu duk da sun san bawani abu zai yi ba illa bata taimakon
gaggawa.
Shiko da bai ma san sunayi ba da harshensa yay nasarar raba lips ɗinta da
haƙoranta dage datse cikin na juna ya turashi cikin bakin nata, sai kuma ya kai
yatsunsa biyu kan hancinta ya matse. Iskar bakinsa mai ƙarfi ya hura mata cike da
salon ƙwarewarsa akan iya ruwa da ceton duk wanda ya samu accident a dalilinsa. Da
wani irin ƙarfi ta zaburo ƙirjinta na ballaƙowa sai ruwan bakinta bulla a kan
fuskarsa. Idanu ya lumshe a hankali yana mai sauke wata irin nannauyar ajiyar
zuciya daga cikin maƙoshinsa da ɗan jan fuskarsa data wanke da ruwan bakinta.
Cikin sauri Ama. Ta miƙama Sayeed ƙaramin towel cikin wanda ke hanunta,
amsa yay ya matsa kusa da Tajwar Eshaan kansa a rissine ya miƙa masa. Bai motsa ba
idonsa a kanta tana cigaba da amayo ruwan saboda ɗan danna ƙirjinta da ya cigaba
dayi har tsawon kusan mintuna biyu, kafin ya miƙama sayeed hannu batare da ya juyi
ba ya amsa. Kan fuskarsa ya kai ya tsane ruwan da tuni yama gangagare har wuyansa
har ya ɗan jiƙa jallabiyar jikinsa mai tsananin ƙyau da ɗaukar idanun kai kallo.
“Duvet”.
Ya faɗa a hankali ganin jikinta ya fara karkarwa har ɗan gadon agajin gaggawar
da aka daurata na ɗan jijigawa. A cikin ƙanƙanin lokaci aka kawo, yanzu ma da kansa
ya rufa mata. Sannan ya miƙe gaba ɗayansa yana ɗan duban Sayeed. “A maidata
gareni”. Ya faɗa can ƙasan maƙoshi tamkar bashine yay maganar ba yana ƙoƙarin barin
wajen. Sai yanzu ya lura da cikar garden ɗin da duk masu faɗa ajin masarautar a
wajen. Idonsa ne ya sauka kan Malikat Bushirat da Malikat Haseenat da ke kusan tare
da juna. Dan Daneen Ammarah da Malikat Ashwaq ne suka ɗan shiga tsakaninsu. Ɗauke
idanun nasa yay ya cigaba da takunsa na bajimta. Dan kowa a wajen kansa a rissine
yake har su Malikat Bushirat ɗin kansu domin tabbatar da girman da ALLAH ya bashi
na shugabanci....
A gaban idon kowa aka wuce da Iffah sashen Tajwar Eshaan ɗin tare da Doctor
da zata sake bata taimakon gaggawa, a hankali ƙus-ƙus ya fara tashi a wajen kowa na
jimanta al'amarin da jinjina faruwarsa kasancewar duk wanda ya kwana ya tashi a
gidan yasan Iffah na kurkuku ne, kuma a yau za'ai zaman shari'a ta biyu, hakama
abinda ta faɗa a zaman waccan shari'ar kowa ya jisa. Sai dalilin faruwar al'amarin
yau ya saka zukata fara rarrabuwa a kan al'amarin ta, masu ganin a wancan zaman
shari'ar ta faɗi waɗan can kalamanne danta kuɓutar da kanta ko sharri, sai a yanzu
suke ganinfa akwai ƙamshin gaskiya tunda a karo na biyu kenan ana yunƙurin kasheta.
Idan babu rami to miya kawo rami? Wannan shine tambayarsu...........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*


*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (17)

........Samun gawar ɗaya daga cikin jami'an dake tsare da Iffah, da ɗaya daga cikin
na sashen Tajwar Eshaan ya sake tabbatar da akwai ƙullalliya. Dan alamomi na
bayyane sun nuna an fara kashe jam'in sashen Tajwar Eshaan ɗin ne akai amfani da
kayansa zuwa kurkuku, sai kuma gawar jami'in dake cikin masu tsaron Iffah da
bayanin sauran jami'an ya tabbatar da koma miye a lokacin da yace zaije ya binciko
gaskiyar zuwan jami'in da yace yazo kawoma Zawjata-almilk kaya ne. Sarƙa-sarƙar ta
ɗaure kan mutane matuƙa da yanda tama faru, sai dai jami'an sun tabbatar da sai sun
gano koma wanene anan kusa cike kuma da alwashi.....

★★.... ★....

Tunda akace ta farfaɗo hankalin duk masu hannu akan al'amarin ke'a tashe
musamman ta-ƙurya da hadimin da yay aikin. Tashin hankalin ta-ƙurya rashin mutuwar
Iffah ne, dan tanada hanyoyin da zatabi na ɓatar da hadimin cikin sauƙi, kai koda
ta barsa da rayuwarsa ma bai san ita wacece ba. Amma kasancewar cigaba da rayuwar
Iffah na nufin MATSALARTA na nan har yau da gobe dama ranar da bata san iyaka ba.
Idan har tace kuma zata sake wani yinƙuri a yanzu akwai matsala, mafitarta ɗaya ce
sake komawa ga UWA ɗin da take hangen ta gaza a baya. Wasu irin zafafan hawaye ne
masu raɗaɗi suka shiga bin kumatunta, ɗuminsu kawai taji batare da tasan ta farasu
ba. Hakan ya ƙara ƙona ranta dan akan ƴar yarinyar data raina hawayenta na zuba a
karo na babu adadi, abinda bai taɓa faruwa da ita ba kasancewarta mai nasara ga duk
abinda ta sanya gaba. Shawarar da zuciyarta ta bata akan sake kiranyen uwa ya sata
miƙewa. Surkullen jiya ta shiga fara maimaitawa. Tsahon lokaci har ta fidda rai a
yanzu ma sautin mummunar dariyar uwa ta fara karaɗe ɗakin. Dariya ta tsaho lokaci
babu alamar za'a daina kafin uwa ta bayyana a gabanta. “Ashe k! ƙaramar mara
kunyace ta-ƙurya. Ashe baki shirya yaƙin ba kika yanki filin yinsa ba! Ashe
b......”
“Tuba nake Uwa mai share kukan masu kuka. Nayi kuskure a gafarceni bazan
sake ba. Ni mai biyayyace ga umarninki a koda yaushe. Wannan ma saɓanin fahimta aka
samu”.
Shiru kamar uwa bazata tanka ba, sai kuma ta hura mummunan hancinta dayin
ƙwafa. “Dalilai biyu zasu sa na miki afuwa ta-ƙurya. Baki taɓa saɓama umarninmu ba
sai a wannan karon. Na biyu darajar wannan masarautar da kike ci. Kije ki kalmashe
bakin zaren aikinmu na ƙarshe, dan aikinki na gab da buɗewa. Ki kuma kiyayi kaima
yarinyar nan hari kai tsaye, dan duk yanda kike tunanin zaki iya a kanta ta waɗan
nan hanyoyin al'amarinta ya fi ƙarfin nan. A yanzu haka Ajlaan ya fara shinshinar
ta. Kuma komai zai iya faruwa, dan muna a gaɓar da zai iya kashe ƙishinsa kanta a
yanzun, babu makawa magajin kujerar daular ruman na kusanto duniya kenan.....”
Zabura ta-ƙurya tai jikinta na matuƙar rawa, sai wani irin rawa da lips ɗin
ta keyi suma tama gagara furta abinda ke bakinta tsabar shiga tashin hankali. Uwa
ta miƙa mata hoto cikin bada umarni. “Itace muke buƙata ta zama uwar Miran mai
jiran gado, ki gaggauta, ki gaggauta tabbatar da ita cikin masarautar nan matsayin
Zawjata-almilk daga nan zuwa ƙanƙanin lokaci. Inba haka ba kiyi kuka da kanki ta-
ƙurya! Kuyi kuka da kanki!! hahaha!! hahahah!! hhhhhh!!!!!”.
Ta ɓace ɓat sautin mummunar dariyarta na amsa kuwwa cikin ɗakin kai kace duk
masarautar za'a iya jinta...

★★....

“Wannan na sake tabbatar mana da ƙamshin gaskiya akan yarinyar nan Mammah”.
Daneen Ammarah ta faɗa cikin sanyin murya da jimamin abinda ya faru ya haddasa
mata. Numfashi mai nauyi Malikat Haseenat ta sauke, kamar bazatace komai ba sai
kuma ta dubi ɗiyar tata. “Akwai al'amarin dake tare da yarinyar mai girma da ko
iyayenta bana jin sun san da shi tattare da ita ba. Inaji a jikina a dalilinta
komai na gab da buɗewa a wannan masarautar”.
Cikin nuna mamaki Daneen Ammarah ta ce, “Babban al'amari kuma Mammah?
Kamar wane iri kenan?”.
A karo na farko Malikat Haseenat ta saki murmushi mai ƙayatarwa, batare da
tace komai ba ta danna kekenta yay gaba. Da kallo Daneen Ammarah ta bita baki sake,
ita kam wani lokacin Mammah na hargitsa mata tunani da sakata a wasiwasi
gaskiya.....

★★....

“Idan har ya kasance bakai bane kamar yanda ka faɗa to wanene kenan? Dama da
gaske kamar yanda muke zargi bayan mu akwai masu harar rayuwar yarinyar nan kenan
akwai ɗin?”.
“Ga alamun hakan ka gani. Sai ma nakega su ɗin sun fimu shiri. Sai dai
abinda ke ɗauren kai su kuma miye nasu dalilin? Dan na hanga na hango a duk cikin
wanda zasu iya aikata hakan burinsu zai kasance irin namu ne amma basu da hujjar
yin hakan. Idan a matan mahaifinsa ne miye ribarsu tunda ba wasu ƴaƴane da su ba
balle ace suna yaƙi irin namu ne? Anya kuwa ba iyalan Sayeed Khairul-Bashar bane ke
son ɗaukar fansa?”.
“Idan kuma zasu ɗauki fansa sai su ɗauka akan wadda ba'ita ta musu laifin
ba?. Idan har sune rayuwarsa zasu hara bata matarsa ba. Kuma ai tun farkon
shigowarta masarautar nan aka fara wannan wasan. Akwai dai wata a ƙasa daya kama mu
sani mu kuma san mai wannan shirin dan dalilinsa mai ƙarfi ne.”
Cikin gamsuwa Miran Jasim ke gyaɗama Miran Arshaan kai fuskarsa ɗauke da
murmushi, dan koda basu suka aikata ba abinda ya farun ya musu daɗi har cikin rai
yake jin farin ciki da nishaɗi..

★.....

Tunda Doctor ta gama dubata ta fice ya cigaba da tsaiwa akan ƙafafunsa lumsassun
idanunsa da suka canja kala kaɗan na ɓacin rai ƙyam a kanta. Kallonta yake tamkar
wata sabuwar halitta a rayuwarsa. Kallonta yake zuciyarsa na harbawa da sauri-
sauri. Kallo yake mata irin na miyasa kika zaɓi shigowa rayuwata a haka?, bayan ba
haka na so ki kasance ba. Ƙanƙance idanun ya sakeyi a kanta yana mai datse lips
ɗinsa da haƙori har yanajin raɗaɗin hakan a karan kansa. Sannu a hankali ya fara
kai kawo a ɗakin hannayensa duk biyu goye da bayansa. Sosai a wannan gaɓar fuskarsa
ta nuna matsanancin fushi. Zuciyarsa ta fara kaiwa maƙura akan abubuwan dake faruwa
a masarautar, ya fara jin bazai iya cigaba da jurewa akai gaɓar da yake buƙata ba
tun farko. Kalaman wasiyyar mahaifinsa ne suka shiga dawo masa ɗaya bayan ɗaya. A
yanzu kam idanun ya rumtse tare da kaiwa zaune cikin kujera. Zuciyarsa na gudu da
sauri-sauri. Sosai yake jin ɗaci mai sosa zuciya. Hawayene suka cika masa ido domin
shima mutum ne kamar kowa, zuciyarsa irin ta kowa ce, yanajin zafi, yanajin farin
ciki. Sosai yake buƙatar son jinsa a jikin wani. Mahaifiya ko mata. Sai dai yasan
hakan shine abu mafi wahala a gareshi bayan abubuwa masu yawa da ALLAH ya azurtashi
da su. Yanada tarin dukiya daya nema da guminsa, mahaifinsa ya bar masa tarin
dukiya da shi kansa bai san iyakarta ba. ALLAH ya bashi mulki, mulki mafi daraja
sama da kowane shugaba da ke a ƙasar ruman. Ya azurtashi da ƙyawu irin wanda ko'a
cikin ƙyawawa yasan zai zama abin kallo. Ya azurtashi da ilimi na boko dana addini
da babu abinda zaice sai Alhamdullah. Sai dai ya tawaya ta ɓangaren mace, shi mutum
ne mabuƙaci, ya daɗe da fahimtar hakan, amma ƙaddarorimsa sun nisanta shi da samun
cikamakin waɗan nan ni'imomin da UBANGIJI ya mallaka masa. A hankali ya sauke
lumsassun idanunsa kan Iffah zuciyarsa na kaikawo. (Abbie miyasa kace na kasance
haka?) Ya ambata a zuciya cike da ƙunar da take masa mai raɗaɗi..

★★......

Jigum-jigum aka yini a masarautar cike da jimamin abinda ya faru. Al'amarin


ya fara ɗaure zuciyar kowa a yanayin da yake da wahalar fassara. Sai dai a zahiri
babu mai iya cewa komai sai ƴar ƙus-ƙus kai da abokin maganarka. Har yamma Tajwar
Eshaan na tare da Iffah, duk da damunsa da na'urar ɗumama ɗakin da aka kunna saboda
ita keyi haka ya cigaba da zama a ɗakin. Hatta da fada da akai zaman fadanci da
tunanin zai fito yace wani abu akan abinda ya faru bai fitan ba. Sallama a ɗakin
yayi ta yau. Hakan ya fara ankarar da mutanen masarautar kenan duk lokacin daya
killace kansa yaƙi fita yana fushi ne ko cikin damuwa. Dan yau dai kusan kowa a
haka ya fassara rashin fitowar tasa.
Su dai ke kiɗansu suna rawarsu, dan shi dai bai ce ba babu kuma alamar zai
ce ɗin har yammaci. A hankali ta fara motsi dai-dai lokacin da yake zaune yana
raira karatun Alkur'ani mai girma da wata irin sassanyar murya mai tsaushi da ratsa
zuciyar mai saurare. A duk lokacin da ya samu kansa a irin wannan yanayi na damuwa
mai ƙuna yafi buƙatar zama yayta karatun Alkur'ani sai ya samu nutsuwa. Da atshawa
ta fara a jere har guda huɗu, hakan ya ankarar da shi farkawar tata. Amma tsabar
ƙasaita da miskilanci baiko motsa ba ya cigaba da karatunsa har inda yaji zai tsaya
dan kansa. Koda ya ajiye Alkur'anin ma bai juyo ɗin ba kai tsaye duk da atishawar
da ta cigaba da jerawa a wahalce kuma a jajjere. A nutse ya miƙe babu alamar
gaggawa ko garaje tattare da shi, sannu-sannu ya sauke manyan ƙyawawan fararen
idanunsa kanta dai-dai ta sake yago tissue dake gefenta a bed side drawer ta toshe
bakinta domin tare atshawan da ya sake taho mata. Kusan uku ta sake jerawa kafin ta
ajiye tissue ɗin inda ta tara sauran cikin ƙanƙanin lokaci. Numfashi take saukewa a
ɗan wahale kumburarrun idanunta na lumshewa da buɗewa.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (18)

.........A haka idanun nata suka kai garesa, zuba masa su tai a yanayin kallo na
ƙasan ido, har ranta take jin bugun zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. Ba yau ta
fara ganinsa cikin ƙananan kaya ba idan yana sashensa a keɓe, amma sai taga yau ɗin
kamar special ne. Baƙaƙen kayan sun masa ƙyau matuƙa da sake bayyana haskensa da
ƙuruciyarsa kamar wani matashin saurayin da bai taɓa mallakar ko budurwa ba.
Tsantsar ƙasaita da izzar mulki dake yawo a jininsa na ƙara masa wani irin kwarjini
mai cika ido da barazana. A hankali ta ƙara ƙasa da kanta jin kamar yana nufota.
Gareta ɗin ko ya iso fuskar nan ɗam-ɗam babu alamar yasan minene murmushi ma balle
a kai ga dariya. Mug ɗin hanunsa da keta faman tururi da tashin ƙamshin haɗaɗɗen
shayi na musamman ya ajiye a side drawer ɗin batare da yayi magana ba. Shayin ta
ɗan kalla da sake maida kallonta gareshi cike da mamaki, dan ya ajiye baice komai
ba ya bar wajen, bathroom ya shige, ta ɗan lumshe idanu batare data iya cewa komai
ba. Babu abinda take buƙata sama da shayin a yanzu, dan haka ta ɗauka ta fara sha
lokaci-lokaci tana atshawa ɗin a wahalce da duban hanyar bathroom ɗin. Tsahon
mintuna biyar sai gashi ya fito yana faman sake tsuke face. Da sauri ta ɗauke
idonta kamar bata gansaba itama, ta ajiye mug ɗin hanunta data kammala shanye
shayin da ya zuba matan tana yaye duvet ɗin da take a ciki jin zufa na karyo mata
tako ina a jikinta. Yunkurin sakkowa take a gadon dai-dai yana isowa gab da ita,
hakan yasa ta dakata da miƙewar ta ɗan dubesa ta kauda kai. Idanu ya tsura mata
kamar mai tunanin ta yanda zaice wani abu, kusan minti ɗaya ya ɗan yamutsa fuska
cikin motsa lips da ƙyar yace, “ki shiga ruwa a bath....” ya haɗiye sauran a
maƙoshi batare da ya ƙarasa ba. Sake ɗago ido tai ta kallesa, ganin nasa idanun a
kanta sai ta tura baki kawai ta kauda fuska gefe sai kace wata ƴar yarinya.
(Taɓara) ya ayyana a zuciyarsa shima yana ɓata fuskar. Ƴan jin kanne yau a
kusa, wanda dama ita su ta sani a zahiri. Bama ta taɓa kallonsa a jerin mutane masu
sauƙi ba. Batare da sake cewa uffan ba kawai taji ya ɗan duƙo kanta, zabura tai
baya, sai dai kafin tai wani yunƙuri ya ɗagata cak kamar wata ƴar baby. Yo akansa
micece wata Iffah. Tsayayyen namiji ne fa ingarma da duban damtsen hannunsa kawai
ya iya saka mai tsoro zawayi a wando. Baka gane hakan sai yana sanye da ƙananun
kaya. Gaba ɗaya ta waro idanunta sai cikin nasa, da sauri taso kauda natan ya hana
hakan ta hanyar sarƙesu. Sai kawai taji zafin zazzaɓinta na ƙaruwa ma...
“Ni dai ka daina kallona”.
Furucin ya fito cikin suɓutar baki tana laɓe fuska kamar zatai kuka, dan da
gaske idanun nan nasa tsoro suke bata. Ta ɗan so bashi dariya, sai dai a zahirinsa
babu ko alamar hakan sai ma sake tsuke face ɗin da yay bai kuma janye idanun nasa
ba. Sai ma tafiya da ya farayi da ita a hankali. Rumtse nata ta samu nasarar yi da
ƙarfi dan gaba ɗaya jikinta yamutsawa yake har zuciyarta na zallo a cikin ƙirji.
Zabura tai da buɗe idanun nata a lokaci guda jinta cikin ruwa mai ɗumi sosai. Taja
ajiyar zuciya da faɗin, “Wayyo Ummuna”.
Bai kulata ba ya ida ajiyeta a ruwan dake ta faman tashin ƙamshi na masifa,
ga wani ɗumi mai ratsa ƙashi da ɓargo. Fuska a ƙwaɓe take duban kanta da yanda ya
sakata ita da kayan gaba ɗaya cikin ruwan. Sai taji kamarma ta saki kuka kawai ta
huta. Wannan wane irin kalar walaƙanci ne. Idan yace mata taje tai wanka kawai ai
ya wadatar, amma yanzu gashi ya jiƙa mata kaya duka al'halin bata da yaƙinin wasu
dan ta fahimci a sashensa take. Bai dai san tanai ba, dan tuni ma shi ya fice
abinsa. Haka ta cire kayan a jiƙe ta ajiye a gefe, nutsa kanta ta sakeyi a ruwan
tana mai lushe idanu kamshin ruwan da ɗuminsa na ratsata, ga yanda kumfar tai a
sama ful-ful na wani irin ƙayatar da ita.....

★Ta jima a bayin kafin ta fito, sam batai tunanin samunsa a ɗakin ba. Dan
haka ta fito kanta tsaye a zatonta ai zai fita ya bata waje tunda ya san wanka ta
shiga. Sai da tazo tsakkiyar ɗakin tana ƙoƙarin sharce ruwan dake sakkowa daga
jiƙaƙƙen kanta data wanke zuwa kan fuska ta tsaya turus. Da sauri ta juya bayanta
kamar zata fasa ihu. ALLAH ma ya sota bathrobe ta sanyo ba towel ba. Ai da yau taji
ƙarshen kunya a duniya.
Babu alamar zai motsa a zaman ƙasaitar da yay cikin haɗaɗɗiyar kujerar da
yake duk da yaji fitowar tata. Sai da ya mula dan kansa ya ɗan ɗago idanunsa ya
dubeta kaɗan ya kauda kai. (Bata tausayama kamata) ya ayyana a zuciyarsa yana jan
sirrin tsaki a can ƙasan maƙoshi. System ɗin dake a cinyarsa ya ajiye saman ɗan
coffee table ɗin gabansa ya miƙe fuska a daƙile, ta gabanta ya raɓa ya wuce kamar
bai ganta ba. Jitai kamar tasa ihu dan takaicinsa, sai dai kuma ta kasa motsawa da
ga tsaiwar har ya sake dawowa. A bazata yanzun ma taji tattausan hanunsa kan dogon
gashinta data naɗe dan ya tsane da wuri kasancewar ta jiƙesa lungu da saƙo dan
wanki ta masa mai ƙyau. Warwaresa yay sannan ya ɗaura karamin towel ɗin hanunsa
baby pink a kanta ya fara tsane mata ruwan. A yanzu kam ba mamaki ne ya kashe Iffah
kawai ba har da suman wucin gadi tai na ɗunbin mamakinsa. Ita Iffah, ɗiyar Babiy da
Ummu ne tsaye Shahan-shan ke mata hidima, Shahan-shan fa ba wai hadimin daular
ruman ba. Shahan-shan gaba ɗaya, wanda ke amsa shugaban na ƙasarta baki ɗaya,
shugaban kuma al'ummar ƙasar ruman baki ɗaya. Sarkin da duniya ke shakka da tsoron
nunama koda ƙasarsa yatsa. Ɗan gata da iyayensa suka haifa shi ɗaya ƙwallin ƙwal a
duniya. Shi ɗin nan dai da duniya ke kallo matsayin wani babban tauraro mai girman
gaske. “Kai ya ALLAH anya ba mafarki nake ba?”
(Idonki biyu) zuciyarta ta bata amsa da tabbatar da abinda takewa kokwanto. Ai
kanta bai nema kwancewa ba sai da ya kama igiyar bathrobe ɗin jikinta ya kwance. A
ɗan zabure ta riƙe hannunsa caraf cikin nata tana waro idanu. “Mi zakayi...?”
kalmar ta fito a suɓuce daga bakinta. Wata irin dariya ce ta nema kufce masa ya
danneta da ƙyar. Cikin ƙara kame fuska ya tsareta da idanun nan nasa masu kaifin
tsiya, hanun nata ya ture zai ƙarasa kwancewa abinsa. Sai kawai ta daka uban tsalle
ta faɗa masa a jiki “Ni wlhy ba ƴar iska bace, babu fa komai a c....” ta kasa
ƙarasawa tana ƙara cikuykuyesa da ƙyau.
Jikinsa rawa ya neman farayi saboda yanda ta ƙanƙamesa, tunda yake a
rayuwarsa bayajin ya taɓa rungumar mace kamar haka. Gaba ɗaya abinda ya ɗauka
tsahon shekaru yana dakon dannewa ya nema yunƙurowa. Ƙoƙarin janyeta yake tana sake
ƙadandanesa a tunaninta so yake ya cire matan koda tsiya. (Ya arrahaman zata
halakani) ya faɗa a zuciya yana mai rumtse idanunsa da masifar ƙarfi a zahiri.
Cikin zafin nama ya finciketa da sauri yana ƙoƙarin riƙe rawar da jikin nasa ya
fara. Cikin wata ƴar sassarfar da bata hana takunsa na ƙasaita fita a yanda yake ba
ya bar wajen, a kujerar da ya tashi ya koma ya zube. Faɗi yake (shike nan ta buɗe
aiki, Fitinanniyar yarinya zata halakani).
Oho Fareedatu batama san yanai ba, dan tana samu ya jayetan daga jikinsa ta
kwasa da gudu sai saman katafaren gadon da aka gyara tsaf kamar ba yanzu ta sauka
akansa ba. Bata da nutsuwar tunanin yanda akai aka gyara ɗin ko wanda ya gyara taja
lafiyayyen duvet ɗin ta naɗe jikinta dake faman kakkarwa. Dan jinta take kamar
wadda ta jonu da lantarki. Shiru ɗakin kowa yay ɗif a cikinsu. Babu ko motsin ac
dan bai kunna ba saboda ita, duk da yana buƙatarsa, sai dai ya kashe na'urar ɗúmama
ɗakin dake aiki tun ɗazun saboda itan. Sai da ya ɗan saita kansa kaɗan kafin ya
miƙe, batare da ya dubeta ba ya nufi hanyar fita. Ƙasa-ƙasa ta bishi da kallo,
ganin ya tsaya tai saurin kauda kanta. Bai juyo ba sai dai yaji a jikinsa ana
kallonsa, murya a shaƙe can ƙasan maƙoshi ya motsa lips ɗinsa kaɗan. “Ki canja
wannan rigan”.
Jitai kamar ana narkama jikinta ƙanƙara, ta wani lumshe idanunta dake faman
yin mar-mar, sai kuma ta sauke ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya dai-dai da rufe ƙofar da yay
bayan ya fice. Jitai gaba ɗaya kanta yama tushe, ta gagara tunanin komai kamar
yanda take buƙata, kamar wadda aka zabura ta miƙe, idanunta ne suka sauka kan wata
ƙyaƙyƙyawar abaya mai ɗaukar idanu. Karasawa tai ta daga rigar, sai kuma ta ɗan
waro idanu ganin b&p a ƙasa, “Kam babbar buta, duk shi ya ajiye wannan ma? OMG!
Wannan Shahan-shan ɗin daular ruman ɗin ko”. Ta ƙare faɗa kamar zata fashe da kuka.
Dan ji take duk ta daburce tsabar wata kunya da take ji na ratsata tamkar tana a
gabansa.........✍️

_🥱🏇🏇🏇🏇Babu abun faɗa yau kam, nayi nan kar ace kuma..... To bara dai nai shiru
kawai._

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*


*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (19)

.......<<★★ TA-ƘURYA ★★>>

_(Itace muke buƙata ta zama uwar Miran mai jiran gado, ki gaggauta, ki gaggauta
tabbatar da ita cikin masarautar nan matsayin Zawjata-almilk daga nan zuwa mako
huɗu. Inba haka ba kiyi kuka da kanki ta-ƙurya hahaha!!! hahaha! hhhhh!!!!)_
Zumbur ta miƙe daga ɗan barcin daya figeta, firgitattun kalaman uwa da
tayi mata su a zahiri ne waccan ranar ke maimaita kansu yanzu a barcinta matsayin
mafarki. Hannu takai ta yarce uban gumin da ya jiƙe mata goshi har yana zirarowa
akan fuskarta. Tana a tsaka mai wuya, irin tsakan da bata taɓa shigaba a duk
umarnin da uwa ta bata a baya. Maganar ƙulla auren nan bazai kasance ƙarami ba
gareta a wannan karon, sakamakon zaman babu wanda ya yarda da ɗan uwansa da akeyi
yanzu a masarautar ta ruman. Gaba ɗaya ta rasa ta inda zata ɓullowa al'amarin nan.
Ji take komai ya sukurkurce mata, sai dai kuma bazata iya yarda da barin cikar
burinta ba na tsawon shekaru da take ganin tazo gab da cimmawa. Dolene ma tai wani
abu, sai dai salon zai banbanta dana baya koda kaɗanne, zatai irin ɓadda kamar data
saba wajen ganin wannan auren ya ɗauru, dan ko zatai yawo tsirara bazata taɓa yarda
Iffah ta zama Malikat ba, mai haihuwar magajin Shahan-shan never for ever hakan ta
faru tana numfashi a doron duniya....

🥱To ta-ƙurya bara mu gani ko zaki iya, mudai ƴan kallo ne😉.

★★... ★.....

A hankali ta matse fuska sai kuma takai hannu kan shafaffen cikinta dake mata
zafin yunwa. Rabonta da abinci tun yammacin jiya, dan ƙin cin abincin da aka kai
mata da dare tai a kurkuku. Zamewa tai a hankali ta kwanta a gadon tana cigaba da
matse fuska. Dubanta ta kai a karo na biyu kan kofin shayin da ya bata ta ɓalla
masa harara kamar shi ya hanata abincin, sai kuma tai juyi ta maida fuskarta ɗayan
side ɗin tana ƙara cure jikinta waje guda hanunnta na kan cikinta..

A hankali ya tura ƙofar ya shiga idanunsa da hankalinsa gaba ɗaya na kan


wayar hanunsa mai shegen ƙyau da ɗaukar ido kamar wani glass. Ciki-ciki yay sallama
a ƙasan maƙoshi, batare da nuna alamar tuna yabar wani a ɗakin ba ya nufi
ƙyaƙyƙywar kujerar zamansa ta musamman ya kai zaune a ƙasaitance. Wani kalan zaman
isa da izzar mulki yay har lokacin idonsa akan wayar da alamar serious abu yake yi.
Sassanyan ƙamshin turarensa dake ratsa mata ƙofifin hanci ya sata buɗe idanunta
sannu a hankali. Har sun canja kala alamar barci ya fara ɗaukarta. Juyowa tai sannu
a hankali batare da tunanin shi ɗin bane da gaske, dan indai ƙamshin sa ne ya riga
ya gama kama duk bedrooms ɗin da yake amfani da su tsabar yanda yake wanka da
turare kamar ruwa. Akan ƙyaƙyƙyawar farar fuskarsa da hasken wayan ya ɗan haska
baƙin sajen siɗik ɗin gashinsa na ƙyalli ta sauke, yanda akai masa gyaran fuskar da
wani irin haɗaɗɗen style yay matuƙar ƙara masa ƙyau. Sai taji tana buƙatar cigaba
da kallonsa kawai, wani abu data kasa banbancewa na tsikarar ƙasan zuciyarta.
A jikinsa yaji ana kallonsa, dan haka ya tsaya cak da ga sarrafa wayar da
yake faman yi cike da ƙwarewa. Sai dai bai ɗago ba har tsawon kusan minti ɗaya. Sai
da yay bala'in shammatarta a bazata ya ɗago nasa kaifafan idanun sai cikin nata
dake tsaye ƙyam a kansa. Da wani irin sauri ta fisge kanta gefe cike da pretending
ta riƙe ciki tana murƙususu ita a dole bata da lafiya ma. Idanun nasa ya kaɗa kamar
wani mai zuƙota ta cikinsu, sai kuma ya yamutse fuska da sake tsuketa ya ɗauke
kansa shima. Ci gaba yay da sarrafa wayarsa batare da ya sake kallonta ba, hakan ya
bata damar sake satan kallonsa ta ƙasan ido tana sake ƙaƙaro kukan ƙaryanta. lips
ɗinsa ya ɗan ciza kaɗan batare da ya bar abinda yake ba a hankali can ƙasan maƙoshi
ya furta, “What happend?”.
Baki ta tura gaba kamar bazatace komai ba. Sai kuma cikin kuka-kuka da kai
tsaye za'a kirashi na shagwaɓa tace, “Ni dai kayan cikina zasu naɗe, yunwa nakeji
ga headache, ga ciwo jikina namun ko'ina da ina”. Ta ƙare maganar tana ƙara tura
baki.
(Yarinyar nan ko...) Ya faɗa a cikin ransa idanunsa na wani binta da kallon
slowly kamar mai zooming ɗin ta a cikinsu. Dan can ƙasa-ƙasa yake mata kallon da
ita sam ta ɗauka hankalinsa na kan wayar ne baya ganinta saboda ganin yanda yake
cigaba da sarrafa wayarsa bai dakata ba. Babu alamar zai sake tanka mata har tsawon
kusan mintuna huɗu data cika tai fam da haushinsa. Tsabar son ƙular da shi sai ta
fashe da sabon kuka ta shiga wani murƙususun tana kiran “Wayyo cikina Ummu yunwa
zata halaka miki ni, nima kasheni zaiyi kamar yanda ya kashe ku. Abbiy ka shirya
tarbana gani nan a hanya inda kuke. Ni wlhy garama a kasheni da wannan azaba da
akemun, wayyo wo wo wo!!”.
Tamkar wani gunki haka ya cigaba da zuba mata ido yana kallon ikon God,
shi kam bai taɓa ganin Fitinanniyar yarinya irin yarinyar nan ba a rayuwanshi. Sam
batajin magana, ga shegen tsiwa kamar wata babyn roba mai battery. Da ƙyar ya iya
ɗaga ƙafa inda take ganin bata da alamar barin kunensa ya huta, yay tsaye a kanta
kamar wanda aka dasa, sai wani binta yake da kallon ƙasaita. “Mike ciyon?” ya faɗa
a fisge kamar ba shine ya tambayeta yanzun nan ta bashi amsa ba. Ɗan zabura tai da
jinsa gab da ita dan batai zato ba, ta yunƙura da sauri zata tashi ya maidata. Sai
kuma ya kai zaune gefenta har jinkinsu na gogar juna. Sake zaburar taso yi ya sake
maidata yana tsatstsareta da mayun idanunsa masu kaifi. “Ni dai ya warke barshi” ta
faɗa da sauri tana ƙoƙarin ture hannunsa dake jikinta. Ko gezau baiyi ba, sai ma
ɗorasa da yay saman kanta ya zare towel ɗin da ya naɗa mata tun ɗazun. Dogon
gashinta mai alamar lema har yanzu dake faman ƙyalli ne ya bayyana, ya ɗan tsirama
gashin ido na wasu sakkani kamar mai nazari, sai kuma ya janye yayo ƙasa da su kan
fuskarta. Da sauri tai ƙoƙarin kauda fuskar, sai dai ya hana hakan ta hanyar taro
fuskar tata cikin tafin hannunsa ya sarƙe idanunsa cikin idanunta ta ƙarfin tsiya.
Wani irin tashi tsigar jikinta ta farayi, cikin rawar lips kamar zata saki kuka ta
ce, “Nifa na warke nace”.
Idanunsa ya lumshe da sake buɗewa a kanta yana kusanta fuskarsu gab-gab da
juna.
“Ban yarda ba”.
Ya faɗa cikin raɗa-raɗa yana hura mata iskar bakinsa mai ƙamshin banana
akan fuskar. Zuƙa tai ta lumshe idanun tana kame jikinta da ke son fara rawa. Da
ɗan rawar lips ɗin ta sake furta, “Da gaske nake ciwon ya daina”.
Yanda tai maganar a hankali cikin rauni kaɗan ya hana Shahan-shan sakin ihu,
amma ya kanne cike da son nuna jarumta yana haɗe tsinin hancinsu waje guda. “Ni ban
yarda ba, ki nuna na tausa miki bada zafi ba fa”.
Da ƙarfi numfashin Iffah ya fisga tsabar shiga ruɗani, sai da ƙyar ta
jawoshi ya koma ƙirjinta, sai dai rawar jikinta ta fara bayyana kanta. Jin saukar
tattausan hannunsa bisa lallausar fatan gefen cikinta zuwa ƙugu da ya matsa ya sata
furta “Wayyo Ummuna”.
“Nima wayyo Ammie-na”.
Ya faɗa cikin kwaikwayon ƴar muryarta yana sake tura hanun saman shafaffen
cikinta. Da sauri tasa hannu biyu ta riƙe hannun tana tura baki, hakan ya bama lips
ɗinsu damar haɗewa, sai tai azamar son kauda fuskar amma ya hana hakan. A bazata
taji saukar lips ɗin nasa kan nata. A tare suka buɗe idanun da suka lumshe, sai dai
ita zazzaro nata tayi saɓanin shi da ya tsareta da nasa cikin kallon data kasa bama
fassara. Da wani salo ya kaɗa nasa alamar ta rufe natan, kamar wata gaula ko wadda
yake juyawa da remote kuwa ta rufesu ruf jinin jikinta na hautsina mata. Dole ta
ƙanƙame hannunsa dake kan cikinta har yanzu da masifar ƙarfi dan bata da zaɓin daya
wuce haka bayan shi.
Sai da yaso dan kansa ya janye lips ɗinsa suna mai sauke numfashi a
jajjere kamar wanda sukai gudun gasa a ƙaton fili, cikin matuƙar dauriya ya kame
nasa yanayin sai dai yaƙi yarda su haɗa ido sam. Itama ɗin dai ba kallon nasa take
ba, hasalima bata da burin da ya wuce ta samu wajen ɓuya ko zata samu sassaucin
halin da ya jefata na rashin tabbas. Tsahon wasu ƴan mintuna ɗakin ya cigaba da
zama shiru, kafin shi ya katse hakan ta hanyar ɗagota gaba ɗayanta ya zaunar a kan
gadon, hannunsa ya tura cikin gashinta, tai azamar rumtse idanunta da ƙarfi. Har
yanzu akwai damshin da yake gudar mata shiga halin muran. A nutse ya miƙe tare da
miƙar da ita, hannunta riƙe a cikin nasa suka isa gaban wadrub ɗin glass ɗin ɗakin
nasa dake cike da kayan barci kawai. Ya ɗan danna wani maɓalli sai gata ta zuge
ƙofa ta bayyana kanta. Saurin dubansa tai mamaki na barazanar halakata, shiko yay
fuska abinsa kamarma bai ganta ba, sai ma janta da yay suka ƙarasa shiga. Ashe anan
abun mamakin yake ba can ba, dan kuwa ɗakine babba zagaye da irin waccan wadrube na
glass ɗin, kai kace wani shagon saida kaya ne mai zaman kansa. Duk wani nau'in
sutura da kayan ado da yake sakama jikinsa ne anan, hatta da takalma sunada nasu
sashen, agoguna masu ƙyau na diamond dasu azurfa dana manyan companys ne gasu nan
ba'a magana. Bataji a ranta hakan mafarki bane ko bazai yiwu ba kasancewar sanin
matsayinsa, Shahan-shan fa, ai ko abinda yafi haka ka gani bakayi mamaki ba. Shi
dai ya fuske abinsa tamkar bai fahimceta ba, ya ƙarasa da ita gaban ƙaton mirror
ɗin da ke ɗauke da nau'in kayan gyaran gashi kala-kala, ko mace albarka, saukar
iskar ɗumin hair dryer ne ya maidota hayyacinta ta sauke nannauyan numfashi da ɗago
idanunta ta dubi madubin.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_


_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (20)

.........Tar-tar take kallonsu a ciki yana busar mata da gashi a nutse fuskar kuma
babu fara'a kota sisin kwabo. Kauda nata tai jikinta gaba ɗaya yay sanyi da
al'amarinsa. Sotake tayi tunanin akansa dan ya gama birkita duk ginin da take
kallonsa da shi a baya yau baki ɗaya, kaikawo kawai zuciyarta keyi. Ada zahirinsa
take tunanin kallo, ashe ba haka bane, dan a yau ta kasa iya banbance zahirinsa na
gaskiya. Ya rikita komai a lokacin daya kamata ace ta fahimci komai ɗin. Itafa
gaskiya man kanta kawai ma ya tsiyaye tas..

_(Nima dai nawa ya tsiyaye ƴar koran taki Iffah. Shahan-shan yazo da babbar
bidi'a fa gaskiya🥱🤣)._

★★ MALIKAT BUSHIRAT ★★

Tun fara faruwar al'amuran nan yau ne zuciyarta ta ɗan fara mata wasi-wasi, a
karan kanta sai take ji tana son sanin wanene ya shugabanci yarinyar domin halaka
mata gudan jininta. Dan tabbas akwai ƙamashin gaskiyar lauje cikin naɗi. Ba komai
ya sata farga ba a yau sai kallon zancen ido data ga yana gudana tsakanin Malikat
Ashwaq da Ameera Haifah a ɗazun sanda aka wuce da Iffah. Sai kuma kallon da taga
shi kansa Tajwar Eshaan ɗin ya musu su dukansu kasancewar suna tsaye duk a waje
guda ne. Ita ta haifesa, duk da bata rayu da shi na tsawon lokaci a zaman kwana da
yini ba, tasan halin ɗanta ciki da bai, ta masa sanin da ko da ido yay magana tana
fahimtarsa. Lallai kallon yana da manufa, manufa irin wadda ya kamata ace ta sani.
Manufa irin wadda ya kamata ace ta farka daga nannauyan barcin dake neman tasiri a
idanunta. Ta jima tana zargin Malikat Ashwaq a duk abinda ke faruwa ga tilon ɗanta,
sai dai a yau zuciyarta na gaya mata akwai wasu bayan itan, a wasun kuwa har Mamma
(Malikat Haseenat) bata cire a ciki ba, dan akwanakin nan take-taken tsohuwar na
rikita mata yardar data mata a baya. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, gaba ɗaya ji
take komai ya cinkushe mata, dole ne ma tana buƙatar yin nazari mai faɗi, ya kamata
kuma ta gana da shi....

★ Zaune yake harɗe a ɗaya daga cikin lafiyayyun kujerun falon. Tun dawowarsa
da ga sallar la'asar ya yada zango anan. Laptop ce a coffee table ɗin gaban kujerar
da yake yana sarrafata sannu a hankali. Sai mug na shayi dake ta faman tururi
ƙamshinsa mai daɗi daya gauraya dana turarensa na tashi sannu a hankali. Sosai
siririn farin gilashin idonsa ya sake masa ƙyau. A yanda gaba ɗaya ya tattara
hankalinsa ga screen ɗin computer ɗin zai tabbatar maka abu mai matukar muhimmanci
yake yi. Dan sai lokaci-lokaci ya kan ɗan ɗauka mug ɗin ya kai bakinsa ya maida ya
ajiye duk hankalinsa na kan abinda yake yin. Sayeed Fayzul-haq dake shigowa ya sake
maimaita sallamarsa cikin nutsuwarsa, a hankali ya motsa lips ɗinsa ya amsa batare
da ya ɗago ba. Sayeed ya ɗan ranƙwafa yana kai gaisuwa duk da basu jima da rabuwa
ba. Kansa kawai ya jinjina masa alamar amsawar kenan.
“ALLAH ya ƙara maka lafiya da nisan kwana. Malikat ke neman izinin ganinka
idan bata shiga lokacin da bai dace da ita ba”.
Shiru ya ɗan tsaya daga sarrafa system ɗin, sai dai kuma bai dagoba har
shurewar wasu sakanni da suka zama mintoci biyu. Maida yatsunsa yay kan keyboard
ɗin kamar bazai ce komai ba sai kuma ya motsa lips ɗin kamar an masa dole ya furta,
“Zata iya shigowa”.
“Malikat na godiya, ALLAH ya cigaba da kare mana kai adalin shugabanmu. ALLAH
ya gafartama magabata”.
Duk da addu'ar ƙarshe ta masa daɗi a cikin rai bai motsa ba balle ya amsa. Har
cikin ransa yana masifar jin maɗaukakin daɗi a duk lokacin da wani yay ma
mahaifansa da suka kwanta dama addu'a..

★Kallo yake mata irin na kewa da lumsassun idanunsa. Sai dai a zahirinsa
baka isa fahimtar hakan ba kai tsaye. A hankali ya ɗan kauda idanunsa da ke binta
da kallo yana rissinar da kansa dai-dai tana zama. Itama fuskarta da murmushi take
dubansa saɓanin shi da tashi babu walwalar sosai. Sai dai ya motsa lips ɗinsa a
hankali ya furta, “Barka da yamma Ammie.”
Murmushi ta sake saki da ke sake fidda ƙyawun da ALLAH ya mata. “Ina fatan
kana lafiya Niger?”.
Maimakon amsa gajeren murmushin da ita kawai keda lasisin ganinsa ya ɗan
saki yana kauda kansa, sai kuma ya sake maidowa yana mai zuba mata idanunsan nan
masu kaifi. Dan ita kanta data haifesa a duk sanda ya tsareta da su tana jin
tasirinsu sosai tattare da ita. Nata ta janye cike da ƙasaita ta furta, “Ya jikin
Ibnati?”.
Kamar bazaice komai ba sai kuma a fisge ya amsata. “Alhamdullah”.
“Thanks God. ALLAH ya ƙara lafiya”.
A zuciyarsa ya amsa amin ɗin. Bata damu ba ta cigaba da faɗin, “Abubuwa da yawa
da ke faruwa suna sake rikitamun kai, sai dai basu ne suka kawoni ba a yanzu. Yaya
maganar shari'ar da aka fara?”.
“Tana nan Ammie, za kuma a ƙarasata”. Ya faɗa a hankali cikin taushin
harshe.
Ajiyar zuciya ta ɗan sauke sai kuma ta ambaci sunansa. Dara-daran idanunsa ya
sake saukewa a kanta da ƙyau. Itama kallonsa take cike da so da ƙauna. “Ina son
tattaunawa da kai mai muhimmanci, sai dai ba'a nan ba Bin Haysam Abdul-majeed”.
Idanunsa ya lumshe ya buɗe a hankali, sunan data kirasa na ratsashi matuƙa,
cike da girmamawa a gareta ya furta, “Ki yanke duk lokacin da kike buƙata ni mai
jiran umarninki ne a koda yaushe”.
Ƙasaitaccen murmushi ta saki ƙaunarsa na sake ratsata. Cikin gyaɗa kai ta
furta, “ALLAH ya cigaba da karemun kai, ya lulluɓeka da tarin albarka da
rahamominsa marasa yankewa. Duk sanda na yanke zaka jini na barka lafiya”.
Kansa ya ɗan rissinar alamar girmamawa, kafin ya furta, “A huta lafiya”.

★★..... ★....

Bayan sallar magrib duk wani mai alaƙa da shari'ar ya kimtsa kansa a
katafaren falon da akai wancan zaman farkon. Shine ƙarshen shigowa kamar a wancan
zaman. Kan kowa rissine har ya zauna a inda aka tanada masa, tuni ƙamshinsa ya gama
danne duk wani turare mai ƙarfi a wajen. Sai da ya gama binsu da kallo ɗaya bayan
ɗaya ta ƙasan ido na tsawon wasu mintuna kafin ya mula dan kansa yay gyaran murya.
Dake nutsuwa kowa yay da maida hankalinsa garesa. Nan ma ya sake jan wasu mintuna
biyun kafin ya ɗaura da faɗin,
“Naso yanke hukunci a zaman ƙarshe na Shari'ar nan a yau, sai dai masu hannu
a al'amarin sun nuna mana su basa buƙatar hakan. Bazan tambayi dan mi akai yunƙurin
kasheta ba a karo na biyu, sai dai zan sanar da duk wanda ya aikata ya sake shiri
akan wanda yake da a baya. Kamar yanda kuka kawo ƙarar neman hakkin yunƙurin kisan
jininku da tayi, nima zan shigar da ƙarar neman hakkin kashe min mata da akayi.
Kamar yanda nai alƙawarin nema muku haƙƙinku matsayina na shugaba, itama zan nema
mata nata hakkin Insha ALLAHU a matsayina na shugaba bayan ta samu lafiya”.
Kan babbar buta kenan, ai ba wanda suka shigar da ƙarar ba hatta masu goyon
bayan Iffah kalaman Tajwar Eshaan ɗin sai da sukai musu tsawar saukar aradu na
wucin gadi. A hankali Malikat Haseenat ta saki wani ƙayataccen ɓoyayyen murmushi, a
zahiri kam ta katse suman zaunen da jama'ar wajen sukai ta hanyar faɗin,
“Hukuncinka adalcine ga kowa koda son zuciya ta rufe idanun kowa. ALLAH ya ƙarama
Zawjata-almilk lafiya, ya tona asirin wanda sukai mata wannan aikin koda a cikinmu
ne”.
“Shugaba ya amsa tare da godiya ga Uwar masu gida abin al'faharin ƴaƴan
ƙwarai. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsohon rai mai albarka baya goya marayu”.
Wannan kalamai sun fito ne da ga bakin Sayeed Fayzul-haq mai yawun faɗa da yawun
Tajwar Eshaan kasancewar yanzu tamkar amintaccensa yake. Babu dai wanda ya motsa a
zahiri, dan tamkar duk sun tafi suman wucin gadi ne, hakan yasa ya cigaba da faɗin,
“Wannan kotu mai adalci ta bada umarnin sakin Zawjata-almilk da alƙawarin bata
kariya har zuwa sanda za'a yanke mata hukuncin daya dace da ita. Ta kuma saki
amintattun hadiman da har yanzu bata kama da laifin komai ba, zakuma su cigaba da
aikinsu da ga yau. Ta bada dama ga duk mai ƙorafi akan wannan hukunci ya faɗa a
zama na gaba”.
Tabbas sun gama yarda cewar Tajwar Eshaan tsohon makirin kansa ne. Sannan
hatsabibancin da suke jifansa da shi fa sun tabbatar da shi ɗin a tattare da shi
yau. Rai ɓace kusan kowa ya fita a falon bayan fitarsa, kowa bakinsa fal da magana
sai dai babu damar yinta anan kuma gudun abinda zaije ya dawo...

★★......
Sam Iffah bata san wainar da ake toyawa ba, dan tun fita sallar la'asar
da yay a ɗakin bayan ya tsareta ta ɗanci abincin da aka kawo bata sake ganinsa ba.
Sai ma wani wahalallen zazzaɓi ne ya rufeta ruf. Da ƙyar ta iya tashi sallar
magrib. Tayi ta a daddafe ta sake komawa saman gadon ta kwanta dan rawar sanyi
jikinta ke mata. Bata iya tashi sallar isha'i ba tana cikin bargo. Sosai jikin nata
ya ɗauka matsanancin zafi ga ciwon kai ga sanyi tana ji. Tun bata damu da ƙin
shigowar tasa ba har ta fara addu'ar hakan, a haka wani wahalallen barci ya
ɗauketa.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (21)

........Har ya kammala shirin barcinsa zai kwanta zuciyarsa taƙi bashi haɗin kan
hakan. Fuska ya ɗan yamutse kai kace bashi da ra'ayin abinda zuciyar tasa ke so.
Sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci tsabar miskilanci ke cinsa da ƙasaitar mulki.
Cike da izzar dake bayyana takunsa a matsayinsa ya nufi ɗakin. A hankali ya tura
ƙofan ya shiga bakinsa da sallama ƙasa-ƙasa. Kallon mamaki yake mata ganinta naɗe a
cikin bargo, ga alamar ɗan rawa-rawa da jikinta ke mata da yake gani. Hannu ya kai
ya ɗan janye bargon daga saman fuskarta. Aiko ta wani zabura, caraf ta damƙe
hannunsa idanunta rufe ruf da alamar tana cikin mayen barcin dai bakinta na motsi
cikin faɗa-faɗa take faɗin abinda baya ji.
(Fitinatu har a cikin barcin ma ba'a kadata) ya faɗa a zuciyarsa yana lumshe
ido da riƙota ganin da gaske fa faɗan take ga zafin hanunta dake kan nasa na ratsa
fatar shi. Jikinta rawa yake sosai, dan mafarkin da tai ya matuƙar firgitata, ta
daɗe batai irin mafarkan nan ba. Da farko mamakin yanda take ɗinne ya shiga, sai
dai ganin abinfa na gaske ne sai hankalinsa ya tashi. Amma bazaka taɓa tantancewa
ba a face ɗin sa. Kaɗan ya girgizata muryarsa a ƙasan maƙoshi ya furta “K!”.
Ina batama san yanai ba, sai ƙoƙarin fisge jikinta da take kamar dai yanayin
da takan shiga a duk lokacin da tai irin mafarkan. Jikinsa ya jawota sosai yana ɗan
bubbuga fuskarta kaɗan-kaɗan, sai kuma ya sake faɗin, “Open your eyes. Iffah k!”.
Karan farko daya taɓa ambatar sunanta, duk da bata a hayyacinta sai da taji
fitar sautin sunan. Buɗe idanun tai a hankali jikinta na ɗan tsuma ta sauke a
kansa, sai kuma taja nannauyan numfashi tana ɗan ƙara warosu domin tabbatar da shi
ɗinne a zahiri ko har yanzu a mafarkin ne dai. A hankali ya mannata da ƙirjinsa ya
rungume. Wani ajiyar zuciya ta sake ja mai ƴar shashshekar data saka tsigar jikinsa
tashi. Sai kuma ta maida idanunta ta lumshe sannu a hankali ganin yanda ya tsareta
da kaifafan nasa idanun. Lafewa tai a jikin nasa kamar wata mage, dan kanta ciwo
yake matuƙa. Ba ƙaramin dauriya yay ba na zamanta jikinsa har tsahon mintuna uku,
cikin son danne yanayin da ke neman halaka shi ya buɗe idanunsa da suka canja kala
akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Wani irin kallo yake binta da shi tun daga fuskarta har
zuwa ƙafafunta, gaba ɗayanta naɗe take a jikinsa. Yanda ta naɗe ɗin ya bama
abayarta mai sanyi damar lafewa a jikin nata ya fidda mata suranta da ƙyau. A
kasalance ya lumshe idanunsa yana kauda kansa jin numfashinsa na wata rawa-rawa. Ga
ɗumin jikinta na matuƙar ratsa nasa jikin.
“What happend?”.
Ya faɗa a cikin kunenta da wata irin shaƙaƙƙiyar murya da bata taɓa ji da ga
garesa ba, gata acan ƙasan maƙoshi matuƙa. Yanda sautin ya ratsa kunenta har cikin
ɓargonta da ƙwaƙwalwar ta ya sata rumtse idanunta da masifar ƙarfi tana wani
ƙanƙamesa. Ihu kawai ya rage ya sakar mata ko zata gane a wane riski ta jefashi,
amma sai ya danne cike da jarumta ya furzar da boyayyan huci. Cikin sigar tambaya
ya sake faɗin, “Uhhuyim?”.
Nan ma kamar bazata amsa ba sai kuma ta nisa tana sauke ajiyar zuciya. Kanta ta
ɗan girgiza a hankali ta ce, “Mafarki”.
“Mafarki?”.
Ya maimaita akan lips ɗinsa yana ƙoƙarin saka idanunsa cikin nata kasancewar ta
ɗago da ga jikin nasa. Kanta ta gyaɗa masa tana ɗan kauda idonta, dan tun abinda ya
faru ɗazu a tsakaninsu sai ta tsinci kanta da jin matsananciyar kunyarsa. Yanzun ma
dan kawai tana a firgice ne. Kamar zai ƙara magana sai kuma ya share, murya a shaƙe
mai tabbatar da ya gaji da magana ya motsa lips ɗinsa a nutse kamar a fisge, “Kinyi
salla?”.
Kanta ta ke girgiza masa batare da ta yarda ta kallesan ba yanzu ma. Komai
bai sake cewa ba ya miƙe kawai, kamar wanda ke'a yanayin sanyi jiki ya nufi hanyar
bathroom. Da kallo ta bisa ƙasa-ƙasa, mummunan mafarkin da tayi a kansa na dawo
mata. (Mafarki ba gaskiya ba ne) zuciyarta ta ayyana mata, hakan ya sata sauke
ajiyar zuciya ta zame ta kwanta jin sanyi na ratsa mata gaɓoɓi. Bai wani jima sosai
ba ya fito, bargon data rufa ya kama ya yaye, tai saurin riƙowa tana ɓata fuska da
turo masa baki. “Ni dai sanyi nake ji”. Ido kawai ya tsirama lips ɗin nata batare
da ya iya cewa komai ba, kafin ya ranƙwafa a kanta slowly ya ɗauke ta cak ɗinta
cikin hannayensa. Ba ƙaramin waro masa manyan idanunta tai ba. Ya ɗan harareta yana
kauda nasa. Itama kauda natan tai tana kumbura bakin gaba sosai.
(Stubborn girl) ya faɗa a ransa, a zahiri kam fuskar ya sake tsukewa da kyau
kai kace da ɗa duniya bai san miye murmushi ba. Yana direta yay fitowansa abinsa.
Binsa tai da kallo, abubuwa masu yawa na mata yawo a zuciya game da shi....

Da ƙyar ta iya bin bango ta fito bayan idar da alwalar, yana zaune a cikin
kujerar idonsa kan television ɗin ɗakin. Kaɗan ya ɗaga idanunsa ya kalleta ta ƙasa-
ƙasa. Duk da yaga yanda take layi tsabar baƙin hali da ƙasaitar mulki ya hanashi
tashi ya sake taimaka mata. Harta ƙaraso inda ya shimfiɗa sallayar kamar bai ma san
da fitowarta ba. Kallonsa ta sata ta kauda kanta, sai kuma hakan da yay mata ya
ƙona mata rai. Cikin jin haushi-haushinsa ta ɗan ƙarfafa kanta, gyalen daya ajiye
mata ta ɗauka ta naɗa a kanta, kasancewar abayar jikinta babu ta inda ta tawaya ta
kabbara sallarta cike da nutsuwar da ke tabbatar da ta samu wadataccen ilimin
addini. Shi kansa yanda take sallar a nutsu duk da wani lokacin jiri kanyi kamar
zai kadata sai yaji wata nutsuwa ta ratsashi. Wani kimar iyayenta da sake ganin
darajarsu na mamaye sa. A zahiri kam bama zaka taɓa ɗauka hankalinsa a kanta yake
ba. Fuskar nan tai ciɗin-ciɗin ko ɗan yankar kanun mutane sai haka😏.
Tana idarwa ta zame a wajen ta kwanta hanunta dafe da kanta dake
matsanancin sara mata, zuwa can kamar wadda aka zabura ta miƙe zumbur hanunta a
baki, sai kuma ta nufi bathroom da ɗan gudu-gudu alamar amai.
“OMG!”.
Ya faɗa a hankali ƙasan maƙoshinsa jin tana kakarin amai. Bai motsa ba duk da
yanda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri, kusan mintuna biyu da wasu sakanni sai
gata ta sake fitowa tana layi. Ga hawaye shaɓe-shaɓe a fuskar gwanin ban tausayi.
Yanzu kam miƙewa yay da ƙyar ya nufeta, kamar jira dai-dai yana isowa gab da ita
tai wani luuuu zatai baya ya tareta cikin zafin nama ta faɗo cikin hannunsa..
A hankali ta dinga jan ajiyar zuciya jin bata faɗin ba. Sai dai ta kasa
buɗe idanunta da ke rufe ruf duk da tanajin alamun nasa kamar na binta da kallo.
Kallon nata kuwa yake cike da kasala, sai kuma ya ɗan lumshe nasa idanun shima yana
sake rungumota da ƙyau har yana jin saukar numfashinta a jikinsa. Yanda nunfashinta
ke saukar masa a jiki sai yake jin tamkar shima hajijiyar na neman kwasarsa, gudun
kar ai abin kunya ya ɗagata cak ya ajiye a saman gadon. Kafin ya zauna a kusa da
ita yana mai tsura mata fararen idanunsa. Sun kai kusan mintuna biyu a haka, kafin
ya katse shirun ɗakin ta hanyar motsa lips ɗinsa a hankali ya furta,
“What again?”.
Kanta ta nuna masa da gyar ta furta. “Kaina kamar zai fashe”. Sai ga hawaye
sharr. Ita kanta bata san miyasa take jin karaya ba a gabansa ko ma shagwaɓa ne
oho. Idanunsa ya zuba mata kawai yana bin hawayen da ke bin ƙyaƙyƙyawar fuskarta da
gudu-gudu da kallo. Haka kawai sai yaji murmushi na suɓuce masa. Kansa ya kauda
gefe yay murmushin sannan ya ɗan sake matsawa kusa da kan nata sosai. Numfashi ta
ɗan ja a sanyaye jin saukar lallausan tafin hannunsa saman goshinta. Shi kansa
yanda zafin kan ya ratsa hanun nasa sai da ya ɗan lumshe ido. Murya can ƙasan
maƙoshi ya ce, “Ta nan ne?”. Kanta ta ɗan jinjina masa, sai kuma ta ɗaura nata
hannun saman nasa ta ɗan matsar zuwa gefen kunenta idanunta na sake kawo ƙwalla ta
ce, “Harda nan da ma duka”. A yanda tai maganar cikin shagwaɓa kamar wata ƴar baby
yaji tsigar jikinsa na wani yamutsawa. Amma jarumin naku sai yay ƙoƙarin basarwa
har da yamutsa fuska kaɗan ya furta, “K raguwa ne ko? Just ciwon kai ki ke ma
kuka?”. Kamar ya tunzurata ta sake turo masa baki da son ture hannunsa da ke kanta.
Ko gezau, dan haka tai yunƙurin juyawa. Nan ma sai da ya nema sakin murmushi amma
ya fuske. Cikin wata murya da mai lura zai iya fahimtar shauƙin da yanayin da suke
cikin ke bashi ya ɗan matso da jikinsa gab-gab da nata yana faɗin, “Kin cika
ragwantaka ne ai. Na miki addu'a?”. Kamar zata sakar masa kuka ta ɗaga kan dan da
gaske kan na mata ciwo ne sosai.
Shiru bai sake magana ba ya kamota, kan nata ya ɗaura saman jikinsa.
Sannan ya sake maida hanunsa saman goshin yana ɗan murza mata sannu a hankali yana
mata addu'an. Idanun ta dinga lumshewa sannu-sannu itama, batare data farga ba
barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Bai daina addu'an da murza mata goshin ba,
sai ma wani mayataccen kallo da yake mata idanunsa a shanye. Ya kwashe tsahon
lokacin da bai fargaba a wajen zaune, dan tun kan da zafi har ya fara hucewa. Inda
wani yace masa hakan zata faru tsakaninsa da wata ɗiya mace zai ƙaryata. Sai dai
shi lissafin ƙaddara bai damu da wanda zai lissafa maka ba komai taka tsantsan ɗin
ka akan nisanta kai ga abu.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_


_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,
INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (22)


........Komai ya ƙara kwaɓema ta-ƙurya, ta rasa wace hanya ya kamata tabi dan ganin
wannan aure ya ƙullu tsakanin Shahan-shan da yarinyar da sai a yau ta saka
amintaccen bawanta bincike a kanta. A ɗan gefen ga jami'an gidan sun mugun duƙufa
domin gano wanda yay tsaurin idon ɗaukar Zawjata-almilk daga kurkuku zuwa cikin
pool har da kashe jami'an dake tsaronta. Da zafi-zafi suke aiki a wannan yini dan
Tajwar Eshaan ya basu kwana biyu ne kacal. Sunko duƙufan matuƙa, domin umarnin mai
gayya mai aiki ba abin wasa bane a garesu.
Tasan amintaccen hadimin nata shi a karan kansa bai san ita ɗin wacece ba,
dan bayan muryar da take masa magana da ita a duk sanda zata sakashi aiki babu
abinda ya sani tattare da ita kuma. To ko muryar ma ai bada tata ta ainahi take
masa maganar ba. Sai dai duk da wannan tsaron data tabbatar tana da shi bata kasa
jin wani ɓurɓushin damuwa ba a ƙasan ranta game da tsananta binciken. Ga Uwa tai
mata alƙawarin bazata taimaketa da komai ba a wannan gaɓar, acewarta shine
hukuncinta. Ta tsani yarinyar nan, tsana irin wanda batajin ta taɓa yima wani
mahaluki irinta a rayuwa. Bata taɓa fuskantar tangarɗa a aikinta ba sai da yarinyar
ta shigo rayuwarta. Matsala bata taɓa shiga a aikinta ba sai da yarinyar ta shigo
masarautar. Tabi hanyoyi da yawa domin ganin bayanta amma ko gezau. Ta rasa wane
kalar shegen taurin kai yarinyar ke da shi. Ita zuciyarta ta fara bata ma anya
yarinyar ba shugabar wata ƙungiyar asiri bace mai zaman kanta? Dan abubuwan da ke
faruwa a kanta sun fara bata tsoro. Sai dai taci alwashin kota halin ƙaƙa ne sai ta
shafe babin rayuwar yarinyar da kaf zuri'arta a duniya nan bada jimawa ba. Wannan
alkawarin ta ne......

(Ni dai nace hummmm).

★★.... ★★....

Fuska cike da murmushi yake duban kayan surkullen da boka Barbushi ya basu.
Cikin ƴar dariya-dariya ya dubi Miran Arshaan da shima a kallo ɗaya zaka fahimci
nasa nishaɗin. “Idan ya isa shi hatsabibi ne a wannan karon ya tsallake mana, ai
idan yasan wata bai san wata ba damu yake labarin da ga shi har ƴar iskar yarinyar
tashi”.
Ƴar dariyar shima Miran Arshaan ɗin yayi, cike da nishaɗi ya ce, “Sai dai
uwarsa Bushirat kuwa ta haifi wani amma ba madadinsa ba. Tunda taƙamarsa taurin rai
sai mu bisa ta hanyar da zai laushi ta dolen dole da ƙaniyarsa. Shegen yaro kamar
jinin aljanu da ga shi har ƴar ƙaniyar yarinyar”.
“Kona ifiritai ne wannan karon dai tasu ta ƙare. Dan haka a daren nan na
yau zamu saka komai a inda ya dace kamar yanda Barbushi ya bada umarni. Dan ubansu
badai sunƙi mutuwa ta sauƙi ba, to ga rayuwar yayita sai dai a cikin ƙunci da baƙin
ciki da ga shi har duk wani mai iya jin zai bashi kariyar.”
Dariya suka sheƙe da ita har da tafawa kamar wasu abokai. Kafin su miƙe cikin
ɓadda kamar da suka gama shiryawa suka nufi fada yanda boka Barbushi ya basu
umarni.....

★★... ★★....

Kamar yanda ta saba farkawa akan lokaci domin gudanar da sallar asubahi yau
ma bata makara ba. Sai dai saɓanin ko yaushe yau a firgice ta farka. Da sauri-sauri
ta ke karanto addu'ar tashi da ga barci tana faman waige-waige a ɗakin mummunan
mafarkin da tai a daren jiya da ya sake maimaita kansa gareta yanzu na sake dawo
mata. Sosai take jin zuciyarta na tsitstsinkewa, dole taja jikinta ta maƙure kanta
a fuskar gadon tana mai naɗe jikinta da son riƙe rawar da yake yi bakinta na
ambaton sunan ALLAH kamar yanda kaka ya horeta da daina ihu a duk sanda tai mafarki
makamantan hakan saɓanin da da take ihun. Ta ɗauka tsahon mintuna shida kafin ta
ɗan samu nutsuwa. Sai ajiyar zuciya da take faman saki a jajjere. Da alama ita ɗaya
ta kwana a ɗakin batare da tasan sanda ya fice ba. Hanunta ta kai saman goshinta da
zuwa yanzu Alhamdullah babu matsanancin ciwon kan nan data kwanta da shi. Sai ma
ɗan sanyi-sanyi da damshin zufar data haɗa ya haddasa mata. Janyewa ta sake yi tana
mai lumshe idanunta, haka kawai take jinta wata daban a yau kamar ba Iffahn Babiy
da Ummu ba. Ko miye dalilin jin hakan bata sani ba. Kabbara salla da aka farayi ya
sata miƙewa zumbur tana ture komai gefe. Gaba ɗaya jikinta babu ƙarfi, ga mafarkin
da tai ya sake nunar mata da gaɓɓan jikin baki ɗaya. Haka dai ta ɗan watsa ruwa mai
ɗumi ko zai saki sannan tayo alwala ta fito. Bayan ta gabatar da salla maimakon ta
koma ta kwanta sai tai zaman karatun Alkur'ani ko zata samu nauyin da zuciyarta ta
mata na kwana biyu ya ɗan rage...

★ Saɓanin ita shi ko rintsawar ma baiyi ba gaba ɗaya. Dan tun bayan
barowarsa ɗakin da take yana zaune ne gaban laptop yana aikin da shi ya barma kansa
sani. Har kusan uku yana zaune kafin ya tattara ya ajiye ya ɗauro alwala. Bai tashi
a sallayar ba sai lokacin asubahi da zai wuce masallaci. A maimakon Gym da ya saba
shiga ko yin wasan takobi a wasu ranakun sai ya nufi sashen Malikat Bushirat ta
sirrintacciyar ƙofar dake kaisa sashen batare da kowa ya gansa ba idan yaso hakan.
Jin nutsatstsiyar muryarsa nayin sallama a can ƙasan maƙoshi Jasrah da Malikat
Bushirat suka dubi juna a yanayin mamaki. Cikin rashin aminta da abinda suka jin
Malikat Bushirat ta bada umarnin shigowa. A maimakonsa shi ɗinne kuwa. Shi kam
baiyi wani mamakin ganinsu taren ba duk da a yanzu aka idar da salla, dan yasan
ɗunbin shaƙuwar dake tsakaninsu ta dabance. Maimakon zama a cikin kujera a hankali
ya kai zaune kusa da Malikat Bushirat dake zaune kan sallaya har yanzun. Dan tana
idar da salla Jasrah ta shigo mata. Gab-gab da ita yake zaune yana mai tanƙwashe
ƙafafunsa tare da ɗaura kansa a kafaɗarta. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana
lumshe idanunsa.
Malikat Bushirat da ke kallonsa cike da tausayawa sanin in har ta gansa a
yanayin nan yana cikin damuwa ta kai hanunta kan tattausar sumarsa yalwatacciya ta
shafa a hankali. Nan ma ajiyar zuciyar ya ɗan ƙara saukewa. Kafin ya motsa lips
ɗinsa kaɗan ya furta “Barka da asuba ya Ammie-na”.
“Ka tashi lafiya Saiful-malik”.
Ta amsashi da kulawa tana sake tura yatsunta cikin sumar kansa a hankali. Kai
kawai ya ɗan gyaɗa mata, sai kuma batare da ya dubi Jasrah da ke kallonsa ba ya ce,
“Aunt good morning”. Murmushi ta saki jin yau kuma ita ake gaidawa. Itama ta
amsashi da kulawa tana tasowa da ga inda take ta dawo ta ɗayan gefen Malikat
Bushirat suka sakata tsakkiya ita da shi. Idanunsa ya ɗan buɗe kaɗan ya mata
hararar wasa, a zahiri kam babu alamar ko murmushi a fuskarsa. Cikin fisgo maganar
tasa da kamar an masa tilas yace, “Ammie kice ta tafi ta barni, ita kullum tana
nane da ke tai auren ma baki huta ba”. Wani sassanyan murmushi Malikat Bushirat ta
saki, dan yanda yay ɗin sai ya tuna mata da ƙuruciyarsa lokacin idan sunje dubashi
harda Jasrah. Yata mita kenan Jasrah ta tafi tunda ita tana ganinta kullum har sai
mahaifinsa ya shiga lallashinsa yake haƙura. Ita kanta Jasrah sai komai yake dawo
mata, fuska ɗauke da murmushi tace, “Nikam babu inda zanje, sai dai kai ka koma
inda ka fito ka barni da mamata”. Fuska ya ɗan kauda gefe yana sake tsuketa, amma
baice komai ba. Ita kuma Jasrah ta cigaba da ɗan tsokanarsa kamar yanda takeyi a
baya Malikat Bushirat na karesa tana musu dariya. Shi dai da ya fara takalo wasan
bai sake ce musu ko kanzil ba.
Bayan wasu ƴan mintuna Malikat Bushirat taci serious tana maida dukkan
hankalinta kansa. Murya cike da kulawa ta ce, “Baka da lafiya ne?”. Kai ya juya
mata alamar a'a. Sai kuma ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta “Ina missing ɗinki ne
my first luv”. Ji tai wani daɗi na ratsata, kanta na sake kumbura da alfaharin
kasancewarta mahaifiya ga wannan ƙasaitaccen bajimin ƙyaƙyƙyawan sarkin. Ta sake
shafa fuskarsa da kulawa matuƙa. “ALLAH yay maka albarka, ya cigaba da kulamin da
kai da baka kariya”.
“Amin”.
Ya furta a saman lips, Jasrah kam a zahiri tana murmushi. Idanunsa ya maida kan
Jasrah, fuskarsa babu alamar wasa ya furta “Mi kikeyi anan da safen nan kika bar
mijinki?”.
Murmushi ta masa ganin a serious yay maganar babu wasa a ciki. Tana ɗan wasa
da yatsunta dan bazata iya kallonsa ba tai maganar dake bakinta duk da a shekaru
itace sama da shi, sai dai ALLAH ya kwace girman ya bashi matsayinsa na namiji kuma
sarkinta, a hankali ta ce, “Maganace mai muhimmanci ta kawoni”. Ta ƙare maganar
tana ɗan ɗagowa ta dubi Malikat Bushirat. Shima kallonsa ya maida ga Ammien tasa.
Malikat Bushirat ta sauke sassanyar ajiyar zuciya tana ɗan shafa kansa, “Magana ce
muhimmiya Jasrah tazo da ita a kanka Saiful-malik”.
Kaifafan idanunsa ya ɗan tsura ma Jasrahn ganin yaƙi yarda ta kallesa ya
janye su ya sake maidawa ga Ammien sa. “Wani abu ya faru ne?”.
Kai Malikat Bushirat ta girgiza masa, “Komai bai faruba, na baya ne dai
da suka faru musamman akan abinda yarinyar nan ta aikata. Ba kowa ne zai fahimci
irin abin da naji ba a lokacin da na fahimci zan iya rasa tilon ɗan dana mallaka a
duniya. Amma sai na danne zuciyata wajen maida hankali na maka addu'ar samun lafiya
fiye da ɗaukar mataki. Bani da jayayya akan hukuncinka, sai dai ƴar uwata tazo da
shawarar dana gamsu da ita nima”........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA


09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (23)

.......Kansa dake a kafaɗarta ya ɗago a hankali jin yanda take maganar a serious,
sai dai baice komai ba. Itama batare data kallesa ba ta cigaba da faɗin, “A nawa
ra'ayin ka rabu da yarinyar nan, sai dai bazan tirsasaka kan hakan ba zan jira har
lokacin da za'a yanke mata hukunci bisa abinda ta aikata. Amma kamar yanda Jasrah
ta faɗa ya kamata ka ƙara aure. Ina son ka samu farin ciki kaima kamar kowane
namiji mai irin shekarunka. Ina son naga zuri'arka Eshaan. Na kuma shirya fito-na-
fito da duk mai son daƙile waɗan nan zaren farin cikin namu ta hanyar kashe yaran
da basu ji ba basu gani ba dan kawai kasancewarsu matanka. Nima a wannan karon na
shirya, na shirya tarar kowa Eshaan...”
Kuka mai tsuma zuciya ya sarƙe ta. Har cikin ransa yake jin kukan nata, sai dai
babu alamar zaice wani abu. Jasrah da itama ke hawayen ta miƙe a hankali zuwa
gabansa, zama tai ta kamo hanunsa cikin nata cike da kulawa ta kira sunansa. Ɗagowa
yay a hankali ya zuba mata idanunsa da baka isa gane yanayin da yake ciki ba koda a
cikinsu. Hawayen da ke cigaba da zubo mata ta share tana ɗan kauda idanunta zuwa
ƙasa, dan kaifin nasa sun mata yawa. “Kayi haƙuri ka fahimcemu Abni, muna tsananin
jin zafin abubuwan da ke faruwa da gaba ɗaya sun ta'allaka da kai ne matsayinka na
shugaba sama da kowa na ƙasar nan. Lokaci yayi da zamu tashi yin fito na fito da
kowa a wannan gaɓar. Ba zai yiwu mu cigaba da zuba ido ba kuma. Kafin yau mun
tattara hope ɗin mu gaba ɗaya kan yarinyar nan, amma daga ƙarshe itama tai shirin
halaka ka ma. Shiyyasa nai tunanin ya kamata a nema maka wata matar dan nasan kai
dai baka da wannan lokacin, mu kuma Insha ALLAHU zamuyi duk shirin da ya dace don
ganin mun kamo bakin zaren. Fatanmu mu dai kawai amincewar ka, dan wannan al'amarin
baya buƙatar cigaba da zuba idanu kuma”.
Uffan bashi da alamar cewa, bai kuma canja da ga kallon da yake musu ba a
zahiri. Suma sai duk sukai shiru, dan sun san halinsa sarai....

★★....

Bayan barowarsa daga sashen Malikat Bushirat ƙayataccen Gym ɗinsa mai ɗauke
da nau'ikan machines na zamani ya nufa. Tuni hadimai masu tsaron wajen suka zube
kan gwiyawunsu suna miƙa gaisuwa. Idanunsa kawai ya lumshe yay shigewarsa batare da
yako kallesu ba. Da alama dai yau ƴan mulki ne bisa kai da miskilancin, ko kuwa
maganar da yay da su Ammien tasa ne ke tsikarar masa rai oho dai. Sosai Gym ɗin ya
ƙayatu ga mai kallo, dan hatta kaya motsa jikin an musu wadrube ne na musamman gasu
nan iri-iri. Tattausar jallabiyar jikinsa ya cire ya ajiye, sannan ya fiddo set
ɗaya na kayan ya ɗauka dogon wandon kawai ya saka. Sosai mutum ne buɗaɗɗe da baka
gane hakan kai tsaye idan baya cikin riga. Cikin zafi-zafin da ke nuna kamar yana
cikin fushi ya fara sarrafa machine ɗin gudun idanunsa a rufe ruf. Ya kwashe tsawon
lokaci yanayi dan sai da yay sharkaf da zufa kafin ya kashe ya koma wajen ɗaga
ƙananan ƙarfe irin na riƙewa a hannun nan ko kana daga zaune zaka ɗaga, duk da dai
a zahiri kallon kitse akema rogo suna da matuƙar nauyi. Nan ma kusan mintuna goma
sha biyar ya ajiye ya koma ɗaga ainahin ƙarfe daga kwance rigingine. Haka ya dinga
caccanjawa har ya shafe tsahon awa biyu da wasu mintuna a ciki. Kafin yaja rigar
wandon ya saka tare da ɗaukar goran ruwa ya kwankwaɗa yana sauke numfashi, dan shi
ɗaya ke zuwa nan kawai bayan hadiman dake tsaren wajen. Ko amintaccen hadiminsa
baya zuwa da shi.
Kamar yanda aka saba ya samu shayinsa na ƙa'ida a ɗakin da ya kwana, dan
masu aikin girka abincinsa sun cigaba da aikinsu tare da amintacen hadiminsa. Zaman
shan shayin yay yana mai shaƙar daddaɗan kamshin da ɗakin keyi na gyaran da ya sha
harya kammala. Da ga haka ya nufi bayi tsaftace jikinsa. Ya kwashe lokaci mai tsayi
anan ma kafin ya fito ya shige inda kayansa suke domin shiryawa.

Masha ALLAH na ambata lokacin da yake fitowa cikin wata irin shiga ta
alfarma. Ga wani ni'imtaccen ƙamshi na musamman da ya sake gauraye ɗakin cikin
ƙanƙanin lokaci. Dubansa ya kai ga agogon ɗakin yana ɗan ɓata fuska. Yana da
buƙatar zuwa ya duba yaya ta kwana. Ga shi kuma ya makara, dan yanada shari'ar da
zai gudanar a fada yau. Batare da ya yanke hukuncin abinda ya dace yay ba ya fito
cike da takun nan nasa na izza da ƙasaita tamkar mai tafiya a saman iska tsabar
yanda yake wani ɗaga ƙafafun da sauke su a nutse. Fuskar nan tsam babu alamar yama
san minene yaran murmushi. Har ya nufi hanyar da zata sada shi kai tsaye da falo ya
ɗan dakata, gajeren tsaki ya ja da juyowa sannu a hankali ya doshi ɗakin da Iffah
ta kwana.
Ƙamshinsa da sautin takun sawayensa da ke alamta isowarsa waje ya sata ɗan
ɗago idanunta ta zubama ƙofar, sai kuma ta kauda da sauri ta cigaba da tsamar
dabinon da aka zuba cikin zuma a wani ɗan farin bowl da ke a cinyarta. Kamar yanda
yay sallamarsa ciki-ciki haka itama ta amsa masa can ƙasan maƙoshi batare da ta
motsa da ga yanda take ba har ya iso tsakkiyar ɗakin.
“Barka da safiya”.
Ta faɗa kanta tsaye batare da ta ɗago ta kallesa ba, duk da kuwa tana matuƙar
buƙatar hakan amma ta kwaɓi kanta. Maimakon amsa gaisuwar da tai masa sai ya jeho
mata tambaya a bazata yana wani shanye idanunsa da ke binta da kallon ƙurilla.
“Kina jin wani ciwon ne a yanzu?”.
Idanunta ta ɗago sannu a hankali ta zubasu a kansa karo na farko. Gabanta yay
wata irin mummunar faɗuwa ganin exactly kayan da tai mafarki da shi dai sune a
jikinsa daren jiya da asubahin yau ne dai abin kamar wani almara. Sai dai kwarjinsa
da wata barazanar cikar haiba ta cika mata idanun. Babu shiri ta maida nata ta
rissinar zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Amma a zahiri ta wani sake
tsuke fuskar ne kamar yanda tashi ke'a tsuke. Kanta ta girgiza masa maimakon amsa
masa da baki.
Sosai fitinar yarinyar nan ke bashi mamaki, a fuska bazaka taɓa tunanin
halayyarta ba, dan tanada suffar mutane masu sanyin hali da rashin son yawan magana
ma, sai dai inta buɗe baki ko kanari albarka ya kada ita. Rigimarta ta musamman ce
sama da duk ta wani rigimamme da ya sani a tsayin rayuwarsa. Lips ɗinsa ya ɗan laɓe
cike da sake tsuke fuska magana can ƙasan maƙoshi a fisge ya furta, “Akwai phone a
side drawer, zaki iya magana da Mammy game da abubuwan buƙatarki, idan kuma zaki
online shopping ne da kanki fine. Da akwai card tare da ita” ya ƙare maganar yana
ɗan matsawa ga table ɗin dake ɗauke da takardun da bata san na minene ba ya ɗauka
pen. Ɗan rubutu yay a takarda ya tako har gabanta ya ajiye batare da ya sake cewa
komai ba ya juya zai bar ɗakin.
“Jazakallahu khairan”.
Ta faɗa a hankali, lumshe idanu yay batare da yace komai ba ya cigaba da
tafiyarsa. Kamar wadda aka tsikara ta miƙe zumbur. Kaɗan ya rage tai tuntuɓe da
lallausan carpet ɗin gaban gadon ALLAH dai ya bata sa'ar tsallakewa ta cimmasa.
Yana ƙoƙarin ɗaura hannunsa kan handle ɗin ƙofar sai ganinta yay a gabansa kamar
wata aljana. Mar-mar ta ɗan yi da idanunta tana motsa pink lips ɗinta a marairaice.
“Indai fita ta wuce iya nan sashenka ka haƙura kar kayi Pleaseee”.
Idanunsa ya tsura mata da wani irin kallo da ta kasa bama fassara, dole ta
risinar da nata tana ɗan wasa da bazar veil ɗin abayar jikinta da tai mata matuƙar
ƙyau kasancewar blue black. Itama dai tashi tai kawai ta ganta bata san daga ina
ba, amma tasan dai shine ya ajiye kamar yanda ya ajiye mata jiya. Idanun ya sauke a
hankali kan hanun nata fari tas da babu wani datti a ƙunbunan suma. Kamar bazai ce
komai ba sai kuma ya sake maida idanunsa kan fuskarta a fisge ya furta, “Akan wane
dalili?”.
Baki ta ɗan turo kaɗan, ta ce, “Kawai”.
“Kawai?”.
Ya maimaita a sigar tambaya da wata irin muryar jinjina wautar ta. Kallonta
ya cigaba da yi cike da nazari.. Tsintar kanta tai da jin ƙafafunta na rawa, dan
idanunsa kaifafa da ya tsareta da su ji take suna sagar da ɗan sauran ƙwarin gwiwar
tata. A hankali ta motsa da nufin barin wajen ya tareta da hannunsa. A marairaice
ta ɗago tana dubansa kamar zata fasa kuka, sai kuma ta sake maida idanun ta risinar
tana ɗan ƙara tura baki dan yaƙi daina kallon nata..
Idanun ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kanta, a wata irin ƙaramar muryar da
inba kusa da su kake bazaka taɓa sanin yana magana ba ya ce, “Kin san a gaban wa
kike kuwa?”.......✍️

_😂Da alama ta manta Shahan-shan, sai ka tuna mata fa🏃🏃🏃🥱._

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_


_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,
INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (24)


........Kasa daurewa tai sai da ta ɗago ido ta ɗan kallesa, babu shiri ta sake
maidawa da sauri. Amma gudun kar yaga gazawar tata sai cewa tai, “Tajwar Eshaan Ibn
Haysam Abdul-majeed. Shahan-shan ɗin ƙasar ruman mana”. Ta bashi amsa tana ƙwaɓe
fuska babu ko gargada a harshenta balle muryarta.. Mutuwar tsaye yay na mamaki, ya
lumshe idanunsa a hankali, shi yau shi Eshaan ƙaramar yarinyar nan ke ambaton
sunansa babu ko gargada a harshenta ko nuna shakkarsa balle akai ga tsoro a gabansa
ido cikin ido. Abune da bai taɓa jinsa ba sai a bakin mahaifiyarsa ko kakarsa. Suma
ɗin akan jima baiji sun ambata ɗin ba. (Kai wannan yarinya zata halaka shi)
“Kada fa kace nayi rashin kunya kasa a ɓatar da ni ban gama cika burina ba,
tunda ai dai kai ka tambayeni ko”. Ta faɗa tana mai langaɓar da kai idanunta na ɗan
cikowa da ƙwalla na shagwaɓa da katse masa tunani da muryar nan tata mai ingiza
bugun zuciyarsa kamar tasan mi yake tunani.
Komai baice mata ba, duk da yanda take kallonsa a kaikaice. Ya dai ɗan matsa
gabanta yana cigaba da kallon ta kawai har tsawon wasu mintuna yanda tai kamar wata
ƴar baby na bashi dariya a ƙasan zuciya. Sai kuma ya janye tare da ɗan matsawa da
ga jikin nata da ya matso a zahiri babu ma alamar yasan minene murmushi. Aiko sai
gata tana jan ajiyar zuciya. Basarwa yay kamar baijita ba.
“Miye burin naki?”.
Kalmar ta fito da ga harshensa a ɗan fisge tamkar wanda akaima dole. Batare da
ta yarda ta kallesa ba ta ce, “Suna da yawa, muhimmai a cikinsu dai yanzu duk sun
shafeka”.
Wani kallo da ke nuna alamar ni ɗin yay mata. Tako ɗaga masa kanta idanunta
na ɗan cikowa da hawaye tana ƙiƙƙifatasu. A raunane kamar ba ita ba ta ce, “Ina son
sanin halin da Iyayena ke ciki duk da an sanar min ka halaka su. Ina son sanin
wanene Ajmaal?. Ina son idasa tabbatar da masu fuska biyun daular ruman wa duniya
koda ni bazan iya wanke kaina ga kowa ba”.
Yanda yake kallonta kamar wata sabuwar halitta sai ka ɗauka idanun nasa sun
kafe ne a kanta. A hankali ya ɗaga kafarsa yay ɗan taku ɗaya zuwa uku, a gabanta ya
dakata gab-gab kamar zai haɗe jikinsu. Sai dai kuma baiyi hakan ba ya ɗan bar
tazarar da bata wuce tsahon yatsa manuniya ba. Da sauri-sauri ƙirjinta ya hau
dokawa ganin ya mata runfa, dan duk da kasancewar ta mai ɗan tsayi a gabansa ba
komai bace duk da shima ba wani dogo bane na bala'i can, sai dai kuma dole a kira
shi da dogon. Kamar yanda yake duban cikin idanunta haka itama ta ke dubansa, sai
dai nata cike suke da ƙwalla ga tsumar da jikinta keyi ta kasa janyewa. Hannunsa ya
dogare jikin lafiyayyar ƙofar mai tsananin ɗaukar ido, sai hakan ya sake bashi
damar rufeta ruf har tana jin shaƙar numfashi ma na neman mata wahala tsabar yanda
kwarjininsa ya cika mata ko'ina, har ji take kamar ma ɗakin ya musu kaɗanne.
Rasa abin cewa ya sashi ɗaura yatsunsa biyu kan haɓarta ya ɗago fuskarta da
ƙyau suna kallon juna, nasa ya sake lumshewa da sake buɗe wa a cikin natan cikin
wani irin yanayi mai wahalar fassara ya furta.
“Bayan kin cika waɗan nan sai me kuma?”.
Yanda yay maganar yana mai sake sarƙe kaifafan idanun nasa cikin nata da ke tara
ƙwallar da bata san dalili ba ya sata shiga jujjuya masa kanta a hankali idanunta
na sake cikowa da ƙwalla dan jin kusancin nasu take kamar wani dabaibayi da ya fi
ma zamanta a kurkuku. Lips ɗinta ta motsa a hankali, cikin raɗa-raɗa muryarta na
ɗan rawa ta furta, “Yi maka hukunci akan laifukanka”.
Da ƙyar ya iya haɗiye murmushin da ke ƙoƙarin yinƙuro masa. Sake matsar da
fuskar tasa yay gab-gab da tata, hakan sai ya sake hauhawar bugun zuciyarta har
yana iya jiyo yanda nunfashinta ke fita a sarƙe. Amma sai ya fuske abunsa ya cigaba
da jujjuya nasa ƙwayoyin idon a nata cike da wani irin salon da ke neman fallasa
sirrin da yake faman dannewa a ƙasan zuciyarsa.
“Bayan hukuncin da kikai min na son kasheni duk bai isa ba *_Niazmina_*?”.
Idanunta ta waro a matuƙar razane, tari mai ƙarfi ya sarƙeta, dan
maganar tasa tazo mata a matuƙar bazata. Duk yanda yaso shanye dariyarsa a wannan
karon hakan ya gagara har sai da lallausan murmushi ya suɓuce masa. Sai kawai ya
jawota ya manna da jikinsa ya cigaba da yin abunsa dan ya kasa riƙewar..
(🥱Wato guy ɗin nan mugun ɗan latsi ne🚶🤭)

★Sosai take tarin har sai da ya janyeta suka koma bakin gado, shi dai
murmushin sa kawai yake yana cigaba da shafa bayanta. Sai da ya ɗan lafa mata ya
ɗauka tambulan ɗin ruwa da ke a side drawer ya tsiyaya kaɗan a ƙaramin cup. Ɗagota
yay, batare da yayi magana ba ya ɗaura mata akan lips ɗinta. Da sauri ta shiga sha
ƙwallar da ya cika idanunta da yay jajir na cigaba da sakkowa. Sai da ta shanye tas
ya janye yana ƙara tsuke fuska kamar bashi ne ya gama murmushi ba yanzun. Ƙin yarda
tai su haɗa ido, sai ma ta zame ta kwanta abunta ta juya masa baya. Shima komai bai
sake ce mata ba yama miƙe.
“Dan ALLAH kada kaje zasu cutar da kai, dan sun saka abu a ƙasan kujerar
zamanka”.
Shaƙaƙƙiyar muryarta da ke fita a dakushe saboda sarƙewar da tai ta sake ratsa
dodon kunensa. Cak ya sake tsayawa tamkar wanda ake juyawa da remote, sai kuma ya
ɗan waiwayo ya dubeta ganin abun nata serious ne. Tana a kwancen da take dai ta
juyama ƙofar baya. Kallon kusan sakkani a shirin ya mata sai kuma ya juya ya cigaba
da tafiyarsa batare da ya tanka ba. Idanu ta rumtse da ƙarfi jin ya fice a binsa.
Ranta a dagule cikin kamar bori-bori ta shiga kaima gadon ƙananun duka da
tittirza ƙafafunta tana fadin, “Ni dai na faɗa ma gaskiya ai, duk abinda ya sameka
kai ka sani mi ma ya shafe ni”.
(🥱Ato idan ya mutu bashi ya huta ba Iffah'r mu🤭🏃😜).

★Tsahon wasu mintuna bata iya ta tashi a kwancen da ya barta ba. Kokawa take
da zuciyarta dake ingizata taje ta duba karfa ya fita ɗin. “In ma ya fita shi ya
sani”. Ta faɗa a fili tana tura baki irin ko'a jikintan nam. Sai kuma can ƙasan
zuciyarta ta ayyana mata (Idan ya mutu shikenan bazaki san gaskiyar rasa iyayenki
da sanin waye Ajmaal ba fa kenan) zumbur ta miƙe kamar wadda aka tsikara, sauri-
sauri ta fisgi mayafin abayarta ta yana a kai tana zira slippers. Ko sanda ta zauna
a sashen bata san wannan ɗakin ba, amma ko gezau ta fito tana kalle-kalle. Da canki
canka ta fito katafaren falon kamar wadda aka jeho.
Da sauri Sayeed Fayzul-haq da ke zaune a ƙasa gefen ƙafafunsa da wasu tarkace
marasa ƙyan gani ya ɗago, shiko hamshaƙin ko motsi bai yi ba idanunsa na kan waya
da ke hanunsa. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke da ɗan galla masa hararar ƙasan ido,
sai dai kuma can ƙasan zuciyarta wani irin bugawa yake da sauri-sauri. Dan tabbas
tarkacen gaban nasu irin abubuwan da ta gani ne a mafarkinta kamar yanda kayan da
ya sanya sukai dai-dai da wanda ta gani sanye jikinsa a mafarkin.
A ɗan daburce Sayeed Fayzul-haq ya sake maida kansa ya rissinar. Tunaninta ya
katse cike da girmamawa ya ce, “ALLAH ya ƙarawa Zawjata-almilk lafiya da tsohon rai
mai albarka. Barka da fitowa”.
Jin al'amarin tai wani gin-girin-gin ganin dattijon da shi kansa Tajwar
Eshaan ɗin zai girmesa nesa ma ba kusa ba amma yana gaisheta da wani sinne kai na
tsantsar girmamawa. Kai ita kam wannan mulkin mallaka na masu mulki baya burgeta.
Tajwar Eshaan ɗin da har yanzu bai nuna yasan da zuwanta wajen ba ta ɗan saci
kallo, sai kuma ta ɗauke a kasalance ta buɗe baki tana gaishe da Sayeed Fayzul-haq.
Bawon ALLAH duk sai ya rikice, duk da kasancewarsa shaƙiƙin a zuri'ar gidan ina shi
ina Zawjata-almilk ta gaidashi. Komai bata sake cewa ba ta juya ta koma hanyar da
ta fito.
Da kallo ya bita ta ƙasan idon da tun ɗazun yake kallon nata dama. Harga
ALLAH ta fara bashi tsoro. Dole yace tsoro, da farko ƙin ɗaukar abinda ta faɗa ɗin
da muhimmanci yayi, amma sai zuciyarsa taƙi yarje masa hakan. Shine ya kira Sayeed
Fayzul-haq akan a sallami shari'ar mutanen da ke jiransa sai nan da kwana biyu bisa
wani uzirinsa. Cikin girmamawa Sayeed Fayzul-haq ɗin ke sanar masa ma ai ɗaya a
ciki bai ƙara so ba har yanzu, dan sunama shirin tura dakaru nemosa ne kasancewar
dama shine wanda ake ƙarar.
A dakatar kawai ya bada umarni ya yanke wayar. Bayan tabbatar da fitar kowa
Sayeed ya sake kira ya sanar masa. Shine ya bada umarnin a duba masa kujerar zaman
nasa da tace an saka abu. Sai gashi kuwa a cikin abinda baifi mintuna ashirin ba
Sayeed Fayzul-haq ɗin ya iso da tarkacen da aka samu ɗin, daka gani kuma kasan
kayan surkulle ne.......✍️
_Tofa kowa sai yay takansa aljanancin Iffah da alama ya fara bayyana yau ɗin
nan😂🏃🏃🏃🏃_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (25)

........Kamar ko yaushe tana kishingiɗe amintacciyar hadimarta Jazaa na da ga


gefenta tana yanka mata tupa. Magana take mata a hankali itako idanunta lumshe.
Jazaa cikakkiyar ƴar leƙen asirinta ce a cikin gidan. Dan duk wani hadimi dake mata
aiki Jazaa ya sani ba ita ba. Ita a karan kanta Jazaar ta ɗauka tsahon shekaru uku
a sanda ta fara mata aiki bata isa faɗin ainahin wacece ita ba a cikin gidan. Dan
takanzo mata ne da fuskoki daban-daban kafin ta bayyana mata ainahin fuskarta. Duk
da kasancewar ta ba'a cikin hadiman gidan ba, kai ita bama a masarautar take ba UWA
ce ta kawo mata ita ta razana a sanda ta san wacece itan. Amma har yau da suka
kwashe tsahon shekaru tare bata taɓa iya ɗaga baki ta faɗama wani wacece ta-ƙurya
ba, ta dai so gwada hakan sau ɗaya taci wahala dan daina ji da magana tayi baki
ɗaya ta koma kurma. Sai da tai kusan shekara a haka sannan ji da maganarta ya dawo
bayan tasha doguwar barazana. Duk wanda zai shaida makirci da tsantsar rashin imani
irin na ta-ƙurya to lallai itace Jazaa. Kuma a hakan ma ba komai ta sani ba itama
sai abinda taso ta sani kawai.
“Bincike na ƙara nisa kan hadimi Israr Uwargijiya ta. Dan a yanzu haka ma
naga baƙuwar fuska a cikin rukunin hadiman da Israr ke aiki. Inaji a jikina kuma
ɗan leƙen asirine aka turo daga jami'an gidan nan”.
Idanunta ta buɗe a hankali kan Jazaa. Kallo take mata mai kaifi da ya sakata
sake gurfane gabanta kamar mai neman gafara. Cikin isa da kaushin harshe ta furta,
“Ya jima yana mana aiki, kuma kowanne an samu nasara. Sai dai a gareni sabo da kaza
bazai baya hanani yankata. Zan yanke masa hukuncin da ya dace da shi, dan dama na
sanar masa in har aka samu matsala hukuncin zai zama dai-dai da irin na kowa. Bazan
taɓa barin wani gaɓa da zai zame min matsala ba”.
Yawu masu kauri Jazaa ta haɗiye. Zuciyarta sai bugu take da sauri-sauri. In
dai har Israr bazai tsira da ga mummunan hukuncin uwargijiyar su ba kenan itama
wataran idan tai kuskure zata iya fuskantar kowane irin hukunci. Ya ALLAH wannan
wace irin rayuwace ta faɗo ciki mai ban tsoro. Wai shin mi matar nan take nema a
duniya bayan wanda ALLAH ya azurtata da shi tari-tari da ita kanta bata san
adadinsa ba?. Tsawar data ratsa kunenta ce ta sata zabura. Mikewa tai jikinta na
rawa. “A gafarceni uwargijiyata”. Ta faɗa illahirin jikinta na tsuma. Sai kuma ta
fice da sauri ta ɓarauniyar hanyar da ta ke shigowa da fita in har ganawa da
uwargijiyar tata ya kama.....

Ba ƙaramin tashin hankali wannan saƙo na Jazaa yazo mata da shi ba. Gaba
ɗaya sai duk wani ɗan farin ciki data tashi da shi yau ta nemesa ta rasa. Tabbas
dole ne hadimi Israr ya bar duniya a yau. Dan duk rintsi ita bata barin ƙurar da
zata zame mata bi baya a bayanta koda kuwa ta wacece. Israr hadiminta ne na amana,
ya matuƙar sanin abubuwa a kanta da in har aka kamashi duk da bai san ainahinta ba
ayyukanta da yawa zasu kwaɓe. Wani irin lumshe idanu tai da mahaukacin zuƙar iska
ta fesar, kafin tabar inda taken cikin sassarfa zuwa cikin bedroom ɗin ta, dan a
yau dole ne tayi aikin nan da kanta.

★Duk yanda Jazaa taso haɗiye mummunan furucin Uwargijiyar tasu kan Israr ta
kasa hakan, gaba ɗaya ta kasa samun nutsuwa. Ba yau ta saba jagorantar ai ma
Uwargijiyar su aiki ba, idan aka samu kuskure kuma a sata da hanunnta ta shayar da
mutum madarar mutuwa. Amma a wannan karon sai take ji bazata iya ba. Badan komai ba
sai dan sanin irin bautar da Israr yay ga ta-ƙurya kamar yanda itama tayi koma take
kanyi, duk haɗarin aiki aka sakashi sai ya zartar da shi koda zai cutu, dan kawai
an samu akasi a wannan karon, akasin ma ba daga garesa bane tunda ya gudanar da
umarnin data bashi sai a halakar da shi. Kai itakam zata samesa ta sanar da shi
gaskiya (Ki kiyayi kanki) wata zuciya ta gargaɗe ta da sauri, tare da tuna mata
wacece Ta-ƙurya idan ta manta...

Ni dai nace, “Hummm”

★★... MALIKAT BUSHIRAT ★....

Kamar ko yaushe kishingiɗe take a katafaren falon nata da ya jiƙu matuƙa da


nau'i-nau'in kayan more rayuwa. Yayinda hadimai uku ne ka ɗai ke tare da ita dan
yau tace bata son hayaniya duk da dama basu isa yin hayaniyar ba gareta. A kallo
ɗaya zaka iya fuskantar tana cikin damuwa, duk da ita ɗin ba wai mace bace mai
fara'a tun fil azal. Ba komai ke mata kaikawo a rai ba sai tattaunawarsu ta ɗazun
da Jasrah. Tabbas tana buƙatar yaronta ya ƙara aure, kodan ya samu nutsuwa irin ta
kowane namiji irinsa. Sannan tana son yakice Iffah da ga jikinsa, dan tunda har ta
iya gwada kashe mata yaro wataran zata iya cin nasara ai. Ba'a ƙaramin damuwa take
da zaman yarinyar nan tare da shi ba gudun karta maimaita abinda ta fara, kallafa
babu tsoro ko shakka tattare da ita take sanar da cewar ita ta bashi madarar ya
sha, ta rasa gane wai Iffah mutum ce ko aljana. Ita kama bata taɓa cin karo da
yarinya mai shekarunta da babu tsoro ko shakka tattare da ita ba. Taya ma zuciyarta
zata iya nutsuwar barin Iffah tare da tilon ɗanta. Ita kam ta rasa ma wane irin
kalar tunani ya kamata tayi. Gaskiya tana buƙatar zama da Malikat Haseenat a wannan
karon, dan ita kam dai zuciyarta ta fara sakkowa da ga zafin da take ji nata. Tana
buƙatar neman shawara ma akan abinda Jasrah tazo da shi, dan shi kansa Tajwar
Eshaan ɗin bai ce komai ba akan batun ƙara auren da sukai masan ɗazun, harma Jasrah
ta nuna jin haushin hakan duk da dai bata fito tace komai ba.....

★... MALIKAT HASEENAT ★...

Tana zaune a keɓantaccen garden ɗinta tana tsakurar farfesun kayan ciki da ta
saka hadima Banou tai mata saboda rashin daɗin baki da take fama da shi na mura da
kwana biyu ke damunta ɗaya da ga cikin hadimanta tazo da saƙon neman iso da ga
Malikat Bushirat. Ɗan jimmm tayi na mamaki, dan ko rabon da ko gaisheta Malikat
Bushirat tazo yi a ƙalla ana neman wata kusan uku kenan, dan tun kafin faruwar
rikicin da har yanzu ya gagara ƙarewa a masarautar ne. Murmushin ta ɗan saki mai
sanyi da jinjina kanta cikin halin dattako. A ƙasaitance ta jinjinama hadimar kai
alamar bada dama. Cikin abinda bai fi mintuna biyar ba sai ga Malikat Bushirat da
Daneen Ammarah tare suna tunkaro ta. Kallo ɗaya ta musu ta ɗauke kanta, har ga
ALLAH tana matuƙar ƙaunar Malikat Bushirat, tana mata so irin wanda takema ƴaƴan
cikinta, bawai dan ta haifa mata jika bane, kawai dai yanda ta ɗauketa tamkar uwa
yasa itama ta ke mata kallon ɗiya. Dan duk da kasancewar Malikat Ashwaq matsayin
jininta Malikat Bushirat ta fiye mata ita sau dubu....
“Barka da hutawa Mamma”.
Daneen Ammarah ta faɗa tana kaiwa zaune kusa da ita. Kai kawai malikat Haseenat
ta jinjina mata, idanunta akan Malikat Bushirat da ta kasa zama ta kasa magana
kanta a risine. Murmushi tayi mai ƙayatarwa ta kauda kanta batare da tace komai ba
ta maida ga Hadima Banou dake tsaye da ga gefe kanta a rissine tana bin Malikat
Bushirat da kallo, dan ita kaɗai tasan wane kalar abun daɗi take hangowa.
“Bamu waje”.
Ta faɗa a hankali cike da ƙasaitar ta. Da sauri hadima Banou ta amsata tana
wucewar yawu taf da bakinta na kwaɗayi. Kwana biyu kenan tana neman mai ƙararren
kwana bata dace ba, tayi alƙawarin sai ta maida asarar kwanakin da Iffah ta satayi
na hanata laƙume kowa. Ganin Banou ta ɓace Malikat Haseenat ta maida kanta ga
farfesunta batare data sake duban Daneen Ammarah da Malikat Bushirat ɗin ba. Hakan
da tai na nufin tana fushi ɗin dai da gaske.
Duk sai Malikat Bushirat kejin ta sake shiga ruɗani, duk da tasan Mammah ɗin
dama zata iya yin fushin saboda mace ce da bata ɗaukar wargi, sai dai batai
tsamanin kamar haka ba. A hankali ta kai zaune kan lallausan carpet ɗin da aka
shimfiɗa saman korayen ciyayin wajen dake kwance luf-luf ko'a filin ƙwallon ƙafa
albarka. Ƙafafunta ta tanƙwashe tana mai fuskantar ta da ƙyau, kanta a ƙasa ta riƙe
kunnuwanta. “Nasan ni mai laifice ƙwarai da gaske Mammah, mai laifin data cancanci
hukunci ga mahaifiya, amma ina mai neman afuwar bazan sake ba. Nima ku fahimceni
ina kan gaskiya ta ne. Duk wata uwa irina zata yi abinda yafi wanda nayi a yayin da
ta fahimci kota kama mai shirin halaka mata ɗa. Har yanzu inajin zafi, zafi matuƙa
akan abinda ya faru, sai dai gani nazo gareki Mammah, dan ALLAH ki fahimtar dani
abinda kike son na fahimta game da wannan al'amarin. Dan maybe ni nawa tunanin a
wannan gaɓar ya tsuke ne waje ɗaya ta inda bana hangen komai sai laifin yarinyar
nan kawai saboda ta taɓa abinda nafi so fiye da komai a wannan duniyar, Mammah wlhy
zan iya fansar da numfashina akan Eshaan iya gaskiyata nake gaya miki”.
Idanu kawai Malikat Haseenat ta zuba mata. Sai dai a cikin ranta tana
ƙara jinjina kalaman ƙarshe na Malikat Bushirat ɗin. Eh tabbas itama tana son
ƴaƴanta, sai dai ba makahon so ba irin wannan, a ganinta a duk lokacin da uwa zata
iyama ɗanta irin wannan makahon son to bazata taɓa iya son wanin ɗanta ba kenan,
bazata taɓa iya maida maraya nata ba, bazata taɓa iya dai-daita ƴaƴanta da wasu
ƴaƴan masu kiranta da uwa ba kamar yanda ita a yanzu take kallonsu duk da matsayin
matan ɗanta da suke. Amma sai kawai ta shanye batace komai ba tama cigaba da shan
farfesunta.
Daneen Ammarah da batace komai ba tun ɗazun ta ɗan ɗago tana kallon
mahaifiyar tasu. Ta santa, ta san in tai fushi tana da wahalar tarowa, duk da kuma
batace komai akam duk abinda Malikat Bushirat ɗin tayi a kwanakin nan ba ta san
ranta ya ɓaci. murya ta sanyaya cike da lallashi ta ce, “Mammah kiyi haƙuri, insha
ALLAH a yanzu mu masu biyayya ne ga dukkan umarninki. Ba zaki samemu a masu
saɓawaba kuma”.
Nan ma shiru kamar bazata ce komai ba, sai kuma ta ture bowl ɗin tana jan
ajiyar zuciya, a nutse ta ja tissue ta goge bakinta kafin ta dubi Malikat Bushirat
da kanta ke risine ita dai, dan a gaban uwa take nata mulkin dole ya zam mai
risinawa........✍️

_(🥱gskiya itama tsohuwar nan akwai hegen mulki🏃)_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*


*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (26)

.........“Idan nace banji ciwo akan kuskurenki ba ƙarya zan miki. Amma tunda kin
fahimta da kanki shike nan komai ya wuce. Akan abinda ya faru kuwa bazan hanaki jin
zafi ba, dan kinyi abinda kowacce uwa zata iya yi har ni kai na. Sai dai kuma ni
bazanyi haka kamar yanda ke ki kayi ɗin ba, saboda wasu dalilai nawa, wanda bai
zama lallai ke a gareki su zama dalilan ba. Amma zan baku shawara matsayina na uwa.
K shugaba ce, sannan kuma uwa. Shi shugaba an sanshi da haƙuri ne, kauda kai,
jarumta, haɗiyewa komai ɗaci, shugaba kowa nashi ne, baya kuma taɓa kallon gudan
jininsa kawai a matsayin ɗa sai ya haɗa da wanda ma bai haifa ba. Eh munji yarinyar
tayi kuskure ƙwarai da gaske, kuskure kuma mafi girma da bai kamata ace an yafe
mata cikin sauki ko sassauta mata ba. Sai dai a matsayinmu na wanda suka san ahalin
da suke ciki ya kamata muyi wani nazari, sannan mu haɗiye dukkan zafin da muke ji
koda ace yana ƙonamu. Domin ta hanyar wannan haɗiyewar ne kawai zamu iya sanin
ainahin gaskiya. Ga duk mai hankali idan zai nutsu a shekarun yarinyar nan masu
ƙaranci kai tsaye zai zamto aikin data aikata ba nata bane, anyi amfani da ita ne
kawai domin samun cikar buri. Iffah yarinya ce da bata iya ɓoye abu, sannan akwai
ƙuruciya a cikin al'amurran ta. Idan har ainahin mai wancan aiken zaiyi amfani da
duk wannan yanayin nata, mu mezai hana bazamuyi amfani da fahimtar ta ba wajen gano
koma wanene ta cikin sauƙi. Bushirat sam ban san lokacin da kika lalace haka ba,
sai dai na fahimci a yanzu kina samun wasu ƴan kazagine da ke amfani da damuwarki
wajen ingizaki. Bazance ki rabu da su ba, sai dai zan baki shawarar nutsuwar
fahimtar manufofin su akan tunzurakin. Lokaci yayi da zaki farka, inba haka ba
zakiyi nadama a gaɓar da nadamar bazata amfanar da ke komai ba face dana sani”
Ba ƙaramin shiga jikinta kalaman Malikat Haseenat ɗin sukai ba. Sun ratsata
matuƙa, ta kuma hankaltu da abinda take son nusasheta cikin hikima. Cike da
girmamawa ta jinjina kanta, muryarta a raunane ta ce, “Nagode Mammah, nagode da
kika farkar dani wannan nannauyan barcin da ya ɗaukeni. Kiyi haƙuri da duk abubuwan
da suka faru, Insha ALLAHU kuma zaki sameni mai canjawa”.
“ALLAH ya tabbatar da hakan”.
Malikat Haseenat ta faɗa. A tare Daneen Ammarah da Malikat Bushirat suka amsa da
Amin. Da haka wajen yay ɗan shiru, sai zuwa can kuma Malikat Bushirat ta sake
nisawa. “Mammah sai kuma abu na biyu, duk da fadakarwarki ta farko ni dai ta janye
min komai dake raina”.
“Ki faɗi ko miye dan a yanzu mu duk wata hanyar mafita abin nemanmu ce”.
Kai Malikat Bushirat ta jinjina, kafin ta cigaba da magana kanta a ƙasa. “Dama
Jasrah ce ɗazun ta sameni akan batun......” tsaf ta zayyane mata komai a to z
batare data rage ba. Hatta da zuwan Tajwar Eshaan ɗin na bazata da ƙin cewa komai
da yay akan zancen. Ta ɗaura da faɗin, “Tun kafin tazo da wannan zancen ni dama
inada burin hakan, sai dai bana nufin tirsasa masa. Amma dai yanzu ina son naji ta
bakinki kema”.
Wani ɗan murmushin manyance Malikat Haseenat tayi idanunta akan Malikat
Bushirat ɗin. Sai kuma ta kauda kanta kamar bazatace komai ba. Kusan minti ɗaya
sannan ta nisa da sake kallonta. “Hakan tunani ne mai ƙyau, sai dai ina son ku tuna
abinda ya faru last ɗin nan. Mun sake rasa ɗaya a cikin matansa, ɗayar kuma saboda
firgita ta tsinta kanta a halin ciwo da dole sai da muka maidata ga iyayenta.
Yarinyar nan dai Iffah da aketa ɗauki ba daɗi a kanta itace ta gagara, gagarar tata
kuma na mana ishara da tabbacin zarginmu, dan yarinyar tana zagaye da kariyar
UBANGIJI ne, da kuma kwananta bai ƙare ba. Shiyyasa aketa bin wasu hanyoyi amma duk
da haka ba'aci nasara ba. Idan munada wayo a wannan gaɓar hakan na nufin ita ɗin ba
abinda zamu banzatar bace, Insha ALLAHU itace wadda ta dace da zama Zawjata-almilk
da taɓata ga maƙiyanmu wani babban yaƙine da idan suka ce zasu ci gaba to
kwanakinsun nan 99 da ake faɗa na ɓarawo na gab da cika”.
A tare Daneen Ammarah da Malikat Bushirat suka kalleta, itako ta gyaɗa musu
kai cike da tabbatarwa...

★...

Kallon juna suma hadiman dake lafe cikin fulawoyin garden ɗin sukai dai-dai da na
su Daneen Ammarah. Sai kuma suka miƙe cikin sanɗar da baza'a gansu ba zasu bar
wajen. Daneen Ammarah ce ta ɗan shiga waige-waige, dan itakam ALLAH ya bata ƙarfin
ji. Jin tabbas kamar fa motsin mutum ya sata miƙewa da ɗan hanzari, inda take jin
motsin ta nufa. Da wani irin rawar jiki suka koma bayan wasu flowers masu duhu
sosai suka lafe. Ganin babu alamar abinda take zargin ta baro wajen, sai dai
zuciyarta na cigaba da tabbatar mata akwai wani bayansu a cikin garden ɗin.
“Lafiya?”.
Malikat Haseenat ta tambaya lokacin da Daneen Ammarah ke dawowa. Cikin nuna
ƴar damuwa ta ce, “Wlhy Mammah kamar naji motsi ne. Sai dai kuma banga komai ba”.
Magana Malikat Haseenat tai kamar zatayi, sai kuma ta haɗiye abunta. Sai
ma duban Malikat Bushirat data miƙe tai da mata alamar ta zauna. Babu musu ta koma
ta zauna badan taso ba. Dan itama dai zuciyarta na raya mata dole motsin da Daneen
Ammarah ta ji ya kasance wani abu......

★★.. ZAWJATA-ALMILK ★.....

Harta nufi hanyar komawa ɗaki ta canja shawara, da baya ta dawo, hanyar da
suka taɓa biyowa da shi randa ta samesa a can sama tare da Miran Arshaan ta nufa,
haka kawai take son sake komawa wajen. Tana gab da isa ta ɗan tsaya a ƙofar da tun
wancan karon taso sanin ita kuma ta miye, babu wani ko ɗar ta nufi ƙofar ta buɗe,
sai taji ta buɗe babu gardama. Ƙaton Gym ne mai ɗauke da nau'i-nau'in machines na
motsa jiki masu ƙayatarwa. “Uhyim” ta faɗa tana ɗan jinjina kanta da taɓe baki
hannayenta duk biyu a ƙugu. Jitai har ma taji sha'awan motsa jikin, dan haka ta
juya ta fita tana murmushi da faɗin, “Zan dawo gareku kuma”.
Hadiman nan dai na wancan lokacin ta sake tararwa yau ma, cikin sauri duk
suka zube suna gaisheta, yayinda na'ura ke yayata sunanta. Murmushi ta ɗan musu
kawai ta wuce abinta, a ranta kam gulmar Tajwar Eshaan take dan tasan iyayinsa ne
yasa aka saka wannan na'uran da in har zaka ƙetare ƙofan wajen sai ta sanar da ko
kai waye ko kuma tsoro ne oho masa.
“Ya rabba”. Ta faɗa a hankali tana mai lumshe idanu jin yanda iskar wajen ta
wani buso mata. Sai kuma ta buɗe idanun ta kaisu ga sararin samaniya da ke ta faman
haɗa giza-gizai alamar haɗuwar hadari. Da alama ruwa zai iya zubowa a koda yaushe
insha ALLAHU. Iffah na matuƙar son yanayin damuna, dan koba komai tayi tsalle-
tsallenta a ruwa ai. Cigaba da takawa tai murmushi na ƙara yalwatuwa a fuskarta har
fararen haƙoranta na bayyana. Ƙyawawan idanunta na cigaba da bin wajen da kallo
daki-daki cike da shauƙi. Inda ya tsaya ranar shi da Miran Arshaan ta ƙarasa,
“Woow!!” ta faɗa tana wani irin ware idanunta ganin yanda take iya ganin masarautar
baki ɗaya da ga wajen. Harma wajen masarautar ana hangowa da kaikawon motsoci dana
mutane ɗai-ɗai. Ai bata taɓa tunanin haka wajen yake ba, da tuni ta maidashi wajen
zamanta. Ɗan yayyafi aka fara a hankali, cike da nishaɗi ta rungume hannayenta tana
sakin ƙayataccen murmushin dake sake bayyana ƙyawun da ALLAH ya azurtata da shi.
Kamar da wasa ruwan ya fara ƙarfi, amma bata da alamar barin wajen kamar ma farin
cikinta ƙaruwa yake, dan sam murmushi yaƙi barin face ɗinta, har ta kai ta fara
ware hannayenta tana ɗan juyawa idanunta a lumshe tamkar mai hajijiya.
Cak ta ɗauke wuta jin ta jingina da abu a yayin da take jujjuyawarta, sai
kuma sassanyan ƙamshin turarensa ya shiga rige-rigen faɗawa hancinta. Sauri-sauri
ta buɗe idanun tana juyowa, ganin shi ɗinne dai tsaye cikin sabuwar shiga yasa tayi
kamar wadda ta ɗan firgita. Sai kuma ta haɗiye sauran murmushin fuskarta tana
saukar da idanunta ƙasa saboda yanda ya tsareta da nasa idanun.
“Baƙya tausayin kanki ko?”.
Ya faɗa can ƙasan maƙoshi cikin sanyi sauti da ko ita ɗin ma dan suna gab da
juna ne tajisa. Lips ɗinta ta ɗan shiga motsawa kamar zatai magana sai kuma ta
kasa, ƙafafunta ta ɗaga da nufin barin wajen. Taku biyu ta tsaya cak tana mai
rumtse idanunta jin ya riƙo hanunta. Kallon hannun nasa fari sol da ke riƙe da nata
tai ta gefen ido, ga wasu dogayen farata farare tas-tas babu ɗigon datti tattare da
su sai ma sheƙi da sukeyi, jitai tsigar jiki ta na wani irin tashi, a ɗan shagwaɓe
ta ce, “Zanje ciki ne”.
Maimakon ya saketa sai ya maidota a hankali ta dawo gabansa. Kallonta ya ke
da ga sama har ƙasa, kallo irin na ƙurilla. Ji tai gaba ɗaya tana neman daburcewa,
dan sam bata son kallo, balle ma irin nasa mai tada tsigar jiki. A hankali ya
lumshe nasa yana ƙoƙarin danne murmushin da ke taso masa ya matsota ta koma
jikinsa, babu yanda ta iya face lumshe nata idanun itama da ɗaura hannayenta kan
ƙarfen wajen tai luf a jikin nasa tana shaƙar sassanyan ƙamshin sa da ita dai a
rayuwarta shi kaɗai ta sani da shi. Nashi hannayen shima yasa a ƙarfen ya ɗaura
kansa a kafaɗarta har lokacin idanunsa a lumshe yayyafin na sauka a kansu kaɗan-
kaɗan, sai ya zam tana a tsakkiyarsa shi da ƙarfen..........✍️

🥱🥱🤫😑🚶

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_
_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (27)

.......... “Kallo nada matuƙar ƙayatarwa da ga nan ba?”.


Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Sosai tsigar jikinta ta yamutsa, dan haka cikin
matse idanunta da jikinta da ke jingine da nasa ta ce, “Uhhm” acan ƙasan maƙoshi
itama. Murmushi ya sake saki da buɗe idanunsa, sai kuma a hankali ya ɗaura
hannayensa kan nata da har yanzu ke'a kan ƙarfen. Itama buɗewar tai suka cigaba da
kallon kaikawon mutane da mafi yawa suka kasance hadimai ne, sai daga can wajen
masarautar kuma da kai kawon motoci yafi yawa. Yanda numfashinsa ke sauka a gefen
wuyanta ba ƙaramin illata ta yake ba, tai dai jarumtar daurewa gudun kar aga
gazawarta (Kun san dai mutuniyar tamu🥱😂).
Jin ruwan na cigaba da sauka kansu dan ya ɗan fara ƙarfi ya sashi sauke
sassanyar ajiyar zuciya da lumshe idanunsa ya sake buɗewa, sai kuma ya miƙe da ƙyau
ya ja hanunta da ke cikin nasa har yanzun, kamar jira suna shiga ɗaya daga cikin
rumfunan wajen ruwan ya kece mai ƙarfi. Hanunnta da take mutsu-mutsun cirewa a
cikin nasa ya saki, cike da basarwa ya kai zaune a ɗaya daga kujerun cikin rumfar.
Zama yay irin na ƙasaita, ga fuskar nan tamau a tsuke kamar bashi ba. Batare da ya
sake kallon inda take tsaye ba ya danna wani ɗan maɓalli ta gefensa sai ga abu na
sakkowa a gefe-gefen rumfar, ruf ya rufesu suka koma kamar cikin ɗaki, dan yana
gama sauka har ƙasa sai ga haske da ya ƙarama wajen ƙyau da ɗaukar hankali..
Iffah bata ma san ta furta kalmar “Woow! Ya ALLAH”. Ba tsabar yanda abun yay
matuƙar ƙayatar da ita. Sai kuma tai saurin ɗaura hanunnta kan baki tana ɗan satar
kallon inda yake. Baima nuna yasan tanai ba, dan ya basar kamar ma bai san da
zamanta wajen ba. Sai ma wani ƙara harɗe zamansa da yay yana lumshe idanunsa. Baki
ta ɗan taɓe ta ɗauke kanta itama. Sosai ruwan ke sauka kamar ba ruwan farko ba, ga
wani sanyi mai ratsa ɓargo duk da suna a rufe. Fara ƙudindine jiki Iffah tai tana
ɗan yamutse fuska, sai dai duk da haka zuciyarta zungurarta take ta leƙa taga yanda
ruwan ke zuba. Amma shakkar kasancewarsa a wajen ya hanata haka.
“Sit”.
Ya faɗa kamar ba daga bakinsa maganar ta fito ba. Da sauri ta buɗe idanunta da
ke lumshe. Har yanzu yana a yanda yake. Kauda nata kan tai itama tana ɗan yamutse
fuska. Sai kuma ta dubi kujerun, ji tai bazata iya musa masa ba, dan haka takai
zaune tana ƙara ɗan matse jikinta dan sanyi takeji yana ratsata.
Idanunsa ya ɗan buɗe a kanta sai kuma ya ɗauke. Cike da ƙasaita ya mike yana
zare jacket ɗin jikinsa, ita dai kallonsa take ta ƙasan ido, jin ya zagaya bayanta
ta maida kanta ta risinar. Sai kuma ta sake ɗagowa da sauri jin ya ɗora jacket ɗin
a jikinta. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, tare da dafe rigar data ɗan zame ta
ce, “Thanks”.
Bai ce mata komai ba sai da ya koma ya zauna inda ya tashi sannan ya sake
dubanta fuska babu alamar wasa ya tsareta da idanunsa masu kaifi, kasa jurewa tai
tai ƙasa da nata tana bin ash color ɗin jacket ɗin nasa mai ƙyalli da ƙamahinta ya
mamayeta da kallo.
“Waya faɗa miki an saka abubuwan nan? Su waye suka saka kuma?”.
Batai tunanin zai tuhumeta da sauri haka ba, dan haka ta ɗan ɗago ta dubesa.
Idanunsa na kanta har yanzu, ga fuskar nan babu alamar yasan miye murmushi ma. Nata
tai saurin maidawa ƙasa ta sake risinarwa dan kallon ya matuƙar ratsata. Kamar mai
raɗa a hankali ta furta “A mafarki na gani”.
Zaune ya tashi da ƙyau, Wani irin kallo yake mata tamkar idanunsa zasu faɗo.
Jin kaifafan idanun nasa har yanzu a kanta ya sata saurin faɗin, “Da gaske a
mafarki na gani, nima kuma banyi zaton abin zai tabbata ba, kawai dai zuciyata ce
ta kasa nutsuwa akan lamarin. Dan duk sanda naita maimaita mafarki to daga baya sai
abun kaga ya kasance a wasu lokutan”.
(Ya arrahaman) ya faɗa a zuciyarsa dake faman bugawa da sauri-sauri. Kallo
yake mata na kin ma rainamin hankali ko ke ba mutum bace halan, dan haka ya ƙara
tsuke fuskar a zahiri. A ɗan kausashe ya furta “Who Are you Zawj? Miya kawoki
gareni? Babu yanda za'ai wanda yay shirin kasheka ya dawo ya taimakeka kan yunƙurin
wani mai ƙudiri irin nasa”.
Yanzu kam ɗago idanunta tai ta ɗan kallesa dan tsabar shiga mamakin
furucin nasa. Maidawa ta sake yi ta risinar tsigar jikinta na tashi saboda yanda
kallon ya wani irin ratsata. Cikin wani irin sanyi da ɗan kaushi-kaushin muryar
tunawa da ahalinta da suka tarwatse a dalilinsa bata san ya akai furucin ya fito ba
ta ce, “FHAREEDAH BINT ZAYYAN!!”. Sai kuma tai shiru na wasu sakanni, kamar wadda
aka tsikara ta ce, “Bani na kawo kaina gareka ba kai ne ka kawo kanka gareni
Sultan. Mu huɗu iyayena suka haifa a duniya. “Hanash, Arfa, Fariha sai ni auta. A
shekara ɗaya kafin yau gidanmu shine aljannarmu ta duniya, dan duk da muka kasance
talakawa muna farin ciki irin wanda masu dukiya ba lallai sunayi ba. Cike muke da
soyayyar juna, ƙauna, kulawa irin wadda ko tuntuɓe ɗayanmu yayi mu duka munajin
ciwon a jikinmu ne. Duk wannan aljannar tamu ta sauya ne daga wani yammaci na ranar
juma'a da bazamu taɓa mantawa ba. Ranar da zaran ƙaddara yay lilon da har Nina Arfa
ta shiga a jerin ɗaya daga matanka.....” Hawayen da suka ciko mata ido suka sarƙeta
ta kasa ƙara sawa. Wajen yay shiru sai saukar ajiyar zuciyarta a jajjere dana ruwan
sama da ake ketawa tamkar ba ruwan farko ba, shikam yana zaune a harɗe baka isa iya
tantance yanayinsa ba, a zahiri ma zakace idonsa a rufe suke, sai dai can ƙasa yake
kallonta a wani irin yanayi da shi ya barma kansa sani.
Hawayen da suka zubo mata ta share badan sun tsaya ba, ta cigaba da faɗin,
“Komai ya rushe, komai ya canja, canjawar da har abada baya bazata dawo da shi ba.
Na rasata, na rasa Fariha duk a dalilin aurenka, da ga ƙarshe na rasa Ummu da Babiy
na rasa Hanash shima duk saboda kai fa. Komai ya ƙare, kamar ban taɓa mallakarsa
ba, kamar ban taɓa zama mai ahali ba, kamar ma ban taɓa zama kowaba duk dai saboda
kai fa. Inajin ciwo, ciwo matsananci mai ƙuna a kowane ɓargona da gunar jini na. Na
kai gaɓar da bana baƙin ciki ko shakkar rasa numfashina nima a yanzu, dan abinda ya
rage min kenan kuma bana jin yana da sauran amfani a gareni balle muhimmanci duk fa
dai saboda kai. Nafi buƙatar na bisu nima, amma sai bayan na tabbatar da nunama
duniya su waye su, wannan alwashi na ne duk da kasancewata mai rauni bazasu sha a
banza ba sai dai mu rasa a tare ni da su duk da kasancewarsu a cikin ahali mafi
girman daraja da kowa ke kallo a ƙasata....” nan ma kuka ya ƙara sarƙeta mai ƙarfi.
A yanzun ma bai iya ko motsi ba binta kawai ya ke da kallo zuciyarsa na wani
irin zallo da bai taɓa fuskanta da ga gareta ba. Zamewa tai daga saman kujerar da
take zaune a hankali ta durƙusa gabansa, kanta a risine hannayenta a haɗe 🙏.
“Ina roƙonka karka sakankance da ni, dan da gaske har yanzu zuciyata cike
take da burin ɗaukar fansa. Ina kuma baka shawarar ka yanke min hukunci da gaggawa
akan laifina kuma dai-dai da abinda na aikata, dan da gaske na shigo masarautar nan
ne domin hukuntaka akan laifin da nake zargin kai kake aikata shi. Da shirin ɗaukar
fansar jinin ƴan uwana na yarda da aurenka, da alƙawarin ɗan ɗana maka mutuwa kamar
yanda na rasasu na shigo wannan masarautar. Kuma har yanzu ban gama tabbatar da
babu hanunka a cikin ba. Ban kuma janye makamaina ba na son tabbatar da hakan. Sai
dai ina rokonka kafin hukuncin ka sanar dani alaƙarka da Ajmaal dan ALLAH. Ka kuma
janye kariyar da kake ƙoƙarin bani dan killaceni anan tamkar raunani ne. Burina
fito-na-fito da su kamar yanda suka nuna min filin yaƙin na shirya. Na shirya tsaf
da shirin bama kaina da kai kariya da ga duk wani sharrinsu koda daga baya kaima
zan dawo na hukuntaka kamar yanda na shigo da ƙudirin yi duk da sun kasance jininka
ne su ɗin”. Hannu ta sa ta share duk hawayenta tana sake miƙewa ta koma saman
kujerar. “Kayi haƙuri da tsaurin idona haka nake. Koda ina so ko bana so haka zan
cigaba da kasancewa domin hallayata ce wani yanayi bazai canja min ita ba, ita ɗin
jinin jikina ce. Kallon cikin idonka na faɗa maka abinda yake gaskiyata bashi ke
nufin baka da kima da daraja a idanuna ba. Kai ɗin shugabana ne, mai daraja da wata
irin kimar da in wani mahaluki ya zageka a ƙetaran ƙasata ta ruman koda yafi ƙarfi
na sai na daka tsalle wajen wanke fuskarsa da marin da sai na zubda haƙwaransa ƙasa
a gaban duk wanda ya ke jin ya isar masa. Kayi a hankali Kanada maƙiya sosai kuma
zagaye suke da kai tako ina, a cikinsu ma kuma har da ni nan da ke a gabanka yanzu
Sultan. Duk ƙanƙantar maƙiyi kada kayi sakaci da shirinsa koda nice nan, dan allura
ma da kake gani fa itama ƙarfece, idan har tsayawar numfashi a iya ƙirji baya nufin
mutuwa kai tsaye to ka sani fa reza zata iya kisa irin na wuƙa har a gagara iya
banbancewa jikin son a tabbatar. Dan haka kamar yanda na roƙeƙa kar sawayenka su
wuce sashenka a yau, dan ALLAH kar kaje. Ina maka wannan roƙon ne a matsayin
*_MATARKA_* ba shugaba da talakarsa ba, ba kuma ƙin fitar taka zai kareka da ga
ƙaddarar ka bane ko hanasu cin nasara a kanka”........✍️

*_Shahan-shan da gaske fa kayi takanka dan da alama aljanar gaskiya aka aura
maka batare da ka farga ba🙆, to nidai ba ruwana kuzo broza ɗinku na cikin haɗari
ƴan DAUƊAR GORA.... CONVERSETION 🏃🏃🤔._*

_Ga alakoro nan na raya gori😎😎_


*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (28)

........Cak numfashinsa ya tsaya da ga kaikawon da yake a ƙirjinsa. Kalmar *_a


matsayin MATARKA_* ɗin nan tafi kowacce matuƙar ratsasa har tsakkiyar kai fiye da
komai data faɗa, duk da suma sauran kalaman nasa nada wani muhimmanci da nasu
tasirin. Amma a zahiri bai ko motsa ba, yana dai kallonta ne a ƙasan ido kamar ya
samu wani television. Shiru na tsawon wasu sakanni kamar masu sauraren saukar ruwan
saman, sai kuma ya ɗago kaifafan idanunsa dai-dai da ɗago nata itama, cikin kallon
ido cikin ido da wata sarƙaƙaƙƙiyar muryar da fitarta bai canja taushin ainahin
muryarsa mai sanyi da nutsuwa ba ya furta, “Mi kika sani game da ni? A bayan burin
da kika shigo da shi masarauta ta?”.
Kamar bazata motsa ba sai kuma ta motsa lips ɗin ta a hankali. Daurewa tai
bata nuna ko gezau ba, itama ta zuba nata idanun da yanayinsu ke wani irin canja
kala-kala maisa tsigar jikinsa tashi cikin nasa da ƙyau. Tai ɗan murmushi mai sanyi
da ya nema ɗauke fitar numfashinsa a baɗininsa, janyewa tai gefe kaɗan fuskarta har
lokacin da murmushin, “Sanin wani abu game da kai abu ne mai wahalar gaske ga baƙon
zaman wannan gidan. Sai dai kai da kanka ya kamata ka duƙufa sanin komai a kanka,
idan kuma ka sani ka ke shanyewa ka tuna kai shugaba ne. Haƙƙoƙin biliyoyin mutane
ne a ƙarƙashinka, idan ka tauye ɗaya da gangan sai ALLAH ya tambayeka koda da
ƙwayar zarra ne, inaji a raina kai ba mutum bane irin mutanen da tunaninsu ke a
takure waje guda, in har bakai kake aikata laifin da mafiya al'ummar ƙasar nan ke
kallonka da shi ba na tabbata kasan masu aikata wasu a ciki koda kaɗan ne, dan inba
haka ba banga dalilin da zaisa su dinga farautar rayuwarka ba irin haka a
matsayinsu na makusantanka”.
(Ya arrahaman) ya faɗa a zuciyarsa. Karo na farko ana faɗa masa gaskiyar da
kowa ke shakkar tunkararsa a kanta hatta da wanda suke sama da shi a shekaru. Amma
gashi yarinya ƙaramar da a haihuwar kaji ya haifeta yau tana jaddada masa shi ɗin
wanene. Tsarge masa komai take a yanda ya jima yana buƙatar ji daga bakin wani koda
mahaifiyarsa ne. Magana mafi dukan zuciyarsa itace ta ƙarshe. Ana farautar
rayuwarsa kuma makusantansa. Yes ya jima da sanin wasu a makusantan sa na bibiyar
rayuwarsa, kuma mahaifinsa ya fargar da shi hakan tun yana raye, amma a yau sai
yaji kalmar daga bakinta ta sake girma matuƙa garesa. Kallonta yake cikin ido a
wani irin yanayin da ke neman sarƙe fitar numfashinsa. Muryarsa a wani irin sanyaye
ya furta, “Sune suka baki guba ki bani?”.
Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta ɗago ta ɗan kallesa. (To Miya
rage kuma? Ai bataga amfanin cigaba da ɓoye masa ba) dan haka kai tsaye kawai ta
jinjina masa kanta. “Ni nasan baka buƙatar sai na maimaita komai, domin ban ɓoye
komai a zamana gidan nan ga Ajmaal ba, hatta randa nake neman dafin macizai ido
rufe na sanar masa, shiyyasa har yanzu zuciyata taƙi daina mamakin miyasa kasha
madarar tunda har kaga saƙon kuma...”
Wani murmushi ne ya nema suɓuce masa a hankali, sai dai bai yarda ya
bayyana akan fuskarsa ba ya hadiye kayansa yana mai lumshe idanunsa da launinsu ya
canja baki ɗaya. Kamar bazai tanka ba sai kuma ya sake buɗe idanunsa ya sauke a
kanta cikin wani irin kasalallen kallo da ya tilastata rissinar da nata.
“A ranar banga saƙonki ba dan bana cikin ƙasar nan”.
Ɗagowa tai da sauri ta dubesa. Idanunta a ware cikin rawar harshe ta ce,
“Kamar ya baka cikin ƙasar nan? Bayan matarka an mata kisan gilla a tsakanin,
hakama tsohon da kowa ke tabbatar da jayayyar da yay da kai ce tasa ka ɓaddashi.
Kana nufin kuma da gaske kai ne Ajmaal ɗin dai?”.
Idanunsa ya lumshe ya buɗe a hankali, sai kuma ya miƙe a nutse zuwa gabanta,
binsa take ita dai da idanunta da ke a waje gaba ɗaya kamar zasu faɗo har ya kai
zaune a kujerar kusa da ita. Zamansa ya maida kafa ɗaya kan ɗaya idanun nan nasa
masu kaifi shanye a kanta. Itama ta kasa daina kallonsa, dan gaba ɗaya kamar a
rikice ma take. “Duk matar da aka kawo Masarautar nan da sunan tawa ni ke kaɗai na
taɓa gani da idanuna, babu wacce ta taɓa rasa ranta ina a cikin masarautar nan
kuma. Zaki san Ajmaal kamar yanda kike buƙata domin ina son muyi aiki tare”. Ya ɗan
yi murmushin da ya nema ɗauke duka numfashinta batare da ya jira amasawarta ba ya
cigaba, “Ki ɗauka anan tare kike da Ajmaal ba Shahan-shan Eshaan Ibn Haysam Abdul-
majeed ba. Mi kike son sani?”.
Da ƙyar ta iya haɗiye yawu da rawar jikinta, dan itakam kallon komai take
kamar a mafarki. Hasalima ya ƙara birkitar mata da kai ne. Cikin rawar murya kamar
mai in ina ta ce, “Cafa kai baka taɓa ganin fuskar su ba, suna mutuwa kuma baka
cikin masarauta? Taya hankali zai ɗauki wannan maganar?”.
“Ta yanda ya ɗauki zaman Tajwar Eshaan tare da ke anan babu wani shamaki
mai shari'a”. Ya faɗa a hankali kamar ba daga shi kalaman suka fito ba. Yawu ta
haɗiye da ƙyar tana ɗan tura baki jin ya kirata mai shari'a, sam zuciyarta tama ƙi
yarda da wancan zancen nasa, “Ya akai ka zama abokin Sir Fawzan?”. Ta faɗa a
hankali tamkar mai tsoron wani ya jita. Shiru babu alamar zai amsa mata idonsa na
kallon ƙasa, dan dauriya kawai yake da surutun nan, da alama ita kuma kamar ma
yanzu ya fara mata daɗi. Ya ɗan ja numfashi ya fesar a hankali, “A baɗini Tajwar
Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed abokin kowa ne a ƙasar ruman da sunan Ajmaal, dan
haka shima Fawzan ya shigo ne kamar yanda kowa ke shigowa, a taƙaice dai na haɗu da
shi ne a ƙasar Cuba, lokaci ina wani couse, abinda ya fara haɗamu so bawai sai an
maimaita faɗarsa bane, kawai dai sanda nasan shi ɗan ƙasata ne naji farin ciki, na
kuma nuna masa cewa nima asalina ɗan canne...”
Yanda yake maganar da ɗaɗɗaya kuma kamar da ƙyar sai taji ya bata tausayi da
dariya, ta daɗe da fahimtar magana abune mai wahalar gaske a gareshi. Kamar ko
yasan mi take tunanin, sai gani tai ya miƙa mata waya yana ɗan murza goshinsa da ke
sarawa. “Mu cigaba a rubuce kaina yana ciwo”.
Dariya abun ya bata, tai murmushi idonta a kan wayar da yake miƙo matan.
Kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa a zuciyarta tana faɗin (Miskilanci ma ai cuta
ce gaskiya), a zahiri kam sai ta ɗan taɓe baki tana rubuta, “Miyasa randa na haɗu
da kai a Eira garden ban ganku tare ba?, bayan kuma shi ya kirani ne dan na haɗu da
Ajmaal?” ta mika masa wayar. Rubutun kawai ya tsirama ido harta fara ƙosawa, dan
bashi da alamar zai bata amsa. Sai da ya gama shan ƙamshinsa sannan ya amsa a
rubucen shima. “Dama banyi niyyar mu haɗun ba, dan ina son na fara sanin waye ke”.
Sosai ta waro idanu tana kallonsa lokacin da ta gama karantawa. Bama ta san
bakinta ya suɓuce wajen faɗin, “Saboda mi to?”. Shiru yay kawai ya tsira mata
idanu, sai kuma ya ɗago a hankali ya zare wayar daga cikin hanunta.
“Saboda yamun bayanin manufarki da kai tsaye ni ta shafa batare da shima ya
san hakan ba” ta karanta. Sake kallonsa tai mamaki na bayyana a fuskarta. Nan ɗin
ma bakinta ne ya suɓuce wajen faɗin, “Anya mutumin nan bada saka hanunka aka kawoni
gidan nan ba?”.
Wani irin lumshe idanu yay cike da salo ya sake buɗewa a kanta, sai kuma ya
saki wani makirin murmushi yana kauda kansa.
“Ka amsa min Please”.
Ta faɗa tana matsowa karshen kujeran da ya maida zaman nasu gab har ƙafanta na
gogan nashi. Nan ma babu alamar zai tanka matan tsahon wasu sakkani, kafin ya
fiskanceta da kyau kaifafan idanunsa a kanta. “Idan na matso da makashina kusa da
ni sai ya zama laifi?”.
Zumbur ta miƙa tafukan hannayenta duk biyu akan fuskarta ta furta, “Ya
arrahaman ka kasheni, wlhy ka gama dani. Na shiga uku ni Fhareedah wace irin
MAKAUNIYAR ƘADDARA ce kuma wannan ɗin?”. Yanda take kaikawo da sambatun jikinta na
rawa kaɗan ya rage ya kwashe da dariya. Amma ya danne da ƙyar, sai dai duk da haka
sai da ya kauda kansa gefe yana murmushi. A mamakinsa sai yaji kawai ta fita a
wajen da ɗan gudu-gudu. Sosai ya zaro idanunsa, sai kuma kawai ya saki murmushi mai
faɗin da har haƙoransa na bayyana a bazata. Murmushin yake shi kaɗai yana faman
kare baki idanunsa akan hanyar da tabi.....

★★..... ★....

A yanda hadiman leƙen asirin nata suka shigo yasa ta bama duk sauran hadiman
dake zagaye da ita umarnin barinta. Jikkunansu har rawa suke suka fice, a yanda ta
zuba musu ido yasa bama su tsaya wani jan jeni ba suka shiga sanar mata komai dan
sun san bata buƙatar jan zance da tsaho.
“ALLAH ya ƙara miki lafiya mai amfani uwargida shugabar matan wannan daula. A
yau Malikat Bushirat ta baƙunci Uwar masu gida. A yanzu haka ma suna a garden ɗin
ta tare har da Daneen...”
Wani irin kallo take watsa musu da kai tsaye suka fahimci manufarta. Sake
gurfana sukai a gabanta cike da girmamawa. “Kamar yanda ki ka fi buƙata mun kasance
da su a wajen muma, duk da kaɗan ya rage Daneen ta ganemu”.
Fuska ta yatsine alamar ba wannan take son ji ba. Fahimtar hakan ya sakasu
cigaba da faɗin, “Sun tattauna abubuwa da yawa, sai dai gaba ɗaya a dunƙule sun
ta'allaƙa ne a neman afuwar Uwar masu gida da Malikat tayi. Ta faɗi maganganu masu
yawa itama na nuna fushi, sai dai da ga karshe ta sakko harta yafe mata abubuwan da
suka farun da dorawa da bata shawara game da al'amarin Zawjata-almilk. Da ga
ƙarshen zancen sun kuma dai ya ƙare akan son ƙarin auren Shugaban wannan daula....”
A karan farko Malikat Ashwaq ta miƙe zaune sosai tana kallonsu. “Sai me ya
faru?”. Ta faɗa kamar idanun nata zasu faɗo a kansu.
“Babu alamar dai Uwar masu gida ta bada goyon baya, daga hakanne kuma
Daneen ta fahimci motsin mu a wajen iyakar abinda muka ji kenan”.
Hannu kawai ta ɗaga musu alamar suje. Suna ficewa itama ta miƙe, da ƴar
sassarfa ta bar falon hutawar tata zuwa ɗakin barcinta mafi zama sirri gareta har
kafafunta na neman harɗewa........✍️

_Tofa, Malikat Ashwaq yaya dai🥱🏃_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (29)

.........Bayan kamar mintuna ashirin da tafiyar Iffah sannan shima ya mike, zuwa
lokacin ruwan ya tsagaita sai ɗan yaf-yaf da akeyi ga garin ya ɗauki wani irin
sanyi mai ratsa ɓargon jiki. A hankali ya lumshe idanunsa ya buɗe a kan sararin
samaniya da tai wani irin fayau, ga garin yay luf-luf ƙamshin ƙasa na ratsa
hancinan mutane. A kan lips ya shiga furta addu'ar nan ta bayan saukar ruwan sama.
*‫ُمِط ْر َنا ِبَفْض ِل اللِه َو َر ْح َم ِتِه‬.*
_Mutirna bifadlil-lahi warahmatih._
(An yi mana ruwa saboda falalar ALLAH da Rahamarsa).
Kafin ya cigaba da tafiya cikin takun nan nasa na ƙasaita da izza tamkar mai
irga steps....
★★.....

Tunda ta dawo ɗakin kaikawo kawai take faman yi hankali a tashe. Duk nacin son
sanin wanene Ajmaal ɗin da takeyi bata kawo a ranta zai zama shi ɗin ne ba.
Tunaninta kawai ya kama Ajmaal ɗin ne kodai wani abu da ba shi take zato ba yana
mata yawo da hankali ne. Ji take komai ya kwance mata, komai ya ƙare mata. Ta
sadaƙar dan tata ta riga ta ƙare kawai. Yaya akai hakan ta kasance, yanzu komai
daya wakana tsakaninta da Ajmaal da Shahan-shan ɗin ne kenan? Kai ina impossible,
taya hakan zai kasance ma? Miyasa sir Fawzan zai mata hakane? Miyasa? Miyasa ya
rabbi shike nan ita kam.
Yanda take yi dolene ya baka tausayi da dariya. Ƙululu taji cikinta ya
murɗa kamar mai jin gudawa. Ta kai hannu ta matse cikin ƙirjinta kamar zai tarwatse
dan tashin hankali da tsabar ruɗanin da take ciki.....
“Nace na gama da ke ne?”.
A wani irin haukace ta ɗago ta kalla ƙofar jin sassanyar muryarsa bazata a
cikin kunneta, shi ɗinne dai tsaye hannayensa duka cikin aljihun wandon jikinsa.
Sam bataji shigowarsa ba, koda yake a buɗe tabar ƙofar tsabar ruɗani. Tafiya ta
farayi da baya-baya, jin zata ma iya sakin gudawar a wajen sai kawai ta sake kwasa
da gudu tai hanyar toilet.

Ta ɗauki tsawon mintunan da zuciyarta ke faɗa mata ƙilama ya gaji ya fita,


sai dai wani sashe na gargaɗinta. Jin an fara kiran sallar azhar ta sauke ajiyar
zuciya, ta san dai tabbas dolene ya fita ai yanzu. Alwala tayi, kai tsaye ta fito
tana ayyanama ranta ta saka ma ƙofar key kawai. Da sauri taja birki ganinsa zaune a
harɗe cikin zaman ƙasaitar nan tasa a saman kujerar ɗakin, sai kuma ta juya da
sauri zata koma dan yayi wani ɗam-ɗam da fuska.
“Zaki sha mamaki idan kika koma”.
Kamar zata fasa ihu ta dubesa, sai kuma ta ɗauke kanta ƙwalla na cika idonta.
(Shikenan Iffah kekam sai abinda ALLAH yayi, gaki dama ba uwa ba uba miya rage
kuma? Kawai yasa a tsireki) a zuciyarta take sambatun tana cigaba da takowa sum-
suma batare data yarda ta sake kallonsa ba. Miƙewa yay shima fuskar nan babu alamar
fara'a, idonsa a kanta. A gabanta ya tsaya mayen ƙamshin turarensa na cigaba da
addabarta, ga mamakin yanda yake abubuwa kamar ba Shahan-shan ɗin nan nasu da suke
hange da ga nesa ba mai shegen isa da izza na ƙara bata mamaki da ɗaukar komai
tamkar wani mafarki. Jinsa a kusa da ita sai kawai ta rumtse idanunta da ƙarfi tana
jiran abinda zai biyo baya.
“Na tafi?”.
Ya faɗa a hankali yana wani shanye idanunsa ƙasa-ƙasa a kanta. Da wani irin
sauri ta buɗe idanunta da ɗagowa ta kallesa tana sakin nannauyar ajiyar zuciya
saboda shock da furicin nasa ya sakata. Sai kuma ta kaudar da kan gefe dan salon
kallon nan nasa birkita ta yake. Muryarta can ƙasa-ƙasa ta jinjina masa kai.
“Magana nake so”.
Ya faɗa a fisge kamar wanda akaima tilas. Tsabar yanda take jin kusancin nasu
kamar zata shiɗe a hankali ta ce, “Uhhm”.
Ɗan sake matsawa yay gareta dab har tana iya jin saukar numfashinsa a kan
fuskarta. Jin saukar yatsunsa kan haɓarta ruf ta rufe idanunta da ƙoƙarin riƙe
rawar da jikinta ke neman farayi. Ya ɗan lumshe idanunsa dake yawo akan fuskar tata
yana ƙoƙarin shanye murmushin dake taso masa. A bazata kawai taji saukar lallausan
lips ɗinsa saman goshinta ya manna mata sumba mai lafiya da har sai da ta saki wata
ajiyar zuciya mai ƙarfi. Batare da ya sake cewa komai ba ya ja da baya ya juya ya
bar ɗakin fuskarsa shimfiɗe da murmushin da duk sonshi da basar da shi hakan ya
gagara. A ransa rayawa yake (Damisar takarda ga tsoro ga ban tsoro)
Da kallo ta bishi har ya fice, ta sauke ajiyar zuciya da kaiwa zaune jagwab
kamar wadda tasha gudu ta gaji, sai faman matse jikinta take waje guda amma yaƙi
daina tsumar dole ta kai kwance na wani ɗan lokaci, badan taji ƙarfi ba dai ta miƙe
tai sallar ganin lokaci zai shige....

Duk yanda yaso dai-daita kansa hakan ya gagara. Tabbas ya yarda SO wani
abune mai matuƙar kaifi. Duk yanda kaso ɓoyeshi da ƙin son bayyanashi hakan gagara
yake. Duk matsayinka, duk girman shekarunka, sai ya kaika ƙasa. Shi shaida ne akan
hakan, tunda gashi yana gani akan kansa. Gaba ɗaya idan yana a gaban mitsitsiyar
yarinyar nan manta shi ɗin wanene ya ke da matsayinsa. Ya rasa wannan abu haka mai
kama da kamar wata almara. A gurguje ya canja shiga da ɗaura alwala ya fita
masallaci. Ya wani tsume kamar bashi ba, dan a Shahan-shan ɗin sa ya fita mai
tsananin ƙasaita da izzar nan ga miskilancin tsiya.
Bayan idar da salla bai shigo ba ya zarce fada, umarnin isar da saƙon
tattaro masa wasu a cikin manyan masarautar ya bada. Cikin ƙanƙanin lokaci duk
wanda sunansa ya fito a zaman saƙo ya riskesa. Kafin cikar wasu mintuna duk sun
hallara. Duk da kasancewar yana a cikin fadar a wani matsakaicin falonsa yake zaune
ba cikin ainahin fada inda karagar mulki take ba. Da ga shi sai amintaccen
hadiminsa na amana da ako ina ka gansa shima zaka ganshi, idan ka cire ɗakin
barcinsa kawai. Suma ɗin yana shiga kai abinda ake buƙata da kuma gyarawa.
A zahiri zaka ɗauka hankalinsa kan television ɗin da ke aiki a falon suke,
dan manyan kaifafan idanunsa na kanta ne. A gabansa ƙyaƙyƙyawar butar shayi ce irin
ta hamshaƙan sarakai kalar golden mai tsananin ɗaukar idon mai kallo. Dan har wasu
irin fararen stones aka jera jikinta da ya sake ƙayatar da ita. Sai dai hankalin
nasa sam ba'a nan ɗin yake ba. Gaba ɗaya a tunanin zantukan Iffah ne na ɗazu. Dan
shauƙin da yake ciki bawai ya mantar da shi bane ba. Ya dai tattarasu ne ya ajiye
gefe domin basu nasu lokaci.
Sallama Sayeed Fayzul-haq ta saka amintaccen Ghazi ɗinsa da ke gefensa tsaye
ko gajiya bayayi amsawa. Sai kuma ya nufi ƙofar domin duba wanene. Shi dai bai
motsa a yanda yake ba, kai kace ma bai san abinda ake ba. Minti ɗaya da wasu
sakanni amintaccen nasa ya dawo, a gabansa ya zube murya cike da tsantsar girmamawa
yace, “Kariyar UBANGIJI ta cigaba da kasancewa zagaye da adalin shugabanmu. Sayeed
Fayzul-haq ne ke isar da saƙon kammalawar kasancewar kowa”.
Shiru babu alamar zai tanka har kusan mintuna biyu, sai ka rantse baima
jisa ba. Sai da ya mula dan kansa ya motsa lips da ƙyar. “Zasu iya shigowa”.
“Umarninka shine abin jiran kowa”.
Hadimin ya faɗa yana rissinar da kai sannan ya miƙe da sauri. Cikin abinda bai fi
minti uku ba dattijai masu cikakkiyar kamala da nutsuwa suka dinga shigowa ɗaya
bayan ɗaya a nutse. Duk wanda ya shigo sai ya miƙa gaisuwa kafin ya wuce ya zauna.
Sayeed Fayzul-haq ne ƙarshe hannunsa ɗauke da ledar da aka zuba kayan surkullen
nan. A gaban Tajwar Eshaan ɗin ya kai ya ajiye yana ɗan matsar da ƙyaƙyƙywar butar
shayin nan kaɗan. Leda ɗin ya buɗe sannan ya ja da baya shima ya zauna.
Yanzun ma sharewa yay tsahon wasu mintuna kamar bashine yasa a tarasu ba,
kowa kuwa a cikinsu ya zubama ledar ido musamman Miran Arshaan da jikinsa har tsuma
yake, sai dai yana ta faman taushe kansa. Tajwar Eshaan da ke nazartar kowa ta
ƙasan ido ya motsa lips ɗinsa da ƙyar yana mai buɗe idanunsa masu saka mara gaskiya
tsuma tar-tar a kansu da ƙyau.
“Bana bukatar sanin wanda ya ajiye su balle dalilin ajiye sun. Sai dai zan
gargaɗi mai ajiyewar da abu uku. Eshaan a koda yaushe yana zagaye ne a cikin
kariyar UBANGIJINSA insha ALLAHU. A komai na ina amfani da zuciya ne fiye da ƙwanji
na da ƙwaƙwalwa. A kuma duk sanda maƙiyi ya sokeni ta baya sunansa matsoraci a
wajena, jarumi gaba-da-gaba yake zuwa filin daga in har ya cika sunansa jarumi.
Saboda haka, idan har ya shirya na bashi tabbaci ɗan Haysam bin Abdul-majeed Aliy
Qutb a shirye yake shima”.
A take falon gaba ɗaya ya ɗauka kalmar neman afuwa da fatan hucewar zuciya
ga Shahan-shan. A baɗini kam baka jin komai sai bugun zuciyoyi, yayinda ake ma juna
ƴar kallon kallo, dan ba ƙaramin ratsasu kausasan kalaman Tajwar Eshaan ɗin suke
ba, duk da a zahiri shi ya yisu ne cikin sanyin nan nasa mai amon nutsuwa da
cikakkiyar ƙasaitar tabbatar da shi ɗin wanene.
Ƙananun maganganu ne suka nema fara tashi kowa na ƙoƙarin son ganin ya kare
kansa. Yi yay kamar bama jinsu ya ke ba, sai da Sayeed Fayzul-haq ya fargar da su
sannan falon yay tsitt. Wani ɗan ƙyamusashen tsoho da suke kira Sayeed Tasadduq-
Husain da fuskarsa ke nuna alamun ɓacin rai ya dubesu cikin ɗacin murya, a karo na
farko da tun shigowarsa falon yay magana. Shima ɗin kamar Uncle ya ke a wajen
Tajwar Eshaan, mutum ne mai tsananin tsage gaskiya a duk yanda tazo shiyyasa bai
cika farin jini a wajen su ba, alokuta da dama idan yaga an dabaibaye rayuwar
Tajwar Eshaan da yawa yakan nuna ɓacin ransa har ya faffaɗi maganganu masu ɗaci, to
a yau ɗin ma tin ganin waɗan nan kayan sirkullen ɗazun ya nuna takaicinsa, hasalima
shine ya ingiza Sayeed Fayzul-haq kan Tajwar Eshaan ya tarasu ayi maganar kar a
wani rufe, gara wanda ya ajiye abubuwan ya san an san ya ajiye ɗin.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN


MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (30)

..........“Ƙoƙarin kare kai bashi zai fidda kowanne mu ba, duk da bazai yiwu ace
dukanmu anan ne muka aikata ɗin ba, sai dai dole duk ma wanda ya aikata a cikinmun
yake dai. Shin wace irin rayuwa ce muke son ta cigaba da yaɗuwa a wannan zuri'ar
tamu ne bayan kasancewar mu jini ɗaya?. Shin mi muke nema wanda UBANGIJI baiyi mana
shi ba? Mi muke buƙata da ga siffofin shugaba na gari da ALLAH bai azurta bawan
ALLAHn nan da shi ba da a kullum muke son nuna bore da hukuncin ALLAH? Ni na rasa
gane mi duk mai ƙoƙarin assasa fitine-finen nan ke buƙata ba ko san zuwa. Shin
mulkin yake so ne? Ko kuwa rayuwar wannan bawan ALLAH da'a kullum alkairinsa ke
zagaye da mu..” takaici ya saka hawaye ziraro masa. Handkherciff yasa ya share tare
da sake dubansu ya cigaba da faɗin, “Shike nan babu mai hana koma waye yin yanda ya
ke so, sai dai ya sani a duk randa yazo hanunmu wlhy ko shi waye a cikinmu sai yayi
dana sani da nadamar kasancewarsa cikin zuri'ar mu. Sannan tarihi zai masa tanadin
da bazai taɓa goge sunansa ba a matsayin azzalumi mai fuska biyu a cikin zuri'ar
mu. Wannan faɗan ba nashi bane namu ne, dan mu nan da mu akeyi ba da shi ba, dan
haka duk wanda ya shirya bismillah muma mun shirya”.
A zahirance duk nuna goyon baya a kan maganarsa sukai, sai dai a ransu ji
suke kamar su shaƙo wuyan Sayeed Tasadduq-Husain ɗin. Yasan da hakan, shiyyasa ko
kallo babu wanda ya ishesa a cikinsu, ya kuma ci dubu sai ceto. Miran Arshaan da
gaba ɗaya ya ke jin kamar ya danne Sayeed Tasadduq-Husain a wajen ya masa yankan
rago ya taushi zuciyarsa da ƙyar, dan wannan wata dama ce a garesa, rashin ganin
Miran Jasim a wajen yay masa da ɗi, dan haka ya miƙe cike da dakewa da tsan-tsar
iya makirci shima ya fuskancesu ya zuba kausasan kalamai, da ga ƙarshe ya rufe da
faɗin, “In ma tsoro da kunya sun hana duk ma wanda ya aikata ɗin zuwa nan batare da
mun farga ba to na tabbata akwai mabiyansa da irinsa anan ɗin, sai su isar da
saƙonmu na tabbatar da duk randa mutum yazo hanunmu sai ya yabama aya zaƙinta a
wannan masarauta kamar yanda Sayeed Tasadduq-Husain ya faɗa”.
Kalamansa kam tabbas sun saka wasu fara hasaso abinda yake son dama ai
hasashen, sai dai babu wanda ya furta a zahirance aka cigaba da tattaunawa.

Ya ɗauka tsahon lokaci da su a falon suna tattaunawar, dan suna fitowa da


ga zaman ma masallaci suka zarce sallar la'asar. Bayan an idar ya koma sashensa.
Bai nema Iffah ba yanzun kam. Dan yana buƙatar ɗan hutawa saboda yau zai ɗanyi
fitar dare ta sirri zuwa cikin gari. Sai dai koda ya shiga ɗakin ma sai yaji baida
buƙatar kwanciyar saboda ransa a matuƙar ɓace ya ke har yanzun. Tashi yay ya canja
kayansa cikin wasu fararen wando da riga tas na kamfanin *Nike* da sukai masa
matuƙar ƙyau duk da ya sane badan kwalliya ba. Takalma ya ɗaura a ƙafarsa baƙaƙe ya
ɗauka p-cap a hannu ya fito cikin takun nan nasa mai tabbatar da shi ɗinne dai ko
da ga nesa. Cikin sauri amintaccensa ya miƙe ƙansa rissine, ba sai yace masa ga
abinda yake buƙata ba, kai tsaye ya fahimci inda suka dosa. Kafin ya ƙaraso gareshi
yay saurin ɗaga waya yay kiran sarkin barga. Ana ɗagawa yay saurin bashi umarnin
shirya dokin amana da kowa ya san in ba shi ba Shahan-shan ɗin baya hawan kowanne
doki a gidan. Wayar ya katse dan dai-dai da isowar Tajwar Eshaan ɗin, ganin ya nufi
elevator batare da ko kallon inda yake yayi ba shima ya zabura. Cikin sauri ya
danna floor 1 bayan ƙofar ta maida kanta ta zuge.
Suna fitowa da ga lift ɗin ɓoyayyar hanyar da zata fiddasu batare da ko
hadiman ƙasan sungansu ba ya nufa, amintaccensa biye da shi. A wani ƙaton fili suka
fito, an gyara wajen da wani irin farin yashi mai matuƙar ɗaukar idon mai kallo da
birgewa. Kasancewar ruwan saman da aka sha sai wajen ya sake bada wani yanayi mai
matuƙar daɗi ga sassanyar iskar da bishiyoyin da aka ƙawata wajen na dabino na
bayarwa. Da ga ɗan nesa da su Sarkin barga ke riƙe da ƙyaƙyƙyawan farin dokin da
shi da kansa ya raɗa ma abinsa suna da ƙyautar ALLAH. Kamar yanda ɗabi'ar dokin
take suna fitowa yay wata irin haniniya da girgiza kai kace ƙamshin Tajwar Eshaan
ɗin yake ji ya shaida kasancewar sa a waje. Da wani irin gudun bajinta ya nufosu,
yana isowa gabansa yay wata irin ƙwafutar ƙasa yay girgiza da haniniya, har gashin
saman kansa zuwa wuya na wani tarwatsewa da haɗe kansa waje guda. A hankali Tajwar
Eshaan ya lumshe idanunsa yana sakin sassanyan murmushi da mutane kan jima basu
gani tare da shi ba sannan ya kai hannu ya shafi fuskar dokin yana masa magana
ƙasa-ƙasa da ko Sarkin barga da amintaccen hadiminsa dake tsaye gefe kawuna a
risine basa iya jinsa. Cikin wani irin salon da ke tabbatar da ƙwarewarsa a iya
sarrafa dokin ya damƙi linzamin sa cikin action mai matuƙar ɗaukar hankali da
bajinta ya ɗane saman sa. Cikin tabbatar da ƙwarewar da dokin ya samu a hanunsa yay
wata irin haniniya da ƙwafutar ƙasa ya ɗiba hanya tamkar a filin polo. Rere suka
fara ɗan gaske da sauran dokunan huɗu da aka sakakarma linzami batare da kowa a
kansu ba. Duk wanda ya ga yanda yake sarrafa dokin basai an faɗaba ya san shi ɗin
ƙwarren ɗan wasan polo ne kuma jarumin gaske. Dan cikin ƙanƙanin lokaci yay ma
sauran dokunan da babu kowa ɗin fintinkau, har ya sake dawowa ya koma sannan su
suka iso. Kaida gani kasan yana nishaɗi da wasan matuƙa. Sosai su sarkin barga ke
murmushi da jinjina jarumta irin ta gwarzon Sarkin nasu. Ko'a cikin dubu shi ɗin na
dabanne da kai tsaye za'a nuna a shaida. Dan suna da tabbacin da a lokacin yaƙi ne
yazo babu abinda zai hana ya zama babban jarumin da tararsa a filin daga abin tsoro
ne. Ya ɗauka tsahon lokaci yana wasan dokin har sai da yaji ya gamsu jininsa ya
tashi fiye ma da yanda yake buƙata sannan yaja linzamin dokin ya dire bisa ƙasa
cike da bajinta yana sauke numfashi ɗaya-ɗaya. Da sauri amintaccensa ya matsa
garesa hannunsa ɗauke da ƙyaƙyƙyawan tray mai ɗauke da gorar ruwa da glass cup.
Goran ruwan ya ɗauka batare da ya haɗa da cup ɗin ba, ya ɓalle murfin ya kai
bakinsa. Yasha kusan fin rabi sannan ya juyo ya juye sauran akan fuskar dokin nasa
yana ɗan murmushi. Haniniya dokin yayi mai nuni da isharar jin daɗin kasancewarsa
da adalin ubangidan nasa. Shima sai ya kai hannu ya share masa ruwan yana murmushi.
Ƙaramin towel Sarkin barga ya miƙo masa da sauri, bai musaba ya amsa ya goge
hannunsa da wuyansa sannan ya kai shi ga fuskar dokin shima ya share masa ruwan da
ƙyau. Yanda yake ma dokin da kansa dolene ka tabbatar akwai matuƙar shaƙuwa a
tsakaninsu mai birgewa da ƙayatarwa. (Ko dabba ma ta san me bata kulawa da nuna
ƙauna kenan☺️
😘)

★★...... ★.... ★...

Karo na biyu kenan da ta sake dawowa ɗakin ta samesa yana kai kawo rai a
ɓace. So take taji miye damuwarsa, sai dai tana matuƙar shakkar hakan. Dan mijin
nasu wani irin bahagon mutum ne da sam baida daɗin zama. Su dake tare da shine kuma
kawai suka san hakan. Amma ga al'ummar masarautar kowa yabonsa yake, shiyyasa a
lokuta da yawa idan suka kai ƙararsa ga Shahan-shan tun ma zamanin Tajwar Haysam
sai kiga ana ganin laifinsu na gajen haƙuri da rashin godiyar UBANGIJI.
Hayaƙin Shishar da ya bulbule ɗakin da shi ta ɗan saka hannu ta kore, dan shi
kansa ma da ƙyar take iya hangosa. Ƙundunbalar shiga tayi dan so take ta sanar masa
kiran da aka aiko ana masa da ga Shahan-shan, amma tsoro takeji ganin yanayin da
yake ciki. Muryarta na ɗan rawa ta risina da ga tsakkiyar ɗakin tana shaƙar hayaƙin
madadin iska da ƙyar. “Barka da wannan lokaci Abu Husam”.
Cak ya tsaya da ga zuƙar Shishar, yay wani masifar bulbulo hayaƙin bakinsa da
ya sake turniƙe ɗakin zuciyarsa na wani irin kumburowa da takaicin wace ƴar ƙunar
baƙin waken ce a matan nasa data manta da dokarsa. Sai da hayaƙin ya lafa sannan ya
iya ganinta da ƙyau, e ai ya sani sai ita ɗin, dan babu mai yawan shiga masa hanci
kamarta. Tsawa ya daka mata yana miƙewa a fusace. “Buhaysah! Ban ce bana buƙatar
ganin wani a sashe na ba da ga nan har sai idan nine na nema mutum?!!”.
A ɗan firgice ta zabura baya, sai kuma ta shiga girgiza masa kai jikinta na
ƙyarma. “Hakane, amma Ka gafarce ni Abu Husam, wlhy bada son raina na karya maka
doka ba. Saƙone da ga Shahan-shan ana buƙatar ganinka. Naga kada kai laifi ne
shiyyas....”
“Tasss!!”
Kakejin saukar wani lafiyayyen mari akan ƙyaƙyƙyawar fuskar ta. Dan mace ce
zankaɗeɗiyar gaske dirarriya. Duk da shekaru sunja gareta ƙyawunta a bayyane yake
gata ƴar gayu. Ba yau ta saba shan mari a wajensa ba, amma sai na yau ɗin yay mata
ciwo fiye da ko yaushe. A hankali ta ɗaga jajayen idanunta ta kallesa, fuskarta na
nuna alamar ɓacin rai, abune kuma da bai taɓa gani da ga gareta ba.
“Abu Husam minene laifina anan da har na cancanci mari dan ALLAH?”..
“Ƙari kike buƙata kenan?”. Ya faɗa a zafafe da sake yunƙurowa zai sauke
mata wani duk da jin wani shakkarta a yau ɗin da yaji ta shigesa.. Abin mamaki da
firgici ga Miran Jasim, sai ga Buhaysah kam ta riƙe hannunsa caraf.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*


*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (31)

..........Abune da bai taɓa faruwa ba a tsakaninsu, a tsahon shekarun da suka


kwashe tare na aure talatin da ɗaya cif. Cikin ido take dubansa da wani irin kallo
mai gigita zuciya “Jasim tsahon shekaru talatin da ɗaya kenan nake zaune a
ƙarƙashin mulkin mallakarka. Nayi juriyar nayi kawaicin amma na fahimci kai ɗin
gafalalle ne da baya gane komai a rayuwarsa sai son zuciyarsa. A da dai na haƙurce
maka na shanye, amma a yanzu zan tabbatar maka dai-dai nake da kai asararre kawai
da ya girma bai san ya girma ba!”. Ta yarfar da hannunsa gefe da wulla masa wani
irin mugun kallo ta juya zata fice. Wata irin zabura yay da ga sumar wucin gadin
mamakinta daya riskesa, ya wani shaƙo wuyan rigarta ta baya ya fizgita jikinsa na
rawa. Kiyyyyy rigar ta shiga kecewa, hakan yasata yin gaba. Tsabar shi cikakken
mugune yasa ƙafa ya taɗeta. Mummunar buguwar da ta sakata ƙwalla wahalalliyar ƙara
tai a ƙasan wajen. Cikin rufewar idanu yasa ƙafar ya taka mata gadon baya sai ga
ƙashi na bada sauti.
A guje suka dinga rige-rigen shigowa dan ƙarar tata ta matuƙar ratsa
kunnuwansu. Basu kaɗai ba hatta da hadiman dake musu hidima a sashen babu wanda zai
ce baiji ƙarar baiwar ALLAHr nan ba. Ganinsu baisa ya dakata da dukanta ba. Cikin
wata iriyar fusata babban ɗansa da itace mahaifiyarsa Husam yay wani irin kukan
kura ya hankaɗashi baya sai da ya daki bango. Baiyi wata-wata ba kuma ya damƙi
wuyan rigarsa ya shaƙeshi dan shima yaron tsageran kanshi ne. Kaf halin Miran Jasim
ɗin ya kwaso, sai dai duk da haka yana bala'i bala'in son mahaifinsa. Ya jima da
ciwon dukanta da mahaifinsa keyi duk da bata taɓa fitowa fili ta sanar masa ba. Tun
yana yaro ko shatin yatsu ya gani a fuskarta ya tabbaya sai tace bakomai ko bigewa
tayi. Sai bayan ya girama ne ya fahimci mahaifinsa ne ke marinta kamar yanda suma
sauran matansa biyu ba tsira sukai ba.
Rawa jikin sauran matan nasa ya shigayi, sun rasa ma wa zasu bama ɗauki,
shi da Husam ya shaƙe ko Buhaysah da ke kwance tana madoɗowar azaba. Gwara kansa da
bango da Husam yayi yana ƙaraji ya sa matan yin kansa da sauri suna kuka da roƙon
Husam ɗin ya sakesa. Amma ina yaron nan ƙara gwara kan Miran Jasim yake yana kai
masa naushi kamar ba mahaifinsa ba. Ga wani irin ƙarajin ɓacin rai yanayi mai haɗe
da kuka.
Sukam al'amarin nan yafi ƙarfinsu, hankali tashe suka shiga neman number
Miran Arshaan amma ba'a daga ba. Har kira uku babu alamar za'a amsa dole suka maida
akalar kiran ga Daneen Ammarah domin ta sanar da Mammah da Sayeed Fayzul-haq
kasancewar sun san yana ɗan jin shakkarsu, dan daga Malikat Haseenat ɗin har Sayeed
Fayzul-haq ɗin basa ɗaukar raini ko wasa a garesu dama masarautar kowa yasan haka.
Wayar ta riski Sayeed ne lokacin da yake fitowa daga sashen Tajwar Eshaan
bayan masa rakkiya daga sallar la'asar da suka idar. Itama Daneen Ammarah lokacin
tana ƙoƙarin tashi da ga abin salla. Hankali tashe duk suka nufi sashen Miran Jasim
ɗin har da Malikat Haseenat ɗin da aka saka a mota, dai-dai da shima Miran Arshaan
ya nufi can dan shima yayi mamakin rashin ganinsa wajen tattaunawar da akayi duk da
yasan dai ransa a ɓace yake matuƙa. Dan tun jin Tajwar Eshaan bai fito fada ba da
safe ransu ke'a jagule. Yanzu kuma a wannan zaman ashe ma akansu ne akayisa duk da
dai shi Tajwar Eshaan ɗin bai fito fili ya ambaci suna ba, amma duk da wannan sanin
da yay akan Miran Jasim ɗin ya zaɓi yimasa zamba cikin aminci dan a ganinsa lokaci
yayi da shima zai dakata da ga rakkiyar Miran Jasim ɗin ya fara yaƙin kansa...

Da ƙayar aka ɓanɓare Husam da ga shaƙar da yay ma Miran Jasim, yaraf ya


zube ƙasa hannunsa kan maƙoshinsa yana kakari. Idanunsa sunyi ruƙu-ruƙu tsabar
yanda yaji shaƙar nan, ga kansa daya fashe saboda ƙuma masan daya dinga yi sai jini
yake yi. A gefe ga Buhaysah da ke kukan wahala Husam ya je ya rungumeta yana kuka
da alama dai yaji mata ciwo a baya koma ya karya ta ne oho. Malikat Haseenat da ta
ɗan girgiza kanta da duban Sayeed. A matuƙar ruɗe Sayeed Fayzul-haq ya jinjina mata
kai. Waya ya ciro yay kiran clinic ya bada umarnin a kawo ambulance ƙofar sashen
Miran Jasim ɗin.....

A gaggauce aka miƙa Miran Jasim da Buhaysah asibiti. Husam kuma Malikat
Haseenat tasa Daneen Ammarah su wuce da shi sashenta, yaron sai kuka yake mai
matuƙar cin rai da zai baka tausayi, dan duk wanda ya kalla mahaifiyarsa yasan
akwai babbar matsala a bayan nan nata da mahaifinsa ya taka
Jigum-jigum sauran matansa da yara suka zauna. Kowa ka gani cikin damuwa. Dan
wannan abun kunya ne da in har ya fita koda a cikin masarautar ne bazasu taɓa jin
daɗi ba. Mijinsu mugu ne, dan ba yau ya fara kai hannunsa kansu ba, sai dai in ka
cire Tajwar Haysam da Malikat Haseenat da mahaifiyarsa Ameera Banafsha kafin ta
mutu babu wanda yasan hakan. Ko ƴayansu Husam ɗinne kawai ya sani sai mai bi masa
Faida data zama babbar budurwa, inda ma ALLAH ya bata miji da tuni tai aure. Koda
yake ba mijin ta rasa ba, taƙi sauraren samarin ne saboda mutuwar son Tajwar Eshaan
da takeyi tun dawowarsa ƙasar ruman. Hatta da mutuwar matansa bai taɓa saka Faida
jin zata iya daina son sa ba. Randa ya bayyana fuskarsa ba ƙaramin hauka tayi ba,
duk da kuwa itama ɗin ƙyaƙyƙyawa ce sosai, sai dai shi kuma baima san tanayi ba..

Abinda suke gudun dai kam sai da ya faru, dan tuni hadiman sashen nasu suka
fara zare jiki kai gulma ga iyayen gidansu. Dan wannan al'adace ta masarautar. Mafi
yawan hadiman kowane sashe zaka samesu ƴan leƙen asirin ɓangarori daban-daban ne,
duk da iyayen gidansu kanji a ransu akwai ƴan leƙen asirin bazasu iya banbance su
ko fitowa suce ga su ba balle su fiddasu a masu hidimar tasu. Hakan yasa dole kowa
ya haƙura da kasancewa cikin taka tsantsan kawai. Fitar wannan magana kuma sai tai
dai-dai da wadda ta fara yawo na sakama Tajwar Eshaan kayan tsafi a kujerar zamansa
da maganar Miran Arshaan da kai tsaye aka fara fassarata da cewar da Miran Jasim
ɗin yake. ga kuma abinda ya aikata yanzu na sake tabbatar da maganar Miran Arshaan
ɗin akwai ƙamshin gaskiya kenan.....

★★.... ★....

Iffah kam da bata san mike faruwa ba rabonta da ganin Tajwar Eshaan tunda ya
bar sashen ɗazun da azhar. Duk da dai itama barcinta ta sha bayan idar da sallar
azhar ɗin. A makare ma tai sallar la'asar. Kaɗan ta tsakuri abincin da aka kawo
mata har ɗaki. Sanin babu mai hawowa floor ɗin na ƙarshe sai shi da amintaccensa
yasa ta ɗauka wayar da ya faɗa da card ɗin data gani ta fito katafaren falon da
wani irin ƙamshi mai masifar daɗi ke tashi. Shiru babu kowa hatta da television a
kashe suke, dan girman falon yasa kusan tv uku ne. Itama kallon bawani ya ɗaɗarata
da ƙasa bane, barta dai da son bibiyar labarai saboda yanda take matuƙar ƙaunar
aikin jarida. Shine burinta, kuma Insha ALLAHU sai ta cika shi in har ta cigaba da
numfashi a doron duniya. Cikin ɗaya daga lafiyayyun kujerun ta shige tana mai bin
haɗaɗɗen falon da kallo kamar yau ne ta fara shigarsa. Komai na ciki ka kalla kasan
an narka dukiya mai ban mamaki, ya fita tsaf kamar ba'a duniyar mutane ake ba (😂to
dama irin wanga falo kam ai sai duniyar novel🤣 lols). Baki ta ɗan taɓe tana
ƙunƙunin da ita ta barma kanta sani, daga haka takai kwance ta fara sarrafa wayar
domin yin online shopping ɗin da ya umarce ta, dan bata son takurama Mamy kunyarta
ta ke ji, akan abin nan daya faru tana jin nauyin haɗuwa da mutane biyu, Malikat
Haseenat da Daneen Ammarah, saboda yanda ta shayar da jininsu guba amma su goyon
baya da son bata kariya ne burinsu, wannan al'amari na bata mamaki da ƙara sakata a
kunyar gudun haduwa da su.
Wasu kayan motsa jiki ne kalar pink sukai matuƙar fara ɗaukar hankalinta, ta
shiga sakin murmushi tana yaba kayan a zuciyarta. Sai dai kuma ganin kuɗin da aka
rubuta na sayensu ya sata zaro idanu waje. Sai kuma ta ɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa
tana ƙunƙuni wai ai dai kuɗin ma nasu ne su talakawan RUMAN, garama ta ci musu. Da
wannan shawarar zuciyar tata ta dinga jidar kaya masu ƙyau da tsada tana ƴar
dariyar muguntar yau sai tama asusun nasa wawason taron dangi zai gane ita Iffah
bata wasan yara bace. (Ni dai nace hummmm 😂)
Ganin magrib ta gabato ga ɗan sanyi-sanyi na ratsata ya tadata a falon ta
koma ɗaki. Shigewarta babu jimawa ya shigo shi kuma da ga wajen hawan doki. Ɗan
waige-waige ya shigayi a falon saboda jin ƙamshin turarenta. Ganin dai babu alamar
mutum ma ya sashi fesar da numfashi cike da basarwa ya nufi ciki. Bai jima ba sosai
ya sake fitowa cikin shirin tafiya masallaci. A kallo ɗaya da zakai mai zaka
fahimci wanka kawai yayi ya fito. Sake ficewa yay gabatar da sallar magrib.....

★★.....

Kamar yanda labarin abinda ke faruwa yaje kunnen kowa a masarautar haka itama
ya isa nata kunnen. Dai-dai amintacciyar hadimarta na sanar mata Jasrah ta shigo a
rikice. Malikat Bushirat da gaba ɗaya hankalinta yay masifar tashi jin wai an samu
kayan sihiri a karagar mulkin Shahan-shan tabi Jasrah da ke shigowa itama a masifar
tashin hankalin da kallo. Tsawa Jasrah ta dakama Hadimar, cikin rawar jiki ta tashi
ta fice.
Kafin ma hadimar ta gama ficewa ta fara magana a masifar tashin hankali
hawaye na zubo mata. “Akia akwai matsala wlhy, ni dai wannan masifa ta isheni, kar
mutanen nan suyi galabar halaka mana Eshaan. Kiga fa da ga wannan musiba sai
wannan, ni wlhy gara ya sauka ya bar musu mulkin nan da dai mu rasa shi, dan ALLAH
ki kirashi muji a wane hali yake, zuciyata ta kasa nutsuwa duk da Abu Harith ya
sanar min bai zauna ba”.
Cikin sake shiga tashin hankali Malikat Bushirat da ke sauke numfashi da
ɗaɗɗaya idanunta a lumshe ta girgiza kanta, sai kuma ta buɗe idanun nata da ke
jajur. Ita duk wannan surutun bashi take buƙata ba, yaronta take son gani, so take
ta gansa da idanunta ta tabbatar da lafiyarsa ƙalau sannan koma miye da ke a ranta
sai ta fitar. Dan wlhy a wannan gaɓar taci matuƙar alwashin in har wani abu ya sami
ɗanta kamar wancan karon du da bai bar duniya ba azabar daya ɗan ɗana fansarta
shine ran kowane shege. Duk kuma wanda yay yunƙurin shiga mata hanci koda Malikat
Haseenat ce zata fyato ta. Ta shirya tsaf a wannan karon koda za'a babbakama DAULAR
RUMAN gaba ɗaya wuta sai ta ƙwatoma ɗanta hakkinsa ga duk wani mai hannu a kan
abinda ya faru bama Iffah kawai ba.........✍️

_Tofa ran manya ya kai ƙololuwa a ɓaci🧐._

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (32)


.........Fitowarta kenan a wanka tana ƙoƙarin shirin barci dan sanyi-sanyin da
garin ya ɗauka yasa tuni masarautar tai wani irin yin tsitt, duk da bawani dare ne
yay ba. A bazata wayar landline ɗin ɗakin ta fara bada sautin dake nuna alamar kira
ya shigo. Kamar wata mai son rarrabe gaskiyar hakan ko akasinta ta tsaya tana
kallon wayar harta yanke. Wani kiranne ya sake shigowa. Da ƙyar ta iya saita kanta
ta kai hannu ta ɗauka tare da kaiwa kunne tai shiru. Daga can ma shiru akai babu
alamar za'a tanka har na wasu sakkani da suka kusa haɗa minti ɗaya. Cikin ɗan
yanayin ƙufula-kufula da ƙosawa tace, “ALLAH zan yanke dan inada abinyi”.
Ba'a tanka ɗin ba, sai dai kuma taji kamar alamar an ɗan motsa da ga can.
bata fahimci motsin na miye ba, sai taji ta ƙara hawa sama. “Na kashe ne?”. Ta sake
faɗa a ƙufule.
(Fitinanniya komai masifa) ya faɗa a zuciyarsa yana ɗan sakin wani murmushin
da shi da babu duk ɗaya, dan sai ma mai tsananin saka ido ne zai tabbatar da yayi.
“Ki sameni a room 2. Idan kika ɓatamin lokaci kuma hummm...” Ya faɗa a can ƙasan
maƙoshi batare da ya ƙarasa ba dai-dai tana shirin katse kiran.
“Ya arrahaman Iffah kin kaɗe”. Ta faɗa a fili cikin waro ido tana sauke wayar
da tunanin ya yanke. Sai dai sarai ya jita. Safa da marwa ta shiga yi kamar wata
wadda ke'a cikin tashin hankalin rayuwa. Ita gaba ɗaya ma ta rasa mima take ji akan
al'amurin ta na yanzu da bawan ALLAHn nan. Tsoro ne ko miye?. Itace fa Iffah ɗin
nan maijin zata iya tunkarar kowa akan gaskiyarta. Mai ikirarin tabbatar da ɗaukar
fansar ƴan uwanta kansa. Mai jin zata fuskancesa fuska da fuska batare da taji zata
iya masa ragi a duk abinda ta shiryo masa ba. Sai gashi tun ba'aje ko'ina ba
lissafinta ya rikice. Abubuwa suna neman canja kansu a canjin data kasa fahimta.
Gargaɗinsa na ƙarshen umarni ya fara maimaita kansa cikin kunenta. Birki taja da ga
kaikawon, fahimtar halinsa data farayi na in har ya faɗa sai ya cika ya sata saurin
neman kaya ta saka a gurguje. Abaya ce mai matuƙar ƙyau red and black data haska
farar fatarta sosai. Ita kanta bata san kiyasa sai da ta zaɓo ba kafin tasa duk da
kayan barci tai niyyar sakawa da farkoa. Ga wani uban ƙamshin turarrukan sa data
baza tare da wanda aka kawo mata cikin kayan online shopping ɗinta da tun ɗazun
suka iso, kayan sunfa yi ƙyau babu na kushewa, amma kuma fa an ciri uban kuɗi da
har sai da ta razana daga baya. Dan hakama yanzu duk takeji ta rikice da tunanin
koma kuɗin data kashe masa ne zai mata faɗa a kai, ita wlhy bata san da gaske kuɗin
kayan da suka rubuta a jikin kowanne zasu iya cirewan ba fa.
Taku take a hankali kamar mai sanɗa ko wata budurwar hawainiya, babu abinda
zuciyarta keyi sai dukan tamanin-tamanin. Idan yace ta biyasa kudinsa itako batama
san yaya zatayi ba. Da ƙyar ta gano room two ɗin duk da bedrooms ɗin biyar ne kawai
take tunani a wajen. Sauran ƙofofin bazata iya tabbatar dana minene ba tunda ba
kowacce karambaninta ya taɓa kaita taɓawa ba bayan ta Gym a ɗazun. Taja wasu
mintuna uku masu ƙyau a ƙofar kafin tai ƙundun balar ɗaura hanunnta a handle ɗin ta
murɗa. Da sallama ciki-ciki ta shigo ɗakin da babu wani haske sosai, sai wani uban
ƙamshi mai ratsa kwanya da uban sanyin ac kamar ba sanyi ake a garin ba. Hannunta
na dama ta ɗan kai kan kafaɗarta ta haggu tana shafawa alamar sanyin ya ratsata.
Can ta hangosa cikin ƙyaƙyƙyawar kujerar da ke gefe guda biyu, yana sanye cikin
kayan barci farare tas da sukai masa ƙyau sosai, yanda hannun rigar ya kamashi sai
ya fiddo murɗaɗɗen damtsensa da a kallo ɗaya zaka san yana samun isasshen motsa
jiki. Lap-top ce a gabansa yana sarrafawa cike da ƙwarewa, sai butar shayi mai ƙyau
da ƙaramin kofin da ke tabbatar da sha yake yi. Duk da motsin buɗe ƙofar tata da
uban ƙamshin turarensa data bulbula ya zo hancinsa bai ko motsa ba balle ya nuna
alamar yasan da zuwanta, aikinsa yake hankali kwance.
Idanunta data zuba masa ta janye, a karo na farko ta fara jin tana son
sanin wai mi yake yi a laptop da a koda yaushe zaka gansa yana sarrafawa. Ko waya
takan daɗe bata ganta a hannunsa ba. Amma computer in har yana zaune to baka
rabashi da ita. Ganin har tazo gaf da inda yake bai nuna alamar yaji shigowarta ba
tai tunanin ko bai jitan bane. Sallamar ta sake maimaitawa ƙasa-ƙasa. Idanu ya ɗan
lumshe kaɗan ya sake buɗewa saboda yanda sassanyar muryarta ta wani ratsashi. Da
ƙyar ya iya danne abinda ke taso masa ya buɗe idanun akan lap-top ɗin ya cigaba da
aikinsa batare da ya motsa ɗin ba dai. Haushi ne ya kama Iffah a karo na farko, ta
san dai in har baiji sallamar farko ba babu yanda za'ai ace baiji ta yanzu ba.
Idanunta ta juya kamar zata ɓalla masa harara dan takaici, amma bazata iya ba, sai
kuma tai tunanin koma ta juya ta koma, nan ma tasan ko giyar kokino ta sha bazata
iya hakan ba dai. Tsaiwar ta cigaba da yi batare data sake motsawa ba itama, sai
bin ɗakin dai take da kallo. Duka bedroom ɗin data taɓa shiga a sashen nasa tasan
sun haɗu matuƙa, sai dai fa wannan ɗin na musamman ne gaskiya. Dan kamar ma duk
yafi waɗancan girma. Ƙatone na gaske, bayan katafaren gadon da zai iya cinye mutane
goma tsaf akwai wadrobe na glass kamar yanda gadon ma take ganin kamar glass ɗinne.
Hakama mirror da duk sauran tarkacen furnitures ɗin sun haɗu. Sai wasu rukunin
haɗaɗɗun kujeru suma pitch and gold ɗin kamar yanda gadon yake... Kai ita fa idan
tace ma zata cigaba da lissafi sai ta gaji, kawai dai ɗakin ya haɗu, komai na
cikinsa pitch and golden ne da suka dace da kansu.....
“Kin koma soja ne?”.
Nutsatstsiyar muryarsa mai cike da kamewa da ƙasaita ta ratsa kunnuwanta a
bazata. Kallonsa tai tana tunzura baki na haushi, yana a yanda yake tunda ta shigo,
ɗan latsin ashe yasan da shigowar tata. A zahiri kam cikin muryar shagwaɓa-shagwaɓa
haushi-haushi ta ce, “To ai ba'a bani wajen zaman ba”.
Shiru kamar bazai tanka ba, sai kuma ya ɗago kamar wani mai ciwon wuya ya
sauke idanun nasa masu haske da kaifi a kanta. Ƙasa tai da nata fuskarta har yanzu
a ɗan shagwaɓe, bata sake gigin ɗagowa ba sum-sum taje kujerar gabansa ta zauna tai
gefe da fuska. Ɗauke idanunsa kawai yay da ga kanta ya cigaba da abinda yake yi,
sai da ya sake kwashe wasu cikakkun mintuna huɗun sannan ya ɗago a hankali yana ɗan
firzar da iska. Ɗahowar tasa sai tai dai-dai da fara ring na landline ɗin gefensa.
Ganin yay kamar baiji wayar ba ta ɗago ta kallesa, bashi da niyyar ɗaga wayar har
ta tsinke, sai da a kira na biyu ya kai hannu ya ɗauka. Bayansa ya kwantar a jikin
kujerar da kai wayar kunnensa yana lumshe ido. Maimakon amintaccensa da yay tunanin
ji sai yaji muryar Malikat Bushirat tana sanar masa gata a falonsa.. kansa ya
jinjina tamkar yana a gabanta, sai kuma ya buɗe baki da ƙyar yace, “To”. Daga haka
ya miƙe yana kallon Iffah da ke binsa da kallo. “Muje” ya faɗa a taƙaice nan ma.
Bata da zaɓin da ya wuce bin umarninsa, bakuma tada hurumin tambayar ina zasuje ko
miya faru. Ta ɗaga kafa kawai a bazata taji lallausan hannunsa cikin nata, da sauri
ta ɗago ta dubesa, sai dai shi sam bama ita ɗin ya ke kallo ba.
Suna kusantar falon bugun zuciyarta na ƙara hauhawa. Da masifar sauri taja
wani irin bahagon burki lokacin da suke ƙarasowa tsakkiyar falon tai ido biyu da
Malikat Bushirat da ke zaune hakimce fuskar nan tata babu alamar ta taɓa sanin
minene ma murmushi a duniya. Hannun nata ta zare a cikin nasa ta fara ja da baya-
baya, cak ya tsaya a wajen tamkar wanda aka dasa, sai kuma ya basar batare da ya ko
waiwaya ba ya cigaba da tafiyar nan tasa ta ƙasaita.
Da sauri Malikat Bushirat da sam bata lura da Iffah ba ta miƙe, kafin ya
ƙarasa isowa inda take ita ta miƙe zuwa garesa ta wani rungumesa. Idanunsa ya
lumshe a hankali da sakin sassanyar ajiyar zuciya, dan abune da ya jima yana buƙata
amma bai samu ba. Kusan sakan ashirin tana rungume da shi kafin ta ɗagoshi tana
share hawaye, kallonsa ta ke cike da son tabbatar da babu abinda ya taɓa mata shi,
dan duk duniya babu abinda take so da ƙauna sama da shi. Tana masa wani irin
makahon so da ya zarta hankalin duk wani mai tunani...
“Ammie”.
Ya faɗa a hankali yana riƙo hanunta cikin nashi. Ɗayan kuma ya kaisa kan
ƙyaƙyƙyawar fuskarta ya share mata hawaye hankalinsa duk a tashe, dan ganin hawaye
a fuskar Ammien sa abune da bazai kasance ƙarami ba. Ya santa ya san mahaifiyarsa
jaruma ce da ko'a cikin dubu zai faɗa babu wani ɗar.
Sake rungumesa tai tana magana cikin ɗacin murya. “Wlhy da yau wani abu ya
sameka kamar wancan karon babu abinda zai hanani ɗaukar mataki akan koma wanene,
dan bazan yafe musu ba, na baya ma ba yafe musu nai ba Eshaan” sai kuma ta sake
ɗagosa da sauri, takarda da biron data ajiye a kujerar data zauna ta ɗauka, ta kamo
hanunsa shi dai yana binta da kallo, a cikin tafin hannun ta saka masa, babu alamar
wasa ko sassauci akan fuskarta ta furta, “A matsayina na UWA mahaifiya a gareka bin
Haysam Abdul-majeed, ina baka umarnin ka saki yarinyar nan, ka kuma janye duk wata
garkuwar da kai mata...”
Wani irin mummunan bugun zuciya mai kaɗawa da tashin hankali da bai taɓa
cin karo da shi ba a rayuwarsa yaji yana taso masa, amma yay jarumtar shanye komai
ya zubamata idanunsa a dake. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa, kamata yay ya
zaunar a kujerar data taso, kafin shima ya kai zaune gefenta a hankali dan ji yake
hajijiya na neman zubdashi ƙasa. Amma kasancewarsa gwanin kamewa ko'a fuska bazaka
taɓa tantance komai da ga garesa ba..........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63
Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (33)

........Ruwan da ke ajiye kan table ɗin cikin jug ya ɗauka ya tsiyaya, cike da
kulawa ya miƙa mata yana lumshe idanu da buɗewa. Kai ta girgiza masa zatai magana,
shima ya girgiza masa nata alamar kartace komai. Ya ce, “please Ammie”.
Ruwan ta amsa, kurɓa biyu tai masa ta ajiye tana sauke ajiyar zuciya, ta sake
yunƙurowa zatai magana ya sake girgiza mata kai dai. “Please Ammie slow dawn ki
faɗa min mike faruwa?”.
“So nake ka saketa kawai, ka janye garkuwar da ka bata, na sani dama
Saiful-malik yarinyar nan bazata taɓa barinka ba. Amma Mammah da kai da Ammarah duk
kuka gagara fahimtata, to gashi tun ba'aje ko'ina ba ta sake aikatawa. Yanzu badan
ALLAH ya sa shi Sayeed Fayzul-haq ɗin ya lura ba wani zancen ake ba wannan ba,
bazan iya jure rasaka ba a duniya wlhy Eshaan, dan haka ni kawai ka saketa na gaji
haka bazan iya ba..”
“Wlhy Ammie ban aikata abinda kike zargina da shi ba”.
A tare duk suka dubi inda maganar ke fitowa, Iffah ce tsaye kanta a ƙasa,
amma duk da haka ana iya hango yanda fuskarta tai jage-jage da hawaye. Abinka da
fara tai jajir musamman ma kan hancinta. Wani irin mugun kallo Malikat Bushirat ke
jifanta da shi, sai kuma ta miƙe cike da takun izza ta nufeta. Ji kake tauuuu!! Ta
ɗauke fuskar Iffah da mari lafiyayyu haggu da dama. “K! Har kinyi isar da ina
magana da ɗana ki kasance a wajen? Wacece k!? Ƴar uban waye k!?”.
Idanunsa ya rumtse da sauri jikinsa na wani irin yamutsawa, amma a zahiri
zaune yake a dake yanda ta barsa ko kallonsu ma bayayi. Malikat Bushirat ta shaƙo
Iffah da ko gezau batai a tsayen da take ba saboda taurin zuciya, duk da kuwa marin
ya matuƙar ratsata dan zata iya rantsuwa ba'a taɓa mata mari mai azaba irin wannan
ba. Yanda ta shaƙontanne yasa fuskarta ɗagowa, da wani irin gudu jini ya shiga
fitowa a hancinta yana sauka har kan hannun Malikat Bushirat, hawayen fuskarta kuwa
tsaf sun ɗauke, sai wani irin mugun jaa da idanun sukayi mai ban tsoro.
Malikat Bushirat da idanunta suka riga suka rufe ta ƙare matse wuyan Iffah
duk da ganin jinin tana zazzaro manyan idanunta da itama suka kaɗa sukai ja.. “Yau
zan kasheki na kashe banza wofi, sai naga ubanda ya tsaya miki da har kike tunanin
idanunki sunyi tsaurin halakamin yaro...”
Wani irin kakarin azaba Iffah ta shigayi, ga idanunta sun fara juyewa, jinin
hancinta ko sake gudu yake dan a tsinke yake (haɓo). Amma tsabar ƙarfin hali bakin
bai mutu ba, jajayen idanunta da ke neman wulƙicewa ta zuba cikin na Malikat
Bushirat tana sakin wani murmushin wahala. “A tunaninki kasheni ne zai canja komai?
To kinyi kus...ku...ren fa... fahimtar hakan Ammie, dan masu san kashe ɗakin zagaye
su...suke da ke. Idan kin kasheni ki ma... maciji kika kashe baki sare kanshi ba,
ki rubuta ki ajiya ko gangar jikina ta daina numfashi sai ruhina ya dawo wannan
masarautar ɗaukar fansar ruhin ƴan uwana......”
Wani irin yarfar da ita Malikat Bushirat da jikinta ke rawa yayi, dan wani
irin guguwar bala'i ta hango a cikin idanun Iffah masu matuƙar gigitarwa tamkar ba
ainahin idanun yarinyar ba. Akan jikinsa Iffah ta faɗa, dan yarfar da ita da
Malikat Bushirat tayi dai-dai da mikewarsa dama, sai dai kalaman Ammien sa da
shaƙar da tai mata kawai suka shiga kunensa da idanunsa, baiji komai na da ga
abinda Iffah ta faɗa ba ita. Hankalinsa ne yay bala'in tashi da ganin jinin da ke
fita a hancin Iffah, yay saurin tarota jikinsa ganin jiri na neman zubar da ita.
Sake harzuƙowa Malikat Bushirat tayi. “Please Ammie, Please! Please” ya faɗa da
wata irin raunananniyar murya mai sage duk wani kuzarin mutum.
Idanunta da suka gama juyewa gaba ɗaya ta watsa masa, tana mai nuna shi da
ɗan yatsa a kausashe. “Na baka nanda awa ashirin da huɗu in bakabi umarnina ba
zakasha mamaki Eshaan”. Fuuuu ta nufi Alevator batare da jiran amsarsa ba ta
shige....

Hankalin Tajwar Eshaan gaba ɗaya sai ya rabu biyu. Furucin Amminen sa ga kuma
jinin da ke zuba da ga hancin Iffah. Tsabar yanda ya rikice sai ya shiga laluben
waya. Hannunsa Iffah da ke ƙoƙarin ganin jinin ya tsagaita ta riƙe dan ba yau ta
fara haɓo ba. Kanta ta shiga girgiza masa tana magana da ƙyar dan ta shaƙu a
wuyantan nan. “Karka kira kowa Sultan Please. Haɓo ne kawai ka samun ruwa a kaina
in munyi sa'a zai tsaya”.
Kansa ya jinjina mata kawai, dan duk da ruɗanin da yake a ciki babu abinda
ya canja a nutsuwarsa da ƙasaitar nan. Wanda ma zai iya ganinsa a haka sai ya iya
ɗauka ai baima wani damu ba. Ɗagata yay cak cikin hannayensa yana tafiya cikin
takun nan nasa step by step babu wani gargada ko garaje a ciki. Ɗakin da suka fito
ya koma da ita. Kai tsaye cikin haɗaɗɗen toilet ɗin ɗakin ya kaita, faɗa masa duk
yanda Ummu ke mata idan tana haɓo tayi, cikin sa'a kuwa sai gashi ya tsaya. Sai dai
ba ita ba hatta shima kayansa jinin duk ya ɗan taɓa, nashi ma sai yafi bayyana
kasancewarsu masu haske. Dole ya cire rigar dan jini na ɗaya daga cikin abinda bai
son gani, yanzu hakan ma tsigar jikinsa sai tashi take yi, dakewarsa ce kawai ta
ɓoye hakan a zahiri. Gama cire rigar dai-dai da ɗagowar Iffah da ke son ce masa
thanks you. Cikin sauri ta maida idanunta ƙasa ƙirjinta na wani irin harbawa, dan
babu komai a cikin rigar, da ya ciren sai ya zam da ga shi sai dogon wandon pyjamas
ɗin kawai ya rage. Koda wasa bata taɓa sanin mutumin nan haka yake a murɗe ba kamar
wani ɗan wasan danbe ba, ita fa duk tsiwar nan tata haka kawai duk wani mai irin
suffar nan tsoronsa ma takeji, shiyyasa bata kallon wristiling koda wasan wasa.
Shiko da tun sanda ta maida kai ta duƙar ya fahimci inda ta dosa hanyar
fita ya nufa, sai da ya je gab da ƙofa a maganar nan tasa kamar ta dole ƙasa-ƙasa
ya furta “kiyi wanka” ya ƙarasa ficewa. Ta jima zaune maganar kiyi wankan na juya
mata a rai, tana da buƙatar wankan, amma tana jin kunyar yinsa saboda sanin bata da
kaya a nan. To amma tunda shine ya ce tayi tasan maybe ya ɗauka mata kamar wancan
ranakun. Da wannan tunanin ta gamsu da yin wankan. Sai da kuma ta kammala ta duba
babu bathrobe duk sai towels a bathroom ɗin. Kamar zatai kuka ganin duk basu da
wani girma, da ga ƙarshe ta samu ɗan babba da ya kai mata gwiwa da ƙyar.
Kamar mai shirin yin sata haka ta fito da sanɗa, ta saki wata wawuyar ajiyar
zuciya ganin babu kowa a ɗakin, da ɗan hanzarinta ta ƙaraso cikin ɗakin tana dube-
duben koya ajiye mata kayan, ganin dai babun tai ƙwalƙwal da idanu kamar zatai
kuka. Zuciyarta na raya mata ta koma ɗakin da kayanta suke, ɗan ɗagowa tai
firgigit dan jin motsi da tai har towel ɗin na neman suɓuce mata saboda tun asali
ita fa bata iya ɗaure towel da ƙyau ba sai Arfa ta mata, shiyyasa tafi son babban
towel da zata iya cikuyewa a hanunta ta riƙe.
Cak ya tsaya sakamakon saukar idanunsa kan wani damɓareren tabon tawadar
ALLAH a bayanta dake fari sol a ta ɓangaren kafaɗar damanta. Iffah da duk ta rikice
da ganinsa tuni ta ɗane gadonsa taja lallausan duvet ɗin sa ta cikuykuye jikinta
dake mazarin rawa. Babu abinda ta tsana kamar namiji ya gammata jikinta. Musamman
ma shi da takema kallon wani abu da ban. Gwanin naku tuni ya basar da haɗiye komai
kamar ma bai san da zamanta a ɗakin ba. Sai ma ƙarasa takowa da yay jikin gadon ya
ajiye mata kayan da ke hannunsa ya kai zaune shima ya bata baya. Idanunsa ya rumtse
zuciyarsa na wani irin harbawa da ganin ƙyaƙyƙyawar surarta da tabon nan na tawadar
ALLAH da ke a bayanta. Buƙatar son sake gani yake dan tabbatar da abinda zuciyarsa
ke cusa masa yana ƙaryatawa. Sai dai yasan haka gatsau gareta bazai yuwu ba, dan
haka sai kawai yama miƙe ya fice a ɗakin domin bata damar shiryawa.

Tsahon mintuna goma sha biyar ya ɗauka kafin ya sake dawowa ɗakin. Ta saka
kayan sai dai tana zaune a kan gadon ta cusa kanta cikin ƙafafunta komai da ya faru
na dawo mata tamkar mafarki. Dan tsantsar tsanarta data hango cikin idanun Malikat
Bushirat yaƙi barin ranta sam. Tasan zata iya ganin fiyema da haka saboda abinda ta
aikatama tilon ɗanta amma sai zuciyarta ke tabbatar mata akwai dai....
Motsin shigowarsa ta sata katse tunanin sai dai bata ɗago ba. Kallo ɗaya yay
mata a cikin kayan nasa da sukai mata burum-burum duk da t-shirt ce fara da wando
3quater ya ɗauke kai. Bayan minti ɗaya da wasu ƴan sakkani taji motsin zamansa kusa
da ita. Ɗagowa tai tana ƙoƙarin haɗiye hawayenta, dan wani kewar iyayenta da yan
uwanta takeji. Shayin da ya ajiye a ɗan coffee table ɗin gaban gadon ya tura mata
batare da ya ce komai ba. Ƙyakyƙyawan kofin ta bi da kallo, sai taji shayin ya
burgeta dan tunda ta shigo ɗazun dama ƙamshin ya cika mata hanci. Ɗan ɗagowa tai,
sai ko suka haɗa ido, ƙif-ƙif ta farayi da nata kamar zata sake sakar masa wani
kukan da take ƙoƙarin haɗiyewa.
“What?”.
Ya faɗa ƙasa-ƙasa shanyayyun idanunsa na bin hawayen fuskar tata da kallo. Sake
ƙwaɓe fuskar tayi a hankali ta furta, “Kai ne ai”.
“Nai miye?”.
Ya tambaya cikin ɗan waro idanunsa waje.
“Ni bana son kallo”.
Yanda ta faɗa tana tura baki da share hawayenta ba ƙaramin tunzurashi yay ba.
Amma sai ya kanne yana ƙara ƙanƙance idanun nasa a kanta da motsa lips ɗinsa kaɗan
yana binta da shegen kallon nan nasa. Sai kuma ya ɗan laɓe baki a fisge ya furta,
“Sadakina na kalla ai”.
Furucin nasa yazo mata a bazata, dakatawa tai daga ƙoƙarin kai kofin
shayin bakinta ta dubesa da sauri domin tabbatar da shi ɗinne ya faɗa ko wani
aljani. Bayan ita da shi ɗin dai babu wani a ɗakin, sannan kuma ya ƙi ɗauke idanun
nasa da ga kanta, sai ma sake narkesu yake da wani salon kallo mai saka tsigar jiki
tashi kamar mai jiran cewarta..........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (34)

..........Wani irin tashi tsigar jikinta ta shigayi da salon kallon nasa, yayinda
bugun zuciyarta ke amsa kuwwa cikin ƙirjinsa. Numfashi ta ɗan ja a hankali ta maida
idanunta ƙasa, batare da ta sake gigin ɗagowa ba dan haka yafi mata kwanciyar
hankali.
Ganin bazatace koman da yake buƙatar ji ba ya wani ɗauke kai gefe cikin
son basar da shock ɗin da ya fahimci maganarsa ta jefata yana wani lumshe idanunsa.
Sai kuma ya buɗe da sake juyowa ya ɗan ɗage gira sama, “Tunda bakin ya mutu mu
cigaba da maganarmu ta ɗazun?, dan da gaske ina son muyi aiki tare”.
Ƙin ɗagowa tai yanzun ma ta jin jina masa kai kawai alamar eh. Shiru ya
ɗanyi na wani lokaci kamar mai tunanin abinda zai fa ɗa, sai kuma ya nisa da ƙyar
ya furta, “Abinda ya faru ki ɗaukesa kamar bai faru ba, tana cikin fushine kawai.
Duk abinda kike buƙatar sani da ga gareni na baki da ma”.
Yanzu ma kanta ta jinjina masan tana wasa da yatsunta, ta fahimci akan
mahaifiyarsa yake magana. Batare da ta dago ba ta ce, “Miyasa ka yarda da ni, bayan
na sanar maka duk abinda ke raina game da kasancewa da kai? Har ma na aikata, na
kuma amsa na aikata”
Ɗan murmushi ya saki kaɗan yana mai bin yatsun kafarta da take wasa da su da
kallo, sai kuma ya kauda kan gefe yana ɗan lumshe idanun da buɗewa. Kai daka ga
yanayin nasa ka tabbatar bazai iya jure doguwar maganar ba, duk ma a takure yake da
yawan surutun. Iffah da ke binsa ta kasan ido da kallo sai ta samu kanta da kasa
daina kallonsa, a zuciyarta kam ayyanawa ta ke (murmushi yana masa ƙyau). Kamar ya
fahimci mi take ayyanawar kuwa ya tsuke fuskar. Wayar da ya ajiye a gefensa ya
ɗauka, yay ɗan rubutu ya ajiye gabanta. Rinannun idanunta ta sauke akan wayar.
_“Ki faɗamin gaskiya ya akai kika san an saka abubuwan can na ɗazun?”._
Shayinta ta cigaba da sha kamar bazatace komai ba. Sai kuma taja ajiyar
zuciya, cikin muryar nan tata dake shaƙe ta bashi amsa. “Kamar yanda na sanar maka
a mafarki na gani. Iya gaskiyar kenan”.
Bawai bai yarda da ita bane, dan ya fahimci ita tana cikin mutane marasa
ɓoye abinda ke ransu koda kuwa laifi ne a kansu. Amma zuciyarsa rawa take da amsar
tata kasancewar al'amarin bazai kama hankali ba, musamman ga irinshi da ba wani
gama sanin abubuwa irin waɗan nan yay ba da ƙyau. Wayar ya sake ɗauka ya rubuta,
“Miye alaƙar wanda kukai aikin farko da wannan?”.
Wayar ta ajiye tana ɗan murmushi, “A baɗinin abinda na gani suna da alaƙa, a
zahiri kam bani da shaidar tabbatar da hakan dan ni kaina ban yarda mafarki na zai
zama gaskiya ba”.
“Ina son na sansu”.
“Bita kawai kake buƙata amma nasan ka sansu”.
Jin yayi shiru ta sake nisawa da ajiye kofin. “Bayan nan mi kake son sani?”.
Kansa ya jinjina mata alamar babu. Ta ƙara faɗin, “Ni zan iya tambaya?”. Nan ma kan
ya jinjina mata alamar eh.
“Kace baka san duk matan da aka aura maka ba sai ni, a ɗan gajeren labarin da
naji kuma ance sai an kawosu sashen nan suke rasa ransu ai, bayan mutuwarsu ka taɓa
ganin gawarsu?”.
“Miyasa kike son sanin wannan?”.
“Saboda kace zamuyi aiki tare”.
“Wannan baya cikin aikinmu”.
“Shine mafi muhimmanci ma acikin aikin da zamuyi tare, dan nafi alaƙa da shi fiye
da wanda kake son alakantani da shi. Inaji a jikina mutuwar matanka bata da alaƙa
da yunƙurin waɗan nan Uncle's ɗin naka. Su nasu yaƙin da banne da wannan”.
Kallonta yake kamar idanunsa zasu zubo. Itako ta kauda kan gefe kamar ba
daga bakinta lafuzzan suka fito ba.
“Mi kike son faɗa?”.
“Abinda ya dace ka faɗa kafin faɗata. Ni nasan kasan su wanene Uncle's ɗin ka
da burinsu a kanka. Masu kashe matanka kawai kake buƙatar sani in har da haske
bakai bane ba”.
Tsabar yanda maganarta ta masa dirar mikiya a zuciya da brain bai ma san
sanda ya juyo da ƙyau yana fuskantarta ba. Eh tabbas ya jima da sanin su wanene
Miran Arshaan da Miran Jasim har da ma burinsu a kansa, tun kuma randa ta bashi
guba yaji a ransa su ɗinne, hakama kisan matansa da su yake dangantawa, su kuma
yake bibiya da son tabbatarwa. Amma magana mafi ɗaukar hankalinsa da ga gareta
furucinta na ƙarshe. “Basu bane ba fa?”. Zancen zuciya ya fito fili batare da ya
sani ba.
Jajayen idanunta ta zuba masa kai tsaye, sai kuma ta saki murmushi mai
ciwo. “Sultan ban shigo masarautar RUMAN domin kallon gine-ginen ƙawa da adon
zinari ba. Idanuna a buɗe suke fiye da yanda na mage basa barci a cikin dare. A
tunaninka na baka gubar da suka bani ne dan ka mutu?”. Ta juya idanunta da suka
fara bashi tsoro ma shikam tana sakin ƙayataccen murmushi. “Lala-lala, madarar dana
baka sam bata da alaƙa da wadda suka kawo na baka, wadda kuma na baka ɗin tun usil
dama bata kisa bace” tai wata ƴar dariya mai ƙayatarwa. “Kayi haƙuri, su fa wawayen
karatunsu karanta musu yake amfani suke da ni, basu san Fhareedah bint Zayyan bace
ke amfani da su. Bari dai na taƙaice maka karna jaka da nisa. Ni da kaina na kawo
kaina nan domin tabbatar da waye masheƙin ƴan uwana. Bani aka kawo domin bama
kariya ba....”
Gaba ɗaya Tajwar Eshaan yama kasa gane suma yayi ne? Ko kuwa ya zama butun
butumi ne oho shi bai sani ba. Abinda kawai ya sani idanunsa nakan aljana zai
kirata ko mima bai tantance ba.
Iffah da ke wata ƴar dariya ƙasa-ƙasa ta yunƙura zata sauka a gadon ganin
kamar ya zama gunki ne ma oho. Cak ta dakata jin an riƙota, maidota yay ta koma
inda ta tashin yana binta da wani irin shegen kallo data kasa bama fassara.
“Wacece ke!?”.
Kalmar data iya fitowa a bakinsa kenan a cikin dubunan da ke masa kaikawo. Da
gaske idanunsa razanata suke, dan haka ta kaudar da natan tana cigaba da
murmushinta. “Nikam maimaita wacece ni ko bitar karatu ne ya kamata an haddace.
Amma kayi haƙuri, Fhareedah bint Zayyan ce, mai jiƙaƙƙen shirin tarwatsa masarautar
ruman kamar yanda suka tarwatsa min ahalina. Wlhy da gaske nake bana yafiya, in har
nace sai nayi to sai nayi ɗin koda zan ƙarasa da bugun numfashina na ƙarshe.”
“Kin san zan iya kasheki a cikin ɗakin nan na binne gawarki kamar ba'ayiki
ba”.
“Shiiii!!”.
Ta faɗa a hankali da ɗaura yatsanta saman tausasan lips ɗinsa, cikin raɗa-raɗa
da ƙyaƙykyafta idanunta cikin nasa dake neman tsaida numfashinsa ta furta, “Da
hakan kake da tuni kayi, amma nasan kai ba mai kisa bane bin Haysam Abdul-majeed
Qutb....” sai kuma ta saki murmushi tana lumshe idanunta da har yanzu basu washe da
ga shaƙar da Malikat Bushirat ta mata ba, tare da yo ƙasa da yatsanta da ke kan
lips ɗinsa a hankali tabi takan kakkauran wuyansa tayo ƙasa kan ƙirjinsa da tai
matuƙar dannewa kafin ta taɓa ɗin, a saitin zuciyarsa ta tsaida ɗan yatsan da buɗe
idanunta dake lumshe. “Wannan zuciyar zinariya ce mai hasken diamond dake bugawa da
harbawar numfashin duk wani talakan ƙasata, ba ita kawai ba, kai a karan kanka
ZINARE ne ESHAAN”. Ta ƙare faɗa tana mai daddaga yatsan nata akan saitin zuciyar
tasa idanunta na cika da hawaye....
Ji kawai yay ɗan sauran ƙarfin da ya rage masa ya ƙarasa guduwa. Gaba ɗaya
jikinsa da yay mata runfa shima ya ƙarasa saki. Miya rage kuma? Miya rage masa da
zai faɗa akan wannan aljanar yarinyar yanzu kam? Taci nasara, kawai taci
nasara.....

🥱 Iffah! Iffah! Anya ke ba aljanar da Shahan-shan ɗin yake ambata bace. Ni ma


dai ƴar koran taki na sallama a wannan gaɓar.🚶

★★..... ★....
“Ashe abin kunyar da wancan wawan yayan naka ya aikata mana kenan yau a gidan
nan?. Wai shi sai yaushe zai san ya girma ne? A haka yake tunanin mulkar jama'a ko
gidansa bai iya adalci ba mtsowww!!”.
Fuska Miran Arshaan ya yatsine cike da rashin damuwar zagin da Ameera
Haifah ɗin kema ɗan uwansa Miran Jasim. A hankali ya zuƙa karan haɗaɗɗiyar tabar da
sai lokaci-lokaci yake ɗan sha shima ya fesar. “Kin kirani nan ne domin zagin wani
ko yin abinda ya dace?”.
Tsaki ta ɗan ja tana balla masa harara, “Naga kaima zagin nasa kake ai. Abinda
ya dace ɗin kuma ai duk dai a kansa ne. Dan kasan tunda wannan tsohon munafukin
Sayeed Fayzul-haq ya sani shi da tsohuwar can sai wannan maganar taje gaban wancan
ɗan ALLAH bani in raya gorin (Tajwar Eshaan take nufi🤭), yana sani kuwa kowa kamar
ya sani ne, ga shegen yaron nan da kaifin basirar tsiya matsiyacin wlhy zai iya bin
ta hanyar ya gano abinda yake fafitikar son ganowa dare da rana. Wlhy na tsani
yaron nan shi da uwarsa, dan duk abinda ubansa yamun a kansa zan rama har sai naga
baya numfashi a duniya zan huta”.
Saurin kallonta yay, Dan shi fa wannan tunanin ma baizo kansa ba yanzu tsabar
abubuwa sun ma kansa yawa..........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN


09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (35)

.........Karan sigarin hannunsa ya ajiye a ƙyakykyawan ƙaramin bowl ɗin gabansa na


glass “Ya akai banyi wannan tunanin ba, ya ALLAH”. Yay maganar yana miƙewa hannunsa
duka kan sumarsa ya shiga cakuɗata. Shi dama akwai ruɗewa idan abubuwa suka masa
yawa. Harara Ameera Haifah ta balla masa tana faɗin, (Kai dama ai jaki ba komai
kake fahimta ba, shegu biyu burina na cika na kawar da shegen yaron nan kuma bazaku
sha ba ai, kubar ganin da taimakonku na shigo masarautar nan, bazaku sha da ga
maidani abinda na za na yanzun). A zahiri kam sai ta saki murmushin yaudara. “Kaga
zauna Shahan-shan ɗin gobe, kai daɗina da kai ruɗiyar masifa”.
“Bazaki gane ba Haifah, duk yanda kike zato da tsammanin hatsabibanci shegen
yaron nan ya wuce nan. Wlhy yace ubansa bai iya komai ba akan taurin kai da shegen
kaifi”.
“Duk kaifinsa da taurinsa mune ajalinsa shi da wannan ƴar iskar yarinyar mai
bakin reza. Na rasa gidan ubanda suka samota sai kace ƴar ifiritan aljanu”.
(Iffah 😂).
“To dama micece inba ƴar ifiritan aljanun ba. Kina gani har yanzu iya
bincikenmu mun gagara gano inda tsinannun mutanen nan suke. Wai mu Barrister Akeem
zaici ma amana bayan mun yarda da shi”.
“Nifa gaskiya bana tunanin haka, nasan waye Barrister Akeem batun yanzu ba,
zaka tabbatar da yana da hujjar ɓoye kansa shima a duk randa ya bayyana kansa
garemu. Ai tunda har ya bamu haɗin kan salwantar da iyalan Barrister Abdallah Aas
da yake abokinsa dolene ya bada ƙafa. Kai dai mu cigaba da jiransa ɗin, Ni yanzu
duk bama wannan ke gabana ba, wannan haukan yayan naka ne, sai kuma ita waccan kuna
bibiyar lamarinta da gaske har yanzu shegen bakin nata na kulle dai ko?”.
Nannauyan numfashi Miran Arshaan ya saki, “Boka Barbushi baya aiki ya
warware sai in da kansa ya warwaresa, amma duk da haka Inaga zan jefa tsuntsu biyu
da dutse ɗaya. Zan ziyarce a safiyar gobe da safe”.
“Hakan ma yayi, ni bara na wuce dan naga asuba ma na gabatowa.” ɗan riƙota ya
sakeyi yana wani ɗan murmushin da kai hancinsa jikinta, murya can ƙasan maƙoshi ya
ce, “Ki ɗan ƙaramin lokaci mana, kwana nawa bamma sakaki a idona ba”.
Baki ta ɗan taɓe da janye jikinta tana cigaba da maida kayanta. Cike da
muryar yaudara tace, “Nima ina kewar taka ai, sai dai lokacin barina nan ɗin yayi.
Kaje ga wawuyar matarka can nasan ta kasa barci saboda kai ƴar wahalar”.
Haka kawai sai yaji zuciyarsa ta ɗan sosu da zagin da akaima Jasrahn yau, duk
da ba yau ne karo na farko da Ameera Haifah ke zaginta ba. Baice komai ba ya koma
ya kwanta yana ƙoƙarin sake kunna karan sigari. Itama tsaf ta gama kimtsawa cikin
kayan ɓadda kamarta, gabansa tazo ta ɗan kamo hanunsa mai riƙe da sigarin ta zuƙa,
a fuskarsa ta bulbula hayaƙin, hannu ya kai zai cafkota ta zille tana ƴar dariya ta
fice....

(Humm, na san dai masu karatu basu mance wacece Ameera Haifah ba. Itace
amaryar Tajwar Haysam mahaifin Tajwar Eshaan kenan. Bari na baku a buɗe. Ameera
Haifah dai itace su Miran Arshaan ke yawan ambata da matar nan. Sun santa ko nace
Miran Jasim ya santa tun kafin ta shigo masarautar. Dan karuwarsa ce, ko nace shine
ya maidata karuwar🤦 . Dan da farko tazo neman taimakonsa ne ya shige mata gaba ta
auri mahaifin Tajwar Eshaan marigayi Tajwar Haysam kenan saboda sonsa da take na
masifa. Ita kuma ɗiyar wani shahararren mai kuɗi ne Anwarus-sadat, ƴar gata ce ta
gaske a gidansu, ta fara son Tajwar Haysam ne lokacin data rako mahaifinta sukai
masa gaisuwar salla. Tunda ta gansa ta rikice itafa sai shi, shiko bai taɓa bi
takanta ba, a wajen mahaifinta ta amshi number sa, ta dinga takura masa da sakwanni
shiko ya share. Iya haukacewa tayi kansa har mahaifinta ya tunkari Tajwar Haysam a
lokacin amma ya bashi haƙuri kasancewar Ameera Haifah bata wuce sa'ar Tajwar Eshaan
ba ma, acewarsa tayi ƙarama a duk cikin matansa, dan ko Ameera Danish-Ara ta
girmeta sosai. Kamar ta haƙura sai kuma ta kasa a wata haɗuwa da sukai da Miran
Jasim cikin jirgi, shi da ya ganta sonta yake a lokacin, sai dai kuma ita kafin ya
furta sai tazo masa da batun yayansa, wannan abu yay masa zafi, amma da yake shegen
kansa ne sai yay mata alƙawarin mallakar Tajwar Haysam amma ta yarda da shi.
Masifaffen son ganin ta zama matar Shahan-shan Haysam ya sata amincewa.
Kasancewarta ƴar gata babu ƙwaɓa a cikin gidansu ya fara lalata mata rayuwa. Tun
kamar za'ai ɗaya a haƙura har ya maidata kamar wata matarsa😭, sai dai da ga ƙarshe
yaci nasarar cika mata burinta na zama matar Shahan-shan Haysam da taimakon Miran
Arshaan daya shige gaba wajen Malikat Haseenat kasancewar shi ɗan ɗakinta ne. Tunda
Ameera Haifah ta auri Tajwar Haysam bata sake yarda da Miran Jasim ba duk da yana
mata nacin hakan, ga shi kuma taƙi samun soyayyar Tajwar Haysam shi kuma, baya
wulaƙantata amma kuma babu ruwansa da ita, dan takai kusan wata bakwai kafin ya
yarda ya kusanceta dan gudun kar UBANGIJI ya kamashi da laifin tauye mata hakki.
Duk matansa babu wadda bata kawo masa mutuncinta ba, hakan ya bada gudunmawar jin
ya ƙara tsanar Ameera Haifah saboda yanda ya sameta. Da ga nan fa ya tattarata ya
watsar ko kallo bata ishesa ba. Itako tarayya da ita da yay sau ɗayan nan taji ta
sake haukacewa a kansa. Zamansu sam babu daɗi a tsahon shekara bakwai da suka
kasance tare, dan sai tayi da gaske yake haɗa shimfiɗa da ita. Farin ciki kam babu
tsakaninsu, dan ko murmushi sai dai taga yanayi amma ba ita ba har ALLAH ya ɗauke
abinsa. Bayan barinsa duniya ta koma cikinsu Miran Arshaan a dalilin jin sirrinsu
da tayi, a nan ne itama take sanar da su burinta na rama duk abinda Tajwar Haysam
yay mata akan Tajwar Eshaan. Daga nanne kuma Miran Jasim ya koma nemanta, a ɓoye
kuma tana tarayya da Miran Arshaan shima. Wannan kenan ALLAH yasa dai kun gane dan
nidai na zayyano babu ruwana🥱).
★... MALIKAT BUSHIRAT ★....

Tunda ta shigo sashen nata ta zube tama kasa motsawa. Babu abinda ke mata zuwa
da dawowa sai fuskar yarinyar da abinda ta gano a cikin idanunta. Tabbas anzo
wajen, kuma lallai anzo gaɓar. Gaɓar da a farko ba ita tai hasashen zuwa ba. Wai
ita, ita Malikat Bushirat, mahaifiyar Shahan-shan mai mulkin karagar ikon ƙasar
ruman baki ɗaya, yarinya ƙarama, ƴar talakawa ta kalla tsabar idanunta, ta sanar
mata _inma ta kasheta ta kashe maciji ne bata sare kansa ba, ko bata numfashi,
ruhinta zai dawo bibiyar fansar ruhin ƴan uwanta_. Kai kai kai, wannan wace irin
rana ce, wace rana ce haka tazo gareta? Itace fa, ita ɗin nan dai, tauraruwar
taurari, farin wata fitilar samaniya, rana mai rabama kowa aiki, taiku mai ruwan
ban mamaki, zakanyar da ba'ai mata wargi, buhun ƙayar da ba'ai masa danni, mace mai
kamar maza kwarine babu. Bahun barkono ba'ai masa shiƙa. Kokino ba giyar yaro ba
sai dai manya karami yasha ya kwana a jeji. Giwa taku da ga nesa isharar yara,
ƙarfe baka karyuwa sai da wuta, MALIKAT matar Shahan-shan uwar Shahan-shan ƴar
asali jinin asali. Takai zaune daɓas jin hajijiya na neman zubar da ita. A hankali
ɗakin ya shiga juya mata, sai kawai ta lumshe idanun ko hakan zai bata salamar da
take buƙata.....

★★.. SHAHAN-SHAN ★★...

Bayan ta gama zayyane masa birkitattun zantukanta guduwa tai tabar ɗakin, har
yayi yinƙurin bin bayanta ya fasa. Amma ko sau ɗaya bai rintsa ba, saboda yanda
kalaman nata masu tsananin saka ruɗani ke masa kai kawo. Zai iya rantsuwar wani
mahaluki bai taɓa bashi tsoro na gaskiya ba kamarta, tabbas yana buƙatar sake sanin
ainahin wacece yarinyar nan bayan sanin da ta sanar masa a baya. A hankali tambarin
nan ya sake masa flash a cikin idanunsa, tare da kalamanta akan bashi madara da
cewar ita ke amfani da su ba sukeyi da ita ba, ita ta kawo kanta nan bashi ya
kawota ba, sai kawai yaji zuciyarsa na wani irin rawa, ga kansa da ke masa sarawar
ciwo tun a dare da ta barsa.
Da ƙyar ya iya ajiye komai a gefe ya tashi zuwa bathroom, sai da ya fara
wanka sannan ya fito yay nafila ya ƙarasa da shirin fita massalaci.

★....

Saɓanin shi kaɗan ita Iffah tana baro ɗakin zubewa tai a inda ta shigo sai barci,
takai tsahon awa uku tana barcin kafin ta farka a firgice. Ta jiƙe sharkaf da zufa
bata wasa ba, ga mummunan mafarkin da tai na mata matuƙar kai kawo, dole ta
dangantashi da mummuna, dan yau ne karo na farko data farayinsa. Addu'a ta shigayi
kamar yanda kaka ya gargaɗeta a duk sanda tai irin mafarkin, sai da ta samu ƴar
nutsuwa sannan ta miƙe. Bathroom ta shiga ta wanke fuskarta, tsaye tai a gaban
mirror tana kallon kanta, sai ta dinga hango kamar duhu-duhu ta bayanta, babu
alamar zata tsorata, sai ma sake ƙurama mirror ɗin ido tayi, amma a ranta addu'oi
take karantawa. Dishi-dishin ta cigaba da kallon abun, sai kuma ya shiga bajewa
kamar wani hayaƙi ya fara ɓacewa. Juyowa tai a hankali, abin mamaki sai ko gashi a
zahiri hayaƙin yana bajewa cikin ƴan sakkani ya ƙarasa ɓacewa ɓat. Ajiyar zuciya
mai nauyi ta ja ta fesar, cikin halin ko'in kila kuma sai ta ɗage kafaɗa da sake
juyawa ga mirror ɗin tana kai hanunta ta baya ta ɗan shafo gefen kafaɗarta ta dama,
zuciyarta na raya mata ta ɗaga rigar ta gani, wata kuma na ture mata tunanin da
cewar mafarki fa ba gaskiya bane. Rashin matsaya ya sata ajiye komai gefe ta ɗaura
alwala ta fito. Nafila tayi kusan awa ɗaya harda karatun Alkur'ani duk da batai mai
yawa ba ta koma gado ta kwanta. Maimakon barci sai abinda ya faru tsakaninta da
Malikat Bushirat ɗazun ya shiga dawo mata a rai, tasan ta shaƙeta, bata tashi
tsintar kanta ba sai a jikin Shahan-shan tana haɓo. Ya taimaketa ya tsaya har tai
wanka ya bata kayansa ta saka ya bata shayi, da ga shan shayin ne bata tashi
tsintar kantaba sai yanzu a ɗakin nan da ta farka da ga mummunan mafarkin nan. Ya
akai ta shanye shayin daya bata da yanda tazo nan ɗakin bata sani ba..........✍️
_🚴Tofa wata jiƙaƙƙiya, Shahan-shan kayi takanka Iffah dai da alama ba.... (🥱
Bara dai na gimtse bakina)_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (36)

.........Yana cikin Gym ɗinsa tun barowarsa masallaci sallar asuba yana motsa jiki
amintaccensa ya isar da saƙon neman iso da ga Sayeed Fayzul-haq. Sayeed Fayzul-haq
shima amintacce ne a garesa yanzu, dan haka ya bada izinin shigowar tasa. Kallo
ɗaya Sayeed ya masa ya duƙar da kai, dan yau motsa jikin yake ko riga babu, dogon
wando ne kawai bai sa rigar ba, sai ƙaramin towel dake saman kafaɗarsa ya taimaka
wajen rufe jikin nasa. Batare da ya daina abinda yake ba balle kallon Sayeed ɗin
cikin ƙasaitar nan tasa da zafin da Iffah ta haɗa masa a daren jiya muryar ta sake
komawa ƙasa ya furta, “Akwai wata damuwa ne?”.
Sayeed Fayzul-haq yay saurin sake risinawa cike da girmamawa yace, “Eh to
badai mai yawa bace. Tun a daren jiya naso sanar da kai sai kuma na fasa dan nasan
ka shiga barci. Akan Miran Jasim ne da iyalinsa......” nan ya zayyane masa komai a
nutse.
Ɗan murmushi yayi a karo na farko batare da ya ce komai ba har tsawon wani
lokaci da Sayeed ya fidda ran cewar tasa ma. Machine ɗin da yake kai ya kashe, ya
sakko yana jan towel dake a kafaɗarsa rataya ya shiga tsane wuyansa zuwa fuska.
Zufa yake sosai kamar wanda yay wanka. Zama yay a kujera, da sauri Sayeed Fayzul-
haq ya ɗan zuba ruwa a kofi ya miƙa masa. Baiyi musu ba ya amsa, sai dai kurɓa huɗu
yay ya ajiye dan bai damu da shan ruwa ba idan ya gama motsa jiki, yafi son shan
shayinsa na ƙa'ida.
A fisge kamar an masa dole ya ce, “Mi Doctors ɗin sukace akan jikin nata?”.
Yasan Matar Miran Jasim ɗin daya daka yake magana, “Ya shugaban sun tabbatar da
taji ciwo musamman a ƙashin bayanta da ya taka. Wannan shine result ɗin binciken
nasu.” ya faɗa yana miƙa masa takardun dake hannunsa. Amsa yay batare da ya duba ba
ya ajiye gefensa. Hakan ya tabbatar ma da Sayeed ɗin yana buƙatar lokaci, dan shima
tunda ya shigo ya fahimci yau ƴan miskilancin ne da mulki a kusa. Dan haka ya
rissina ya masa sallama. “Afito lafiya”.
Idanunsa kawai ya lumshe batare da ya tanka ba. Shiru yayi a gurin kamar
mai nazari, idanunsa ƙyam akan file ɗin.....

★★....
Makarar da tai ya ja mata yin salla ba'a kan lokaci ba, ga jikinta na mata
ciwo sosai tako ina har tana jin buƙatar ɗan motsashi ko zata samu sassauci. Gym
ɗin da ta gono ranar a leƙe-leƙenta ta tuna. Yanda ya ƙayatu ya sake zaburar da ita
ta miƙe tana murmushi. Fitowa tai da ga ɗakin data kwanan batare data damu da
rashin ganin Tajwar Eshaan ɗin ba kasancewar tasan ɗakin barci dama ai sai wanda ya
zaɓa. Ɗakin jiya ta koma, ta buɗe kayan da tai online shopping ɗin nan da har yanzu
suna a jakar da aka kawosu. Pink kayan training ɗin nan na Company Adidas da suka
ɗauka hankalinta tun a waccan ranar ta ciro ta fara kimtsawa. Tsaf ta fito cikinsu
kamar wata babyn roba, bata damuba da yanda rigar ta tsaya mata iya kan ciki har
ana ganin jikinta, hakama wandon ya matuƙar kama jikin nata. Kayan sun fidda mata
ainahin shape ɗin ta masha ALLAH. Duk da tasan babu kowa da zai ganta sai da ta
ɗaura after dress a sama. Cikin ranta take addu'ar ALLAH ya sa dai yana can sama
yana motsa nasa jikin dan tasan dai da wahala ace ya fita iyanzu.
Ganin hadiminsa a ƙofar Gym ɗin da yay saurin zubewa yana gaisheta bai sa
takawo a ranta yana ciki ba, dan idanunta sun rufe da son zuwa ta ɗana machines ɗin
nan masu ƙyau. Cikin sassanyar muryarta tai sallama tana shigowa kanta tsaye. Kamar
wanda aka farkar da ga barci ya buɗe idanunsa da ke a lumshe. Sai dai kuma bai
motsa ba ya kai dubansa ga ƙofar shigowar inda yaji muryar tata ta gefen ido.
Mamaki ne ya kamashi dan baiyi zaton tama san da Gym ɗin ba, ganin kamar bata lura
da shi ba ya sake lafewa yana kallon ikon ALLAH.
Da ƙyar ya iya riƙe numfashinsa yana lumshe idanu da buɗewa lokacin data
gama yaye after dress ɗin data ɗoro saman kayan training ɗin ta ajiye kan wani
machine. Tun da ga saman gashin kanta dake ɗaure da ribbon a tsakkiya yana lilo har
zuwa takalma ɗin ƙafarta yabi da kallon nan nasa na ƙasan ido. Idanun ya sake
lumshewa yana ambaton sunan ALLAH, dan yau ne karan farko da ya taɓa ganinta a
ainahinta kamar haka, dan kayan sun lafe mata da ƙyau da fidda ainahin surarta fiye
da jiya da ya ganta da towel.
Oho ita dai bata san yana yi ba, sai ma faman kokawar yanda zata kunna
machine ɗin data hau take yi. Hararar Machine ɗin tayi tana ɗan diddira ƙafa na
haushi. Ya ɗan murmusa yana kauda kansa. Kusan sakkani ashirin ya miƙe a hankali
yana ajiye towel ɗin hannunsa. Tana ɗan duƙe da cigaba da ƙoƙarin son kunnawar taji
ɗumin mutum a bayanta. A zabure ta ɗago gabanta na faɗuwa, jikinsa ta jingina
kasancewar tsaye yake bayanta daf da ita sosai, shigewar idanunsu cikin na juna ya
sake ruɗar da ita ta janye jikinta da sauri tai baya sai ta koma tana fuskantarsa.
Kif-kif ta farayi da idanunta daka ganta kasan a ruɗe take, dan cikin sarƙewar
harshe ta furta, “Good morning”.
Ɗauke kansa yay cike da basarwa ya ɗan sake matsowa batare da ya amsa
gaisuwar datai masan ba, idanunta ta rumtse da sauri ta sake juyawa a yanda take
farko ta bashi baya. Kallon bayan nata ya sake ɗan yi ya kauda idanun, kaɗan ya
motsa lips ɗinsa murya can ƙasan maƙoshi cikin kunnenta ya ce, “Bissmillah” yana
kai hannu ya kunna mata tare da jan jikinsa baya duk a lokaci guda. Ji take inama
ƙasa ta buɗe ta shige ciki kawai ta huta. Tayi dana sanin shigowa Gym ɗin nan a
zuciyarta yafi sau dubu. Jin machine ɗin na neman zubar da ita ƙasa yasa dole ta
fara ɗan yin gudun, sai kuma ta sauke nannauyar ajiyar zuciya hangosa ya juya mata
baya ta cikin mirrorn da aka zagaye Gym ɗin gaba ɗaya. Yanzu kam ya saka riga, duk
da haka ta kasa sakewa, kaɗan-kaɗan sai ta kai dubanta kansa da ga inda yaken gaban
teburin wasan basket ball dan shima game ne mafi soyuwa a ransa bayan wasan polo da
ƙwallon ƙafa.
Duk abinda take yana hankalice da ita sarai, amma ya fuske domin bata
damar motsa jikin yanda ya kamata. Cikar mintuna ashirin da hawanta machine ɗin ya
ajiye ɗan abin 🎾 wasan basket ball ɗin ya nufeta. Ta gabanta ya zagayo, idanunta a
rufe da alama hakan yafi mata daɗi ko ta rufene dan shi oho. Da haƙori ya danne
lips ɗinsa yana kauda idanunsa da ga inda suka sauka, kashe machine ɗin ya sata
buɗe ido da sauri, dan duk da taji ƙamshinsa ya sake kusanto ta batai zaton shi ɗin
bane ba. Kamar zata fasa kuka ta duƙar da kanta da sauri tana tura baki gaba.
Lips ɗin nata ya ɗan zubama idanu, sai kuma ya janye yana ƙoƙarin barin wajen
da faɗin, “Next..” a hankali. Wani irin kwarjini da shakkarsa takeji, sai taji
bazata iya masa musu ba sam. After dress ɗinta ta ɗauka tana maidawa jikinta tana
nufarsa inda yake gaban wani machine ɗin. Komai baice mata ba akan after dress ɗin,
ya nuna mata yanda zatai da hannu ya bar wajen. Yanzu ma tanayi tana satar
kallonsa, ji take rigar na neman taɗeta amma ta fuske sai ɗan tattarota da tai a
hannu ta cigaba da yi da sauri-sauri dan ya fara mata daɗi. Yanda ya basar da ita
baya kallon ko inda take sai take jin ƙarin ƙaimi...
“Wayyo ALLAH na!”.
Siririyar muryarta ta ratsa kunensa a bazata, dan basket ball ɗin da yake ta fara
janye hankalinsa shima ba kallonta ya ke ba. Tsabar ƙasaita ta zame masa jiki a
hankali ya juyo duk da zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri-sauri, ganinta a
ƙasa wanwar ya sashi nufarta da ƴar sassarfar da bata canja komai a takun
nutsuwarsa ba. Itako ganin yanda yake tafiya kamar ma bai ga faɗuwar da tai ba sai
kawai ta fashe da kukan da ita kanta tasan na taɓara ne, dan koda ta faɗi ba wani
ta bugu bane sai dai tanajin zafi a ƙafarta da ƙugunta sosai gaskiya. Kaifafan
idanunsa ya sauke a kan hanunnta dake dafe da ƙugun nata, ɗayan kuma a agarar
ƙafarta madaidaiciya fara sol.
“What is Happening?”.
Ya faɗa da ƙyar fuskar nan babu alamar fara'a tattare da shi balle nuna alhini,
a can ƙasan ransa kam zafi yake ji a jikinsa shima kamar yanda ya fahimci tana ji.
Wani kukan taɓara-taɓara ta sake fashe masa da shi tana nuna masa agarar ƙafarta da
faɗin, “Shikenan ƙafana ya cire, ni dai ka kiramin Mamy da Jaddah wayyo ni Ummu,
Iyyani ƙafana ya karye Hanash Akhi”.
(Stubborn girl) ya faɗa a zuciyarsa idanunsa na wani shanyewa a kanta. A
zahiri kam yi yay kamar zai share sai kuma ya kai duƙe gabanta a hankali. Maimakon
duba ƙafar da take faman riƙewa cak ya ɗagata a wajen. Babu shiri tai saurin saƙalo
hanunnta a wuyansa jin kamar zata faɗi tana waro manyan idanunta. Fahimtar magana
zatai ya kauda idanunsa, a can ƙasan maƙoshi kamar an masa dole ya furta,
“Ban son surutu..”
Takaici kamar zai shaƙe Iffah ta cuna bakin nan gaba ta kauda kanta gefe itama
lips dinta na motsawa da alama magana take wadda ba'aji. Ganin inda ya nufa da ita
ta ɗan sauke ajiyar zuciya a ɓoye, yana sauketa a gadon ta yunƙura zata tashi,
maidata yay ya kwantar yana watsa mata shegen kallon nan nasa na ƙasan ido da Iffah
ta kasa gano fassararsa har yanzu, ba zato taji ya ture hanunta da ke dafe da
ƙugunta dan anan tamafi jin zafin faɗuwar ya maye gurbinsa da nashi........✍️

_🥱To kuma dai, Ni na gaji da wagga lalata ta Iffah. Anya bazan koma team
Shanshani ba😒😬🚴._

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (37)

.........Da sauri ta sake maida natan kan nasa ta danne ta hanashi motsawa. Fuskar
data kumbura yabi da kallo yana sake tsuke tashi, babu alamar wasa tattare da shi
ya ce “Miye kuma?”.
“Ni wlhy ba sai ka taɓa ba zan yi da kaina, kuma ai yama daina”.
(Yarinyar nan zata kasheni wlhy) ya faɗa acan ƙasan ransa yana mai ture
hannun nata ya matsa wajen. Zabura ɗaya tai ta kanannaɗe jikinsa tana fasa ƙara dan
taji zafi na gaske. Yanda ta faɗo jikin nasa a bazata, ga hannunsa da yake ƙoƙarin
toshe kunne saboda ƙarar da tai har cikin kansa. Baya sukai su duka, shi ya faɗa
kan bayansa ita kuma tana a kansa. Bashi da zaɓin da ya wuce riƙota kawai. Wani
irin dab-dab da juna fuskokinsu suka kasance, har hancinansu na gogar juna. Hakama
idanunsu sun sarƙe cikin juna. Wani irin al'amari da ya sake rikita mata lissafin
data manta da zafin ciwon da take ji ta gano cikin tsakkiyar ƙwayar idanunsa, da
sauri ta kauda ƙwayoyin idanun nata a cikin nashi da son zame jikinta gaba ɗaya
tsigar jikin nata na wani irin tashi, numfashinta kam fita yake da sassarfa.
Hannunsa dake saman ƙugunta yasa ya sake maidota jikin nasa. Zafin da taji wajen
bigewar ya sata matse fuska, sai kuma ta tura baki tana buɗe idanun nata kan
ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da gaba ɗaya kwarjininsa ya sa takeji ta kamar a wani kogon
dutse suke a matse.
Yanda taki yarda ta sake kallonsa ya sa yaji murmushi na zuwa masa. Amma
tsabar iya miskilanci da jin kai sai ya haɗiye kayansa yana ɗan lumshe idanun da
sake buɗewa kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da tai wani takwaf-takwaf kamar zata saki
kuka. Cike da son ta magantu ya ɗaura hannunsa kan inda ta bugun da ƙyau, murya a
shaƙe kamar mai raɗa ya ce, “A kira Doctor?”.
Yanda yay maganar yana busa mata numfashinsa kan fuskarta ba ƙaramin
yamutsawa tsigar jikinta tai ba. Cikin sauri ta jujjuya masa kanta tana ƙara ƙwaɓe
fuska. Ita kanta bata sanin sanda take masa shagwaɓar nan, kawai samun kanta take a
hakan. “Ni dai ya daina, ka barni na tashi ba ƙyau”.
Kafeta yay da kaifafan idanun nasa da suka sake shanyewa can ƙasa, cikin
wani irin salon ɗagesu ya furta, “Mike nan?”.
A hakali saman lips. Idanunta a rufe ta nuna yanda suke tana kauda kai.
Wani makirin murmushi ya suɓuce masa a karo na farko, a hankali ya juyata suka koma
kwance a gadon su duka kan hannayensu suna fuskantar juna. Baya tai yunƙurin ja ya
tareta da hannunsa ya sake maida fuskarsu daf da juna.
“Nace na gama da ke ne?”.
Iffah fa gaba ɗaya ji take ma bada Shahan-shan take tare ba wani aljanin ne
yazo mata a siffarsa. To inba haka ba taya za'ace ma Shahan-shan ne wannan. Mutum
data sani ko kallo mutane basu ishesa ba, gaskiya wannan aljani ne, aljanin da ta
jima tana gani kafin shigowarta masarautar nan....
Iskar da ya busa mata kan fuska ya sata jan numfashi mai nauyi alamar
dawowa hayyacinta. Ya ɗan yamutse fuskan ta sa dake tsuketa, sake maida idanunta
tai ta rissinar. Shima sai ya lumshe nasan ya ɗan sake buɗewa kanta yana motsa lips
ɗinsa a hankali kamar wanda akaima dole. “Shi kuma wanda ya biya sadakinsa fa?”.
Idonta a rufen kanta tsaye, duk da muryarta a kasalance alamar ta fara
laushi ta ce, “Kai dai ai baka biya ba, dan ta ƙarfi aka kawoni masarautar nan dan
a lasheni kamar yanda aka lashemun yayu na”.
Da ƙyar ya iya gimtse murmushin da ke son kufce masa ya sake tsuke fuska a
zahiri duk da ita bama kallonsa take ba. Daɗin biye mata yake ji, dan haka cikin
ƙara ƙasa da murya ya ce, “In ma ban biya ba ai lokaci ne zai nuna. Mun taɓa lasar
wani ne a gabanki zaki mana sharri?”.
“Babu wani sharri. So babu adadi ma”.
“Sai ki faɗa dawa-dawa muka lasa a gaban naki?”.
“Matarka da ta mutu mana. Kuma nima dan namana da ɗaci ne yasa kuka kasa, dan
nifa nafi ƙarfin mayu, kaima nasan tsorona kakeji yanzu haka”. Ta faɗa da ƙarfin
ikon son tabbatarwa tana wani ƙara tsuke fuska.
(Bazaki kasheni ba yarinyar nan) ya faɗa a zuciyarsa yana danne dariyar
dake taso masa. A zahiri kam hannunsa ya maida a ƙugunta dai-dai inda ta bugu yana
wani lumshe idanu da buɗewa, a hankali yake murza mata wajen batare data farga ba
duk da tana ɗan jin zafi kaɗan-kaɗan. “Yaushe kika fara gano inajin tsoron naki?
Dan nima dai naga kamar tsoron naki nakeji da gaske. Da alama baki barni haka ba
kema mayyar ce ko?”.
Lips ɗinta tai wani irin turawa tana ƙwaɓe fuska, ita ala dole taji haushi
yace mata mayya, “Ni ALLAH ya kiyaye na zama mayya. Tsorona kuwa tun randa ka fara
ganina mana, kuma inba tsoro ba miya maidaka Ajmaal ka dinga naɗar min sirri...”
Yanda ta ƙare maganar da yin takwaf-takwaf da fuska kamar zatai kuka ya sashi
jan wata irin wawuyar ajiyar zuciya jin numfashisa na fisga, kansa har ya fara masa
ciwo saboda ya gaji da surutun, itako oganniyar ya fahimci ko'a jikinta ma. Cikin
nuna alamar gajiyawar har cikin harshensa ya ce, “Ashe dai ni kike jin tsoron,
saboda na kasance Ajmaal duk wani sirrinki na sani?”.
Idanunta da ke rufe ta buɗe fes a kansa, cikin son dakewa ta ce, “Hu'im
lallai ma tsoro fa? To kaima ai naka sirrin na a tafin hannuna basai na faɗa ba”.
“Ni ɗin?”.
Ya faɗa a fisge yana waro duk girman idanunsa kanta. Jikinta tai ƙoƙarin
janyewa da ga nasa dariya na taho mata ganin yanda ya waro idanun, a nata ganin ai
ya tsorata ne. Sake riƙota yay suka koma daf-daf fiye ma da ɗazun, cikin wani salon
da ke neman girmar kanta ya kai hancinsa kan wuyanta yana busa mata numfashinsa. Da
wani irin karyayyar murya data sata zabura can ƙasan maƙoshi ya ce, “Faɗamin wane
sirrina kika sani? Na yi alkawarin zan ƙara miki da wani ma yanzu duk ki haɗa”.
Yanda yay maganar numfashinsa ma sauka saman wuyanta tare da murza hannunsa wajen
ciwonta batare daya fargaba babu shiri ta zabura zatai magana, rufff ya rufe bakin
da tausasan pink lips ɗinsa. Ɗifff komai na jikinta mai aiki da motsin ruhinta ya
tsaya cak da aikin na wucin gadi kamar yanda nashi ya kasance. Idanunsa ya lumshe a
hankali da sake buɗesu kan fuskarta, kafin ya kai hannunsa baya ta ƙeyarta ya tura
yatsun kan tattausan gashinta, a hankali ya fara warwaro ribbon ɗin data ɗaure
gashin a tsakkiya da juya lips ɗin nasa kan nata ya mirginata suka sake komawa kan
hannayensu ta ɗaya ɓarin yanzu ma suna fuskantar juna. Wannan ne karo na farko da
hakan ta faru a tsakaninsu, abune kuma da bai taɓa faruwar ba, hakan ya sata shiga
cikin ɗimuwa da gigita, dan da wani irin salon dake neman ɗage numfashin nata da ga
gangar jikinta yake juya lips ɗin nata cikin nashi tamkar ba Shahan-shan ɗin nan ba
mai tsananin miskilanci da izza da ƙasaitar mulki, wanda hatta magana wahala take
masa. Murmushinsa kam abune mafi tsada ga duk wanda ya sanshi. Gaba ɗaya duk sai ta
daburce jikinta ya shiga rawa, ciwon ma da ƙafar ke mata da ƙugun ta nemesu ta
rasa... (🤭Bily ki kiyayi kanki🏃)

Da alama Shahan-shan Eshaan ya tafi, tafiya irin mai toshe kunne daga jin
ko wane irin motsin sauti da ke a doron duniya, dan dukkanin takaicinsa akan waɗan
nan lips ɗin masu masa tsiwa yau da alama sai ya hucesu. Ita kanta ɗalibar tasa tun
zaburar farko da tai na dawowa hayyaci bata sake motsin kirki ba. Sai da taji
hannunsa na ƙoƙarin shiga cikin ƙaramar rigarta ta sake zabura da ƙoƙarin dafe
hannun nasa da nata tana son janye lips dinta da ya riƙe da nashi cikin kar-kar-war
jiki. Babu alamar zai bata damar da take buƙatar, dan da gani dai yayi zurfi shi
kam. Da sauri tasa dukan ɗan sauran ƙarfinta wajen jan jikinta baya, kamar zai
riƙota sai kuma ya barta yana mai rumtse idanunsa da sukai wani irin mahaukacin
kaɗawa jazur da ɗan ƙarfi. Baya ta juya masa tana mai dunƙule jikinta dake tsuma
har yanzu waje ɗaya. Tunda Ummu ta haifeta tai hankali tai wayo babu wani da ya
taɓa kai hannunsa inda Tajwar Eshaan ɗin ya kai yau a jikinta, kai itafa ko riga
bata yarda ta saka gaban su Arfa ma dake yayunta tsabar yanda take jin kunya. Amma
yau sai ga abinda batai zato ba, da ga mutumin da batai tsammani ba, wayyo ita
Fhareedah ta ga takanta. Wani irin yarrrr yarrrrr take ji kamar har yanzu hannun
nasa na'a jikin nata ne tsabar yanda ta firgita. Ɗaya da ga cikin filos ɗin da aka
ƙawata gadon ta fisgo ta ƙanƙamesa a ƙirjinta dan ta kasa nutsarwa waje guda, da
gaske ta tsorata tsoro irin wanda batajin ta taɓa shigarsa a rayuwarta, sai kawai
wasu hawaye masu ɗumi da bata san na minene ba suka shiga rige-rigen sakko mata a
kan fuskarta.
Ajiyar zuciyar da take ja mai tafiya da kamar shashshekar kuka-kuka ta
sakashi buɗe lumsassun idanunsa da sukai wani irin shanyewa sosai, akan bayanta
data juya rigar ta ɗage sosai saboda tattareta da yayi ya sauke su. Ya ɗan rufe ya
ƙara buɗewa yana mai ƙarema bayan nata fari sol kallo. Wani irin harbawa zuciyarsa
ta sakeyi da ɗan ƙarfi lokacin da idanunsa ke sake sauka kan wannan dai tawadar
ALLAHr babba da ke a ɗan sama-saman bayan nata ta gefen kafaɗar dama. Da sauri yake
ɗan girgiza kansa alamar hakan bazai yuwuba kama ce kawai da ga ALLAH. Ta inama
hakan zata faru? (Kai noo.. noo.. ba haka bane) ya faɗa a cikin ransa da kaushi
sosai yana ɗauke idanun nasa da ga wajen. Sai ma ya miƙe a matuƙar kasalance, zama
yay ya ɗan bata baya, cikin muryarsa dake a matuƙar sarƙe ya furta, “Ga wani sirrin
nan nawa na baki ki haɗa ki adana min”.
Batare da ya sake yarda ya kalleta ba ya nufi bathroom kawai yana mai sake
ƙaryata zuciyarsa da taƙi amsar dagiyar tasa kan abinda idanunsa suka sake gani yau
ma a jikintan........✍️

_Oh ohh girma ya daɗi🥱🚴🚴🚴🚴_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171
SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (38)

........Da wani irin zazzaɓi mai masifar zafi da ƙullewar ciki ya fito da ga bayin,
amma kasancewar sa jarumin jarumai ya shanye komai yana cigaba da ƙoƙarin shanye
wanda ma ke taso masa sabo. Babu kowa a ɗakin da alama Iffah ta gudu, dan rigarta
da ya cire ce kawai yashe a ƙasa, sai dai babu after dress ɗin da alama ita ta saka
ta fice. Samun kansa yay da ɗan sakin wani miskilin murmushi yana cije lips ɗinsa
da azabar ƙarfi. Duk yanda yake son dannewa hakan ya gagara, dan wannan shine karo
na farko da ya iya nisan kiwo da mace kamar haka. Hakan na nufin ya tsokaloma kansa
abinda ya fi ƙarfin jarumtarsa, dan yanda cikinsa ke cigaba da ƙullewa har
numfashinsa ya ɗan fara fisga lokaci zuwa lokaci. Duk da sanyin da ya fara ji na
ratsa shi bai iya ya canja bathrobe ɗin jikinsa ba ga sumarsa ma jiƙe take da ruwa
ya kai kan gado da ƙyar ya zauna, zufa yake ga jikinsa na tsuma abun kamar wani
tsafi. Addu'ar da duk tazo bakinsa ya fara ambato da damƙo fillon data runguma
ɗazun ya matse cikin hannunsa da azabar ƙarfin da ke bayyana asalin gwarzantakarsa.
Wannan ranar yake gudu, wannan ranar ya ɗauka tsahon shekaru yana kaucemawa. Amma
duk da haka sai da ta zo masa a gaɓar da bai shirya amsarta ba. Gaɓar da bai shirya
fuskantarta ba. Gaɓar da bai shirya komai na yanda zai fara gudanar da ita ba. “Ya
arrahaman”. Ya furta a hankali komai na masa kaikawo cikin gizo. Ya tabbatar idan
har aka cigaba a haka to tabbas yau aiki zai buɗe, dan babu shakka kwaɓarsace zatai
ruwa. Da ƙyar ya iya miƙewa, maganin da ya jima da daina sha ya shiga nema a inda
ya tabbatar ya killacesa, da ƙyar ya samosa dan yayi nisa kasancewar ya daɗe da
kauda idanunsa a shansa saboda abinda ka iya zuwa ya dawo kamar yanda doctor ya
sanar masa har yay sanadin ajiyewar. Kwalin ya buɗe ya ciro, sai dai a mamakinsa
babu komai a ciki sai kwafsan ashe ya shanyesa ma a wancan lokacin, bashi da zaɓin
daya wuce sakin kwalin a wajen ya kai kwance yana jan bargo jikinsa dan rawar
sanyinsa ƙaruwa yake yi, ga wani irin sarawa da kansa kemasa. Da gaske abubuwa sun
masa matuƙar yawa, har ma yakan rasa wane irin tunani zaiyi. Ammien sa da
sharaɗinta? Ko Iffah da abubuwan ban tsoronta? Ko Uncle's na sa da son zuciyarsu?
Ko matsalolin talakawarsa da dogaransu kan jiran adalcinsa a koda yaushe? Ko....
Ko.... Ko.... Ɗin sun masa yawa, yawan da matsalar dake tattare da shi a yanzu
kamar tana son nuna fin ƙarfinsu. Dan ya jima da fahimtar kansa, amma ya zama
mayaƙi na gaske akan kansa da kare mutuncinsa da ga taɓa ƴar kowa. Babban fatansa a
koda yaushe ALLAH ya bashi ikon riƙe kansa har zuwa ga halalinsa da zai iya bama
sirrinsa, sirrin da yake fata bayan matar aurensa kar wani mahaluki ya taɓa koda
kwatanta sani insha ALLAH. yana ganin ko yaƙi ko yaso lokacin yayi, sai dai lokacin
yazo da wasu abubuwa masu nauyin gaske. nauyin da ya rasa ma ina ya kamata ya fara
kamawa......

★A ɓangaren Iffah data sulale ta gudu tun bayan shigarsa bayi duk yanda tayi
domin ganin ƙamshinsa ya bar jikinta hakan ya gagara. Tayi wanka, ta shafa nau'in
turarruka daban-daban sai dai ƙamshin jikinsan na nan daram a cikin hancinta da
yaƙi bata damar jin kowane ƙamshi bayan shi. Kamar wadda aka zarema lakar jiki tai
sakwat a jikin bango tana lumshe idanu. Ita kanta bata san ainahin mima take ji a
kansa ba, abinda kawai ta sani komai kawai ya ƙwace mata, bata da wani ƙarfi a
zuciya da jikinta a halin yanzun, abinda ya farun kuma yay mata tsaiwar sojan
badakare a ƙahon zuciya babu alamar zai motsa. Hanunnta ta kai ta shafi lips ɗinta,
sai kuma tai saurin janye yatsun biyu tana mai girgiza kanta kamar wadda akema
magana a kunne. Buɗe idanun nata tai cikin sauri ta sake nufar inda turarrukan
suke, ɗaya bayan ɗaya ta dinga binsu tana shafama jikinta, ita dai a dole sai ta
daina jin wancan ƙamshi. Abin dariya abin tausai harta gama ƙamshin na nan dai bata
daina jinsa a cikin hancin nata ba duk da yanda ɗakin yay wani masifar haukacewa da
ƙamshin data baza har ana jinsa waje. Miya rage kawai ta saki kuka ta huta, sai ko
tai takwaf-takwaf da fuska kamar zata fashe...
Haka taita kai kawonta a ɗakin har mai gyarawa yazo gyara da sanar mata an
gama shirya break fast. Da gaske yunwar take ji, amma bazata fita su haɗu da shi
ba, dan haka ta bada umarnin kawo mata nan tana mazurai a karo na farko. Cikin
ƙanƙanin lokaci aka cika umarnin nata kuwa....

★★.... ★....

A can fada tun kusan awa ɗaya baya ake tsammanin fitowarsa, amma shiru
kakeji. Hakan abune da ba faruwa yake ba. Tajwar Eshaan mutum ne da baya saɓa
alƙawari. In har yace zaiyi abu to zai yisan komai girman ƙalubale da zai iya
fuskanta a yayin yinsa kuwa. Hakama in har yace bazai yiba tofa ko kai waye bazaiyi
ɗin ba. Kaifi ɗaya ne shi, mai faɗa da cikawa. Mai gaskiya da son tabbatar da ita a
mulkinsa, waɗan nan halayensa ne dake matuƙar sake ƙawatashi da kwarzantashi ga
al'ummar sa a bayyane.
“Anya kuwa lafiya yau?”.
Miran Arshaan daya matsu da ganin fitowar Tajwar Eshaan ɗin ya taso zuwa inda
Sayeed Fayzul-haq ke tsaye ya faɗa cike da nuna damuwa. Kai Sayeed Fayzul-haq ɗin
ya jinjina masa shima da ƴar damuwar a fuskarsa. “Banajin matsala ce insha ALLAH.
Dan ban daɗe da ganawa da shi ba, sai dai kasan mutum mai iyali...” ya ƙare maganar
da wani ɗan murmushin su na manya. Kamar Miran Arshaan ya sokama Sayeed Fayzul-haq
wuƙa a ƙirji yaji, dan haka kawai maganar iyalin na Tajwar Eshaan ta soki ransa,
murmushi Sayeed Fayzul-haq ya ɗanyi yana kauda kai kamar bashi ya takalosa ba, dama
kuma ya fadane da biyu....

★★..... ★....

Shikam mai gayya da aikin har akai sallar azhar bai gama samun kansa yanda ya
kamata ba, dan haka yay sallarsa a ɗaki cikin ƙarfin hali. Rashin fitowarsa salla
ya sa su Sayeed Fayzul-haq suka tabbatar da akwai dalili mai ƙarfi daya hana shi
fitowar kam tabbas. Ya cigaba da son ganin ya dawo normal, hakan bata samu ba sai
kusan gab da la'asar da ya sake komawa Gym ya maida kansa busy, dan wani irin
mahaukacin work out yayi, kafin ya fito sharɓan da zufa idanun nan babu alamar
rahama yau kam an tsokalo maza. Tsaf yay shiri cikin ɗan sauran ƙarfin da ke
jikinsa, dan gaba ɗaya jinsa yake sai a hankali. Haka dai ya daure ya fito domin
zuwa massalaci.
Iffah dake sharce ruwan alwala da tayo a fuskarta da wani irin sauri ta
buɗe idanunta jin an buɗe ƙofar. Ido huɗu sukai da shi, da wani shegen sauri ta
maida nata idanun ta rumtse da juyama ƙofar baya, cikin salon nasa na basarwa da
shegen miskilanci da ƙasaitar nan tasa shima sai ya ɗauke kai tamkar bai ganta ba.
Ta bayanta ya raɓa ya wuce, wasu takardu da ya ajiye ya ɗauka a kan study table ɗin
ɗakin ya sake zuwa zai gittata. Tsaye take har yanzu idanunta a rufen ita a dole
bata son su haɗa ido. Ƙirjin Iffah bugawa ya dingayi da sauri-sauri jinsa a kusa da
ita, idanun ta buɗe kaɗan dan son tabbatarwa. Shi ɗinne dai a gabanta ya zuba mata
idanunsa da ke cikin eyeglasses masu ɗan duhu. (Wayyo ni ALLAH) ta ambata a
zuciyarta tana maida idanun ta rumtse a daburce ta ce “Barka da rana”.
Idanunsa dake a wani irin yanayin da ya tilasta mishi saka gilashin ya ɗan
lumshe yana sake buɗewa a kanta. Cikin dakewar muryarsa dake ɗan shaƙe fiye da koda
yaushe data sani kamar wanda akaima tilas acan ƙasan maƙoshi ya furta, “After Isha
ki sameni”. Idanunta ta buɗe a firgice, sai dai shi tuni ma har yayi gaba abinsa.
Dai-dai yana ƙoƙarin ficewa taji kamar ta fasa kuka, amma sai ta haɗiyesa tana
ƙoƙarin aro jarumta. A hankali ta furta, “Zanje na ga Ammie to kafin sannan
Please”.
Cak ya dakata sai dai bai juyo ba har na wasu sakkani. Kin san dai kina a
ƙarƙashin umarnin shari'a ne ko?”.
Kanta ta jinjina kamar yana kallonta, kafin ta ce, “Eh na sani, alfarma
kawai nake nema. Jiya ranta ya ɓaci, matsayinta na mahaifiyata bai kamata na kwanta
cikin nutsuwa ba tana fushi da ni. Ina son naje gareta domin neman afuwa”.
Gaba ɗaya jijiyoyin jikinsa ne suka ƙarasa saki, wani sanyi na ratsa masa tun
daga kan yatsun ƙafa har tsakkiyar kansa. A sannu ya waiwayo ya zuba mata idanunsa.
Kallo yake mata irin na kin mamaye komai da komai ɗin nan, a zahiri kam baka isa
tantance komai bai tattare da shi, dan fuskar na'a yanda taken nan tsuke tamau. “Ki
jira ni”.
Ya faɗa kai tsaye dai-dai yana ficewa. Numfashi ta sauke a hankali da yin ɗan
baya kamar maijin jiri ta manne da bango, mamaki takeyi, mamakin kanta da komai ma,
ta wani gefen kuma ta fara tsoron abubuwan da ke neman cigaba da wajabta kansu a
ƙarƙashin mafarkinta, toso ture wannan amma zuciyarta nata ingizata akai, abu mafi
ɗaure kai kamar yanda tai mafarkin ta tambayesa zuwan a mafarkin a zahirin amsar da
ya bata acan ne anan ma, mi hakan ke nufi? Tayaya ma kanta zai cigaba da ɗauka,
gaba ɗaya sai kewar iyayenta ta sake dawo mata sabuwa a zuciya, ta shiga jan ajiyar
zuciya hawaye na ciko mata idanu. Iska ta ƙara fesarwa ta buɗe idanunta tana sakin
murmushi, murmushi mai ciwo da ita kaɗai ta barma kanta sani sai ALLAH. Sai kuma ta
taɓe baki kaɗan da tuno furucinsa. _Wai ta sameshi, to ta sameshi kamar ya? Itakam
wace ƙaddara ce ma ta sata amincewa auren mutumin nan? Jibafa yanda yake wani ɗacin
rai da ɗa duniya bashi ya gama murje mata lips da jikinta ɗazun ba, halan ma wai ya
manta tsiyar da ya aikata ne. (Ko zaki tambayosa) zuciyarta ta ayyana mata. Zabura

✍️
tai cikin masifa da tsiwa kamar zuciyar tata mutum ce, sai dai kuma batace komai ba
aka dai cuna bakin gaba. (Gwara dai kiyi shirun ta gidana)........

______________
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku
anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama
Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya
zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da
matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani
prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa
jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using
mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki
kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi
gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai
na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin
keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏

____________________

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_


_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (39)

.........Zuwa yanzu labarin abinda ke faruwa da iyalan Miran Jasim ya gama kewaye
cikin masarautar. Hasalima babu wani ka-ce-na-ce dake kai kawo sama da zancen.
Musamman da ya kasance Umm Husam na ƙarƙashin kulawar likitoci har yanzu, duk da
dai Alhamdullah sun sami nasarar mata ɗorin karayar data samu a cinyarta. Amma taji
mummunan ciwo a ƙashin bayanta da bama a saka ran zata iya ƙara cigaba da takawa da
ƙafafunta. Malikat Haseenat ta fita dubasu a asibitin har shi Miran Jasim ɗin dan
shima dai ya jigatu a hannun Husam ƙwarai da gaske. Lokacin da take fitowa bisa
rakkiyar Daneen Ammarah da hadimanta amintattu irin su Banou tawagar Tajwar Eshaan
ke gabato Clinic ɗin shima. Malikat Haseenat ta kafeshi da idanu na tsahon lokaci,
yanda yake tafiya ɗaɗɗaya cike da ƙasaita da izza, ga wani mayataccen ƙamshinsa da
tun kafin ya iso shi ya iso hancinansu. Sai dai fuskar ciɗin-ciɗin fiye da kullum
alamar akwai ɓoyayyar damuwa tattare da shi. Idanu ta ɗan lumshe tana ɗan murmushi
da jin tarin ƙaunarsa na sake mamaye zuciyarta. Tana ma jikan nan nata so mai
ƙarfin gaske da itama bata san adadinsa ba. Zubewar Hadimanta bisa gwiwunsu ya
fargar da ita isowarsa gab da su. Itama ƙasa tai da kanta alamar girmamawa garesa.
Tun kusantowarsu wajen idanunsa shima na'a kanta, sai dai bashi da damar tsayawa
gareta kasancewar a Shahan-shan ɗin sa ya fito ba jikanta ba. Har cikin ransa yana
ƙaunar wannan baiwar, ƙauna irin wadda shi kaɗai ya barma zuciyarsa sani.
Sai da suka shige sannan ta dubi Daneen Ammarah tana murmushi. Itama murmushin
tai mata sai dai batace komai ba suka nufi motar da suka zo Clinic ɗin a ciki.

Fuskar nan a matuƙar tsuke cike da barazanar da ke sake fidda ainahin


kwarjininsa yake duban Miran Jasim da gaba ɗaya yake jin ya ruɗe bazai iya ma haɗa
ko ido da shi ba. Gaba ɗaya yaron ya sake masa wani kwarjini mai ban mamaki fiye da
da. Duk da ya tako zuwa Clinic ɗin ko uffan bai furta ba sai kaifafan idanunsa da
ke sakaye a gilashin nan dan ɓoye yanayinsa da ya zuba masa. Sai su Sayeed Fayzul-
haq ne ke tambayar lafiyar tasa da yawun Tajwar Eshaan ɗin. Shiko ko sau ɗaya ma
bai motsa lips ɗinsa ba a wajen, hasalima shi hankalinsa kamar rabi da rabi ne a
tare da su nan kawai. Basu wuce tsaiwar mintuna biyar ba suka nufi ɗakin da Umm
Husam take itama. Itako ganin Tajwar Eshaan da kansa yazo dubata sai ta fashe da
kuka. Idanunsa ya ɗan lumshe kawai, sai Sayeed Fayzul-haq ne ke bata haƙuri. Nan
ɗin ma dai basu wuce mintuna biyar ɗin ba suka fice.
Da ga shi sai Miran Arshaan da Sayeed Fayzul-haq suka koma sashensa, sai
amintaccen hadiminsa da baya rabo da shi a koda yaushe, jami'an da ke bashi tsaro
biye da su kowanne hannu ɗauke da mahaukaciyar bindiga. Tako ina hadimai zubewa
suke, sai dai ransu fari tas da ganin sarkinsu duk da ba suna ganin fuskarsa bane.
Amma suna jin alfaharin sun taɓa ganinsa, koba komai suna jin shauƙi da sanin
fuskarsa sau ɗaya koda bazai sake buɗeta a gare su ba har abada.

Shigarsu da ƴan mintuna shugaban jami'an tsaron ya nema iso. Kasancewar


Sayeed Fayzul-haq ya san da zuwansa cike da girmamawa yake sanar da Shahan-shan
tare da neman afuwar sanar masa a ƙurarran lokaci. Alama yayi ta abashi izinin
shigowar kawai. Takaici ya sake kume Miran Arshaan da ke zaune shima. Ya ballama
Sayeed Fayzul-haq hararar gefen ido yana ƙwafa a zuciyarsa.
Cikin girmamawa shugaban jami'an tsaron ya miƙa gaisuwa, amintaccensa ya amsa
a madadinsa. Zaune ya kai a inda Sayeed yay masa nuni, cikin sake risinar da kai na
girmamawa ya miƙa files na hannunsa guda uku. “ALLAH ya ƙarama adalin shugabanmu
lafiya da nisan kwana masu albarka. Alhamdullah mun kammala binciken da mukai
alƙawarin yi yanda ya kamata, sai dai muna mai neman afuwar jinkirin da aka samu
bisa wasu dalilai. Wannan files ɗin na cases ɗin ne duka uku. Alhamdullah mun sami
nasarar gano hadimin da ya ɗakko Zawjata-almilk daga kurku ya jefata cikin swimming
pool, a yanzu haka kuma yana hanunmu dan a daren ranar litinin muka cafkesa yana
shirin guduwa da ga cikin masarautar nan. Mun gano shine ta hanyar zanen yatsun
hanunsa da muka samu a jikin ƙofar kurkukun daya kasance ɗaya da ga cikin shaidun
mu. Ya tabbatar mana da cewar sakashi akayi sai dai shima bai san wacece ba, amma
ta jima tana sakashi ayyuka masu kamanceceniya da wannan tun ba yau ba. File na
biyu akan kisan Sayeed Khairul-Bashar ne....”
Wani irin bugawa mai azabar ƙarfi ƙirjin Miran Arshaan yayi kamar zuciyarsa
zata faso ta faɗo. Shugaban jami'ai da bai san yanayi ba ya cigaba da faɗin,
“......shima mun gano an kashesane ta hanyar kaisa ɗakin baya da ke a can wajen
tsohon kurkukun can akai masa kisan gilla. A binciken da mukai cikin ɗakin ne muka
gano zobensa da ɓalin gilashin jikin eyeglasses ɗin idonsa daya fita, tare da
suffar hadimin da ya dinga azabartar da shi har ya mutu a gwajin ƙwayoyin idonsa da
muka bibiya. Jinkirinmu ya samo asaline ma a dalilin binciko hadimin kasancewar
yana rufe fuskarsa ne a lokacin aikata laifin. Shima dai kamar wancan ya tabbatar
mana sakashi akayi, sai dai shi yanada matuƙar taurin kai dan yaƙi faɗar waɗan da
suka sashi, da alama kuma shi ya sansu sani na zahiri saɓanin wancan.”
Fitsari kawai ya ragema Miran Arshaan ya saki, amma illahirin jikinsa tsuma
yake yana ƙoƙarin dannewa. Shugaban jami'ai ya cigaba da faɗin, “File na uku tushen
samuwar madarar da aka kai sashen Zawjata-almilk ne.....”
(Kun mutu Arshaan) zuciyar Miran Arshaan ta faɗa cikin matsanancin tashin
hankali. Da ƙyar ya iya haɗiyar busashen yawu da fisgo numfashisa da ke neman
suɓucewa da ga gangar jikinsa. Shugaban jami'ai ya cigaba da faɗin, “...madarar ta
fito ne da ga sashen gidajen kuduncin wannan daula, dan an ɗauke ta daga can ne
zuwa sashen uwar masu gida saboda yin ɓadda kama. Dan haka suspect ɗin mu dole zai
kasance a ɗaya da ga waɗan can gidajen guda shida dake a cikin file ɗin. Domin a
daren ranar ɗaya daga cikin jami'an mu ya ga wani a suffar ɓadda kama ya fito ta
wata ɓarauniyar hanya da muma bamu san da ita ba a gidan nan. Munbi diddigin masu
bin hanyar a tsahon kwanakin nan daya tilasta jinkirinmu, mun samu mutane huɗu sai
dai har yanzu bamu tabbatar da fuskokinsu ba kasancewar a shirin ɓadda kama suke
fitar. Amma hakan ba matsala bane saboda hanyar tabbatar da su ɗin su waye tana a
hanunmu muna kan sake tabbatarwane gudun samun kuskure. Albishir dai da zamu bayar
akan shi wannan case ɗin a yanzu haka wanda ya samar da dafin macizan yana hanunmu.
An kamosa ne kuma a safiyar yau”.
A karan farko Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ya saki wani malalacin
murmushi da ya nema sumar da Miran Arshaan da ke jin kamar ya rumtse ido ya gansa a
sashen sa ko clinic wajen Miran Jasim ko ma wajen boka Barbushi shi ma bai san ina
yafi so yaga kansa ɗin ba. Sayeed Fayzul-haq kam kansa kawai yake faman jinjinawa
ransa na mamakin waɗan nan abubuwa abin kamar wani shirin film. Amintaccen hadimin
Tajwar Eshaan kam abun ya masa daɗi, musamman ganin murmushi mafi tsadar gani a
fuskar shugabansa adali, sannan koba komai a su kansu ma amintattun hadimansa suna
fatan kowaye ɗin kodan wahalar da suka fuskanta ta kusan wata guda a kurkuku. Shi
dama ya daɗe daji a ransa Zawjata-almilk bazata iya aikata abin nan ba sai da
jagorancin wani sheɗanin da ya fi ƙarfinta. Dan haka kawai yake jin ƙaunarta matuƙa
musamman da ya fahimci wani abu ɓoyayye da ke tare da shugabansa game da ita duk da
yana ƙoƙarin ganin ya danne. Amma kuma shi a yanzu babu wanda ya kaisa sanin wanene
Tajwar Eshaan, koba komai barci ne kawai ke rabasu sai ko idan ya shiga ciki ko ya
yini bai fito a bedroom ba. Kuma ko'a hakan tabbas tabbas sai ya gansa a yinin sama
da sau biyar. Zai iya cewar da ga matarsa a yanzu sai shi ko a mafi ƙololuwar ganin
Tajwar Eshaan ɗin.
Wani irin kirari ya shiga jeroma shugaban jami'ai, tare da jinjinar ban
girma na ƙoƙarin sa da yawun Shahan-shan da bayan murmushi babu alamar zaice wani
abu. Magana da ga bakin amintaccen Tajwar Eshaan tamkar kai tsaye ne da ga bakin
sa, dan yana cewa ne da say ɗin sa bawai raɗin kansa ba. Sannan koba komai shima a
idanunsa Tajwar Eshaan ɗin ya saki murmushin nan da zai iya rantsuwa bai fi a karo
na ƙalilan kenan ya taɓa gani ba. Hakan na nufin da gaske Shahan-shan ɗin ya yaba
da ƙwazon jami'an tsaron gidan koda bai furta ɗin ba.

Jiƙewa iya jiƙewa jikin Miran Arshaan ya gama yi da zufa. Ga wani irin
hajijiya da idanunsa suka fara gani. Kaɗan ya saci duban Tajwar Eshaan da babu
alamar hankalinsa a kansa yake, hakama Sayeed Fayzul-haq. Yawu ya haɗe masu kaurin
da har yanajin suna kamar ɗaɗa masa maƙoshi. Da ƙyar ya iya jarumtar cigaba da zama
har shugaban jami'an tsaro ya gama ya fice. Babu alamar Tajwar Eshaan zai sake cewa
wani abu akan batun, hakan yasa shima Sayeed Fayzul-haq haɗiyewa ya ɗakko zancen
Miran Jasim da iyalansa, sai ɗansa dake a sashen Malikat Haseenat har yanzu. Ba
ƙaramin dauriyar danne tashin hankalinsa yay wajen saka musu baki ba gudun kar
Tajwar Eshaan ya harbo jirginsa. Dan ya mugu-mugun sanin hatsabibancin yaron nan,
babu abinda ya baro a halin ubansa sai ma finsa taurin kai da yayi. Tattaunawar ta
ɗan jasu wani lokaci dan har gab da magrib sannan suka tashi..........✍️
______________

Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku
anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama
Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya
zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da
matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani
prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa
jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using
mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki
kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi
gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai
na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin
keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏

__________________

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (40)

______________
Lifestyle_Nig for everything that makes your lifestyle complete ..👌
Furnitures
Decoration
Kitchen items &
Boutiques
Quality is our watch word at lifestyle shop kano/kaduna
Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and
second gate near kashe magana suya spot
Instagram Lifestyle_Nig
Facebook Lifestyleng
Tik tok Lifestyle_Nig
Delivery nation wide 08036414048
Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah

_______________

..........A bala'i bala'in matsanancin tashin hankali Miran Arshaan ya nufi clinic,
yaji daɗin samun Miran Jasim da ke tambayarsa lafiya ganinsa a firgice shi kaɗai.
Maimakon amsa masa sai ca yay, “Kasa a sallameka da ga clinic ɗin nan a daren nan”.
Cikin kallo mamaki Miran Jasim ya ce, “Kamar ya nasa a sallameni, kai bakaga yanda
shegen yaron nan nawa ya fasan kai ba. Ga wuyana tsabar yanda ya nema karyashi sai
da aka samun wannan abun”. Ya kare maganar da nuni da abin wuyansa. Tsaki Miran
Arshaan yayi yana ji kamar ya sake shaƙesa shima. “Shaƙar da Husam ya maka ba komai
bace akan wacce ke tunkaro rayuwarka”. Ya ɗan ƙara waw-wai-gawa alamar gudun kar
wani ya jisu. Cikin sake ƙasa da murya ya cigaba da faɗin, “Idan ka bari ka sake
awa biyu anan nadamace ta har abada zata zama abokiyar rayuwarka in har ma
matsiyacin yaron nan ya Barka da ran naka kenan”. Yana ƙare faɗa ya ficewarsa da
ƴar sassarfa dan dama yay amfani da lokacin shiga sallar magrib da akayi ne......

★.... ★....

Bayan idar da sallar isha'i koda ya nufi sashensa maimakon ƙarasawa ciki
sashen Malikat Haseenat ya nufa ta ɓoyayyar hanya. Tayi sallamar wutiri kawai sai
ganinsa tayi. Ba yau ya saba mata irin wannan zuwan ba na sirri, sai dai yafi yinsa
a bayan sallar asuba. A nutse take dubansa bayan shafa addu'ar data taƙaita cike da
kulawa. Shima sai ya taso a hankali da ga zaman ƙasaitar da yay a bakin gadonta ya
dawo inda take kan lallausan carpet ɗin dake fes babu datti sai ma tashin ƙamshi da
yake da ɗaukar ido na sabunta. Ga taushi matuƙa da ko'a ido zaka iya fahimtar
hakan. “Barka da dare Jadda-ti”. Ya faɗa a can ƙasan maƙoshi ya na kaiwa kwance
bisa carpet ɗin ya ɗaura kansa kan cinyarta ya wani lumshe idanunsa da a kallo ɗaya
ta fahimci damuwar dake tattare da shi a cikinsu tama ƙaru fiye da ɗazun. Murmushi
ta saki mai sanyi a ranta tana faɗin, (Yau kuma ƴan shagwaɓan ne a kusa haka), a
zahiri kam hanunnta kawai ta ɗaura kan ƙyaƙyƙyawar baƙar sumar sa siɗik ta fara ɗan
tausa masa kan kaɗan-kaɗan. Idanun ya sake lumshewa da ƙyau har yanajin barci-barci
na ɗibarsa. Tsahon mintuna kusan uku sannan ta magantu cike da kulawa.
“Waya taɓamin kai Niger?”.
Shiru bai motsa ba har wasu sakanni. Kafin ya buɗe idanunsa da suka ɗan fara
shanyewar barci a hankali. Sai kuma ya ɗan ɓata fuska yana ƙoƙarin kaudawa gefe.
Riƙo fuskar tai cikin tafukan hanunnta tana murmushi da faɗin, “Oh oh beautiful
Hafidi na faɗamin kaji”.
Idanunsa ya ɗan lumshe da jujjuya mata kansa kaɗan ya motsa lips ɗin da
ƙyar da maganar nan nasa kamar ta dole, “Kawai ina son jin ɗuminki ne”.
“Uhyim, ita kuma Hafida-ti na aka barta ita kaɗai”.
Shiru yay kamar bazai tanka ba. Sai kuma ya yamutse fuskar daɗa duniya har cikin
zuciyarsa ne ya wani kauda kai gefe, “Tanada hayaniya, gata da surutu”.
Mi Malikat Haseenat zatai banda dariya. Cike da nutsuwarta da ƙasaita ta
shiga yin abinta. Ta ce, “Wayyo ni kai kuma gashi baka son hayaniya da surutu.
Nikam ai ta burgeni, gara ta koya maka hayaniyar tata da surutun ko zamu samu ka
dinga amsa mana magana biyar cikin goma. Naji daɗin hakan, dan itace dai-dai da
kai”. A yanda take maganar zaka san lallai tana matuƙar jin daɗin. Shima dai acan
ƙasan ransa murmushi kawai yake, dan ya sake tabbatar da kakar tasa mafi soyuwa a
ransa na matuƙar ƙaunar ƴar hayaniyarsa da gasken gaske. Dama shi baya shakku a
kanta, dan duk abinda Malikat Haseenat ta so to da gaske tana sonshi ne har cikin
rai, idan kuma ta nuna ƙi to da gaske take ƙin nasa. Kamar tasan abinda yake
tattaunawa da zuciyarsa ta cigaba da shafa kansa har yanzu da sauran murmushin
dariyar da tai akan fuskarta. “Eshaan da gaske ina son yarinyar nan har cikin raina
batare dana san dalili ba nima. Halayyarta kuwa na tuna min wasu abubuwa masu yawa.
Yarinyar nada shiga rai, sannan tana da ɓoyayyun abubuwan ban mamaki tattare da
ita. Karo na uku kenan ina aikawa nemomin iyayenta batare da kowa ya sani ba amma
ana tabbatar min wai basa gidansu, a binciken ƙarshe ne na samu cikakken bayanin
dalilin barinsu gidan, nasaka an bibiyar min kakaninta a ƙauyensu da aka tabbatar
min su suna nan amma sai suma aka taki rashin sa'a. Na fara jin tsoron kar wani a
cikin masarautar nan ne ya shirya cutar da su, dan tabbas abinda ya faru tsakaninka
da yarinyar nan aike ne.. Bazaka tabbatar da hakan ba sai ka kusanta kanka da ita,
kusanci mafi girma da a yanzu shine babban mafarki na, ina fata kafin na bar duniya
naga jininka, a koda yaushe kuma na ayyana hakan zuciyata hoton yarinyar nan take
kawo min matsayin uwar ƴaƴanka”
Yanda muryarta ke fita da sautin tabbatar da abinda ke zuciyarta ne ya saka
shi ɗan buɗe idanu kaɗan yana kallonta, sai kuma ya tashi zaune shima a serious ɗin
sa, shiru babu alamar zaice wani abu, ita har ta fidda rai ma da cewar tasa. Sai
kuma a hankali taji sassanyar muryarsa ya ce, “Jaddah”.
“Yes Niger”
Ta amsa masa da kulawa. Kaifafan idanunsa masu nutsuwa da haske mai cika idanu
da a yau launinsu ya ɗan surka ya zuba mata. Murya a can ƙasa maƙoshi da kamar an
masa tilas ya jefa mata tambayar da ba ita tai tsammanin ji da ga garesa ba.
“Tambarin baƙi mai kamar tawadar ALLAH duk wani zuri'ar gidan nan ke da
shi ko wasu ne a ciki?”.
Yanzu kam kallonsa take da mamaki matuƙa da ya gaza ɓoyuwa har a kan fuskarta.
“Ban san miye dalilinka na wannan tambayar ba, ko kake son sani. Faɗamin miya
faru?”.
Kansa ya girgiza mata alamar babu komai, sai kuma a hankali ya ce, “Ina son
sani ne”.
Sam zuciyarta bata aminta da haka kawai bane, sai dai bazata matsa da son ji
ba dan yana da hujjar ƙin faɗar, idan yaso wataran da kansa zai sanar mata. “In dai
daga zuri'ar Aliy Qutb (mahaifin kakanka Abdull-Majeed) ka fito wannan tambarin
shike tabbatar da kai. Sai dai bawai haka kawai ake gane kai ɗan zuri'ar bane da'an
gansa. Akwai ajiyayyun hujjoji da ke tabbatarwar domin ana haihuwar jariri bayan
yanke masa cibiya shine abu na biyu da ake duba masa. Yin wannan tambari a jikin
duk wani jinin ahalinku ya samo asaline a dalilin kakanku na huɗu da yake da shi,
mahaifin Aliy Qutb kenan, shi kuma Aliy sai yazam bashi da shi lokacin da aka
haifesa amma sauran yan uwansa na baya duk sukazo da shi, maƙiya sai suka riƙe
wannan hujjar a lokacin da za'a naɗashi sarki suka shigo da wata magana mai ban
tashin hankali data girgiza masarautar nan baki ɗaya, har sai da ta kai anbi
diddigin jinin Aliy da mahaifinsa. Wannan al'amari shi kuma sai ya riƙesa, bayan
hawansa mulki duk wanda aka bincika bashi da tambarin sai an masa da wata alama da
ke tabbatar da a cikin masarauta aka masa da hujjojin masu ƙarfi a rubuce. Idan aka
haifi jariri kuma bayan yankan cibi shine abu na biyu da ake masa idan har babu
shi...”
Idanunsa da ya zuba mata tun fara maganar ya ɗan motsa kaɗan zuciyarsa na
wani irin bugu da sauri-sauri. Amma a zahiri bazaka taɓa fahimtar a wane yanayi ya
ke ba. Murya acan ƙasan maƙoshi ya sake furta, “An cigaba da samun masu tambarin da
yawa ne? Ko wanda akai mawa ne suka fi rinjaye bayan farawar?”.
Shiru na wasu sakkani Malikat Haseenat batace komai ba, sai kuma taja
ajiyar zuciya. “I to ni dai a yanda na samu labari a ɗan binciken tarihi wani
lokaci akan samu yawaytar masu shi, wani lokacin kuma sai kaga anata haihuwar
marasa shi, al'amarin kamar yana tafiya a ƙarni-ƙarni ne, amma kaga tashi kaga”.
Babu musu ya miƙe kamar yanda ta buƙata, da taimakonsa ta hau wheelchair
ɗinta, kai tsaye inda ƙaton hoton kakansa Tajwar Abdul-majeed ke manne kamar ka
masa magana ya amsa ta nufa. Yatsanta manuniya ta kai a saitin fuskar hoton ta
shafa, zuuu ƙaton frame ɗin hoton ya shiga wani naɗe kansa kamar ana naɗe tabarma
da ga sama yayo ƙasa. Ƙofa ce ta bayyana, bai wani nuna mamaki ba dan ya riga yasan
da kofar nan tun ba yanzu ba, dan shi wannan sashe da Malikat Haseenat ke rayuwa
yanzu a ciki asalinsa sashen kakansa ne Tajwar Abdul-majeed, shiyyasa akwai sorrika
masu yawa a cikinsa da ita kaɗai tasan da su sai wanda kuma taso ya sani. Da
taimakonshi ta shiga yana biye da ita a baya. Ɗakine madaidaici mai ɗauke da tarin
littattafai kala-kala. Gurin yayi ƴar ƙura alamar bawani shigarsa ake akai-akai ba.
Kekenta ta wulwula zuwa bangaren arewa tana bin jerin manya-manyan littattafan
wajen da kallo, shi dai yana tsaye da ga tsakkiyar ɗakin yana binta da kallo a
ƙasaitance. Juyowa tai ta yafitoshi da hannu, cikin takun nan nasa na izza da
ƙasaita ya nufeta. Littatafai biyu masu girma da tudu sosai-sosai ta nuna masa.
“Ciro min su”. Hannu ya kai a hankali yana ɗan yamutse fuska ya cirosu, duk sunyi
ƙura, amsa sai ta shiga karkaɗesu, yanda ƙurar ke tashi sama ya sashi ja da baya
har sai da ta kammala. Ƙara yafitosa tai da hannu ya sake dawowa gabanta, ta kamo
tattausan hanunsa cikin nata ta ɗaura masa littattafan. “Wannan zasu taimaka maka
samun duk amsar da kake nema, duk wanda ke cikin zuri'ar nan da aka haifa da
tambarin ko akai masa akwai bayaninsa anan. Ka kula da ƙyau suna da muhimmancin da
ba kowa yasan inda suke ba a cikin wannan masarautar”.
Kai ya jinjina mata yana lumshe idanunsa da buɗewa a kanta......

★★......

Taso share umarninsa na ta samesa bayan sallar isha'in amma zuciyarta taƙi
bata haɗin kai. Sai ma ta samu kanta da yin sabon wanka da canja kayan jikinta zuwa
wata ƙyaƙyƙyawar abaya mai laushi da santsi kalar fari da akaima adon manyan fulawa
da golden mai ɗaukar idanu, ga stones taji farare da duk inda ta motsa sai sunyi
ƙyalli kamar wani diamond. Samun kanta tai da nutsuwar naɗa veil ɗin ya zauna ɗam a
kanta har wani ɗan gashi siriri data zubo ta gaban goshin na reto a fuskarta. Tayi
ƙyau matuƙa, dan ko maƙiyinta sai yaji ta burgesa kasancewar Iffah yarinya ce mai
shiga rai, ga ta ƙyaƙyƙyawa komai nata dai-dai da ita. Yau dai har an ɗauki
turarurrukansa za'a bulbula sai kuma aka fasa. A cikin wanda tai shopping akai
amfani da su, sai kuma aka koma dai aka saka nasan ƙaɗan. Yanda tayi haɗin sai ya
bada wani irin ƙamshi mai sirrin da ko shi mai gayya mai aikin da wahala ya iya
gane ainahin nasa ƙamshin. Taku take a nutsenta kamar wata ƴar wahainiya. Bedroom
ɗin jiya ta nufa dan tafi tunanin samunsa a can duk da bata da tabbas.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (41)

_______________

Lifestyle_Nig for everything that makes your lifestyle complete ..👌


Furnitures
Decoration
Kitchen items &
Boutiques
Quality is our watch word at lifestyle shop kano/kaduna
Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and
second gate near kashe magana suya spot
Instagram Lifestyle_Nig
Facebook Lifestyleng
Tik tok Lifestyle_Nig
Delivery nation wide 08036414048
Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah

______________

.........Da ƙyar ta iya danne zuciyarta cikin rumtse idanu ta murɗa handle ɗin
ƙofar ta shiga. Kamar jiya ɗakin diff babu yawaitar haske sai wani ni'imtaccen
ƙamshi mai saka zuciya nutsuwa da sanyin ac. A hankali ta saki ajiyar zuciya tana
mai bin ko'ina da kallo. Babu alamar akwai mutum a ciki kam duk da ita dai tana ji
a jikinta yana nan. Tafiya ta cigaba da yi kamar wadda ta shigo sata da sanɗa tana
ɗan lalleƙawa.
“Bani shayi..”
Cak ta tsaya ƙirjinta na wani irin dif-dif, sai kuma ta juyo da sauri domin
tabbatarwa. Shi ɗin ne dai zaune cikin ƙyaƙyƙyawar kujerarsa mai ƙyawun gaske da
laushi, a yanda yay zaman ƙafa harɗe bayansa kwance a kujerar sai ka ɗauka ma
idanunsa a lumshe suke. Sanye yake da ga shi sai bathrobe da tausasan slippers
alama wanka ya fito, cikin sauri ta sake juyawa tana rumtse idanu duk ta daburce.
Sai da ta ɓata minti guda tsayen kafin tayi dauriyar jan ƙafa da ƙyar zuwa centre
table na tsakkiyar kujerun da ke gefe kaɗan inda taga butar shayin. Mita take tayi
a zuciyarta harta kammala zubawa ta zabga zuma a cikin ɗan kawai neman magana.
Murmushi ta saki na mugunta ta ɗauka cup☕ ɗin da shayi keta turiri ta nufesa. Sai
dai idanunta a rissine dan kunyar kallonsa take a haka duk da bawai jikinsa a buɗe
bane. Tana ƙoƙarin ajiyewa a ɗan coffee table ɗin gabansa ya miƙa mata hannu alamar
ta bashi. Miƙa masan tai har yanzu idanunta a ƙasa.
“Thanks”.
Ya faɗa a hankali yana kai kofin kan lips ɗinsa. Da sauri ya janye jin zaƙin
zuman ya wani ratsa masa harshe zau-zau. Dai-dai kuwa da ɗaga ƙafar Iffah zata bar
wajen. A hankali ya riƙo hanunta cikin nashi, ta rumtse ido da ƙarfi batare da ta
juyo ba. Matsota yay jikinsa, a bazata ta jita zaune ɗare-ɗare a cinyarsa. Da sauri
ta zabura zata miƙe ya maidata ya zaunar. (Ya ALLAHU wannan mutumin yana lafiya
kuwa?) ta faɗa a ranta kamar zata saki kuka.
“Haka ake haɗa shayi dama?”.
Wani irin yamutsawa tsigar jikinta tayi saboda yanda yay maganar a saitin
kunnenta da sassanyar muryar nan tasa da a yau gaba ɗaya yinin take jinta a shaƙe.
Kasa cewa komai tayi, sai mutsu-mutsun son tashi shiko yaƙi yarda ya bata damar
hakan. Sai ma hannunsa da ya saƙalo takan cikinta ya ɗaura kan nata da ke wajen
tana ƙanƙame jiki. Tare da sake matsota jikinsa bayanta ya manne da ƙirjinsa. Ɗayan
hannun kuwa shayin ya ɗauka ya kawosa bakinta.
“Hhaah!”.
Ya faɗa babu alamar wasa tattare da shi. A shagwaɓe ta ce, “Ni bance zan sha
shayi ba fa”.
“Ko?”.
Ya faɗa cikin sigar tambaya yana ɗage gira sama. Sai kuma ya shiga yin sama da
hannunsa zuwa saman jikinta, kansa kuwa na'a kan kafaɗarta yana wani irin kalan
shinshinar ƙamshinta. Daburcewa tai duk da sautin fitar numfashinsa kawai take iya
ji a kunnenta veil ɗin data naɗa ya lulluɓe wuyanta. Hannun tai saurin riƙowa ta
damƙe, cike da in ina ta furta, “Za..zan sha kayi haƙuri”.
Ɗan murmushi ya saki a karo na farko, batare da ya ce komai ba ya sake kai
kofin bakinta. Ita kanta sai da ta ɗan rumtse ido jin yanda zaƙin ya ratsa mata
harshe. Dan abu mai zaƙi bai cika damun Iffah ba. Baifi kurɓa uku ba tai ƙoƙarin
kauda kanta gefe. Hannun ya sake ƙoƙarin kaiwa sama, da sauri ta riƙe kamar zata
saki kuka ta ce, “Zan sha fa”. Nan ma ƙin tanka mata yay ya sake kai kofin lips
ɗinta. Babu yanda ta iya dole sai da ta shanyeshi tas.
“Ai na shanye”.
Ta faɗa a marairaice tana ƙoƙarin janye hannunsa da ga jikinta. Amma sam yaƙi
bata damar hakan. Sai ma kofin da ya ajiye ɗayan hannun ma ya kawo shi kan ƙugunta
sai tin inda taji ciwon ya ɗan murza. Zabura tayi dan wajen har yanzu akwai zafi
mai raɗaɗi saboda ya tsuma bata bari an murza ba. Sake maidata yay ya zaunar, yanda
zafin ke ratsata sai batama san sanda ta maƙalƙalesa ba har ƙafafunta ta naɗe a
jikinsa, hannayenta duka biyu kam ta saƙalosu a wuyansa tare da cusa kanta a
ƙirjinsa da bathrobe ce kawai.
“Karyani kike son yi ne?”.
Yay maganar acan ƙasan maƙoshi kamar mai mura da son danne abinda ke ratsashi.
Baki ta ɗan tura gaba tana ƙara cusa fuskarta ta gefen wuyansa, saukar numfashita a
wajen gaba ɗaya ya ƙara hargitse masa lissafi har jikinsa na wani irin yamutsawa.
Amma sai ya dake kamar yanda ya saba. Sai dai tambaya da ya sake jeho mata da
muryarsa dake ƙara shaƙewa. “Kinyi salla?”.
“Uhm”.
Ta faɗa itama kamar wadda aka shaƙe. “Zaki tayani tawa?”. Ya sake faɗa shima a
ƙasan maƙoshin yana ƙoƙarin dai-daita fuskarta da ke a kan kafaɗarsa da tashi. Bata
da zaɓin da ya wuce ɗaga masa kai jikinta na tsumar da har yana ji. Tausayi da
dariya take bashi, a ransa kam faɗi yake (Stubborn girl matsoraciya). A zahiri kam
cak ya miƙe tsaye da ita a hannunsa, sake ɓoye fuskarta tai da cusa kai a ƙirjinsa
jinta take kamar ta saki ihu dan kunya. Har cikin bayin ya kaita ya dire gaban tap,
yana tsaye a bayanta ya kai hannu ya kunna mata.....

Da kallo ya bita lokacin da suke fitowa ganin tana ɗan ɗingisa ƙafarta. Da
alama dai faɗuwar da tai ɗin har yanzu na damunta. Baice komai ba kamar yanda itama
taƙi yarda su haɗa ido. “Ina zuwa”. Ya faɗa ƙasa-ƙasa yana raɓata ya wuce, cikin
closed room ɗin sa ya nufa, ta bisa da kallo ta gefen ido har sai da ya ɓacema
ganinta ta saki ajiyar zuciya da kaiwa zaune a table ɗin gaban gadon mai laushin
tsiya. Bata gama dai-daita ba ya sake fitowa cikin jallabiya kalar ash sai ɗaukar
idanu take ga wani sirrintaccen ƙamshi. Shi da kansa ya shimfiɗa musu sallaya.
“Mi zaki roƙa mana?”.
Ya faɗa yana ɗan juyowa shanyayyun idanunsa a kanta. Fuska ta ɗan yamutse
batare data kallesa ba kanta tsaye ta furta “Naga iyayena”. “Nifa?”. Ya sake
tambaya har yanzu idanun dai na kanta. Sai da ta ɓata fuska da tura baki gaba
sannan ta furta, “Kai mi kake buƙata kuma a duniya?”.
(Tofa wata sabuwa) ya ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai ya murmusa kaɗan
da ɗan ƙara matsawa kusa da ita gab ya kai yatsunsa biyu kan haɓarta ya ɗago
fuskarta da ƙyau. Lumshe idanunta tayi. Bai damu ba ya cigaba da kallonta sosai.
“K! Mana”. Idanu ta waro waje da sauri. Sai ya waske, ya cigaba da faɗin, “K! Nake
buƙata ki haifamin yara masu kama da ke?”. Baki ta laɓe da kauda kanta gefe ta ce,
“Hu'um ALLAH ya kiyaye”.
“Sai dai kuma na gaba”.
Ya faɗa yana sakin mata fuska ya gyara tsaiwarsa. Itama gyarawar tai tana ƙara
takwaf-takwaf da fuska, dan badan tana tsoron karya maimaita mata na jiya ba da
tuni ta fece a binta. Sun gabatar da salla raka'a hudu da bibbiyu, ya kwararo
addu'oin da suka sata jin nutsuwa a ranta harda ƴan ƙwallarta da bata san na minene
ba. Bayan sun idar tana ƙoƙarin miƙewa ya riƙota. Bata da yanda zatai dole ta koma
ta zauna a tunaninta wata maganar zai mata. Sai taga ya ɗaura farin hannunsa sol da
ke ɗauke da dogayen farce ƙal-ƙal a saman ƙafarta, a hankali ya janyo ƙafar a saman
tafin hannunsa ya ɗan riƙe yatsun, ɗayan kuma ya tallafo diddigen ya ɗagota gaba
ɗaya ya ɗaura saman ƙafarsa da ya tanƙwashe. Kaɗan ya rage numfashin Iffah ya ɗauke
dan mamakinsa, Shiko ko'a jikinsa ya shiga murza ƙafar a hankali cikin salon
kulawa. Da sauri ta ɗan ɗaura hanunta a kan nasa tana narai-narai da fuska.
“What?”.
Ya faɗa yana tsareta da idanunsa da suka wani ƙanƙance sosai a kanta. Kamar
zata saki kuka ta ce, “Zafi”. Komai bai sake ce mata ba ya ɗauke kansa cike da
basarwa ya cigaba da murza mata ƙafar. Tsahon minti biyu kafin ya ajiye ƙafar ya
miƙe. Itama miƙewar tai ƙoƙarin yi taji kawai anyi cak da ita an dire saman gado
shima ya kai zaune gefenta. Man zafi ya ɗauka a side drawer ya sake kamo ƙafar ya
shafa mata, ita dai tayi kurum yanzu sai binsa kawai take da kallo dan ƙafar ya
fara sakin mata. Hannunsa ya janye yana ƙoƙarin rufe kwalban suka haɗa ido. Da
sauri ta maida nata ta risinar da faɗin, “Thanks”. Yanzun ma komai baice ba ya
miƙe, ita kuma ta zubama ƙafar ido tana sauke ajiyar zuciya. Bayan kamar minti biyu
tana kan ƙulla shawarar barin ɗakin ya dawo inda ya tashi hannunsa ɗauke da lap-top
da kofin shayi.
Laptop ɗin ya ajiye a table ɗin gabansu tare da juya mata fuskanta batare da
yace komai ba. Zamansa ya gyara cike da ƙasaita ƙafa ɗaya ƙan ɗaya ya ɗauka cup ɗin
shayinsa ya kai baki yana wani ɗan lumshe idanunsa da ke mata kallon nan dai dake
hanata sukuni... Itama ta gefen ido take kallonsa yanzu, a zahiri kam tayi wani
irin gefe da fuska ita a dole ba kallonsa take ba...
“Autah!”.
Wata sassanyar murya da ko a cikin tsakkiyar barci ta jita a kunenta bazata
taɓa manta mai ita ba. Ƙirjinta ne yay wata irin yankewa ya faɗi, sai kuma ta juyo
da sauri jin an sake kiran sunan nata. Idanu huɗu sukai da Ummu, Babiy a gefen
damarta, Hanash gefen haggunta. Kamar wadda ta firgita ta miƙe a zabure jikinta na
rawa. Sai kuma ta dubi Tajwar Eshaan da ke zaunensa kamar baima san mike faruwa ba.
Dan shayinsa yake sha a hankali cike da nutsuwa idanunsan nan a lumshe. Kai ta fara
girgizawa, sai kuma ta dubi fuskar laptop ɗin. Still dai Ummu ɗin ta ce, da Hanash
da Babiy data gama yarda ta rabu da su har abada. Sai Kaka da Iyyani da suka ƙaru.
Sai kawai ta diro a gadon ta durƙushe gaban laptop ɗin ta fashe da kuka. “Dan ALLAH
gaskiya ne ko mafarki nake? Gizo kuke mun ko video recording ne aka ɗauka?”.
“Live ne auta. Video call ba mafarki kike ba”.
Hanash ya faɗa fuskarsa shimfiɗe da murmushi. Yi tai kamar wadda tai suman
wucin gadi, sai kuma ta dubi Tajwar Eshaan baki sake. Idonsa shima a kanta suke, ya
sakar mata wani shegen murmushin da kanne mata ido ɗaya ya ɗauke kai..........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (42)

_____________

Lifestyle_Nig for everything that makes your lifestyle complete ..👌


Furnitures
Decoration
Kitchen items &
Boutiques
Quality is our watch word at lifestyle shop kano/kaduna
Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and
second gate near kashe magana suya spot
Instagram Lifestyle_Nig
Facebook Lifestyleng
Tik tok Lifestyle_Nig
Delivery nation wide 08036414048
Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah

______________

.........Zubewa tai a ƙasan lallausan carpet ɗin wajen da ƙyau kamar wadda aka
zarema dukkan kuzari. Duk da basu san mita kalla ba tai wannan irin zubewa zaune
baki ɗaya duk sai suka saki dariya. Kaka yace “Rigimammiyar yarinya har yanzu ɗin
baki yarda ba dai?”.
Kuka ta sake fashewa da shi a karon na biyu kamar wadda kaka yay ma allura.
Idonta kan Laptop ɗin ƙuri tace, “Kaka! Babiy! Iyyani! Ummu! Hanash Akhi. Dama duk
kuna raye? Kuna raye kukai nesa da ni?. Kuna raye nake kuka babu dare babu rana ba
mai share mun? Miyisa haka? Why! Why Iyayena? Miyasa akacemin kun mutu har yanda
aka kasheku aka nuna min......”
Wani irin kuka mai ratsa zuciya ya sake kufce mata. Idanunsa kawai ya lumshe
yana ɗan matsesu da ƙarfi, dan har tsakkiyar zuciyarsa yake jin kukan. Ga wani abu
na zaburo masa tun daga tsakkiyar kai har yatsan ƙafa. Jin zata ɓallo masa ruwa ya
miƙe da ɗan sassarfa. A zahiri kam babu abinda mai kallo zai iya gani sai tarin
nutsiwarsa da cikar kamala. Shiko shi kaɗai yasan sirrin dake tattare da baɗininsa.
Sirrin da yake adanawa tsayin shekaru duk tsananin bamai iya ganosa akan fuskarsa.
Da ga shi sai UBANGIJINSA. Sai amintaccen manomin ganyayyakin shayinsa da yake sha
domin cigaba da binne raɗaɗin sirrin nasa. Jikin glass window ɗin ɗakin koma ace
bango dan kamar da shi ne gaba ɗaya akai ginin sashen nasa ya ƙarasa. Huci yake
faman firzarwa a jajjere, idanunsa da sukai wani irin kaɗawa launinsu ya canja
nabin wajen masarautar dake ƙwanyar da haske tako ina da kallo. Babu yawan zirga-
zirgan mutane, sai masu tsaro tako ina dake kaikawo kowanne da makami a hanunsa,
dan tun abin nan na ƙarshe da ya ƙara faruwa da Iffah aka sake ninka tsaron gidan
tako ina.

A ɓangaren Iffah kam kalamanta sun matuƙar karya zukatan su babiy, tuni suma
sun fara share hawaye musamman Ummu da Iyyani. Kaka dai murmushi kawai yake da bin
ƴar jikallen tasa da yake matuƙar so da kallo kawai. Haka ma Babiy ya kafeta da
idanu zuciyarsa cike da tausayinta da so. Iffah'r sa jaruma ce, amma kuma mai rauni
ce. Kura ce, ga tsoro ga ban tsoro. Murmushi ya saki a karo na farko shima, kafin a
hankali ya katse koke-koken nasu. “To ya isa haka ko? Wani ya akai? mi akayi? Duk
ya wuce Fhareedah kinji, kiyi haƙuri bamuyi nesa da ke ba dan son zuciyarmu. A duk
motsinmu kina ranmu. Ƙaddara ce ta rabamu dake badan mun so haka ba. Amma ki
gafarcemu kinji autan Babiy. ALLAH yay miki albarka, ya cigaba da baki kariya”.
Hawayenta ta shiga sharewa tana gyaɗa kai, haka take sam bata da gardama ko
jayayya. Dan bata taso taga na sama da ita nayi ba. Sai da ta share hawayenta tas
sannan ta sake kallonsu. Murmushi ta saki a yanzu kuma, cike da jin daɗin ganin sun
canja mata gasu fas-fes da su. Gaishesu ta fara ɗaya bayan ɗaya, kowanne yana amsa
mata cike da kulawa da ƙauna. Su kansu duk ta sauya musu, gani suke ta ƙara musu
girma a ido, dan ma tasha wahala a kwanakin nan. Ga wani ƙyau na musamman ta ƙara
da uban haske kamar mai yaron ciki. A ɗan marairaice ta ce, “Amma Kaka akace min
duk an kashemin ku?”.
Dariya ya ɗanyi cike da dattakonsa. “Uhm uhm Iffatu duk gudun son tabbatar da
ƙaddarar wani ga masu buri ai dole suyi haƙuri hukuncin ALLAH da zartarwarsa. A
tunaninsu kam mun mutum, sai da wani bawan ALLAH damu kammu har yanzu bamu san waye
ba ya tallafi rayuwarmu ya ƙuɓutar da mu..”
Da sauri Iffah ta kai dubanta inda Tajwar Eshaan ke tsaye har yanzu jikin
window. Sai kuma ta sake maidowa ga su Kaka. “Har yanzu kuma baku san waye ba da
gaske? To amma ya akai nake wannan video call ɗin da ku kuma?”.
A yanzu kam Babiy ne ya bata amsa. “Har yanzu bayan Barrister Abdallah ba
mu san takamaimai wanda ya jagoranci fiddomu zuwa wannan ƙasar ta Saudiya ba. Waya
kuma ance mana kawai zamuyi magana da ke ne. Mu harma mun fara tunanin ko kece”.
Idanunta ta waro da ƙyau, sai kuma ta sake kallon inda Tajwar Eshaan yake har
yanzu, still dai yana tsayensa. “Ko kaɗan bani nace Babiy, hasalima ni an riga an
sanarmin na rasaku. Shiyyasa a kullum nake cikin alhini da baƙin ciki.”
Kallon juna suka shigayi da mamaki, sai dai Kaka mutum mai hangen nesa ya
ce, “K waya haɗamu da k?”. Baki ta buɗe zata bashi amsa, sai kuma ta sake kallon
wajen window ɗin. Cikin sa'a yanzu kam ya juyo, ya wani tsatstsareta da kaifafan
idanunsa. Kansa ya girgiza mata, da mata alamar zip a baki da yatsunsa biyu cike da
gargaɗi. Jiki a sanyaye ta maida dubanta gasu Babiy, kanta ta ɗan girgiza musu ta
ce, “Wani bawan ALLAH ne, asirrance ya kawo min nima ban gama tantance ainahinsa
ba”.
Cike da gamsuwa suka shiga jinjina mata kawuna. Kaka kam dai murmushi kawai
yayi ya basar. Da ga haka taci gaba da zaƙulo musu tambayoyi suna bata amsa ɗaya
bayan ɗaya. Sun kwashe kusan awa biyu kamar ba kuɗi ake ci ba kafin yay mata nuni
da sallama dan tuni ya baro window ɗin ya dawo inda ya tashi. Badan taso ba tai
musu sallama. Suma ɗin dai da alama basu gaji da kasancewar da ita ba.

Yanda take ta sakin murmushi ya sashi kasa daina kallonta. Sai dai murmushin
nata mugu-mugun birkita masa lissafi yake. Jiki a saɓule ya miƙe da nufin barin
wajen yana rumtse ido da cije lips, a bazata, bazatar data nema kifo zuciyarsa ƙasa
kawai yaji ta rungumeshi ta baya. Cak numfashinsa da duk wani abu mai motsi a
jikinsa yay tsaiwar mutuwar wucin gadi. Iffah da gaba ɗaya farin ciki ya lulluɓe
mata idanu tama rasa mizata masa yasan tana cikin shauƙi ga neman abokin da zai
tayata wannan farin ciki batare data kawo komai a ranta ba ta rungumesa dan yau
kallon Hanash take masa ba Shahan-shan ɗin ƙasar ruman ba. Kanta ta sake kwantarwa
a faffaɗan gadon bayansa da baifi iyakarta rabi da kwata ɗin tsahonsa ba ta sake
matse hannayenta data sakalo ta saman shafaffen cikinsa waje guda tai masa ƙamƙam
tana murmushi mai bayyana haƙwara.
A hankali ta furta. “Jazakhallahu khairan Eshaan Akhi. Yanda ka faranta
raina kaima ALLAH ya ninka maka farin cikinka na tsahon shekarun da zakai a duniya.
ALLAH ya ƙara ɗaga darajarka ya baka kariya. ALLAH ya yafe maka kurakuranka ya baka
ikon sauke nauyin daya ɗaura maka na jarabawar shugabanci. ALLAH ya jiƙan
mahaifinka da kakaninka da duk wani makusancinka da baya numfashi. UBANGIJI ya biya
maka buƙatinka harma wanda ka barma zuciyarka da wanda ma baka jisu a ranka ba har
yanzu. ALLAH ya share maka hawayenka a duk lokacin da kaji son yinsu tun kafin su
zubo....”
Rawa jikinsa ya farayi, numfashinsa na fisgar fita da gudu-gudu. Dan gaba
ɗaya Iffah ta hargitso duk wani rauninsa na baɗini da ya ɗauki tsahon shekaru yana
adanawa. Hannayenta da ke akan cikinsa ya zare a hankali cikin son dai-daita kansa,
janyota yay ta dawo ta gabansa, kafin ta iya cewa wani abu ko samun damar kallon
fuskarsa a wani irin slowly ya rungumeta gaba ɗayanta cikin jikinsa da gaba ɗaya
ƙofifin gashi suka buɗe. Ɓat ta ɓace cikin jikinsa tsabar yanda ya fita girma da
tsayi, tsam-tsam yay mata har sai da ta saki ƴar siririyar ƙara da masa ƙaramin
dundu (ƙulli inji Katsina wa😀) a baya. Ko gezau baiyi ba, sai numfashi da yake ta
saki a sarƙe, itako da taji matsan yayi yawa sai ta shiga mutsu-mutsun son ya
saketa. Yo ina dalili wannan matsar kamar za'a ɓalla mata ƙashi. Ganin fa zai
ɓaɓɓalatanne a shagwaɓe kamar zata fasa kukan ta ce, “Wayyo Eshaan Akhiiiiii!!”.
(Ya arrahaman) ya faɗa sauran notikan da suka rage suna aiki a jikinsa na
ƙarasa kwancewa jin yanda ta fitar da kalmar Akhiiii ɗin. Ga wata irin hajijiya da
ke juya masa ɗakin na neman zubar da shi ƙasa. Cak ya ɗagata da ga kan ƙasa. Da
sauri ta ƙanƙamesa gabanta na faɗuwa jin yanda jikinsa ke wani irin tsuma kamar ba
Shahan-shan da ta sani ba. “Am sorry” ya faɗa yana zubewa da su saman gadon da
jawota jikinsa ya manne lips ɗinsu waje guda.
Wani irin salo yake mata mai matuƙar birkita tunani da susuta rai. Kamar ba
shi ba, kamar ba Shahan-shan ɗin nan ba mai tsananin miskilanci da ƙasaitar mulki.
Idanunsa ya matuƙar rufewa, babu yaren da yake fahimta sai yaren isar da saƙonsa ga
Iffah. Sai da ya tabbatar ya gama lausasata da dukkan iyawarsa da shi kansa bai san
ya iya ɗin ba. Lips ɗinta kam har wani irin zafi-zafi radaɗi-raɗaɗi suke tsabar
yanda suka sha wahala a hannunsa. Yana sakin mata su baya taja tana mai jujjuya
masa kanta. Da matuƙar tashin hankali da tsoron da ke bayyane cikin idanunta ta.
Har numfashinta sarƙewa yake tsabar yanda ta tsorata da yanayinsa wajen furta
“Please Eshaan Akhiii Please”.
“Bazan iya ba My Sohaa”.
Ya faɗa cikin wata irin sarƙaƙaƙƙiyar murya da bata taɓa jinta tattare da shi
ba. Ƙirjinta ne yay wata irin sake harbawa. Ta ɗan ƙara jan jikinta baya still tana
jujjuya kanta. “Kai shugabane kamun adalci ban shirya hakan ba”.
“Gareki ni bawa ne, ke kaɗaice sirrin Eshaan bin Haysam Abdul-majeed Aliy
Qutb Fhareedah bint Zayyan”.
A cikin matuƙar tashin hankali ta sake ja baya tana girgiza masa kai dan
idanunsa basu taɓa firgita rayuwarta irin yau ba, yau ɗin ma yanzun nan. Wani irin
murmushi da ya nema ɗauke numfashinta ya sakar mata, tare da ɗora hannunsa saman
zip ɗin gabar rigarsa ya zugesa zuwa ƙasa, ya ɗaga rigar kawai ya zare baki ɗaya.
Ai a wani irin mahaukacin gigice Iffah ta fasa ƙara jikinta na karkarwa ta tusa
kanta cikin filos ɗin gadon ta cure gaba ɗaya jikinta waje guda........✍️

_😬🚴Lamarin ya girmi ƴan shekaruna bara nayi nan._

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (43)

........Murmushi ya saki yana mai lumshe rinannun idanunsa. Lumshesu yay a hankali
yana cije lips ɗinsa, yayinda wani abu mai sanyi ke saukar masa tun daga saman kai
har yatsar ƙafar sa. Tabbas shi yasan juriyarsa tazo maƙura, maƙurar da in har bai
samarwa kansa abinda yake so ba akwai babbar matsala, matsala irin wadda doctor
ɗinsa ya sanar masa a ƙasar Cuba shekaru huɗu kenan da suka shuɗe. A hankali ya
buɗe fitinannun idanunsa a kanta ya sake lumshewa tare da kaiwa kwance kusa da ita
shima. Idanun ya sake buɗewa tare da kamo hanunta cikin nasa, cirota yay daga cikin
filos ɗin da take ƙara cusa kanta ya maidata jikinsa ya rungume ya na wani irin
tsuma. Cikin disashiyar muryarsa da ke ƙara sarƙewa ya shiga faɗi a kunnenta “Kin
yarda ke ce sirrin Eshaan bin Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb? Tabbas kece, ki yarda
kece Fhareedah bint Zayyan. Lokaci yayi da kowama zai yarda kece sirrin Eshaan,
dole su tabbatar, dole ne na sakasu su tabbatar”. Ya ƙare maganar da ɗago fuskarta
saitin tashi da tai jazur abinka da fari. Hawaye take sosai tana ƙara rumtse
idanunta, itama tata fuskar duk ta birkice, jikinta kuwa rawa yake sosai har yana
iya jin yanda bugun zuciyarta ke harbawa da azabar gudu. Dan yau tayi gamo, gamo
mai tsananin saka ɗimuwa da tsayawar bugun zuciya musamman ga irinta.
“Open your eyes my Sohaa. Please Open”. Ya faɗa cikin muryarsa da ke ƙara
komawa can ƙasan maƙoshi yana ɗan bubbuga fuskarta. Maimakon buɗe idanun da ya
buƙata sai kawai ta sakar masa kuka tana girgiza masa kai alamar bazata iya ba.
Wani irin lallausan murmushi ya saki a wahalce da har take iya jin sautinsa cikin
kunenta. Ya sake kusanta fuskokinsu dab-dab har hancinansu na gugar juna. A hankali
ya sake matso da ita jikinsa yana shafa kanta da ɗan bubbuga bayanta yana hura mata
iskar bakinsa cikin kunne alamar lallashi. Sannu-sannu ta fara sassauta rawar
jikinta tana haɗiye hawayen da takeyi, sai kuma ta koma sauke ajiyar zuciya da sake
yin luff a jikinsa kamar wata ƴar mage. Sai da ya tabbatar nutsuwar da yake buƙata
gareta ta dawo jikinta sannan ya ɗan ɗago yana kallon fuskarta da tai shaɓe-shaɓe
da hawaye. Dariya ta bashi ganin duk bakin tsiwar nan da baya mutuwa tun kan aje
ko'ina har ya mutu yau murus. Cikin ƙoƙarin son danne dariyar ya furta, “Na ƙyale
ki?” acan ƙasan maƙoshi.
Da sauri ta ɗaga masa kai tana taɓe fuska zata sake sakin kuka.
“No bana son kuka”.
Saurin haɗiyewa tai tana jinjina masa kai.
“Open your eyes muyi magana, in ba hakaba babu batun haƙuri”.
Mar-mar ta farayi da idanun kamar zata buɗe amma kuma ta kasa, da ƙyar ta
motsa lips ɗinta da ke rawa tana sake takwaf-takwaf da fuska. “Ka saka kaya to dan
ALLAH”.
Murmushi yayi, tare da riko hanunta ya ɗaura a saman lallausan duvet ɗin gadon
ya ce. “Lulluɓeni to”. Da ƙyar ta iya riƙo bargon saboda yanda hanunta ke rawa,
ganin yanda take yi ɗin ya taimaka mata suka janyo a tare.
Cikin ƙara ƙasa da muryarsa ya ce, “Tom buɗe”.
Ta jima tana kokawa da kanta kafin tai ƙundinbalar buɗewar ta saukesu kan
ƙyaƙyƙyawar fuskarsa da gaba ɗaya ya canja mata kamanni kamar ba Shahan-shan ba. Da
sauri tai ƙoƙarin sake maidasu zata rufe ya girgiza mata kansa. Bata rufe ba sai
dai taƙi yarda ta sake kallonsa. Yatsun hanunsa ya saka cikin nata yana murmushin
nan nasa na iya lips, yana shaƙar numfashinta da busa mata nasa tana shaƙa itama.
“Miyasa baki so mu zama abu ɗaya?”. Kanta ta girgiza masa alamar bata sani
ba. “Magana nake so”.
“Ba komai”.
Ta faɗa cikin muryarta da ke a matuƙar ɗashe dan gaba ɗaya wani irin kalar
tsoronsa take ji.
“Dole akwai dalili, gashi ni kuma na kai matsayar da bazan iya amsar
uzirinki ba balle tunanin zan dakata. Sai dai zan miki alkawarin kasancewa da ke
ina mai lallashinki daga nan har lokacin da hawayenki zasu daina kwaranya Niazmina.
K ba MATATA bace kawai RAYUWATACE, ke RAYUWATA ce ki riƙe wannan ki faɗama duniya
da ƙarfin iko”. Ya nisa a hankali yana ɗan kai hannu saman goshinsa ya murza alamar
ya gaji da maganar dauriya kawai yake. “Bazan so tilastaki ba, ba kuma zan iya
barinki ba. Am so sorry zan baki sirrina da ban taɓa koda kwatanta bama wata ba a
duniya, sirrina da nake ɓoyewa a tsahon rayuwar hankalina gaba ɗaya, sirrina da
nake faman adanawa domin ke dana ɗauka tsahon rayuwar hankalina ina addu'ar
samuwarki da ƙyawawan suffofi matar ƙwarai. ALLAH ya tsare miki ni ne domin wannan
ranar Fhareedah, kamar yanda kema nake ji a jikina ya killacemin ke domin ni kaɗai,
mijinki bai taɓa koda kwatanta aikata Zina ba, wata mace daba muharramarsa ba bata
taɓa raɓarsa ba, mijinki ya jure wahalar ƙishin yini da tsahon dare domin ya
kasance naki ke kaɗai, ke kaɗai ɗin da nake fatan ki zama ke kaɗai har ƙarshen
numfashina, ki yarda zan baki wannan sirrin domin *KECE SIRRINA* Fhareedah bint
Zayyan...”
Kalamansa masu tasiri ne ga rauninta, ita bamai jayayya bace mai saurin
sallamawa ce. Ita bamai taurin kai bace mai saurin karɓa ce. Ita ba mai saurin
ƙaryatawa bace tana da rinjayen gaskatawa musamman ga mutum mai daraja irinsa da
ƙarfin iko. Bata da zaɓin da ya wuce shigewa cikin jikinsa ta sake masa siririn
kuka mara sauti da tasirinsa yafi amsa kuwwar baradan mayaƙa dubu bisa dubu a
katafaren filin gumurzin yaƙi na ƙarƙashin daular mulkinsa.
“Karka cutar da ni”.
Ta faɗa tana mai ƙara ƙanƙamesa cike da sallamawa baki ɗayanta. Hannu biyu ya
amsheta cikin tsumar jiki ya ƙara matsota ya rungumeta jikinsa da ƙyau, “Eshaan ba
mai cutarwa bane ga maƙiyansa ma balle ke da ke ce rayuwarsa my Farishta (My
Angle)”.
“Na baka amanar rayuwata, na baka tukuycin hidimata domin ALLAH da girman
hidimtawarka gareni da zuri'ata”.
“Ni shugabane, bama kowane rai kariya a cikin ƙasata dolene gareni balle
zuri'arki Niger. Ba ahalinki kawai ba, ko ƙasar gidanku idan wani yace zai damƙa da
cutarwa baza'a sake jin labarinsa ba a duniya sai dai wani ba shi ba”. Ya faɗa yana
ƙoƙarin rabata da duk abinda yay masa shamaki da ainahinta. Tai ƙoƙarin kanƙamesa
amma yaƙi bata damar hakan, ga lips ɗinta ya riƙe cikin nasa alamar baya buƙatar
sake jin komai da ga gareta kuma. Daga haka dukkan labarin ya canja kansa. Canjawa
mai girman da girmansa ya wuce fassara da baki ko rubutu. Abinda kawai na sani
shine Iffah ta zama Eshaan, Eshaan ya zama Iffah a wata gaɓa mai wahalar hasashe ga
duk masu iya zama ƙololuwa a hasashen. Da gaske itace ɗin sirrinsa, sirrinsa da ke
matsayin sirri mafi girma a duk cikin zagayen sirrikansa....

★★..... ★.....

Duk yanda doctor ya so fahimtar da Miran Jasim da ya matsa a sallamesa ya ƙi


saurarensa, akan dole ya sallamesa a daren. Motar asibiti ta kaisa har ƙofar
sashensa. Duk ruɗewa matansa sukai da ganinsa, sai dai ko kallon inda suke baiyi ba
ya shige ɗakin shi. A falonsa ya samu Miran Arshaan na faman kaiwa da komowa. Bai
yi mamaki ba dan yasan shegen ruɗewa irin na Miran Arshaan ɗin, shi sam bai iya
controlling tashin hankali ba ta siyasa a wani lokutan. caraf kawai yaji Miran
Arshaan ɗin ya cafki hannunsa ya nufi bedroom ɗin sa da shi abinda bai taɓa faruwa
ba.
“Anya kana lafiya kuwa Arshaan?”. Ya tambaya yana dafe wuyansa da ke masa
zafi ko magana yayi, cikin gatse Miran Arshaan ya ce, “Haukacewa nai”. Dai-dai da
shigarsu ɗakin. Miran Jasim ya fisge hannunsa yana mai dalla masa harara, “Ai na
fahimci hakan tun ɗazun, nikam ka ajiye wannan shirmen naka kamun bayanin da zan
fahimceka kasan ban cika son hauka ba fa”. Wata irin shegiyar dariya Miran Arshaan
ya kwashe da ita yana nuna Miran Jasim, “Idan hauka nake kaima wlhy yanzu zaka fara
Jasim.......” tiryan-tiryan ya kwashe komai ya sanar masa. Ashe kam haukan Miran
Arshaan ɗin ƙarami ne da gaske. Dan take Miran Jasim ya rikice yana rantsuwar lasar
takobi akan sai ya datse numfashin Tajwar Eshaan da Iffah kafin su su tona musu
asiri.
“Wannan duk bashi ne mafitarmu ba in faɗa maka, neman barbushi a wannan
daren shine. Sai dai kuma akwai matsala, dan a haƙe wancan matsiyacin yake da son
ganin wanda zai fita a daren nan. Shawara ɗaya gareni muyi fitar rana kuma a daban-
daban”.
Miran Jasim ya gamsu da hakan, anan suka tsaida maganar Miran Arshaan ya
wuce. Sai dai a wannan daren kam babu wanda ya rintsa a cikinsu. Dan hatta Jasrah
kasa gane kan Miran Arshaan tayi gaba ɗaya.....

★★.. TA-KURYA ★....

A wani irin matsanancin firgici ta farka da ga mummunan mafarkin da ya nema


zama sanadin bugawar zuciyarta cikin barcin jiran uwa da ya figeta. Sai kuma ta
zabura dan farkawar tata dai-dai da dirowar UWA kamar wadda aka jeho. A gaban uwa
ta zube babu alamar tana cikin hayyacinta, “Uwa ki tabbatar min mafarki nake, kice
min ba Saiful-malik ɗina ba, kar kicemin tabbatacce al'amari na gani......”
“Tabbatace ne, tabbas tabbatacce ne. Taci nasara, taci nasara ta-ƙurya taci
nasara a kanki Ajlaan ya sallama mata. Ƴar shilar kanari ta zama mai nasara saman
nasararki, ya bata sirrinsa fiye da girman kowane sirrinsa da wani ya sani a
duniya, kin karya mana alƙawari da sakacinki. Dukkanin wahalarki ta baya ta rusa.
Kina cikin matsala. Ke ce a matsala Ta-ƙurya, dan mu ba'a karya mana alƙawari ta-
ƙurya, ba'a saɓa mana alƙawari, domin mu sharaɗinmu baya tashi hhahaha!!!!!.....”.
Rawa jikin Malikat Bushirat yake kamar mazari, ga zufa tai mata wani irin
mahaukacin sharkaf a jiki. Idanunta kam duhu-duhu take gani a cikinsu, tun tana iya
jin furucin Uwa a kusa da ita har ya fara nesa-nesa, a cikin mintuna biyu tai rufff
tare da yin baya yarafff ta zube alamar babu rai.......✍️

_Tofa abin na gaske ne. ✈️


Wanda duk wanda ya shirya yazo mu ware kawai😷😷🙆🙆_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_


_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (44)

........Bai fahimci gagarumar ɓarnar da ya aikata ba sai da ya dawo jayyacinsa.


Tun-tuni azaba tasa Iffah ta sume masa batare da ya farga ba. Ba ita da dama ya
zama dole ta jigatun ba, hatta da shi kansa a jigacen yake kasancewar wannan shine
lokaci na farko a tarihin rayuwarsa. A kallo ɗaya zaka fahimci tabbas maza sunyi
laushi, laushi bana faɗuwa ko gazawa ba, laushi na jin-jina girman UBANGIJI da
godiya a garesa dan shine mai azurta bawa da ni'imomin kala-kala iri-iri daban-
daban da kai kanka baka fahimtar girman wannan ni'imar sai randa ta isa gareka.
Babu ɗan gata a ma'aurata mace ko namiji sai mafi ƙololuwar iya riƙe kansa da
nisanta kansa da ga ZINA har sai randa ALLAH ya azurtaka da halal ɗinka. Ya shaida
yau kam ya shaida. Bayan uwa da uba da kakarsa bayajin ya taɓa jin ƙauna da
soyayyar wani mai tsananin ƙarfi a zuciyarsa kamar yarinyar nan. Ƙololuwa yake
jinta, ƙololuwar da in har akace yay fassara ba lallai masu jinsa su iya yarda ba
ko zaman saurarensa har ya kai inda yake buƙatar gamsar da su. Badan kar ace ya
bada maza ba da shimafa kukan zai fashe da shi kawai a wannan gaɓar. Da ƙyar ya iya
ɗagota yana ɗan bubbuga fuskarta da kiran sunanta cikin sarƙaƙaƙƙiyar muryar sa. A
baɗini a birkice yake, amma a zahiri da zaka iya ganinsa a nutse yake komai tamkar
ma koman da mai kallo zai kalla komai bai zama komai ba. Iya jijjiga da kiran
sunanta da yayi babu alamar rai tare da ita. Ya rumtse ido da ƙarfi tare da kai
hannunsa saman goshinsa yana murzawa tsabar baima san miya kamata ace yayi ba.
Shifa ɗan gata ne, ɗan hutu ne, ɗan lele ne, tunda ya tashi bai san komai ba sai ai
masa cikin bada umarni, a inda ya rayu zagaye yake da masu hidima daban-daban da ko
abinci inda zai yiwu tauna masa za'ai a zuba masa a cikinsa. Sai da yay matuƙar
yaƙi da iyayensa kafin ya samu wasu damammaki na dogaro da kai dan shi yafi son
tsayawa a kan ƙafafunsa koda ace shine mafi zama ƙololuwar gata a wannan rayuwar.
Bai taɓa ƙyamatar rayuwar talakansa ba sai ma birgesa da basa tausayi yake.
Shiyyasa ya zaɓi shiga cikinsu ta hanyar ɓadda kama, ya kuma ƙir ƙiri wasu hanyoyin
tsaya musu a duk lokacin da ya fahimci ana zaluntar su.
Bashi da zaɓin da ya wuce sake maidata a jikinsa kawai ya rungume tsam-
tsam ya shiga bata wasu irin manya-manyan sumbata masu daraja da ba'aima macen data
ɓarar da darajar a wajen marasa daraja. “Kiyi haƙuri, kiyi haƙuri na tuba my
Ashna”. Ya faɗa cikin kunnenta yana ɗan hura mata isaka a sautin muryar nan tasa da
ta sake disashewa matuƙa cikin maƙoshi kai kace zata iya jinsa. Kamar ko wani
siddabaru sai kawai tai wani irin zaburowa da jan numfashi a fisge. Da sauri ya
janye hannunsa da ke saman goshi ya dubeta, sai kuma ya sake riƙota da ƙyau cikin
jikinsa da take neman kufcewa yana ambaton sunan ALLAH a daburce. Wani irin siririn
kuka data sake birkita masa lissafinsa ta sake sakar masa tana ƙanƙamesa da jera
masa magiyar roƙon ya barta, ya barta zata mutu, dan a rayuwar Iffah bata taɓa cin
karo da azaba makamanciyar ta wannan gaɓa ba.
“Am sorry relax, cool down babie” ya faɗa yana ƙara ƙanƙameta cikin jikinsa
da tura yatsun hanunsa cikin birkitacciyar sumar kanta da ya gama harmutsawa. Har
aka fara kiraye-kirayen sallar asubahi bai daina lallashin da bai san taya zai mata
magana mai tsahon da zata fahimcesa ba. Shi gaba ɗaya ma ya wani mance kansa a
matsayin Shahan-shan, duk ta gama harmutse masa ɗan sauran lissafin da ya rage masa
da rikicinta. Yasan zai fiskanci ma fiye da haka in dai yarinyar nan ce, ba'ace
mata kule ba ma tace cas inaga yau shi ya taro fitinarta da karan kansa, ai yasan a
darunta ma bata fara komai ba kam dan har yanzu bata gama dawowa a hayyacinta ba
ballema ta fara. A hankali yay ƙoƙarin kwantar da ita domin sauka ya samu mafita
amma ta ƙanƙamesa ta na sake sakar masa wani sabon kukan da ko muryarta ma ba'a iya
ji tsabar yanda ta gama galabaita. Ji yay kawai murmushi mai sanyi ya suɓuce masa,
sake riƙota yay yasa a cikin jikinsa yana hura mata iska a kunne cike da soyayya da
ƙaunarta da ke neman fallasa kansu a zahirinsa. Ajiyar zuciya ta cigaba da saukewa
jikinta na saki kaɗan-kaɗan, da ga haka wani wahallen barci yay awon gaba da ita.
Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke ya kwantar da ita a hankali sannan ya sauka a
gadon.
Cikin ƴar sassarfar da a zahiri bazaka taɓa gani ba, dan babu abinda ya
canja a salon tafiyarsa ta ƙasaita ya nufi bathroom, ƙarƙashin shower kawai ya
shiga, babbar gaba ɗaya ya kunna ma kansa tare da dafe bangon glass ɗin da aka
zagaye wajen shower ɗin kamar wani ɗan ɗaki. Duk da sanyin da garin ya ɗauka na
hadarin da aka haɗa ya ƙare da isaka da ɗan yayyafi ya baje dana ruwan baya jinsa
ma. Cikin ƙanƙanin lokaci ruwan yay masa sharkaf, tattausan yalwataccen gashin
kansa duk sun kwanta masa a goshi har wasu na ɗan taɓa saman idonsa saboda ɗan
tsayin da suke da shi. (She's my everything. Ta daban acikin daban ƙololuwa!....)
Kawai yake iya maimaitawa a zuciyarsa hakwaransa cije da lips ɗinsa kamar zai
hudasu kawai ya huta. Sai da ya kwashe kusan mintuna bakwai a ƙarƙashin shower ɗin
sannan yasa hannu ya danne makunar yana sauke numfashi a jajjere. Har lokacin
hannunsa ɗaya dafe da bangon glass ɗin. Jin atshawa na taso masa sannan ya buɗe
idanunsa da sukai wani irin jajir da ƙanƙancewa. Sanin in har ya fita da wannan
sanyin a jiki zazzaɓi salamu alaikum ya sashi sake kunna shower ɗin, sai dai yanzu
ruwan ɗumi ne saɓanin ɗazun. Sumar kansa ya shiga yamutsawa a kasalance ruwan ɗumin
na ratsashi da ƙyau, da ace zai iya kuwwar tattaro hankalin mutanen duniya baki
ɗaya zai faɗa musu itace komansa, idan yace komai, komai da komai yake nufi akan
komai. Sake jin kiran salla ya sashi ƙarasa komai a gurguje ya fito..
Yana fitowa a kanta ya fara sauke birkitattun idanunsa da launinsu ya zama
abin firgitarwa ga mai kallo. Tuni barcin da ya ɗauke ta ya ƙara nisa, barcin da
shi a karan kansa yasan na wahala ne kawai. Janyewa yay ya cigaba da takowa cikin
ɗakin sannu a hankali kamar mai sanɗa, dan gaba ɗaya jikinsa babu wani ƙarfi kona
sisin kwabo. Sai dai jarumtarsa ta ɓoye komai bayan canjawar launin idanunsa baka
isa fassara yanayinsa ba. A gurguje ya busar da kansa domin rage laimar cikinsa ya
shirya cikin jallabiya mai taushi fara tas, ya ɗaura baƙar alƙyabba irin ta
sarakunan Saudiya da mayafi a kansa tare da daɗaɗan ƙamshi kamar ba sallar asubahi
zai fita ba. Gaban gadon ya tako a hankali, barcin kam da nauyi ya ɗauketa, sai dai
a kallo ɗaya zaka fahimci a matuƙar wahalce takeyinsa, dan sai yamutsa fuskarta da
yake ɗan gani a hasken ɗakin da yake dimmm take ga ajiyar zuciya da take ta faman
saki a jajjere. Idanunsa ya ɗan lumshe ya sake buɗewa a kanta yana sakin guntun
murmushi da jan jikinsa baya a hankali ya fice fara gabatar da salla kafin ya dawo
su ɗora daga inda suka tsaya dan yasan sabon daru kam zai fuskanta. Shi kuma ko a
yanzu badan yana jin tausayinta ba sake zuwa mata zai a yanda yake jin kansan nan.

★Ana idar da salla ya baro massalin, dan gaba ɗaya hankalinsa na gareta
saboda yasan tana matuƙar buƙatarsa kusa da ita da taimakonsa a wannan gaɓar. Yanda
ya barta haka ya dawo ya sameta. Yanzun ma baiyi wani motsin da zata farka ba har
ya kammala zame kayan jikinsa ya canja da ƙananu. Bathroom ya nufa ya haɗa ruwa na
musamman sannan ya dawo gareta. Kai tsaye ya kunna wutar ɗakin da ta haske ko'ina
ko allura kuwa ka yarda kaga abunka. A hankali yake bin ɗakin da kallo tamkar yau
ne karo na farko da ya fara kasancewa a cikinsa. Ya ɗan saki murmushi yana mai
lumshe idanunsa da sake buɗewa. Shi kansa ɗakin ya ƙara zama mai wata irin daraja
da kima ta musamman a garesa, dan ya zamar masa ɗaki mafi zama ƙololuwar sirri sama
da duk sauran sirrikansa. Dubansa ya kai ga gadon inda Iffah ke ƙudindine sai faman
sauke ajiyar zuciya take yi cikin barcin wahalar da take yi. Magiya roƙo neman
agajin da ta dinga jera masa na dawo masa daki-daki, da'ace gilashin ɗakin nan ba
mai hana fitar sauti bane babu abinda zai hana a daren na jiya gaba ɗaya daular
ruman su jiye masa sirrinsa, dan bakinta bai mutu ba sai da ta sume masa. Ya ɗan
sake murmusawa da takawa sannu-sannu kamar wanda baya so zuwa gaban gadon ya zauna
gefenta. Fuskarta da tai luɓu-luɓu na kukan data sha ya shafa yana kaima lips ɗinta
da sukai bushewar wahala sumbata. A firgice ta farka tamkar ɗazun, ta saki wani
irin wahallen kuka da jujjuya kanta tana mai jero masa roƙon ya barta, dan ALLAH ya
barta karya kasheta bazata iyaba. Yanda take yi ɗin dole ne ya baka tausayi, dan a
kallo ɗaya zaka fahimci har yanzu bata cikin hayyacinta. Shi baima san ta ina zai
fara ba duk da ya jima da shiryama irin wannan ranar ba tun yau ba, amma a yanda
yaje mata shi kansa yasan ya jigata ta, irin jigatawar da da'ace wani ne ya aikata
aka kawo masa ƙara sai ya hukunta mutum. Sai gashi shi da kansa ne, shi da kansa ya
kasa control ɗin kansa yay ma ƙaramar yarinya kamarta zuwa har uku a dare ɗaya duk
da ta kasance tamkar jaririya a hannun uwa garesa.
“Shiiii!!” ya faɗa a hankali yatsansa kan lips ɗinta. Riƙeta yay da ƙyau
tare da manna mata wata sumbar a goshi kafin ya miƙe cak ya ɗagata zuwa bathroom.
Wata gigitacciyar ƙara ta saki jinta a ruwan zafi tana rirriƙesa azaba na ratsata,
jikinta sai rawa yake shi kansa har abin ya bashi tsoro. Dole ya shiga cikin ruwan
shima ya rungumeta a jikinsa. Kuka take matsananci da ƙoƙarin ganin tabar jikin
nasa amma ya hanata damar hakan. Kansa ya dafe yana riƙota jikinsa da ƙyau cike da
takaicin kansa, sai dai kuma shima ba laifinsa bane, gaba ɗaya idanunsa ne suka
rufe, duk wani haƙurinsa da jarumtar da yake dannewa a tsahon shekaru sai da suka
amayar da kansu. Tunfa yana da shekarun da basu haura ashirin ba yake dakon wannan
matsalar, taya ma zai iya tuna abinda ya dace yayi a wannan gaɓar, ta yaya, ta yaya
ake son ya tuna.......✍️

_🚴🚴🥱Bazaka tunaba kam mai Rumawa._

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (45)

........Sai da ya tabbatar ta samu isasshen gashi sannan ya taimaka mata tayi


wanka, har lokacin bata daina hawaye ba. Idan kuma ya ɗan motsata da ƙarfi ko yaya
ne sai ta saki siririyar ƙara da ƙara ƙarfin kukanta. Babu abinda ya ke iya jera
mata sai kalmar “Sorry, I am sorry”. Bai san tunzura mata zuciya kalmar haƙurin nan
take sake yi ba. Koda ya saka mata bathrobe shima sai da ya cire kayan jikinsa dan
duk sun jiƙe. Yanzu ma cak ya ɗagota zuwa ɗaƙi, ganin lokacin salla ya ƙwace da
yawa ya ɗakko mata rigar jallabiyarsa ya saka mata, veil ɗin ta na jiya ya naɗa
mata sannan ya saka mata sallaya ya sake ɗakkota da ga kan sofar da take kwance ya
ajiye kan sallayar. Ta kasa tsaiwa yanda ya kamata tsabar yanda ƙafafunta kansu
sukai mata tsami, sai da ya dinga lallaɓata sannan tai dauriya da ƙyar, lokacin da
take kaiwa ruku'u da sujida yana jin yanda kukanta ke ƙara ƙarfi alamar a wahalce
take, zaman tahiya kam ta kasa zama da ƙyau. Duk sai hankalinsa ya ƙara tashi, dan
ya fahimci lallai akwai matsala. Tana yin sallama ta zame kwance tana rusar kuka da
kiran Ummu ta zo ta taimaketa. A gabanta yazo ya durƙuso tare da kamota jikinsa,
yanda ya motsatan yasa ta ƙanƙamesa sosai.
“Please stop crying babie”.
Ya faɗa da wata irin murya mai tsananin sanyi da taushi yana rungumeta da ƙyau
idanunsa a lumshe. Duk yanda taso tsaida kukan ta kasa, dan ciwo takeji sosai a
jikinta. Ga kanta na mata wani irin ciwo mai azaba shima. Ga zazzaɓi mai zafi
sosai. Gaba ɗaya ta birkice kamar ba Iffah'r Babiy mai shegen tsiwar nan da tsaurin
ido ba. Dama irinsu bakin ne kawai ba iya jurar wahala sukai ba (lols😆).
Bawan ALLAH Shahan-shan gaba ɗaya ta susutashi ya daina gane komai, yanda
take kukan jinsa yake har tsakkiyar zuciyarsa dan shi mutum ne mai tausayi tun da
can ma. Amma akan fuskar babu alamar wani abu kamancin hakan tattare da shi, yayi
masifar dakewa kamar komai ma bai faru ba. Ɗagata yay daga wajen ya kaita saman
kujera dan gadon gaba ɗaya ya ɓaci gashi farin bedsheet. Rirriƙesa tai da sauri
alamar bazata iya zaman ba, dole ya ɗan kai gaban kujerar durƙushe yana riƙe da
ita.
“Faɗamin minene ke damunki?”.
Yanda ya zuba mata fitinannun idanunsa ba shiri ta shiga ƙoƙarin ganin ta
haɗiye kukan, da ƙyar ta iya furta, “Zafi yake wajen, zafi mai azaba kamar sanda
k.......” sai kuma ta kasa ƙara sawa ta fashe da kuka.
“Stop crying please, bara na duba naga ko kinji ciwo ne”.
Da sauri-sauri ta shiga girgiza masa kai tana matse jikinta waje guda da
faɗin, “Ni bazaka gammun ba, ka kiramin Ummuna”.
Hannunsa ya ɗan kai bisa goshinsa ya murza. Sai kuma ya sake ɗago kan a
hankali, har yanzu durƙushe yake gabanta tamkar ba Shahan-shan ba. Cikin ƙara
tausasa murya da shima har yanzu bata gama dai-daita ba ya kai hannu saman fuskarta
ya tallafo da duk hannayensa, babban yatsansa yasa yana share mata hawaye. “Kiyi
haƙuri, ki zaɓi wanda zan kira miki bayan Ummu, dan ko tana a ƙasar nan bazan iya
haka gareta ba, bazan so ta ganki a haka ba. Faɗamin wa kike so na kira miki bayan
ita? Ammie, Jaddah, ko Mammy, ko Aunty Jasrah? Ko na baki wayar ki zaɓa wanda kike
so yazo?”.
Kanta ta ɗaga masa hawayen na cigaba da kwaranyowa. “Okay tom bar kukan, Ni
bana son ganin hawaye nan suna sake raunani, rauni na kuma yana nufin sake maimaita
abinda nai a daren jiya ko kina so a ƙara?..”
Har zabura take tana girgiza masa kai wani sabon kuka na taso mata, amma
sai tai saurin danne bakinta da hannayenta duka biyu tana ƙoƙarin haɗiyewa. Tausayi
ta bashi da dariya, amma sai ya dake abinsa yana yi a cikin rai. Dan da gaske badan
kar ya kashe musu yarinya ba babu abinda zai hanashi sake kai mata ziyara. Shi
kaɗai yasan mi yake yaƙin dannewa da ga safiya zuwa yanzu, kawai dai abar kaza
cikin gashinta. Ɗan kwantar da ita yay da ga zaman karkacewar da tayi, ya miƙe ya
ɗauko ɗaya da ga cikin wayoyinsa. Gabanta ya sake zuwa ya dirƙusa ɗin dai maimakon
zama da ya saba yi, ita inba a gaban UBANGIJINSA ba yayin bauta masa bata taɓa
ganinsa durƙushe haka gaban wani ba. Duk da bawai yayi wani durƙuso bane na
ƙasƙanci. Hasalima yanda yay ɗin sai ya ƙawatar irin masoyi a gaban masoyiyyarsa
ɗin nan da suke cikin tsananin shauƙi ma juna. Contact ɗinsa ya shiga sannan ya
miƙa mata wayar. Karɓa tai tana sake kumbura fuskar nan da tai jazur duk a suntume
musamman idanunta. Kalmarsa ta zai ƙara ne ya sata danne hawayen tilas badan ta
gaji da kukan ba. Number Mammy ta lalubo, taja wasu sakkani kamar mai tunani ko
tsoron kiran sannan tai dialing. Bugu biyu zuwa na uku kuwa aka ɗaga. Da sauri ta
rumtse idanunta hawayen da take riƙewa na ɓulɓulowa. Da ga can jin anyi shiru
Malikat Haseenat da ta ɗauka wayar kasancewar Daneen Ammarah ta shiga wajenta sanar
mata Malikat Bushirat babu lafiya tace ta haɗa mata ruwan wanka shine ta bar wayar
gefenta, ita kuma ganin number Tajwar Eshaan yasa ta ɗauka da tunanin ko shima
zancen Malikat Bushirat ɗin ne. Amma sai kuma taji anyi shiru ga kuma kamar ana jan
ajiyar zuciyar kuka da ake ƙoƙarin dannewa yana son fita.
“Assalamu alaikum”.
Ta faɗa a nutse cike da dattakonta. Kamar an ƙwalama Iffah farantin silver saman
kai da sauri ta ɗauke wayar a kunnenta ta miƙa masa kukan da take dannewa na kufce
mata. Bashi da zaɓin amsar wayar shi ya kai nasa kunnen, tunda har aka riga aka
ɗaga bashi da hurumin cewa zai yanke sai ya sakata a tashin hankali. Wayar ya kai
kunnensa yana mikewa da yin sallama cikin sassanyar muryar nan tasa mai cike da
nutsuwa da kame kai. Malikat Haseenat ta lumshe idanu da sakin ajiyar zuciya ta
amsa masa. Cikin mamaki yace, “Jaddah ke ce? Ina Mammyn?”.
“Tana haɗamin ruwan wanka ne. Ina fatan lafiya dai ko naji kamar ana kuka
da farko?”.
Ji yay duk yama kasa cewa komai, a karo na farko na rayuwarsa yaji yana jin
nauyin kakar tasa. Amma sai ya daure da ƙyar acan ƙasan maƙoshi ya furta,
“Fhareedah ce Jaddah. Dama muna buƙatar Mammyn ne anan”.
Malikat Haseenat tsohuwar ƙwarai mai ran ƙarfe da cikar kamala. Sai kawai
ta saki murmushi batare da ta nuna ma ta fahimcesa ba tace, “Oh to bara ta fito sai
a sanar mata”.
“Uhum”.
Ya faɗa ciki-ciki. Bata sake cewa komai ba itama ta yanke wayar... Nannauyan
numfashi ya sauke yana ɗan murza goshinsa. Sai kuma ya kalli Iffah da ta rufe idanu
hawaye na cigaba da tsiyaya. Shi kam yama rasa gane kan wannan kuka, amma ya
fahimci harda shagwaɓa da ragwantakar tsiya sai shegen tsiwa bakinta babu mai iya
kadata a zance. Amma gashi a ɗan tabatan da yay da bai wuce ko ƙwayar zarra da ga
abinda ke tattare da shi ba ya sauke take wannan rakin. Lallai ashe akwai aiki
gabansa dan ba'a fara komai ba wannan sharar gona ce. (🚴🚴Taɓɗi).
Tashi yay ya yaye bedsheet ɗin gadon dan yayi ma kansa alkawarin gyara
sirrinsa da kansa. Gudun karma ya barsu a gani closed dinsa ya wuce da su ya adana.
Sai kuma yama ga su bar ɗakin kawai, dan haka ya zo ya ɗauketa zuwa ɗakin kusa da
wannan ɗin ya rufe wannan...

Cikin abinda baifi mintuna goma ba sai ga kira da ga amintaccensa. Bayan


gaisuwa da yay masa cike da tsantsar girmamawa ya nema wa su Daneen Ammarah iso.
Duk da yaji mamakin jin kamar su biyu ake nufi kai tsaye ya bada umarnin ya shigo
da su room 3. Karo na farko kenan bayan ita da ke matsayin matarsa da wani zai
shigo jerin bedrooms ɗin sa na saman nan gaba ɗaya. Dan ko su matansa da duk aka
kawo nan suka rasa ransu a hawa na huɗu ake ajiyesu. Iffah ce ta farko da ta taɓa
hawowa hawan ƙarshen nan.
Ba shi kawai ba, hatta da Iffah da tayo gayyar sai da ta daburce da jin
sautin muryar Malikat Haseenat na sallama. Amma jarumin naku sai yay ɗam da fuska
daɗa duniya bai aikata komai ba babu alamar ko gezau tattare da shi. Sai dai
kasancewar sa mutum mai tsananin kunya sai ya kasa yarda ya haɗa ido da Malikat
Haseenat ɗin. Dan ita kaɗai ta shigo Daneen Ammarah na falo ta kasa shigowa. Bata
san dalili ba kawai taji bazata iya ba, dan zuwan ma sai da Mammah ta tilasta mata
harma yanda ta nuna ya bama Malikat Haseenat ɗin mamaki matuƙa dan kunya ce a
bayyane kamar wadda zatai gamo da surukinta.
A hankali ta cigaba da gara kekenta cikin ɗakin idanunta na yawo kan
Tajwar Eshaan da tun kallo guda da yay mata bai sake ba da Iffah da ke duƙunƙune a
gado cikin bargon da ta sashi ya lulluɓa mata saboda rawar sanyi da takeyi. A gaban
Iffahn ta dakata, a hankali cikin dattakonta da ƙasaita ta kira sunanta da kai
hannu ta janye bargon data lulluɓe har kanta da shi. Ɗan zabura Iffah tayi, sai
kuma tai saurin maida kanta tana hawaye. Tausayi yarinyar ta bata, dan duk wanda ya
kalleta yasan tana cikin wani halli. Batace komai ba ta juya kallonta ga Tajwar
Eshaan da ke ɗan satar kallonsu...
“Barka da safiya Jaddah”.
Ya faɗa a taƙaice yana wani ƙara fuskewa abinsa. Itama sai tai kamar bata
fahimci komai ba ta ce, “Barkan ka dai. Mike damunta haka jikinta zafi zau ga fuska
duk ta kumbura idanu sun ɗashe yarinya duk ta fita a hayyacinta”.
Wayyo shikam ina ƙasa ya ɓuya ciki ko zai kuɓuta da ga bata amsar da bai
ma san ta ina zai fara ba. Amma sai ya dake yana ƙara ɗan kauda kai gefe tsahon
sakkani kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya motsa lips a hankali a gaɓar da ma ta
gama fidda rai da samun amsa.
“Ta girma ne”.
Kallonsa kawai Malikat Haseenat keyi, da jinjina murɗaɗɗen hali irin nashi mai
cike da shegen miskilancin tsiya. Sai kuma ta janye a hankali ta maida kan Iffah
dake raira kuka a hankali. “Niger (Sweetheart)” ta kirata a hankali. Da ƙyar Iffah
ta iya amsa mata murya a ɗashe.
“Daure ki tashi zaune muga”.
Kwatanta tashin tai har sau biyu amma ta kasa, sai ma wani wahallen kuka da
take saki saboda yanda zafi mai azaba ke ratsata. Ta shiga jujjuya kai da faɗin,
“Jaddah bazan iya ba. Zafi kamar zan mutu”.
Idanu ya lumshe a hankali. Ji yake kukanta na wani irin sukar masa zuciya.
Itama kanta malikat Haseenat ɗin wani irin tausayin Iffah'r ne ke ratsata. Ita
tasan ba lalaci bane ko raki kawai. Dan zuri'ar su Tajwar Eshaan ɗin fitinannun
mutane ne da indai mace taje hannunsu basa iya mata ta sauƙi. Shiyyasa mafi yawansu
basa iya zama da mace ɗaya, sannan suna aure da wuri gudun faɗawa halakar zina duk
da akwai bijirarru a cikinsu da kan ringa aikatawar. Amma ita a karan kanta ta daɗe
tana mamaki akan Tajwar Eshaan da ya nuna baya buƙatar aure tun a shekaru fara
girmansa, hakama yanda ya kai har shekarun da aka masa auren fari na sata jin
waswasin ko yana neman matan banza ne ko baida isasshen lafiya. Dan tasan duk wanda
ya kasance jinin zuri'ar wannan daula baya iya kauda kai ga mace irin hakan da ya
nuna shi.........✍️
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (46)

.......Shiru Malikat Haseenat tai kawai tana kallon Iffah da ta koma ta kwanta,
hanunta ta riƙo cike da lallashi ta ce, “To ya isa haka kukan kinji yarinyar
albarka. ALLAH yay miki albarka. Ya jaddada rahama a gareki da yalwataccen farin
ciki na har abada. ALLAH ya sa ki cigaba da zama haske mai haskaka wannan zuri'a”.
A saman lips ya amsa da Amin. Yayinda Malikat Haseenat tai amfani da
wayarta tai kiran Daneen Ammarah. Wani irin yamm ya dinga ji a jikinsa jin Mammah
na bada umarnin Daneen Ammarah ta shigo. Sai yaji kamar kasancewar su a waje guda
yau wani abu ne mai girman gaske. Da ƙyar ya iya dauriyar cigaba da tsaiwa a inda
yake har ta shigo ɗakin. Itama yanda take yi ɗin kamar wadda ta daburce. Sam taƙi
yarda ta dubi inda yake kamar yau ne rana na farko da suka kasance ƙarƙashin inuwa
ɗaya. Koda ya gaisheta kamar yanda ya saba cike da jarumtar danne nasa yanayin
shima a hankali ta amsa masa batare da ta dubesa ba.
Ita dai Mammah hankalinta nakan Iffah ne bata san mima sukeyi ba. Sai da taji
tsaiwar Daneen Ammarah kusa da ita ne ta ɗago. Daneen Ammarah da idanunta ke akan
Iffah wani irin tashin hankaline ke ƙoƙarin mamaye fuskarta amma tana dannesa.
Muryarta a ɗan sassauce ta furta, “Mike damunta haka?”.
“Ɗanki ne”.
Malikat Haseenat ta bata amsa a dunƙule. Ta fahimta dan haka bata sake
magana ba sai da Malikat Haseenat ta ce, “Kamamun ita ta tashi zaune da ƙyau. Sai
ki sake haɗamun ruwan ɗumi da waɗan nan turarrukan”. Kai kawai Daneen Ammarah ta
jinjina ma Mammah, ta matsa ta kama Iffah ta tayar, kuka take sosai tana rirriƙeta
amma Malikat Haseenat ta ce mata ta barta so take ta zauna ɗin sosai. Ba yanda
zatai haka ta zaunar da ita ta zame jikinta batare da ta sake yarda ta kalla sashen
da Tajwar Eshaan ya ke ba ta wuce bathroom abinta. Shima sai kawai yaji zaman ɗakin
bazai yiwu masa ba. Dan haka ya fito abinsa yana mai satar kallon Iffah da ke kuka
da mutsu-mutsun kasa zama da ƙyau. Kai tsaye Gym ɗinsa ya nufa. Jallabiyar jikinsa
ya zame ya canja da sport wears ya shiga motsa jiki da zafi-zafi kamar wanda ake
tunzurawa.....

★Da ƙyar Iffah ta iya kai kanta bayi da taimakon Daneen Ammarah. Ashe ɗazu ba
ƙaramin taimako yake mata ba da yake ɗaukar ta a komai. Sosai hankalin Malikat
Haseenat da ita kanta Daneen Ammarah ɗin ya sake tashi da yanda tafiya ma ta gagari
Iffah. A bayin ma duk yanda taso ganin ta nutsu a cikin ruwan ta kasa zama. Sai
faman rirriƙeta take da magiyar “Mamy dan ALLAH ki fiddani, wlhy da ciwo sosai”.
Kwantar da kanta Mamy tai akan ƙafarta tana shafa kanta cike da lallashi dan
tana zaune ne a bakin kwamin. “Yi haƙuri to ba'a magana a bayi zai daina”.
“Mamy bazai daina ba ƙarawa yakeyi”.
Dauriya kawai Daneen Ammarah keyi, amma ji take kamar tai kuka. Ta fahimci
dole Iffah taji ciwo ne, ciwo kuma bawai ƙarami ba. Ita kam takan rasa miyasa maza
basu da tausayine sam. A shekarun Iffah bai kamata namiji yay mata irin wannan
zuwan na lokaci guda ba. Duk da tasan su waye mazan ahalin nan nasu akan mace,
balle kuma shi da ya kasance tsahon shekaru ma babu macen, ko da ya samesu kuma ita
dai Iffah'r ce ta farko dama take hasashen ya kusanta kenan ko yaya. Tunda kaf
yaran randa aka kawosu garesa washe gari ake zuwa a ɗauki gawarsu sun rasa ransu.
Ɗaga Iffah tai da ga ruwan, ta ɗaure fuska sosai babu alamar wasa tattare da ita,
“Ki tsaya a duba ko kinji ciwo ne a wajen, dan wannan zafin da kike ta ambata dole
zai kasance akwai damuwa Ibnati. Idan kuma aka bar mace da irin matsalar nan yana
lalatata koma ya taɓa mata brain. Ko kina so ki samu matsala a brain ɗin ki?”.
Da sauri Iffah ta jinjina mata kai alamar a'a tana hawaye. Daneen Ammarah
ta haɗiye murmushin da ke taso mata dan ta mata hakane dan ta tsoratar da ita dama
kawai. Ai ko sai gashi ta yarda ta duba cikin sauƙi amma fa ta ɓoye fuska cikin
tafukan hanunnta, wani irin matsanancin kunyar Mamyn na ratsa ɓargo da jinin
jikinta. Amma sai take jin inba itan ba bazata taɓa iya nunama wani ba sai ko Ummu
ko su Arfa da suna raye.
Rasama abin cewa Daneen Ammarah tayi, sai kawai ta miƙe jiki a saɓule cike da
tausayin Iffah. Tabbas dolene ta dinga kuka, a hakan ma sai taga dauriyarta, dan in
har watace tofa sai duk masarautar nan sun fahimci halin da ake ciki. Fitowa tai ta
samu Malikat Haseenat da ke zaman jiran fitowarsu. “Mammah akwai matsala fa
gaskiya, dole a nema likita dan yarinyar nan taji ciwo bana wasa ba”.
Idanu Malikat Haseenat ta ɗan lumshe tare da buɗewa a lokaci guda. Dama ita
ta fahimci hakan ai tun sanda tasa Iffah zama, ta kuma yi hakanne dama danta
fahimta. Amma saboda ta sake tabbatarwar tasa Daneen Ammarah ɗin sake taimaka mata,
turarrukan data bada a saka mata in har Iffahn taji ciwo mai yawa to bazata iya
zama ba daman. “Ammarah wannan sirrine mai girma na shugaban daular ruman. Bazai
yiwu ya fita ba kema kin san bama zai yarda ba. Dole ke zaki bata kulawar da ta
dace”.
“Hakane Mammah, amma ni na ɗauka shekaru rabona da yin wani abu a
matsayin likita. Kar'a samu kuskure”.
“Baza'a samu ba insha ALLAHU Ammarah. Na sanki akan komai shiyyasa nake
alfahari da ke”.
Da ƙyar Daneen Ammarah ta iya haɗiye kukan da ke taso mata. Dan in har
aka tuna mata ita ɗin ƙwararriyar likitace a baya yakan sosa mata wani ɓangare na
rayuwarta data shuɗe da bata son tinawa. Dan tamkar fami akan gyanbon da tasan har
gaban abada bazai taɓa ya warke ba a zuciyarta ne. Muryarta na ɗan rawa ta ce,
“Zanje clinic na samo kayan aiki”. Da ga haka ta fice. Da kallo Malikat Haseenat ta
bita zuciyarta itama na raunana. Tana son Ammarah, matuƙar so da duk a cikin
ƴaƴanta sai dai a biyo bayanta. Sai dai tana dannewa da nuna iya tausayinta kawai
gudun karta raba kan zuri'arta da kanta....

★....

Tsaf Daneen Ammarah taima Iffah da ke kuka na fitar hankali ɗinkin, wai dan
ma ta mata allurar kashe raɗaɗi fa kafin ma ta taɓata. Ana kammalawa ta dinga rawar
sanyi na zazzaɓi kanta kam ai kamar zai fashe da ciwo. Malikat Haseenat ta tafi
domin basu waje, sai dai ta aiko da lafiyayyen farfesu na musamman da wani irin
kunun madara mai zafi shima na musamman. Sai tarin wasu sirrika da Iffah zata dinga
amfani da su yayin sit bath da zai taimaka mata warkewa da wuri da kuma wanda zata
sha dan tasan in dai wannan yaƙinne kam Iffah yanzu ta farashi. Dan in ma fitinar
ce shi kam kamar yacema kowa bai iyaba a ahalin nasa. Gashi yana ɗage-ɗagen waɗan
nan shegunan ƙarafunan abu goma da goma.
Daneen Ammarah sai da ta tabbatar ta gyara toilet ɗin ɗakin tsaf duk da
bawani datti tunda ba'a nan suka kwana ba. Bata canja mata rigar Tajwar Eshaan ɗin
da har yau take jikinta ba duk da ta mata girma da tsaho, dan ko'a wajen gashin
dama sakata tai ta nannaɗe kawai. Zaunar da ita tai kan filos masu taushi amma ta
kasa zama da ƙyau sai da ta karkace. Bata hanata ba ta zuba mata madarar da ke ta
turiri tare da farfesun naman tsuntsayen da ke ta tashin kamshi.
“Mamy na ƙoshi bakina ɗaci barci zanyi”.
“A'a Ibnati daure kinji, idan kika sha madaran nan kikaci wannan naman sai na
ƙarasa miki ɗayan alluran ki kwanta barci har sai sanda kukaso tashi kinji. Bakiji
jikinki yayi zafi ba sosai. Haba ɗiyar albarka haihuwar alkairi”.
Da wannan lallaɓawar Iffah ta fara shan madarar a hankali, Daneen Ammarah
na bata farfesun da kanta cike da kulawa. A haka Tajwar Eshaan ya shigo ɗakin da
sallama ya samesu. A cikin kwalliya ya ke tsaf ta alfarma ga uban ƙamshinsa da ya
cika ko'ina na ɗakin, a taƙaice dai a Shahan-shan ɗin sa yake. Cikin dakewar nan
tasa mai ɓoye duk wani sirrin zuciyarsa da ainahinsa yake. Idanunsa sakaye da
eyeglasses. Ya wani ƙara ƙyau da cikar kamala ga wani kwarjini mai ƙara yalwata
haibarsa ga mai kallo. Daka gansa kasan shi ɗinne dai ɗaya tilo Shahan-shan ɗin
ƙasar ruman mai rumawa da ƙasar ruman. Sai wani shining yake da ke tabbatar da yau
ɗin ranarsa ce ta musamman mai ɗunbin daraja da tarihin da bazai taɓa goguwa a
garesa ba.
Tun a kallo ɗaya da Iffah tai masa lokacin da yake sallamar shigowa ƙasa-ƙasa
bata sake gigin hakan ba. Daneen Ammarah ma dai da ga kallo ɗaya bata sake wani ba,
dan gaba ɗaya kwarjininsa ya cika ɗakin, ga wani kunyarsa da ke ɗawainiya da ita
kamar itace ta aikata tsiyar ba shi ba. Koda yake shima ɗin dai ji yake Mamyn nasa
a yau ta musamman ce a garesa, dan kasancewar ta a sashen nema ya sashi jin gara ya
fita zuwa fada, sai kuma ga kira ya samu da ga Malikat Haseenat bayan fitowarsa Gym
an wayi gari Ammien sa babu lafiya, yana shirin fitowar nan ma Jasrah tai kiran shi
itama tana kuka dan tun ɗazun take kiransa ba'a ɗaga ba.
Cike da dakewa ya sake gaida Daneen Ammarah idanunsa kan Iffah da ke kai
kofin madara bakinta tana sha kaɗan-kaɗan. Miƙewa Daneen Ammarah tai cikin hikima
ta ce ta cigaba da shan madarar da nama bara ta amso saƙon sauran magungunan ta
data bada a siyo....

Shiru ɗakin ya ɗauka sai sassanyan ƙamshin da ya gaurayesa ke tashi. Taƙi


yarda ta kallesa koda da kuskure duk da yanda take jin ɗakin yay mata tsukuku
saboda kasancewar sa. Idanu ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kanta sannan ya ɗan taka
gaban gadon gab, zaune ya kai inda Daneen Ammarah ta tashi a gefen gadon kusa da
ita sosai. Sai kuma ya kai hannu ya zare eyeglasses ɗin da ya sakaya launin
idanunsa.
“Good morning Mrs Eshaan Qutb”.
Ya faɗa da wata irin shaƙaƙƙiyar murya mai sanyi matuƙa yana kai yatsunsa
biyu kan haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau. Har tsakkiyar kai muryar da yay amfani
da itan ta ratsa Iffah, ga wata matsananciyar kunya da shakkarsa da ke ratsata.
Idanun ta da hawaye ke cikosu ta lumshe da sauri.
“Please open your eyes my life”. Ya faɗa fuskarsa gab-gab da ita batare data
san lokacin da ya matsota haka ba.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (47)

........Hawayen da take riƙewa ne suka ziraro, ta girgiza masa kai alamar bazata
iya ba. Komai bai sake cewa ba, sai riƙo hanunta mai riƙe da kofin madarar yay
cikin nasa tare da kofin, bakinsa ya kai ya sha madarar. Ta masa matuƙar daɗi fiye
da duk madarar da yake sha. Still dai hanunsa nakan nata da kofin ya sake kaiwa ya
sha. Sai da ya sha kusan sau biyar sannan ya kai bakinta itama.
“Hhah”.
Ya faɗa a narke yana wani irin busa mata iskar bakinsa kan idanunta da suke mar-
mar, gaba ɗaya neman daburcewa take.
“Kina so na buɗe da kaina?”.
Da sauri ta girgiza kai da buɗe bakin kaɗan ya ɗaura mata kofin. Kaɗan tasha ta
janye, sake ɗaura mata yay. Babu yanda ta iya dole ta cigaba da sha. Bai barta ba
har sai da ta shanye duka sannan ya ajiye kofin. Naman ya ɗauka shima ya shiga bata
yana ci har suka cinye tare da shanye romon ma duka a tare.
“Sai mi kuma?”.
Ya faɗa yana riƙo hanunta a nashi. Fuska a shagwaɓe ta ce, “Barci”. Murmushi yayi
tausayinta da ƙaunarta na sake mamaye shi, sannu-sannu ya kai hanunta kan lips
ɗinsa, babu zato taji saukar kiss a tsakkiyar tafin hannun. Idanunta ta rumtse da
ƙarfi tana matse jikinta dan har cikin ɓargo sumbar ta shigeta. A tare suka sauke
ajiyar zuciya, tai ƙoƙarin zamewa zata kwanta ya riƙota jikinsa. Tsam-tsam ya
rungumeta yana shinshinar wuyanta da busa mata numfashinsa da ke saka tsigar
jikinta yamutsawa.
Luf tayi tana mai shaƙar daddaɗan kamshin turarensa mai saka zuciyar mai
shaƙa nutsuwa, yanda yake hura mata iska a cikin kunne da murza yatsun hannunta
dake cikin nashi tuni barcin da keta rinjayar idanunta ya fara tasiri kanta. Jin
jikinta ya saki gaba ɗaya ya sashi ɗan sakin murmushin ta sake gyarata ta kwanta da
ƙyau, cikin abinda bai wuce mintuna biyu ba numfashinta ya fara sauka a hankali
alamar barcinta yay nisa. Numfashi ya ɗan furzar da gyara filos ɗin gadon ya
kwantar da ita. Lumsassun idanunsa ya zuba mata batare da ya ɗago da ga ranƙwafawar
da yay a kanta ba. Wasu kalamanta ne na jiya suka shiga dawo masa a rai, wani
lallausan murmushi ne ya suɓuce masa ba shiri, ƙoƙarin haɗiye kayansa yay da sake
matsawa da ƙyau jikinta ya sumbaci goshinta da hancinta da lips ɗin da sai da ya
ɗan juya su a cikin nasa sannan ya saki. Bargo yaja ya lulluɓe ta da ƙyau ya
miƙe...

Koda ya fito falon bai saurari abincin breakfast da aka shirya masa ba.
Hakama Daneen Ammarah bata falon, sai amintaccensa kawai da ke dakon fitowarsa.
Gaisuwar amintaccen hadimin nasa ya ke amsawa yana nufar lift.. yayinda shima yake
biye da shi da hanzarinsa.
Fada ya fara nufa cikin takun nan nasa ɗaɗɗaya na izza da ƙasaita. Shigowarsa
da aka sanar tun kafin ya iso ya sa duk wanda ke a wajen miƙewa kai a ƙasa har sai
da ya kai zaune. Suma duk zaman sukai cike da girmamawa suka shiga miƙa gaisuwa
suna satar kallonsa dan yay musu wani fayau da sake cikar kamala kamar wanda akaima
wankan inji. Saɓanin ko yaushe kuma yau fuskar da ɗan sassauci duk da bawai dariya
yake ba ko murmushi. Tana nan dai kadaran kadahan bata tsuke sosai ba bai kuma
saketa ba. Kamar ko yaushe amintaccensa ne ya amsa da yawunsa. Da ga haka aka ɗanyi
zaman fadanci masu ƙorafe-ƙorafe suka kawo yana saurarensu. Hakama masu shawara
akan masarautar ko wani abu da ya faru harma da wajenta. Na masarautar dai duk sun
samu rinjaye ne akan abinda ya faru tsakanin Miran Jasim da iyalansa.
Komai baice akai ba, yana dai jinsu da kunne bisa ra'ayinsu har gardama ma
ta ɗan nema sarƙewa sai da Sayeed Anwarus-sadat ya tsawatar. Baice komai game da
rashin ganin Miran Arshaan ba, shima kuma Miran Jasim ɗin da aka sanar masa ya
matsa an sallamesa tun a daren jiya baice komai ba a kai. Zaman gaba ɗaya bai wuce
na awa biyu ba lokacin sallar zuhur yayi....

Bayan an idar da salla ya samu rakkiyar manyan masarautar duba mahaifiyarsa.


Duk da amota suke duk inda motocin suka gitta hadimai ƙasa kawai suke zubewa kawuna
a sunkuye har suka ƙarisa ƙofar sashen. Motar da yake ciki ma har cikin barandar
gaban falonta ta tsaya. Amintaccensa da yay saurin fitowa da ga gaban motar ne ya
buɗe masa. Shiru babu alamar zai motsa balle ya fito har sai da minti ɗaya da
sakkani ya shuɗe. A hankali ya ziro ƙafarsa dake cikin takalman masu tsananin ƙyau
da ɗaukar idon mai kallo farare tas heif cover, sai da ya sake jan wasu sakkanin
kafin ya zuro ɗayar, nan ma ya sake jinkirtawa sannan ya fito gaba ɗayansa. Tuni
mayataccen ƙamshinsa ya mamaye sashen tunkan ma ya shiga. Hadimai kam rige-rigen
shigewa suke dan mai RUMAN ne fa da kansa ba aike ba. A waje kam jami'an tsaro sun
zagaye sashen tamkar ba'a cikin gida ba. Ameera Danish-Ara da ke zaune a falon tare
da Ameera Haifah da wasu a cikin matan masarautar masu faɗa aji da suka shigo duba
Malikat Bushirat ɗin tuni sun miƙe kawunansu a ƙasa. Takun sawayensa kam tuni ya
saka kowa nutsuwa kowa na satar kallon hanyar da zai shigo da kallo. Yayinda
ƙafarsa ke taka cikin falon babu wanda bai ja numfashi ba, dan a wajen ado kam kowa
shaidane Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed ɗawusu ne. Ƙamshi kam ba'a magana
idan yana waje kowane turare disashewa yake duk ƙarfinsa. Ko sau ɗaya bai kalli
kowa ba, takunsa yake a nutse cikin izza da ƙasaita da ka gansa kaga gwarzon
gwaraza mai gwara kawunan gwarzo mai son nuna gwarzantaka. Gaisuwar da suke ta
faman masa Sayeed Fayzul-haq ne dake take masa baya kawai ke amsawa. Dan sauran
jama'ar da ke a tare da shi duk a farkon shigowa falon suka ja birki.
Sayeed ɗin ma a ƙofar ɗaki ya dakata bayan ya buɗe masa ƙofar ɗakin da akai
musu iso Malikat Bushirat na ciki. Isar ƙamshinsa ciki kafin shi ya saka Jasrah da
ke kusa da ita tana bata shayi miƙewa da sauri. Malikat Bushirat kam idanunta dake
matuƙar jazur ta zubawa ƙofar zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Tunda
ya shigo shima kaifafan idanunsa dake sakeye cikin gilashi na kanta. Nata dake
cikowa da hawaye ta rintse da sauri tana kauda kanta, wani irin zafi takeji, zafi
mai amsa suna zafi na gaske a ƙirjinta har tana jin turirinsa a maƙoshi. A maimakon
zama a kujerar da Jasrah ta gyara masa bakin gadon ya kai zaune. Hannun Ammien tasa
ya kamo a hankali cikin nasa ya sumbata. Maimakon murmushi da take sakar masa a da
idan yay mata hakan yanzu hawaye ne masu zafin gaske da ta kasa riƙewa suka ziraro
da gudun tsiya kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta da duk ta dame kamar ba Malikat Bushirat
ɗin nan ba ƴar gaye, hamshaƙiya ƴar ƙwalisa. Idanunsa ya rumtse a hankali hawayen
na ratsa har tsakkiyar zuciyarsa. Ya jima a haka kafin ya buɗesu ya sauke a kanta.
Handkherciff ɗin jikinsa ya zaro ya miƙa mata, tare da motsa lips ɗinsa a hankali
ya furta, *“‫ َال َبْأَس َطُهوٌر ِإْن َشاَء اللُه‬.*
_La ba'asa tahoorun in sha'al-lah._
(Ba komai, tsarkaka ce in ALLAH ya yarda).
)‫(سبع مرات‬.* ‫ َر َّب اْلَع ْر ِش اْلَعِظ يِم َأْن َيْش ِفيَك‬، ‫*َأْس َأُل اللَه اْلَعِظ يُم‬
_Asalul-lahal-'azeem rabbal-'arshil-'azeem an yashfeek._
(Ina rokon ALLAH mai girma, UBANGIJIN Al'arshi mai girma, ya warkar da kai)”.

_(MANZON ALLAH, tsira da aminci su tabbata a gare shi, ya ce; “Babu wani bawa
Musulmi da zai ziyarci mara lafiya wanda ajalinsa bai riga ya zo ba, sannan ya faɗi
wannan (addu'a) sau bakwai face ya sami lafiya".)_ (ALLAH ya azurta marasa lafiyar
mu da lafiya, ya basu ikon cinye jarabawa, yasa ta zama kaffara garesu. Masu ita
ALLAH ya ƙara musu, ya karemu daga cutukan zamani masu haɗari da hana nutsuwar
zukata😭🙏).
Damƙe handkherciff ɗin kawai tai taƙi share hawayen da suka gagara tsayawa.
Sai Jasrah ce ke faman amsa addu'oin sa da sannu. Cikin damuwa ya kalli Jasrahn
batare da yace komai ba. Ta fahimcesa, dan haka ta fara bayani tana sharar hawaye
itama. “Nima ban san ainahin abinda ke faruwa ba wlhy. Amma dama kwana biyun nan
duk bata cikin walwala. Na kuma tambayeta amma tace min babu komai yanayine kawai,
sai jiya dai da ƙyar ta ce min akan matarka ne, tace ka saketa amma ka share ko
zancen baka sake tadawa ba, ta nema iso gareka ance ka shige ciki a jiya after
isha'i. Ni dai na bata haƙuri da nuna mata abi komai dai a sannu kodan abubuwan da
suka faru na rasa matanka da kai idan kuma akace ka saki wannan haka ɓakatatan ba'a
kai ƙarshen case ɗin nan ba maimakon ita da bata da gaskiya sai a koma zarginka
kai. Ta nuna kamar taji ma wuce, amma sai banyi barci cikin nutsuwa ba dan nasanta
da saka abu a rai, shine ana idar da sallar asuba nazo dan gaisheta na sameta a
ƙasa babu alamar rai tattare da ita. Na nemeka amma baka ɗaga ba, dole nai kiran
amintacciyarta dan ta sanar da Mammah. Sai da ma sukazo ne muka iya ɗagata a ƙasan
ni da Nina Ammarah da ƙyar, kafin a kira Doctors sukazo kanta har dai ALLAH yasa ta
farfaɗo suka sake maidata barci dan tanata zabura kamar wadda ke a firgice. Sun
tabbatar jininta ya hau ƙololuwa har yanama zuciyarta barazana ma. Amma dai yanzu
data farka Alhamdullah Dr Aliyah tace jinin ya ɗan sauka bakamar ɗazun ba”.
Idanu ya kafe Malikat Bushirat ɗin kawai da su na wani tsawon lokaci, kafin
ya furzar da iska cikin damuwa ya furta, “Why Ammie? Why zaki jefa kanki irin
wannan haɗarin saboda ni. Kina tunanin idan wani abu ya sameki zan iya yafema
kaina? Haba Ammien na, ki tausaya mun karki maidani maraya gaba ɗayana babu uwa
babu uba mana. Yayin da na rasa Abbie sai nake kallon fuskarsa tare da taki a waje
ɗaya, hakanne ke samun nutsuwa na share hawayen da suka kwaranyo min kafin su zubo
a kowane lokaci saboda kewarsa. Banƙi biyayya gareki ba, sai dai ina son kareki da
ga abinda zai iya zuwa ya dawo game da umarninki gareni. Yarinyar nan tabbas mai
laifi ce, laifin data ambata da bakinta ta aikata. Sai dai kuma ni shugaba ne,
tanada hakkin da zan bata kariya a yayin da akai yunƙurin cutar da ita itama akan
dalilai biyu. Ita ɗin MATATA ce....” wani irin rumtse idanu Malikat Bushirat tayi,
kalmar matata ce ɗin na mata wani irin sukar mashi a ƙirji, ya cigaba da faɗin,
“Akwai haƙƙoƙinta a kaina dolen dole. Sannan ni Shugaba ne, banda hurumin yanke
hukunci cikin fushi ga talakawana har sai nayi bincike. Sannan ma abu na ƙarshe da
kike zargin ta aikata ba'ita bace ba. Zaki tabbatar da hakan kuma a zaman shari'a
na uku gobe insha ALLAHU. Nayi miki alƙawarin gaggauto da sake zaman shari'ar gobe
kodan mukai inda kike buƙata. Fatana dai yanzu ki kwantar da hankalinki, ki sama
ranki haƙuri Eshaan ɗin ki na tare da ke ɗari bisa ɗari, mai kuma bin umarninki ne
a duk sanda kika bashi, bazan taɓa zama mai bijirewa ba in har ba'a taɓa hurumin
UBANGIJINA ba”.........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_
_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

Book two(48)

....Sam kalamansa babu abinda suke kara mata sai suka a zuciya, Amma sai ta dake ta
daga masa kai kawai tana dan murmushin karfin hali. Tare da kai hanunta saman
fuskarsa ta shafa da fadin, "ALLAI yay maka albarka". A hankali.
Murmushi ya mata shima a karo na biyu yana mai lumshe idanunsa da budewa lokaci
guda ya ce, "Amin nagode Ammie, ALLAH ya kara miki lafiya da tsohon rai mai
albarka" akan lips dinsa. Da ga haka ya dauka shayin da ya samu Jasrah a bata ya
cigaba da bata da kanshi. Sha take tana kallonsa tare da kara tabbatar da zancen
uwa. Dan kuwa babu abinda kake gani a tattare da shi sai nutsuwa da tarin cikar
kamala. Fuskarsa kam sai shining take da daukar idon tabbatar da shi ango ga duk
mai iya kallonsa. Ga wani kamshi da take i can kasa-kasa a cikin nasa da ke bata
tabbacin na mace ne. Hawayen da ke sake taso mata take dannewa, dan yanzu kam tama
fi bukatar kowa ya fice a barta ita daya saboda tana bukatar ganawa da wa. Dole ta
samu mafia, dan bazata taba barin yaronta daya tilo ya sake kusantar mafi zama
makivarta kololuwa ba. Ko zatai vawo tsirara sai taga bayan yarinyar nan, sai taga
banda ya tsaya mata, sai taga yar ban wacece ita, mita taka ne haka da zata zamewa
cikar burinta barazana, burin data dauka tsahon shekaru tana ginawa da kauda duk
wanda ya nema shiga gabanta koda a kuskure ne.
Itace fa ki gudu sa maze gudu TA-KURYA sa maza kurya. Wutar gobara kasheki koda
taro sai an dace.
Matar Shahan-shan din RUMAN war Shahan-shan.
Never for ever ta fadi kasa a dalilin var cikinta da da'ace dan cikinta auren wuri
yayi babu abinda zai hana ya haifeta".
Ganin kamar ta dan saki jikinta har tasha magani bayan tea din da tasha Jasrah ta
hada mata ruwan wanka sai kawai yay musu sallama dan sallar la'asar na gabatowa. A
can kasan ransa kam hankalinsa ya rabu biyu ne. Wani na nan wani nakan Iftah da
itama ya baro cikin halin da ya jefata. Sosai Jasrah taji dadin zamansa tare da su
gain yanda yar war tata ta dan sake, hakama Malikat Bushirat din ta nuna jin
dadinta a zahiri, amma ita kadai tasan kunci da dacin da ke zagaye da ruhinta...
Barci tayi sosa dan har akai sallar azhar bata farka ba. Daneen Ammarah da ke a
sashen zaune takan lekata lokaci zuwa lokaci. Sai kusan 3 ta farka. Yanda ta danvi
dama-dama fuskar ta sabe sosai da kumburin ido ya sata in sanyi a zucivarta, Ga
zazzabin ma ya sauka da ciwon kan. Ta rage rakin zafi-zafin sai dai idan ta motsa
da dan karfi takan aije lips. Ruwa mai dumi sosai Daneen Ammarah ta hada mata. Da
taimakonta ta kara sit bath sannan ta barta tai wanka da karasa kimtsa jikita.
Kafin ta fito an sake gyara dakin da kunna masa turarruka komai ya dauki haramin
kamshi. Kayan da aka kawo da ga sashen Malikat Haseenat masu kyau da daukar idanu
ta alive mata ta fice da dan mata short not ta ajive.
Cikin dabara ta fito tana cizar lips. Jinta take sakayau kamar iska zata iya
daukarta. Ga bakinta daci sosai, Hatta tsamin da jikinta yay dazun yanzu duk ya
saki sal can da idan ta motsa take in ciwon kadan-kadan. Yanzu ko data shiga ruwan
zafi da sake gasa ikinta ma sai ta kara in dadi ko'ina ya mike mata. Ta dan ji
dadin rashin gain Mammy, dan kunyarta take ji
ALLAH dauriva kawai take vi. Da kanta ta dan daddogara ta shirya cikin kyakykyawar
abayar baka da tasha adon duwatsu sai walkiya take. Harda b8p a cikin kayan. Salla
ta fara gabatarwa a daddafe, tai achar tai la'asar da taga lokacinta vayi. Tana
sallar
Daneen Ammarah ta sake shigowa har sau biyu. Sai da ta idar ta lura da kyawawan
kwanikan dake ajiye.
Tana kan sellayar zahe Daneen Ammeran ta sake dawowa. Zama tai a kusa da ita tana
tambayarta yaya ilkin. A shanwabe ta amsa mata cewar da sauki.
Daneen Ammarah tai murmushi kawai batare data sake cewa komai ba. Sai ma abinci da
tai kokarin zuba mata da talmakonta kuma ta dan ci dan girki ne na musamman da ga
Mammah. Ta dadin vanda taga tari ganoshen naman da dan Rirk, ta bata magunguna
sannan tai zaman busar mata gashi da dazum balar ba. Tsaf ta gyana mata shi ta
daure sannan ta gyara mata fuska da kara saka mata was turarruka masu masifar
kamshi da bata san da su ba.
Ta kuma sakata yin tsugunno kan was turarrukan dai bavan wanda tai wanka da su a
bavi lokacin da zatayi.
Daneen Ammarah ta sauke duk wans neuvin da taken tai zaman ima Iffah nasiha da bata
shawarwarin da
Jaav taimaka mata a matsayin da take a yanzun mai banbanci da na baya. Sosai
nasihar ke shigarta vanda ya kamata, da da karshe ta sanya mata albarka tari-tari
sannan ta dore mata wayar Tajwar Eshaan da ta gani akan side drawer ta rike dan ta
debe mata kewa kalm ya dalo, ta Kuma icunna mate television dir dakin ma ta aive
mata remote kusa da ita da barpusm da Mammiali duk ta aiko mata elkin kavan abincin
lunch.
Ji Iffah tai kamar tai kuka, dan toro take ji a sake barinta da ga dasal shi a
vanza. lla kadar lasan abinda ta fuskanta a daren jiya a hannun bawan. ALLAHn nan.
Ita kanta Daneen Ammarah tausavin barin nata take. Amma yaya zatayi sai kawai ta
zabi
binta da addu'a dan bata so ya davo ya sake taddata
a sashen.. Ajiyar zucia ta dan sauke da hadiye
hawayen da suka ciko mata idanu, wani irin kewar
yan uwanta take ji fiye da ko yaushe a yau din nan.
Ganin zata saka kanta a damuwa tai musu addu'ar
samun rahamar UBANGIJI ta dauka remote di da
Mammy ta ajiye mata ta kunna tv. Searching channels ta faravi a hankali harta samu
inda wani film mai kvau
ya dauka hankalinta, sai dai film din akwai abun tsoro
a ciki. A kan lips cikin disashiyar muryarta ta furta,
"Bari muga kozan iva". Tana gara zamanta ta jingina da fuskar gadon tare da daukar
popcorn din ta tasa a
cinya tana kaiwa baki da daddaya....
Koda wasa bataji shigowarsa ba, dan hankalinta gaba daya ta maida shi ga kallon
film dinne, duk da
atsorace take kuma, wani gun ma har sai ta boye
fuska an dan wuce take iva cigaba da kallon.
Zamansa kusa da ita da saukar numfashinsa a gefen wuyanta ya sata yar zabura harda
shirin fasa kara.
Guntun murmushinsa din nan kamar na dole ya saki yana rikota. "Hy relax". Ya fada
cikin rada kamar mai tsoron aji su.
Idanunta ta rumtse da karfi ta sake budewa zuciyarta na wani irin gudu da sauri-
sauri dan ta toratan fa da gaske. Cikin tura baki ta juya idanunta da har yanzu
basu gama bajewa gaba daya ba tai masa yar hararar data nema tsarga masa zuciya. A
hankali ta ce, "ALLAH kaban tsoro ka nema afuwa na".
Yanzun ma murmushi ya sake yi, batare da yace komal ba ya gara zamansa yana daura
kansa a kafadarta idanunsa akan television da take kallo. Cikin rada-dara da kamo
hanunta da ke cikin popcorn din ya kai wanda ta dakko guda daya bakinsa yana fadin,
"Babu tayi ne?" ya kare maganar da kallonta. Da sauri ta kauda idanunta da ga
kallon da take masa ta maida ga tv cike da basarwa, a shagwabe ta ce, "Gashi kaci
ba'a baka ba. Ina vini".
Idanunsa va dan lumshe da budewa va tashi da kyau yana matsota jikinsa sosai kanta
da bayanta suka koma saman kirjinsa, yayinda take a tsakkiyar kafafunsa. Ita duk
jitai zaman ma ya bata kunya, amma ya ta iya dole ta dake dan Mamy ta mata nasiha
sosai akan ta saki tiki da milinta karta bada wata kofa da zai y dana sani kan
auranta ko tunanin mallakar wata mace saboda gazawarta. Kafarsa daya ya ajive a dan
dogare yanda ta sake samun jin dadin zaman. Kusan mintuna biyar bai sake cewa komai
ba itama bata sake ba idanunsu duk suna a tv. Yayinda yake kamo hanunta da take
dibo popcorn din yana kaiwa bakinsa. Cikin maganar nan tasa kamar ta dole ya ce,
"Kinci abinci?".
Kanta ta daga masa tsigar jikinta na tashi saboda yanda yay maganar cikin kunnenta.
Hannunsa na dama ya sakalo saman cikinta yana shinshinar wuyanta. "Ban yarda ba, mi
kika ci?".
Cikin yar in ina da son janye jikinta amma ya hana hakan ta ce, "Mammy ta bani
gasashen jan nama da madara"
"Uhm yar gatan Mammynta. Shine baki rage mun ba kuma? Gashi ina jin yunwa sosai
banci komai ba tun wanda kika tsammin".
Ita gaba daya jitake kamar an canja mata shi da wani ba Shahan-shan din nan miskili
mai shariva da magana ma sai ya jinjina ta ba kafin yayi, duk da a yanzun ma
daddaya yake yinta kamar abun dole.
Kasa cemasa komai tai, dan gaba daya ita yamasa ta daina fahimtar film din ma. Shi
kansa baima san mi yake ba, abinda kawai ya sani ta gama mamayesa da komansa.
Tsananin begenta yake da jin kishin sake kasancewa da ita. Amma zai daure bazai
aikata ba kodan tausayinta, ballema dinki da akai mala. Da. kyar ya dan dai-daita
kansa, itama cikin dan rawar murya ta ajiye popcorn din zata mike. Riketa yay kamar
mai tsoron ta gudar masa (g . A shagwabe tana narke fuska ta dubesa, sai kuma ta
risinar da idanun da take kyakykyaftawa, "Zan samo ma abincin ne fa". A hankali ya
saki hanun nata yana lunshe idanu da sake budewa a kanta gaba daya laurun idanuma
ya canja Yanda take tafiya kaman a hahharde kuma a hankali yabi da kallo,
tausayinta duk sai ya sake mamayesa.
Yaso ya dakatar da ita, amma sai maganar kuma ta masa wahala dan yunwar kuma yakeji
da gaske. Tan madarar da ya sha a wajenta da dan naman nan bai sake cin komai ba.
Koda ya shigo bayan sallar la'asar kuwa baiko kalla dining room din ba ya shilge.
Wanka kawai yay ya canja kayansa ya taho dubata tuna vasan a vanda ya barta sharban
da safen nan....

DAUDAR GORA....!!
Chapter: 49
Kyakykyawan bowl din data dauro saman
tray mai kyau shima da tambulan din madara
yabi da kallo. Ta ajiye a saman dan table din
data janyo kusa da gadon kasancewar a baki-
baki ya ke zaune shi ta daura. Bowl din ta bude
tana dan kallonsa kasa-kasa kamar yanda yake
binta da shegen kallon nan nasa. A saman lips
ta furta "Kana son shi?". Gasashen naman da ke
ta tashin kamshi mai tada kwadayi ya dan kalla.
Batare da yace komai ba ya kamo hanunta da ke
rike da murfin ya zaresa ya ajiye. Rikota yay ya
zaunar a kusa da shi. "Sai dai in zaki bani da
kanki. Hannuna ciwo suke min". Yanda yay
maganar acan kasan makoshi matuka ya sata
kallonsa da sauri, ido daya ya kashe mata da
sakar mata wani lalataccen murmushi daya
nema raba jikinta na numfashinta. Da sauri ta
maida kan ta risinar zuciyarta na wani masifar
harbawa da sauri-sauri.
Hannunta ya riko cikin nasa ya dan murza
yana kara narkar da idanunsa kan fuskarta
Cikin sake tausasa harshe da cigaba da murza
hannun ya ce, "A duk lokacin da kike tare da15:37
hannun ya ce, "A duk lokacin da kike tare da
<
an ki kallesa abokin ki, amininki, yaya
A
kal harma kaninki idan ya kama, sannan farin
cikin ki. Ina son gidana da iyalina su kasance
aljannar duniyata da duk inda naje na dawo da
damuwa za'a goge min shi da farin ciki, duk
sanda kaina ya dauka zafi za'a sanyaya min shi
da nishadi. Duk sanda na shigo da farin ciki za'a
tayani yi har ma a ninka min shi da wani da yafi
wanda nake tare da shi. Anan Eshaan sunansa
Eshaan Ion Haysam Abdul-majeed MIJIN
Fhareedah (Iffah) bint Zayyan ba Tajwar Eshaan
ko Shahan-shan ba. Ki raineni kamar jariri a
fadarki, Ni kuma mai sallamawa ne gareki duk
rintsi TAURARUWA TA".
Wata irin nutsuwa ce ke ratsa mata zuciya,
tabbas tana jin dadin kasancewa da shi, amma
har yanzu bata san mi takeji game da shi ba. Ita
dai kawai yana burgeta, a cikin ado ko sabanin
hakan. Sannan duk da taji ciwo da a jikinta da
jigatuwa a jiya batajin haushinsa ko jin bai
kyauta ba, dan koba komai tayi ilimin addini,
tasan hakkokin mace aka mijinta, tasan
hakkokin miji akan matarsa, tasan muhimmancin
aure da fa'idarsa. Ta kuma san Shahan-shan
bazai taba sakinta ba koda ace zata bukaci
haka. Mammy ta sake tisa mata fiye da abinda
ta sani, har ma da wanda zatayi domin tabbatar
da kanta a matsayin diya MACE a gabansa ko gaban wanin sa
"Wayyo!".
A
ada yana matse ciki, da sauri ta kalles
yamutse fuska kamar gaske shi adole yunwa
yake ji.
Cike da nuna damuwa ta ce, "Sorry". Sai
kuma ta dakko tray din saman cinyarta. Cokali ta
dauka zata diba naman ya rike hannun. Kallonsa
ta sakeyi da mamaki. Cikin dan dage gira ya ce,
"Nikam da hannu nake so". Komai batace ba ta
ajiye cokalin kawai, tare da ajiye trayn ta mike,
bai ta nufa bata wani jima ba ta dawo da alama
hannu ta wanko. Tray din ta sake maidawa
saman kafarta bayan ta koma inda ta tashi ta
zauna ta debo naman ta kai bakinsa. Hannun ya
riko da kyau ya karasa da naman bakinsa yana
lumshe idanunsa, harda sakin siririyar ajiyar
zuciya. Ita sai ma abin ya bata dariya harda
murmusawa.
Wani irin sanyi da nutsuwa yaji har cikin ranta
ganin tayi murmushin. Dan gaba daya yau bakin
ya mutu kamar ba ita ba, shi kuma yafi son yaga
ta saki jiki da shi tana kiriniyarta da surutu
kamar da. Sosai yaci naman har hakan ya bata
mamaki, hakama madaran. A hankali ta rumtse
idanunta sanda yake tsotse yatsun hannun abin
kamar da gayya. Da gayyar kuwa yake yi, dan
yana kallon yanda take faman matse ido yana murmushi a zuciyarsa
Bai bar dakin ba sai da ana kiran sallar magariba
<
. Yace ta shirya kafin ya dawo zata
rakasa wani waje. Da to ta amsa masa kanta a
kasa, dan duk wannan abun da ake bata yarda
su hada ido sai da kuskure. Bayan fitowarsa
alwala a bathroom har ya wuceta ya dawo da
baya, kama ta yay ya mikar tsaye da ga zaunen
da take. Fuskarta ya dago dan taki yarda ta
kallesa, shima bai matsa da sai ta kallesan ba ya
manna ma goshinta sumba mai lafiyar da har sai
da ta sanya jikinta motsawa. Idanunta a rufe har
sai da ya fice sannan ta bude tana sauke
nannauyar ajiyar zuciya, ita har yanzu ta kasa
sabawa da salon nasa sam.
Sai da ta dan kara gasa kanta kamar yanda
Mammy tace ta dinga yi akai-akai sannan tayo
alwala ta fito gabatar da sallar magriba. Bayan
ta idar zama tai tunani mai zurfi akan Tajwar
Eshaan, mutum nan nada abubuwan ban
mamaki boyayyu, tabbas ta yarda hatsabibin
kansa ne kamar yanda su Miran Arshaan ke
fada. Gaskiya tana bukatar sanin yanda akai su
Baby suka kasance a wata kasa bayan su Miran
Jasim sun mata karyar ya kashesu. Kenan video
din data gani jabu ne ko mi?. Rashin amsa da
bukatar samunta ya sata mikewa ta gabatar da
sallar isha'i da ake kira. Bayan ta idar ta shiga
gyara jikinta dan haka kawai take dokin fitar duk
da bata san ina suka nufa ba. Tsaf take cikin bakar doguwar rigar abayar datai mata
kyau,sai Ver din nan da in aka nada yake yi kamar baoy
hijab fari. Fitowa tai tsabar zumudin son fitar ta
su. Dakin da suka kwana ta nufa duk da bata
zaton ya isa dawowa salla.
Kusan a tare suka aura hannayensu kan
handle din kofar, ita ta tura shi kuma ya ja batare
da kowanne yasan da dan uwansa ba. Cak ta
tsaya kanta a kasa tana mai rumtse idanunta
dan wata irin kunyarsa takeji har cikin kashinta.
Ga kwarjini mai irin mamaye waje din nan da ya
kara mata. Kusan minti daya suka kwashe a
wajen ita bata tanka ba shima bai ce ba. Tasan
in zasu kwana ma zai iya, dan haka ta dan saci
kallonsa ta gefen ido. A hankali ta janye idanun
nata gain yanda ya kafeta da shegen kallon
nan nasa mai hanata sukuni. Sai ta samu kanta
da in inar fadin, "Barka da dawowa". Karamar
ajiyar zuciyar da bata ji ba ya yayi a ciki, batare
da ya amsa gaisuwar tata ba ya karasa fitowa,
fuskar babu fara'a sam kamar ko yau she, sai
wani irin kwarjini mai cika idon mai kallo, a fisge
ya furta, "Muje" yana rabata ya wuce cike da
takun nan nasa daddaya. A hankali ta dan sauke
numfashi dan jinta take kamar an daureta a
wajen, sai kuma ta bisa da kallo kasa-kasa tana
mai tsarkake sunan UBANGIJI mahaliccin
wannan kyakykyawar halitta. (Kyau dai kam ALLAH ya bashi, sai dai miskilancin nan
da jin
nan da ke zagaye da shi) ta dan nal
fuska kamar zatai magana, sai kuma ta fasa
ranta fal tunanin ina ma zasu je a daren nan?
rashin mai bata amsa ya sata dan zabura tabi
bayansan. Ganin ya nufi lift.. taji duk ta tsure. Ita
dai harga ALLAH abin nan baya wani birgeta.
Dan indai ta shiga sai tayi hajijiya. Shiyyasa ya
zamto sai ta rike wani dan batama taba gigin
shiga ita kadai ba. Jiki a sabule ta shiga, jin
kofar ta rufe kanta ta rumtse idanu da sauri, sai
kuma ta bude akan yatsansa da ke kokarin
danna inda yake bukatar suje. "ALLAH ina jin
toro" ta fada kamar zatai kuka. Sarai ya jita,
amma sai bai nuna yaji ba ya gyara tsaiwarsa
bayan ya danna 2 floor. Iffah da ke jin kamar ta
fasa kuka a hankali tai yunkurin zamewa dan
gara ta zauna zai fi mata sauki. Babu zato taji an
riko mata hannu, kafin ta iya ko bude idanunta
tajita cikin jikinsa da ke fidda wani irin
sirrintaccen kamshi mai ratsa zuciya da bargo
da bazata taba iya mantawa ba. Da sauri ta
bude idanunta sai ko cikin nasa da ke kallonta,
dole ta maida nata ta rufe da sauri zuciyarta na
wani irin bugawa da sauri-sauri, tabbas bazata
mance wannan turaren ba, dan turarene da ta
dinga fafitikar nema a washe grin da aka
dakkota da ga sashenta cikin dare aka maidata
nashi. Kenan da gaske shi dinne ya je ya
dakkota kokuwa yaya akai? Dan wannan Kamshin dai shine. Tsaf ya fahimci inda ta
nura,
kuma a randa ta dinga neman turaren ya sani
sarai, abinda bata sani ba ya ajiye abinsa ne
kawai inda bataima zaton ganinsa ba o kawowa
a ranta zai ajiye din.
"Zamu kwana anan ne?". Ya fada a kasan
makoshi yana kallon kyakykyawar fuskarta da
ke kwance a kan kirjinsa. Idanun ta bude, sai
kuma taja jikinta baya kunya na wani mamayeta.
Dauke idanunsa yay da ga kallonta ya fice,
itama sai ta bisa tana sauke ajiyar zuciya a
jajere, sai kuma ta saki murmushi dan ita da
kanta kunyar kanta taji. Wata hanyar da batama
san da ita a wajen ba suka nufa, koda yake
bawai ta taba shiga wani waje a floor 2 din nan
bane bayan falo, shima a randa Malikat
Haseenat ce ta kawota da suka biyo komai daki-
daki ba kamar yanda yay ba yanzu
Inda suka shigo dinne ya sakata tsayawa
turus tana kallonsa. Sai kuma ta dan waiga ta
kalli hanyar da suka fito, ita fa gaba daya notikan
kanta sun kwace, ta ma rasa ta yanda zata
misalta ta inda wannan hanyar take a zahirin
cikin gidan, dan ita shaidace tsakanin sashensa
da na Malikat Bushirat akwai nisa. Duk da sunyi
yar tafiya suma amma sai gasu cikin sauki.
Kallonsa tai fuska a marairaice kamar ba Iffah'r
nan matsiwaciya ba da ya sani ta ce, "ALLAH toro nake ji". Kallonta yake da
shanyayyun
idanun nan nasa masu kaifi kamar bazaice
komai ba, sai kuma jitai a hankali kamar mai
rada ya furta, "Nima tsoron nake ji ai". Idanu ta
dan waro alamar mamaki tace, "Kai din?". Kansa
ya dan kada mata da lumshe idanunsa ya bude
duk a lokaci daya. Sai kuma ya kai hannunsa kan
nata ya matsota jikinsa. "Ki karamin karfi". Ya
fada yana rungumeta cikin jikin nasa.
Daburcewa tai ma ita gaba daya. Tai kokarin
dagowa ya hana hakan. Dole ta hakura tai luff
tana mai shakar kamshin da jikinsa ke fitarwa
mai azabar dadi. Kusan minti biyu suka kwashe
a wajen kafin ya dagota a hankali, kin yarda tai
su hada ido sam, shima sai bai matsa ba ya ja
hanunta kawai yana dan murmushin da iyakarsa
makoshi suka shige.

15:39
DAUDAR GORA...II
Chapter: 50

Zaune take kan gado tun bayan idar da sallar magrib da Jasrah ta taimaka mata tayi
kafin ta wuce. Idanunta tsaye suke kyam a waje
guda alamar tayi matukar zurfi a tunani, dan sam hankalinta ma baya a cikin duniyar
mutane,
ya tafi ga yanda zata shawo kan uwa ne kwai da kuma gusar da Iffah datai kane-kane
a cikin
rayuwar danta, dan tasan abinda uwa ta fada babu fashi bazasu taba canja sharadinsu
ba inhar bata karasa cika alkawransu ba. Ita mai bada labari ce akan bijirewar da
surikinsu
(Tajwar Abdul-majeed) yay da abinda ya biyo bayan hakan, dan har yanzu hukuncin uwa
na biye da su daki-daki wanda shine ma
makasudin komai akan kanta yanzu haka da tushen faruwar komai akanta. Tun dazun
gaba
daya hankalinta a tashe yake. Tana ta kokarin kiranyen uwa amma babu alamar zata
ziyarceta,wannan shine mafi zama kololuwar tashin
hankalinta a yanzu. Motsi da kamshinsa ya sata dago manyan idanunta farare tas da a
yanzu
launinsu gaba daya ya koma jazur har baka iya gane bakin ma da kyau. Duk da fushin
da take
da shi bai hanata jin sanyi da ganinsa ba a cikin ranta, dan da gaske shine abu
mafi kololuwar
soyuwa a gareta a kaf abinda take ganin ta mallaka a diniva KAfesa tai dA kallo
rike da so da kauna, sai dai tana kokarin dannewa a zahirance. Wani irin harbawa
zuciyar Iffah da girarta ta dama sukayi a lokaci guda, tai saurin ja ta tsaya da
kokarin son janye hannunta da ke a cikin nasa. Amma sai yaki sakinta har sai da
suka isa gaban Malikat Bushirat da sai yanzu ta lura da Iffah da ke faman boyewa a
bayansa
Hannunta ya jawo a hankali ta dawo gabansa idanunsa akan Malikat din dake wani irin
kallonsa. Sassanyan murmushi ya saki kadan dai-dai yana sakin hanun Iffah'r da
kaiwa duke
ya kamo na Malikat Bushirat ya saka na Iffah ciki sannan ya ja da baya zuwa bakin
gado ya zauna
abinsa tamkar baiga kallon da Ammien tasa ke masa ba. A wani zafi Malikat Bushirat
ta yarfar
da hannun Iffah'r tana watsa mata mummunan kallo. Iffah da kanta ke wani irin
yamutsawa tun
shigar hanunta cikin na Malikat Bushirat din ta bude idanunta da suka kada jajur.
Amma sai taki
kallon kowa a cikinsu tama risinar da kanta da fadin "Ammie ina yini?".

"Mi wannan tazo yimun nan?".


Ta fada ranta a matukar bace tana maida kallonta ga Tajwar Eshaan maimakon amsa war
da Iffah tai mata. Shiru kamar ba Adi ba, ran Malikat Bushirat ya kara sos matuka,
duk da sanin halinsa ne dama hakan. Sai da ya mula dan kansa sannan ya dubeta yana
dan guntun murmushin daya sake harzuka Ammien tasa. A hankali ya motsa lips dinsa
yana lumshe idanu da budewa. "Ammie! Munzo mu baki hakuri ne, ta kuma dubaki.

"Hakuri? To nace mata ina bukatarsa ne.Saiful-malik ka fita idanafa ko. Ka


fita idona karka bari akan yarinyar nan mu samu matsala da kai. Ita bata kai
matsayin da zata zama kO abin kallona ma balle har a saurari wani abu daga bakinta.
K! Tashi ki fitar min anan, karna sake ganinki a cikin idanuna, inba hakaba sai
kinyi nadamar sake maimaita wanna kuskuren.

"Ammie.

Da sauri ta daga masa hannu, "Na fada maka bana bukatar jin komai daga gareka, kuma
ina
akan bakana na sai ka saketa. Inba haka ba Eshaan zan baka mamaki da ga nan zuwa
safiyar gobe in har baka janye garkuwar daga bama yarinyar nan ba tare da takardar
saki
uku.

Wani irin lallausan murmushi Iffah ta sakikamar ba'a kanta ake dambarwar ba. Ta
dago a hankali ta dubi Malikat Bushirat, sai kuma ta maida kan Tajwar Eshaan. Hada
ido sukai, ta sakar masa wani murmushin da yafi Nafarko neman wargaza masa lissafi.
"Mutuwa da rayuwa gaskiya ne *_Sultan_*, kamar yanda kaddara da jarabawa suke
abokan rayuwar kowane dan adam. Ammie tayi gaskiya, ban cancanci GARKUWA da ga
gareka ba, sannan kuma igiyar aurenka bata dace da cigaba da zama kan mace irina
ba. Nima a yau na fahimci komai, na gano komai, babu abinda ya rage kuma, tabbas
babu. Ka bani dama zan bata hakuri da kaina, zan kuma fahimtar da ita yanda zata
fahimci komai dan nasan yanzun ma bayin kanta bane masu zuga ne.Kallonta kawai yake
a narke da jin kaunarta na kara ratsashi. Wayonta yana rinjayar duk wani karfin
ikonsa a zahirance. Ya fahimci tana son ya basu wajene. Sai ko ya mike a hankali
yana kai waya kunnensa kamar wanda ke shirin
kiran wani.

Wani irin shegen murmushi Iffah ta sake saki idanunta akan Malikat
Bushirat da ke jin kamar ta hadiyi zuciya ta mutu. Itace wanna yarinyar zata nunama
danta da ke matsayin Shahan-shan tacika mace a garesa. Iffah dake danne dariya ta
wani kashe mata ido daya da kada mata yatsun hannunta biyu akan fuska. "Hy my
Mather in-law ya da suman zaune haka tun ba'a fara wasan ba. Kin damu kanki da
saki-saki kinmanta danki sarki ne, bai isa sakin n Ahaka kawai bai sai da hujja mai
karfi? Oh!! Kina son a sakeni saboda na zame miki kadangaren bakin tulu ko? Ayya!!
Ayya!! Mather in-law kinyi sakaci ai, kinyi sakaci tunda har kika bari Fhareedah
bint Zayyan ta kasance daya da ga cikin Zawjata-almilk. Kinyi sakaci tunda har
danki ya zama a tsakkiyar tafin hannuna. Kinyi sakaci tunda har kika yarda hanunki
ya taba jikina a karo na farko yau ma karo na biyu kika sake. My Hamäh idon Iffah
bude yake tun a randa ta shigo wannan masarautar, sannan biye nake da takun kowa
hatta ke kanki. Dan haka nice zan baki mamaki kafin safiyar goben da kika shardanta
masa idan baki bi a hankali ba ba kece zaki bada mamakin ba. Bara na bude miki
zancen a bayyane, naba danki gubar dafin macizai a cikin madara badan ya mutu ba,
sai dan na kusanta da shi. Dan wannan hanyar ce kawai zata bani damar zama a
sashensa din-din, saboda na tabbatar duk wadda ta kasance tana aikata ko yana
aikata barnar da kisan matansa da ma duk wani mugu mai boayyen nufi a kansa bazai
barni ba zai yi yunkurin ganin ya kashe ni tun a cikin kurkukun, shiko bazai bari
ba zai bani kariya dan dole-dole yana son sanin dawa mukai aikin ai. Kinji na farko
kenan"ta kare maganar da dage mata gira. Sai kuma ta juya idanunta masu rikita
lissafin Malikat Bushirat da har yanzu basu gama sabewa ba

"'Na biyu tun a randa aka kawoni gidan nan wika zama suspect dina na farko.
Dan nagano matsanancin tashin hankali a cikin idanunki
lokacin da naki shan madarar da kika saka a bani. Kinji na biyu in-law. Na uku
randa nake kwance asibiti dalilin rigar da aka sanya mun akwai kallon da kikai mun
da ya saka na ajiyeshi a kyakykyawar ma'adana. Na hudu randa kuka zaunar dani akan
kunaso na koa sashen Eshaan da zama danna gano muku wai shike
kashe matansa ko wanine. kai jama'a" ta fada tana kyalkyalewa da siririyar dariya.
"Wihy
kinada basira in-law. Kin iya makirci da in har mutum bai san ainhinki ba sai ki
gama halakashi
bai sani ba. A ranar na fahimci abubuwa da yawa a cikin kalamanki, kawai kina boye
kanki
ne cikin rudanin bayin ALLAH. Uhhm kin dan birgeni fa. Randa Eshaan yasha gubar
dana
bashi shirunki ba yana nufin baki da abin fada bane, ni nasan kinfi kowa zama a
kololuwar
bala'i dan naga haka a cikin idanunki. Randa kika bashi umarnin ya sakeni na gano
abinda ke bakiyi tunanin zan gano ba a cikin kwayoyin
idanunki da taba jikina da hanunki yayi. Hhhhhh Iffahr nan da kike gani batta a
inda kika ganta batta, tafi karfin zama yar wasan kura, ni din hazabibiya ce fiye
da yanda kike tunani
Mamana. A yau kuwa shigar hanuna cikin naki ya sake tabbatar min da ke ce, ke ce
Malikat Bushirat da ke hallaka matan danki da kika haifa da cikinki. Mi kike bukata
ne? Minene a rankine? Minene burinki ne? Mi kike son zama ne?Bayan duka ALLAH ya
baki?. Ki fada min, nikuma na miki alkawarin taimakonki bazan kuma tona asirinki ba
ko dan daraja da mutunci dakimar danki, dan bazan bar ZUCIYAR MIJINA ta buga ba a
dalilin son zuciyarki. K uwa ce garesa,kuma ina kallonki da wannan kimar ne har
yanzu saboda mutuncinsa Ammie. Sai dai bazan iya yafe miki jinin yan uwana guda
biyu ba. Kar kiyi sakaci da wannan damar, in ba haka ba ki sani da ga yau wannan
lokacin na yaki ne, tabbas na
yakine.

Tabbas Malikat Bushirat a sume take, sumar da kunne na ji ido na gani amma
gangar jiki bata motsawa. Suma irin na mamaki da tsantsar tashin hankali. Dan babu
abinda ake iya gani sai wutar masifar da ke ci a tsakkiyar idanunta dake kallon
Iffah. Iffah da tuni ta fahimci haka murmushi ta sakar mata da buga hanunta na dama
dake dunkule a tsakkiyar na haggu taialamar yanka wuya a saitin wuyanta tana kashe
ido da cije lips.

Wani irin mikewar zabura tayi kamar wadda aka dawoma da dukkan karfinta dai-
dai da dawowar Tajwar Eshaan akin. Fashewa Iffah tai da kuka da durkushewa gaban
Malikat Bushirat da ta mike tsaye a zafafe. Ta riko duka kafafunta tana kukan da
fadin, "Ammie nasan zaki fadukkan bayani na, kuma zakimun adalci a cikin dukkan
abinda ya farun nan. Nima ba laifina bane tirsasani sukayi da mun barazanar karar
da ahalina dama ku musamman ke da kike mahaifiya ga adalin shugabanmu. Ni kuma a
shirmena idan na bashin za'ai saurin kaisa ga likita kafin ma dafin macizan yay
tasiri. Ki yafe min Ammie nayi kuskure da wauta ki yafe min…

Gaba daya Malikat Bushirat sai ta sake mutuwar tsaye. Eh lallai yau taga
masifa, anya yarinyar nan mutum ce kuwa? Shikam mai gayya da aikin yay wata irin
tsaiwar da ko bai fito fili yace komai ba Malikat Bushirat da kanta ta hango abinda
ta hango a cikin idanunsa da ke tsaye kyam akan Iffah da ke a gurfane
gabanta.Tabbas idan tai wani abu a yanzu akwai matsala,zakuma tayi kuskuren da yafi
na yarda da shigowar yarinyar nan masarautar nan. Hadiye abinda yay mata tsaye a
makoshi tai da kyar, ta rankwafa ta kamo kafadun Iffah ta mikar da ita tsaye. (Ya
ALLAH hawaye fa share-share a fuskar Iffah kamar gasket). Bata da zabin daya wuce
rungumeta itama tana matsar kwallan karya ta shiga fadin. "Ban san haka bane Ibnati
miyasa kika ki fahimtar da ni da ban miki irin wannan mummunan zaton ba ai. Kiyi
hakuri ki gafarceni"……….✍️

_Wannan yarinya ta zama abin toro gaskiya


😂. Ahe haka take 🥱

🥱Ni wannan ya ta Babiy kodai sunada sarauta ne a kauyen Jumna bamu da labari.
Wannan hayen izza na dauran kai gaskiya 😂

15:43
DAUDAR GORA…
Chapter: 51

Sake kankameta Iffah tai, cikin diddishe dan ta fita tsayi ta kai bakinta
saitin kunenta tana
wani kuka kuka. "Hhhhh da dina dake akwai daukar haske Mather in-law. Why ki
sallamemu
mu tafi naje mijina ya rungumeni dan ban gama dawowa hayyacina da ga faffarkanin da
yay ba".
A zahiri kam raba jikinta tai dana Malikat din tana share hawaye da jera godiya.
Sai kuma ta
kashe mata ido dan ta fahimci yanzu ma fa ta sake kamewa ne ta juya ta kalli Tajwar
Eshaan
da ke kallonsu da alamar nuna jin dadin canjawar komai akan fuskarsa. "Ka tayani
godiya *_My Asad_* (Zakina), Ammie ta
fahimceni, na sanar mata komai kamar yanda na fada maka".

A hankali ya wani lumshe idanu da takowa gabansu. Gaban Malikat


Bushirat ya tsaya tare
da kamo hannayenta cikin nasa. Firgigit ta dawo hankalinta kamar wadda aka kodama
mari a
cikin barci. Cikin kamewar nan tasa dake boye dukkan sirrikan fuskarsa yake dubanta
a nutse.
"Ammie nagode sosai, Nagode da kika fahimci abinda naketa son ki fahimta tun
tuni.Fhareedah yarinyar kirki ce mai cike da tarin alkairai daban-daban, kuma nasan
zaki sake
tabbatar da hakan anan gaba. Na miki alkawarin aiki tare da ita har sai duk wani
markiyinmu ya bayyana batare da shi kansa ye sani ba. Ki cigaba da mun addu'a ke
dai,gaskiyar danki na gab da fitowa zahiri ga kowa.Dan yanzu haka dukkan wasu
bincike akan cases din nan suna'a hannuna, hatta wanda yay tushen bada madaran, da
wanda ya sakata a ruwa duk sunzo hanun hukuma. Kallonsa tai da wani irin sauri, sai
kuma ta hadiye tana mai kankame hanunnsa a cikin nata. Idanunta ta lumshe hawaye
sukai wani irin zubowa. "Ashe zanga wannan ranar, wanna ranar zatazo gareni haka
Saiful-malik?". Ta fada cikin subutar baki.

Ko kadan Tajwar Eshaan bai fahimci kalaman nata ba, ya fassarasu ne


akan nuna farin cikinta na zataga wannan raar da za'ai walkiya halin wanda batai
zato ba ya fito. Sai kawai ya saki murmushi da kai hannu yana share mata hawaye.
"Zaki gani Ammie. Ai dama komai yay farko zakiga karshensa na zuwa. Ki cigaba da
mun addu'a ke dai indai nasarorin ne yanzu kika
fara gani. Sai kin zama mafi kololiwar uwa da zatai alfahari da haihuwar da daya
tilo tamkar da
dubu insha ALLAHU"

"Na yarda da hakan Bin Haysam Abdul-majeed, tabbas na yarda, ALLAH ya


makaalbarka kuje dare nayi ku huta ma karasa dasafe".

15:44
Godiya a sake mata da dan lallashi, hakama harda durkusawarta. Kafin ta wani
kananna de ma Malikat Bushirat ido a kaikaice ta sakar mata gwalo. Tajwar Eshaan na
juyiwa ta fuske kalar tausayi. Hannunta ya kama a hankali yana mai kallon fuskarta
ya sakar mata murmushin nan nasa mai narke zuciyarta. Murtani ta maida masa da dan
saka hannu ta kare fuskarta ita a dole taji kunya ne. Duk Malikat Bushirat na
kallonsu. Suna ficewa ta zube kasa yarafff wani irin mahaukacin jiri na dibar
idanunta. Sai kawai ta fashe da kuka tana kiran sunan Uwa.

Tantabaru biyu iyayen soyayya da alkawarin kam suna fita ya duke kasa ya
bata bayansa alamar ta hau. Idanu ta waro masa waje alamar mamaki. Ya dan juyo yana
kada mata kai da lumshe idanu. Babu yanda ta iya ta tattare rigarta kadan ta hau
tare da makalkale masa wuya dan sam bata iya gardama ba. Takun nan nasa yake a
hankali cikin izza da kasaita har zuwa sashensa tana a bayansa kwance luff
mamakinsa na neman kasheta, duk wanda yasanshi a Shahan-shan din sa bazai taba
mafarkin abinda yake mata yanzu zai iya ba.Koda suka shiga elevator ma bai sauketa
ba sai boye fuskarta da tai a wuyansa. Aiko gaba daya numfashin da take busa masa
ya nema birkita masa lissafi.Maimakon ajiyeta a daki da ya shiga sai kawai ya wuce
da ita bathroom ya direta ta bude idanunta. Da sauri ta kallesa a dan rude gain
inda ya kawosu. Sai kawai yay wani luuu da idanunsa cike da basarwa ya danne
makunnan shower ya sakar musu ruwa a kansu mai dumi. Babu shiri ta zabura ya rikota
a hankali, jikinsa ya matsota ya rungume ruwan na cigaba da sauka a kansu.

Kusan mintuna uku suna a hakan kafin ya bude idanunsa ya sauke a kanta yana
mai kai hannunsa saman veil din ta ya shiga warwarewa a hankali. Tanaji tana gani
ya raba jikinta da kayan da suka gama jikewa sharkaf shi ma ya cire nashi. Jikinsa
ta fada kawai nata na rawa ga wata matsananciyar kunyarsa na ratsata. Sosai hakan
da tai yay masa dadi, dan ya samu damar sake gain tawadan ALLAH din nan ta bayanta
yanda ya kamata, yanda har sai da ya haddace ta. Ita kam har aka kammala wankan
bata yarda ta bude idanunta da ta rufeba..

"Nagode"

Ya fada a hankali lokacin da yake goge mata laimar ruwan fuskarta da towel zuwa
wuya da bayan keyarta. Dan dago idanunta tai ta dubesa, itama a hankalin ta ce,
"Akan mi?".

“Ammie"

Ya bata amsa a takaice. Baki ta dan tura masa tana narke fuska, a dan shagwabe ta
ce,
"Saboda Ammien ka ce kai daya?".

Murmushi ya dan yi da lakace mata hanci. "K ta musamman ce".

Baya ta juya masa tana murmushi, hannunta ya kamo ya sake juyo da ita. Ya dago
fuskarta da kyau ta hanyar dago da habarta. "Baki yarda ke ta musamman ba ce?"

Tana dan danne murmushin ta ta ce, "Ka dan dai", Yanda ta fada da yin kamar
zata dan kashe ido daya sai kuma ta jujyasu wani luuuu hakan nan zuwa gefe ya sashi
jin jikinsa duk ya saki,amma sai ya kanne yayi dan murmushi kawai da sake
rankwafawa suka zama dai-dai tsaho. "Zan tabbatar miki k ta musamman ce Mrs
Eshaan.Dan bazaki sake rayuwa babu Eshaan a gefenki ba har abada insha ALLAHU"

Cikin dan waro idanunta kadan ta ce, "Har a kurkuku idan na koma".

"'Koda a tandun mai ne Babie. Hukunci na gama yankuwa zamu tafi can abunmu
muyi zamanmu har sai kin haihu".

Takwaf-takwaf tayi da fuska kamar zata sakar masa kuka. "Wai da gaske kake sai
ka maidani kurkukun?".

*kyar ya iya danne dariyarsa, a zahiri ya dan Kara tsuke fuska da daga mata gira.
"Way,miki ko Mrs Eshaan zata tsira da ga hukuncin Shahan-shan ne. Ai sai munje
kurkuku dole, irin wanna laifi haka da muka rakitowa kammu".

Baki ta bude a hankali zata sake magana ya manne lips dinsu waje guda,
dole ta hadiye. Duk da a tsorace take da shi batai yunkurin hanashi ba, sai dai
kuma bata bashi kowane irin gudunmawa ba har yay kidansa yay rawarsa ya barta. Da
ga haka bakin ya mutu suka hau shirin barci, dama da biyu yay hakan dan ya gaji da
maganar. Ya fara kula yarinyar nan so take tamaidashi parrot na karfi da yaji su
Jaddah su sami abin masa gori. Wasu shegun kayan barci da bata san ina ya samo su
ba ya dakko zai sakamata. Tako zaro ido zatai magana dan bakin faya fara dawowa
(lols 😂)). Yatsansa ya daura saman bakinta ya ce, "Shill!!!". Dole ta hadiye abin
cewar tanaji tana gani ya saka mata su. Ina kasa Iffah ta shige ta buya kota huta
da kunyar da bawan ALLAHn nan ke dawainiyar jefata ciki itakam. Shiko gogan naku
ko'a jikinsa. Sai ma nasa shirin da yay cikin pyjamas dinsa shima marasa nauyi ya
jata suka fito. Zaunar da ita yaya daya daga kujerun dakin shima ya zauna kusa da
ita. Idanunsa da basu ko kyaftawa a kanta ya motsa a kasalance. "Zaki sha madara?".
Bawani tana jin yunwa bane, dan haka ta daga masa kai batare da ta yarda ta kallesa
ba ita. Dan harga AllaH tsoron ma kallon jikin nan nasa take a tsaye, ga shi ya sa
kaya marasa nauyi da gaba daya suka bayyana ainahinsa. Shi da kansa ya zuba madarar
ya bata, ta amsa tana fadin, "Nagode". Shi dai nasa kawai kallonta. Yanda take shan
tata a takure harya kammala ita bata gama ba, dan haka suka dan jima wajen a zaune
har ta fara hammar barci.

Koda suka kammala brush suka sake yowa ya ce mata ta kwanta dan ya fahimci
barci takeji sosai. A darare ta kwanta har fuskarta na bayyana tsoronsa. Yi yay
kamar bai lura da ita ba, yama koma cikin sofar da ya tashi ya zauna.Itako luff tai
zuciyarta cike da toro da kuma mamakin abubuwan da tai yau a sashen Malikat
Bushirat. Ta jima da sanin akwai wasu lokuta da take ganin abu baro-baro a zahiri
bayan ta gansa a mafarkinta, amma fa yau ita kam kawai jitai tana zano zantuka ga
Malikat Bushirat din wanda itafa kamar ana nuna mata su ne cikin idanunta a
lokacin, sannan tana jin wani karfin iko da izzar fadar tasu babu o dar tattare da
ita. Ta dafe kanta da ke dan mata ciwo kasa-kasa, ga wani barci da ke rinjayar
idanunta mai nauyi. Dole ta tattara tunanin da tsoron ta hakura tai addu'a sai ko
barci.

Shima da ke zaman kallonta duk dahankalinsa nakan waya ne a zahiri sai ya


shirya tattarawa ya bar dakin, dan ya tabbata idan fingilar rigar barcinta ya
dagata sama kadan cikin sa'a ya iya ganin abinda yake son ga Hoton wajen ya dauka
da waya ya maida mara rigar a yanda take ya mike yana sauke ajiyar zuciya. Dan ya
tabbata ido biyu bazata yarda yay hakan ba cikin sauki, maybe ma tafassarashi da
wani abu daban...

Maimakon shiga wani dakin barcin ya kwanta karamin falonsa na hutawa dake
rukunin dakun barcin ya shiga, agogo ya kalla, ganin sha biyu ta dan gota kadan ya
dauke kai. Wayar dake gefensa ta landline ya dan daddana, batare daya dauka yakai
kunne ba harta shiga ta yanke.Cikin abinda baifi mintuna biyar ba sai ga
amintaccensa da butar shayi. A saman lips ya amsa sallamarsa batare daya dago ko
motsa daga abinda yake ba. Koda ya gaisheshi ma bai ko amsa ba, ya dai daga masa
hannu kawai, shiko bai damuba ya ajiye komai yanda ya dace ya zuba masa a karamin
cup yasa yar zuma kadan dan yasan baima cika shan wannan shayin da komai a ciki ba.
Bayan ya kammala cikin girmamawa kansa a risine ya ce, "Ko akwai abinda shugabana
ke bukata?". Yaja kusan minti daya da rabi sannan ya daga masa hannu. Duk wani
yaren jiki da Tajwar Eshaan zai yi magana da shi hadimin nan ya haddacesa, dan haka
cikin risinar da kai ya furta, "A huta lafiya, ALLAH ya kareka da kariyarsa". Daga
haka ya fice...

DAUDAR GORA

Book two ( 52)

Duk da barcin dake cikin idanunsa tattaresa yay ya ajiye gefe guda ya tattara dukan
hankalinsa kan littattafan da Malikat Haseenat tabashi. Inda zuciyarsa ke zallon
zuwa kawai ya nufa bayan ya dan karanta tarihin mafarin komai. Babu bambanci da
wanda Mammah ta bashi, dan haka ya ajiye gefe da burin sai ya nutsu zaiyi komai
daki-daki. Bai san adadin shekarunta ba, amma sai ya kiyasta da adadin shekarun da
yake kallonta da su. Yaci karo da kusan hudu da yay dai-dai da hasashensa, a ciki
uku na mata daya na namiji, gefe ya maida na namijin, ya dauka wayarsa yana kallon
natan da na sauran matan uku kozai dace da wanda zasuyi dai-dai. Wani irin masifar
harbawa zuciyarsa tayi gain tambari na karshe bashi da banbanci da natan. Bayanin
dake kasan tambarin na tabbatar da dashi aka haifeta, a duk ma wanda aka haifa a
tsakanin lokacin ita kadaice wadda aka haifa da shi sauran duk yimusu shi akayi. An
haifi mai tamarin a daren ranar juma'a 22 a shekarar 2003 uku ga wata.Sai dai ita
kuma ta rasu ne bayan haihuwarta da kwana uku. Wani irin kai hannu yay saman kansa
ya yamutsa sumarsa yana ambaton sunan ALLAH. Ya akai haka? Ta yaya ma? Idan har ya
tabbata ita din ce ya akai take raye bayan ance kuma ta mutu? Idan kuma wadan can
dinne Iyayenta tayaya suka bar masarautar ma?bata mutum ba suka boyeta sukace ta
muturn? Kai ina akwai dai abinda ya kamata ya sani, farkoma shekarunta ita. Sannan
sanin asalin iyayenta.Lokaci yayi da zaisa a maidosu kasar ruman.

**

Kanta sara mata yake da cio mai azaba. Ga wani irin ja da idanunta sukai. Kofar da
suka fita kawai ta tsurama ido tamkar suna a wajen har kusan awanni uku bayan
fitarsu. Sosai take jin kuna mai radadi a zuciyarta. Har yanzu ta kasa yarda a ido
biyu take, ta kasa yarda a zahiri komai ke faruwa, ta kasa yarda ita ta-kurya wata
ta tsaya a gabanta tai mata wannan in kashir.Ta kasa yarda ita ta kurya yau wani ke
tabbatar mata yasan itace silar mutuwar matan danta. Ta kasa yarda, ta kasa yarda
da komai.

"Ta-kurya!!".

Muryar UWA ta shiga cikin kunnenta a bazata.Firgigit ta kai dubanta ga inda


taji sautin kuryar.Ita dince kuwa, zaune cikin kujerar nan tata.Yanda fuskarta ke
tsuke hancinta na fidda hucin bacin rai sai ta kara muni ga mai kallo. Idanunta
jajurta kara budewa akan Malikat Bushirat itama kallonta kawai take babu alamar
jikinta na aiki bayan fitar numfashi.

"Kin bani kunya ta-kurya. Kin bani kunya da har kika kasance a haka kan
wata karamar barazana da ga yar cikinki. Ashe bazaki iya yakin ba kika amsa
takardar gayyata? Dama duk baki shirya zuwan irin wadan nan ranakun
ba…

"Uwa ya kike so nayi? Ya kike so na kasance?.Ni fa yarinyar nan ta kalla


cikin idona ta fadamin abinda bayan ni da ke babu wanda ya sani a kaf duniya. Ni
yarinyar nan ta shiryama makirci a gaban dana dana zama sanadin zuwansa duniya,
wanda dukkan gwagwarmayata akansa ne da tabbatar da wanzuwarsa a matsayin da yake
yanzu, wanda da shi take ado, da shi take takama da jin kanta ita har takai mace
abar kallo. Uwa shiyyasa nace miki ki kasheta tun a farkon farawarta amma kik....

"Na fada miki na kara fada miki kashe wannan yarinyar kai tsaye ba abune
mai sauki ba. Domin akwai wani boyayyen al'amari da yake zagaye a kanta. Tsaye nake
kuma akan ganoshi dare da rana dan ba dake kawai ta shirya yakin ba har dani nan
kaina. Sai dai abinda bata sani ba ni nafi karfin iyawarta, zan kuma tabbatar mata
da hakan nan kusa. A cikin sharuddanmu kin tafka kurakurai da yawa ta-kurya, ciki
harda kasa bamu alkyabba da ke a sashen mai babban daki. Tun a ranar farko kin kasa
shayar da yarinyar nan madara, bayan gagara yimata wankan turare da saka mata
alkyabbarmu. Kinyi yunkurin kasheta da hanunki bayan na sanar miki hakan babban
kuskure ne amma kika ki jina. Kinyi kuskuren kasa saka ido har aka kaita sashen
Ajlaan bada saninki ba. Kinyi kuskuren kasa hadiye abubuwa da dama dangane da
ita.Wadan nan abubuwan dama wanda ban lissafaba sun taimaka mata wajen bude kofar
samunki ta inda bakiyi zato ba. Babban na karshe daya bude komai kasancewarta da
jininki matsayin abu guda, bayan kuma tun a farko mun sanar miki mune zamu bama
Ajlaan matar aure mai kwaranye kishinsa...

"Na amsa dukkan laifina gareki Uwa, ina kuma mai neman afuwa da agajinki
karki barni na fadi kasa a gabar da makiya ke burin ganin bayana. Ki fadi mi kuke
bukata na diyyar laifukana komai wahalarsa zan zama mai cikashi da gaggawa ni bazan
kasance mai butulci irin wanda akai miki a baya ba. Ina son yarinyar nan tayi
nadamar sanin kanta ma balle ni a karan kaina".

"K mai kokarin cika sharudda ce ta-kurya shiyyasa bana iya dogon fushi da ke.
Kije an miki, sai dai ki shirya dan shirinmu na yanzu zai zama a saman a bayane.
Zaki biya diyyar kurakuranki da jinin bakaken shanu goma, na rakuma goma, na
bakaken karnuka goma suma. Jariri sabuwar haihuwar kwana uku kamar yanda akai a
wancan karon mai tambarin masarautar nan. Bayan sati guda zaki cika mana da jinin
barin ciki na mata biyu masu sabon shigar ciki dan watanni hudu. Tare da namijin
hadimi sabon aure shima da yay kwanciya da mace sau daya. Da ga yau madarar da
Ajlaan zai koma sha zata dinga fita da ga hanunki ne, akwai shayi da yake sha a
kullum kisa a nemo miki mai masa nomansa ya noma da wannan irin amaimakon wanda
yake noma masa, dakin zai dawo tafin hanunki komai sai da umarninki zai aikata shi.
Tana makirci da danki a tsakkiyarku,kenan sai kibi ta karfin ikon shi da ke a
hanunki da ga yau. Zamu sama mata amintacciyar hadima, dan haka ta koma sashenta da
zama.Muna akan bakanmu, waccan yarinyar zata shigo domin da ga gareta kawai muke
bukatar magajin daular ruman kiyi gaggawar gain an kulla aurensu. Da ga shi har ita
ki tabbatar sun sha wannan ruwan, shine zai hanasu sake kasancewa da juna har
abada".

Cike da farin ciki Malikat Bushirat ta amsa tana jera godiya ga uwa cikin
gurfana. Ji take a daya duk wani bacin ranta da tashin hankali sun kwaranye kamar
ma ba'ayi ba

"Uwa sai dai akwai hadimin nan daya sakata a ruwa, Saiful-malik ya
tabbatar min yana haninsu".

"Wannan bashi da wani muhimmancin da zai dameki, dan baisa ke wacece ba


ai".

"Amma Uwa ita ai ta sani, baki ganin zata iya yin yanda kowa zai fahimci
ni din ce?".

"Bata isa sanarma kowa ba koda shi Ajlaan ne, dan akwai soyayyarki a
zuciyarsa fiye da yanda duk wani mai hasashe ke zato".

Nidai bilynku na ce, "humm" 🥱)

*

Ta farka sau daya vin fitsari taga baya dakin,17:38


Ta tarka sau daya yin titsari taga baya dakin, sai hakan ya kara mata nutsuwa. Sai
dai kuma Can tikin dare ko tace gabanin asuba taji a mata wata irin runguma data
sakata farkawa a firgice. Gabanta faduwa yay lokacin data tabbatar da shine.
Muryarta har kakkarwa take na son magana. Sai dai ma kafin ta furta ya ce mata
"Shilli!!" dole ta hadiye tai luf. Yamutsata ya dingayi da jagwalgwalata yanda yake
so, ta riga ta gama kaiwa makura a rudewa. Sai dai bai mata komai ba har aka kwala
kiran salla ya mike a gadon ya nufi bathroom. Kusan mintuna goma tana nan kwance
lamo da share hawayen da tasha na tsoro ya fito da alamar wanka ma yayi.Luff tai
bata motsa ba har ya gama tsane gashin kansa ya wuce wajen canja kaya. Wuff tayi ta
tashi zuwa bayi, lokacin da ya fito cikin shirin massalaci ya nufi gadon da shirin
tadata ya samu wayam. Shi yama zata barin akin tai, sai kawai ya fice abinsa gudun
kar ya makara kuma.

Koda ya dawo da ga salla Gym ya wuce abinsa cike da kokarin danne abinda
ke damun gangar jikinsa da ruhinsa. Wani irin mugun motsa jiki ya ringayi na tashin
hankali duk dan ya samarwa kansa nutsuwar manta abinda ke bijiro masa. Sai dai
maimakon samun nutsuwar da yake bukata hankalinsa ne make cigaba da tashi. Ya dauki
tsawon awa biyu a Gym din kafin ya fito ,ya koyi zufa sharkaf kamar wanda iyo a
cikin ruwa.Tana tsaye gaban gadon tana canja bedsheet ya shigo da sallamar nan tasa
ciki-ciki. Dan juyowa tai kadan ta dubesa sai kumata dauke kanta. A can kasan
makoshi ta ce,
"Good morning".

"Ya kike?".

Ya fada a takaice yana cigaba da mata kallon mamaki. Kamar zai share dai ya
kasa hakuri."Waya saki wannan aikin?". A dan shagwabe tace, "Ni na sa kaina, shike
nan mutum bazai motsa jikinsa ba sai dai komai ai masa ni banaso". Takowa yay
gabanta gab sosai, tare da riko hanunta da ke rike da filo.Dagowa tai ta
kallesa.Zata maida ya girgiza mata kansa. Dole ta hakura, sai dai tai kasa-kasa da
idanunta.Shikam dai idanunsa kyam kan kyakykyawar fuskarta da yau dai ta gama
komawa normal kamar komai bai faru ba, ya dan matsa hannuna hankali yana dan huro
iskar bakinsa kan fuskar tata. "Akwai muhimman ayyuka da yawa da zaki motsa jiki ai
ba sai wannan ba Niger".

Fuskarta a dan narke ta dago idanunta da kyau tana dubansa, "Wannan ma fa


Mammy tace ni ya kamata na dingayi yanzu ba amintaccenka ba. Nima kuma kaga dai a
gida Ummu ko mu bata yarda mu gyara cakin Babiy,ko Bata da lafiya sai tace bari ta
danyi ko sama-sama".

Gaba daya ta sake narkar da shi a halin da yake ciki, bai ma san sanda ya
furta, "Kowane salonki kasheni yake autar mata". Yanda ya fada a narke da kai
hannunsa ya shafo jikinta sai taji kunya. Da sauri ta juya masa baya tana rufe
fuskarta da tafukan hanunta. Shima murmushin yayi ya ajiye filon yana nufar
bathroom. Sai da taji shigewarsa sannan ta bude idanunta ta cigaba da aikinta. Haka
kawai take jin kanta cikin wani irin nishadi yau.

"Mammah wai yau ma zakije zaman kotun nan kema? Naga kamar kina jin kafar nan sosai
fa?".

Dan murmushin karfin hali Malikat Haseenat ta saki idonta akan Daneen Ammarah
mai maganar. "Karki damu ai bawani ciwo take mai yawa ba. Ke dai yi sauri ki bani
kunun nan nasha, kin sanshi dan ka'ida ne akan bin lokaci".
Yar dariya Daneen Ammarah tayi kawai, Da ganta itama zaka fahimci tana cikin
farin ciki. Daga ita har Malikat Haseenat din tun jiya fuskokinsu sun kasa daina
murmushi, da dare kam zama sukai suka ding hirar Iffah. Su kansu sun kasa gane ta
yanda akai yarinyar ta shiga ransu matuka har haka, kuma take ma kara shiga a
kullum musamman ma ita Daneen Ammarah din da kwanakin nan taketa mafarkai da ta
kasa gane kansu……………✍️

DAUDAR GORA

Book two( 53)

Wata shegiyar dariya ya saki idanunsa kan takardar da aka aiko masa ta sake zaman
shari'ar yau. Ya kai hannu ya yarce ruwan wankan dake kan goshinsa zuwa fuska. Tun
safiyar jiya basa gidan shi da Miran Jasim. Sai yau ne shi yake dawowa Miran Jasim
kuma da daddare.

Wayar landline dake gefe gadonsa ya dauka,yay yan danne-danne yana da ga


tsayen da yake. Ana dauka ya kwashe da dariya, sai kuma ya kai zaune a bakin gado.
"Yaya dai kawun mai sharia kaima an kawo maka takardar ne?".

Wani irin shegen tsaki Miran Jasim yaja da ga can. Ya ce, "Bar wawa dan
wahala mana. Shifa gani yake kamar ya wani kai anan. Muje zuwa idan ya isa sake
zaman wata shari'ar da ga wannan. Zamuyi maganinsa ne shida shegiyar yarinyar nan
mai bakin akkunaye".

Sake kwashewa da dariya Miran Arshaan yayi, tare da fadin, "Ai boka dan
gurguzu yayi,tunda muka fita muka dawo masarautar nan babu wani shege da yay magana
shima bai isa
yinta ba yau".

Dariya suka kwashe da ita a tare kamar wasu mahaukata...

_Tofa, mi Fir 'auna da hamana suka shiryo ne


haka🥱😂🚴🚴🚴🚴

Yau kam a tare suka fito zuwa dining room. Amintaccensa ya zube kansa a kasa yana
gaishesu cike da girmama. Iffah ce kawai ta amsa masa cikin kulawa. Gogan nata kam
lips kawai ya motsa ya wuce abinsa. Da kansa ya ja mata kujera, itama sai ta ja
masa tana kallonsa da murmushi. Shi dai bai murmushin ba, amma ya juya idanu cike
da salon birgewa. Koda amintaccensa ya taso domin hada masa abinci kamar yanda ya
saba dakatar da shi tai. Sai ma ta sallamesa akan yaje idan sun kammala sai ya
dawo.

Sai da ta gama bubbude duk kwanikan wajen sannan ta kallesa alamar mi yake
so? Kaifafan idanun nan nasa ya zuba mata, sai kuma ya daga yatsarsa manuniya a
hankali ya nuna ta.Baki ta tura gaba tana wani kyaf-kyaf da idanu."Ni abinci nace
fa". Yanda tai din sai ya bashi dariya. Amma sai ya gimtse abarsa ya dauke kai
Itama sai ta tabe baki ta dauke nata kan dan ta fahimci yau kuma yan mislinacin ne
da mulki a kansa. Zabar abinda taji tana so a ranta tai kawai ta zuba musu ta ajiye
komai gabansa da fadin bismillah. Abincin kawai ya zubama ido yana jinsa wani daban
yau din. A da sai daiamintaccensa ya hada masa, yau kuma gashimatarsa ce, abinda ya
jima yana mafarki. Rayuwa kenan mai farko da karshe.

A nutse suka fara cin abincin, Iffah na satar kallonsa da jinjina mulki da
kasaita. Yanda yake cin abincin ma kansa abin birgewa ne. Suna gab da kammalawa
kanta yay wani irin sara mata. Da sauri ta kai hannu ta dafe tana ambaton sunan
ALLAH. Kallonta yay shima da mamaki, sai kuma ya riko hanunta da ta dafe kan da
shi. Dago idanunta da sukai wani irin jajaja cikin kankanin lokaci tai ta kallesa.
Shi har sai da ma yaji tsigar jikinsa ya tashi, amma sai ya dake kasancewar shima
akwai nasa abebadan a kansa. Da ido ya mata alamar minene? Dan da gaske yau
miskilancin ne a kusa. Ji yake motsa lips din ma yay magana babban aiki ne.

A hankali ta furta, "Kaina ke dan mun ciwo

Tun yaushe?".

Ya fada a fusge. "Da safen nan ne fa. Amma ba wani ya matsa bane karka damu.
Dan ALLAH ka barni na fara tafiya kotun nan sai kai kuma ka taho da ga baya".

Idanu kawai ya tsira mata. Ita kuma ta langabe kai gefe alamar roko. Dauke
idonsa yay kawai da ga kanta batare da ya ce komai ba. Ya lima yana zargin akwai
junnu a jikin yarinyar nan, yanzun ma kuma abinda yake zargin kenan. (Ya arrahaman,
komai na yarinyar nan sake sakashi a rudani yake). Sai kuma maganar data fada masan
yanzu ta shiga masa kaikawo a rai. Ya barta ta fara yin gaba kafin shi na nufin
akwai wani abu kenan. Shikam yaga takansa da wadan nan ahali nashi. Wani abu kenan
wani ya sake masa ko kuma dai aljanun nata ne ke neman raina masa hankali. Cikin
rashin bama abin muhimmanci ya cigaba da cin abincinsa, sai dai kuma abinda ta fada
kuma ya faru a wacan ranar na masa kaikawo. Iffah dake binsa da kallo kamar zatai
magana sai kuma ta hadiye kayarta tana sakin nannauyar ajiyar zuciya da jan jikinta
baya.

Komai baice mata ba, sai da yaga ta mike. A can kasan makoshi ya furta "Ina
zuwa?".

Agogo ta nuna masa. Kallon agogon yay ya dauke ido. Batare da ya sake kallonta
ba ya ce ,Kina bukatar masu rakkiya ne?".

"A'a".

Ta bashi amsa a takaice.

'"Amma kin san bazai yuwu kije ke kadai ba. Kije akwai masu jiranki a can kasa".

"Nagode".

Da kallo kawai ya bita ganin yanda ta sauya lokaci guda. Ga fuska ta wani
daure tamau babu alamar wasa. Shi sai ma ya fara jin ko dai itace aljanar da kanta.
*Yau kam da alama shari'ar zatai zafi. Dan kotun tacika fie da zaton mai
hasashe. Abinda Kuma zai birgeka duk ahalin masarautar ne.Cikin wani irin takun
kasaita da izza da ya jawo hankalin duk wanda ke cikin kotun Iffah ta shigo da shi.
Ga hadimai na take mata baya. Tayi matukar kyau cikin shigar jikinta, ga wani irin
kyawu da fuskarta ta kara sai shining takeyi fiye da hasken tauraruwa zarah. A
zahiri ita tafiyarta takeyi normal, amma ga masu kallonta babu abinda suke gani
tattare da ita sai tsantsar izza mai ban mamaki. Wani abin birgewa da tai ya
kayatar da was a wajen shine kai tsaye inda Malikat Haseenat take ta nufa. Takai
kasa cike 17:42
yanzu bayan Tajwar Eshaan da Malikat haseenat sama da ita a duniya.

Shigowar mai gayya mai aiki tasa tunaninsa katsewa…. a take kotun tai tsitt kowa ya
mike domin girmamawa. Taku yake cikin tsantsar kasaita da izza data zame masa jinin
jiki. Ga wani irin kamshinsa mai kada zuciyar mai shaka na tashi. Yammatan wajen da
suka dade da folawa a sonsa tuni zukatansu suka shigar narkewa, duk da babu abinda
ake gani bayyane a fuskarsa. Dan ya sakayata hatta da idanunsa saye suke cikin
eyeglasses dake nuna blue daga waje. Addu'ar neman tsarin ALLAH da ga duk wani abin
cutarwa ya karanto lokacin da yake kaiwa zaune a hadaddiyar kujerar da ke a
mallakin zamansa. Ya dan saci kallon sashin da yake tunanin ganinta. Tana a wajen
kuwa, sai dai abin mamaki ita sam bama shi din take kallo ba.Ajiyar zuciya ya dan
sauke a hankali wadda ko amintaccensa da ke gefensa da masu tsaro guda hudu haggu
da damansa basu isa ji ba.

Bayan an tabbatar da kowa ya natsa Sayeed Hanifud-Din ya mike ya dubi jama'a.


"Alhamdullahi muna godiya ga ALLAH da ya sake dawo damu zama na uku akan wannan
shari'a. A zaman daya gabata wadda ake kara ta amsa laifinta, sai dai ta Bama
wannan kotu mai adalci damar bincike mai zurfi akan tushen shugaba na wanna daula.
Inda wannan kotu mai adalci ta amshi korafinta har ta bada dama ga masu bincike.
Matsala ta ratsa ta yunkurin son halaka Zawjata-almilk da akai, inda dalilin haka
aka samu tazarar daga wanna zama har sai da ta samu lafiya. To yanzu dai alhmallh,
wanna zama a wanna gabar duka zai ta'allaka ne ga jin bayani da ga bakin shugaban
jami'ai da aka danka wanna bincike garesa. Shugaban jami'ai bismillah".

Sai da ya mika gaisuwa ga Shahan-shan cike da girmamawa kafin ya juya ga


jama'a. "Assalamu alaikum kamar yanda aka bamu damar bincike a gaban wannan kotu
mai adalci mun gudanar. Mun bibiyi tushen samuwar madara da kaita sashen Zawjata-
almilk. Inda bincikenmu kuma ya kaimu har ga wanda ya shigo da wannan madara mai
dauke da dafin macizai a ciki. Karna cikaku da surutu waka bakin mai ita tafi dadi.
Ina rokon alfarmar wannan kotu da ta bani damar gabatar da Dafiq in Ghalib a
gabanta".

"An baka".

Cewar Sayeed Hanifud-Din.

Kallon juna Miran Arshaan da Miran Jasim sukai suka saki murmushi. Sai kuma sukai
saurin duban wanda jami'ai ke kokarin shigowa dashi kirazansu na wani irin mummunan
harbawa.Kokarin mikewa Miran Arshaan yay da sauri Miran Jasim ya danne masa hannu
jikinsa na rawa. Iffah da ke kallonsu ta saki murmushi,cikin Sa'a kuwa suka hada do
da Miran Jasim.Ido daya ta kashe masa da dauke kanta tana dan wani cizar lips cike
da salo.

Dattijo da jami 'ai suka shigo da shi bazai wuce shekaru hamsin da takwas a
duniya ba. Cikin nutsuwa ya gurfana gaban Shahan-shan yay gaisuwa, bai o motsa ba
da ga zaman kasaitarsa. Dattijo Dafiq in Ghalib ya gyara tsaiwarsa yana fuskantar
kotu. Dubansa Sayeed Hanifud-Din yayi ya ce, "Dattijo waye kai?".Cikin dan rawar
harshe ya ce, "Dafiq ibn Ghalib. Ni masanine akan macizai. Ina zaune a kauyen
Bansh".
"Miye alakarka da daular ruman?".

"Alakata da Daula ruman alakace irin ta kowanne dan kasa. Wato fadan shugaban
kasata adali".

"Amma duk da haka ka iya bada dafin macizan da za'a cutar da shi?"

"Ko kusa ba haka bane, ko wani naga zai cutar da hadimin wannan daula bama
shugabana ba sai inda karfina ya kare ai. Ni dai a ranar daren wata laraba wani
bawan ALLAH ya sameni akan shi din jami'in ne na hukumar bincike akan sanin nau'in
dabbobi masu dafi.Yazo kuma wajena ne da bukatar samun kalolin dafin macizai zaiyi
bincike a kansu. Da farko naso naki, dan nasan dan adam na wannan duniyar ba abin
yarda bane. Amma sai ya nuna min katin shaidar aikinsa. Hakan yasa na yarda da shi
na dauka na bashi"……….✍️

DAUDAR GORA

Book2 (54)

......."Ko zaka iya gane mutum idan ka sakeganinsa".

"Sosai ma kuwa. Dan akwai ma cctv footage na abinda duk ya faru a tsakaninmu
batare da shi ya san inada camara a wajen ba." ya kare maganar yana duban shugaban
jami'ai. Ya fahimci mi yake nufi, dan haka ya mike ya mikawa Sayeed Hanifud-Din
flash da ke a hannunsa, anan take kuwa aka saka flash jikin lap-top aka kai gaban
Tajwar Eshaan, sai ko ga duk abinda ya fada din dalla-dalla.

An shigo da wanda ya amso dafin macizan, wanda ya kasance amintaccen hadimi


ne ga Miran Jasim, kowa ya sani kuma a masarautar nan, dan tun yana a matashin
saurayi ma yake tare da hadimin, shine ke masa duk wasu ayyuka na sirrinsa dama na
mugunta. Ai Miran Jasim baima san yay wata iriyar zaburar tashin hankali ba jikinsa
na kakkarwa. Yayinda gaba daya kotun ta dauka yan kananan magana har sai da aka
tsawatar. Sayeed Hanifud-Din da shima dai gaba daya jikinsa yay sanyi da al'amarin
ganin daga inda ya fito, dan koba'a fada ba komai a bayyane yake. Fuskantar hadimin
da gaba daya ya fita hayyacinsa a hannun jami'ai yay. "
"Bama bukatar wani kwana
ja da ga gareka ko ja' in ja, fadar gaskiyarka na nufin zaka iya samun sassauci,
zabar yin taurin kai kuwa ya rage naka. WANENE YA
SAKA?".
A hankali hadimin ya dago ya dan dubi inda
su Miran Jasim suke, idanu suka hada da Miran
Arshaan da yake masa kallon kasa-kasa yana
wani dan motsa yatsunsa. Ajiyar zuciya ya ja a
hankali, kafin ya maida dubansa ga Sayeed
Hanifud-Din. Kai tsaye babu wata kwana-kwana ya ce, "Shugabana Miran Jasim ne ya
sakani

A take kotun ta dauki wani irin hun karajin Miran Jasim da ya zaburo kan
hadimin nasa, sai da jami'ai suka rirrikesa. Yayinda jama'a suka hau salati suma
har sai da aka tsawatar. Hadimin ya cigaba da fadin, "Sai dai ni ban san mizaiyi da
ita ba, amma a gabana ya zubashi a cikin madara ya bani madarar yace na kai sashen
Zawjata-almilk nace daga sashen uwar masu gida. Bani da ikon cemasa a'a, amma navi
niyyar kin kaiwa sai dai nasan zai iya sawa a bibiyeni idan nai hakan zai halakani
kuma, dan haka na cika umarninsa amma ni duk tunanina ma Zawjata-almilk din zai ba.
A ranar nata kokarin ganin samun ganawa da ko amintaccen adalin shugabanmu ne amma
hakan bai faruba,da ga karshe ma sai naji wai ashe shine za'a bama madarar ta
hanyar Zawjata-almilk ba kamar yanda nai tunanin itace zai bamawa din
ba. Kuma zan fadi gaskiya, ba laifin Zawjata-almilk bane ba asiri yay mata kan duk
yanda yaso haka zaiyi da ita, daga baya itama zai kasheta.

Duk yanda akaso samun nutsuwar kotun kam hakan ta gagara. Salati kawai kake
ji da la'antar Miran Jasim da akeyi. Iffah ta saki wani irin shegen murmushi tana
mai kallon Miran Jasim da yay sumar tsaye. Sai kuma ta maida kan Miran Arshaan da
gaba daya yay sharkaf da zufa. Wata dariya ta kyalkyale da shi a zuciyarta tana
fain (tun banzo kanka ba) a zahiri kam baka isa fassara yanayinta ba.

A bangaren Miran Arshaan kam ya dauka makircinsa ne yay tasiri kan Miran
Jasim. Dan kuwa hasalima shiya tura hadimin ya shiga jikinsa duk tsawon wanna
shekarun da suke a tare, dan kawai ya san duk wani motsinsa Abinda bai sani ba a
yanzu hadimin ba aikinsa yake ba aikin Iffah yake yi, ita kuma ta zabi tattara
laifin ga Miran Jasim a karan kanta saboda haka ta tsara binsu daddaya, shi kuma
zata cigaba da jansa a kasa har zuwa gabar da take so..

Wata irin daddagewa da fashewa da kuka da Miran Arshaan yay ne ya katse mata
tunaninta. Ta zubama drama din tasa ido dan ya wani daddagene ya fashe da kuka yana
duban Miran Jasim kai kace dada duniya har zuciyarsa ne. "Jasim! Jasim Akhi mu
zakama haka? Kai da kanka zakaci amanar dan uwanmu ka zama jagoran shirya
halakashi. Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un.…. Mi kake bukata ne? Miye dan uwanmu
bai mana na gata ba a wannan duniyar? Ya rikemu tamkar yanda Abie (Tajwar Abdul-
majeed) zai rikemu, amma mu mu kasa rike jininsa daya tilo a duniya da bashi goyon
bayan mulkin da ALLAH ya daura masa. Dama na jima ina zargin kana kwadayin mulkin
nan ne,ban tabbatar da hakan ba sai randa aka samu kayan tsafin daka saka a kujerar
da adalin shugabanmu yake zama, kaki zuwa kuma wajen meeting da ga karshe ma bakin
cikin an ganoka ka nema halaka iyalinka" ya sake fashewa da kuka.

Wata irin mahaukaciyar shaka Miran Jasim da jikinsa ya hau kakkarwa ya kaima
Miran Arshaan da kyar kuwa aka bangaresa yana fadin sai ya kashe Miran Arshaan din.

Duk da wannan dambarwa mai gayya mai aiki Shahan-shan na zaune ne yana binsu da
kallo ta cikin gilashinsa. Shi kansa a wannan gabar sai ya shiga dan rudani, dan a
iya bibiyar rayuwar uncle's din nasa da yake yi tun lokacin da ya fara zarginsu a
tare suke aikata komai sai dai a sirrance ne kam. Kuma ita kanta Iffah ta sanar
masa su biyu ne ai, amma yaya akai hakan ta kasance komai ya juye kan Miran Jasim
shi kadai.

Tamkar Sayeed Hanifud-Din kam yasan mike ransa ya ambato sunanta. "Ko Zawiata-
almilk nada wani karin bayani akan alakarta da Miran Jasim da har hakan ta kasance
tsakaninsu?".

Shiru kamar Iffah bazata motsa ba, sai kuma ta yunkura da kyar fuskarta jage-
jage da hawaye. Handkherciff din da Malikat Haseenat ke miko mata ta amsa ta goge
fuskar sannan ta fuskanci kotu bayan ta saci kallon Tajwar Eshaan da takeji a
jikinta kallonta yake, dan tun dazun takejin kaifafan idanunsa a kanta. Hakama
Malikat Bushirat kallonta takeyi. A nutse cikin nuna rauni ta ce, "Ni ban san mizan
ce ba, amma abinda na sani kawai bani da wata alaka da shi nikam, hasalima ban
sanshi ba a zahirance sai a randa aka nunani gaban dai iyayen wanna gida mai
albarka. Kuma ko'a ranar bazan iya cewa ga kamaninsa ba. Sai a randa Zawjata-almilk
farko ta rasa ranta ne dai-dai da rasuwa sayeed Khairul-Bashar na nufi sashen mai
girma Shahan-shan hankali tashe dan ina son tabbatar da abinda al'umma keta fade
akan shine ke kashe matansa. Ina tsaka da dube-dubena akan gawar suka shigo tare da
shugaban jami'ai, Ni kuma sai naji tsoro na buya, bayan an fita da gawar ashe shi
ya ganni shine ya dawo da baya. Na tsorata amma sai ya ce na nutsu muyi magana, zai
rufamin asiri amma yana so muyi aiki tare. Ya dan mun maganganu dai da yawa. A
ranar ya kawo min maganganu masu rudarwa, mafi girma a cikinsu nunamin video cewar
adalin shugabanmu ne ya halakamin iyayena da tsafin maciji kamar yanda naga alamar
saran maciji a jikin Zawjata-almilk da ta rasu, ya kuma sanar min nima na tsira
zanyi ba dan haka nima nayi takaina. Nazo mu hada hannu mu yakesa dan baza'a
hukuntashi ba. Ni a lokacin maimakon cemasa wani abu ma rudani na shiga da tashin
hankali akan iyayena,dan haka bamma gama saurarensa ba, ganin bana a hayyacina ya
tashi ya fita. Sai kuma A ranar 9 ga watan 2 dai nanma na samu kiransa misalin
karfe takwas a dare. Nayi matukar mamakin hakan, dan bai boyemun ba ya sanar min
aiki fa yake son miyi tare kamar yanda ya a waccan ranar amma zai sanar min abu.
Ban katsesa ba nace ina saurarensa.Yasanar min magana bazata yiwu ta wayar landline
ba, amma ga number dinsa na kirashi direct video call. Har lokacin ban kawo komai a
raina ba, duk da dai inajin toro ganin shiga uncle dinsa ne, idan na fadama wani
bama za'a yarda dani ba. Dan haka nabi umarninsa na kira din dan bangama sanin
yanda akeyi anan din ba. Tun daga wannan ranar ban sake fahimtar komai ba da ga
yanda yake bibiyata sai da nakai madara ga adalin shugaban wannan kasa ya sha. Daga
nan na fara fahimtar makirci ne musamman yanda ya dage akan sai an kaini kurkuku.
Bayan an kainin kuma ya bini har can yana fadamin maganganun banza harda na rashin
da'a". Ta fashe da kuka mai cin rai, wanda a yanzu kam da gaske kukan take, dan
kalmar KARUWA da Miran Jasim ya ce zai maidata na mata radadi har yanzu a cikin
rai.

Dolene yanda Iffah ke bayanin yasa kaji hawaye yazo maka, kuma ko kai waye
sai kaji ka yarda da ita. A nan din ma fa rudewa kotun ta sake yi, yayinda Miran
Jasim ke hargowar sai ya batar da ita, sai ya shafe babin rayuwarta baki daya ita
da Miran Arshaan da sukaci amanarsa. Babuma wanda ke saurarensa sai ALLAH wadai da
ake jifansa da shi da tausayin Iffah da gaba daya yau kowa ya fahimci an mata
makirçin ashe ,Dama can wasu da yawa tunma a ranar data aikata suke fadin bayin
kanta bane, tayi kankanta da aikata laifin ita daya. To sai gashi yau kam komai ya
fito filin ALLAH. Kotun tai bala'"in daukar turiri har sai da Tajwar Eshaan da
kansa ya tsawatar. Dan danan kowa ya nutsu kotun tai tsitt. Ya dauka tsahon mintuna
uku babu alamar zai ce wani abu, kafin ya nisa da kyar cikin maganar nan tasa a
fuse kamar wanda akaima dole. Da kyar ya iya danne zafi da radadin da zuciyarsa ke
masa kanjin wai uncle dinsa yama matarsa magana ta rashin da'a,amma ta boye masa.

"Alamu da kalaman Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb sun tabbatar da duk abinda
aka sanar anan game da shi ya aikata. Sai dai duk da haka wannan kotu mai adalci
zata bashi damar sanar damu dalilinsa na aikata duk wannan a zama na gaba. Za'a
tsaresa a kurkukun da Zawjata-almilk tai rayuwa har zuwa ranar da kotu zata sake
bukatar ganinsa a gabanta. Wannan kotu kuma ta wanke Zawjata-almilk da ga zargi,
tare da bada damar kawo bokan da yay sihirin gaban shari'a shima. Tanada damar
shigar da kara itama a karan kanta game da amfani da ita da Jasim yayi. Daga karshe
ni Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ina shigar da kara nima bisa yunkurin
kashe min MATA da akayi har karo biyu ta hanyar yimata allurar guda da jefata cikin
ruwa..." da ga haka ya mike anutse cike da salon nan nasa yayinda ya bar jama'ar
kotu gaba daya a yanayin mutuwar zuune da kalamansa na karshe. Malikat Haseenat kam
murmushi ta saki mai sanyi da kayatarwa, hakama Daneen Ammarah. Yayinda zuciyar
Malikat Bushirat ke bugawa da wani irin sauri-sauri a cikin kirjinta dake yin kamar
zai bude.

A bangaren Iffah kam idonta akan Miran Jasim ne, a cikin iska ta rubuta
*_FINAL_* da yin alamar yanka wuya ta kashe masa ido daya…….✍️
_Mai RUMAN sai kayi takanka kaima to, dan da
gaske Iffah kaza zata koma uwar tone-tone🥱_

17:14
DAUDAR GORA..
Book2 (pg55)
Il
A
..Wani irin fadawa tai saman gado cike da farin ciki tana sakin siririyar dariya.
Babu abinda take hangowa sai idanun Miran Jasim da na Malikat Bushirat harma da
Miran Arshaan. Tai wani irin juya ta sake juyawa a gadon sai kace tarwada. "Kina
lokacinki Fhareedah bint Zayyan". Ta fada a fili tana sake kyalkyalewa da dariyarta
kai kace an mata albishir ne da dawowar su Baby kasar ruman. Yanda take ji kam
kamar ta tashi tayita taka rawa. Daya da ga cikin burikanta ya cika, ya cika a
gabar da ALLAH ya bata abinda baya cikin lissafinta. Tabbas zama mallakin Shahan-
shan baya cikin lissafinta. Lissafinta na daukar fansa ne kawai,fansar jinin yan
uwanta da bazata iya yafewa ba. Sai dai kuma dukkan labarin ya canja, ya canja da
canjawar shigowar su Miran Jasim cikin tattakinta batare data tsaro da su ba.
Shigowar Tajwar Eshaan in Haysam Abdul-majeed matsayin wani abu mai daraja a ciki
labarinta batare da ta rubuto da hakan ba nan ma. "Ya rabba" ta fada a zahiri tana
lumshe idanunta da sukai wani tar-tar na haske fuskarta na kara kawatuwa da
murmushi mai kayatarwa.

"Miyasa kika boye min?".

Bata fahimci mi yake nufi ba, dan haka ta idanunta da jan cikinsu ke dan raguwa a
hankali ta zuba masa. Bazata iya jurar kallonsa cikin ido ba dan haka ta dauke su
ta maida gefe. "Ban san akan mi kake magana ba Sultan".

Sai da ya dan furzar da hucin baci ran da yake ta dannewa, a dan fuse ya furta,
"Jasim! Miyasa kika boyen ya sameki a kurkuku da maganar banza?"

Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta motsa cikin sauke ajiyar zuciya ta
ce, "Kayi hakuri, a lokacin ban san ta yanda zan tunkareka ba. Ban kuma san ta
yanda zaka fahimceni ba. Kuma ai ALLAH ya kareni da ga sharrinsa tunda ga shi yau
gaskiya tayi halinta".

Shiru baice komai ba, dan zuciyarsa tafasar kishi take har yanzu akan wanna kalmar,
tafi komai tsaya masa a zuciya fiye da abinda Miran Jasim din ya aikata masa dan ya
jima da sanin dama suna farautar rayuwarsa. Sai maganar rashin fitowar sunan Miran
Arshaan shima na masa kaikawo, kamar zai mata magana akan hakan sai kuma dai ya
hadiye kayansa da tunanin ko Miran Jasim din ne kawai ya fiddo mata da nasa hali.
Amma in bai manta ba ranar a kalamanta ta masa nuni ne da mutane biyu ko yace fiye
da daya. Hakan na nufin bayan Jasim din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi
baice komal ba ya dal cigaba da kallonta. Kusan minti daya sannan ya motsa da
cigaba da don takawa a hankali cike da kasaitar nan tasa. gabanta yaja ya tsaya,
tare da zare hannunsa dake cikin aljihun wandon jeans dinsa ya mika mata. Idanunta
ta dago ta kalli hannun da ke fari tas da shi, ga jini nata kaikawo a tafin kamar
ba namiji ba. Idanunsa ya dan lumshe da budewa a lokaci guda yana gyada mata kai
alamar ta daura nata. Kamar mai jin tsoron hakan ta dago natan ta dora a cikin
nasan. Sake lumshe idanun yayi kamar wani wanda maganadisu ya taba,batare da ya
bude ba ya dagota ta mike tsaye itama. Matsota yay kawai jikinsa ya rungumeta tsam-
tsam. Sassanyar ajiyar zuciya ta saki nutsuwa na ratsata, sai kawai ta kankamesa
itama tare da kwanciya luff a faffadan kirjinsa tana shakar daddadan kamshin
turarensa mai saka zuciyar mai shaka nutsuwa
_Oh oh su Iffah an waye an manta da mu dangi

Mammah duniya abin tsoro ce why, duk da mun jima da sanin Jasim baya kaunar Abni
sai yau din da komai ya fito fili ya bani mamaki. Har zuciyata iya abinda nake
kallonsa da shi shine nuna adawa kawai ga mulkin tunda shine burinsa. Amma why ban
taba kawo zai iya shirya halaka rayuwarsa ba haka. Wace irin rayuwa ce wannan wai
dan uwanka jininka ya zabi cutar da kai akan abin duniya mai yankewa. Wai ina
mahaifinmu da ya zama sanadin kawomu duniyar ma? A da shine a wannan kujerar, amma
ya shude kamar ba'ayisa ba, aka daura dan uwanmu, shima ya shude kamar baiyi ba,
idan sukai hakuri shima wataran bashi bane anan din. Bazan boye miki ba
Mammah,zuciyata ta fara min sake-sake da kokwanto akan rasuwar Haysam Akhi, haka
Zawjata-almilk da muka rasa, anya kuwa hakan baida alaka da su Jasim Akhi ya karba
makamancin tayin da muka jima da tsigesa a cikin jininmu?. Dan zuciyata ta fara
rabuwa biyu bayan zargin mushirakar can data dade da shudewa a tarihinmu kamar
akwai wata mai irin al'amuranta a yau zagaye da wani namu".
Malikat Haseenat da ke ta faman jinjina kai taja ajiyar zuciya mai karfi tare da
fesar da iska zazzafa da ga bakinta. "Tabbas duniya ta cancanci zama abar toro kam
Ammarah, nima kuma kamar ke zuciyata ta fara rawa, ta fara rawa da wannan gabar har
inajin ni kaina ban yarda da kaina ba. Tabbas mushirikar can ta shude ita da
tarihinta, amma sai zuciyata ta gagara nutsuwa da hakan duk da tsahon shekarun nan
da suka shude da kasancewarta.Babu abinda Jasim bazai iya aikatawa ba,musamman idan
na kalla irin mugun zaman da mukai da mahaifiyarsa a masarautar nan. Dan haka shima
kam yanzu abin tuhuma ne. Sai dai akwai wani furuci da yarinyar nan tayi yafa tsaya
mun a rai, tun dazun kuma yake mun kai kaWO….

"Wane furuci kenan Mammah?".

"Furucin bibiyar gawar Zawjata-almilk ta karshe da muka rasa, inda ya zama sanadin
haduwarta da Jasim. Lallai ina bukatar ganawa da Zawjata-almilk".

Shiru Daneen Ammarah tai tana kallon Mammah, sai kuma ta nisa itama zuciyarta
na mata kai kawo akan hakan. Eh tabbas wannan furuci abin a bibiya ne, dan sai a
mahanga ya ke da nasaba da abu biyu. Shi kansa Jasim suspect ne a wannan case din
shima. Duk da dai duk Zawjata-almilk na baya da suka rasa ransu suke fara zuwa su
ganta kafin kowa.

Firgigita ta daw hankalinta sakamakon tabatan dan Malikat Haseenat tayi, taja
ajiyar zuciya mai nauyi da sauke numfashi. "Yi hakuri mammah, why na tafi wata
duniyar tunan nima. Za'ai bincike ga Ibnati dinne? Ko kuwa ya kike nufi?".

Kai Malikat Haseenat ta jinjina da fadin, "Fara nemo min ita a waya".

*Har yanzu Iffah na kwance a kan gado cike da farin ciki da nishadi kira ya shigo a
landline din dakin. Wayar ta kalla kamar bazata tashi ba. Sai kuma ta mike lokacin
da take gab da yankewa ta daga. Kin yin magana tai, sai da Daneen Ammarah tai
sallama sai kuma duk ta rude. "Lah Mamy kece, Barka da wannan lokaci a gafarceni".
Murmushi Daneen Ammarah ta saki mai sanyi da ga can tamkar Iffah'r na gabanta, tana
matukar kaunar yarinyar nan ta yanda ita kanta ma bata san adadi ba. A hankali ta
nisa da sakin ajiyar zuciya ta ce, "Ba komai Ibnati, Mammah ce ke bukatar magana da
ke daman". Tamkar Iffah na gaban Malikat Haseenat ne cike da girmamawa ta gaisheta
duk da yanzun nan suke rabuwa da ga zaman kotu. Da ga can ta amsa mata cike da
nutsuwa da dattakonta, kafin ta aura da fadin, "Mijinki ya shigo ne?". A hankali
Iffah da kalmar ta bama kunya da yi mata nauyi ta ce, "A'a Mammah".Murmushi Mamma
ta sakeyi da gyada kai da fadin, "Idan har bakya wani uziri bayan sallar isha'i ina
son ganinki". Cike da girmamawa ta ce,

"To Mammah insha ALLAHU".

Shiru tai tana kallon wayar bayan ta yanke.Zuciyarta sai faman mata kaikawo take da
tunani kala-kala. Sai kuma ta dage gira da dan tabe baki tana ajiye kan wayar ta
mike. Ficewa tai da ga dakin ta nufi can saman ginin dan wajen na matukar kayatar
da ita. Tana kaunarsa fiye da kowane waje a masarautar.

"Abu Harith kana lafiya kuwa? Tunda muka baro kotu ka kasa zaune ka kasa tsaye. Duk
da dai nasan abinda dan uwanka ya aikata ga wannan bawan ALLAH dole ya tabaka, amma
sai nake ga damuwar taka da rudanin kamar sunma fi na kowa. Ka tuna nima fa dan yar
uwata ce dat rikeni tamkar uwa, sannan shugabanmu baki daya. Mu dukanmu ya sakamu
muka haukace akan baiwar ALLAHr yarinyar nan da bataji ba bata gani ba. Why har
kunyar haduwa da ita nakeji yanzu. ALLAH sarki Mammah tai ta son nuna mana gaskiya
muna bijirewa, duk da
nuna mana gaskiya muna bijirewa, duk da ALLAH ne shaidata kai ne ka dinga kara
tunzurani har idanuna sukai makancewar kasa hasashen komai gashi na kare da dana
sani"

Kallonta kawai yake tana zabga zance ko hadiyar yawu batayi, bata san jima yake
tamkar ya shakota ba tsabar takaici da takura masa da tai. Shifa shi kadai yasan
irin kalar tashin hankali da rudanin da yake ciki akan al'amurin nan. Da farko yayi
zaton hadiminsa na aikine bisa aikinsa na tsawon shekaru da ya daurasa a kai akan
bibiyar dan uwansa, sai dai kallon da yarinyar nan Iffah tai masa sanda suke fitowa
daga kotun ya matukar saka zuciyarsa neman bugawa. Idan har ya canka dai-dai
lokacin da take shigewa *_Next.…_* ta rubuta masa akan iska fa. Wannan kalmar itace
ta tsaya masa a zuciya taki fadawa sai faman kaiwa da komowa take.....

"Ya ilahi Abu Harith!!".

Jasrah da ke hargowar kwala kiran sunansa ta katse masa tunani. Cikin bacin rai ya
nuna mata kofa alamar ta fice masa. Rai bace take dubansa itama, har taji ta kasa
hakuri ta ce,"Kamar ya na fita bayan kuma magana muke?Wai shin kodai kaima da naka
kashin ne a jiki banda labari, dan wannan yanayin naka kam ya fara sakani a
rudani..

"Jasrahhh!!!".

Ya fada cikin karajin da ya sakata zabura. Cikin wata irin birkicewa da bata taba
fuskanta da ga garesa ba ya sake nuna mata kofa. "Wihy idan baki fita min ba sai na
kwashe fuskarki da maruka. Banza kawai kin dameni, ki barni naji da abinda ya
isheni ban san wawanci".

Ba karamin tsorata Jasrah tayi ba kam, dan wutar bala"i ta gano kuru-kuru
cikin idanunsa da kan fuskarsa. Cike da sassarfa ta nufi hanyar fita ranta a bace
da tsawar da yay mata.... Tana gama ficewa yaja wani shegen wawan tsaki da raka
bayanta da harara ya ce,
"Tinkiya kawai, ban san damuwa",. A wani irin zafafe ya koma jagwab cikin kujerar
ya zauna yana dafe kansa da ke sara masa da karfin masifa. Dai-dai nan kira ya
shigo wayarsa. Sharewa yay bai dauka ba har ta tsinke, sai kuma ga wani ya sake
shigowa. Tsaki yaja da finciko wayar daga aljihu da niyar kashewa gaba daya yaci
karo da sunan Ameera Haifah baro-baro. Kamar bazai daga ba nan ma sai kuma ya amsa
a fusace da kaita kunnensa. "Ke kuma miye kike wani kirana a wannan lokacin bayan
kin san mi ake ciki".

Da ga can cikin muryar tashin hankali ta ce,"Dolene na kiraka Arshaan. Dan tabbas
akwai matsala. Matsala babba why. Na kasa gane komai, ka saka zuciyata a rudani
gaba daya game da abinda ka aikata a kotu. Shin mi hakan ke nufi? Taya komai da
muka aikata mu ukkoma kansa shi kadai? Kai ne kai hakan kokuwa hatsabibin yaron can
ne ya kulla mana gadar zare ta hanyar yar iskar yarinyar can. Wihy kaina ya kwance
gaba daya, dan ALLAH ka zaba mana wajen haduwa yanzu da gaggawa kar zuciyata ta
buga".

"Da zata buga din ma da kowa ya huta.Please malama ki kyaleni bana bukatar magana
da kowa okay". Kittt ya yanke wayar batare da jiran cewarta ba."Ashe zan kasheka na
kashe banza idan kace zaka zamar min matsala Arshaannn!!!".

Ta fada cikin karaji da cije lips dinta jikinta na rawa. Wayar ta cilla saman
gadonta ta cigaba da kaikawon da take tun dazun a cikin dakin. Tunda ta baro kotu
ta gagara zaune ta gagara tsaye.Tasan in har Miran Arshaan ne ya shirya komai ga
Miran Jasim hakan na nufin itama bazata tsira ba dan tare sue kulla komai. Idan
kuma Tajwar Eshaan ne ya ganosu kama Miran Jasim kawai ba komai bane garesu face
talala. Don dole ma akwai wani abu da ya kamata ta sani, dole ta sanshi a yau din
nan yanzun nan basai gobe ba. Idan Miran Arshaan ya cigaba da wofantar da tuhumar
da take masa to lallai zai ganta yanzu a sashensa kuwa. Sai dai duk ma abinda matar
tasa zata zarga ta zarga. Ko kuma in ma barewa zatai why sai dai ta bare da su su
duka amma bazata taba barin Miran Arshaan ya sha ba shima ko ya kaita kasa kamar
yanda ya kai Jasim. A fusace ta sake fisgar wayarta ta hau rubuta masa dogon text
message jikinta sai tsuma yake. Ga uwar zufa ta mata sharban kamar wadda taci gudu
a cikin dokar jejin da babu komai sai sahara mai zafi da ta dauki zafin rana.

Yi take kamar zata tsumbula cikin wayarta dake a hanunta. Ihu kawai ya rage ta
kurma akan kiran Daneen Waheeda da take faman yi tun bayan fitowarsu kotu amma bata
daga ba.Ta bata lokaci da tunanin zatai kiranta in ta gani amma babu alamar hakan
zata faru. Kuma asha ba shima ko ya kaita kasa kamar yanda ya kai jasim. A fusace
ta sake fisgar wayarta hau rubuta masa dogon text message jikinta sai tsuma yake.
Ga uwar zufa ta mata sharban kamar wadda taci gudu a cikin dokar jejin da babu
komai sai sahara mai zafi da ta dauki zafin rana..
Yi take kamar zata tsumbula cikin wayarta dake a hanunta. Ihu kawai ya rage ta
kurma akan kiran Daneen Waheeda da take faman yi tun bayan fitowarsu kotu amma bata
daga ba.Ta bata lokaci da tunanin zatai kiranta in ta gani amma babu alamar hakan
zata faru. Kuma a kalla kira na goma sha bakwai kenan take mata.Banda text message
da zai iya zama biyar koma fiye da hakan.

Kamar almara aka daga wayar, cikin rawa da kakkarwar jiki ta kaita kunnenta tana
fadin.

DAUDAR GORA
Book 2 Chapter: 56

."Haba Waheeda ina kika shiga kekuwa haka kinsa zuciyata na neman karasa harbawa a
tsaye".

Da yar raha-raha da ga can Daneen Waheeda ta ce, "Oh oh Kinga kwantar da hankalinki
nabar wayar ne a daki why ina sashen surukinki. Halan wani masifar shegiyar can ta
sake jangwalowa?".

"Uhhm ai wannan karon ba ita ta jangwalo ba ita aka jangwalowa. Ni Ashwaq naga
abinda zai kasheni a wannan masarautar yau da raina. Wai kin san kuwa madarar da
aka shayar da dakinki wai Miran Jasim ne ya samar da ita".

"What!"

Daneen Waheeda ta fada cikin zabura da ga fasa zaman da tai niyyar yi da ga can.
"Wait! Wait wait Ashwaq wai nikam mi kike son fada minne haka. Jasim Akhi namu kike
nufi yake shirin kashe Eshaan din komi? Ni Wihy gaba daya ma kin rikitamin
lissafi".

"Bake lissafinki ke a rikice ba, ai kowa ma yau a masarautar nan lissafinsa a


rikice yake wallahi.

Tiryan-tiryan ta kwashe komai na zaman kotu a yau ta fada mata kamar yanda ta saba
kai mata gulmar duk wani motsin yan masarautar musamman Malikat Bushirat. Wani irin
irin tashin hankali Daneen Waheeda ta shiga tana zungura manya-manyan zagi dan ita
dama can mace ce masifaffiya mai zafin tsiya. A wani lokutan akance tafi kowa gado
mahaifinsu a kaf yayan Tajwar Abdul-majeed. Daga can ta ce, "Gobe ki tsumayi zuwana
RUMAN yar uwa wannan dambarwar ba'ayita babu ni kusa ba. Amma karki fadama kosu
Mammah. Shin yaya bakar dagarki tayi ne za'a kashe mata tilon dan gwal din ta da
take hura muku hanci".

"Uhm-iuhm ai labarin kam dai babu dadin ji, amma tunda kince kina tafe ke dai
kwantar min da hankalinki sai kin iso kawai".

"Okay bara kiga naje na fara shiri ma tun yanzu. Amma da mutuniyarki zan taho dan
wannan karon kam inaga sai na nunama Eshaan kwanji akan Iftihal dan ko yaki ko yaso
sai ya aureta tunda dai matan sun daina mutuwar".

"Ina tare da ke dari bisa dari kuwa. ALLAH ya kawo ku lafiya".

Da ga haka sukai sallama Malikat Ashwag na faman sakin murmushi, dan itafa ranta
fari kal da abinda ya faru a yau din.
(Ina fatan kun gane matsayin Daneen Waheeda dai. Itace kanwa ga Daneen Ammarah da
Tajwar Haysam mahaifin Tajwar Eshaar ta uku ga Malikat Haseenat da mukace tana aure
acan yankin larabawa. Kawace sosai ga Malikat Ashwaq, kuma yar uwa, dan kusan ma
itace tai ruwa tai tsaki wajen gain Malikat Ashwag din ta auri Tajwar Haysam duk da
shima dai ya sota a karan kansa. Tare sukai karatu dan haka akwai shakuwa mai karfi
a tsakaninsu da har take tayata kishin Malikat Bushirat. A duk sanda ta sami wani
sabon labari musamman akan koma bayan Malikat Bushirat sauri take taga ta sanar ma
Daneen Waheeda. Shiyyasa a randa hadimanta sukazo mata da bayanin Malikat Bushirat
taje wajen Malikat Haseenat akan kara auren Tajwar Eshaan tai azamar kiranta ta
sanar mata dan tasan babban burin Daneen Waheeda din shine hada auren babbar
diyarta da Tajwar Eshaan da suke kusan sa'anni. Ta matukar mutuwa a kansa amma shi
ko kallo bata ishesa ba. Hakan yasa ita Daneen Waheeda din taso a hada auren amma
Malikat Bushirat taki bada hadin kai. Dan ta fahimci so Daneen Waheeda keyi Tajwar
Eshaan ya auri yarta su koma juya akalarsa data mulkin kasar ruman din. Ga kuma
sharadin da UWA ta gindaya mata na karta yarda Tajwar Eshaan ya auri wata da ga
cikin zuri'ar masarautar sam. Yin hakan gagarumin abune da zai rusa komai da yake
komai a hanunsu. @) ALLAH yasa kun gane)

Dan daburcewa uwa taso yi, dan bata so akazo wannan gabar da wuri haka batare data
Karmala shirinta ba. Anya kuwa batayi babban sakaci akan ta-kurya ba. Itama fa
itace tsanin cikar nata burin data dauki tsawon shekaru tana bi matakala-matalaka
domin maida murtani ga ahalin wanna masarauta baki daya.…... Ganin irin kallon da
ta-kurya ke mata ne ya sata hadiye komai ta dai-daita yanayinta. Fuskarta ta sake
tsukewa da gyara zaman kasaitarta. "Ta-kurya ban boye miki domin wani dalili ba,
sai dan kareki da ga shagala kan al'amarin sa, amma ki sani na jima biye da Jasim
da hana makircinsa tasiri kan Ajlaan. Shin bakiyi mamaki ba ne yau? Bakiyi mamakin
faruwar abinda ya faru din ba ne? To bari na kaiki inda baki sani ba. Nice nan da
kaina na budewa Jasim aiki yau, kuma na fara ne tun a randa ya kai kayan asiri
fadar Ajlaan. Ban miki maganar bane ba dan ina son sai an kai karshe. Kuma duk
abinda ya farun yau a kotu nima ina tare da ku".

Wata irin wawuyar ajiyar zuciya Malikat Bushirat ta sauke. Gaba daya sai taji
abinda ya tsaya matan a makoshi ya fada a cikin cikinta.Dari bisa dari ta yarda da
zancen uwa, dan bata taba mata karya ba (hummmm). Fuskarta dauke da murmushi ta
sake gurfana a gabanta. "Yanzu kam na fahimta, na fahimci komai uwa. Dama ni nasan
bazaki bari na fadì ba. Amma naso ace kin sanar min tuni, da sai na daidaita rayuwa
jasim,sai na kafa tarihi akansa irin wanda harara wani bazai sake kwatantawa ga
Saiful- malik dina ba a wanna masarautar"

Wani irin shegen dariya uwa ta kwashe da shi."K yar halak ce ta-kurya, shiyyasa
nake sonki fiye da duk wanda ya kasance a karkashin baiwata. Na miki alkawarin
bazaki sake yin kuka ba, zan cigaba da tsaya miki fiye da tsayawar da nai miki a
baya. Zan cigaba da kare Ajlaan fiye da kariyar da kike tunanin yana da
(Wa"iyazubillah. Ya rabba ka tsaremu da aikata shirka koda a cikin duhun jahilci ne
@ A). Zan baki mamaki, tabbas zan baki mamaki ta-kurya".

"A kullum cikin bani mamaki kike ai uwa, shiyyasa bazan gaji da fada ba, bazan gaji
da maimaitawa ba ke ta dabance a cikin daban".

"Hhahahahahaha!!!!!!!".

Uwa ta kyalkyale da wata irin mahaukaciyar dariya har ta-kuryar najin sautinta
cikin iska, kai kace gaba daya masarautar koma kasar ruman dinne baki daya zasu
jita.

(Uhm uhm da alamafa akwai wani kulli tare da Uwa, ko minene shi@? Muje dai zuwa
sannu sannu ai bata hana zuwan sai dai a dade ba'a je ba)

A wani bala' in firgice ta farka da ga barcin da ya figeta bayan idar da sallar


azhar. Kanta dake wani irin sara mata ta dafe tana ambaton sunan ALLAH. Ta kai
tsahon minti uku a haka kafin ta mike daga saman sallayar da anan barcin ya
kwasheta. Gaba daya jikinta tsuma yake, yayinda zuciyarta ke mata tariyar mafarkin
nata dalla-dalla. Jin jiri na neman zubdata kasa tai saurin zubewa bakin gado tana
sake dafe kai. A hankali ta furta, "Uwa!! Wacece ita? Ta ina zan fara bincike
saninta",. Kantane ya sake sara mata, tunda take mafarke-mafarkenta bata taba mai
nauyi irin wannan ba. Duk da bataga fuskar wadda ke zaune a kujerar karfen nan ba
zagaye da wasu irin munanan halittu taji a ranta dole ta kasance abar toro. Sai
kuma gain Malikat Bushirat da tai a gabanta dirkushe, shin minene hadin Malikat din
da wadan nan munanan hallitun? Tajwar Eshaan a gefe daddaure da wasu irin igiyoyi
wuta, sai dai shima bata ganin fuskarsa amma tana iya jin yanda yake ambaton
sunayen ALLAH radam.

"What's wrong..

Dagowa tai da sauri dan sam bata san da shigowarsa cikin dakin ba, hasalima bata
san ya dawo ba. Idanunta data kafeshi da su ta dan janye tana kara tsarkake sunan
UBANGIJI mahaliccin wannan bawa. Komai nasa mai kyau ne da birgewa. Hatta kayan
zaman gida dan ya saka badan kwalliya ba sai su fidda cikar kamalarsa da zati.

"Kaina ke ciwo".

Ta fada kanta a kasa dan kallon nan nasa na kasa-kasa da ke daburta mata lissafi
bata son shi. (Aljanun sunzo kenan) ya fada a zuciyarsa yana wani dan yamutsa
fuska. A zahiri kam baice komai ba ya dai cigaba da kallonta. Kusan minti daya
sannan ya motsa da cigaba da takawa a hankali cike da kasaitar nan tasa. A gabanta
yaja ya tsaya, tare da zare hannunsa dake cikin aljihun wandon jeans dinsa ya mika
mata. Idanunta ta dago ta kalli hannun da ke fari tas da shi, ga jini nata kaikawo
a tafin kamar ba namiji ba. Idanunsa ya dan lumshe da budewa a lokaci guda yana
gyada mata kai alamar ta daura nata. Kamar mai jin tsoron hakan ta dago natan ta
dora a cikin nasan. Sake lumshe idanun vavi kamar wani wanda maganadisu va taba.
din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi da mai basa amsa baya kuma bukatar
sonji gareta yanzu dan ransa duk babu dadi yake ji. Itama da kanta ta fahimci
hakan, dan fuskarsa a tsuke take fiye da sanda suka fita kotun. Sai duk take jin
kuma babu dadi. Dan haka kawai take jin tausayinsa. Idan har zai shiga damuwa
saboda halin wancan karen uncle din nasa, yaya zai kasance kuma a randa zai san
mahaifiyarsada kanta ke halaka masa matan aurensa da duniya ke kallonsa a mai
halakasu tsahon shekaru. Kai kai wannan al'amarin fa na taba mata zuciya why sosai
matuka. Ajiyar zuciya ta dan sauke a hankali, sai kuma ta kai hanunta saman
lallausan gashin sajen fuskarsa ta shafa. Murya can ciki ta ce, "Kayi hakuri? Ka
amsa da hannu biyu jarabawace. Badan UBANGIJI baya sonka ba ya jarabeka da su. Shi
kansa mulkin ma da kake kai ai jarabawa ce. Kai numfashinmu ma kansa jarabawace a
garemu, dan UBANGIJI ya azurtamu da shine domin yaga zamu kasance masu bin
dokokinsa ne ko kuwa masu bijire masa".

Idanunsa da ke lumshe tun sanda ta daura hanunta saman fuskarsa ya bude a


hankali,sunyi zajur fiye da yanda ya shigo da su a dan birkice. Hannun ya kamo yana
kallonta, cikin tsananin kasala ya daura lips dinsa a tsakkiyar tafin ya sumbata.
Sai da ta matse jikinta tsabar vanda lininta vAv wata irin vamuitsawa har cikin
fara son kwatar kanta. Sai dai kuma babu hanyar samun wanna damar da ga jarum Shin
yaya lafiyar giwa da ma. Balle kuma ita da kanta ta balle likin.

Duk yanda taso tuna masa dinkin dake a tare da ita babu alamar yana ma iya
jinta balle fahimta. Burinsa kawai yake kokarin cimmawa a cikin rufewar idanu..

(* Tsun-tsun da ya ja ruwa (?))


***

Da karfi, karfin karfi yake buga kansa a bangon dakin kurkukun mai tsananin duhu da
ta iya karamin windown kawai ake iya gain dan ziririn haske. Gaba daya zuciyarsa ta
bushe, zafi
yakeji a cikinta mai tsananin tururi dake kona zuciya. Shi shi Jasim ibn Abdul-
majeed Aliy Qutb ne wata karamar yar iskar yarinya yar cikin cikinsa tai sanadin
kawowa cikin kurkuku. Shi Arshaan da ya koya sanin kansa a wajensa zai yima cin
amana? Shi hadiminsa da ya dauka tsahon shekaru yana kyautatama zaici amanarsa a
gaban makiyansa. Wace irin wannan, mai tsananin duhuwa da babu lissafinta a cikin
duka lissafe-lissafensa. Ta yaya shi Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb zai yi irin
wannan faduwar bakar tasan a gaban karfin ikon dan makiyansa kuma makiyinsa.

Cigaba da buga kan yake da karfinsa yana ihu mai tsananin karaji da ya saka masu
tsaron dakun kurkukun nasa da Tajwar Eshaan ya bada umarnin bama tsar mai tsananin
tsauri tsora. Cikin karfin hali daya a cikinsu ya dan leko, ta dan hasken da ya
hasko da ga karamin windown ya hango fuskar Miran Jasim da tai wani irin jage-jage
da jini dan ya fasa goshinsa. A zabire yay baya yana zazzaro idanu. Yan uwansa ya
sanarma, babu bata lokaci sukai kiran shugaban jami'ai suka sanar masa dai-dai da
yanke jikin Miran Jasim da jini ke rinjayarsa va fadi kasa....

Rungumeta yay tsam-tsam a cikin jikinsa idanunsa a lumshe. Jin kukanta yake har
tsakkiyar zuciyarsa. Dan kuka take sosai five a daren shekara jiya kasancewar yau
fami yay akan ciwo.

"Ni ka kaini wajensu Ummu".


Ta fada cikin kuka. Yanda tai magana tana sake barke masa da kuka ga hawaye shabe-
shabe harda su majina ya sa yaji dariya na yunkuro masa. Kamar ba yanzu ta gama
iyayi a kotu ba,dan duk abinda ta dingama Miran Jasim akan idonsa ne tsaf. Amma
jiba yanzu a dan abinda bai taka kara ya karya ba ta koma abin tausayi.Ya fahimci
sai ya dage matukar dagewa akan dorata a irin layin da yake bukata ta hau inba
hakaba ragguwa za'ai, bakinne kawai cike da zance da tsiwa. Bashi da burin sake
wani auren bayan ita, dan haka dolene ta shirya karbarsa a duk sanda yazo.
Murmushin da ke neman kufce masan ya hadiye da kyar da saka hannu yana goge mata
fuskar data kwabe da hawaye. Cikin dadisashiyar muryarsa data kara komawa can kasan
makoshi a fusge ya furta, "Am sorry bazan kara ba".

"Why zaka kara, ranar ba sai da kace bazaka sake ba amma yau ka kara, ni bazan sake
zama a sashen na a kasheni kwana na bai kare ba". Ta kara barke ma sa da kukan
tabara.

Yanzu kam kasa rike dariyar yayi, dole ya Murmusa har jerarrun fararen hakwaransa
masu è da siririyar wushirya na bayyana Bashi da zabin da ya wuce sake rungumeta a
jkinsa tsam-tsam yay murmushinsa iya san ransa. (Shi kam wannan Fitinanniyar
yarinya ALLAH ya bashi, kuma yana so da kaunar abinsa fiye da zaton mai hasashe). A
zuciyarsa yake maganar yana bata sumbata masu kyau a wuya. Kafin ya mike ya dagata
cak zuwa bathroom. Idanunta ta rumtse sosai da kankamesa ita a dole karya gammata
jiki kar kuma ta gansa itama.

Gashi yay mata mai kyau bayan ya duba yau baiyi barna ba dan ciwukan wancan ranar
ma sun warke sai abinda ba'a rasa ba, taimaka mata yay tai wanka, hawaye kuwa da ya
ga ba dainawa zatai ba bai sake ce mata komai ba kansu. Da zasu fito cewa tai ita
why bazata iya ba sai dai ya dauke ta. Baice komai ba, illa murmushi da yay a
zuciyarsa ya dauke ta cak suka fito tana faman tura masa karamin bakinta.Ga idanu
sunyi luhu-luhu na kukan da tasha.

"Idan baki bar turamin bakin nan ba zan maimaita ni babu ruwana". Ya fada yana
tsane mata laimar ruwan kanta da towel. Narai-narai tai da fuska zata sake masa
kuka ya daura yatsansa saman bakinta ya ce, "Shilli!! Harda kuka ma". Babu shiri ta
hadiye abunta da maida bakin da sauri.Murmushi ya saki ya cigaba,Da tsane mata mata
gashin…. kiran da ya shigo ta sashi dakatawa su duka suka dubi wayar, kamar bazai
daga ba dan har tana gab da tsinkewa sai kuma ya kai hannu ya dauka batare daya
matsa da ga gabanta ba ko dauke towel din da ga kanta.

Cikin girmamawa shugaban jami'ai ya shiga gaishesa da ga can, a takaice ya amsa


masa murya a dake kamar bashine ke hidimtawa yar yarinya ba. Da ga can shugaban
jami'ai ya kara nutsuwa sannan yay masa bayanin abinda ke faruwa. Shiru kamar
bazaice komai ba kafin ya nisa a dan fisge da maganar nan tasa kasa-kasa ya ce,
"Doctor Afif ya je ya dubasa a cikin kurkukun". Daga haka ya yanke kiran.

Kallonsa Iffah tai da jajayen idanunta, gaba daya ya sauya kamar bashi ba ya
koma mata Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed da ta fara gani a sashen Mammah.
Muryarta a dashe saboda kukan da tasha ta ce, "Miya faru?".Kamar bazai kulata ba
yana cigaba da goge mata kan tsahon minti biyu kafin ya motsa lips da kyar ya furta
"Jasim"……………✍️

DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 57

"Kinci abinci?".

Kanta ta girgiza masa alamar a'a.

"Mi yasa?".
"Banajin yunwa ne".

Shiru bai sake cewa komai ba har kusan minti daya. Hannunsa da ke kan bayanta ya
dago ya daura saman goshinta data kwantar jikinsa, kan da zafi sosai har ma yana
iya jinsa.

"Na miki addu'a?".

Nan ma kan ta daga masa. Komai bai sake cewa ba shima. Sai matsawa da su da yay
zuwa gadon, tana a jikin nasa ya kai zaune itama ya zaunar da ita a cinyarsa.
Addu'a ya fara mata a kan idanunta a lumshe, bayan ya kammala ta kwantar da kanta a
kafadarsa tai luff tana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Nan ma sun jima a zaman
shiru kafin ya kirata muryarsa a can kasan makoshi.

"Mrs Eshaan?".

"Uhmyim".

Ta amsa itama can kasa batare data dago kanta da ke a kafadarsa ba.

"Miyasa kika boye min?".

Bata fahimci mi yake nufi ba, dan haka ta dago idanunta da jan cikinsu ke dan
raguwa a hankali ta zuba masa. Bazata iya jurar kallonsa cikin ido ba dan haka ta
dauke su ta maida gefe. "Ban san akan mi kake magana ba Sultan". Sai da ya dan
furzar da hucin baci ran da yake ta dannewa, a dan fuse ya furta, "Jasim!
Miyasa kika boyen ya sameki a kurkuku da maganar banza?"

Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta motsa cikin sauke ajiyar zuciya ta ce,
"Kayi hakuri, a lokacin ban san ta yanda zan tunkareka ba. Ban kuma san ta yanda
zaka fahimceni ba. Kuma ai ALLAH ya kareni da ga sharrinsa tunda ga shi yau gaskiya
tayi halinta".

Shiru baice komai ba, dan zuciyarsa tafasar kishi take har yanzu akan wanna kalmar,
tafi komai tsaya masa a zuciya fiye da abinda Miran Jasim din ya aikata masa dan ya
jima da sanin dama suna farautar rayuwarsa. Sai maganar rashin fitowar sunan Miran
Arshaan shima na masa kaikawo, kamar zai mata magana akan hakan sai kuma dai ya
hadiye kayansa da tunanin ko Miran Jasim din ne kawai ya fiddo mata da nasa hali.
Amma in bai manta ba ranar a kalamanta ta masa nuni ne da mutane biyu ko yace fiye
da daya. Hakan na nufin bayan Jasim din akwai wani kenan. To miyasa ta boye? Bashi
da mai basa amsa baya kuma bukatar son ji da gareta yanzu dan ransa duk babu dadi
yake ji.Itama da kanta ta fahimci hakan, dan fuskarsa a tsuke take fiye da sanda
suka fita kotun. Sai duk take jin kuma babu dadi. Dan haka kawai take jin
tausayinsa. Idan har zai shiga damuwa saboda halin wancan karen uncle din nasa,
yaya zai kasance kuma a randa zai san mahaifiyarsa da kanta ke halaka masa matan
aurensa da duniya ke kallonsa a mai halakasu tsahon shekaru. Kai kai wannan
al'amarin fa na taba mata zuciya why sosai matuka. Ajiyar zuciya ta dan sauke a
hankali, sai kuma ta kai hanunta saman lallausan gashin sajen fuskarsa ta shafa.
Murya can ciki ta ce, "Kayi hakuri? Ka amsa da hannu biyu jarabawace. Badan
UBANGIJI baya sonka ba ya jarabeka da su. Shi kansa mulkin ma da kake kai ai
jarabawa ce. Kai numfashinmu ma kansa jarabawace a garemu, dan UBANGIJI ya azurtamu
da shine domin yaga zamu kasance masu bin dokokinsa ne ko kuwa masu bijire masa".

Idanunsa da ke lumshe tun sanda ta daura hanunta saman fuskarsa ya bude a hankali,
sunyi zajur fiye da yanda ya shigo da su a dan birkice. Hannun ya kamo yana
kallonta, cikin tsananin kasala ya daura lips dinsa a tsakkiyar tafin ya sumbata.
Sai da ta matse jikinta tsabar la jininta yay wata irin yamutsawa har brain.
Yunkurawa tai da nufin tashi a jikinsa ya hanata hakan, sai ma fuskarta da ya kamo
cikin tafukan hannunsa ya manne lips dinsu waje guda. A tare suka saki ajiyar
zuciya Iffah na rumtse idanu da karfi. A tsorace take matuka,amma ta danne ta
karfin tsiya domin taimaka masa ya samu nutsuwar zuciya kamar yanda Mammy ta mata
nasiha akan a duk sanda taga ya shigo da fushi tai kokarin gain ta cire masa wannan
fushin da damuwar ta hanyar jansa jikinta da hira da raha ko nasiha. Idan kuma ya
nuna bukatar wata hidimtawarta ko ita ta fahimci akwai abinda ke sakashi shagala ko
kwaranyewar damuwarsa da wuri to tazama jaruma wajen aikatawa kota bashi hadin kai.
Tunanin a iya abinda yake yi din baza'ai gaba ba ya sata sakar masa jiki harta fara
bashi hadin kai. Gaba daya ta sake rikita masa lissafi, dan abune da bai zaton samu
da ga gareta ba anan kusa haka. Tuni idanunsa sun rufe ya juyesu a gadon ya shiga
yamutsata yanda yake so cikin nutsuwarsa, dan a rayuwa komai na Tajwar Eshaan babu
gaggawa a ciki, koda kuwa yana a wani yanayi ne da zai iya canjawa sai kaga a
zahirance babu wanna canjin a gaggawa garesa. Dan nutsuwa da kasaita a jinin
jikinsa take yawo da harbawar bugun zuciyarsa. Jin al'amarin ya fara zarce karamin
tunaninta tuni ta fara son kwatar kanta. Sai dai kuma babu hanyar samun wanna damar
da ga jarumin ,Shin yaya lafiyar giwa da ma. Balle kuma ita da kanta ta balle
likin. Duk yanda taso tuna masa dinkin dake a tare da ita babu alamar yana ma iya
jinta balle fahimta. Burinsa kawai yake kokarin cimmawa a cikin rufewar idanu..

(* Tsun-tsun da ya ja ruwa (?))

***

Da karfi, karfin karfi yake buga kansa a bangon dakin kurkukun mai tsananin duhu da
ta iya karamin windown kawai ake iya gain dan ziririn haske. Gaba daya zuciyarsa ta
bushe, zafi
yakeji a cikinta mai tsananin tururi dake kona zuciya. Shi shi Jasim ibn Abdul-
majeed Aliy Qutb ne wata karamar yar iskar yarinya yar cikin cikinsa tai sanadin
kawowa cikin kurkuku. Shi Arshaan da ya koya sanin kansa a wajensa zai yima cin
amana? Shi hadiminsa da ya dauka tsahon shekaru yana kyautatama zai ci Amanarsa a
gaban makiyansa. Wace irin wannan, mai tsananin duhuwa da babu lissafinta a cikin
duka lissafe-lissafensa. Ta yaya shi Jasim in Abdul-majeed Aliy Qutb zai yi irin
wannan faduwar bakar tasan a gaban karfin ikon dan makiyansa kuma makiyinsa.

Cigaba da buga kan yake da karfinsa yana ihu mai tsananin karaji da ya saka masu
tsaron dakun kurkukun nasa da Tajwar Eshaan ya bada umarnin bama tsar mai tsananin
tsauri tsora.Cikin karfin hali daya a cikinsu ya dan leko, ta dan hasken da ya
hasko da ga karamin windown ya hango fuskar Miran Jasim da tai wani irin jage-jage
da jini dan ya fasa goshinsa.A zabire yay baya yana zazzaro idanu. Yan uwansa ya
sanarma, babu bata lokaci sukai kiran shugaban jami'ai suka sanar masa dai-dai da
yanke jikin Miran Jasim da jini ke rinjayarsa va fadi kasa....
Rungumeta yay tsam-tsam a cikin jikinsa idanunsa a lumshe. Jin kukanta yake har
tsakkiyar zuciyarsa. Dan kuka take sosai fiye dana daren shekara jiya kasancewar
yau fami yay akan ciwo.

"Ni ka kaini wajensu Ummu".

Ta fada cikin kuka. Yanda tai magana tana sake barke masa da kuka ga hawaye shabe-
shabe harda su majina ya sa yaji dariya na yunkuro masa. Kamar ba yanzu ta gama
iyayi a kotu ba,dan duk abinda ta dingama Miran Jasim akan idonsa ne tsaf. Amma
jiba yanzu a dan abinda bai taka kara ya karya ba ta koma abin tausayi.Ya fahimci
sai ya dage matukar dagewa akan dorata a irin layin da yake bukata ta hau inba
hakaba ragguwa za'ai, bakinne kawai cike da zance da tsiwa. Bashi da burin sake
wani auren bayan ita, dan haka dolene ta shirya karbarsa a duk sanda yazo.
Murmushin da ke neman kufce masan ya hadiye da kyar da saka hannu yana goge mata
fuskar data kwabe da hawaye. Cikin dadisashiyar muryarsa data kara komawa can kasan
makoshi a fusge ya furta, "Am sorrybazan kara ba".

"Wlhy zaka kara, ranar ba sai da kace bazaka sake ba amma yau ka kara, ni bazan
sake zama a sashen na a kasheni kwana na bai kare ba". Ta kara barke ma sa da kukan
tabara.

Yanzu kam kasa rike dariyar yayi, dole ya Murmusa har jerarrun fararen hakwaransa
masu da siririyar wushirya na bayyana a zahiri Bashi da zabin da ya wuce sake
rungumeta a jkinsa tsam-tsam yay murmushinsa iya san ransa. (Shi kam wannan
Fitinanniyar yarinya ALLAH ya bashi, kuma yana so da kaunar abinsa fiye da zaton
mai hasashe). A zuciyarsa
yake maganar yana bata sumbata masu kyau a wuya. Kafin ya mike ya dagata cak zuwa
bathroom. Idanunta ta rumtse sosai da kankamesa ita a dole karya gammata jiki kar
kuma ta gansa itama.

Gashi yay mata mai kyau bayan ya duba yau baiyi barna ba dan ciwukan wancan ranar
ma sun warke sai abinda ba'a rasa ba, taimaka mata yay tai wanka, hawaye kuwa da ya
ga ba dainawa zatai ba bai sake ce mata komai ba kansu. Da zasu fito cewa tai ita
why bazata iya ba sai dai ya dauke ta. Baice komai ba, illa murmushi da yay a
zuciyarsa ya dauke ta cak suka fito tana faman tura masa karamin bakinta.Ga idanu
sunyi luhu-luhu na kukan da tasha.

"Idan baki bar turamin bakin nan ba zan maimaita ni babu ruwana". Ya fada yana
tsane mata laimar ruwan kanta da towel. Narai-narai tai da fuska zata sake masa
kuka ya daura yatsansa saman bakinta ya ce, "Shilli!! Harda kuka ma". Babu shiri ta
hadiye abunta da maida bakin da sauri. Murmushi ya saki da cigaba da tsane mata
gashin…. kiran da ya shigo ta sashi dakatawa su duka suka dubi wayar, kamar bazai
daga ba dan har tana gab da tsinkewa sai kuma ya kai hannu ya dauka batare daya
matsa da ga gabanta ba ko dauke towel din da ga kanta.

Cikin girmamawa shugaban jami'ai ya shiga gaishesa da ga can, a takaice ya amsa


masa murya a dake kamar bashine ke hidimtawa yar yarinya ba. Da ga can shugaban
jami'ai ya kara nutsuwa sannan yay masa bayanin abinda ke faruwa. Shiru kamar
bazaice komai ba kafin ya nisa a dan fisge da maganar nan tasa kasa-kasa ya ce,
"Doctor Afif ya je ya dubasa a cikin kurkukun". Daga haka ya yanke kiran.

Kallonsa Iffah tai da jajayen idanunta, gaba daya ya sauya kamar bashi ba ya
koma mata Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed da ta fara gani a sashen Mammah.
Muryarta a dashe saboda kukan da tasha ta ce, "Miya faru?".Kamar bazai kulata ba
yana cigaba da goge mata kan tsahon minti biyu kafin ya motsa lips da kyar ya furta
"Jasim"……….✍️
DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 58

Bayan sallar isha'i cikin dauriya Iffah ta amsa kiran Malikat Haseenat. Tafiya take
cikin dabara dan ko yau din ma dai tanajin zafin, ga zazzabi tun dazu yaki saukar
mata. Ita bata san randa zatai sabo da wannan al'amari ba kamar yanda ya fada mata
dazun. Ta dan yamutse fuska da cigaba da tafiyarta a hankali, dan ita kadai ta fito
babu wani dan rakkiya, Tajwar Eshaan ma yana massalaci tunda ya tafi sallar magrib
bai shigo ba. Kadan-kadan take dan cin karo da hadimai, duk da ko'ina na masarautar
zagaye yake da haske ba ganeta suke ba, sai dai yanayin shigarta kansa su mata
gaisuwar girmamawa kamar yanda suke ma duk wani ahalin masarautar babba ko yaro.
Hannu ta dinga daga musu kawai dan batajin yin magana har takai sashen Malikat
Haseenat din. Nan din ma bawani sun ganeta bane sosai, dan sanda take kokarin shiga
falon Malikat Haseenat din da sauri Banou tai niyyar dakatar da ita. Sai dai mi,
kallon ido cikin ido da sukai ma juna ya sa Hadima Banou din zubewa kasa cikin
rawar jiki da tsananin kaduwa. Har taune harshe take wajen gaida Iffah da ke mata
kallon tsaf kamar mai son gano ainahinta. Sai da ta mula dan kanta ta yamutsa fuska
da watsa mata harara. "K! Har yanzu baki daina bibiyar mutane ba ko?Karki fasa ina
tafe kanki ai". Ta fada tana wuceta batare data amsa gaisuwar tata ba.

Jagwab Hadima Banou ta zube zaune a wajen zuciyarta na wani irin masifar
harbawa. Sosai take tsoron wannan baiwar ALLAH, dan ita kadai tasan mi take ganowa
tattare da ita. Ta jima a wajen kafin ta mike cikin rawar jiki ta fita. Can baya ta
nufa cikin karamin garden din Malikat Haseenat da takan hutawa, da ga cikin wasu
dunkulallun fulawoyi ta zaro yar tukunyar kasa da bakinta ke daure da kyalla an
nannade da zare. Warware zaren tai har yanzu jikinta na rawa, abubuwane a daddaure
ciki kamar tsokokin nama, haka ta shiga fiddosu tana ware wasu a kasa, sai da ta
gama zabowa ta maida sauran ta sake daurewa ta ajiye. Wanda ta fiddo din kam ta
kwance hudu ta sakesu, biyu da ga ciki tasa a baki ta cinye tana faman tande lips.
Duk abinda take yi tanayi ne tana waige-waige, har dai ta kammala ta mike da sauri
ta fito..

Tarba ta mutuntawa Iffah ta samu da ga Malikat Haseenat. Dan an shiryama zuwan nata
da zuwa na musamman kamar yanda akan yima Tajwar Eshaan idan zai zo. Iffah har
mamakin hakan tayi, dan bata taba tunani ko tsammanin tanada kimar da wani zai mata
haka musamman idan akai dubi da shekarunta da kuma gidan data fito na talakawa.
Malikat Haseenat dame binta da Kallo kuwa a kallo daya da taima takunta ta fahimci
halin da Iffah take, idanu ta dan lumshe tana mai jin tausayinta, dama tasan bazai
iya hakurin barinta ta warke yanda suke bukata ba ai, dole ne sai ta dage ma
yarinyar da abubuwan da zasu taimaka mata batare data dinga jigata ba. A zahiri kam
hannu ta ware mata alamar tazo gareta. Iffah da ke murmushi kanta a kasa ta karasa
a nutse ta ko shige jikin nata. Wata irin tagwayen ajiyar zuciya ta dinga saukewa a
jajjere haka itama Malikat Haseenat din. Kusan minti biyu suna a haka kafin ta
zaunar da ita kusa da ita gab-gab dan har cikin rai take jin kaunar yarinyar nan.

Duk yanda Iffah ta dinga nuna jin kunya Malikat Haseenat bata barta ba sai da
sukaci suka sha a tare cike da farin ciki, suna tsaka da cin abinci ne ma Daneen
Ammarah itama ta shigo. Cike da girmamawa Iffah ta gaisheta, ta amsa mata da kulawa
cike da so da kauna. Bayan sun kammala hadimai suka gyara wajen, Malikat Haseenat
kuma ta bama Iffah wata yar madara a kofi mai dadin tsiya data kasa gane ma wace
irin madara ce, dan an mata wasu hadi ne na musamman. Dagawa daya ta shanye ta
ajiye kofin, karamin bowl dake dauke da hadadden hadin zuma da dabino da kwa-kwa
dama abubuwan da bata sani ba nan ma ta bata tare da karamin cokali a ciki da zata
dinga diba kadan-kadan tana ci.

"Hafidah!"
Malikat Haseenat ta kirata a hankali. Amsawa Iffah tai kanta a kasa. Mammah bata
damu ba ta cigaba da fadin, "Kin san miyasa nace kizo ki sameni?". Kai Iffah ta
girgiza mata ta ce, "A'a Jaddah"., Malikat Haseenat ta kalla Daneen Ammarah suka
dan sakarma juna murmushi kafin ta sake maidawa kan Iffah. "Magana nake so muyi mai
muhimmanci dan nasan bazakimin karya ba".

"Insha ALLAHU Jaddah".

"'Dazun a zaman shari'ar can kinyi wata magana ce data kasa barin raina akan
ganin gawar Zawjata-almilk da kikai. Shin ko akwai wasu alamomi da kika gani
tattare da ita? Ko kuwa kisa ne kawai na kai tsaye da raunika?"

Shiru Iffah tai da dan mamakin tambayar a ranta, ta kasa gane wann al'amarin,
shi mai matan yace bai taba ganinsu ba, bayanan suke mutuwa, kuma ko gawarsu baya
gani. Shin itama Jaddah din du matsayinta a masarautar bata taba gain gawarsu kenan
amma har wadan can rubabbun su Jasim ke iya gani ko mi?

''Ibnati"

Daneen Ammarah ta katse mata tunani. Firgigit ta kawo numfashi da kallonsu, sai
kuma ta maida kanta ta risinar tana mai sauke ajiyar zuciya. "Jaddah zan fada miki
duk abinda kike bukatar j, amma dan ALLAH ki gafarceni nima zanyi wat tambaya".

"Bismillah".

Malikat Haseenat ta fada kai tsaye cikin bata dama. Numfashi Iffah ta dan fesar ta
nisa. Kafin tace, "Jaddah na kasa ganewa, shin duk matansa da suka rasu kuma baku
taba ganin gawarsu ba kamar yanda shima yace bai taba gani ba kenan?".

Daga Malikat Haseenat har Daneen Ammarah kallon Iffah suke mamaki fes a kan
fuskokinsu. Daneen Ammarah ta ce, "Shi Abni din ya fada miki bai taba ganin gawar
matansa ba?".

"Har suna raye bai taba ganinsu ba ma yace".

Kallon juna Daneen Ammarah da Mammah sukayi, sai kuma duk suka dubi Iffah da
itama su take kallo ta gefen ido. "Tofa babbar magana".Cewar Malikat Haseenat.
Daneen Ammarah ta ce, "Babbar magana kam, ta gaske ma Mammah. Ni kaina ma ya sake
kullewa akan Al’amurin”.

"Dole ne kam Ammarah. Amma Hafida-ti bara na baki amsar tambayarki, masarautar nan
nada tsare-tsare irin nata da ka'idoji, a ciki harda zama iya huruminka, dan haka
ni bana a cikin masu hurumin kan duk abinda ya shafi Zawjata- almilk na Hafidi,
wannan hakkin mahaifinsa ce, ni kuma nawa hakkin a kansu yake tunda sune matan
dana. Wannan ne dalilin da yasa ban taba gani ba. Kema da kike ganina tsaye a kanki
saboda matsalolin da aka samu ne da har yasa ita Bushirat janyewa da ga al'amuran
ki, ni kuma naga bazan iya yardawa ba na dauka na adana".

Cike da gamsuwa Iffah ta jinjina kanta. Sai kuma ta cigaba da basu bayani akan
abinda suke bukata. Riko hanunta Daneen Ammarah tai kamar a razane ta ce, , "Cizon
maciji kuma?". Cike
da mamakin yanda suka razana Iffah ta gyada mata kai. "Eh Mamy saran maciji. Sai
dai da alama kafin ma hakan tayi yunkurin kare kanta da har ya zamto dakin ya
kasance a harmutse".

"Ya rabba! Uwa. Mammah tabbas wannan alama ne na UWA. Itace, itace azzalumar bata
barmu ba. Bata barmuba Mammah, tana raye why tana raye". Daneen Ammarah ta fada
tana rike kanta da ke mata wani irin sarawa ta fara layi kamar zata fadi. Da sauri
Iffah ta mike ta riketa cikin tashin hankali. Hakam Malikat haseenat duk ta rikice,
dan ta fahimci ma tsahon shekaru data shude ce da ga garesu ke neman dawowa ga
Ammarah din kanta. Da kyar suka iya samu suka kwantar da ita, a tare suka dinga
tofa mata addu'oi. sannu a hankali ta fara lafawa tana sauke ajiyar zuciya a
jajjere sai kuma barci ya dauke ta mai nauyi.Ajiyar zuciya Malikat Haseenat ta
shiga saukewa da sauri- sauri, yayinda Iffah sunan uwa da Daneen Ammarah ta ambata
ke faman mata kaikawo kirjinta na wata irin bugawa..

"Jaddah waye UWA kuma?".

Kalmar ta subuto da ga bakin Iffah batare da ta shirya hakan ba. Idanu kawai
Malikat Haseenat ta zubama Iffah batare da tace komai ba. Har Iffah ma ta fidda rai
da ga cewarta. Dan tsahon kusan mintuna biyar kafin Malikat Haseenat din ta nisa.
"Uwa. Uwa.. uwa…. sanin wacece uwa na kunshe ne a cikin labarin masarautar nan
Hafida-ti. Labarine mai tsaho da ya zama a cikin manyan labaran da suka kasance da
ZUCIYAR ahalin Aliy Qutb gaba daya. Duk da ya shude, shudewa ta tsahon shekaru da
muke tsammanin karnin ya shafe da fatan daina tunashi koda a cikin tarihinmu da
alama hakan bamai yiwuwa bane."

"Jaddah idan na dage akan son na sani ban shiga cikin hurumin daba nawa ba? Dan ina
mutukar so da zumudin na sani din".

Murmushi mai ciwo Malikat Haseenat ta yi, sai kuma ta zuba idanunta akan Iffah
tana dan jinjina kai. "Baki tsallake huruminki ba Hafida-ti,
tunda kin rigada kin zama mu mun zama ke. Sai dai dokar wanna zuri'a ta dade da
shardanta goge wanna tarihin domin mantashi da daina tunashi garemu har abada..."
taja nannauyan numfashi mai hade da ajiyar zuciya. "Da zan iya wofantar da
bukatarki da nace karki sake tambaya. Amma inaji a raina bazan iya ba, dan inhar
dai da gaske baya ce ke son dawowa ta maimaita kanta kamar yanda nake hasashe a
kanki tun zuwanki masarautar nan dolene labari biyu ya dawo a lokaci guda domin
kasancewarsu cikin juna duk da raina namin wasi-wasin taya hakan zata kasance bayan
anyi ruwa ne an dauke kasa ta shanye kayanta?"

Sam Iffah bata gane cudaddun kalaman karshe ba, dan haka ta tsurama Malikat
Haseenat idanu kawai ko kyaftawa babu.Murmushi Malikat ta sakar mata tare da lumshe
idanu ta bude a kanta lokaci guda. "Idan har zan samu warwarewar lissafina zan
sanar miki abinda kike son sani Hafida-ti. Zan sanar miki tarihi da tushen
kasancewar uwa a cikin tarihin wannan DAULA kamar yanda kike bukata".

A hankali Iffah ta saki murmushi mai kayatarwa maimaita kanta kamar yanda nake
hasashe a kankii tun zuwanki masarautar nan dolene dayan biyu ya dawo a lokaci guda
domin
kasancewarsu cikin juna duk da raina namin wasi-wasin taya hakan zata kasance bayan
anyi ruwa ne an dauke kasa ta shanye kayanta?"

A hankali Iffah ta saki murmushi mai kayatarwa da jinjina kanta. "Nagode sosai
Jaddah, ALLAH ya kara girma da lafiya mai albarka da tsahon rai".

"Amin".

Malikat Haseenat ta amsa tana gyara zamanta cikin wheelchair dinta da fuskantar
Iffah da kyau……….✍️
A muma to bara mu gyara zaman. @) 🥱😂

DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 59

."Labarin ya fara ne tun zamanin iyaye da kakanni da ya kasance akwai karancin


ilimin addini. Ba a daular ruman kawai ba hatta da sauran dauloli da ma talakawan
kasar RUMAN kowa yasan ani matukar imani da tsafe-tsafe a karnikan da suka shude.
Zaki samu duk talaucin mutum duk yawan arzikinsa yanada wani boka da ke fada masa
motsinsa ko wani abu dake tunkarosa, ko bashi Sa'a a abinda zai yi ko yake yi. A
lokacin da addinin musulunci ya fara kutsowa cikin wanna kasa tamu idan akaji ka
amsa sai an halaka ka, dan kuma kai shugaba ne to fa za'a tubeka a koreka kai da
duk ahalinka. ALLAH sarki, masu shiga musulunci da masu hidimar gain an shiga
sunsha matukar wahala a wancan karnin. Komai ya canja da cajawar labarin wanna kasa
dalilin wani fari da akai na tashin hankali, ruwan dake zagaye da wannan tsuburi da
kasar RUMAN take ya zagaye komai hadda gidaje da dukiyiyi har ma da rayuka. Ba
kasar ruman ce kawai ta girgiza ba, Africa da ma duniya baki daya wannan al'amari
ya matukar girgizasu, inda aka shiga kawo mana dauki ta kowane bangare. Wannan
shine mafarin fara samun canji, domin a cikin wanna yanayin ne tarin bayin ALLAH
mabiya addinai daban-daban suka fara yakin ganin sunja ra'ayoyin mutane da dukiyoyi
da wasu abubuwan kyale-kyale na duniya, harda masu yimusu tayin binsu kasashensu
suyi rayuwa.
Babu mai son yabar kasarsa tushensa dan haka mutane suka fara bijirewa, sai ko wani
bawan
ALLAH ya basu goyon baya mai suna SHEHU UTHMAN DAN-FODIYO da ga kasar NIGERIA.
shine ya tabbatar musu kasarsu itace yancinsu, itace gatansu, itace martabarsu, su
tashi da
karfin kwanji su gyarata yayi alkawarin tallafa musu da karfin jiki da ga
tawagarsa. Zantukansa
sun kayatar da kowa sun saka karsashi a jikin mutane, musamman yarima mai jiran
gado Miran Aliy Qutb. Ganinfa Miran Aliy Qutb ya amshi wannan tunatarwa tun ya samu
mabiya.
Abu mafi daukar hankalin mutane SHEHU UTHMAN DAN-FODIYO ya kasance MUSULMI
ne, hakama almajuransa da sukayi masa rakkiya, amma sai bai taba cema wani dole sai
ya shiga addininsa ba ko masa tayi da wata dukiyar da zai shigan, ya dage dai
tukuri da
taimakonsu yana ibadarsa. Hakan sai ya shiga birge mutane tuni suka fara karbar
musulinci.
Sai kuma cikin kankanin lokaci kasashen musulunci manya irinsu Saudi Arabia suma
suka
fara yunkurowa, mabiya addinin islam suka hada karfi da karfe wajen hidimtawa wanna
kasa ta
RUMAN ta sake ginuwa ta komawa kan kafafunta. A cikin abinda bai wuce shekaru
kalilan ba abubuwa suka cigaba da canjawa acewar munada tarin tattalin arziki ka
davan-daban. An dauki babban mataki akar
ruwan dake zagaye da mu, aka kuma kara fadada kasar ilimin addini ya yawaita,
kafirci ya
fara nisa a cikin al'ummar mu. Masu bautar gumaka da yin imani da bokaye duk suka
fara
janye jiki, wasu bokayen ma da kansu suka dinga ajiye kayan tsafe-tsafen suma suka
koma
ga ALLAH. Masu taurin kan cikinsu kuwa sai suka bijire da jan tunga, wasun su suka
koma
dazuka wasu kuma suka koma yi a boye."

Ta dan ja ajiyar zuciya da daukar ruwa takai bakinta. Kafin ta cigaba da fadin,
"Uwa diyar
wata bokanya ce babba a wannan masarautar,bayan mahaifiyarta da ake kira bokanya
Ta-bunu ta mutu itace ta gajeta. Shekaru masu yawan gaske da suka shude itake
tafiya da jan
zaren yi da hani na wannan gida harta mutu yarta ta gajetan (wato Uwa). Ta kuma
gajeta ne
ana gab da samun wannan iftila'i da ya faru,lokacin da abun ya faru tana farkon
fara jin
dadin kar fin ikonta dan tafi mahaifiyarta hatsabibanci. Domin kuwa komi za'ayi sai
an
sanar mata tace ayisa, idan ko ta hana akan dakata koda ana sonshi. Hatsabibiya ce
matuka.
Dan duk da mahaifin Miran Aliy ya yarda yan kasarsa suyi addinin da suke so shi ya
kasa
rabuwa da Uwa har ALLAH ya masa rasuwa Miran Aliy Qutb ya zama Shahan-shan. Shi dai
men hirans da farbn amma hahmands yaso bijirewa da farko, amma babu wanda yasan
miya faru hakan ta gagara ya cigaba
mata biyayya akan abinda ta shardanta kota hana. Na takaice miki zance fa ikon Uwa
sai da
ya kasance itake kamar mulkar kasar ruman dan har shi Shahan-shan din sai da
cewarta yake
cewa ga talakawansa. Haka yay mulkinsa ya shude Miran Abdul-majeed dansa, mijina ya
karbi kasar ruman. Muma mun cigaba da kasancewa a karkashin say na UWA, sai dai
abun na matukar damuna kasancewar nayi ilimin addini mai zurfi. A lokuta da dama
idan tace ai abu nakan kalubalanta har sai na
fahimtar da Tajwar Abdul-majeed illarsa. Duk bayan wata uku takan saka ayi yanka na
bakaken shanu da karnuka da rakuma wai tsarine na wannan daula. Takan tilasta daya
daga cikin yayan Shahan-shan a aura mata wani talakan kasa ko bawa ta samu ciki ta
hainu,da zaran ta samu cikin dole kuma ya saketa. Shi
kuma abinda aka haifa zai cigaba da rayuwa a cikin masarautar bashi da wani karfin
iko da shi.
Sai dai kin san wani abun mamaki da ya fara jan ra'ayina harna bijirema wanna
al'amarin?".

Jiki a sanyaye Iffah ta girgiza mata kai. Nisawa Malikat Haseenat tayi da
cigaba da fadin, "Duk wadan nan yaran da aka haifa ta wannan hanyar basa zarce
shekaru bakwai a duniya suke rasa ransu. Na fahimci hakane ta hanyar bibiyar
tarinhin wanna masarautar kasancewa mutum mai son
sanin tarihi. Lokacin dana fara
kalubalantar yankan da akeyi duk bayan wata uku na bakaken shanu da karnuka ne tasa
Abdull-Majeed ya auro mahaifiyar su Jasim. Ban
damuba dan wannan bashine gabana ba, ban kuma canja daga bijirewata ba da cigaba da
nusar da su akan sanin ma'anar yankan nan.Alhamdullah naci nasara, naci nasarar
dawowar
hankalin wasu jikinsu akan hakan aka fara ja"injar a daina a canja da wani abu na
sadaka bakwai sai yankan ba. Yayinda wasu kuma ke fadin ai yankan ma sadaka ne
tunda raba naman
ake wa talakawa da hadimai. A cikin tsaka da wannan dambarwa na haifi Haysam.
Mahaifin
mijinki kenan. Haysam yaci wahala sosai da cututtukan da aka gagara gane kansu, sai
dai
ALLAH ya kaddara kwanakinsa basu kare yana yaro ba. Bayansa na haifi Ammarah,
Ammarah
ta zo da wasu abubuwan ban mamaki a rayuwarta tun tanada karancin shekaru. Sai
Waheeda, auta Nayyar, zuwa lokacin matan Abdul-majeed mu hudu ne, kowacce kuma ta
haihu da shi, akwai maza kuma akwai mata. Bari na sake dawo miki akan yanka,
bijirewata da
mabiya dana samu yasa aka daina a zahirance,ashe a boye ana cigaba da yi batare da
sanin
Tajwar Abdul-majeed da ni ba. Sai da wata ranar juma'a da yamma fadan yara ya hada
Jasim da Haysam shi da yan uwansa suka masa taron dangi Ammarah ta shiga dukan,mata
kai da akai ta yanke jiki ta fadi ,abinka da yaro sai duk suka hadu kanta suna ihu
ganin jini ta hancinta. An kinkimota an kawomin tana zubda wanna jini, cikin ikon
ALLAH sai ban rude ba na fahimci habo ne. An bata taimakon gaggawa jini ya tsaya
har tai barci, sai dai lokacin da take farkawa bayan sallar magriba sai ta tashi a
firgice. Koda na tambayeta bayan na mata addu'a ta samu nutsuwa sai ta sanar min
mafarki tayi ana yanka shanaye da yawa bakake da karnuka da rakuma. Ga mahaifinsu
cikin bacin rai an dauresa da rufe masa baki. Da farko ban dauki wanna mafarki nata
a komai ba, sai kawai nace tai addu'a mafarkine kawai. A'a bayan kwana biyu da
hakan tai wata faduwa nan ma sai habo, akai mata magani dai ta kwanta sanda zata
farka a firgice, nan mana tambaya ta maimaita min wancan dai mafarki da tayi. Abin
ya dan fara damuna sai dai ban maida hankali ba. Da ga ranar kuma bata karayi ba
har ta cika shekaru kusan goma sha biyar a duniya.Da ga lokacin kwanaki dai-dai ne
bazaki samu Ammarah ta tashi a firgice a barci ba, idan ka tambayeta tace ba komai.
Ban taba matsa mata ba duk da abun na dan damuna, sai dai ina binta da addu'oi
akoda yaushe ita da sauran yan uwanta. Abu ya cigaba da faruwa daban-daban daga
Ammarah naban mamaki, bamu fara sarguwa da ita ba sai a randa aka samu gawar Nayyar
a cikin ruwa. Abubuwan data dingayi sai da ya tada hankalin duk wani mai numfashi a
cikin masarautar nan, inda ta dinga ihu da jadada sai ta dauka fansar jinin dan
uwanta. Anyi-anyi kuma ta fada miya faru take irin wannan magana taki cewa komai,
harma abin ya ban haushi na tattarata na kyale, a kuma lokacinne ita kuma ta
tattara ta tafi makarantar koyan aikin likitanci a kasar America, Sai lokaci-lokaci
take zuwa mana hutu ta koma. Ta maida hankali sosai saboda tana so, gashi kuma
makarantar da aka sakata makarantace ta musamman. A shekarar da take kammalawa a
shekarar yayansu Haysam yay aure, hakama kanwarta Waheeda, anyi-anyi ta fidda miji
itama tace a barta ba yanzu ba, ita akwai wanda take jira. Sam bamu takurata ba,
dan tanada karamin jiki sosai, shekarun nata ma dai ba wasu bane masu yawa, in bama
mun fada ba zaka dauka Waheeda ce babba gareta. Anyi bikin Haysam da Waheeda
Ammarah ta cigaba da aikinta a cikin clinic din masarautar nan da kuma karatunsa a
cikin wannan kasa ta ruman, a sati kuma takan zagaya jahohi biyu sau biyu domin
bada gudunmawarta ita da wat kungiya da suka hada. Tsahon shekaru hudu babu haihuwa
da ga matar Haysam, tadai samu ciki sau daya ya lalace bama ya haura wattani uku
ba, harma Waheeda itama acan bata haihu ba. Nata bai damu kowa ba, amma na Haysam
an fara kanan magana akan sai ya kara aure kasancewar shine Miran mai jiran gado.
Bai son kara aure, amma mahaifinsa ya takura masa, ya nema damar a basa lokaci zai
nemo da kansa. Anan kam sai ya bashi dama. Ba'a rufa watanni uku ba kuwa ya kawo
sunan Bushirat, ta kasance kanwa ga wani abokinsa da sukai karatu, amma suma yan
nan kasar ruman din ne, sannan kuma manyan mutanene dan mahaifinta babban malami ne
masani sosai. Kyakykyawar nasabarta yasa bamu wani tsananta bincike ba akai biki.
Sai dai me itama shiru, dan garama Ashwaq ta taba bari sau daya. Shekarar Bushirat
biyu a masarautar nan itama babu labari sai ma Ashwag din ce dai ta kara bari, dan
haka aka sashi ya kara auro Danish-Ara, cikin ikon ALLAH Danish-Ara bata rufa wata
guda ba sai ga ciki da ga Bushirat. Kowa yayi farin ciki sosai musamman ma shi da
ita da mu kammu, hakama Ammarah kai kacema ita keda cikin, dan gaba daya ta tattara
ta koma sashen dan uwanta tana kula da Bushirat. Bamu hanata ba, duk da rashin
aurenta na damunmu, sai dai mun fahimci akwai matsalar junnu tattare da ita, dan
haka muka dage da addu'a gareta kawai"………..✍️

DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 60

."An haifi ciki lafiya, kuma da namiji sanbalele da yaci suna *_Eshaan_*, Eshaan
kyakykyawan yaro mai lafiya da ban sha'awa ga kowa, ga
shiga rai. Wata irin makauniyar soyayya Bushirat ke nuna masa har takai Ni kaina
sai nayi da
gaske nake ganinsa, hakan da take yasa Waheeda yimata tas kafin ta dan canja aka
dinga kawomin shi nan. Ya taso yaro mai wayo, miskili da baka iya gane abinda yake
so ko baya
so sam. Shi ko irin abokan wasan nan na kuruciya Eshaan bayayi, yafi so ya zauna
shi kadai shiru ko yayta karance-karancen
abubuwa musamman a litattafan tarihin wannan daula da suka shude. Sai dai yana
matukar son wasan doki da basket ball, da wasan takobi, idan kuma yana tare da
Kakansa
ko mahaifinsa zaki dingajin maganarsa ko babu yawa. Al'adar wannan masarauta da
Miran mai jiran gado ya kai shekaru bakwai zuwa goma
ake kaishi can wani boyayyen waje ya rayu har sai girmansa, ko kuma sarki ya zabi
murabus
kafin ya mutu shi ya daurasa, idan kuma bazaiyi murabus ba za'a dawo da shi cikin
masarauta
da iyalansa dan su basa wuce shekaru ashirin basuyi aure ba gaskiya. Shiyyasa sai
kiga yaro
ya taso mahaifinsa bai wani tsufa ba. Da farko Bushirat ta tsaya tsayin daka akan
baza'a rabata
da danta ba, nima kuma na bata goyon baya dan banji dadi ba sanda aka rabani da
Haysam,
sai dai was tsurface-tsurfacen tsafi da Uwa ta fara kawowa a kansa yasa nace a
kaisan, ta
nuna bakin cikinta sosai akan hakan da nayi, har tai gargadi mai girma akaina da
cewarta ni na
cika shiga mata hanci ni da zuri'ata. Sam wani kurarinta da tsubbace-tsubacenta
basa bani
toro, dan da UBANGIJI NAna dogara akoda yaushe. Dan haka na cigaba da dagewa har
sai
da Tajwar Abdul-majeed ya yarda aka kaisa kasar Cuba. Haukane kawai Uwa da Bushirat
basuyi ba, sai dai kamar ALLAH ya saka tsorona ne a zukatansu ni ban sani ba. Dan
duk
hatsabibancin uwa iyakarta borenta a kaina a bayan idonane, taci alwashi sosai a
kaina dalilin
dauke Eshaan har ma abin ya dinga daure mun kai amma sai na daukesa aikin banza dan
bata
isa mun abinda bai kasance jarabawata ba. Komai ya lafa kowa ya cigaba da
harkokinsa aka shiga watan azumin ramadan. Azumi nada
kwanaki bakwai sai Tajwar Abdul-majeed ya sameni akan zan masa rakkiya ya duba
Eshaan da ga can muje umrah da shi bayan salla sai mu
maidasa Cuba mu dawo gida. Ban kawo komai a raina ba na shirya mukai wannan tafiya
har da Haysam. Munyi-munyi Ammarah ta bimu taki,
ashe lokacin ta samu wani saurayi ne ya kuma mata alkawarin dinga zuwa shan ruwa
wajenta. Sai da na nuna bacin raina kan rashin son binmu 12:47
Sai da na nuna bacin raina kan rashin son binmu a zatona bata son taje ne su hadu
da yar uwarta, sai da ta zauna ta fahimtar dani. Naji dadi sosai, dan tace tana son
bashi damane ta karanci halayyarsa anay in bikin sallah ai aurensu
kawai. Muni farin ciki da hakan, mun kuma mata fatan alkairi."

Malikat Haseenat tai shiru tana jan ajiyar zuciya, yayinda Iffah kejin kaguwa
matuka da
son jin cigaba, sai dai batayi magana ba har sai da Mammah ta cigaba dan kanta
bayan tasha
ruwan zam-zam dake gabanta.

"'Tafiyarmu itace mafarin kaddarar Ammarah,sannan itace mafarin yakice uwa da ga


wannan zuri' ar, sannan itace mafarin yin kuka garemu
dama duk al'ummar kasar ruman, sannan itace mafarin hawan Haysam karagar mulki
matsayin
madadi ga mahaifinsa. Bayan wucewarmu umarah, bisa yarjewar Jasim UWA ta sakasu yin
yankan nan dai dana sa Tajwar Abdul-majeed bijire mata akansa, ta kuma basu umarnin
daura auren daya daga cikin kannensu da wani bawa
ko cikin talakawan gari. Son zuciya da sanin makomar dan da ake so a samar ko ya ta
wannan hanyar suka aurar da Ammarah ga dan mai dinka kayan dokin masarautar, domin
a
ranar sunzo kawo kayan kwalliyar dokuna na bikin al'ada dake tunkarowa. Babu waya a
lokacin balle ta sanar mana ko wani ya sanar mana,hasalima sunyi auren ne a
sirrance sai ita
da suka dauka suka kai wa yaron bisa tirsasashi Ya kusanceta in ba hakaba zasu
kashe dukkan
ahalinsa da shi kansa. Dolene ya tsorata ya aikata abinda suke bukata yana kuka
itama
tanayi. Shi UBANG|JI mai hikima ne, sun taya ya kuma isar musu bisa ikonsa, badan
baya son
Ammarah da wannan bawan ALLAH bane, ba kuma dan yana son nuna Uwa a saman kokarin
mu bane. A'a wannan itace kaddararsu. Kuma ALLAH ya rubuta sai an samar da wannan
abun haihuwar ta wannan hanyar. Sai dai alhmallh, ina godema ALLAH da sake gode
masa, dan kuwa koba komai ta hanyar biyan sadaki da sheda aure abinda ya farun ya
faru. Mun dawo muka
tadda Ammarah a wani irin yanayi, dan kuwa ta birkice musu matuka, a lokacin kowa
ya sake
tabbatar da iska a tare da ita. Muni kuka ni da Mahaifinsu da dan uwanta sosai,
mahaifinsu
kuma ya fusata a wannan karon har ya kulle Jasim a kurkuku tare da duk wanda suka
goya
masa baya akan aikata aikin, yayi kiranyen uwa amma taki zuwa, an sa malamai domin
mata
kiranye nanma taki zuwa. Har takai an hada da bokaye irinta amma amsa daya suke
bamu tafi
karfinsu. Hankalinmu ya tashi matuka, musamman bayan wasu watanni da ciki ya
bayyana ga Ammarah, gashi lafiya taki samuwa gareta, tama koma wata iri kamar mai
ciwon
hauka, ta daina magana da kowa, sai kuka,abinci ma sai an tsaya kanta take ci.ALLAH
ne kawai
ya zama kariya ga wannan ciki har zuwa ranar haihuwarsa. Tajwar Abdul-majeed ya
sakka
a nemo masa mijin da suka aura matan, sai dai anje ba'a dace da samunsu ba, wai sun
bar asalin kauyensu a wani dare. Iya nema da bincike kuma ba'a dace ba dole aka
hakura. A daren wata juma'a ALLAH ya sauki Ammarah
lafiya, sai dai tasha matukar wahala kafin ALLAH ya kawo haihuwar. Ta haifo
yarinyarta mace kyakykyawa, sai dai babu ta inda take kama da ita sai tambarin
tabon tawadar ALLAH da zuri'ar wannan gida ke da ita, bamu san mahaifinta ba kuma
balle musan ko da shi take kamar. Mun amsheta hannu biyu, sai dai zagaye take da
addu'ar neman kariyar UBANGIJI da ga sharrin uwa. A randa aka haifi yarinyar a
ranar ALLAH ya
kawo wani mai magani.
Malikat Haseenat ta saki murmushi mai ciwo.Tare da fadin "kin san wani abu?" kai
Iffah da ke sharar hawaye ta girgiza mata. Malikat Haseenat ta sake sakin murmushi.
"Mai maganin nan hatsabilin kansa ne, dan kira daya yayma uwa a randa ya cika kwana
uku a masarautar nan a take ta bayyana gabansa
gaban kowa wujiga-wujiga. Ya tabbatar mata shi ba azzalumi bane, da sai ya wahal da
rayuwarta ta yanda bata isa sake numfashi a duniya ba, amma ko'a yanzu bazai
kyaleta ba sai ya nakasa rayuwarta ta yanda bazata kara tunanin cutar da
Wani ba. Ya sakata ta warware duka wani tsafi data aikata zagaye damu batare da mun
sani ba, sannan ya bude dukkan surukanta a gabanmu yay mata korar wulakanci da
gargadi
mai tsaurin gaske. Sosai ta dinga kuka da neman gafara da tabbatar masa ta zubda
makaman yakinta bazata sake ba a barta taci gaba da rayuwa damu amma yaki
saurarenta.
Majiya karfin hadimai aka saka suka kwasheta zuwa can tsakkiyar dokar jeji mai
tsananin rintsi da hadari suka jefar da ita. Wannan shine mafarin barin uwa tare
damu, sai dai kuma a
wannan dare ALLAH yay ma jaririyar da Ammarah ta haifa rasuwa, washe gari shima
Shahan-shan Abdul-majeed yabar duniya sakamakon bugawar zuciya da saran macijin da
aka rasa tushensa, sai kuma ya kwana da tashin hankalin abubuwan da Uwa ta dinga
sakasu sunayi na shirka da yanda bayan ya tsawatar wasu suka zagaye sunayi ciki
harda dansa
Jasim. Abdul-majeed ya rasu, uwa ta shude,jinjirar Ammarah ta koma. Haysam ya zama
Shahan-shan. Bayan duk faruwar wadan nan abubuwa da shudewarsu zukata suka hakura
abubuwa suka fara komawa dai-dai. Saurayin nan da Ammarah ta shirya gabatar mana
matsayin miji ya dawo da burin aurenta duk da ba'a boye masa komai da take ciki ba.
Yace yaji
ya gani, dan ko a baya da ya janye jikinsaJasim
a samesa da gargadin karya sake zuwa an mata aure. Bayan kuma yaji an saketa dan
auren kwata-kwata na sati biyu ne ya sake dawowa amma aka hana mishi ganinta ma
kwata-kwata.
Ammarah taso bijirewa, dan har lokacin bata dawo dai-dai ba, amma naita lallabata
da mata
nasiha ni da yar uwarta hatta hakura aka daura aure. Sai dai sam auren bai wani je
ko'inaba ta
fito, sakamakon wata sabuwar kaddarar data afka mata, a duk sanda mijinta zaije
gareta sai a
sauya halittar matancinta ta koma ta namiji.Dole babu yanda zaiyi ya rabu da ita ta
dawo
gida, daga nan bata sake aure ba, daga nan bamu sake jin labarin uwa ba, daga nan
bamu
sake jin labarin bawan ALLAHn nan da ya taimake mu ba akan Uwa ba, daga nan Jasim
ya
nuna mana ya tuba, sha'anin mulkin Haysam ya cigaba da tafiya a tsaftace dan a masa
gargadin nisantar duk wan mushiriki akan al'amurin mulkinsa..

Hawaye sosai Iffah takeyi na tausayin Daneen Ammarah, da tausayin su Malikat


Haseenat dan labarin nan ya matukar girgizata, al'amari haka
kamar a wasan kwaikwayo, wannan wace irin duniya ce mai cike da son zuciya. Kowa
burinsa
ya kasance a sama, mai nasara bisa nasarar dan uwansa, kai kai rayuwar gidan
sarauta dabance,
dabance a cikin duk wani rikicin gidaje da zuri'arsu. YaYanda Iffah ke kuka sai
Malikat Haseenat ce ta koma lallashinta. Sai da ta
tabbatar ta samu nutsuwa sannan ta mikar da ita. "Hafida-ti, kinga tashi ki tafi
dare yayi maybe ma mijinki nacan na jiranki".

Cikin share hawaye Iffah tace, "Ai bai san ma na taho nan ba".

Idanu sosai Mammah ta waro da fadin "Ya ALLAH, aiko kinyi laifi, maza wanko
fuskarki muje na miki rakkiya to".

Bata musa ba taje ta wanko fuskar, Malikat Haseenat ta mika mata wata yar
kyakykyawar
jaka tana murmushi. "Kije da wannan, duk abinda ke ciki kiyi kokarin dinga amfani
da shi
kamar yanda na rubuta, ki yawaita shiga ruwan zafi har ki saba da daina jin ciwon".

Kai Iffah ta sunkuyar cike da jin kunya, sambatai tunanin Mammah din zata gane ba
yau,
musamman yanda take dauriyar dai-daita tafiyarta duk da zafin da take ji……..✍️
Hummmm babu abin cewa kam yau 🥱🚴

DAUDAR GORA…..I
Book 2
Chapter: 61

Tunda suka shigo idanunsa kyam a kansu, yana zaune a falo zama na kasaita da izza
da jiran ta inda zata bullo. Tun bayan dawowarsa sallar isha'i ya duba bai ganta
ba. Shegen miskilanci ya hanashi tambaya har sai bayan kusan awa daya sannan ya
bincika ta cctv camaras. Anan yaga fitarta harma da nufar sashen Malikat Haseenat
ita kadai ko tsoro babu tattare da ita duk da darene. Yayi tsammanin zuwan bamai
jimawa bane, amma sai gashi har yay wanka yaci abincin dare yay yan ayyukansa babu
labarinta, harya kwanta da tunanin zai iya shareta sai hakan ya gagara, gangar
jikinsa da zuciyarsa suka tabbatar masa bafa zai iya rayuwa babu mahadinsa ba.
Shine ya dawo falo yay zaman jiran ganin ta inda zata bullo kusan awa daya kenan.

Gaba daya sai Iffah taji ta tsure da kallon nasa, dan haka ta koma da baya-baya ta
labe a bayan Malikat Haseenat. Idanunsa ya dauke daga kanta ya maida ga Malikat
Haseenat din shima. Cikin dan motsa lips dinsa ka dan ya furta, "Barka da dare
Jaddah".

Amsa masa tai cike da kulawa, tare da juyawa ta kamo hanun Iffah da ke labe a
bayanta ta maidota gabanta. "Ga matarka nan tane tare dani tun dazun, ALLAH ya
tashemu lafiya". Daga haka ta saki hannun Iffah ta gara kekenta ta nufi Elevator.

'"ALLAH ya huta gajiya". Ya fada a hankali yana dan lumshe ido da risinar da kansa
alamar girmamawa a gareta. Shiru falon bayan tafiyarta babu wanda ya sake
kwakwkwaran motsi. Shi ya
zuba mata idanun nan nasa masu kaifi, ita kuwa tana tsaye a inda Malikat Haseenat
ta barta kanta a kasa tana wasa da yatsun hanunta, tsigar jikinta sai yamutsawa
take dan har cikin jininta takejin tasirin kallonsa a kanta. Sun kwashi mintuna
masu dan tsaho a haka kafin ya mike, gabanta yaje ya tsaya, ta rumtse idanu da
karfi a tunaninta saukar mari ko wani abu dai mara kyau zata ji daga garesa. A
mamakinta sai jin tattausan tafin hannunsa tai a saman nata ya zare jakkar hanunta,
cikin takun nan nasa daddaya cike da izza ya rabata ya wuce.Numfashin da ta rike a
kirji da makoshinta ta saki da karfi, sai kuma ta bude idanunta tabi bayansa da
kallo har ya bace ma ganinta. Dan tarin dake neman rike makoshinta ta fara, dole ta
nufi dining room ta samu ruwa ta sha. Daga haka takai zaune tana sauke numfashi.
Sai da ta dan samu nutsuwa sannan ta tashi tabi bayansa tana addu'a a ranta.

Bata da tabbacin a inda yake, dan haka kawai ta nufi inda zuciyarta ke raya mata
da fatan ALLAH yasa ba'a nan din yake ba. Sai dai kuma da alama ta taki rashin
sa'ar. Dan tana shiga taci karo da shi zaune a kan gado da lap-top kan cinyarsa.
Dakin babu haske mai karfi, sai hasken screen din laptop dinne ya haske kyakykyawar
fuskarsa ma'abociyar kamewa da
kwarjini. Sum-sum ta wuce hanyar bathroom tana dan turo baki. Sai da ta gama
tsaftace kanta ta fito cikin bathrobe, yana a yanda ta barsa, hakan sai ya bata
damar tsayawa ta bayansa ta shirya cikin kayan barci masu dan kauri da turarruka. A
take kamshin dakin ya sake karfi. Fahimtar kamar fushi yake ya sata takowa inda
yake cikin sanda, zaune takai gefensa amma ya share abinsa bai ko nuna ya san da
zamanta ba. Cikin dan bata fuska da jin haushi sharetan da yay ta zame ta kwanta
tare da dan ture lap-top din tasa kadan ta daura kanta a cinyarsa ta kwanta. Da
kyar ya iya cigaba da rike kansa yaki kulata. Ganin ya cigaba da aikin dai ya sata
kurama fuskarsa idanu, sai kuma ta kai hanunta kan kwantaccen gashin kumatunsa ta
fara masa tafiyar tsutsa. (@) Yarinyar nan da tsokale-tsokalan masifa kike * ).
Yayi kokarin ganin ya danne ya cije amma aikin na neman gagararsa, baima san sanda
ya cije lips dinsa da rumtse idanunsa da dan karfi ba.

" ALLAH kayi hakuri bazan sake ba.ALLAH banyi zaton zan dade ba na samu Mammy
batajin dadi ne fa".

(Yarinyar nan sai ta kasheni zata huta) ya fada a zuciyarsa dake faman bugawa da
sauri-sauri cikin kaikawo. A hankali ya janye hannayensa dake sarrafa lap-top din
ya daura na damar kan nata dake cigaba da shafa fuskarsa. Rikesa yay yana kokarin
son gain ya janye amma sai tai wani irin juyi ta maida fuskarta saitin cikinsa ta
sakalo dayan hanun nata a bayansa ta kankamesa.

'"Kasheni kawai ki huta" ya fada cikin subutar harshe jikinsa na saki gaba daya.

Iffah da bata fahimci ita mima yake nufin ba ta kyalkyale da siririyar dariya
har yana jin dumin numfashinta a kan Fatar cikinsa. Ita a nata shirmen kankamesan
da tai ne yaji zafi. "dan na kasheka dawa zan zauna?". Ta fada cikin dariyar tana
kara cusa kanta jikinsa. Dole ya ajiye lap- top din ya kai kwance tare da dagota
gaba dayanta ta hau saman jikinsa. Fuskarsa take kallo cike da dakewa kamar yanda
shima yake kallon tata idanunsa a shanye. "Miyasa baki son a zauna lafiya?". Ya
fada a hankali yana sake kankance idanunsa cikin nata. Idanun ta juya tana shagwabe
fuska da dan cuna masa lips dinta. "Toni mi nayi? In dai zuwa wajen Jaddah ne ai
nace kayi hakuri".

Dariya maganar ta bashi amma sai ya gimtse baiyi ba, ya dan tabe baki da
tsatstsareta kaifafan idanunsa. Cikin dan dage gira
"Har na kai ki?".

"Hu'um, ni a suwa kuma, kana kallon kanka a mirror kuwa da kyau?. Badan kar ace
nayi karya ba sai nace kafi kowa kyau a kasar ruman". Harga ALLAH ta bashi matukar
dariya yanda ta fadi maganar cike da yarinta, yayinda zuciyar sa tai wani irin
shiga farin ciki, domin kuwa bawai yafi kowa kyau din bane kamar yanda ta fada a
zahirance, ya fahimci ta fara caukar karatunsa son sa ya fara shiga zuciyarta.
Domin abinda kake so ne kawai kake ma kallon kasancewarsa a sama dana kowa. Shi
kansa duk da yasan akwai kyawawan da suka fita ganinta yake samada kowa saboda
kawai ita kadai yake so,kyawuntane kawai ke kayatar da shi. Bai fahimci murmushi
yake ba sai da yaga yanda ta kura masa ido. Ya dan waro idanun waje alamar miye
kuma, ita kuma sai ta girgiza masa kai tana murmushi da dan kauda idonta dake cikin
nashi."Murmushi na maka kyau, gashi kuma baka son yi".

Hannayensa duk biyu ya doro a saman bayanta ya sake matso da ita ta kwanto jikinsa
sosai, fuskarsu ta koma gab-gab har hancinsu na gogar na juna. "A komai k ta
dabbance my sohaa".

"Kaima haka ai".

Ta fada tana dan sumbatar lips dinsa, sai tai saurin jan jikinta zata sauka dan sai
da tai babban kokari wajen masa kiss din, amma kunya take ji. A hankali ya rikota
bayan ya fisgo numfashinsa da ya nema kufcewa da kyar.Mirginasu yay suka koma saman
hannayensu suna fuskantar juna, batare da jiran wani abu ba ya manne lips dinsu
waje guda..
Anfi karfin alkalamina anan.

Babu alamar wasa tattare da shi, da ga tsayen da yake a kofa yana dubanta a
yatsine ya ce,"Kifadi abinda zaki fada ina jinki, dan bazan wuce minti ashirin ba
anan".

Rai bace Ameera Haifah ke duba Miran Arshaan mai maganar, tai karamar kwafa da
tabe baki," Arshaan kenan, idan kana ganin Kanada mafitar da zata iya kwabemin ne
ma,dan har da kai sai dai ka shirya mu duka zata kwabe Dar harda kai, idan har ban
tsira ba da ga yarda ka maida Jasim kaima zan bude maka aiki ne. Zan kuma tabbatar
maka na fika iya makirci dan mace sunana idan ka manta".

"hhhhahh! Ni kike tunanin zaki iya budema aiki Haifah? to ina baki shawarar fita a
hanyata da ga yau, in ba hakaba why zan kasheki na binne gawarki a cikin masarautar
nan kuma na kashe banza".

"Oh really? To Dan ALLAH ko zaka gwada ne? Nace ko zaka gwada kashenin muga!!!".

Tai maganar cikin tsananin hargowa tana wani hahhankada kirji a gabansa. Wani irin
tafarfasa yaji zuciyarsa nayi, dama a wuya yake, a fusace ya kaima wuyanta wani
irin shegen shaka na tashin hankali. Cikin kankanin lokaci manyan idanunta suka
sake yowa waje ruku-ruku, ga kakarin mutuwa da ta fara da mutsu-mutsun ganin ta
fisge hannunsa da ga kan wuyanta. Sai dai kuma hakan ya gagara, dan karfinsu ba
daya ba. Tafiya ya dingayi da ita cikin rufewar ido har jikin bango, ya kara matse
wuyan da karfi tare da wajigata ya buga kanta jikin bango. Wata irin wahalalliyar
kara ta fasa da ta jawo hankalin Jasrah dake daki kwance ta farka tana nemansa, dan
su suna'a falon baki ne kasancewar cikin shigar badda kama Ameera Haifah tazo a
nufin bako tasa amintaccensa imata iso saboda baya daga mata waya yanzun. Sai da
yazo yaga itace. Gaba daya idon Miran Arshaan da alama ya rufe, dan tuni ya sake
jijigata ya buga a bango, jini ko ya samu hanya ya balle.

lya karfi da budewar murya Jasrah ta daddage ta kwalla wata irin kara na firgita,
dan ganin jini ya wanke fuskar Ameera Haifah ga Mijinta shake da wuyarta sai ta
dauka ta mutu.Wani irin wancakalar da Haifah Miran Arshaan yayi yana duban Jasrah
data yanke jiki ta fadi. Har rige-rigen shigowa hadiman masu tsaron sashin keyi,
ganinfa abinda ke faruwa tuni wani ya firgita ya kyalla a guje ya sanarma jami' an
tsaron gidan dan wannan faninsu ne...✍️
DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 62

...…….Tofa dan-dan-dan, da alama dama irin wannan damar Iffah ke jiran samu, dan
cikin
kankanin lokaci duk da darene masarautar ta dauki dumi, yayinda aka kwashi Ameera
Haifah da Jasrah zuwa asibiti, Miran Arshaan kuwa da jikinsa ke tsumar toro gaba
daya ya gama
gigicewa, dan sai zuwa yanzu ya dawo a hayyacinsa. Tuni kuwa ya tsure da ganin
abinda ya aikata, sai kawai ya bige da borin kunya.
Sudai jami'an babu wanda yace da shi komai,sun tattara komai akan sai zuwa da safe
za'a kai
maganar ga Shahan-shan. Abu dai mafi daure kai shine miye tsakaninsa da Ameera
Haifah din
har haka a irin wannan tsohon daren, dan a kala fa karfe biyu na dare kenan.

大大

A lokacin da duk ake waccan dambarwar anan ta-kurya ce ke ganawa da manomin


ganyayyakin shayin Shahan-shan. A cikin badda kamarta take, dan haka shi bai san
wacece ba.Hasalima magana da Jazaa sukeyinta ita dai tana hakimce komai batace ba.
Da farko yaso ya, amma ganin wata lukutiyar jakkal da zinare ga barazanar halaka
zuri'arsa kunne tuni ya mika wuya akan an gama. Malikat Bushirat tai murmushin
basawa ta dauke kanta.Kwalayen ganyen shayin da uwa ta kawo kan ya fara kaiwa
sashen Shahan-shan din kafin wanda zasu noma ya tsiro nan ma Jazaa duk ta ajiye
masa su har uku..

Hummm🥱🚴

**

Zaune take bayan idar da sallar asuba, yanda ta kurama waje daya ido zai baka
tabbacin tunani take. Sai lokaci zuwa lokaci da takan saki murmushi, harda cusa
kanta cikin kafafunta kamar mai jin kunyar wani da ke gabanta. Ta dan jima a hakan
kafin ta mike kamar wadda aka tsikara idonta kan agogon dakin. Tasan yanzu kam yana
Gym ne tunda har ya kai yanzu bai shigo ba. Itama tsaf ta shirya cikin kayan motsa
jiki ta, sun mata matukar kyau da fidda ainahin surarta komai dam. Dan wani bana ta
saka a kanta siriri kalar kayan sannan ta daura talda daura after dress saman sport
wears din. Shiru tai tana bin Gym din data shigo da kallo, babu kowa komai ma a
kashe yake, da alama banan yazo ba. Fuska ta dan bata da tura baki gaba, har zata
koma sai kuma ta tuno randa ta samesa a can sama yana wasan takobi shi da Miran
Arshaan. "Yes!" ta fada tana wani kashe ido daya da yin juyi sannan ta nufi can
cikin takunta na nutsuwa

Shelanta sunanta da na'urar kofar tayi kamar yanda ta saba duk wanda zai gitta ta
cikinta ya sashi dakatawa da jujjuya takobin ya juyo a hankali. Tuni hadiman wajen
sun jujjuya bayansu sukam. Yanda take takowa garesa kamar wata tarwada yasa shi
gagara cigaba da abinda yake yi.

"Good morning

Ta fada cikin rashin tsoron nan nata na bayyane tana daura yatsanta saman
tsintsiyar hannunsa ta zano a hankali ta dire kan kyakykyawar takobin da ya rike
rikon kasaita da kwarewa. Da kallo kawai ya bita batare da ya amsata ba. Itama sai
bata nuna tasan yana kallonta ba ta zare takobin a cikin hannun nasa fuskarta da
murmushi. kin sakar mata yay, sai ma cike da salo yay wani irin juyata bata ankara
ba ta dawo saman jikinsa takobin a wuyanta sai dai bai daura a kan fatar jikinta
ba. Iffah jitai zatayi fitsari na neman kufce mata tsabar yanda ta tsorata har yana
jin yanda jikinta ke tsuma. Dan dukowa yay kansa a kafadarta bakinsa saitin
Kunnenta ya furta, "k takamarki tsokala ko?".

Idanunta da ke kawo kwalla ta shiga kikkifatawa da girgiza masa kai a hankali.


Cikin rawar harshe ta ce, "Eshaan Akhi na tuba".

"Daga baya kenan".

Ya fada yana kara matsar da takobin jikinta gaf.Sake tsurewa tai. Shiko sai faman
danne dariya yake.

"Ki fanshi kanki".

Da sauri ta ce, "Da mi?".

Dan lumshe idanunsa yay ya bude yana mai busa mata numfashinsa a wuyan. A dan salon
tabe baki ya ce, "Komai ma".

"Shike nan, shike nan naji na amince, amma dan ALLAH ka janye sau daya fa ake
mutuwa, rai daya ne". Yanzu kam kasa daurewa yay sai da murmushi ya subuce masa. Ya
janye tare da dauke hanunsa dake saman cikinta ya juyota suna fuskantar juna.
Hawaye fa da gaske sun cika mata idanu. Da kyar ya iya gimtse dariyarsa. Idanunsa
ya maida ga hadiman wajen da suka juya bayansu tun dazun, dasss daga yatsunsa sau
biyu, cikin abinda bai sakkani ba sun bar wajen a ka barsu su biyu. Da baya-baya
yaja zuwa table din gefensu kadan,wata takobin ya dakko a cikin kyakykyawan kufanta
ya dawo gabanta, hanunta ya riko ya daura mata takobin sannan ya zare abayar ta ya
ajiye tare da mata alamar bismillah. Kamar ba ita ta gama hadiyar hawayeba yanzu ta
wani dubi takobin shima ta dubesa ta dan murguda baki. Kansa ya maida gefe yana
murmushi, tare da ajiye tsinin tasa takobin bisa kasa ya fara zagayata. Yana a
tsaye daga bayanta ya juya takobin cikin salon tsokanarta kawai a bazata yaji tama
kanta garkuwa. Idanu ya dan waro waje, da bin takobin da kallo kawai ta zuke ta
maida masa harin. Cikin zafin nama ya kare kansa shima mamakinta na nan kasheshi.

"Dama kin iya wasan takobi?".

Ya tambaya da mamaki idanunsa cikin nata Murmushi ta sakar masa da kara zukewa ta
kai masa suka ta kasa. Nanma baya yay cikin zafin nama yay wata irin bahaguwar
zukewa. Dariya tayi da dire takobinta ta fara zagayashi kamar yanda ya mata dazun,
cikin salon dage gira da kashe masa ido daya ta ce, "Zaka cigaba da tsayawa
tambayar a ina na iya ne na kaika kasa?". Tsaiwarsa ya gyara da kyau yana murmushi
da kamo lips dinsa na kasa ya tura ( paki suka cigaba da zagaye juna. Sai kowa ya
yinkuro cikin ragabza akai tsaiwar zakaru. Cikin kwarewa da nuna bajinta ga kowa
suka cigaba da wasan mamaki na nan kashe Tajwar Eshaan a zuciya. Duk da ya fita
kwarewa yanda ta iya din itama na bashi mamaki matuka.Sai dai ya bita da salon
saffa-saffa yanda bazai cutar da ita ba dan karfinsu ba daya bane

Tamkar wanda aka jeho kawai sukaji sallamarsa a kusan tsakkiyar wajen, dan kamar
sai da ya matso gab da su ne ma yake sallamar.Da ga shi har Iffahn juyowa sukai,
musamman Iffah da kamar wadda ta ma firgita, dan jikinta har rawa yake wajen neman
abinda zata yafama jikinta, tsabar yanda ta rikice tama ki ganin after dress din
nata. Bata san yanda akai ba, tayaya ma kawai jinta tai a jikinsa, jin kamshinsa ya
sata kankamesa da sauri tana kokarin boye kanta.

"Miya kawoka nan babu neman izini? Kabar wajen nan Aam!!" ya fada a matukar tsawace
shima yana kankameta da juyawa da ita suka bama Miran Arshaan da yay mutuwar tsaye
baya.

"I say out!!!".

Ya sake fada da wata irin mummunar tsawa mai karaji da har jikinsa na girgizawa, ga
idanunsa sun yi wani irin kadawar masifa kamar wanda ake kadama gangi. Miran
Arshaan har tuntube yake yi tsabar firgicewa da tsawar Tajwar Eshaan din. Bai taba
sanin yaron nan dan bala'i bane irin yau. Next surar yarinyar nan ta matukar
kidimashi, ashe abinda Jasim kenan ya gani kullum yake cikin sambatu da santin
yarinyar, shi manemin matane tun yana da kananun shekaru, yayi mu'amula da mata
kabila daban-daban a duniya da bai san adadi ba. A sanda yake ji da rashin ji har
order din mata suke ta online, yaga matan ma da sukafi Iffah kira amma wannan jikin
dabanne. Ji yake yama kasa cigaba da tafiyar yanda jikinsa ke bari, sai kawai ya
samu bango ya manne yana sauke numfashi gudu-gudu. (Humm)

Yanda Iffah taji zuciyarsa na bugawa da sauri- sauri kamar zata ballo
kirjinsa ta fito ga tsawar da yayma uncle din nasa ya matukar sake rudar da ita
fiye da tsoron ganinta a yanda take da tai gudu. Kanta ta shiga jujjuya masa da
kankame hanunsa, sai kuma ta dan dago ta kalli fuskarsa. Ta wani irin kadawar
masifa jazur hakama idanunsa gaba daya sun juye mata cikin canjawar kammani. Dole
ta maida idanunta kasa jikinta na rawar toro da yanayin nasa. Jitai kawai ya wani
irin fisgar hanunta zuwa hanyar kofar da ta shigo, bai tsaya da ita ko ina na
bedroom. Yarfar da hannun yay yayi shigewarsa bathroom. Da kallo ta bisa hankalinta
a tashe itama, dan ita kadai tasan kalar wutar masifar data gani a cikin idanunsan.
Raya mata zuciyarta ta dingayi kawai tabar dakin nan karma ya fito ya sameta...

Koda ya fito bayan tsahon lokaci da ya dauka a bayin bai nema Iffah ba dan yana
bukatar kadaici saboda ya shiga bacin rai, shi mai kishi ne, tabbas yanada matukar
kishin da yake ji akan yarinyar nan zai iya badda mutum. Wata irin tsanar Miran
Jasim da Miran Arshaan yake ji irin wadda bai taba ji a kansu ba a dukkan abubuwan
da suka aikata masa a baya, ga wani irin sara masa da kansa yake yi na ciwo. Jikin
window ya karasa hannunsa goye a bayansa batare da ya cire ko bathrobe din jikinsa
ba yana kallon sararin samaniya da ke hada was irin manyan bakaken giza-gizai na
hadari, du da safiyar tayi sosai garin yaki washewa sai ma rinewa yake sake yi
kamar za'ai wata sabuwar magriba. Kiran waya ne ya shigo, ya share kamar bai jiba,
aka sake kira nan ma kamar zai share sai kuma ya nufi wayar a fusace ya daga. Sai
dai yay shiru baice komai ba. Da ga can Sayeed Fayzul-haq ya gaishesa cike da
girmamawa.Haushin kowa yake ji, duk da bashi yay lefin ba ya samu rabonsa. Dan
maimakon amsa gaisuwa a dake ya ce, "Ya akai". Dan rikicewa Sayeed Fayzul-haq yayi,
amma sai cikin dauriya da sake kankan da kai ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa
tsakanin Miran Arshaan da Ameera Haifah tun a daren jiya. A zafafe ya ce, "Kaima
jami'ai magana su kamashi a hadashi da dayan sakaran, a saka na'urar daukar magana
cikin akin kurkukun kuma.Itama Haifah din Doctors su sallameta idan babu wata
matsalar data shafi lafiayarta jami'an tsaro su rufeta",. Daga haka ya ajiye kan
wayar yana huci. Duk yanda yake kokarin rike kansa da bin komai a sannu ya fahimci
ba haka makiyansa suke bukata. Fushinsa suke son gani, ainahinsa suke bukatar ya
nuna musu. Ya barsu da yarinyar nan ne kawai domin shi din shugaba ne, shugaba kuma
da hadiyewa aka sansa, amma tunda so suke shi ya fito musu a Eshaan In Haysam
Abdul-majeed Aliy Qutb din sa to yanzu ne wasan zai fara..
😆🥱TOFA ran yan maza ya baci, al'ummar kasar ruman kuyi takanku mai RUMAN dinne da
kanshi 🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴

DAUDAR GORA
Book2
Chapter: 63

A bangaren Iffah kam itama dai wanka tai ta gyara jikinta, yunwa ta hanata cigaba
da zaman dakin ta fito neman abinci. A irin wannan lokacin. Babu kowa a falon sai
daddadan kamshi da sanyin ac mai ratsa bargon jiki, mamaki ya kamata, duk da dan
sanyi-sany in garin na hadarin dake tasowa dan fitina sai an kunna na'urar sanyaya
waje, baki ta tabe abinta ta nufi dining room din da glass ne kawai ya gitta
tsakaninsa da falon dan komai a tsare yake.

Shayi tai kokarin fara sha dan shi take bukata, wani irin masifar sarawa kanta yay
lokacin da hanunta ke sauka kan abinda aka zuba shayin. Janye hannun tayi da sauri
ta kurama flaks din shayin ido, sake kai hannu tai a karo na biyu, nan ma kanta ya
kara sarawa al'amarin kamar wata almara. Sake janyewar dai tayi tana kaiwa zaune
jagwab idonta akan flaks din dai. Ta kwashe mintuna uku tana kallon sa sannan ta
sake daurawa a karo na uku, yanzu kam duk da abinda takeji a jikinta na azaba bata
cireba tsahon wasu mintuna. Idanunta sunyi jazur cikin kankanin lokaci, gaba daya
kamanninta sun canja kamar ba Iffah'r ba. A wani irin fusace ta mike dauke da tray
din da flaks din ke kai zuwa kitchen.

Taku take cikin nutsuwarta da kasaita ki tarwada ko budurwar hawainiya.


Kwarjininta da cikar kamalarta kan shafe karancin shekarunta musamman dan tana a
cikin irin wannan yanayin. Kasancewarta a kitchen ba karamin rudani bane ga
ma'aikatan cikinsa. Hannu kawai take daga musu da ga gaisuwar da suke mikowa
gwiyawunsu kan kasa. Kwalayen gayen shayi uku da daya daga cikinsu ke kokarin
fitarwa ta zubama idanunta da sukai jazur.

"Wannan fa?".

Cikin sauri suka bata amsa da "Ganyen shayin shugabane".

"Daga ina ya fito?".

"Wanda ke kawowa a koda yaushe".

'"Ina bukatar ganinsa daga nan zuwa awa biyu".Daga haka tai gaba tana
kokarin hada sabon shayi da kanta. Sunyi kokarin ganin sun amsheta amma ta hana
hakan, cikin kankanin lokaci ta kammala ta fice batare data sake bi takan kowa ba.
Dai-dai kuma da fitowar Tajwar Eshaan cikin shiga mai sauki ta zaman gida alamar
bazai fita ko'ina ba. Har yanzu fuskar cidin-cidin take babu alamar yasan minene
murmushi. A sanyaye Iffah ta karasa cikin dining room din kamar yanda shima can din
ya nufa kamar bai ganta ba.Kama kanta tai itama suka kai Zaune a tare tana dan
satar kallonsa tai ta Kasan ido ganin ya kai hanunsa kan jug mar dauke da madara.
Ta zubama madarar ido itama, wani irin kallo takema jug din na kurilla,sai kuma
cikin dauke kai da cije lips muryarta a sanyaye da girmamawa ta ce, "Shi wannan
madaran illane ga duk wanda ya sha shi, barinsa a inda aka gansa shi yafi alkairi".

Shiru kamar bai jita ba, sai kuma ya waiwayo a hankali ya dubeta, fuska ta
shagwabe tare da marairaiceta ta jinjina masa kai. "Dan ALLAH karka sha akwai
matsala tare da madaran".

(Ya arrahaman wai yarinyar nan mutum ce kuwa?) ya fada a zuciyarsa kaifafan
idanunsa a kanta. A hankali ta daura hanunta kan nasa ta zare jug din madarar ta
ajiye gefe. Shayin ta hada masa, tare da ajiyewa gabansa tana fadin "Zakaji dadin
wanna shayin fiyema da madaran".

Nan ma shiru babu alamar zaice wani abu, ya kumaki daukar shayin. Sai ma gani
tai ya yunkura zai mike cike da izzar nan tasa ya taka zuwa kofar barin dining room
din, Iffah ta bisa da kallo ta gefen ido zuciyarta na wata irin tafasa itama. Sai
dai girmansa da kimarsa bazai barta ta nuna ba koda a fuska. Kanta kawai ta dukar,
da karfi ta matse idanunta da cije lips dinta shima da karfi. Kadan ya dawo da
jikinsa baya alamar dama bai fice daga dining room din ba ya kafeta da kallo.A
karon farko ya saki kasaitaccen murmushin da ganinsa a fuskarsa ba karamin yaki
bane. Dawo wa yay a hankali ya zauna ya dauka shayin ya fara sha. Sosai kam ya masa
dadi, amma babu alamar hakan a fiskarsa. Itako ta dauke kanta gefe tama daina
kallonsa. Cak taji anyi sama da ita batare da tasan sanda ya gama shan shayin ba
ma.Wutsil-wutsil ta farayi da kafafu tana tura baki, bai kulata ba har sai da ya
kaita bedroom ya dire a gado….

😏 Yau dai bazan dauki rahoton ba.

* *

Cikin kankanin lokaci zartar da umarnin Tajwar Eshaan na rufe su Arshaan da Ameera
Haifah ya zagaye masarautar. Nan fa aka fara yan kananun maganganu kamar yanda
al'adar take.Yayinda kowa ke tambayar kansa mi yakai Haifah sashen Miran Arshaan
din sanin babu wata alaka tsakaninsu ta zahiri face matar yayansa. Anya kuwa babu
wani abu a kasa shr Tajwar Eshaan din ya shinshino dan kasancewar tasu tare kam
dole akwai wani al'amari mai girma na boye. Wasu ma dai tuni suka fara fassara
al'amarin da cewar akwai dai abinda suke aikatawa. In ba hakaba minene ya kaisu
haduwa a irin tsohon daren nan ba mata ba, ba kanwa ba, ba uwa ba ko wata
shakikiya, kuma har takaisa da neman kasheta irin haka. Labarin ya fara zama
gaskiya lokacin da Jasrah ta farfado. Cikin kuka take sanarma Mammah da take dubata
tare da Malikat Bushirat cewar dama ta taba zargin Haifah a wani lokaci da tai
kiransa tsakar dare, ranar ta samu damar ganin kiranne dalilin manta wayarsa da yay
ya fita wani kiran ujila da batasan wayayi masa ba. Tana dagawa Haifah ta yanke
kiran, sai dai ta riga taji muryata, koda ta dauki number ta kira da wayarta ba'a
daga ba, washe gari ta bada a mata bincike kan number din aka tabbatar mata bata
akan waya. Taci gaba da saka masa ido akan hakan amma ba'a sake kuskuren kiran
ba,sai dai a wasu lokuta takanji kamshin wani irin turare na mace wanda shine taji
a daren jiya Haifah nayi. Ta rushe da kuka mai cin rai da zuciya. Babu abinda
Malikat Bushirat keyi sai cika da batsewa, tana matukar son Jasrah a rayuwarta,
sannan ga Haifah da ke matsayin kishiya da ma akwai burbushin wani abu a kasan rai
na kishin zama da miji daya da sukai,duk da ita shaida ce mijinsu bai taba son
Haifah k harva bata taba zama mai wata power a cikin masarautar ba shi yasa tuni
bata a cikin jerin wanda suke a gabanta itama, duk da tayi aiki a kanta kamar su
Malikat Ashwaq, dan acewar uwa ba'a sakaci da makiyi komai kankantarsa.

Ta tabbata Jasim da Haifah neman juna suke a bakin kowa bisa zancen Jasrah,
sai abinda Tajwar Eshaan din yayi yay matukar burge ahalin
masarautar har wasu na saka masa albarka da rage jin zafinsa a zukatansu. Oho shi
baima san duk anai ba, dan yana can tare da yar shilarsa suna hutawarsu. Shirunsa
kuma na nufin bazai fitoba yau gaba daya kenan.

****

Kamar yanda Iffah ta bada umarnin gain mai kawo kayan shayin Shahan-shan an isar da
sakonta. Bayan sallar la'asar tana tsaka da nazarin littafi aka sanar mata zuwansa
ta hanyar wayar landline. Bataso katsewar karatun nata ba, sai dai kuma haduwa da
mutumin nada nada matukar amfani dan haka ta tashi ta kimts dazun ta riga ta gama
tsara shirinta yanda ya dace, dan sun tattauna da Daneen Ammarah ta kuma bata
shawara duk da a farkon bayanin Iffah din jimm tayi na rashin fahimtar manufar
hakan. Sai da Iffah tai mata bayani dalla-dalla dai-dai da yanda ta tsara sannan ta
gamsu ta Kuma bata goyon baya dari bisa dari.

Hurumin duk wani bako a sashen Shahan-shan iyakarsa falon farko ne, wanda har
va tsallake zuwa na biyu ya kai babban bako kam na musamman, balle na uku kuma da a
tarihi ma bayan masu hidima Malikat Haseenat da Malikat Bushirat ne kawai suka taba
iya tsallake wannan hurumin sai ko Daneen Ammarah da tai dalilin Iffah, dan Tajwar
Eshaan fa bai zauna a sashen da mahaifinsa ya rayu ba. Shi da kansa mahaifin nasa
yasa akai masa wannan ginin tunkan ya dawo kasar ruman. Hakan yasa har yanzu babu
wani mahaluki daya san sirrikan tsarin wannan sashe sai mai shi din.

A kowane falo Iffah na samun gaisuwar girmamawa, dan ta stairs ta biyo ko'a
jikinta duk da wahalar hakan, yayinda amintattun Hadiman Tajwar Eshaan da'a ka'ida
basa sakkowa ko falo na biyu sai da dalili ke biye da ita. Dattijon mutum da alamu
suka nuna shima din dai wani babbane dan babu wata kazamar shiga tattare da shi vav
saurin mikewa domin girmamawa ga zawjata-almilk din. Iffah takai zaune tana satar
kallonsa ta gefen ido batare da kowa zal iya lura da hakan ba. Rissinawa yay domin
gaisheta ta daga masa hannu kawai da masa nun da wajen zama.

"Godiya nake ranki ya dade".

Ya fada cikin kankan da kai yana kaiwa zaunen".

Sai da taja kamar minti biyu falon shiru kafin ta nisa. "Na bukaci ganinka nan
ne bisa wani dalili da bai gaza biyu ba. Na farko daga yau na dakatar da kawo duk
wani ganyen shayi da sunan Maleek a gidan nan. Na biyu akwai aikin da zakamin".

Hankali tashe ya dan dubeta sai kuma ya rissinar da kansa. "Ranki ya dade ki
gafarceni, wani abu ya faru ne?".

"Komai bai faru ba. An samu sauyin sabon tsarine kawai. Shin kozan iya sanin
sunayen abubuwa da ake hada kayan shayin Maleek?"

"Sosai kuwa ranki ya dade, mi kike bukatar sani?"


"Komai"

Ta bashi amsa a takaice. Da sauri ya bude jakkar gefensa ya zaro wani littafi.
Da sauri daya daga cikin hadiman ta amso ta kawo mata bayan ta kai har kasa.

A dake Iffah ta amsa babu alamar wani dar tattare da ita ta fara duba littafin
Kavance dan babba.

Duk da yasan babu wani abu na cutarwa a ciki tunda a sirrance kuma aka bashi
ganyen shayin da ya aiko jiya da dare a tsorace yake, dan harga ALLAH gizagon
wannan baiwa da kwarjininta ya cika masa ido matuka har yana jinsa a takure cikin
falon ma. Da din dadawa kuma wannan shine karo na farko da akai masa irin wanna
kiran ma sabanin da da sai ya hada wani samfur na sabon ganyen shayi yakan zo ya
gabatar kozai birge Shahan-shan.

Kusan mintuna biyar Iffah nabin littafin daki- daki har kusan tsakkiyar, dan
gajerun bayanai ne akan yanda ake hada ganyayyakin da sunayensu. Rufewa tai tare da
dan dagowa ta dubesa. "Uhm komai dake anan kam bashi da wani aibu, sai dai
sabaninsa daga yanzu muna bukatar fresh ganyayyakin ne. Kuma za'a dinga noma su ne
a cikin masarautar nan".

"Yanda kike so haka za'ayi ranki ya dade". Ya fada cikin tashin hankali a bayyane.
Iffah da tai kamar bata fahimcesa ba ta mike, "Ka hada duk abinda ya dace a
turamin, idan na kammala da nawa shirin zan nemeka".

"Godiya nake ya Zawjata-almilk. ALLAH ya kara miki lafiya da tsohon rai mai
amfani".

Hannu kawai ta daga mai tai wucewarta,hadiman da al'ajabi ya sandarar a tsaye


suka
take mata baya da sauri….✍️

(Wato wannan yarinyar ko? Humm 🥱😂

DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 64

Tunda aka shigo da Arshaan dakin kurkukun da ke makwaftaka da juna da na Miran


Jasim sukema juna kallon kallo, duk da dai shi Jasim bai ko motsa da ga zaman
takurewa waje dayan da yay ba, su dukansu dakin babu yawaitar haske, sai dai ta dan
hasken da ke lekowa sukan iya gain junansu. Sun kwashe awa guda a haka kafin Jasim
ya mike cikin dan tangadi, dan baya cin abincin da ake bashi ga raunikan da ya jima
kansa duk an masa tretiment dinsu. Jikin karfen da ya raba dakin nasu ya tsaya, sai
kuma ya kece da wata irin dariya kamar wanda hauka ya kama. Cikin bacin rai da
kunar zuciya Arshaan ke kallonsa, sai dai baice komai ba har yayi ya gama yay shiru
dan kansa. "Oh!! Kai dama a tunaninka Jasim ne kawai ta karewa Arshaan? Lallai kai
jaki ne bazan gaji da maimaita fada ba, why da ace uwarka na raye zuwa yanzu nayi
imanin bakin cikin haihuwar wawa da tai irinka ne zai zama ajalinta. Kai anya ma
kuwa bada cikinka ta shigo gidan nan namu b

"Jasimmmmm!!!!!!!".
Arshaan ya fada cikin karaji da wani irin girgiza karfen tsakanin nasu kamar
zai babbagesa,amma da yake a gine yake cikin kasa ko gezau shegen baiyi ba. Ka dan
Jasim yay baya yana dage hannaye sama kamar wanda yay surrunder, sai kuma ya sake
kwashewa da dariya kamar zai fadi ya sake dafe karfen yana fadin, "Shegen kaya ashe
kasan abinda kake. To to naji uwarka anan ta haifeka, sai dai wlhy bazan daina
tantama ba nikan kodan kasancewarka kasurgumin annamimi, butulu,sannan rago mai
labewa a bayan mace domin kubutar da kai. Shin nawa ta siyeka ne har haka?"

"Yanda aka sayo uwarka a gidan karuwai. Why da ga yau idan ka sake kuskuren
zagin uwata, sai na maka lahanin da sai ruhin uwarka ya dawo duniya yana mai cikin
garari Jasim.Wawa jaki kawai maybe ma uwar takace ta shigo mana da cikinka da ga
wajen dan tsautsayi kawai. Ko an fada maka bamusan tarihin tushenta bane a gidan.

"Amma kasan zan iva kasheka na binne gawarka a cikin kurkukun nan ko? Idan ka
manta bari na tuna maka wanene Jasim in Abdul- majeed Aliy Qutb, domin ni a gareka
sai dai kallo sai kuma hange daga nesa koda bakin cikina zai ajalinka. Ko an fada
maka ban san kulle-kullen da ka jima kanayi a kaina bane?, Kana goyamun baya domin
in mun kauda shi nima ka kaudani, sai dai kuma kayi kuskure, domin kafin kaga biri
shi birin ya ganka dan hau. Da ido daya Jasim ke barci,sannan a tafin hannuna kake,
zakuma ka tabbatar da hakan nan gaba jadan". Ya kare maganar yana wata yar iskar
dariya cikin rangaji harya koma wajen zamansa ya sake zama rigija yana dariyar har
lokacin.

Shiru Miran Arshaan baice komai ba, sai dai yana tsaye kamar gunkin da aka
ajiye dan tarihi idanunsa nabin Jasim din da kallo, da alama dai tattaro abin fada
yake, ko kuma maganar Jasim din ce dai ke masa kaikawo dan bai taba tunanin yasan
da wannan burin tattare da shi ba.

** BAYAN KWANAKI BIYAR **

Kwanaki biyar kenan da mika su Arshaan suma a makargama, Jasim kuwa sati guda. Sai
dai kuma Tajwar Eshaan bai sake cewa komai ba game da su, hasalima a yau da ake
saran ganin watan azumin ramadana ya dauka hutun fitowa fada har sai bayan salla.
Tare da daura Sayeed Fayzul-haq akan komai dan zaije Umrah shi da iyalinsa kamar
yanda ya sanar.Tabbas a wannan karon babu wasa a cikin al'amarin Tajwar Eshaan din,
dan haka kowa ya shiga taitayinsa har su manyan masarautar. Duk da akwai abubuwan
fada a bakinsu har game da karasa zaman shari'ar da aka fara amma sun gagara cewa
komai har ya gama jawabin fara azumi da gamashi lafiya yay musu bankwana.

A lokacin da Tajwar Eshaan ke can yana bankwana da jama'ar fada anan Iffah
ce cikin babban bitalmanin kasar ruman bisa jagorancin babban dan Sayeed Khairul-
Bashar mai suna Abdul-Shakhur in Khairul-Bashar tana bada umarnin ware kayan
masarufi nau'i-nau'i domin dorasa a jagorancin rabawa talakawan kasa. Sai matasan
masarautar da ta saka shi Abdul- Shakhur din ya samo har su hamsin da zasu
jagoranci sauran jihohi da wanda za'a kai wasu kasashen da yaki ya samarwa yan
gudun hijira da ma iftila' in rayuwa na talauci.

Wannan al'amari ya matukar jjiga kunnen duk wanda ya samu labari a cikin
masarautar, dan abinda bai taba faruwa bane, duk da duk azumi akan fitar da kayan
masarufi a dan kai jihohi suma kuma ana da kasune ga Tajwar na jihohi bawai a
wakilta wasu suyi aikin ba a cikin masarautar. Sannan a duk shekara tun ba hawan
Tajwar Eshaan din Malikat Bushirat ce ke da wanna karfin ikon matsayinta na
mahaifiya ga Shahan-shan. Sai kuma a yau labarin ya canja akaga Zawjata-almilk kan
komai cikin kuma sauyi.

Kamar yanda labarin ya isa kunnen kowa kuwa yaje ga Malikat Bushirat din da
take zaman tsara yanda zatai fitar da wanna abinci bisa tsarawar uwa kamar kowace
shekara. Ba kuma a bada abincin ma sai bakwai da azumi, sai kuma gashi yau ana gobe
saka ran daukar azumi za'a fara rabon. Kayan da aka fitar kuma sun ninka wanda ita
take sakawa a fitar sau dari. Dan duk wani abinci dake shekara ta uku a cikin bital
mali Iffah tasa an fito da shi ana da kasa a hannun wakilan. Su kuma kasancewar
matasa masu zafin nama da son dama su nuna tasu baiwar amma basu da wanna damar sun
bata goyon baya dari bisa dari, duk da kasancewarta karama a shekaru kuma sun bata
girmanta matsayin Zawjata-almilk, to kwarjini da cikar kamalar ta da barazana ma
bazai bari ko kaso kawo mata wargi ka iya aikata hakan ba.

Tsaf numfashin Malikat Bushirat ya dauke na wucin gadi lokacin da Jazaa tazo
mata da mummunan labari. Ta wani zuba idanunta kamar mai son gano gaskiyar maganar
a jikinta. Kafin ta yunkura ta mike cikin wani irin zafin rai ta shiga bedroom din
ta. Cikin kankanin lokaci ta canja shiri, tana kokarin fitowa Jasrah ta shigo dakin
da sallama, dan tunda aka sallamota da ga asibiti nan sashen ta dawo take zaune, a
kallo daya datai mata ta fahimci bacin rai dake tattare da ita. Itama yanzu take
jin labarin komai a bakin hadiman sashin, dan haka ta biyota daki sanin yanzu yayar
tata zata birkice. Ita mamaki take da yanda gaba daya yanzu wasu halayenta ke neman
canjawa. Tunda ta dawo sashen kokarin ganin ta fahimtar da ita wacece Iffah take
amma taki fahimtarta, gashi kuma yanzu Iffahn ta sake dangwalo wani al'amarin.

"Akia Please kiyi hakuri, zuwanki wajen yarinyar nan a yanzu bashine mafita ba,
sai dai maya zubar miki da mutuncinki. Ni a ganina nemanta ya kamata kiyi bayan
tabar wajen sai muji dalilinta na zartar da hukuncin da kece ke zartar da shi, ko
kuma ki tuntubi Abni kiji tunda dai bazatai komai bada saninsa ba".

"Bani hanya Jasrah".

Ta fada a zafafe kamar ma bataji mi Jasrahn ta fada ba. Cikin dakewa itama Jasrah
tace,"Bazan barki ki fitaba gaskiya Akia, kiyi tunani abinda kike son aikatawa.
Akia na miya canjaki haka? Bayan kuma a baya ba hakan kike ba. Karfa ki manta
shekaru kusan hudu muna kuka akan matsalar dake zagaye da mu ta mutuwar matan Abni,
amma a yanzu UBANGIJI ya kawo mana iyakar komai, a kanta komai ya canja har mutane
suka fahimci makarkashiya ake masa sabanin da da shi kai tsaye kowa ke zargi.
Kamata yay mu rungumi yarinyar nan muyi farin ciki da kasancewarta mata ga danmu
bawai bore ga duk yunkurinta ba. Matsalarmu da ita dama can akan abinda muke zargin
ta aikata ne, amma yanzu mun fahimci ba haka bane ba, to mizaisa bazamu manta komai
ba mu maidata komai dinmu kodan farin cikin da yaronmu ke samu da ga gareta.

Tassss! Kake jin saukar lafiyayyen mari a fuskar Jasrah, idanu kawai ta rumtse
tana mai kauda kanta, yayinda Malikat Bushirat ke wani irin huci. Abune da bai taba
faruwaba, dan ko sanda Jasrah a karama bata taba dukanta ba, shagwabata tai kamar
yar data haifa ba kanwa ba, ta kyautata rayuwarta tai mata raino kamar Kwai a cikin
cokali. Idanunta da sukai jazur ta bude, ta dan girgiza kai tana murmushi mai ciwo.
"Zan iya amsar duk hukuncin da zakimun Akia dan ke uwa ce a gareni ba yar uwa kawai
ba. Amma why bazan taba barinki ki zubar da mutuncinki ba". Tana gama fada ta zare
key din kofar ta fice da sauri ta maida kofar ta kulle
gaba daya. Duk kiran sunanta da Malikat Bushirat keyi cikin karaji batako kulata ba
tai shigewarta dakin dake matsayin nata a yanzun tana hawaye. Ita kam ta fara shiga
rudani akan canjin halayen yar uwar tata, ta sara mike damunta a yanzu. Anya ba
masu son cutar da Eshaan bane suka dawo kanta suka saka kiyayya a tsakaninta da
yarinyar nan. Ita kam yanzu ta fahimci Iffah, tanajin kaunar yarinyar a ranta kamar
tun a da can farko, matsalar data biyo baya ma a dalilin abinda suke tunanin ita ta
aikatane. Amma yanzu kunyar haduwarsuma take ji. Dan bata san da bakin da zata fara
rokonta gafara ba. Amma koba komai ALLAH ya sakama yarinyar tun ba'aje ko'ina ba,
tunda gashi wanda ta yarda da shi fiye da kowa da komai yau shine kecin amanarta da
matar dan uwansa, wannan wace irin mummunar kaddara ce. Hawaye masu zafi suka
silalo mata, dan abune dake mata matukar kuna da zafi a zuciya tunda ya faru, ga
kunyar fitama da takeyi dan ko hadimai shune suke mata akaikaice matsayin matar mai
neman tsohuwar matar Shahan-shan……..✍️

14:23
DAUDAR GORA
Book2
Chapter: 65

A gajiye tibis ta shigo sashen, yana zaune a falo harde kamshinsa ya karade falon.
Da sauri amintaccensa da ke gefen kafafunsa zaune da ga kasa yana ware masa wasu
takardu da suka barbaza ya sake kasa da kansa yana gaisheta.Da hannu ta amsa masa
idonta akan zakinta da ke mata kallon kasan ido ta yanda ita kawai ke fahimtar
hakan. A hankali ya motsa lips dinsa ya Bama amintaccensa umarnin tafiya. Zaram
kuwa ya mike dan dama abinda yake jira kenan. Saboda a yanzu kam shigowarsa wannan
falon sai da notis saboda yanda iyayen gidan nasa ke manne da juna akoda yaushe
suna baje kolinsu yanda suka gadama. Shifa har mamaki yake da jin anya kuwa ba'a
samu canji da ga Shahan- shan din nasu ba zuwa waninsa. Shifa yasan abinda yake
gani kawai.

A hankali ya bude mata hannayensa alamar tazo garesa idanunsa kyam akan
kyakykyawar fuskar ta dake a shagwabe kamar zata saki kuka. Kafada tadan noke tana
tura baki, sai kuma ta fara takawa a hankali zata wucesa, a hankali ya riko hanunta
da dan murmushin iya lips din nan nasa. Gaba dayanta ya jawo ta fado jikinsa. Wani
irin sakin ajiyar zuciya sukai a tare.Tare da rungume junansu tsam-tsam kamar masu
tsoron a rabasu.

K ta dabance".

Ya fada a hankali cikin kunnenta yana sake kankamta.

"Kai ne na daban a cikin daban ai Zakina". Ta fad itama tana sakar masa
manya-manyan sumba a kan kirji. Sai kuma ta dago kanta suka zubama juna ido cike da
kewar juna kamar ba da safe suka rabu ba. Cikin motsa lips dinsa da kyar ya ce"
"Kin gaji ko?".

Kanta ta jinjina masa tana marairaice fuska, sai kuma takai hanunta kan
kyakykywar fuskarsa tana shafa kwantaccen gashin wajen dan tana matukar son sa.
"Amma tunda aikin lada ne banajin gajiyar". Dan sumbatar lips dinta yay a fisge ya
ce, "Da gaske?"

"Yap".

Ta fada cikin fari da kashe masa ido daya.Murmushi ya dan saki da lakace mata
hanci, sai kuma ya maida bakin nasa kan nata ya shiga bata kyakykyawar sumba, ba' a
barta a baya ba ta shiga taimaka masa cike da nuna kwarewar haddace dukkan
karatunsa. Kafin akai wani dogon labari gaba daya yanayinsa ya canja. Dan shifa
Tajwar Eshaan bai san wani yaren dandani haukaci ba. In har aka fara sai an kai
karshe.Sannanake iya samun kansa dari bisa dari kuma dalibar tasa da alama dai
irinsa ce, dan zuwa yanzu duk da ta kasa zama mai juriyar mika wuya yanda yake so
saboda rashin sabo tana kokarta kamantawa musamman a bashi hadin kai a duk sanda
yace kule takance cas. Da ga baya kuma ta dawo tana masa raki da shagwaba, Shiko
yay ta mata murmushin miskilancin nan na..

Bayan sun samu daidaito ta lallabasa yay mata kiran su Babiy, sun jima suna
hirarsu dan a yanzu kullum ne sai ta saka ya kira mata su, sai dai kuma duk sanda
za'ai wayar yana dakin, bai kuma taba yarda shi sun gansa ba ko tayi wata magana a
kansa, tayi-tayi ya barta suna gaisawarsu ita bazatace komai a kansa ba yaki bata
damar hakan, ya dai yarda ya kira mata su su gaisa suma jima suna hira yana da ga
gefenta yana saurare da jin komai.

Bayan sallar magriba ta samu sakon kiran Malikat Bushirat da ga wajensa. Dama
dai suna da shirin zuwa mata sallama, dan insha ALLAHU ana kai azumin farko a gobe
zuwa dare jirginsu zai daga zuwa Saudiyya. Sanin abinda ta kullama ranta tace ya
barta to ta fara vin gaba yazo da ga baya tunda zaije ya ma Malikat Haseenat ma
sallamar, ita kuma da safe Insha ALLAHU sai tayoma su Malikat Haseenat din sallama.
Bai wani kawo komai a ransa ba yace taje, dama yana bukatar yin magana mai
muhimmanci da Mammah din kuma akantane baya kuma bukatar taji.

Tunda ta fito a mota hadimai ke fama zubewa gaisheta. Kafin ma ta karasa


ciki an kaima Malikat Bushirat labarin zuwan nata. A zahirance dai batace komai ba
har Iffahn ma ta karaso. Gaba daya hadiman dake zagaye da ita ma wani irin zubewa
sukai bisa gwiwunsu lokaci guda, dan wani irin kwarjini Iffah'r ta musu naban
mamaki, sannan koba komai ita din dai Zawjata-almilk ce. Hannu kawai ta dan daga
musu dai-dai tana kaiwa cikin kujera da wani irin salon zaman kasaita na kafa daya
kan daya. A hadiman babu wanda bai girgiza da salon Iffah'r ba, dan kowa yasan duk
da take matsayin Zawjata-almilk a gaban Malikat Bushirat dole ta risina kuma kasa
ne wajen zamanta. Sunta satar kallon Malikat Rushirat din da tunanin ko zatace abu,
amma sai sukaji shiru, hasalimal sau daya bata motsa da ga zamanta ba balle a
karanci wani abu da ga gareta.

Wani irin kallo Iffah ta watsa musu da masu alamar fita da yatsunta. Har ko
rige-rigen fitar suke duk da sun so ganin yaya wasan zai kare. Falon ya dauki shiru
na tsawon lokaci batare da wani cikinsu ya motsa ba, hasalima ita Iffah ta maida
hankalintane ga wayar Tajwar Eshaan da ke a hannunta tsabar rainin hankali ma
browsing abu takeyi hankalinta kwance kamar ta manta gaban wanda take.

Malikat Bushirat ta dago idanunta da sukai wani irin kadawar bacin rai ta zuba
mata, tsahon sakanni kafin ta nisa da kyar cike da zafin rai. "K har kina ganin kin
kai wani matsayin da zaki iya jayayya da ni kenan?".

Duk da sarai Iffah ta jita sai batako motsa ba tsahon wasu sakanni. Kafin ta
motsa lips dinta batare da ta daina abinda take a wayar ba ta ce,"naga ai bakya
bukatar amsa tunda har kin fahimci hakan Mother in-law. Kuma duk abinda kikaga
Iffah tace zatayi sai ta yishi ki rubuta ki aje, dan hakan halitata ce bana manta
gabar daukar fansa musamman akan jini na".

"Humm ki taka a hankali, na fiki hatsabibancin yariya. Ki kama kanki kodan


cigaba da rayuwar ahalinki a doron kasa".

14:24
cigaba da rayuwar ahalinki a doron kasa".

*murmushi mai sanyi Iffah ta saki tare da dagowa ta dubeta ido cikin ido. "Barazana
ne hakan in-law? To in barazana ce ki sanarma bokanyar taki bata iya aiki ba tunda
har bata sanar miki ahalin Iffah sararin samaniya ne ba ganinsu sai da ga nesa akan
yaro da babba. Ki fada min miyasa kika kirani da ina da yan ayyuka a gabana masu
muhimmanci, idan kuma kin kirani din ne dan kawai ki jajjadamin karfin ikon naki da
kasancewarki damisa da bata da banbanci da damisar takarda a wajena to".
Ba karamin dukan zuciyar Malikat Bushirat kalmar (Bokanya) nan yay ba, dan
maganganu ma da suka biyo baya sam bata jisu ba ko fahimtarsu, amma sai ta dake ta
basar kamar shima bataji ba. Sai tama saki wani murmushin kasaita cike da izzarta
tana ma Iffah'r kallon ke karamar kwaruwa.

"Bazan hanaki wasa da Zakanya ba, koba komai zan ajiye darasin da zai zama
izna ga yan baya gareki yarinya. Ina son sanin dalilinki na shiga hurumin da ba
naki ba kan shiga bital mali ki fidda kayan azumi".

Dan murmushi Iffah tayi yanzu ma, sai kuma ta ajiye wayar hannuta ta sauke
numfashi mai nauyi. "Ammie na yarda ke Zakanya ce, sai dai ki sani duk karfin
bajintarki da iya farauta a saman kowa watarana tsufa kan iya sa ki rissina ji inki
ta zama sarauniya bisa karfin ikon Ni bance nafi karfin kaddara ba, sai dai ki sani
a tafin hannunna kike ke da komanki. Bana son cigaba da jayya da ke ko nuna karfina
akan karfin ikonki da har mutane zasu kalla gazawarki ko kaskancinki a cikin
idanunsu saboda daraja. Eh tabbas daraja, darajar abinda kika haifa ya zama mai
daraja a cikin al'umma badan yafi kowa ba a wajen ALLAH ko ke da kika haifesa kinfi
wani. Ammie why inada abubuwan ban mamaki da daga labulen sirrinki sau daya kawai
sai ya hana wannan idanun naki barci. Sai dai bazanyi hakan ba, bazanyi ba saboda
mutunci da kimar danki har sai in kin bijirema hanyar da nake son ki dawo. Kwana
biyar da suka wuce naci karo da bakon ganyen shayi mai hadari matsayin wanda
Shahan-shan zai sha. Na kuma cin karo da madara itama, dana bincika sai na gane da
ga sashenki madarar take, ba kuma na raba dayan biyu shima ganyen shayin naki ne.
Na gagara fahimtarki ko inda kika dosa a zahirance. Kowa dai ya kalla fuskar Maleek
da taki basai ya sake kallo ba yasan jininki ne shi,dan kamminku a bayyane suke ta
abubuwa masu yawa. Kema a karan kanki kin fada kin kuma maimaita shi din danki ne.
To wai nikam wane buri ne kike son cimmawa mai alaka da makiyi a tsakaninki da shi?
Kin ko san da ace yasha ganyen shayin nan ko madarar nan illar da zatama rayuwarsa
sai tafi wadda zatama tawa rayuwar? Sannan ke da kanki sai kin dawo kina kuka da
dana sani. Idan ma wani ke baki wadan nan abubuwan matsayin wani kariya washi ko
gurbata tawa rayuwar to tabbas ki farka. Ki farka why tunkan guri ya kure miki ki
rasa kofofin fita a wannan masarautar. Na rasa mikike nema? Mikike bukata? Mi
kekike son zama bayan abinda kike a yau dinki da har in kika rike zata jagoranceki
zuwa gobanki cikin salama kamar yanda Jaddah take a yau ga kowa". Taja numfashi mai
nauyi tare da dafe kai cikin kunar rai, sake dagowa tai tamkar bataga kallon wutar
bala'i da tsanar da Malikat Bushirat din ke binta da shi ba ta cigaba da fadin………✍️

DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 66

."UBANGIJI ya halicceki mace bayan akwai maza da yawa dake kwaikwayo son zama macen
amma basu isa komawa ba. Ya halicceki kyakykyawa, bayan awai wasu da yawa da kyawun
da bai kai naki ba suke fafutukar nema ta hanyar sabama UBANGIJI suna amfani da
abinda yace haramunne garesu. Ya baki lafiyar jiki babu ta inda kika nakasa. Bayan
ga dubunki can su nakasar itace jarabawarsu. Ya baki lafiya
matsayinki na yar adam. Bayan ga dubunki can kwance a asibitoci da gidaje basu da
kudin shan magani, masu kudin ma basu isa iya sayawa kansu lafiya ba koda sun kai
karuna dukiya. Ya azurtaki cikin nagartaccen addini, bayan ga dubunki can na bautar
wanin ALLAH cikin batan da su a karan kansu basu san bata bane ba. Ya azurtaki da
tarin dukiya. Bayan akwai dubunki da abincin yini daya ma gagararsu yake ci saboda
basu da kwabo na saya. Ya azurtaki a cikin katon gidan aure dana haihuwa, karkashin
kyakykyawar nasaba bayan akwai dubunki da a kan titi ko cikin bukka suke rayuwa
badan kin fisu ba. Ya azurtaki da karfin iko na mulki, bayan akwai dubunki da su
wanna matsayin naki suke kwadayon kaiwa, ke wasu ace ma su din hadimanki ne kawai
farin ciki yake sanyasu. Ya azurtaki da ilimin addini dana zamani, bayan akwai
dubunki da suke zagaye da jahilci, wasu ko suna son karatun rashin mai tallafa musu
Yasa suka hakura suka zama masu aikata miyagun laifuka koda zukatansu basa so, sai
dai basu iya banbance abinda ya dace da wanda zai dace da tasu rayuwar. Ya azurtaki
da da daya tilo tamkar da dubu da nagartaccen mijin da duniya bazata taba mantawa
da su ba, bayan akwai mata da yawa da su jarabawarsu mazajen aurensu ne da yayan da
suka haifa. Duk da ya miki wadannan abubuwane badan kinfi sauran halittun duniya
ba. Badan bazai dandana miki mutuwa ba. Badan bazai iya jaraftarki ki kasance su
ba. Badan kinfi karfinsa ba. Sai dan kawai ya miki talala har zuwa ranar da zaki
tabbatar ke din bakomai bace a cikin komai. Ke din yar adam ce, yar adam din nan da
aka halitta da ga yunbun kasa, yar adam din nan mai rauni, mai barci, mai kashi,
mai ciwo mai jiran kwanakin mutuwa. Badan kiyi alfahari da duk wadan nan abubuwan
ba kuma ya halicceki, ya baki su ne domin jarabawaki itace su, kamar yanda ya bama
wasu sabanin naki domin jarabawa suma. Dan ALLAH mi kike bukata a bayan duk
wadannan? Minene burinki da fatanki da fafutukar ki da har halaka rayuwar yayan
wasu ke sakaki a farin ciki amma baki son ko kuda ya rabu daya naki tilo da sunan
cutarwa? Ke uwa ce, ya kamata kiyi hasashen zafi da ciwon da zaki iyaji dan akace
babu wannan tilon dan naki kafin idonki ya rufe ki zama sanadin hana wasu. Ni
Fhareedah bint Zayyan b yafe daukar fansa ki shaida haka, bakuma zan gajiya da fada
miki na, amma ke uwa ce ina mutuntaki da wanna matsayin, dan ba'a bani tarbiyyar
raina koda wanda ya girman da kwana daya ba a duniya balle ke da nasan zaki iya
haihuwar wanda ya haifan musamman ace Maleek mace yazo ba namiji ba. Sannan koba
komai kin haifamin gwarzo kuma barden miji da tun kan bakina ya tabbatar da
alfahari da shi gabbaina isarwa suke. Shi mutum ne adali, mai addini, mai yawan
bautar ALLAH da mika masa lamuransa. Baya jin wani alfahari da matsayin da ALLAH ya
bashi kamar ke face takatsantsan dan yana kallonsa a matsayin jarabawarsa. Akwai
tarin abubuwa masu dunbin yawa da nake bincikawa akanki da alakarki da halaka yaran
mutane, idan kikace zaki cigaba da bina da izzarki why why Ammie baza'a ganeki ba.
Ki bini a sannu-sannu ni zan kaiki inda kike son zuwa bake zaki kaini ba. Kamar
yanda ni na kawo kaina masarautar nan bake kika kawoni ba. Kamar yanda ni nai
amfani da Arshaan da Jasim da Haifah basu sukai amfani da ni ba, ke shaidace kuma
ga irin makomar da suka kasance duk da somin tabi ne ma na fara musu.Kamar yanda ni
na bama Shahan-shan din da kike takamar da shi garkuwa bashi ya bani ba har kike
hakilo da hura hancin wai ya janyeta gareni.Kin san ALLAH kiyi maza ki dawo
hayyacinki ina tsoratar miki shiga jerin mutanen da zan kwancema zani a bainar nasi
cikin Masarautar nan dank kuma ya musu hukunci, kiyi azamar ajiyewa ki labe bayan
mutuncin danki hukuncina ya kasance tsakanin ni da ke ne kawai. Dan saura kiris a
fara bankada, idan kuma aka fara akwai gagarumar matsala, dan na fahimci ke kanki
har yanzu baki gama sanin wanene danki ba da ainahinsa, kinama rogo kallon kitsene
kawai, sannan kina kallon kasurgumin Zaki ne da fatar mage" ta saki murmushi tare
da takawa gabanta a hankali. Hannunta ta kamo ta daura saman cikinta, "Ina tayaki
murna da albishir din insha ALLAHU kafin mu dawo daga hutun in amarcinmu da iznin
UBANGIJI zamu dawo da jikanki a wannan babbar garkuwar, dan haka kibar wahal da
kanki akan sai Maleek ya auro wadda kike son ta haifa miki shi dole ko nisanta
shakuwar iyayensa da zata zama sanadin samar da shi ta hanyar madara. Da ga kuma
randa kika tabbatar da samuwarsa, ki fara irga kwanakin nadamarki da dana sani har
zuwa ranar haihuwarsa. Hukunci da karfin ikon Iffah a saman naki, yanzun ne zai
fara Mother in-law". Ta dan kyalkyale da dariya da sakin hannun, yako tafi yaraf
alamar duk wata mahada mai motsi a jikin Malikat Bushirat din ba aiki take ba a
yanzu. A hankali ta koma kasa kusa da kafafunta ta zauna, tare da hannu ta dago
afar ta fara matsa mata. Zabura Malikat Bushirat tai kamar wadda aka kodama mari ko
ta suma aka zubawa ruwan sanyi drum guda, sai hakan kuma yay dai-dai da shigowar
Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed. Yar dariya Iffah tai kamar bata san da
shigowarsa ba ta cubi Malikat Bushirat din. "Ammie irin wannan zabura haka na sake
tabo wajen da yay dayin kenan?".

Idanun Malikat Bushirat ne suka sauka akan Tajwar Eshaan din dake takowa a
nutse idonsa a kansu fuskarsa da dan sakewa. Sai dai kafin ta iya cewa komai da ga
daurin goro ko makircin Iffah zatace mane oho Tajwar Eshaan din ya karaso yana dan
gyaran murya. Dagowa Iffah tai ta kallesa har yanzu fuskarta da murmushi. Cikin yar
shagwaba ta ce, "Yauwa ai garama da kazo, Ammie na nan zata kasheni da dariya, tace
fa na matsa mata kafarta ya mata dan nauyi saboda zaman waje daya amma da nayi-
nayi sai ta fara fadin ya isa a bari ta huta".

Wani dan moso yayi iya lips yana dauke idanunsa da ga kallon da yakema Iffah'r
na kasa-kasa ya maida kam Malikat Bushirat da mamakin duniya a makircin
matsiyaciyar yarinyar ke neman dauke numfashinta. A hankali
cikin dan sanyin nan nasa da kamewa ya ce,
Ammie shiyyasa nace ki dinga motsa jiki tun last year, wannan zaman waje dayan da
kuke ai ba gata bane, gashi nan shi ya kashema Jaddah kafafu anata fama".

Da kyar ta iya dannewa ta dan saki murmushin karfin hali da yafi kuka ciwo ta
ce.
"To ya za'ayi Saiful-malik, mizamuyi da wani motsa jiki a wannan shekarun namu?".

Kafin ya bada amsa Iffah ta amshe da fadin, "Ai Ammie kike da motsa jiki kuwa,
dan motsa jikin nada amfani sosai, kuma ya kamata ko dan cikin badda kama kuna fita
kwamaga yanda talakawan kasa ke yan sabgoginsu, sannan koba komai ai hakama karin
imani ne da lafiyar jikin harma da ta zuciya".

Wani irin ji Malikat Bushirat tai kamar ta shako wuyan Iffah, dan ta fahimci
maganace cikin ta jefa mata. Itakam ta farama tunanin anya yarinyar nan mutumce
kuwa ba aljanaba a sufar mutane? Ya kamata a bincika mata kam dan al'amarin ya fara
girman tunaninta. Amma a zahiri sai ta cije tai dan yake. Tajwar Eshaan da ke dan
jinjina kai batare da ya fahimci komai ba shi kam a zancen idanunsa dake akan Iffah
ya lumshe kadam da budewa lokaci guda. "Ammie shawaran nan nata mai kyau ne, ni
kaina naso na miki tayin hakan tuni sabgogina basu barni na zauna ba. Amma
Alhamdullah tunda gata yanzu bayan ni da Aunt kin sake samun diya daga ALLAH nasan
zata kula mana da ke kamar mu din. Sannan kusantar al'ummar mu yanda ya kamata a
zahirance zai kara saka mana son su da kaunar su a zukata kamar yanda ta fada.
Zakiji dadin hakan, ki samu lokaci ki fara gwadawa koda tare da itane ni mai yarje
muku ne".

"Uhm kai dai. To ALLAH ya shige mana gaba kawai".

Amin suka fada a tare shi da Iffah, sai dai a ransa yasan bata amshi lamarin
ba. Dan haka ya basar da zance ya dakko mata na tafiyarsu.Cikin mamaki take
kallonsa sai dai batace komai ba. A ranta kam wani irin zafi takeji mai kuna. Har
itace sai yau Saiful-malik ke sanarma zaije Umrah, Umrah din ma na azumi baki daya.
Kai anya bata fara rasa danta ba kuwa? Bata fara rasa danta daga jikinta ba kuwa?
Jifa maganganun da yarinyar nan ta fada mata a yanzu, irin wanda ko mahaifiyarta
sanda tana a raye bata jin ta taba fada mata su, amma shi ya hau ya zauna Kamar ma
bai fahimci manufarsu ba. Tabbas akwai matsala, matsala babba da uwa sam bata
lissafo ba a lissafinta. Yanda fa rawar take neman canjawa dole ne shima kidan ya
canja inba hakaba zata kona Masarautar nan ne baki daya why, dan bazata dauki
faduwa a saman nasararta ba. Never for ever……..✍️

DAUDAR GORA
Book 2
67

…. Suna barin sashen cikin tashin hankali tashige ciki tai kiranye uwa. Cikin
kankanin lokaci kuwa sai gata ta bayyana alamar dama a kusa take. Ido rufe Malikat
Bushirat ta zayyanema uwa duk abinda ya faru tsakaninta da Iffah. Yanda uwa ke huci
sai ya koma tsorata Malikat Bushirat din, tuni nata fushin da harzukar suka bace.
Zabura tai gefe jin sautin kakkausar muryar uwa mai tsananin amo acikin
kunnenta.

"Wannan fadan ba naki bane damu takeyi!!! Lallai damu takeyi. Ita wacece? Yar
wacece? Mitake takama da shi?! Zan tabbatar da ba uwarta kawai ba, hatta dukkan
ahalinta sai sunyi nadama da dana sanin kasancewarta jininsu!!!!. Wanda suka fitama
sunja bata kai musu ba balle ita haihuwar jiya-jiya.".

Ta fada cikin wani irin karaji da dukan kasa da tafin hanunta, tare da rantsuwa
da wani kasurgumin gunkin da take bautawa wanda sam Malikat Bushirat ita bama ta
fahimta ba. Ji Malikat Bushirat din tai hatta dakin girgizawa yake, tamkar tashin
guguwa uwa ta bace bat a dakin. Wani irin numfashi ta sauke mai nauyi, tare da zama
jagwaf. Ta jima numfashinta na kai komo kafin ta samu daidatonsa, sai kuma ta saki
murmushi mai matukar kayatarwa da dan tabe baki ta dage kamafada irin ko'a jikinta
din nan,wanna kuma fadan yimata shi za'ai.

Ni dai nace, "Humm" 🥱😂🚴

*. WASHE GARI*.

Kasancewar ba' a ga wata a jyan ba basu wuce ba. Hakan sai ya saka Iffah yini a
sashen Malikat Haseenat. Sai bayan sallar la'asar ta dawo. Lokacin su Tajwar Eshaan
da was manyan masarautar na'a can saman ginin da agogon da duk ta inda ka bullo ta
birnin Dahab City din zaka gansa da na'urorin ganin wata, Cikin amincewar UBANGIJI
kuwa sai gashi an gansa, Dan danan kafofin yada labarai suka fara sanarwa da yawn
Shahan-shan, dan shi da kansa yake duban wata tun hawansa mulki babu wani wakili.

Alhamdullah washe gari an wayi gar da azumin watan Ramadan a bakunan mutane.
Yayinda jirgin Tajwar Eshaan da Iffah sai hadimai hudu mata shida maza. A ciki
akwai hadiman sashen Malikat Haseenat da Iffah ta roka ta bata su su biyu har da
hadima Banou. Lokacin da akace mata zatabi Iffah rikicewa tai harda kukanta a boye.
Sal Diwa amintacciyar hadimar Malikat Bushirat ta zahri, wadda itama dai Iffah!r ce
ta nema ta bata a gaban Tajwar Eshaar babu yanda ta ya ta bata, sai hiyu da suka
kasance daya a cikinsu hadimar da Uwa tace zasu batane samun wanna damar yasa suka
cusata a ciki.Tafiyace ta sirri dan haka babu wanda yasan da ita a Kasar, ko'a
cikin masarautar a ba kowa ya san da Shahan-shan din za'ai ba. Kowa ya dauka
Iffah'r ce kawai zatai gaba kafin su Malikat Haseenat da ake hasashen kila sue su
samesu acan tunda suma sukanje duk kusan bayan shekara uku, tun bayan hawan Tajwar
Eshaan din kuma sau daya sukaje,shiko tunda ya hau mulkin ma bai taba ma zuwa ba
sai yanzu.

Lokacin da jirgi ke barin kasa wani irin kudindinewa Iffah tai a jikinsa na
toro. Ta bashi dariya dan ya fahimci duk irin abubuwan nan tsoronsu takeji. Ga
Elevator ma in zata shiga yanda take kasancewa balle kuma anan, tafa gwammace tabi
stairs duk wahalarsa idan ita kadai ce. Rungure kayarsa yay dan su kadai ne,
hadiman na nasu sashe daban. Koda jirgin ya gama dai-daita bata bar jikin nasa ba:
sai ma barci da yay awan gaba da ita mai nauyi. Ajiyar zuciya ya saki yana mai
sumbatar idanunta. Azuciyarsa ya ce, (Fitinanniyar yarinya nima nadan huta da
surutunki) a zahiri kam sai ya gyara mata kwanciya nutsuwa na sake saukar masa. Shi
kadai yasan kaunar da yakema yarinyar nan, ALLAH dai yasa karta zama ajalinsa.

😂Oh oh masoyan asali. 😉


*_SAUDI ARABIA_*

Mamaki hade da al'ajabi ne ya mamaye Iffah lokacin da suke fita a cikin jirgin
hannunta cikin nasa. Wasu zuka-zukan motocine na alfarma da tawagar masarautar
Saudiya, yayinda Sultan a Saudiyya ne da kansa yazo tarbar Tajwar Eshaan ibn Haysam
Abdul-majeed Ally Qutb ba sako ba. Cikin farin ciki sarakunan biyu masu karfin fada
aji a duniyar musulinci suka tarbi juna. Sam Tajwar Eshaan bai saki hannun Iffah ba
har suka rungume juna da Sultan din. Bayan sun saki junan ne ta dan rissinar da
kanta alamar girmamawa ga Sultan din.Fuskarsa kawance da murmushi yay mata kallo
daya da musulunci ya shardanta ya dauke kansa. Ya fai mata barka da zuwa DAULAR
MUSULUNCI cike da mutuntawa a gareta duk da yasan zai iya haihuwarta. Dan manyan
yaranta maza twins guda biyu suma bazasu wuce 20years ba karnar Iffah'r..

A hankali ta sauke ajiyar zuciya tana lumshe idanunta jin sanyin ac da kamshi mai
shegen dadi ya ratsa hancinta lokacin da suke shiga daya daga cikin manyan motocin
da sukazo tarbarsu. Dubanta Tajwar Eshaan yay tare da rungumota jikinsa da kyau.
Tako late kamar yar mage tana shakar daddadan kamshinsa. Ashe Iffah ba komai ta
gani a airport din nan ba. Sai da suka shiga babbar daular da lissafin dukiyar
cikinta ma da kawatuwa bata lokacine. Tabbas tasan Daular ruman ta had, irin
haduwar da babu wanda zai shiga bai yi santi ba. A tunaninta da anya akwai
makamanciyar irin daularsu a duniya? Amma a yau ta tabbatar akwai, dan duk da
daular Saudiyya bazatafi tasu ba, suma tasu bazata fita ba, dan nan clin ma dai
badaga baya ba Dan in za'a baka zabima zaka ya kasa banbancewa ne tsabar shiga
rudani.

An musu tarba ta mutuntawa da tsantsar girmamawa, tare da masauki dan gaske da


ko'a kasarsu iya abinda zasu iyama kansu kenan. Tattare suke da gajiya, musamman
I/fah daba sabawa tai ba ga kuma azumi, saukin ma farkon farawa ne. Da kyar ya
lallabata tal dan wanka ta kwanta. Kafin kace mi barci yay awan gaba da ita.

Bata samu kanta ba sai la'asar, shima da kyar ya tadata sanda zai wuce
massalaci. Bayan ya dawo yace ta shirya zasu wuce madina ne da ansha ruwa, da ga
haka ya fice ita kuma wasu mata sukazo mata da kaya inji matar sultan. Sun jirata
ta shirya sukai mata jagoranci zuwa sashen matar sultan din, inda ta samu tarba ta
mutuntawa da har ta dinga jin kanta ya kara girma itama a yau. Dan duk da matar
sultan din ta girmeta sosai janta ta dinga yi a jikinta cike da kulawa harda cewa
itafa tana so ta saki likinta da ita ne dan sun zama kawaye. Murmushi kawai Iffah
tayi mai sanyi. Ta wani nutsu kamar ba Iffah'r nan mai shegen surutu ba mai addabar
Tajwar Eshaan. Magana ma an koma amsata ne dai-dai cikin nutsuwa da kamewa ita a
dole ga matar Shahan-shan na kasar ruman (Ashe akwai a inda bakin Iffah zai mutu
haka (😂). Suna a tare har aka sha ruwa, a tare suka gabatar da sallar magrib sannan
suka fito kayataccen falo karami na musamman da aka shirya musu kayan alatu na shan
ruwa. Daga ita sai uwargidan Sultan da Shahan-shan din ta. Sai wani irin binta da
kallon nan nasa na kasan ido yake kamar zai hadiyeta dan ta masa matukar kyau cikin
kykyawar bakar abayar data haske farar fatarta ga walwalin fararen duwatsu da akai
mata ado dasu. Itama dai uwargidan Sultan irin kayanne a jikinta. Haka shima da
Sultan din kayansu iri gudane. Lallausar farar jallabiya mai tsadar gaske an daura
bakar alkyabba da akaima adon golden da mayafi fari tas a saman kawunansu. Kamshi
dai nasa ne, dan daga su sai turarrukansu sukazo kasar. An sake gaisuwa irin ta
manyan attajirai masu mulki da karfin iko, sannan a nutse sukai buda baki mai sauki
(ba irin na su bily ba da sai anji ciki yay nak babugurin tura kosai 🥱), Karancin
lokaci ya saka sarakunan biyu mikewa zuwa gabatar da sallar isha'i. Suma kuma su
Iffah suka kora bedroom din uwarg/klan Sultah suka gabatar da tasu. Suna idarwa
basu zauna ba, dan tafiya tsakanin nan da Madina akwai nisan gaske, dan ma
lafiyayyun motocine. Sai lokacin Iffah ta san ashe tare da Sultan din da matar tasa
ma zasu wuce. Tofa wayaga in da ranka kasha kallo, dan kuwa dal acikin zukekiyar
motar da zasuyi tafiyarma dai an shirya musu abincine, ga an shiryar motar daga
aiki kamar wani daki ha musamman. Iffah dai da al'amarin ya zame mata sabo ga
kauyanci ga son nuna class t3, haka mutunivar tamu akaita basarwa kamar komai ba
komai dai kun gane ai 😉(Kuka yarda naje gurin nan alkur'an sai na nuna hali, dan
kowa sai yasan Bilyn Abdull daga 9ja nazo 🤣😆🚴).

A yanzun kam sarakunan biyu sun baje filin hirarsu a nutse ga matansu a
gefensu. Har takai ita dai Iffah ta fara ma hamma. Cikin mamaki Tajwar Eshaan yake
mata kalion nan nasa na kasan ido, dan ya fara sakama yawn barcin nan nata alamar
tambaya. Abu kadan ta fara hamma, yanzu zata tashi anjima kadan ta sake kwanci.
Kuma bazaka taba ji tace barcin yaisheta ba. Anya kuwa? (Sa a bincika mana mai
rumawaja🚴).

* MADINA BABBAN BIRNI BURIN ZUWAN DUK WANI MUSULMIL*

Duk da dare yayi kai tsaye massalacin MANZON ALLAH (S.A.W) suka wuce, inda nan ma
suka samu tarbar da ga shugaban garin na Madina da tawagarsa cikin girmamawa ga
Sultan din nasu a Saudiya gaba daya da kuma babban bakonsa shugaban kasar ruman.
sai da suka gabatar da salla raka'a biyu sannan sukai zaman jira karasawar lokacin
asubahi Basu bar mascalacin ba sal bayan sallar asuba. Yanzun ma dai wani katafaran
gida aka kaisu. Gida daya amsa sunansa gida bawai muna gida ba. Gajiyar da ke
tattare da kowa yasa ruwa kawai suka watsa kowa ya kwanta musamman ma Iffah dake
jin kamar zatayi adungure tun a massalaci…..✍️

DAUDAR GORA
Book 2
68

...……….Lokacin da azhar ta gabato Tajwar Eshaan ya tashi yay wanka ya kimtsa babu
alamar Iffah zata motsa, kwance take sharkaf tana kwasar barci kamar wadda ta mutu.
Zama yay a bakin gadon ya zuba mata ido, tare da kai yatsunsa saman goshinta da
wuyantan amma babu alamar wani zafi da ke nuna tana a cikin ciwo. Da kyar ya tadata
tana faman tura baki gaba, ya kafeta da kaifafan idanunsan nan, sake tunzura bakin
tai ta kauda kai. Sai shima ya dan girgiza kan a fusge ya furta, "Ki daina turamin
wannan bakin na dinga kai azumina lafiya batare da ya raunana ba. A haka za'ai
ibadan Nigar?".

Kwalkwal tai da idanunta kamar zata saki kuka tace, "Nima zuwa fa barcin kawai
yake, konace bazanyi ba sai na kasa". Shi dai kallonta kawai yake zuciyarsa na raya
masa abubuwa masu yawa. Amma sai bai furtaba ya ce, "Okay tashi ki shirya muje
massalaci ga su Sultan na jiranmu". Babu yanda ta ia dole ta tashi ya taimaka mata
ta shirya din, dan a hakan ma sai faman lumshe masa idanun take da sakin hamma. Shi
dai lallabata yay suka wuce dan ya fahimci abin bana lafiya bane. Kilama Aljanun
nata ne ke sakata barcin dan kar tai ibadar....

(A gurguje Please munada sauran aiki, gashi nagaji walle. Gara muyi mu gama kowa ya
huta ).
Rayuwa a Saudiyya wani rubutaccen al'amari ne da Iffah bazata taba mantawa da shi
ba a rayuwarta, dan rubutaccen labarine tsakaninta da Maleek dinta mai zaman kasan
ga ma'abocin bibiyar labarinta, amma ta tattara ta killacema zuciyarta kawai kuma
sai ku kiyasta da hasashenku. Duk da dai ta samu nakasun raunana a dalilin barcin
da bata san kansa ba balle karshensa. Amma duk da haka tana matukar yaki da shi da
ganin tayi cikakkiyar ibada. Dan abu mafi birgeta shine yanda Tajwar Eshaan ke
tsaye akan kafafunsa koda yaushe babu wasa tattare da shi ko nuna gajiyawa a dare
da rana. Gaba daya ya maida hankalinsa a bautar Sarkin sarakunan nan mahaliccin
duniya da kayan cikinta, mai rahama da mukullin aljanna. Sarkin da babu kamarsa kai
koda kwatankwacinsa ma babu. Gaba daya ya mika lamuransa garesa cikin kaskantar da
kai da zubda gwiwunsa bisa kasa. A duk sanda yake addu'a zaka samesa da hawaye
share-share da inba gaban UBANGIJINSA ba bazaka taba gani ba. Kullum cikin gayama
ALLAH yake kan samun warwarar al'amuran da suka shige masa duhu musamman akan
mutuwar yaran da basujiba basu gani ba a daliln aurensa. Duk da wannan jajircewar
tasa kuma yana bata kulawa a dan kankanin lokacin da suka daukarma kansu na hutawa.
Dan ko bayan kammala Umrah din su bai lamunce su zama a karkashin inuwar lalaci ba.

A gefe kuwa wata Irin shakuwace ta shiga. tsakaninta da uwargidan Sultan. Mace
hamshakiya ma'abociyar kyawawan halaye da nuna tsattattacen iko saman na kasa da
ita. Nutsuwa sosai Iffah tai tana koyan abubuwa, yayinda itama bata tsaya boye-boye
ba ta fito tana gyarama Iffah'r duk abinda zai bata martaba da kima a wajen mijinta
da al'ummar da mijin nata ke shugabanta. Dan tayi dubi ne da karancin shekarun
Iffah'r da ma labarin data bata na cewar ita iyayenta basu da alakan mulki. Ba
halayyar Iffah da dabi'u ba hatta jikinta wani irin gyara yake samu na musamman ga
uwargidan Sultan din.

Hadimanta kam tunda sukazo bata gamsu sun ganta sau cikakken biyar ba. Hakama
duk dokinta da tsammanin zal hadata da su Babiy tunkan su taho babu alamar zai yi
hakan. Har magana ta masa cikin hikima amma sai baice mata komai akan hakan ba.
Dole ta hadiye komai ta nuts bisa shawarar uwargidan Sultan din.

Shanyewar tai kuwa, dan yanzu Iffah an koyi halin dattako da shanye abu a ral,
sai dal fa à gaban Tajwar Eshaan bakin baya mutuwa, idan kin jita shiru barci take,
a lokacine kawal zai huta da tsiwarta.

Alhamdulillah yau an kai azumi na ashirin da shida, a yau ne kuma su Iffah sukayi
ziyarar bankwana cikin dakin ka'aba ita da Tajwar Eshaan da Sultan na saudiya, da
uwargidansa, sai wasu manyan masarautar tasu. Iffah tasha kuka lokacin da taganta
cikin tsakkiyar dakin ka'aba, Abune da bata taba zaion kasancewarga ba koda a cikin
matarkinta. Kal ita ketare kasar ruman ma bata taba zaton tana da rabon yi ba a
rayuwarta. Amma yau sai gata da kwanaki ashirin da biyar cikin kasar Saudiyya, tare
da mijin aurenta shugaban kasarta. Hannunta kawai ya rife cikin nasa alamar
lallashi har suka fito, suna shige mota kuwa ta fada jikinsa ta kankamesa. Murmushi
yay mai sanyi da dagota yana mata yan harara tare da lakace mata hanci. "So kike ki
karyamun azumi ne?"

Baki ta dan tura tana wan kikkitata Idanun dake cike da hawaye, a shagwabe tana
war idanun da yanayin mamaki ta ce, "Dama maza azuminsu a karyewa ne?". Murmushi
kawal yay ya dauke kansa, sai kuma ya sake juyowa a yanayin wanda ya tuna wani abu,
kallonta yay da ga sama har kasa kafin ya jeho mata tambayar data daure kanta da
bata yar kunya-kunya. "Mrs Eshaan kin sha wani magani ne dan kar kisha azumi?". Da
kunya-kunya mamaki-mamaki ta dubesa, sai kuma ta girgiza kanta alamar a'a. Itama
kuma sai kirjinta ya shiga harbawa da sauri-sauri. To al bama watan azumi kawal ba,
idan bata manta ba rabonta da ganin proud din ta fa kamar tun wanda ta gama da
kwanaki kadan ya ziyarceta bafa ta sake ba. Kai kodai ta sake ta manta, to idan ma
ta sake din ai a watan nan ne na Ramadan ya kamata ta gani farkonsa, juya mata
kanta ya fara yi saboda neman takurama kanta da tai na sai ta tunano. "Kinga relax
karki takurama kanki"., Ya fada a hankali yana kwantar da ita a kujerar.Gaba daya
jiyay yama kagara su koma cikin masarauta, suna isa kuwa masaukinsu aka zarce da
su. Duk da an bude mata kamar yanda aka bude masa kofa shima sal ya fito da ita ta
inda ya fita, basu fi zaman mintuna goma ba doctor din da ya bukaci gani ya iso
tare da uwargidan Sultan da hankalinta ya tashi da tunanin ko kukan da Iffah tayi
ne ya zame mata matsala,

ita Iffah sai ma abin nasu ya bata mamaki da dariya,ta kal dubanta ga Tajwar
Eshaan da yay zaman kasaitar nan tasa. Cikin langabe kai ta masa magana da ido
alamar wai mike faruwa? Dauke kansa yay gefe a ransa shi kadal yasan miyake ji na
farin ciki, ya kagara doctor din tace wani abu. Amma a zahiri baka isa fassara
abinda ke ko"a kan fuskarsa ba balle zuciyarsa. Doctor da tai yan gwaje-gwajenta a
gabansu abinka da gidan manya ta dago tana murmushi, cikin girmamawa ta fuskarci
uwargidan Sultan ta mika takardar da tai yan rubuce-rubuce.

"Ya ALLAH"

Uwargidan Sultan ta fada fuskarta da kayataccen


murmushi. Ta kai dubanta ga Tajwar Eshaan da ke jin kamar ya fisgo takardan
hanuntan amma ya dake a zahiri. "Ina mai farin cikin kasancewa ta biyu bayan doctor
akan sanar muku samun karuwa da mukai, ALLAH ya sauki Zawjata-almilk lafiya". Wani
irin lumshe idanunsa yay da sauke sassanyar ajiyar zuciya kamar wanda aka zarema
numfashi. Yayinda Iffah tai fakare tana kallonsu cikin rashin fahimta sam. Dan ita
kanta ma sat ya toshe kawai a wanna gabar. Har suka gara bidironsu Uwargidan Sultan
ta wuce bata iya tofa komai ba..

Wani irin dagata yay bayan ficewar kowa a falon ya shiga juyi da ita. Kawal ita sal
abin ma ya bata dariya ta shiga kyalkyalawa. Bai hakura ya direta ba sai da yaga ta
fara date kal alamar jujuyatan da yake akwai matsala. A tare suka dinga sauke
numfashi, ya tsareta da idanun nan nasa masu kaifi ga kayataccen murmushi mai
matukar tada da yakan dace baka gani a fuskarsa ba, Sal dal kuma a zahirance bakin
ya gagara cewa komai. Sal da ya mula dan kansa a hankali ya furta "Mrs Eshaan kin
mallakeni da komal na. Da gaske fa ni din bawanki ne". Da sauri tasa hannu ta rufe
bakinsa tana zaro idanu da girgiza kanta. Cikin rawar murya kamar mai shirin sake
masa kuka ta ce, "Please Sultan ka daina fadar haka karma yan kasar ruman suji
sumin yankan rago. Kai fa shugabana ne, sannan ashekaru ka fini, gaka mijina,uban
yayana", Hawayen suka silalo mata a hankali. Hannunsa ta kamo ta daura akan
cikinta. "Nagodema ALLAH da ka kasance mahaifinsu badan ya baka daukakar mulki data
dukiya ba. Domin su a duniya aka samar mana da su a cikinta kuma zamu tati mu bari
wataran. Ina alfahari da kai ne matsayin uban yayana saboda nagartarka da
adalcinka. Tsoron ALLAHn ka da kyakylyawar zuciyarka. Maleek kai na dabanne a cikin
daban. Ba yan kasar ruman bane kawal suka dace a dalm shugaba ba. Daular musulunci
ma kai abin alfaharinta ne. Sannan kuma nice kololuwar dacewa da ka kasance miji
gareni, Nauyin mulki bai sa ka gaza bani farin ciki da sauke duk wasu hakkokina ba.
Kana samar da nishadi a tsakaninmu ka manta da kai sarki ne mai jagorantar
talakawan kasa bawai jaha ko wani dan yanki ba,
Kwanciyar hankalin da nake samu da ga gareka bana jin wasu matan da mazansu basu da
nauyin kowa na sarun makamancin sa. Maleek kai ne gwarzo na, kai ne Barde na, kuma
kaine gagara badau dina".

Idanunsa kawai ya lumshe a zahiri, maimakon ita da ke kuka a bayyane shi a


zuciya yake yin nasan. Tabbas yaga ribar hakuri, kai shi baima san mizaice da
UBANGIJI ba akan kyautar wanna yarinya da ya bashi. Ita din ta dabance. Tabbas
itace komansa. Tsam-tsam ya rungumeta a jikinsa na tsawon lokaci, sal da ya ji tana
sauke numfashi a hankali alamar barci ya dauketa sannan ya dagota. Kwantar da ita
yay a hankali ya cigaba da kalionta hannunsa saman shafaffen cikinta da kamar babu
komai a cikinsa abubuwa da yawa na masa kaikawo tun daga randa ya fara ganinta
soyayyar farat daya ta shigesa har zuwa yau da ajiyar gudan jininsa ke à cikin
jininta…..✍️

DAUDAR GORA
Book2
69

.....WASHE GARI ta kasance ranar da zasu koma kasar ruman. Da safe bayan Tajwar
Eshaan ya gama ganawa da Sultan na saudiya sunyi sallama amintaccensa da Sayeed
Tasadduq-Husain da sai daga baya yazo ya samesu a saudiyyan da wasu mutane biyu
suka samesa. Cikin girmamawa suka mika gaisuwa, kafin Sayeed Tasadduq-Husain ya
mika ma Amintaccensa file din hannunsa. Amsa yay da sauri yaje gaban Tajwar Eshaan
din shima ya ajiye.

"Wannan shine result din binciken ALLAH ya kara ma adalin shugabanmu lafiya da
nisan kwana. Sannan wadan nan sune sukai binciken. Sun kuma kasance kwararrun
likitoci ta wanna fanin".

Da sauri daya a cikinsu ya karbe zancen Sayeed Tasadduq-Husain din cikin harshen
turanci, "Idan mukai bincike so daya ba'a samun kuskure, amma domin cire tantama
sai da mukai wanna sau uku. Abu daya yake tabbatar mana shi namijin mahaifinta ne,
mace kuma ba ita ta haifeta ba. Bayan muni sau uku mun sake bayarwa was asibitocin
ga results din nan dai duk abu guda suke bayarwa".

Baice komai ba, sai amintaccensa ne ya amsa da


yawunsa. Da ga haka sukai masa sallama Sayeed Tasadduq-Husain yay musu rakkiya. Duk
abinda akeyi Iffah na daga kofar falo na biyu ne tsaye zata fito zuwa sashen
Uwargidan Sultan da zasuyi sallama. Duk da bata san manufar zancen ba sai duk taji
ta tsargu, amma kasancewar yanzu an koyi wasu halaye musamman akan hadiye abu koda
ta fito wucewarta kawai tavi tunda yasan da fitar tata.. Koda taje can kuma abun
nata mata kaikawo har tana jin kwadayin son sanin abinda ke a tattare da file din
da son sanin akan wama ake maganar da har sai anzo wata kasa za'ai binciken bayan
kowa yasan kasar su suna daya a cikin masu kwararrun likitoci a duniya. Sai kuma a
ka kara yin sa'a lokacin da take dawowa sashen ta samu Sayeed Tasaddug-Husain da
Tajwar Eshaan din suna maganar again. Cikin kasaitar nan tasa da magana a fisge
yake sanar masa. "Ayi musu komai da ya dace, nan da kwanaki biyar bayan anyi salla
sai ku biyo bayanmu, dan ina son ku iso ne randa zamu koma zaman shari'ar".

"Umarninka da cikawa shine abin jiranmu Insha ALLAHU"

Iya abinda Iffah kenan ta iya ji ta shige. Lokacin da ya shigo dakin zai shirya
tata fatan ya shigo da file din amma sai ya shigo babu komai. Kuma bai mata maganar
ba. Amma koda suka kammala shirinsu suka fito Sultan da kansa yau ma da yayansa
maza biyu da uwargidansa sukai musu rakkiya har airport Iffah harda kwallarta
hakama Uwargidan Sultan abinka da sabon mata bayan shigarsu jirgi sun zauna tana a
jikinsa yana lallashinta sai ga file din nan ajiye a gefensa. Ta danyi mamaki amma
sai ta basar, sai dai zuciyarta na sake tabbatar mata da koma akan wa file din ya
kunsa yanada matukar muhimmanci ga mijin nata. Jirginsu na dagawa babu dadewa barci
ya kwasheta…...

* KASAR RUMAN
Duk da saukar dare sukai tako ina a airport din zagaye yake da matakan tsaro. Kai
da gani kasan mai kasar ruman dinne da kansa zai sauka. Ta bangaren masu tarbarsu
kuwa manyan masarautar ne masu fada aji. Ga wasu lafiyayyun motoci ababen birgewa
ga mai kallo. Sosa barcine a idon Iffah dan yanzu kam bata da aikin da yafi wannan.
Hakan yasa ta kasance a kusan rabin jikinsa lokacin da suke fitowa, Dole duk wanda
ke wajen yay kasa da kansa cikin jin nauyi. Shika gogan nasu ko'a kwallar rigarsa
rungume yake da ita hankali kwance yana daga musu hannu daya alamar amsa gaisuwarsu
har zuwa motar da aka ajiye domin su kawai. Sai da suka shiga har aka rufe sannan
hadiman da sukal masu rakkiya ke fitowa a jirgi suma. A wannan tawaga musamman ta
matan Diwa ce kawai zuciyarta ke a tsarkakake game da nado labari, amma sauran duk
yan daukar rahoto ne. Sai dai kuma basu samo yanda suke so ba sam kasancewar
su/Iffah'r sun musu wahalar ma gani ba kamar yanda su Uwa sukai tunani ba.

Tun daga airport har cikin masarauta jami'an tsaro ne, a cikin masarautar ma
tarba suka samu da taima Iffah dadi, dan harda Malikat Haseenat da Daneen Ammarah
da kanta. Sal wata da Iffahr bata sani ba amma suna kama da Daneen Ammarah sosai
kuma tana kama da Jaddah. Haka kawai taji a ranta itace Daneen Waheeda da aketa
fada. Lokacin da take dagowa da ga rungumar da taima Malikat Haseenat zata rungume
Daneen Ammarah idanunta suka sauka kan wata kyakykyawar farar budurwa sol tana
balla mata harara. Bata santa ba, dan haka ta dauke idanunta ta maida hankali ya
Daneen Ammarah din cikin rashin damuwa. A hankali ta saketa ta nufi Daneen Waheeda
da ke tsaye tana kallonsu kusa da Malikat Ashwaq fuskarta babu yabo babu fallasa.
Gabanta ta rissina ta gaisheta tare da Malikat Ashwag din. Amsa mata tai da dan
murmushin yake sakamakon kallon da Malikat Haseenat ta watso mata. Sai kuma ta nufi
Malikat Bushirat ta rungume, itama dai gain kallon da ake musu ne yasata shafa
kanta tana yake, Jasrah kam saita boye bayan Malikat Bushirat din dan da gaske
kunyar Iffah take ji. Murmushi Iffah tai itama ta rungumeta, dan koba komai kafin
faruwar hakan al ta nuna mata soyayya ta gaskiya..

Tuni shi Tajwar Eshaan ya shige ciki, dan haka itama Malikat Haseenat ta kama
hanunta tana facin,"Kinga zomuje kema ki huta kunyi buda baki a jirgi babu
nutsuwa". Da ga haka ta nufi ainahin sashenta da ita dan an sake masa gyara na
musamman. Bayan wucewarsu abubuwa da yawa sun faru a cikin masarautar, ciki hard
jajircewar Malikat Bushirat akan komawar Iffah sashenta. A zahirance dai babu wanda
ya kawo komai a ransa game da hakan, sai Malikat Haseenat ce ma take gain Malikat
Bushirat din na son hakanne da tunanin Iffah ta kanainaye mata Eshaan, ta kuma san
sai dai Bushirat din tayi ta gama Iffah da Tajwar Eshaan sun riga sun gama zama abu
daya. Ga tabbaci nan ma a yau ta sake gani, dan duk mai hankali da zai kalli
Iffah'r a yau yasan tana tare da juna biyu. Komai nata ya canja, ga kyau data kara
da budewa. Yanzun ma Malikat Bushirat na gain sun nufi can ta saki wani lafiyayyen
murmushi tana fadin, (yes) a zuciyarta alamar akwai abinda suka kulla a sashen
kenan.

Ko dar Iffah bataji da komawarta sashenta ba. Sai ma farin ciki data tsinta
kanta a ciki. Ga hadimanta duk an dawo mata da abinta, a ganinta ma ita wannan wata
dama ce da zatai yakinta da kyau a yanzun. Wanka ta farayi bakinta dauke da addu'a,
kasancewar duk tayi sallolinta tun a jirgi shirin kwanciya kawai tai ta haye gado
abinta sai ko barci.

Cikin barci take jin kamshinsa na sake shige mata hanci, a zatonta mafarki
take, sai tai kokarin yin juyi abunta. Jinta jikin mutum a gaske ya sata bude
idanunta da kyar. Akan kyakykyawar fuskarsa ta sauke idanun nata. Tashi tai a dan
zabure ya rikota, maidata yay ya kwantar yana mai tura yatsunsa cikin gashin kanta,
sai kuma ya matso da fuskarsa saitin tata ya daura goshinsa kan nata hancinsu na
gogar juna.
"Yaushe kazo?"

Ta fada cikin muryar barci. Shiru kamar bazaice komai ba, sai da ya mula dan kansa
sannan. "Dama zaki iya barci babu ni a tare da ke?". Kankamesa ta sakeyi tana sakin
ajiyar zuciya, itama a hankalin ta furta, "Kawai dan banda yanda zanyi ne".

"Toni gani nayi yanda zanyi ai".

Ya bata amsa yana sake matseta cikin jikinsa kai kace amshe masa ita za'ai. Luf
ta kwanta kuwa suna sauke ajiyar zuciya a tare. Sai kuma ya hade bakinsu a hankali.
Da ga haka labarin ya sauya salo...

Karfe uku nayi ya gudu, sai farkawa tai taga babu shi a dakin. Murmushi kawai
tayi ta tashi zuwa bayi tai brush da tsaftace jininta ta fito. Madara mai dumi
kawal tasha matsayin sahur. Duk da barcin dake cin idanun nata sai bata kwanta ba
tayo alwala ta danyi nafilfili da karatun Alkur'ani. Bata tashi a wajen ba sai da
tai sallar asuba, Tana idarwa kwanciyar ta sake yi, bata tashl ba sal azhar. Tayi
mamakin barcin da tayi, amma kuma sanin yanayin da take ciki da rashin isasshen
barcin da bata samu a Saudiya ba yasa ta fahirci akwai ramuwa dole dama.

Tsaf tai shirinta cikin kyakykyawar abaya kamar ka sace ta ka gudu. Dama ga
ko'ina ya sake fita da fitar kwarjini da kyawun haiba na ciki. Cike da girmamawa a
gareta hadimanta ke zubewa Rasa gaisheta lokacin data fito. Nuni tai musu da su
tashi, cikin sanyin da ciki ya haifar mata yanzu ta basu izinin mata rakkiya zuwa
sashen Malikat Haseenat da ga nan su wuce na Malikat Bushirat. Da girmamawa suka
arsa mata tai gaba suna take mata baya. Duk da akwal tazara a tsakaninsu bata shiga
motar da aka ajiye domin ta ba tunda ta fito, A kafa ta taka hadimanta na take mata
baya. Dolene ta birgeka, dan yanda ta fito da kafan ma sal ta kara kima a idanun
hadiman. Ta ko'ina kuwa ta gitta hadiman ne ke zubewa mika gaisuwa, hannu kawal
take daga musu fuskarta da dan murmushi dan sam bata daureta ba. Yayinda
Amintacciyar hadimarta ke amsa musu da baki ita kuma.

Tun kan shigowarta aka sanar da Malikat Haseenat da ke zaune Daneen Ammarah da
Daneen Waheeda tare da ita. Sai Iftihal diyar Daneen Waheeda dake zaune a can gefe
tana latse-latse a laptop. A nutse ta shigo bakinta dauke da sallama. Dan haka suka
dago a tare. Sai dai kuma a hankali Iftihal taja sirrin tsaki da maida kanta ta
cigaba da abinda take yi. Babu wanda ya jita, sai dai Iffah kam taga kallon da tai
mata sarai. Amma tai kamar ma ita bata ganta ba ta nufi Malikat Haseenat da ta bude
mata hannu fuska duke da murmushi alamar tazo gareta. Ita din ta nufa cike da
kunya, ta durkusa a gabanta tana murmushi da gaisheta. Cikin murmushi Malikat
Haseenat ta ce, "A'a kinga Hafidah tashi ki zauna keda ke fama da kanki, ALLAH dai
ya raba lafiya".

Sosai kirjin Daneen Waheeda ya buga, yayinda Daneen Ammarah ke murmushi kawai
tana bin Iffah'r da kalion kasan ido, Bayan ta gaishe da su duk cikin girmamawa
Daneen Ammarah ta nuna mata Daneen Waheeda. "Ga wata maman taki nan tazo kuna
Saudiyya, nasan kin san dai sunanta da labarinta tun kafin yau". Fuskar Iffah cike
da murmushi ta jinjina mata kai. Kafin ta kara gaishe da Daneen Waheeda din da
zancen cikin nan va sata sumar zaune, cikin murmushin yake ta kai hanunta kan
Iffah'r ta shafa. Daneen Ammarah ta sake waiwayawa ta nuna mata Iftihal da tai
kamar ma bata san mi ake ba "Wannan yar uwarki ce ita kuma, sunanta Iftihal, itace
first born a wajen mamanki. Tanada kanne maza har uku".

Murmushi kawai Iffah tai sai dai batace komai ba kamar anda itama Iftihal din ko
dagowa batai ba. Yanda tai din kuma sai ya zafi Daneen Ammarah. Ita kanta malikat
Haseenat dai tayi shiru ne amma fuskarta ta nuna jin zafin abinda Iftihal din tayi.
Ita kam Iffah ko'a kwalar rigarta, hankalinta kwance suka cigaba da hirarsu da
Daneen Ammarah da Jaddah...✍️
DAUDAR GORA
Book 2
70

....Sai da tai sallar la'asar a sashen Malikat Haseenat sannan ta baro, fuskarta
dauke da murmushin abinda take kullama Iftihal. Dan ta dau alwashin sai tayi dana
sanin zamanta a masarautar nan duk da gidan kakanninta ne. Da ga nan sashen Malikat
Bushirat ta nufa, sai dai ta samu wai bata nan tana a sashen Shahan-shan. Hakan bai
bata mamaki ba, ba kuma ta nuna ya dameta ba ta koma sashenta ita da tawagarta. Sai
kusan karfe biyar ta nufi sashen Tajwar Eshaan..

***

A lokacin da Iffah ke nufar sashensa a lokacin shi kuma yake fita ta kofar sirrinsa
zuwa sashen Malikat Haseenat. Cikin sa'a kuwa ya sameta ita daya a dakin. Kyawawan
idanunta na tsufa ta zuba masa har ya kammala sakama kofar key ya cigaba da takowa
gareta a nutse. A hankali ya kai zaune gabanta ya tankwashe kafafunsa.

"Barka da yamma Jaddah".

Ya tada a kan lips a dan fisge kamar baya so.Murmushin ta sakar masa cikin yar
tsokana ta amsa da "Barkan ka dai Abbien unborn". Idanunsa ya dan waro mata na
alamar mamaki, sai dai kuma bai iya cewa komai ba dan yama rasa bin fadar. Dariya
Malikat Haseenat tayi mai kayatarwa, tace, "Ni dai bana fata ko mace ko namiji da
za'a haifa su gado min wanna miskilancin naka Hafidi. Ace magana a bakin mutum amma
furta ta ta zama aiki", Kasa ya dan yi da kansa kawai yana murmushi. Kafin cikin
son kauda maganar ya ce, "Amm Jaddah! Kamar yanda kika bada shawara nayi amfani da
ita. Ani musu gwaji ta wasu abubuwan hallitar jikinsu kamar gashi da yawu jini
batare ma da sun san duk muni hakan ba. Ita na bada nata, Sayeed Tasadduq-Husain
kuma ya samomin na iyayen nata dan kamar yanda na fada miki dama tunda na saka a
kaudasu a kasar shine yay aikin kuma shi kadai suka sani ya kuma san inda suke a
yanzu haka ma".

Cike da zumudi Mammah tace, "Ya ake ciki? Mi result din ya nuna kuma?"

Sai da ya dan ja iska kusan minti daya kafin ya nisa. "Al'amarin gaskiya yazo
da rudani zance ne koba haka ba oho. Result din sun nuna shi Mahaifinta ne,amma
macen ba itace ta haifeta ba".

"What! Kamar yaya kenan?".

"Shine na kasa fahimta why Jaddah. Tun a Saudiyya a rikice lissafina yake. A
daidaiton kwanakin watan haihuwarta da na yarinyar Mamy dake rubuce kwana uku ne,
sannan tambarin da ke nan a ajiye iri dayane da na jikinta, ita waccan ta mutu a
randa aka haifi ita Fhareedahn. Sai nake ji kamar akwai abinda ya kamata mu sani,
amma idan na auna yiwuwarsa ni a karan kaina sai naji abin yazo ba daidai ba".

"Kai mi kake tunani akan hakan?".

Nan ma sai da yay jima kafin ya bata amsa. "Itama Mammy a mata gwajin halitta
tare da ita. Kinga muma sai mu samu nutsuwar yarda ba ita bace, ko itance. To amma
ya akai ta samu tambarin zuri'armu bayan mahaifinta bashi da alaka da wanna
masarautar? Sosai nakejin kaina a rikice a duka abinda nake tunani da fatan ya
tabbata".

"Tabbas al'amarin akwai rudanin, rudanin kuma suna da yawa, dan inhar babu
alaka tsakanin wannan yarinya da Arnmarah to tabbas tana da alaka da wani a wannan
masarautar kuma dole ne mu sani. Sai dai dabi'un yarinyar na rikita mun lissafi
Eshaan. Dan babu abinda ya banbanta da na Ammarah tana a irin shekarunta. Sai dai
ni nasan diyar Ammarah ta rasu tunda da hannuna na mata wanka da hadata aka kuma
kai ta aka bizne".

"Kamar yanda na fada miki Jaddah akwai abinda ke boye. Dan da gaske yarinyar nan
akwai aljanu a kanta wilhy. Naga alamominsu da yawa tattare da ita, dan a wan
lokacin ita kanta aljanar ma nake kallonta".

Dan murmushin karfin hali Malikat Haseenat tayi, amma a ranta fal yake da
rudani... Sun cigaba da tattaunawa har zuwa gabanin magriba sannan ya baro sashen
domin zuwa yay shirin massalaci…..

A bangaren Iffah kam data nufi sashensa kai tsaye kitchen ta nufa, inda masu kula
da abincinsa ke ta kaikawon lissafin abinda zasu shirya masa na buda baki. Tana
shigowa duk suka zube kasa suna kwasar gaisuwa. Hannu kawai ta daga musu, kafin tai
zaran bibiyar duk abinda suke shirin yin da kallo. Duk lissafinsu sal da ta wargaza
ta shimfida nata, karshe ma ita ta koma shirya abincin da taimakonsu. Wannan
al'amari ya matukar basu mamaki kam, dan ko'a tarihin masarautar basu taba jin a
inda wata Zawjata- almilk ta shiga kitchen girka abinci ba koda na Shahan-shan ne
kuwa. Sai gashi a yau Itfah ta ajye tarihin,

A matukar gajiye suka kammala aikin, tayi tibis da ita saboda a yanayin da take,
duk da dama cikin nata nada saukin laulayi da tsurfan abinci. Sannan ita dai
bazatace ga wani waje na mata ciwo ba mai jigatarwa. A dining room din ma tana
tsaye suka shirya komai, aka kara turaren wuta ko ina ya dauka harami. Bayan duk
wucewarsu bedroom nashi ta nufa, ta dinga binsu daya bayan daya tana lekawa har sai
da ta shiga a inda ya kwana. Kamar ko yanda tai hasashe ba'a gyarashi ba, tunda ita
da kanta ta hutar da amintaccensa tun kan su wuce. Duk da yanda take jin kanta haka
tai dauriyar gyarawa, sannan ta shiga toilet din tayo wanka shima bayan ta
tsaftacesa Bata da matsalar kaya anan kam tunda tasan tabarsu tunkan su tafi ba,
tako shirya cikin wandon jeans 3quater blue da karama roga mara nauyi fara tas, sai
hoton heart da akayi babba a gaban rigar. Kayan sun mata kyau. Tana barbaza
gashinta da haushi na rashin son a taba mata shi ya shigo dakin da sallama. Dan
turus yayi yana kallonta irin na rashin tsammani. Dan a yanzu haka da yake
shigowarnan da ita a ransa ya shigo, kewarta yake ji sosai, dan duk yau bai ganta
ba, rabonsa da ita tun daren jiya da ya kai mata ziyarar sirri sashenta.

A hankali ya cigaba da takawa cikin dakin yaje gabanta ya tsaya. Jitai kawai an
tura mata yatsu cikin gashi. A firgice ta dago dan ko kadan bayaji motsin shigowar
tasa ba. Cikin juna idanunsu suka shige, kowanne cike da kewar dan uwansa kamar sun
hada watanni basu hadu ba. Itace ta fara janye nata a slowlv. kamar mai in kunvarsa
ta maida kanta kasa ta dukar. Numfashi ya dan furzar kadan, tare da dukowa
ya zare ribbon din hanunta ya saka cikin tsintsiyar nasa hannun kamar maisa
bangles, sai kuma ya maida duk hannayen biyu saman kanta ya tattaro gashin a
tsakkiya ya dare mata.

"Thanks you".
Ta fada cikin siririyar muryarta da ke ratsa masa jiki, yasan tsaiwarsa a wajen
bazata hafar masa da da mai ido ba. Dan haka ya rabata ya wuce cikin tafiyar tasan
nan daddaya dan azuminsa ya isa lafiya. Da kallo ta bisa har ya shige bayi, sai
kuma ta saki sassanyar ajiyar zuciya ta mike. Closet dinsa ta nufa kasancewar akwai
finger print dinta yanzu akai itama. Lallausar jallabiya kalar maroon ta zaba masa,
tare da alkyabba irin ta sarakan saudiyya. Fitowarta dal-dai da tashi. Kallo daya
ta masa ta dauke kai dan har yanzu ta kasa sakewa da kalion wanna jikin nasa. Kanta
a kasa ta karaso gabansa, karamin towel da ke hannunsa ta amsa, babu musu ya sakar
mata, sai da ta lumshe idanunta sannan ta fara tsane masa jikin. Dan garetan
murmushi ya saki idanunsa kan kyakykyawar fuskarta harta kammala. Man da yake
amfani da shi ta ajiye zata gudu ya rikota a slowly yaNmaidota baya. Sai da ya gama
kare mata kallo da gaNsama har kasa sannan ya dire kan fuskarta da idanun ke
lumshe. A can kasan makoshi ya furta, "Shi man wazai shafa?". Batare data bude idon
ba ta ce, "Ka tayani".

"Naki wayon".

Ya bata amsa yana maidota gabansa da kyau. Dan murmushi tai zatai magana ya ce
mata, "Shilli!!!" Shiru tai ta hadiye abunta. Shi kuma ya daura mata man a kan
hannu. "Oya zan makara sallar magrib". Babu yanda ta iya dole ta shafa masa.
Kirjinta sai bugawa yake da sauri-sauri dan da gaske jikin nan nasa toro yake bata.
Ta rasa mike birge maza suke maida kansu haka ita kam. Rashin mafita ya sa dole har
shiryawa sai da ta taimaka masa wajen yi. Tana kammala saka masa turare ya kamo
fuskarta cikin tafukan hannunsa ya sumbaci goshinta da idanunta da karan hancinta,
sai kan habarta. Sassanyar ajiyar zuciya ta dan saki. Bata ankara ba kawai ta gansa
duke gabanta ya dan daga rigarta ya sumbaci cikinta. Da ga haka ya wuce abinsa
cikin dakewa kamar bai aikata komai ba. Da kyar ta iya bude ido ta bisa da kallo,
dai-dai zai fice ya dan tsaya a jikin kofar tare da juyowa suka hada ido. Kauda
nata tai da sauri, shi kuma ya dan sakin murmushi a iya lips da fadin, "Idan kika
bar sashen nan kafin na dawo sai na hukuntaki". Da ga haka ya fice ya barta da
murmushi a fuska..

Bai shigo gida ba sai da aka idar da har sallar isha'in da asham, dan bayan idar da
sallar magrib ya sha ruwa da dabino a can. Da ga haka yay zaman karatun Alkur'ani.
Kowa yasan hakan yake yi a duk shekara, dan baya shigewa sai bayan an kammala salla
baki daya kamar yanda yake yi idan ba'a azumi sai ani har sallar isha'i. Bisa
rakkiyar su Sayeed Fayzul-haq ya dawo sashensa. Hadiminsa kam tun da yaji a bakin
masu girki Zawjata-almilk tazo itamace taima Shahan-shan girki da kanta baiyi gigin
biyosa har nan ba sai ya lake a 3 floor din. Babu kowa a faion sai sanyin ac da
kamshi mai dad ba irin wanda ya bari ba. Bedroom ya nufa domin rage kaya, zuciyarsa
na raya masa tama gudu kenan bataji gargadinsa ba. Sai dai yana murda handle din
kofa itama tana budewa, kusan cin karo sukal da juna ALLAH dai ya kiyaye taja baya
da sauri, sai kuma ta kusan faduwa sai da ya rikota jikinsa. A jiyar zuciya ta
sauke cike da shagwaba ta ce, "Thanks you"

Maimakon amsa. mata godiyar cak ya dagata bisa kasa suka koma dakin. Tana watsal-
watsal da kafafu da rokon ya sauketa ita yunwa takejl bai ma saurareta ba sai da ya
direta inda yake bukata ya rufe bakin tsiwar dan iya yaren da zuciyarsa da
kwakwalwar ke bukata kenan kawai…….✍️

DAUDAR GORA
Book2
71

_..Taji a jikinta kasancewar da gaske yunwar take ji,dan itama ruwan kawai tasha da
dabino sai dan madara mai zafi da take matukar so a yanzu tunda akasha ruwan. Ta
hakura ne tai salla dan tasan in har taci abu da yawa to tabbas bazatai sallar ba
barci zatai. Duk yanda take wani tuttura masa baki na shagwaba bai kulata ba, da
taimakonsa sukai wanka a tare sannan suka fito daning room din. Sai da ta tabbatar
ta gam harare-hararen kwanikan abincin tsaf duk da tasan bayan sun ajiye babu
mahalukin da ya sake shigowa nan sai shi bata aminta ba kai tsaye. Komai a tare ta
hada musu, hatta shayi a kofi daya ta zuba duk da kasancewar dan mitsitsin nanne na
larabawa. A haka suka dinga cin abincin kowa na ciyar da dan uwansa har sukaje iya
inda suke bukata. Falo suka dawo, yana kokarin kuna Laptop din tasa ta fama ta je
ta haye cinyarsa tana tura baki.

"Wai nikam kodai computer din nan kishiyata ce?".

A yanda tai maganar ma sai abin yaso bashi dariya. Amma dai ya gimtse bai yi ba
ya dai tsareta da idanunsa kawai. Lumshewa yay ya dan bude tare da tallafo fuskarta
cikin tafin hannunsa. A kasalance ya furta, "Ko dai ke ce ke kishi da ita".

'"Ai dai banyi laifi ba".

Murmushi kawai yay dan bashi da abin cewa kuma.Sai kawai ya dauka remote ya
kunna musu television ya kamo babban gidan tvn kasar. Basu fara labarai ba, sai
wani shiri mai suna * ZAUREN MUSULUNCI_*. sannin muhimmancin shirin yasa bai canja
ba ya bar musu nan, itako harda gyara kwanciya a jikinsa ta lafe kamar wata mage.
Shima sai ya gyara mata yanda zataji dadì sosai hannunsa saman cikinta da duk
duniya a yanzu babu abinda yafi so da bukatar gani kamar girmansa da haihuwarsa.
Koda wani takaici ya tuno a ransa daya tuna Iffah'r sa nada cikin gudan jininsa sai
yaji nutsuwa ta saukar masa..

*
-*

Washe garin aka tashi da fatan gain watan salla,Iffah na zaune tana karatun
Alkur'ani bayan idar da sallar asuba Tajwar Eshaan ya dawo da ga massalaci. Komawa
yay ya dan kwanta dan barcine a idonsa sosai. Ta idar itama tana shirin hawowa
gadon yake sanar mata sakonta ya iso yanzu Sayeed Fayzul-haq ke sanar masa. Fasa
kwanciyar tai cike da doki ta mike ta hau shiri, shi dai kallonta kawai yake dan ya
santa da barcin tsiya amma da ga cewa sakonta ya iso ta fasa yi. Ganin sauri-saurin
nata yay yawa a hankali ya furta, "Madam a hankali karki jamin asara abuna baiyi
kwari ba fa".

Ita kunya ma maganar ta bata, dan haka ta juya masa baya tana rufe fuska. Shima
sai ya dan murmusa kawai ya lumshe idanunsa. Kirtsawa ta karasa yi ta zo gaban
gadon ta manna masa sumba a goshi. Hannu ya kai zai damkota ta zille. Murmushi yayi
da kara gyara kwanciya yana fadin (Fitinanniyar yarinya) a zuciyarsa…..

Duk da safiya ce sosai tuni kayan da aka shigo da su cikin manyan motoci kusan goma
masarautar ta dauki dumi. Kowa jira yake ya ga da umarnin wa aka kawo kayan, dan
abune dai sabo da ba'a san da shi ba, ga kuma wasu kayan da suka dan fitgito sun
nuna suturu ne ma. Tuni fitowar Iffah da ga sashen Tajwar Eshaan Sayeed Fayzul-haq
da amintaccensa biye da ita kallo ya koma sama, sal kuma ga tawagar matasan
masarautar da ta saka suka mata aiki a wancan karon ma sun fito, a gabanta duk
sukal rankwafawar gaisuwar girmamawa. Ta amsa musu itama da kulawa fuskarta da
murmushi har da yar tsokanarsu wai kwanan nan zata fara saida form din aurar da
samarin masarautar ta ga sun fara yawa. Dariya suka shigayi da barkwancin nata.
Harda Sayeed Fayzul-haq da ke jin kaunar yarinyar, gata dai karama amma da halin
manya, manyan ma sai an tona. Haka ma amintaccen hadimin Shahan-shan na jin kima da
girmanta, dan yanda take kula da shugabansa kawai da sakasa farin ciki ma abin a
jinjina mata ne. Shi baya ma ganin karancin shekarun sam sal wata kimarta da girma
irin wadda yake kalion Shahan-shan da ita.

Ta musu bayani akan kayan suma da za'a rabasu kamar yanda aka raba kayan
abincin azumi ne. Akwai kuma kaji da shanu suma zuwa yammaci zasu isa. Sai dai su
baza'a kawosu nan ba a kowace jaha aka samar da masu kiwonsu aka siya idan kowane
wakili yaje inda zai raba kayan da aka bashi zai amsa. Sai kuma wanda za'a rabama
hadiman masarautar suma da nasu daban, sukam harda kudi wanna kuma Sayeed Fayzul-
haq ne zai bada su sakone da ga Shahan-shan da kansa

Abdul-Shakhur in Khairul-Bashar shugaban tawagar ya share kwallar da suka ciko


masa ido. Cike da girmamawa a gareta ya ce, "Lallai ke alheri ce garemu gimbiyarmu.
Ke haske ce mai haskaka fararen fitulun da ke zagaye da daular ruman. Kasancewarki
damu sake buda mana sanin wanene adalin shugabanmu yake da kyawawan halayensa a
koda yaushe. ALLAH ya kara miki daraja, ya albarkaci rayuwarki data shugabanmu, ya
zagayeku da kariyarsa da ni'imominsa. Yay riko da hannayenku ya baku ikon sauke
nauyin al'umma da adalci. ALLAH ya bamu ikon muku biyayya ya karemu zaginku koda a
bayan idanunku. ALLAH ya karya makiyanku koda jininmu ne ya azurtaku da zuri'a masu
irin kyawawan halayarku da dabi'unku. ALLAH ya jika magabata, wanda suka rage ALLAH
ya rabaku da su lafiya...

Haka ya cigaba da jero addu'oi sauran a amsawa da Amin tare da hadiman da suka
zagayesu cike da farin ciki. Iffah kam sai taji har hawaye na ciko mata idanu.
Tabbas babu abinda ya kai kyautatawa dad da soyayyar mutane. Da ace dan adam ya
gane da ya kasance mai kyautatama mutane sabanin munana masu. Kyautatawa na bada
muhimman abubuwa uku a lokaci guda. *_DARAJA. SOYAYYAR MUTANE.
SANNAN LADA A WAJEN UBANGIJI_* Cikin kankanin lokaci masarautar ta harmutse, bakin
kowanne hadimi ka kalla a washe da farin ciki musamman idan ya kama yan kudadensa
da kayan sakawa kusan kala biyar uku a hannu. Ga iyayen kaji da shanu an zube musu
na girkin salla. Ga albishir na basu damar yin shagalin bikin sallarsu kamar yanda
kowa keyi. Harda damar yin gyaran jikinsu matsayinsu na mata Iffah tabama matan,
dama albishir din kawo masu gyaran jiki €ikin masarautar saboda hadimai matan
kawai. Kai jama'a harda masu kuka, kaunar Iffah kam da Shahan-shan din kansa ba'
magana a zukatansu. Sai sukejin kamar an yanta rayuwarsu ne da wani haske na
musamman a yau din.

Ba cikin masarautar ruman kawal ba. A cikin al'ummar. kasa ma duk wanda ALLAH ya
tsaga da rabonsa a kayan' nan ya tsinta kansa a farin ciki mara musall. Badai ta
wadata kowa da kowa ba. Amma ta ragema was radadin talaucin da suke ciki. Ta
faranta
ran marayu marasa iyaye. Duk da alkairi ne na sirrince da akaki bama yan jarida
damar sani sai gashi ya fita karar wata amsa kuwwa a katafen yada labarai, Ya koma
latest topic na wanna ranar harma da washe gari. Dan cikin aminci, UBANGIJI a ranar
akaga watan salla washe gari aka tashi da farin cikin zagayowar wanna rana. Inda
karfe tara dal-dai Shahan-shan da Kansa ya jagoranci sallar idi a massalacin
Masarautar da mutane kasar suka ziyarta ta ko'ina a jar, harma abin ya bada mamaki,
dan duk da ana cikashi dama duk shekara sai gashi a wannan shekarar ya ninka da
ninki mai ban mamaki,. Talakawa da yawa sunzo cikin Dahab City yin salla domin
kawai suga Shahan-shan.(Haka rayuwa take, duk kasancewarka mai mugun hali ko wanda
za'a gogama bakin fenti da kayi alkairin da yay shura tsakaninka da ALLAH badan
duniya ta gani ta fada ba ko a yaba maka sai kaga ALLAH ya saka soyayyarka a
zukatan wadan nan mutanen dake aibantaka da kyararka a baya. Yan uwa mu dage da
alkairi domin ALLAH, idan ka cire Naira dari a cikin dubu da ya baka sai ya sakama
sauran albarka ya kuma daga darajarka. Dan shi alkairi da gaske danko ne baya
faduwa kasa banza inji hausawa. Dan ko yayan cikinka kaima shi sake kaunarka suke,
hakama iyayenka)

Tajwar Eshaan yayi addu'oi masu ratsa zukatan bayan idar da salla. Hakama lokacin
khuduba kalamansa masu ratsa zukata ne da hikima a cikinsu da mutare duk jikinsu
yay sanyi da yanda suke kallonsa a baya. Bayan kuma kammala addu'oin yay wani dan
gajeren nasiha da Fatan alheri ga kasarsa da ma al'ummar kasar da musulman duniya
baki daya. Ya rufe da musu Barka da shan ruwa.

Wannan jawabi a Tajwar Eshaan Ibn Haysarn Abdul-majeed Ally Qutb shine ya dinga
amsa kuwwa a kafafen yada labarai, masu fashin baki nayl talakawan kasa da basu
samu halarta ba nayin nasu suma,

*Duk gayun da Iffah taci domin kayatar da zuciyar Maleek dinta bata samu ganinsa ba
har sallar zuhur. Bataji haushi ba, sal dal ta kagu su hadun. Duk da itama da kanta
tai masa shirin fita sallar. Yayi matukar kyau kamar wani dan saurayin dawusu (lols
😉😂)) harda fada masa ita why kamarma ya fasa kishin fitarsa a kalle mata shi takeyi
haka. Amintaccensa da ke jinsu (okacin da take bashi shayi sai kasa ya karayi da
kansa kawai yana murmushi.

Bayan ta idar da sallar azhar ta fito domin zuwa gaida Jaddah da Malikat
Bushirat da ya kasance dole tayi. Sai lokacin ta fahimci yanda masarautar ke cike.
Ashe dole ne duk wani Tajwar a sauran jihohi sai yazo a yau din yayma Shahan-shan
barka da shan ruwa, Hakama manyan attajirat da masu fada ajin kasar da dattijai.
Zasuci abincin salla da Shahan-shan su kuma tattauna matsalolin kasa da shawarwarin
magancewa. Gaba daya sai Iffah taji ta Kara tausaya masa. Dan lallai mulki ba wasa
ba, yanda ta sanshi bal son hayaniyar nan yana can cikin takura ne.

Sashen Mallkat Bushirat ta fara nufa yau tawagarta zagaye da ita. Kowa ya kalleta
sai ya sake kallo dan kyawun da tai cikin walliyar sallar tata mai tsananin
kayatarwa da daukar idanun mat kallo. Ga kyawu da cikin jikinta ya sake sakatayi
kamar ka saceta ka gudu. Tako ina hadimar da jami'an tsaron masarautar gaisuwa
kawai suke mikawa. Itako fuskarta kawace da murmushi mai sanyi da ke sake saka
kaunarta a zukatan talakawan nata masu jin yanzu kam babu kamarta a cikin
masarautar bayan Malikat Haseenat da itama ta kasance adalar shugaba…..✍️

DAUDAR GORA
Book2
72

.....Cike Iffah ta samu sashen Malikat Bushirat da danginta da sukazo mata Barka da
salla. Hakan ya mata dadi, dan duk wani wanda ke da alaka da Tajwar Eshaan a rayuwa
tana ganinsa da kima da mutunci. Cikin mutuntawa suka tarbeta, dan sakonta da na
Tajwar Eshaan yaje garesu har gida a jiya. Duk da suma sun kasance mafi yawansu
basu nema komai na rayuwa sun rasaba. Amma alheri dadine da shi, musamman da ya
kasance wani abu bai taba zuwa garesu ba ace daga dan yar war tasu kuma Shugabansu.
Abinda ya basu mamaki da tabbatar da an samu sauyi yar uwar tasu ma sai da suka zo
yanzu duk suke mata godiya har tasan Tajwar Eshaan din wai ya musu aike suma.
Murmushin yake kawai ta musu, dan tun jiya dama a tunzure take da abinda Iffah'r
tayi. Koda Iffah'r ma ta gaisheta cikin yake ta amsa gain yan uwanta duk sun zuba
mata ido.Amma zuciyarta tafasa take da yanda suke ta sanya albarka da yaba abinda
Iffah'r tayi, tare da tabbatar da shugabansu kuma dansu yayi dace da mace ta gari
mai buda masa hanyar alkairi. Sukam suna farin cikin shigowarta cikin ahalinsu.
Wasunsu harda kiranta gagara badau wadda tafi karfin duk wani shedanci a azzaluman
masarautar.

Iffah da mur mushi kawal ta dingayi kasa-kasa. Tayi zaman kamar awa guda sannan
tai musu sallama akan zuwa anjima zata aiko azo da su su gashe da Shahan-shan.
Wannan zance nata na karshe ta sakasu sake shiga jin dadi, dan a cikinsu ma akwai
wanda rabonsu da Tajwar Eshaan din tun kan a bar kasar da shi, Kuma uwa daya uba
daya suke da Malikat Bushirat din, Sun baje babin hira da sanya albarka ga Iffah
Jasrah ha kara basu labarinta. Babbar yayar su Malikat, Bushirat din da suke kira
Akia Badiha cikin nuna jin dad) ta furta, "Al ni babban abinda ma ya sakani farin
ciki fiye da komai wannan cikin na jikinta, dan zamu samu tsatson alkairi a
zuri'armu, ALLAH dai ya raba lafiya".

Kusan a tare duk suka dubeta. Malikat Bushirat da ke kishingide tana shakar iska
da fesarwa harda zabura. Jasrah ce tai karfin halin fadin, "Akia wal waye mai
cikin? Kin samu a rudan!" Baki ta Kara washewa, cikin barkwanci ta ce, "Aw to tunda
baku ramfo ba ku bada goron albishir tukkanna. Kudi sabbi kal-kal Jasrah ta sauke
cikin tafin hannun Akia Badiha, cike da zumudi ta ce, "Muna saurarenki".

"Uhm wadan nan din ma babu laifi, sai dai da kanku ma zaku karo idan kunji. Insha
ALLAHU muna gab da samun Miran, ko Daneen a wannan masarautar. Dan da alama
Zawjata-almilk tana tare da shigar ciki".

"Whattt!!!!!!".

Suka fada cikin hada baki da hun murna. ALLAH ma ya sosu hadimai yau an basu
freedom din kansu sai dai-daiku dakan dan shigo dan an bukaci ganinsu. To su sunama
a falon Malikat Bushirat din nacan ciki ne iya su dan yau ranar baje kolin hirar
zuminci ce. Wani irin diff-diff kirjin Malikat Bushirat keyi, zuciyarta kamar zata
faso ta fito. Ga kanta da yay wani irin azababben sarawa, sai ta fara ganin falon
na juya mata da su da ke ciki. Tashi tai da sauri ta nufi daki ta kulle kanta. Tana
gama sakama kotar key ta daura goshinta jikin kofar tai wani irin fashewa da kuka
mai tahowa irin gaba dayan nan mutum yaji kamar numfashinsa zai bar gangar
jikinsa..

Bama su fahimci halin da take cikiba su balle tashinta, sunata murnarsu, sai da
mai bima Malikat Bushirat din ta juyo tana magana idonta ya sauka a wajen zamanta
wayam. Bata kawo komai a ranta ba a tunaninta duk murnarce ta kebe yin abunta dan
sun san yar war tasu da shegen kasaitar son mulki kamar itace Shahan-shan din ba
matarsa ko uwa ba…..

*A bangaren Iffah kam tana sashan Malikat Haseenat, taso ta samu Iftihal dan yau
tayo mata tanaji sai dai aka samu rashin sa'a wai ta fita ita da Husam babban dan
Miran Jasim. Anan ma Iffah ta jima sai bayan sallar la'asar ta baro, sunata shan
hirarsu ita da Mammah da Mammy. Daneen Waheeda dai bata saka baki sai lokaci-
lokaci...
Tattauna zancen cikin Iffah ga zuri' ar Malikat Bushirat ya sa ya fito har ya fara
yawo a cikin masarautar. Dan danan fa aka fara wani karamin bikin murna da sam
Iffah da Tajwar Eshaan da sai da akai sallar la'asar ya samu kansa basu sani ba.
Hasalima suna can manne da juna abinsu hankalinsu kwance da jin tamkar suma kadaine
a cikin duniyar (Su bily duk an mutu ashe 😏🤔👹). A kankanin lokaci zancen ya cigaba
da shiga lungu da sako. Da ga masu shiga farin ciki sai masu shiga rudani da tashin
hankali dan abune da basuyi zato ba...

"Aiko lokaci yayi da zaki bijiro da zancen auren nan Waheeda".

Malikat Ashwag ta fada cikin tashin hankali bayan gama sauraren Daneen Waheeda.
Daneen Waheeda da gaba daya ita tasan kunar da zuciyarta ke mata ga rikicin Iftihal
taja numfashi mai matukar zafi. "Hakane Ashwaq, amma kin san kafiyar Mammah, ga shi
Ammarah sam nunawa ma take tafi son yarinyar nan sama da Iftihal din, taya kike
ganin hakan zai yiwu cikin sauki?".

"Yuwuwarsa daya ce, mu nema su Sayeed Tasaddug-Husain da zancen shi da su Sayeed


Hifzur-rahaman, da Sayeed Fayzul-haq tunda sune dai iyaye a gidan nan, duk da yake
shugaba suma ai sama suke da shi, kuma dama a duk aure-auren nasa ai sune dai
Mammah ke sakawa gaba ko da su Jasim".

"Eh hakane, kema kin kawo shawara mai kyau.Yaushe kike gain zamu samesu?".

"Ko zuwa anjima dan ba'a bori da sanyin jiki. Bara na kiga mu nema ganawar sirri
da su, da ani ishan'i insha ALLAHU sai kawai mu zauna"...

(To koyaya zata kasance,Iffah'r mu ga Abar nan na tunkaro ki ki hira 😝😢)

Su Malikat Ashwaq sun gana dasu Sayeed Fayzul. haq, sun kuma tattauna sosai da
sauraren abinda Daneen Waheeda tazo da shi, shi dai Sayeed Fayzul- haq ma baice
komal ba. Garama Sayeed Hifzur- rahaman yace su basu lokaci zasuyi magana da Mammah
a kuma jira Sayeed Tasaddug-Husain ya dawo daga Umrah gobe insha ALLAHU. Daga haka
suka rabu.

A lokacin da suke tasu tattaunawar Iffah na can taima yan wan Malikat Bushirat
rakkiya ga Shahan- shan da ya sakko hawa na biyu. Ya nuna farin cikin ganinsu
shima, dan bai taba zama irin wanna dasu ba tunda yasan kansa, ballema yanzu da
yake a shugaba. Suma duk wanda ka kalla zaka fahimci tsantsar farin ciki a tare da
shi. Sun kuma ji dadin yanda ya dan sake dasu yay hira duk da maganar daya biyu ce
dai. Sai dai abu mafi kayatar da su yanda ya girmamasu ya mutunta su. Sai kuma komi
yake idonsa aka matarsa Iffah. Kusan zaman awa daya da rabi sannan sukai masa
sallama...
Bikin sallah ya cigaba da gudana masu ziyara nata zuwa gaishe da Shahan-shan.
Yayinda Malikat Bushirat ke a birkice, gaba daya Jasrah tama kasa gane kanta. Tayi
kiranyen uwa har ta gaji amma taki zuwa. Sai taji komai ya karasa kwace mata. A
kwana na uku da salla sai da doctor ya dubata. Jasrah dai tai
shiru da bakinta babu wanda ya sani gudun kananun maganganu. A washe garin cikar
sallar kwana hudu Maganar komawa zaman kotu taje kunnen kowa, dan haka wasu suka
kasance cikin zullumi da tsoron karfa garin tone-tone ga su Miran Jasim suma tasu
allurar ta tone galma..

* KOTU*

A yanda zaman shari'ar ma ya cika yau sai ya baka maraki. Dan tarin matasan nan a
yanzu da Iffah ta dunkule waje daya bisa jagorancin Sayeed Fayzul- haq kaf dinsu
sai da sukazo. Abinda basu taba yi ba tunda ake zaman shari'ar. Hakama wasu a mata
da mazan masarautar sun karu. Kotu dai ta cika tai hani'an masha ALLAH.

Tsabar yau Iffah da jin kai ta shigo da yafi na kullum ma Shahan-shan ya rigata
zuwa. Dan kusan itacema karshen shigowa da hadimanta. Nana kowa ya zuba mata ido
harda uban gayyar ta cikin glasses din da ya boye idanunsa. A ransa kam kara
jinjina fitinar yarinyar nan yake. Tafa rigashi kammala shiryawa amma tsabar taso
neman magana sai ta gudu sashenta har sai da ya rigata zuwa kotun. Yau ma sai da
taje ta gaida Malikat Haseenat da su Daneen Ammarah. Hakama Malikat Bushirat da tai
wani irin ramar fita hayyaci da mai lurane kawai zai fahimta, dan abin dariya yau
harda eyeglasses a idonta itama, da alama akwai abinda take boyewa. Hannu kawai ta
dagama Iffah a maimakon amsa mata gaisuwa, ko a kwalar jikin Iffah tama mike abinta
tana takun nan nata na neman magana.

Bayan nutsuwa kotu yanda ya kamata aka shigo da su Miran Arshaan. Sunyi duhu
sosai sun rame. Ba duka ba zagi babu harara zaman duhun nan kawai da suka saka
Iffah ciki a wancan karon da bakin cikin kamar su a cikin kurkuku ya maida su haka.
Yan kananan magana ne suka fara tashi a kotun har sai da aka tsawatar. Ameera
Haifah dai sai faman rufe fuska take da mayafi, gashi yau kuma harda iyayenta itama
a kotun dan habanta yazo akan maganarta tun washe garin rufesu amma bai samu gain
Tajwar Eshaan ba.

Bayan kotu ta sake nutsuwa Sayeed Hanifud-Din ya karanto karar haka. "Har yanzu
dai muna kan zaman shari'a ne akan Miran Jasim da ya bada madara mai dafi ga
Zawjata-almilk ta shayar da wanda suke son halakawa. A wancan zaman kotu ta bada
damar kawo bokansu a zama na gaba, sai kuma aka samu wani al'amarin akan Miran
Arshaan da Ameera Haitah, wanda yay dalilin kaisu kurkuku suma, zaman makwaftakar
Miran Jasim da Miran Arshaan ta zakulo wasu sabbin abubuwa masu ban mamaki da ya
karata ace an fara saurare a wannan shari'a kafin a cigaba da yinta. Idan adalin
shugabanmu ya bada damar hakan to".

Hannu Shahan-shan ya daga a hankali da yin alamar an baka dama. Godiya Sayeed
Hanifud-Din yayi sannan ya kalla shugaban jami' an tsaron. Mikewa shugaban jami 'an
tsaro yayi, yayinda Miran Arshaan da Miran Jasim ke kallon juna a rikice, dan sun
dai san karn kalar tabargazar da sukaira juna da tone-tonen tsiyatakunsu a cikin
kurkukun. A hankali Iffah ta
saki wan irin sassanyan murmushi. Cikin Sa'a kuwa sai a idon su Miran Jasim din
kamar an kirawosu su dubeta........✍️

😂Gaskiya Iffah virus ce 😆🚴🚴🚴🚴

DAUDAR GORA....!!
Book2
Chapter: 73

…...…..Kallon da Iffah ta musu shi ya kara girgiza zukatansu, sun kuma tabbatar
akwai abinda shegiyar ke kullawa. Sannan recording din nan da akai musu
batare da sanin su ba in fa har aka budeshi kowa yaji anan akwai matsala. Dan basa
raba dayan biyu zama a iya kashesu a cikin kotun nan kuwa. Saboda basa
tantamar duk abinda suka yi na tsiyatakunsu a cikin masarautar za'a samesa a ciki.
Miran Jasim da yasan kwabarsa sai tafi ta kowa ruwa ya fashe da kuka yana
girgiza kai. Ya fahimci idan har ya mika wuya da kansa zai iya samun tausayawar
mutane ma. llai kuwa tsitt kotun tayi, yayinda Shahan-shan ya dan jin jinama
Sayeed Hanifud-Din kai. Ya fahimci mi yake nufi, dan haka yay saurin dakatar da
shugaban jami'ai da ke shirin playing recording din. Dakatawar kuwa yay cikin nuna
girmamawa. Kotun tai shiru aka zubama Miran Jasim idanu. Shi kansa Miran Arshaan
sakare yay kawai yana kallonsa dan ya kasa fahimtar ma'anar
kukan. Iffah kam wani shegen murmushi ta saki da har sai da ya bayyana farare
hakwaranta.

Ganin kukan Miran Jasim bana karewa bane ga lokaci nata tafiya Sayeed Hanifud-
Din ya gyara tsaiwarsa da fuskantarsa. "Shin ko Jasim na da wani abin cewa ne
haka?". Kuka Miran Jasim ya sake fashewa da shi da fadin, "Tabbas nine mai abin
cewa, na kumayi alkawarin fadin duk abinda ake bukatar jiNda ga gareni, domin nayi
nadama, nayi nadama matuka akan biyema Arshaan da mahaifiyarsa da tawa, Dan komai
ya faro asaline da ga su...."

Ba Arshaan kawai ba, hatta Malikat Haseenat zura masa ido kawai tai, dan kowa
yasan wacece mahaifiyar Arshaan. Mace ce mai kirki da kyawawan halaye. Haka kuma
mahaifiyar shi Miran Jasim din. Mace ce mai mugun hali da son kanta, duk wanda ya
kwana ya tashi a masarautar kuma ya san mahaifiyar Jasim din da ta Arshaan basa ma
zama inuwa daya. Amma dai bara aji mi jasim din yazo da shi. Kuka ya cigaba da yi
wiwi kafin ya nisa da cigaba da fadin, "Nasan a zahirance kowa zai ce iyayenmu mata
basa shiri da juna ne, sai dai abin ba haka bane. A boye su din aminai ne matuka,
dan mahaifiyar Arshaan ta shiga jikin Mammah (Malikat Haseenat) ne kawai danta
dinga zakulo musu sirrikanta tana kawo musu. Burinsu shine muyi mulki, tare da
mallake dukiyar Abbu (Tajwar Abdul-majeed) gaba daya, dan sun san Haysam ne zai
gaje komai tunda shine babba. Sunta kulla-kullar gain mun halaka Haysam tun ma muna
yara amma hakan bai kasance ba, dan haka suka yanke shawarar uwa ta kashe Abbu da
Haysam tun a wancan lokacin.

"Why karya kake matsiyaci makiri!!!".

Miran Arshaan ya fada cikin karaji da fashewa da kuka yana kaima Miran Jasim
duka. Dan fa shi duk lalacewarsa yana son uwarsa, kuma yasan sam bata taba saka
kanta a cikin wanna al'amarin ba, koshi bai fito da maitarsa a fili ta son mulki ba
sai bayan mutuwarta. Da kyar aka rabasu, har Miran Arshaan ya jima Miran Jasim ciwo
da farce a fuska. Rumtse idoNkawai Shahan-shan yayi cikin kunar zuciya. Sai da
kotun ta lafa da kananun magana da ta dauka sannan aka sake bama Miran Jasim damar
ci gaba da magana. Kafin yace komai Miran Arshaan ya tare da fadin, "Ba gaskiya ya
shirya fada ba, dan haka ni wihy zan fadi komai, na kuma bada damar bayan duk na
gama fada a bibiyi recording din nan namu dan baiyi dai-dai da abinda zan fada ba
amun duk hukuncin da ya dace. Dan da ya tozarta mahaifiyata da ke kwance a cikin
kabari da mata kazafi akan abinda bata aikata ba gara na fadi gaskiya koda ace
itace karshena. Abinda ya fara fada ya faru amma a iya shi da mahaifiyarsa ne banda
Ummi na, shi da kansa ya bani wanna labarin a randa muka yarda zamu hade kai domin
yakar dan uwanmu Haysam. Dunkulewar tamu kuma ta samo asaline kan ima diyar Hifzur-
rahaman fade da mukai ta mutu, muka bizne gawarta a cikin masarautar nan batare da
sanin kowa ba ranar bikin al'ada. Tabbas mune muka aikata ni da shi, kuma duk neman
da akai taima yarinyar har zuwa wannan shekarun da kowa ke tunanin saceta akai ko
bata tai a bikin al'ada ba haka bane ba. Bayan mun dunkule mun shiga yakin gain
bayan Haysam tako ina amma bamuci nasara ba. Muna a cikin wannan yakinne kuma yazo
mana da zancen yin murabus ya daura dansa. Hankalinmu ya tashi matuka, a lokacin
muka bazama neman bokaye kwararru da suka iya aiki, har muka had da boka Barbushi.
Boka Barbushi ya mana alkawarin taimaka mana, da kuma tabbatar mana kashe Haysam da
dansa. Munji dadi matuka tare da kasancewa cikin farin ciki mara musaltuwa, dan
haka muka ware akai bikin nadinsa kamar babu komai a ranmu. Sai dai kuma mi, a
randa Barbushi ya bamu gubar da zamu zubama Haysam sai muka iske Haysam ba'a cikin
hayyacinsa ba. Shi kadai a daki yana ta aman jini da kiran sunan Eshaan da Mammah.
Ganinmu yasa ya fara kiranmu akan mu taimakesa mu kira masa su, amma sai mukai
fitowarmu mamaki fal zukatanmu, duk da ta wani bangaren murna muke zai mutu. Mun
garzaya wajen boka Barbushi muka sanar masa komai, nan fa take shima ya shiga
mamaki jin bama mukai da basa tamu gubarba. Gubar ya amsa ya ce mana muje mu dawo
washe gari zai bincika, dan tabbas bayan mu akwai mai farautar rayuwar Haysam din.
Gabanin asubahi muka dawo cikin masarauta, sai muka iske ALLAH yay masa rasuwa ma.
Muni farin ciki, sai dai zukatanmu sun karkata da son gano wanene keda irin
burinmu, domin mu a ganinmu dole ne shima mu kaudashi dan karya zame mana matsala
idan shima burinsa yin mulkinne. Abinda fa zai baku mamaki a duk hadin kan nan namu
muma bawai muna kaunar juna bane. Mu dikanmu burinmu shine muga bayan juna idan mun
kauda Haysam da dansa. Abinda ya kara rikita lissafinmu mutuwar matan Eshaan guda
biyu a washe garin mutuwar Haysam, babufa shiri muka koma wajen Barbushi.

Boka Barbushi ya tabbatar mana da lallai akwai matsala, sannan bayan mu akwai
wasu masu kudirirrika sosai a cikin masarautar zagaye da rayuwar Eshaan. A yanzu
hakama bayan wadan nan matan nasa biyu da suka rasu wasu zasu sake. mutuwa da shima
bai san adadi ba. Sai dai akwai gabar da abubuwa zasu canja kansu dalilin auro wata
yarinya da bata cika ashirin ba. Wannan yarinya akwai al'amari mai girman gaske
tare da ita, sannan tana tare da manyan sirrika, a cikinsu ma harda babba daya
kasance sirrin wanna masarauta. Idan kuma har ta shigo gidan burinmu bazai taba
cika ba na mulkar kasar ruman. Mun tashi hankalinmu amma sai ya dakatar da mu da
cewar mu kwantar da hankalinmu, munada hanya daya ta bullewa. Hanyar itace bibiyar
duk matan da Eshaan zai aura, zamu gano wanna yarinya ne kawai ta hanyar auren yara
biyu da ga gidansu itace cikon ta uku, biyun zasu mutu bayan suma sun shigo
masarautar. Sai muyi kokarin shafe ahalin wanna yarinya gaba daya ita kuma muyi
amfani da ita ta karasa halaka mana Eshaan shike nan zata kare rayuwarta a kurkuku
koma a tsireta Jasim ya hau karagar mulki ni kuma na zama magajinsa batare da
wancan sirrin ya bude ba. Komai ya mana, sai dai mu burinmu sanin wanene zai dinga
kashe matan nasa? Ya sanar mana shima bai iya gano su wanene ba gaskiya. Amma
sunada hadari sosai, kuma a cikin gidan nan suke suma, bai kuma kamata mu damu da
abinda zasu aikata ba dan zasu mana aikinmu ne cikin sauki muma, Eshaan bazai samu
soyayyar mutane ba a dalilin wanna kashe-kashen, dan kowa zai kallesa a mai kashe
matansa.
Shi kuma zai maida hankalinsa ne a neman wanda ke kashe masa mata mu kuma muna
aikinmu a kansa cikin sauki, Mun gamsu mun kuma dawo gida cikin farin ciki. Tun
daga nan abubuwa suka cigaba da gudana, muma muka dage, bama sanya waien kokarin
shiga da fita da gain an aurama Eshaan mace bayan mutuwar wasu. Ga kuma abinda duk
boka Barbushi ya fada yanata faruwa daki-daki, tako ina zaginsa ake da la'antar
mulkinsa har mutane na kiransa da Fir'auna. Hakan a mana dad, shiyyasa ma muka baza
yaranmu tako ina suna gano mana kyawawan matan da za'a aurama masa, da munzo muka
kalame Mammah da zance musamman ni sai ta amine da fatan ALLAH yasa karshen
al'amarin kenan. A haka har lissafinmu ya kai ga wasu yara da mahaifinsu ke kawo
zuma masarautar nan. Wani kuma yaronmu dake mana aikine ya kawo mana zindensu ashe
abokinsa ne. Mun tabbatar da auren ta farko kamar yanda aka saba itama ta mutu,
kasancewar munga biyu bayanta muka sake shigewa gaba aka auro ta biyu. Itama dai ta
rasun, dan haka muka dira akan ta uku. Shekarun yarinyar da wanda Barbushi ya fada
ne ya samu farin cikin da fahimtar itace wadda muke nema, dan haka bayan an aurota
muka fara shirya yanda zamu tarwatsa ahalinta. A wanna ranarce wanda yay mana
hanyar sanin gidan yaji hirarmu (abokin nasa kenan), bamu nuna masa mun sani ba,
sai muka bibiyi rayuwarsa ta hanyar matarsa. Kudi muka bata mai uban yawa da
firgita mata rayuwa, harma Jasim yay amtan da ita sannan muka bata gubar data bama
mijin nata sannan muka wuce. Washe gari bamu san miya faru ba ta kiramu a rikice
wai mijinta ya tafi sanarma iyayen yarinyar nan komal amma ta bashi gubar da muka
bata. Hankalinmu ya tashi, babu sanya muka samar da yan sanda suka je gareta da ga
nan tai musu jagora zuwan gidan. Anan ne muka saka aka kama mai gidan da babban
dansa. (Nasan dal baku manta kama babiy da Hanash ba?)".

Arshaan yaja numfashi ya fesar cikin kunar zuciya, sai kuma ya cigaba da fadin,
"Makwafcinsa da wani tsoho da akace mahaifin matarsa ne sun cigaba da fadi tashin
gain sun san inda suke, sai dai hakan ya gagaresu, a da burinmu kawai mu kashesu a
lokaci daya, sai dai yanda Barrister Abdallah Aas ya shiga zance sai mukai sha'awar
cigaba da buga wasan. Dan haka muka cigaba da wasa da hankalinsu, mun shirya kawo
karshen rayuwarsu a gabar da muka gama shirya kawo karshen rayuwar Eshaan. Sai dai
su bamu maida hankali kansu ba sosai dan a ranar muka damka madara mai duke da
gubar dafin macizai ga yarsu, dan haka tunaninmu ya karkata kan yarsu gaba daya da
kuma aikin da muka sakata. Da ga baya aka sanar mana suma an kashe mana su.…..✍️

DAUDAR GORA
Book 2
74

…...……….Komai ya zama an yanka ta tashi, kashe ahalinta


ne kawai bata tashi mana ba, dan su kam an tabbatar mana sai dai was basu ba.
Eshaan bai mutu ba, ita kuma ta samu nasarar barin kurkuku, sannan mun neman
Barrister Akeem daya jagoranci kashe mana iyayenta mun rasa. Tun daga lokacin komai
ya rikice mana, wasan ya fara sauya salo. Koda muka tunkari Barbushi sai ya kwantar
mana hankali da cewar ya samo wata mafitar. Zai kauda mana yarinyar cikin sauki,
zai kuma kwantar da Eshaan ciwo da komai sai dai a masa. Dolene a lokacin a yarda
daya da ga cikinmu ya zama Shahan-shan. Wannan shine dalilin samun kaimi da ga
kowannenmu na ganin ya kuma kada dan uwansa kasa. Yayinda muka cigaba da kulla
makirce-makirce ga Eshaan ciki hard kashe Sayeed Khairul-Bashar da haddasa zanga-
zangar mutanen kasa, da tada bomb a cikin motar Barrister Abdallah Aas, da hada
videon yanda yake kashe mutane da tsafi muka Bama matarsa da tunanin zata yada
duniya ta gani, amma sai duk batai haka ba...

Wata irin hayaniya ta tashin hankali ce ta tashi a kotun, musamman iyalan Sayeed
Khairul-Bashar. Babban dansa yay wani irin daka tsalle sai gashi a gaban su Miran
Arshaan din. Shaka ya hadasu ya kai musu, take yan uwansa suma suka iso. Da kyar
aka kwaci Miran Arshaan da Miran Jasim a hannun yayan Sayeed Khairul-Bashar, dan
sai da Shahan-shan ya tsawatar da kansa. Sai dai shima karfin hali kawai yake, duk
da kuwa yasan abubuwa da yawa da Miran Arshaan din ya fada a yanzu ta dalilin
bibiyarsu da ya rinkayi, akan su Bably kuwa randa Iffah tai masa rakon nan na ya
binciko mata iyayenta a matsayin Ajmaal a ranar ya fara bibiyarsu har ya gano sune,
shine kuma ya kubutar da Barrister Abdallah as da ga tashin waccan nakiyar da har
yanzu mutane da yawa suke dauka ya mutu. Kisan Sayeed Khairul- Bashar ne kawai bai
gama tabbatar da wanda yayisa ba sam sai yanzu da suka fada. Bayan kotun ta natsa
da kyar, masu kuka nayi, masu tsine musu nayi Sayeed Hanifud-Din da gaba daya
jikinsa yay sanyi ya dubi Miran Arshaan din da fadin, "Ita kuma Ameera Haifah
minene alakarku kenan?"

Kallonta Miran Arshaan yay, ganin yanda ta kakkafesa da idanunta ya sashi sakin
murmushi. "Duk abinda na lissafa maka anan harda ita a ciki, alakarmu ta fara
kasancewa a tare ne bayan mutuwar Haysarn Akhi. Sai dai ita da Jasim tun kafin
shigowarta masarautar nan suke tare. Dan ta kasance ma tarkar matarsa ce a yanda
yake tarayya da ita a duk sanda ya yaso…

*Tsinanne kaima ai naga kana tarayyar da ita, kuma garama ni kafin tai aure ne,
kaiko a cikin gidan nan tana matsayin matar Haysam din kake tarraya da it...

"Karya kake gatalalle, ban taba kusantar Haifah ba sai da Haysam ya rasu, ita
kuma ta kawo min kanta da kanta bani a gayyato ta ba. Idan karya na mata gata nan
ta misalta mana.......

Wani irin mahaukacin buga guduma Tajwar Eshaan yayi, sai da kowa ya zabura a
cikin kotun har Miran Arshaan din da ya karbe Miran Jasim a fusace. Tabbas da ace
idanunsa ba cikin gilashi suke ba babu abinda zai hana juyewarsu firgita kowa da ke
a wajen. Sai dai fuskarsa fa tayi masifar sake tsukewa,

Sayeed Hanifud-Din da ya fahimci maganar ce baya bukatar a cigaba da yi, ya ce,


"Kowa ya fahimta. Sai dai akwai abubuwan da bamuji da ga gareka ba,wanda kuma kowa
yake ji a jikinsa kune kuka aikata din. Na farko ima Zawjata-almilk allura lokacin
da take a kurkuku, sannan jefata a cikin ruwan shima".

"Tabbas allura mune, sai dai Bama allurar komai bace face ta sihiri da Barbushi
ya bamu domin kame mata jiki ta kasa tsinana komai, dan haka mukai amfani da rigar
da ke jikin Eshaan a randa ta bashi madara dan ta dauka shine, Haifah ce kuma tare
da ni muka je mukai mata allurar a ranar. Amma jefata cikin ruwa wlhy bamu bane
ba...."

"Karya kake kune Jasim, dan duk wanda ya aikata wadan can ayyukan to shine ya
aikata wannan, kana son ka boyene domin kuwa al'amarin yayi iri daya da saka Miran
Nayyar ruwa da akai shekarun da suka shude….

"Gaskiya ya fada basu bane ba!!".

Kusan a tare duk wanda ke'a cikin kotun ya dubi wanda yay maganar, yayinda Iffah ta
mike a zabure dan wanna muryar ko'a mafarki bazata taba layance mata ba. Kaka
kenan, dattijo ko muce tsoho mai ran karfe. Ya kara wani fes abinsa saboda canjin
rayuwa da ya samu duk da jikin tsufarsa na nan tare da shi. A hankalin Tajwar
Eshaan ya lumshe idanunsa da ke a cikin glasses, duk da shima dai abinda kakan ya
fada ya girgiza mamakinsa, ga zuciyarsa dama a takure take da zancen su Miran Jasim
na tabbatar da basu ke kashe masa mata ba kamar yanda Iffah ta taba fada masa.....
Sayeed Hanifud-Din ne ya katse shirun idanunsa a kan Kaka ya furta,"Taya akai ka
sani bawan ALLAH? Idan kuma har basu bane wanene?".

Kaka da ke fitowa da ga wajen zamansa ya tsaya gaban kotu yana mai sake jinjina
kansa. "Tabbas kamar yanda na fada basu bane. Abinda kuma ya fada sun aikata iya
shi din suka aikata sai wanda ALLAH ya barma kansa sani da su da suka aikata
abinsu. Amma tabbas kamar yanda basu da alaka da kashe duk Zawjata-almilk da suka
rasu, haka basu da alaka da kashe Miran Nayyar, itama kuma Zawjata- almilk
Fhareedah basu ne suka sakata a cikin ruwa ba".

"To wanene?".

Murmushi kawai kaka yayi sai dai baice komai ba. Yayinda kowa ya zuba masa ido a
cikin kotun. Malikat Haseenat son tuno inda tasan fuskar take. Malikat Bushirat kam
zuciyarta wani irin mugu mugun harbawa take da masifar karfi kamar zata fito ta
bakinta saboda abinda kakan ke fada. Sai dai zuciyarta kwantar mata da hankali take
akan ta nutsu ko shi hadimin da ya aikata aikin bai isa ganita ba balle wannan
shashashan tsohon da ke jiran ranar mutuwa….. Shirun kaka yasa Sayeed Hanifud-Din
sake maimaita masa tambayar. Yanzu ma kaka murmushin ya saki mai sanyi sannan ya
dago ya duba kowa da ke cikin kotun, idanunsa ne suka tsaya akan Iffah dake
kallonsa tana jin kamar ta taso ta rungumesa. Murmushin ya sake sakar mata ya dauke
idanunsa
"Ina rokon afuwa ga wanna kotu mai adalci akan kartsalandan da mai mata. Ban
kasance anan dan sanar da wanda ya aikata abinda ake son ji ba, domin kowanene a
wanna gidan yake kuma yana a cikin wannan waje sannan da kansa zai fallasa kansa a
gabar da ya dace kowa ya sansa..."

"Tofa babbar magana, kotu zata so sanin miya kawoka baba?". Sayeed Hanifud-Din ya
fada saboda inkiyar da Sayeed Tasadduq-Husain ya masa.

Gyara tsaiwa kaka yay da kyau, sannan ya ce, "Kamar yanda na fada a farko basu
bane, tabbas basu din bane. Su kawai ALLAH ya jarbcesu ne ta hanyar bibiyar wata
tushiya da suka zama sanadin samar da tsirranta a shekarun baya batare da sun
sani ba. Ta tafi ta sanadin su, sannan ta dawo ta sanadin su, duk da asali basu
bane mafarin komai, dan suma a karan kansu suna aiki ne akan aikin daba nasu ba".

"Baba ka sake sanyani a rudani, ko zaka bayyana mana komai a bude dai-dai da
fahimtar mu?".

"Mizai hana in har kotu ta bani dama?".

"Kotu ta baka dama, domin kana akan abinda take bukatar sani ne dan zartar da
hukunci ga masu laifi, da yin adalci ga masu gaskiya".

"To Alhamdullah ". Kaka ya fada yana murmushi. Sai kuma ya maida dubansa ga su
Miran Jasim da suke a rudanin son tuna inda suka san fuskar, dauke kai yay kamar
bai gansu ba ya sake maidawa ga Sayeed Hanifud-Din. "Mune ahalin Zawjata-almilk
Fhareedah. Mune kuma suka bada kwangilar halakawa, sai dai ALLAH ya kubutar damu
tare da Barrister Abdallah Aas da ya dinga fafitikar taimkonmu tun sanda suka fara
bibiyar mu". Ya karen maganar da nuna inda ya taso can karshen kotun.

A kusan tare Miran Arshaan da Miran Jasim suka zabura na tsabar kaduwa da gain
Barrister Abdallah Aas da su Baby. Dai-dai kuma da zaburar Daneen Ammarah da
idanunta suka sauka kan Babiy. Ba shekara ashirin ba, koda shekara dubu ashirin ce
bata jin zata manta da wanna fuskar duk da ganin kwanaki goma sha uku kawai ta taba
masa. An musu auren zalunci a wancan lokacin bada san ransu ba bada amincewarsu ba.
Amma sun hade kai sunyi kuka tare, sunyi murmushin kuma a tare, sun kuma shaku a
tare, sun kumaji radadin rabuwa da juna a tare, yayinda sukai kewar rashin juna a
tare, Hankalin duk mutanen da ke a cikin kotun ya rarrabu, wasu akan Daneen Ammarah
da ke nuna Baby cikin rawar lips alamar tana son magana ta kasa. Wasu akan su Miran
dasim da suka rikice. Was akan su Ummu da ke fitowa:

"Zayyan!! Tabbas kai ne! Kai ne Zayyan ko bayan shekara ashirin sau ashirin ne
bazan taba mantawa da kai ba!!!".

Wadan nan zantuka na Daneen Ammarah ne suka zaburar da kowa da kowa ido ya koma
kanta har Babiy da kansa ke a duke bai san anai ba, sai dai zuciyarsa wani irin
harbawa take da sauri-sauri tunda ya shigo cikin masarautar dama a yau. Shima dai a
karo na farko idanun nasa suka sauka akan Daneen Ammarah din, tsaf numfashinsa ya
dauke, yay taga- taga zai fadi sai da Barrister Abdallah as da Hanash suka tarosa.
Yan kananun magana ne suka fara tashi a kotun, yayinda Tajwar Eshaan ya kafe Iffah
da idanu ta cikin eyeglasses dinsa, sosai jikinta ke tsuma itama kamar wadda take a
rudani. Sai yaji ta bashi tausayi, wai a hakama bata san tushen al'amarin ba kenan.
Ji yake kamar ya rufe ido ya gansa da ga shi sai ita kawal ya rungumeta dan sarar
mata nutsuwa shima ko zai samu da ga radadin da zuciyarsa ke masa. Badan karya raba
kan mutane ba da zai dage shari' ar nan ne har sai gobe idan ALLAH ya kaimu. Amma
sai ya hadiye komai kamar yanda ya saba dan shi a karan kansa so yake yaji ta inda
aka fadi a ragaya, tunda dai gashi gwajinsu ya tabbatar da Daneen Ammarah matsayin
mahaifiyar Iffah'r itama. Sannan yanayin Babiy da Mammyn mana yanzu ya sake bude
komai a bayyane….✍️

DAUDAR GORA...
Book2
Chapter: 75

Da kyar da kyar aka samu kotun ta lafa, yayinda kalaman Daneen Ammarah dake kuka
sukai matukar daukar hankalin kowa. Fadi take, "Wlhy Mammah shine, shine wanda suka
cutar da mu a tare. Bazan taba yafe musu ba, wlhy bazan yafe musu ba, sun haddasa
bakin ciki mai ciwo a zuciyata. Sun nisanta ni da shi bayan sun alakanta mu".

Sosai hankalin Malikat Haseenat dama duk wanda ke'a kotun ya tashi, dan yanda
take kuka haka Babiy make kuka sai dai shi kansa duke yake a kasa. Ummu ma dai
tasan komai da ya faru, dan a lokacin bai boye mata ba. Hakama lyyani. Iffah nason
tashi taje garesu amma babu dama, dan ita Zawjata-almilk komai nata nada ka'ida da
son nutsuwa. Dole ta hakura ta zuba musu ido kawai musamman Babiy da Ummu da Daneen
Ammarah.

Tajwar Eshaan ya nisa tare da motsa lips dinsa a hankali, "Wannan kotu na bukatar
Daneen Ammarah a gabanta, da son jin fassarar kalamanta".

Sayeed Hanifud-Din ne ya maimaita abinda Tajwar Eshaan din ya fada, dan haka
Daneen Ammarah ta fito da taimakon Daneen Waheada,dan da alama abubuwan kanta ma
neman sukeyi, idanunta har sun kada.

"Ko zamu iya sanin abinda kike nufi da kalamanki Daneen Ammarah. Sannan ko
kinada alaka ne da wanna shari'ar?"

"Bani da alaka da wannan shari'ar face a farkon ta mai bada kariya ga Zawjata-
almilk. Sai dai inada alaka shudaddiya da wannan bawan ALLAHn". Ta nuna Babiy.

'"'Ko zamu iya sanin alakar taku?"

"Mun taba kasancewa mata da miji kusan shekaru ashirin da daya da suka shude".

Ba Iffah kawai ba, mafi yawan wanda ke'a cikin kotun sai da suka waro idanu
saboda razana.

Sayeed Hanifud-Din ya ce,


"Ta yaya?".

Shiru kamar batace komai ba, sai kuma ta nisa da share hawayenta. "Komai ya faru
ne a cikin littafin kaddara ta. Na san duk wanda yake anan in har ya kai shekara
talatin da biyar zuwa sama yason tabon da ke a jikin bangon littafin labarina da
duka shafukan cikinsa. Bazan kirasa abin kaico ba, amma zan kirasa zalunci mai ciwo
a gareni dama duk wanda yake cikin wannan masarautar. Faruwarsa kuma ta fara ne a
bisa son zuciyar dan uwana Jasim dake a gaban shari’a a yanzu. Sun kulla min aure
da wan nan bawan ALLAH bisa umarnin wata mushirika da ta shude ita da labarinta a
wannan masarauta. Sai dai aure ne na kwanaki goma sha uku kacal suka saka ya
sakeni. Bisa kudirar UBANGIJI kuma ya samar da haihu a tsakaninmu batare da shi ya
sani ba ma, dan ban sake ganinsa ba tun wannan ranar sai a yau, sai dai ALLAH yayma
yarinyar rasuwa a kwana uku da haihuwarta...

"BATA MUTU BA!!".

Kalmomi uku masu razanarwa da ga bakin kaka. Wani irin zabura Babiy da Daneen
Ammarah, da Malikat Haseenat, da Iffah, da Ummu, da Daneen Waheeda, da Malikat
Bushirat, da Miran Jasim sukai a lokaci guda kuma a tare kamar wanda aka saita da
camara.Su dukansu kuma suka zubama Kaka da yay maganar idanu kowanne da irin kalar
luguden dakan da zuciyarsa ke masa a zahirance da badini. Cikin karfin hali Malikat
Haseenat ta furta, "Taya wadda naima wanka, na shirya a cikin likafani, aka
sallaceta a gaban kowa, aka gina kabari aka sakata za'ace bata mutu ba. Kai wanene?
Ya akai kuma kasan hakan?".

"ALLAH ya kara miki lafiya da tsohon rai mai albarka. Nine mutumin da ya kora
waccan bokanyar mushirikar a waccan raar dai da nasan bazaki manta ba".

Ya arrahaman! Bawan ALLAH dama kana raye? Amma ka sakani a rudani.

"Nasan zan saka kowama a rudani, sai dai wannan ranar ita naita rokon UBANGIJI
zuwanta gareni kafin ya dauki rayuwata dan na cika wasiyyar mahaifina. Duk da
burina ya cika na dawowar Fhareedah cikin zuri'ar mahaifiyarta a dalilin aure".

Kowa zubama Iffah idanu yayi, kamar yanda itama take kallon Kaka jikinta na dan
rawa. Malikat Bushirat ma wani irin bugawa kirjinta keyi, hakama Daneen Ammarah da
Babiy. Cikin rawar baki data harshe Babiy ya ce, "Baba na kasa fahimtar komai".

"Yanzu zan fahimtar da kai dama duk wanda ke anan. Kamar yanda Daneen Ammarah ta
fada an aura mata miji kuma an saka ya saketa a sati biyu bisa umarnin mushirikar
dake katantanwa da ikon wanna gida. Ba kowa bane wanda aka aura matan nan face
Zayyan in Abbas. Zayyan dai da ne ga wani aminina da zan iya cewa ma ya zama
jinina. Dan tunda muka taso babu abinda ke rabani da Abbas. Hatta aure an mana a
rana guda ne, hakama haihuwar yaranmu tana zuwane a kusa da kusa. Sai dai shi nashi
basa zama sai akan Zayyan. Sana'ar gidan su Abbas dinka kayan doki ne, dan haka ita
ya gada ita kuma yake yi tunda yasan kansa, wannan dalilinne ya sani koyo a
wajensa, danni gidanmu abinda na tashi naga anayi bana ra'ayinsa. Mahaifina babban
mutumne mai bada magani sannan yana cire kowadanne irin aljanu a jikin mutum duk
taurarin kansu. Ni kuma sai nake ganin kamar wani abun akwai kauce hanya, dan haka
naki yarda na dingayi duk da tunda na taso yanayi a gabana na kuma san magunguna da
sirrika kala-kala. Mukan dinka kayan doki ni da Abbas mu kawosu cikin Dahab City,
anan ne muka hadu da wani bawan ALLAH da yay sanadin fara kawo wadan nan kaya namu
cikin masarautar nan. A duk sanda muka kawo akan bamu kudinmu ne gaba daya, sai ma
yazamindai mun dinka din nan kawai muke kawowa. A haka muka cigaba da rayuwa har
shekarun yayanmu suka kawo girma, iyayrnmu suka bamu shawarar hada yaranmu aure.
Munko yi farin ciki da shawarar, babu bata lokaci aka sha bikin Jumayma da Zayyan.
ALLAH ya azurtasu da haihuwar fari da wuri, ta biyu ma haka, hakama ta uku. Zuwa
sannan idan mun dinka kayan doki duk wanda zai o kawowa yakan taho ne da Zayyan da
shine kadai keda sha'awar irin sana'ar tamu. Sauran yarana biyu maza kuwa suna nasu
aikinne da sukafi so suma. A wata rana data kasance nine zan kawokayan da muka
dinka masarautar a cikin azi sai na tashi da ciwo na zazzabi, dan haka Abbas ya
amsa suka tafi kaiwa tare da Zayyan. Basufi awa takwas da tafiya ba sai gashi ya
dawo min yana kuka. Hankalina tashe na tarbesa da tambayar lafiya. Bai boyen komai
ba ya sanar min wai amma Zayyan aure da diyar Shahan- shan, cikin mamaki nace aure
kuma? Wane irin aurene haka kamar auren kaza? Kuma da yar Shahan-shan guda anya
kuwa?. Ya tabbatar min hakane, amma yanaji a jikinsa akwai dalili mai karfi nayin
hakan dan yaji wasu yan samari da basu wuce sa'an Zayyan din ba na labari. Nan ya
zayyane min komai dake faruwa ni da baba. Na lallashesa da kwantar masa da hankali
na shirya a boye naje masarautar bisa umarnin mahaifina. Anan nake jiyo komai dama
asalin dalilin hadin auren. Hankalina ya tashi dan na fahimci babban al'amari ne
kam gashi ance Shahan-shan ma baya kasar shi da uwargidansa da Miran mai jiran
gado. Kannensa ne da wannan aika-aikar. Na koma gida cikin damuwa mukai zaman jiran
tsammani, tun muna irga kwanaki harya koma sati har sati biyu. anar kwatsam sai ga
Zayyan ya dawo mana. Duk mun tarbesa da tambayoyin yaya akai ya kubuta. A take ya
zayyane mana komai yana hawaye. Murmushi mahaifina dake kwance yana jiyya yayi, sai
dai baice komai ba, sai daga baya 22:58
¡kirani yake sanarmin ya fahimci Zayyan ya kamu da soyayyar matar aurensa ta sati
biyu dan haka a karo na farko yana son nayi wani abu, ya kuma tabbatar min ba
shirka bace kamar yanda nake dauka dan shi ba mushiriki bane. Komai sai da ya
zayyane mun, dan haka na dauka alwashin bibiyar al'amarinta har sanda zata haihu
kamar yanda mahaifina ya bani umarni. Shi kuma ya sakashi baro cikin Jumna dan yace
ya tabbata za'a iva zuwa nemansa, za kuma a nemesa a ko'ina dan haka yace yaje
cikin Dahab City din inda bazasu taba tsammanin zasu samesa a kusa da su din ba,
wannan ne dalilin dawowar Zayyan wanna gari, su kuma su Abbas ya sakasu dawowa
cikin gidanmu yanda mutane zasuyi tunanin suma sun gudu. Haka kuwa akayi, bayan
tafiyarsa da kwana biyu shi da matarsa da yaransu uku sai gashi anzo nemansa. Sai
dai iya bulayi basu samesan ba, da ga baya dole suka hakura. A wannan dan tsakanin
Abbas ya kamu da rashin lafiya ta kwana hudu kacal ALLAH yay masa rasuwa. Wannan
mutuwa ta gigitamu matuka,hakama matarsa da Zayyan. A wajen zaman gaisuwar Abbas da
Zayyan ke zuwa a sirrance ya hadu da Abu Musa, wanda shine silar masa hanyar kai
zuma cikin masarauta dama abokinsa ne na yarinta. A tsorace yazo ya sanarma
mahaifina abinda Abu Musa yazo masa da shi. Sai yay murmushi tare da kwantar masa
da hankali tare da bashi kwarin gwiwa saboda wani hasashe da yace yayi akan
hikimar cigaba da zuwan nasa masarautar. Duk da shima yana da mai kawomasa duk wani
rahoton da yake so na cikin masarautar, a haka nema muka san samuwar cikin
Fhareedatu, wanda kuma yay dai-dai da samuwar ciki na hudu ga diyata matar Zayyan
itama. Abubuwa sun cigaba da kai da kawo har zuwa ranar haihuwa, a lokacinne kuma
mahaifina yasa na shirya yin abinda ban taba yi ba. Wato aiki da kayansa.
Alhamdullah sai kafin ma nai wani yunkuri sai ga kiran mahaifina da ga masarauta
wai zasuyi aiki. Da farko banyi niyyar zuwa ba dan shi mahaifina bazai iyaba saboda
ciwo, amma sai ya zaunar dani yay min bayanin komai dama ban hasaso ba. Tunda dama
ni nayi shirin shiga masarautar ne kawai na dakko abinda za'a haifa na fito kamar
yanda ya sani sai a yanzu kuma labari ya canja. Bani da ikon bijirema umarninsa,
kamar yanda shima bashi da ikon bijirema kiran masarauta dan haka na shirya zuwa
kamar yanda ya umarceni tunda a duk abinda ya sanin banga shirka ko wani tsafi a
ciki ba. Ina cikin shirin tafiya masarautar a dai-dai lokacin sai ga labarin
haihuwar Fhareedatu da ga bakin amintaccen mahaifina. Wannan shine ya zaburar dani
zuwa a gaggauce. Lokacin dana iso bokanyar ta riga ta gama shirya komai da su
basuyi zato da tsammani ba ma, amma duk da haka nai iya kokarin da zan iya na mata
kiranye da hadata ita da yan kayanta na Koreta a cikin masarautar kamar yanda
mahaifina duk yace nayi. Ni nasan a korar da mahaifina yasa nai mata bazata iya ta
dawo ba, amma kuma sai zuciyata keta faman mini kikawo. Idan uwar masu gida bata
mantaba, nine na fadi cewar yarinyar ta rasu a lokacin da nasa a kawota gareni na
dubata".

"Tabbas anyi haka".

Cewar Malikat Haseenat. Murmushin Kaka yayi, da cigaba da fadin a lokacin


amintaccen mahaifina ya bani gawar wata jaririyar dana canji jaririyar da ita ya
fito da wadda aka haifa. Bakowa bane kuma sai wanda a yanzu kuke kira da Baba mai
magani a gonar yaro, shugaban masu magajin gargajiya na wanna masarautar, saboda
shi din yaron mahaifina ne"…..✍️

DAUDAR GORA
Book2
Chapter: 76

.....…."Na iso gida da farin cikin wasan ya kare, sai dai ina danka jinjirar a
hannun mahaifina ya kalleta da juya bayanta ya tsirama tambarin tawadar ALLAH dake
a bayan nata idanun, sai cewa dani yay (A sanadin ta kullika da yawa zasu bude.
Harma da wanda ba'ai zato da tsammani ba. Zata zama tauraruwa mai hasken gaske a
cikin taurari, zata kuma zama shahararriya a duniya bama a kasar ruman kawai ba.
Zata auri mutum mai daraja da cikar kamala, amma sai kunyi hakurin jure rasawa
kafin ita ta samu. Sai kun boye komai kafin komai ya bayyana. Hatta da mahaifinta
zai raineta ne batare da yasan ita bace) ban fahimci mi yake nufi ba, Ni damuwarta
ma a lokacin yanda zamuyi da yarinyar nan. Kamar da ga sama sai ga Zayyan, baba ya
sani na boye jinjirar sannan aka bashi izinin shiga. Bayan ya gaishemu yake sanar
mana Jumayma na nakuda ne, yazo amsar mata magani ne a wajen kaka kamar yanda ya
saba basu. Babu musu mahaifina ya hada masa komai ya basa, tare da sanar masa ya
gaggauta komawa a bata tasha. Bayan wucewarsa da kadan mahaifina ya ce nai haramar
daukar jinjirar nan nabi bayansa, dan Jumayma zata haihu yarta babu rai, na dakko
waccan na alive musu wannan din. Da mamaki na tambayesa yanda akai yasan haka,
danni dai dama wadan nan abubuwan nasa yasa nake kyamatar harkokinsan. Dan murmushi
kawai yay, da fadin kusan wata guda kenan Jumayma a sanarmin batajin cikinta na
motsi, a ranar karshe da tazo kuma na fahimci yaron cikinta ya mutu mata a ciki ne,
shiyyasa ma nace matarka taje ta zauna da ita a can ita da Maman Zayyan. Nan ma a
tsorace nace to kace baka son kowa ya sani, amma taya zan canja yarinyar bayan su
zasu amshi haihuwar? Nan ma sai da yay yar dariya sannan yace karka damu jeka kai
dai ka basu. Kaina a daure da wannan lamari nasa na tafi, na sake dawo da jinjira
cikin Daular ruman. Ban yarda na shiga gidan ba, na saka aka kiramun matata
(lyyani) a sirrance, a mamakina koda ta fito na bata jaririyar bata nunamin damuwar
komai ba face rungumeta da tai da sumbatarta ta shige abunta. Ashe ni ban fahimci
yanda al'amarin yake ba sai da na dawo gida yake sanarmin ba lyyanin bace, suffarta
kawai aka shiga. Nasan zaiyi fiye da hakan ma, sai bance komai ba dan banda abin
fadar. A takaice dai yarinya taci suna Fhareedatu, amma iyayenta na mata alkunya da
Iffah, da gani sai babana muka san ba yarinyar da
Jumayma (Ummu) ta haita bace. Sun cigaba da rainonta cikin yanayin ciwuka daban-
daban, dan tanata laulayi har sat da takai Jumayma ta dawo da zama Jumna tare damu.
A lokacin jikin baba yayi tsanani, amma haka ya dinga fadamin abubuwan maganinta,
dan ya tabbatar min abinda sukai niyyar yi da itane ya tabata tun tana a ciki,
ALLAH ya bata kariyane baiyi tasiri ba, sannan iskokin da ke akan mahaifiyarta ma
masu karfine, a yanzu haka ma sun dawo jikinta itama. Kwanan Jumayma bakwai da zuwa
gida ALLAH yay ma mahaifina rasuwa shima, inda ya barni da wasiyya mai girma akan
Iffah. Ya tabbatar min hatsabibiyar bokanyar nan zata dawo, zata dawo cikin wanna
masarautar dan akwai wanda ke tare da ita da jimawa, zata dawo ta jikinsu kuma zata
cigaba da illar daukar fansa. Dan tun fil'azal tanada burine darna akan karagar
mulkin Shahan-shan. Ya umarcenta karna sake zuwa cikin masarautar, amma Zayyan ya
cigaba da kai zumarsa babu wanda ya isa ya ganeshi, hatta ita mahaifiyar yarinyar
ma bazasu tapa hada koda hanya ba sat bayan komawar iffah cikin masarautar matsayin
matar aure. Hankalina ya tashi, na tambayesa ta yaya kuma zata koma. Ya cemin la
kudirar UBANGIJI, amma st kansa bai sani ba. Abinda kawai zanyi shine a duk lokacin
da hakan yazo duk abinda na gani a mafarkina har sau uku
yana maimaita kansa to na aiwatar. Cikin damuwa na sanar masa ni bana son al'amuran
nan nasa. Yay murmushi idanunsa a kaina. Kafin ya kira sunana da fadin, (Baka isa
canja abinda ALLAH ya rubuta ba daga kaddararka, tabbas al'amarin dake zagaye damu
baiwace da ga ALLAH, sai dai wasunmu na kaucewa wajen tafiyar da ita har su hada da
shirka ko saka wasu a shirka. Why why Ban taba aikata shirka da wannan baiwar tawa
ba, sai dai ina bada maganin da ALLAH ya sanar dani akan duk wani shaidani da
cututtuka. Kai jinina ne, a kuma dade da tabbatar da abinda yake tare da ni kaima
yana a tare da kai, sai dai bazan tilastaka yin abinda ni nayi ba, zan dai rokeka
tsayawa a bayan yarinyar nan da izinin UBANGIJIN har ranar da makiyanta zasuyi
kuka. In ba hakaba ba iya ita ba, kasar ruman gaba dayanta na cikin garari inhar
waccan mushirikar ta samu cikar burinta a kanku. Domin burinta shine mulkar kasar
ruman ne, ta taka wasu tsanikan nasararta kuma a dalilin son zuciyar wasu dake
cikin masarautar da karancin toro da dogaro ga ALLAH. ALLAH ne ya daura maka wannan
nauyin bani ba, dan haka jeka, jeka maza da iznininsa ka magance matsalar). Wanna
wasiyyar ta mahaifina sune sanadin komai, sune suka cigaba da jagorantata har zuwa
yau. Fhareedatu ta tashi yarinya mai shiga rai, kyakykyawar gaske da akoda yaushe
mukanta mamakin wama ta biyo a kammani, dan duk da tana kama da yan uwanta idan ka
nutsu zaka fahimci kamanin nata sunada sirrika masu yawa kuma duk ta fisu kyawu.
Kamar yanda mahaifina ya fada nakanyi mafarki akan abubuwa da yawa da suka shafeta,
wani lokacinma akan min abu kamar wanda aka budema idanu, duk yanda nake gudun bada
magani ko taimako akan masu hatsabiban iskoki wani lokacin saina tsinta kaina nayi,
amma dai ina iya bakin kokarina na ganin na kaucema hakan. Dan da gaske abubuwa da
yawa basa kwanta min a rai, duk da Alhamdullah ni dai wani aljani bai taba sakani
yin yanka na zubda jini ba ko shardantamin wasu abubuwa. Kawai nakan samu kaina da
yin abunne.Komai ya fara fitowa ga Fhareedatu a lokacin data fara mafarkai akan
abubuwa, duk mafarkin da tayi nima sai nayisa cikin amincewar UBANGIJI. A lokacin
na fahimci komai yana tunkarowa kenan, ban fahimci kalaman baba ba na sai muni
hakuri mun rasa kafin ta samu sai lokacin da Arfa ta rasa ranta, aka kuma na Fariha
itama. A jiyyar da Fhareedah tayi na kusan wata bakwai kamar wadda ta fita a
hayyacinta ne na fahimci komai da ga wasiyyar mahaifina, da ga lokacin ne kuma
abubuwa suka fara daki-daki har zuwa yau. Hatta bibiyarmu da suka saka anayi na
barsune kawai, hatta kubutar damu da akayi da ga shirinsu nasan wanda yayi. Duk
kanin kalubalen da Fhareedah ke fuskanta a gidan nan nasani duk. Sai dai abinda
masu hakilon basu sani ba tana zagaye ne da kariyar UBANGIJI, ya saka wasu halittu
gadinta domin masu talala da ita da ruguza ayyukansu badan ta banbanta da sauran
mutane ba ko zama ta daban. Kawai dai UBANGIJI idan yaso karya azzalumi sai yay
masa talala da abinda ya raina. To hakance akan Fhareedah da mushirikar bokanya da
ma duk mabiyanta dan sun san kansu".

Kotu fa tayi matukar yamutsewa, yamutsewa ta tsananin tashin hankali da


al'ajabin wanna labari mai rudarwa. Rudarwar da ke neman hargitsowa da zukatan
wasu. Wasun da har shi kansa Shahan-shan din a wannan gabar ya matukar girgiza.
Tabbas yasan labarin Bokanya uwa da aka kora a masarautar, sai dai lokacin baya
kasar. Ya kuma san Aunt dinsa Daneen Ammarah tayi aure ta haihu yar ta mutu amma
bai san tushen auren ba tunda a lokacin duk baya nan,sanda zai dawo kuma an binne
labarin da binnewar dokar mahaifinsa. Idanunsa da ke cikin eyeglasses ya sauke akan
Iffah da tun dazun kanta ke a duke, yana bukatar sanin halin da take ciki a yanzu
fiye da komai. Dan hatta da tunani akan wanda ke tare da bokanyar ya kasa nutsuwar
yi so yake ya fara sanin halin da take ciki. Yanda aketa kokarin son ganin kotun ta
nutsu amma hakan ya gagara dole aka dage zaman har sai zuwa washe gari domin
yankema su Miran Jasim hukunci dai-dai da laifinsu, sannan a dora sabuwar sharia da
bincike akan wanda ya saka Iffah a cikin ruwa saboda alakarsa da uwa....

* SASHEN MALIKAT HASEENAT*

Rungume Iffah take a jikin Ummu da Daneen Ammarah da suka sakata a tsakkiya suna
kuka, kuka mai ban tausayi da taba zukata. Hakama Babiy da Hanash da lyyani nasu
sukeyi. Duk taurin zuciyar Daneen Waheeda kukan takeyi, Kaka da Malikat Haseenat ne
kawai zaune shiru sai dai kowa yasan suma kukan zuci sukeyi. Yar gyaran murya kaka
yay da gyara zamansa. Hakan yasa duk suka dubesa.

"Inaga kuka bashi bane mafita ayi hakuri hakanan.Abinda ya faru ya riga ya faru.
Komai daya faru hikimar UBANGIJI ce da ga cikin hikimominsa da rahamarsa. Ya boye
komai a inda kuke batare da saninku ba. Ina naman afuwarku na boye komai da mukai
ni da mahaifina. Bamuyi hakan domin son zuciya ba. Sai dai kawai dan hakan itace
kaddararmu mu duka dake anan din. Mu talakawanku ne, amma a sai UBANGIJI ya fidda
tsiro a tsakaninmu domin nuna ikonsa akan shi fa talaka da mai arziki da mai mulki
duk daya suke a garesa, wanda yafi waninsa shine wanda yafi tsoronsa kawai. Dan
haka ya rinjayar da Fhareedatu garemu matsayin iyaye maza ku kuma mata, shiyyasa ta
dawo ta rayu a hanunmu duk da a zahiri bamu da wannan karfin sam. Sannan ya kaddara
Jumayma itace zata shayar da ita da rainonta matsayin uwa batare da ta taba farga
da ba'ita ta haifeta ba. Wannan na nuna mana cewar da na kowa ne, hakama uwa ta
kowane da ne. Ka haifa bashi ke nufin naka bane kai kadai, baka haifaba bashi ke
nufin bazaka samu daga samuwar wasu ba. lyaye dake kallon yayan da suka haifa ne
kawai yaya masu daraja da soyayya a zukatansu sai su canja. Kima dan wani
kyakykywar addu'a yayinda kika gansa a wata hanya kema sai mala'iku su amsa da
fadin(Amin!! Tare Da naki) wasu mutanen kuma su masa batare da kin sani ba. Ki
tausayama maraya da dan daya tashi a yanayin wahalar talauci na iyayensa ko tsintar
kansa a wani yanayi kema sai ALLAH ya tausayama naki da hadashi da masu tausaya
masa, dan dole kema akwai abinda rayuwarku take bukata. Ki kyautatama dan wani
ALLAH zai kyautatama naki koda bakya a raye a duniya. Kar kiga gazawar yaye akan
kaddarar yayansu tayasu masa aadu'a da musu fatan alkair ALLAH zai katange naki,
Hikimar UBANGIJI babu ta inda baya zartar da ita ga bawansa"….✍️

DAUDAR GORA
Book2
Chapter 77

....………"' Tabbas hakane, yau kuma na kara tabbatarwa. Auran Ammarah da Zayyan
abunne da bamu shirya masa ba, hakama samuwar wannan yarinya da rasata duk cikin
tsarin UBANGIJN talikai ne. Baku aikata laifin komai a garemu ba face taimako.
ALLAH kuma ya kaddara Zayyan matsayin miji ga Ammarah dan ya sanar damu abinda bamu
da ilimin saninsa. Lallai jini ba karya bane ba. Dan tun a randa na fara ganin
Fhareedah naji kaunarta mai karfi a raina, hakama mahaifiyarta. Komin kankantar
al'amarin da ya shafeta Ammarah bata wasa da shi. Zuciyata ta fara rawa a kanta a
lokacin da was al'amura nata ke kamanceceniya da Ammarah. Sai dai ban san ta ina
zan kamo al'amarin ba balle na bashi fassarar da ya dace da shi. Dan ko'a randa
mijinta yazomin da batun tambarin tawadar ALLAH dake jikinta irin na wannan zuri'a
al'amarin ya jima yana mun kai kawo da kasa banbance makamar rikewa. Hakan yasa a
cikin watan azumin nan dukkan addu'oina suka karkata ga al'amarinta. Sai gashi ya
sake zuwa min da batun gwaji, yau kuma gashi kun tabbatar mana da komai ALLAH ya
saka muku da alkairinsa, ya baku kariya fiye da wadda kuka zama sanadin bama wanna
yarinya da ahalinmu bisa zartarwar UBANGIJINMU da ya sakaku zama sanadi. Yanda
UBANGIJI ya hada jininmu a duniya, muna fatan ya hadamu a aljannarsa.Ina farin ciki
matuka da kasancewar Fhareedah a cikin jikokina jinina, dan ita abar so ce ga
kowa".

A tare duk aka amsa da Amin kowa na sharar kwalla. Kafin kuma rikici ya balle
tsakanin Ummu da Mammy (Daneen Ammarah) akan Iffah. Ummu ta tabbatar har yanzu
Iffah bata sauya ba kuma bazata taba sauyata matsayin wadda ta haifaba a zuciyarta
ba. Tana mata kauna irin wadda takema su Hanash, dan haka bafa zata barma Daneen
Ammarah ba. Itako ta marairaice mata akan tunda ta dana na shekara goma sha tara
itama ta barta tai goma sha tara sai a koma yar sati-sati. (Iffah mai iyaye da
yawa😂) Dariya Kaka da Mammah da lyyani da Hanash, Daneen Waheeda suka dinga yi
musu. Shi dai Babiy kansa a kasa yana murmushi kawai, lokaci-lokaci yakan saci
kallon Mammy din kamar yanda itama take satar kallonsa. Ummu duk tana lure da su,
amma sai bataji komai na jin zafi a ranta ba sai ma tausayi da suke bata. Hakama
Malikat Haseenat tana lure da su. Sallar la'asar ce ta tada zaman. Fuskar Iffah
murmushi da hawaye sun kasa tsayawa. Ana dawowa da ga salla sashen Tajwar Eshaan
suka nufa gaba dayansu bisa umarninsa. Kallon Iffah da duk tayi wani sukuku yake ta
kasa ido zuciyarsa cike da tausayinta. Tun dazu hankalinsa na kanta, ko abinci bai
iya ci ba sai madara kawai da ya dan sha kadan, yata tsammanin shigowarta amma
shiru, dan haka ma yama Malikat Haseenat aiken son ganinsu gaba daya. Yau dai kam
gasu Baby ga Shahan-shan a zahirancensa dan ko eyeglasses babu a idanunsa ma. Sun
mika gaisuwar girmamawa a garesa yayinda shi kuma ya amsa musu da mutuntawa. Sun
kara tattaunawa sosai inda shi babu wata kwana-kwana ya bukaci jin ta bakin Babiy
da Mamy (Daneen Ammarah) akan maida musu aurensu. Diri-diri sukai su dukansu kamar
wanda suka shiga rudani da maganar. Yayinda Kaka da Malikat Haseenat ke murmushi,
hakama Hanash da Iffah kallon juna sukai sai kuma suka saki murmushi. Jin kowa ya
kasa cewa komai Ummu da tai shiru kanta a kasa ta dago fuskarta da murmushi. Cike
da nutsuwarta ta ce, "ALLAH ya karama adalin shugabanmu lafiya da tsohon rai mai
albarka. Idan akai hakan tabbas zamu kasance a cikin farin ciki, dan an mutuntamu
da karamci mafi girma da ba'a tabama wani a wannan kasa ta ruman ba. Nima zanso
kasancewa da yar uwata kodan karta kwacemin yarinyata, why zan shiga wani hali". Ta
juya ta kama hannun Baby dana Daneen Ammarah cikin roko tace, "Dan ALLAH karku bani
kunya ku amince mu sake zama abu daya.

Karan farko Tajwar Eshaan ya saki wani dan murmushi mai ban mamaki, ji yake wata
irin kimar Ummu da darajarta ta karu a ransa. Murmushinsa ya matukar birgesu, ya
kuma sake sanyasu a farin ciki, sai dai kuma bai sake cewa komai ba.....

• MALIKAT BUSHIRAT*

Daga kotu da kyar ta iya fitowa zuwa mota, suna isa sashenta dakinta ta shige ta
kulle kanta. Jiri take ji da wani irin mahaukacin ciwon kai ga bugun zuciyarta kara
hauhawa yake. Shin mike shirin faruwa da ita ne haka, mike tunkaro rayuwarta. Danta
Eshaan, Eshaan dai data sha wahala kafin samunsa ne yake auren yar Daneen Ammarah.
Mai tambarin tawadar ALLAH a jiki, yarinyar da ke cikin lissafin ayyukansu. Mai
tambari dai irin wanda Uwa ta shardanta mata a cikin sharudanta. Mike faruwa haka?
Ta yaya hakan zai kasance? _(Ina tayaki murna da albishir din insha ALLAHU kafin mu
dawo daga hutun in amarcinmu da iznin UBANGIJI zamu dawo da jikanki a wannan babbar
garkuwar, dan haka kibar wahal da kanki akan sai Maleek ya auro wadda kike son ta
haifa miki shi dole ko nisanta shakuwar iyayensa da zata zama sanadin samar da shi
ta hanyar madara. Da ga kuma randa kika tabbatar da samuwarsa, ki fara irga
kwanakin nadamarki da dana sani har zuwa ranar haihuwarsa. Hukunci da karfin ikon
Iffah a saman naki, yanzun ne zai fara Mother in-law)_ kalaman Iffah suka shiga
mata kaikawo da amsa kuwwa a cikin kunne kamar yanzu ne take fada mata su. _(Ammie
na yarda ke Zakanya ce, sai dai ki sani duk karfin bajintarki da iya farauta a
saman kowa watarana tsufa kan ¡ya sa ki rissina jikar bayanki ta zama sarauniya
bisa karfin ikon naki, Ni bance nafi karfin kaddara ba, sai dai ki sani a tafin
hannunna kike ke da komanki....)_. Kuka ta fashe da shi, cikin karaji ta furta
"Bazai yiwu ba, bazan dauki faduwaba, wihy Uwa bazan dauka ba sai dai duk mu fadi
tare, sai dai ai mutuwar kasko mu dukanmu baki daya" wani irin kuka ya sarketa,
wasu kalaman Iffar ne suka sake shiga dawo mata…. _(Ammie wihy inada abubuwan ban
mamaki da daga labulen sirrinki sau daya kawai sai ya hana wannan idanun naki
barci.....)_ wani irin naushi ta kaina mirror din akin da sake kwala kiran sunan
uwa_(…..……To wai nikam wane buri ne kike son cimmawa mai alaka da makiyi a
tsakaninki da shi? Kin ko san da ace yasha ganyen shayin nan ko madarar nan illar
da zatama rayuwarsa sai tafi wadda zatama tawa rayuwar? Sannan ke da kanki sai kin
dawo kina kuka da dana sani. Idan ma wani ke baki wadan nan abubuwan matsayin wani
kariya washi ko gurbata tawa rayuwar to tabbas ki farka. Ki farka why tunkan guri
ya kure miki ki rasa kofofin fita a wannan masarautar.…)_ "Har abada! Har abadan
abada bazan taba faduwa kasa ba, bazan rasa komai ba a lokacin da komai ya zama
nawa ba....

"Dole ki rasa! Dole kirasa!! Dole kirasa ta-kurya!!Hahahahaha!!!!". Uwa ta fada


cikin karaji da amsa kuwwar mummunar muryarta alokacin da take bayyana. A kallo
daya zaka fahimci itama a birkice take. Dan idanun nata sun sake jajur, fuskarta ta
sake muni matuka. Da wani irin karsashin wutar bala'i Malikat Bushirat ta
fiskanceta, a yau babu wani tsoro ko shakku tare da ita balle girmamawar da ta saba
ga uwar. Gabanta taje ta tsaya tana mai nuna ta da yatsa.

"Sai dai mu rasa gaba dayanmu, amma ba Malikat Bushirat kawai ba. Miyasa kika
yaudareni?..

"Ke kika yaudari kanki, domin a yarjejeniyar mu akwai sharadin kin auren yarinyar
data fito a wannan zuri'ar musamman mai tambarin na hakika".

"Amma da umarninki ta zama matar Saiful-malik, shin bokancin naki ya fara


raunine ko dama ke din mayaudariyace kamar yanda yarinyar ta fada?!!!".

"Ki iya bakinki ta-kurya!!!".

*Bazan iyaba, nace bazan iyaba uwa. Wihy why, kinji na rantse, bazanyi asarar
wahalata ba. Sai dai ni da ke duk muyi mutuwar kasko".

"Kece da danki zakuyi mutuwar kasko, kuma dole ki bamu jinin Ajlaan madadin
sauran ayyukanmu da baki cika ba!!".

"Har abada, har gaban abada jinin Saiful-malik yafi karfinki azzalumar
mushirika. Nima da kike gani hatsabibiyar kainace uwa, dan tun kafin ke gwanace a
iyawata!!"

"Kin san da iyawar taki miya hanaki iyama kanki sai da taimakona. Butulu ke
wacece, har wacece ke nace ta-kurya? Har mi kike takama da shi? In ce dai Ajlaan ne
ko? Kuma mune muka samar miki da shi a lokacin da kike neman samuwarsa do rufe
(Wa'alaikissalam 😭ALLAH ne kadai ke badawa da hanawa a lokacin da yaso, ga kuma
wanda yaso. To ki rubuta ki ajiye mune zamu shafe babinsa da tarihinsa, kamar yanda
muka shafe na ubansa da kakansa a doron duniya.Idan kin isa, Kin cika sunanki
tsagera mu zuba!!!!"

Bat uwa ta bace a akin kamar tashin guguwa. Wani irin fashewa da kuka Malikat
Bushirat tai cikin ihu da fisgo duk abinda ya tare mata gaba ta dinga ratsawa da
kasa. Jikinta want rin jiljigar rawa yake na masifa, da ga karshe ma kawai sai ta
yanke jiki ta fadi dan jini ya balle mata sosai saboda raunikan da ta jima kanta a
dalilin fashe-fashe.….✍️

🥱 Tofa anzo wajen kenan, wannan da alama fadan


cikin gidane fa. Akwai kuma babban kulli akan
haihuwar Tajwar Eshaan ma kansa 🤔. 🚴 Bari dai mu
cigaba da bin uwa da diyarta muga yaya wasan zai
kaya ne.

DAUDAR GORA
Book2
Chapter 78

.....…..Bayan idar da sallar magrib dunbin al'ummar dake cikin masarautar ruman
suka shaida daurin auren Zayyan ibn Abbas Jumna. Da amaryarsa Ammarah bint Abdul-
majeed Aliy Qutb, akan sadaki mai darajar gaske, inda Kaka ya zama waliyyin ango,
Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ya zama waliyyin amarya. Ba mutanen
daular ruman bane kawai suka girgiza, masarautar ce gaba dayanta ta girgiza da
wanna al'amari na bazata. Duk da ana cikin dunbin jimami na abubuwan da suka faru a
kotu yau, babu wanda yay zato ko tsammanin faruwar abinda ya farun kamar haka ba. A
take sabon topic ya sake barkewa a saman wanda dama aka yini anayi har
a cikin hadimai…

**

Tun bayan sallar la'asar da suka shigo da su Kaka bata koma ba tana a sashen nasa.
Dan sanda zasu fita domin gabatar da sallar magrib har zata bisu itama Malikat
Haseenat ta dakatar da ita. Kasancewar sallar magrib da ake kira ita da shi babu
wanda yacema dan uwansa komai. Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke a bayan fitarsa
sallar, sai kuma ta shiga wanka dan a karo na farko tun bayan samuwar cikinta yau
ne take jin zazzabi a jikinta. Doguwar riga mara nauyi kawai ta saka ta tada salla,
bayan ta idar ta zauna komai na dawo mata daki-daki kamar wani shirin film. Kuka
sosai tayi fiye da wanda tayi a dazun, a haka kunnenta ya tsinkayi shelanta sake
aura auren mahaifanta guda biyu da kaddara ta hada. Kuka ta sake rushewa da shi har
kanta na mata ciwo batare da tasan dalilinsa ba. Shin farin ciki ne ko sabon
rudani, da kyar tai sallar isha'"i ta zame akan abin sallar ta kwanta.....

Tana kwance a wajen cikin yar takurewar sanyin zazzabin da take ji ya shigo
dakin da sallamar nan tasa ciki-ciki. Bata motsa ba har ya karaso gabanta, jin
tsaiwarsa a kusa da ita ya sata bude idanun a hankali ta sauke kansa. Kallon juna
suke kamar yau suka fara ganin kansu, kafin itama ta fara janye nata idanun ta mike
a hankali. Ganin yanda take dan layi na wandda jiri ke kwasa ya sashi mika mata
lallausan farin hannunsa sol mai dauke da dogayen farata. Nata ta daura a hankali
cikin nasa, ya dagata gaba dayanta ta mike tsaye a gabansa. Yanda yake binta da
kallo kamar sabuwar halitta ya sake raunana mata zuciya, sai kawai ta sakar masa
wani shagwabebben kuka da fadawa jikinsa ta kankamesa. Bashi da zabin da ya wuce
amsarta hannu biyu shima ya kara matseta a jikin nasa yana mai lumshe idanunsa dake
cike da so da kaunarta. Kuka take sosai dake sake sukar zuciyarsa, sai dai baice
mata uffan ba har kusan tsahon mintuna uku suna tsayen. Sai da yaji ya daina jin
dumin hawayenta dake sauka masa a kan kirji ta koma sauke ajiyar zuciya sannan ya
dagota. Mayafin da tai rolling ya warware, yaja hanunta a hankali ya zauna a bakin
gado ita kuma ya daurata a saman cinyarsa.

"Shi kukan baya isa ne".

Ya fada a fisge fuskarta a cikin tafukan hannunsa. Fuskar ta sake kwabewa zata
saki wani sabon kukan ya girgiza mata kai da fadin, "Please bana son gani kuma, kin
cika shagwaba fa". Shaaa hawayen suka zubo dan ta kasa rikesu, sai kuma ta turo
masa baki gaba. Murmushi yayi a zuciyarsa, tare da matso fuskarta dab da tashi ya
tura yatsunsa cikin gashin kanta ya zare ribbon din data dauke gashin a tsakkiya ya
shiga yamutsa mata shi yana goga mata hancinsa kan nata, lips din ta sake dan
turowa, shiko ya samu damar hadesa da nashi kirif. Iya kokari yayi na ganin ya
tsaya iya hakan, sai dai zuciyarsa gaba daya taki bashi hadin kai. Sai kawai ya
zarce da abinda gangar jikinsa ke tsananin bukata da kwadayi, da ga haka labarin ya
canja da salo mai matukar nauyi dake kara tabbatar musu yanda suka narke a so da
kaunar juna mai tsananin gaske.

Dakin yay shiru sai fitar sanyin na'ura tana lafe a jikinsa cikin muryarta da ta
disashe take fadin, "Komai kamar a mafarki ko? Ji nake kamar idan na farka zanga ba
haka bane ba Maleek. Har yanzu gaba dayan zuciyata taki yarda da komai dari bisa
dari".

Murmushi yayi mai sanyi da sake gyara mata kwanciya a jikin nasa, hannunsa kam na'a
kan cikinta. Lumsassun idanunsa ya bude a kan kyakykyawar fuskarta da hatta dan
kumbura saboda kukan da ta sha a yinin yau. Motsa lips dinsa yay a hankali ya furta
"Rayuwar ma gaba dayanta tamkar mafarkice Niger. Yanda muke kwantawa mu tashi da
wucewar gobenmu haka kwanakin kaddarar rayuwarmu ke shudewa da abubuwan da suka
gabacemu. A duk abinda kikaga ya far a yau tabbataccene da tabbatar rubutun
alkalamin kaddara. Wata hikimace kuma da ga hikimomin UBANGIJI. a randa na fara
hacuwa dake komai ya cigaba da maimaitamn kansa tamkar mafarkina. Da ga cikin duk
abinda ya faru har kina tunanin akwai abinda zai iya gagara da ga tarkar UBANGIJI?

"Murmushi ta danyi mai sanyi a karo na farko tare da dagowa tana kallon
kyakykyawar fuskarsa. "UBANGIJI gagara misalin masu misali ne ai, duk abinda ya
zartar haka yake babu kokwanto ko shamaki a cikinsa. Kai dabanne a cikin daban
MIJINA RAYUWATA" tai maganar da dan ja masa hanci. Murmushi yayi mai Kayatarwa da
dungure mata kai. Ya ce, "Ai kin fini zama daban. Mai mama biyu, yayu biyu, kakanni
biyu, gida biyu, kefa hatta duniyarki biyu ce My sohaa".

Dariya ta kyalkyale da shi kamar ba yanzu ta gama rusar kuka ba. Ta kankamesa da
fadin, "Idan na hada da taka duniyar ma uku garan FARIN CIKINA".

"Oh oh, yarinyar nan fa naga alamar kin fetsare". Yay maganar yana dagota. Gashin
da ke a gemunsa ta kamo da yatsunta tana wasa da shi, cikin shagwabe fuska ta ce,
"To ai duk karatunka ne, su Ummu ma shaidane ba haka suka baka ni ba, ni da ko
kallon mutane bana iyayi cikin ido..."

"K din dai dana sani?".

Ya fada cikin katseta da dan waro idanunsa waje. Fari ta masa tana murmushi cikin
dage gira sama da fadin, "Kaima ai shaidane, saliha dani aka kawo maka ga hakuri ga
shiru-shiru"., Mizai yi inba dariya ba, sai da yay mai isarsa tana kallonsa cike da
jin dadi sannan ya dungure mata kai. "Wai ke din nan ce mai shiru-shiru, bayan
randa na fara ganinki da rashin kunyarki nai karin kummalo. Lallai an cuci masu
shiru-shiru kuwa indai aka sakaku. Ke Fitinanniyar nan. Ranar fa harda fadin wai ko
Shahan-shan ne sai kin sashi ya tsaya dole. Kai yarinyar nan ke abar toro ce".

Dariya ta kyakykyale da shi, sai kuma ta shiga boye fuskarta dan sai yanzu
abinda tai din yake bata kunaya ma. Kanta a boyen ta ce, "Wai dan ALLAH ranar
bakaji kamar kasa a tsireni ba?".

"Ke dai kika tsiremun zuciya ban shirya ba. Danni kadai nasan dauriyar da nayi
ban fallasa abinda ke a raina ba tun a wajen".

Dariyarta mai tada masa tsigar jiki tayi da fadin, "Nima fa kadan birgeni a
ranar, dan kamshinka ya tafi dani matuka da wadan nan fararen idanun masu kyalli
kamar madara. Kawai dai ranar haushin kowa nakeji ne sai na samu na sauke akan
yaranka. Wai kuwa suna ina ma?".

Murmushi kawai yayi baice komai ba, sai da ya mula da kansa sannan ya magantu.
"Uhm ashe nayi babban kamu tun a ranar faro amma aka tsiwaceni tas. Ke ta dabbance
yar kanwata. Su Azaan suna nan abinsu, ma'aikata ne a gidan jaridata ta AFRICAN
EYE. Inda kika so zuwa ki tone mun asiri da min zigidir a bainar nasi ALLAH ya
taimakeni".

"Shine ka tareni ko? Ashe dai kanajin tsorona?".

"Kai sosai ma kuwa. Mra Eshaan ko bakin nan naki da baya gajiya da magana ai yasa
aji tsoronki."

Harara ta dan masa tana tura bakin, sai kuma kamar wadda aka tunatar ta ce, "Wai
dama dan ALLAH gidan jaridar Africa eye naka ne?".

Kai ya gyada mata idanunsa a lumshe ya ce, "Shine burina na farko dana cika bayan
kammala karatuna".

"Uhm Masha ALLAH, shiyyasa akema manyan duniya tone-tone ba ragi babu ragowa kuma
komai
bai faru ba. Amma gaskiya kayi kokari. Nima wannan
shine burina"

"Ki dauka kin cikashi insha ALLAHU My Sohaa, Kina haifomin babyna makaranta zaki
koma, insha ALLAHU arena bazai tauye miki cikar duka burikanki ba. Zan tsaya miki
da tsayawar UBANGIJI har sai kin cika duk burin da ALLAH ya rubuto a cikin kaddarar
rayuwarki na alkairi".

Wani irin rungumesa tai da fashewa da kuka. Hannu biyu ya amsheta yana murmushi.
Gain kukan na gaske ne aka sauya masa salon lallashi kamar ba yanzu aka fito a
komar ba. Da alama dai Iffah'r mu ta haddace karatun gwarzon nata har sun zama dai-
dai,🚴

Hankalin Jasrah ba karamin tashi yay ba da yanayin data samu yar uwarta.
Rasama abinda ya dace tayi tai, a rikice tai kiran number likitan Malikat Bushirat
din. Cikin kankanin lokaci kuwa sai gashi. Shima hankalinsa ya tashi, dan shi
abinda ma zuciyarsa ke raya masa da ban da wanda ke a hakika. Zai zauna bin ba'asi
Jasrah ta katsesa da fadin, "Yanzu ba lokacin sanin miya faru bane. Ceto rayuwarta
shine mafita first".

"Hakane"

Ya fada cikin gamsuwa. Da taimakonsa suka maidata saman gado, babu bata lokaci
ya shiga aikinsa, ya samu nasarar tsaida jinin, tare da ceto numfashinta da tuni
yabar gangar jikinta. A tare suka saki ajiyar zuciya bayan daidaiton komai. Jasrah
ta dubesa cikin roko ta ce, "Doctor Please wanna al'amarin ya tsaya da ga ni sai
kai dan ALLAH. Dan yana da kyau mu fara sanin abinda ya faru da ga bakinta karmu
tashi hankalin mutane. Musamman ma Shahan-shan abubuwan zasu masa yawa. Ga wanna
rikicin da yake ciki ga kuma wannan. Shima mutum ne kamar kowa yana bukatar
sassauci".

"Gaskiya ne ranki ya dade. Insha ALLAHU baki da matsala. Dan aikina ne wannan.
Ki dai kasance a kusa da ita dan zata iya farkawa a firgice kasancewar daga suma
muka maidata barci, Sannan gaskiya ya kamata kusan abinda ke damunta Kinga wanna fa
shine karo na biyu, zata iya samun matsala idan haka ya cigaba da faruwa. Dan yanzu
haka da kyar na samu bugun zuciyarta ya daidaita, ga jininta ya hau matuka sai tana
samun kulawa lafiyarta zai samu daidaiton da muke bukata".

"Insha ALLAHU Doctor za'a kiyaye".

"ALLAH ya tabbatar, zuwa safiya zan kawo magunguna ko kuma zuwa anjima kadan"

"Okay inaga ka kawo anjima din zai fi".

"Shike nan bara naje sai na dawo"….✍️

5:21 m
DAUDAR GORA
Book2
79

…..Bayan wucewar Doctor jagwaf Jasrah takai zaune idonta akan yar uwar tata.
Abubuwane da yawa ke mata kaikawo, ga dunbin mamakinta da al'ajabin wai mike faruwa
haka? Ko ita dake a cikin halin tashin hankalin hallayar mijinta batajin tana a
rabin wannan yanayin. Amma ita da bata nema komai na rayuwa ta rasa ba tarasa mike
faruwa da ita. A kwanakin nan fa har rama tayi, sannan zaka ganta jigum kamar mai
tunani duk ta hargitse. Gaskiya ta fara ji a ranta lamarin ya fara zarce na
kiyayyar Iffah kawai. Akwai dai abinda take boye musu da ya kamata ace sun sani,
dan al'amarin ma kamar gaba- gaba yake. Jiba dai yanda ta hargitsa dakin yau gaba
daya, ta fasa abubuwa masu daraja da tasan ko sanda suna yara bata bari su taba
mata. Tashi tai da kanta ta gyara komai, dan kiran wata hadima ta gyara kamar yana
nufin fitar zancen ne, dan hadimai da yawa dake akowane sashe zaka samu an leken
asirin wasu ne. Musamman ma ita da girman ikonta yasa kowa kunnensa bude yake da
son jin labarin wani al'amari ya bullo da ga gareta makamancin haka. Tana cikin
gyarawar doctor ya kirata ya dawo, ajiye aikin tai taje ta amso magungunan ta daw
sannan ta karasa gyara komai ya koma need.

Gabannin asuba ta farka a wani irin firgicen da yafi wanda ma Doctor ya ce zata
iya tsintar kanta a ciki. Yanda jikinta ke rawa haka gadon ke rawa, ta fasa wata
irin gigitacciyar kara ganin halittun da suka firgitata a cikin barcinta zahiri
muraran a cikin dakin. Gaba daya sunma gadon zobe ga wani kalar kuka da sukeyi mara
dadin saurare a cikin kunne., Sotake ta ambaci sunan ALLAH koda sau daya ne amma
bakinta ya gagara furtawa, sai rawar da lips dinta keyi kamar yanda jikin nata ke
rawa. Duk da sanyin ac dake dakin ita a jike take sharkaf da zufa kai kace wanka
tayi.

"Hahahaha!!!!"

Uwa ta bayyana cikin mummunar dariyarta. Kamar koda yaushe a kan kujerar tata
take cikin jajayen kayan nan. Mummunar fuskarta ta tsufa ta sake munancewa tsabar
itama bata a cikin hayyacinta.Dariyar ta sake kyakyalewa da shi da fadin, "Kikace
zaki ¡ya hahaha! Dama na fada miki ke karamar mara kunyace Bushirat, k! Karamar
tsagerace!! Hahaha!!!!! Daga yanzu zuwa ranar cikar burina saina dandana miki
azaba, kisa a ranki yanzune wasan zai fara na gaskiya. Kuma dole ne ki biya diyyar
da jinin dan da mune mukai sanadin samuwarki garesa (Wa'iyazubillah🙏) da ga karshe
zan tona miki asiri ta yanda jama'arki su zasu idasamin rayuwarki karamar yar iska
kawai butulu. Hahahaha!!! Kuje gareta, ku sauyamun kamaninta". Ta fada cikin bada
umarni ga munanan halittun nan ita kuma tana bacewa. Wata irin zabura sukai kanta,
hakan yay dai-dai da bude kofar da Jasrah tayi a rikice, dan ta farka saboda kiran
sallar asuba kawai ta dinga jin kamar dokuna na sukuwa a cikin masarautar, shine ta
fito a zabure, amma maimakon jin da take duka masarautar ne sai taji kamar a dakin
Malikat Bushirat din ne kawai, shine ta nufo nan a rikice. A take duk suka bace
batare da taga komai ba, sai Malikat Bushirat da gaba daya ta gama fita a
hayyacinta. Sallallami ta dauka tare da haurawa gadon a rikice, bata kawo komai a
ranta ba face maganar doctor da yace dama zata iya farkawa a rude, ita kuma ta koma
daki ne dan taji yace zata iya kaiwa ma safiyar gobe bata farkaba saboda nauyin
allurar da yay mata.

Rikota tai ta rungume a jikinta hawaye na ciko mata idanu na tausayin yar uwar
tata. Zuciyarta ta fara bata kodai asiri akai mata ne wai....

**..

Itama a gabanin asubar ta farka a razanen da ta saba a duk sanda tai mafarki mai
nauyi irin haka. Ta dafe kanta dake sara mata tana mai karanto addu'a. Taja kusan
minti biyar a haka kafin nutsuwa ta dan dawo jikinta. Hannunta ta janye da ga saman
kanta tare da kai dubanta ga Tajwar Eshaan da ke getenta yana barcinsa hankali
kwance. Fuskarsa ta tsurama ido kamar mai son karanto komai data gani a cikin
mafarkinta kan fuskar. Ta jima batai mafarki mai sakata a rudani irin wannan ba.
Itakam wadan nan abubuwa sun fara damunta, Shikenan da ga wannan sai wannan kullum
babu hutu, da anyi maganin wannan sai was su sake ballowa wace irin rayuwace
wannan. "Ya rabba ka kawo mana iyakar wadan nan
musibu". Ta fada a hankali tana sauke ajiyar zuciya. Yunkurawa tai zata sauka a
gadon taji an rikota. Juyowa tai ta dubesa dan sam batai tunanin ya farka ba.
Maidota yay ta hawo saman jikinsa, cikin yanayin muryar wanda ya tashi a barci ya
kai hannu saman wuyanta da fadin,"Zazzabin ne?".

Kai ta girgiza masa a hankali. Cikin yar damuwar mafarkinta da bai gama sakinta
ba ta ce, "A'a na farka ne kawai asubama yay". Ajiyar zuciya kawai ya dan sauke
batare da ya sake cewa komai ba. Itama sai ta sake yunkurawa ta mike....

Tana idar da sallar asuba ta fito a dan harzance, dan so take taje ta dawo
kafin ya dawo da ga massalaci. Sashen Malikat Bushirat ta nufa a yanayin badda
kamar data fito. Kasancewar da dan sauran duhun asuba duk da ko'ina zagaye yake da
haske babu wanda ya fahimci wanene a cikin tsirarun hadiman da suka fara ayyukansu.
Koda ta shiga sashen ma tsirarune a hadiman suka fito fara shara. Cikin dabara ta
dinga wucesu batare data yarda kowa ya ganta ba. Koda ta iso kofar dakin da
zuciyarta yafi karkata da samunta sal data dan nutsu a kofar domin tabbatar da babu
motsin komai sannan ta murda handle din a hankali ta shiga. A hankali ta sauke
ajiyar zuciya tana bin dakin da kallo, babu kowa a ciki sai Malikat Bushirat din da
ke zaune jingine da gado tana sallah a haka. Da alama bazata iya yi a tsaye ba. Key
ta murzama kofar sannan ta karasa shigowa cikin dakin, dai-dai da ta idar. A dan
yatsine Iffah ke mata kallon mamakin gain yanda tai wani irin zuru-zuru, duk rashin
gane abubuwan mutum idan ya kalleta yasan akwai matsala a tattare da ita....

"Miya kawoki nan?".

Ta fada muryarta a shake sai dai cikin bacin rai. Baki Iffah ta labe itarna cikin
tunzura ta bata amsa. "Kin san abinda ya kawo ni ai. Wai ke dan ALLAH bazaki dawo
cikin hayyacinki ba. Inata nuna miki hanya, inata miki kanta farga amma kin kasa
fahimta saboda son zuciya ya toshe tunaninki. Wai shin dole ne sai kin saka rayukan
masoyanki cikin kunci da bakin ciki ne. Wlhy ki fadama bokanyarki ta fita a
hanyata, danni nafi karfin ta da izinin UBANGIJI, hakama shi wanda kuke fadan a
kansa yanzu duk da dank ne. Ta shiga hankalinta ta tsaya a iya kanki ke da kika
gayyaceta a rayuwarki. Why duk randa ta sake gigin zuwa sashenmu sai kunyi nadama
da ga ke har ita. Ni babu abinda ya shafeni da abinda zata miki matsalarkice
wannan, tunda na nuna miki qujema irin wanna ranar tun kan tazo amma kika nun ban
kai ba. Idan kuma ta cika cikakkiya dan ALLAH ta zo gareni a zahiri taga ikon
ALLAH, wlhy sai na sauya mata kamannin halitta da tambarin da harta mutu bazai gogu
a jikinta ba".

Tana gama fada ta juya tal tafiyarta fuuuu ta fice tana bugo kofar. Da kallo
kawai Malikat Bushirat ta iya binta, zuciyarta na.raya mata anya kuwa (wannan
yarinyar mutum ce? Koma dai wanda aka kira uban nata bashi bane Aljanun Ammarah din
ne suka mata cikinta).…... Fitowar Jasrah da ga bayi ya katse mata zancen zucin.
Sai kuma yanda Jasrahn ke mata kallon tuhuma da rudani ya sata shan jinin jikinta,
ita sai yanzu ne ma hankalinta ya dawo jikinta. Duk da abinda yarinyar nan ta fada
kenan Jasrahn ta jisu tunda tana a cikin bathroom...

"Akia!".

Jasrah ta katse mata tunanin. Dan firgigit tai ta dubeta. Sai dai ta kasa amsa
mata. Babu alamar wasa tattare da Jasrahn ta sake fadin, "Akia kamarfa maganar
Zawjata-almilk naji, shin wane maganganu take fada miki haka masu rudarwa? Mike
faruwa ne?".

Dauke idanunta tai da ga kan Jasrahn zuciyarta na wani irin gudu a kirjinta......

"Hakan na nufin hasashena nakan gaskiya kenan,Akia akwai abinda kike boye mana
tsakaninki da yarinyar nan? Taya kamarki da ke matsayin mahaifiyar mijinta,
shugabanta amma tazo tana datsa miki irin mijinta, shugabanta amma tazo tana datsa
miki irin wadan nan maganganun cikin kaushin harshe amma ko tari bakiyi ba. Anya
kuwa Akia.....

"Jasrah!!"

Ta fada a zafafe cikin dakatar da ita, muryarta adan kausashe da bata fita.
Shiru Jasrahn tayi sai dai ta kasa dauke idanunta da ga kanta. Babu abinda ke mata
kai da kawo a zuciya sai kausasan kalaman Iffah masu nuni da akwai wata jikakkiya a
kasa tsakaninsu. Sannan kalmar bokanyar nan ya matukar tsaya mata a kahon zuciya ya
kasa fadawa...

**.

Koda ta koma ta iske ya dawo sai dai ya wuce Gym.Ajiyar zuciya ta dan sauke ta
canja kayan jikinta ta nufi kitchen. Yau ma da kanta ta hada masa abincin breakfast
din, suko masu girkin duk sun tsargu duk da tare da su take yi. Sai dai aikinsu
kawai bani kaza yankamin kaza wanke mun kaza. Amma komai ita da kanta ta hada
abunta. Ta kuma tsaya a kansu har sai da aka kawo komai dining room din.

Ya fito da ga wanka kenan ta shigo da sallama hanunta dauke da tray mai dauke
da kofin shayi da keta faman turiri. Ido ya dan tsira mata har ta iso gabansa ta
ajiye. "Good morning ". Ta fada tana zuba zuma kadan a shayin. Cikin dan lumshe ido
da budewa ya amsa mata da "How Are you".

"Alhamdullah".

Ta amsa masa itama tana mika masa kofin shayin.Amsa yay dan dama shi yake jira. ya
ce, "Thanks". Kai kawai ta dan jinjina masa tana murmushi. Da ga haka ta wuce
bathroom dan yin wanka. Kallo ya bita da shi kasa-kasa zuciyarsa na masa kaikawo.

Lokacin da take fitowa har ya kammala shiryawa,dan haka ya taimaka mata itama ta
shirya cike da tattali da kulawa. A tare suka fito cin abincin gwanin sha'awa. Duk
abinda take kallonta kawai yake cike da so da kauna harta kammala hada musu komai.
Bismillah ta masa tana masa nuni da abincin da ido ya make kafadarsa yana kauda kai
gefe. Hannu ta kai ta dan ja masa kunne tana murmushi, sai hakan yay dai- dai da
fitowar amintaccensa da basu san da shi ba da ga cikin karamin falonsa ya gyaro. Da
wani masifar sauri ya juya har yana cin ban tuntube dan idonsa ras akan hanun Iffah
da ta ja kunnen Shahan-shan din nasu. Itama idanu ta waro da sauri ta mike da sauri
ta rungumesa. Dan harga ALLAH bata san bayan su akwai wani a wajen ba. Da kyar ya
danne dariyar dake taso masa ya danna mata mintsini a gefen ciki shima, tako zabura
gaba dayanta ta haye saman cinyarsa……✍️

DAUDAR GORA
Book2
80

……..• KOTU * Yau din ma kotun ta cika sosai,harma wanda basu halarta a jiya ba yau
kam sunzo, Sai dai babu Malikat Bushirat. Dan tana can wani irin zazzabi mai
masifar zafi da ciwon kai sun lullubeta har sai da Jasrah ta sake kiran likita ya
dubata. Ta gama shirya ana gama zaman kotun nan gida zataje, dan ita kam har yanzu
a cikin rudani take. Zataje ta sanar da babban yayansu da a yanzu shine kamar uba a
wajensu komai tunda ita taki fada mata. Maybe su sai suzo su binciki wane irin
TAKUN SAKA ne tsakaninta da surukar tata da har irin wadan nan maganganu ke shiga
tsakaninsu. Yanke wannan hukuncin ya sata nufo kotun kamar yanda kowa ya hallara.
Iffah tare da su Daneen Ammarah da su Ummu yau ta shigo. Dan suna kammala breakfast
sashen Malikat Bushirat taje ta gaishesu kasancewar lyyani da Ummu a can suka
kwana. Barrister Abdallah Aas da Abu Zainab kuwa tun a jiyan suka wuce gidajensu da
iyalansu. Kaka ma kin kwana yay, sai suka wuce gida shi da Babiy da Hanash akan yau
sa dawo. Ya kumayi hakane dan yana so suje su tattauna inda za'a nemawa Daneen
Ammarah (Mammy) wajen zama itama. Saboda Tajwar Eshaan ya sanar musu ana yanke
hukuncin nan zuwa jibi insha ALLAHU Mammyn (Daneen Ammarah) zata tare gidanta.

Shine karshen shigowa. A take kotun ta sake nustuwa kayin kowa a kasa har sai da
ya kai zaune.Kamar ko yaushe Sayeed Hanifud-Din ya fito hannunsa rike da takardu.
Bayan yay gaisuwar girmamawa da Shahan-shan aka fara gabatar da Shariar.

"Bayan jiya kotu ta gama sauraren bayani da ga bakin Arshaan wata shari'ar mai
alaka da juna ta sake shigowa a cikin zaman. Inda muka saurari babban al'ararin da
ya rikita kowa har sai da aka yanke wannan zama da alkawarin yau za'a kawo karshen
komai. To Alhamdullah domin tabbatar da abinda muka ji a bakin Arshaan. Da wanda
muka ji a bakin dattijon nan gamu yau rike da hujjoji. Hujja ta farko zamu saurari
recording din da aka shirya saurara a tun farkon shari'ar ta jiya hakan bai faru
ba. To a yanzu zamu ji domin sake tabbatarwa. Sannan zamu gabatar da hadiman da
sukai aikin kisan gilla ga Sayeed Khairul-Bashar bisa sawar su Jasim, da kuma
bokansu mai suna Barbushi dorin jin karin bayani da ga garesu. Hakama bayanan wanna
dattijo duk da a jiya Daneen Ammarah ta tabbatar mana da abinda mukaji itama wanna
kotu mai adalci ta saka anvi gwaje-gwaje da zasu sake tabbatar mana da komai.,
Shugaban jami'ai bismillah"

Bayan shugaban jami' ai yay gaisuwa ga Shahan- shan shima ya cika umarnin kotu na
saka recording din da aka nada a zaman su Miran Jasim cikin kurkuku batare da sun
sani ba. Kotu tai tsit kowa na sauraren kasancewar an saka speaker mai karfi a
kowacce kusurwa kowa radam yake ji. Rikicin Miran Jasim da Miran Arshaan tun da ga
ranar farkon kasancewar tare a cikin kurkuku daki-daki suna fallashe kansu da zagin
juna da tsinema juna har zuwa jiya da safe. Tiryan-tiryan sai ga abinda Arshaan ya
fada na fitowa harma da wanda bai fada ba. Jikin kowa da ke kotun duk sai ya kara
sanyi. Yayinda aketa la'antarsu da ALLAH wadi da mummunar hallayar tasu duk da fa
suma yan zaman kotun akwai masu wasu boyayyun al'amuran a cikinsu suma. Sai dai
tunda tasu bata fitoba mai sauki ce. An fito da boka Barbushi shima da tunda aka
kawosa masarautar aka rabashi da duk kayan tsafinsa aka aske masa kai da basa kaya
bayan an sashi wanka. Gaba daya sai kamanin nasa suka canja kamar bashi ba. Sai
faman sinne kai yake kuwa da satar kallon su Miran Jasim kamar yanda suma suke masa
kallon mamaki. Shima yay gaisuwa ga Shahan-shan sannan Sayeed Hanifud-Din ya fara
jefa masa tambayoyi.

"Kane mushirikin da ke basu tsubbun da zasu cutar


da mutane ko?".

"Ina neman afuwa kuskurene ranka ya dade".

"Tun yaushe kake tare da su?".

"Mun kai shekara goma sha takwas".

"Kace ka dade kana basu lakanin kashe mutane da


musu illa?"

Shiru ya kasa cewa komai,

Sayeed Hanifud-Din ya cigaba da fadin, "Kotu na bukatar jin duk tsiyatakun daka
jagorancesu aikatawa".

Cikin rawar murya data baki ya shiga zayyane komai. Da ga karshe ya dora da
fadin, "Naki fada musu gaskiya ne tun farko saboda karsu daina bani kudin da suke
bani. Amma ni nasan anfi karfinsu a duk inda suke kai hari. Bakuma zasu samu cikar
burinsu ba har abada".

Ba wanda suke a kotun ba hatta Miran Jasim da Miran Arshaan wan irin kallo suke
masa mai ban mamaki, sai dai ko sau daya yaki yarda ya dubesu shikam, Bayan shi an
fiddo hadiman da suka kashe Sayeed Khairul-Bashar. Inda suka zayyane komai har
yanda Miran Jasim ya sakasu aikin, da yanda suka sacesa lokacin da yake fitowa da
ga sashensa zaije sallar asuba. Sun azabtar da shi matuka, dan azabtarwarce ma ta
kaisa ga rasa rayuwarsa. Sosai wasu ke kuka, iyalansa kam su kadai suka san irin
zafin da sukeji a zukatansu. Babu abu mafi ciwo sai gain amintaccen hadiminsa a
cikin wadanda suka halakashi.

Sayeed Hanifud-Din ya ja numfashi da fesarwa yana mai sake fuskantar kotu. "To
Alhamdullah wanna kenan. Sai kuma gwajin kwayoyin halittar da wanna kotu ta bada
akai mata tsakanin Zawjata-almilk da mahaifanta guda uku, inda gwajin ya tabbatar
da Zayyan ibn Abbas da Ammarah bint Abdul-majeed Ally Qutb matsayin mahaifanta na
gaskiya. Wadan nan sune gwaje-gwajen, gashi za'a jaranto.", tiryan-tiryan ya
karanto komai, a take matasan nan da Iffah yanzu ta jawo jikinta suka cika kotun da
kabbara. Da kyar aka tsawatar suka lafa.Miran Jasim kam sai kawai yaji ya fashe da
kuka tsabar yanda zuciyarsa tai wani irin kunci da takurewa waje daya a kirjinsa,
Bayan shirun da kotun ta dauka kowa ya zuba ido da baza kunne na jiran yanke
hukunci ga Shahan- shan da kuma makarrabansa da ke zaune yau a kusa da shi domin
yanke hukuncin. Yaja tsahon mintuna hudu shiru kafin yaja numfashi mai sanyi, cike
da nutsuwar nan tasa da kamewa ya motsa tausasan lips dinsa idanunsa kyam akan
Iffah ta cikin bakin gilashin daya sakaya su. Tana kwance ne a jikin kafadar
Malikat Haseenat idanunta a lumshe da alamar har yanzu batajin dadin. Janyewa yay a
hankali ya maida ga takardun gabansa ya sake motsa lips dinsa.

"A bisa hujjoji da kwararan shaidu da ji da ga bakin masu laifin wannan kotu mai
adalci tayi dubi da nauyin laifukansu da hukunce-hukuncensu masu nauyi daya dace ta
musu. Domin saukaka wahalarwa ga kotun ta yankema Miran Jasim da Miran Arshaan
hukunci ta hanyar rataya a tsakkiyar al'ummar wanna kasa a dunkule bisa
laifukansu.....

A take kotun ta dauki kabbara cikin motsuwar zukata da tsananin rudani musamman
ga Miran Jasim da Miran Arshaan da sukai wata irin zabura. Da kyar aka samu aka
lafa ya cigaba da fadin. "Za'a yanke musu hukuncinne a ranar bikin al'ada dake hada
kowa da kowa da za'a iya bukata da fatan su shaida Kafin hakan zasu cigaba da zama
a cikin kurkuku, zakuma su bayyana dukkan laifukansu a gaban yan jarida. Bama
bukatar wata kungiya a duniya wajen mana katsalandan akan hakan, zakuma su biya
diyyar ran yarinyar Sayeed Hifzur-rahaman da ta Sayeed Khairul-Bashar ga iyalansa.
Hakama zasu biya kudade masu nauyi ga ahalin Fhareedah bint Zayyan da suka wahalar
bisa son zuciya. Bokansu an bashi damar zaman kurkuku na daurin rai da rai idan
yana da rabon shiriya ALLAH ya shiryar da shi. Hakama hadiman da sukai musu
ayyukansu an yanke musu hukuncin daurin rai da rai suma. Wannan kotu ta sallami
wanda ya samar musu da dafin macizai abisa gargadin kiyayewa. Idan ya sake sakaci
makamancin wanda yay zai yabama aya zakinta. Haifah za'ai mata hukuncin bulalar
aikata Zina tare da zaman kurkuku na shekara goma bisa yunkurinta da hadin bakin
son yin kisa. ALLAH yasa mufi karfin zukatanmu, ya yafe mana kurakuranmu mu da
zuri'armu da al'ummar mu baki daya". Da ga haka ya mike. Babu wanda ya iya motsawa
har sai da ya fice. Kotun tai wani irin harmutsewa kowa na ALLAH wadai da halayyar
su Miran Jasim da kuna da tashin hankalin karshen su Miran Jasim da kuna da tashin
hankalin karshen su yama hanasu iya duban kowa. Arshaan sarkin rudiya ma kuka
yakeyi, dan yayi nadamar biyema Jasim a rayuwarsa duk da shima da nasa kudirin.
Amma bai taba samun kwarin gwiwar aikatawa ba sai da suka dunkule. Haka aka wuce da
su da kyar da ga cikin kotun aka maidasu kurkukun...

Gaba daya Iffah bawani son hayaniyar take ba yau, dan batajin dadi gaba daya saboda
gumurzu sosai tasha da uwa a cikin mafarkinta na daren jiya. Ga yanayin da take
ciki na laulayi duk da bata jin wani ciwo kafin jiya da rana. Ta riga su Malikat
Haseenat baro kotun ma ita, kai tsaye kuma sashenta ta nufa dan kwanciya kawai take
bukata da kadaici, Hannu kawai ta iya dagama hadimanta, kafin a takaice ta shige ta
bada umarnin a kawo mata dafaffen madara. Cikin sauri kuwa Amintacciyar hadimarta
ta amsa. Ita kuma ta shige cikin takun nan nata sai dai yau tattare yake da kasala.

Da sallama ta shigo dakin da ya sha gyara sai tashin kamshi masu dadi yake. Ta
maida kofar ta rufe. Juyowar da zatai gaba dayanta idanunta suka sauka akan Uwa da
ke zaune zama irin na izza da kasaita cikin kujerar ta ta gado ko nace ta tsafi
tana wani irin cika da batsewa katon hancin nan nata ya sake budewa….✍️

DAUDAR GORA
Book2
81

...._..Wani irin wawan tsaki Iffah taja mai masifar karfi ta dauke kanta. Babu
alamar ko dar tattare da ita ta cigaba da shigowa cikin dakin, kai tsaye gaban
mirror din ta ta nufa, dai-dai tana cire bangles din hannunta batare data sake
duban inda Uwa ke zaune a harzuke ba ta furta, "A haduwa daya kawai harkin tsorata
kin bayyana kanki karamar agwagwa mai wanka da ruwan dagwalon gulbin wasu. Ai
nazata karfin ikon naki zaisa ki cigaba da kawomin harin a cikin barci?".

"Idan tunaninki ke kin iya to da sauranki". Uwa ta fada cikin tsananin kaushin
murya mai fita da dacin da ke har a kasan ranta. Wata yar dariyar rainin hankali
Iffah tai tare da juyowa, ta dan jingina da mirror hannayenta harde a kirjinta.
gaba da idanunta sun canja kamanni mai firgitarwa. Sama da kasa take kallon uwa da
itama nata idanun ke jazur kamar garwashin wuta."Tsohuwa iyawa ba yawan shekaru
bane ko kwarewa a mishirikanci. Karkiyi wasa da wannan dagwalon tabon dan shi
zameki zaiyi ya kaiki kasa wanwar. Da ace iyawar taki ta cika iyawa, da kin iya a
gabar da Iffah bata san komai ba sai UBANGIJIN da ya halliceta. Indai har wannan
jinjirar yar kwanaki uku da haihuwa zata bacema ganinki da jinki, basirarki ta
toshe a gabar da kike gab da isa ga nasararki ki sake dawo da ita a inda karfin
ikonta ke a saman naki to ki sake tabbatar da k ba komai bace face batacciya mai
jahilin tunani. Ni wlhy da ga lokacin dana san kana gaba daya sai kika kara komawa
kasa wanwar a karkashin kasan tsinin takalmana. Ashema ke karamar kwaruwa ce tunda
har sai kin jinginu jikin raunin wasu a fagen cimma burinki. Ashe ke ba komai bace
face makaskanciya da dan yanzu UBANGIJI yace mutu dole ki amsa kira a shafe babinki
kamar yanda aka shafe na uwar data haifeki harta nuna miki wanna hanyar shiga
wutar. To wai ni banda ke din jahilar dabba ce a cikin kaskantattun dabbobi a
wannan shekarun naki kike tunanin mulkar kasa irin ruman wai harma da duniya. Oh oh
lallai kin cika babbar aladiya wih...

"K! Karamar halittar da muka samar da samarwarmu!!…

"K! Babbar dakikiyar da ALLAH ya halitta domin zama makamashin wutar jahannama in
har bata tuba ba!!!!'". Iffah ta katseta a tsananin tsawacen da har sai da ta
zabura acikin kujerar tsafin nata. Cikin rufewar ido da nunata da dan yatsa ta
cigaba da fadin "La'ananniya gatalalliya butulu. K! Har wacece da kika isa samar da
koda halittar kwarkwata tsinanniya mai kwana da tashi da tsinuwar UBANGIJI tattare
da ita.Why wihy ina miki gargadi na karshe, da ga yau idan
kafarki ko wanna kujerar tsafin naki ta sake rabar inda nake sai na sabauta miki
rayuwa. Sai na miki kisan gilla irin wanda ya kamata ama mushirikai batattu irinki
a doron kasa". Ta wani irin rarumi wani dunkulallen abun fulawa na tangaran irin
mai tsananin kaurin nan bakinta da bismillah ta wulwula sai gashi ya tarwatse a
saman fuskar Uwa. Yanda kasan ta jefa wuka mai kaifin masifa ko mayen karfe sai ga
hancin uwa a kasa ya gundulo gaba daya namansa. Dama gashi katon gaske mara fasali.
Wata irin gigitacciyar kara uwa ta fasa jikinta ya hau kakkarwa ta dafe fuskar da
tai faca-faca da jini da duka hannayenta biyu. Wani Iffah ta sake rarumowa, tana
ambatar bismillah kafin ta wulwula uwa ta bace kamar walkiya, sai hancinta da digo-
digon jininta da ya faffalatsa kasan harma da bango. Bata fasa wulwulawa ta jefa ba
sai ko a keyar uwa da ke kokarin ficewa ta jikin bango ta salon tsafinta.

"Karamar yanyan ki tsaya mana, ki tsaya kiga yanda ake jifan shedan a zahirin
rayuwa",. Ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ke kumbura da cika da batsewa ba da.
Sai da tayi mai isarta harda fadawa gado. Sai kuma ta dan dafe kanta dake mata ciwo
har yanzu. Dai-dai nan akai knocking kofar, damar shigowa ta bada dan tasan
hadimarta ce. Ita dince kuwa dauke da madaran da ta saka a dafa mata. Cikin
girmamawa ta ajiye a inda ta nuna mata. Kafin ta bata umarnin gyara wajen da jinin
uwa ya faffalatsa, sai dai abun mamaki yanzu babu bantalen hancin uwar da alama dai
ifiritan aljanunta sunzo sun dauke..

**....
Kamar wadda aka wurwuro kwallo da ga nesa haka ta fado da ga ita har kujerar tsafin
nata a tsakkiyar wasu irin bakaken bukkokin bamboo da ke a jajejin. Firgitaccen
ihunta da gumzar azabar da take yasa dajin amsawa, kamar busa kaho wasu irin mutane
marasa kyawun gani da mummunar suffa irrin tata suka fara tururuwar fitowa. Duk
dinsu babu mai kaya a cikinsu, tsirara suke yara da manya maza da mata, sai dan
ganyen da suke rufe iya al'aurarsu kawai. Matan ko da ga samansu ma duk a bude yake
tun daga yammata har tsoffi. Cikin kankanin lokaci duk suka zagayeta, yayinda wasu
tsoffi da bazasu kaita shekaru ba suka rufu a kanta su kusan biyar maza biyu mata
uku. Dagata sukai gaba dayanta ita da kujerar, daya da ga ciki kuma yay saurin yafa
mata jan kyalle a saman fuskar datai kaca-kaca da jini. Daya da ga cikin dakunan
Bamboo din suka shiga da ita, shikam da yar sabuntarsa kuma babba ne, sai dai cike
yake da da was irin tarkacen bakaken gumaka da akaima ado da ja. Kujerar suka ajiye
tare da fara zagayata suna was irin surutai da dukawa da tashi kamar wanda zasuyi
ruku'u. Tuni nacan waje ma sun tattaru a kofar dakin yara da manya a layi, idan
wadan can suka fadi surkullen sai su kuma su amsa musu da ga waje suma suna dukawa
da mikewa. Gaba daya jajejin babu wani sauti da kakeji sai wanna surkullen nasu.
Haka suka dingayi tsahon lokaci kafin a ciki su fara dibo was ruwa dake a manya-
manyan randunan kasa na cikin akin suna zubama Uwa da cigaba da zagayeta cikin
surkullen. A haka suka wanke mata jinin fuskarta tsaf, hancin dai ya fita babu
kyawun gani sai fuskar ta kara munancewa fiye da da can. Amma jinin ya tsaya.
Magunguna suka sassaka mata a ciwukan dan duk ta yayyanke dan ba hancin kawai ba.
Bayan sun nutsa itama ta daina mummunan nishin da takeyi sai dai har lokacin a
wajige take. Cikin mummunar muryar nan tata ta shiga kwala kiran wasu irin sunaye,
jif!! jif!! jif!!! Kakejin abubuwa na fadowa cikin dakin, babu alamar toro a
tattare da su, sai dai duk suna gabanta a tsaye kawunansu a kasa alamar girmamawa a
gareta, Da wani irin zafin rai ta shiga nuni da bakaken hallitun dake ta fadowa. Ta
nuna na farko cikin karaji da fadin, "Keje jajjal, da ga yau na baka umarnin, karka
sake barin ta-kurya barci lafiya, a zagaye jikinta da kuraje masu warin da babu
wanda zai iya rabarta koda danta ne, a dinga firgitata a ido biyu da cikin
barcinta".

"Fadi naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa".

Ya fada yana mai zabura a guje kamar iska ya bace bat. Na kusa da shi ta nuna,
shima cikin bada umarnin, "Zurnini kaje ga dan da muka samar mata(Shahan-shan 😱),
da ga yau karya sake tunani irin na mutane, a maidashi majanuni, yayta dariya da
soshe-soshe. Ya tsani shegiyar matarnan tasa fiye da komai a duniya, nanda kwanaki
kadan jininsa halattacene garemu".

"Fadi naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa".

Shima ya fada yana bacewa. Ta sake nuna na kusa da shi shima "Rudde! Kaje ga
tsohuwar can (Malikat Haseenat 52 ), ka taya Banou aikinta, da ga nan zuwa kwana
uku jininta halattacce ne agaremu".

"Fadi naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa".

"Zambo kaje ga karsugumar shegiyar yarinyar can,ka zukemin gudan jinin da ke


jikinta, ka ringa
firgitamin ita da wajiga rayuwarta, har saita san wacece Uwa kafin masana nayi
gareta".

"Fadi naki, Cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa".

"Gamberu! Ina bukatar jinin shegun iyayen da suka haifi yarinyar nan da umarnin mu
(Wa'iyazubillah)".

"Fad naki, cikawa tawa Uwa magajiyar Uwa".

Wani irin mahaukaciyar dariya ta shiga babbagawa da fadin, "Sai na ga bayansu, sai
na haukata rayuwarsu, saina gigitasu. Yanda suka hanamu zama cikin alkaryar kasarmu
suma basu isa su rayuwuba. Sai na mulki ruman, sai na mulki duniya, zan zama mafi
girma a karfin iko. Matsiyacin tsoho (Kaka) gani nan gareka, nice da kaina zan
tsireka a tsakkiyar kasar ruman. Hahahahaha!

Gaba daya na wajen suma suka dauki dariya. Dandanan dajin ya dauki amsa kuwwa.
Tako ina dariyarsu amsawa take a cikin dajin..

*****

"Akia, an taba ciwo babu cin abinci, ki daure ko kadan kisha madarar nan sai kisha
magani". Jasrah da dawowarta kenan da ga gidansu tun bayan tashi a kotu data tafi
sai yanzu take dawowa, ta sanar ma babban yayansu komai yay mata alkawarin zuwa
kuma duk da dama Shahan-shan ya tura masa sako, dan yana daya daga cikin
mashawartansa ma akan yankema su Miran Jasim hukunci, kasancewarsa babban malami
masani. Kai tsaye dakin Malikat Bushirat ta nufi, shine ta iske ta farka. Ganin
jikin nata duk babu karfi tai zaman fara bata madara mai dumi akan tasha kafin ta
watsa ruwa sai tai sallolin azhar da la'asar da suka wuceta. Amma Malikat Bushirat
din taki amsa sam, gaba daya ta gama fita a hayyacinta. Lallashinta Jasrah ta
cigaba da yi har ta samu ta dan sha madarar kadan. Magungunan ma da kyar tasha.
Mikewa tai zuwa bayi ta hada mata ruwan wanka sannan tazo ta kamata ta kaita.
Fitowa tai ta barta da rokon tayi wanka koda ruwanne kawai ta zubama jikinta kozai
danyi karfi.

Kamar jira ake Jasrah ta fita aka fara kyalkyala dariya. A firgice ta fara
waige-waige sai dai bataga komai ba. Kuka aka fashe dashi kuma. Nama duk ta kidime
tuni ta mike zumbur kamar ba itace aka kawo bayin da kyar ba. Sake kwashewa akai da
dariya. Sosai jikinta ke wani irin rawar mazari kamar zata amayo zuciyarta ta baki.
Tako ina waigawa take amma babu komai sai ita kadai a bayin. Da mugun sassarfa ta
nufi kofa da nufin ficewa. Amma ina kofar ta rufe gam-gam babu alamar zata bude,
Tanata kiciniyar budewa akai mata wani irin harrrrr!!! Daga jikin kofar sal ga
mummunar suffa ta bayyana, baya taja a razane ta kwalla wata irin kara mai tsananin
firgitarwa data saka Jasrah dake gyara mata gadon kafin ta fito zabura itama tayo
bathroom din a razane….✍️

DAUDAR GORA....!!
Book 2
Chapter: 82

..A guje Jasrah ta fado toilet din da tunanin ko faduwa tayine tunda taga jikinta
babu kwari. Wanwar ta sameta a tsakkiyar bayi sume harta farke hannu da wani dan
karfe da akaima bayin ado da shi. Ai batama san ta fasa razananninayar kara ba tai
kanta itama a kidime. Jijjigata ta shigayi amma babu alamar rai tare da ita. Sai
kawai ta sake fashewa da kuka, dan a rayuwa tana matukar kaunar yar uwar tata,
itace ta zame mata uwa a lokacin da suka rasa mahaifiya. Ta mata gata irin na Va da
uwa bata taba banbantata da dan data haifa ba. Zama ta iya cewa ta fishi samun gata
dan shi an dauke sa a gabanta.Itako tunda tasan kanta a gabanta take,duk abinda
tace tana so shi take yimata.Idan tashin hankali yay tashin hankali baka tuna-mai
ma ya dace kayi, kuka kawai take faman rusawa tama manta a bayi suke.

Diwa da ke tsaye a bakin kofar dauke da kayan lunch da ta kawo ma Malikat


Bushirat din ce ALLAH ya jiyar kukan Jasrahn. Dama kuma itace tace ta hado abinci
mara nauyi ta biyota da shi. Bata da hurumin shiga dakin sai da izini, ga kuma
kukan tashin hankalin da takeji Jasrah nayi. Tray din ta ajiye cikin dan rawar jiki
ta fice zuwa sashen Malikat Haseenat. Suna zaune a falo Daneen Ammarah na faman
lallaba Ummu ta sake kwana itako ta ce yau sai gida zataje suyi shirin tarbar
amarya gobe insha ALLAHU sai ga Diwa ta shigo a firgice. Kallon mamaki gaba daya
suka bita dashi, Daneen Waheeda Sarkin masifa ta daka mata tsawa dan abinda Diwar
tayi babban tsaurin ido ne. Malikat Haseenat ce ta katseta da fadin, "'a Waheeda
wannan ba dai lafiya ba bita a hankali. K! Miya faru ne?". Kuka Diwa ta fashe da
shi tana nuna bayanta bayan ta zube a kasa. "Ku gafarceni ranki ya dade, babu
lafiya ne gaskiya. Ga Aunty Jasrah can nata kuka a dakin Malikat, da alama akwai
matsala ne why, tabbas akwai matsala, dan dama likita nata zaryar dubata tsakanin
jiya da yau"

Babu wanda gabansa bai fadiba


a cikinsu, dan dama basu jima dayin maganar rashin ganinta a kotu ba. Daneen
Waheeda ce make cewa kila bata da ra'ayin zuwan ne yau tunda sun san halinta. Gudun
kar maganar tai tsaho ga Ummu da take bakuwa a tare da su yasa Daneen Ammarah kauda
zancen ta dako wani.

Gaba dayansu suka kunduma sashen Malikat Bushirat, Ummu kawai aka bari. A gaban
idon Banou da ke tsaye da wata bakuwar fuska a jikin fulawoyi suka wuce.Da wani
mummunan kallo suka bisu, sai dai babu wanda yace komai. Su Malikat Haseenat da
basu san sunayi ba ko mota suka shiga zuwa sashen Malikat Bushirat din. Sun sami
Hadiman sashen Jigum-jigum, dan zuwa yanzu kusan duk sunji irin kukan da Jasrahn
keyi. Babu wanda ya saurari gaisuwar hadiman sukai ciki da hanzari, dan suma dai
suna shigowa da kukan Jasrahn suka fara cin karo. A bathroom din suka sameta har
yanzu, da kyar Daneen Ammarah ta dagata, rungumeta tai cikin jikinta dan ta sami
nutsuwa, Malikat Haseenat kuwa inda Malikat Bushirat ke kwance wanwar ta nufa,
tattabata ta shigayi. Daneen Waheeda dai na tsaye babu alamar damuwa tattare da
ita. Sai ma bin toilet din take da kallo baki a labe. Da kyar Daneen Ammarah ta
lallashi Jasrah har ta dan musu bayani a takaice. Dole aka kara kiran Doctor sannan
aka saka hadimai shigowa suka kakkamata aka fiddota aka kwantar saman gado.

Zuwan doctor ya tabbatar musu ba mutuwa tai ba, ta dai suma ne. Ajiyar zuciya
suka dinga saukewa, shi kuma ya shiga kokarin ganin ta farfado, yayinda Malikat
Haseenat ke faman tofa mata addu'oi. Wani irin numfashi ta kawo tare da zabura mai
karfi, wadda har doctor dole ya kai hannu a kanta domin maidata amma ya gagara shi
kadai. Dole Jasrah da Daneen Ammarah suka matso domin taimaka masa. Amma fa sun
kasa dan wani karfi na masifa ta musu, ga fisge-fisge tanayi na tashin hankali.

(Tofa al'amarin fa babbane) cewar Daneen Waheeda a cikin zuciya tana dan tabe
baki. Suko da basu san tanayi ba sunata kici-kicin son gain ta lafa, Malikat
Haseenat kuma na tofa mata addu'a. Da kyar suka iya tankwarata, har sun hada zufa
sharban kamar yanda itama tayi.Numfashi suka shiga saukewa na jigata. Doctor kuma
ya shiga aikinsa. ya sake maidata barci sai dai fa barcin yaki yiwuwa. Dan da ya
dan figeta sai ta zabura sai sun sake dannata ta
koma kwance. Al'amari fa tun anayi da marmari harya fara gundurar kowa aka karo
doctors da was alluran masu karfi sosai da sukafi na farko da akai mata..
Cikin kankanin lokaci zancen rashin lafiyar ya zagaye masarautar. Masu tausaya mata
nayi masu farin ciki nayi. Masu kuma fassara al'amarin da wani abu daban nayi. Dan
danan labarin ciwon nata ya zama latest topic à cikin masarautar. Dama ga nã
hukuncin su Miran Jasim da bai gama disashewa ba.

***

Duk wanna al'amarin Iffah nacan kwance tana shan barcinta bata san bikin da ake ba.
Dan sai la'asar ta tashi. Wanka tai tayi salla. Bayan ta kammala kimtsawa ta fito
neman abinci dan yunwa takeji. Hadimanta da ke dan kus-kus din su suma akan
al'amurin Malikat Bushirat din sukai saurin mikewa. Kallo daya ta musu ta dauke
kanta, dan har yanzu zuciyarta babu dadi. Zama tai tare da bada umarnin a kawo mata
abinci anan. Cikin ko kankanin lokaci amintacciyarta ta jere komai. Ta bude zata
zuba mata ta dakatar da ita idanunta kur akan abincin. "Waya dafa wannan
abincin?"Ta fada tana kallonsu. Cikin rawar jiki amintacciyar tata ta sanar mata
itace da mai girki. Ta nuna mai abincin. Shiru Iffah tana duban wadda aka nuna
matan sai faman sinkuy da kai take. Ai bama tasan ta daka mata tsawa ba tace ta
dago. Ba ita da taima tsawar ba hatta sauran hadiman sun matukar razana. Dan abu ne
da bata taba musu ba. Wani irin kallo Iffah take ma matar rai bace. Jikinta har
tsuma yake ga idanunta sunyi jazur na tashin hankali. Duk wanda ya dubeta sai ya
razana, idan ma irin su Bily ne fitsari zamu saki a zani😝Dan gaba daya ta juye
tabbacin ba Iffah bace.

Wani irin shakota Iffahir tayi ta dauke ta da bahagon marin da ya idasa tsurar da
sauran hadiman jikunansu suka fara rawar mazari. Marin matar nan Iffah take tamkar
ALLAH ya aikota. Gashi ta shaketa da iya karfi. "Ubanwa ya aikoki nan?". Ta fada da
wata irin gigitacciyar murya mai matukar razanarwa da amsa kuwwa. Cikin kakarin
azaba matar da gaba daya ta gama jiyo kamshin mutuwa da kyar ta ce, "Uwa."

"Uwa. uwa. Iffah ta fada kamar mai bitar sunan, sai kuma ta kyalkyale da dariya
ta kuma hade fuska. Cikin dage gira da zuba jajayen idanunta a tsakiyar na matar da
ke a shake har yanzu a hanunta ta ce, "Ohhhyyyyo ita bata gane karatun kurma kenan.
Bakuma ta gane gargadin makawo sai ya doka sandarsa. Shin wai dolene sai ta
fusatani ne?!!!!!. Nace sai ta ga ainahina sannan zata tabbatar nafi Karfinta?!!".
Ta sake fada cikin karaji tana gwara kan matar da centre table. Wata iriyar
wahalalliyar kara ta sake illahirin jikinta na rawa dan fa ta bugu matuka duk da
katako ne. Tuni hadiman sun fara sakin fitsari a wandunansu. Yayinda Iffah da bata
san sunayi ba tana cigaba da maka kan matar nan jikin centre table. Sai da tai mata
ligi-ligi har numfashinta na fita da kyar ga jini yay mata faca-faca sannan ta
dagata tsaye, cikin daka tsawa ta dubi amintacciyarta tace a kira mata Ghazi guda
biyu. Cikin kankanin lokaci suka iso kuwa. Jefa musu matar tayi taki zube yaraf a
gabansu. Rai bace ta ce, "Ku dauketa, a dauremin ita a tsakkiyar masarautar nan".
Cikin rawar jiki suka amsa mata da "Umarninki shine abin jiranmu ranki ya dade".
Kota kansu batabi ba ta nufi dining, wajen wanke hannu ta nufa ta wanke hanunta da
jini ya dan bata, har yanzu a birkicenta take. Bedroom dinta ta koma, babu jimawa
ta sake fitowa cikin sabuwar shiga. Har yanzu hadimanta na lafe jikin bango a
tsorace. "Ku biyoni da wannan abincin". A zabure duk suka mike, Itako tuni ta ma
fice abinta. Kamar yanda ta saba tafiya duk inda take so a kafa yanzun ma hakane.
Sai dai yau ko sau daya bata kula gaisuwar kowanne hadimi ba. Koma kallo basu
isheta ba har ta isa sashen Malikat Haseenat. Anan din ma babu hadimin data kula
Sai dai tana binsu da kallo daya bayan daya. Ganin babu wadda take nema cikin wata
irin razananninayar murya ta kwala
kiran sunan "Banouuuu!!!"

Ba Banou din da taima kiran mafarautan ba, hatta Ummu da Iftihal a dari suka
fito, hakama duk wani hadimi dake sashen dama wanda basu san da zuwanta ba har
tuntube suke wajen fitowa. Banou da jikinta ke wani kakkarwa ta zube a gabanta,
wani irin mari ta kai mata itama tare da shakota ta mikar da ita tsaye. Cikin murya
mai razanarwa ta furta, "Ina bakuwar takini?!!!!"

Ba Banou din kawai ba, kowa ma a wajen jikinsa rawa yake yi, hatta Ummu data
raineta yau ji tai Iffahn na bata toro. Iftihal kam ai tuni ta jike dogon wandon
jeans din jikinta da fitsari, jikinta ko tsabar rawa da yake tuni har wayarta taje
kasa bata sani ba

Banou dake watsal-watsal din kakarin mutuwa ta nuna matar da suke tare dazun
lokacin da su Malikat Haseenat ke fita zuwa sashen Malikat Bushirat. Sakin Banou
din tai, sai gata a kasa rikica. Tako kwalla karar azaba. Da hannu taima waccan
nuni da tazo. Zatai mata wani noke-noke tai wani irin fisgota ta buga da bango.
Gaba daya falon ya sake ridewa, Iftihal ta shige jikin Ummu ta fashe da kuka. Cikin
karaji Iffah ta ce, "Ku nawa ne?!!". Jikin matar na rawa ta ce, "Karki kasheni,
nayi alkawarin zan fada miki duk abinda kike bukata, na rokeki.

'"'Na ce dan uban ubanka ku nawa ne?!!".

"Mummu biyar ne?"

"Kai mi aka aikoka yi? Da har ka koma suffar mata?"

"'Z.z zan taimakawa Banou ne mu karasa uwar masu gida, d. d. Dan ta dade anan din
tare da ita…✍️

DAUDAR GORA....!!
Book2
Chapter: 83

…Babu wanda bai zaro ido ba a falon. Cikin bacin rai Iffah ta ce, "Na fika sanin
wannan"Jikin matar na rawa ta cigaba da zayyano mata sauran. Yayinda tuni Ummu dake
rude Iftihal mamuke da ita ta yunkura da niyyar zuwa ta nemi Kaka a waya, dan dazun
da sukazo sun kawo mata wayarta shima Babiy yana amfani da nashi. Kin sakinta
Iftihal tayi, dole sai tare suka tafi. Iffah kam juyawa tai ta dubi hadimanta da ke
dauke da abincin data bada umarnin a biyota da shi, ta nuna na hannun
amintacciyarta. "Ajiye musu shi suci"

Da ga Banou har abokiyar aikin nata kuka suka sanya, dan su suka san abinda suka
gani a abincin. Ko kallo basu ishi Iffar ba, tana tsaye a kansu fuskarta kawai abar
firgitarwa ce. Haka suka fara cin suna kuka da rokon tayi hakuri, a haka su Malikat
Haseenat da akeje aka sanarmawa suka shigo hankali tashe. Dan can sun samu Malikat
Bushirat tayi barcin da kyar bayan an rufu kanta da addu'oi. Kallon Iffah da su
Banou din kawai suka tsaya yi cirko-cirko. Daneen Waheeda kam tuni ta koma bayan
Mammah ta makale, yayinda Daneen Ammarah itama nata kamanin suka fara canjawa dan
idanunta sun kada sunyi jazur. Ture abincin Iffah tai da ga gabansu, ta wani irin
hankada Banou gaban Malikat Haseenat. "Jeki sakar mata kafafu!!". Cikin madaukakin
mamaki Malikat Haseenat ke duban Banou da Iffah. Sai dai razananniyar tsawar da
Iffahr taima Banou din ita kanta sai da zuciyarta ta shiga tsitstsinkewa. Banou
dake kuka cikin rawar jiki ta kama kafafun Malikat Haseenat, wani fushin kumburi da
kafafun sukai tsahon shekaru an kasa gane kansa sai gashi yau yana bajewa, Kusan
minti biyu tace mata ta mike, mikewar tai jikinta sai kakkarwa yake, du da girman
jikin nan nata ga tsaho amma Iffah dake yar digila gabanta ta zame mata dodo. "Na
baki minti hudu, ki dakko tukunyar da kika ajiye a cikin flowers".

"Umarninki shine abin jirana ranki ya dade".

Banou din ta fada cikin sake gurfana. Suna tsaitsaye har yanzu babu wanda ya iya
cewa komai sai ga Banou ta dawo da tukunyarta, A gaban Iffah ta zube, ta bude
tukunyar ta shiga fiddo abubuwan da ke ciki. Abinne kamar tsokar nama, duk ta
daure. Kwancewa ta shigayi tana sakinsu, firrrr suke tashi kamar tsuntsaye, wasu ko
da kyar zakiga sun tashin saboda ta jima tana wahalar da su. Cikin
bada umarni ta dubi sauran hadiman ta ce, "Aje a duba duk wanda yake a halin ciwo
ya mike a yanzu a kaimun shi tsakkiyar masarautar nan. Ina bukatar Ghazi guda biyu
anan".

Cikin kankanin lokaci Ghazin data bukata suka shigo, su tasa suka tasa mata keyar
su Banou.

*Tun fito da Hadimar da ta jibga a sashenta al'amarin ya fara zagaye masarautar.


Abin mamaki sanda take fitowa su Malikat Haseenat biye da ita masarautar ta gama
cika. Dan sashe-sashe an fito kamar busar kaho. Cikin kankanin lokaci duk wani mara
lafiya dake gidan aka fito da shi, harma wanda ba Banou din ce ta tabasu ba. Tana
kuka da faman rufe fuska ta tsatstsallakasu. Tana gamawa suma sawa tai aka daure
mata su tare data farkon. Dai-dai nan su Baby suke isowa cikin masarautar. Hakama
Tajwar Eshaan a rikice Malikat Haseenat tai kiransa ta sanar masa babufa lafiya a
gidan da ya kamata ya
fito. Dama shirin fitowa yake, dan amintaccensa yazo masa a kidime babu dadewar
nan, hakama Sayeed Fayzul-haq ya kirasa shima.

Lokaci daya wajen ya dauki shiru sakamakon fitowar tasa, dan abunne da babu
wanda yay zato. Kowa a wajen sai da yay kasa da kansa har Iffah, dan a zahirinsa
yake kyakykyawar fuskar nan a bayyane, sai dai fa cinkus take babu alamar wasa ko
sassauci. Amintaccensa ya ajiye wata yar kujera mai kyau dake a ninke aka budeta.
Sai kuma katuwar umbrella da aka bude masa duk da bawani ranar nada zafi bane dan
ta la'asar ce ma dake neman faduwa. Sai dai kuma a mamakin kowa ma bai zauna ba.
Sai duban Iffah da yay na kusan mintuna biyu. A hankali ya furta, "Mike faruwa".
Cike da irin girmamawar dake nuni da ba ita bace ba ta kai kasa gurfane gabansa.
Gaisuwa ta fara mikawa,kafin dukkan abinda ke faruwa ta zayyane masa. Idanu ya dan
lumshe da sake budewa. Kamar bazaice komai ba sai kuma yay mata nuni da ta tashi,
tare da fadin,"Duk da ba itace a tare da gangar jikinta ba kuskurene kai Zawjata-
almilk kuma * Malikat * kasa a kowane irin yanayi a gaban al'ummar kasar ta"

Wanna furici nasa ne yasa kowa fahimtar ba ainahin Iffah'r bace iskokinta ne
yau suka bayyana kansu abinda basu taba yi ba, sannan kuma maganar cikin jikinta
tabbataccene tunda har shi da kansa ya kirata (MALIKAT). Neman afuwa suka shiga yi,
da tsayawa tsaye akan kafafun Iffah'r. Alokacinne Sayeed Fayzul-haq ya yafito Kaka
dake tsaye kawai yana murmushi. Sai da ya fara mika qaisuwa ga Shahan-shan shima
sannan ya duba Iffah, kamar yanda sukaima Tajwar Eshaan bayani haka shima kakan
sukai masa. Kansa kawai ya jinjina da cire jakar hannunsa ya ajiye. Ruwa ya bukata,
cikin kankanin lokaci aka kawo masa. Magunguna ya fiddo da yawa ya shiga zubawa a
ruwan nan. Wani irin ihu su Banou suka dingayi da rokon yayi hakuri, bama su ishesa
kallo ba ya fara dibar ruwan maganin yana watsa musu. Ihu na gaske suka dinga
kwallawa da surutai suna girgiza da gunji. Sai da yay musu ligif sannan ya basu
umarnin bayani da bakunansu. Biyun sun tabbatar da su ba mutane bane sun rikidane
kawai. Kuma a yau din nan suka shigo cikin masarautar bisa umarnin uwa da Iffah ta
raunata a dazun. Banou kam mutum ce ita, sai dai akwai aljanun maita tare da ita,
irin kusan duk zuri'arsu ke da shi, dan itama cikin zuri'ar uwa take. Cikin
galabaita ta shiga fadin tun sanda take tare da su.

"Ni shekarata goma sha tara anan, tun bayan korar uwa da akayi da ga wannan
masarauta. Ina daya daga cikin zuriarta da aka kora shekaru masu yawa da ga cikin
wannan alkaryar, a da kakanninmu wannan filin masarautar shine garinsu. Amma sanda
za'a kafata sai aka tashesu aka canja musu waje. Ransu ya baci matuka da wannan
al'amari, dan tunda suka taso anan suka samu iyayensu da kakanni suma, nan kadai
suka sani matsayin kasarsu kuma gari, ga abubuwan bautarsu masu tsahon tarihi
tsahon shekaru duk an ruguza musu. Dan haka sukaji zafin tashinsu da akai da bata
musu wajen bauta da abubuwan bautarsu saboda gina masarauta bayan akwai filaye da
yawa da babu kowa a cikinsu miyasa baza ai acan ba. Wannan haushin yasa sukaki zama
inda aka basu sukai hijira zuwa cikin jeji. A haka suka cigaba da sabuwar rayuwarsu
wadda da kyar suka saba da wajen, sai ya zam duk wanda aka haifa a cikin zuri'ar mu
wannan
shine labarin da za'a raineka a kansa, da kuma kiyayyar wannan gida. A haka duk
muka rayu da burin daukar fansa. Mun dade da shiga jikinku muna muku illa da suffar
bokanci, hatta lokacin da kuka samu ambaliyar ruwa a kusan kasar baki daya zuri
'armu ne suka balle wani yanki na kogin da ke zagaye da ku. Mu bamu taba jingina da
ku domin mu taimakeku ba sai dan mu ruguzaku, a haka iyayenmu da kakanninmu suka
dinga shudewa. Uwa ta kasance mafi girman hatsabibanci da yin tasiri a al'amuranku
a cikin duk wanda suka zo da nufin masu taimako a gareku a cikinmu. Duk da dai akaf
zuri'armu daga maye sai matsafi, kuma kowannenmu nada abinda yake yi domin ku.
Jajircewar uwa da zamowarta mafi iyawa a kan iyawar kowa cikinmu yasa ta zama
shugaba a garemu, kuma ita muke fata da gain ta kusa karbo mana wanna masarauta
data kasance tushenmu ta koma tamu. Amma sai abubuwa suka fara canja salo a dalilin
tsohuwar can (ta nuna Malikat Haseenat) ta kanainaye komai tana faman rushe duk
wahalhalinmu da muke gain saura kiris komai ya kare. Dan haka mukaita kawo mata
hare-hare amma bam samu nasara a kanta ba. Ana cikin hakan rana tsaka ma sai ga Uwa
mun tsinta a yashe cikin mawuyacin hali anci zarafinta a dalilin wanna mutumin da
mahaifinsa (ta nuna kaka). Hakan ya mana ciwo matuka, ga uwa nakan gangarar mutuwa,
a take muka tattara duka karfinmu wajen cetonta, dan duk karfin dake tare da ita na
tsafinmu na gado da ma wanda ta samarwa kanta wannan mutumin ya lalatashi. An bada
umarnin wasunmu su sake dawowa cikin masarautar nan, duk da zuwane na kasada ni a
kasance a daya da ga cikinsu. Kuma nice nan a kashe Shahan-shan Abdull-Majeed a
cikin suffar maciji, dan inada maita mai karfin gaske fiye data kowa a cikin
zuri'armu. Bayan mutuwarsa na cigaba da bibiyar rayuwar war masu gida, sai dai na
kasa kaita kasa saboda abubuwan kanta, nadai samu nasarar nakasar mata kafafu ta
hanyar ciyar da ita abubuwa a cikin abincinta. Amma tun randa na had da Zawjata-
almilk abubuwa da yawa suka lalace min, dan tanada iskoki masu karfin gaske, itace
ta dakusheni akan abubuwa masu yawa. Ta kuma min daurin da bazan iya barin wannan
gidan ba duk da naso yin hakan tun a ranar farko dana hadu da itan. Uwa tayi iya
kokarinta itama na son ganin ta fiddani amma ta gagara".

Ajiyar zuciya kawai kakeji na sauka da al'ajabin wadan nan abubuwa wai kamar
wata almara. Banou da kowa ya sani mafi zama kololiwar amintacciya ga Malikat
Haseenat dai, wadda inba abincin data girka mata ba batacin abincin kowa sai Daneen
Ammarah. Kai to ai yanzu kowama ba abin a yarda da shi bane hatta hadiman nasu.

Kaka ya jefama Banou tambayar, "Mutane nawa kika cutar a shekarun zaman nan naki?"

"Ni ban san adadi ba. Amma na halakasu da yawa, dan akwai ayyukan da na dinga ma
uwa da yarjewar wata babba a gidan nan. Sannan akwai wadanda na kashe dan radin
kaina da wanda na dinga cinyewa cikinsu. Na karshen nan dana cinye shine na Jasrah
a randa Zawjata-almilk bata da lafiya…..✍️

DAUDAR GORA
Book2
84

..Salati wajen ya dauka da sallami, kowa na tsinema wa da banou. Cikin girmamawa


Kaka ya dubi Shahan-shan da shi gaba daya ma komai ya tsaya masa cak. "ALLAH ya
karama adalin shugabanmu lafiya da tsohon rai mai amfani, a ganina barin wadan nan
bashi da wani amfani, a samu dutsina a juye musu ruwan maganin nan kawai a musu
rajamu anan, dan wadan nan mutane nada karfin tsafin da rufesu ko musu hukuncin
zaman kurkuku bazai taba iya magance matsalarsu ba. ALLAH yasa ban shiga hurumin da
ba nawa ba".

Shiru baice komai ba. Kusan minti uku sannan ya dubi Sayeed Fayzul-haq. Da ga
haka ya taka a hankali gaban Iffah. "A gusa daga jikinta",. Iya abinda ya fada
kenan. A take kuwa tai hamma jikinta ya saki gaba daya. Rikota yay cikin jikinsa ya
rungume. A take kowa da kowa na wajen yay saurin yin kasa da kansa cikin hanzari.
Shiko ko'a jikinsa ya dagata cak dagakasa kamar ya manta ma da wasu halittu a wajen
yay wucewarsa.

🥱Wannan fa shine ga abin fada babu damar magana 😝

Kamar yanda kaka ya fada kuwa haka akai, tuni hadimai suka cika wajen da
duwatsu, kaka ya yayyafesu da ruwan magani, Kamar jira suka shiga diba ana ambaton
sunan ALLAH ana jifan su Banou.Ihu suke mai tsananin kururuwar sauti. Amma mutanen
nan ko'a kwalar rigarsu. Dama wasu harda fushin Banou tai musu sanadin yaya wasu
iyaye, wasu maza, wasu matansu. Dan a cikin wanda ta halakar mafi rinjaye hadimai
ne. Babu wanda ya tausaya musu a haka aka jefesu har sai da suka daina numfashi.

Kakane ya ce abar gawawwakin a wajen masu su zasu aiko a debe su, dan sune aiken
farko da zasu turama kabilarsu. Haka kuwa akayi, sai dai dan daukar da was samari
da yammatan gidan sukayi a wayoyi suka saka a social media cikin kankanin lokaci
al'amarin yay amsa kuwa. Wasu kungiyoyin kare hakkin dan adam suka shiga caccakar
al'amarin a bayyane ta kafafen ya da labari, kafin wasu awanni labarin ya shiga
zagaye duniya, ya zama video mafi rinjaye da ke yawo kuma ake kallo.....

**

Sun iso gareta a whale, wahalar da duk wanda ke cikin wanna zuri'a sai da ya
girgiza. Hakan yasa su yin cirko-cirko da zaman sauraren abinda sukazo da shi. Ita
ko tana zaune a cikin kujerar tsafinta hancinta da Iffah ta gundile ya kara saka
fuskar munana matuka. Hakama sauran raunikan da taji sun kumbura fuskar ta kara
zama humm.

Cikin gurfana da garshekar hakin rudani daya da ga cikinsu ya shiga zayyane mata
abinda ke bakinsa, "Shugaba wannan aikin yafi karfinmu, ba namu bane ba sai dai ke.
Sun halaka Rudde da Zambo da Banou Sun halakasu har lahira uwarmu mai share
kukanmu".

Yanda take huci har Kirjinta na dagawa sama zai baka tabbacin tafa kai
kololuwar hasala. Cikin wata irin mummunar tsawa ta nuna su da yatsanta mai dauke
da zurkeken farce. "Ni uwa nizan sakaku aiki ku dawo kuce anfi karfinku. Idan kun
gujema mutuwarku acan anan ma ita kuka tarar. Ahamanu a daure min su, a aka angulu
ta dakkomin gawawwakin su Banou!!"

"Fadi naki cikawa tawa, uwa magajiyar uwa". Wanda aka kira da Ahamanu ya fada
cike da girmamawa a gareta. Cikin abinda bai wuce awa daya ba angulu ta dawo da
gawawwakin su Banou, ta jima tana kallon gawarwakin guda uku da ke jina-jina da
raunikan jifa,hakama sauran mutanen garin tsaitsaye suke yara da manya maza da
mata. Sirkullensu a tsafi ta fara sauran suka dauka da amshi kowa ka gani ransa a
jagule da bakin ciki. Bayan sun dauka lokaci sunayi ta bada umarnin daukar gawar
Banou zuwa dakin gumaka. kasancewar sauran su aljanu ne dama wani ruwa kawai ta
yarfa musu namansu suka shiga zaganyewa, a hankali a hankali suka bace bat.

"Lokacin da zamu shirya akin gaba-da-gaba yayi, Jajjal ne kawai ya jurema


umarninmu har yanzu bai dawo ba. Na sani shi dama mai jajircewa ne da naci akan
komai. Kuma duk wani dan da ya cika dan halak a zuri'armu irinsa ya kamata ace ya
zama. Kuje maza kuje ku shirya yaki. Sai mun sabauta gaba daya al'ummar kasar
ruman. Sai mun sake dawo musu da tarihi irin na baya koma mafiyinsa. Kuje maza
kuje!!!!!"

Wani irin hun fusata suka fasa a tare ikkunansu na jujjiga irin an kada musu
gangin nan. A take kowa ya nufi dakinsa na Bamboo suna kwada kiran sunan babban
gunkinsu suka shiga shirin yaki. Ba wai wuka ko bindugu suke tanada ba. A tsafinsu
suka shiga sake tsimawa. Shiri suke karshen shiri dan gaske. Maza da mata, yara
kuwa anata faman tsumasu da abubuwa.…. Babu wanda ya sake fitowa sai cikin dare,
inda aka dakko gawar Banou dake tire jikin wani katon mashi aka kafe musu a
tsakkiya. An yanke wasu sassan jikinta da ke matsayin hakkin uwa, su kuma suka rufu
akan gawar suka dinga yagar namanta sunaci da ihu kamar wasu kiyashi sun samu nama,
suna kwala kiran sunayen gumakansu da dodanni Jejin har wani girgiza yake saboda
tashin sautin muryiyinsu…..

()

Washe gari an tashi masarautar a rincabe da tashin hankali kala-kala matuka. Dan
haka kawai aka samu gawawwakin hadimai da Ghazi da jami'an taro sama da hamsin an
musu kisan gilla a daren jiya. Ga Iffah tun fitar aljanun nan jiya da ga jikinta
barci kawai take, lokacin salla ne kawai idan yayi take tashi da kyar tayita. Tana
idarwa kuma zata sake komawa ta kwanta kamar wadda tasha wani abu ko batun abinci
ma ba'ayi. Tashin duniya Tajwar Eshaan yayi amma taki tashi in har ba lokacin salla
ne yayi ba. Ga a jiya da dare yaje ya duba Malikat Bushirat dake ta faman zabura da
ihu sam batai barci ba itama jikin ya sake rikicewa. Hakama duk wanda ke zagaye da
ita bai barci ba. Safiyar yau kuma kawai ta tashi da wasu irin manya-manyan kuraje
masu radadin azabar zafi dana kaikayi. Kuka kawai take tana rokon a cire mata. Ga
sunayen Zawjata-almilk da suka rasu sai lissafowa take daki-daki wai sunzo zasu
kasheta, sun zo daukar fansa.

Gaba daya kowa ya kasa fahimtar komai da ga zantukanta, sai dai duk mai imani ya
ganta sai ya ji tsoron ALLAH ya sake kamashi. Kusan a tare babban yayansu da Kaka
da akaima kiran gaggawa cikin masarautar suka iso. An fara taruwa an ma gawawwakin
wadanda aka rasa salla harda Tajwar Eshaan, bayan an kammala biznesu ne kuma aka
rufu kan Malikat Bushirat da zuwa yanzu kurajen duk sun rure da ruwa. Duk wanda yay
mata kaikayi ta sosa kuma azabace mai zaman kanta. Shiru kawai kaka yay yana
kallonta, yayinda duk wanda ke cikin dakin dan yan uwanta duk sunzo kuka suke
sosai. Babban yayansu da shima ke kallonta ya juyo yana duban kaka. Cike da
girmamawar kasancewar ya fisa shekaru ya ce, "Baba wannan aikin jinnu ne kam
tabbas. Amma miya hada Jinnu da Bushirat duk da dal an sanar min da dambarwar da
ake fama da ita a gidan.

Ajiyar zuciya kawai kaka yayi kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya nisa a hankali
da fadin, "Wannan al'amari ne kam da ya kamata muji a bakinta, dan babu rami babu
abinda zai kawo rami kam. Ambaton sunayen wadanda suka mutu da fadin karsu kasheta
da take babbar ayar tambayece a gareta Abni".

Babu wanda bai gamsu da zancen kaka ba a wajen, sai dai kuma hankalinsu ya tashi
da jin abinda ya fada din. Dai-dai yana fiddo wani magani Tajwar Eshaan ya shigo
dakin rike da hanun Iffah da farkawar ta kenan ta zabura. Riketa yay amma ta rokesa
ya barta sashen Ammie zataje. Shima bai jima da baro sashen ba, dan tafiyarsa babu
jimawa su kaka suka shiga. Zaunar da ita yayi sannan shima ya kai zaune, take aka
shiga mata sannu sai dai babu wanda ta amsawa. Kaka da babban wan su Malikat
Bushirat din suka sake mika gaisuwa ga Shahan-shan dan sun gaisa tun shigowarsu
masarautar. Da ga haka Kaka ya bada maganin da ya fiddo yace amata hayaki da shi.
Cikin sauri suka amsa aka zuba a burner da aketa bulama turaren wuta saboda kurajen
Malikat Bushirat din duk wanda ya fashe wari yake yi kamar an tono rubabben nama a
cikin kasa. Wani irin fisge-fisge ta dingayi da hun da ya saka Tajwar Eshaan lumshe
idanu kawai idanunsa sun kada jazur abin tausayi, shi Iffah ta tsurama ido, ji take
da'ace tanada damar sashi ya bar masarautar nan a yau data sakashi, dan sam bata
son ai wannan tone-tonen a gabansa. Amma yaya ta iya, bazai yuwu ace a wannan
dambarwar babu shugaban wanna kasar gaba daya a cikinta ba. Malikat Bushirat ta
jima tana fisge-fisge gashi babu damar taba ta saboda kurajen jikinta itama in ta
taba radadi take ji, dan kanta ta lafa bayan ta gama jigata. Yanda ta nutsu yasa
kowa tunanin ma Kota mutu ne. A razane Jasrah ta shiga kiran sunanta tana kuka, sai
da Kaka yace ta kwantar da hankalinta tanada ranta, turaren zai rage mata radadin
kurajenne matuka. llai kuwa sai gashi ta bude ido. Gaba dayansu tabi da kallo daki-
daki, yayinda wasu keta tofa mata addu'oi kamar yanda yayanta ya basu umarni tun
dazun. Wasu. hawayene masu radadi suka shiga zaryar zubo mata lokacin da idanunta
ke sauka akan Tajwar Eshaan da Iffah. Ta jima tana kallon su, sai kuma ta sake
fashewa da kuka.

Yayanta ne ya katseta da fadin, "Sai hakuri Bushirat, kuka baya daya da ga cikin
mafita, ki daure ki sanar mana abinda ke faruwa domin musan makamar rikewa wajen
yimiki magani. Shin garin aya wadan nan abubuwan masu alaka da aljanu ke zagaye da
ke? Minene kuka sani ke da Zawjata-almilk da mu bamu sani ba? Mi kuke boye mana da
Jasrah har taji kuna sa'insa a shekaran jiya?".

Idanu Tajwar Eshaan ya bude da sauri ya zubama Iffah idanunsa da suka kada
jazur, amma ita sam taki kallonsa ga fuskarta kicin-kicin kamar yanda tashin take,
Malikat Bushirat kam kuka ta sake fashewa da shi. Kafin a hankali ta motsa lips
dinta wajen fadin, "Ni na jama kaina Akhi. Ni na siyama kaina komai. Komai kuma ya
farane a dalilin HAIHUWA. a dalilin neman haihuwa da tsananin bukatar samuwarta.
Buri da kwadayin gani da son haihuwar magaji shine silar labarin zamana a wanna
masarautar da ma duk abinda na aikata a tsahon shekaru arba'in da a yau nake girbar
abinda na shuka tun daga nan duniya........

🤔Tofa UBANGIJI gagara misali, Nama rasa abin cewa.

DAUDAR GORA
Book2
85

."Duk wanda ya sanni tun a kuruciya yasan ni yarinya ce mai yawn kirinki, nayi
rashinji matuka, dan a fada biyar da za'ai dani cikin yara to da wahala ka samu
daya a ciki da nake da gaskiya. Tun ina karamata na kasance mutum mai son gain kowa
ya zama a karkashin ikona. Hakan yasa ban yarda da abota da wanda muke shekaru daya
ba ko ko sukafi gidanmu arziki. Duk kawayena na girmesu, na kuma fisu wayo, gidanmu
kuma yafi nasu komai. Hakan yasa dole sukemun biyayya da bin abinda nake so koda
ace su basa son sa. Mahaifiyarmu na yawan mun fada akan wannan halayyar, hakama
mahaifinmu. Nakan nuna naji na dan wani lokaci amma da kura ta lafa sai na koma
gidan jiya. A haka na taso da wannan rayuwar har girma. Kowa yasan Bushirat boss ce
a cikin kawaye, idan kuma kana son ka zauna lafiya tilas ne kamun biyayya. Gidanmu
gidane na manyan mutane, masu ilimi kuma Alhamdullah munada dukiya. Ina alfahari da
hakan, amma kuma inada buri na kai da kai. Kasancewata kyakykyawa nayi samari kala-
kala, duk da dokar mahaifinmu shike zabama kowace yarinya a gidan mu miji, a nawa
bangaren babu wannan ra'ayin. Sai dai na shanye ban taba sanarma kowa ba. Duk wanda
zai zo gurina sai nayi duk yanda zanyi na bibiyi nasabarsa da nauyin aljihunsa,
idan ka kasance baka da ko sisi zan tattaraka na watsar, tare da kashedi mai girma
na ka fita a hanyata. Wasu sukan barni cikin sauki, wasu ko saina yi jan ido kona
hada musu tuggu a wajen yayuna sun kore su. A haka na kammala karatuna na boko,
wanda na taso naga anayi a gidanmu kam shima na samu gwargwadon iko wat ilimin
addini. Sai dai sam bana maida hankali garesa, dan ni salla ma sai mahifiyarmu
tamun jan ido. Da girmana da hankalina nasha daukar azumi na karya batare da an
sani ba, kawai dan inajin wata kaina sama can. A haka wata rana naji Akhi kazo ma
da baba batun wai Miran Haysam mai jiran gadon karagar mulkin Shahan-shan ya baka
zabin nema masa matar aure. Kai kuma kayi tunanin dubawa a cikin yarn gidanmu amma
har yanzu baka gama yanke hukunci tsakanin ni da Hubba ba. Abinda ya girgizani
shine, jin Abie kai tsaye ya furta ("Uhm-uhm Muhammad, ajiye maganar Bushirat gefe,
bata jin magana, sakata a babban gida irin wannan zai iya zubar mana da kimar mu da
nuna gazawar tarbiyyar da muka baku. Yarinyace mai kaudi da hange, ina tsoron
al'amarinta. Akance a cikin yaya an fidda maka zakka, to tabbas Bushirat ni itace
zakkata. Ka bashi Hubba kawai zamuyi alfaharin da ita") wannan bayani na Abbie ya
tayarmu da hankali matuka. Dan ga koshi ga kwanan yunwa ne. Zama nai naita nazarin
mafita, dan har wata zuciyar na bani shawarar kashe Hubba dan itace kawai
matsalata.Naki karbar wannan shawarar, dan ko yaya ina matukar kaunar yan uwana,
Haka na cigaba da saka ido a duk motsinka da na Abbie, sai dai shiru bakayi maganar
ga Hubba ba balle iyayenmu mata. Dan duk da mahaifiyarmu ta rasu wajen haihuwar
Jasrah bamu taba kukan rashin uwa ba ga matan babanmu, sun rikemu hannu biyu tamkar
sune suka haifemu. A cikin dogon nazari dana bama kaina kwana biyu a samo mafita.
Ranar na yini cikin farin ciki sosai dan inaji a raina na gama zama matar Shahan-
shan. ALLAH kuwa ya yarjemin, dan a randa na gama yanke wanna shawara a bibiyar
Akhi da nakeyi da Abbie na samu jin Akhi zai tura sako ga Miran Haysam ibn Abdul-
majeed Aliy Qutb na zabin matar da ya nema.Tuni na garzaya na rubuta wasuka mai
nutsuwa tare da saka hotunana a ciki da dama na tanada. Dakin Akhi na lallaba
batare da sanin kowa ba, nai sa'a kuwa yana wajen karatu dan haka a shiga bincike
dakinsa. Na samu nasarar gain hotunan Hubba da ya shirya tura masa cikin jin dadì
na kwashesu na ajiye nawa da wasikar nan na sake sabon manne envelope din. Gudun a
yanka ta tashi na kone hotunan Hubba a cikin toilet batare da sanin kowa ba…. Kamar
yanda Akhi ya fada ya aika sakon Miran Haysam batare da sanin na canja hotuna ba.
Kwana biyar tsakani sai ga masu neman aure sunzo. Hankalina ya tashi naita kaikawo
da neman hanyar da zanji yaya akai amma ban samu ba. Dole na hakura har bakin suka
tafi Abbie da Akhi suka shigo gidan. Cikin muryar damuwa najiyo Abbie na sanarma
Ummu cewar maganar da sukayice ta taso, sai dai sabanin Hubba da su suka zaba shi
yanzu ya aiko cewar Bushirat, harma sun rasa a ina ya sanni. Kokwanton da suka
shiga yasa Akhi tashi da kansa zuwa masarauta dan tabbatar wa. Amma magana daya ce
dai Bushirat ya zaba. Babu alamar damuwa akan fuskar Ummu tace ai duk kai da kaya
mallakar wuyane ALLAH yasa haka shine mafi alkairi, dan itama dai batai magana bane
kawai amma abin na damunta. Kar ace dan Hubba yarta ce aka tsallakeni aka bata
alhalin nice babba. Oho ko dar banji da kalamanta ba, ni dai tunda burina ya cika
damuwa ta kare. An shiga shirye-shiryen biki, yayinda niko keta nokewa kamar bana
so dan harda kukana. Sai gashi su Abbie sun zubda makaman su sun koma lallashina.
Da wanna salon nai amfani na cinye wasan akan bikina cikin kwanciyar hankali kowa
na lallabani. An kawoni masarautar ruman masarauta mai abubuwan kawa da na birgewa.
Duk da na tashi a gidanmu akwai kudi sai naga ashe muma yayan malam Shehu ne dukiya
na'a inda take. Abu na farko da bai munba shine dole na zauna a kasan ikon Malikat
Haseenat mai amsa sunan mahaifiya ga mijina, sai dai kuma babu yanda zanyi dan ta
hakanne kawai zan samu yanda nake so. Na hakura na mika wuya anan dan koba komai
tana nunamin kauna babu bambanci da yayanta. Abu na biyu shine Ashwaq a matsayin
uwargidana wadda kowa ke jingina zamanta Malikat. Na shiga damuwa matuka a kanta
tare da neman hanyoyin dakile al'amarin ta. Ban gama da itab ba aka auro Danish-
Ara. Wannan shine mataki na farko da ya hada alakata da UWA. Dan tun sanda naji
labarinta da dambarwar dake faruwa tsakaninta da Mammah a daura dammarar neman
kusanci da ita. Nako sami nasara ta hanyar amintaccen hadimin Haysam, bayan na
shaka masa makudan kudade amma ya nunamin har abada bazai ci amanar shugabansa ba,
raina ya baci dan haka na koma barazana akan iyalansa, harma na aikata masa a
aikace ta hanyar sakawa matarsa ta kawo min diyarsu daya da suka haifa sashena. Na
tabbatar masa zan kasheta wanna shine dalilin amincemin badan yaso ba ya hadani da
uwa. Na razana a ganin farko dana mata, dan mutumce mummunar gaske, da zaka iya
rantsewa badaga yankin wanna kasa ta fito ba koma na dake zuciyata. A ranar batako
kulani ba, hasalima korani tai wai ban shirya ba. Naji zafi amma na daure harda
dukawa kasa ina bata hakuri akan laifin da ban san nayi ba. Bata dai kulanin ba
haka na taso na taho. Na shiga damuwa dan tun daga wanna ranar bata sake yarda mun
haduba har tsawon wata uku. A haduwa ta biyu ma dai bata kulanin ba sai da ta mula
dan kanta sannan ta dubeni a kaskance da fadin, "Kije ki daina sallar la'asar dan
kin shirya kasancewa da Uwa mai share kukan masu kuka". Na mata godiya na taso.
Banyi wani tunani ba na fara bin dokarta har tsawon watanni uku. Kawai wata rana
sai gata da dare ayam ta bullomin ta bango. Hankalina ya tashi na tsorata amma
tsawar data mun ta sani nutsuwa. Cikin jan tsaki ta furta a haka zaki iya zama tare
da uwa kina matsoraciya, Sosai na dake zuciyata wajen bata amsar ni ba matsoraciya
bace. Ta sake maimaita min nima na maimaita mata nawa. Munyi haka har sau uku kafin
ta kyalkyale da dariya da fadin, (Ke abokiyar tafiya ce. Mike tafe dake wajen
uwa?). Cikin matukar farin ciki na qyara zama, na shiga zayyano mata haihuwa nake
so, dan ina son zama Malikat bawai Zawjata-almilk ko Ameera kawai ba. Ni wannan
matsayin duk yamin kankanta. dariya sosai ta shiga babbagawa har sai da na koa dan
haushi amma dai na hakura na shanye. (Lallai ke abokiyar tafiya ce). Ta fada tana
nunani har lokacin fuskarta da sauran daiyar. Murmushi nai mata cike da jin dad. Ta
cigaba da fadin, (Nice da kaina na hana Haysam haihuwa saboda abinda uwarsa ke mun,
idan tana takama ita Malikat ce dan ta haifi Miran mai jiran gado na shirya
tabbatar mata komai a gidan nan sai da karfin ikona yake tabbata). Hakuri na dinga
bata nidai, dan babban burina kawai bukatata ta biya nidai. Cikin tabe baki ta
furta, (Ai kin wanke komai yar gari, indai zaki iya bin sharadinmu ki dauka kece
Malikat a wannan karnin). Babu wani tunani nace na amince da duk wani sharadin ta
tunma kan ta fada min su. Nan ma dariya tayi sosai kafin ta ajiye min wata takarda
da koko mai dauke da jini wai a saka hannu da wannan jinin, itama zata saka wannan
itace yarjejeniyar mu ta farko, Banji ko wani dar ba na saka ta saka. Ta bani daya
ta dauki daya tana fadin, (Daga yau sunanki a wajenmu shine *_Ta-kurya_" ta kurya
sa maza kurya kenan). Yar dariya nai ta farin ciki itama tana tayani. Ta wuce a
ranar batace dani komai ba acewarta sai zama na biyu. Na matukar nustuwa a sati na
uku da babu ita babu labarinta, dan haka na shiga bulayin nema. Harma a fiddla rai
ranar kawai sai gata ayam ta kawo min ziyarar dare kamar wancan lokacin. Kafin nace
komai ta tabbatar min doka ta biyu bayan suna dolene a duk sanda ta bayyana a
gareni zansa gwiwuna kasa dan girmamawa a gareta, sunan da zan dinga kiranta da shi
shine uwa. Nan ma babu musu na amince mata. Nanma dariya tayi kafin ta ajiye min
kullin garin magani guda biyu. (Wannan sune maganin matsalarki Ta-kurya, daya zaki
sha daya ki shayar da Miran Haysam. Ina mai tabbatar miki kafin watan ya mutu zaki
samu ciki) na matukar kasancewa a farin ciki, sai kuma nai sansarakwai da ga baya
na jeho mata tambayar to amma idan ya kasance wata a cikinsu nada ciki fa ko kuma
muka samu cikin tare na haifi mace ita namiji?…✍️

DAUDAR GORA
Book2
86
-."Anan ma dai tayi dariya da fadin (Ke ta dabance ta-kurya, sannan kanki na kawo
wuta fiye da yanda nake bukata). Naji dadin yabonta harda godiya ta. Wasu
magungunan ta sake bani, ta tabbatar min nai duk kokarin da ya dace na shayar da
Ashwaq da Danish-Ara. Na mata godiya nan ma ta sake bace mun. Na shayar dasu
maganin su duka uku nima kuma na sha wanda ta umarceni, sai dai kuma washe garin da
Ashwaq tasha nata akawayi gari tayi barin cikin da ni ban taba sanin da shi ba.
Ranar nayi farin ciki sosai, a wani gefen kuma ina mamakin toda miye na boyewar da
tayi? A nufinta da karmu taba sani sai ranar haihuwa kenan? Lallai kasancewata da
uwa alkairine. Abu mafi kara sakankancewa da uwa shine bayyanar ciki a jikina kafin
cikar wata gudan data fada. Nayi farin ciki nayi farin ciki, duk wani masoyina ma
yayi farin ciki. Itama kanta uwa tazo ta tayani farin ciki tare da sake kawo min
wasu magungunan dazan na amfani da su har na haihu. Tace kariyane ga abun cikina
dani kaina. Dan suma su Ashwaq zasu iya kawoma cikin nawa hari. Na yarda da ita
fiye da kowa da komai a duniya zuwa yanzu, dan haka babu wani dar a tare dani na
amsa. Haka na cigaba da rainon ciki, tare da soyayyar da ban taba zato da tsammani
da ga Haysam ba. Ashe haka yake tsananin so da kaunar haihuwa. Hakama mahaifiyarsa
da yan uwansa su Ammarah kowa tattalin rayuwata yake yi, Masarautar ma gaba daya
wani irin girmamawa akemun data kara sakamun kaina fadì da jin babu kamar uwa a
tare dani a wannan duniyar. A haka watan haihuwa ya kama mun, kowa fatansa ALLAH ya
saukeni lafiya, ni kuma babban fatana na haifi da namiji, dan inata fargabar
tambayar uwa hakan, kar tacemun bata da tabbaci. A haka dai na wayi gari wata
safiyar laraba ina nakuda a tsaitsaye, uwa ta gargadeni fadama kowa, dan haka naita
dauriya sai Jasrah dake nane dani, idan taga ina murkususu taita kuka, idan ya
lafamun ta sani gaba da tambaya naita dai lallabata. Har safiyar Alhamis babu
haihuwa babu alamarta, ranar mana cinye wannan yinin a wannan wahalar babu wanda ya
farga har dare, dan ko Ammarah dake tare dani naki barin ta sani. Sai zuwa dare da
ya ke tafiya daren juma'a kenan ina tsaka da shan murkususu na sai ga uwa. Naji
dadin zuwanta, dan koba komai ina saka ran taimakonta. Tako zomin da taimakon sai
dai ta hanani, acewarta yau ne ranar da zata sanarmin sharudanta, idan na amince
zata bani maganin da zan haihu lafiya kuma da namiji da zai zama magajin kujerar
Shahan-shan, idan kuma na bijire zata barni tai tafiyarta babu kuma tabbacin zan
rayu balle dan, idan kuma na rayu na haifi mace ta warware abinda taima su Ashwaq
su sami ciki wata a cikinsu ta sami da namiji, dan dama dai tun farko ita ta hana
Haysam haihuwa saboda abinda Mammah take mata. Cikin riko da magiya nace mata dan
ALLAH ta bani, indai nice na amince, koma mi tazo da shi zan amsa. Sai da ta
jadadada min sau uku nima na
amsa mata sau uku. Maganin ta bani nasha kadan ta karbe abunta sai ko na samu
lafawar ciwon, harna samu damar zaman saurarenta. Ta ce da ni (Bushirat ke ce kika
kawo kanki gareni ban gayyatoki ba, kika kuma zo min da bukatarki ta magance miki
ita?) Kai na daga mata alamar hakane, taci gaba da fadin (Gadai abinda kike nema
nan kin samu, da ga yau zuwa gobe sunanki ya koma *_MALIKAT BUSHIRAT ne, zaki samu
girmamawa da ga kowa. Ada nayi alkawarin hana Haysam gadar sarautar kujerar Shahan-
shan, dan in har bashi da magaji ko ubansu mutuwa yay bai isa hawa ba. Amma a yanzu
saboda ke na janye komai, Zan hukunta Abdul-majeed da Haseena akan laifukansu su da
zuri'arsu, amma ke kam kin tsira keda danki, zan baku gata zan maidaku yan lele)
godiya na mata cike da jin dadi. Cigaba tai da fadin, (Sharadina na farko bayan kin
haihu zan dauke mahaifarki gaba daya, dan wanna dan kwara daya ya isheki yakar kowa
a masarautar nan, sannan haihuwarsa shi kadai a nufin shine kawai magajin wanna
masarauta) na amince Uwa. Na bata amsa babu wani tunani ko kyakykyawan nazari.
Murmushi
tayi tamun jin jina. Ta cigaba da fadin, (Sharadi na biyu bayan haihuwarsa zakiyi
yankan bakaken shanu guda goma, rakuma mata da basu wuce shekara uku da haihuwa ba
suma goma zaki soke. Sai bakaken karnuka) anan ne na dani diri-diri da jin karnuka,
amma sai tai saurin fadin (Karki damu su wannan karnuna zaki yankasu domin kariyar
duk wani cutarwa da wani zai kawoma danki ne, dan kina haihuwar magaji tofa babu
mai zama haka kuma bayanki za'aita yunkurin gani ke da dan) hakane kuma uwa. Na
gane mi kike nufi na amince. Na bata amsa cike da gamsuwa da bayanin ta. Nan ma
tayi murmushi da cigaba da fadin (Zaki cigaba da wannan yanka ne duk bayan watanni
shida, sannan zaki sadaukar da jinin macen hadima mai dauke da ciki karami bayan ya
cika wata uku, idan ya kara wata wata ukun zaki sadaukar da hadimi mai sabon aure
da basu wuce wata daya ba shima) nan ma nadan shiga rudani amma ta nunamin idan
bana bukata zatai gaba, ai duniya babu abinda ake iya samu cikin sauki. Sannan kuma
bawai tace na kashesu bane da kaina, nawa kawai shine bata sunansu, sauran aikin
nata ne) nifa matsalata kawai shine a haifi magaji, na zama abar kwatance akan
karfin iko fiye dana Malikat Haseenat dan haka na amince. Ta cigaba da fadin
(Saradi na biyu lokacin da yake cika shekaru goma sha biyu a duniya zakiyi kokarin
a hada aure tsakanin wani makaskancin talaka da wadda kukafi shakuwa a kannen
Haysam idan an samu ciki aka samu kuma mai tambarin zuri'arsu a gado bayan kwana
uku zamu amshe yarinyar, inma babu tambarin ma dai ahakan zamuyi, za kuma mu kauda
Abdul-majeed a doron duniya Haysam ya gajesa. Haysam zaiyi mulki na tsahon shekarun
girman danki, yana cika shekarun gadar mulki zaiyi murabus ya daurasa. A ranar
nadin zamowarsa Shahan-shan za'a aura masa mata hudu, matan nan dukansu zasu zama
sadaukarwarmu tare da Haysam, dan in har yana raye tofa zaki cigaba da zama yar
kallo ne sai abinda Haseenat tace danki ma yayi zai yi.…..) Da sauri nace na
amince, dan bazan taba iya cigaba da zama karkashin ikon wata ba bayan kuma dana ke
mulki. Tayi murmushi a lokacin da fadin (Shiyyasa nake jinki kamar yar dana haifa a
cikina ta-kurya. Zan saki ki zama mai nasara kuwa bisa nasarar kowa. Wannan yaro da
zaki haifa zai cigaba da aure muna kauda matan har sai sun cika adadin da zasu zama
ginshikin rike karagar mulkinsa. Da ga karshe zamu kawo masa matar aurensa da zata
zama duk wani motsinta sai da umarninki ne, koda ta haifa masa magaji kece zaki
cigaba da amsa suna MALIKAT. Dan hatta shi a karan kansa ko hukunci bazai iya
zartarwa ga wani ba sai da umarninki. Ki kula ki nutsu kisa hankali a jikinki a duk
aure-auren sa kada ya auri wata mai alaka da zuri'arsa, idan kuma har kikai hakan
to komai ya lalace kenan, duk wahalarki ta tashi a banza, mu kuma bazamu taba amsar
kuskure ba, in har kika
gagara cika wadan nan sharucidan namu zaki bamu
madadinsu ne da jinin abinda zaki haifa, dan shine diyyar kuskurenki. Kuma shine
hukuncinki) hankalina ya matukar tashi dan duk duniya a yanzu babu abinda nafi so
kamar abinda ke cikina din, a shiga rokonta da magagiya. Ta tabbatar min itafa
saina kuskure mata ne zata aikata hakan, dan bijirewar Abdul- majeed ga ayyukanta
bisa shishshigin matarsa yasa zatai masa hukunci da mutuwa da mutuwar dansa
(Haysam) da ya fi so, zakuma ta tabbatarma Mammah ita ba komai bace a wanna
masarautar shiyyasa ta hanyar yayan da take takama da su, dan haka Ammarah ce zata
zama wadda za'"aima auren sati biyu ta haifi yar da muke bukata, dama ta kashe
Miran Nayyar a cikin ruwan swimming pool na gidan, Waheeda kuwa dama bawani tanada
zuciya mai kyau bane kanta kawal ta sani dan haka bata gabanta, Jin wanna kashe-
kashen hukunci da zatai ga zuri'ar Mammah saboda abinda Sukai mata a bijirewa yasa
na karajin tsoronta, dan haka na amince ga dukkanin shardanta. Ta bani magani
nasha, tare da tabbatar min zata kaworin hadimar da zata kasance amintacciyata
wajen gudanar da ayyukana. Dan dolene zan boye kaina tsahon rai batare da kowa yama
taba kawowa kansa nice ta-kurya ba. Koda kuwa a cikin hadiran da zasu dingamun aiki
ne matsayin ta-kurya, Bayan tafiyarta haihuwa ta tashi gadan-gadan, Alhamdullah na
haifo yarona namiji mai kamanina dana Haysam. A hankali, abinda duk ta fada ya
cigaba da tabbata, babu wata matar Haysam da ta kara koda kwatanta samun ciki, dan
haka na kara sakankancewa da ita, duk kan umarninta na fara cikasu kamar yanda ta
bada, kuma komai na tafiyamun babu wata damuwa har zuwa lokacin da aka dauke Eshaan
daga gabana. Ta nuna bacin ranta, kamar yanda na nuna damuwata, sai dai duk wani
kokarin mu babu wanda ya saurareni, da Mammah ce ma, itama daga baya ta bada goyon
bayan dauke san. Duk da tafiyace ta wani shekaru naji zafinta, sai dai bana iya
cika wata guda banje na dubeshi ba. Yawan zuwana yasa Abbu (Tajwar Abdul-majeed)
yayi magana a lokacin, aka kuma sakamun dokar sai bayan shekara-shekara. Naci kuka
a ranar amma uwa ta kwantar min da hankali akan daukar mataki da tabbatar min ba
sai yana raye dokar zatai aiki ba.Lokaci yayi da Ammarah zatai aure. Da taimakon su
Miran Jasim aka cika wanna aikin, bayan wucewar su Mammah Umrah. Anyi auren Ammarah
an kuma samu cikar burin samun ciki. Bayan dawowarsu an kwashi rikicin da har yay
sanadin kai Jasim kurkuku. Da ga baya dai komai ya lafa Ammarah ta haihu. Bayan
haihuwarta abubuwa suka nema cabewa dalilin samo wani hatsabibin mutumn, sai dai
duk da haka muni nasarar mallakar abinda ta haifa da kuma kauda Abbi (Shahan-shan
Abdul-majeed) nafi kowa jin ciwo da shiga tashin hankalin abinda akaima Uwa a
masarautar nan dan ranar ni nasan irin kukan da naci na tashin hankali. Kwatsam
bayan na gama fidda rai da rasa uwa a wata raar da Haysam ke cika shekara uku da
hawa karagar mulki sai ga uwa ta bayyana.Farin cikine ma da bazan iya musaltashi
ba, itama har taitamun dariya, ta kuma nuna jin dadinta da yanda na damu da rashin
ta, ashe tanada y an leken asiri da ke kai mata rahoton komai a shekarun nan da
bata nan…✍️

DAUDAR GORA
Book2
87

…..……….Bayan dawowar uwa al'amuran mu sun cigaba da tafiya, dukan shardanta a


cigaba da cikasu, dan dama ko bayan batanan ban fasa ba, dan ina tsoron abinda ta
fada akan Saiful-malik ya tabbata. Dan wannan tsoron da son cimma buri ne suka
jagoranceni har zuwa wannan lokaci. Ni naita zungurar Haysam akan yin murabus
lokacin da Saiful- malik ke cika shekara talatin da uku a duniya, nayi hakanne kuma
bisa umarnin uwa. A duk sanda nai maganar yakan yi murmushi ne kawai, amma baya
cewa dani komai, Sai hakan ke cimun rai da tunanin baya son ya sauka ya daura
Eshaan din ne. Ni kuma abinda nake hange adadin shekarun da Uwa ta tabbatar min zai
rasa ransa a dalilin shayin da nake shayar da shi gabatowa suke, ta kuma tabbatar
min infa ya mutu ba'a daura Saiful-malik a karagar mulki ba akwai rikici sosai,
domin Haysam nada kanne, shekarunsu kuma sunfi zama shekarun hankali da yan kasa
zasuyi jayayya da samun rabuwar kai akan magajinsa Eshaan. Na sake takura masa da
tada hankalina akan hakan har takai wata rana ya furta min abinda ya girgizani. Ya
ce (Bushirat basai kinyi gaggawa akan mutuwata ko rayuwata ba. Idan kaddarar mulkar
kasar ruman na rubuce a littafin kaddarar Eshaan sai yayi ko ina raye ko bana raye,
abinda na sani kawai ina matukar tausaya masa, ina tausaya masa yaki na cikin gida
da waje. Yakin da zai masa matukar wahala musamman kasancewarki ke wa mahaifiya da
kika zamto a cikin manyan makiyansa) rai bace nace ban gane ina cikin manyan
makiyansa ba? Bai sake cemin komi ba, illa murmushi kawai da ya saba mun. Maganar
ta zauna min a rai matuka, har ta kaini da fadama uwa. Itama naga alamar ta
girgiza, dan haka take anan ta tabbatar min dole muyi motsin da Haysam fa zai bada
mulkin nan sannan mu kaudashi, dan alamominsa na nuni da akwai abinda ya sani game
da ni, idan kuma har mukai sakaci wahalarmu ta baya zata zama a banza. Babu wani
damuwa a raina na bata goyon baya, dan saima tashin hankali da nakeji akan cewar
Haysam yasan wani abu game da ni din, ina tsoron ya fadama mahaifinmu, dan wilhy
zai iya tsireni ne kawai kasancewarsa mutum mai zafi da bin dokar addini. Haka
akai, ta kawo abinda naita saka masa a madara yana sha har tunaninsa ya karkata a
yin murabus, babu zato babu tsammani kawai ya dawo da Eshaan gida, ya kuma tabbatar
da zai yi murabus ya daurasa a karagar mulkin Shahan-shan. Kalubalen dana so
fuskanta shine Eshaan da kansa, dan yaso bijirewa da cewar shifa baya son mulkin
nan, bai taba ma birgesa ba, yafi son rayuwar yanci, yayi abinda yake so a lokacin
da yake so, a cikin tarin burukan rayuwarsa ma babu maganar mulki a ciki. Na tashi
hankalina Uwa tace na kwantar, ta bani wani turare tace na basa kyauta, in har yay
amfani da shi na kwana uku sai ya amince. Hakan ce kuwa ta kasance. dan satin bai
shigeba sai gashi da cewar ya amince. Uwa ta kara shiga raina da jin bani da
kamarta duk duniya, zata kuma iya sakani komai nayi amma banda sadaukar mata da
Eshaan, dan shine abinda nafiso fiye da komai a duniya. Anyi nadin sabon Shahan-
shan tare da shagalin bikin aurensa na mata hudu, ko sau daya bai tanka akan auren
ba, baice bai son su ba bai kuma ce yana so ba. Ni kuma bam ma damu da tambayarsa
ba tunda nasan makomarsu. Kamar yanda uwa ta fada Haysam ya shude, matan Eshaan ma
daya bayan daya sun zama labari, an cigaba da auro masa was suma tarihinsu na
shudewa, a haka har nazo gab da cikar burina na gama wannan sharadin. Rana tsaka,
ina gab da cimma abinda na faro kwatsam yarinyar ta shigo rayuwata. Ba kai tsaye ta
shigoba, dan bana jin ma ta sanni ita. Yaki ta shirya, ya ki domin yakar Eshaan
saboda rasa yayunta biyu da suka shigo cikin aikina. Itama tanada tunani ne irin na
sauran mutanen kasar ruman akan Saiful-malik ne ke halaka matansa. Wanna itace
mafarin matsala, dan tunkan ta shigo ita nacema uwa ta kauda min ita, dan ina a
gabar da zuciyata ta gama dakewa da bushewa zuwa yanzu, hatta hadiman dake mun
ayyuka da sunyi kuskure mafita daya nake hangoma kaina shine kawai na kaudasu, idan
na kaudasu matsalata ta kare kenan. Da nayi din sai inga ta kare kuma, dan haka
nake kallon kashe duk wanda ya shiga gabana akan cikar burina kawai na kauda san
Uwa ta tabbatar min babu kaddarar mutuwar yarinyar a wannan tsakanin, sai dai mu
nemo wata hanyar, a cikin neman mafitar ne muka yanke zamowarta a daya da ga cikin
matansa, domin a ganinmu idan ta matso gab da mu sai munfi cin nasara a kanta. Sai
dai kuma al'amarin bai kasance yanda mukai hangesa ba, dan tunda ta shigo rayuwar
gidan komai ya daina yiwuwa a cin sauki. Labarin farko ya canja zuwa wanda bashi
muka tsara ba. Dan hatta madarar farko da nake shayar da duk Zawjata-almilk ita kin
sha tai, alkyabba da turaren da nake badawa a musu wanka da shi a sako musu tun
daga gidansu shima basu akai mata ba, ban hakuraba na bibiyeta da su nan ma taki
yarda tai amfani da shi, duk ta inda muka bullo sai ta waske, da ga karshe ma wata
rigar da mu bamu san ta ina ta fitoba ce ta sanya, daga haka ta koma sashen Mammah
da zama, ita kuma ta kaita sashen Saiful-malik batare da shawarar mu ba bayan mun
yanke a yanda zamu mata rakkiya zuwa can. Dan saboda na rabota da sashen Mamma da
uwa bata iya zuwa yasa na bada shawarar maidata sashen Saiful-malik ta mana
bincike, amma sai Mammah ta canja shirin namu gaba daya. Wannan abu ya konamin rai
matuka, ya kuma zafi zuciyata na kasance a bakin ciki. Mairakon nasara komai sai
sake tabarbarewa yake, da kyar muka samu cikon ayyukan mu akan Zawjata-almilk data
tarar, Itako dai ta kasa tabuwa a garemu a duk ta inda muka bullo. Tun ana yakin
sunkuru har komai ya fito fili da fitar da ban san mafari ba da ga gareta, yakin ya
koma na kasanni na sanka......" ta rushe da kuka mai karfi. Sai da tayi mai isarta
babu wanda yace mata ko kanzil sannan ta cigaba da fadin, "Babban tashin hankali na
a yanzu da jagorantar dukkan karfin halin iya maida martanina ga uwa a wannan gabar
da komai na tabbatar da ya lalace shine rasa Saiful-malik, ta sake tabbatar min sai
sun amshi jininsa matsayin diyyar kin cika shardansu, bana son na rasashi, shine
kadai ya kuka ya sarketa ta kasa cigaba. Jasrah ma kuka take iya iyawa, sauran yan
uwanta kam tagumi duk sukayi kawai. Hankalin Iffah gaba daya akan Tajwar Eshaan
yake, dan tunda ya dukar da kansa da kamo hanunta ya rumtse a cikin nasa har yanzu
bai ko yi wani motsin kirki ba, hannun nata kuma na rumtse a nasan duk da azabar da
takeji saboda yanda yake matse a cikin nasan haka ta cigaba da daurewa tana mai
ambaton addu'oi da duk sukazo bakinta. Fatanta ALLAH ya saukaka masa zuciyarsa, ya
bashi juriyar dauka.

Gyaran muryar kaka ne ya katse tunanin kowa. Ya nisa a hankali tare da gyara
zamansa. "Lallai kinyi kuskure, kin kuma shiga rigar yaudara irin ta wadda bokaye
kanyima bayin ALLAH saboda son zukatanmu da burin gina DUNIYA mai yankewa. Wannan
mushirika tai tasiri da tasirin gurbataccen burinki ne da niyyarki ta shigowa
wannan gida. Amma karya take bata da alaka da samuwar cikin Shugabamu da kikayi,
dan dama sanda ta baki maganin kina tare da shigar cikinsa…....

Babu wanda bai zabura ba, hatta da Malikat Bushirat din kanta. Tajwar Eshaan kam
sake kankame hanun Iffah yay cikin nasa tsam-tsam fiye da farko.
Kai Kaka ya jinjina musu, "Wanna maganar da nake fada muku haka take, dama akwai
cikin. Koda ace babu shi ta bada taimakon magani shi wannan maganin sai dai ya
magance matsalar wani ciwo da ya zama sanadin jinkirta samuwar haihuwar bawai ya
samar da dan ba. To sai a wannan labarin ma akwai samuwar cikin ma kafin ta shigo
cikinsa. Rashin samuwar haihuwa jarabawace ga duk wanda baiyiba, jarabawa kuma mai
ciwon gaske da radadi a zuciya, bazaka fahimci haka ba sai in ka kasance daya daga
ciki. Ya halatta ka nema magani da ga kowace irin cuta a rayuwa. Sai dai fa akwai
matakan da ya kamata mumini yabi wajen neman magani kowane irine balle ma akan
neman haihuwa. A duk lokacin da muka rasa haihuwa idanunmu kan rufe da fadi tashin
neman mafita ta kowanne yanayi. Burinmu shine kawai mu haihun. Sam babu tunanin
maybe ita haihuwar ba alkairi bace a tare damu, a ganinmu kawai mun rasa shine mu
nemota ta kowace irin hanya. Duk da abinda UBANGIJI ya baka ya fika sanin dalilin
baka shi, idan kuma ya hanaka ya fika sanin dalilin hanaka da yayi. A rayuwa babu
abinda yafi karfin addu'a, sadaka, yarda da kaddara mai kyau ko sabaninta. Idan
kuma har ta kama saika nema maganin ka zama sani ba a wata gabar. A neman haihuwa
wajen bokaye da malaman tsibbu zakaci karo da abu hudu in har ka samu daya da kaje
nema. Na farko rasa imaninka da cire yardarka ga UBANGIJI mai badawa da hanawa, dan
zaka cigaba da ji a ranka shifa wanna din nan ne ya baka wannan haihuwar
(Wa'iyazubillah). Na biyu zata iya yiwuwa dan aljani ma aka samar a cikin naka
batare da kasan hakan ba kai tunda kai a kai kanka ai. Na uku wasu matan ko da
saninsu, ko bada saninsu ba zata iya yuwuwa bokan yay mata cikin a zahirance ko
kuma ta hanyar tsafe-tsafen sa batare da ita tasan hakan ta kasance ba domin shi
tsafi gaskiyar mai shine. Idan kuma ALLAH yasa dama ana a kan gabar da ALLAH ya
iyakance ne dama haihuwar
tata ta kusanto gareta batare data sani ba sai a samu dai-daito da bada maganin
nasa haihuwar ta samu amma zuciyarta na tabbatar mata ta sametane daga wannan bokan
ko malamin tsubbun……..✍️

Mu hadu in ALLAH ya kaimu Please🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴 hannuna ya gaji😂

DAUDAR GORA
Book2
88

."Kamar dai yanda ta kasance a gareki. Ita tana da buri akan wannan masarautar, sai
akai sa'a ke ma kinada naki burin da kika kai kanki gareta. Ita kuma sai tai amfani
da haka kika zame mata yar aiken isar da sakonta ta yanda babu wanda zai fahimci
ruhinta ya sake dawowa wanna masarauta balle ma a zargeta akan dukkan abubuwan da
suka faru har a maida hankali. Wanna labarin naki yasa na fahimci maganar mahaifina
da ya ce, duk saninka kankanuwar samarwace da ga taskar ALLAH da bata yankewa.
Sannan haihuwar ita Fhareedah wani mashine da ga UBANGIJI da zai zama sanadin
tarwatsa al'amuranku batare da kun fargaba, shiyyasa ya boyeta a cikin sirrinsa har
zuwa ranar da
zata dawo gareku cikin karfin ikonsa da zai tabbatar muku babu wani karfi da ke
saman nashi. Shirka babbar faduwa ce, ginshikine na gina kaskanci a duniyar bawa
dama lahirarsa. A duk lokacin da ka dauki cewar wanin ALLAH a iya baka koda
kariyane da ga wani abin tsoratarwa to akwai babbar matsala,dan kuwa shi wanna
mushirikin zai bika mataki-mataki ne wajen kaika fie da inda bakai hange ko
tsammanin zuwa ba. Kamar dai ke din nan. A matakin farko bukatar haihuwa kikaje
mata da shi, sai ta ce miki kada kiyi sallar la'asar. Tayi hakane saboda
kasancewarki mai bautar ALLAH, sannan kina jingine da wasu muminai da zasu iya
saurin fargar dake kuskurenki kuma ki gyara. Amma data kafa miki wannan tarkon sai
ta busar miki da zuciya ta yanda duk yanda za'a kiraki bazakiji wannan kiran ba, ba
kuma zaki saurari mai kiran ba koda ace kin jisa. Hanaki bautama UBANGIJI itace
allurar farko mai tsananin dafin data sakaki shagaltuwar da bijire mata zai miki
wahala koda ace kina so. Shiyyasa maganin ayima kar a fara, tun farko ma yi kokarin
yin addu'a da yakar kanka daga son zuciya ko tunanin nema daga wanin ALLAH. Miyasa
musulunci ya mana gatan cewa mu tashi mu nemu na kammu? Saboda kare kammu da ga
biyayya ga abinda zai iya cutar damu. Dan a mafi yawa ko nace rinjayen dan adam
yana son a duk sanda ka nema daga garesa duk sanda wani abu ya taso da zaka iya
masa to ya tuna maka wannan taimakon da yay maka wanda zai iya sakaka jin kunyar
yimasa abun nan koda ace bai dace ba. Kamar dai cin hanci da rashawa. A duk lokacin
da mai bada cin hanci ya mika ga mai karba zai iya aikata aiki komai muninsa koda
ace zai iya cutarwa ga rayuwar mal karbar shi kansa ne ma. Dan haka maganin data
baki a tun farko ma bashi da alaka da abinda kikaje neman. Ta baki shine domin
cutar da abinda ke cikin ki data riga ta tabbatar da akwai. Sai dai ALLAH ya riga
ya kaddara babu abinda zata iya yi sai ya zo duniya, dan haka ta tafi mataki na
biyu wajen rabaki da mahaifarki gaba daya. Mataki na uku ta rabaki da mijinki,
mataki na hudu tai amfani dake wajen gogama rayuwar danki bakin fentin da zai
bakantashi ga al'ummar kasar sa da mulkinsa. Lokacin da ake ihun yay murabus badan
Iffah ta shayar da shi wannan madarar mai dafin macizai ba da burinta a tsigesan,
hakan yana cikin plans dinta da idan wanna baiyi tasiri ba zata tsallaka na
gabansa. Da ace taci nasarar kun hada auren wadda taso ta haifi magajinsa da taci
nasarar duka wasan. Dan sam wadda take burin ya aura bama mutum bace cikakkiya yar
zuri'arsu ce aka raina a anan duk saboda zuwan wannan lokacin. Daga kuma sanda ta
samu ciki burinta shine ta kasheki, shima ta kasheshi wanna jinjirin ya amsa suna
magaji, da ga haka ta karbe mulkin ta karfin tuwo da ga wanna ahalin. UBANGIJI bai
gitta rayuwar Iffah a cikin al'amurran ki da rayuwar danki ba sai dan shi
tsarkakakkene mai tarin tsoron ALLAH da kiyaye dokokinsa. Ya gadar da shine da ga
kyawawan halayyar mahaifinsa sabanin naki dabi' un. Addu'oin da al'umma ke masa na
tasiri a tare da shi tare da yin dubi da tsarkakakkiyar zuciyar kakarsa da tai yaki
da yakar mushirikai. Mutuwar mahaifinsa da kakansa tazo ne akan gaba bawai bisa
karfin ikonta ba. Da ace ma tayi hakuri zasu musu, tabbas zasu mutu a dai-dai wanna
gabar har su matan nasa. Amma a yanzu hakkin ruhinsu duk ya rataya a gareku ke da
ita domin harda amincewarki akai komai ba tilastaki tai ba a aikace.Kaiconmu da
irin wannan burin duniya, kaiconmu da irin wannan hangen da babu hango iyakar
karewarsa, kaiconmu da zuciyar da ke jin hakkin wani ba komai bane komai
Kankantarsa komai rashin muhimmancinsa, Wlhy duk
abinda akace maka ba naka bane sunansa ba nakan ba. Idan kuma harka taba da son
zuciya ko izgili sai ka biyashi a ranar da babu kudi irin madadin a duniya. A ranar
da cuniya ce zata taru, a ranar da ake biyan hakki da lada ko zunubi. Dan duk
hakkin wanda ka taba zaka biyashi da ladanka, idan baka da lada za'a dibo zunubinsa
a lafta maka. Shiyyasa mutane da yawa zasuje lahira da tarin lada a taskokinsu,
amma yayin kammala musu hisabi sai su koma basu da korai sai tarin zunubai dan an
biya duk wanda suka cima hakki da wanna ladan nasu. Haba yan uwa har wane aiki muka
tara da har mukejin cin hakkin wani zai isa mu biyasa har mu sami rarar shigar
aljanna da sauran. Wani ma har kaji yana izgilin shi hakkin wani ko ALLAH ya isa
bata masa komal a jiki, why da tabon da zatai maka a rayuwarka gara ace a jikinka
take tsirowa maybe kaji tsoron ALLAH da wuri ka sauke hakkin. Shi kuma wanda ma ya
hadiye bai ce dakai komai ba yafi ban tashin hankali fiye da wanda zai furta maka
maybe ka razana ka sauke. Wai miyasa bama tunanin cewar wanda muka cima hakkinsu
sune masu nasara akan mu ne? Tabbas masu nasara a kammu, dan sun kasance masu
ajiyewa a dauka a kuma biyasu a ranada ake farautar ayyukan cika mizani. Kawai akan
son farantama was mu mu tauye kammu mu daga nasarar wasu. Wai a hakan dan wawanci
murna mukeyi, farin ciki mukeyi mun karya wane, mun kaskantar da wane, mun maida
wane baya, waya fada maka dariya ya kamata kayi ko kiyi?Wlhy kuka, kuka ya kamata
ki fara tun kafin ganin anar nasarar mai wanna hakkin da taki faduwar,Wadan nan
hakkokin da muke rainawa suke hauhawa
su gawurta su zama manyan abubuwan ruguza ayyukanmu. Kamar dai ita, ta fara ne tun
a kuruciya, zalinci wancan, tirsasa wancan ana gain yarintace hakan ba komai bane
amma sai abin ya cigaba da tasiri a rayuwarta har yay gawurtar da ayanzu ta fado
kasan-kasan kafafun wadan da take gain ba komai ba, wanda take ganin murjesu ta
taka ko cin hakkokinsu ba komai ba. Gadai shi taji dadin, tayi farin cikin, ta
dauki kanta a mai nasarar, amma a karshe itace ta zama mara nasarar, mafi
kaskanci.Mafiya masu cin hakki da ruguza rayuwar wasu zamu samu matasane masu
tasowa, maybe batai aure ba ko baiyi aure ba, kokuma bata jima da yin auren ba,dan
duk wanda, ko wanda ya kai shekaru arba'in a duniya ya zabi take hakkin wani babu
babban wawa sama da shi. Amma su wadan nan masu tasowar gani suke abinda sukeyi ba
korai bane, yanzu ma aka fara rayuwar. Waya gaya miki koya gaya maka ba komai bane
ba. To ko kasa mutum ya gino ya tara kikazo wucewa ko kazo wucewa ka barbaza masa
ai hakkine balle abinda ya killace koya nunama duniya abun nan mai muhimmanci ne a
garesa koda ace kai baka ganin muhimmancin nasa. Kanada kananan shekaru kana ta
daukar hakkin mutane da kake gain bamai muhimmanci ba kana tarawa yana hauhawa a
mizanin aikinka yana rusaka, yana rusa rayuwar yayanka masu tasowa, yana rusa
cigabanka na duniya dana lahira kai kana shirmen kana nasara akan mai hakkin.
Kajifa toshewar basira, shi kana kara masa nasara ne fa, tunda dole-dole ka biyashi
a inda babu kudi sai aiki inhar baka biyasa da kudin daya shardanta akan kayan nasa
ba. Kamar dai ita a yau, komai yazo mata a gabar da bata da damar neman gafarar
wadanda ta zalunta ta cutarma da rayuwa saboda nasararta da neman cikar burinta. Ta
rasa a lokacin da su kuma suka samu, wata tayi amfani da ita dornin nasararta ta
barta da katon nauyi bisa kai. Kaicon rayuwar da ba'a tuna mutuwa a cikinta. Kaicon
rayuwar da ake ginata kamar bazata yanke ba. Kaicon rayuwar da ake daukar hakkin
wani kamar ba hakki ba. Kaicon rayuwar da cikar buri ke jagorantar imani da tsoron
ALLAH a zuciyar mai shi. Kaicon zuciyar dake bushewa da jin komai tayi dai-daine.
Ya ALLAH ka karemu, ka kara tsaremu, ka tsarkake mu, ka kiyaye mu. Ka killace mu,
ka karfafa mu, ka jagorance mu bisa tsoronka da tsoron shirka, da tsoron cin hakkin
wani komai kankantarsa, ka kyautata neman mu da ga halak, ka karfafa ayyukanmu bisa
umarninka da kiyaye saba maka badan halinmu ba. ALLAH ka shiryar da wanda suka
kauce, idan ba masu shiryuwa bane UBANGIJINMU mun barka da su kafimu sanin miya
dace da su. ALLAH ka rabamu da ruin duniya da kyale-kyalen cikinta. Ya rabbi ka
saka DUNIYA a tafukan hannayenmu ka nisantata zama a cikin zukatanmu. Ya rabbi ka
wajabta mana tsoronka, ka karfafa imaninmu. Ka yafe mana kura kuranmu, ka bamu ikon
kyautatama duk wanda ka hada kaddarar zaman mu a tare ko mu'amularmu, Ya rabbi ka
hana mugayen halayenmu cin nasara a kammu, kasa muci nasara akan mugayen halayenrnu
da ayyukanmu".

A tare suka dinga amsawa da Amin kowa na sharar hawaye, yayinda Malikat
Bushirat ke kuka mai tsananin gunji. Matuka takejin radadi a zuciyarta da azaba a
cikin jikinta, So take ta kara cewa wani abu koda ga tilon danta ne da har yanzu
bai dago kai a dubi kowa ba balle ita amma ta kasa hakan. Da ga karshema mikewa yay
a hankali cikin tangacfin juwa hannunsa cikin na Iffah har yanzu batare daya kalla
kowa ba balle cewa wani abu ya jata suka fice. Ta hanyar sirrin da suka fito ta can
suka koma hankalin Iffah a tashe da yanda yake tangadì mai bada tabbacin akwai
matsala….✍️

DAUDAR GORA
Book2
89

...... Suna shiga bedroom din sa ya wani irin rungumeta tsam-tsam a jikinta tamkar
zai maidasu su zama abu guda. Yanda Iffah kejin gudun zuciyarsa da bugawarta
hankalinta ya tashi matuka. Tayi yunkurin dagowa ta kallesa amma yaki bata koda
kankanuwar dama. Sosai numfashinsa ya fara fisga, gashi ya ki sakinta balle ta
bashi wani taimako, mutsu-mutsun kwatar kanta take amma ta kasa. Sai kawai ta fashe
masa da kuka. Sakinta yay da sauri, sai dai bai yarda sun hada ido ba ya rabata ya
wuce. Gaban window yaje ya tsaya kawai ya tsirama harabar masarautar ido. A gurin
Iffah ta durkushe ta cigaba da kukanta. Tsahon mintuna goma suna a haka sautin
kukanta kawai ke ratsa dakin, shiko yana a inda yake tsayen kamar gunkin da aka
dasa domin tarihi. Mikewa tai itama jin jiri ya fara dibar idanunta, dan akwai
yunwa tare da ita, rabonta da abinci tun jiya. A bakin gadon ta zauna jagwaf, ta
dafe kanta tsahon minti daya kafin ta janye. Ciwo hannayenta ke mata sosai saboda
matsar da suka sha a wajensa, har sun dan kumbura dan matsar bata wasa bace. Jin
sun mata tsami babu dadi ta shiga murzasu a hankali ko zataji sassauci. Bata san
sanda ya baro wajen window din ba, ganinsa kawai tai durkushe gabanta ya kamo
hannun nata a cikin nashi. Kallo daya taima fuskarsa tai saurin dukar da kanta, dan
idanunsa sun yi masifar firgitata. Sun yi wani irin kadawa jazur irin wanda bata
taba gani ba,hakama fuskarsa gaba daya tayi jazur kuma babu alamar yayi kuka, kawai
tsabar tashin hankaline ta sauya masa kamanni. Hannayen ya shiga murza mata a
hankali, kafin tsahon lokaci kamar wanda aka fisgo furucin da ga halshensa ya ce,
"I am sorry".

Da sauri ya dago ta dubesa, ganin yanda ya tsurama tafin hanunta idanunsa masu
ban tsoro yasata jin hawaye sun sake cika mata ido. Dayan hanunta ta daura akan
habarsa mai cike da lallausan bakin gashi ta dago, cikin dauriya da dakiya ta saka
idanunta cikin nasa, muryarta na karkarwa ta furta, "Dan ALLAH kayi kuka koda
kadanne Zakina. Kayi kuka! kayi kuka!! kayi kuka!! Zan shanye hawayen a cikina na
adanasu cikin manyan SIRRIKANKA da ka bani ajiy....."

Kafin tama kai karshe sai ga hawaye sharrrrr da ga idanunsa kamar an bude fanfo,
wani irin murmushi mai tsananin ciwo da kuna ya sakar mata hawayen na kara gudu. Da
sauri ta tara hannayenta suka sauka a ciki, kallon tafin hannun nata da hawayen
nasa ke sauka yayi, sai ya sake fashewa da kukan, hawayen na cigaba da sauka a
cikin tafin hannun nata. Sai da suka taru sosai sannan tasa harshenta ta shiga
lashe hawayen tana hadiye tare da fashewa da sabon kukan itama. Kansa ya daura a
saman cinyarta yana zaune da ga kasan lallausan carpet din gaban gadon itako tana
daga zaune a kan gadon, itama sai ta daura kan nata a kan nasa suka cigaba da kukan
a haka zabban tausayi…

Bayan sallar azhar da ya kasa fita saboda zazzabin da ya rufesa mai zafin gaske
itama ciwon ciki ya takurama Iffah na jin yunwa, abinka da ba ita kadai ba. Haka ya
tashi cikin kakkarwar sanyi ya bata madara ta sha, tana sha ta amayar da ita, a
hakan dai ya taimaka mata cikin karfin hali ta gyara jikinta, sake bata madarar yay
tasha kadan, shima sai ta takura masa wai sai ya sha dan rabonsa da abincin kirki
tun jiya. Kin sha yay ta sanya masa kuka, dole yasha rabin kofi ya kauda kansa, da
ga haka suka dunkule waje daya kwance zafin jikinsa na matukar ratsata. Ganin
zazzabin baida alamar sauka sai ma karuwar da yake yi yasa Iffah kiran Sayeed
Fayzul-haq. Babu bata lokaci suka iso da Doctor Afif da ke matsayin amintaccen
likitansa. Doctor Afif din kansa sai da hankalinsa ya tashi gain yanda jinin
Shahan-shan din yay wata irin kololuwar hawa, ga bugun zuciyarsa har ya canja.
Cikin sauri ya danna masa allurar barci mai matukar karfi dan in har aka cigaba da
zama a hakan akwai babbar matsala kam. Da farko kin yarda ma yay ayi allurar sai da
Iffah ta sanya masa kuka sannan ya kauda kansa kawai baice komai ba. Sai Sayeed
Fayzul-haq ne yay ma Doctor din nuni da yayi aikinsa dan kauda kan nasa a nufin
amincewa, Iffah dai na zaune ne kansa a saman cinyarta tanata faman sharar hawaye.
Duk da karfin allurar ya jima baiyi barcin ba, dan sai da Iffahr ta hada da tofa
masa addu'oi sannan aka dace barcin ya daukesa.

Haka ta cigaba da zama kansa a saman cinyarta har aka kira sallar magrib,
kafafunta duk sunyi tsami,da kyar ta gyara masa kansa ya koma kan fillo, sannan ta
mike ta gabatar da sallar magrib din. Alkur'ani ta dauka ta shiga raira karatu a
nutse tana hawaye, bata ajiye ba har aka kira sallar isha'i nan ma ta gabatar. Ta
jima tana addu'oi akan wadan nan al'amura da suka cure musu, tashinta babu jimawa
Malikat Haseenat da Daneen Ammarah da Daneen Waheeda da Iftihal sukazo dubashi.
Basu shigo ciki ba iyakarsu falo, Iftihal nata yan kalle-kalle dan wanna shine karo
a farko a rayuwarta ma data shigo sashen nasa. Iffah na fitowa ta wani dukar da kai
dan ita kam tsoranta takeji matuka yanzu. Cike da kauna da tausayi Malikat Haseenat
ta rungumeta, kafin ta dagota da fadin, "Hafida-ti kema ai ba lafiyarce da ke ba
ma, dan zazzabin ne a jikinki. Kin ma ci abinci. Idanun Iffah cike da hawaye ta
girgiza kai da fadin, "Na koshi Jaddah".

"Bazai yiwu ba dan bake kadai bace. K Iftihal hadomin abinci mai sauki acan.
Cikin rawar jiki Iftihal ta nufi dining room, har yanda tai din ya bama Daneen
Waheeda haushi sai dai babu damar magana. Babu jimawa ta kawo abinci, Malikat
Haseenat ta amsa da kanta ta na bama Iffah'r. Da kyar take amsa da taunawa kamar
magani, batafi cokali hudu ba tace ta koshi. Lallabata Malikat Haseenat da Daneen
Ammarah suka shiga yi, da kyar ta kara biyu, daga haka suka shiga lallashinta da
nasihar ta kwantar da hankalinta, dan saita kwantar da hankalin natane shima zata
taimaka masa ya kwantar da nasa. Ta gamsu da nasihar tasu, anan ma takejin Ummu sun
wuce, Malikat Bushirat ma jikin nata ya sake rikicewa yanzu haka ga likitoci can
sun kasa shiga su dubata dan kurajen jikinta nata cigaba da fashewa warin na kara
karuwa. Batace komai ba illa hawaye da suka zubo mata sharr. Wanna ranar ita take
guje mata, gashi tun kan aje ko' ina kuwa har tazo din. Basu wani jima a sashen ba
suka tafi, haka ta koma dakin ta zauna ta saka Tajwar Eshaan gaba tana tofa masa
addu'oi da fatan ALLAH ya sanya masa nutsuwa da Karfin zuciya akan al'amarin. Haka
dai ta kasance bata wani samu isasshen barci ba, koda ya farka cikin dare da
taimakonta ya samu yay salloli, ta debo masa abinci amma yaki ya ci, sai da ta fara
masa kuka ya danci spoon biyu shima dole ta hakura ta kyalesa dan barcine bai gama
sakinsa ba.Dan haka ya koma ya sake kwanciya……

Gabanin asuba wan irin ihuface-iface na tashin hankali ya farkar da ita, zumbur
ta mike kamar wadda aka tsungula. hun yayi yawa matuka dan haka ta fita a razane,
ALLAH ma yaso doguwar riga ce ta abaya a jikinta. Hadiman sashen Shahan-shan din
duk wasu sunyi barci ma, sai jami'an tsaro dake kai kawo a ta waje da Ghazi. Sai
dai duk an firgitasu ashe sune keta hun, Wani irin sarawa kan Iffah yayi, a take ta
birkice alamar mutanen sun zo. Wani irin jan takobin dake a hannun masu tsaron
kofar shiga falon farko na kasa Iffah tai da ga cikin kubenta ji kake wani
zuuuuuu!! Sharbebiyar takobi ce mai tsananin walkiya da tada tsigar jiki, tuni tayi
tsakkiyar masarautar ta wani irin karta takobin bisa kasa. Kamar yanda mafi yawan
mutanen masarautar sukaji wanna tashin hankali haka sukaji karta takobin da Iffah
tayi akan kasa da yin wani irin kara ji ta ce. Duk wanda ya shirya idan ya isa yazo
gabanta. Saiko ga kusan mutum hudu sun bayyana gaban nata tsirara sai dan ganye a
gaba suna wani irin huci da bulbulo da wutar tsafi ta baki, Juyi ta sake. yI, da
wulwula takobin ta cake akan kasa, kafin tai wani irin zarota tai juyi bakinta na
ambaton sunan ALLAH tamkar kyattawar ido sai ga kawunan shegun a kasa hudu reras.
Zo kaga ihu, ga hadiman da duk suka farka saboda tsabar tashin hankalin firgitasu
da wadan nan mutane sukayi, wanda sune a
daren jiya suka shigo sukai musu kisan gilla dama. Ba kowa bane kuwa face a cikin
zuri 'ar su uwa. Tuni fa masarautar ta kara rikicewa, wanda ma bai farka ba sunata
farkawa. Can sai ga Jasrah ta fito cikin kuka da kururuwar an dauke Malikat
Bushirat. Ba kowa yasan mike faruwa akan Malikat Bushirat din ba sai su shakikanta,
duk da dai dazun anga duk ahalinta sunzo gidan, sannan Malikat Haseenat ta fito
ranta a bace da sashen ita da Daneen Ammarah. Dama Daneen Waheeda bataje ba dazun
din dan haka maganar dai har yanzu bata fita akan tsiyatakun da Malikat Bushirat
din ta fada ta aikata da bakinta ba. Kowa dai nata hasashe da son bin kwakwkwafin
al'amarin. Masarautar ta rude gaba daya, ALLAH dai yasa itama Daneen Ammarah da
nata kwankwaman a ka da kyar ta rike Iffah. Barci dai a wannan dare yara kanana ne
da basu san komai ba a wannan masarauta suka yisa. Dan tuni shima Tajwar Eshaan ya
farka. Tun a daren Iffah tai kiran kaka a waya, asubar fari kam a cikin masarautar
ta masa. Ana idar da sallar asuba aka shiga meeting na gaggawa. Kaka, Iffah, sai
manyan masu fada ajin masarautar irin su Sayeed Fayzul-haq da sauransu........✍️

DAUDAR GORA
Book2
90

.....Kaka ne ya fara magana rai bace. "Wadan nan mutanen yaki suka shirya dan gaske
bawai wasan yara ba. Daren shekaran jiya sun zo sunyi kisan gilla jiya ma sun dawo
harda daukar Malikat. Wadan nan da Fhareedatu ta sarema kawuna jiya bawai su kadai
bane, guduwa sauran sukayi. Dolene a nemo mafita dan a dawowa ta uku zasu sake
sabon shiri ne. Shakaran jiya sun kashe kusan mutane hamsin, yau ga kusan mutum
tara fa, dan ma yau ALLAH ya fargar da da sai sun gama illarsu sun tafi kamar ta
shekaran jiyan sannan za'a sani".

Sayeed Hifzur-rahaman ya ce, "Tabbas akwai matsala kam, dan da gaske suke ba
wasa ba. Sai dai fa matsalar idan munce wani yunkuri zamuyi ta ina zamu kama ne?.
Ku dubesu kamar ba daga jinsin mutane suke ba, ko kyawun kallo basu da. Ga su da
karfin tsafin mai ban tashin hankali.....

'"Babu wanda yafi karfin UBANGIJI ai. Dan haka zamu tunkaresu gaba-da-gaba". Iffah
ta fada cikin bacin rai. Duk kallon toro sukai mata, sai dai kafin wani yace komai
da ga bayansu aka amsa da "Tabbas mune zamu tunkaresu kamar yanda ta fada".

A razane duk suka juya suna kallonsa. Shi din ne dai ba wani ba. Shahan-shan
Eshaan Ibn Haysam Abdul- majeed Aliy Qutb. A kallo daya idan kai masa bazaka sake
marmarin karawa ba dan firgicin a yanda yake yau. Cikakken GWARZON BARDE abin
tsoratarwa ga duk wanda zai iya kallonsa. Karasa takowa yay cikin takun nan nasa
daddaya da yau ya kara zama cikin izzar damuwa da bacin rai. Ga ido ya toshe da
bakin gilashi alamar yau babu koda digon sassauci. Dole kowa ya mike cike da
girmamawa a garesa.Maimakon zama tsaye yay kikam idonsa akan Iffah, cikin bada
umarni ya ce, "Cigaba da bayanin ki".

Kai ta jinjina masa cikin girmamawa sannan ta dubi


kaka. Shima kai ya jinjina mata dan haka ta sake fuskantarsu. "Tunkararsu itace
babbar mafitarmu kamar yanda Kaka ya fada, dan tsafinsu da wani karfin maita babu
abinda zai mana da karfin tasirin UBANGIJI. Dan dole ne mu shafe babinsu gaba daya
in har muna son cigaba da rayuwa cikin salama.Mataki na farko a yanzu shine
Taswirar jejin da ake saka ran samunsu, sannan hada manyan baradan mayaka da ga
yanzu zuwa awa biyar kacal da muke da ita….

'"Amma ranki ya dade ai bamu san jejin da za' a iya riskarsu ba. "Sayeed
Aashiq-Muhammad ya fada cike da girmamawa ga Iffah'r".

Kaka ne ya amshe da fadin, "Wannan bazai zama mai wahalarwa ba, dan dukkanin
abinda ke zagaye da wanna kasa muna dasu a rubuce a kundin litattafan tarihinmu.
Za'a iya bincikawa tunda kabilar tasau dadaddiyar kabila ce".

Itama Iffah kanta ta jinjina da fadin hakanne kam, dan nima a karance-karancen
tarihi da nai a kwanaki akwai wani littafi daya tabo makamancin dabi unsu. Dan haka
muna bukatar Sayeed Aynul-Hassan shima anan".

Ba'a wani bata lokaci ba wajen kiransa, sai ko gashi da tarin littafai da wasu
manyan takardun taswura da ke kunshe da gaba daya kasar ta ruman da dazukanta. Kaka
ya bada umarnin tattara mayakan da ake da kyakykyawan zato a kansu, dan haka Sayeed
Tasadduq-Husain ya fice domin yin wanna aiki. Sayeed Aynul-Hassan mai alhakin kula
da da books room na masarautar, wanda kuma yayi rubuce- rubuce da yawa hakama
mahaifinsa da kakansa a take ya bada littafin da ake kyautata zaton sune a wannan
tarihin, dan bayan su din akwai dazukan da wasu mutanen daba su din ba ke zama sai
dai su sun banbanta da su. An aika amintaccen Tajwar Eshaan wajen Malikat Haseenat
domin amso wasu taswuriri nan ma da ke a daki littatafan sirri dake ainahin dakin
karatun Tajwar Abdul-majeed. Nan take su Iffah suka shiga bincike aka kuma baje
manyan taswuririn a bangwayen babban dakin meeting din. Annan ne fa Tajwar Eshaan
ya bama kowa mamaki, dan ashe masanin taswurane matuka. Komai da shi akayi, kusan
shine ma gaba wajen bada sirrikan dazukan, kaka da Iffah na bada shawarar yanda ya
kamata a shigesu a kankanin lokacin da ake da shi suma. Suma dai sauran kowanne da
irin rawar da yake takawa.

Da ga can cikin masarautar Kuwa kowa ka gani hankalinsa a tashe yake, dan hadimai
masu karfin hali ne kawai suka iya gudanar da ayyukansu. Wanda aka kashe kuma anata
kokarin musu sutura amma na iya cikin masarautar. Wadan da Iffah ta fillema kawuna
ko ace aljanunta kam suna a nan tsakkiyar masarautar rufe yara da mata dama wasu a
mazan sun zagayesu sunata kallo. Yan uwan Malikat Bushirat tuni sun iso masarautar
suma hankali tashe da jin cewar wai Uwa ta dauke ta. Duk da tsiyatakun data aikata,
da kuma ciwon da ke jikinta sai ya zam maganar nan ta malam ba haushe da kan ce
*_DAUDAR GORA CIKI KA SHATA_*

Hankali iyaye musamman mata na masarautar bai kara tashi ba sai da suka ga ana
tattara matasan masarautar ga dokuna majiya karfi ana fiddowa, Sayeed Tasadduq-
Husain nata waya da shugaban sojoji na kasa ana shirya motsocin yaki da jirage uku
da ya bada umarni. Hakan na nufin mataki na karshe ake shirin tunkara wato yakin
gaba-da gaba da matsafan mutane irin su uwa, kafirai da basa gane komai da ga
tsoron ALLAH. Wasu tuni suka fara nuna basu yarda yaransu suje ba. Amma matasan
samarin nan da Iffah ta dunkule akan sakasu aikin raba abubuwan azumi dana salla
sun hade kawuna akan sufa babu gudu babu ja da baya zasu kare martabar masarautarsu
da sarkinsu da kasarsu ne. Duk da
basu san wahala ba, bama su taba gain yaki na zahiri ba. Gain fa abinda matasan nan
sukai yay matukar burge was hadiman suma suka fito da shirinsu na kasancewa a
cikinsu..

Ga al'ummar gari ma ba'a barsu a baya ba. Dan tun zuwan labarin abinda ke
faruwa ta hanyar matasan nan da suka yada a social media sai ga mutane nata yo
gangami musamman matasa da dama jirafa suke ace kule suce cas, Dan shi matashi a
duk inda ake dan shirin a mutu ko ai rai ne, shiyyasa a mafi yawan gaba ta rayuwa
inhar wani rikici ya tashi sai ka samu matasa ne sukafi zama gaba-gaba akan
al'amarin.

**.

Da sauri Iffah tabi bayan Tajwar Eshaan da ya fice da ga dakin meeting din,
Shigowarta dai-dai da fitowarsa da ga closet dinsa rike da sulken yaki da bata taba
sanin da su ba ma a masarautar. Da ga shi har kayan takema kallon mamaki. Shiko ya
dauke kai kamar bai fahimci abinda take kalion ba ya hau shirinsa. Dammarar da yake
kokarin daurawa ta rike jikinta na rawa. "Maleek mi kake shirin yi ne haka?!".

"Fita bama kasata kariya mana da al'ummar cikinta, ko kina nufin zan bar yayan
mutane su tunkari wannan hadarin su kadai Sohaa".

'"Ba haka nake nufi ba, sai dai ka tuna mutanen nan kai ne fa abin harinsu kai
tsaye a wanna gabar shiyyasa ma suka dauki Ammie, fitarka wannan yakin akwai
damuwa. Kayi hakuri ka barmu mu muje".

Ido ya tsira mata na wasu mintuna, sai kuma ya saki murmushi ya cigaba da daura
dammararsa. "Ai ke badake ma za'aje din ba..."

"Saboda mi?".
Ta fada cikin tsananin damuwa. Nan ma shiru kamar bazai amsa mata ba, sai da ya
mula dan kansa a fisge yace, "Saboda matata kwai ce a a hannuna, tattalinta shine
abu mafi girma a gareni, kuma kin manta kinada karamin ciki ne."

"Amma..

"Shini!!!!"

Yay saurin katseta ta hanyar aura yatsarsa akan bakinta idanunsa da har yanzu suke
jazur a cikin nata. Kif-kif ta farayi da nata sai ga hawaye sharrr. A hankali ta
daura hanunta saman nashi da ke a bakinta ta janye, hannunta biyu ta saka ta rike
hannun har yanzu idanunta dake cikin nasa na zubda hawaye. "Bazan Iya barinka ka
tafi kai kadai ba".

Murmushi ya sake sakar mata yana lumshe idanunsa A hankali ya ce, "Sohaa idan
mun tafi gaba daya waye zai rike al'ummar kasar? Dole kece madadina anan, roko daya
zan miki koda a rasa rayuwata a wanna gabar ki zama shugaba adala, karkiyi sakaci
da hakkin, al'ummar wanna kasa. Kiyi gaskiya da adalci akan masu gaskiya, ki
hukunta duk wanda yay kuskure akan kuskurensa. Ki zama uwa ta gari da zata bama ya
ko dan da zaki haifa mana, ki tsaya akanta ko a kansa da ilimin addini dana zamani,
ki cusa masa muhimmanci tsoron ALLAH da gaskiya a zuciya.....

Kuka ta wani irin fashewa da shi ta fada jikinsa.Rungumeta yay tsam-tsam shima
yana sauke ajiyar zuciya. Gangi da aka fara bugawa na umarnin fitowar mayaka ya
sashi janyeta a jikinsa a hankali, shirinsa ya karasa sai gashi ya fito a cikakken
gwarzon barden sa. Bai bata wata damar cewa wani abu ba ya kama hanunta kawai suka
fito. Tsitt kakeji masarautar tayi da mamakin ganin har da shi za'ai fitar, sai
kuma hankalin iyaye da yawa ya dan kwanta, al'amarin kuma ya kayatar da kowa. Sai
da ya gama kallonsu daya bayan daya duk kawunansu a kasa sannan ya nisa yana lumshe
ido da budewa. A hankali ya furta,"Kuyi hakuri! Kuyi hakuri!. Kuyi hakuri da
gazawata a matsayin shugaba gareku. Ina jin ciwo fiye da irin ciwon da kuke ji, duk
abinda zan iya fada muku a yanzu kun riga kun sanshi. Wanda zan maimaita kawai
shine koda na rasa raina a wannan yakin MATATA itace mai gadon shugabancin da ALLAH
ya daura min, inada yakimin zata samar muku fiye da abinda ni na samar muku. Idan
kuma inada rabon dawowa gareku akwai abubuwan fada a bakina sosai zan kuma isar da
su gareku. Duk wanda nama ba dai-dai ba a wannan hukunci ya gafarceni, ina hango
muku abinda ba lallai ku hangoma kanku ba. Nagode da tarin kaunar da kuka nunamin a
tsahon shekarun dana dauka matsayin shugabanku".

Hawaye kowa keyi a wajen.

Ya dan murmusa yana hadiye abu mai ciwo da ya tsaya masa a makoshi. Hannun Iffah
kawai ya kama ya nufi fada, gaba daya aka take musu baya, sai dai manyan ne kawai
suka shiga. Can ya dagata ya ajiye akan kujerar karagar mulkin Shahan-shan. Wani
irin kabbara aka dauka Iffah kuma ta fashe da kuka. Murmushi yayi tare da kaiwa
gabanta ya ajiye guywarsa kasa ya tokare kafa daya kamar wanda ke shirin saka mata
zoben baiko. Hanunnta ya kamo cikin nasa ya rike tare da kaiwa saitin bakinshi ya
sumbata. Cikin wata irin murya mai sanyi da nutsuwar ya ce, "Kin tuna ranar da kika
sanar da Ajmaal burinki na hawa wannan kujerar? To ki dauka yau ALLAH ya cika miki,
ALLAH ya baki ikon sauke nauyin hakkin al'umma My Sohaa".

Gaba dayanta ta zubo kasa ta fada jikinsa suka kankame juna. Dole gaba daya kowa
ya fice kawuna a kasa…

Bayan minti kamar biyar suka fito hanunsu cikin na juna, a gaban barden dokinsa
dan amana suka tsaya, kamar yanda ya saba yay haniniya tare da kwafutar kasa yay
wata irin girgiza. Murmushi yayi a hankali tare da daura hannunsu dake cikin a juna
akan fuskar dokin. Sai ko dokin ya kara girgiza da matsawa gaban Iffah sosai.
Murmushi Iffah dake hawaye tayi, ya kalleta shima murmushin har yanzu akan
fuskarsa. Dayan hamunsa yasa ya goge mata hawayen sannan yay wani irin salon tsalle
na bajinta ya haye saman dokin. Take suma sauran suka haye nasu dokunan aka cigaba
da buga gangi. Iffah ta kallesa ta kalli Babiy ta kalla kaka ta kalli Hanash da duk
suna a cikin wanna tafiya sai kawai ta fashe da kuka..........

🚴🚴🚴🚴Basai munga yakin ba kawai a tsallake ALLAH na gaji 😫

DAUDAR GORA
Book2
91

....Sun hadu ne a mahadar shiga jejin su da sojojin kasar da suka rigasu isowa
kasancewar su a dokuna ne. Shine ya fara dirgowa da ga dokin nasa. A tare sojojin
suka mika gaisuwar girmamawa ga Shahan. shan din nasu. Ya amsa musu da kulawa, tare
da basu umarnin mikewa. Duk mikewar sukai, sannan shugaban sojojin ya iso garesa
tab…. a hannunsa ya mikama Sayeed Tasadduq-Husain dake a gefensa. Amsa Sayeed
Tasadduq-Husain yayi tare da matsawa kusa da Tajwar Eshaan, shi din masanine na
gaske akan ilimin sanin taswura da bibiyar waje, dan haka cike da kwarewa ya fara
sarrafa tablet din cikin bibiya ya saita abinda suke bukata. Tab.. din a maidama
Sayeed Tasaddug-Husain yana mai dubansu gaba daya. Kowa sake nutsuwa yayi akan
kafafunsa har shugaban sojojin.

Taku daya biyu yay sai kuma ya tsaya cak hannayensa goye a bayansa. "Bazai yuwu
ace mun fito wannan yakin batare da an rasa ran wani ba a cikinmu, ina fatan koza'a
rasa din to ya kasance ni ne!?.……." babu wanda maganarsa bata razanar ba a cikinsu.
Dan sai da duk suka zabura suka kallesa.Basarwa yay tamkar bai fahimta ba ya cigaba
da fadin, "Kowanne shugaba yakanyi yaki ne domin kare al'ummarsa da kasarsa. Haka
ma kowace al'umma kanyi yaki ne domin kare shugabansu da kasarsu. To a wannan gabar
ina son kuyi yakine domin kare kasarmu da kayinku. Karku damu da bada kariyarku
gareni zan kasance a karkashin kariyar UBANGIJINA.Mutanen da zamu tunkara duk nan
mun san mutane ne masu hadari, wanda kuma bai sani ba ya sani anan sunada hadari,
sannan an raini zukatansu ne da daukar fansa tamkar yanda uwa ke rainon yaronta da
abincin jikinta. A mu duka da muke nan akwai masu mata da iyaye da yaya, akwai masu
yaya da mata kawai, akwai masu yaya kawai, akwai masu iyayen ma kawai. Mu duka mun
barsu ne suna kuka, kuka, mai ciwon shiga kila wa kala a saran dawowarmu ko mun
rabu kenan. Ya zama dole musa a ranmu mun barsu da wannan tabon, musa a ramu koda
bazamu dawo ba to mu kasance su mun karesu da ga sharrin wadan nan mutanen ta
hanyar shafe babinsu a doron kasa na har abadan abada. Dukanmu bamu taba yaki ba a
zahirance, amma sanin kowane dan kasar ruman iyayensa kan horesa da iya wasan
takobi tun yana kankaninsa musamman mu maza. Wanna yasa bana jin ko dar da ga
gareku jarumaina. Zamu tunkaresu da karfin ikon ALLAH, da karfin zukatanmu, da
karfin kwanjinmu, da karfin horaswarmu, da karfin kare
kasarmu, da karfin kare al'ummar mu da addininmu.
Ka tuna a ranka mafifici a halitta ya yaki kafirai ne da duk wadan nan karfin ikon
domin mu kasance a yau din mu cikin bautar UBANGIJI babu wani mai kuntatamu. Sai
dai idan har mune muka wofantar da darajar daya sama mana tun a wancan lokacin sai
mu rayu a karkashin mulkin mallakar kaskastattun kafirai. Bana fatan mu kasance
hakan da karfin ikon ALLAH "

A tare sukace insha ALLAHU. Murmushi yay a karo na farko tare da duban kaka da
shugaban sojoji. "Mu ukun nan mune kwamandojin wannan yakin, kar'a taba kananan
yara, dan zamu iya zama jagororin canja musu alkibla bayan sun dawo hanunmu. Daga
basu ba kowa abin harinmu ne. A lokacin da kuke shagalta da yakarsu, ni zan tunkari
shugabar tasu ne..

Duk sun amsa da girmamawa. Daga haka aka fara nufar abin hawa. Wasu a cikin
sojoji sun shiga jirage, inda aka bukaci Tajwar Eshaan shiga daya da aka kawo domin
shi amma ya ce shi akan doki zaije. A dai duk cikin matasan idan da mai sha'awar
haka ko rashin jimirin tafiya a doki ya kasance a cikin sojojin.Wasu sunyi hakan,
wasu ko suna tare da shi a dokunansu. Bayan anyi doguwar addu'a masu bibiyar hanya
ta na'urori suka fara aikinsu. Masu dokuna ne a gaba, motocin yaki na sojoji a biye
da su, ta sama jiragen yaki da suka rarrabu a jejin domin sanar musu motsin komai
da zai iya tunkarosu a tafiyarsu su da suke kasa musamman ma nakan dokuna. Kamar
yanda Tajwar Eshaan ya bada shawara kowannensu bakinsa dauke da addu'oi..

Anan ma cikin kasa da kewaye tuni an dukufa addu'oin musamman ma cikin


masarautar ruman.Yara da manya kowa ya nutsu gayama UBANGIJI da fatan kariya ga
wadan nan bayin ALLAH da suke tunkaran hadarin rayuwa ko mutuwa. manyan malamai da
al'ummomin yankunan su an dukufa gayama ALLAH.Yayinda mutane suka dinga cincirindon
taruwa a kofar jejin ta kowacce kusurwa zaman jiran tsammani..

**

Sun nausa matuka cikin jejin da bakajin motsin halitta irin ta mutane sai tsuntsaye
nau'i-nau'i,yayinda a farko-farko suka dinga wuce kauyuka. Duk kauyen da suka gifta
aka sanar da Shahan-shan ne da kasan sai kaga matasan kauyen sun daura dammarar bin
bayansu suma. Dan sunfi kowa sanin dazukan wajen da abinda ya kunsa. Ga sojoji ta
sama suna isar da sakon duk inda suke tunkara. Tafiyar awanni biyu cur ta iso da su
gab da bataliyar sansanin da su uwa suka kafa gari. Anan suka taka birki bisa
umarnin Shahan-shan aka gabatar da sallar la' asar, yayinda jiragen sojoji keta kai
kawo da sake bincike jejin ta yanda su Uwa bai zama lallai su fahimta ba a
tunaninsu.

Sai dai kuma abinda basu sani ba su Uwa nada yan leken asiri a wasu kauyuka,
hakama sunada na hatsabibanci tsaface-tsafacensu da suka kafa domin shirin kota
kwana a irin wanna yanayin. A yanzu haka ma yan leken asirinsu sun isar musu da
sakon shigowar su Shahan-shan din. Jin harda Tajwar Eshaan wata irin kyalkyalewa da
mahaukaciyar dariya uwa ta shiga babbakawa da dukanin budaddiyar muryarta, sautin
yay wani irin karade dajin. Sai da tayi mai isarta sannan ta bada umarnin kowa ya
kasance
cikin shirinsa. Dandanan suka fara shiryawa mazansu da matansu, masu hayewa kan
bishiyu nayi, masu hawa kan dunitsina nayi, yaran aka tattaresu cikin wani kogon
dutse gaba dayansu dake nan jikin kauyen.

Dai-dai nan jiragen sojoji suka mamaye garin ta sama. Dabbobin da su uwa ke kiwo
kawai suka iya gani, dan haka suka sanarma da Tajwar Eshaan akwai matsala fa. Dan
kauyen babu kowa cikinsa sai dabbobi. Da mamaki yace,

"Kamar ya babu kowa?".

Shugaban sojoji ya ce, "Wlhy babu kowa sai dabbobi”.


Yanke wayar Tajwar Eshaan yayi, kaka dake kusa da shi duk yaji komai, murmushi
kawai yayi, kansa a kasa batare da ya kallesa ba ya furta,"Babu inda sukaje ranka
ya dade, hakan na nufin sun san da zuwanmu zuwa yanzu. A sanar musu kar jirgi ko
daya ya sauka kasa har sai mun fara shiga".

Sayeed Tasadduq-Husain Tajwar Eshaan ya mikama wayar, dan haka shi yay kiransu
ya sanar musu.Shugaban sojoji zaiyi gardama Tajwar Eshaan ya sake amsar wayar, babu
alamar wasa tattare da shi ya furta, "Kuyi yanda akace". Cikin girmamawa yay saurin
amsawa. Daga haka suma suka hau dokunansu, kaka ya juya yana kallonsu, "Kowa ya
kasance bakinsa da addu'a, duk abin tsoron kuma da za'a iya bude maka do da shi
karka razana. Kar kuma mu yarda addu'a tabar bakinmu dan itace babban makamin da
zai iya rusa wadan nan mutanen bakwai makaman hannunmu ba".

Duk sun amsa da girmamawa garesa, da ga haka Tajwar Eshaan ya yunkura. Shi da
Kaka sune a gaban,sai tawagar masu dokunan biye da su, sai motoci sojoji da duk
wanda bazal iya tafiyar kan doki ba. Har suka iso tsakkiyar garin suma basuga komai
ba sai farin dabbobi. Shiru sukai tsaiwar shirin kota kwana suma da baza idon son
gain ta inda wani zai fara bullowa. Mintuna uku shiru sunata ambaton ALLAH sudai,
sai jirage da ke ta kai kawo ta sama.

"Kodai zamu sauka mu bincika ne?".

Daya da ga cikin samarin ya fada. Alamar yay shiru kaka yay masa. Kai ya jinjina
masa. Cikar minti daya da hakan bai karasa ba dajin ya dauki wani irin sautin kuka
mara dadin ji. Hatta wanda ke cikin jiragen sal da zukatansu suka shiga bugawa da
sauri-sauri. Sai dai kowa yayi tsam bakinsa da addu'a. Kukan sake cika musu kunnuwa
yake da tunkarosu, hakan yasa kowa sake shiri. Wasu inn halittune masu ban tsoro da
rashin dadin kallo suka zagayesu. Cikin dakiyar zuciya Kaka ya furta. "Kar wanda ya
firgita". A zahiri dai kowa ya amsa masa da to, amma a zukatansu wasu dai kam sun
razana. Amma sai ambaton ALLAH da sukeyi ya saka musu wata jarumta da jin karfi,
kafin ma halittun sun yunkura su sun yunkura a dokunan batare da jin zasu gagaresu
ba duk da yawansu. Na cikin motoci ma duk sun fito, haka ma wanda ke cikin jirage,
jirgin na daga sama suka dinga silalowa ta sama sai ya zamto sunma halittun
kawanya. Su Tajwar Eshaan a tsakkiya, sai halittun,sojoji a karshe. Cike da jin
karfin zuciya Tajwar Eshaan ya fara ketawa cikin halittun sai ga kawunansu yana
saukewa da takobin hanunsa shi da kaka. Gain hakan yasa a cikin samarin ma wasu
suka afka sura. Tuni halittun suma sun fara tsalle a kawunansu, sai kusan uku su
taru a kan mutum daya, cikin dai amincewar UBANGIJI suka gama kaudasu a abinda bai
wuce mintuna ashirin ba. Da yawansu sun jijii musu ciwuka da farautansu. Ganin haka
su Uwa suka sake turo wasu. A yanzu kam kaka ne yay wani irin dirowa daga saman
dokinsa. A kausashe ya dubi halittun da suka sake zagayesu da fadin, "Ku kananun
hatsabibai, idan har baku kasance matsoratan kafurai ba ku bayyana kayinku mana
mushirikai. Ko kun tsorata ne? Nace ko kun tsoratane Uwar gijiyar taku ta reneku
da tsafine kawai amma babu karfin zukata
da jarumta!!!".

Tabbas wadan nan kausasan maganganu na kaka sun matukar musu dacin, dan kuwa jikin
uwa da ke a dakin gumakansu ga Malikat Bushirat shimfide sun zagayeta cikin wata
kaya da kayan tsafi rawa ya kamayi, cikin wani irin kara ji da mummunan sauti ta
ce, "Ku fito ina bukatar kan shugaban nasu a gabana. Kuma ina bukatar karagar
mulkin ruman a gabana a yanzun itama tare da kan tsohon nam dana matar shugaban
nasu da ya bari gadin gida"….✍️

DAUDAR GORA
Book2
92
-.Maganarta ta zama tamkar busa musu kaho da kada musu gangi ne. Dan saukar kibau
kawai su ka fara ji shuuuuuu daga sama. Da sauri Sayeed Tasadduq-Husain
yace,"Garkuwa sojoji masu karfi da karfafawar ALLAH!!".

A take suka dunkule waje daya suka zagaye Tajwar Eshaan ya koma tsakkiya tare
dama kansu garkuwa kibiyiyin suka dinga sauka akan saman garkuwar karfen hannayen
nasu. Da wanna damar yan kabilar su uwa da ke saman bishiyu da duwatsu fara dirgowa
kasa suka zagayesu. Sanda suke janye garkuwar bayan gama saukar kibau din sun gama
zagayesu. Ko kadan hakan bai razanasu ba, dan kowa a fusace yake da jin tsanar
wadan nan kafirai. Sannan sunyi alkawari duk rintsi bazasu bari a taba musu Shahan-
shan din su ba. Tuni sukai wata irin rabewar da kaka duk ya tsara musu. Su kuma
gain hakan sai sukai tunanin tsorata sukayi ne suka afka kai tsaye da tunanin korar
su. Wannan itace damar farko data basu nasara akan wadan nan mutane, cikin kankanin
lokaci kura ta tashi waje ya hargitse. Kabilar uwa sunyi shiri ne irin shirin da
wuka ko bindiga bazata ratsasu ba. Yayinda Kaka ya bada shawarar fara tunkararsu da
wuka sai sunzo hannu ai amfani da maganin daya tanada wajen karyasu su da karfin
yakin nasu. Gurin na cakudewa kam wadanda zasuyi feshin maganin ta sama da ga cikin
jirgin sojoji suka fara. Tun anan fa ihu-da-ihu ya hargitse, suka fara kaiwa kasa
samarin nan a gille kawunansu. Yayinda kabbara ke tashi da amsa kuwwa a cikin
jejin. Cikin abinda bai wuce awa uku ba an gama da kaso biyu da rabi bisa uku a
cikinsu. Zuwa yanzu fa hankalin uwa da ke kwasar dariya ya fara tashi. A take ta
bada umarni ga wadanda ke zagaye da ita fara aiwatar da shirinsu akan Malikat
Bushirat. Dan hakanne plan c dinsu, plan b shine wasu kason mutanensu da ke can
masarauta dakko karagar mulkin Shahan-shan..

** MASARAUTA **

Kukan da taci ya haifar mata da matsanancin ciwon kai, duk yanda taso kin kwanciya
sai da Malikat Haseenat ta takura mata. Kwanciyar tayi, sai dai bata
rufa mintuna ashirin cikakke ba ta tashi a matukar firgice. Hankali tashe Malikat
Haseenat da Daneen Ammarah sukai yunkurin riketa amma ta girgiza musu kai. Sun
fahimci tabbas akwai matsala, dan haka Daneen Ammarah ta ce, "Mammah barta. Barta
kawai akwai matsala ne".

Hankalin Malikat Haseenat tashi ya karayi, dan tuni itama Daneen Ammarah din ta
birkice a cikin kankanin lokaci. Dai-dai nan ko Amintacciyar hadimar Malikat
Haseenat ta shigo hankali tashe, cikin hakki take sanar musu babu lafiya, ga was
irin mutane nan da ba'asan ta inda suka shigo masarautar ba sun zagaye ko ina. Wasu
a cikin jami' ai sun fara harbinsu amma ko gezau da alama ma bindigar bata kamasu.
Wasu kaso a cikinsu kuma sun nufi fada ne inga karagar mulki take.

Kafin ma takai karshe Iffah ta fice, Daneen Ammarah biye da ita. Gaba daya
masarautar ta gama harmutsewa. Tuni kowa ya fara gudun ceton rai.Yayinda jami'an
masu karfin hali da Ghazi da wasu a cikin hadimai da samari da aka bari sunata
kokarin kai musu hari amma mutanen nan babu alamar razani a tare da su, saima wani
irin dariya sukeyi cike da karfin iko na ko gezau. Ai babu wanda yasan ta yaya, ta
ina
ma, kawai saukar kawunansu aka fara gani bisa kasa. Hankalin Ghazi ya tashi, ganin
SARAUNIYA Iffah ce da kanta ba sako ba. Tare da Daneen Ammarah da a yau kowa ya
shaida eh lallai ba ita kadai bace itama da nata ifiritan aljanun bisa kai.

Duk wanda ya tunkari Iffah kai kawai take sauke masa ta matukar fita a
hayyacinta da canjawar kamanni. Suko hatsabiban wani irin bulbulo wuta suke ta
bakunansu suna kokarin tunkarar fada da tuni aka rufo ruf. Masarautar tayi masifar
rikicewa, mata da yara kuka kawai suke. Hakama wasu a cikin mazan tuni sun nema
wajen buya. Hatta su Miran Jasim da ke a cikin kurkuku sun tabbatar yau gidan babu
lafiya kam......

**
*

Su uwa na tsaka da zagaye Malikat Bushirat da aka gama jikewa da ruwan tsaffi a
tsakkiyar gumaka Tajwar Eshaan ya fado musu. Da wani irin jarumta dokinsa yay
haniniya mai razanarwa kawai yay kansu.Daga dokin har shi Tajwar Eshaan din gani
sukai sun koma musu wata halitta daban. Yau sai ga uwa tsaye akan kafafunta ta mike
da ga kujerar tsafinta cikin matsanancin tashin hankalin gain dokin nan fa babban
gunkinsu ya nufa. Kafin tai wani yunkuri yay ma butum-butumin gunkin wani irin duka
da dukan karfin kwanjinsa shi da dokinsa sai gashi tarwatse a kasa. Ai ko kashin
hannunsa yay wata irin karar masifa da ke tabbatar da yaji ciwo a cikin kashi.
Hannun yay kokarin rikowa da dayan Hannunsa dake rike da linzamin dokinsa yaji
saukar kakkaifar wuka a cikin damtsen hannun.

"Ya Arrahaman!!"

Ya ambata da dukkan karfin murya dana jiki da ya masa saura. Dan wata irin azabar
zafi ce ta ratsasa har cikin kwakwalwa, Dai-dai juyowarsa kan wanda ya sokesa da
wukar a dartsen hannun ya sauka kasa. Babiy ne da ya biyo bayansa, dan tun barowar
Shahan-shan din a cikinsu ya farga yay azabar biyo bayansa. Bummm!!!! Shima Baby
uwa ta sauke masa wani mulmulen ice saman kai, kara ya saki shima cikin ambaton
ALLAH ya dafe kansa da jini ya balle, luuuu ya tafi kan dokinsa zai zubo cikin
karfin hali Tajwar Eshaan yay wani irin juyi ya tallafosa. Gaba dayansa ya dago ya
ajiye saman dokinsa. Kafin ya fisgo sarkar da suka shirya rataye Malikat Bushirat a
ciki ya watsata, cikin amincin UBANGIJI ya samu nasarar sarko wuyan uwa da ke
kokarin zare wata takobin tsafi da ga jikin wani gunki. Razananninayar karar data
fargar da wanda ke waje ta saki, dan sarkar ta tsafi ce, amma cikin amincewar
UBANGIJI shi Tajwar Eshaan din sai bata masa komai ba. Duk da da yawansu an musu
jina-jina haka suka dinga dannowa dakin dan zuwa yanzu suma sun gama da wanda suke
wajen, wadan da suka rage kuma an kamesu an daure bisa umarnin kaka.

Cikin tashin hankali suka nufi Shahan-shan, amma sai ya girgiza musu kai alamar
su barsa. Da kansa ya dirgo kasa, su kuma suka kama Baby da babu numfashi tare da
shi suka sauke aka fita da dokin Shahan-shan. Shi da kansa ya daure uwa da sarkar
nan tare da bama matasan sa umarnin rushe gumakan: a gabanta, rushewar kam suka
farayi itako tana kukan bakin ciki da wata irin jijiga a cikin sarkar da ya
dauretan.

Shi kam takawa tay a hankali gaban Malikat Bushirat. Hannu ya kai ya yaye jan
mayafin da suka. lulluba mata, dai-dai nan ta bude idanunta sai ko a cikin nasa,
kallon juna sukai na kusan sakkani goma. Shi ya fara janye nashi da sukai wani irin
jazur cikin lumshesu da budewa. Batare da ya yaye farin mayafin dake a kasan jan ba
yasa hannayensa biyu ya dauketa duk da yanda hannunsa a haggu da yaji ciwo ga wuka
a ciki jini na zuba ke masa azaba da rawa. Wasu irin hawaye ne masu zafi suka shiga
rige-rigen sakko mata, dan su kadaine ke aiki a jikin ta, amma su Uwa sun sandarar
mata da jiki gaba daya babu abinda ke aiki tare da ita sai kanta da idanun.Duk
yanda ta kuresa da ido shi yaki yarda ya kalletan.Cikin sauri masu bada taimakon
gaggawa da aka taho
dasu cikin sojojin suka nufosa da gadon daukar marasa lafiya. Amma bai daurata ba
har sai da yaje ga jirginsu na sojoji da suka sauka. A hankali ya shimfidar da ita,
sai da ya tabbatar ya gyara mata mayafin da take ciki dan tsirara take sannan ya
dubi matukin jirgin yana lunshe ido. Ya fahimci abinda yake nufi, dan haka ya kame
jikinsa tare da salute nashi.

A gaban su kaka ya tsaya ya wani rumtse danunsa da daura hannunsa saman wukar
nan dake kafe a jikinsa zai fincike kaka yay saurin dakatar da shi. "A'a ranka ya
dade, hakan da zakai matsalane, dan wukar ba wuka bace takai tsaye kamar saura
akwai dafi tare da ita. Kawai ka shiga jirgi dan bai kamata ka koma damu ba a
doki".

Bai cire din ba, sai dai ya bama kaka amsa da cewar"Tare da ku zan koma Jaddi".

Murmushi kawai kaka yayi shi da Sayeed Tasadduq- Husain, dan yau ne karo na
farko da Tajwar Eshaan din ya kira shi da kaka. A dai-dai nan aka fito da Uwar dake
daddaure cikin sarka. An tsareta da tambayar ina yaran garin suke amma taki fada,
sai ma dariya data sanya musu da cewar, "Bazan fada ba, bazan taba fada muku ba.
Dan ku tabbatar karar da mu iyayensu kamar kashe maciji ne baku sare kansa ba
hahahahaha!!!!!".

Babu wanda ace da ita komai saboda isowar jiragen sojoji da shugaban sojoji ya
bada umarnin a karo, dan yanda suka jigata din nan babu mai karfin iya komawa ta
mota ko doki. Ga wasu shimfide babu alamar rai ma tare da su. Wasu kuma sun jigata
matuka da ko yatsansu basa iya dagawa ma. Kin fadar inda yaran suke yasa sukai
tunanin ko sun dauke su ma daga jejin ne gaba daya yasa shugaban sojoji bada
umarnin ana gama kwashe su a sakama garin wuta kawai. Uwa bataji wannan furuci ba,
kasancewar an tisa keyarta ita da sauran mutanensu ashirin da daya daba'a kashe ba
cikin motar yaki.Hakama sauran mayakan duk an sakasu a jirage su, marasa lafiya
sune farkon wucewa domin zuwa a basu taimakon gaggawa. Kaka da Tajwar Eshaan da
Sayeed Tasaddug-Husain da shugaban sojoji sune karshe, za'a warema Tajwar Eshaan
jirgi ya dakatar dasu.

Tuni sauran sojojin da aka bari suka sakama garin wuta gaba dayansa bayan an
tabbatar da babu wani kauye a kusa da su da wutar zata iya shafa. Dan su tsabar
bakin hali ma basu yarda yin makwaftaka kota kusa da wasu kauyukan ba. Wannan wuta
itace ta dinga wasar kogon dutsen da suka boye aransu zafin ya dinga ashes batare
da an san anan din suka boyesu ba.

Abinda ya far a cikin masarautar ya sasu iske cikin Dahab City a hargitse. Dan
jiragen a inda suka dauke su farkon jejin dole anan suka dakata aka dinga kwasarsu
a motoci. Nan din ma cike suka samesa da jama'ar gari ga yan jarida. Jinin da
Tajwar Eshaan ya rasa sakamakon sukar wukar da aka masa mai dafi a hannu dama ga
kananun raunuka yasa idanunsa har sun fara rinjaya, dan sal da taimakon shugaba
sojoji da kaka aka fito da shi aka daura a gadon marasa lafiya zuwa mota Hankalin
mutane ya tashi matuka dan sun fahimci Shahan-shan dinsu kenan gariin yanda sojoji
suka zagaye gadon, hakama da aka saka shi a motar an zagaye motar da uban tsaron da
korna miye ya gitta zal iya zama gawa ne….✍️

DAUDAR GORA
Book2
93

……..Cikin masarautar ma a hargitse suka sameta,dan tuni an is da Malikat Bushirat


da aka fara tahowa da ita. Ga Iffah da jini ya balle mawa ta yanke jiki ta fadi
itama aka shiga da ita ciki har yanzu likitocin da ke kanta basu fito ba. Tashin
hankalin hakan yasa ko wanda suka sarewa kawuna ita da Daneen Ammarah bama a janye
ba. Ba'a bari kowa ya ga halin da Tajwar Eshaan ke ciki ba aka shige da shi
sashensa. Hakama sauran mayakan da sukaji munanan raunika aketa nufar cikin clinic
da su duk da kukan da iyayensu keyi ba'a bar kowa matsowa kusa da su ba, wanda
sukaji kananan raunuka ne dai aka zube a harabar masarautar suma ana basu taimakon
gaggawa na ruwa da magani. Ga magrib ta gabato. Amma burin kowa dai yaji yaya
Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb yake. Yanda suka tada hankalinsu
yasa dole sai da Sayeed Fayzul-haq ya fito yay magana da yan jarida akan kowa ya
kwantar da hankalinsa Shahan-shan na nan raye, sai dai yana bukatar addu'oin Su...

*WASHE GARI*

Alhamdullah an wayi gari da dadin rai, dan su Babiy duk sun farfado. Hakama Tajwar
Eshaan kaka ya saka masa magani an kuma masa na asibiti da dorin karayar sai dai
ace Alhamdullah. Itama dai Iffah an samu nasarar tsayar da jinin kuma cikin da
aketama damuwar zai iya lalacewar dai yana nan. Malikat Bushirat ce dai idanun nan
da kai kawai ke aiki, sai dai duk abinda za' a fada tana ji. ALLAH sarki Jasrah
bata gazaba a yi mata hidima. Jama'"ar gari dama na masarautar da basu san komai
akan al'amarin nata ba sunata tausayinta da gain Uwa ta tsafeta ne saboda cikar
burinta. Was har addu'a suke mata na samun lafiya. Gawarawakin dangin uwa an
tattaresu anyi rami acan daji an biznesu, wanda kuma suka rage tare da uwa an
zubasu a kurkuku har sai ALLAH ya bama Tajwar Eshaan lafiya.

Tako ina labaran abinda ya faru a kasar ruman dinne ke yawo a duniya, wasu na
caccakar Shahan- shan akan abinda akai bai dace ba suma mutanen nada yancin kansu,
wasu ko na ganin hakan da akai shine dai-dai. To koma dai yaya ne yan kasar ruman
sudai hakan da akai yayi musu. Dan babu wata kasa da zata so rayuwa da masu bakin
kafirci irinsu uwa.Masu ganin ba'a musu dai-dai ba ma son zuciya ne kawal.

Lokacin da Iffah ta tartado taci karo da Tajwar Eshaan jikinsa ta fada kawal ta
fashe da kuka. Ya rungume kayarsa yana murmushi shima idanun nasa dai sun kada. Sai
da tayi mal isarta sannan ta dago, babu zato kawai yaji ta manne lips dinsu a waje
guda. Idanu ya zaro itama sai ta zaro nata tare da janyewa tana dariya. Da sauri ya
rikota da hanunsa mai lafiyar ya maidota jikinsa yana murmushi.

"Wannan ai mugunta ce a lasama mutum zuma a baki a gudu". Ya fada cikin rada a
kunnenta. Dariya ta shigayi a hankali tana boye kanta a cikin jikinsa, da ga haka
ya canja wasan a yanda yake bukatar kasancewarsa, duk da kuwa komai da yake na
karfin hali ne kawai, dan sam zuciyarsa babu dadi, shi kadai yasan halin da yake
ciki akan mahaifiyarsa. Amma yanata kokarin dannewa da gayama ALLAH kukansa.

Lokacin sallar azhar domin sake Kwantan da hankalin mutane ya fita sallar cikin
karfin hali duk da
hanun nasa an masa dorin karaya ne. Ga yankan wukar nan da yay matukar shiga
jikinsa sosai, saukin ma dal anyi maganin dafin. Bayan anyi salla an fito ya dan
gana da manema labarai da yasa a tara masa. A nan yay ma al'ummar kasarsa godiva da
fatan alkairi bisa kokarinsu da addu'oinsu. Ya kuma sake jaddada Iffah matsayin
SARAUNIYARSU har yanzu dan bazai amshi mulki ba sai ya samu lafiya. Babu wanda yay
jayayya da wannan al'amari. Sai ma Tajwar na jihohi da manyan kasar dake ta layin
zuwa dubashi tako ina, tare da sauran mutanen da suka fita wannan gumurzu. Musamman
yan kauyukan nan da Hadimai da wasu a jama'ar gari da suka taimaka musu anhadasu da
manyan kyautuka, hakama itama SARAUNIYA Iffah ta bisu su dukansu da manyan
kyaututtuka da ya sakasu a farin ciki, dan ita dukansu ta hada har matasanta.

Lokacin da don Malikat Bushirat ke gain bayanin Shahan-shan akan Iffah zata
cigaba da rike matsayinsa har sai ya samu lafiya, da lokacin da ake nuna Iffah'r
akan karagar mulkin Shahan-shan din randa take zartar da hukuncin kyautukan da ta
bama wanda sukaje yakin a matsayin Sarauniya kuka ta dingayi, kuka mai zafi da
tsananin kona zuciya. Sosai takejin radadi matuka a cikin kirjinta, ji take inama
kafin zuwan wanna ranar ta mutu ta huta. Bayan tasha kukanta ta godema ALLAH ta
cema Jasrah a cire mata tvn daga dakin. Jasrah har ta amsa da to Malikat Haseenat
ta ce kar a cire. Dan tsaf ta fahimci manufar Malikat Bushirat din. Tana ammakin
taurin zuciyar matar nan, ace duk wadan nan abubuwan daka gani basu isheka izna ta
saraya ba. Ko dan data haifa ta kasa neman gafararsa ma balle su. Kai ALLAH ya
rabamu da irin wanna mummunar zuciyar ta kafuran farko,

Kullum sai Tajwar Eshaan yabi ta barauniyar hanyarsa dubota. Zasuje da safe shi
da Iffah da an idar da sallar asuba. Zakuma suje bayan sallar isha' i. Da ga
gaisuwa da tambayarta yaya jiki bai iya kara sake cewa komai. Sai ma ita Iffah'r ce
kan dan mata addu'a ta tofa mata, duk da dai kaka nata kokarin bada magani ana mata
ko za'a dace. Haka zatayi ta kallon Tajwar Eshaan tana hawaye, amma shi daga kallo
daya na gaisheta baya sake yarda ya kalleta har yabar dakin kansa a kasa yake.

**.

Bayan kwanaki bakwai abubuwa da yawa sun dai-data, musamman masu kananun raunuka
sunji sauki sosai, sai wanda suka jigata ne sosa ke cigaba da karbar magani. Baby
ma dai da yake buguwace Alhamdullah jikinsa da sauki, dan haka Tajwar Eshaan yace
kawai Daneen Ammarah ta tare haka nan. Duk yanda taso zamewa sai da aka shirya wani
dan kwarya-kwaryar walima data kayatar. Dan anyita ne irin ta manyan mata masu aji
da ilimi. Zuwa dare aka shirya mika amarya dakinta, Iffah kuwa ta dage sai taje.
Sai da aka tuna mata itafa SARAUNIYA ce a yanzu, babu yanda ta iya dole ta hakura,
amma tanata ima Mamyn (Daneen Ammarah) tabarar wai shikenan ita haka kowa zai tafi
ya barta. Ita an kawota gidansu ita kuma za'a maidata gidansu. Itakam data san
hakane kawai kowa yay zamansa gidansu. Dariya sosai Malikat Haseenat da Daneen
Waheeda keyi da drama din tasu. Dan wata shakuwace ta musamman ta sake shiga
tsakanin Iffah da Mamyn (Daneen Ammarah) taja yarta jikinta sosai da sake tabbatar
mata da kaunar da take mata dabance a rayuwa. Haka itama Iffah'r tana kaunar
mahaifiyar tata matuka duk da bata rayu da ita ba. Sannan tana kaunar Ummu dinta da
Baby. Hanash Akhi kam ai shi na musamman ne gareta da Kakanta abin alfaharinta.
Kullum cikin lallabasa take shi da lyyani su dawo cikin masarautar da zama ko zata
dan ji saukin kewarsu da tayi. Shi dai ya nuna bazai dawo ba. Amma Tajwar Eshaan ya
ce ta kawantar da hankalinta zai dawo mata dasu, Ba karamin farin ciki tayi da
hakan ba.Dan shima Babiy an gyara masa gidansu sosai dan bazai iya barinsa ba
saboda gidan gonarsa.

Lokacin da za'a wuce da Daneen Ammarah sai gashi tana kuka, ta rungume Malikat
Haseenat da Iffah sunata kuka. Da kyar Daneen Waheeda da Malikat Ashwaq suka rabasu
aka fita da ita. Yau kuma sai dakin mijinta ban yarta.

Tarbace ta mutuntawa suka samu da ga su Ummu, kowa halayen Ummu na birgesa, dan
mace ce data amsa sunanta cikakkiyar mace jaruma abin koyi da nunawa a duniya ga
kowa, Yan kawo amarya basu wani jima ba suka wuce abinsu. Lokacin da ango zai shigo
Ummu da kanta tayo masa rakkiya cakin amaryarsa. Zata gudu Daneen Ammarah tace
saifa ta zauna sunyi hira. Babu yanda Ummu ta iya dole ta zauna. Sai dai hirar ma
dai duk akan rayuwarsu ta bayace data shude. Kuruciyar Iffah da su Arfa Daneen
Ammarah har kuka tayi, ta jinjinama hakuri irin na Ummu. Ta kumayi alkawarin
kyautata zamansu tamkar yan wan juna har abada. Zasu zama aminan juna bawai
kishiyoyi ba. Ganin dare yaja da wayo Ummu ta tattare kwanikan da sukaci abinci ta
gudu. Dama shi Hanash Akhi yana can masarauta Iffah ta rikesa wai shine
amintaccenta, nan ko duk wayone dan taita gain dan uwanta ne. Dan babu wani abu da
yake yi sai idan sun dan shiga fada zatai wani zama mai muhimmanci da manyan
masarautar ya kasance a gefenta. Hakan sai ya saka mata zaman lafiya da Tajwar
Eshaan sarkin kishi, dan tana ambata maganar Hanash Akhi dinne zai kasance
amintaccenta harda kyauta sumba aka bata. Wai hakan shine dai-dai.

Ummu na fita Babiy sauka yay kasa gaban Daneen Ammarah ya zabga tagumi ya wani
zuba mata idanu. Murmushi tayi da jan mayafin jikinta ta rute fuska cike dajin
kunyarsa. Ya lumahe idanu da budewa yana murmushin shima, Kafin ya mike tsaye ya
yaye mayafin gaba daya ya kama kafadunta ya mikar da ita ya rungume abinsa. A tare
suka dinga sauke ajiyar zuciya, sai kuma hawaye na tsananin kewa da tuna baya.

"ALLAH na gode maka daka maimaitamin wannan rana a rayuwata. Ka gamamin komai
UBANGIJINA daka bani mafi tsadar nan a cikin mata matsayin matata"

"Ni zan godema ALLAH da samunka matsayin miji kuma uban yayana Zayyan. Tare da
yar uwa jaruma Saliha irin Jumaymah. Yanda kuka sharemin hawayena, da zama silar
canja labarin da ban taba tunanin zai canju daga kaddarata ba kuma ALLAH ya share
naku hawayen. ALLAH ka hana shaidan shiga tsakaninmu. Nayi alkawarin in har inada
rabon sake haihuwa a duniya zan malakama Jumaymah (Ummu) yayan nan har abada".

Cikin rada-rada a kunenta ya furta, "Insha ALLAHU a yau din nan zan dasa kwam
Arfa da Fariha gimbiyata." cike da jin kunyar furicin nasa ta wani kankamesa da
boye kanta a jikinsa. Wani irin rungumeta tsam-tsam Baby ya sakeyi shima yana
dariya, tare da bata sumbata tako ina a jikinta harya sauke akan lips dinta, Jin
tsaiwar na neman gagararsu ya dauke abarsa tsamm suka shige daga ciki, dama dai ga
Daneen Ammarah yar dum-dum kai kace bata wuce talatin a duniya ba. Jin an rufo kofa
harda murza key nayi baya dan wanna fagen na manya-manya ne ba gain kanana irimmu
ba 🥱😉😂🚴

* BAYAN WATANNI SHIDA DA FARUWAR YAKI TSAKANIN SU SHAHAN-SHAN DA SU UWA

Kai kawo yaketa famanyi a cikin bedroom din nashi bakinsa dauke da addu'a. Duk ko
yanda waya ta motsa sai ya daga da tsammanin su Malikat Haseenat ne. Babu abinda
yafi burin ji a wannan gabar kamar ace ALLAH ya sauki Sohaa dinsa dake nakuda tun a
daren jiya lafiya. Duk yanda yake da tarin ayyuka a fada ya kasa fita. Su Sayeed
Fayzul-haq ma sun hakura da fitowar tasa yau tun sanda labarin nakudar Iffah'r daya
iso kunensu. Sai kowa ya koma fatan saukarta lafiya.

Daga wayar da tai dai-dal da bugawar agogo karfe sha biyu dai-dai na raar
litinin din ya wani irin sauke ajiyar zuciya da zama cikin kujerarsa a hankali.
Murmushi ne mai sanyi ya subuce ma kyakykyawar fuskarsa. A hankali ya motsa lips
dinsa ya ambaci "Alhmdullah"., Sai kuma hawaye suka dan ciko idanunsa. Shi Eshaan
Ibn Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb ne yau ALLAH ya azurta da kyautar yayan har guda
biyu mace da namiji daga jikin yar uwarsa kuma matarsa, farin cikinsa Fhareedah
bint Zayyan. A take bakin ciki da kuncin dake tare da zuciyarsa a cikin watanni
shidan nan yaji ya wani fada masa daga makoshi zuwa cikin ciki. Babban yatsarsa ya
kai a idanun nasa a hankali ya dauke hawayen da sake furta. "Abbie an haifo maka
jikoki har guda biyu a rana daya, lokaci daya da ga tilon danka. Insha ALLAHU za'a
sake haifo maka wasu biyun kamar haka har sau hudu Abbie na. ALLAH ya gafarta maka,
ALLAH ya yafe maka kurakuranka kai da Jaddi da ma duk zuri'ata data musulmi baki
daya. Kai da Jaddi da Jaddah ne abin AL'FAHARINA ABBIE NA"……✍️

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (94)

*_MAAB LUXURY HOME._* _Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini.
Ina uwar gida da Amarya, Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano
state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook
@maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._

_____________________

.........Cikin ƙanƙanin lokaci zancen haihuwar Iffah ya karaɗe ƙasar ruman baki
ɗaya. Tuni farin cikin kowa ya bayyana, tare da addu'oi ga waɗan nan jinjiraye da
ga bakin al'umma. Yayinda Tajwar Eshaan daya matsa a kai masa su ke can rungume da
kayansa tsam-tsam a jiki. Jinsa yake a yau ɗin kamar wani sabon mutum, final shima
dai ya zama Abbie. Ga yaran sun ɗakko kamanninsa sosai musamman ma mace kamar an
tsaga kara an karya da shi, gara namijin yafi rinjaya da Iffah shi kuma. Da kansa
ya tauna dabino ya basu tare da musu huɗuba.
Duk yanda yaso ganin Sohaa ɗin sa hakan bata yuwuba sai bayan la'asar tai
barcinta ta huta sannan. Murmushi ta dingayi kanta a sinne saboda irin kallon nan
na ƙasa-ƙasa da yake faman binta da shi. Duk sai taji kunya ta lulluɓeta. Har ya
ƙaraso gaban gadon bata yarda ta ɗago ɗin ba sai da ya zauna a kusa da ita ya ɗago
fuskar tata da kansa. Bai tsaya wata wata ba kawai ya manne lips ɗinsu waje guda.
Sai da yayi yanda yake so da ita ya barta dan kansa sannan ya rungumeta yana jero
mata daɗaɗan kalamai masu sanyi da ratsa zuciya da bata san yayi nisa a sani ba har
irin haka. Jitai kawai idanunta sun cika da ƙwalla. Dan ita kanta bata san adadin
ƙaunar da takema wannan bawan ALLAH ba zuwa yanzun. Tana jinsa daban a cikin daban
a duniyarta. Shi ɗin na musamman ne a gareta fiye da yanda yake jinsa na
musamman...

Lokacin da aka kaima Malikat Bushirat da har yanzu ake nan yanda ake babu
abinda ke motsi sai kai da ido Jasrah baiwar ALLAH nata wahala da ita kuka sosai ta
fashe da shi. Suko yara kamar sun san inda aka kawosu suka wani dage da tsanyara
kuka tsiyau-tsiyau kamar ƴaƴan magena da yau mukasha bikin sunansu (Na manta ban
faɗa muku ba magena ta haihu ƴaƴa hudu kowa sai ya kawo kayan barka haihuwar fari
ce babu ɗaga ƙafa😂🚴🥱) kuka sosai suka dingayi har abin ya bama kowa mamaki, ana
fita da su sukai shiru kuma kamar basu ba. Koda aka maidasu anan bama Malikat
Haseenat da Iffah labari murmushi kawai Iffah tai batace komai ba. Garama Malikat
Haseenat tsohuwar ƙwarai ta tofa kaɗan.
A can ko jikin Malikat Bushirat rikicewa yay sosai. Dan har sai da takai an
kira Shahan-shan da Malikat Haseenat. Al'amarin kam yau dai bana wasa bane. Dan
doctors da suka rufu a kanta ma dai sunyi iya ƙoƙarinsu amma bata bar jijjigar da
ta dingayi ba, daga baya ma sai ga aman jini. Hankalin kowa ya tashi musamman
Tajwar Eshaan, dan da kansa ya hau gadon ya rungumeta jikinsa ta dinga bulesa da
aman jinin nan. Addu'a ya dinga tofa mata, ganin fa tafiyar mai tsaho ce Malikat
Haseenat ta fara maimaita kalmar shahada ko za'a dace Malikat Bushirat ɗin ta
karɓa. Hakan yasa suma sauran jama'ar dake a ɗakin suka dinga maimaitawa, Jasrah
dai kuka take kamar ranta zai fita. Sai dai kuma ita rayuwa duk yanda kaso, bai
zama lallai abinda kaso ɗin ya kasance a yanda kaso shi ba. Dan kuwa dai Malikat
Bushirat ta koma ga UBANGIJI batare da ta iya neman gafarar koda ɗan cikinta tilo
data jefa kanta a halaka domin haihuwarsa ba. Tayi mutuwa mai ban tsoro da tashin
hankali, dan kuwa maimakon kalmar shahada da suka so ji daga bakinta sunan UWA ne
ƙarshen ambaton ta cikin wani irin gurnani mai ƙarajin gaske daban tashin hankali.
Wannan al'amari ya matuƙar kiɗima Shahan-shan. Dan jikinta na gama saki shima ya
kife kansa akan fuskarta. Tsahon lokaci bai ɗago ba har sai da kowa ya fita a ɗakin
Malikat Haseenat tazo tana lallashinsa. Sannan aka samu ya ɗago idanun nan nasa
jazur matuƙa abin tausayi, sai dai baiyi kuka ba, ya jima yana kallon fuskar
mahaifiyar tasa abubuwan data lissafa ta aikata na dawo masa tiryan-tiryan kamar
yanzu take yinsu....

Masarautar gaba ɗaya ta gama rikicewa. Dan mutuwar nan kam ta daki kowa
musamman da Malikat Bushirat ta zama tamkar wata tauraruwa a zamaninta a cikin
gidan. Sai dai yanda mutuwarta tayi dai-dai da mutuwar kaf mutanen nan ƴan ƙabilar
uwa abin ya bama kowa mamaki. Dan kamar waɗanda aka shayar guba kawai aka samesu
duk a mace su kusan goma sha uku. Dama wasu sun ɗan mummutu ɗaɗɗaya. A yanzu dai
kam Uwa kawai ta rage a raye. Itama ɗin dai sai a hankali dan duk ta ƙara wani irin
yamushewa na tashin hankalin faɗuwa ƙasa da tai. Wai yau itace mai zaman kurkuku a
cikin masarautar ruman kuma da ranta da lafiyarta tsahon watanni shida. Ai ko'a iya
haka aka tsaya ta gama kunyata a wannan duniya.

Jasrah ce ta mata wanka tana kuka abin tausayi ita da yayarsu Badiha. Bayan
an mata sutura aka fiddota Tajwar Eshaan ya jagoranci sallatarta tare da miƙata
gidanta na gaskiya aka barta da halinta kuma. Dan ya rage ita da UBANGIJINTA. A
yanzu kam. Wannan itace ranar da ya kama kowa ya kasance yana gudu a rayuwarsa. Dan
ko kaƙi ko kaso sai tazo. Ko kai mutumin kirki ne kona banza ne ma dai sai tazo. Ko
shekara dubu bisa dubu zakayi a duniyar sai tazo. Koka shirya ko baka shirya ba sai
tazo. Yau dai gashi Malikat Bushirat ta tafi tafiya ta har abada. An shafeta an
shafe babinta dama iyakarta kenan akan duk wani abin kirki ko ɓarna da zaka shuka a
duniyar....
Tajwar Eshaan bai samu hawayen dake riƙe da maƙoshinsa sun zubo ba sai da yaje
ya rungumi ƴaƴansa da matarsa sannan. Kuka yayi sosai Iffah na tayasa. Sai da
sukayi mai isarsu abin tausayi. Ranar ma har zazzaɓi yayi dole Iffah ta kwana tare
da shi da ƴan yaransu da sukaci sunan Ajwaad da Ajwaa (Dan su bawani al'adar suna a
sati ɗaya suke ba ba irin ƴan 9ja bane😝). An dai yankama yara raguna da shanu akai
sadaka a washe gari tunda ranar mutuwar Malikat Bushirat ta hana. Gida kam ya cika
maƙil, ƴan gaisuwa da taya murnar haihuwa ta ko ina ketowa suke. Su Mamy (Daneen
Ammarah) sun zo suka kwana itama da cikinta ɗan watanni biyar da wasu kwanaki. Da
alama dai zancen Babiy ya tabbata. Ita da Ummu idan ka gansu abin sha'awa kamar
yaya da ƙanwa. Sai ma shirye-shiryen bikin Hanash da sukeyi dan shikam ya koma ɗan
ɗakin Mamy, Iffah dai na nan ƴar gaban goshin Ummun ta kuma autarta. Dan duk
ƙurarta idan ta yaya Ummu dai, itace abokiyar shawararta itace abokiyar sirrinta.
Sai an gama Mammy kanji da Babiy. Iyakarsu dariya idan na dariyane. Idan na fatan
alkaicine kuma suyi addu'a. Iyyani da kaka kuwa ai dama tuni sun dawo cikin
masarautar. Ko yaushe zaka sami Iyyani tare da Malikat Haseenat ne da ƙanwarta
Yamma. Tsaffin sun matuƙar haɗe kansu sun zama iyayen kowa. Hakama Kaka da su
Sayeed Fayzul-haq sun zama aminan juna dattijan ƙwarai kuma a masarautar kuma
iyayen kowa har shi kansa Shahan-shan ɗin....

*_BAYAN WATTANI UKU DA HAIHUWAR IFFAH DA MUTUWAR MALIKAT BUSHIRAT (BIKIN


AL'ADA)_*

Kamar kowacce shekara a wannan karon ma tarin al'ummar ƙasar ruman da


kewaye sun cika birnin Dahab da akafi sani da DAULAR RUMAN tako ina domin gudanar
da bikin wasan al'ada. Kowa ka kalla a wannan karon yasan wasan na musamman ne
sannan ana gudanar da shine cikin tsafta da nutsuwa. Duk wani wasan ganganci da
za'a iya rasa rayuka an kafa masa doka, hakama matakan tsaro tako ina an baza domin
kare kowa da kowa. Duk wani boka ko ɗan bori ko malamin tsubbun an hanasu yin
kowane motsi a yanzu. Dama yanzu kam dokane, in har aka kamaka to hukuncin kisa
kawai ake yanke maka.
A yau kam Iffah taga mutane da yawa da suka kawoma Shahan-shan gaisuwa. Ciki
harda Sir Fawzan da tuni yay aurensa. Tare da yaran Shahan-shan su Azaan da a yau
kam sukaita faman sinne kai na kunyar abinda ya faru tsakaninsu da ita a shekarun
baya. Ita dai murmushi ma ta dingayi, shi kansa uban gayyar Shahan-shan murmushin
yaƙe yi dan kawai ba'a ganin fuskarsa ne. Su Ajwaa da Ajwaad sunsha addu'oi yau a
wajen mutane. Duk da ma bawai kowa ake bamasu ba. Yaran sunyi ɓul-ɓul abinsu gwanin
sha'awa. To mi yafi ransu suna samun kulawa da tattali da soyayyar iyayensu. Dan
zuwa yanzu ma dai kam Iffah ta tattara inata-inata ta koma sashen Shahan-shan ɗin
gaba ɗaya ita da yaranta. Dan yace shikam babu wani sashen matarsa da ban nasa
daban. Idan ka ganta a sashenta sai in tayi baƙine ko yin wani abun dai tunda babu
mai hurumin zuwa sashen Shahan-shan ɗin sai ita. Hatta da amintaccensa ma zuwa
yanzu iyakarsa hawa na na uku ne kawai, idan ka gansa a hawan ƙarshen sai
ƙwaƙwƙwaran dalili.....

★Alƙawarin ALLAH ya cika akan zartar da hukuncin su Miran Jasim da Miran


Arshaan a yau. Dan kuwa wanda ya kashe dole ne a kasheshi. Hatta da malikat
Bushirat Tajwar Eshaan ya gama yanke hukunci a yau ɗin zai zartar da hukunci a
kanta irin hakan sai ALLAH kuma ya ɗauki ranta kafin zuwan yau ɗin. Sosai al'amarin
ya girgiza kowa matuƙa, musamman ganin iyalan Miran Jasim ƙalilan ne a cikinsu suka
koka saboda wahalar daya basu a rayuwa. Shi dama Arshaan ba'a ajiye kowa ba. Amma
duk da haka Jasrah mai karyayyar zuciya sai da tai kuka. Al'ummar ƙasa sun taru
wajen nema musu afuwar ƙarƙashin cigaba da zama a cikin kurkuku tsahon rayuwa.
Hakan yasa duk sai jikin Tajwar Eshaan ɗin yay sanyi, dan shima yanajin ɗaci fiye
da irin ɗacin da kowa ke ji kasancewar su kaɗai ne Uncle's nasa makusanta da
mahaifinsa da suka rage a duniya sai mata. Ganin dai jama'a sun dage ɗin kuma harda
iyalan Sayeed Khairul-Bashar da kansu dana Sayeed Hifzur-rahaman ɗin suma yasa aka
maidasu cikin kurkukun a bisa sassaucin ɗaurin rai da rai. To saima dai ta ALLAH
dan shi Miran Jasim ma bawani cikakkiyar lafiya ce da shi ba. Hatta Miran Arshaan
ɗin kansa kawai dai a rufe rufau ne.
Uwa kam da aka fiddo cikin sarƙa cike da ƙarfin iko kowa ke shelanta a
kasheta!! A kasheta!!! A kasheta!!!. Kallonsu kawai take tana kuka da dariya da
kiran sunayen gumakansu duk a lokaci ɗaya. A haka aka ɗaureta jikin ƙarfen. Mutane
zasu fara jifanta da dutsina aka dakatar da su. Dan wannan aikin ba nasu bane na
mai gayya da aikine da kansa tare da matarsa. Bayan lafawar kowa fiye da yanda ake
buƙata Shahan-shan ya fito hannunsa na dama riƙe da na Iffah, na haggun rungume da
Ajwaa da aka canjama gayu ita da Ajwaad. Da shi kuma ke a hannun Iffah. Masha ALLAH
aka shiga ambata, dan a zahirinsa ya fito ga mutanensa babu wani shamaki yana son
su gansa ya gansu. Haka itama Iffah duk jikinta a rufe amma fuskarta a bayyane ga
al'ummar ƙasarta. Bayan sunyi gaisuwa ga al'ummar ƙasar su da fatan alkairi aka
kawo kwari da baka na tsire Uwa da zasuyi. Iyyanni da Malikat Haseenat ne da ke
tare da su suka amshi twins, yayinda Tajwar Eshaan ya kamo hanun Iffah a hankali
cikin nasa yana kallonta ƙasa-ƙasan nan nashi ya tsayar da ita gabansa. Matsawa yay
ya jingina jikinsa a nata tare da kamo duka hannayen nata biyu cikin nashi ya saka
mata kwarin tare da ɗaga hannayen nasu a tare ya daidaita su sannan ya daidai
mashin da zasuyi amfani da shi cikin bakar saitin manya-manyan idanun nan na uwa da
ke kwasar dariya da kuka kamar sabon kamu...........✍️

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA


09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (95 END)

______________

*_MAAB LUXURY HOME._* _Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini.
Ina uwar gida da Amarya, Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano
state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook
@maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*_.

__________________

..........Wata irin mahaukaciyar razananniyar ƙara ta saki lokacin da kibiyar


mashin ke sauka a cikin idonta ɗaya. Kafin ta gama dawowa cikin hayyacin azabar
data shigeta suka sake soke ɗayan ma. Tuni jikinta ya shiga matsanancin karkarwa ta
cigaba da ihun ambaton gumakansu. Na uku kama sai da suka saita maƙogwaronta sannan
suka sakeshi. Kakari ta shigayi irin na mai fitar rai. Yayinda al'umma ke ta faman
kabbara. Gaba ɗaya Iffah ta juya ta rungume Shahan-shan tsam-tsam ta fashe da kuka.
Hannu biyu ya amshi abarsa ya rungume ko tuna ɗunbin mutanen dake a zagaye da su ma
bayayi. Ai tuni jami'an tsaro da Ghazi dake zagaye dasu suka musu zobe, yayinda
ƙatuwar umbrella ta musu runfa daga sama. Ganin wannan damar ta samu Shahan-shan ya
ɗago fuskar sohaa ɗinsa ya manne lips ɗin sa a kan nata cike da ɗunbin so da ƙauna.
Murmushi mai sanyi da ƙayatarwa kawai Malikat Haseenat tayi ita da Iyyani....

Shike nan kuma an shafe da babin Uwar mushirikai itama. Wanda mutuwarta
itama kuma yay dai-dai da haihuwar Daneen Ammarah ta samɓalo ƙyaƙyƙyawar ƴarta mace
mai kama da babiy. Ai sai bikin al'ada ya cigaba dana murnar haihuwa, yarinya taci
suna Arfah. Zo kaga farin ciki wajen Iffah Nina Arfa ɗin ta ta sake dawowa. Daneen
Ammarah kuma ta cika alkawari, dan a ranar a gaban kowa ta damƙa Arfa ga Ummu. Ummu
tasha kuka matuƙa Mamy na tayata. Daga ƙarshe ta dawo mata da Arfa akan ta bata
shawayarwata har yaye. Babiy da Kaka dai nasu murmushi ne hakama Hanash da shima
matarsa ɗauke take da ƙaramin cikin itama dan tanata fama ma da laulayi.....

*_BAYAN WASU SHEKARU_*

Abubuwa da yawa sun faru, wasu masu daɗi wasu marasa daɗi. Wasu a tuna wasu
baza'a ma iya tunawar ba. Haka rayuwa ta gada dama. Zuwa yanzu kam zamu iya cewa
hankalin Iffah da Tajwar Eshaan ɗinta ya kwanta sosai, dan manyan matsaloli dai sun
ɗan ragu musu musamman wanda suka shafi tsafe-tsafe da sauransu. Amma na maƙiya kam
har goben-gobe a kwaisu. Dan duk inda bawa yake, komai ƙyautatawarsa ya sani akwai
wanda su burinsu kawai cin dunduniyarsa. Ƴar uwa karki damu, kamar yanda Bily bata
damuwa. Dammu masoyanmu sun wadatar damu😘. Haka dama rayuwar take dole ka kasance a
zagayen abu biyu, (Masoya da maƙiya) idan ka kwantar da hankalinka duka sai su
amfanar da kai. Idan har MANZON ALLAH da yafi kowa a halitta, ɗan gatan ALLAH zai
fuskanci ƙalubale na maƙiya, masu hassada da kushen abinda yazo da shi daga umarnin
UBANGIJI kai waye da bazaka samu kanka da irin waɗan nan mutanen zagaye da kai ba.
Kai dai kawai yi abinda zaka iya, kuma ƙyautatama duk wanda ke tare da kai maƙiyi
ko masoyi duk zakai alfahari da hakan wataran. Wannan shine abinda su Iffah da
Tajwar Eshaan suka haƙƙaƙewa rayuwarsu da zukatansu suka zauna lafiya. Sun ajiye
komai, basa ganin komai sai kansu da masoyansu. Sun fi kallon masoyansu fiye da
tuna maƙiyansu, suna shimfiɗa mulki a tare cikin gaskiya da riƙon amana, randa suka
sami saɓani kuma sukan binne a tsakaninsu suyi haƙuri dan yau da gobe sai ALLAH.
Duk inda zo mu zauna take sai ka samu zomu saɓa.
Iffah ta ƙara haihuwar ƴarta mace taci suna *_Bilqeesa_* (Dan bazanyi a
banza ba sai na ma kaina takwara a ƙasar ruman ehe🥱😂). Ajwaa da Ajwaad sun girma
abinsu masha ALLAH. Yara ƙyawawa da ke samun soyayya ga mutane, wasu ko basu da
wanda suka tsana kamar su a yanzu musamman ma Miran Ajwaad da kowa kema kallon
magajin mahaifinsa. Sai dai kuma babu abinda suka isa yi dan tun ran gini tun ran
zane.
Burin Iffah ya cika akan karatu, inda a yanzu haka ta zama cikakkiyar ƴar
jarida koma muce shugabar gidan jaridar nan na *African eye* da mijinta ya kafa. A
zahirance dai kamar yanda yake ɓoye kansa a baya itama haka take ɓoye kanta a
yanzu. Sai dai rubuce-rubucenta da zaƙule-zaƙulen sirrikan munafukai na matuƙar
tada hankalin wasu. Dan a duk lokacin da tai wani rubutu game da wata ɓarnar da
akeyi koma ta fitar da muryar wasu da abin ya shafa kusan duniya ɗauka take aita
cecekuce musamman da ya kasance bayan kafofin yaɗa labarai a yanzu social media ma
na taka rawar gani akan yaɗa abu cikin sauri. Sai ta gama zaƙulowa da tallace mutum
mijinta kuma gwarzonta ya zama gaba-gaba wajen hukunta mai laifin idan a ƙasar sa
ne. Idan ba ƙasarsa bane zai yi duk yanda zai yi ga shugaban da ke shugabanta ƙasar
da mai laifin ya fito dan ganin an hukuntashi, cikin ƙananan lokaci sunan da take
amfani da shi yay wata irin amsa kuwa, mutane har zalamar jiran fitar wani abu da
ga African eye sukeyi, dan sun san mai amfani ne kuma na gaskiya ne. Takanyi
ayyukanta a gida, idan kuma fitar sirri ta kama sukanyi ita da Mijinta harma subar
ƙasar batare da wani ya sani ba koda a masarautar ne kuwa.

★★...
Ƙoƙarin kamota yake tana zillewa, ya kwaɓe fuska da ɓata rai kamar gaske. Gwalo
ta masa da ga inda take tana cigaba da dariyarta mai narkar da shi.
A hankali ya furta, “ALLAH Sohaa karki bari na kamaki, kizo nan na yarda zamu
raba 50-50”.
Kafaɗa ta maƙe masa tana mar-mar da idanu da tura baki gaba. Fuskarta a shagwaɓe
ta ce, “Naƙi wayon sai dai na baka 30 na ɗauka 70”.
“Tunda na fara jin tsoronki ko?”.
Ya faɗa cikin ɗage gira sama. Baki ta ɗan murguɗa masa itama. “To dama ai tun
tuni tsorona kake ji”. Murmushi ne ya suɓuce masa, shi baima san yanda zaiyi da
tsiwar yarinyar nan ba. Fitinanniyar yarinya ce ta bugawa a jarida, yara uku har
yanzu bata san ta girma ba. Hannayensa ya tura cikin aljihunsa wandonsa har yanzu
fuskar tasa da murmushi ya nufeta. “Okay shikenan na yarda 30-70 ɗin, sai dai yanzu
yarana najin yunwa zo muje a fara cin abinci amma da sharaɗi”.
“Nami?”.
Ta tambaya tana matsawa da baya-baya. Tana ganin ya kusa isa inda take tai
yunƙurin sake zurawa da gudu. Wani ɗan tsalle yayi ya cafkota, bai saurari ɗan ihun
da take masa na taɓara ba ya murɗe hannun ya amshe ɗan box ɗin dake cikin hannun
nata. Cak ya ɗagata ta shiga watsal-watsal da ƙafa. Dariya ya shigayi ganin yanda
take kukan taɓara da faɗin ita sai ya bata abunta. Sai da ya zauna akan kujera ya
ɗaurata a kan cinyarsa sannan ya dungure mata kai da faɗin, “K yarinyar nan
rigimarki tayi yawa, wai nida abuna”.
Da sauri tace, “Nawa dai, dan 30 ne naka a ciki”.
“Tun kan kiji sharaɗin nawa ma kin yanke hukunci”.
“Ka faɗi sharaɗin mana banga wanda bazan iya ba”.
“Okay haka kika ce?”.
“Eh”.
Ta faɗa cike da ƙarfin gwiwa. Murmushi yayi ya ce, “Okay muje a fara cin abinci mu
dawo zamu gani ai”.

★Kamar ko yanda ya faɗa yaransu na zaune a falo zaman jiran fitowarsu.


Balqeesa dake tsalle-tsallenta ita kaɗai da gudu ta nufesu, a hankali ya kai duƙe
fuskarsa da ƙayataccen murmushi dan a rayuwarsa yana matuƙar ƙaunar yaransa, bai
haɗa su da komai ba. Hakan kuma bai hanashi tsayawa akan tarbiyyarsu ba. Mulkin
al'umma kuma bai hanashi shaƙuwa da su ba, rungumeta yayi tare da miƙewa da ita a
hannunsa duk da kuwa takai shekaru shida a duniya. Cikin ƴar muryarta ta ce, “Abbie
ina sonka kai da Ammie”.
Idanunsa ya lumshe fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce, “Muma muna sonku mai
gadon zinari na”.
Sosai yarinyar ta ƙanƙamesa tana dariyar jin daɗi. Kallon juna sukai shi
da Iffah suna murmushi. Dai-dai nan Ajwaa da Ajwaad suka iso garesu suma. Yara masu
nutsuwa da shiru-shiru kamar mahaifinsu. Suma hannu ya miƙa musu alamar suzo
garesa. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka rungumesa. Baki Iffah ta zumɓira ita a
dole taji haushi. Murmushi yayi itama ya mata alamar tazo. A hankali ta matso
jikinsu tana murmushi ya haɗesu gaba ɗaya ya rungume........✍️

*_🥱To nima dai na haɗaku gaba ɗaya na rungume masoyan albarka ababen
alfahari. Alkairin ALLAH da rahamarsa da ni'imarsa sukai gareku ku da zuri'armu
baki ɗaya._*

*ALHAMDULILLAHI🙏*

_Ya rabba na gode daka kawoni wannan rana badan iyawata ba ko dabaruna. Ina
roƙonka ka yafemin kurakuraina, abinda ya kasance dai-dai a cikin wannan ɗan
littafi ya rabbi ka haɗamu a ladan. ALLAH ka amfanar damu amfanin cikinsa, wanda ya
kasance mai cutarwa ALLAH ka hanashi tasiri a zukatanmu.🙏_

Bazan gaji da faɗa ba. Rubutun nan nishaɗine. Fadakarwa ce. Wani lokacin ma
harda ban haushi. Wasu abubuwan akan saka ne kawai domin ayi nishaɗi. Ina roƙonku
yin watsi da duk abinda bamai amfani ba a ciki.

_Mungode! Mungode!! Mungode masoyan Zafafa. Alkairin ALLAH ya kai gareku, yanda
kuka kasance damu kuma ALLAH ya kasance daku cikin rahama da amincinsa. Yanda kuka
somu domin ALLAH kuma ALLAH ya soku haka_

*_Yanda muka fara lafiya muka kammala lafiya ALLAH ya haɗamu ana gaba cikin
lafiya da nutsuwar zukata. Wanda duk naima kuskure ko ba daidai ba dan ALLAH ya
yafemin a yayin wannan rubutun ajizanci ne banda burin ƙuntata kowa koda da magana
ne🙏. Ngd Ngd sosai masoya ƴan DAUƊAR GORA CONVERSATION, ku ɗin na dabanne a cikin
daban gareni. Alkairin ALLAH ya kasance daku a duk inda kuke. Ku na dabanne a
zuciyar Bilyn Abdull 😘😘Nikam kune Sohaas ɗina TAURARINA⭐._*

*Bilyn Abdull ce 😘😘🙏*

*_ƙaunarku nake irin trillions ɗin nan🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰😘😍😘😘_*

_🙈🙈Yau sunan magena har yanzu banga kun fara kawo kayan Barka ba 😂😂 fa. Bye bye idan na
mutu da ga nan kowa ya yafe min_

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_


_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD,


INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_


_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA


Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN
MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

You might also like