Huriyya1&2 Complt by Khadeeja Candy

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 536

https://chat.whatsapp.

com/LimnMeG0kWvIfT6JQvVMh1

☆❁ 𝗛 𝗨 𝗥 𝗜 𝗬 𝗬 𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

*©®Hakkin mallaka nawa ne ni Khadeeja Candy, ban yarda a sarrafamin labari ta


kowace siga ba balle har a dorashi a Website ko YouTube ba tare da izinina ba, yin
hakan kuskure ne babba domin zai iya janyowa mutum matsala saboda haka a kiyaye ⚠*

Wannan Littafin Sadaukarwa ce ga.

Zainab A Baba Abokiyar Hira.

Asma'u Badamasi Bauchi

And

Hafsat Muhammad Betuwa Maman An-noor

i appreciate your love 🥰❤

H U R I Y Y A -Labari ne mai ban tausayi da taɓa zuciya. Story of the 2nd October
2023

𝐑𝐚𝐧𝐚𝐤𝐮𝐧 𝐏𝐨𝐬𝐭𝐢𝐧𝐠 𝐌𝐨𝐧𝐝𝐚𝐲 𝐓𝐮𝐞𝐝𝐚𝐲 𝐖𝐞𝐝𝐧𝐞𝐬𝐝𝐚𝐲 𝐓𝐡𝐮𝐫𝐬𝐝𝐚𝐲 𝐅𝐫𝐢𝐝𝐚𝐲.

Idan kina da wani abun da kike so a tallata miki you can chat me on 08036126660 or
https://wa.me/qr/3D4THFJXLUGTM1

Bismillahi Rahmanin Rahim...

1️⃣
1️⃣
𝗣
𝗲
𝗴
𝗮

Babban gidan sama ne mai dauke da bangare biyar, na farkon da na biyu zuwa na uku
da hudu sukansu suna facing din babban gate din gidan. Yayinda dayan wanda shi ne
na biyar yake dama da part din hudun, dukannin part din suna da karamin gate da
zaka iya hango wanda zai shiga ko ya fita, haka zalika ko wane part yana da gurin
aje mota kamar uku sai kuma karamin filin da za a iya wata hidimar idan da bukata.
An kawata kowane entrance na parts din da fulawowayin na kasko, a ko wane bangare
akwai kujeru da aka tanada domin hutawa ko shan iska.

Babbar harabar gidan wani katon fili ne da za a iya gina kananan gidaje hudu ko
biyar, ko wace kusurwa da ginin na jikin gidan an dasa masa dagayen itatuwa,
tsakiyar compound din kuma an yi masa round da flowers. Ko masu gadin gidan kadai
ka kalla ka san ba kananan kudi suke samu ba, balle kuma ka sauke idonka akan
manyan motoci da aka jere a harabar da aka tanada domin aje motocin Alfarma, bayan
mota biyu wasu daya wata uku da suke aje a kowane bangaren uku da suke gidan.
End of discussion shi ne sunan da mafi akasarin jama'ar unguwar suke kiran gidan
da shi, ba a unguwar Millions Quarters ba kawai, kusan duk wanda yake cikin garin
Gusau ya san gidan Alhaji Haruna Mai Yadi, saboda yadda jama'a suke yawan labarin
gidan da irinsa a rare a garin Gusau. Kasancewar ba kowa yake damuwa ya gina gida
mai kyau da fasali kamar yadda shi ya zabi ya bayyana nashi arzikin ba a fili ba.

A cikin part hudu da suke gidan uku ne suke dauke da iyalai yayinda dayan da ya
banbanta da saura kuma ya kasance na Alhaji Haruna Mai Yadi, part din farko na
Hajiya Kaltume ne uwargida ran gida, wato Uwargidan Alhaji Haruna a yanzu, sai mai
bi mata Hajiya Nafisa da ake kira da Momy, sai ta ukunsu wadda ta zama turmin
tsakar gida hausawa suka ce sha luguden mahassada wato Hajiya Iyami ake kira da
Amma. Dayan part din wanda shi ne cikon na hudu, part ne da ba a taba zamansa ba,
kasancewar matansa uku ne a yanzu tsabanin hudun da ya ci burin yi.

A kowane part akwai dakin yara na maza dabam na matan dabam, akwai sitting room har
biyu karami da babba, sai bedrooms din ko wace mata dake dauke da mayan furnitures
na alfarma, dukannin furniture din parts din iri daya ne sai dai kala ta banbanta.
Na dakin Hajiya Kaltume red color ne tun daga kan kayan dakin kujeru har zuwa
curtains dinta, sai dai an yi musu ado da ratsin golden hakan ya kara musu kyau
gashi yaranta na taya ta gyara bangarenta kasancewarsu yan mata masu wayo da son
kwalliya domin yan matanta hudu, Umm Kultoon wadda ta ci sunan mahaifiyarsu ake
kiranta da Maama, sai mai bin ta Umm Salma, Umm Khairi, da kuma yar auta Umm Ruman,
sai dai dukansu suna bin bayan babban ďanta Yassar ne da ya kasance namiji daya
tilo a yayanta.

Bangaren Hajiya Nafisa kuma wato Momy ta kawata nata bangaren ne da ash color,
white curtains dinta ne kadai suka banbanta da Turkish cushion din da suke falon
ita ma tana da yaya uku mazanta biyu Musib, Miwan sai auta mace Namra.
A dayan part din kuma wanda ya kasance na Hajiya Iyami wato Amma ya fita
dabam da sauran dakunan domin komai nata na daki da falo fari ne fol, irin farin
nan mai kyau da burge idon mai kallo, duk kuwa da kasancewar nata yaran kanana ne
Hurriya sai mai binta Hamad sai kuma cikin da take dauke da shi a yanzu, ita ce
karama a cikin matansa kana kallon Alhaji Haruna ka kalleta ka san ya kusa
haihuwarta ko ma ace ya haifi kamar ta.

Bayan wadannan iyalan Alhaji Haruna Mai yadi yana da wata yar da ya haifa da
matarsa ta farko mai suna Maryama, sun yi zama a tare tun a lokacin da yake amsa
sunansa na Haruna Mai Yadi, kusan duk wata wahala da fadi tashin rayuwa tare da ita
aka yi, kamin daga bisani ya auro Hajiya Kaltume wadda ita ce uwargida a yanzu
sakamakon rasuwar da uwar yarsa ta farko ta yi wato Sapna wadda take a gidan
aurenta a yanzu, sai dai kulawarta da ta mijinta duk yana karkashin mahaifinta ne,
abun da hausawa ke cewa an siyar da akuya ta dawo tana cin danga, domin an aurar da
ita ne ga talaka kuma a lokacin da mahaifinta yake talaka kamin arzikin ya bude
masa, hakan ya saka a yanzu gidansa ya cika da ƴaƴan yan'uwansa da na yan'uwan
matansa.

Daga uwargidansa mai rasuwa Maryam har Hajiya Kaltume irin matan nan da ake cewa
auren fari auren talauci, ya auresu sun kamin yayi arziki ba tare da duba kyau
hallita ba, kyau hali dai abu ne da yake a bayyana domin uwargidansa ta farko da
kuma Uwargidansa ta yanzu basa ga maciji da juna, basa da aiki sai yawan fitina da
fada da juna, har Allah ya dauke rayuwar Maryamu.
Arziki kashi inji hausawa, bayan rasuwarta ne Haruna mai Yadi ya fara samun
daukaka kofofin arziki suka bude masa gabas da yamma, a cikin lokacin ne ya auro
Hajiya Nafisa yar mai gidansa, kasancewarsa mutum ne da ba shi da ra'ayin zama da
mace daya, ba laifi tana da nata kyaun kuma ya dauko mace yar gidan mutunci da
karamci sai dai ko kadan albasa ba ta yi halin ruwa ba, domin tana zuwa gidansa ta
fara yi masa gorin arziki duba da nata mahaifin ya ninka Alhaji Haruna Mai Yadi
kudi ta ko'ina, a lokacin da ya auro ta nasa arzikin be kai kamar yanzu ba, abu
kadan idan aka taba ta sai tace ita yar Alhaji Garba kudi Kasa ce, hakan yana daya
daga cikin abubuwan da suke yawan hada ta fada da Hajiya Kaltume da kuma Mijinta
Alhaji Haruna, domin tana yi ma Hajiya Kaltume gorin arziki Hajiya Kaltume kuma
tana mata gorin anga mijinta da kudi an aure.

Ta bangaren Alhaji Haruna kuma ba sha da dadi a hannunta domin so take komai sai ya
banbanta mata da Hajiya Kaltume saboda ita yar masu hannu da maiko ce, shi kuma a
gurinsa yana ganin hakan kamar rashin adalci ne, kuma be yarda ya aikata abun da
zai hana shi zaman lafiya bayan mutuwarsa ba. A haka dai aka yi ta zaman da dadi ba
dadi har Allah ya kara buda masa ya tashi daga Alhaji Haruna Mai Yadi zuwa Alhaji
Haruna Mai Motoci. Duk wanda ke garin Gusau ya san Mai Yadi Motors a ciki da wajen
Zamfara, domin babban kamfani ne mai kawo manyan motoci na zamani, ba a iya nan ya
tsaya ba, ya raba hannu ta bangaren shigo da kayan masarufi da gine gine na zamani
a garin Gusau, Kaduna da kuma Abuja. A lokacin da ya zama cikaken mai kudi ne
Hajiya Kaltume ta nemi daukar masu yi mata hidima ta komai a gida miji, domin Momy
da nata masu aikin ta zo tun daga gidansu tsabar nuna isa da gata.

Sai dai ko kadan surukarta kuma mahaifiyar Alhaji Haruna Mai Yadi bata so haka ba,
Wato Hajiya Binta, Hajiya Kaltume har Momyi ba su saurareta ba saboda rashin ganin
kimarta da girmamata, ita ma kuma tana taka tsantsan da matan ďan nata gudun kar
suce ta shige musu hanci domin mace ce mai gudun fushi da kiyayyar zuciyar kowa.
Wannan ya saka a lokacin da Allah ya buda masa ta nemi yayi mata nata gidan dabam,
ta zauna tare da nata yayan idan sun zo da kuma jikokinta. Balkisu ce farkon mai
aikin da aka fara kawowa a gidan a bangaren Hajiya Kaltume, Balkisu yarinya ce mai
tsabta da iya aiki ga far'a da son aiki, hakan ya saka Hajiya Kaltume ta riketa da
kyau ta sakar mata ragamar komai ciki har da kula da yayanta da kuma girka abincin
mijinta. Daga lokacin da ta karbi girki komai ya canja ko yaranta sai da suka yaba
da canjin da aka samu domin Balkisu wadda ake yi wa inkiya da Iyami tun tashinta
yarinya ce yar zamani ce da ta san kan kalolin girki da ďanďannonsu, shi kansa
Alhaji Haruna sai da ya yaba da girkin sabuwar mai aikin tasa tun kamin ya yalla
idonsa a kanta.

A lokacin da idonsa suka yi arba da ita kuma sai kimarta da kwarjinta suka karu a
idonsa, kasancewarta kyakkyawa mai kurciya fiye da matansa ga jiki daidai ba mai
ƙiba da baƙi kamar Hajiya Kaltume ba, fara doguwa ba guntuwa da kiba kamar Momy ba,
jikinta be yi yawa ba kuma be yi kadan ba, yar bulbul da ita, haskenta mai kyaun ne
cikin ma bata samu hutu da jindadi ba.
Ga tarbiya da girmamawa idan zata gaishe shi sai ta kai har kasa, idan ya bata abu
hannu biyu zata saka ta karba, da haka ta fara siye zuciyarsa har ta kai ya fara
ninka albashinta kamin ya fara nuna mata alama, daga baya kuma ya fito fili ya fada
mata burinsa bayan ya san komai a akanta.

Tsoron Hajiya Kaltume da duban level din arzikinsa da nata ba daya ba, ya karya
mata guiwa gurin amsa masa bukatar da ya zo mata da ita. Sai dai kuma rabo idan ya
rantse dole komai sai ya afku, rabon samun Hurriyya da Hamad da kuma karamin cikin
dake jikinta ya saka Alhaji Haruna yayi nasarar lurar da ita cewar tana cikin irin
matan da yake so tare da nuna mata shi ma a da can talaka ne kamar ita, kuma a
yanzu zai saka zane ya tare duk wata ƙura da zata taso.

Kwadayi irin na talaka ya leka gidan mai arziki da kuma burin son taimakon iyaye da
samun rayuwar jindadi ya saka Iyami ta amince da bukatar Alhaji Haruna. Sai aka
shirya auren a boye sai bayan da da Hajiya Kaltume ta tafi Ummara sannan aka daura
auren, Amarya ta tare da Mahaifiyarsa Hajiya Binta, daga lokacin ne sunan ya tashi
daga Iyami wanda ta taso da shi tun kirciya ya koma Amma domin a lokacin ta wuce
ƴaƴansa su kirata da sunanta Iyami dole su sakaya saboda mahaifinsu.
A lokacin da Hajiya Kaltume ta dawo sai zaman lafiya ya gagari Amma da mijinta
saboda fitina irin ta Hajiya Kaltume da gori da wulakanci saboda tana ganinta yar
aikinta, gashi kuma Momy ma da take ganin kamar ita aka yi kishiyar bata raga mata,
ba ita kadai ba kusan duk wanda ya san ta yi aiki a gidan kuma ya ji ta aure mai
gida zai jefeta da kalmar cin amana.

Wannan abun ya tabata matuka sai dai samun Hajiya Binta wato mahaifiyar Alhaji
Haruna ya wanke mata rabin damuwarta domin tana sonta fiye da yadda take son abokan
zamanta Hajiya Kaltume da Momy, domin Amma tana yi mata biyayya gwargwadon hali, ta
dauke ta tamkar uwa da ta haifeta, ta rike da mutumci abun da sauran matan suka
gagara yi mata. Tana jin dadi zama da ita kamin Hajiya Kaltume da Momy su ta da
fitinar cewar sai dai ya hade su guri daya, suna ganin kamar ita Iyami da ya ware
dabam ya hade da mahaifiyarshi ya fi bata jindadi fiye da su, hakan ya saka shi
gina babban gida a unguwar Millions Quarters cikin rukunin manyan gidajen da ake ta
gasar ginawa a unguwar.

Na shi gidan ya fita dabam saboda kyau da tsari da aka yi ma katon gidan. Bayan
haihuwar Hurriya Alhaji Haruna ya tare a gidan tare da Iyalinsa, a lokacin Amma
tana da tsohon cikin Hamad, bayan tarewa gidan da wata daya ta haifo ďanta Hamad
mai shekara goma da daya a yanzu, tun daga lokacin kuma sai haihuwar ta yi mata
shiru tun tana damuwa har ta daina, ta rumgume yayanta biyu da Allah ya bata
Hurriya da Hamad. Amma ba mace ce mai yawan shige shige ba wannan ya saka a duk
lokacin da aka ce ta nemi taimako sai ta ki, domin bata san gurin waye zata duka ta
tara hannu ya bata magani ba, sai Allah.

A yanzu kuma da Allah ya tashi bata haihuwar sai ya kawo cikin na uku daman da
kurciyarta a yanzu ne take cin nata lokacin ba kamar abokan zamanta da mijinta da
suka bata kusan shekara goma sha biyar biyar ba, mijinta kuma ya bata kusan shekara
ashiri. Domin yarta ta farko Hurriya a yanzu tana da shekara goma sha biyar ne, a
yayinda ita kuma take da shekara goma sha shida da auren a gidan Alhaji Haruna Mai
Yadi wanda shi ne mijinta na farko. Hajiya Kaltume da Momy kuma duka last born
dinsu shekarunsu goma sha bakwai ne a yanzu. Iyami ta sha wahala sosai a gurin
abokan zamanta na makirci da tukgu irin na kishiyoyi, yarta Hurriya kuma ta sha
wahalar yan'uwa wadanda suke uba daya tun tana karama har girma, suna yawan
hantararta da gori ga duka kamar ita din ba ďaya take da su ba.

Hurriya kyakkyawa ce sosai irin kyau nan mai matukar daga hankalin wanda ya san
kyau da sirrin kyau, irin kyau da ke shiga cikin ido ya afka a kwakwalwa ya zauna a
zuciyar mai yinsa, irin kyau da idan ka kalleta sai ka sanar da zuciyarka tabbas
tana da kyau, irin kyau da sai bakin ya bawa dan'uwansa labarin kyauta, ko kadan
bata dauko mahaifinta a baki da muni ba, domin kowa ya san Alhaji Haruna ya san ba
kyakkyawa ba ne, wasu har kirari suke masa ba dan kudi ba da sai bola, shiyasa a
lokacin da aka yi aurensu da Iyami kowa yake cewa ta bi kudi shi kuma ya bi kyau.
Hurriya mahaifiyarta ta dauko sai dai ta dara mahaifiyarta kyau nesa ba kusa ba, ta
fita haske ta fita komai hakan ya saka ta fita dabam kamar ba yar gidan ba, domin
yaran Momy ma da suke da kyau ba su kai Hurriya kyau ba balle kuma yaran Hajiya
Kaltume da suka dauko ta wasu kuma suka biyo mahaifinsu, ba laifi suna da nasa
kalar kyau, domin ko wace halitta ta Allah kyakkyawa ce.

Duk tarin kyau da haibar da Hurriyya take da shi tana da wata lalura da aka haife
ta da ita ta rashin gani, bata iya tantance komai sai da gilashi, idan babu
gilashin ido a tare da ita wato medical glasses bata iya banbance fuskar kowa sai
dai ta yi amfani da murya, tana iya ganin abun da ke gabanta ko gefenta haka ma ta
kan iya banbance mace da namiji ta hanyar sifar da tufafin jiki, sai dai ba zata
iya fadar yadda fuskarsu take ba, domin dishe-dishe take gani, kusan eyeglasses shi
ne rayuwarta bata iya komai sai da shi idan yana a idonta tana ganin komai clearly
kamar yadda kowa zai gani ko ma fiye da haka, idan kuma babu bata iya karatu bata
iya ganin kyau ko munin mutum, hakan ya saka bachi kadai ke rabata da gilashi.

An nema mata magani har an gaji amman babu sauki babu alamarsa, wani gurin ma a
madadin samun sauki sai idon ya kara dishewa, tsoron kar ta rasa idon gaba daya ya
saka aka daina nema mata magani Alhaji Haruna ya saka likita kwarare ya duba idonta
ya fadi kalar gilashin da zai dace da ita mai kyau da tsada, mahaifinta ya saka aka
kera mata har guda biyar a lokaci daya.
Biyu daga cikin gilasan da mahaifinta ya saka aka kera mata ne suke hannunta,
sauran ukun suna gurin Yayanta Yassar ya aje mata a bangarensa gudun kar su bata,
domin tasu ta zo daya shi kadai ne take jin sanyinsa a cikin Yayan Hajiya Kaltume
ya ke sonta da nuna mata kulawa tsakani da Allah kamar kanensa da suke uwa daya uba
daya, Yassar kam ya fita dabam kusan ya fi sabawa da Hurriya ma fiye da sauran yara
da suke gidan, yana sake mata fuska tana wasa da shi kamar ita da shi din abokan
wasa ne. Idan yana gidan bata da hutu ga tsokanarta da yake yawan yi. Yassar yaro
ne mai mutunci da kamanta gaskiya, domin yana ba wa Amma da Momy dukanin girmansu
sam baya biye hudubar da mahaifiyarsa take masa, be taba yarda ya hau turbar da
take dorashi ba, Munib da Miwan suke kan gaba gaba gurin taya Momy kishi dama da
hagu har sun fi yar'uwarsu maace taya mahaifiyarsu kishi.

*** *** ***

Wannan Kenan, shimfida ce da share fagen yadda labarin zai tafi, labari
ne mai ƙayatarwa da sarkakiya da kuma ƙulla-ƙulla sannan yana dauke da darasi na
rayuwa. Allah ya sa mu amfana da shi kuma ya ba ni ikon gamawa lafiya kamar yadda
na fara. Sannan ina son ku sani labarin nan ban yi shi dan wani ko wata ba, idan ma
ya yi daidai ko ya ci karo da rayuwar wasu, to arashi aka samu. Tare da fatar za ku
tara hannu biyu ku karɓa kamar yadda kuka saba karɓar labaraina cikin farinciki da
ɗauki, sai a taya ni da addu'a na baku abun da kuke so, ma'ana na faranta ranku
fesss 😀

Masoyana Asallamu Alaikum mun sake haɗuwa a wata sabuwar tafiya, Allah ya
sa mu wanye lafiya kuma mu kai karshenta cikin farinciki da Amince.
Sakon gaisuwa da fatan Alheri daga taku mai son farincikinku Khadeeja Candy🥰
08036126660.

https://chat.whatsapp.com/LimnMeG0kWvIfT6JQvVMh1

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

2️⃣

Ta aje plate din hannunta da sauri ta zari tissue ta goge bakinta.

“Amma na tafi kar na yi latti”

Amma dake kokarin jefa tawul a ruwa ta ce

“Kya ji da shi, kullum ke ce uwar yan latti sai an jiraki, ga kokari ga buga latti”

Hurriya ta dauki jakarta ta makaranta da sauri ta goya tare da daukar lunch box
dinta ta fice daga falon da gudu, kamar zata fadi haka ta isa bangaren Appanta sai
haki take kamar wadda aka yi yakin duniya tare da ita. Hannu ta mika jikin window
falon kamar yadda sauran yan mata sa'aninta da wandanda suka girmeta suke mika na
su hannu suna karbar karamin hollandia da chocolate da yake raba musu, tana son
karba yan'uwanta na tureta tana yin baya har sai da suka gama karba sannan ta samu
karba daga gurin mahaifinta, kyautar wani abun ci da ko abun sha a kowace safiyar
week days wani abu ne da ya sabawa yaransa da shi tun suna kanana.

“Na gode Appana”

Ta fada tana murmushi jindadi, shi ma murmushin yayi yana kallon kyakkyawar yarsa,
mai yawan yi masa godiya da nuna masa jindadinta a duk lokacin da yayi musu kyauta
komai kankantar kyautar domin haka mahaifiyarta Amma ta koyar da ita, kusan ita ce
karama a cikin yayansa mata a cikin maza kuma kanenta Hamad ne karami ƴaƴansa na
jini amman ya fi sauran yayansa godiya da yabawa idan yayi musu abu.

“Allah ya miki albarka Hurriya, ga ladabi ga basira”


Ta yi yar siririyar dariya mai sauti.

“Appa haka Uncle dinmu yake cewa, har da cewa yayi wai akwai wata gasar da zan sake
shiga”

“Da kyau ni ma ya fada min haka, kuma yace wannan gasar ma mai tsoka ce, suna
kyautata zaton idan kika yi ta daya za su dauki nauyin karatunki domin haka suke yi
ma duk wadda yayi na daya, ni kuma na kara musu da cewa ko da ba su fitar da ke ba,
zarar kin kallama makarantar da kike yanzu zan fitar da ke waje ki yi karatu mai
kyau, duk kuwa da bana sha'awar fitar da ƴaƴa mata waje yin karatu amman ke zan
fara akanki”

Ba shiri Hurriya ta bude baki tana mamakin jin furucin mahaifinta.

“Appa da gaske?”

“Da girmana zan yi karya?”

Ta saki chocolate din da hollandia ta rufe baki tana zaro ido kamar zai fado. Sai
kuma ta daka tsalle ta dire.

“Appa i love you i can't wait”

“Ki dage da karatu Allah ya taimaka ina alfahari da ke, Allah ya miki albarka”

Ya fada yana murmushi yana nuna mata alamar lokaci a hannunsa da babu agogo, sai ta
duka ta dauki abun da ta zubar ta.

“Ameen ina sonka Appana, na tafi sai na dawo”

“Allah ya kiyaye,”

Ta amsa da Ameen already ta sauka entrance din tana hadawa da gudu domin yan'uwanta
sun kusa isa gurin bus din dake kaisu makaranta ta maido su. Tana daf da isa ta ji
an fisge chocolate din dake hannunta kamin ta juyo aka fisge madarar hollandia din
dake dayan hannunta. Suna hada ido ta bata fuska ta buga kafa kasa, shi kuma ya
saka dariya yana kokarin bude ledar chocolate din.

“Yaya Yassar dan Allah ka ba ni”

“Wallahi ba zan baki ba”

Ya fada kai tsaye yana mata dariyar keta, juyawa ta yi cikin yanayin damuwa ta koma
bangaren Appanta wannan karon bata tsaya gurin windows din ba ta murda kofar
falonsa ta shiga, sanin talkamin makaranta ne daure a kafarta sai ta fadi kasa tana
rarrafe dan kar ta taka masa carpet.

“Appa Appa Appa”

Alhaji Haruna ya fito daga dakinsa da sauri jin yarsa na kiransa.

“Hurriya baki wuce ba?”

“Appa YaYa Yassar ya kwace min abun da ka ba ni, na kowa yana nan ni ya karbe nawa”

Appa yayi murmushi ya juya ya koma ciki, be dade ba ya fito rike da wani chocolate
din da hollandia ya mika mata.
“Appa dan Allah ka kora Yaya Yassar daga gidanka ka ce ya tafi ya bar maka gidanka,
Wallahi takura min yake yi da yawa”

Tana fada tana saka hannu biyu ta karba.

“Idan kin hadu da shi a yanzu ki fada masa na ce ya hada kayansa ya bar min gidana,
saboda ya cika takuraki ke da gidan Appanki”

“Appana na gode, zan fada masa haka a yanzu kuwa”

Cikin shagwaba da jindadi ta fadi haka sannan ta mike tsaye shi kuma ya kai hannu
ya shafa kanta dake cikin hijab domin ya fahimci a bakin gaskiyarta take fadar
Yassar ya bar gidan. Tana kokarin juyawa Amma ta shigo falon dauke da tray, bata yi
mamakin ganin Hurriya a sitting room din mijinta ba, daman ta fi kowa yin latti
zuwa makaranta ko fita unguwa. Musamman idan mahaifinta yana gari, a dole sai ta
ganshi sannan zata fita, idan kuma bata zuwa ko'ina to tana zaune tare da shi a
bangarensa babu ruwanta da ranar girkin Amma ne ko na Hajiya Kaltume ko Momy, ko da
bata shiga har inda yake ba indai ta san yana nan zata zauna a part dinsa ne, hakan
ya haifar da shakuwa sosai a tsakaninsu.

“Daman ai duk wanda yayi shiririta a garin Gusau a bayanki yake, ke kam Allah ya
shiryar da ke Hurriya”

Dariya kawai ta yi ta fice tana fadin.

“Appa ka fada mata abun da Yaya Yassar yayi min. . .”

Daga mahaifiyarta har mahaifinta binta suka yi da kallo jindadi da farinciki har ta
fice, sannan Amma ta girgiza kai ta maida dubanta ga Appa.

“Bismillah Appan Hurriyya muje ka karya”

Kamar wanda aka jefo a wata duniyar haka yanayin fuskarsa ya sauya daga murmushi da
jindadi zuwa bakinciki da bacin rai da be san dalilinsa ba, ba dan komai ba sai dan
jin muryar Amma a bayansa.

“Zan shigo”

Ya amsa ba tare da ya jiyo ba, domin baya son kallonta a yanzu, fuskar dake masa
kyau da kwarjini, mace da yake gani yana jin kamar shi da ita sa'anin juna ne, a
yau ita yake kyamar gani, muryar da ta fi kowace murya yi masa dadi a duniya yau
muryar ce yake jin kamar tana sanar masa mutuwa. Cikin hikima da kokarin danne
damuwa ta sauke ajiyar zuciya domin ta san shekaru da aka fito da watanni mijinta
ba haka yake ba, a da idan ta kawo masa abinci jiki na rawa yake tarbarta ya fara
zuba santi tun kamin ya ci, ba zai ma bari ta fara isa bedroom dinsa ita kadai ba
sai ya rika mata tray ko ya dauki wani abun yana zolayarta, amman a yan kwanakin da
idan aka a hada su aka kirga zai bada wata daya ya sauya mata gaba daya.

Sai da ya tabbatar ta shige sannan ya juyo ya kalli kofar dakin, hannu ya saka a
kirjinsa ya danne tashin hankalin da yake jin yana kusantoshi. Cikin wani yanayi
mai kama da nauyin jiki da na zuciya ya cira kafarsa ya fara takawa tare da maida
hannayensa baya ya rumgume yana tafiya a hankali. Yana shigowa cikin dakin Amma ta
juyo ta kalleshi da damuwar da ta gagara boyuwa a fuskarta.

“Ranka ya dede waya canja Bedsheet din nan?”

Tsaye yayi yana kallonta kamar mai tunanin kalar amsar da zai bata, kana kallon
idinsa zaka karanci damuwar dake tare da shi. Can kuma ya kawar da fuskarsa ya dawo
da hannayensa dake rumgume a bayansa ya zuba su cikin aljihu.
“Kaltume ce ta canja”

Da matukar mamaki Amma take kallonsa, domin al'adarsu ce duk wanda ke da girki ita
zata gyara bangaren mijinta kuma zata tafi da Bedsheets dinta ta shimfida, idan
wata zata karbi girki sai ta kwashe kayanta wadda ta karba ta shimfida nata ta kula
da bangaren, hakan ya saka ko wace mace da kalar kamshin turaren dake fita a part
dinsa idan girkinsu ya zo.

“Ban gane ta canja ba? Jiya na shimfida shi fa, kuma jiya da yau girkina ne, ai ta
jira har sai girkinta ya zagayo tukuna ta canja”

“Ni na saka ta canja kuma na karya zaki iya dauke abincinki”

Kamar an watsa mata ruwa sanyi a jiki haka ta ji duk wata kusurwa da logo dake
jikinta ya saki, lakkar jikinta ta yi kasa.

“Gaba daya na daina gane maka a yanzu Appan Hurriyya ka canja min”

Ta matsa inda yake tsaye ta risina kasan guiwowiyinta ta hade hannayenta kamar mai
rokon gafara.

“Wannan shi ne karo na biyar da zan sake rokonka idan wani laifi na yi maka ka fada
min na nemi yafiyarka, ka dubi girman Allah ka yafe min, ka daina hukunta ni da
wasu dabi'u da halayya da ban sanka da su ba, kuma baka saba yi min ba”

“Baki min laifin komai ba Iyami, Wallahi ban rike ki da wani abu ba a zuciyata ba”

Ta daga kai ya kalleshi.

“Toh me yasa kake min haka? Akan wani dalili zaka saka Hajiya ta canja zanen gado
kuma ta kawo maka abun karyawa bayan ni ce da girki?”

“Saboda zata karbi girki a yau”

Kamar an tsinke wutar cikin jikinta haka ta ji, sai ta mike tsaye tana kallonsa ta
kasa sake furta komai.

Hannayensa ya cire aljihu zuba ya nufi kusa da inda ta aje masa tray ya zauna
gefen gadonsa sannan yayi mata alama da ta zo ta zauna.
Ta kalli gurin da ya nuna mata amman ta kasa cira kafata ta isa gurin.

“Zo ki zauna Iyami”

Sai a lokacin ta ji kuzari ta cira kafarta ta taka har ta isa gurin ta zauna jiki a
sanyeye tana kallonsa. Ajiyar zuciya ya sauke kusan sai uku sannan ya kai hannunsa
ya bude bedside drawer ya dauko wata yar karamar jaka ya bude ya dauko wasu takardu
ya mika mata.

“Wannan takardun gidana ne da yake a Samaru, na saka lawyer na ya canja komai daga
sunana zuwa naki, na kafa shaida da lawyer na kuma ta bangarenki na yi magana da
Bappa shi ma ne shaida domin a gabansa aka yi komai, sai dai na bukaci kar ya fada
miki saboda ina son ya zama ni zan fara sanar da ke, saboda haka yanzu gidana dake
Samaru mallakinki ne halak malak...”

Ta mika hannu biyu ta karba cikin yanayin mamaki da faduwar gaba, ta kasa godiya
haka kuma ta kasa jin farinciki ko kishiyarsa. Wata karamar Envelop ya dauko a
cikin jakar ya mika mata.
“Wannan Cheque ne na Naira miliyan Ashiri, ina son ki yi amfani da kudin ta hanyar
da ya dace ki yi kasuwanci ki rike kanka dan Allah”

Ta karba idonta na cika da hawaye.

“Wannan duk na minene?”

Yayi shiru ya kasa ce mata komai, sai ya sake saka hannunsa ya dauko wani envelop
din ya mika mata.

“Ki yi hakuri Iyami, ina jin rashin natsuwa da faduwar gaba da tashin hankali a duk
lokacin da girkinki ya zagayo, idan na tuna kina a cikin gidana karkashin kulawata
sai na ji kamar zan mutu, na yi ta daurewa ina ganin kamar abun nan zai wuce amman
ban ga alamar haka ba, a kullum sai kara yin gaba abun yake, akan hakan na yanke
hukuncin yin abun da zai zame mana mafita gudun kar na cutar da ke, domin idan muka
daure a haka ban san a gaba yadda zama zai kasance ba”

Kasa mika hannu ta yi ta karba kuma ta kasa ta kasa cewa komai, ta kasa dauke
idonta daga barin kallonsa, hawaye kuma suka ce mata ga rabarsu. Ganin haka ya
saka ya aje mata takardar a saman takardun da ya mika mata.

“Bana son ki bar min komai duk wani abun da na siya miki tun daga kayan daki har
tufafi da duk wani abun more rayuwa, mallakinki ne zan saka a kawo miki har gida,
amman dan Allah ki bar min Yayana a hannuna ban yarda ki tafi da ko daya ba, cikin
dake jikinki ma idan kin haihu zan dawo da abu na a gidana”

Sai a lokacin ta samu kuzarin bude bakin da yayi mata nauyi ta yi magana.

“Babu uwar da zata so wasu yayan kamar nata, kuma babu yayan da za su jidadin wata
uwar kamar ta su, musamman a gida irinka”

“Kin fi kowa sanin yadda nake son ƴaƴana, da uwa ko babu uwa za su jidaɗin zama a
gidan mahaifinsu, zan kula da su”

Ta haɗe wani abun da ya tsaya mata ta miƙe tsaye da tunani kala kala, ta bude
takardar ta duba me ke ciki saki ne ko akasin haka? Idan sakin ne saki nawa ne? Ko
kuma dai ta faɗi a ƙasa ta yi masa kuka ta roƙi ya maida ita bayan ya faɗa mata
baya jin natsuwa da kwanciyar hankalin a zamansa da ita yanzu?

“Allah yasa hakan shi ne alheri, kuma ya baka ikon kula da su Hurriya da Hamad”

Ita kanta sautin murya mai kama da tata take jin tana fita a bakinta, domin bata da
tabbacin tana da kuzarin furta masa wani abu a yanzu. Tana jan ƙofar ɗakin nasa ta
ji ƙafafuwanta sun yi nauyi, mararta ta murɗa wani irin tashin hankalin da bata
taɓa samun kanta a ciki ba ya baibayeta. Da gaske Appan Hurriya sakinta yayi? Anya
zata iya tafiya ta bar ƴaƴanta? Ko dai wasa yake mata wata ƙila kuma wunin yau gaba
ɗaya be faru ba. Tana tafiya jini na mata zuba amman bata sani ba zafin zaton sakin
da bata tabbatar ba ya manta da ita zafin mararta dake murɗawa, ya hana hankalinta
kusanto jikinta ya juya tunaninta a gurin abun da bata taɓa mafarkin faruwarsa ba.

Arzikinta ɗaya, ko wane part an yi masa corridor da zai sada ɓangaren da ɓangaren
Alhaji Haruna ba sai ta gaban gidan ba. Kuma zaka iya fita ko shiga ba tareda sanin
kowa ba, har sai idan mutum ya isa part ɗin. Kamar wadda ta sha giya haka ta isa
ɓangarenta ta zarce bedroom ɗinta ta zauna a kan gadonta.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ta furta daker tana kokarin dawowa hayyacinta.


“Haka ake ji? Haka saki yake? Ko dan ina da kurciya ne? Ko kuma saboda ban saka
tsammanin zuwan sakin ba ne gaba daya a zaman rayuwata? Ko kuma saboda ina tsoron
barin ƴaƴana ne? Allah ka sassauta min, ka saka min natsuwa da kwanciyar hankali,
ka hallata aure ka hallata saki, Allah ka yaye min wannan damuwar da zata rufe ni,
Ubangiji ka tsaya min”

Rahamar Allah ga bayinsa, da kuma dace ya ƴan amin a kusa, tana gama addu'ar ta ji
natsuwa ta sauko mata, numfashin da take jin kamar zai danne mata kirji ya daga
mata, mararta ta sake murdawa har sai da ta lumshe ido ta kai hannunta ta taba
cikin dake jikinta na wata shida.

Kamar wadda aka yi ma allurar kuzari haka ta tashi ta aje takardun hannunta ta
shiga bandaki ta gyara kanta ta fito ta gyara dakin inda ta ɓata ta cire Bedsheet
din ta bar gadon a haka, ta dauki ruwa da tsumma ta bi tana goge jinin da bata san
ya zuba ba sai a lokacin. Kamar mai shirin yin sata haka ta shiga ɓangaren ta goge
jinin sannan ta juyo gabanta na tsananta faɗuwa ta fito daga ɓangaren. Ganin jinin
yaƙi tsaya mata ya saka ta sake tsabtace jikinta ta saka pant da pad ta tare sannan
ta kwanta saman gadon tana sauraren zuciyarta da ke bugawa da karfi, mararta kuma
na cigaba da murdawa.

“Me na yi ma Appan Hurriya?”

Shi ne abun da take ta tambayar kanta, tambayar da bata da amsarta, mulmulawa ta yi


saman gadon tana karewa katon dakinta kallo kamin ta tashi zaune ta fashe da kuka
mai karfi, a rayuwarta bata taba fuskarta wani abu na tashin hankali irin yau ba.
Cikin kuka da bakinciki ta dauko akwatunanta ta fara zuba kayanta ba tare da ta
tsaya shiryasu ba, wani abun ma sai dai ta gwamatsa shi cikin wani talkaminta da
atamfa ta saka su a kwati daya, sai da ta gama ta rufe ta kaisu gurin kofa ta aje
ta dawo cikin dakin ta zauna kasa ta rasa me ya rage mata ta yi, kuma ta kasa fita
daga dakin.

Misalin Karfe biyu da mintuna Bus dake dauko yaran makaranta ta shigo gidan, a
harabar da aka tanada domin aje motoci direban ya faka motar. Sai da manyan suka
fara fita sannan Hurriya ta fito, Hamad kan cikin manyan yayyunsu ya kutsa ya fita,
daman shi yana daga cikin sarakunan kiriniya da rashin kunya na gidan, babu kalar
dukan da basa masa ko hantara amman kowa yace masa kule zai ce chasss, Amma ta yi
fada har ta gaji, Appa ma har baya son a kai masa kararsa domin ko ya masa fada ba
zai hana gobe ya sake ba, Hamad irin yaran nan ne da ko kallonsu ka yi a karkace
sai sun rama.
Hurriya na shiga part dinsu ta jefar da jakarta a kan kujera ta nufi bedroom din
mahaifiyarta, a hankali ta tura kofar dakin ta shiga tsaye ta yi bakin kofar tana
kallon kanenta Hamad dake ta fadawa Amma abun da ta yi masa a makaranta.

“Amma karya yake, karfe 1:30pm aka tashe mu shi ne na ce nasa yaje yayi sallah
saboda bus din mu sai 2pm take zuwa ai, shi ne ya taso min fa masifa har zai yi
dambe da ni gaban yan makaranta har da yan ajinsu fa”

Hamad ya juyo ya kalleta a fusace.

“Toh ina ruwanki da ni da zaki ce na tashi na yi sallah, kafiri ne ni ko bana


sallah aka ce miki? Salon friends dina su fara tsokana ta suna cewa bana son
sallah”

“Na ji ba zan sake maka magana ba, amman ni ma karka sake zuwa class dinmu ka ce na
ara maka wani abu, ba ruwana da kai karka sake taba min komai kuma safata da ka
saka yau ban yafe ba karka sake min taba min komai”

Amma ta mike tsaye tana kallonsu kowane zuciyarsa ta kawo kamar abokan gaba.
“Wannan fadan duk na minene wai? Ku kullum baku zaman lafiya? Kai kake binta amman
kai da ita babu zaman lafiya, abinci ma ba zaku ci a plate daya ba, magana mai dadi
babu tsakaninku kullum sai fada?”

Hamad ya ce.

“Ita ce bata ba ni respect ai”

“How? Kai ne babba or ni? Ni ce babba ai kai ya kamata ka ba ni respect”

“Ni ba zan taba baki respect ba i hate you kuma kika sake min wata maganar banza
sai na ballaki”

Hamad na kaiwa nan ya juya ya fice rike da jakarsa har yana bankade Hurriya.

“Amma kin ga ko? Imagine”

Amma ta dafe kanta ta zauna bakin gadon tana fashewa da kuka.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

A take jikin Hurriya yayi sanyi ta bar jikin kofar ta karasa inda Amma take ta
zauna kusa da ita, domin suna yawan samun tsabani da Hamad saboda rashin jituwa
dake tsakaninsu su yi fada wani lokacin har dambe suke, Amman Ammansu bata taba
kuka ta zubar da hawaye ba akan haka ba sai yau.

https://chat.whatsapp.com/LimnMeG0kWvIfT6JQvVMh1

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

3️⃣

“Amma I'm sorry laifin fa duk na Hamad ne shi ba a masa magana ya ji”

Amma ta dago da idanuwanta da suka kumbura ta kalleta.

“Ke ai kina ji? Kuma ke ce yayarsa ki daina biye masa mana, ki zauna lafiya da
dan'uwanki dan Allah, kullum ina fada muku haka amman baku ji, Hurriya ki daina
biye masa kina kallon ba sonku ake a gidan nan ba, a madadin ku so kanku kullum sai
rigima da junanku”

Amma na magana Hurriya na yawo da idonta akan akwatunan da suke tsaye gefen kofar
dakin da bata lura da su ba sai a yanzu.

“Amma kayan miye a akwaitinki?”

“Tafiya zan yi”

Hurriya ta dubeta da sauri tana kallonta da ya kumbura sosai.

“Amma ina zaki je?”

“Gida zan koma gurin Gwaggo”


“Saboda me?”

Amma ta yi murmushi hawaye na sauko mata.

“Hurriya abincina ya kare a gidan mahaifinku”

“Kamar Yaya? Toh ba sai ya kawo wani ba? Amma me ya faru kika yi kuka? Me yasa zaki
tafi?”

Amma ta rufe ido ta dantse baki.

“Je ki kira Hamad”

Hurriya da bata gama fahimtar abun da yake faruwa ba idonta ya cika da hawaye har
ya zubo ta kasan gilashin da shi ne rayuwarta. Ta mike tsaye ta fice daga dakin
kamin ta isa dakin Hamad ta cire hijabin dake jikinta ta rike a hannu tana tafe
tana hawaye har ta isa bakin kofar dakin. Murda kofar dakin ta yi ta tura ta shiga,
Hamad dake sanye da short yana kokarin cire safar kafarsa ya kalleta.

“What? Amma ta miki fada ko? That's good next time sai ki sake shiga min hanci”

Ya fada azatonsa Amma ta yi mata fada ne sosai, daman haka take sometime idan aka
yi mata fada kuka take.

“Ba saboda haka ba ne, Amma ta ce na kira ka kuma kuka take yi, ban san abun da aka
yi mata ba”

Be tsaya ya karasa cire safar daya ba ya sauko da kafar ya biyo bayan Hurriya da
tuni ta juya bayan ta isar masa da sakon Amma. Hamad na shiga dakin ya karasa inda
take zaune ya zauna bakin gadon babu abun da zuciyarsa take nuna masa sai fadan da
suka yi da Hurriya.

“Amma saboda Hurriya ne ko?”

Amma ta share hawayenta ta kalleshi, sannan ta kalli Hurriya ta mika mata hannu.
Hurriya dake tsaye jikin kofar dakin ta karaso da sauri hawaye na sauko mata ta
kasan gilashin dake idonta. Amma ta kama Hamad ta dauki hannu Hurriya ta dora a
saman hannun na Hamad.

“Dan Allah ku zauna lafiya, ku so junanku ku kaunaci junanku, kai baka da wata
yar'uwa da ta fi Hurriya, Hurriya ke ma baki da wani dan'uwa da ya fi Hamad, wannan
yawan fadan da kuke yi ku daina anyi ance da rashin bawa juna girma duk ku aje shi
a gafe, musamman ma kai Hamad idan baka canja wannan hallayar ba zaka sha wahala a
gidan nan kana kallon yadda kake rayuwa ma yanzu balle kuma idan bana nan”

“Amma ina zaki je?”

Hurriya ta tambaya daman ta kagu ta ji domin hankalinta yayi matukar tashi akan
hawayen da ta gani a idon mahaifiyarta ga kuma tufafinta a shirye. Amma ta kalli
Hurriya sai ta rasa ta ina zata fara amsa mata tambayarta, at her age it's too
early ta fada mata sakinta mahaifinsu ya yi, ita kanta kalmar tana mata nauyin
furtawa a yanzu balle kuma yadda ƴaƴanta za su ji idan ya sauka a kunnesu har su
fahimta.

“Gida zan tafi gurin Gwaggo ba na fada miki ba? Sai na haihu zan dawo, za'a rika
kai ku kuna duba ni”

“Me yasa ba zaki haihu a nan ba? Kuma kike kuka?”


Hamad ya tambaya ya tambaya yana kallon cikin idonta kamar mai kokarin kure
karyarta. Amma ta yi murmushi ta share hawayenta.

“Saboda bana jindadi a yanzu, bayan kun fita rashin lafiya ta taso min, kuma ina
yawan yin haka a duk lokacin da kuka tafi makaranta, kuma kin fi kowa sanin bana
son mai aiki na fi sha'awar na yi komai da kaina, ni da mahaifinku muka yanke
shawarar zan koma gida na zauna har sai na haihu na samu lafiya, shiyasa ban tafi
ba na jiran har sai kun dawo na sanar da ku, kuma na ja muku kunne dan Allah ku
zauna lafiya”

Kalaman da Amma ta yi a yanzu sun sanyaya zuciyar Hurriya har ta samu kuzarin cire
gilashin idonta ta goge hawayenta ta maida abokin rayuwarta.

“Allah ya baki lafiya Amma, zamu rika zuwa kullum”

“Ba kullum ba dai sai a lokutan da mahaifinku ya zaba, kuma ku masa biyayya dan
Allah ku zauna lafiya da kowa, ke dai na san baki da rigima Hamad ne mai matsala”

Hamad dai be sake cewa komai ba sai kallon mahaifiyarsa yake zuciyarsa na raya masa
wani abun na dabam.

“Ku rike karatunku, boko da Islamiya karku saka wasa”

“In Shaa Allah Amma zamu zama yara masu kirki”

Hurriya ta fada da murmushi a fuskarta. Hamad kam kallonta kawai yake kamar wadda
aka cewa mutuwa zata yi anjima.

“Je ka saka tufafinka ku rika min kayan na kai mota”

Ya mike tsaye ya fice daga dakin cikin wani yanayi kamar ba shi ba, yadda ya natsu
a lokaci daya wani tunani ya zo masa sai ka dauka wani babban saurayi ne.

“Amma wa zai rika ba mu abinci?”

“Haka ne na manta ma yau ban girka muku komai ba, sai da ku sarrafa wani abun ku
ci, ko kuma ku sha tea, idan mahaifinku ya dawo zai fada muku gurin da zaku karbi
abinci, gurin Momy ko Hajiya Kaltume shi zaku tambaya”

“Toh Amma Allah ya dawo mana dake lafiya”

“Ameen”

Ta amsa tana danne abun da take ji a zuciyarta, sannan ta mike tsaye ta dauki
hijabinta ta saka ta fara fitar da kayan Hurriya na taya ta kamin Hamad ya fito shi
ma ya saka hannu suka dauka suka kai mata gurin mota. Ta saka wasu a bayan mota
wasu kuma a back seat sannan ta shafa kan ƴaƴanta tana murmushi Hurriya ma
murmushin take Hamad kuma ya hade rai kamar wadda aka yi ma laifi.

“Allah ya muku albarka ya tsare ku, kuma na fada muku zan kara jaddada muku ban da
fada ku daina fada dan Allah”

A nan din ma Hurriya ce ta amsa Hamad kuma yayi kamar be ji ba, shi dai sai kallon
mahaifiyarsa yake fuska babu annuri.

“Toh Amma”

Amma ta kalli Hamad tana jin wani yanayi na rashin jindadi.


“Hamad ba zaka ce komai ba?”

Juyawa kawai yayi ya shige cikin falon ba tare da ya ce mata komai ba. Sai ta
lumshe ido hawaye suka sauko mata.

“Hurriya shiga ciki idan ina ganinku ba zan iya tafiya ba”

Ta fada still idonta na rufe, babu abun da take a zuciyarta sai ambaton Allah.

“Amma ko mu rakaki mu dawo”

Ta bude idon da sauri.

“Aa zan tafi da kaina ku kula da kanku”

“Toh Amma Allah ya baki lafiya ya dawo dake lafiya”

“Ameen”

Ta bude motar ta shiga tana share hawayenta. Hurriya ta daga mata hannu tana
murmushi a tunaninta Amma na kewar rabuwa da su ne shiyasa take kuka, a kurciya da
rawarkai irin nata bata damu sosai da tafiyar da Amma zata yi ba a yanzu, domin a
ganinta gidan Gwaggo da gidan Appanta duk daya ne kara ma gidan Gwaggo tana musu
gata tana barinsu su yi duk abun da suke so, ba kamar nan ba da wani abun Hajiya
Kaltume ko Momy zata hana, wani abun kuma Amma ce da kanta zata hana. Juyawa ta yi
ta koma cikin falon tana rufe kofar ta nufi dakinta ta cire uniform dinta ta dauki
na islamiyarsu ta saka sannan ta sauko ta shiga Kitchen ta dauko cornflakes ta jika
a two cups daya nata dayan kuma na Hamad, sai dai wanda yake na Hamad ya fi yawa
domin shi baya wasa da cikinsa komai sai ya ci ya ji baya iya tashi yake bari, ita
kuwa abinci be dame ta ba, bar ta ma ga kayan kwalama, ko abu mai ruwa dangin tuwo
da shimkafa ba babinta ba ne shiyasa kullum gata nan kamar wadda ake diba ana miyar
gidan. Jiki na rawa ta dauki cup din Hamad ta nufi dakinsa ta shiga sai ta same shi
kwance ruf da ciki yana kuka.

“Hamad ga cornflakes na jika maka, ka ci mu tafi Islamiya...”

Yana jin sautin muryarta sai yayi tsif numfashi ma a hankali yake fitarwa dan kar
ta ji.

“Hamad kuka kake yi?”

“Ina ruwanki bana shan ki dauke abunki ki fice daga dakina”

“Na maka kirki ne fa, Amma ta ce mu zauna lafiya amman baka ji ba, miye laifina dan
na kawo maka abu”

“Ba zan sha ba bana so”

“Kar Allah yasa ka sha din, wanda baya jin maganar Mamanshi ya ji haushi ai, ko
Sallah be yi ba kalleshi”

Sai a lokacin ya dago daga saman gadon ya sauko fuskarsa shabe-shabe da hawaye ya
yi kanta, sanin dukanta zai yi ya saka ta saki kofin cornflakes din ta kama shi da
kokawa daman sun saba, abu kadan idan ta yi masa sai ya ce zai daketa saboda ya
fita girma jiki da karfi, idan ma ba wanda ya sani ba zai dauka ita ce kanwar shi
ne yayan. Suna fara kokawa ya buga kanta ga kofar dakin sai kawai ta saka kuka ya
fisge glashin idonta ya jefar a kasa ya saka kafarsa ya taka haka be masa ba sai da
ya dauko talkaminsa ya saka ya bubbuga glass din ya fasa shi, domin zuciyarsa ta
kawo idan kuma yayi fushi sai ya ji kamar ya tashi gidan, gashi baya tsoron kowa
har Appa, idan za a masa dukan mutuwa sai yayi magana, sai dai yana da wata dabi'a
na baya shiga safgar kowa sai idan an shiga ta shi.

“Wayyo Allah na...”

Hurriya ta fada tana kuka tana lalaba kofar fita dakin, domin ta daina ganin komai
da kyau a yanzu sai dishe dishe saboda Hamad ya cire gilashin idon dake bata damar
banbance fari da baki. Ta bude kofar ta fita tana lalaben hanya irin yadda makafi
suke yi tana kuka har ta sauka kasa, da lalaben ta isa kofar falon ta bude ta fita
tana kuka, dishe-dishe ta fita daga part din ta shiga part din Hajiya Kaltume har
lokacin kuka take kuma ta san by that time Appanta baya gidan balle ta kai masa
karar Hamad, idan kuma Appa baya gidan Yassar ne mai yi ma Hamad hukunci yadda take
so, wani lokacin ko Appanta ta fadawa cewa yake ta fadawa Yayanta.

Da kuka ta nufi bangaren Hajiya Kaltume ta isa har bakin kofar falon ta tura ta
shiga. Hannu ta kai tana kokarin lalabawa ta ji waye a tsaye jikin kofar, sai ta ji
an sauke mata lafiyayyen mari a fuska. Tsaye ta yi cak kamar wanda aka daukewa wuta
tana kallon kasa, ta san kowa zai iya marinta a bangaren Momy ko Hajiya Kaltume,
saboda suna ganin abun da take kamar da gangan take yi, shiyasa dole kawai ke kawo
ta bangaren Hajiya, bangaren Momy kuma ko shiga bata yi idan ta shiga sai da wani
kwarran dalili, domin Hajiya Kaltume na sake mata fuska irin na munafurci, Momy kam
bata sakewa kowa fuska a gidan, har gobe ganin take level dinta ya fi na kowa a
gidan, wannan na daga cikin dalilin da ya saka komai nata ko na ƴaƴanta take
banbanta shi da na sauran, komai nata is unique and Expensive, gashi bata son ganin
ƴaƴan Amma da Hajiya ko kusa da ďakinta, sai dai ita Hajiya tana karbar Ƴaƴan Momy
har so take suje a gurinta yanzu da suka girma.

“Haba Musib Haba Musib miye haka?”

Musib dake rike da wayarsa a hannu ya kalli Yassar da ya doso inda suke tsaye cikin
bacin rai.

“Baka ga abun da ta yi min ba?”

“Amman dai ka san idan kana gani ba zata maka haka ba? So take ta gane waye a
gurin, me yasa kuke kyarar yarinyar nan ne please? Ku ba ku tausayin halin da take
ciki? Ba ku ganin lalura da take tare da ita?”

“Tana tare da lalura take yawo babu glass? Ni fa bana daukar wannan iskanci”

Ya amsa a fusace sannan ya saka talkaminsa ya fice daga falon, har lokacin Hurriya
na tsaye bakin kofar ta kasa yin komai sai hawaye, a nan ta gane wani abun ake iya
yi ma magana ko kuka, ta sani sarai tana kuka ko furta wani abun zai iya kara mata
ko ya rufeta da duka, domin ba yau ya saba ba. Ko kwakkwaran motsi bata yi ba sai
da ta ji ta a jikin Yassar ya rumgune yana bata hakuri sannan ta fashe da kuka.

“Yi hakuri Allah zai saka miki”

Hajiya Kaltume dake saukowa rike da plate ta soma fadin.

“Ya saka mata ga wa? Wai Yassar ba zaka daina wannan bakin shisshigin ba? Yadda
kake da alaka da ita fa haka yake da alaka da ita, idan ma kwantar da ita yayi ya
yanka ina ruwanka?”

Dagowa Yassar yayi ya kalleta.

“Haba Hajiya ai ko mai aikin gidan nan wani abu ba zai same ta na yi magana ki ce
ina ruwana ba balle kuma Hurriya, marinta fa yayi kamar ya samu babbar mace”
Hajiya Kaltume ta yi fuskar tausayi kamar gaske yadda ta tambaya sai ka rantse bata
san abun da ya faru ba, bayan kuma tana sama a tsaye stairs tana magana da Umm
Khairi lokacin da Hurriya ta shigo.

“Ayya ah gaskiya be kyauta ba, me ta yi masa?”

“So take ta tantance waye a gurin kawai ya sauke mata mari”

“Oh Subhanallahi, Sannu Hurriya ina glass din naki?”

Cikin wani irin kuka mai tsarke numfashi Hurriya ta soma magana.

“Hamad.... Hamad... Hamad.. Ya fasa.. Shi..”

“Saboda me? Kai Hamad akwai mugun hali ita Iyami tana aikin me yayi miki haka?”

Line by line ta fada musu abun da ya faru tun a school har dawowarsu gida, ciki har
da tafiyar Amma da hudubar da ta yi musu. Ciki wani yanayi na damuwa da rashin
fahimta da kuma faduwar gaba a lokaci daya Yassar ya kalli Hajiya Kaltume, Hajiya
Kaltume kuma ta juya ta kalli ƴarta Umm Khairi, suna haɗa ido fuskarsu ta soma
fadada da murmushi, tunawa da Yassar na dakin ya saka Umm Khairi ta fara tarin
karya, Hajiya Kaltume kuma ta daure fuska.
Yassar da ya tattara hankalinsa gaba daya gurin kanwarsa Hurriya ya ce

“Kamar ya sai ta haihu zata dawo?”

“Haka tace mana, kuma bata jima da tafiya ba, har ya fara min duka, Wallahi kashe
ni zai yi idan muka zauna a can mu kadai”

Ya kalli Hajiyarsa cikin yanayin damuwa sai ta girgiza masa kai alamar bata san
komai ba, hannun Hurriya ya rika.

“Zo muje part din na ku”

Har lokacin kuka Hurriya take tana biye da yayanta dake rike da hannunta suka fice.
Umm Khairi ta sauko da sauri tana murmushi ta dafa Hajiya Kaltume da ta kai zaune
baki har kunne tana mamakin jin kalaman Hurriya.

“Hajiya Appa ya saki Amma kenan?”

“Ina kyautata zaton haka, domin dazun da safe shi ya kira ni da kansa ya ce min na
dauke Bedsheets dinta na kawo masa abun karyawa, har na ce masa bana son ta ga
kamar ina shigar mata hakki, sai ya ce min baya son digon zance zan karbi girki a
yau”

Umm Khairi ta rumgume Hajiya Kaltume da sauri tana murna.

“Wayyo Allah na dadi, amman me yasa ba ta fadawa Hurriya gaskiya ba?”

“Waya sani? Toh ko ganin take zata dawo? Zama be gan ni ba ungo wannan kai min
Kitchen bari na kira Hajiya Fatee”

Ta mike tsaye da sauri, daga ita har yarta Umm Khairi kallo daya zaka yi musu ka
fahimci farinciki dake zuciyarsu, da rawa Umm ta karasa kitchen ta aje plate din ta
fito ta shiga dakinta ta dauki wayarta ta fara kiran yan'uwanta da basa gidan tana
musu albishir domin sun dadi ba su samu wani labari mai dadi da faranta zuciya ba
irin na yau.

Hajiya Kaltume na shiga dakinta ta maida kofar dakin ta rufe ta saka key dan
tabbatar da ita kadai ce a dakin sannan ta nufi wayarta cikin nauyin jikin dake
hana masu kiba da teba hanzari a duk lokacin da suka yi yunkurin yin haka. Sai da
ta fara zaunawa sannan ta dauki wayar ta lalabo number aminiyarta Hajiya Fatee duk
kuwa da kasancewar ta girme ta nesa ba kusa ba, sai dai friendship be duba age ko
level idan jini ya hadu, cikin natsuwa Hajiya Kaltume ta aika mata da kira,
zuciyarta har wani bugawa take irin na jindadi da farinciki da tun da aka auro
Iyami rabonta da irinshi.

“Assalamu Alaikum Hajiya Kaltume”

“Na'am Hajiya Fatee ke kadai kike?”

“Ni kadai nake yanzu yar iskar yarinyar nan ta fita”

“Ba dai Afra ba?”

“Ita fa”

“Ikon Allah yaushe kuma ta fara zuwa gidanki?”

“Yanzu fa, ina zaune sai gata ta zo ita da yara wai an zo a gaishe ni, waya sani
ko wani mugun abun aka kullo min a kawo min, ta mallake ni kamar yadda ta mallake
min ďa”

“Tsab kuwa zata iya shi, indai magani ne wannan yarinyar babu inda bata sani ba,
gashi ta tsaneki ko maganin mutuwa ma zata iya miki”

“Kamar an yi a gabanki, ai an sha fada min ta yi ta yi samun sa'a ne bata yi ba,


shiyasa na tsaya a kafata bana wasa kar ta jedar da ni a zuciyarsa kuma Wallahi
idan ina da rai sai Fadil ya kara aure”

“To ke Hajiya Fatee anya wannan shedaniyar surukar ta ki zata yarda ta bar Fadil
yayi aure?”

Hajiya Fatee ta yi dariya.

“Hajiya Kaltume kenan kina magana kamar baki san wacece ni ba, ai idan ta kwana da
shiri wani a hanya ya kwana, daga ita har uwarta sai sun kyale min ďana, komai
shige shigensu da tsafe tsafe da yardar Allah sai hankalin Fadil ya juyo kaina ni
ma sai na sarrafa ďana yadda nake so”

Hajiya Kaltume ta jinjina kai tana kara yarda da zancen Hajiya Fatee.

“Na yarda da haka, domin a yanzu na sarawa lamarinki, ni yanzu ma kira na yi na yi


miki albishir, dazun da safe Alhaji yake ce min na kawo masa abun karyawa na cire
Bedsheets din da Iyami ta saka, ni tun a lokacin na san wani abu zai faru, kuma na
tambaye shi lafiya be fada min ba, yanzu kuma Hurriya ta shigo tana kuka wai Hamad
ya daketa a nan take fada mana Amma bata gidan wai ta tafi gidansu har sai ta haihu
zata dawo”

Hajiya Fatee ta daki cinyarta da karfi ta kyalkyale da dariyar ƙeta da jindadi.

“Ke daga jin haka ai kin san abun da muke nema ya samu, ai duk wanda ya ci tuwo da
mu miya ya sha, kuma gadon ari sai fanna, sirrin iya sai marɗibo, yanzu kam sama ta
yi wa yaro nisa sai dai ya tada kai yayi kallo, ai na faɗa miki kowa yace zai iya
haɗeye gatari to sakar masa ɓota, kuma idan ta sha mu ba mu karya ba, yaro baya ja
da mu muja da ubansa...”

Haka Hajiya Fatee ta rika jero kirari da karin magana cikin alfamari da tinƙaho.
Hajiya Kaltume ta miƙe tsaye ta fara yawo a ɗakin tana jin kamar ta taka rawa.

“Wallahi sai a yau na ji wannan ƙunci da nauyin da ya tsaya min a zuciya ya sauka,
tun da Alhaji ya auri Iyami farinciki ya gagareni, duk wani abun da zan samu a
duniyar nan farincikina raggage ne, saboda Iyami, yarinya daga zuwa aiki kin aure
mai gida har da su ƴaƴa gashi ya murje ido ya nuna kamar ya fi sonta da kowa,
ƴaƴanta ma kamar ya bude ciki ya saka su ya rufe haka yake ji”

“Toh daman ina ke ina kwanciyar hankali da farinciki Hajiya? Mai aiki ta aure miki
miji? Ai haka suke shiyasa ake cewa ďan iska na birni shege na kauye sai tsoron
ɗansa, ai da zarar sun yalla ido sun ga ana jindadi a gida to sai sun aure miki
miji, ita wannan shegiyar gorar Afra da ta fahimci duniya kin ga duk bokonta bata
son ko mai raino balle kuma wata mai aiki”

“Tana da gaskiya Wallahi, sai dai haka kuma ba zai hana ďan mu kara aure ba”

“Aure kadai? Ai sai ta bar gidan nan matukar ina raye, duk wata mallaka da ta yi ma
ďana sai na kwance ta, kuma ki zuba ido ki gani ba dai wannan Malamin ya iya aiki
ba zaki sha mamaki”

“Yanzu so nake ki shirya mu kai masa sallama kuma na sake fada masa bukatar domin
ina gudun kar ya maida ita”

“Karki damu, bari sai kura ta laba zamu sake komawa, daman ai na fada masa duk abun
da aka ba shi karin alkalami ne kawai, biya sai bukata ta biya”

“Lallai kuwa zan masa biya mai kyau, domin ya yaye min bakincikin da nake kwana na
tashi da shi, a kullum burina Iyami ta tafi ta bar min miji, yau kuma wannan burin
ya cika Alhamdulillah”

Dariya suka yi a tare sannan Hajiya Kaltume ta yi mata sallama ta sauke wayar tana
jin kamar an mata bushara da gafara.
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

4️⃣

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Shi ne abun da Hajiya Binta take ta nanatawa idonta a rufe domin danta be zo mata
da labari mai dadi ba, a cikin matansa daga wanda ta rasu har wadanda suke a
gidansa yanzu babu wanda take so irin Iyami, domin macece wadda ta san kanta take
bata girma take rawar jiki da ita tana kyautata mata kamar uwarta.

“Subhanallahi Tsoho baka kyauta ba, ka yi gaggawa kuma daman gaggawa aikin sheidan
ne, ina ma baka aikata ba ka dan daga mata kafa ko kuma na turata gidansu har sai
ka samu natsuwa”

Cikin wani kalar rauni da rashin sukunin abun da ya aikata ya sake noce kansa kasa
ya sauke ajiyar zuciya.

“Hajiya natsuwar ce ta gagare ni samu, ba yau na fara jin bana da sukuni idan bana
tare da Iyami ba, ji nake kamar wani abu ne a saman kaina, sai a yanzu da na
sauwake mata sannan na ji nauyi ya sauka, ni kaina ina son Iyami amman bana jin
natsuwa a zamantakewarmu yanzu, kuma na yi ta addu'a ina fatan samun sauki abun
amman hakan ya gagara wata kila sakin shi ne mafi alheri daman aure rai ne da shi”

“Har saki nawa ka yi mata tsoho?”

“Daya na yi mata Hajiya”

“To da sauki idan abubuwa suka daidai wata kila za a iya gyarawa, ko dan yan
diyanta Tsoho, dubi Hurriyya da Hamad ga cikin dake jikinta yaran nan ba za su taba
jindadin zama a gidan idan bata ciki ba, ko ma kallon iyayen kowa na nan ta su bata
nan sai ya saka su jin wani iri”

“In Sha Allahu zan ba su duk wani jindadi da farinciki da yaya suke bukata a gurin
uwa da uba, ban taba fadar maganar nan a gaban kowa ba sai yau a gabanki, Hajiya
duk cikin yayana na fi kaunar Hurriya, saboda kokarinta ga kuma lalurar da take
tare da ita, Allah ya saka min tausayin yarinyar nan, fitowa daga gida zuwa nan
Wallahi yaran nan kawai nake ta tunani a raina”

“Tsoho”

Ta kira sunansa sai ya dago ya kalli mahaifiyarsa da fatar jikinta ta fara zazzaga
saboda tsufa.

“Dan Allah idan ka samu sukuni ka dawo da Iyami dakinta, ko ba komai ta saba da
rayuwar jindadi ga kuma ciki ga tunanin yaranta be kamata ka saka mata da haka a
irin wannan lokacin ba, idan ma baka yi hankali ba tana cika idda wani zai dauke ta
mace mai kyau da kurciya haka nan, ka kusan haihuwarta fa amman tana zaune gidanka
gwanin sha'awa ga girmama mutane yarinya mai hankali da tarbiya”

Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi.

“Hajiya ban sake ta sai da na bata kyauta gidana da yake samaru, kuma na bata kudin
da zata iya rike kanta da su naira miliyan ashiri, kuma babu abun da zan karba daga
kyautar da na taba mata, kayan dakinta da komai ma gobe zan saka a kwashe a kai
mata har gidansu, wata kila dai zaman auren ya kare gaba daya, dan Allah karki
cilasta ni aikata abun da zai hana ni samun natsuwa ki yi mana addu'a kawai”

“Toh Tsoho Allah yasa hakan shi ya fi alheri, ya kawo mafita a tsakaninku”

Hajiya ta fada muryarta na rawa hawaye na cika idonta har suna kokarin zubowa,
mikewa ta yi tsaye ta shige dakinta ta bar shi a katon falon dake cike da sanyi ac.
Hannu ya saka ya dage kansa yana jin wani karin rashin natsuwar da bakinciki na
kusanto shi, ada yayi tunanin idan ya rabu da ita zai samu sakewa, sai dai
bakinciki rabuwa da ita ba dan zuciyarsa na so ba, da kuma tunanin damuwar da
yaransa za su shiga ya hana shi samun natsuwa, arzikinsa daya a yanzu ya daina jin
wannan nauyi da yake ji a lokacin da yake tare da ita. Ya dade zaune a cikin falon
kamar wanda ya rasa makama sannan ya tashi ya fice yana gyara babbar rigarsa. Yana
fitowa direbansa ya fito ya bude masa motar ya shiga ya maida kofar ya rufe
sannanya zagaya ya shiga mazaunin tuki ya tashi motar suka fice daga gidan, kamin
ya isa gurin da yake gudanar da kasuwanci kiran Bappa ya shigo wayarsa ya fi a
kirga amman yaki ya daga saboda ya san maganar Iyami za su yi masa.

HURRIYA POV.

Yassar na riga da hannunta har suka isa part dinsu, shi ya fara tura kofar falon ya
shiga sannan ya rikota ta shigo.
“Careful”

Ya fada yayinda take saukowa kan karamin stairs din dake bawa mutum damar shiga
cikin falon.

“Hamad....!”

Yassar ya kira sunansa a tsawace sai ya juyo rike da kofin kankara yana kallon
kofar falon fuska babu annurin ido sun masa ja alamar yayi kuka sosai.

“Akan me zaka daki Hurriya kuma ka fasa mata glass?”

Yassar yana fada ya saki hannun Hurriya ya nufi inda yake tsaye cikin bacin rai, a
maimakon Hamad ya gudu kamar yadda sauran yara ko kuma kanen Yassar suke idan zai
dake su, shi sai yayi tsaye yana jiran isowar Yassar idan ma yanka shi zai yi sai
dai yayi, amman taurin zuciyarsa da jin zai iya karawa da kowa a gidan ya hana shi
tsoron kowa.

“Ba magana nake maka ba?”

“Ita take shiga min hanci”

“Ba hanci ta shigar maka ba ido, ko laifi ta yi maka ba ita ce Yayarka ba? Kana
namiji zaka rika fada da mace? Kuma macen ma yar'uwarka? Sannan duk abun da zaka
mata be isa a fatar baki ba sai ka kai ga fasa mata gilass gashi nan ai ka ja Musib
ya mareta”

Yassar na kaiwa ayar karshe Hamad ya ji ransa ya yi mugun baci zuciyarsa ta kawo
kamar wani babba.

“Me ta yi masa to?”

“Ba a sani ba, da baka fasa mata gilashin ba zata tafi tana lalaben fuskarsa ne har
ya kai ga marinta? Haba Hamad kai baka jin tausayin yar'uwarka ne? Kowa yana zaune
lafiya amman kai ban da kai? Gidan ka fitini kowa? Ita din ma ba zaka raga mata
ba?”

Yassar ya juya ya kalli Hurriya.

“Hurriya zo nan”

Daga inda take tsaye ta fara takowa cikin abun da Allah ya yassare mata na gani har
ta iso gurin ta tsaya daidai inda Yayanta yake tsaye.

“Ka bata hakuri”

Hamad ya kara murtuke fuska.

“Ita zata fara ba ni hakuri ai ita ta fara taba ni”

Kasancewar Hurriya mai son zaman lafiya ce ta tsoron fitini ko tashin hankali yana
rufe baki ta bude nata.

“I'm sorry”

Yassar ya kai mata duka a saman kai

“Waya aikeki shi ya kamata ya fara baki hakuri ai, ba ki ce babba ba”
“I'm sorry too”

“Okay bata hannu ku gaisa”

Yassar ya fada, nan kam ba musu Hamad ya mika mata hannu, sai ta mika hannayenta
duka biyu ta lalabo hannunsa ya mika masa nata suka yi musabaha.

“Good ba fada daga yau kun yarda”

Hurriyya ta daga kai, shi kuma goga ya ki cewa komai. Yassar ya juya yana fadin

“Bari na dauko miki glass dinki da yake dakina”

Yassar na fita falon, Hamad ya kama hannun Hurriya suka isa dinning yaja mata
kujera ta zauna, ya aje kofin kankarar dake hannunsa sannan ya juya ya nufi sama,
kai tsaye dakinta ya shiga yana shiga ya bude gurin da take aje kayanta ya dauko
box din glass din daya daya rage dakinta ya sauko da saurinsa ya tsaya gabanta ya
bude glashin ya saka mata da kansa, sai gata tana murmushi ganin ganinta ya dawo da
kyau kamar kowa.

“Thank You”

“Ki sha cornflakes dinki zamu tafi Islamiya”

“Kai ba zaka sha ba?”

“Na sha zobo”

“Amma ta ce... ”

Tunawa da ta yi da cewar idan ta fada masa Amma tace su daina zama da yunwa zai iya
rufe da fada wata kila ma ya hada mata da duka ya saka ta fasa fadar hakan.

“Toh”

Hannu ta mika ya janyo kofinta na dazun da ta jika cornflakes din ta fara sha, bata
juyo ba sai da ta ji karar bude kofar falon.

“Kin dauko wani?”

“Hamad ya dauko min, daman shi daya ya rage”

Yassar yayi murmushi daman ya san masu saurin fushi da fitina sometimes sun fi kowa
zuciya mai kyau.

“Ya kyauta bari naje na aje wannan”

Ya juya sai Hurriya ta kira shi.

“Yayana”

Ya juyo

“Thank you”

Yayi mata murmushi.

“Ur welcome”
Ya fada sannan ya fice daga falon ita kuma ta juya ta cigaba da shan cornflakes
dinta. Yana rike da box din glass din ya shigo part dinsu, stairs ya hadu da Hajiya
Kaltume tana saukowa shi kuma yana kokarin hawa, kiran sunanta yayi sai ta tsaya
tana kallonsa.

“Hajiya me kika fahimta da maganar Hurriya?”

“Wace maganar?”

“Cewar Amma zata tafi gida har sai ta haihu”

“Ikon Allah Yassar ina ce dai ni da kai duk kunne biyu muke da shi kuma kai ma ka
ji maganar nan, bakin halin ne da tashi da zaka ce me na fahimta? Ina ruwanka da
fahintata? Aunata fahimtata akan wane dalili?”

“Haba Hajiya magana ce kawai fa, tsoro nake ji kar dai a wani abu ya faru?”

“Koma minene ai idan ta yi tsami zamu ji, miye a hannunka?”

Ta tambaya a kokarinta na kawar da maganar. Ya kalli box din.

“Gilashin Hurriya ne”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi.

“Sai ka yi dan gatan Hurriya, gar yanzu kana ajeye da gilasanta”

“Uku ne kawai a hannuna, biyu suna hannunta Hamad ya fasa dayan yanzu sauran hudu”

“Yayi kyau ka cigaba da aje su da kyau, Allah ya raya maka yar kanwar nan taka
Yassar”

“Ameen”

Ya amsa sannan ya wuce ya haye sama, Hajiya Kaltume ta bishi da harara.

“Kai kan ba dan a cikin gida na haife ka ba, sai na ce canja min kai aka yi, yaro
sume sume sai munafurci fal a ciki oh ni Kaltume”

Ta ja tsaki sannan ya karasa saukar ta nufi kitchen dinta, tana shiga hannunta ta
fara wankewa sannan fara juya miyar dake kan wuta, da gudu Umm Salma ta shigo
kitchen da wani irin murna har haki take.

“Hajiya Khari ya kira ni tace Appa ya saki Amma?”

Hajiya ta yi mata alama da ta yi shiru da sauri tana nuna mata kofar kitchen din.

“Bari sai Yayanki ya fita kume farincikinki”

Salma ta daga kai cikin murna ta fice daga kitchen din tana tsalle saboda jindadi.
Sai da Hajiya ta gama miyarta tsab sannan ya kwashe ta kawo ta a dinning kana ta
nufi stairs tana kwalawa yaranta kiran

“Umm Salma ko Umm Khairi waninku ya zo ya jera mana abinci a dinning”

Salma ce ta fito har wani tangadi take tana rawa kunneta na makale da ipod, Hajiya
Kaltume ta yi murmushi ta dauke kai ta shige dakinta, da sauri ta karasa gurin
gadonta cikin nauyin jiki irin nata ta dauki wayarta da kiran ke daf da tsinkewa.
“Hello Hajiya ina wuni”

Daga dayan bangaren Hajiya Binta ta amsa.

“Lafiya Kalau, Kaltume ke kadai kike?”

Hajiya Kaltume ta yamutsa fuska daman a gurinta uwar miji bata da wani muhimmanci.

“Eh Hajiya ni kadai nake, Lafiya dai?”

“Toh Lafiya ba kalau ba, magana nake son yi dake akan yaran nan Hurriya da Hamad”

“Me ya faru da su?”

Hajiya Binta ta sauke ajiyar zuciya.

“Dazun mijinki ya zo nan ya fada min hukuncin da ya yanke akan Iyami, ba mu san
abun da Allah zai yi a gaba ba, amman kamin nan Kaltume ina son ki ji tsoron Allah
ku rike Hamad da Hurriya amana, domin su da marayu duk daya a yanzu”

Hajiya Kaltume ta kai zaune saman gadonta farinciki a mamaye ta, domin dazun
hasashe take yanzu kuma gaskiyarce zaharan Hajiya Binta zata fada mata.

“Hajiya ban fahimce ba”

“Ai kin san komai Tsoho ba zai rasa fada muku ba”

“Wallahi be fada mana komai, wata kila dai ita Nafisa ya fada mata, amman ni ban
san komai ba”

“Dazun ya zo nan ya fada min cewar sheidan yayi nasara akansa ya sallami Iyami, sai
dai saukin abun saki daya yayi mata, kuma be sallame ta ba sai da ya damka mata
gidansa dake samaru area kuma ya bata kyautar naira miliyan ashiri, duk da haka dai
ina kyautata zaton zata dawo dakinta kamin lokacin ke da Nafisa duk ina son ja muku
kunne akan yaran nan”

Hajiya Kaltume bata san lokacin data mike tsaye ba ta daki kirjinta da karfi.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un... Amman Alhaji yayi kuskure abun da ba ayi da


kurciya tun can da ba za'ayi yanzu bayan ga yara”

“Ni dai na kira na ja muku kunne ne kawai, domin na san ko na nemi ya bani yaran ba
zai aminta ba saboda yana son yayansa kamar yadda yake son uwarsu, Allah ya
tabbatar mana da alheri”

Hajiya Binta na kaiwa nan ta katse kiran. Wani irin bille baki Hajiya Kaltume tayi
ta kube shi.

“Munafurcin banza da wofi, wato ga Kaltume makiyiyar Iyami da yayanta har da wani
kira ki bani amanar yara, ko mutuwa ta yi ai ba zan karbi amanar yayanta ba balle
tana da rai, idan kin isa ki saka ya dawo da ita mu gani, har kina fada min yana
son yayansa kamar yadda yake son matarsa tsabar kin raina ni”

Duk wani farinciki da walwala dake zuciyarta da fuskarta ya gushe tun daga lokacin
da ta ji cewar sakin ďaya aka yi ma Iyami kuma an bata kyautar kudi da gida.

“Wallahi Iyami kin cuce ni, ko a haka dai kin ci ribar mijina, kin haihu da shi dan
ki ci gado, kuma yanzu ya sake ki ya dauki gida da miliyan ashirin ya baki, waya
taba yi ma kyautar gida a cikinmu matansa, sai dai ko wace ta siya da kudinta”
Password din wayar ta cire ta duba kiran dake kasam na surukarta Hajiya Binta ta
taba na Hajiya Fatee. Kamin ta amsa duk ta kagu har ta fara saba da marwa a dakin.

“Assalamu Alaikum Kaltume”

“Hajiya Fatee zama be gan ni, tsugune bata kare ba, Saki daya Alhaji yayi ma Iyami,
kuma wani abun da ya fi ko wane bakin ciki kudi ya dauka ya bata har naira miliyan
ashiri”

“Million ashiri?”

“Ai ba nan haushin yake ba, ya bata kyautar gidansa dake samaru, yanzu uwarsa ta
kira tana fada min har wani gargadi take min saboda ya san gatan jikokinta, kin san
ba jikokin da take so irinsu, kuma tun da saki daya ne zata iya buga kafa a kasa
tace sai ya maida uwarsu”

“Tsab kuwa wannan shegiyar tsohuwar zata iya, saboda ba sonki take ba”

“Ina fa, kuma ba ba zancen dawowarta kina ganin zan yarda Iyami ta bar gidan mijina
kuma ta yi arziki da dukiyar mijina? Wallahi bata isa ba ai yadda ta ci amanata
haka ni ma zan nuna mata ruwa ba sa'an kwando ba ne, sai an koya ma Iyami hankali,
dan haka ki shirya tafiya gobe goben nan nake son mu tafi ba sai wata rana ba, kar
mu sake ayi mana sakiya, domin ita ma zata iya shiga nata malaman ta janyo
hankalinsa”

“Maganarki haka take Kaltume, karki damu zan kira shi tun yau na fada masa gobe
zamu zo, amman fa ki zo da wuri saboda kin san dajin nan babu ďan mutum ga halin da
ake ciki kara mu yi tafiyar safe kar mu yi mugun gamo”

“In Sha Allah karfe 8am a gidanki zata yi min, sai na zo”

Daga haka suka yi sallama, Hajiya Kaltume tana kwafa tana jinjina lamarin.

IYAMI POV.

“Ban san me ya hana shi daukar wayata ba, kunyar abun da ya aikata yake ji ko kuma
rainin wayo ne da raina talaka”

Gwaggo ta kalli Bappa dake maganar ta girgiza kai.

“Alhaji Haruna ba shi da dabi'ar raina talaka, domin be taba mana haka ba wata kila
dai yana jin kunyar abun da ya aikata ne, wata kila kuma baya son ka yi masa magana
komawarta ne”

Iyami ta kalli Bappa cikin karfin hali ta ce.

“Bappa da dai zaka kyale shi da ka kyauta min, domin na yi ta tambayarsa ko na masa
wani laifin ne, amman ya ce ban masa komai ba, kawai dai bana jin natsuwar zaman
aure da ni ne a yanzu”

“Tun da can be san da wannan ba sai yanzu? Kuma be tashi sakinki sai yanzu da ciki
wata shida?”

“Ba saki yayi mata na wulakanci ba, ya kyautata mata daidai gwargwadon yadda ake
son kyautatawa a saki da zaman aure, kuma aure rai ne da shi ko babu komai idan
lokacin rabuwa yayi dole sai an rabu, mu dan bashi lokaci har ya dawo hayyacinsa ni
na tabbatar Alhaji Haruna yana son Iyami akwai dai abun da aka yi”

Wannan karon Gwaggo ce take maganar. Bappa ya mike tsaye yana ja tsaki.

“Akwai yadda aka yi na me? Ku yi komai ba za su bar shi ga Allah ba sai kun ci wani
abu, yanzu zaki iya cewa asiri aka yi masa, kar ma ki kawo wannan maganar, ni na
fita”

“Toh Allah ya dawo da kai lafiya”

“Ameen”

Ya fice yana sake gwada kiran number Alhaji Haruna Mai Yadi. Fitarsa da kamar minti
uku Hindu ta shigo dakin tana sallama, Gwaggo ta amsa mata. A bakin kofar dakin ta
saki jakar hannunta tana kallon amiyarta.

“Iyami da gaske Alhaji ya sake ki?”

Iyami na kallonta sai hawaye suka zubo mata, Gwaggo na ganin haka ta mike tsaye ta
fice daga dakin domin bawa kawaye damar tattaunawa.

________________

Masu karatu kuna ganin Alhaji Haruna ya yi ma kansa mai kyau kuwa? Ya Hurriya zata
ji idan ta san cewar Appa sakin Ammanta ya yi?

https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

5️⃣

“Akwai matukar mamaki ace duk son da Appan Hurriya yake miki ya sake ki, saki fa
Iyami?”

Amma ta saka hannu biyu ta share hawayen fuskarta.

“Ni ma dai ganin nake kamar ba sakin ba ne, saboda ban saka ran ba mutuwa ce zata
raba ba, har yanzu tunani nake ko dai boye min yayi? Wata kila na masa wani laifi
ban sani ba”

“Bayan kin ce ya fada miki baki masa komai ba?”

“Hindu namiji na sakinka haka nan? Ai na ga sai da dalili”

“Dalili daya ne Iyami sa'ar da matansa suke nema sun samu, kin mata a cikin manyan
mata kuma tsofin mata kike zaune? Matan da sun kusa sa'ar gwaggo? Wace ce warinki a
cikinsu? Iyami babu kalar kazafi da kage da ba su miki ba duk dan saboda ki bar
gidan amman burinsu be cika ba sai a yau, maganin ma na san sun gwada Allah dai ne
be ba su sa'a ba sai yau”

“Hindu Waallahi ina son mijina, mijina kuma yana so na amman yau komai ya kare”

Amma ta fashe da kuka.

“Har sai kin fada? Ai kowa ya san yadda kuke zaune ya san mijinki yana sonki kuma
ke ma kina sonsa, sakin ma da zai miki Iyami na musamman yayi wane namiji ne zai
saki mace ya dauki dukiya ya danka mata? Ai sai zababbu cikin mata, kuma ko yanzu
karki yanke kauna In Shaa Allah zaki koma dakinki ki cigaba da addu'a nima kuma zan
taya ki kuma ki saka ayi miki a islamiyayo nima kuma zan zaka ayi miki”

Kasa cewa komai Amma ta yi sai kuka take kukan da da zaka iya rantsewa mutuwa aka
yi mata, idan ta tuna da sakinta Appan Hurriya yayi sai ta ji zuciyarta ta narke ta
rasa me ke mata dadi a duniyar nan da ace mutuwa yayi sai ta dangana amman tunawa
cewar yana raye kuma shi da kansa ya zabi rabuwa da ita ya fi komai daga mata
hankali.

“Toh wai a can kika bar su Hurriya?”

“Ya ce zai rike su”

Ta amsa mata cikin kuka. Hindu bata wani dade a gidan ba ta mata sallama ta fita
domin komawa nata gidam ta dora girki. Haka ta wuni a daki idan Gwaggo da jikokinta
suka shigo sai ta boye fuskarta ta danne kukanta har sai idan ta kadaita ita kadai,
tunanin yaranta ya tsaya mata a rai, tana ta auna lokacin dawowarsu makaranta da
kuma irin abubuwan da suke idan sun dawo, da dare yayi sai ta kasa bacci domin
wannan ne daren farko da zata kauna a gidansu tun bayan aurenta shekara goma sha
shida. Ko biki ake a gidan ko wata hidima Appa baya barin ta kwana ko da kuwa ba
girkinta. Daren sai ya zame mata wani dare na dabam da bacci ya gagara kusantar
idonta ma balle har ya sace ta, kukan ma sai ta neme shi ta rasa wata zuciyar nata
raya mata hanyoyin da zata bi ta shirya da mijinta sai ta saka zaren idan ta karshe
sai ga ba hanya ce mai bullewa ba, dare ne da yayi mata tsawo fiye da sauran
dararen da suka gabata, karfe biyu da rabi ta doro alwala ta fara raya daren da
sallah nafila a haka aka kira sallah asuba akan idonta.

HURRIYA POV.

Da murna ta shigo dakin Appanta ta zauna kusa da shi a kasa kamar yadda ta saba,
sai ya kai hannu ya shafa kanta zuwa bayanta yana murmushi irin murmushin nan dake
dauke da so da kauna da kuma farincikin abun da idanuwa suka yi arba da su.

“Hurriya toh yaya?”

“Lafiya kalau Appa, ka dawo lafiya?”

“Lafiya Kalau, ina can gurin aiki zuciya na nan tare da ku sai tunaninku nake Ina
Hamad”

“Shi ya ce ba zai zo ba?”

Ta amsa tana kai hannu ta gyara gilashin idonta. Hajiya Kaltume dake zaune kan
carpet ta yi murmushi, irin murmushin nan da ya zame mata dole ne, domin ta kasa
hadeye maganar da Appa yayi cewa yana gurin aiki zuciyarsa na gurin yayansa ta ce.

“Hamad ai ba zai zo ba, dazun ma dukanta yayi ya fasa mata gilashi sai da Yasir ya
shiga tsakaninsu”

Appa ya kalli Hurriya cikin yanayin damuwa.

“Me ya hada ku?”

Ta zayyana masa abun da ya faru daga karshe ta rufe da fadar Yasir ya shirya su.
Appa ya sauke ajiyar zuciya

“Ina ganin yaran nan za su koma gurin bangarenki sa zama Kaltume, saboda a rika
saka musu ido, kar wata Hamad ya ji ma yarinyar ciwo, daman ko dan kula da abincin
da wasu abubuwan dole su koma can”

“Gurina kuma Alhaji? Ni da nake da yan mata cike da daki? Kuma ka san yadda bama
jituwa da uwar yarinyar nan yanzu nan Hurriya ko kaya ta taka na cire mata cewa za
ayi na cutar da ita, ba zan hana ta zama ba idan haka kake so, amman dai da zaka
barta a hannun Nafisa wata kila zamu samun zaman lafiya, daman Nafisa bata da yara
da yawa uku ne kawai kuma mazan fita suke Namra ce kawai ka ga ta samu yar'uwa a
kusa ko? Amman ni Hajiya ma sai tace na mata ba daidai ba domin ta kira ni tana ja
min kunne akan yaran nan”

Ko kadan maganar da Hajiya Kaltume ta yi bata yi ma Appa dadi ba, sai yake jin
kamar bata son zaman yaransa a gurinta ne, hakan kuma sai ya kara jefashi a cikin
damuwar sakin mahaifiyarsu da yayi gashi nan ya koma nema musu gurin zama domin ba
zai iya barinsu a katon part din uwarsu su biyu kawai ba babu mai kula da su.

“Hurriya yata ina kike son zama?”

Ya tambaya yana kallon fuskarta, Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume sannan ta kalli
mahaifinta ta ce.

“Gurin Hajiyarka ko Gwaggo”

“Ba zan iya bari ku zauna hannun kowa ba matukar ina raye, na fi sonku a kusa da ni
na rika yaran wasu ma ta ina zan bada nawa riko? Idam har ba zan iya bari ku zauna
gurin Iyami ba to ba zan iya hakurin ku zauna a gurin kowa ba, je ki kira Hamad”

Hurriya ta tashi ta fice, Hajiya Kaltume ta bita da kallo Appa kuma ya sauke ajiyar
zuciya.

“Yaran nan sun zamar min kamar wasu marayu, Wallahi yau saboda tunanin abubuwan da
suka faru na kasa sukuni”

“Akwai damuwa kam sosai, na da zaka hakura ka dawo da mahaifiyarsu da duk yafi
wannan nema musu gurin zama da kake, idan ma wani laifin ta yi maka ka yafe mata
dan Allah ko mu da muka kwana biyu aka saki a yanzu ai sai mun ji dabam balle kuma
ita da take da sauran kurciyarta”

Appa be ce komai ba bayan sauke kai da yayi kasa, domin baya jin dawowa da ita
mafita ne kamar yadda sakin ma ya kasa zame masa mafita domin ko yanzu jin yake
kamar akan ƙaya yake saboda tunaninta domin yana matukar son matarsa ga kuma
tunanin makomar yaranta. Hajiya Kaltume ta tsare mijinta da ido ganin ya noce kai
kasa sai zuciyarta ta raya mata zai iya dawowa da ita kenan ganin yadda ya zurfafa
a tunani ga kuma son yaranta da yake. Sai a lokacin da Hurriya ta dawo dakin tare
da Hamad sannan Hajiya Kaltume ta kawar da kai tana kwafa a zuciyarta, Appa kuma ya
dago ya kalli Yayansa. Hurriya ta zauna a inda ta zauna dazun Hamad kuma ya tsaya
jikin kofa fuskarsa ba yabo ba fallasa.

“Hamad ka ci abinci?”
“Aa”

Ya amsawa Appa da kai. A take Alhaji Haruna ya kalli Hajiya Kaltume.

“Ba a basu abinci ba Kaltume?”

“Tuwo na girka, ka san Hamad ba ya cin ciwo kuma basa cin abinci da ake girkawa
masu aiki”

“Idan shi baya ci ita Hurriya bata ci? Haba Kaltume kin san uwar yaran nan bata
cikin gidan nan a matsayinki na babba ki kasa kiran yaran nan ki ba su abinci?”

“Ban yi tunanin ba su ci ba, ranka ya dade ayi hakuri ba za a koma ba In Shaa


Allahu”

“Hurriya zaki ci tuwo?”

Hurriya ta daga kai a hankali daman tuwo is one of her favorite saboda abincin
Appanta ne ita kuma duk abun da Appanta yake so tana sonshi, kuma yawan girka shi
da Amma take ya saka ta saba da cinsa, domin Alhaji Haruna ba shi da wani abinci da
ya fi tuwo duk arzikinsa ya fi son agirka masa tuwo a gidansa domin abun da ya saba
da shi tun kamin zuwan arzikin.

“Zan ci tuwo Appa”

Ya kalli Hamad da ko a yau ko sannu da zuwa be masa ba kuma be gaishe ba, abun da
be saba ba domin duk tsaurin kansa yana gaishe da Appa yana masa sannu da zuwa
kamar yadda Amma ta koya masa.

“Kai kuma me kake son ci? Je ka kira Dahiru ko Bello ya kaika Restaurant ka siyo
abun da kake so”

“Bana son komai”

Ya amsa kai tsaye ba tare da ya kalli kowa ba. Appa ya kalleshi da kyau.

“Hamad zo nan”

Ya shiga cikin dakin sai ya zauna nesa da Appa kamar wani bakonsa ko wanda be saba
da shi ba, bayan kuma a da can ba haka yake masa ba idan yayi nesa da shi to yayi
laifi ne, amman idan babu laifi baya zama nesa da mahaifinsa kuma sukan zauna su yi
hira da juna ayi wasa da dariya sai dai ba kamar yadda suke yi da Hurriya ba.

“Me aka yi? Waya taba ka?”

“Babu ba ayi min komai ba”

Hajiya Kaltume ta tabe baki tana murmushi.

“Kai ma dai Alhaji, a gidan nan ba zai taba Hamad ya kwana lafiya? Idan ma an fi
karfinshi ai kasan yadda yake yi ma mutane ruwan duwatsu ko kuma ya shammaci mutum
yayi masa wata ƙetar”

Hamad ya dago ya kalli Hajiya Kaltume da irin kallon da ya fi kama da harara, daman
can shi ne mai taya Amma kishi wani lokacin, Hurriya kam team babu ruwanmu ce.

“Toh na ga yana ta bata rai ne kuma yace ba zai ci abinci ba?”


“Uhm. Hmm”

Kawai Hajiya Kaltume ta ce ta cigaba da kallon Appa dake tambayar Hamad ina yake
son zama.

“Ina Hurriya zata zauna?”

“Gurin Momy”

Appa ya amsa masa.

“Nima zan zauna a can”

“Toh yayi kyau, amman dai ka saki ranka Hamad ka ji? Kuma ka ci wani abun yaushe
rabonka da abinci?”

“Na sha zobo da rana”

“Zobo ai ba abinci ba ne, zaka sha tea da bread a hada maka?”

“Bana son komai Appa bana jin yunwa”

“Shikenan zan yi ma Nafisa magana sai ku maida kayanku part dinta”

Appa ya fada cikin yanayi na rashin jindadin dansa be saka komai a ciki ba. Hamad
ya mike tsaye ya juya. Appa ya bishi da kallo yana fadin.

“Hamad babu ko sai da safe?”

“Sai da safe Appa”

Ya fada ba tare da juyo ba har ya fice. Hurriya ta mike tsaye domin yunwa ta matsa
mata lamba.

“Appa ina tuwon?”

Appa take tambaya sai Hajiya Kaltume ta amsa mata.

“Je bangarena ki zuba ki ci, mahaifinki ya rima ci balle ku ci tare”

“Toh”

Ta nufi kofar fita da saurinta. Sai da ta fice Appa ya kalli Hajiya Kaltume ya ce.

“Dan Allah a rika kula da yaran nan, su da marayu duk daya yanzu”

“Alhaji, dan Allah na ci wannan alfarma dan Allah ko dan yaran nan, mahaifiyarsu ma
tunaninsu sai ya isheta kuma kai yanzu baka lura Hamad fushi yake da kai ba?”

“Fushi me?”

“Ka kore mahaifiyarsu mana”

“Ba kin cw bata fada musu ba?”

“Eh amman ka san shi ya yafi yar'uwarsa wayo, ba mamaki ya gane, ita kanta Hurriya
idan ta fahimta ba zata jidadi ba”

Appa ya sauke ajiyar zuciya.


“Ba zan iya ba ne Kaltume, gobe za a zo da motoci akwaishe mata kayanta”

“Subhanallahi Alhaji har saki nawa ka yi mata ne?”

“Daya”

“Amman za akwashe kaya da wuri haka? Wai me yayi zafi ne shi ba wuta ba?
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ta fashe da kuka ta mike tsaye ta fice daga dakin tana rusar kuka kamar gaske. Appa
ya busar da iskar bakinsa shi kansa ya san it's too early ace an kwashe kayan Amma
a gidan daga sakinta, sai dai kiran da Bappa yake masa yake son amfani da damar ya
nuna musu babu sauran zama tsakaninsada Amma, domin ya kasa amsa wayarsu tun jiya
saboda be san abun da zai fada musu ba. Kai ya gigirza sannan ya tashi tsaye ya
fice daga part dinsa zuwa part din Hajiya Nafisa wato Momy.

HURRIYA POV.

Hurriya na shiga bangaren Hajiya Kaltume ta samu Umm Khairi zaune a dinning tana
cin nata abincin daren, da a bangaren mahaifiyarta ne sai da ta bude ta zuba amman
a nan dole ta tsaya a zuba mata ko kuma a bata izinin zubawa.

“Yaya Khairi Hajiya ta ce na zuba abinci”

“Gashi nan ai dauki plate ki zuba mai isarki”

Hurriya ta dauki plate ta bude manya warmers din ta ta dauki mulmular tuwon da aka
nade a leda ta raba uku ta zuba daya a plate ta rufe ta bude dayan ta zuba miyar
kubewa ďanye ta saka nama da man shanu sannan ta rufe ta ja kujera har ta zauna ta
tuna bata wanke hannu ba ta tashi ta shiga bandakin dake falon ta wanke hannunta ta
dawo ta zauna ta fara cin tuwon, sai da ta yi nisa da cin abincin sannan Khairi ta
kalleta.

“Hurriya”

Hurriya ta dago a hankali ta kalli yayarta Khairi wadda ta kira sunanta.

“Na'am?”

“Me Appa yace miki da ya aiko a kira ki?”

“Tambayarmu yayi ina muke son zama”

“Toh ina kika zaba?”

“Ni dai na ce gurin Gwaggo ko Hajiya, amman yace aa sai dai gurin Momy”

Khairi ta yi fuskar tausayi.

“Allah sarki, Wallahi na tausaya muku babu dadi rayuwa gidan babu uwa a gida, da ma
dai Appa zai yi hakuri da ya dawo da Amma, Hurriya na ga Appa yana jin maganarki
why not ki roke shi ya dawo da Amma idan ma wani laifin ta yi masa ya yafe mata”

Hurriya ta yi mata wani kallo na rashim fahimtar inda zancenta ya dosa.

“Amman zata dawo idan ta haihu ai”


“Toh Allah yasa ya maida ita, wata kila akwai gyara ai Wallahi duk ban jidadi ba
dazun har da kukana”

Hurriya na jin haka sai kwakwalwarta ta dauka sarai ta gane karatun Khairi a take
wani irin tashin hankali ya same ta, idonta dake cikin farin gilashi suka cika da
hawaye ta kasa hade lomar tuwon dake bakinta. Slowly ta mike tsaye taja kujera baya
ta fara tafiya zuciyarta na buga kamar zata fasa kirjinta ta fito, tana fita falon
ta watsa da gudu bangarensu da karfi ta tura kofar falon Amma ta shiga. Hamad na
kwance kan kujera yana kallon remote a hannunsa.

“Hamad wai Appa sakin Amma yayi? Wai rabuwa suka yi? Yaya Khairi ta fada min”

Tana maganar yana kuka even though bata gama tabbatarwa ba. Hamad ya tashi zaune
yana kallonta.

“Ai ke ce mahaukaciya shiyasa baki gane ba”

A nan Huriyya ta samu damar fashewa da kuka mai karfi, ta juya da sauri ta nufi
bangaren mahaifinta.

*** *** ***

“Ah Ah Alhaji ina ce Kaltume ce Babba a gidan nan? Me zai hana su zauna a
bangarenta?”

Appa ya mike tsaye.

“A nan nake son su zauna, kuma nan za su zauna ko kin yarda ko baki yarda ba, domin
ke da su duk a karkashin ikona kuka kuma a gidana”

“Aa Alhaji gaskiya ban ci ƙashi ba ba zan ci aman tsoka ba! Har ina? Yara da
girmansu da komai a kawo min su? Da wani abun arziki ne ai matarka take tarewa ta
karbe sai a yanzu da yake wahala ce za a kawo min”

Appa ya nuna kansa.

“ƴaƴane wahala Nafisa? Ke dai har abada ba zaki taba zama matar kirki, har abada
mai hali be taba fasa halinsa ba, kowa yana girma yana kara hankali da hali na gari
amman ban da ke”

“Daman ni ban taba haske a idonka ba, masu haske Iyami ce da Kaltume, ka san ni ka
san halina ni bana son a shiga sabgata ina bangarena babu ruwana da kowa, akan me
yanzu za a dauko yayar sarauniyar gida mace da ta hana ka ganin martaba a kawo min”

Alhaji Haruna ya nuna ta da yatsansa.

“Sau daya tak bakinki ya sake furta wata magana marar dadi akan Iyami da yayanta
sai mugun saba miki, ni na zabi su zauna a nan kuma a nan din za su zauna, idan
baki son zama da ƴaƴana jinina ƙofar gidan a bude take..!”

Momy ta aje numfashi da karfi.

“Bismillah ga dakuna nan su zabi wanda suke so su zauna, gidan naka ne yaya naka ne
ni ma taka ce Allah ya ba mu hakurin zama”

Fuuuu! Appa ya fice daga falon nata cikin mugun bacin rai. Namra da Musib suka
bishi da kallo su kansu sun manta when last su ga mahaifinsu a cikin bacin rai irin
wannan sai yau.

“Tsakani da Allah takurawa ce dawowarsu a nan, musamman ma dan iska yaron nan Hamad
ni ubansa zan ci Wallahi”

Cewar Musib yana jin haushin hukuncin da mahaifinsu ya yanke. Bakinciki ya hana
Momy sake cewa komai ta kai hannu ta dauki sarkar zinarinta dake kan aje a hannun
kujera ta mike tsaye ta nufi upstairs, kamin ta isa dakinta ma wani aiki ne saboda
izza da isa kamar wadda bata son taka kasa haka take tafiya.

Bakin gadonta ta zauna ta rike da sarkar sai cika take tana batsewa, ita dai ta
san tana daga kafa akan kishi da matan Alhaji Haruna domin ganin take babu sa'arta
a cikinsu Hajiya Kaltume dai yar talakawa ce arzikin na Alhaji Haruna Mai Yadi ne,
Iyami ma haka rufin asirinsu na Alhaji Haruna ne domin har gidan da iyayenta suke
ciki a yanzu shi ya siya musu shi yake dauke da nauyinsu.

Kuma Iyami ba sa'arta bace a shekaru, kuma ta fi Hajiya Kaltume zama makaskanciya a
idonta domin ita ga aiki ta zo yi a gidan ta aure Alhaji Haruna, ba dan ma da
kaddarar aure ta hana ba kuma yara sun shiga tsakani ba wata kila da ba zata iya
hakurin sharing miji daya da yar aikin gida ba, kallon da take yi ma Amma bata da
ajin da zata yi kishi da ita sai idan abun ya motsa.
Ita dai abun da ta fi tsana shi ne a shiga sabgarta, idan ta shiga sha'aninta na
masu arziki har mantawa take da Hajiya Kaltume da Amma, a yanzu kuma kawo mata
Hurriya da Hamad da Appa ya dage sai shi ne abun bacin ranta a yanzu, domin da su
zauna a gurinta kara ya dawo da uwarsu ta rainin abunta, sam sam Momy bata son
yayan kowa idan ba nata ba, bata mutanta kowa sai masu kumbar susa, idan baka da
arziki har ganin take kamar baka cika mutum ba.
https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

6️⃣

Da tunanin Amma Appa ya dawo apartment dinsa, tsansar biyayyarta da yadda take
gujewa bacin ransa da nuna kulawa akan duk wani abu da ya shafe shi. Ya tabbatar da
ita ce ba sai ya bukaci a bawa Hurriya abinci ba, matukar ta san uwar yaran bata
gidan zata yi kokarin kwatantan kyautata musu kuma ta ja su a jiki, haka ma da ita
ce ya zo mata da zancen dawowa ƴaƴan abokiyar zamanta a bangarenta zata yi marhabun
ta karba da hannu biyu ko da kuwa bata son haka ba zata nuna har ya gani ba, duk
wani abu da Amma ta san Appa yana son kokarin raya shi kaunar abun take ba ta bata
masa rai ba.
Hannayensa hade a bayansa yake tafiyar fuskarsa a yanutse zuciyarsa a hargitse yana
jin kamar ya fashe da kuka gaba daya ya rasa me ke samunsa ya rabu da matarsa
rabuwar ta haifar masa da rashin kwanciyar hankali da bacin rai, zamanta a gidan
kuma masifa ce a gidansa masifar da be san ta micece ba domin shi dai ya san
matarsa bata masa laifi ba, be san dalilin da ya saka ya tsane ta ba. Kukan Hurriya
ne abun da ya fara masa maraba da zuwa a lokacin da ya kunna kai cikin falonsa,
kuka take sosai irin kukan nan da ya hana gilashin idonta tsaya saboda hawayen da
ke cika shi, ta rike gilashin a hannu lipa dinta da jikinta sai rawa suke, dishe-
dishe ta ga alamar shigowar mutum bata bukatar saka gilashi domin tantance waya
shiga, ta san tsayinsa da yanayin tafiyarsa ta haddace komai. Shi ya taho da sauri
ita ma ta nufo inda yake da sauri tana rike da gilashin dayan hannunta kuma yana
lalabensa.
“Appa. ..apa... Appa... Appa wai ka rabu da Amma?... Sakin Amma ka yi?”

“A gurin wa kika ji wannan maganar Hurriya? Waya fada miki haka cikin daren nan?”

“Yaya Khairi.... Appa da gaske? Appa why? Yanzu mu kadai ne zamu rasa uwa a nan
Appa! Me Amma ta yi?”

Tambaya take tana wani irin kuka numfashi na fitar mata da karfi kamar ranta zai
fita. Idon Appa ya cika da hawaye

“Bata yi komai ba Hurriya, be kamata ki shiga cikin magana irin wannan ba, zauna a
nan ina zuwa”

Ya nufi kujera da ita ya zaunar da ita, ya juya ya fita gaba daya abubuwa sun rike
masa har ji yake wani abu na juya masa cikin kai, kamar za a haukata shi haka yake
ji. Bangaren Hajiya Kaltume ya nufa tun a tsakar falon ya fara kiran Khairi rai a
matukar bace daman ciwon sakin Amma da ya kama shi, ga bacin ran da Momy ta saka
masa yanzu kuma Khairi ta kara masa wani ta hanyar batawa Hurriya. Umm Khairi ta
fito daga dakin Hajiya tare da Maama Umm Ruman na biye da su a baya, Umm Salma da
Yasir kuma suka fito a nasu dakuna duk suka sauko kasa.

“Alhaji Lafiya?”

Cewar Hajiya Kaltume da ta riga su saukowa gabanta har faduwa yake.

“Akan wane dalili Umm Khairi zata fadawa Hurriya sakin mahaifiyarta aka yi? Ita
mahaifiyar bata fada ba sai ke yar iya? Wannan ba rashin hankali da rashin tarbiya
ba ne? Ki shiga cikin maganar iyayenki?”

Ya juya gurin Hajiya Kaltume.

“Kin ga abun da kika hanyo ko? Kin maida yaran nan kawayenki da maganar da ya dace
da wanda be dace ba duk fada kike a gabansu, har suna jin sun isa sun kai su saka
baki a zaman takewar mahaifinsu, sai na koya miki hankali sai na koya miki hankali
Ummul Khairi”

Jikinta ya dauki rawa domin ta san halin Appansu idan hau yana wuyar saukowa. Yasir
ya karbawa Appa.

“Iskanci ne da rainin hankali, ta fi uban kowa baki da bakin iyayi a gidan nan
kamar wata babbar mace, yau sai kin fadi wanda ya aike ki”

Hajiya Kaltume na jin haka ta yi saurin zunguje Khairi.

“Ba zaki bada hakuri ba yar iskar yarinya? Idan kuma ba haka ba ne sai ki fadi
yadda aka yi ai ko?”

“Appa Wallahi karya take min, yarinyar nan munafukace sai dai idan labe ta yi, ko
kuma so take ta hada min sheri”

Tana rufe baki Yasir ya fara dukan bakin nata ya saka hannnunsaya kama lips din ya
jan sai da ta ti ihu sannan ya rufe ta da duka gaba daya, Hajiya Kaltume ta fara
kokarin kwatar yarta Appa kuma ya fice daga falon ba tare da ya hana Yasir dukan
Khairi ba.

“Ai fa an taba yar gata yar gaban goshi yar lasa da halshe, kai dan Allah karka
kashe min ƴa saboda ƴar wasu da ba zata amfana maka komai ba”

Hajiya Kaltume na masifa tana kwatar Khairi dake ta rusar ihu, Maama da Salma sai
haushi suke ji saboda ana dukan yar'uwarsu Ruma ce kadai take jin abun da yayarta
ta yi bata yi daidai ba.

A bangaren Hurriya Appanta na fita sai ta tsagaita kukanta ta share hawayen da suka
ki tsaya mata ta saka gilashin da zai bata ganin kofar fita dakin daidai ta mike
tsaye ta fito daga bangaren mahaifinta ta dawo na su bangaren tana tafe tana hawaye
har ta isa. Sai ta ta tura kofar falon ta bude sai kuma ta kasa shiga domin jin
take kamar Amma ma mutuwa ta yi ba barin gidan ba bata taba sanin haka kewa take ba
sai yau da ta yi kewar mahaifiyarta. Kusan da ita da wanda ba shi da lakka a jiki
duk daya domin tun a yanayin tafiyarta zaka fahimci zuciyarta ta karaya salulu ta
shigo falon ta zauna kan kujera har lokacin Hamad na zaune a inda ta barshi, sai
dai a yanzu fuskarsa na nuna danuwar dake zuciyarsa domin ya bata rai sosai ba
kamar dazun ba d ya bar abun a cikin zuciyarsa. Fashewa Hurriya ta yi da kuka tana
girgiza kai ji take kamar ace mata ba gaske ba ne, da ace ta san sakin Amma Appanta
yayi babu abun da zai hana ta binta, da ba zata yarda ta zauna a gidan ba, a yanzu
kam ta yarda ita wawuya ce da bata yi saurin ganewa ba, domin tana da saurin yarda
idan aka fada mata abu dauka take ko da kuwa ba gaskiya ba ne. Kukanta ne ya saka
Hamad hawaye yana ta dantse baki yana boye cikarsa domin zuciyarsa kawowa take
kamar wani zaki, amman sai duk da hakan sai ya gagara rike kansa shi ma ya fasa
kuka, ita da shi suka zama kamar wadanda aka cewa Amma ta mutu ta bar su.

“Hurriya Hamad”

Kusan a tare suka dago suka kalli kofar gefen Dinning din kofar da Appa ke tsaye,
kofar cikin falon Amma ce dake basu damar shiga bangaren Appansu. Hurriya ta tashi
da sauri ta nufi inda yake tana kuka sosai Hamad kuma ya dauke ido alamar baya son
ganin Appa.

“Wannan kuka sai kace an yi mutuwa? Haba karku saka kanku a damuwa tsakanin halshe
ra hokora ma ana basawa balle kuma mutum da mutum, dan tsabani muka samu shi ne
Amma ta tafi gida, amman da zarar al'amurra sun daidaita zata dawo”

Hurriya ta kasa magana sai kuka take, Hamad kuma ya mike tsaye ya share hawayensa
ya nufi sama.

“Karka shiga, ba a nan zaku kwana ba, na yi magana da Momynku a can zaku kwana ku
zo muje”

Be jira cewarsu ba ya kama hannun Hurriya zuciyarsa na masa babu dadi, daman can
shu baya son kukan wani ko ganin wani a damuwa balle kuma yaransa, sanin cewar shi
ne silar damuwar ya saka shi jin babu dadi gaba daya abubuwan sun zo masa ta yadda
be yi zato ba. Ganin Appa ya nufi kofar fita falon tare da Hurriya ya saka Hamad ya
bi bayansu, sai da suka fita harabar gidan gaba daya, sannan Appa ya tsaya ya
tsayar da yarsa ya daga kanta ta kalleshi.

“Haka zamu shiga bangaren Momynki kina ta kuka Hurriya? Dan Allah ku yi hakuri idan
ba so kuke ni ma na yi kukan nan ba, ba ku san abun da yake cikin zuciyata ba, ina
cikin wani irin tashin hankali da rudani marar misaltuwa”

Kai kawai ta iya daga masa ta saka hannayensa ta share hawayenta tana ta aikin hade
kukan dake neman ya gagari tsayawa a iya bakinta da idonta.

“Ammanku ba mutuwa tayi ba, zaku iya zuwa ku ganta a duk lokacin da kuke so, ita
zata iya zuwa ta ganku, Hamad na san kai ne mai zuciya ka sakawa kanka hakuri dan
Allah ko dan yar'uwarka”

Ko saitin gurin da Appa yake tsaye Hamad be kalla ba, yadda ya dauke kai yana
kallon wani gurin sai ka rantse da Allah ba da shi Appa yake magana ba, domin a yau
kam ba shi da abokin tsana kamar Appansa saboda sanin cewar ya rabu da Amma, ko da
kuwa ba zai iya fadar abun da ya faru tsakaninsu ba, hausawa suka ce mai lalabe a
duhu balle an haska masa, a banza yayi fushi balle an taba shi. Appa ya dauke kai
ya rika hannun Hurriya suka cigaba da tafiyar, da kansa ya shiga falon, be zarce ko
ko'ina ba sai Stairs kai tsaye ya nufi dakunan da suke gefen bedroom din Momy kamar
yadda suke a kowane bangare, ya san dakin Namra da na Musib da Miwan dan haka be
taba dakunansu ba ya nufi wani dakin ba dabam ya tura kofar dakin sannan ya saki
hannun Hurriya daki ne dake dauke da furniture na mutum daya domin Appa ya saka an
zuba furniture an gyara ko wane daki duk kuwa da kasancewar wasu dakunan babu kowa,
ba dan komai ba sai dan irin haka ko kuma idan an yi baki ko ma idan yaransa sun yi
sha'awar canja daki daga wani zuwa wani. Hurriya ta daga kafarta ta shiga cikin
dakin ta isa bakin gadon da zai wadaci mutum daya ta juyo ta zauna ta a hankali
tana kallon Appanta dake jan kofar dakin. Gam... Kofar na amsawa gabanta ya yanke
ya fadi, gaba daya sai ta ji kamar wata duniyar aka kawo ta, sai ta ji kamar wani
gidan da bata san kowa ba kuma bata da gatan kowa a ciki aka kawota. Rabon da ta
shiga bangaren Momy ma an dade, babu ruwanta da bangare sai da dalili ita ma Momy
bata shiga nasu bangaren ita ta ware kanta dabam a gidan. Dayan dakin dake kusa da
na Hurriya Appa ya budewa Hamad

“Nan zai mana Hamad?”

Ya daga kai sannan ya saka kai ya shige dakin da kansa ya turo kofar dakin ba tare
da ya jira mahaifinsa ya rufe masa ba. Appa ya sauke ajiyar zuciya ya juya ya
sauka, Namra da Musib suka hada ido suna mamakin yadda Appa ya shigo da Hurriya be
ma bari ta zo da kanta ba.

“Musib ina Miwan?”

“Ya fita da magariba nan Appa”

“Namra da Musib dan Allah a zauna lafiya, yaran nan kanenku ne, jini daya ne ku da
su, bana son na ji wani tashin hankali ko fada, Hamad dai kun riga kun san halinsa
ba sai an fada muku ba, duk wani abun da zai yi ku kawar da ido ni kaina da nake
mahaifinsa hakuri nake da shi, Hurriya kuma kun san babu ruwanta da fita dan Allah
a zauna lafiya”

Nasiha yake musu amman zuciyarsa cike take da kunci da damuwa narar misaltuwa. Appa
ya amsa cike da ladabi

“In Shaa Allahu Appa”

Ya dan motsa kansa kadan alamar gamsuwa sannan ya nufi kofar fita.

“Sai da safe Appa mu kwana lafiya”

“Allah yasa”

Ya amsa sannan ya fice. Yana sakin kofar falon Musib yayi kwafa ya mike tsaye ya
nufi stairs Namra ta bi bayansa, ita ta shige dakin Momy Musib kuma ya nufi dakin
da zuciyarsa ta raya nasa Hurriyya na ciki. Ya tura kofar dakin kamar abun arziki
ya tsaya daga bakin kofa yana kallonta idonta shar da hawaye.

“Yar gatan Appa, da kansa ya riko hannunsa ya kawo ki, kuma saboda ke yayi ta fada
da Momy”

Uffan Hurriya bata ce masa ba, har ya gaji da tsayuwa ya bar mata kofar a bude yayi
tafiyarsa. Runtse ido ta yi tana jin wani sabon kuka na zo mata, ta dawo a rakube
gurin ta ta san cewar zata sha azaba da wahalar zama, da ma ace bangaren Hajiya
Kaltume aka ajeta ko ba komai zata samu sauki ta wani bangaren saboda Yasir, amman
a na bangaren ta san babu mai sonta, gaba daya sai ta ji ta zama wata marainiya
ashe ba sai da rashin uwa da uba ake maraici ba. Musib na barin kofar dakin Hurriya
ya nufi dakin Hamad ya tura, kwance ya hango shi saman gadon ya baya kofar baya,
kuma budewar da Musib yayi be saka Hamad juyo dan ya duba ko waye ba. Wani mugun
kallo da tsana irin ta yan uba Musib ya jefi kanensa da shi, sannan ya bar kofar
dakin shi ma be rufe masa ba, Hamad na jin alamar an tafi ya juyo ya sauko saman
gadon ya iso gurin kofar ya rufe ta da karfi ya saka key, Musib da be jima da barin
bakin kofar ba ya juyo ya kalli kofar jin yadda aka bugata da karfi.

“Zaka sha wahala yaro”

Yayi kwafa ya nufi dakin Momy sai wani huci yake kamar mace, daman shi ne mai
kishin da matan ubansa a gidan sai dai yana boye abun a zuciyarsa, yadda yake jin
kiyayyar Iyami da Hajiya Kaltume ko Momynsa bata jin kiyayyarsu haka domin ita sai
idan kishin ya motsa mata ne take kula su ko kula wani abu da ya shafesu.

Daren sai ya zamewa Hamad da Hurriya dabam, sanin cewar rabuwa mahaifiyarsu ta yi
da mahaifinsu ya hana Hurriya rutsawa har safe, sai ta raya daren da kuka Hamad
kuma bayan ya gama nasa fushin bachi ya sace shi. Ta bangaren Appa ma yadda ya ga
rana haka ya ga dare, kwanan Hajiya Kaltume ta bangaren be kuranye masa damuwarsa
ba, sai ma ya kasa kwantar daga karshe ya koma falo ya zauna ya kunna Tv sai dai
kuma babu mafitarsa a cikin kallon kamar yadda babu shi a cikin bacci sai ma karin
damuwa, me yasa ya aikata shi ne abun da ya tsaya masa a rai yake ta tambayar
kansa, idan kuma ya tuna da abun da yake ji idan tana gidan sai ya ga kamar yin
haka shi ne daidai.

Washe gari da wuri Hajiya Kaltume ta tashi, daman duk ranar girkinta da wuri take
tashi ta shirya masa abun karyawa, kasancewar bata da mai aiki tun bayan da ta
dauki Iyami aiki ta aure mata miji bata sake yarda ko mai sharar gida ta sake dauka
ba, sai dai ta yi komai da kanta ba kamar Momy ba da masu aiki ne suke mata komai
sai dai ta ci idan kuma ranar girkinta ne sai dai ta dauki na Appa ta kai masa.
Ko da bakwai ta yi ta gama hada masa ruwan zafin tea da gasa masa bread dan ya
fada mata tea kawai zai sha baya son cin komai. Yana shan tea yana hamma saboda
bachi da ya gagareshi da dare da alama yana neman fansa a yanzu da safiya.

“Wai dazun ina barin bangarenka Hajiya Fatee ta kira ni”

Ya dan juyo kadan yana kalleta alamar ina saurarenki.

“Wai danta Fadeel ya samu tsabani da matarsa shi ne take son na zo”

“Allah ya kyauta...”

Yadda ya amsa mata ya karantar da ita izinin zuwa ne, daman kuma ta san ba zai
hanata ba.

“Ameen zaman auren ne na su, zaman lafiya ta gagara Allah ya shirya tsakaninsu”

Appa dai be sake cewa komai ba, har ya shaye tea ya aje cup be taba bread ba. Hakan
kuma be yi ma Hajiya dadi ba domin ta san damuwar ba zata wuce ta ƴaƴan Iyami ba ko
kuma ta Iyamin ma gaba daya. Ta dauke cup din ta fita ba tare da ta fada masa yanzu
ta tafi ba da safen nan. Ta isa bangarenta rike da cup din. A dinning din da duka
matansa suke fara cin karo da shi a kowane falo idan suka fito daga bangarensa ta
aje cup din sannan ta nufi dakinta, tana shiga ta raba jikinta da tufafin da ta
saka da safen nan ta daura tawul ta shiga bathroom, a gaggauce ta yi wanka gudun
kar ta yi latti sanin cewar inda za su je kaune dake gaba daji baya daji. Ko da ta
fito ta samu Khairi zaune akan gadonta fuska a kumbure musamman bakinta.

“Subhanallahi haka Yasir ya fasa miki baki saboda yar iskar yarinyar nan?”
“Ba laifin Ya Yasir ba ne Hajiya, laifin Appa ne yana mugun son yarinyar nan, ya fi
kaunarta da duka sauran ƴaƴansa, dubi yadda ransa ya bace saboda na fada mata
gaskiya bayan kuma gaskiyar ce”

“Hmmm ai ni ganin nake kamar ba banza uwar yaran nan ta bar Alhaji ba, ita kanta ai
ba a banza ta aure min miji ba, yanzu kuma saboda yaran nan Allah kadai ya san ran
mutun nawa zai ɓace a gidan nan”

“Wallahi sai na rama komai ta dade”

“Toh ki rama dai ta sigar lalama, in ba haka ba Alhaji ko Yasir su ci ubanki kin
san jira kawai suke”

Ta tashi ta fice dakin tana wani zakuɗa ita ga balagaggiya. Hajiya ta shirya cikin
koriyar Atamfa ta saka farin mayafi ta sauki jakarta mai kala daya da gyalen da
kuma talkaminta ta saka sannan ta dauki wayarta ta kira daya daga cikin drivers din
gidan ta sanar masa fitarta. Gurin da take aje kudi ta bude ta dauko kudi mai yawa
ta zuba a jakarta sannan ta rufe ta rataya jakar ta fito rike da wayarta sai kamshi
take zubawa irin na manyan matan masu kudi kuma masu miji da ikon gida.

“Hajiya fita zaki yi?”

Maama ta tambaya.

“Eh wani guri zamu je da Hajiya Fatee”

“Allah ya tsare, Hajiya kin ga yadda Ya Yasir ya fasa bakin Khairi”

“Na gani, ku ma sai kun yi taka tsantsan ai, ni ba dan ubansu daya ba ai sai na
tsora ta na ce aurenta yake son yi”

“Lallai ya fi sonta da mu ma”

“Hmmm Allah dai ya kyauta, ki tashi sauran yan 'uwanki kar su yi latti makaranta,
ni na fita”

Daga haka ta fice daga falon Maama na yi nata Allah ya tsare. Ko da ta fito direban
har ya tashi motar ya juyata tana fuskantar gate domin ya san uwargidan Alhaji
Haruna Mai Yadi bata daukar raini. Tana shiga motar be tsaya da ita ko'ina ba sai
gidan aminiyarta Hajiya Fatee, yana aje ta ya juya a can ma ba su bata lokaci ba,
Hajiya Fatee ta kira direban dake kai su kauyen ta sanar masa sun shirya, ba su
yarda su tafi da motarsu ba saboda tsoron masu kidnapping da kuma tonon asiri, sai
dai su dauki shatar motar kasuwa ta zo ta dauke su har gidan Hajiya Fatee ta kaisu
inda za su je, kasancewarsa mijin Hajiya Fateen ya dade da rasuwa ita kadai ce a
katon gidan sai yan matanta biyu da kuma masu aiki da danta Fadeel ya zuba mata.

Misalin karfe tara da rabi na safe suka kama hanyar kauyen gidan zalla dake cikin
local government din Kwatarkwashi. Suna tafe suna hira Hajiya Fatee na kara fada
mata yadda matar danta Afrah ke son mulkar mata ďa ta saka shi ya manta da ita.
Idan ta kai aya sai Hajiya Kaltume ta dauko nata zancen na abun da ya faru
tsakaninta da Alhaji a jiya. Sanar da shi da suka yi cewar suna nan tafe ya saukaka
musu wucewa kai tsaye dakin da yake gabatar da tsiface-tsifacensa. Sai da ya fara
yi musu maraba da zuwa sannan Hajiya Kaltume ta ciro kudi 300k ta aje masa tana
masa godiya.

“Aiki yayi Malam, dan haka na zo da kaina na kawo maka goronka, kuma na yi maka
godiya”

Malamin da hakoransa ke daskare da jan goro ya yi dariyar jindadi da farinciki ya


jinjina kai.

“Hajiya ai na fada miki, indai muka yi aiki ba a dawo mana da shi, kuma kar tunanin
kin yi kin yi baki dace ba yasa ki karaya a gurinmu, idan kin ji ana malam anjima
da nisa ba ma gobe da nisa ba to kika zo nan kakarki ta yanke saka kawai”

“Na gani ai Malam Wallahi na gode, domin shekara da shekaru ina neman yadda matar
nan zata bar min mijina amman abu ya garara sai an yi kamar za a rabu sai kuma ka
ga ba rabuwar bace, sai yanzu Allah ya kawo karshen abun, sai dai ko yanzu ni ina
jin tsoro domin na lura ya shiga damuwa matuka gaya saboda sakinta da yayi, ina jin
kar ya ce zai dawo da ita domin saki daya yayi mata”

“Ina ko alama! Karki damu Hajiya, idan har mutum zai mutu ya dawo to kishiyarki
zata dawo gidan, ai farraqu muka musu ita tana gabam yana yamma har abada ba zama a
tsakaninsu”

Wani kalar dadi ya lullube Hajiya Kaltume.

“Haka nake so, kuma ina son a koya mata hankali so nake ka yi mata wani aikin da ba
zata sake aure ba har abada, tun da ta zabi kishi da ni to ko bayan ta bar gidan
mijina sai ta dandana bakincikin da nadanar auren Alhaji da ta yi, sannan be sake
ta sai da ya damka mata kudi har miliyan asirin, Malam ina son a lalata duniyar da
ya bata, har da gidan da ya mallaka mata idan akwai yadda za'ayi a ruguza gidan ko
ma ya karbe abunsa, kuma a daureta ko kare kar ya sake sha'awarta balle har ta yi
aure”

“Wato so kike a lalata duniyar da ya bata, ba wadda ya bata kawai ba, har tata
duniyar da ta mallaka za a iya lalatawa idan kina so”

“Aiko idan ka yi min haka, ina mai tabbatar maka aikin Hajji bana da kai za'ayi,
kuma zan maka kyautar kudi har naira miliyan daya”

Malamin ya sake yin dariya yana gyara babbar rigarsa.

“Hajiya na miki alkawari akaifa kishiyarki ba zata sake amfana da ita ba, ba
duniyarta ko ta mijinki da ya bata ba, har dukiyar wani idan ya dauka ya bata ba
zata taba amfanarta ba, ita da aure ko sai lahira idan ana yi, kuma yadda ba a
mutuwa a dawo haka ba zata sake dawowa a gidan mijinki ba”

“Alhamdulillah”

Hajiya Kaltume ta fada tana daga hannu sama ta yi ma Allah godiya, sannan ta kalli
Hajiya Fatee suka taba suna dariya. Daga bisani Hajiya Fatee ta kora masa da nata
bayanin.

“Malam nima da tawa mtsalar na zo yau, suruka ce ta saka ni a gaba, ta mallake min
ďan yaki ya kara aure kuma baya jin maganar kowa sai ta matarsa, ga kudi yana da
shi amman ko kyauta zai yi sai abun da ta so yake bayarwa, ni so nake a raba su ya
sake ta saki uku idan da dama”

Malamin ya amsa mata da kai.

“Ya sunanta, ya kuma sunan ďanki?”

“Afrah ake kiranta, shi kuma Fadeel”

Ya dauko kasa dake cikin farantin katako ya dora a cinyarsa yayi zane zane ya
jinjina kai ya dago ya kalli Hajiya Fatee.
“Lallai sai kin tashi tsaye, ta mallaki danki Mallaka bata wasa ba, kuma idan ba ki
yi da gaske ba abu ne mai wahala ya sake yin aure ko da kuwa ta mutu”

“Ka ji irinta ba, shedaniyar yarinyar na sha wahalar yarinyar da can babu ruwansa
da ni ma, sai da na tashi tsaye, dan abun da ubansa ya bar min duk a can ya kare,
ba dan Allah yasa nasa gadon yayi albarka kuma ya samu babban aiki ba da yanzu mun
kade”

“Toh lallai dai gata nan ko yanzu a tsaye take akan danki”

“Dan Allah a zaunar da ita, idan da dama ma a kwantar da ita a saka ta bacci ko a
sumar da shegiya”

Malamin yayi dariya

“Ai tun da kika zo nan komai zai zama tarihi Hajiya, ki bada kudin karan alkamin
kawai a saka aiki”

Da sauri ta bude jakarta ta dauko kudin da ba zai wuce 30k ba ta aje masa.

“Ga wannan ban zo da kudi mai yawa ba, amman dai a fara saka aiki da wannan idan
zan dawo zan ciko jaka da yardar Allah”

“Toh shi ke nan ba matala idan na gama aiki na hada abubuwa zan kira na fada muku
sai ku zo ku karba ko kuma ku aiko ko kuma ni da kaina na aiko muku”

A bisa wannan suka yi masa sallama suka fito suka dawo cikin motar. Direban ya a
kama hanya, ba su yi nisa da garin ba suka rage gudu ganin an tsayar da motocin
dake gabansu a zatonsu sojoji ne, hankalinsu be tashi ba sai da suka fara jin harbe
harbe wasu na ihu.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un Bandits ne”

Direban ya fada, da sauri Hajiya Fatee ta kalli Hajiya Kaltume da cikinta ya soma
murdawa.

“Mun shiga uku mun lalace, ya zamu yi?”

“Shiyasa bana son shigowa dajin nan gari gaba daya ya lalace a yanzu”

Cewar Hajiya Kaltume ido na raina fata.

“Kai direba ya zamu yi?”

“Hajiya ni ba ku kuka kawo ni nan ba, kuma gashi motoci a bayanmu balle mu juya”

Maganar yake yana leken motocin dake bayansu ga karar bindigar sai matsosu take.

“Toh ko dai mu kira Malamin nan mu fada masa”

Hajiya Fatee da fitsari ya fara zubo mata ta kalli Hajiya Kaltume.

“Ya mana me? Soja ne shi ko dan sanda?”

“Ya turo aljannu su dauke mu mana, Hajiya mutanen nan suka kama mu ai mun shiga
uku, kuma na cewa Alhaji me? Daga zuwa sulhun aure!”

Cikin tashin hankali Hajiya Fatee ta ce


“Aljannu suka dauke mu ai shikenan mun bar duniya kuma kara ma wadannan da aljannu
dan su kai mu za su inda babu kowa su aje, ko su kai mu China aljanni ai ba zai
dauke ka ya aje ka nan kusa ba sai wata duniyar”

Hajiya Kaltume ta fashe da kuka tana neman agajin Allah.

“Allah ka yafe mana Allah ka dube mu Allah Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, ni


har na bata zane”

Direba ya bude kofar a hankali ya sulale ya yanki daji cikin ciyayi. Hajiya Kaltume
ta saka kalma shada, Hajiya Fatee ta kama mata suka karasa suka kallon juna kowacce
na kai hannu ta taba yar'uwarta. domin sun san yadda suka ci suka koshi nan ba za
su iya gudu ba ko sa sun gwada hakan.

____________________

Hmmmmm masu karatu kun taba gani ko jin mugun kishi da bakar hassada irinta ta
Hajiya Kaltume?
Ni dai Hurriya ta ba ni tausayi domin rayuwa gurin da baka bukatarka yana da
wahala, musamman idan babu uwa a kusa.

Ta wani bangaren kuma Iyami tana da laifi daga zuwa aiki sai ki aure mijin mata?
Ina laifi ki rumgume talaucinki ki shafawa kanki lafiya, yanzu wa gari ya waya...?

Mu hadu da ku page din gobe, amman kamin nan ina son na ga Comments baza-baza line
by line in ji Bature...

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

7️⃣

Ana kiran sallah asuba ta sauko daga kan gadon ta nufi kofar dakinta ta bude ta
fito, a hankali ta sauko downstairs, tana isa bakin kofar falon bata tsaya komai ba
ta kai hannu zata bude kofar.

“Ina zaki je?”

Ta juyo da sauri domin bata yi tsammanin wani zai iya fitowa at this early ba.

“Fita zan yi”

Ta amsawa Namra. Cikin mamaki Namra ta wara ido.

“Asuba ne fa”

“Na sani, Hijab zan dauko na yi sallah”


“Haba Hurriya shiga dakina ki dauko nawa mana, saboda Hijab sai ki fita tun a asuba
ki koma part dinku kamar wata bakuwa, ke a gida kike fa”

Hurriya ta dan sauke kai kasa daga barin kallon yayarta wadda ta bata shekara uku
da haihuwa. Namra bata sake ce mata komai ta nufi kujerar da ta zauna a jiya ta
dauki agogonta da assignment din da ta yi, sai da ta kusa hayewa sannan Hurriya ta
rufa mata baya, cikin ladabi da natsuwa ta shiga dakin Namra ta tsaya jikin kofa,
haka Hurriya take bata sakewa da mutane tana da wahalar sabo, musamman idan ta san
zaka tsangwame ta ko ka yi mata fada. Namra ta juyo ta jefo mata hijab din cikin
hanzari Hurriya ta cafke.

“Akwai carpet din Sallah a can?”

“Aa babu”

Namra ta dauki nata ta jefa mata Hurriya ta sake cafkewa ta juya ta fice daga dakin
zuwa dakinta. Bata shiga nata dakin ba sai da ta kwankwasa kofar dakin Hamad tana
kiran sunansa.

“Na tashi”

Ya amsa mata daga can ciki, sannan ta wuce dakinta ta maida kofar ta rufe. Tun
bayan da ta yi Sallah bata sake fitowa ba sai da ta auna lokacin makaranta yayi
mata, sannan ta bude kofar a hankali kamar wata bakuwa ta rufe ta nufo hanyar
saukowa kasa gabanta har faduwa yake kar ta hadu da Musib ko dan'uwansa Miwan balle
kuma Momy da ta san bata ishe ta kallo ba. Sai dai ta yi rashin sa'a Momy da duka
yaranta suna falon zaune, abun da bata saka tsammani ba domin Momy bata tashi da
wuri sai idan tana bangaren Appa shi ma da zarar ta kai masa abun karyawa zata sake
komawa bachi kuma babu mai tashinta sai gidan maigidan ne da kansa if not kowaye ya
tasheta zai gane kurensa a ranar.

“Baka fada min zaka zo ba, ai da na saka an shirya mana abinci mai kyau”

Cewar Momy tana kallon kyakkyawan saurayin dake zaune a kujerar dake facing nata,
kyakkyawan saurayin farin saurayin mai jini a jika ya girgiza mata kai yana duba
agogo hannunsa.

“Noo Momy na gode tafiyar ta gaggawa ce, yanzu zan kama hanya, kawai na ce bari na
biyo mu gaisa ne”

Momy ta yi murmushin kasaita irin na manya mata.

“Daman na sani, abinci idan ba na Hajiya Turai baka ci na kowa”

Ya dan fadada fuskarsa da murmushim da ya kara masa kyau da haiba yana daga kai ya
kalli Hurriya dake saukowa. Momy ta dan juya ta kalleta kadan ta dauke kai irin ba
ki isheni kallo ba din nan.

“Momy ina kwana”

Hurriya ta gaisheta cikin ladabi Momy har ta yi kamar ba zata amsa ba sai kuma ta
ci albarkacin bakonta amsa ciki ciki kamar an mata dole.

“Yaya Musib ina?”

Ya amsa, ta juya gurin dan'uwansa shi ma ta gaishe shi, sai ya amsa mata fuska a
sake kamar dan'uwansa, ta kalli Namra ta gaishe ta kamin ta rufe baki Namra ta amsa
tana mata an tashi lafiya, daga karshe Hurriya ta cike gaisuwarta da bakon da take
kyautata zaton yana da muhimmanci a gurin Momy da yaranta ganin yadda suke ta murna
da ganinsa kuma suka fito dukansu da sanyin safiyar nan suka zauna a falo just
because of him.

“Ina kwana”

Ya d'auki 'yan dak'ik'u kafin ya amsa gaisuwarta, shi ma kuma ba da baki ba kai
kawai ya daga mata and light smile. Binta yayi da kallo har ta wuce ta gabansa ta
nufi kofar fita.

“ƴar Mijina ce, kanenta ne ka ga ya fita dazun”

Momy ta fada masa domin ta san ba zai tambaya ba, ta san kallon da yake mata be
wuce na neman sanin wacece ba, dan zuwan da yake gidan jefi jefi be taba ganinta
ba, haka ma bata yi masa kama da masu aikin Momy ba balle yace ko yar aiki ce, ba
zai ce ya san kowa a gidan ba, amman yadda ya san familynsu musamman Momy idan har
ta bawa wani damar shiga ma a falonta to yana da muhimmanci a gareta, sai dai abun
da be sani ba wannan shigar ta dole ce ta cilastawar Appa ba dan Hurriya tana da
muhimmanci a gareta ba.

“Yaya ance an daga bikinka”

Miwan ya tambaya yana kallonsa. Mutumen da Miwan ya kira da Yaya ya juyo ya


kalleshi.

“Ka aje wannan Yaya aside ka kira ni da real sunana Jamal”

Momy ta yi murmushi mai sauti.

“Haba dai Captain dukansu fa kanenka ne ta ina za su iya kiranka da sunanka kai
tsaye, dole sai da girmamawa”

“Wallahi na tsani wannan Yayan na fi son a kira ni da sunana na gaskiya”

Ya amsa mata da murmushi sannan ya mike tsaye sai zuba kamshi yake. Namra ta mike
tsaye kamar sauran yan'uwanta tare da fadin.

“Tafiya nan da nan Yaya ba zaka dade ba”

Da hannu ya nunata.

“Yanzu na gama yi ma Miwan gargadi shi ne ke ma zaki ďana ko?”

Sai duk suka saka dariya ban da shi da ya nufi kofar fita yana yi ma Momy sallama.
Momy ta mike tsaye ta rako shi har bakin kofar falon Miwan da Musib suka karasa
gurin da ya faka motarsa suna masa a sauka lafiya, Momy da Namra kuma na tsaye
jikin kofar har sai da ya shiga motarsa yayi musu horn ya fice sannan suka dawo
cikin falon.

“Captain baka iya masa, Allah kadai ke masa daidai, komai ka yi sai yace ba haka ba
ga zuciya abu kadan ya fusata shi”

“Ai gaskiya Ammy tana hakuri da shi”

Cewar Namra Momy ta ce.

“Toh ya zata yi haka Allah yayi shi, kuma shi kadai ya bata daga ita har Yayana
magajin da suke da shi kenan”

“Kuma Allah ya hada jininsa da ke, duk ya zo garin nan sai ya zo nan”
“Kin ji Namra da wata magana, uwa daya uba daya ai ta wuce wasa, ko kin manta
alakata da mahaifinsa ne, ga kuma Hajiya Turai a bata da kawa a familynmu sai ni”

“Duk da haka dai Momy, Wallahi idan baya ra'ayinki ba zai zo ba, ba ke kadai kuke
uwa daya uba daya da mahaifinsa ba amman ke kadai ce yake zuwa gurinki, duk ya zo
gurinsu Hajjo sai ya zo nan, waya ma akai akai yana yawan kiranki”

“Haka kuma da maganarki, je ki taso masu aikin nan yau muyi tashi dole su zo su
fara aiki, ke kuma ki shirya ki wuce makaranta”

“Okay”

Ta amsa sannan ta nufi sama, Momy ta dasa hirar da su Miwan.

“Ku yaushe zaku koma hutu ne wai?”

“January nan zamu koma, ni ai gaba daya na samu na bar garin nan na huta”

Musib ya ce.

“Kai gari kake son bari, ni Wallahi kasar ce ya isheni, ba dan halin Appa ba kamar
mu zai hana a fitar waje, maza ne mu fa kuma yawanci yayan sa'ainsa duk suna waje
suna karatu amman ya hana a fitar da mu kuma shi ba zai fitar da mu ba”

“Jami'ar nan kawai zaku kare a nan, amman masters da duk wani abu da zai biyo baya
a waje zaku yi shi, na gaji da halinsa shi har yanzu be gama jefar da wannan halin
nasa na da can ba, kuma a yanzu tun da na fahimci baya bin ra'ayi toh kowa yayi
nasa ra'ayin kawai, duba yadda ya daga mana hankali jiya saboda kawai Hurriya ta
zauna a nan”

“Wai me yasa ba zata bi mahaifiyarta ba?”

“Kai kana ganin uwarta zata yarda ta bita su zauna a can? Ai ba zata yarda ba tana
ganin ga gidan arziki”

“Toh ai ko da sun koma Appa zai mata komai”

Musib ya sake fada.

“Amman dai ba kamar idan tana gidan nan ba, kuma Kaltume ba zata yarda Alhaji ya yi
haka ba, yadda ba ta bar shi ya kula da yarsa Sapna ba haka ba zata bar shi ya kula
wadannan yaran ba matukar suka bar gidan nan”

Miwan ya ce.

“Wai Momy saki nawa yayi mata ne?”

“Ina ruwana? Balle na tambaya can ta matse musu idan uku ne sun hutu, idan daya ne
ma ya dawo da ita duk ruwansu ne ba nawa ba, ni ta harkokin gabana nake shirya ba a
kaina take zaune ba, daga ita Iyamin har Kaltume babu wadda zata nuna min komai
gaba da baya, mu da talauci sai a baki shi ma dan ambata kawai, su ko babu wadda
bata tashi a cikinsa ba, ni ko babu wadda be san ubana ba a garin nan ba”

“Ai shiyasa Hajiya take shakkarki, yadda take ma Amma da yayanta bata mana haka”

“Ai bata ga fuska ba ne, ita kanta ta san na fi karfinta ta ko'ina, kuma ni bana
jiran abun Alhaji ita da Iyamin dai suka dogara gareshi”
Hira sosai suka yi ta yi Momy na koda kanta a garin gusau ma jin take ba ko wace
matar mai kudi ce sa'ar yinta ba balle kuma cikin gidan Alhaji Haruna Mai Yadi.

HURRIYA POV.

Tana shiga part dinsu sai kewar Amma ya kara daduwa a ranta, ta san da a jiya ne da
kwanakin baya da Amma take gidan sai dai ta fito daga dakinta ta sauko kasa ta yi
breakfast ba dai taje wani bangaren ta kwana ba har tana fargabar arba da Momy.
Kujera ta nufa ta zauna ta rike hannayenta hawayen dake idonta suka zubo mata.

“Huriyya...”

Ta kalli kofar kitchen din da sauri tana zabura domin ta tsorata ba yi zaton akwai
mai kallonta ba. Da sauri ta cire gilashin idonta ta share hawayenta da hannu biyu
ta mike tsaye.

“Ya Yasir yaushe ka shigo?”

“Tun dazu abun karyawa muke hadawa da Hamad”

Ta fara takawa ta nufi kofar kitchen din da yake tsaye.

“Kuka kika kwana kika yi jiya ko? Idonki har ya kumbura, kuma kin san matsalar
idonki why zaki jawa kanki wata matsalar”

“Yaya idan na tuna Amma bata nan sai na ji babu dadi, kukan zo min yake”

“Addu'a zaki yi, kuma ki daina damuwa Amma zata dawo da yardar Allah”

“Haka Appa yace maka?”

Ta tambaya tana kallonsa wasu hawayen na sauko mata zuciyarta kuma cike da daukin
ya amsa mata da eh zai haka yace.

“Aa haka dai nake sashe, kuma ni na san haka zai faru ko dan ku, baki ga yadda
hankalinsa ya tashi ba jiya saboda fada miki da Khairi ta yi, karki so ganin
fuskarta yau sai da na kumbura mata baki”

Hamad dake can cikin kitchen yana juya plantain yayi murmushin jindadi jin cewar an
kumburawa Khairi fuska. Hurriya kuma zuciyarta ta cika da tausayinsa.

“Da baka doke ta ba Yaya ai gaskiya ta fada min”

“Ba haka ya kamata ta yi ba, kuma be kamata daga ke har ita ace kuna shiga maganar
manya ba, dan haka ke ma ki kiyeye kar na cire miki ido”

Ta yi dariya tare da maida gilashinta bayan ta share hawayenta. Saboda ya dauke


musu kewar Amma ya zo part din ya fara hada musu abun karyawa yana cikin hadin ne
Hamad ya shigo sai ya kira shi suka cigaba da yi tare, bayan sun gama suka hadu a
dinning har Hurriya suka soma karyawa tea kawai Hamad ya sha sai yankan bread daya
ya ce ya koshi, Yasir ya kalleshi sai dai be ce masa komai ba domin ya fi kowa
sanin ba a cilasta Hamad yin abun da be tashi yi ba a kwashe lafiya, zai iya
cilasta masa kuma ya ci amman kuma za su yi fada su rabu da bacin rai.

“Jiya ma haka yayi be ci abinci ba”

Hurriya ta fada tana tauna bread din dake bakinta.


“Ya saka tunanin abun da ya faru ne a ransa, kina ganinsa kamar be damu ba ko? Ya
fiki damuwa daman mu maza haka muke muna boye abu a ran mu babu mai sanin muna da
damuwa sai idan an bincika ko kuma an saka mana ido”

Hurriya ta dan yi murmushi kadan.

“Amman mazan ba kowa yake da zuciya kamar Hamad ba, ya cika fushi”

“Akwai su, wasu sunada fushi sosai a mata ma ana samu balle kuma maza, baki dai
taba haduwa da su ba ne, ai halitta ce za a iya samunta a gurin mace haka ma gurin
namiji, shi ma Hamad zai daina idan ya kara girma yayi wayo”

Bata sake cewa komai ba har ta gama karyawa sannan ta tashi da sauri ta nufi
upstairs.

“Bari na yi wanka na saka uniform”

“To sai ki yi sauri domin kusa latti”

Ya mike tsaye ya fice daga bangaren zuwa bangaren mahaifinsa domin gaishe, kamin ya
isa bangaren mahaifinsa ya hango shi tsaye waya a hannunsa yana dannawa, hakan ya
saka Yasir ya cira kafa ya karasa gurin mahaifinsa sai yaja ya tsaya yana sauraren
wayar da Appa yake.

“Kamar da karfe goma dai, amman ina son a kwashe komai kamin yara su dawo daga
makaranta”’

Yasir ya dan kalleshi zuciyarsa na raya masa kayan Amma za a kwashe. Ashe kuwa ya
canka daidai domin a karshen zancen sai Appa ya karasa da fadin

“Zan turo address din da kuma number wayarta ko da ba ku gane gurin ba”

Ya sauke wayar ya shiga message dinsa ya fara rubutu location din. Yasir ya mika
gaisuwa cikin girmamawa kamar yadda ya saba.

“Lafiya kalau an tashi lafiya”

“Lafiya kalau Appa”

Daga haka Appa be sake cewa komai ba shi ma kuma be ce ba, daman baya tunanin Appa
yayi maganar Amma ko wani abun da ya shafe ta da shi idan dai ba umarni zai ba shi
akan wani abun ba, shi kuma be isa ya daga kai ya kalli mahaifinsa yayi masa
magana akan lamarin aurensa ko wani abun da ya shafi matansa ba.

“Hurriya sun tashi kuwa”

Appa ya tambaya, domin tun tashinsa zuciyarsa take son zuwa duba yaransa sai dai
gudun kar ace ga nuna banbanci ko kuma su ya fi kaunarsu da sauran yara ya saka ya
danne ya boye abun.

“Sun tashi tare muka karya ma, amman Hamad be ci wani abun kirki ba?”

“Ba shi da lafiya ne?”

“Lafiyarsa kalau Hurriya tace jiya ma be ci komai ba”

Appa ya sauke ajiyar zuciya a hankali ba tare da ya bari sautin saukar numfashin ya
fito ba. Har lokacin kuma be kalli Yasir dake tsaye gefensa ba kamar mai jin
kunyarsa. Suna tsaye gurin har yara suka fara zuwa karbar chocolate da juice din da
ya saba raba musu idan za su tafi makaranta, Appa ya koma ciki sai Yasir ya bishi
ya riko masa suka fito da kayan waje sannan ya zauna a one of kujerarun dake gurin,
ya fara raba musu suna karba yaran Hajiya Kaltume ne a gaba, Khairi kam baki ya
kumbura gashi ta turo shi gaba ita ala dole an mata ba daidai ba fushi take, sannan
Namra ta zo ta karba, a da can Hurriya da zumudi da far'a take zuwa karba kuma a
kullum Hamad sai ya rigata karba, domin shi baya bata lokaci a komai ba kamar ita
ba sarkin latti, cin abinci ma sai kowa ya cinye ita bata cinye nata ba.

“Appa ina kwana”

“Lafiya kalau Hurriya an tashi lafiya?”

“Alhamdulillah”

Ta mika hannu biyu zata karba, Yasir ya rigata ya karbe yana dariya kamar yadda ya
saba, kasancewar bata a cikin yanayin farinciki sai kawai ta yi murmushi ta hade
hannayenta. Appa ya dauko wani ya mika mata.

“Karbi, ina Hamad?”

Ta saka hannu biyu ta karba taba ba shi amsa.

“Yana bus ya ce shi ba zai karba ba yau”

Appa ya ji babu dadi sai dai be nuna ba kuma be sake cewa komai ba, Hurriya har ta
juya sai kuma ta juyo ta kalli Appa.

“Appa yaushe Amma zata dawo?”

Kallonta kawai mahaifinta yake, kamar yace me yasa kika min wannan tambayar domin
be gama saka kalar amsar da zai ba su ita da Hamad, musamman ma ita da take da
shakuwa da shi sosai wata kila Hamad zai bar abun a zuciyarsa dai dai yayi ta fushi
da shi. Yasir ne yayi hanzarin tarewa Appa numfashin da ya rasa ina sauke shi.

“Hurriyya idan zaki yi magana mai tsada da Appa, daga ke sai shi ya kamata ku yi,
ki daina yi a gaban mutane kin ji”

Ta amsa masa da kai, sannan ta kalli Appa

“Na gode Appa Allah ya saka da alheri”

Ta juya ta fara tafiya zuciyarta babu dadi. Godiya ce ta yi masa irin wadda ta saba
masa a duk lokacin da ya bata chocolate din ko kuma yayi mata kyauta kasancewar
abun da Amma ta koya musu kenan, amman a yau sai ya ji godiyarta a wata sigar ta
dabam, yake jin kamar abun da ya aikatawa mahaifiyarsu ne take masa godiya a kai,
gashi dan murmushi da far'a da kuzarin da yake gani a fuskar yarsa yau ya kau,
dan'uwanta kuma ko ganinsa be yi ba.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Shi ne abun da ya iya furtawa yana binta da kallo zuciyarsa na masa zafi, tunanin
dama da hadu na kokarin hade masa su rikita masa kwakwalwa. Yasir ya kalleshi sai
dai be ce komai ba.

“Idan sun dawo makaranta kai ko daya daga cikin direbobin gidan nan wani ya kai su
gida su duba Amma”

“Toh Appa In Shaa Allah”


Appa ya juya ya koma ciki, Yasir na binsa da kallo kansa a daure yana mamaki wane
kalar laifi Amma ta yi masa da har ya yanke wannan tsatsauran hukunci haka.

*** *** ***

Ruma ta turo kofar dakin ta tsaya daga jikin kofar ta kalli Khairi dake zaune gaban
madubi tana shafawa bakinta magani ta ce

“Khairi wai Ina Hajiya tace miki zata tafi?”

“Ba ni ta fadawa ba, Maama ta ce gidan Hajiya Fatee zata tafi”

“Toh amman har yanzu zata dawo ba? Na kira wayarta be shiga”

“Maybe can zata wuni, ai dole dai idan dare yayi kin san zata dawo”

“Khairi karfe 6:30pm ake magana fa, kuma ta fita tun safe”

“Aa Ruma kin cika matsala, Hajiya ai ba yarinyar ba ce idan lokacin dawowa yayi ai
ita zata dawo, kika san abun da ya saka ta dade? Kin san dai Hajiya Fatee aminiyar
Hajiyarmu ce, waya san me taje yi a gidan”

Khairi ta amsa mata da kamar fada domin ta hana ta shafa maganin da take cikin
salama sai damunta take da tambayoyi. Ruma ta tabe baki ta fito taja mata kofar
tana sake gwada line Hajiya domin ita idan Hajiya bata a gidan duk jinsa take ya
zama dabam wannan ya saka wani lokacin ma har bin Hajiya take idan zata fita, kusan
duk kawayen Hajiya sun san yar autar Hajiya Ruma saboda yawan lake mata da take.
Har ta isa dakinta gwada line take amman kiran yaki shiga baturiyar sai tabbatar
mata take da ba a samun Hajiya.

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

8️⃣

Suna shigowa cikin gidan Gwaggo Hurriya ta shiga dakin da sauri tana neman Amma.
Gwaggo ta yi dariya tana daurawa jikarta dankwali

“Maraba da Hurriya yanzu ake tafe”

“Eh Gwaggo ina wuni”

“Lafiya kalau ina Hamad?”

“Shiga nan shigowa, Gwaggo Ina Amma?”

“Tana dayan dakin dake kusa da na su Rukayya”

Da sauri Hurriya ta tashi ta fice daga dakin Kakarta zuwa dakin da Amma take, tana
shiga dakin ta fada jikin Amma kamar bata san tana dauke da cikin kanensu ba, sai
kuka ya biyo baya ta kankame Amma sosai kamar za a kwace nata ita. Cikin karfe hali
da dauriya irin na uwar da bata son raunin yayanta ya kamata har ta yi kuka a
gabansu ta shafa bayan Hurriya tana dariyar da sautinta yaki fitowa, hakan kuma ba
karamin taimakawa idonta yayi ba gurin zubar da ruwan hawayen da a da su kwana a
idonta. Kanwarta Rukayya ta bata fuska sosai kamar ta fasa kuka.

“Amma da baki nan gidan babu dadi, kuma Appa ya kwashe kayanki daga gidan”

“Na sani, ya aiko min da su nan ai, suna nan a zuba a gareji, wasu an saka a falon
waje”

Hurriya ta dago tana kuka ta kalli Amma.

“Ba zaki dawo ba kenan? Khairi ta fada min Appa ya rabu dake?”

“Na fada miki tun ranar ai, abincina ya kare a gidanku, ina Hamad”

Amma na rufe baki Hamad ya karaso gurin kofar sai ya tsaya yana kallonsu kamar wani
bako.

“Hamad shigo mana ya ka tsaya a jikin kofa”

Rukayya ta fada, sai ya nufo cikin dakin yana jin wani irin tausayin mahaifiyarsa
da ya kasa nunawa a fuskarsa, sai dai sanin halinsa da Amma ta yi ya saka ta
fahimci akwai damuwa a tare da danta domin fuskarta babu walwala kuma ba hade rai
yayi ba alamar fushi, yana a wani yanayi ne da ita kadai take gane damuwarsa.

“Hamad kuna nan kuna ta fadan ko?”

“Ba mu yi fada ba, ba mu yi fada ba Amma, amman dai gidan babu dadi...”

Dorawa ta yi da labarin abubuwan da suka faru bayan bata nan ciki har da komawarsu
bangaren Momy da suka yi.

“Daman gidan ko da ina ciki ya kuke zaune balle bana nan, sai dai ku yi ta hakuri
karku saka komai ranku”

“Ni dai na ce Bappanku ya tafi gurinsa yayi magana da shi, yaran nan ya bar su
zauna a gidan nan idan ba haka ba, wannan matan uban na su za su iya saka musu guba
su mutu ma”

Cewar Gwaggo a lokacin da take kokarin shigowa dakin. Sai Amma ta amsa mata tana
hawaye.

“Allah ya fi su Gwaggo, na san Allah baya bachi kuma baya son zalinci, zai kare su,
amman abu ne mai wahala Alhaji ya yarda yaran nan su zauna a gidan nan”

“Amma me yasa Appa ya sake ki?”

Hamad ya tambaya kai tsaye yana tsare ta da ido.

“Ban sani ba Hamad, Wallahi ban sani ba, da ace na san laifin da na yi masa wata
kila da zan fi jin sanyi fiye da yadda nake ji a yanzu, shi kan shi ya ce ban masa
laifin komai ba”

“Saboda Hajiya ne? Ko Kuma Momy”

Amma ta kama hannunsa ta rike


“Ba saboda kowa ba ne, kar kaje ka yi ta fada da mutane wahala zaka sha a gidan
nan, dan Allah ka zauna lafiya da kowa Hamad wannan fushin da saurin kai hannu ka
daina, ku kenan Allah ya ba ni sai wannan idan na haifa, ban sani ba ko zan kara
wani ko kuma iyaka kenan, dan Allah ku hada kanku ku zauna lafiya, ina gidan nan
amman tunanina yana can tare da ku saboda na san yadda kuke yawan samu tsabani da
juna, ba ku mai raba ku a yanzu idan kuka yi fada ma dadi za su ji”

“Be ci abinci Amma tun da kika bar gidan nan, da safe ma tea kawai ya sha”

Amma ta dauke idonta daga barin kallon Hurriya dake fada mata ta kalli Hamad.

“Saboda me? So kake ka jawa kanka wani ciwo kuma?”

Kamar an zunguro idonsa haka ya fara hawaye yana kallon mahaifiyarsa, duk yadda ta
so ta daure sai ta kasa ita sai da kukan ya ci karfinta balle Hurriya da ke da
raunin zuciya. Rukaiyah ta share hawayenta.

“Kai Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, Wallahi idan raba ku aka yi an ci amanarki


an ci amanar yaran nan, mu ma kuma anci amanarmu an daga mana hankali”

Gwaggo ta girgiza kai cike da tausayawa.

“Toh Allah ya kyauta, arzikinsu ma suna da wayo da ace kanane ai da sai sun fi shan
wahala, kuma ubansu yana sonsu za su samu sauki ta wani bangaren”

A gidan suka wuni har dare, abincin da Hamad ya kasa ci a gidan Ubansa sai gashi ya
ci a gidan kakarsa kasancewar Amma ce ta dafa masa da kanta, kuma ta saka shi gaba
ya zauna ta cinye abincin tass ya dora da lemu, tukuna hira ta biyo baya, sai da
dare yayi misalin tara da rabi sannan Yasir ya zo daukarsu daman ya fada musu a
lokacin da direba zai kawo su cewar shi zai dauko su. Nasiha sosai Amma ta yi musu
sannan ta aika Hamad ya shigo da Yasir ya zauna saman kujerar karamin falon suka
gaisa.

“Yasir ga kanenka nan, na san kana kokari amman Dan Allah a kara, a rika ja musu
kunne idan suka yi ba daidai ba, kuma a rika duba su dan Allah”

“Amma dan Allah ki daina wannan maganar, ko minene Allah ya kawar da shi ya kawo
maslaha ki dawo gidan kamar yadda aka saba”

“Toh Ameen, duk da haka dai a kula da su musamman Hamad”

“In Shaa Allah”

“Allah ya taimaka ko a kawo maka abinci”

“Aa idan na koma gida zan ci, yau Rukayya bata gidan”

“Tana ciki karatu take yi kasan idan suka samu littafan nan na hausa basa son
tashi, yanzu haka bata ma san ka shigo, bari a kirata ku gaisa”

“No kyaleta Amma, a gaisheta dai, bamu mu tafi kar dare ya kara yi”

Yana rufe baki wayarsa ta bude nata ta fara kuka, hannu ya saka aljihu ya ciro
wayar ya duba ganin mai kira ya saka ya amsa da sauri.

“Hello Appa”

“Yasir Hurriya bata dawo ba?”


“Gasu na zo dauko su”

“Sai yanzu? Kasan bana son ana kaiwa dare a waje ko? Me yasa direba be je dauko su
tun wuri ba?”

“Affuwan Appa, laifina ne ni nace zan dauko su kuma yanzu haka ina gidan”

“To ku dawo yanzu nan, karka sake yaran nan su ce zasu kwana a nan”

“In Shaa Allah, yanzu zamu taso”

“Sai kun iso.....ka gaishe da Mamansu”

Ya fada daga karshe bayan yaja dogon numfashi, da mamaki Yasir ya amsa masa da toh
sannan ya sauke wayar.

“Appa ne, ya ce na gaishe ki”

Wani irin faduwa gaban Amma yayi, mutumen da ya sake ta ya kwaso kayanta ya yace a
kawo mata kuma shi zai ce a gaisheta.

“Ina amsawa”

Mikewa yayi tsaye yayi mata sallama Hamad da Hurriya suka bi bayansa, Amma kasa
raka su ta yi har suka fice daga gidan. Daga gidan Gwaggo Yasir be tsaya ko'ina ba
sai gidansu ya faka a bangaren Hajiya Kaltume, Hamad ya riga fitowa motar sannan
Hurriya, Yasir kuma ya tsaya gyara parking din.

“Me yasa baki fadawa Amma na fasa miki gilashi ba?”

A jere suke suna tafiya Hamad ya tambayeta domin abun da ya tsaya masa a rai kenan
tun a lokacin da ta boyewa Amma cewar sun yi fada.

“Idan ta ji zata ji ba dadi ba, baka ji tana cewa mu zauna lafiya ba? Idan kana yin
fada ran Amma zai bace”

“Ni dai bana son Hajiya bana son Momy bana son kowa a gidan nan”

Yana fada yana wani cin magani kamar wani babban saurayi, Hurriya ta tsaya kallonsa
da mamakin furunci, shi kam tuni ya juya ya fasa shiga bangaren Hajiya Kaltume ma
ya nufi na su bangaren duk kuwa da ya san Amma bata gidan. Hurriya ta cigaba da
tafiya har ta isa bakin kofar falom ta muda kofar ta shiga da sallama farin
gilashin dake kara mata kyau yana fuskarta.

“Wa'alaikassalam”

Fadeel ya amsa mata yana zaune daga gefen kujera yana gwada kiran Hajiya Fatee.

“Ni yanzu hankalina ya tashi sosai, ace har karfe goma Hajiya bata dawo ba? Ga
wayarta baya shiga, daman tun da Ruma ta dawo makaranta take ta damu na da ina
Hajiya”

Cewar Maama tana gwada kiran Hajiya Kaltume.

“Amman fa ce mana ta yi gurin Hajiya Fatee zata je”

Fadeel ya ce

“Bata gidan, domin daga can na fito masu aikin suka ce min tare suka fita da
Hajiya, shiyasa na zo nan ko tana nan domin wayarta har yanzu bata shiga”

Yasir ne ya shigo falon yana motsa keys din dake hannunsa.

“Hurriya ke da Hamad Appa yace na kira ku, Ina Hajiya?”

Ya karashe zancen yana kallon Maama da hankalinta ya tashi sosai kamin ya karasa ya
mikawa Fadeel hannu su gaisa.

“Ita muke ta nema?”

“Ban gane ita kuke nema ba?”

Tambayar Fadeel dake fadar haka yake da mamaki.

“Dazu na shiga na gaishe da Hajiya aka ce sun fita tare da Hajiyarka, yanzu kuma na
dawo masu aikin suka ce min bata nan, na gwada kiran wayarta kuma ba a samu shiyasa
na zo nan ko zan sameta sai kuma na tarar nan din ma kanenka neman Hajiyarka suke”

“Wai tun fitar da ta yi da safe bata dawo ba? I thought ta dawo ba fa, yanzu ma
Appa ne ya ce a kirata”

Maama da tuni ido ya raina fata ta fara kuka ta ce.

“Wallahi bata dawo ba har yanzu, ni hankalina ya tashi”

“Subhanallahi, to ina ta ce zata je?”

Maama da Salma suka amsa masa, duk abun da ake Hurriya da ido kawai take binsu,
Fadeel kuma yana jefa mata kallo time to time, farar fatarsa sai daukar masa
hankali take kasancewarsa baki, ba shi kadai ba har Yasir da duka yan matan Hajiya
Kaltume babu fari ko daya, sai wanda ya dara wani baki, domin an yi gadon bakar
fata ta uwa ta uba, kamar yadda shi ma yake baki sai dai nasa bakin mai kyau ne
irin mai shaike da ya dace da fatarsa ya karawa hancinsa fa fararen hakoransa da
idanuwa kyau. Hurriya ta mike tsaye ta nufi kofa domin amsa kiran mahaifinta Fadeel
ya bita da ido yana kallonta kasa kasa har ta fice, ba wannan ne karon farko da ya
fara ganinta ba, amman a yau ta tafi da shi, domin ta kure iyakar ganinsa ta cika
idonsa.

*** *** ***

Wasa-wasa aka nemi Hajiya Kaltume aka rasa babu amo babu labari, duk inda ake saka
ran za'a gane an bincika bata nan, haka ma Aminiyarta Hajiya Fatee ita ta bangaren
danta Fadeel babu inda be bincika ba amman be same ta ba, gashi be san direban da
ya daukesu ba balle ya neme su, wayoyinsu kuma idan an kira ba mai shiga, shi kansa
Appa sai hankalinsa ya tashi balle kuma yayanta da bachi ma ya gagaresu, Hurriya ma
da ba yarta ba sai da nata hankalin ya tashi domin bata son ta ji wani abu marar
kyau ya same mutum.

Tun ana maganar kwana daya, biyu har aka yi sati, sai da Hajiya Kaltume da Kawarta
Hajiya Fatee suka yi kwana goma cif sannan aka kira wayar Appa ana neman ya fada
miliyan dari, domin sun tambayi Hajiya kuma ta fada musu waye mijinta, ta bangaren
Hajiya Fatee ma haka suka nema gurin ďanta. A lokacin Appa ya zo musu da labarin
yana mamaki su ma mamakin suka yi, ba su mamakin jin cewar tana hannun kidnappers
ba daman sun saka tsammanin haka domin sun bincika ko'ina ba a same ta ba, kuma su
kai report gurin police an saka addu'a amman duk shiru, kudin da suka bukata ne
abun mamaki.
“Miliyan dari kuma? To a ina suka samu number ka Appa?”

Yasir ya tambaya cike da mamaki da kuma tashin hankali a lokaci daya.

“A gurinta suka samu, na yi magana da ita na ji murayarta?”

“How taya suka kama su? Wannan abun sai idan da na gida aka hada kai”

“Ban sani ba, amman dai mai maganar yace sun kama su a wani kauye dake kusa da
gidan zalla nan kwatarkwashi”

“Ikon Allah, amman dai tana lafiya ko Appa”

Ruma ta tambaya tana kuka.

“Ba mu sani ba dai, ba mu gama magana ba suka yanke wayar kuma na kira bata shiga”

“Kamata yayi a sanar da police tun wuri”

“Zan kira yanzu na sanar musu”

Appa ya juya ya fice, cikin wani karin tashin hankali sa be gama warkewar daga na
Amma ba an kara masa wani.

HURRIYA POV.

Hurriya na zaune falon Momy plate din shimkafa a gabanta tana cin abincinta na
dare, Namra zaune saman kujera tana duba dogayen rigunan dake zube gefenta kan
kujera. Momy ta shigo daga bangaren Appa. Namra ta mike tsaye da sauri tana nuna
mata rigar da ta zaba.

“Momy wannan nake so, Hurriya ta dauki bakar”

Momy ta tsaya kallonta.

“Idan ta dauka ke zaki biya? Ka ji min wani rainin hankali”

“Momy toh ai na ga na shagonki ne”

“Idan na shago ne mutuwa na yi balle ki ci gado har ki dauka riga mai tsada ki ce
abawa Hurriyya?”

Namra ta juya ta kalli Hurriya sannan ta juyo ta kalli Momy tana mana alama da zata
iya ji.

“Ta ji mana, tsoronta nake? Ke ce baki san ciwon kanki ba har kika hada kanki da
ita, kina kallo a gidan nan duk kudin da mahaifinsu zai bada na siyen abu sai na
ciya na siyo muku wanda ya fi na sauran yan'uwa, amman yanzu har kika maganar ki
saka riga Hurriya ta saka irinta”

Da kamar mamaki Namra ta ce.

“Ubanmu daya da ita fa, kudin da Appa zai bata su zai ba ni duk daya ne”

“Eh amman ai ina kara miki? Tufafin da kuke sakawa wake sska su a gidan nan? Karki
sake min wani abu makamancin wannan, rai na a bace yake kin kara min wani”
“Me ya faru Momy”

“Kaltume ce wai kidnappers sun kamata suna neman milyan dari”

Momy ta fada tana kiran sunanta domin ita kadaice a gidan bata sakawa Hajiya
Kaltume ta ce Hajiya sai dai ta ce Kaltume kawai. Hurriya ta juyo da sauri jin abun
da Momy take fada, Namra kuma ta zaro ido.

“Innalillahi daman sai da na fada tana ina yanzu?”

“Ke kin yarda? Ai talaka babu abub da ba zai iya ba, wannan Kaltume zata iya
kidnapping din kanta da ta karbi wannan kudin gurin Alhaji, balle tana ganin yadda
nake tafiyar da kasuwanci ai abun yana tsone mata ido”

“Haba Momy taya? Kuma har wannan kwanakin bata fito ba?”

“Ke makira ce wannna matar fa, ni na san yadda na zauna da ita, kin ji ta a waya
sai kukan munafurci take wai wani idan ta kara sati a gurin mutuwa zata yi, tana
cikin bala'i da masifa a Alhaji ya taimaka ya kawo kudin da wuri hmmm”

Momy har wani kwaikwayon muryarta take tana nufar hanyar Kitchen Namra ta rufa mata
baya dan kara jin labari, ita sam bata yarda an sace Hajiya Kaltume ba ta fi yardar
Hajiya Kaltume ce ta sace kanta. Hurriya mamakin ya hana ta cigaba da cin abinci
mamakin jin cewar an sace Hajiya Kaltume take, da dayan bangaren kuma tana mamakin
yadda Momy take ganin kamar ita da Namra suna da banbanci bayan uba daya ya haife
su, tana mamakin yadda Momy take duban Hajiya Kaltume ma dake da tarin rufe asiri a
gidan tana ganinta talaka. Da sauri Hurriya ta cire hannunta a abinci ta fice daga
falon zuwa bangaren su Khairi.
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Hello Habibaties 😍🥰
Amin kara please ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

9️⃣

Hurriya na shiga falon Hajiya Kaltume ta fara rabon ido ganin yadda kowa yayi
jigun, wasu daga yayanta kuma suna amsa waya suna kuka. Gurin da ta tafi wayo ta
nufa wato gurin yayanta ta tsaya kusa da shi tana kallonsa har ya gama wayar sannan
ta ce.

“Yaya wai garkuwa aka yi da Hajiya?”

Kamin ya bata amsa Khairi ta watsa mata harara.

“Tsohuwar munafuka, hala dadi kika ji?”

“Dadi dai? Me ye abun jindadi a ciki da har zata ji dadin? Wace irin magana ce
wannan?”

“Toh Yaya idan ba haka ba, me yasa take tambaya?”


“Bata da hakkin sani ne? Ni kuna bani mamaki a gidan nan Wallahi, miye laifi a ciki
idan ta tambaya? Karki bata min rai yanzu na fara dukanki”

Yasir ya karashe maganar yana nunata da yatsa, sai ta dauke kai domin ta sani sarai
zai iya, ba wani jutuwa suke da juna ba. Ya dubi Hurriya dake gefensa tsaye.

“Eh sace ta aka yi, mu ma yanzu Appa ya zo mana da maganar sun ce za a ba su


miliyan dari”

A take hankalinta ya tashi, tana son ta sake cewa wani abu tana tsoron kar Khairi
ko Salma su kwatseta, dan haka ta ja bakinta ta yi shiru tana cigaba da sauran
yadda ake ta kiran yan'uwa ana fada musu.

**** **** ****

A haka sai da Hajiya ta kara sati daya a hannun mutanen nan ita da Hajiya Fatee
domin police aka saka a lamarin su kuma suka hana a aika da kudin, suka ce za a
gano inda take, sai da Appa ya ga abun na su ba mai yi ba, ga hankalin yaransa da
yan'uwan Hajiya Kaltume ya tashi ya nemi sassauci suka rage kadan ga miliyan dari,
a sake neman sauki, daker da addu'a da sudin goshi aka samu suka sauko a miliyan
goma, bangare Hajiya Fatee ma haka suka karba, Appa ya hada kudinaka rasa wanda zai
kai, sai da wani kanen Hajiya Kaltume yayi jihadi yace shi zai tafi kai musu kudin,
ranar da zai tafi suka fadi inda zai tsaya a dajin su zo su tafi da shi, haka kuwa
aka yi Fadeel ya kawo nasa kudin aka hada da na Appa suka shiga mota aka kaishi har
inda suka bukata suka fito suna masa addu'a, su kawo wajen gari suka tsaya. Ba zan
wani jima ba suka kira suka ce aje a dauke ta a wata gona dake nan dogon dutse a
nan za su aje su. Abun ka da mai nema Yasir da Fadeel da Uncle din Fadeel din suka
nufi gurin da moto suna gudu kamar ba za su je su same su a gurin ba. Kamin su isa
kowannensu hankalinsa ya tashi kuma zuciyarsa ta cika da zullumi, domin suna tsoron
kar su je su tararda gawarta domin sun saba haka wani lokacin sai su ce aje a dauka
sai an tafi a tararda mutum a mace.
A bakin titi suka faka motar suka fita suka shiga cikin gonar domin dubawa, Yasir
da waya a kunne yana fadawa Appa sun isa gurin Appa kuwa sai gargadi yake masa.

“Yasir ku kula da kyau, zai iya yiyuwa dabara suka muku saboda idan kun shiga gurin
su sace ku”

“Aka yi mana Addu'a Appa In Shaa Allah babu abun da zai faru, fatanmu dai a samu
Hajiya da rai”

Yana rufe baki ya ji muryar Fadeel yana fadin ya karaso nan gasu a nan, da sauri
Yasir ya katse wayar ya nufi gurin, Hajiya Fatee ce da Hajiya Kaltume daure jikin
itace, kansu babu ko dankwali sai wani zane atamfa kala daya da suka yafa kamar
wasu yan kauye sun yi yaushi kai kace allayahun da yayi sati ne a daure, fuska ta
yi burun-burun kana ganin kasan an dade ba a sadu da ruwa ba, baki ya bushe idanuwa
sun kode kamar wadanda suka kusa kusantar rame. Hajiya na ganin Yasir ta fashe da
kuka, Hajiya Fatee kuma ta fara zubar da hawaye.

“Alhamdulillah Alhamdulillah”

Shi ne abun da sukr ta fada bayan sun kwance su.

“Ku yi sauri muje kar su biyo sawunmu, Sannu Hajiya”

Fadeel ya fada yana kallon mahaifiyarsa cike da tausayawa.

“Bana iya tafiya Fadeel bana iya komai”

Tana maganar tana nishi hawaye na mata zuba, Hajiya Kaltume kam kuka take riri
domin da yanzu da aka sako su da kuma lokacin da aka kama su duk yayi mata kamar
mafarki, ita kadai ta an bakar azabar da suka sha. Duk yadda Yasir ya so su yi
sauri hakan be samu ba saboda Hajiyoyin duk basa iya sauri tafiyar ma sai daker
gashi jikin ba kadan ba balle yayansu su ce za su taimaka musu, a haka dai suka isa
gurin motar, Hajiya Fatee ita ce mai tafiya kamar mai tatata, Hajiya Kaltume ce mai
dan kuzari shi ma ba wani da yawa ba sai na karfin hali. Hankalin kowa be kwanta ba
sai da suka isa gida, domin kin amincewa suka yi da maganar Appa da kuma na yaransu
cewar a tafi da su asibiti a duba lafiyarsu, Hajiya fatee ce ta fara nuna karfiya
sannan Hajiya Kaltume ta rufa mata baya. Daga gidansu Yasir Fadeel ya dauki
mahaifiyarsa ya fice da ita zuwa family house dinsu bayan ta yi wanka, sai dai ta
kasa saka komai a baki duk kuwa da irin lallabata da Fadeel yake. Be isa gida ba
Yasir ya kira wayarsa yana fada masa wai sun kira sun ce shi ma wanda aka aika yana
da mai da alama za a samu wani abu dan haka sun rike shi sai an bada miliyan 20.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, mutanen nan ba su da imani ko kadan, kai yaushe


aka gama wannan kuma ace sun kama wani? Wai anya ana son mu cigaba da rayuwa a
kasar nan kuwa? Wannan wane irin bala'i ne?”

Haka yayi ta fada, Hajiya fatee tsabar tsoro ji take kamar ta rufe masa baki, domin
ta ga tashin hankali da bata taba mafarki ba.

“Ka rufawa kanka asiri da zagin mutanen nan, ba au da imani ko kadan, su hanyar da
imani ya bi ma ba su santa ba”

Fadeel ya juyo ya kalleta a daidai lokacin da ya faka motarsa a harabar gidan,


yan'uwa da abokan arziki suka fito da gudu suka yo gurin motar domin taron Hajiya
Fatee ciki har da Afrah da Hajiya Fatee take zagi wato matar Fadeel da kuma yaranta
masu aure.

“Wallahi Hajiya Kaltume ce taja min, ita na raka a kauyen”

“Toh me kuka je yi kauyen?”

Bata samu amsa masa ba sakamakon bude gambun motar da aka yi ana murna da zuwanta,
daman kuma tana neman dalili da zai hanata yi masa wani bayani dan bata shirya
tonawa kawarta asiri ba. Ta bangaren Hajiya Kaltume after ta samu ganawa da mutane
ta huta zuwa dare danta Yasir ya dauketa zuwa asibiti kamar yadda mijinta ya
umarta. Sun dubata suka mata duk wani gwaje gwajen da ya dace sannan suka bata
maganin zafi domin kafarta na ciwo sosai saboda tafiya, sai kuma na ciwon jiki da
ciwon kai da na ido saboda kukan da suka sha har kammaninta sun sauya.

BAYAN KWANA BIYU....

Hajiya Kaltume ce zaune kan kujera Maama na matsa mata kafafuwan da har yanzu ba su
daina mata zafi ba, domin bata taba gwada yin tafiyar da ta yi daga inda yan fashin
dajin suka kamata ba zuwa sansaninsu, ko a lokacin da take da kurciya balle yanzu
da girma ya fara kamata. Momy ce ta yi sallama ta shigo falon tana sanye da wada
tsadadiyar shadda yar mali sai sheki take kamar an watsa mata ruwa, kana kallon
shaddar ka san ranar ta fara sakata, wuyanta na cike da sarkar zinarin da ba ko
wace matar mai kudi ce zata iya sakawa ba, gamshin da take ma na dabam ne domin
Momy bata yarda ta siye turaren irin wanda Hajiya Kaltume ko Iyami za su iya siye
ba ko da kuwa kudin da take da shi zai kare. Idan kana neman dake ji da kansu
asalin ji da kai da nuna isa idan ka yi arba da Momy ka kai karshen aya. Maama ce
ta amsa mata sallamar tana hada baki da Khairi dake fitowa daga kitchen rike da
bowl din kankana. Hajiya Kaltume tun da ta kalli kofar falon ta ga Momy ce bata
sake sha'awar kallon gurin ba. Tsaye Momy ta yi kusa da kujerar da Hajiya Kaltume
take zaune abun ka da matan da tsibbo ya waya kuma suka wayance shi sai Hajiya
Kaltume ta zame kafafuwanta daga hannun Maama ta matsa daga inda Momy take tsaye,
jiki be bata banza ta kawo Momy bangaren ba, tunani take wani abun ta zo yi mata.
“Kaltume ashe an dawo”

Momy ta fada cikin izza tana Kiranta da Kaltume kai tsaye kamar yadda ta saba, tun
zuwanta gidan taba taba kiranta da Hajiya ba balle kuma Yaya kamar yadda wasu matan
suke yi idan za su kira uwargida ko da kuwa da sunan yaranta ne.

“Eh Allah ya nufa Nafisa”

Hajiya Kaltume ta amsa kamar an mata dole tana wani kashe ido. Momy ta tabe baki
kamar wadda ta manta a falon Hajiya Kaltume take idan ma Hajiya bata ganinta kuma
yaranta suna kallonta, amman tsabar raina uwarsu da ta yi da kuma rashin tsoron
anyi an ce ya saka ta yin haka.

“Toh Allah kyauta gaba”

Maama da Khairi ne suka sam da Ameen, sukan tsoronta ya dade da cika musu ciki ba
kamar mahaifiyarsu da take jin zata iya karawa da ita ba. Momy ta juya ta fara
takawa kamar wanda bata son tafiya, haka yanayin ya ke tun tashi, sai dai lamarin
ya samu promotion ne a lokacin da ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, saboda ta nunawa
Hajiya Kaltume da Iyami ita yar sarauta ce kuma yar masu kudi ba Kamarsu.

“Mtsssss”

Hajiya Kaltume taja guntun tsaki tana bin bayanta da harara.

“Wallahi matar nan ta raina min hankali, wato na fahimci so ta yi na mutu gaba daya
idan ba haka ba ace ma samu na kubuto hannun azzaluman mutanen nan da ba su san
Allah ba, amman bata shigo ta min barka da dawowa sai yau da aka kwana biyu?”

Khairi ta mika mata bowl din watermelon din tare da fadar

“Hmmm Hajiya ai da baki dawi ba sai matar nan ta zuba ruwa kasa ta sha”

“Ai ni bayan Iyami bana da makiyiya irin Nafisa, kuma ita ma sai ta bar gidan nan
da yardar Allah, komai sai ya dawo karkashin ikona sai na bata mamaki, ai Wallahi
da ban dawo ba da sai Iyami ta ci ubanta dan sai ta gane kuskurenta, duk saboda ita
na sha wannan bakar wahalar, duk dalilinta ne da bata aurar min miji ba da yanzu
ban san wadannan yanta'adda da ba su da imani ba, yanzu na fito ga kanen can a
daure”

“Hajiya ba su da Imani ko?”

Maama ta tambaya.

“Ina fa, ai babu imani a tare da su, abinci sa mun ji yunwa suke ba mu, idan dare
yayi muna nan cikin hudu sai idan sun haska mu, sun dauremu sai kace awaki, sannan
a ciyayi muke bacci, baba kalar kwaron da be cize ni ba, shi kam sauro ya samu abun
nema style style yake mana na cizo, kuma duk ranar da aka yi waya ba a samu
daidaituwa ba sai sun mana duka, kuma a kafa muka yi tafiyar nan har ciki daji,
yara kanana na haife su amman haka suke juya ni kamar waina, Allah dai ya isar min
akan Iyami kawai zan ce, kuma kiyayya yanzu na fara, dacan ina boyewa Wallahi
yanzu a fili zan nuna bana sonta bana son yaranta, duk sai na ga bayansu”

“Hmmm Hajiya karki ga yadda Hurriya ta shigo falon nan tana ta zumudi ta ji dadi an
kama ki har tambaya take”

Khairi ta shimfida mata fahimtarta akan Hurriya. Hajiya Kaltume ta cize baki.
“Shegya bakar dagga, daman idan bata yi murna ba ai bata cika yar kishiya ba, aiko
sai ta gane shayi ruwa a gidan nan, ke shiga dakin yayanki ki kwaso min gilasan
yarinyar nan gaba daya ki boye min su”

Kamar mai jiran umarni haka Khairi ta tashi da zafinta da murnarta ta nufi hanyar
stairs. Maama ta tashi daga kasan da take zaune ta zauna kan kujera.

“Amman Hajiya Yaya Yasir zai iya gane dauka kika yi fa?”

“Ta ina zai gane fada masa zaki yi? Ko ma ya gane ai ba bayarwa zan yi ba, idan ya
matsa min har shi ba zan ragawa ba, dan ni mai kaunar mai kaunar Iyami da yayanta
ma bana kaunarsa, arzikinta daya ma dawo Wallahi da na mutu can da sai ta gane
kurenta, kuma ita da Alhaji har abada”

Sosai ta hade fuska tana maganar irin hadewar da ya kara mata muni da bakin fata.

“Hajiya ai ba ita kadai ba, Hajiyar su Appa ma fa bata zo ba sai a waya ta kira,
amman Wallahi da Amma ce da tun ranar zata iso gidan”

“Hmmm ita ai bata da wata power yanzu, ko ba komai a bakin rame take, kuma babu
yadda zata yi da ni, bugu da kari kuma na kore matar da take so, sai na ga uban da
zai dawo da ita a gidan nan”

Sun dade suna hirar Hajiya Binta da Maama kamin Khairi ta fito daga dakin Yasir da
gilasan har uku ta nunawa Hajiya.

“Kin gansu Hajiya cikin closet dinsa ya saka su”

“Je ki yi musu mugun boyo idan ma bala'i yayi bala'i ki ce masa ni na dauka da
kaina”

“Ba sai ance haka ba, kawai kowa yace be shiga dakin ba kuma babu wanda ya dauka”

“Shi ke nan, ya ma fi sauki”

Khairi ta fada a ganinta shawarar da yayarta Maama ta bada ta fi, sama da ta Hajiya
Kaltume. Kamin Khairi ta isa stairs aka dauke wuta, a take hankali Hajiya Kaltume
ya tashi domin har yanzu bata gama wartsakewa daga tashin hankali da azabar da ta
sha a dajin ba.

“Innalillahi Maama kunna haske, na shiga uku... ”

Kamin Maama ta kunna fitilar wayarta Mekano dake aikin bada hasken wuta a gidan ya
fara aikinsa, haske ya cika ko'ina. Hajiya Kaltume ta dafa zuciyarta tana sauke
gajiya.

“Kai Allah raba musulmi da wahala, har yanzu ji nake kamar ina kusa da dajin nan,
shiyasa ko waya bana son karba, mun ga tashin hankali mun ga shiga uku duk saboda
bakar Iyami”

Hajiya ta karasa tana fashewa da kuka, domin Iyami ta hana ta zaman lafiya ta hana
ta rawar gaban hantsi.

*** *** ***

Ta dayan bangaren Iyami tana ta fama da nata, tunanin da damuwa sun hana ta walawa
ko da kuwa tsakar gidan ne, ga wani sabon lalurar laulayi da ya same ta bayan
dawowarta gidan iyayenta, iyakar kokarinta tana yi na nunawa Gwaggo da Bappa ta
karbi kaddara, sai dai a kasan zuciyarta tana fama da tunani domin kuwa tana son
mijinta, domin tana zaune lafiya a gidan tana rumgume da yayanta ciwonsu lafiyarsu
duk ta sani, ba kamar yanzu da tunanin halin da suke ciki yake hana ta sukuni ba.
Gashi a duk lokacin da Hamad ya zo gidan sai ya fada mata abun da aka yi musu,
Hurriya ce bata fada saboda bata son tashin hankali Amma kuma tana da zurfin ciki.
Gwaggo ma tana iyakar kokarinta na kwantar mata da hankali ganin cikin dake jikinta
gudun kar ta jawa kanta wata matsala. Addu'a kuma su dukansu suka dukufa da yinta
ta neman Allah ya daidaita tsakaninta da Appa, sai dai ta bar kyau tun ranar
haihuwa domin bata damu da yin azkar din neman tsari ba, tana ta tawaya a wannan
babin, duk kuwa da ta san tana cikin kishiyoyi irinsu Hajiya Kaltume da Momy.

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Hello Habibaties 😍🥰
Amin kara please ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

1️⃣0️⃣
0️⃣
1️⃣1️⃣
0️⃣

Washe garin ranar...

Hurriya na cire uniform dinta na makarantar boko ta dauki bakar abaya ta saka, ta
bude gurin da take zuba hullunata tun bayan da ta kwaso kayanta daga bangaren Amma
ta dawo da su bangaren Momy a dakin da aka bata, ta dauko farar hulla ta saka a
kanta. Sannan ta fara gyara dakinta ta kintsa komai, cikin natsuwa ta fito daga
dakin ta shiga dakin Hamad da ya watsar nasa uniform din akan gado ta dauka ta aje
masa ta gyara masa dakin, daman shi be kula da gyara daki ba ko a lokacin da Amma
na gidan balle kuma yanzu da tufafinsa ma sai da Hurriya ta kwaso ta dawo masa da
su dakinsa dake bangaren Momy. After ta gyara nasa dakin ta sauka kasa domin dauko
abun shara da mopper haka take kullum idan ta dawo take gyara nata dakin da na
Hamad domin Momy ta hana masu aikinta share dakin Hamad da Hurriya haka ma ta hana
ko cokali suka aje masu aiki su dauka, kamar ya yaran gidan ba haka Momy take
treating dinsu, musamman ma Hurriya da bata iya budewa kowa cikinta, Hamad kuma
idan ya ci abinci a nan yake bari sai dai Hurriya ta dauke masa, ba kowane rules
and regulations na Momy ya sani ba, ko na ya sani ba amfanin da za su masa domin ba
bi zai yi ba.

Gurin da ake aje kayan taje ta dauko ta hauro sama a hankali, domin Momy ta jaddada
mata bata son jin karar tafiyar kowa a saman, hakan ya saka take kokarin ganin ta
kiyaye dokokinta, ta san ba dan komai take nata haka ba sai dan ta takura mata idan
kuma ta fadawa Appa wata kila zata iya jawa kanta matsala a gurin Momy. Dakin
dan'uwanta ta fara gyarawa sannan ta shiga nata dakin ta fara sharewa. Cikin ɗoki
Hamad ya shigo dakin nata.

“Hurriya za mu je dauko Hajiya yanzu”

Ta juyo ta kalleshi da sauri.

“Wace Hajiya”

“Hajiyar Appa tace zata zo, Appa ya kira ni yace na zo muje daukota yanzu nan”

Hurriya ta daka tsalle tana murna, daga ita har Hamad suna matukar son zuwa gurin
Hajiya Binta kuma suna daukin ganinta a gidan ubansu, al'adace ta Alhaji Haruna,
duk ranar da mahaifiyarsa zata zo gidansa da kansa yake zuwa ya daukota idan kuma
ta tashi tafiya shi zai maidata gidanta, komai yake zai aje ya dauko ko ya kaita
gida matukar gidansa zata zo, wannan ya saka tun ana sauran kwana biyu ta zo gidan
take sanar masa, shi kuma ya sanar ma matansa a shirya mata tarba mai kyau.
Murmushin da murnar da Hurriya ta gani a fuskar dan'uwanta Hamad ya ninka farinciki
zuwan Hajiya Binta da take a gidan, domin tun tafiyar Amma bata san wata rana da
Hamad ya sake fuska yana far'a kamar yau ba.

“Zan mata wanka mai kyau kin san ta iya tsokana ta tana cewa ban iya wanka mai kyau
ba, tufafi zan canja yanzu nan”

Da karfi yake maganar, kamar yadda ya saba yi a bangaren Amma idan yana cikin
farinciki. Hurriya ta yi saurin yi masa alama.

“Yi a hankali kar Momy ta ji ta fara maka masifa?”

“Saboda me?”

“Bata son hayaniya kuma tace idan zamu hauro ko sauka stairs mu yi a hankali kar mu
yi making sound bata son ana hawa mata da karfi”

“Yaushe tace haka?”

“An dade, kai ai ba zama kake bangaren ba sai idan zaka kwanta shiyasa baka sani
ba”

“Sai na fadawa Hajiya duk abun da ake mana a gidan nan”

Hurriya ta saki mopper dake hannunta ta nufo kofar dakin gun da Hamad yake tsaye.

“Hamad kar ka yi haka, kasan zata yi ma Appa fada shi kuma zai yi ma Momy, idan aka
yi Momy kuma kan mu zai dawo”

“Sai na sake fada mata, Appa ma dan ina fushi ne da shi shiyasa ba zan fada masa
ba, ni ba zan ma iya zama bangaren nan ba i hate them”

Ya saki kofar ya nufi tasa kofar ya bude, Hurriya ta dora hannu daya akai tana jin
ina ma ace bata fada ba, tsoro take kar ace daga dawowarta bangaren ta fara hada
munafurci, kuma ta san at the end abun gurinta zai dawo. Hamad na canja tufafi ya
dauki turare ya saka ya canja shoes ya fito daga dakin ya sauko kasa ya fice daga
falon daga Miwan har Namra dake falon be cewa kowa komai ba. Miwan ya bishi da
harara

“Yaro nan fa ya raina mutane, idan zai shigo haka zai shigo babu sallama idan ya
tashi be iya gaishe da kowa”

“Yaya idan ka ce zaka biye ta Hamad za ku yi ta samun matsala ne fa, Amma ma da


tana nan fama take da shi balle kuma mu”

“Ba ruwana da rashin jinsa ko rashin kunya ni ubansa zanci Wallahi”

Ya amsawa Namra yana ayyana yadda zai yi ma Hamad mugun duka idan ya shiga gonarsa.
Namra dai bata sake cewa komai ba ta shiga ta jera warmers din da masu aikin Momy
ke ajewa a kasan dinning, Hurriya ce ta fito rike da boket din da ta yi mopping da
mopper ta nufi hanyar tsakar gidan dake ta cikin falon Momy ta bude kofar baya ta
fita ta wanke komai sannan ta dawo cikin falon, a daidai lokacin da aka turo kofar
falon aka shigo wata doguwar mace ce tana sanye da bakar abaya da aka kawata da
blue stone ta daura dankwalin atamfa saman kanta sannan ta dora mayafin abayar a
sama ya sauko mata, hannunta na rike da Gucci bag, tsalle Namra ta saka ta kwala
ihu ta nufi matar da alama ta nuna murmushi sai ma sai yayi yaki yake samun mazauni
a fuskarta, kallo daya zaka masa ka fahimci ta ninka Momy kasaita da ji da kai.

“Ammy sannu da zuwa”

Cewar Namra cikin zumudi tana rumgumeta, Miwan ya mike tsaye yana gyara rigarsa
tare da yi mata barka da zuwa.

“Namra...ana gida”

Ta fada kamar mai jin wahalar magana.

“Eh Ammy sannu da zuwa, tun safe muke duban hanyarki”

“Toh gani na iso, Ina Hajiya Nafisa?”

Ta tambaya tana kallon Hurriya da ta yi tsaye da ta fito daga dakin da da ake aje
mopper.

“Momy Momy Momy...”

Namra ta daga murya tana kiran Momy, Hurriya kuma ta dan risina kamar yadda ta saba
ta gaisheta.

“Ina wuni”

“Lafiya...”

Ta amsa tana binta da kallo tare da dan yamutsa fuska.

“Ita ce .....”

“Hurriya”

Namra ta karasa mata, sai ta watsawa Hurriya wani kallo daga sama har kasa ta
yamutsa fuska kamar wadda ta yi arba da wani abun kyama. Hurriya ta kalli jikinta
sannan ta kalli matar da tuni ta kama hanyar stairs gurin Momy dake saukowa da
saurinta tana mata lale marhabun. Da alama Namra bata ji dadin abun da matar da
take bakuwa a idon Hurriya ta yi ba, sai ta kama hannun Hurriya ta nufi kitchen da
ita suna shiga ta rufe kofar kitchen din ta kalli Hurriya da har lokacin mamakin
yadda matar ta yi mata kallon wulakanci take, bayan kuma bata da wani abun
wulakantawa a jikinta ko suturarta, gashi alama ya nuna ta santa ita kuma bata
wayanci wacece matar da Izza ta cikawa ciki har ta bayyana a kamaninta ba.

“Hurriya dan Allah kar abun da ake miki a gidan nan ya dame ki, kin san dai
matsayinki a gidan nan, dan haka karki kula komai kin ji?”

Hurriya ta amsawa yar'uwar tata da kai.

“Wacece wannan Matar Yaya Namra?”

“Big Brother din su Momy to natarsa ce wannan, ba a nan suke ba, a Kaduna suke
zaune ta zo duba mahaifiyar mijinta ne da bata jindadi maybe shiyasa ta biyo ta nan
saboda suna good time da Momy sosai”

Nan ma da kai ta amsa mata sannan ta juya zata fice daga kitchen din.

“Kin ci abinci?”
“Aa Hamad ya ce Hajiyar Appa zata zo, ina jiram ta zo ne sai mu ci abinci tare”

“Yayi yar gidan Hajiyar Appa”

Hurriya ta yi murmushi ta bude kitchen din ta fito tana rike da hannayenta ta nufi
upstairs, Miwan ya wurga mata harara yana jin haushin yadda Namra take mata sanyi
ko a lokacin da Amma take nan balle kuma yanzu, hakan ya saka suke mata kallon
munafukar cikinsu, domin ita halinta dabam da na su, kishi da ya kamata ace tana
taya Momy bata yi ta bar musu sai dai su yi. Hurriya na shiga dakinta ta maida
kofar dakin ta rufe ta nufi gadonta ta kwanta ta takure gurin daya kamar wanda aka
tsare sai hawaye ya fara saukowa a idonta, tunanin barin gidan da Amma ta yi ya
dawo mata sabo.

**** **** ****

Cikin annashuwa da ďaukin gani Momy take kallonta.

“Ai har ina cewa maybe ba zaki biyo ba, na ga Yamma ta yi”

Matar dake kawar da kai daga barin kallon aikin Momy dake jera mata kayan da aka
shirya mata ta kalli Momy.

“Ai kin san halin Captain shi ya fi son tafiyar dare”

“Tare da shi kuka zo kenan? Amman be shigo ba?”

“Yana waje, waya yake”

“Oh Soyyayar da bata karewa, ai dai an kusa auren nan a huta, ke ma ki samu hutawa
Ammy”

“Toh sai a taya mu da Addu'a Allah ya daidaita tsakaninsu”

Tana maganar tare da kai hannu ta dauko plate din grapes din da aka rolling ta cire
ledar ta fara ci.

“Tsabani suka samu ne?”

Cikin mamaki Momy ta bukaci sani. Kamin ta bata amsa sai da ta juya ta kalli kofar
dakin Momy da daya daga cikin masu aikinta taja.

“Wai har cikin daki kike barin masu aikinki suna shigowa?”

“Toh ya zan yi Hajiya Turai? Kin san dai ba zan yi aiki da kaina ba, dole su zan
saka”

“Ai ni iyakacina da mai aiki falo sai kitchen da haraba, har yaushe mai aiki ta yi
matsayin shigo min bedroom? Kina gani ai idan kika je gidana, su Larai ke kula min
da daki”

“Toh ni wa zan saka? Ke ai kina rikon su Larai da Aliya”

“Wannan yar mijin na ki da kika fada min ta dawo nan hutu ta zo yi? Idan ma baki
sonta sai ki duba a cikin dangi ki dauko wadda zata iya kula miki da daki, amman ba
dai masu aiki ba”

“Zan duba a dangi, yar miji ina sakata za ace bana kaunarta”
Hajiya Turai ta yi murmushi mai sauti tana mamakin sakarcin Momy domin a gurinta
abun da Momy take fada ko take gi sakarci ne.

“Ke ma dai ban da abun ki Hajiya Nafisa waya taba son ɗa ko ƴar kishiya? Ai ba wani
boye boye, ba zan hana ka aure ba amman fa ba zan so matarka da ƴaƴanta ba”

“Ai Wallahi Hajiya Turai ba karamin sa'a kike yi ba, da yayana baya sha'awar aure-
aure, ba kamar nawa mijin ba, domin ni ko a yanzu da ya saki Iyami tunani nake ko
dai ta dawo ko kuma ya auro wata”

“Shi ne banbancin tashi a gidan arziki da kuma cintar arzikin, da ace mijinki ma
kamar tashin Engr ne, da ba zai yi wannan aure-aurenba, ai talauci mugun abu ne, da
zarar sun ga sun yi kudi sai su ga babu abun da ya dace da su kamar aure, amman
Engr kam ai rayuwarta turawace da shi, babu ruwansa da wannan hange-hange”

“Wallahi ya huta, da alama ma ďana halinsa zai gado”

Hajiya Turai ta tabe tana girgiza kai cike da kasaita.

“Hmmm Captain? Ai idan ba Allah ya sauya masa hali ba, da wahala ma ya iya zaman da
mata, yanzu ma addu'a muke kar ya ce ya fasa auren, shiyasa na ce ban yarda ya
zauna ko'ina ba sai a kusa da ni”

Momy ta kasa dariya.

“Haba dai Hajiya Turai”

“Hajiya Nafisa kin manta halin ďan naki? Wannan mugun fushi da bakar zuciyar ta
Captain tsoro take ba ni, komai aka yi masa a duniya ba a masa daidai, ko kallonsa
kika yi zai iya cewa kallon ya wuce kima ya fara masifa ko ma ya ce hararasa kika
yi, yadda kika san shaidan aka nade aka saka masa a zuciya haka, abu kadan sai
masifa sai fushi baya iya controlling kansa, ga zafin hannu a family babu wanda be
san halinsa ba, ita kanta yarinyar da zai aura yanzu, ba dan tana hakuri da shi ba
da yanzu rabu da ita, da inda abun ya zo da sauki ita mai sanyi hali ce kuma tana
gudun zuciyarsa”

“Toh ai sai a kiyaye, haka Allah yake son ganin kayansa, Captain murdaden mutum ne
iya masa sai Allah”

“Ina ta addu'a dai Allah ya sauke masa wannan mugun fushi da bakar zuciyar, idan ba
haka ba zaman auren ba zai jima ba, kuma ya fada min idan yayi wannan auren ba zai
sake yi ba har abada, wai ko matarsa mutuwa ta yi ko suka rabu a haka zai zauna har
karshen rayuwarsa, ni kuwa ba fatan haka nake ba, ni da nake son na yi ta ganin
jikoki a makwafin ƴaƴan da Allah be ba ni ba”

“Gaskiya kam, muma muna son gani ai balle kuma ke da shi kadai kika haifa...”

Hajiya Turai na taba kayan marmarin suna hira da Momy har time ya fara ja, hakan
kuma be saka sun yanke hirar ba har sai da Namra ta shigo turo kofar dakin ta
shigo.

“Momy Hajiya ta iso”

Momy ta yatsina fuska domin ta san wace


Hajiyar ake magana, wato Hajiyar Binta surukarta uwar da ta haifi mijinta.

“Toh shi ne kuma sai an fada min? Kin san ai ba nan take fara zuwa ba sai ta gama
da ko'ina take lekowa nan, to miye damuwata da ita, je ki fadawa masu aiki su kai
mata abinci”

"Okay”

Ta juya ta fita. Momy ta yi tsargi da fuska.

“Idan ban je na gaisheta ba, sai ki ga ya shigo yana ta bala'i, alhalin ba so take
ba, idan ta zo bata sauka bangaren kowa sai na Iyami, kuma sai ta fara shiga
bangaren Kaltume sannan take leko nan”

“ikon Allah haka take ita kuma! Allah kyauta rayuwarku sai ku Hajiya Nafisa”

Cewar Hajiya Turai da kamar gatse tana jin ita duk ba zata iya daukar wannan ba,
domin kowa yana da yancinsa. Namra na fitowa bedroom din Momy ta nufi dakin Hurriya
ta tura kofar dakin, Hurriya na ji an taba kofar ta yi saurin juya fuskarsa ta boye
kukanta.

“Hurriya Hajiyarki ta iso, Appa ya aiko Ya Musib ya fadawa Momy”

Hurriya ta share hawayenta da sauri ta juyo, sai gata ta sauko daga saman gadon
bata ko kula Namra ba ta ratsa gefenta ta fice da gudu, duk wata dokar sauka ko
hawa stairs na Momy manta su Hurriya ta yi a lokacin saboda zumudin zuwan Kakarta
Hajiya Binta a gidan, kamar yau ne zata fara ganinta a gidan haka Hurriya ta ji. Da
sauri ta bude kofar fita falon Momy bata kula komai ba ta saka kai zata fice, da
mugun karfi ta ji kanta ya daki wani abu mai karfi har sai da ta yi baya kamar zata
fadi. Dagowar da zata yi ta duba me ta buga domin be yi mata kama da karfe ko icce
ba, ta ji an wanke mata fuska da lafiyayen marin da ya haddasa mata ganin wadansu
kananan taurari, gilashin da yake mafaka ne a idonta ya fadi kasa, sai hudu da buji
suka mamaye ilahirin idanuwanta. Sai ta tsaya cak irin tsayin da ta saba yi a duk
lokacin da wani bakon al'amari ya ziyarceta.

Gafen fuskarta ya hau zugi yayi ja, idanuwanta suka masa tantance mutunen da ke
tsaye a gabanta, fafadane ta ga hakan a cikin hudun idanuwanta, dogo ne irin tsayin
da ta tsaya iyakar kirjinsa. A hankali ta sulale ta kai kasa ta saka hannayenta
tana lalaben gilashinta hawaye na kwankwaso mata kofa. Lalabe ta yi ta yi amman ta
kasa jin gilashin, kamar yadda ta duka haka ta mike tsaye a hankali ta juya ta
lalabi kofar falon ta fara tafiya.

“Hurriya... Me ya same ki”

Namra ta tambaya tana nufota da sauri ta kama hannayenta ta rike domin hawaye take
kamar an bude kofar fanfo.

“Ya... Ya... Namra... Gilashi... Na...”

Namra bata tsaya komai ba ta rika hannunta ta juya da ita suka fita tana janye da
hannunta, har lokacin Mutumen da ya mareta yana a gurin tsaye ko yatsansa be motsa
ba. Namra ta kalleshi kamin ta sako hannun Hurriya ta fara duba gilashin, can gefe
ta hango shi ta nufi gurin da sauri ta dauko mata.

“Har gefen ido daya ya fashe daga sama, me ya faru Hurriya”

Ta saka mata gilashin da kanta, lokaci daya ganinta ya dawo fashewar da gilashin
yayi ba irin wadda zai hanata gani ba ne, daga sama ne ya fashe shi ma kuma kadan.
Hurriya ta daga ido ta kalli mutumen da be mata uzuri ba ya wanke fuskarta mai
tsada da mari. Hawaye be daina mata zuba ba, hakan kuma be hana idanuwanta ganin
mutumen da kyau, dubansa ta yi ta dube shi, ta sake dubansa sannan ta sauke idonta
kasa ta ratsa gefensa ta fara sauka kasa. Slowly ya juya ya kalleta kamar mai son
gasgata wani abu ko karyatawa.
“Bata gani sai da gilashi, me ya faru Yaya?”

Ya juyo ya kalli Namra a fusace.

“Aza min bindiga sai na fada miki”

Jinin jikinta ta sha ta kauce ta ba shi hanya ya shiga ciki, ita kuma ta ja kofar
sannan ta bi bayan Hurriya domin gaishe da Hajiya Binta, kamar yadda Appa ya
sabarwa kowa a gidan ko baka cikin gidan idan mahaifiyarsa ta zo matukar kana cikin
garin sai ka zo ka gaisheta...

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Hello Habibaties 😍🥰
Amin kara please ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

1️⃣1️⃣
1️⃣
1️⃣1️⃣
1️⃣

Hanya Hurriya ta hadu da Hamad ya zo zai kirata domin ita Hajiya Binta ta fara
tambaya daga isowarta gidan.

“Me ya same ki? Hajiya na kiranki tana bangaren Appa”

Ya tambaya kamar irin hankalinsa be tashi ba dan ya ga hawayenta.

“Momy ce ta yi baki shi ne namijin ya mare ni”

“Me kika masa?”

“Ban masa komai ba, kawai saboda na je fitowa da sauri shi kuma zai shiga na buge
shi, shi kuma ya mare ni gilashina har ya fashe, da jikinki kamar itace mugu kawai”

Ta farasa tana kuka ita ma kanta ciwo yake an karon da suka yi, balle kuma shi da
bata san yadda ya ji ba.

“Ina yake?”

“Yana bangaren Momy”

Ta bashi amsa ta bar shi a gurin tsaye yana kallon apartment din Momy kamar mai
tunani tafiya, ita dai ta yi gaba abinta, har Namra ma ta zo ta wuce Hamad na tsaye
a gurin yana kallon part din. Hurriya na shiga bangaren Mahaifinta ta rungume
Hajiya ta fashe da kuka. Hajiya Binta da tsayi ke neman gagararta sakamakon rikon
da Hurriya ta yi mata kalli Alhaji Haruna.

“Kalli abun da ka yi”

Appa ya sauke kansa kasa ba tare da ya ce komai ba.

“Allah ya kyauta”

Hajiya Binta ta fada sannan ta taka a haka ta isa gurin kujera ta zauna Hurriya na
rike da ita, har jikokinta da matar ďanta Momy suka shigo suka gaisheta, suka fita
Hurriya bata dago daga jikinta domin ji take kamar Amman ce ta rumgume, wani gatan
ma da kakanin suke mata Hajiya Binta da Gwaggo Amma bata mata irinshi.

“Kullum idan na zo gidan nan bangaren Iyami nake sauka, amman yau ka raba wannan a
dole na sauka a nan, mace mai hankali da girmamawa, wannan matar ta san kimata, har
abada ba zaka taba samu mace mai irin tarbiyarta ba tsoho”

Appa ya sauke ajiyar zuciya domin ya san gaskiya Hajiyarsa take fada, iri irin
Iyami masu son iyayen miji da girmamasu kadan ne a duniya ba su da yawa.

“Hajiya ga abinci ki bari na zuba miki”

“Aa Hurriya zata zuba sai mu ci tare ai kasan da ita na saba cin abinci idan na zo”

Appa yayi murmushi.

“Hurriya dago haka Hajiya ta ci abinci mana”

Hurriya ta dago ta bude kulolin ta dauki plate ta fara zubawa. Sai a lokacin Appa
ya lura da fashewar da gilashinta yayi.

“Me ya sami gilashinki Hurriya?”

“Faduwa na yi”

Ta yi karya kai tsaye. Hajiya ta kalli Hurriya sannan ta kalli Appa ta ce

“Kana da dai jin abun da Hamad ya fada min a mota, idan ba zaka dauki mataki ba ni
zan zo da kaina na dauke yaran nan na maida su gidana, domin ba zan bari a rika
wulakanta kamar wasu bare ba”

Appa ya shiga mata rantsuwa domin kare kansa.

“Wallahi Hajiya, ban san da duk wannan ba, ai kin san idan na sani ba zan bari ba,
ni kaina sai a yanzu nake ji a gurin Hamad din, kuma In Shaa Allahu zan dauki
mataki, Hurriya me yasa baki fada min abubuwan da suke faruwa ba?”

Hurriya ta kalli Appanta ta sauke kai ta cigaba da zuba abinci, daman ta sani ko da
Hamad be yi ikirari ba zai iya fada balle ma har yayi.

“Wallahi ban sani ba, amman zan dauki mataki yanzu da yardar Allah”

“Na dai fada maka, dan ba zaka saki uwarsu ba, kuma ka barsu ana musguna musu kamar
wasu ba yi, har dokoki ake saka musu a gida, kuma duk tarin masu aikin gidan nan
ace Hurriya sai ta share dakinta da na Hamad su sauran yaran ai ba haka take musu
ba, shiyasa tun a lokacin da na ji ka saki Iyami na kira Nafisa da Kaltume na ja
musu kunne akan yaran nan ashe na yi a banza, da Iyami ce ko ba zata jefar da
magana ta ba”

“Za a gyara Hajiya, amman dan Allah ki aje maganar daukarsu ko maida su gurinki,
tun da Iyami ta bar gudan nan yaran nan kawai nake gani ina jin sanyi, idan kika
dauke su karin wata damuwar ne a gareni”

Hamad ne ya shigo falon rike da karamar wuka a hannu ya zauna kusa da Hajiya Binta
ya aje wukar gefe.

“Me ya hadaka da wuka Hamad?”


“Apple na yanka”

Ya amsa tare da daukar spoon ya saka a abinci da Hurriya ta zuba.

“Hamad abinci Hajiya ne fa kana ganin na saka nama da yawa shi ne kuma zaka saka
spoon”

A take ya daka mata tsawa.

“Toh ina ruwanki da ni, ba zaki daina shiga min hanci ba ko? Hajiyar ta ki ce ke
kadai”

Hurriya ta kalli Hajiya tana turo baki alamar ta fusata.

“Hajiya kin gani ko?”

“Kyale shi zuba mana wani”

Hamad yayi kwafa, Hurriya ma ta yi kwafa daman tana da haushin marin da aka yi mata
zuginsa be gama wucewa a kuncinta ba. Ai a take Hamad ya daga hannu zai kai mata
duka Appa yayi saurin rikewa.

“Kai Kai Kai Kul daga magana sai ka ce zaka duketa, ita ce yayarka fa, ba zan
daukar maka wannan ba Hamad, haka Iyami ke ta fama da kai kai baka san ka ragawa
kowa ba?”

“Amman Appa ai ita ta fara”

“Yi mata hakuri kyaleta ai yar'uwarka ce baka da kamar ta, kyaleta”

Ba dan kakarsa Hajiya Binta ta saka baki ba zai bar Hurriya ta zauna lafiya ba,
hakan kuma be hana shi sake yin kwafa ba sannan ya fara cin abinci.

“Ni wannan zuciya ta Hamad ban san gun da daukota ba, fushinsa har tsoro yake ba
ni”

Appa ya fada yana shafa kan dansa, Hajiya ta ce.

“Zai daina kurciya ce, da zarar ya girma ya mallaki hankalin kansa zai daina, wani
lokacin yara idan suna jin tashin balaga haka suke jin kamar daidai suke da kowa,
ka bar shi ya cike 20 ko 18 fushin nan duk zai hauka”

“Allah yasa, ya shirya mana”

Hajiya ta amsa da Ameen. Sai da suka gama cin abinci sannan Hajiya ta tashi tare da
jikokinta Hamad da Hurriya Appa na gafenta suka fito daga bangaren na Appa zuwa
bangaren Hajiya Kaltume domin yi mata jaja da kuma barka da kubuta. Ko da suka
shigo falon na Hajiya Kaltume yana cike da yayanta da kuma yayan yan'uwanta da ma
ita kanta sai hira ake har da Namra. Kamar ta Allah haka Hajiya Kaltume ta washe
baki tana maraba da zuwan Hajiya Binta.

“Sannu da zuwa Hajiya, ai da ma baki zo ba, ga kafafuwa suna ciwo ni kaina idan na
warware ai sai na zo na gaishe ki, kuma ai kin kira waya haka ma ya wadatar”

“Aa kara dai na zo, fatar na same ku lafiya”

“Lafiya Kalau Alhamdulillah, ya ciwon kafafuwan yayi sauki?”

“Alhamdulillah”
Sama sama dai suka yi ta gaisawa Appa na zaune kusa da Hajiyarsa daga kasa, Hajiya
Kaltume kuma na daga kan kujera ita da duka yaranta, Hurriya da Hamad ne kadai a
kasa domin haka Amma ta koya musu idan babba yana kan gado ko kujera to su kuma su
zauna a kasa, kar su zauna tare da shi ko kuma a yadda yake zaune. Da hira ta yi
hira ne Hajiya Kaltume ta dauko zancen wahalar da suka sha a dajin tana fadar yadda
aka rika mistreated dinsu kamar wasu dabbobi.

“Shiyasa ake son a samu soji masu kishin kasa da za su iya yakarsu idan ba haka ba,
kasar nan da wahala ta gyaru domin Shugabannin ma sun zama sai a hankali”

Cewar Yasir. Cikin murmushi Hajiya Binta ta kalli Hamad ta ce.

“Da yardar Allah Hamad soja zai yi, wannan fushi da zuciyar ta soja ce”

Hamad ya girgiza kai.

“Aa ba soja nake so ba?”

Namra ta ce.

“To me kake so? Wannan zuciyar taka Hamad ai soja ya dace da kai”

“Aa ni Likitan idanu nake son zama, idan na kware zan yi ma Hurriya aiki ta, ita ma
ta rika gani kamar kowa”

Tsit katon falon na Hajiya Kaltume yayi domin babu wanda ya za ci abun da zai fito
daga bakin Hamad kenan. Hurriya ta yi murmushi tana masa kallo irin na so da kaunar
dan'uwa, ita kanta ba yi zaton Hamad yana sonta kuma ya kula da damuwarta har haka
ba.

“Come here my friend”

Yasir ya mika masa hannu, sai ya taso ya iso gurin Yasir din Yasir ya rumgume yana
buga bayansa.

“Yayi kyau babban mutum”

Cikin jindadi da alfahari Appa ya kalli Hamad ya ce.

“Da yardar Allah da yardar Allah, Hamad ba zaka yi karatu a kasar nan ba, waje zan
kai ka ka sha ilmin akan idanuwa har ka gaji, da ikon Allah wannan kudirin naka sai
ya cika ko da bana raye”

Hajiya Kaltume da ta rasa abun da zata yi ta kalli Appa da murmushin dole.

“Za a karya dokar fitar da yara waje karatu kenan Alhaji akan Hamad?”

“In Shaa Allah, ba shi kadai ba Hurriya ma ba zata yi karatu a kasar nan ba, yadda
take da kokarin nan waje ya kamata ta yi karatu, kuma ko ba ni ba Principal dinsu
ya fada min suna sa ran da zarar ta gama secondary school zata samu scholarship mai
kyau a manya kasasshe saboda kokarinta da yadda take cin gasa ta bangaren lissafi”

“Maa Sha Allahu, Allah ya nuna mana yara masu albarka Allahu akbar Allah dai yayi
albar....ya bar zumunci”

Sai ta kasa karasa da Allah yayi albarka ta canja zuwa Allah ya bar zumunci, domin
ta san hausawa sun ce addu'ar makiyi karɓaɓɓiya ce, ita ko ba zata so su yi albarka
ba. Gashi abun da Appa ya fada cewar yaran Iyami za su karatu a waje ya daki
zuciyarta mugun daka irin dakan da ace mashi ne, babu abun da zai hana ya bullo ta
bayanta, yanayinta ma gaba daya sai ya sauya hankalinta yayi mugun tashi, ba dan ta
yaki zuciyarta ba wata kila ma da ta rasa sukuninta har kowa ya gane halin da take
ciki.

“Allah sarki dan'uwa mai kaunar yar'uwarsa, duk da fadan nan da kuke da rashin
jituwa wannan soyayyar da kaunar tana nan a zuciyarsa, Allah ya kara hada kanku, ya
shirya mana”

Kowa ya amsa addu'ar da Hajiya Binta ta yi da Ameen ban da Hajiya Kaltume da gume
ma ya karye mata kamar wadda aka kwancewa zane a kasuwa. Daga bangaren Hajiya
Kaltume Hajiya Binta ta fito ta shiga bangaren Momy suka gaisa sannan ta fito tana
jin kewar Iyami. Sai addu'a take ma Appa idan dawowar Iyami alheri ce Allah ya
daidaita tsakaninsu, ya kasa amsawa da ameen bayan kuma abun da yake nema kenan a
zuciyarsa. Mota daya suka shiga Hurriya bayan ta dauko mayafinta, ita da Hajiya
suka zauna a back seat, Appa da Hamad kuma suka shiga gaba, Appa yana jan motar
suka fi daga gidan.

After mintuna goma da tafiyar Hajiya Binta, Momy ta fito tare da bakuwarta da kuma
ɗanta da be ci komai ba a cikin abubuwan da Momy ta saka a shirya musu, Miwan na
bayansu tare da dan'uwansa Musib sun yi ma bakuwar Momy da ďanta rakiya ban da
Namra da har yanzu tana can bangaren Hajiya Kaltume.

“Captain ai yana yawan zuwa nan, duk lokacin da zai zo garin na ba ya tafiya sai ya
shigo, ina jindadin haka Wallahi”

Hajiya Turai ta yi murmushi.

“Ai danki idan yana son mutum to ya huta, Allah ya hada jininku”

“Sosai kam, Allah dai ya nuna mana lokacin auren nan mu rakwashe”

Cewar Momy, Mutumen da aka ta maganar akansa be ce uffan ba ya fara sauko Entrance
din hannu dafe a kirjinsa yana murza a hankali domin ba karamin zafi ya ji ba a
lokacin da suka yi karo da Hurriya, taku daya biyu uku hudu yayi kamin ya ja ya
tsaya yana kallon yadda tsaddadiyar motarsa ta yi ta kasa gaba daya, saboda tayun
motar da aka succe duka hudu. Ya juyo ya kallesu.

“Waya taba motar nan?”

“Wace motar?”

Kusan a tare suka kalli motar Musib yayi sauri sauka ya karasa gurin motar da
mamaki.

“Lafiya kalau kuka zo da ita?”

“Idan bata da lafiya zamu zo da ita ne? What kind of stupid question is this!”

“Subhanallahi, garin ya haka ta faru!”

Cewar Momy tana saukowa ta nufi gurin motar. Miwan ya ce

“Gaskiya wannan succe tayun aka yi”

“To waya aikata haka? Wannan dai rainin wayo ne da neman mutum yayi magana ace ya
cika masifa”
Ya fada da karfi wani karin bacin dai na tunkarosa, cikin bakinciki ya sauka ta isa
gurin motar. Momy ta kai hannu ta dafa karjikinsa.

“Kwantar da hankalinka Captain, a cikin yaran nan dai wani ba zai yi gigin yi maka
haka ba, akwai dai matsalar da aka samu”

Momy na rufe Hajiya Turai ta miko masa hannu kamar wani karamin yaro dan yaye.

“Captain shigo ka zauna, sai mu shiga wata motar”

Ya sauke ajiyar zuciya tare da jan dagon numfashi ya fi sau goma, sannan ya shuri
motar da kafarsa da karfi.

“Duk wanda yayi min haka da gangan yayi, saboda a bata min rai”

“Toh waye zai maka haka Captain? Dan Allah karka bata ranka, na gano, yanzu haka ba
zai wuce bakar matar can ba Kaltume, domin na dade da lura da yar bakinciki ce ta
karshe”

Momy tana maganar tana jin kamar ta yi tsalle taje ta shake wuyan Hajiya Kaltume.

“Oh kekam baki zaune cikin mutane kwarai Hajiya Nafisa, rayuwa a gidanku tana da
wahala”

Momy ta amsawa Hajiya Turai tana kwafa.

“Barta na san yadda zan yi maganinta, da ni take zancen, Captain yi hakuri shigo ka
huta sai ka dauki motata ku tafi da ita, idan an gyara wannan Musib zai kai maka
ita gida”

Jameel ya juyo ya nufo hanyar falon, sai duk suka dugunzuma suka biyo bayansa, ban
da Hajiya Turai da bata matsa daga inda take tsaye ba tun bayan da suka fito daga
falon. Cikin natsuwa da kamala ya shiga falon, sai ka rantse ba shi ne ya gama
bacin rai a waje ba, zaunawa yayi ya hade hannayensa ya sadda kai kasa ya rufe ido
yana motsa bakinsa a hankali, kokari yake na ganin be bar bacin ransa ya ninku a
zuciyarsa ba...
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Hello Habibaties 😍🥰
Amin kara please ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

1️⃣2️⃣
2️⃣
1️⃣1️⃣
2️⃣

Musib ya aje ma Captain keys din motar Momy da ta bada umarnin a dauko masa. Kallon
Keys din yayi sannan ya mika hannu ya dauka ya mike tsaye. Tsabar bacin rai
zuciyarsa har zafi take kamar zata fashe, baya jin yana da sauran wata magana a
yanzu kuma baya bukatar yi ma Momy sallama bayan an bata masa tayun mota a gidanta.
Shi ya fara fita sannan mahaifiyarsa ta bi bayansa Momy da Musib suka biyo shi suna
ba shi hakuri kamar su suka masa laifin shi dai be ce uffan ba ya matsa key
hannunsa motar ta fita key ya sannan ya nufita har suka bar gidan kalma daya bata
sake fitowa daga bakinsa. Ran Momy be yi dadi ba ganin ďan ďan'uwanta da take ji da
shi ya fita cikin bacin rai.
“Ni abun nan ya ba ni mamaki, wai waye yayi wannan aika-aikar”

“Zai wuce Kaltume? Ai bata son kowa da alheri a gidan nan kuma ta ga mota mai tsada
ina za so haka, ballantana fitowar nan da ta yi dan uwa ko daya be je ya mata barka
da fitowa ba”

“Amman Momy Yasir dai ba zai yi haka ba kin san ko da ta saka shi”

“Su matan fa? Kuma shi ma ba munafurci ba ne da nuna soyayyar ido, ai ta ciki na
ciki dan'uwa be taba son dan'uba ba har abada”

“Ko kuma ta aiko wani yayi ba”

Ta juyo tare da Musib suka shigo falon, ko zama ba su yi ba motar Appa ta faka a
harabar ya bude ya fito ya shigo cikin falon fuska a dauke.

“Ku ba mu guri zan yi magana da mahaifiyarku”

Appa ya fada immediately after ya rufe kofar falon, Musib ya dubi Miwan sannan suka
tashi suka haura sama, Momy kuma ta zauna ita ma nata ran a bace tana sauraren da
wacce Appa ya zo.

“Nafisa ina son na tambaye ki, akwai laifin da Hurriya ta yi miki ko kuma Hamad?”

“Wani abun aka fada kuma?”

“Akan wani dalili zaki nemi banbanta su da sauran yayanki? Fada min banbanci dake
tsakinsu da Namra ko Miwan, dukansu ba Yayana ba ne? Akan wane dalili zaki ce
Hurriya sai dai ta share dakinta da kanta kuma idan zata hau stairs ko ta sauka ba
ta hau kamar yadda Namra ko Musib suke yi ba?”

Momy ta rike baki.

“Oh Allah na ni Nafisa, yaushe aka yi haka? Kuma shi kenan daga fada maka zance
karya da gaskiya sai ka hau ka zauna har da zuwa gurin fada ba tare da ka tsaya ka
bincika ba? Shiyasa ka dauko su ka kawo min? Me yasa ba a kaiwa Kaltume ba? Ita da
yake tsoronta kake sai Nafisa da aka raina itace mai dadi hawa, gashi sai mulki
take mana ciki gidan ita da yaranta”

“Daga ke har ita karkashin kulawata kuke kuma karkashin ikona, dan haka duk gurin
da nake ra'ayi a can yarana za su zauna, kuma ina gargadinki wannan ya zama na
karshe da zan sake jin wani abu marar dadi akan Hurriya da Hamad, zan iya canja
mata ban zanja yaya ba, gaba daya yarana babu na yarwa kuma bana son a batawa kowa”

“Eh amman ai ka ware wadanda kake so kake kauna, na tabbatar da nawa yayan Kaltume
ko Iyami take yi ma wani abu ba zaka yi magana ba, amman da yake yayan mowa ne ai
gashi nan ka shigo falo cikin bacin rai saboda an taba yan gold, ni da zaka nuna
musu kauna ka dawo da uwarsu ai da duk yafi wannan nema musu yanci da kake, idan ya
so sai ta rike yayanta na rike nawa”

“Abun da na ga damar aiwatarwa shi zan aiwatar, babu mai fada min gabas, na san
Allah, daman ke haka kike banta zuwa da wata magana ba ki musa min ba, ban taba
fada kin yi shiru kin saurareni ba sai kin fada, sa'insa da ni ba yau kika fara ba,
daga ke har Kaltume babu wadda nake jin sanyinta kowacce ku da lagon da take
matsawa ta bata min rai”

Momy ta fashe da kuka domin kalaman Appa sun mata zafi, ta san abun da Appa ya fada
akam Iyami gaskiya ne, domin ya saba yi mata fada ko a gabansu kamar yadda su ma
zai iya musu a gabanta ko kuma ya tara su gaba daya yayi musu fadan idan wani abu
ya faru, su kan tanka shi su kare kansu ko maida martani amman Iyami bata cewa idan
yana fada har yayi ya gama, ko daga kai ba zata yi ta kalleshi ba, wannan ta saka
suke yawan yi mata kallon munafuka, hawaye shar Momy take yi daman kuma bata gama
hucewa daga bacin ran abun da aka yi ma Captain ba.

“Eh sai Iyami, abar kaunarka, yanzu gashi nan ka rufe da fada akan yayanta, matarka
Kaltume kuma ta takura min ta takurawa bakina, yanzu Captain ne ya zo, ka san dai
yadda nake da Captain amman haka matar nan ta saka aka fasa mata tayun mota saboda
bakin ciki, ban gama huce wannan haushin ba gashi nan kai kuma ka zo ka rufe ni da
wani, toh Wallahi ka jawa yayanka kunne su daina munafurci, kuma ka jawa matarka
matarka kunne ta fita safgata da ta bakina babu ruwanta da ni idan ba haka ba
Wallahi za 'ayi tashin hankali da ba taba yi ba ko a lokacin da ka auro karamar
yarinyar can Iyami”

“Ni dai na fada miki, karki sake banbanta min to ƴaƴa duk daya suke a gurina, babu
wanda ya fi wani, zan iya canja mata ban canja ƴaƴa ba bana ni da kamar ƴaƴana!”

Yana kawai nan ya juya ya fice, cikin motarsa ya koma yaja ta zuwa bangare ya ajeta
ya fito ya taka da kafa ya nufi bangaren Hajiya Kaltume yana shiga ita ma ya
salllami yaranta suka haura sama ban da Yasir da baya gidan ma a lokacin ya fita
gurin safgoginsa, Namra kuma ta fita zuwa bangarensu. Fada yayi mata sosai yana ja
mata kunne akan abun da ta saka aka yi ma Momy.

“La'ilaha Illallahu ni Ummul Kultoon, yaushe kuma aka yi haka? Ni miye ruwana da
Nafisa balle kuma bakinta, yanzu Fisabillahi na rasa me zan saka ayi mata sai fashe
tayar baki? Abu dai kamar karamar yarinyar? Ni da nake ta kaina ma? Yaushe na fito
daga daji? Kofar daki ma bana sha'awar fita balle kuma har na saka ayi wani abun,
shigowar nan da ka yi ma hankalina sai da ya tashi”

“Ni dai na gargadeku, bana son wani tashin hankali kowa ya zauna lafiya kuma ya
tsaya a iya matsayinsa, ku bar ni da abun da yake damuna, kullum ni ne cikin fitina
kamar akaina aka fara mata aure da mata biyu”

“Mata uku dai Alhaji, yaushe ka saki yarinyar can Iyami da har zaka dawo kanmu nu
kadai, musamman ni, taya za a ce na fasa tayar mota? Yara ma wa zan saka yayi
wannan aiki? So take ta zugaka ka koreni a gidan kamar yadda ka kori Iyami, to
Wallahi ni kam zama daram dam dam dam sai mutuwa, kuma Alhaji dan Allah ka rika
bincike kamin ka fara fada, Wallahi sheri ne kawai na kishiya da neman hada mata da
miji, abun da ba ayi ba da kurci ayi shi yanzu”

“Na dai ja muku kune, kowa ya tsaya iya matsayinsa bana son sake jin wata fitar”

Har Appa ya fice Hajiya Kaltume bata gama mamakin jin irin kagen da Momy ta yi mata
ba, Salma ce ta fara saukowa sannan Khairi suna tambayar me ya faru domin sun lura
da yadda mahaifinsu ya shigo cikin fushi.

“Wai munafurci matar nan ta hada, wai na tura an fashewa bakinta tayun mota, shi
kuma babu tsayawa bincike da yake ta mallake shi komai ta fada masa shi yake yi
kawai ya zo ya rufe ni da fada, ai bari Wallahi ita ma sai ta bar gidan nan Kamar
yadda Iyami ta fitar da ni, waya sani ko gurin tsafinta ta tafi aka bata wani
asirin ace ta zo ta hada mu, gaba daya ta mallake Alhaji ta juye masa kai komai ta
fada sai ya hau ya zauna”

“Tab Lallai Momy ta yi nisa, wane irin fasa tayun mota kuma?”

Hajiya Kaltume ta kalli Salma dake maganar.

“Sheri ne kawai a samu yadda za a hada ni fada da Alhaji sai ya sake ni”
Haka Hajiya ta yi ta jininin maganar tana ta masifar har yamma.

*** *** ***

Hajiya Binta dake gidan baya tana shafa kan Hurriya dake kwance jikinta ta ce.

“Tsoho kamin ka kai ni gida, ina son ka biya da ni gidansu Iyami na dubata yaranta
ma su ganta”

Kamar wadda aka cewa ya shiga ramen wuta haka Appa yaji, ko kadan be son abun da
zai kusantashi da Iyami gashi kuma be isa ya musawa Hajiya ba.

“Toh Hajiya amman idan na aje ki Yasir zai zo ya dauke ki ya maida ke gida su kuma
yara ya dawo da su”

“Toh zamu tafi gidan makiyiyarka ba, Allah ya kyauta”

“Haba Hajiya irin wannan maganar be dace ba a gaban yara ban da alheri me iyami ta
yi min da zan dauki kiyaya na bita da ita”

Hajiya dai bata sake cewa komai ba har Appa ya canja hanya ya dauki hanyar gidansu
Iyami. A bakin gate din ya faka, ya fito ya budewa Hajiya ta fito tare da Hurriya
sannan Hamad ya bude front door ya fito.

“Ba zaka tsaya ta fito ku gaisa ba?”

“A gaishe ta dai Hajiya”

Ya amsa yana kin hada ido da Hajiya Binta, girgiza kai kawai Hajiya ta yi ta cira
kafa suka karasa bakin madaidaicin gate din da tuni Hamad ya bude har ya shiga
ciki. Yanayin yadda Hajiya Binta ta tararda Iyami be mata dadi ba, daman kuma ta
san za'a rine wai an saci zanen mahauciya, mai ciki ba a rabata da laulayi balle
kuma ita da take cikin damuwa, sai dai ganin Hajiya Binta ya saka ta ji kamar an
dauke mata ciwo, suka ta yi hira kamar yadda suka saba.

“Jiya muke zancenki da Gwaggo na ce ina tuna haihuwar Hurriya da irin hidimar da
kika yi”

Hajiya Binta ta yi murmushi.

“Abu kamar jiya, yanzu Hurriya ta cika sha shida cif”

Hurriya ta wara ido tana mamaki yadda ta manta birthday dinta.

“Eh fa Hajiya amman ai sai October 10”

“To October ba ya kusa ba? Miye rage yan kwanaki ne kawai”

“Hajiya zaki yi ma Appa magana yayi min celebration please”

Iyami ta ce.

“Kin san halin Appanki ba son irin abubuwan nan yake ba, shi gaba daya rayuwarsa
irin ta mutanen da ne”
“Zan masa magana da kaina, maybe zai yi min gashi ma dazun ya fada mana a falon
Hajiya ya ce ni da Hamad a waje zamu yi karatu”

Mamaki ya cika Amma har sai da ta bude baki ta kalli Hajiya dake murmushi.

“Shi da kansa?”

“Shi da kansa fa, sai dai ki yi ta addu'a kuma ki yi musu, ai maso uwa ya so
yayanta, abu dai ne idan ya zo babu yadda za'ayi sai hakuri kawai, amman sakin nan
ba karamin mamaki ya ba ni ba”

Amma ta sauke kai kasa tana jin wani rashin dadi yana ziyartar zuciyarta. Hurriya
ta tashi ta fice zuwa dakin Anty Rukayya haka take jjnta kamar wata sa'arta saboda
tana wasa da ita sosai kamar yaya da kanwa, wannan ya saka Hurriya bata kallon
Rukayya a matsayin kanwar Amma sai idan babin girmamawa ne, ba ita ba ko Hamad wasa
yake da ita, daman kuma hausawa sun ce karamar uwa madaukar zunubi. Amma ta ce

“Haka Allah ya so Hajiya komai Allah ne yake tsarawa Allah dai ya ba mu ikon cinye
jarrabawar wannan jarabarwar”

“Toh Ameen ina nan ina ta addu'a, da yardar Allah Iyami sai kin koma dakin domin
sakin nan naki har hawan jini yake son tasar min, Allah ya sauke ki lafiya, da na
shiga gidan ma sai na ji duk yayi min dabam”

“Ameen”

Amma ta amsa tana jin zafin barin gidan Appa da ta yi, ba tare da laifin komai ba.
Gwaggo ce ta shigo suka suka ta hiran kowa yana fadin abun da ya fahimta game da
lamarin, Amma kuma tana fadar yadda Appa ya canja mata tun kamin sakin. Cikar da
cikin Hajiya Binta yayi a gidan danta be hana ta cin abinci a gidan Amma ba, saboda
tana son Amma kuma ta san idan bata ci ba Amma zata ji babu dadi domin abinci Amma
take fara ci kamin ta ci na kowa wani lokacin ma bata taba abincinsu sai ta ce ta
koshi. Bayan sallah la'asar Yasir ya iso gidan daukar Hajiya Binta kamar yadda
mahaifinsa ya umarce shi, cikin gidan ya shigo suka gaisa da sannan ya fito tare da
su Hurriya a daidai lokacin da Rukayya ta sallami bakonta ta nufo karamar kofar
shiga tsakar gidan da suka fito.

“Yasir ya gida”

Ya sake mika masa gaisuwa a karo na biyu bayan gaisuwar farko da suka yi a lokacin
da ya shigo.

“Mutumen da na gani saurayinki ne?”

Wani kallo ta yi masa jin yadda yayi mata tambayar kai tsaye kamar da zolaya kuma
kamar gaske, domin murmushin dake fuskarsa ya hanata fahimtar komai.

“Dan makarantar mu”

“Dan makarantarku har cikin gida? Lallai yana da matsayi da alama”

Murmushi kawai ta yi ta maida dubanta gurin Hajiya da Amma ta rakota suna tafiya
suna hira.

“Allah ya kiyaye hanya, Hurriya sai kun dawo”

“uhmmm za a shiga a cigaba da karatun ko? Ko last time da na zo har na fita baki
sani ba tsabar karatun littafan soyayya, to aje a karasa kar a manta page din da
ake”
Ta girgiza kai still tana murmushi.

“Yasir ka cika shiga min hanci fa... Haka kemin idan na je gidanku ko zama na yi
sai ka ce ba daidai na zauna ba”

“Toh ki fyato ni mana idan kin isa”

A nan ma murmushi ta yi ta shige ciki, shi ma ya bita da kallo yana murmushi


Hurriya da Hamad kam tuni sun kai cikin mota, inda sabo sun saba da ganin tsokanar
yayansu akan kanwar Mamansu ba sabon abu ba ne a gurinsu Amma ma ta saba gani balle
kuma su. Amma da kanta ta budewa Hajiya mota ta shiga ta rufe sannan ta juya ta
koma ciki Yasir ya shiga ya fara jan motar.

“Yasir na ce ko a fara sabunta kayan dakina ne na kusa samun kishiya?”

Hurriya ta saka dariya Hamad kuma yayi murmushi tare da cewa

“Hajiya yanzu kuma kin fasa aurena?”

“Eh ga babba me zan yi da yaro! Yasir ya ishe ni gashi har yana nema min kishiya,
ko da yake Kaltume ai ba zata yarda ka dauki wannan ba sai dai wata”

“Ke tsohuwa waya fada miki har yanzu ana irin zamaninku da ake yi ma mutane auren
dole? Ni zan zabo wadda nake so na yi aurena”

“To Allah ya nuna mana, kuma ya bada ta gari”

“Ameen”

Ya amsa yana cigaba da jan motar. Sai da ya fara isa gidan Hajiya ya sauketa sannan
ya juyo ya kama hanyar gidansu, a harabar Hajiya Kaltume ya faka motarsa ya bude ya
fito Hamad ma ya fito tare da Hurriya gaba dayansu suka nufi hanyar falon Hajiya
Kaltume.

“Hurriya me ya samu gilashinki?”

Yasir ya tambaya domin tun zuwansa daukarsu ya lura da fashewar gilashin nata. Ta
kai hannu ta taba gilashin.

“Faduwa na yi”

Karaf Hamad yayi ya ce.

“Karya take wani bakon Momy ne ya mareta ni kuma ya na fasa masa tayun mota gaba
daya”

Daga Huriyyar har Yasir tsayawa suka yi kallonsa da mamakin furucinsa.

“How?”

“Wuka na saka wukar Momy ta yanka ƙashi na yi ta cakawa ina yanka har da sai da na
fashe duka tayun”

Maganar yake yana nuna yadda yana yana cize baki alamar ƙeta. Cikin mamaki Yasir
yayi dariya ya bugo kan Hamad.

“Baka da kyau yaron nan bura'uba”


Hurriya ta yi murmushi for the second time ta sake jin Hamad ya burge ta a yau,
bayan da ya fadi cewar zai zama likita saboda yayi mata aikin ido yanzu kuma ya
fasa tayun wani saboda ya mareta, ita dai ta san bata jituwa da Hamad suna yawan
yin fada da samun tsabanin amman kuma yana nuna damuwarsa da kulawa a duk wani abu
da ya shafeta, idan wani ya taba ta yana jin zafi fiye da yadda shi idan aka masa
yake ji. Yasir ya shiga tambayar me ta yi ma bakon yayi mata marin da ya saka
gilashinta fashewa.

“By Misteke na fito... ”

Shi kansa be ji dadin jin karami dalili da be taka kara ya karya ba ya saka bakon
marinta marin kuma mai zafi.

“Mutane ba su da hakuri kuma ba su da hakuri...”

Ya rufe baki yayinda yake tura kofar falon ya shiga.

“Toh Wallahi ba zan dauka ba, wannan wulakanci da rainin wayon da Nafisa take min
yayi yawa”

“Me ya faru?”

Yasir ya tambaya domin shi kadai ne be san wainar da ake toyawa ba. A take ta amaye
masa cikinta tana wani cika domin ba karamin cin mutunci ne a gareta ba Momy ta
zargeta da haka duk kuwa da irin rashin zama lafiyar da suke. Yasir ya kalli Hamad,
Hurriya ma ta kalli Hamad Hamad ya kalleta kowa yayi shiru, shi dai Hamad ba zai yi
laifi yace shi yayi ba, kuma idan an gano shi yayi hakan ba zai dame shi ba,
Hurriya kuma ba zata tonawa dan'uwanta asiri ba, balle kuma Yasir da ko da yaushe
yake kashe wutar fitina.

“Toh Hajiya Ki yi hakuri, dan Allah ku daina wannan fadan, bana jin dadi haka Appa
ma ba dadi yake ji ba, kuma dai ba yara kuke ba be kamata ace kuna biye zuciya ba”

Hajiya ta daki cinyarta

“Wallahi ba zan hakura ba, sai ta dandana kudarta, kuma Wallahi na fi karfinta
bokanta yayi karya Wallahi, Iyami ma ta kara da ni ta bar ni balle ita bukkar
banza, mai karyar arziki sai ka ce kanta farau arziki duk ta fi ta cikawa mutane
gida da bakin kuri da iyayi ita diyar mai kudi, mun ji karuna duk arzikin ubanta be
kai karuna ba, ni kuwa sai na zame mata fir'auna a cikin gidan nan”

“Subhanallahi Hajiya dan Allah ki daina irin maganar nan haba”

Yasir ya fada cike da damuwa, domin baya jin yadda matan ubansa suke samun tsabani
a gidan.

“Babu ruwanka babu ruwanka idan ba zaka taya ni yaki ba karka sake shiga tsakanina
da kowa, dan iya. Ke kuma yar gadon munafurci bace min da gani”

Ta karasa tana watsawa Hurriya dake tsaye tare da Hamad harara, babu bata lokaci
Hurriya ta juya ta fice daga falon, Hamad kuma ya tsaya a gurin kamar ba zai tafi
ba, irin yadda yara masu fama da rashin kunya suke yi, sannan ya fice yana wani
tukuki saboda saka sunan uwarsa a fadan da Hajiya Kaltume ta yi kuma ta kira
Hurriya da yar gadon munafurci.

____________________
Masu karatun suna hango abun da nake hangowa? 😳
Akwai Bomb fa ba karami ba? Fatan dai kun shiryawa tafiyar? 😁

Idan kun karanta ku yi sharing 🥰

☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Pease ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

1️⃣3️⃣
3️⃣
1️⃣1️⃣
3️⃣

Da kallo ya bi Hurriya da Hamad har suka fice sannan ya kalli Hajiya Kaltume ya
dauke kai ya nufi stairs. Yana shiga dakinsa abun da ya fara yi shi ne duba gurin
da ya aje gilasan Hurriya, amman be ga ko daya ba, a nan ya fara tunanin ko ya
canja musu gurin ajiya ya manta, haka ya bi komai na dakin ya duba ba gilasan babu
alamarsu, fitowar yayi mamaki duk ya cika fuskarsa ya sauka kasa sai ya samu
mahaifiyarsa a gurin da ya barta zaune sai dai wannan karon waya take amsawa,
gefenta ya zauna a hannu kujera har sai da ta gama wayar sannan ya tambaye ko ta
dauka.

“Me zan yi da gilasai kuma? Komai dai ni, ubanka ya dora min laifi matan ubanka su
adabe ni kai kuma yanzu ka zarge ni da satar gilasan Hurriya saboda ga Kaltume
makiyiyarta ko?”

Maganar Hajiya bata masa dadi ba kuma ya san duk wani kalami da zai dora bayan nata
a yanzu ba zai fahimtar da ita. Dan haka ya tashi ba tare da ya sake cewa komai ba
ya nufi dakin yan'uwa daya bayan daya ya bi yana tambayarsu kowacce tace masa bata
dauka ba, Khairi har da hadawa da rantsuwa saboda ta fi kowa rashin tsoron Allah.

‘Toh ko Hurriya ta zo ta dauka ko Hamad ban sani ba?’

Ya tambayi kansa, sai dai ya san ba su taba masa haka ba, idan tana bukatar abu
zata yi masa magana kuma idan ma ta dauka zata fada masa. Fitowa yayi daga
bangaresu ya nufi bangaren Momy, kamar ance masa juya ka gani, yana juya ya kalli
bangaren Appa sai ya hango Hurriya tsaye tare da Appanta ta rike hannunsa tana ta
bata rai da alama makiya take masa kan wani abu. Fasa nufar bangaren Momy yayi sai
ya nufi bangaren mahaifinsa domin tambayarta ko ta dauko gilashin be sani ba.

“Appa dan Allah daga wannan ba zaka sake yi ba”

Ta fada cike da shagwaba tana kara rike hannunsa.

“Haramun ne, ba kyau Hurriya ni bana sha'awar irin abubuwan nan”

Appa ya fada yana kallon Yasir da ya iso gurin fuska a sake.

“Me take so Appa?”

“Birthday kuma ka sa be da kyau ba al'adar mu ba ce hausawa wannan dabi'un turawa


ne”
“Oh Appa yanzu kai ya waye fa, ba wani abun ba ne kawai dai ana samun tsabanin
fahimta ne ga mutane, kuma yanzu zamani ya canja ba kamar lokacin baya ba”

“Ko zamani ya canja ni ban canja ba Yasir, abun da duk ba tarbiya ba bana sha'awar”

“Appa sau daya zamu yi fa, daga wannan ba zaka sake ba? Appa please kawaye na duk
ana musu sai ni”

Tana maganar tana son yin kuka Appa yayi murmushi.

“Shi ke nan na ji, za a dafa shimkafa fara ayi sadaka”

Ta buga kafa daya a kasa tana kukan da babu hawaye, Yasir kuma ya saka dariya.

“Appa dan Allah dai Appa”

Ba kasai Hurriya take zuwa masa da bukata ba, kusan duk wata bukata da take gabatar
masa da ita kidayayyyiya ce, hakan ya sak idan ta zo masa sai ya biya mata ko dan
tausayinta da yake na lalurar dake tare da ita, balle kuma yanzu da tausayinta ya
ninku a zuciyarsa saboda rashin Amma a gidan, sai yake ganin yaransa kamar wasu
marayu da uwarsu ta mutu ta bar su.

“Na ji amman daga wannan ba za'a sake ba?”

Ta amsa da sauri tana tsalle.

“Na yarda Appa na yarda Allah ya saka da alheri, Appa Allah ya biya maka bukatunka
na alheri ya rabaka da Hajiya Lafiya ya kara buda maka a kasuwanci ya kyautata
karshenka”

Ta masa kwatankwacin addu'ar da Amma take masa idan yayi mata wani abun kyautata da
ta ji dadi. Appa ya shafa kansa yana jin zuciyarsa da tausayin da be san na minene
ba. Yasir ma murmushi yayi yana taya ta murna yadda Appansy ya amince da wuri.

“Bari mu fara neman Gift din da zamu bawa mai birthday”

“Har da kyauta ake badawa?”

Appa ya tambaya sai Yasir ya amsa masa.

“Eh Appa idan mutum yayi birthday ana ba shi kyau sosai ma, kowa da kalar abun da
yake ba shi”

“Oh toh saboda ki ci kudinmu kike son yi birthday kenan?”

Cewar Appa yana kallonta da zolaya, sai ta saka dariya kamar ba ita ta rufe idonta.

“Appa ba da kai ba an yafe maka”

Shi ma dariyar yayi, ya bita da kallo domin tuni ta nufi bangaren Momy domin
labartawa Hamad cewar Appa ya yarda zai mata birthday kamin ya isa gurin hawaye ya
cika idonta domin ta saba idan aka mata albishir Amma take fara fadawa sai dai a
yau babu Amma a gidan kuma ta san babu wanda zai taya ta farinciki da murna sai
dan'uwanta. Tana ahiga falon sai ta ja ta tsaya tana kallon Musib da ya hada
hannayen Hamad ya rike yana zabga masa mari.

“Ba zaka yi magana ba? Waye yaje ma fadawa Appa karya da gaskiya ya zo ya rufata ta
fada? Tsakanin kai da Hurriya”
“Ni ce”

Ta amsa kai tsaye domin ba zata jure ganin ana duka dan'uwanta ba da yaki yayi
magana kuma ya ki yayi kuka sai dai idanuwansa sun kada sun yi ja sosai sai wani
cika yake yana batsewa alamar zuciyarsa ta gama kawowa.

“Okay zo nan bakar mufuka wato daga dawowarku za ku fara hada Momy fada da Appa
ko?”

Bata zo ba kamar yadda ya bukata sai dai kuma bata matsa daga inda take tsaye ba
ssi hawayen da ta shigo da su suka fara sauko mata, Hamad ya juya ya kalleta har
lokacin be ce komai ba, daman tun shigowarsa falon Musib ya rike shi wai sai ya
fada masa waya fadawa Appa gulma har ya shigo yana mata fada ta yi kukan, Hamad ta
kafiya ya ki magana hakan ya saka Musib dukansa. Musib ya saki hannun Hamad ya
nufi gurin da Hurtiya take tsaye ya fara kai mata duka sai ta boye fuskarta ta fara
kuka, yadda Hamad ya nufo gurin da suke tsaye sai ka dauka zai yi dambe yayansa
Musib ne, ficewa yayi daga falon Musib na kokarin rikoshi ya fisge ya fice da gudu,
be zame ko'ina ba sai gurin da Garden din gidan yake ya samo manya manyan duwatsu
ya dauko har uku ya fito da su ya nufi gurin da Motar Momy take ta fara jefan
gilashin a take ya fasa mata gilashin mota ya koma dayan bangaren ya sake jefawa.
Kamin yayi na uku Appa da Yasir da suke tsaye a gurin da Hurriya ta bar su, suka
iso gurin da sauri domin sun lura da lokacin da ya dauko duwatsu sun san ba za'ayi
mai kyau ba, Yasir yayi saurin rike Hamad.

“Kai miye haka?”

Sai a lokacin Hamad ya fashe da kuka yana maida magana.

“Ya Musib ya yi min mari hudu, kuma gashi can yana dukan Hurriya, wai ya ce mun yi
munafurci mun hada Momt da Appa fada”

Appa da ransa ya bace saboda abun da Hamad aikata, a take abun da ya fada ya gusar
da bacin ran abun da Hamad yayi. Ya nufi falon fuska a hade Yasir dake rike da
Hamad har lokacin yana ta zillo sai ya sake kwaso wasu duwatsun ya fasa motar ya bi
bayan Appa. Da karfi Appa ya tura kofar falon ya shiga sai ya samu Hurriya duke
kusa da kofar ta rufe fuskarta tana kuka marar sauti.

“Musib...!”

Appa ya aika masa da wani irin kira da karfin murya mai razanarwa. Musib dake boye
kitchen ya fito baki kofar kitchen din yana amsa kiran muryarsa na rawa.

“Na'am...”

Appa ya taka ya karasa har inda yake ya dauke shi da mari. Daidai lokacin da Momy
ta sauko tare da Namra.

“Akwai wanda na taba duka cikinku? Akan wani dalili zaka dokesu? Kai da ya kamata
ka ga wasu musguna musu ku shigar musu kai zaka saka hannu da kanka ka dokesu?
Karka sake! Ina gargadinka ba su ba Hurriya da Hamad kadai ba duka yayana kar ka
sake saka hannu ka dake su”

Appa ya juyo ya kalli Momy dake tsaye kamar hoto tsabar mamaki ya ce.

“Na rantse da Allah idan wani ya sake dokar min ƴaƴa sai na masa abun da zai yi
bakinciki da na kasance ubansa, ban doka ba ba zan yarda wani ya dokar min ba”

“Saboda ƴaƴan Iyami ne?”


Momy ta tambaya tana jin wani tuƙuƙi a zuciyarta, shi kuma ya amsa mata ba dan suna
ƴaƴan Iyami kaɗai ɓa sai dai baya daukar a zalinci kowa, amman saboda ta ji haushi
sai ya amsa mata da haka.

“Eh saboda suna Ƴaƴan Iyami...”

Yana fadar hakan ya juya ya fice daga falon, a nan ma Yasir da har lokacin yana
rike da Hamad dake ta jan numfashi da karfi saboda zuciya, ya rufa masa baya tare
da Hamad din, Hurriya kuma da ta tuni kuka yayi mata bankwana ya tafi ya barta
tsaye tana kallon dramar da ake ta bi Appa da kallo kamin ta juyo ta kalli Momy.

“Ba hakka, haka ne... Daman ance maza ke bude wata kofar wani lokacin yau na gani,
kuma ya bude muku kofa, za ku wahala a gidan nan. Musib yi hakuri”

Ta juya ta fara hawan stairs din daman bata sauko gaba daya. Musib ya watsawa
Hurriya wani mugun kallo ya dauke ido ya bi bayan mahaifiyarsa. Zaunawa Hurriya ta
yi a gurin ta rafka uban tagumi, gaba daya kwakwalwarta ta rike ce ji take kamar ba
zata iya dauka ba.

*** *** ***

BAYAN WATA UKU....

Tun daga lokacin sai Hurriya da Hamad suka samu salama, ta duka Hamad kuma ya samu
ta magana, ba a dukansa ba a fada masa magana marar dadi, saboda ana tsoron ya
fadawa Appa, Musib da Miwan ma sai duk suka shafa musu lafiya, sai dai tsanar da
Hajiya Kaltume take mata sai ya karu, har ta kai a gaban Hurriya Hajiya Kaltume
take zagin Iyami sai dai ba zata yi a gaban Hamad ba, Hurriya tana jin zafin abun
sosai sai dai bata taba fadawa kowa ba sai dai ta bar abun a zuciyarta. Hurriya na
tsaye ita da Hamad suna wanke motar Yasir Hajiya Kaltume ta fito rike da jakarta
Yasir din yana bayanta rike da makullin mota.

“A gaishe da ku, amman idan Appa ya gani karku ce ni na saka ku ku ce ku kuka saka
kanku dan kar ya fara fada ya ce ban kai wankin mota ba na saka ku yi”

“Hamad ya fada masa zamu wanke maka mota ai kamin mu fara, ya ce mu je mu yi Allah
ya mana albarka”

Hurriya ta amsa tana watsawa motar ruwa, domim wankin mota yana daga cikin abun da
yake matukar burgeta, kuma ta taba yi sau daya a motar Appanta tun a lokacin da
Amma take gidan. Hajiya Kaltume ta kallesu irin kallon nan na rasa ya zan yi da ku
ta dauke kai ta nufi motar da za su shiga, tana nufar motar gabanta na kara
tsananta faduwa har sai da taja ta tsaya.

“Yasir anya ba za mu fasa tafiyar nan ba? Gabana sai faduwa yake Wallahi tsoro nake
ji ganin nake kamar wani abun zai sake faruwa”

Yasir ya ce.

“Babu abun da zai faru Hajiya dan Allah ki kwantar da hankalinki, ki yi imani da
Allah, kuma kin ga tun da abun nan ya faru baki sake fita ba, yau kusan wata uku
kenan dole ki ji haka”

Ta girgiza kai domin bata gamsu da kalaman Yasir ba.

“Ko dai mu hakura har wani lokacin?”


“Hajiya idan baki kawar da komai a ranki ba, babu ranar da zaki sake fita, rasuwa
nawa aka yi baki je ba, ga haihuwa ba an yi ba daya ba amman baki fita ba, Hajiya
Fatee ma tare abun nan ya same ku amman zuwanta biyar gidan nan, dan Allah ki daina
tsoro babu abun da zai faru da yardar Allah”

“Toh Allah yasa”

Ta amsa tare da bude motar ta shiga ba dan ranta ya so ba, sai dan fitar ta zame
mata dole ne saboda kiran da Hajiya Fatee ta yi mata tana kuka ba zata fita ba,
balle kuma da ya kasance gidanta na farko da zata fara zuwa tun bayan da aka yi
kidnapping dinsu, sai take ganin kamar hakan zai sake faruwa ne. A hankali Yasir ya
rika jan motar suna tafiya yana dan taba mata hira, ita kuma ta kasa cewa komai sai
kallon gari take har lokacin tsoro be fice ta ba, garin kuma tana ganin kamar ya
sake saboda dadewa da ta yi bata fita ba.

“Bismillahi”

Ta furta yayin da ta bude motar zata fita, zuciyarta nata rawa, Yasir ya rakata har
cikin falon Hajiya Fatee, yan aikin Hajiya Fatee suka fara gaisheta.

“Lafiya Kalau Ina Hajiya Fatee”

“Tana dakinta”

Hajiya Kaltume ta juya ta kalli Yasir.

“Bari na kirata ku gaisa”

“Okay”

Ya nufi kujera ya zauna, Hajiya Kaltume kuma ta nufi dakin Hajiya fatee ta tura
kofar ta shiga da sallama. Kuka ya hana Hajiya Fatee amsawa sai dagowa da ta yi ta
kalleta da idanuwanta da suka gama kumbura.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Hajiya Fatee abun har ya kai haka”

“Ya wuce, Hajiya Kaltume ina cikin bala'i da tashin hankali”

Hajiya Kaltume ta juya ta leka falon saitin da yasir yake zaune.

“Yasir ka tafi kawai idan zaka dawo daukata sai ku gaisa, amman fa da zarar na
kiraka ka zo da sauri”

“Toh Hajiya”

Ya tashi ya fice cike da ladabi. Sannan Hajiya Kaltume ta koma dakin ta zauna kusa
da kawarta da rabin kibar jikinta ta zube saboda tashin hankali.

“Wannan abu be yi dadi ba, yanzu miye abun yi?”

Hajiya Fatee ta share hawayenta ta kalli aminiyarta.

“Ban sani ba Hajiya Kaltume, wannan shi ne likita na uku da ya fada min haka”

“Hajiya Fatee duk laifinki, da tun farko kin yarda anje asibitin an duba lafiyarki
da duk be kai ga haka ba?”

“Haba Hajiya, ina zan yarda aje asibiti a fadawa ďana abun da mutanen nan suka min?
Tsoron kar ya kalleni da abin kuma kar bakinciki ya zauna masa a zuciya ya saka na
ki amincewa da zuwa asibitin, kuma ni ma na san idan har ya sani ba zan samu salama
ba”

Hajiya Kaltume ta rafka tagumi.

“Wallahi duk wannan Iyamin ce ta ja mana, ba zan tana yafe mata ba, ni kaina yanzu
sanadinta har tsoron fita nake”

“Ni yanzu ba ta Iyami nake ba Hajiya ta kaina nake, kar asirina ya tonu, ga ni ta
surukar da bata kaunata, ga makiyi babban tashin hankali kuma rashin auren nan, yau
shekara goma da rasuwar Alhaji me zan fadawa duniya idan abun nan ya fito da
shekaru na haka har da jikoki”

Hajiya Kaltume ta sauke ajiyar zuciya.

“Hajiya ko dai daurewa zamu akara yin allurar nan ne? Ko Allah zai saka abun ya
zube”

Hajiya Fatee ta dauki robar yawu ta tsargar da yawunta cikin ta aje ta kalli Hajiya
Kaltume.

“Likita nan fa ya fada min, ta farko ma da na auna arziki ne, da yanzu na wuce, ni
kadai na san azabar da na sha lokacin da aka min allurar nan kuma gashi bukata bata
biya ba, kuma cirewar sun ce ko na mutu ko na yi rai ne”

Hannu biyu Hajiya Kaltume ta dora saman kai ta fashe da kuka tana taya aminiyarta
alhini.

“Kai wayyo Allah wannan Iyami wannan Iyami Allah ya isar mana gareki, kin aure min
miji kin fitine ni yanzu kuma sanadin nan mun fada cikin bala'i, ni Wallahi ma rasa
ya zan yi da matar nan da yaranta, kin ga cikinta ya shiga wata na tara kenan wani
zata haifowa Alhaji, yayanta da suke gidan ma be hada kowa da su ba, birthday nan
da Hurriya ta yi sarkar zinari ta miliyoyan kudi yayi mata kyauta, ni da nake
matarsa be taba siya min ba, sarkar da Nafisa take ta kuri da ita yau Alhaji ya
siya irinta ya mallakawa Hurriya, ga birthday Hamad tafe waya san iya abun da zai
masa shi ma, kuma saboda ita yanzu ya budewa kofa kofar birthday, abun da da ya
hana”

Hajiya Fatee ta daki kirji.

“Sarka Hajiya? Lallai Iyami ba zata gama da duniya lafiya ba, ta mallake shi yanzu
ta bar gida ta bar muku ya ku yi kishi da ita”

“Hmm abun nan ya ishe ni, ai saboda na san kina cikin taki matsalar ne ya saka ban
kawo miki kukana ba, amman ciwon matar nan yana nan a kirjina, a yanzu bana da
burin da ya wuce na ga Alhaji ya fita lamarin yaran nan, kuma dukiyar da ya bata ta
lalace”

“Ba ke ba, ai ko ni ba zan iya yafewa Iyami ba Hajiya, sanadinta yara kanana
sana'in yayana suka daure mu a daji babu kalar wulakancin da ba su min ba, yanzu
kuma ga wani abun bakinciki ya sake biyo baya, ban san ya zan yi ba”

Ta karashe zancen tare da fashewa da kuka.

“Toh ni dai ina ganin abun da ya kamata kawai mu saka a nemo mana malamin nan ko
Allah zai saka mu dace”

Hajiya Fatee ta mata wani kallo galala.


“Waya zai koma a wannan dajin? Ko gawata ba za a kai ba”

“Aa ina fa? Ni ma ai ba zan yarda ba, ba komawa zamu yi ba nemansa zamu yi idan ya
so shi sai ya zo ya same mu”

“Ta ina? Duka wayoyin mu suka karbe fa, ba ni da number ba, kuma da aka yi welcome
din Sim din har yanzu be kira ni ba, waya sani ma ko shi ya turo a dauke mu?
Mutanen nan kauye nan fa ba su da kyau”

“Kai bana tunani haka, kin ga ni fa na ga kyau aikinsa domin shi kadai ne yayi min
aiki kuma aikin yayi yadda nake so har Iyami ta bar gidan nan, shekara nawa ina
kashe kudi a banza ban dace ba sai a gunsa, sa zaki yi a nema mana shi waya nuna
miki gurin Malamin”

“Wata kawata ce Salame”

“Toh ita zaki saka ta je ta dauko mana shi, sai mu saka gurin haduwa da shi ba dole
sai ya san gidan mu ba, mu gabatar masa da bukatanmu mu basa kudin aiki, daga nan
ma sai na tambaye shi ina aka kwana zancen aikin Iyami, ke kuma sai ki saka yayi
miki na wannan mugun abun da yake cikinki”

Kallon rashin fahimta Hajiya Fatee ta yi mata

“Ya danne miki shi mana, ba zai taba tashi ba har ki mutu, ko baki san ana haka ba?
Na Iyami ma so nake a danne shi kar ta haifa ma Alhaji mugun abu, dan na san duk
wayonta be wuce Alhaji ya mutu ta ci gado ba”

Hajiya Fatee ta kalleta wata rahma na saukar mata a ruhi, jin kamar ta samu mafitar
masifar da take ciki.

“Kuma kina ganin hakan zai yi?”

“Me zai hana? Ki dai ki zuba masa kudi kawai, ni ma kudin zan zuba masa, kuma a
hannun Alhaji zan karbe su, kudin sarkar zinarin da ya siyawa Hurriya da kudin da
ya bawa Iyami duk sai na fanshesu a hannunsa, yanzu ne za su gane sun yi kuskuren
taba mace kamar ni, kuma Wallahi sai na malleke Alhaji ko ta halin yaya, sai ya
dawo a tafi hannuna Iyami da ƴaƴanta sai sun ɗanɗana kuɗarsu, Iyami sai ta gane
kuskuren da ta aikata na aurar min miji, sai ta yi nadamar hada shimfida da Alhaji,
matsayin da ta taka a baya na tana Matar Alhaji ina Matar Alhaji sai na saka ta yi
nadamar haka... Ba ita ba har Nafisa sai na sake mata sabon karatu na goge mata
hadda. Dukansu sai sun dawo a tafin hannuna”

Ya daki tafin hannunta tana kashe ido alamar yanzu ta shiryawa rashin imani, da
kuma fada da Iyami da Momy.

________________

Hmmmmmm Allah yasa kuna hango abubuwan da nake hangowa 🤔

Tafiyar fa duk duka yanzu aka fara.... Ku daura ɗamara ku zage damtse domin domin
alkalinmin da zafinsa ya zo 😁

Kar a manta idan an karanta ayi sharing 🥰


☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

1️⃣4️⃣
4️⃣
1️⃣1️⃣
4️⃣

Namra ta dago ta dubi kofar shigowa falon tana amsa sallama, sai ta mike tsaye da
sauri tana kallon Captain da mamaki, zuwansa a yanzu ya bata mamaki tsabanin baya
da bata mamakin zuwansa domin ya saba zuwa gidan a duk lokacin aiki ya kawo shi ko
ziya, tana mamakin zuwansa ne kasa da wata uku da faruwar abun da ya fusata shi,
wato fasa masa tayun mota da Hamad yayi suke zaton Hajiya Kaltume ce ta saka aka
aikata haka. Ba kasafai yake sake zuwa gurin da aka bata masa rai ba, idan ma zai
sake komawa a gurin sai ya dauki lokaci mai tsawo har an manta da shi yake sake
zuwa, wannan ya saka duk wani makusancinsa da yake son alaka da shi ta daure ko da
iyayensa yake kokarin kiyaye duk wani abu da zai batawa dan gatan Ammy kuma ďa daya
tilo ga Alhaji Aliyu Turaki. Wata kila haduwar jinin da Allah ya saka tsakanin Momy
da ďan Yayanta ya wuce yayi mata haka. Fuska ba yabo ba fallasa ya shigo falon
hannayensa duka biyu suna bayansa.

“Sannu da zuwa Ya... Captain”

Tunawa da ta yi baya son ace masa Yaya ya saka ta kasa karasa sai ta kiranshi da
sunan da kowa yake kiransa.

“Yauwa hutawa kike?”

“Eh bari na kira Momy tana ciki”

Tana juyawa ya dakatar da ita.

“No Wait... Ina yarinyar nan take Namra?”

Ta juyo tana wara alamar bata fahimce wadda yake tambaya ba.

“Wata fara haka mai dan tsayi marar jiki, mai saka glasses”

“Oh Hurriya, tana bangaren Hajiya a kirata”

Ya daga mata kai, sai ta aje remote din hannunta ta nufi kofar fitar ta fice da
sauri, da mamaki da tunanin dalilin kiran Hurriya ta isa bangaren Hajiya Kaltume,
sai ta ci karo da Hurriya tana rike da tiyo tana watsawa motar Yasir ruwa, Hamad
kuma na ta kada kumfa.

“Hurriya”

“Uhmm”

Ta juyo ta kalleta.
“Wai ki zo ana kiranki Captain...”

“Waye Captain...?”

“Ina wani wadda na ganku tsaye a bakin kofar Momy har na dauko miki glashinki da ya
fashe? Kin tuna”

Hurriya ta yi shiru ta dan bata fuska, kuma ta kasa amsawa Namra da ta tuna ko ba
ta tuna ba.

“Wanda ya mareki?”

Hamad ya tambaya, Hurriya ta daga masa kai Namra ta zaro ido domin bata saka ran
marinta yayi ba, ta san dai akwai abun da yake faruwa.

“Au daman marinki yayi? Ikon Allah me kika masa?”

“Wucewa na zo yi ban gani ba muka yi karo shi ne ya mare ni har gilashina ya fashe”

“Ni kuma na fasa masa tayun mota duk biyu da wuka”

Namra ta rufe baki with mamaki. Hurriya ma masa kallon rashin jindadi fadar da yayi
a yanzu.

“Daman kai ka fasa tayun nan? An kusan yaki a gidan nan fa saboda an fasa tayun
Captain, Allah ya tsare ka Momy bata sani ba, da sai ka zama abun tausayi”

“Ni ina ruwana”

Ya fada yana turo baki.

“Captain akwai zafin zuciya ko shi zai iya maka hukunci babu ruwansa da alakarka a
gidan nan, to yanzu dai shi ya ce a kiraki”

Hurriya ta ake tiyon kasa ta nufi fanfon ta kashe sannan ta bi bayan Namra, Hamad
kuma ya cire hannayensa daga cikin kumfan da yake kadawa ya bi bayan Hurriya. Ita
dai bata san ta masa laifi a yanzu ba balle ta yi zaton mari ne ko cin mutumci, sai
idan kuma cewa za'ayi ta haifar masa da ciwon kirji saboda kanta ya bugi kirjinsa.
Namra ce ta fara shiga sannan Hurriya sai kuma Hamad dake bayanta. Yana tsaye a
gurin da Namra ta barshi sai dai wannan karon gefen kujerar da Namra ta tashi yake
kallo ma'ana kofar falon ta koma gefensa na dama sabanin dazun da ya bata baya.

“Gata nan”

Namra ta fada, sannan ta zauna Hurriya ta karaso inda yake ta tsaya gabansa ta
kalleshi sau daya ta sauke kai kasa, Hamad kuma yake tsaye kusa da kofar falon yana
kallon ya ga abun da za'ayi ma yar'uwarsa. Captain ya maido ta hannayensa gaba ya
mika mata box din da ke hannunsa da hannunsa na dama ba tare da ya ce komai ba. Ko
be fada mata ba, ta san box din glasse ne domin shi dabam yake ta ka ganshi kana
ganewa balle kuma ita da take 5&6 da glass. A hankali ta dago ta kalli fuskarsa
bayan ta kalli gilashin sannan ta kalli Hamad ya watsa mata harara duk ya bi ya
bata rai, domin har yanzu haushi Captain din yake ba shi, daman kuma shi be iya
tsana ba idan ya tsane ka sai Allah ke kasa ku sake shiri da shi. Captain ya
karkarata da kansa kadan ya kalli Hamad da sai a lokacin da ya san da shi tsaye a
gurin sai kuma ya kalli Hurriya. Ita ma ta kalleshi ta dauke kai ta nufi kofar fita
daga falon ba tare da ta ce masa Komai ba balle kuma har ta karba, sai da ta fara
ficewa sannan Hamad ya bi bayanta yaja kofar falon ya rufe. Captain ya matse box
din gilashin dake hannunsa da mugun karfi ya daga kansa sama ya rufe ido.
“Allah ya sassauta min kar na kashe yarinyar nan....”

‘Tab ka kasheta Wallahi kai ma sai an kashe ta dan gata be fi gata ba, ita ma yar
gatan banbanta ce’

Namra ta fada a ranta a fili kuma sai ta ce.

“Glasse ne?”

Ya sauke kan ya kalleta.

“Wuka ce”

“Gilashin da Appa yake siya mata mai kyau ne daga waje ake kawo mata”

Ta fada a zahiri a badini kuma sai ta ce.

‘Captain dai kamar ka fi kowa iya bakar magana’

Kamar ta san zai kara mata.

“Wannan a bula na dauko shi”

“Tambaya ce kawai, daman ai na san Hamad ba zai bari ta karba ba, amman ka ba ni
zan bata hakuri sai na bata daga baya”

Ya kai dayan hannunsa yana zagayen gilashin da shi.

“Waye Hamad?”

“Kanenta ne wanda ka ga ya tsaya jikin kofa har ta kalleshi, shi ne ya fasa maka
tayun mota saboda ka mareta, ni ma ban sani ba sai yanzu yake fada”

Murmushi yayi mai sauti, ya dago ya kalleta ya sake yin murmushi mai cike da
mamaki.

“Wow... Nice...”

“Haka ya kamata dan'uwa ya zama, mai kokarin kare yan'uwansa i like him”

Ya fada after yayi taking few seconds yana kallon wani bangare na falon, because he
know yayi missing wani part na shi da be taba samu ba, wato yan'uwa da suka hada
uwa ko uba ko ma uwa da uban gaba daya.

“Amman haka ba zai hana a hukunta shi ba, they have to pay for what they did”

Ya juya ya fice daga falon ba tare da ya nemi a kira masa Momy ba, daman kuma ba
dan ita ya zo ba wannan karon, ya zo ne domin baya Hurriya gilashin da ya siyo
Saudiya saboda ya fasa nata, and that slap da yayi mata ya tsaya masa after ya bar
gidan saboda lura da yayi da bata gani sai da gilashin kamar yadda Namra ta
tabbatar masa tun a wacan ranar. Namra ta san me yake nufi they instead of he, wato
Hurriya saboda ta ki karbar gilashin Hamad kuma saboda ya fasa masa tayun mota. Sai
da ta leka ta ga tashin motarsa sannan ta saki curtains din tana fadin.

“Ban da kai Captain ana kyauta dole ne, ko ni ce ai ba zan karba ba, ka yi zafin
hannu ba wani uzuri da an maka abu sai zafin zuciya”

Ta nufi upstairs, sai da ta fara leka dakin Momy ta ga har lokacin bachi take sai
ta ja mata kofar a hankali ta nufi dakinta.
HAJIYA KALTUME POV.

“Yanzu kina da number Salame?”

“Eh ina da ita, ai ko shekaran jiya ta zo gidan nan, har take min zancen Malamin ni
dai ban tanka ta ba, domin damuwata ta isheni kar na yi abun kunya”

“Kunya Hajiya fatee? Tofar da yawu, har abada ba zamu taba kunyar duniya ba lahirar
ma muna fatan nasara, saka number ki kirata ki ce ta turo miki number Malamin ko
kuma idan ta samu lokaci ta shigo sai ku yi magana”

Hajiya Kaltume na rufe baki Hajja Fatee ta dauki waya ta shiga laleben number
Salame. Knocking aka yi har sau biyu sannan Hajiya Fatee ta amsa.

“Waye?”

“Hajiya Yaron nan ne ya sake dawowa fa, kuma mai Baba mai gadi ya ce yayi yayi da
shi amman ya ki tafiya shi sai ya ganki”

Hajiya Fatee ta hanye wayar ta rafka tagumi.

“Oh wannan fitinanne yaro ba zai bar ni da abun da ya ishe ni ba”

“Waye haka?”

“Wallahi wani yaro ne na dauka aikin ba fulawa ruwa, ashe barawo, ni ban sani ba,
irin yaran nan yan sare sare, wata rana suka zo nemansa har da fasa mana gida aka
ayi, tun daga lokacin sai na sallame shi, amman yaron nan ya ki ya rabu da ni, duk
lokacin da wani abun ya same shi sai ya zo ya fada ko mai dadi ko marar dadi, ko
kuma ya ce ya zo gaishe ni, yanzu ya bi ya fitine ni yau sati biyu kullum sai ya zo
wai mahaifiyarsa bata da lafiya ni yake son gani”

“Ikon Allah toh ke Hajiya irin wadannan yaran ai suna da amfani wata rana”

“Hmmm baki san yadda suke fitinar mutum ba ne, ga su da shegen na ci idan sun ga
samu”

“Bari na yi magana da shi, ki kira Salame yanzu”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye tabur tabur ta fice daga dakin, Hajiya Fatee kuma ta
shiga kiran Salame da wayarta.

“Ina yake?”

Hajiya Kaltume ta tambayi one of masu yi ma Hajiya Fatee aiki da ta zo sanar da


Hajiya.

“Yana can gate”

“Muje na ganshi”

Mai aikin ta wuce gaba Hajiya ta sauko tana bin bayanta har suka fita falon suka
isa gate ta tambayi mai gadin ina yake.

“Yana waje Hajiya kullum sai ya zo kuma ita Hajiya ta ce kar a barshi ya shigo”
Ya bude mata karamar kofar gate din ta leka waje ta ganshi zaune daf da gate din, a
take gabanta ya yanke ya fadi domin ya tuna mata da lokacin da suke cikin daji
hannun yan ta'adda, ga fuskarsa duk tambo alamar ya sha sara har ya gaji, bakinsa
baki kirin ido kamar an daka tarugu tsabar ja, jiki a murda kamar gashin kansa,
kana ganinsa ka ga rikakken dan ta'adda.

“Kai ne kake neman Hajiya Fatee?”

Hajiya Kaltume ta tambaya cikin karfi hali domin zuciyarta har wani zillo take.

“Ni ne Allah ya taimakeki, Hajiya Wallahi ina cikin matsala ne, su kuma wadan nan
watsatsin masu aikin kullum na zo sai su hana ni shiga, ba dan ina ganin mutumcin
Hajiya Fatee ba da yanzu na farka cikin mai gadin nan Wallahi, sai dai Hajiya tana
da kima a idona kamar uwa take a gurina ba zan iya haka ba”

Magana yake da irin muryar mazan nan da shaye shaye ya gama canja kalar muryarsu ta
koma mai ban tsoro. Hajiya Kaltume ta yi murmushin karfin hali.

“Ka kyauta haka ake so ai, ya sunan ka?”

“Sunana Isiyaku, amman dai wasu kan ce min Danja yan sunanayen nan dai na zamani
Hajiya”

“Toh Amman me kake so gurin Hajiya?”

A take ya fara kuka kamar wani yaro ko wawa kukan da babu hawaye sai zallar
iskanci.

“Hajiya Gyatuma aka kwatar a asibiti, kuma ba ni da ko sisin na magani, ita Hajiya
Fatee ta sani ba na wani aiki bana sana'ar komai tun da na bar gidan nan ban sake
samun wani aikin ba, ina cikin matsala bana da gata sai Allah sai Hajiya Fatee so
nake ta taimaka min da kudin magani, kar gyatuma ta mutu Wallahi Allah akwai
matsala idan ta mutu ba a taimaka min ba, duk mai hannu a ciki sai na ci uwatar...”

Yana fada yana hada hannu biyu ya buga, Hajiya Kaltume ta dan ja baya sannan ta
kalli mai aikin ta ce.

“Zaki iya tafiya”

Sai da mai aikin ta yi nisa sannan ta taka kafarta ta fito daga cikin gidan ta taka
nesa da gate din yadda mai gadin ba zai ji abun da zata fada ba. Sannan ta tsaya ta
kalli Danja ta ce.

“Nawa ne kudin maganin?”

“Toh Hajiya dubu talatin ne, amman dai ko dubu biyu ko biyar aka taimaka min da su
duk taimako ne”

“Kana da account”

“Akwai account Hajiya amman bana da shi aka Wallahi, kwanyar ce mun sha miyar kuka,
daddawa duk ta kwashe basirar, tuwon dawa ma haka ake baza mana shi a ture, kai mun
ci wuya Wallahi ga talaucin nan har yanzu be bar mu ba”

Hajiya Kaltume ta yi dariya har lokacin tsoro be fice ta ba, domin muryarsa ma abar
tsoro ce balle kuma ka kalleshi.

“Kana da waya?”
Ya dan sosa kansa ya shafa aljihu.

“Wayar ce Hajiya ko an siya idan ka ji eh ya ne tana damun cikinka dole mu siyar mu


siye abinci, line ma dari da hansi na siyar da shi shekaranjiya”

“Toh yanzu idan ina son magana da kai za mu yi kenan?”

“Ki fada min gidanki kawai zan zo na sameki har dakinki”

“Aa ni da Hajiya Fatee duk ba mu gama warkewa daga damuwar da muka shiga ba, baka
san yan ta'adda suka kama mu ba?”

“Kai na ji Hajiya, zuwana talatin gidan nan sai ace min bata nan, wai wasu ne suka
kamata, da an fada min ba za a biya sisi ba zan karbota ni sai a ba ni kudin, akwai
mutanenmu fa masu harkar kuma ni Wallahi jan wuya ne, bana inda bana iya shiga,
karfe be fasa ni bundiga bata kama ni sai dai ayi min tambo, danjar nan da kika ji
ance Hajiya ni fa danja ne, uban fitina kuma bana tsoron kowa”

“Kai zaka iya aikata komai kenan Danja?”

“Zan iya komai Hajiya mun zubar da hannaye mun cire kafa, rai ma mun wulgar da shi
barzahu, Allah dai ya shirya mu kawai”

“Shiyasa Hajiya take tsoron ka, ni ma ina gudun na janyo ka jiki na jawa kaina
matsala”

“Kai... Kuturi”

Ya rike baki.

“Wai Hajja Fatee tsorona take? Ita din ai uwa ce ba za a mata komai ba, wani ma be
isa ya mata ba balle kuma ni, ba dan ita ba da yanzu na barar da hanjin masu aikin
nan nata, alkur'ane da yanzu ka ga hanta ya lilo shushushushushuuuuuuu”

Ya nuna yadda hantar zata rika raea idan ya sareta.

“Toh yanzu dai zan shiga gida, zan aiko mai aiki da number wayata idan ka samu waya
sai ka kira ni mu yi magana, amman dan Allah ka daina damun Hajiya Fatee da yawan
zuwa”

“An gama amman Hajiya yanzu akwai wani abu nan? Ina fatar ke ma kina da yan abubuwa
yan timatinmai eh... Eh.. Kin dai gane”

“Zan aiko mai number tare da kudin da zaka hau babur ka koma”

Tana fadin haka ta yi gaba tana nufi gate zata koma ciki, shi kuma ya bita da
kirari yana daga mata hannu.

“Chau chau chau chachachau lafiya lau ne Hajiya, Allah dai ya kara miki kwanciyar
hankali ya kara miki ƙiba kai kana ganin Hajiyar nan ka san akwai manyan kaya,
Allah ya kara sutura”

Cikin gidan Hajiya Kaltume ta koma ta shiga dakin Hajiya Fatee ta samu biro ta
mikawa Hajiya Fatee domin ita bata iya rubutun ba.

“Rubuta masa number ta a nan”

“Numberki kuma? Me ya faru? Karki jawa kanki matsala fa irin wadannan ba su jin
magana”

“Ke dai rubuta babu komai, ke na ke yi ma jihadin ai, wayo yake masa”

Hajiya Fatee ta karba ta rubuta mata number ta mika mata. Hajiya Kaltume ta bude
jakarta ta dauko 3k ta hade ta takardar ta fita falo ta bawa mai aikin ta umarce ta
da ta kai masa. Sannan ta juyo ta dawo dakin tana tambayar Hajiya Fatee ya aka
karkare da Salame.

“Na kirata na mata bayani, ta ce ai ya canja line saboda rufe masa wacan da masu
gidan line suka yi, amman yanzu zata turo min sabuwa numbersa kuma zata kira ta
masa bayani”

“Haka nake son ji, to yanzu ki kwnatar da hankali ki kira ki fada masa ya shirya
komai na sa ya zo garin nan zamu aika da mota a dauko shi a kawo mana har gida,
daga nan sai mu gabatar masa da matsakarmu”

“Amman kina ganin zai yarda ya zo?”

“Hajiya Fatee miye kudi ba zai yi ba? Muradi dai abashi kudi shi kuma ya biya mana
bukata kawai”

“Ni dai Allah yasa cikin nan ya tausu, idan ba haka na zan shiga uku ga shegiyar
suruka zata ji dadi”

“Komai zai wuce Hajiya Fatee ki kwanatar da hankali”

Cewar Hajiya Kaltume ga aminiyarta tana murmushi.

IYAMI POV. .

“Iyami ba a zama haka, ke kanki kin san mijinki yana sonki, ga yaya yanzu kuma ga
cikin nan da kika shiga watan haihuwa, kamata yayi ki nemi taimako idan ma wani
asirin aka yi masa aka rabaku a karya shi, ki koma dakinki bana son ki haihu a gida
Wallahi”

Amma ta yunkura da katon cikinta ta tashi zaune daker tana kallon Hindu dake
maganar.

“Hindu, Wallahi ban taba yi ba, su kansu da suke ganin kamar asiri na yi ma Alhaji
yake ta so na ko na malleke shi, ban taba bada naira biyar na ce a mallake min
Alhaji ba, tsantsar biyayya ne kawai da kawar da kai da kuma jin maganar duk abun
da ya fada, ni yanzu ko zaki dora wuka a wuyana ba zan iya fada miki sunan Malami
daya da na sani ba a garin nan, ban taba yi ba, Gwaggo ma bata taba ta yi ba mu ba
mu da kowa sai Allah”

“Na sani, to ai tambaya ake kin ga har na tsarin jikinki sai ki sha kuma ki bawa
yayanki, domin su ma ba barinsu zata yi ba”

“Ni dai ba zan iya ba, na kai kukana ga Allah shi zai min magana, ko yanzu ai ba
yadda suke so suka samu ba, duk wata sai ya aiko min da abinci da kudi saboda cikin
nan, yanzu kuma kina ganin yadda aka cika harabar gidan nan da itace saboda na
shiga watan haihuwar, na san idan ra'ayinsu za a bi ba zasu so haka ba, yarana kuma
idan ya auna lokaci ya kan aiko da su su gan ni na gansu, an rabu ne kawai amman
kamar ana tare, idan Allah yayi zan koma sai ki ga na koma kamar yadda ban saka ran
auren Alhaji ba Allah yayi kuma aka yi auren”
“Toh Allah yasa haka shi ya fi alheri, amman dai da kin tafi ba a san inda za a
dace ba”

“Allah ya hada mu da dacewar”

“Ameen”

Ta amsa ba dan ta jidadin yadda Iyami ta ki amincewa da zuwan ba.


☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Pease ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy

1️⃣5️⃣
5️⃣
1️⃣1️⃣
5️⃣

Salame na turo number Malamin Hajiya Fatee ta kira shi a waya, suka gaisa ta fada
masa abubuwan da suka faru ya jajanta mata, ya kara mata da cewar shi ma layinsa
aka rufe shiyasa bata ji shi ba. Hajiya Kaltume ya karba suka gaisa sannan ta dora
masa da banin abun da ya sami Hajiya Fatee, daga karshe suka yanke ranar da zai
shigo garin. Sannan Hajiya Fatee ta iya fita dakinta ta samu ruwan tea ta sha domin
bata iya cin komai. Hajiya Katume bata jima a gidan ba Fadeel ya shigo gaishe da
mahaifiyar, da zai fita Hajiya Kaltume ta bukaci ya sauke ta gida.

*** *** ***

Ba kadan ran Momy ya ba ce ba, jin cewar Captain ya zo gidan tana bachi, kuma ya
fita da bacin rai saboda Hurriya.

“Oh to wai miye na siya mata gilashin ma?”

Namra ta aje spoon din hannunta.

“To nidai ranar da ya zo last na ganta da shi cirko cirko, gilashinta a kasa tana
lalabe to shi ne yau take fada min ai marinta yayi saboda sun yi karo”

“Ai gara da mareta ma, yarinyar nan bata da hankali, sannan yanzu ya zo ta ki ta
karbi box din wata kila ba zai sake dawowa gidan nan ba kuma, ta ja min ya fara
fushi da ni kenan”

“Shi ma fa Captain din nan ya cika zuciya ga zafin hannu, amman dai bata kyauta ba
da bata karba ba”

“Bar yar iska bata san su waye iyayensa ba ne shiyasa, shi ma dai miye na kawo mata
glass ko makancewa ta yi iya ruwansa”

“Kila ya ga be kyauta ba, ko kuma...”

Momy ta kalleta da duba kyama.

“Ko kuma me? Allah ya kiyaye ai ko mata sun kare duniya Captain ba zai yi komai da
wannan yar tatsitsiyar yarinyar na duka ma nawa take shekaranjiya ta yi 16yrs fa,
kuma shi da yake da matar da zai aura”
“Toh ba sai idan anyi auren ba, wannan me bakar zuciyar? Ba kowa ce zata iya zama
da shi ba”

“Ai ko fasawa aka yi sai dai ya aureki, daman Hajiya Turai ta so a hada wannan
zumunci shi din ne ya ki, kuma kin san basa masa dole ”

“Ni”

Namra ta nuna kanta domin bata taba jin makamacin haka daga bakin Momy ba.

“Ke fa mun sha yin maganar da Hajiya Turai ai, amman shi Jameel din ne be yarda ba,
yanzu dai ya samu wadda yake so an huta”

Namra bata ce komai ba ta maida idonta kan abincin da take ci tana motsa shi a
hankali kamar mai tunani. Momy kuma ta tashi daga dinning din tana ta masifa saboda
Namra bata tasheta daga bacci ba.

“Kiransa zan yi yanzu Allah yasa ya daga, kar wannan yar filfilwar ta jazamin
masifa ni Nafisa”

Nan ma Namra bata ce komai b ta cigaba da motsa abinci tana tauna wanda yake
bakinta ta kasa hadewa sai tunani take. Kamin ta juyo ta kalli falon da aka bude,
Hurriya ce ta shigo kanta ba dankwali rabin kan nata a tsire.

“Yi sauri ki dauki abun da zaki dauka ki fice kamin Momy ta fito, dan na san sai ta
miki fadan kin karbar box din da Captain ya baki”

“Abinci zan zuba”

Ta nuna abinci tana kallon stairs gabanta sai tsananta faduwa yake.

“Zo ki zuba”

Ta nufi dinning din da sauri ta dauki plate ta zuba abincin mutum biyu ita da Hamad
ta saka naman kaza a sama ta dauki spoon biyu ta saka.

“Ke da Hamad zaku ci?”

“Eh”

“Dazun shi ya hana ki karbar glass din ko?”

“Na ga ya bata rai yana hararata, na san idan na karna zai iya min masifa kuma yayi
fada ni, ko ya dukeni”

“Ke dai Hamad ya raina ki ya maida ke kamar kanwarsa, ko dan ya ganshi babba ke
kuma ba ki ba”

Hurriya ta yi dariya mai sauti ta shiga Kitchen ta dauko tray ta dora ruwa da lemu
a kai sannan ta fito ta dauki plate din abincin ta dora a tray ta dauka ta fice da
sauri. A harabar Apartment din Hajiya Kaltume ta dawo ta zauna a balcony kusa da
Hamad ta aje tray.

“Hamad zo mu ci abinci”

Ya kalli abinci sai ya bata rai.

“Waya ce ki hade? Waye zai ci abinci da ke to?”


“To ai ni ina sauri ne, Yaya Namra ta ce Momy nemana take zata min fada saboda ban
karbi abun da bakonta ya ba ni ba”

“Toh ina ruwana ki je ki zuba wani”

Ya saka hannu ya dauke abincin da ba zai iya cinyewa shi kadai ba ta dora a
cinyarsa.

“Idan ba zaka ci da ni ba, ba sai ka je ka debo na ka ba?”

“Ba zan ce ba, ni ki daina ba ni umarni”

“Wannan dai nawa ne ka ba ni abinci na Hamad”

Yayi mata kunne ne shege yana ta cin abinci ko kallonta be yi ba. Har ta tashi zata
tafi debar wani sai kuma wata zuciyar tace mata Momy na nan falo, sai ta koma ta
zauna ta dauki lemun ta sha tana ta kallonsa yana cin abinci. Ita ma dai kamar
mantawa ta yi Hamad be cin abinci da kowa kuma be cin ragin kowa har da na Appansa
da na Amma. Hakura ta yi ta saka masa ido ta can kuma ta ji ba zata iya ba tunawa
da ta yi baya son gashi idan yana cin abinci sai ta cigaba da sifar kan tana
kallonsa wai ko zai ji kyama ya aje abinci. Instead of yayi haka sai ya kifar da
plate din ya riko gashin kan nata a daidai lokacin da Mota ta faka harabar Hajiya
Kaltume. Da wani irin karfi yake fisgar gashi da karfi bata san lokacin da ta fara
ihu tana rike hannunsa ba. Da sauri Fadeel ya bude motar be ko tsaya kashewa ba ya
fito ya nufi inda suke daker ya banbanre hannun Hamad Hurriya ta koma bayansa da
sauri tana kuka.

“Kai wannan ai sai ka tsinke mata gashin ka rage mata sadaki, miya hada ku?”

Hurriya bata iya magana saboda kuka, Hamad kuma ba gwanin maida magana ba ne daman
sai cika yake kamar wani zaki. Hajiya Kaltume tana kawowa kusa da su ta ce

“Ai haka suke, uwa daya uba daya amman baya raga mata, basa zaman lafiya kamar
Annabi da Kahiri suke”

Cikin mamaki Fadeel ya kalli Hamad.

“Wai kanwarsa ce yake mata wannan jan gashi haka?”

“Ita ce yayar ai, dan ka ganshi da girma shi ne kanen ai, baya ragawa kowa a gidan”

Hamad ya juyo yana watsawa hara Hajiya Kaltume dake korawa Fadeel bayani saboda ta
tabo shi tun da ta ce be ragama kowa.

“Idan ba kai ba, wake fada da mata? Ba yayarka ba ce?”

Ya juyo ya kalli Hurriya da ta boya bayansa.

“Ke kuma ki rika kiyaye, yi hakuri ki daina zama babu dankwali ba kyau”

“Ai Allah yasa ma aljannu da ifiritai da shaidan duk su tattara su shige a cikin
kan nata, ita ma ai ba karamar marar jin magana ba ce”

Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume dake fadar haka tare da yin gaba da bar su a gurin.
Ta share hawayenta ta kalli Hamad sannan ta kalli Fadeel.

“Ina wuni”
Dariya yayi.

“Lafiya Kalau, Allah ya tsare gaba Hurera ko?”

“Hurriya”

Ta gyara masa.

“Yeah ki rufe kanki”

“Toh”

Ya juya ta sauka balcony din ya nufi motarsa dake kunne har lokacin sai da ya shiga
motar daga mata hannu sai kallonta yake sannan yayi reverse ya fice.

Two Week Later....

Hajiya Fatee ta gyara zama ta kalli kawarta kamin ta kalli Malamin da suka sauka a
garage din gidan.

“To yanzu Malam akwai yadda za'ayi a danne cikin nan kar ya bayyana? Kuma wannan
tofe tofen yawun da kin cin abinci da nake ga kasala duk na daina shi?”

Malamin dake sanye da babbar riga ya kalli Hajiya Fatee yana murmushi.

“Za'a iya sosai kowa, ba yau na saba ba, za a iya danne cikin nan har tsawon
shekarun da kike so”

“Alhamdulillah, ina son a danne min shi har nan da shekara dari, na san dai ba zan
yi shekara dari a duniya ba”

“Ko kuma nan da lokacin da zaki yi aure ba, Hajiya yadda kike da surar nan Maa Shaa
Allah, ai sai idan mutum be samu dama ba, shekarunki ba ba za a ce kin yi ba, ai na
san ba za a rasa namema ba ko?”

Maganar yake yana dariya kamar wata abokiyar wasarsa.

“Aa kai aure kuma? Wake ta aure yanzu? Aa mun bar wa yara, ni dai yanzu bukatata a
fara danne cikinki, idan an samu nasara hakan yayi sai a shiga yi Farraqu tsakanin
yaron nan Fadeel da Matarsa Afrah domin ina kwana da bakincikinta a kullum Wallahi”

.“Babu Matsala Hajiya, za a danne ciki, matukar ba a daga dutsen da zamu saka layar
mu rufe ba, cikin nan ba zai taba tashi ba har abada, amman fa zaki zuba kudi kam”

“Karka damu zan biya ka ko nawa ne, ammam dan Allah a saka dutsen a inda ba za a
iya dagawa ba”

“Aljannu za mu saka su yi aikin, karki damu”

Hajiya Fatee ta kalli Kaltume suka yi murmushin jindadi sannan Hajiya Kaltume ta
kora da nata bayanin.

“To ni Malam na ji shiru, kasan na baka kudi akan za ayi ma Iyami aiki ina son
komai nata ya lalace amman har yanzu ba labari, kuma ni yanzu so nake a mallake min
kowa a gidan nan daga mijina har Nafisa ikon kowa ya dawo karkashina, ina son
Alhaji ya zama be iya aiwatar da komai sai abun da na fada masa, kuma ina son a
shiga tsakaninsa da yaran nan, ya maida su banza a cire masa su a rai, ya ji baya
bukatar ganinsu ma, domin na ji yana zancen fitar da su waje karatu, kuma ko be
fitar da su ba, ita wannan da take da kokari na san gwanati ko wasu za su iya kaita
waje karatu, so nake a lalata karatun nata, kai ni duk wani abu da zai saka Iyami
farinciki bana sonshi a toshe komai Malam”

“Hajiya, aiki ai mun aiwatar jefa muka mata kuma yana nan yana tafiya kin san jifa
wani lokacin tana dauka lokaci kamin ta isa, amman kuma da zarar ta isa zaki sha
mamaki ba dan karami ba, sai kin tabbatar da ba ki min biyan banza ba, mijinki kuma
zaki mallake shi a hannu, sai dai wannan Nafisa kishiyar taki fitinanniyar mace ce
akwai yan ƙwanƙwanmai a kanta, kin san mai yawan masifa da mai addu'a asiri be cika
saurin kama su ba, amman zamu gwada”

“A gwada Malam zan biya ko nawa ne karka ji haufi”

Malam ya san washe baki. “To Mallada ai mu haka muke so”

Hajiya Fatee ta ce.

“Toh ni Malam ya za'ayi na gane idan cikin ya dannu?”

“Idan na yi aiki, zaki ji motsi sosai a cikinki idan motsin be daina ba har safe,
to cikin ne dannu ba wata kila sai mun sake yi, idan kuma kin ji motsin kadan to
aiki yayi kuma zaki daina duk wasu dabi'u da kike na masu ciki, cikin kwana biyu”

“Alhamdulillah, ni da zaka cire cikin ma ni ka dauki cikin na bar maka, ko ina da


aure me zan yi da mugun iri? Balle kuma an kwana biyu har na kai ga jikoki”

“Komai zai wuce Hajiya karki samu damuwa”

A ranar da farinciki Hajiya Kaltume ta dawo gida, saboda ta samu fadawa bokanta
abun da take so kuma ya tabbatar mata da zai iya. Wani karin abun farincikin ma sai
da babbar yarta Mace mai bin Yasir wato Umm Kaltoon da ake ma inkiya da Maamata
saboda sunan Hajiya Kaltume mata albishir da mai cewar mai son ta zai zo ya gaishe
da Hajiya da Appanta sai Hajiya ta rasa ina zata saka kanta dan dadi, daga ita har
Hajiya Fatee sun kwana da farinciki a daren kowa da bukatarsa da kuma burinsa,
Hajiya Fatee bata da burin da ya wuce a danne cikin nan kuma a raba Fadeel da
matarsa Afrah saboda ta tsokane mata ido.

Washe gari...

A tare da Hamad Hurriya ta fito bangaren Momy da far'arta tana hira da Hamad, kai
ka rantse ba sa fada da juna labari take ba shi na wata class mate dinta da ya sani
sai dariya yake. Sai da suka fara zuwa gurin Appa suka karbi na na su lemun da
Chocolate Hurriya ta masa godiya, sannan suka nufi box din dake kai su makaranta
suka shiga. A makarantar ma sai suka wuni kamar ba su ba, daman tare suke breakfast
amman kowa da abincinsa dabam, a ranar duk abun da Hamad ya siya sai ya iskota har
cikin ajinsu ya bata, kasancewar ajin maza dabam na mata dabam. Misalin karfe daya
da rabi suka tashi suka tafi Masallaci suka yi sallah sannan suka tsaya jiran
direbansu dake zuwa karfe biyu daukarsu gaba dayansu yan gidan. Biyu da mintuna ya
iso suka shiga box Hurriya tana can baya Hamad kuma yana a inda ya saba zama, wato
front seat babu mai zama a gurin sai shi kuma baya zama da kowa sai shi kadai.
Kilometers kadan ne tsakaninsu da Family house dinsu wata bakar motar ta shiga
gabansu ta tara musu har sai da direbansu ya tsaya gashi gurin babu mota ni motoci
ma ba kasafai fa, shi ma direban yana biyo hanyar ne saboda ta fi saurin kawo su
gida.

“Malam baka gani ne?”


Ya fada cikin tsawa ganin yadda yake masa ganganci kamar ba akan titi suke ba. Bude
motar aka yi wasu maza hudu suka fito fuskarsu a rufe biyu daga cikinsu na rike da
bindiga suka bude ma direban da tuni ya fara salati ya fito Hamad ma ya bude ya
fito jikinsa na rawa suka sa ya zagayo gurin direban sannan suka bude gambun bus
din.

“Kowa ya fito”

Kowa ya fito cikinsu na rawa suna ihu.

“Ku yi shiru ko na halbe mutum yanzu”

Dayan ya fada sannan biyun da ba sa rike da makami suka iso gurin dayan ya rika
Hurriya dayan kuma ya rika Ruma suka fara jansu zuwa motar. Hamad ya fashe da kuka
sosai yayi saurin riko Hijabin Hurriya da ita ma kukan take, kamin ta kai bakinta
ta gantsawa wanda ya rike mugun cizo a hannu, aiko ba shiri ya sake ta sai ta ranta
ana kare, abun ka da marar jiki kamin dayan ya rikota ta yi nisa, sai yayi wuf ya
cafke Hamad dake kokarin guduwa, suka dauke shi tare da Ruma sai motarsu. Suka
shiga da sauri suka fisgi motar sannan Salma da Khairi suka fara ihu tare da Namra
suna kuka, Hurriya kam tun da ta sa gaba bata dawo ba sai da direban ya wasu mutane
da suka tsaya bayan bata garin sun gudu suka bi sawunta, sai suka same ta tsakanin
wani gida da kwararo ta duke a gurin ta runtse idon ta saka hannayensa ta danne
kunnuwanta.

“Hurriya”

Ta razana ta bude ido jikinta da zuciyarta na rawa, gilashinta ya fadi gurin gudun
da dake, shiga kwararon ma da ganinta dishe-dishe ta shiga lalabe ya taimka mata,
shi ne silar tsayarwa a gurin ma, domin da tana ganin hanya da kyau ba zata kusa ba
guduwa zata yi. Jin muryar direbansu ne ya saka ta fashe da kuka, tana lalabensa
shi ya rikota yana matsar kwalla suka fito gurin. Kin yarda ta yi su koma gurin
saboda tsoro sai da direban ya janyo motar ya kawo gurin sannan ta yarda zata
shiga.

“Ina Hamad?”

Ta tambaya yana taimaka mata ta hau bus din har lokacin kowa kuka yake, ita kuwa
bata ji kukan dan'uwanta ba kuma bata ji muryarsa ba.

“Sun tafi da shi”

A take ta saki hannun direban ta yi shiruuuuu kamin ta fara haki.

“Wayyo Allah na Hamad”

Ta dora hannu akai ta fadi a gurin ta fashe da kuka mai karfi.

______________________

Masu karatu shin suwaye wadannan mutanen da suka dauki Hamad?


Me suke so? Za su dawo da shi ko kuma yaya?
Anya Hajiya Kaltume da Hajiya Fatee za su nasara akan kudurinsu?
Wai ni kam me Afrah ta yi ma Hajiya Fatee ne ta tsane ta har take neman raba
aurenta da danta? Anya ana samun uwar mijin dake neman raba auren danta ta hanyar
asiri?
Anya asirin da Hajiya Kaltume ta saka aka yi ma Iyami akan karta sake aure zai yi
kuwa? Amma zata dawo gidan mijinta Appa ko kuma wani auren zata yi ko kuma dai ba
zata auru ba kamar yadda Hajiya Kaltume take fata?
Waye wannan Captain din?
Waye Wannan Fadeel din?
Anya Momy zata daina halinta na kyamar Iyami da yayanta kuwa?
Akwai tsabtataciyar Soyayya a cikin littafin mai taba zuciya ta zauna a ruhi, ku
dai kun san ba mu fara komai ba. Kuma da yardar Allah ba zan ba ku kunya ba. 😀

Duk amsoshin wannan tambayar tana nan ƙumshe a cikin littafi na biyu da zamu fara
ranar Litanin mai zuwa In Sha Allah. Sai dai shi Book two din ba free ba ne na kudi
akan 500 only.

If you want subscribe biya 500 to

2451879008
Zenith Bank
Hadiza Abubakar

Sai ku turo shaidar biyan ta wannan number 08036126660

Ƴan Nijar kuma za su turo katin Zain ko Orange na 500 ta wannan number 08036126660.

Za ku iya bibiyar Litfafin nan a Arewabooks ga wadanda basa ra'ayin karantawa a


Whatsapp. A username dina @khadeejacandy ko kuma ku yi searching book din Hurriya.

Sai mun hada ku a Paid Group Real Masoya masu Patronizing dina a ko da yaushe.🥰
Ku huta lafiya, Allah ya bawa masu niyar siya kudin biya. 🤲
https://www.arewabooks.com/chapter?id=653656a358cd413f0dc70b74

Kamin direban ya isa gida duk wanda ke cikin motar ya dauka Hurriya shudewa zata
yi, saboda kukan da take yana yin sama da nufashinta kamar nunfashin zai fice daga
jikinta gaba daya. Namra ce take rike da ita tana kuka tana bata hakuri.

“Yi Hakuri Hurriya In Sha Allah zai dawo lafiya Allah zai tsare su”

Hurriya bata iya furta komai, gashin idon nata ya rufe gaba daya saboda kukan
hawayen ya hanata ganin dishe-dishe ma da take gani idan babu gilashi a idonta.
Direban na fakawa Salma da Khairi suka fita suna kuka suka nufi bangaren Hajiya
Kaltume suna kuka, Namra kuma ta tsaya ta riko Hurriya suka fito.

“Bana ganin komai Yaya Namra idon ya rufe gaba daya... Karki bar ni nan dan Allah
tsoro nake ji... Kira min Yaya Yasir ko ki kaini gurin Amma ko ki kira min Appa na
dan Allah”

Tana maganar muryarta na rawa saboda numfashim da ya sarke ta. Ta san a gurin dayan
su ne kadai zata yi kukanta ta more kuma ta fada musu abun da ya faruwa. Kowane ďa
ko ƴa idan abun farinciki ko kishiyarsa ya same shi guduwa yake gurin uwarsa, sai
dai ita a yau bata da wannan gatan, ba dan mahaifiyarta bata raye ba sai dan bata
tare da ubanta, bata taba sanin zafin rashin Amma a gidan ba sai yau, ko wane ďa
yana bukatar uwa a kusa da shi balle kuma ita da take da lalaurar ido. Dukawa ta yi
a gurin ta dora duka hannayenta biyu a kai ta kwalla ihu da kukam muryarta tana
kuka har sai da duk wanda ke harabar gidan hankalinsa ya dawo kanta.
“Wayyo Amma ma, Amma..... Amma... Amma... Ke..... Amma na”

Namra ta yi saurin rika hannunta tana kuka.

“Hurriya ba gani nan ba, ta zo muje ciki Momy tana nan ai”

Ta fisge hannunta, sanin kanta ne daga Momy har Hajiya Kaltume babu wanda ta isa ta
jingina a cikinsa ta yi kuka, domin ba su dauke ta kamar sauran ƴaƴansu ba.

“Kira min Yayana kira Yayana”

Domin karanta labarin ziyarci shafin dake sama na arewabooks @Khadeejacandy ko kuma
ku yi searching din Hurriya.

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza
Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣

Kamin direban ya isa gida duk wanda ke cikin motar ya dauka Hurriya shudewa zata
yi, saboda kukan da take yana yin sama da nufashinta kamar nunfashin zai fice daga
jikinta gaba daya. Namra ce take rike da ita tana kuka tana bata hakuri.

“Yi Hakuri Hurriya In Sha Allah zai dawo lafiya Allah zai tsare su”

Hurriya bata iya furta komai, gashin idon nata ya rufe gaba daya saboda kukan
hawayen ya hanata ganin dishe-dishe ma da take gani idan babu gilashi a idonta.
Direban na fakawa Salma da Khairi suka fita suna kuka suka nufi bangaren Hajiya
Kaltume suna kuka, Namra kuma ta tsaya ta riko Hurriya suka fito.

“Bana ganin komai Yaya Namra idon ya rufe gaba daya... Karki bar ni nan dan Allah
tsoro nake ji... Kira min Yaya Yasir ko ki kaini gurin Amma ko ki kira min Appa na
dan Allah”

Tana maganar muryarta na rawa saboda numfashim da ya sarke ta. Ta san a gurin dayan
su ne kadai zata yi kukanta ta more kuma ta fada musu abun da ya faruwa. Kowane ďa
ko ƴa idan abun farinciki ko kishiyarsa ya same shi guduwa yake gurin uwarsa, sai
dai ita a yau bata da wannan gatan, ba dan mahaifiyarta bata raye ba sai dan bata
tare da ubanta, bata taba sanin zafin rashin Amma a gidan ba sai yau, ko wane ďa
yana bukatar uwa a kusa da shi balle kuma ita da take da lalaurar ido. Dukawa ta yi
a gurin ta dora duka hannayenta biyu a kai ta kwalla ihu da kukam muryarta tana
kuka har sai da duk wanda ke harabar gidan hankalinsa ya dawo kanta.

“Wayyo Amma ma, Amma..... Amma... Amma... Ke..... Amma na”

Namra ta yi saurin rika hannunta tana kuka.

“Hurriya ba gani nan ba, ta zo muje ciki Momy tana nan ai”

Ta fisge hannunta, sanin kanta ne daga Momy har Hajiya Kaltume babu wanda ta isa ta
jingina a cikinsa ta yi kuka, domin ba su dauke ta kamar sauran ƴaƴansu ba.
“Kira min Yayana kira Yayana”

Namra na cira kafa da zimmar tafiya kiran Yasir sai ta hangoshi ya fito da saurinsa
ya nufo inda yake.

“Hurriya”

Hurriya na jin muryarsa ta mike tsaye da sauri ta fara lalaben inda zata ganshi.

“Yayana Yayana Yayana”

Kusan duk wanda ke tsaye yana kallonta sai da ya tausaya mata, domin lalurar rashin
gani babbar matsala ce. (Alhamdulillah da kyautar Allah, if you can read this ku
gode Allah, ba zabinku ba ne, kyautar Allah ce, and don't forget littafin na kudi
ne idan kika karanta baki biya ba, ko kika min sharing na barki da Allah)

Yasir na isowa ya rika hannunta dake ta rawa take da fatar bakinta.

“Yayana dan Allah ka kai ni gurin Amma... Dan Allah..”

Without second thought yaja hannunta ya karbi key hannun dayan direban da ya aje
Hajiya Kaltume few minutes before the incident happen. Ya bude motar Namra bata
kara jin tausayinta ba sai da ta ga yadda take lalaben motar zata shiga, Yaisr ya
taimaka mata ya saka ta a back seat sannan ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya
murza key ya juya motar cikin tashin hankali, ba dan yana namiji ba da tuni shi ma
ya fashe da kukan kamar yadda kanensa da mahaifiyarsa suke kukan. Shiru Hurriya ta
yi a cikin motar domin bata ganin komai sai duhu zucuyarta kuma ta cika fa tsoron
abun da ya faru. A harabar gate din gidan Yasir ya faka motar sannan ya budr ya
fito da Hurriya. Sai da ya daga gate din gidan sai kuma ya ji ba zai iya shiga ciki
ba domin ba zai iya zama mutum ya farko da ya labartawa Amma labarin an sace danta
ba, ya san idan ya shiga gidan ta ga yarta a wannan halin sai ta tambaye shi shi
kuma ba zai iya mata karya ba. Haka kuma ba zai iya barin Hurriya ta shiga cikin
gidan ita kadai ba a wannan yanayin.

“Hurriya ko dai ki hakura mu koma? Ba zan iya shiga cikin gidan nan ba, bana son na
daga hankalin Amma a yanzu”

Tana jin haka sai ta saka dayan hannunta ta kwance hannunsa dake rike da nata.

“Tafi zan.... Iya... Shiga... Daga... Nan”

Be san bata gani gaba daya ba, a zatonsa tana gani dishe-dishe kamar da, dan haka
be musa mata ba ya bude mata gate ta lalaba ta shiga, ya maida kofar ya rufe sannan
ya koma cikin motar ya fice daga unguwar. Hannu Hurriya ta mika tana lalaba hanya,
tare da amfani da zuciyarta tana ayyana yadda hanyar take a lokacin da take gani.

“Ke Hurriya...”

Ta ji muryar Rukayya sai wani sanyi ya ziyarceta. Ta karaso kusa da ita ta rika
hannunta.

“Waya kawo ki? Mun ji an bude kofar gate ba mu ga an shigo ba shiyasa na fito na
duba”

“Yaya Yasir ne ya kawo ni, ya tafi Mama Rukayya kai ni gurin Amma na”

“Me ya same ki Hurriya?”


“Kai ni gurin Amma please, bana gani yanzu bana iya ganin komai sai hudu, gaba daya
idon ya rufe, na daina gani dishe-dishen ma”

“Innalillahi”

Rukayya ta fada tare da jan hannunta suka shiga ciki, Amman dake zaune dakin Gwaggo
tana kwadon zogale ta aje kwanon zogalen ta yunkura da cikinta wata tara ta mike
tsaye da sauri ganin Hurriya da hawaye a fuska kacha-kacha har ya bata gaban
hijabinta, gata sanye da uniform din makaranta da bata cire ba kuma babu gilashi a
idonta.

“Hurriya me ya same ki?”

Kunne da jikin da yayi kewar uwa ne kadai zai iya fahimtar yadda ruhu yake ji idan
ya ji ko yayi arba da uwa.

“Amma ina kike?”

Ta saki hannun Rukayya ta fara lalaben inda take jin muryar Amma. Amma ta mika
hannu ta rikota sai Hurriya ta rumgume ta ta kwanta jikinta tana wani irin kuka da
ya saka Amma ta kasa rike kanta ita ta fashe da kuka.

“Me ya faru Hurtiya? Me ya same ki? Waya kawo ki? Me ya samu idon naki ina
gilashinki”

Har Hurriya ta bude baki ta yi magana, zancen da Yasir yayi a waje ya fado mata a
rai. Shi ma kenan ya ce ba zai iya sanar da Amma ba balle kuma ita da take yarta.
Kamar an saka allura da zare an dinki bakin Hurriya haka ta zama, ta kasa furta
komai kuma ma sai ya koma mata cikin zuciya hawaye kawai take ita yi.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Amma ta furta gabanta na bugawa da karfi. Ta san ba lafiya zata kawo yarta a irin
wannan yanayin ba, kuma gashi ta kasa fadar komai sai rumgume ta take kamar zata
shige jikinta.

“Hurriya yi a hankali mana, kin san akwai kanenki a jikinta, ko kuma ki zo ni na


rumgume ki idan rumgumar kike so”

Gwaggo ta fada, sai Hurriya ta girgiza kai tana kara kankame Amma.

“Hurriya dukanki aka yi?”

Ta girgiza kai.

“Wani abu aka watsa miki a ido?”

Ta girgiza kai.

“Fada kika yi da wani?”

Ta girgiza kai.

“Dan Allah ki bude baki ki yi magana mana minene? Ko dai fada kika yi da Hamad? Na
san zai iya cewa yayi miki mugun duka saboda bana gidan?”

Maganar da Amma ta yi ta Hamad ta saka Hurriya fashewa da sabon kuka.

“Yasir ya kawo ta, ta fa yi magana dazun yanzu ne dai ta kasa cewa komai”
“Wata kila fadan ta yi da Hamad shiyasa ta kasa fada tana tsoron kar na yi masa
fada ya kara mata”

Zuciyar Amma ta fi aminta da fada suka yi da Hamad shi yasa har ta furta hakan,
ganin Hurriya ta fashe fa kuka a lokacin da ta ambace shi.

“Kai Hamad yana da matsala Wallahi sai ace baka iya zaman lafiya fa yan'uwarka, ko
tausayinta baya ji”

Rukayya ta fada. Sai Gwaggo ta ce.

“Kusan duk mabiyi da mabiyi haka ake, ba kowa ke shiri da juna ba”

“Amman dai shi nashi yayi yawa”

Amma dai ta yi shiru tana ta saurare numfashin Hurriyya dake fita da karfi..

FAMILY HOUSE...

A rikice Appa ya fito motar tun kamin direban sa ya gama fakin, ya nufi hanyar
Falon Hajiya Kaltume cikin tashin hankali, hausawa suka ce ba a saka masa rana.
Gaba daya kuka suke cikin falon har Namra da ta shigo. Hajiya Kaltume na ganin Appa
ta kara mulmulawa a kasa tana dafa kai ta tashi zaune ta koma ta kwanta kamar wata
bayarba...

“Eyyyy Eyyyy Eyyyy ni Kaltume yau na shiga uku yata, wayyo Umm Ruman, Alhaji ina
cikin matsala da bala'i sun sace min yar auta, wai ni mi na yi ma mutane ne ne?
Wayyo Allah na”

“Haba Hajiya ki yi hakuri mana, idan ke kina haka su kuma yara waye zai
rarrashensu? Dan Allah ki tashi”

“Alhaji wasu sun tare mota sun tafi da Ruma”

“Hamad ma yana can hannunsu ai, ba ita kadai ba, kuma In Shaa Allahu zaku dawo
lafiya”

“Mutanen nan ba su da imani shi Hamad ai namiji ne, ita kuma mace ce yarinyar yar
shawalwala”

Appa ya zauna a kujera ya cire hular kansa duk sanyin ac falon gumi ne ke keto masa
ta ko'ina. Salma da Khairi suka fara fada masa abun da ya faru suna kuka ba tare da
ya tambaya ba, Kamin ya dago ya bi kowa da kallo.

“Ku daina mana kuka tun da ba mutuwa aka yi ba, ku yi ta addu'a, idan ma wani abun
suke so ai dole za su kira. Ina Hurriya?”

Appa na rufe baki Yasir da shigowar falon kenan ya amsa masa.

“Yanzu na kaita gida?”

Appa ya masa wani kallo.

“Gida ina?”

“Gurin Amma tana ta kuka ta ce a kaita can, shiyasa na kaita amman ban shiga gidan
ba”

Appa ya dafe kai cike da takaici kamin ya dago ya kalli Yasir yana jin kamar ya
mareshi.

“Ban taba sanin baka da hankali ba, sai yau Yasir ka kaita ta fadawa Iyami abun da
ya faru kamar baka san halin da Iyami take ciki ba? Ciki ne fa a jikinta kuma
tsohon ciki idan ta fadi ta rikice wani abu ya same ta ko ya samu abun da ke
cikinta kai zaka mata magani? Wani irin shashanci ne wannan?”

Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin
wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.

“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa,
al kara ma Hamad namiji ne”

Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman
kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka
shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso
duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake
tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.

“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”

“Tana gidansu”

“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”

Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.

“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”

“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma
din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun
Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”

“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da


ita”

Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.

“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”

“To Appa”

Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da
direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude
masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa
allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.

“Bala, ka sallamo Hurriyya”

“Toh ranka ya dade”

Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba
ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me
zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da
iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk
wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan
ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya
gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme
ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada
girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.

“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar
abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan
makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo
wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru
domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”

“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta
bakinta”

“Can gida ba su fada maka komai ba.?”

Appa ya ki yarda su hada ido.

“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”

“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”

Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab
har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana
kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.

“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin
hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana
kawai nake bukata a yanzu...”

“Iyami zauna”

Amma har ta yi kamar ta ce masa ba zata zauna ba, domin niyarta ta kawo Hurriya
kuma ta jadda masa amanar yayanta ta koma, sai kuma ta zauna domin bata saba musa
masa a komai ba. Sai da ta zauna sannan shi ma ya zauna.

“Ba wani abu aka yi mata ba, ki daina saka kishi da son cusa kiyayyar Kaltume ko
Nafisa a zuciyar yayanki, ba dukan Hurriya aka yi ba, ba wata bakar magana aka fada
mata ba, babu wanda ya mata komai, ba mutuwa aka yi ba”

“To miyasa ta zo tana min kuka? Kuma Yasir da ya kawo ta be shigo gidan ba ya
fita?”

“Ni ma shi na zo tambayarta”

Amma ta kalli Hurriya har lokacin hawaye take sai dai ba kamar dazun ba. Ta kalli
Appa

“Ina Hamad...!”

Appa ya ji tambayar kamar saukar aradu. Appa ya kalleta ya kasa cewa komai.

“Ina Hamad Appan Hurriya?”

“Dan Allah kin kwantar da hankalinki”

“Kamar ya na kwantar da hankalina? Miye abun tashin hankali a tambayar Hamad? Ko


kuma shi ya aikata wani laifin?”
“be aikata laifin komai ba Wallahi, ki ba mu guri zamu yi magana da Hurriya”

Amma ta kalli Hurriya kamin ta mike tsaye ya fice daga falon. Appa ya tashi daga
inda yake zaune ya koma kusa da Hurriya ya zauna ya rika yarsa.

“Hurriya”

“Na'am Appa”

“Ki kwantar da hankalinki kin ji, Hamad zai dawo soon da yardar Allah, babu abun da
zai same shi, kuma na ji dadin da baki fadawa Iyami abun da ya faru ba, kin ga tana
da ciki zata iya daga hankalinta,”

Ta daga kai ta kama hannun Appa ta jimke da karfi.

“Appa bana ganin komai yanzu, bana ganin komai sai abun da ya faru, me yasa suka
dauke Hamad? Me yayi musu?”

“Wallahi dukanmu ba su sani ba, amman dai an san ba zai wuce su ce a ba su kudi ba,
kamar yadda suka yi ma Kaltume kuma shi ma za su sako shi”

“Hadda Ruma aka kama”

“Na sani duka zamu biya kudi mu karbo su Da yardar Allah, amman yanzu zamu tafi
dake gurin police za su miki tambayoyi akan abun da ya faru, saboda kun sanar da ya
sanda, kamin nan kuma ina son ki min alkawarin ba zaki fadawa Iyami ba, kuma ki
daina kukan nan har sai mun karbo shi”

Kamin Hurriyya ta dauki alkawarin suka jiyo Amma daga jikin curtains din kofar
dakin tana furta.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un.


Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”

Daga Appa har Hurriya ba su san Amma ta yi labe ba sai a lokacin. Appa ya taso ya
fito da sauri yayinda Gwaggo ma ta fito da sauri daga dakin Amma ta nufota.

“Gwaggo sun dauke min Hamad, su biyu Allah ya ba ni sun dauke daya, kashe shi za su
yi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Gwaggo ma ambaton Allah ta shiga yi tare da rike Amma dake shirin faduwa.

“Allah yasa kaddara ba musanya zata min ba, Allah yasa ba Hamad za a dauke a ba ni
wani ba, La'ilaha Illallahu, Allah kasa kari zan samu ba musanya ko ragi ba, su wa
suka dauke shi? Na san ďana be jin magana amman su yi hakuri dan Allah idan wani
laifin yayi, kowa ya min haka be kyauta min ba, me suke so Innalillahi wa'inna
Ilaihiraji'un”

Gwaggo ma sai da ta fashe da kuka saboda kukan da Amma take yi. Appa kuma yayi
tsaye a gurin hopeless yana kallon tsohuwar matarsa dake dauke da cikinsa ya rasa
me zai yi.

Littafin nan kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza
Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
________________

https://chat.whatsapp.com/F1ch00M9VNvFxrVVgCEeXo

Ina Yan uwan Yan gayu makotan Masu Kudi?


Daku nake Magana.
Matan da suka san ciyon kansu masu hada goma ta zamo ishirin kuzo ku sari Kaya
acikin sauki da rahusa a Ummu Ahmad store muna kawo kayan mu ne daga Lagos masu
quality da karancen farashi akwai kayan kitchen akwai shoes and bags, Akwai kayan
abinci na awo laces,kayan yara,da sauransu
Sannan akwai kayan gyara irin su tsimi kala kala gumbar mata daban daban maganin
sanyi
Akwai kaza me rubutu da wadda akeyi da sanyun magani
Akwai taimako na haihuwa ga wadda taje asibiti akace batada matsalar komai akwai
rubutun da muke badawa Wanda idan ta gama Al adarta zatayi amfani dashi za adace da
yardar Allah
Akwai kayan kamshin daki da na jiki

Location dinmu zamfara


Muna tura Kaya a koina kk cikin aminci da yardar Allah payment validate ur order
Ummu Ahmad 08032350261

Ni Khadeeja Candy nake tabbatar muku ba zaku taba nadamar siyen kayan Little Mommy
na ba, uwata ce ta jini ba lake lake ba, please patronize her tana siyar kaya masu
kyau da imganci, zaku iya tuntubarta ko ma ku tuntube ni kai tsaye 💃 sai ku zo 🥰
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza
Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞2️⃣

Sai da Gwaggo da Mama Rukayya suka yi da gaske sannan suka iya rarashin Amma ta yi
shiru, suka dagata suka shigar da ita falon har lokacin Appa ya tsaye ya rasa abun
cewa, Hurriya ma kuka take sosai tana tausayin kanenta tana tausayin mahaifiyarta.

“Dan Allah Gwaggo a kwantar mata da hankali, ba yau aka saba daukar mutane kuma ana
dawowa da su lafiya, na san dai ba zai wuce su ce suna bukatar kudi ba, kuma ba mu
biya mu karbo shi”

“Toh Allah ya bayyana shi cikin aminci”

Gwaggo ta fada cikin kuka, sai a lokacin Appa ya samu courage din fice daga cikin
gidan tare da Hurriya, a mota ma Appa ya wahala kamin ya samu Hurriya ta yi shiru,
hankalinsa be kara tashi ba sai a lokacin da take bada labarin yadda abub faru. Duk
wani abu da ya kamata su tambayeta sun tambaya kuma ta ba su amsa sannan Appa ya
dauko ta a motarsa tare da Direbansa suka nufo gida.

“Appa ka kar ni a gurin Amma please bana son nan”

“Zan maida ke can Hurriya, ita ma ai ganinki zai saka ta dan ji sanyi, zaki dauki
tufafinki, sai kuma Yasir ya baki dayan glass dinki da yake can”

“Toh”
Daga haka bata sake cewa komai ba har suka isa gidan. A harabar Momy Appa ya umarci
direban ya faka, sannan ya fito direban ma ya fito da sauri ya budewa Hurriya mota
Appa ya rikata ta fito, suka nufi bangaren ransa a jagule gaba daya shekarar nan ta
zo masa a yadda be yi zato ba. A hankali ya tura kofar falon Momy sai da ya fara
shiga sannan ya rikota ta shigo. Captain dake zaune ya mike tsaye yana amsa
sallamar Appa, Appa ya karaso cikin falon cikin yanayin dake nuna yana cikin
tsananin damuwa.

“Momy bata nan”

“Oh to ina taje? Ina zuwa Hurriya”

Ya saki hannunta ya juya ya fice daga falon.

“Ance kananki?”

Captain ya furta a hankali yana kallon kwayar idonta dake ta juyawa alamar bata
ganin komai. Kamar ya tsikaro mata allurar kuka sai ta fara hawaye tana rawar
murya.

“A yadda Namra ta fada min ke suka zo dauka, kin san su waye?”

Ta girgiza kai.

“Waye kai?”

Ta tambaya domin bata wayanci ko waye ba. Yayi shiru yana juya invitation card din
dake hannunsa for some seconds.

“Soja ne...!”

Ta mika hannu ta fara lalaben inda take jin sautin muryarsa.

“Dan Allah zaka nemo min kanena?”

Tana daf da taba fuskarsa ya kawar da fuskar ya kai hannunsa ya rika hannunta, ba
tare da ya amsa mata da eh ko aa ba.

“Dan Allah ka nemo min kanena idan zaka iya, shi ne farincikinmu, shi yake tare min
fada dan Allah ka taimaka Malam Soja ka nemo min shi”

Yayi shiru har lokacin be ce komai ba ya saki hannunta daman ya rika hannun ne
kawai a kokarinsa na kawaicewa taba fuskarsa. Shi dai abun da ya kawo shi gidan
dabam ya zo ya tararda wannan tashin hankali.

“Malam Soja...”

Jin shiru kamar babu kowa a gurin. Sai ya kai hannunsa ya rika 5 fingers dinta ya
matsa a hankali domin tabbatar mata yana tsaye a gabanta har lokacin.

“Dan Allah ka nemo min kanena, ku ne sojoji ai ku kuke kama masu aikin yan ta'adda”

Kallon fuskarta yake kamar ance masa tana ganinsa.

“Dan Allah ka taimaka mana, Appa na kudi zai iya ba ku please”

Ya sake rika 5 fingers dinta ya matsa hannunta.

“Idan ka min alkawari ka matsa sau biyu...”


It take him ten seconds kamin ya sake matsa 5 fingers dinta for the third time,
sannan ya saki hannunta ya zari Invitation card daya a cikin wadanda suke dayan
hannunsa na dama, ya dora su akan mini table dake kusurwar kujerar ya juya bayan
dayan card din ya yaga ya ciro pen dinsa yayi rubutu akai sannan ya maida pen din
ya sake barkar takardar ya kama hannunta ya danka mata rabin.

“Karki fadawa kowa, kuma karki taba jefar da wannan takardar matukar ina fatar
Kanenki ya dawo”

Ta jimke yar ficikar takardar a hannunta tana sauraren takun tafiyarsa har ta ji
lokacin da ya bude kofar falon ya rufe. Bayan kamar minti biyar tana tsaye a gurin
aka sake bude kofar falon aka shigo.

“Hurriya Appa ya ce na zo dake”

Yasir ta karaso ya rika hannunta yaja suka fita daga falon.

“Na duba ko'ina ban ga gilashinki, zamu je asibiti a siya miki wani yanzu kamin a
ga wadancan”

“Ya Yasir yaya zai dawo ko?”

“In Shaa Allah”

Yasir ne ya kaita asibitin gurin likitan da ya saba dubata, suka bata wani gilashin
da ya dace da idonta, sai dai idon nata sun sake samun matsala ko da ta saka
gilashin bata iya gani da kyau kamar da, hakan ya saka likitan ya sake duba idonta
kamin ya rufe ta fada da kuma Yasir wai an barta ta yi kuka mai karfi da yawa har
yana son tana gilashin idonta, daman idon lafiya be ishe shi ba. Magani ya bata
wadanda zata shafa a idon safe da kuma dare idan zata kwanta sannan ya bata wanda
zata diga a idon kamin ta kwanta. Sannan suka dawo gida, kusan duk wanda ya kalleta
ita yake tausayawa domin ita ce bata da uwa a gidan kuma ita ce kadai take da kane
daya, Hankalin Hurriya be kara tashi ba sai da ta zo zata dauki tufafinta da suke
bangaren Momy ta kalli dakin Hamad sai sabon kuka ya taso mata, tana ganin kamar
mutuwa yayi ya barsu. Ta saka tufafin da zata iya diba a jaka, ta fito tana kuka ta
fice daga falon Momy. Momy dake aikin duba invitation card din da ta tarar a
falonta ko kallo gurin da Hurriya take bata yi ba sai yana katin take, Namra ta
tashi ta bi bayan Hurriya ta rakata har gurin motar Appa, domim shi yace zai kaita
gurin Amma da kansa, sakamakon kiransa da Hajiya Binta ta yi ta ce ya zo ya dauketa
ya kaita gurin Amma kuma ya kawo mata Hurriya. Namra ma sai da ta yi kuka saboda
yadda Hurriya take ta kuka. Sai da suka fice sannan Namra ta dawo bangarensu tana
share hawaye.

“Wallahi duk wani mai imani sai ya tausaya, kowa ya aikata haka Allah ya hana shi
zaman lafiya”

Momy ta daka mata tsawa.

“Ina ruwanki shegiya yar iskar yarinya yar neman suna, ke aka sata? A gidan nan wa
kika ga yana damuwa da rayuwar wani?”

“Haba Momy idan aka sace ni ya zaki ji?”

“Allah ya mayar miki da aniyarki, ni ai wanda ya sace yaron kuma ya gama da yar
wajen Kaltume ya kyauta min Wallahi, daman shi Hamad ya fitini kowa, karshen mai
cin amana kenan, ita kuma Ruma satarta zai hana Kaltume kwanciyar hankali”

Miwan dake saukawa ya karbawa Momy.


“Wallahi kin fadi abun da yake zuciyata, daman shen yaron nan ya isheni, saboda shi
nan kwanan baya babu fadan da Appa be yi miki ba, har kuka sai da kika yi, kuma
saboda shi aka mari Musib Allah yasa ma su kashe shi”

“Ato... Da ma Hurriya ce wata kila na tausaya mata, amman Hamad shegen yaro. Kaji
min yarinya wai ita mai zuciyar tausayi, ke idan ke aka kama waye zai yi wannan
kuka? Kuma ni bana raba dayan biyu, Wallahi Kaltume zata iya sakawa a sace yaran
nan saboda muguwar mata ce, yaushe ta dawo? Ta sace kanta kudin be mata ba yanzu
kuma ta koma gurin yara, balle kuma ta san Hurriya Alhaji yana ji da ita, ke ma
kuma idan baki kula ba sai ta saka an dawo kanki, wannan bakar matar mutuwa kawai
zata yi kowa ya huta, ni daga yau ma ba zaki sake komawa makarantar ba, canja miki
makaranta zan yi, kuma direba dabam zai rika kai ki yana dawowa dake”

“Amman Momy baki ga yadda Hajiya take kuka ba, haba Momy za'ayi ta sace yarta?”

“Kukan munafurci ne, ke yarinya ce baki san kan duniya ba, ni dazun da na san
Captain zai zo ai ba zan ma shiga bangarenta ba, ke kuma kika ki kirana gashi har
sake zuciyar ya tafi”

“Shi yace kar na kira ki na barki sai kin kare abun da zaki yi, bayan ya tambaye ni
abun da ya faru”

Miwan ya zauna yana daukar katin ya duba.

“Wallahi Momy Captain yana sonki sosai if not wulakancin nan da aka yi ta masa ba
zai sake dawowa ba”

“Ai nima na san haka, shiyasa nake son zage dantse na kyautata masa a bikin, ga abu
dai ya matso kusa”

Daga haka suka dauko zancen bikin kamar babu ruwansu da damuwar kowa. Appa sai da
ya biya unguwar Gidan Dawa ya dauko Hajiya Binta sannan ya nufi gidan Gwaggo, a
mota Hurriya na kara fadawa Amma abun da ya faru tana kuka. Appa be shiga ciki ba,
daga Hajiya Binta sai Hurriya suka shiga, Hajiya ta hadu ita da Gwaggo suka yi ta
bata magana suna kwantar mata da hankali. Sannan taja ma Hurriya kunne kan fita
waje duk kuwa da ta san Hurriya ba ma'abociyar yawo bace, daman kuma Appa yayi mata
nasa jan kunne a mota.

*** *** ***

Wasa wasa aka kwashe kwana uku shiru babu Hamad da Ruma babu labarinsu, police din
da aka damkawa case din kuma ba su samu wani bayani ba, sai dai suna ta kokarin
zafafa bincike iya yinsu. Tun daga ranar kuma Amma bata iya bachi, dare take rayawa
tana fadawa Allah bukatarka ya kare mata danta ya dawo mata da shi cikin aminci.
Abinci ma Amma bata iya ci sai Gwaggo ta yi da gaske. Hurriya kuma tun daga ranar
bata sake zuwa makaranta ba saboda tsoron fita da take ko kofar gidan bata yarda ta
tafi, daman kuma Appa ya daukarwa yaransa hutun sati daya a school dinsu har zuwa
lokacin da abun zai dan sake su. Appa ma ya yarda Hurriya ta zauna a gurin Amma ne
kawai saboda Hurriyar ta zaki haka, kuma ya san hankalin Amma zai dan kwanta idan
Hurriya tana kusa da ita, ba dan ransa yana so ba, domin gani yake ko a can za a
iya tafi a dauki Hurriya ko Amma.

Ranar da Ruma da Hamad suka cika kwana bakwai da sacewa su aka kira wayar Appa ana
neman miliyan dari na Hamad, miliyan dari na Hurriya. A ranar hankalin Appa ya
tashi sosai ya nemi su hada shi da yaransa su yi magana, sai suka ce mutum daya za
su ba shi wato Ruma, suka bata wayar ta yi magana da shi tana kuka sosai tana fadar
sun ce za su kashe su idan ba a kawo kudi ba. Appa ya bukaci ta ba sake ba su
wayar, ta mika musu suna karba Appa yace yana neman ragi sai suka jaddada masa babu
abun da za su rage masa kuma idan be biya kudin da wuri ba za su kashe su. Kamin
Appa ya sake cewa wani abu suka kashe wayar a take ya sake sanar da yan sanda.
Bayan ya sauke wayar Hajiya Kaltume ta share hawaye ta ce.

“Alhaji ka ba su kudin nan dan Allah su sako yaran nan kar su kashe su, kana jin
sun ce za su kashe su fa, mutanen nan ba su da imani ko kadan ni na san yadda suke
yi ma mutane”

“Dole ai za mu nemi sassauci ai, miliyan dari biyu wasa ne?”

“Amman ai kana da su, ba su fi karfinka ba, dan Allah ka ba su kudin nan, idan ma
sun maka yawa, ni zan hada da dan abun da yake hannuna ita ma Iyami a fada mata ta
bada abun da take da shi a hada a karbo yaran nan”

“Aa babu kudin da zan karba, kuma idan za a fadawa Iyami sun kira ba sai kun ce
mata yace zai kashe su ba”

Hajiya Kaltume ta sake fashewa da kuka.

“Alhaji kenan kana jin matar nan kamar ranka, waya ke ta tashin hankalinta a yanzu?
Ni ta yara nake ba nata ba”

Appa ya mike tsaye ya fice daga falon. Hajiya Kaltume ta dauki wayarta ta fadawa
Hajiya Fatee abun da ya faru tana kuka kamar ba ita ba, Hajiya Fatee sai hakuri
take bata, sai da suka gama wayar sannan ta fito bangaren Appa ta dawo nata
bangaren ta fadawa yaransa abun da ya faru, haka suka yi ta juya maganar suna kuka,
daga karshe ta umarci Yasir ya je ya fadawa Iyami halin da ake ciki.

“Kar naje kuma Appa ya zo yana fada”

“Amman ai tana da hakkin sani, tun da danta aka sace, shi kansa be hana a fada mata
ba, yace dai kar a fada mata sunce za su kashe su, fada mata mana ta hado dan abin
da take da shi ni na hada a karbo yaran nan”

“Amman kudin nan be fi karfin Appa ba, kamin ku yi wannan yunkuri da dai kun ba shi
lokaci ku ga abun da zai yi”

“Ni zan iya jira ba, na san yadda mutanen nan suke ba zan so ko kwana daya Ruma ta
kara hannunsu ba, idan ita ba zata yi ba ni zan bada nawa a sako min yata”

Yasir ya girgiza kai.

“Gaskiya ni ba zan iya zuwa ma Amma da wannan labarin ba”

“Ina fa zaka iya, da dai ni ce da gudu zaka zo ka fada min ai”

Ta fashe da sabon kuka, Yasir ya tashi ua fice daga dakin. Yana fita Hajiya Kaltume
ta kalli Maama ta ce.

“Maama shirya direba ya kaiki tafi ki fadawa Iyami yadda suka fada”

“Sai kin masa magana Hajiya kin san tun da abun nan ya faru Appa ya saka dokokin
fita masu tsauri”

“Zan masa”

Hajiya Kaltume da kanta ta fita ta yi ma masu gadin magana da kuma direban. Burinta
dai a fadawa Iyami abun da mutane suka ce ko da hankalinta aka daga dadi zata ji a
yanzu, domin ta san hawan jinin mai ciki yana da illa sosai balle ita da take da
tsohon ciki haihuwa yau ko gobe. Sai da ta fadawa direba ya jira ta fito sannan ta
fita motar Maama ta shiga gidan Gwaggo kamar a ita ba, rabon da ta je gidan ma ta
manta amman a yau zata tafi ta sanar da bakin labari ga Amma. Ko da ta shiga ta
samu Amma na zaune waje harabar gidan kan tabarka, hannunta yana kan Hurriya dake
kwance gefenta tana bachi.

“Wa'alaikussalam”

Amma ta amsa tana kallon Maama gabanta ma faduwa, kusa da ita Maama ta zauna har da
gaisheta abun da bata saba ba, domin babu mai bata girma a cikin ƴaƴan Hajiya
Kaltume sai Yasir.

“Maama lafiya? Fuska ki ya nuna akwai damuwa fada min me ya faru?”

Maama ta fede mata daga biri har wutsina na abun da ya wakana tsakanin Appa da masu
satar mutanen ciki har da zancen da Appa ya ce kar a fada mata cewar sun ce za su
kashe su.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”

Shi ne abun da Amma ta iya furta idonta na cika da hawaye, furucinta yayi sanadin
tashin Hurriya daga bachi ta tashi zaune da sauri ta gyara zaman gilashin idonta
tana kallonsu. Gwaggo da Rukayya suka iso gurin suna jin abun da ya faru kowa ya
dora hannu saman kai, Gwaggo ta daki kirji.

“Miliyan dari dari?”

“Eh shiyasa Hajiya tace ita dai zata bada abun da yake hannunta Appa ya hada ya
karbo mata Ruma, domim shi Appa so yake sai ya tsaya ciniki da su, ita kuma ta ce
ita kadai ta san azabar da ta sha, mutane ba su da imani”

“Miliyan dari biyu be fi karfin Alhaji ba, rayuwarsu ta fi kudin amfani idan ma
kyashin badawa yake ji ni ma zan hada abun da nake da shi na ba shi, ni dai a dawo
min da yarona rayuwar yarona ta fi min komai, dan Allah ki karbo min number da suka
kira a hannun Alhaji zan kira na yi magana da su”

“Toh”

Bata wani dade ba ta tashi ta fice ta bar Amma da Hurriya suna ta kuka. Sai da ta
fita sannan Gwaggo ta kalli Amma ta ce.

“Allah masani, amman anya babu sa hannun Hajiya Kaltume a lamarin nan? Akan me zata
nuna miki ki hada kudin da yake hannunki ki bada?”

Amma ta kalli Gwaggo tana hawaye ta ce.

“Wannan rashin imanin yayi yawa, Hajiya ba zata iya aikata haka ba, idan ma zata
aikata ba zata aikata tare da yarta ba, ni dai zan gada komai nawa na bada dan
Allah Gwaggo karki hana ni”

“Duk da haka dai, ki saurara har ki ji ta bakin Alhaji Haruna din, zan saka
Bappanku ya kira shi yayi magana da shi ko ma yaje ya same shi mu ji yadda ake
ciki”

“Appan Hurriya yana da kafewa wani lokaci ni ba zan iya jira har lokacin da zai
karbo su ba, Allah kadai ya san halin da Hamad yake ciki”
“Toh ke yanzu ina kika ga miliyan dari Iyami?”

“Ba za a rasa ba Gwaggo ko kudin be kai ba, akwai kaddara”

Amma na fada tana kuka ji tana kamar ta tashi yanzu yanzu ta gada kudin ta mika
musu su sako mata Hamad.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza
Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞3️⃣

Tun a ranar Bappa ya so ya samu Appa su tattauna kan lamarin amman hakan be samu ba
sakamakon dare da yayi, daman daf da magariba Maama taje gidan. The following the
day Bappa yayi ta kiran Appa a waya amman yaki dagawa, cikin yanayin damuwa Bappa
ya kalli Iyami dake rike da carbi ya ce.

“Haka nake da bawan Allah nan, babu ranar da zan kira shi ya amsa min, tun da
lamarin nan ya faru idan na kira shi baya daga wayata”

“Wata kila har yanzu yana jin kunyarka ne, ina ganin abun da zai fi ka shirya ka
same shi gida da safen nan da wuri sai ka yi magana da shi”

“Ko kuma ita Iyamin ta kira shi a wayarta ba, ta yi magana da shi ko kuma ta ba ni
wayar mu yi magana”

Ya karasa yana kallon Amma. Amma ta dauki wayarta ta lalabo number Appa da rabon ta
yi waya da shi tun tana gidan, kamin ta danna masa kira ma sai da ta yi da gaske ta
danne zuciyarta, sanin cewar saboda matsalar Hamad zata kira shi ya karfafa mata
guiwar kiran, sai ita ma ta yi rashin sa'a kamar Bappa, be daga kiran ba, tun kiran
na ringing har ta kai an fara rejecting.

“To wai lafiya ko kuma dai yana tsoron kar a fada miki ne, wata kila be san Maama
ta zo gidan nan ba, ina tunanin a boye ta zo ta fada miki, domin irin wannan magana
mai nauyi shi ya kamata ya taho da kansa ya fada miki, anya ba Hajiya Kaltume ta
taro ta ba?”

A take Bappa ya gwatsale Gwaggo daman shi be cika yarda da irin abubuwan nan na
zafin kishi ba, ko wani abun da za ace kishiya ta aikata ganin yake duk karya ne,
ko wane bangaren daman ba zai so dayan bangaren ba dan haka kazafi da kage babu
kalar wanda ba zai yi ma abokin adawarsa ba.

“Ku dai kullum baku da wata magana sai ta Hajiya Kaltume, ina ce saboda Hajiya
Kaltume nan Iyami ta hadu da Alhaji, ni fa a gurina bani da kamar Hajiya Kaltume
domin sanadinta Iyami ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, idan na fita har nuna ni ake
ga surukin Alhaji, da can ba a kwano muke zaune ba? Amman ya zo ya siya mana babban
gida ga kuma lalurar komai ya dauke mana, duk sanadin waye ba Hajiya Kaltume me?
Dan Allah ku daina kawo min maganarta ma”

Gwaggo ta rausayar da kai.

“Toh Malam ai daman ba zaka yarda ba, baka san makircin mata ba”

“Ban sani ba, kuma bana son sani, yanzu ki tashi ki shirya mu tafi tare can mu same
shi mu yi magana da shi”

“Toh bari na dafawa Hurriya Indome ta fi son karyawa da ita”

Amma dai bata ce komai ba, har suka ci suka shude, ita dai tunaninta na halin da
danta yake ciki ne. Sai da Gwaggo ta dafawa jikarta Indomie ta zuba mata a karamar
cooler sannan ta yi wanka Bappa ma yayi wanka suka shirya sannan suka bar gidan.

MAI YADI'S HOUSE.

Hajiya Kaltume ta dan leki wayar da Appa ya aje a gefe daya ta kalleshi.

“Iyami ce fa Alhaji?”

Appa kamar wanda aka rikita sai ya fara fada ta inda yake shiga ba nan yake fita
ba.

“To me zan mata? Ba za a bar mutum da damuwarsa ba? Ta san halin da nake ciki ne?
Mahaifinta yanzu ya gama kirana ita kuma ta dora da nata”

A kaikace Hajiya Kaltume ta ce.

“Ka sani ko zancen dawowarta za su maka ko kuma na Hamad?”

“Dawowarta? Ta zo ta yi me? Hamad kuma ai ni ma dana ne ba ita kadai ta haife shi


ba balle ta nuna min sonsa”

“Gaskiya kam, ni ma da aka dauke min Ruma ai dole na zuba ido sai abun da ka yi,
amman duk da haka dai Alhaji da dai ka bada kudin”

Appa yayi shiru kamar mai tsoron musa mata, ya kasa cewa komai.

“Kuma ba ka san shakkuwarta ba, da ka karba wayar ka ji abun da za su fada”


“Bana son na ji wani abun da da ya shafi Iyami ko gidansu a yanzu, damuwa ta min
yawa kaina ma kamar ya fashe nake ji, na san kuma damu za su yi da maganar Hamad”

“Ikon Allah yau Alhaji Iyamin ce baka son jin wani abun da ya shafe ta? Toh Allah
ya kyauta bari na kwashe kayan”

Ta fara kwashe kayan da ya ci abinci zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fado
tsabar farinciki. Jikinta har rawa yake kamin ta bar part din, tana shiga
bangarenta ta aje tray a falo ta shige dakinta ta dauki wayarta sai kira ta aikawa
Hajiya Fatee.

“Toh Allah dai ya sa lafiya wannan kira haka tun da safe?”

“Lafiya kalau sai alheri, Hajiya Fatee yau bana da inda zan saka ki, bani da wanda
ya fi min ke a duniyar nan, Hajiya Fatee kin biyani Allah dai ya bar zumuncinmu”

Cikin mamaki da farinciki kawar tata ta amsa.

“Toh Ameen, amman ba ni an sha me ya samu?”

“Komai ma ya samu Hajiya Fatee yanzu zan fara samun kan mijina, abun da na kwashe
shekaru ina nema ban samu ba, Hajiya Fatee yau Alhaji da kansa yake ta fada saboda
Iyami da mahaifinta sun kira shi a waya, har yake fadar shi yanzu baya son wani
abun da ya shafi iyami ya hada shi da ita”

Hajiya Fatee ta saka dariya irin mai ruguzawar nan.

“Hajiya Kaltume ni kaina na gasgata aikin Malamin nan, kuma na yarda ba da wasa
yake aikinsa ba, domin ni na fi kowa shaidar hakan tun da ga ciki ya kwanta lafiya
kamar babu shi, wata kila ma cireshi yayi gaba daya, amman har asibiti na tafi an
auna babu ciki babu labarinsa”

“Ni Wallahi da farko nan na dauka ko aikin be yi ma, kwana nawa aka dauka amman
shiru sai yau na fara ganin ikon Allah”

“Ai daman wani abun haka yake, kin manta yadda muka yi na auren Iyami? Shi ma ai
sai da kika fara korafin be yi be yi ba, har ya ce kin yi gajin hakuri, yanzu ba
gashi ta tafi ta bar miki idan ba”

“Na yarda, tabbas ni kuwa zan saka masa da sakamako mai kyau, sai yayi alfahari da
ni”

“Ni ma ai na fada masa idan yayi abun da zai raba auren Fadeel da Afrah sai na masa
kyauta mai tsoka da sai ya kasa mantawa da ni, kuma ya ce zai yi, sai dai ta inda
lamarin ya sanyaya min guiwa cewar da yayi idan yayi mata aika dawo masa ake da
ita”

Hajiya Kaltume ta rike baki. “Ai kin san bata tsawaya kanta ba, ita ma shigen
shigen take”

“Ai na sani, shiyasa ta mallake min da komai sai Afrah gaba daya baya jin maganar
kowa sai nata, kuma bana da ikon zaginta a gabansa sai ya fara masifa, ni daman tun
farko bana son aurenta da yaron nan Wallahi, Allah dai ya riga da kaddara ne kawai”

“Ki sa ido ki yi kallo kamar yadda Iyami ta bar gidana, Afrah ma sai ta bar gidan
danki da yardar Allah”

“Haka nake fata Hajiya Allah ya amsa”


“Ameen”

Hajiya Kaltume ta aje wayar tana murmushi kamar wadda aka yi ma bushara.

“Hmmmm Iyami.... Lallai kin zama labari a gidan nan, yaranki ma da yardar Allah sai
sun zama su da babu duk daya a gidan nan”

Ta nufi bakin gadonta ta zauna tana kokarin sake yin wani kiran Khairi ta shigo
dakin ta zauna kusa da ita ta kwanta jikinta.

“Hajiya yaushe Ruma zata dawo ne?”

Hajiya ta yi saurin saka wayar key tare da gefenta.

“Babu jimawa Khairi, mahaifinki ne yace a bashi lokaci zai nemi ragi, kuma kin ga
ai ana neman ragi a komai”

“Toh Hajiya da zai yarda da sai ya bada kudin ya karbo Ruma, albashi Hamad din a
barsa sai an shirya daman ya fitini kowa a gidan nan”

“Ai kin san ba zai yarda ba, kuma mutane ma sai su saka mana ido, ace saboda uwarsa
bata gidan ne, kara dai a karbo su tare gaba daya”

“Allah sarki Ruma, Allah dai ya tsare ta”

“Ya ma tsare In Shaa Allah ba za su mata komai ba, ai yarinya ce kuma kin ga ba ita
kadai suka dauka ba ko dan ganin idon Hamad za su raga mata tun da dan'uwanta ne”

“Allah yasa”

“Ameen tashi kuje ku karya, ni wanka zan yi yanzu”

“Na karya ai”

“Yayi kyau Maama da Salma duk sun karya? Yayanki fa?”

“Ban sani ba gaskiya”

“Je ki fada masa ya fito ya karya”

Khairi ta tashi ta fice daga dakin, sai da Hajiya Kaltume ta tabbatar ta rufe kofar
dakin sannan ta fiddo wayarta ta fara danne danne. Misalin sha daya na safe Bappa
da Gwaggo suka dira a gidan, Bappa ya faka a harabar da ya saba fakawa duk lokacin
da wani abu mai muhimmanci ya kawo shi gidan, duk kuwa da kasancewar Iyami bata
gidan. Shi ya fara fita sannan Gwaggo ta fito tana sanye fa farin hijabinta.

“Ki fara shiga ki yi magana da Hajiya Kaltume a sallamo mana Alhaji mu yi magana da
shi”

“Ko kuma dai ayi mana iso ba”

Gwaggo ta gyara masa domin a ganinta ba bara ko roko suka zo gurinsa ba da za ace a
sallamo musu shi. Bappa dai be sake cewa komai ba domin be shirya musu da Gwaggo a
yanzu ba, ya san duk gyaran da zai mata ba zata fahimta ba. Gwaggo ta daga kai ta
kalli apartment din Amma da kyau sai ta ji ranta ya bace, domin a yanzu yarta bata
cikin gidan ba kamar da ba. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta fito ta nufi bangaren
Hajiya Kaltume, ba dan zuwan ya zame musu na dole ba ba za su zo a gidan ba,
musamman ma ita da Hajiya Kaltume har Hajiya Nafisa basa girmamawa, Hajiya Nafisa
na yi musu kallon matalauta masu kwadayi Hajiya Kaltume kuma na yi musu kallon
maciya amana wadanda suka hanata zaman lafiya da kwanciyar hankali, Appa ne mai
girmamata idan yaje mata ko kuma ita ta zo gidan ya rasa ina zai dauke ta ya dora
tsabar farinciki da girmamawa. Ta murda kofar falon ta shiga da sallama fuskarta
dauke da damuwar data kasa boyuwa.

Salma da Maama suka amsa mata ba dan sun ga fuskarta ba, domin su ma ba girma suke
bata ba. Yasir ya aje cup din hannunsa da sauri ya baro dinning din ya nufota yana
mata sannu da zuwa har da dan risinawa.

“Sannu Yasir ya hakurin lamarin nan?”

“Alhamdulillah Gwaggo Bismillahi zauna”

Ya nufi kujerar da sauri ya dauke pillows din da suke kai ya mata mazauni.

“Ya gida ina Rukayya?”

“Gida Lafiya kalau, Rukayya ta tafi makaranta tun safe”

“Ya Hurriya da Amma?”

“Toh Alhamdulillah Hajiya Kaltume na ciki? Tare muke da Malam ai”

“Oh... Ya tsaya a waje?”

“Eh ai ba jimawa za mu yi ba, magana kawai za mu yi da Mahaifinku”

“Okay Salma shiga ki kira Hajiya bari na tafi gurin Bappa”

Salma ta motsa hanci ta mike tsaye ba tare da ta gaishe da Gwaggo ba ta nufi


upstairs, Maama tun da ta kalli Gwaggo sau daya bata sake juyowa ba balle har ta
gaishe ta. Ba abun mamaki ba ne a gurin Gwaggo domin sun saba yi mata haka kishi
suke taya uwarsu. Daga kiran Hajiya Salma bata sauko ba balle Gwaggo ta san halin
da ake ciki haka ta zauna a gurin har kusan minti ashiri sannan Hajiya Kaltume ta
sauko tana sanye da wata gizna mai fari da baki irin ta mutanen nijar ta irin
aikinsu a gaban rigar da ta sauko mata har guiwa.

“Gwaggo ce yau a gidan na mu”

“Ni ce, halan Salma bata fada miki na zo ba Hajiya Kaltume”

“Ta fada min ba shi na sauko ba? Ina dan abu ne shiyasa Allah yasa dai lafiya”

Gwaggo ta tabe baki ta girgiza kai.

“Ba lafiya ba kan, tun da kowa ya san abun da ya faru, tare muke da Malam muna son
magana da Alhaji ne”

Hajiya Kaltume ta zauna tana yamutsa fuska irin an takura musu din nan, kamin ta
fara magana da izza.

“Oh Allah sarki, dazun ma ai na ga Bappa ya kira Iyamin ma ta kira, Alhaji sai fada
yake Gwaggo ba a haka, ku baku san shirinsa ba, kuna son daga masa hankalin ne
kawai shi ma fa ya damu da yaran nan kuna neman ku daga masa hankali”

Gwaggo ta nuna Hajiya Kaltume da yatsa.

“Ke Kaltume ke kin sani ko ban haife ki ba, na yi kanwa da ke, dan haka na cancanci
girmamawa a gareki ko dan Iyami”
Hajiya Kaltume ta yi murmushi da ya fi kama da yar siririyar dariya.

“Wannan kuma ai da ne Gwaggo, yanzu babu wannan alakar, kuma da kuke neman daga
mana hankali ni ma fa tawa yar tana can tare da Hamad aka sace su, ko kuma ita ba
mutum ba ce?”

Gwaggo ta mike tsaye.

“Kwarai kuwa mutum ce, shiyasa ai na ganki kin sha wanka kina ta far'a da jindadi
an sace miki auta, gashi nan ai ya nuna a fuskarki”

“Gwaggo karki gayan magana, to faduwa zan yi na yi birgima? Ko kuma an fada miki ni
din kamar yarki ce Iyami da bata yarda da kaddara ba? Ai ma dai da kunya Wallahi ku
tako gidan nan da sunan ganin Alhaji shi be nemu ba ku za su neme sa, abu dai kamar
ba Fulani ba”

“Ba rokonsa muka zo akan ya ba mu wani abu ba, kuma ba zuwa muka yi akan ya maida
Iyami ba, shi ne abun kunya, mun zo ne saboda Hamad, ai kin san ko an rabu idan
akwai yaya kamar ba a rabu ba ne, sai hakuri Hajiya Kaltume Iyami dai ta zama
murucin kan dutse, ta zama kadangaren bakin tulu, kuma ta zama ƙashin wuya bata
haɗuwa bata amayuwa”

Maama ta juyo tare da tasowa daga dinning din zata fadawa Gwaggo magana Hajiya
Kaltume ta yi saurin daga mata hannu.

“Babu ruwanki Maama je ki cigaba da cin abincinki, Allah dai baya baci zalinci da
kuka min sai ya saka min macuta kawai masu abun kunya”

Hankali kwance Gwaggo ta ce.

“Ba mu da abun kunya, da muna da abun kunya mijinki ba zan lallaba ya nemi hada iri
da mu ba, kuma Alhamdulillah ko yanzu kasuwa ta watse ɗan koli mai rabo ya ci riba,
tun da ga ƴaƴa nan Allah ha raya su ya saka musu albarka”

Gwaggo na kaiwa nan ta kabe Hijabinta ta fice daga falon ta bar Hajiya Kaltume da
ciwon rai. Ko da Gwaggo ta iso gurin Bappa na nasa masifar Yasir na bashi hakuri.

“Bappa ka yi hakuri Wata kila ransa ne a bace”

“Idan ransa ne a bace be san waye ni ba da zai fada min maganar banza?”

Gwaggo ta dubi Yasir ta dubi Bappa.

“Malam lafiya?”

“Yasir ya shiga ya kira min Alhaji Haruna, daker mutumen ya fito, kuma abun da yake
fada min shi be da miliyan dari biyu da zai bada yanzu, kuma ina damunsa da kira
ban san damuwarsa ba, ai ba Hamad kadai aka dauka ba har da yarsa amman mun daga
masa hankali kamar Hamad ne kadai ďa, idan muna da kudin mu ba su mu karbo Hamad
din har da rubuto min number mutanen ya turo min, wai shi ba zai bada kudi ba
police sun ce za su karbo su”

“Hmmm Allah ya kyauta, tun da ya baka Number mu tafi Malam”

Yasir ya nufi Gwaggo cikin rashin jindadin abun da ya faru yana bata hakuri

“Gwaggo dan Allah ku yi hakuri, maybe damuwa ce ta yi ma Appa yawa, dan Allah ku yi
hakuri ba halinsa ba ne Wallahi”
“Karka damu Yasir babu komai”

Gwaggo ta fada sannan ta bude motar ta shiga, Bappa yaja motar sai masifa yake ta
yi domin yau Alhaji Haruna yayi masa abun da be taba masa ba.

“Har yana cewa muje mu biya kudin ganin yake kamar ba zamu iya ba ko? Har yaushe za
a bata lokaci gurin jiran abun da baka san faruwarsa ba? Ko bayan haka ni bana je
akan ya bada kudi ba, naje ne mu yi magana ta fahimta da shi na ji halin da ake
ciki, amman mutumen ko kallona baya son yi, sai fada yake kamar shi ne uban ni ne
dan, na fada masa ni ba zan dauki wannan rainin wayon ba, kuma ni da gidansa har
abada, wato saboda ya saki Iyami shiyasa yanzu baya ganin kimarmu ko?”

“Allah kadai ya san abun da yake nan Malam, Allah dai ya isarwa Iyami da yaranta
Allah ya saka mata da gaggawa”

Gwaggo tana addu'a tana kuka daman idan ranta ya bace bata da wuyar kuka.

_________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza
Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞4️⃣

“Gaba daya an juye kan Alhaji Haruna, kuma ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba,
ba zai wuce Kaltume ba, domin bata hada hanya da imani ba, kai ko gurin da ya bi ya
wuce bata bi ba”

Amma ta share hawayenta bayan ta gama sauraren Gwaggo dake fada mata abun da ya
faru.

“Ni yanzu ba ta Kaltume nake ba ko Alhaji, ta dana nake burina ma ga ya fito, kuma
tun da har ya kai ga furta cewar ba zai bada kudin ba, ni zan bada albashi shi sai
ya bada na Ruma”
“Ko daukar yaron nan da aka yi bana raba dayan biyu, Kaltume ce ta saka aka sace
shi, yadda na ga ta sha ado ta sauko hankali kwance har tana neman fada min magana
ya isa ya tabbatar da cewar da sa hannunta aka sace yaron nan, tasan yarta tana
cikin kwanciyar hankali shiyasa hakan be daga mata hankali ba, kuma yanzu na kara
tabbatar da ita ce ta aiko Maama gidan nan saboda ta rabaki da dan abun da kike da
shi, ni dai da zaki yarda da shawarata da kin saurara karki kira su ki kyale su da
yaron ki gani shi za a karbo Ruma ba a karbo Hamad ba?”

Amma ta daga kai ta kalli Hurriya dake zaune a waje tana cin indomie da Gwaggo ta
dafa mata kamin ta fita.

“Gwaggo shin idan wani yayi garkuwa da ni yace sai an bashi kudi alhalin kina da
hanyar za ki bi ku bada kudin nan zaki bada ko kuma zaki tsaya jiran sai ranar da
wani ya bada ne?”

“Zan fada”

“Toh ki saka kani a matsayinki, ni ma fa uwa ce tun daga lokacin da na baro gidan
uban yaran nan kullum da kalar tunanin da nake kwana a raina balle kuma yanzu da
yarona yake hannun wasu mutane da ba mutanen kirki ba, marasa tsoron Allah, duk
abun da nake da shi a duniyar nan be kai ran Hamad ba, Gwaggo ko rayuwata suke ce
sai na basu sannan za su sako Hamad Wallahi zan ba su”

Tana maganar hawaye masu zafi na sauko mata, ita kadai take iya jin abun da ko wace
uwa take iya ji idan danta ya shiga mugun hannu.

“Kana ina dana? Ka ci abinci baka ci ba? Wane kalar abinci suke baka, ina kake
kwanciya? Suna azabtar da kai ko basa yi? Ka yi marmarin gida?”

Amma ta gargiza kai tana kara jin ba zata iya jure har lokacin da Appa zai ga dama
ya biya kudin ba. Haka kuwa aka yi, Bappa ma ya bata goyon baya domim ransa ya bace
sosai akan abun da Alhaji Haruna yayi masa, Amma da kanta ta kira number da aka
bata sai suka tararda line a kashe, sai dai mai neman baya fitar da rai, jajircewa
suka yi ta yi suna kiran line kullum ba dare ba rana ba safiya, har suka yi sa'a a
rana ta uku kiran ya shiga da misalin karfe goma sha daya na dare. Abun da baka
saba ba zuciyar Amma ta hau zillo tsoro ya kamata kamar suna gabanta, duk kokarin
da Bappa yayi na ba su Hamad su yi magana da shi sai mutanen suka ki, Bappa ya
tambaye ina za a kai musu kudin suka fadi gurin da za akai musu kudin a aje, wani
kasurgumim daji ne dake tsakanin mafara da Gusau.

Bayan sun gama wayar Bappa ya ce.

“Allah yasa dai yaron nan yana raye, na ga duk kokarin da muka yi sun ki yarda su
ba mu shi mu yi magana”

Amma ta girgiza kai.

“Yana nan raye Bappa, yana raye In Shaa Allah”

“Yanzu waye zai shiga wannan guri ya kai kudi mai yawa haka? Ai shi ma sai su rike
shi kamar yadda suka yi ma kanen Hajiya Kaltume, ni dai da zaki hakura mu ga abun
da hukuma za su yi, ko kuma idan za a je kai musu kudin aje tare da police”

Bappa ya kalli Gwaggo dake maganar ya ce.

“Baki ji sun sake jaddada mana kar mu kuskura saka police a ciki ba, kai kuma kuma
zan iya zuwa na kai, indai za su sako yaron nan hankalin kowa ya kwanta zan aikata
haka, kawai ku yi ta mana addu'a”
Cikin yanayin damuwa Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya.

“Kowa ke da hannu a cikin lamarin Allah ka wulakanta shi ka tona asirinsa”

“Ameen”

Bappa ya amsa. Gidan da Appa ya bata a lokacin da zai sake ta aka fara sakawa a
kasuwa, domin filayen da ta mallaka guda biyu a gidan Appa ta san idan ta saka su a
kasuwa ba lallai ne ayi saurin siya kamar gidan da yake gyararre ba, duk da haka
kuma sai da aka siyar da shi a nakashe, gidan da zai yi miliyan 45-50 aka siyar da
shi a miliyan 35 ta hada da kudin da Appa ya bata da dan abun da take da shi ciki
har da sarkar gold din da Appa ya siyawa Hurriya duk ta siyar ta hada kudin ta bawa
Bappa, ranar da za aje kai kudin babu yadda Gwaggo bata so a saka police a cikin
lamarin ma amman Amma ta ki yarda ganin take idan aka yi haka an bata lokaci kuma
za su iya kashe mata da kamar yadda suka yi ikirari, Gwaggo kuma na ta ganin rautar
Bappa da Amma taya za a dauki kudi mai yawa haka a shiga daji a kaiwa barayi ba
tare da sanin sami'an tsaro ba, abu dai kamar a shirin film.

Cikin karfin hali da yarda da kaddara Bappa ya shiga dajin tare da wani dan'uwansa,
bayan yayi addu'o'in da be san adadinsu ba, Gwaggo da Amma, Rukayya da duk wani
dan'uwa ma suka raka shi da addu'a. Dan'uwa ya tsaya daga waje shi kuma ya shiga
ciki ya kai kudin ya aje a gurin da suka bukata. Har ya kai ya fito babu abun da ya
same shi, a lokacin da ya fito ya kira gida ya fada musu ya fito sai kowa yayi ta
hamdala ana jin sanyi. Kamin hankali ya karkata gurin ganin kiransu ko sakon inda
za su ce a je a dauki Hamad amman shiru. Daga bisani suka bi sawun kiran da number
da suka kira da ita last time, domin kullum canja number suke idan za su kira. Haka
aka kwashe two days babu kira daga garesu kuma babu wani sako kuma idan aka kira
wayar bata shiga, hankali Amma sai ya kara tashi, ta kai bata iya cin komai rashin
lafiya ta taso mata har sai da aka kwantar da ita asibiti kowa yayi zaton haihuwa
ce duba da tsohon cikin da take da shi, sai dai likitocin sun tabbatar musu ba
haihuwa ba ce hawan jini ne, har suka so riketa saboda jinin nata ya hau sosai kuma
bata iya cin komai sai dai ruwan da suke saka mata suna taimaka mata ta bangaren
kuzari. Sai dai yadda ta nuna bata son zaman asibitin da kuma rokon da aka yi ta
musu sannan suka yarda suka sallame ta bayan sun fada musu cewar a rika kokarin
kwantar nata da hankali if not idan ta zo haihu zata iya samun matsala ta kasa
haihuwar da kanta ko ma arasa danta ko ita ko a rasa duka. All zaman da ta yi
asibitin Appa be zo ya dubata ba, even for once be daga waya ya kira ya ji jikinta
ba, Hajiya Binta kan kwana ne kawai bata taba yi aabitin ba amman kullum can take
wuni, babu yadda bata yi ba Appa ya zo ya duba tsohuwar matarsa, na dan Hurriya da
Hamad kadai ba har dan cikinsa da take dauke da shi, amman ya kasa zuwa bayan be
saba mata musu ko jayyaya mai tsauri haka ba. Yaran Kaltume ma babu mai mata fatan
tashin sai na mutuwa, Yasir ne kadai yayi ta zirga zirga a asibitin gurin dubata ta
kuma biyan duk wani bills na magani ko na gado, Namra ma taje duba sau daya tare da
wata Neighbor dinsu kawar Hurriya da suke good time da ita, shi ma a sace domin
idan Momy ta sani sai ta karya kafafuwanta. Hankalin Hurriya ya tashi sosai ta fara
nata zazzabin a tsaye, tunanin sai ya hade mata biyu tana ganin kamar zata rasa
mahaifiyarta ta kuma rasa dan'uwanta ne a lokaci daya.
Washe garin ranar da aka sallamo Amma asibiti bayan ta shafe kwana biyar a
asibitin, Yasir ya zo gidan sake dubata yake musu albishir da cewar Appa zai bada
kudin a yau, sun ce a yau din nan za su fadi gurin da za aje a dauko Hamad da Ruma.

“Kai.. Allah ka sasauta mana mutanen nan ba su da imani ko kadan, yanzu bayan kudin
da suka karba gurinmu kuma za su za su karba?”

Cewar Gwaggo tana ta juya zancen.

"Wallahi kuwa, ni da kun yi shawara da ni ba za ku bada wannan kudin ba, komai dai
ta kama daman na san dole Appa zai biya kudin”
Rukayya ta kalli Yasir tana masa alamar yayi shiru ta ido.

“Kasan jiya muka dawo daga asibitin nan kuma ta nanata zancen nan sai ku saka ranta
ya bace”

Amma ta kalleta tana murmushi.

“Rukayya kenan, rai ba zai bace ba dan na bada kudin, ni dai burina su dawo min da
ďana”

“In Shaa Allah, zai dawo inda ba sun yaudare mu ba to zai dawo yau din nan tare da
Ruma”

Hindu ta kalli Yasir dake maganar ta yi masa tambaya.

“Waye zai je ya kai kudin?”

“Rilwanu me zai kai, yace zai iya zuwa domin gurin da suka fada hanyar garinsu ce
yana yawan bi ta gurin?”

“Waye haka dan'uwanku ne?”

“Eh da yake ga Hajiya ta bangaren kanenta”

“Allah sarki Allah yasa su cika alkawari”

“Ameen”

Daga haka babu wanda ya sake wata magana a falon, har Yasir ya mike tsaye ya yi
musu sallama ya fice. Hindu ta kalli Rukayya ta ce.

“Je ki raka shi mana”

“Anty Hindu ban saba yi masa rakiya ba”

“Toh ki fara daga yau, je ki raka shi mana, daga can ba sai ki jiyo mana wani
labarin ba”

Tashi ta yi ta bi bayansa ba dan ranta ya so ba sai dan ba zata iya musawa kawar
Yayarta ba. Ko da ta fita yana tsaye bakin kofar tsakar gidan tsaye yama jiranta
kamar ya san zata fito. Suna hada ido sai yayi murmushi ya juya ya cigaba ta
tafiyarsa ita kuma ta bi bayansa har gurin mota, ta tsaya yana juyawa kunya duk ta
rufeta.

“Ke lafiya kike?”

“Lafiya kalau sai anjima”

Ta juya da sauri ta bar shi tsaye ya bita da kallon mamaki, before murmushi ya
baibaye fuskarsa. Misalin karfe hudu na yamma Yasir ya kira wayar Amma yayi mata
bushara da cewar an kai kudin kuma sun fadi gurin da za a je a dauko su Hamad da
Ruma yanzu haka suka hanyar daukosu tare da Kanen Appan Alhaji Sa'idu sai kuma Kawu
Garba wani dan'uwan Hajiya Kaltume da kuma Yasir din duk a mota daya.

“Alhamdulillah”

Amma ta bada tana sauke wayar, jikinta ya hau tsuma ma dadi farin ciki ya ziyarci
zuciyarta ya mamaye ilahirim jikinta, dan zazzabin da take ji sama sama da rashin
kuzari duk sai ta neme shi ta rasa. Hurriya ta mike tsaye da sauri tana murna.

“Amma zan hau Napep na tafi gidan yanzu ina son Hamad ya dawo ina nan”

“Ai ni ma ba zan iya jira a nan ba, kira Gwaggo na fada mata”

Hurriya ta fita dakin da sauri ta kira Gwaggo, a nan murna ta kaure Gwaggo sai
Hamdala take, ta waya Gwaggo ta fadawa Bappa halin da ake ciki, sannan ta dauki
permission din fita tare da Iyami, sanin yadda ďa da uwa suke ya saka Bappa ya
amince su tafi ba dan wannan babban dalili ba ba zai taba yarda dayansu ya sake
takawa gidan ba, domin be manta cin mutunci da kuma wulakancin da Appa yayi masa
ba. Gwaggo da kanta ta fita makota ta samo direban da zai tukasu a motar Amma domin
bata iya tuka mota yanzu ita kuma ba iyawa ta yi ba, haka ma Rukayya balle kuma
Hurriya da bata gama girma ba ma. Gwaggo da Amma suka shiga baya, Hurriya ta shiga
gaba aka bar Rukayya tsaron gida, ba su isa gidan ba sai da suka biya suka dauko
Hindu domin dazun kamin ta bar gidan ta fadawa Amma idan aka dauko Hamad a fada
mata.

“Alhamdulillah Allah ya kawo mana su lafiya”

Shi ne abun da Gwaggo da Hindu ke Fada, direban da ya dauko su kuma yana kara basu
labarin yadda aka sace wani shi ma suka karbi kudi mai yawa.

“Kasar ce ta lalace Allah ka kawo mana sauki”

Amma ta amsa addu'ar da Hindu ta yi da Ameen daman bata cewa komai sai murmushi
take tana ta daukin arba da ďanta. Sai da ta isa gidan sai kuma ta soma tambayar
kanta me yasa ta zo? Wani bakinciki ya rufeta ta kasa shiga bangarenta da babu
komai ta tsaya, kuma ta ki yarda ta shiga bangaren Hajiya Kaltume daga ita har
Gwaggo a babbar harabar gidan da direba ya faka motarsa a nan suka tsaya suna jiran
isowar su Hamad.

**** **** ****

“Iyami kuma?”

Namra ta daga kai.

“Me ta zo yi?”

“Tarbon su Hamad mana Momy, kin manta yau za su dawo? Ya Yasir ma sun tafi gurin
dauko su”

“Au haka ne fa, kin san badan da babu ruwanka dadin kallo gareshi, ni na manta ma”

“Toh ina take”

“Tana can babbar haraba tsaye ita da wadanda suka zo har da Gwaggo da Hurriya”

Momy ta dan yi jimm kamin ta girgiza kai.

“Wallahi har ta bani tausayi, ta yi going though alot shekarar nan, ga ciki ga saki
ga sace ďa, da dai Appanku zai tausaya mata ya dawo da ita, ta rike yayanta ni na
huta ma, daman bana son rikon yayan wasu, dan na san yanzu Alhaji zai ce su dawo
gidan nan da zarar sun dawo kuwa ba su da gurin zama sai bangarenna.”

“Ni tausayi suke ba ni”


“To sarkin tausayi je ki ce su shigo cikin falon nan mana su zauna”

Namra ta wara ido with surprise.

“Su shigo Momy? Ko bakar mana kike min?”

“Toh ya za'ayi, ai da anyi haihu kuma zance ya kare, ba dan tana da yaya a gidan ba
ai ba zata zo ba, da zarar an haihu ai kuma shi ke nan sai hakuri, kuma dai an
girma kishi na miye ina zan tsaya kishi da karamar yarinya kamar Iyami? Level dina
kuma ba zai taba haduwa da nata ba, har abada dukansu na fi karfinsu sai dai ta
kara da Kaltume bakar akuya”

Namra ta tashi da kuzarinta ta fice daga dakin ta sauri ta sauko downstairs ta bude
kofar falon ta fita. Sai da ta fara gaishe su bayan ta isa gurin da suke a lokacin
Amma har ta kai zaune a cikin mota domin bata yarda ta zauna ko da a kujerun baki
da ake ajewa a gidan ba.

“Amma Momy ta ci ku shigo ciki ku zauna kamin su iso”

Amma ta kalli Namra tana murmushi.

“Ki ce mun gode zamu tsaya a nan”

“Ai tun da ita tace mu shiga, mu shiga kawai zai fi mana tsayuwa a nan”

Hindu na rufe baki, masu gadi suka bude gate motar da aka je dauko su Hamad da ita
ta kunno kai cikin gidan, gaba daya sai hankali ya koma can Hajiya Kaltume, Salma,
Maama Khairi suka fito daga bangaren Hajiya Kaltume da gudunsu har Hajiyar da jiki
ya hana ta walawa yadda take so, Namra ta shiga bangarensu da gudu kiran Momy. Appa
ma ya fito da waya a kunne sai dai fuskarsa babu annuri ko kadan, ba irin da wanda
ransa ya bace ba, rashin annuri ne irin na wanda ya rasa wani abu fuskarsa ma gaba
daya launinta ya canja. Amma ta fito daga cikin motar ta nufi motar da Yasir ya
sauko yana hawaye Ruma kuma na rutsar kuka.

“Ina Hamad? Ina Hamad?”

Amma ta tambaya domin yaronta ne kadai bata ga ya fito daga cikin motar ba. Aka
rasa mai ce mata komai har ta isa gurin ta tsaya tana kallonsu murmushin dake
fuskarta na kokarin gushewa.

“Yasir ina Hamad? Dan Allah ku amsa min...!”

“Amma sun kashe shi, sun kashe Hamad...!!!!!!”

Ruma ta fada da karfi tana kuka. Momy ta dora hannu saman kai tana fadin
Innalillahi. Amma kuma ta yi baya baya kamar mai tafiyar baya sai Hindu ta rike ta,
runtse ido ta yi ta kai hannunta ta dafa cikinta dake zillo ta durkusa a kasan
guiwoyinta ta dafa kasa. Hajiya Kaltume ma kuka take ta nufi yarta ta rika hannunta
da niyar rumgume sai Ruma ta buge hannun Hajiya Kaltume ta nufi mahaifinta tana
kuka ta rumgume shi yana hawaye, kusan kowa a gurin sai da yayi hawaye.

“Su ba mu gawarsa mana to mu gani, idan da gaske ya mutu su ba mu gawarsa mu gani


Wallahi be mutu ba, boye shi suka yi Hamad yana nan da ransa”

Hurriya ce take maganar tana kuka, Gwaggo ta rikota ta rumgume tana kuka.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya kin daukar
kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci
pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞5️⃣

Hurriya first lost her sight a jikin Gwaggon, before ta yi going blank aka kwasheta
ita da Amma sai Asibiti. Amma aka wuce da ita dakin haihuwa Hurriya kuma aka kaita
Emergency. After 49hours of labor Amma ta haihu tagwayenta biyu duka maza. A
madadin ta yi murnar ta haihu ta samu yan biyu sai murnar ta koma mata ciki saboda
tunanin Hamad bata da wani kuka sai na Hamad. The following day aka sallamo ta daga
asibitin bayan sun mata dinki kuma sun dorata akan maganin da zata rika sha na
hawan jini sannan suka hana ta wankan ruwan zafi domin jinin nata ya hau sosai irin
hawan da ba dan Allah ya kawo sauki ba, da abu ne mai wahala ta fita lafiya.

Har lokacin Hurriya tana asibitin Hajiya Binta na jinyar tare da taimakon Rukayya,
kwananta biyu bata san inda kanta yake ba a asibitin, kamin ta farfado sai kuma ta
zama so weak sai da ta sha drip da manyan allurar sannan ta samu sauki, the
following day ita ma aka sallame ta two days after an sallami Amma. Wani abun da ya
bawa kowa mamaki ciki har da Momy kuma ya daurewa Amma da Hajiya Binta kai shi ne,
kin lekawar Alhaji Haruna a asibiti ko gida da sunan duba Amma ko kuma duba yaran
da ta haifa masa, yan'uwansa na nesa da na kusa duk sun je duba twins din kuma sun
je duba Hurriya wasu ma ba su samu labarin abun da ya faru ba sai a da suka je
barkar twins. Sai dai Appa be bar rashin zuwa duba yaran da kowa ke musu lale da
zuwa duniya, ya hana shi kyautata musu ba, duk wata hidima ta ya kamata uba yayi ma
yayansa Appa yayi tun daga kan tufafin mai jego Amma har na jaririnsa, sai dai Amma
bata yi taron suna ba, duk kuwa da kasancewar ba ayi taron gaisuwa a gidanta ba, an
yi zaman makoki a gidan Appa kuma an masa sallatul ga'if wato sallar da ake yi ma
gawar da bata kusa. Ta ko'ina Appa ya karbi gaisuwar mutane ana ta jajanta masa.
All those days, hour's Hurriya a daki take rayuwa, domin bata son ganin kowa, idan
zata yi alwala sai ta shiga bathroom ta yi idan ta yi sallah ta kwanta, bata son
ayi mata gaisuwar Hamad, bata fitowa idan mutane suka tambayi ina take, idan kuma
aka shigo sai ta rufe kunnuwanta bata sauraren kowa, she's the only one da ta kasa
yardar Hamad ya mutu, ranar sunan yaran ma sai da ta saka kowa kuka, domin ihu take
ta yi me yasa Amma ta sakawa little one din Hamad yayan kuma Hamid.
“Amma da baki saka Hamad din ba, Wallahi Hamad be mutu ba, karya suke yi Amma dan
Allah ki cire, ki saka masa wani sunan ba Hamad ba”

Tana kuka tana rokon Amma a canjawa jaririn suna, Amma ta aje Little Hamad ta kama
Hurriya ta rumgume.

“Hurriya dole mu karbi wannan gaskiyar, tana da daci amman dole ne mu karbi
kaddara, duk yadda kike son Hamad na fi ki sonsa domin ni na yi nakudarsa na haife
shi, una jin fiye da yadda kike ji”

“To me yasa kika sama Amma? Why? Why?”

Amma ta girgita da karfi tana kuka.

“Saboda ya mutu Hurriya, baki daya Allah ya karba ya bamu biyu ba? Toh sai mu gode
masa, yadda ya so haka yake aikatawa, Hamad ya tafi tafiya ta har abada ya kamata
ki karbi wannan, wannan shekarar haka ta zo mana”

Hurriya ta saki jikinta sai ta lankwasa ta yi baya Amma ta sake ta ta fadi kasan
carpet din. Ita kam ta kasa yarda dan'uwanta ya tafi ya barta, fadan da suke yawan
yi yake damunta a yanzu, why take ramawa idan yayi mata abun? Ko wane motsi yana
tuna mata da dan'uwanta ne, bata taba sanin tana kaunarsa ba sai a yanzu da baya
kusa da ita, ina ma ita aka dauka ba shi ba haka take yawan ayyana a ranta. Kusan
kowa a gidan sai da yayi kuka kuma aka kasa wanda zai rarrasheta sai Yayanta Yasir,
domin shi kadai ya fahimci manufarta kuma ya mara mata baya cewar Hamad be mutu ba,
domin karbar gaskiyar cewar ya mutum shi ne ƙarya a zuciyarta.

**** **** **** ****

“Hajiya ki yi haƙuri dan Allah, bana son ina musa miki akan abubuwa, amman yaran
nan da Iyami ta haifa nawa ne, idan ina buƙatar ganinsu ba sai na jira wani ya ba
ni shawara ba, ayukan ne sun min yawa a yanzu amman da zarar na samu lokaci zan je
na duba su, idan suka yi ƙwari ma aka yayensu ɗauko su zan yi na dawo da su gidana
domin zuciyata ta fi amintuwa da haka”

Hajiya Binta ta kalleshi tana mamakin yadda yake ita bude baki ya musa mata a duk
lokacin da ta yi masa maganar zuwa duba Twins din da Amma ta haifa.

“Tsoho me yake damunka? Wani lokaci ne baka da shi akan iyalinka?”

“Hajiya kin san kasuwanci ba daya ba, kuma idan ina son ganin yaran nan ni zan je
da kai na, ina cw dai na sauke duk wani hakki na uba?”

“Toh baka bukatar ganinsu kenan? Haka kake nufi? Toh ni da nake bukatar ganinsu zan
tafi, ko miye ya rufe maka ido ka kasa taka kafarka gidan Iyami Allah ya yaye maka
shi tsoho, yau sati daya da haifa maka yan biyu kyautar Allah amman ka kasa taka
kafarka ka duba yayanka”

“A gaishe su, Hajiya zan leko in Shaa Allah, kuma idan kin tafi ki fada mata next
week Hurriya zata dawo zan aiko da mota a dauke ta saboda makaranta”

Yana maganar yana mikewa tsaye abun da be saba yi ba, ko magana Hajiya Binta take
masa baya iya daga kai ya kalleta tsabar biyaya amman a yanzu duk ya canja mata,
abun da be yi mata da kurciya ba a yanzu da girma ya kama shi yake canjawa. Baki
saki Hajiya Binta ta fi danta da kallo har ya fice sannan ta girgiza kai hawaye na
cika idonta.

“Allah ka shirya bawan nan naka, Allah ka karya duk wani abu da aka yi masa
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ta rafka uban tagumi tana kokarim ganin bata bar hawayenta sun zubo ba, domin ta
san illar zubar hawayen uwa ga ďanta. Appa har ya isa gida bw daina ganin laifin
Hajiya ba, ganin yake tana kusa masa cikin al'amurran da be kamata ta saka kanta
ba, shi dai aka haifawa yara to damuwa kuma na me tun da har be ce ba yayansa ba
ne, kuma yayi musu duk wata hidima da ya dace uba yayi ma ƴaƴansa. Ba ta inda ya ji
sayin kamar ta gurin da Hajiya Kaltume take taba masa ita ma tana dorawa Hajiya
Binta laifi, tana bashi gaskiya na kin son zuwan da yake.

“Gaskiya Hajiya ba a haka, ai sai ta saka maka ido ta gani, ina laifin bayan duk
wata hidima, kuma yara idan suka yi wayo ai sai ka dawo da su nan gurin Momy ta
cigaba da kula da su, tun da tana da masu aiki ba daya ba za su rika musu komai”

“Ni ma haka na gani, amman ta kasa fahimtata sai laifina take gani, gaba daya ta
rufe ni da fada”

“Toh ya ka ayi, sai hakuri ka san bata hada Iyami da kowa ba a gidan nan, duk dai
abun da yayi dalili ya raba amman dai Hajiya bata dauki kowa sukarta ba sai Iyami,
wai ni yaushe Hurriya zata dawo ne Alhaji”

Tana maganar ya aje kofin ruwan dake hannunsa ya amsa mata.

“Next week, na fadawa Hajiya idan ta je ta fadawa Iyami zan aiko da mota a daukota
saboda makaranta”

Hajiya Kaltume ta dan tabe baki tana shafa zanen atamfar dake jikinta.

“Makaranta ma ai bata jira Alhaji, yanzu kan sai dai a canja mata makaranta a maida
ita Government School, ko ba komai ta dan rage kewar Hamad dan na san abun zai yi
da damunta, amman idan ta koma wata makarantar sai ta samu sabin kawaye kewar zata
dan ragu, kuma ka ga yanzu private school ai duk an yi nisa da karatu sai dai ta
Gwafnati ita ce za su karbe ta ko dan lalurarta”

Appa yayi shiru kamar mai nazari, idea Hajiya Kaltume na cewa a saka ta wata
makarantar ta government be masa ba, sai dai ba zai iya nuna mata haka ba.

“Ko kuma a kaita wata makaranta, amman makaranta government bata cika kyau ba,
bayan kuma ga duka yan'uwanta a private suke, kuma kudin biya makaranta ai akwai
shi ba babu ba”

“Ba shi zaka duba ba, yadda Hurriya take da kokari a makaranta ko'ina zata iya
karantu, kuma zata gane kamar sauran yan'uwanta daman kuma ta fi su basira, ni dai
gaskiya shawarar da nake baka Alhaji a kaita government schools kuma bana son ka
musa min akan haka, kai fa ka san Hurriya kamar ƴa take a gurina, yadda ba zan so
abun da zai cutar da Ruma ko Khairi ba ita ma ba zan so abun da zai cutar da ita
ba”

“Shi ke nan, tun da haka kike so, za'ayi, Allah ya tabbatar mana da alheri”

Fuskar Hajiya Kaltume ta fadada da murmushi.

“Amin Alhaji na, Allah dai ya kara rufa asiri, ya kara wadata”

“Ameen”

Ya amsa cikin rashin dadin rai da be isa ya nuna a fili ba. Abun ku da makirar mace
haka ta rika jan sa da hira tana tabo bangagori da dama na kasuwanci, sai dai be
yarda ya fada mata abubuwan da take son sani ba, sai dai ta fahimci wasu bangarorin
da kuma har ta nuna masa sha'awar na son fara kasuwanci. Appa ya saka dariya.

“Kaltume ina zaki iya kasuwanci crude oil? Kina mace? Wannan kuma ai sai mu maza”

“Hmmm Alhaji ka manta karin maganar da hausawa suke cewa duk abun da namiji zai iya
mace ma zata iya? Ai mata ma kansu ya waye yanzu ana damawa da su sosai akan crude
oil a yanzu”

“Amman yan boko Kaltume ke da ko primary ba ki yi ba ina ke ina wannan kasuwanci?


Da ma dai Nafisa ce tace zata yi ba zan musa mata ba, domin ita tana kasuwanci
sosai ta san kan kasuwanci domin shi ta karanta kuma mahaifinta ma kin san waye shi
ba sai na fada miki ba, amman ke Kaltume ina ke ina wannan kasuwanci?”

A take fuskarta ta canja domin ya tabo mata inda bata so, dauko zancen Momy ya ce
ta fita wani abu, bayan kuma ya gama yaga fuskarta cewar ko primary bata yi ba.
Alhalin kuma gaskiya ya fada haka ta yi rayuwa rayuwar kauye ba arabi ba boko sai
talla kamin ya aurota.

“Alhaji na ga dai kai ma ba kasuwanci ka karanta ba, amman kake kasuwancin nan
gashi nan kuma yanzu ka koma dam bokon har turanci kana ji”

Appa ya cire gilashin idonsa yana dariya.

“Kaltume ni fa na yi boko kuma na yi zurfi kawai dai rayuwa ce ta yi tsanani kuma


kasuwancin ya fi tsaya min a rai shiyasa na watsar, na fara kasuwanci kuma da yake
arzikin a nan yake kin ga a yan bokon ne a karkashina, amman ke Kaltume da ko
sunaki ba zaki iya dubutawa ba Allah cutarki za ayi”

“Ga yayana zasu min komai”

“Matan dai ai kin san aure za su yi, Yasir kuma abu ne mai wahala ya rike kasuwanci
domin na lura hankalinsa ya fi karkarta a bangaren aiki, bayan nan ma kasuwancin
Crude oil yana bukatar kudi mai yawa sai mutum ya tsaya da kafarsa”

“Zan dan hada abun da yake hannuna na ga zai kai nawa, sai ka kara min da wani haba
Alhaji ina matar Alhaji Haruna Mai Yadi ai wannan kasuwancin ba zai gagara ba”

Tana maganar har da wani daga masa gira kamar wata tsohuwar kasuwa. Appa dai yayi
murmushi ya girgiza kai. Sai da aka kira sallah azahar sannan ya fita gidan ita
kuma ta fito daga bangarensa ta nufo nata tana tunanin yadda zata zama daya daga
cikin attijiran matan jihar Zamfara idan ta fara kasuwancin, bayan kasancewarta
matar Alhaji Haruna Mai Yadi, so take ta mamaye ko'ina ta sha gaban Momy a yanzu,
ta yadda ita kanta Momy sai ta yarda Hajiya Kaltume ta fita komai. Ta shigo falonta
cikin yanayi na farinciki da jindadi ta tararda duka yaranta suna zaune falon suna
hira ban da Ruma da tun da ta dawo ta ware kanta daban take rayuwarta ita kadai ba
tare da sauran yan'uwanta ba, haka ma ba ta sake kusantar mahaifiyarta ba, a baya
kuma ba haka take ba ita ce yar autar Hajiya Kaltume kuma ita ce shagwababbiyar yar
rikon jakar Hajiya.

“Hirar me kuke yi?”

“Yadda zamu tashin garin nan idan Allah ya nuna mana bikin Maama”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi.

“Gaskiya ne, za ayi biki na ban mamaki daman wasu daga cikin abokan mahaifinku ba
su san ma ya taba aurar ba”

Maama ta saka dariya


“Hajiya wake maganar auren Sapna auren kauye kuma tun kamin Appa yayi suna, aurena
dai za'ayi aure na ji da fada da zai tashi hankali media ya zama topic of
discussion a Gusau”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi kamin ta bi kowa da kallon.

“Toh Allah ya nuna mana, shi ma angon na ki na lura ai dan son riya ne”

“Wallahi haka yake, yace aurensa na farko auren hadi ne shi kuma baya son matar aka
masa dole shiyasa be wani bada jiki ba, amman aurena ko hmmmm”

Duk suka dariya. Khairi ta ce

“Yaya Maama yana sonki Wallahi da alama kan waccan matar tasa zata sha wahala a
hannunki”

“Kar ma ki ji yadda yake zaginta ni har tausayi take ba ni”

“Ba a tausayin mata ai Maama raba kanki, kina shiga gidan nan idan ta samu sa'arki
waje za ayi da ke, wai ina Ruma?”

Hajiya ta karasa tana tambayarsu yar autarta domin ta zagaye falon da kallo bata ga
Ruma ba. Salma ta ce.

“Hajiya kin san Ruma tana dakinta fa, yanzu ta mai da kanta aljanna bata son mutane
ko kadan”

“Oh ni wannan yarinyar”

Hajiya ta nufi hanyar stairs, sai da ta yi kamar ta shiga dakinta sai kuma ta nufi
dakin Ruma ta tura kofar dakin ta leka, zaune ta hangowa akan studied table dinta
tana rike da wani textbook tana karantawa.

“Ke...!”

Ta juyo ta kalli Hajiya Kaltume. Sai ta shigo cikin dakin ta maida kofa ta rufe ta
nufeta tana fadin

“Wai ke wani sabon iskanci kika kirkira yanzu da rainin wayo? Sai ki ware kanki
dabam kina rayuwa kamar wata mayya?”

A take idonta ya cika da ruwan hawaye.

“Bana son gidan nan Hajiya, na fada miki ina son na koma gurin Hajiya Binta da zama
ko Anty Farisa”

“Babu inda zaki je, babu gidan uban da zaki zauna idan ba zaki iya rayuwa a nan ba
sai ki hadaye zuciya ki mutu”

Hajiya ta fada cikin bacin rai sannan ta juya daf da zata kai hannu ta bude kofar
dakin Ruma ta mike tsaye ta ce.

“Har yanzu Hajiya gani nake kamar ba ke bace, na san baki son Amma amman kisan kai
Hajiya kisan kai? Baki ga yadda suka fasa masa kai ba, ko'ina jini yake, still kuma
suka karbi kudin nan gurin Appa, Hajiya mamaki nake yadda zuciyarki zata iya aikata
haka, kullum sai na yi mafarkin Hamad abun da na gani ya kasa fita a idona ni kam
ina ma ba ke ce uwata ba...”
Hajiya Kaltume ta juyo a fusace ta nufo Ruma gadangadan, tana isa gurin da Ruma
take tsaye tana hawaye Hajiya Kaltume ta dauke ta da mari ta rufe ta da duka.

“Yaushe wuyanki yayi tsauri haka har bakinki ya iya furta kalamai irin haka? Dan
ubanki fuskata kika gani tare da mutanen ko kuma gurin kika gan ni?”

Cikin kuka Ruma ta soma bata amsa.

“Amman sun yi magana dake lokacin da suka dauko mu, Hamad ma ya ji muryarki shiyasa
kika ce a kashe shi”

Hajiya Kaltume ta yi saurin rufewa Ruma baki tana juyata ta kalli kofar dakin,
sannan ta juyo ta kalli Ruma tana kuka.

“Wallahi ban ce a kashe shi ba, Yaushe zan ce a kashe shi? Wallahi ban ce a kashe
shi ba, kuma Wallahi idan wani ya ji maganar nan Ummu Rumana sai kin yi bakincikin
zuwa duniya”

Hajiya Kaltume ta sake ta fice daga dakin da sauri tana share hawayenta, da hakki
ta isa nata dakin ta zauna bakin gado kamar wadda ta yi gasar tsere hakki ne na mai
jin tsoro da fargaba faruwa wani ba, ba na wanda yayi wani aiki ba. Da sauri ta
lalabi wayarta ta kira macen da ke share mata kukanta...

“Hajiya Fatee ke kadai kike?”

“Ni kadai nake Hajiya Kaltume Lafiya?”

Hajiya Kaltume ta fashe da kuka tana fada mata abun da Ruma ta yi mata.

“Ah toh ita kuma duk saboda wa kike abun?”

“Ita wannan bata gani ai, da ma Khairi ce ita ce mai irin zuciyata, kuma ni Wallahi
ban dauki yaron nan dan a kashe shi ba, kaddara ce kawai ni ba ma shi na so a dauka
ba, yar makauniyar na so a dauka, amman abu ya zo a haka”

“To yanzu me ye abun yi?”

“Abun yi kawai a rufe mata baki, domin na lura tona min asiri zata yi, tun da ta
dawo gaba daya ta bi ta canja, sai zancen barin gidan take nan gaba kadan zata iya
cewa zata fadawa wani idan abu ya cika”

“Lallai da maganarki, haka ya kamata, daman ita bata san kan duniya ba shekara goma
sha bakwai miye ta sani, ai da gaskiyarki da baki saka ta a lamurranki duk da shige
miki da take da sabon da kuka yi, wannan ai sai ta fadawa duniya mun je gurin kaza
da kaza”

“Ina zan yarda? Ai duk yarana bana zuwa da ko daya, sai dai na fada musu”

“Haka ya kamata gaskiya ki kirashi ki fada masa komai idan akwai yadda za ayi a
danne bakinta nan dan kar ta fada”

“Zan kira shi, daman ban gama fita bakincikin Iyami ba yanzu kuma ita zata tsirar
min wani sabon shafi”

“Wallahi kuwa shegiyar dagar ta sake jefo masa yan biyu haihu kamar karya kuma duk
maza, ta dai rantsa sai ta ci gadon Alhaji daman shi ne take ta yi ma wannan haife
haifen, ai Wallahi an rage mugun iri ma, yaron nan ba fadar kike yana damunku”

“Wallahi ya addabi kowa, kuma ni ba shi na ce a dauka ba, iya yar macijiyar na ce
a dauka, su kuma sai suka bata aikin suka kira wayata a gabansu yaro ya ji muryata,
shi ne duk sila ni kaina kullum tunanin yaron nan nake nake Wallahi abun ya hana ni
sukuni sam”

“Allah dai ya rufe asiri kar wannan yar autar taki ta janyo mana jagwal”

“Ameen, ai maganinta zan yi”

Daga haka suka yi sallama, babu bata lokaci Hajiya Kaltume ta lalabo number
Malaminta a wayar ta kira shi domin kai masa kukanta, daman kiran Hajiya Fatee da
ta yi na neman jin shawarar abun da zata ce ne domin bata yanke hukunci sai ta
shawarci aminiyarta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
.𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞6️⃣

The following week Appa ya aika mota dauko Hurriya, a lokacin ne hankalin Amma ya
tashi sosai daman babu irin magiyar da bata yi ma Hajiya Binta ba a lokacin da ta
zo mata da sakon cewar Appa zai aiko da mota a dauki Hurriya next week, Hajiya
Binta ma ta yi iya kokarinta amman be saurareta ba, saboda ba zai iya tsabawa abun
da Hajiya Kaltume take so a yanzu ba, ita kadai zata ba shi shawara ya dauka bayan
ita baya sauraren kowa ciki har da mahaifiyarsa da kuma Momy da bata ma gane kansa
yanzu, sai dai bata cika damuwa da al'amurransa ba domin ta bussinees dinta take da
harka da manyan mutane. Son ta mallaki gida ko ta mallake Alhaji Haruna baya
gabanta domin jin take kamar ma ta kusa gogawa da shi a arziki. Hurriya kamar zata
shide haka aka fito da ita daga gidan ita kuka Amma kuka Gwaggo kuka Rukayya kuka
tana rikon Amma amma na rike ta kamar wadanda za a raba rabuwa ta har abada. Ita
dai bata son komawa gidan saboda babu dan'uwanta mai tare mata fada a cikin haka
kuma babu mahaifiyarta, kuma a yadda ta fahimta ba zata sha da dadi kamar da ba a
hannun Appa yanzu. Amma kuma tana jin kamar za a kara mata kewa ne domin babu Hamad
a kusa da ita a yanzu Hurriyar take gani tana jin sanyi yanzu kuma za a dauke ta.
Har aka iso gida da ita kuka take sosai kamar na mutuwa, gaba daya ta bi ta rike ce
da direban yayi parking ta rasa ina zata shiga bangaren Hajiya Kaltume ko Momy
gurin da dakinta yake a yanzu, ko kuma bangaren mahaifiyarta da babu kowa a cikin,
kamar wata bakuwa haka ta rika kallon gidan.

“Hurriya”

Ta dago da sauri ta kalli Dattijon direban da ya kawo ta, jikinta na rawa.

“Ki yi hakuri ki yi da addu'a babu abun da yake daurewa”

Tana kokarin amsa masa da kai sai ta kasa, daman shi kam baki ba zata iya furta
komai ba.

“Ina zaki je? Gurin Momy ko gurin Hajiya Kaltume?”

Sai kawai ta fashe masa da kuka.

“Ko kuma gurin Alhaji zaki je? Yana nan ciki daman yace ba zai fita ba sai kin
dawo”

Ta daga kai da sauri, sai ya kama hannunta suka isa bangaren mahaifinta sai da suka
isa daf da kofar falonsa sannan ya saki hannunta.

“Ki shiga ciki”

Ta daga masa kai, sai da ya wuce sannan ta kwankwasa kofar part din kamar wata
bakuwa bayan ba haka ta saba ba, idan zata shiga bangaren Appanta sai dai ta tura
ta shiga da murnarta tana rangada sallama. Sai da ta yi knocked sau uku sannan ta
tura kofar falon ta shiga, sanyin ac ya fara yi mata maraba da zuwa, kaminnta juyo
muryar mahaifinta a dayan falon da alama waya yake, babu komai a hannunta sai
carbin Amma da ta dauko, tufafinta ma sai daga baya za a dauko mata ko kuma ta yi
using wadanda suke gidan na bangaren Momy. Hawaye na sauko mata kamar ba gobe haka
ta shiga karamin falon tana ta son ta bude baki ta yi sallama amman ta kasa. Appa
na ganinta a take annurin dake fuskarsa ya gushe kamar wanda yayi arba da bakin
maciji, a take ya yanke wayar da yake ya mike tsaye ya nufota yana fada.

“Ya aka yi? Kin dawo kina ta yi ma mutane kuka mutuwa aka yi? Ni ba dan Kaltume ta
matsa ba ai sai ki zauna can a gurin uwar taki”

“Appa”

Ta furta tana kallonsa gilashin dake mata garkuwa na daf da faduwa. A madadin ya
amsa sai yace waye bana son jin muryarsa ba ke ba, a take korata ya saka ta gaba.

“Muje can bangaren Nafisa tafi tafi”

Ta tsaya a gurin tana kallonsa kamar hoto har ya iso, ganin ba tafiya zata yi ba ya
saka shi fisgar hannunta ya wuce gaba ya hanyota sai kallonsa take har suka isa
cikin falon Momy ya sannan ya saki hannunta. Kamin ya ce komai Momy ta aje plate
din doyar dake hannunta ta rafka salati.

“Haba Alhaji, ina laifi ka barwa Iyami yarinyar tana ganinta tana jin sanyi? Ni dai
tsakani da Allah hankali ya fi kwanciya yarinyar ta zauna a gurin uwarta”

Ita ma kamar Appa na jiranta sai ya rufeta da fada.

“A nan nake son ta zauna, a nan zata zauna ke kanki gurin da na ga dama zaki zaun
balle kuma ita da take yata, karki sake fada min abun da ya kamata na yi, ba
shawararki nake nema ma”
Tabe baki ta yi bata sake cewa komai ba har ya fice, sannan ta ce

“Ni ma dan an rasa ya za'ayi da ni ne, na cika na make gurin kuma sai hakuri
Wallahi, ni da zai maida Iyami ki koma can gurinta ya fi min kwanciyar hankali, ina
zan iya da rikon yayan wasu yayan da idan suka girma suka samu arikin uwarsu za su
nema”

Hurriya dai tana tsaye a gurin da Appa ya barta ta kasa matsawa ko'ina sai hawaye
take. Mahaifinta ya canja mata, ta rasa dan'uwanta kuma ta rasa mahaifiyarta a kusa
da ita.

“Lafiya kika tsaya nan kika zuba min ido? Mahaifinki ma baki da amfani a gurinsa
yanzu balle kuma ni, wuce ki tafi dakinki tun da an kawo min kaya ya zan yi, Iyami
ta haifa mana ta tafi ta bari”

Huriyya ta dauke kai da sauri ta fara tafiya, sai kuma Momy ta kirata.

“Hurriya”

Ta juyo a hankali ta kalleta ta kasa amsawa har lokacin hawaye take.

“Zo ki zauna yi hakuri kinji”

Hurriya ta dawo ta zauna saman kujerar dake dama da Momy.

“Gaskiya dai Alhaji ya ci amanarki Wallahi, ni ai ko da bala'i sai na karbi yayana,


ko da yake Iyami ba zata iya ja da Alhaji ba, ta ina talauci zai ja da arziki,
amman dai gaskiya be dace ya rabaki da Iyami yanzu ba, ai sai tunanin ya hade miki
ga na dan'uwa ki kamu da hawan jini da kurciyarki, kai Kaltume bata da imani, haka
fa ta raba Sapna da ubanta, Sapna bata isa ta tako garin nan ta ce zata zo gurin
ubanta ba, tana can kauye cikin talauci shi kuma ya kyaleta... Hmmmm”

Ta mike tsaye tana kwalawa mai aikinta kira.

“Bilki”

Tsohuwar ta fito da gudu daga kitchen, daman haka take da yan aiki idan tana falo
sai dai su boya a wani guri bata zama daki daya da su, idan har ka gansu a falo to
tana dakinta ne ko kuma ta fita.

“Hajiya ga ni”

“A dauke plate din nan kuma ga yar Iyami nan idan zata ci abinci a zuba mata”

“Toh Hajiya”

Tsohuwar ta dauke plate din sannan ta kalli Hurriya dake zaune.

“Hurriya a zuba miki abinci?”

Hurriya ta girgiza kai alamar aa, Momy tabe baki ta dauki wayarta.

“Dan kan masa in ji sure, cikinki ko na wani, kin san dai ba rarrashinki zan yi dan
ki daina kuka ko ki ci abinci ba, ina da tausayi da zuciyar imani amman laisa son
dan wani kamar nawa kam karya haram babu boye boye ba munafurci, shiyasa ni na fi
sha'awar uwarku ta dawo ta rike yayanta”

Tana fadan tana hawa sama har ta haye ta shige dakinta, Mai aikinta kam tuni ta san
inda dare yayi mata. Hurriya ta bi ta kallo har ta haye stairs din, ji ta yi kamar
ace wani na nan ta fada jikinsa ya rumgume ta yi kuka ammab babu wannan damar,
saukowa ta yi daga saman kujera ta zauna kasa sai ta dora kanta sama kujera ta
takure guri daya. Ta rufe ido hawaye na sauko mata. After like 30min ta ji an
zungureta sai ta farka da sauri gilashin idonta ya fadi da sauri ta dauka ta saka
ta gyara mayafin abayarta ta kalli Musib dake tsaye kanta.

“Miye na yi ma mutane bachi a kujera kin wani takure salon wani ya shigo ace ke ce
marar gata a gidan ke ga munafuka, wato kin dawo babu zaman lafiya, mun rabu da
Hamad ke kuma zaki kirkiri mugun abu ko?”

Kamar wani mace haka yake fada da ita yana gautsina fuska, gently ta mike tsaye
domin ita ma bata san bacci ya dauke ta sai da ya tasheta. Tafiya ta fara yi ta
haye sama ta dade a tsaye tana kallon kofar dakin Hamad tana jin kamar idan ta tura
zata ganshi kwance ya ba kofar baya kamar yadda ya saba kwanciya. Wani hawayen ya
sake cika idonta wani abu mai kama da dutse ya tsaya mata a tsakiyar zuciya ya mata
nauyi. Cikin karfin hali ta kai hannu ta tura kofar dakinta ta shiga sai da maida
kofar ta rufe ta jingina jikin kofar ta rumgume hannayenta not knowing what to do
ita dai ba kuka take ji ba a yanzu, hawaye ne kawai ke mata zuba, tunanin dake
mabanbantan duniyoyi ya hade mata guri daya, idan ta tuna Hamad ta tuna Amma, ta
tuna Appa. Jin ta yi an yi knocking kofar dakin wani abu mai kama da tsoro ya
fisgeta ta tashi tsaye da sauri jikinta na rawa ta yi baya tana kallon kofar, Namra
ce ta turo kofar ta shigo da far'arta.

“Hurriya kin dawo”

Kamin ta rufe baki Yasir ya shigo cikin yanayi na damuwa yana kallonta.

“Hurriya”

Ta kasa amsawa Namra balle Yasir da ya shigo bayanta, ta hade yawu da karfi tana
kallonsu. Yasir ya nufi gadonta ya zauna ya rasa me zai ce mata shi kansa be jin
dawowarta gidan a yanzu mafita ne a gareta, babu yadda be yi ba wajen ganin ya
fahintar da Hajiya Kaltume akan ta hana Appa dauko ta amman ta kasa fahimtarshi.

“Hurriya zauna”

Ta zauna a gurin kamar wata wadda tunani ya birkicewa kwakwalwa. Namra dai ta tsaya
jikin kofar ita ma tara ran duk babu dadin ganin yar'uwarta cikin damuwa.

“Hurriya ki yi hakuri dan Allah, idan kina kukan nan sai ki saka kanki a damuwa”

Yasir ya daga ma Namra hannu alamar ta daina maganar sai ta yi shuru ta juya ta
fice daga dakin, dan zumudin da ta zo da shi na murnar dawowar Hurriya sai ya
gushe.

“Hurriya kina son zama nan ko kin fi son zama gurin Amma? Idan gurin Amma kike so
zan mu tafi tare da ni dake mu yi ma Appa magana, idan be amince ba sai mu fadawa
Hajiya Binta”

Ta girgiza kai alamar bata aa.

“Kina son zama nan din?”

Ta daga masa kai.

“Shi ke nan zo ki kwanta, kin yi sallah ko?”

Ta amsa masa da kai sannan ta nufi gadon ta kwanta shi kuma ta tashi ya fice, kai
tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa sai dai yayi rashin sa'a be tararda shi ba, domin
tuni ya fita after ya kai Hurriya bangaren Momy daman ita kawai yake jiran a dawo
da ita gidan ya fita, saboda Hajiya Kaltume ta fada masa idan be yi da gaske ba
Amma ba zata ba shi Hurriya ba.
Hurriya bata tabbatar da mahaifinta ya daina yayinta ba sai da ya canja mata
makaranta ya saka ta makarantar government, yayinda sauran yan'uwanta da suke ajin
karshen a private school suke can suna karatu. Ita kuma aka bata direba daya da zai
rika kaita makaranta yana daukota ita kadai, ba karama ta kaddama aka yi ba kamin
Appa ya saka ta government school, domin malaman dake karantar da ita a private
school suna sonta sosai saboda kokarin da take da shi, ga kuma gasar da suke ta
shirye shiryen turata. Har komiti suka hada na manyan makarantar suka zo har gida
suka tarardar Appa suka tattauna da shi tare da nuna masa illar cire Hurriya a
makarantar amman ya ki saurarensu saboda Hajiya Kaltume ta ba shi shawarar kaita
makarantar Government, daga karshe ma sai suka rabu cikin rashin dadin rai domin
Appa rufe su yayi da fada ya nuna musu Hurriya yarsa ce shi ke da iko da ita babu
wanda ya isa ya fada masa me zai yi akan yarsa hukuncin da ya yanke ke nan kuma
babu fashi.
Ta bangaren Hurriya ma hakan ya taba ta sosai domin yin sabin abokai da kuma canja
wasu abubuwa na karantu domin malaman ba daya ba be ya zama abu ne marar sauki a
gareta, hakan sai ya saka ta zama weak ta yadda bata iya maida hankali ta yi
karatun yadda ya dace, gaba daya ta koma kamar ba ita ba, karatun da take ganewa a
can bata ganewa yanzu, sai ayi darasi a gama bata fahimci komai ba, tunani da
damuwa suka taru suka yi mata yawa, gashi kullum ita ce cikin kebe kanta bata son
shiga cikin yan makarantar da bata saba da su ba.

**** **** ****

Hindu ta mika mata jaririn dake kuka.

“Iyami ina ta fada miki banza bata fitar da ke gidan Alhaji, amman kika sa kafa
kika yi biris da maganata, yanzu gashin bayan fitar da ke ta dauke hankalinsa daga
kan Yayansa, bayan an a kashe miki daya, kuma han karbe dan abun da yake hannunki,
ina dadi ka haihu gari daya da miji amma yaki ya tako ya duba yara, ke da da ns
yadda Alhaji yake sonki ai kin Allah kadai ya san yadda zai rika dauki yana hauka
kin haifa masa yaya biyu kuma maza”

Amma ta Hamid dinta dake shan nono ta ce.

“Hindu ban saba irin abubuwa nan ba, ni Wallahi ban san kowa mai irin wannan aikin
ba, kuma ni ina tsoron kauce hanya”

“Babu zancen kauce hanya, ai ba shirka zamu yi ba, kuma ba cewa zamu yi ayi mana na
Sherri ba, aa mu dai kawai a karya sihirin da ta yi miki da na yayanki hankalin
mijinki ya dawo ki koma gidansa ki rike yayanki, domin nan gaba kadan ma zai iya
cewa su ma wadannan karbe su zai yi, tun kina cikin idda na so a nemi taimakon nan
kika ki gashi yanzu har sai an sake daura aure”

“Hindu da dai mun hakura, komai fa yana da iyaka wata rana zai karye ko da ba ayi
komai ba indai asiri ne.”

“Toh shi ke nan zauna a gurin, kina sakawa zuciyarki bakinciki ki lalace a banza ki
zama bar tausayi daman haka suke so, yar ki kuma ta koma yar aikin gidan, idan ma
ta yi sa'a kenan ita ma ba su kashe ta ba, nan gaba kadan idan ta girma ki rasa wa
zai aureta, domin Wallahi ba zata yarda Hurriya ta yi aure ba ga nata yayan ko da
kuwa sun yi aure, yanzu kina kallon yadda aka cireta ko ran mahaifinta, makaranta
ma sai ya sakata a jnda karatunta zai lalace ba dan kuma ba shi da hali ba, sai dan
an shiga tsakani”

Amma ta kalleta tana nazarin kalamanta ita kanta a yanzu ta yarda ba a banza Appa
ya canjawa Hurriya makaranta ba, yarinyar da yake alfahari da basirarta har yana
ikirarin fitar da ita waje ta yi karatu amman a yanzu ya cireta daga makarantar
kudi ya maida ita makarantar government.

“Tun ina Amarya lokacin da aka hade mu, ta taba ce komai ta dade sai na bar mata
mijinta, kuma sai ta saka ni na yi nadamar auren Alhaji, har abada kuma ba zata
taba son ko ta so yayana ba, domin kallon da take min na yar aiki be canja ba a
idonta, sai ta kakkabe ni kamar yadda ake kabe tabarma a gidan da yardar Allah, tun
da na ci amanar ta sai na gani”

Hawaye ya sauko mata.

“Gashi kuma na fara gani, Wallahi da na san zuciyar Hajiya Kaltume ta kai haka da
ba zan yarda na auri Alhaji ba duk kuwa da irin magiyar da zai min”

“Oh Allah mai iko, toh wai haka zaku zuba mata ido shikenan ta kashe Hamad ta ci
bulus”

“Ba mu da tabbacin ita ta kasheshi, ba Hamad din muka gani ba balle ya fada mana
ita ce ko ba ita ba, ko da ma ance yana raye ba lallai ne ya gane ita ta aikata ba,
kuma ba jami'an tsaro suka kamata ba, ba mu da wata hujja ta cewar ita ce kawai dai
zato muke yi”

Hindu ta sauke ajiyar zuciya ta yi tagumi.

“Toh ni Kam Alhamdulillah ina da kishiya amman Wallahi ba kamar ta ki ba, ba a aure
aka aurota miye laifinki wani yace kar ta iya kula da mijinta, ba mai aiki ba
namjji ko uwarki aka hallata masa aure Wallahi wani sai ya aureta balle kuma mai
aiki, har yaushe zaka dauki hakki ka dorawa kanka”

“Wallahi ni kadai na san abun da yake damuna, wata rana ji nake kamar na yi ta ihu
wani lokacin kuma na ji kamar na bi hanya na yi ta tafiya, wani sa'in na ji kamar
zan yi hauka, gaba daya ni ma neman fita hayyacina nake”

“Au kuma shi ne kike zaune? Kuma Gwaggo ta saka miki ido? Wallahi zama be gan mu
ba, idan ma ke ba zaki iya ba ni zan nema idan na kawo miki karki sha”

Hindu ta mike tsaye a fusace ta figi mayafinta tare da jaka ta nufi dakin Gwaggo,
domin fahimtar da ita abun da Iyami ta gagara ganewa. Amma ta share hawayeta da ya
zuba a fuskar Hamid.

“Wallahi na yi damar auren mahaifinku, na janwa kaina bala'i na kai kaina cikin
manyan mata da ba su da imani babu tausayi, gashi na jefa yarana a cikin matsala,
ban san kuma gaba ba me zan gani ba”

Ta fashe da kuka sosai tana jin zafin mutuwar Hamad, ga zafin rabata da Hurriya da
Appa yayi ga kuma zafin mutuwar aurenta a lokacin da bata yi tsammani ba, ga kuma
zafin ta haihu ya kasa zuwa ya duba abun da ta haifa balle ya saka musu albarka.

______________

Wai ni kam Tsakanin Hurriya da Amma waya fi kowa ban tausayi?

A Next page zamu dunguma a labarin Hurriya, karku manta sunan littafin Hurriya, a
yanzu ne zai amsa cikaken sunansa.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞7⃣

Two days later...

Hindu ta ciro gorar ruwa dake cike da rubutu ta aje a gaban Amma.

“Yace wannan ki sha shi a tsaye kuma ki shafa zaki yi haka har kwana 7, na karya
sihiri ne da tsari sosai”

Amma ta kai hannu ta dauka tana juya rubutun.

“Rabawa zan yi har bakwai kenan”

“Eh wannan kuma na hayaki ne, wato matar nan ba karamin asiri ta yi miki ba na
shiga tsakaninki da Alhaji, kuma yanzu haka tana nan tana shirin yin wani akan
Hurriya”

“Shi ma dai tsafin yake kenan?”

“Aa ba tsafi yake ba, kawai dai yana duba ne da kasa, ke ya dubo mana abubuwa da
yawa fa, Wallahi ya ce yanzu haka ta yi miki jifa kuma tana daf da samun idan kuma
ta same ki rayuwarki zata canja sai kin zama abar tausayi, ya ce idan baki tashi
tsaye an yi yanka ba an maida mata da jefarta to zaki koma kwance ne, kuma ya
tabbatar min idan aka yi haka ba jefarta ko asirin da ta yi sai ya karye”

Amma ta aje rubutun da sauri.


“Subhanallahi, Subhanallahi Hindu kin ji abun da nake gudu, wannan ai shirka ne”

“Wane irin shirka kuma? Ke fa matsala ne da ke, mu da muke neman warware sihiri? Ba
fa sheri zamu yi ba warware ne”

Amma ta girgiza kai.

“Hmm hmm Hindu ba zan taba komai nasa ba, ba zan iya kauce hanya saboda duniya ba,
komai mukaddari ne daga Allah”

Hindu ta rike baki.

“Toh ke ma dai ba a banza ta barki ba, wato sai da ta kwantar da ke ta yadda ba


zaki iya yin komai ba”

“Ko ma dai minene ni dai ba zan yi yanka ba, ba zan aikata wani abun da zai hana ni
kwanciyar kabari lafiya ba, saboda rayuwar duniya mai karewa, ni dai na bar komai
ga Allah shi zai isar min, Allah ka isar min ga duk wanda yayi min cuta, ga duk
wanda ya hana ni zama da mijina, ga duk wanda ya raba tsakanin Uba da Yarsa, Hindu
Wallahi ba zan iya shirka ba, ki yi hakuri dan Allah zan baki kudin da kika kashe”

“Ba sai kin biya ba, ai na san mai kudi kika aura Hajiya Iyami, ni dai ban tafi
gurin wani na ce yayi min tsafi ba, kuma dai ina sane ba zan yi shirka ba, amman na
miki alkawari daga yau ba zaki sake jin bakina akan neman taimako ba kin yi da yar
halak”

Ta fara tattara kayan tana sakawa a jakar, Amma na kokarin fahimtar da ita amman
bata saurareta ba ta fice daga gidan cikin bacin rai. A gurin Amma aikata irin
abubuwan nan shirka ne, neman taimakon wani wanda ba Allah ba shirka ne, Hindu kuma
tana ganin matukar ba shari suka je nema ba, kuma ba wata ibada suka yi da Allah
kadai ake yi ma ba, to ba su aikata shirka ba, fahimta ta sha banban sai aka samu
sabanin ra'ayi kowa ya kasa fuskantar inda dan'uwansa ya dosa. Gwaggo ce ta fito
daga dakinta ta zauna falon cikin yanayi na rashin jindadin abun da ya faru domin
tana jin komai dake faruwa.

“Ai da baki mata haka ba, da sai ki karba ki aje ba dole sai kin yi amfani ba, kuma
abun da be tsabawa addinin ba, ba a hanawa kai aikatawa Iyami, ke kanki kin san
ruwa baya tsami banza kuma na tsorata da lamarin matar nan domin bata da imani”

“Gwaggo idan na karba kamar na yarda ne, kuma idan Kaltume bata da imani ta aikata
tsafi mu ma sai mu biyeta mu aikata? Saboda namiji? Namijin da ko babu asiri zai
iya cewa ya gaji da zama da ni, namijin da zan iya faduwa na mutu yau da dare ya
sadu da abokiyar zamana? Ni kam ba zan yarda na zama daya daga cikin matan da
Annabi ya ce mafi yawansu suna wuta ba, domin farkon abun da ke shigar da bawa a
wuta tsabawa Allah ne da kin bin dokokinsa”

“Duk da haka dai, Iyami ki nemi tsarin jiki kuma ki nemi na karya sihiri ban ce ki
yi tsafi ba, amman ki yi tunani”

Gwaggo ta tashi ta fice daga falon zuwa harabar gida. Amma ta girgiza kai.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, wai duk saboda kishi zai saka Kaltume ta aikata
min haka kuma ta aikatawa yarana? Duk saboda namiji? Ka bata lahirarka? Appan
Hurriya dama ban aureka ba, ina ma ban je gidan aiki ba”

Tana maganar hawaye na sauko mata. Ta dora duka hannayenta a kai tana jin kamar ta
bude bakinta ta saka kara ba tare da an mata komai ba, gaba daya duniyar ta rikice
mata kashe ya hade ta rasa ina zata sa kanta ta ji sanyi ina zata saka rayuwarta ta
ji sassauci.
(Ni kan na ce anya akwai irin su Iyami kuwa🤔)

Kuka ta yi sosai har sa da ta gode Allah, sannan ta tashi ta nufi dakin Gwaggo ta
shiga ta wanke fuskarta ta fito ta nufi dakinta dake wajen falon, kamin ta karasa
ta soma jin gabanta na faduwa irin faduwar da bata saba ji ba. A take ta fara
ambaton Allah har ta shiga dakin. Tana taka kafarta sai ta ji kamar ta taka kaya da
sauri ta daga kafarta ta duba sai ta ji a dayar da sauri ta koma baya ta fita daga
dakin. Ta sake saka kafarta sai ta sake jin kamar tana taka kaya ta sake fita, sai
da ta yi haka sau uku har ta juya kamar ta kira Gwaggo sai kuma ta fasa gudun kar
ta daga musu hankali.

“Rukayya”

“Na'am”

Rukayya ta amsa daga dayan dakin sannan ta fito

“Gani”

“Dan Allah shiga ki dauko min twins”

“Okay”

Amma ta juya ta koma dakin Gwaggo ta zauna, a dakin Rukayya ta kawo mata su, ta
shimfida su a saman gadon Gwaggo, Amma ta dauki Hamid ta bashi nono sai da ya koshi
sannan ta bawa Hamad shi ma, ta kwantar da su ta kwanta gefensu ta kai hannu ta
shafa Hamad tana murmushi sai hawaye suka zubo mata. A ranar Amma ta kwana cikin
tunani kala kala. Misalin karfe uku na dare ta ji kamar an tashe ta sai ta bude
ido, ga mamakinta arba ta yi da rana ta haska sosai kamar karfe biyun rana. Da
sauri ta sauko saman gadon tana mamakin wane irin bachi ta yi haka bata farka ba
har rana, kuma wani be tashe ta ba.

“Gwaggo Gwaggo Gwaggo”

Ta shiga tashin Gwaggo. Gwaggo ta tashi zaune tana murza ido.

“Lafiya Iyami?”

“Gwaggo rana ta yi kalle fa”

Gwaggo ta juya ta kalli dakin har zuwa windows ita dai dare take gani, Gwaggo ta
tashi ta nufi makunnin wutar dakin ta kunna, sai haske ya baibaiye dakin, a take
ranar ta bace a idon Amma.

“Karfe ukun dare ne fa yanzu Iyami, lafiya kike kuwa?”

Gwaggo ta fada bayan ta duba agogo falon. Sai dai Amma bata ji da ganin komai sai
muryar mutum hudu da fuska daya, mace ce mai manyan idonawa kamar girman kwai, ga
bakin gashi da aka birkita ya yamutse, da bakin tufafi, wannan na nuna mata Yamma
tana cewa ki bi nan. Wannan na nuna mata gabas tana cewa ki bi nan, wannan na nuna
arewa dayar na nuna kudu, kowa kuma cewa yake ki bi nan bi nan.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un


Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un ”

Shi ne abun da ta yi ta maimaitawa ta sai dayar dake hadu ta miko hannu ta buge
mata baki. Amma ta yi baya ta fada kan twins dinta har sai da Gwaggo ta dagota
daker ta janye yaran sannan ta fara tofa mata addu'a, kamin ta fita ta kira Bappa
da Rukayya. Haka suka zo suka rufe tana suna ta tofa mata addu'a sannan Rukayya ta
dauko alkur'ane ta fara karanta mata, daman daga iya sai Iyamin ne suka yi sauka,
Rukayya sai ta maida hankalinta bangaren boko bayan saukar Iyami kuma bata cigaba
ba bayan Primary domin a lokacin babu hali, sai kawai ta saka ga aiki a gaba da
kuma karatun addini.

Har safe Iyami bata motsa ba har lokacin kuma idonta a rufe yake. Gwaggo ce ta fara
bada shawarar a nemi masu maganin hausa, Bappa kuma ya karkata bangaren Asibiti.

“Wane irin asibiti kuma rana fa ta fara gani kamin komai ya faru kuma na fada maka,
karfe uku na dare amman tana ce min rana ta yi”

“Toh tun da kun fi sha'awar na hausar sai ayi, amman dai da mun fara kaita asibiti,
wata kila ma damuwa ce ta yi mata yawa damuwa babu abun da bata sakawa”

“Shi ke nan Malam mu tafi asibitin”

Ba dan ranta ya so ba aka dauki Amma zuwa asibiti, suna zuwa kuwa aka bata gado
likitoci suka hau dubawa. It take them a week ba su gano komai dake damunta ba,
daga lokacin aka dawo gida aka fara yin na hausa shiga nan fita nan babu wani canji
ko'ina kuma da abun da ake fada, wasu su ce kishiya ce wasu su ce karo ta yi wasu
kuma su ce gidan ke da aljannu. Kowa da abun da yake fada, withing 5 Months Amma ta
zama abar tausayi domin bata iya komai sai an mata a kwantar a tayar bakinta kuma
bata iya cewa komai sai dai ta yi ta kallon mutane da ido. Wani karin abun tausayi
idan twins dinta suka kuka sai dai a daukesu a ciro nononta a basu idan suka gama
sha a ciresu. Haka zata yi ta kwanciya idan aka auna kwanciyar ta isheta sai a
tayar da ita zaune a jingina. Ganin abun ba zai yi ba aka sake maida ita asibitin a
lokacin da suka sake bincike sai suka ce hawan jini ne ya same ta har ya haifar
mata da wannan matsalar, sai kuma hankali ya koma gurin shan maganin asibitin, haka
dai aka yi ta yi asha na asibitin ayi na hausa amman babu sauki babu alamarsa. Kusa
kullum sai an saka mata karatun kur'ane wani sa'in kuma Rukayya zata zauna kusa da
ita ta yi ta karatun kur'ane.

THREE YEARS LATER....

A dakiku ma akan samu canjin rayuwa, balle kuma azo ga mintuna da awanni, ranaku
sati ko wata ba a lissafinsu balle kuma shekaru. Da yawa an shafe wasu shafunka a
rayuwar Hurriya an sabunta wasu, an busawa wasu rayuwa. Ta kan manta abubuwa da
yawa, kuma ta karbi wasu kadarorin ta rumgumi sabuwar rayuwar dake fuskarta, ta
saba da wasu dabi'u da halayya. Sai dai har yanzu ta saka yarda dan'uwanta ya tafi
ya barta, ta kasa karbar wannan kaddarar, kuma ta kasa manta ranar da aka sanar
mata da mummunan labarin da har gobe take karyatawa. Musamman a yanzu da girma ya
gina mata sabon daki, a duk lokacin da wani abun dadi ko akasin haka ya same ta
babu wanda take tunawa sai dan'uwanta, idan wani ya tsangwame ta a gida, mai bude
hannayensa ya tare mata fada take tunawa, ranar da suka yi Candy idan ta kalli dama
da ita bata ganin kawayenta sai dan'uwanta, babu daren da bata mafarkinsa, babu
sallah da bata addu'ar dawowarsa.
Yar karamar takardar ce a hannunta tana shafa harrufan da tuni ta da haddace
rubutun dake jiki, hawaye na jika kumatunta, a ranta take ta maimaita karatun da.
Numfashi ta ja da karfi ta daga kanta ta kalli madubin dake gabanta wata mace ce
zane a gaban madubin mai tsananin kyau sura da kyawun halitta da haifa, mai fari da
yalwar gashi kamar ƴar Ethiopia. Garin gilashin dake mata mata garkuwa ya kara mata
kamala. A natse ta lumshe ido ta hade yawu a hankali.

“Hurriya kina ina? Jiranki fa ake”


Ta bude idon da sauri, ta bude drawer madubin ta saka takardar ta rufe sannan ta
mike tsaye ta share hawayenta ta dauki mayafin abayarta ta shafa a saman kanta
sannan ta nufi kofar fita da saurinta. Tana bude kofar Momy na bude tata kofar da
kan kace kwabo Hurriya ta sauko idonta kasa ta tsaya jikin kofar har sai da Momy ta
sauka sannan ta sauko ta fice daga bangaren. Tun kamin ta isa bangaren ta fahimci
kowa ya gama tafi domin babu mota ko daya a bangaren Hajiya Kaltume, cikin zullumi
ta karasa ta shiga falon sai ta ga ko'ina wayan babu kowa. To daman waye zai tsaya
jiranta ita banza a banza.

“Yauwa yar abaya daman a komai ai ke ce baya, kowa ya tafi ke kina can boye yanzu
zaki fara karyar baki san sun tafi ba, daman ina bakinciki zai barki ki tafi abun
yan'uwa? Hassada ai ta gama cinye ki”

Ta dago tana duba Hajiya Kaltume dake saukowa tana jefar Hurriya da duk kalmar data
fado bakinta. Hurriya ta rike hannayenta kana kallon fuskarta zaka san kalaman
Hajiya Kaltume ba su mata dadi ba, sai dai ta saba jin wadanda suka fi su ma daga
bakinta ko na yayanta babu abun da yake sabo a gareta yanzu, ɗacin kuma ta barwa
zuciyarta. Ta juya jiki babu gwari da zimmar ficewa sai aka turo kofar falon,
kyakkyawan bakin saurayin nan mai matukar cikar kamala da mazantaka ya shigo falo
fuskarsa dauke da murmushi bakinsa kuma kunshe da sallama. A take Hajiya Kaltume ta
washe baki.

“Maraba da Fadeel yanzu ake tafe?”

“Eh ina wuni Hajiya?”

“Lafiya kalau ya aikin?”

“Alhamdulillah”

Har ya zauna Hurriya dake tsaye yake kallo, be dauke idonsa ba har sai da ta mika
masa gaisuwa da muryarta mai matukar sanyi, so innocent.

“Ina wuni”

Kamar daman gaisuwar yake jira sai ya dauke idonta after ya amsa ya kalli Hajiya
Kaltume.

“Hajiya ce tace na zo na dauki Khairi wai ko bata samu mota ba?”

Hajiya Kaltume ta dan yi shiru kamar mai tunani kamin ta karasa saukowa ta amsa
masa.

“Eh... Amman ta samu daga baya, sai dai ko idan zaka ka leka ne”

“No daman akwai inda zan je kawai saboda Hajiya ta matsa ne ya saka na zo na kaita,
amman tun da ta samu shi ke nan ai”

Ya mike tsaye, Hurriya ta dan kalleshi tana jin kamar tace masa ya aikata ya kaita,
kuma bata isa ba domin Hajiya Kaltume na tsaye a falon, ko da ma ace bata gurin abu
ne mai wahala Hurriya ta iya rokon abu.

“Ba zaka tsaya ka sha ko ruwa ba? Hurriya kawo masa ruwa mana”

“No tafiya zan yi ai”

“Sai fa ka sha zauna mana sa nan da gurin Hajiya Fatee ai duk gidanku ne, kunya
kuma na miye?”
Baya son musa mata dan haka ya zauna yana murmushi kamar yadda ita ma take
murmushin. Hurriya ta nufi hanyar kitchen bata jima ba ta fito rike da gorar ruwa
da cup tana kokarin ajewa ya mika hannu ya karbi gorar ya bar mata cup din, kamar
ya san burin da take da shi a zuciyarta sai ya tambaye ta.

“Ke miyasa baki je ba? Ko baki samu motar ba ne?”

Ta daga masa kai a hankali kamar wadda bata son motsi.

“Muje na sauke ki”

Ta juya zata kalli Hajiya sai ta jiyo Hajiyar na fadar.

“Aa haba ka tafi kawai gurin aikinka, ai bata yi niyar zuwa ba ne, shiyasa ta boya
sai da kowa ya watse sannan ta fito”

Kalma daya bata isa ta musa ba a cikin kalaman Hajiya Kaltume, dan haka bata ce
komai ba ta sauke kanta kasa.

“Ko maybe bata son shiga mutane ne, na lura she's different, can i drop you?”

Ya karasa da son ya ji amsarta sai ta daga masa kai ba tare da ta kalleshi ko ta


kalli Hajiya ba, domin har ga Allah tana son zuwa birthday party din na Khari da ta
hade da graduation dinta.

“Hajiya na gode zan ajeta sai na wuce”

“Toh Allah ya kai ka lafiya”

Ya wuce gaba, Hurriya ta bi bayansa har lokacin kanta na kasa, Hajiya Kaltume na
watsa mata harara kamar ta fisgota ta yi ta duka haka take ji. Suna ficewa ta tashi
ta nufi stairs duk yadda ta so yin sauri bata iyawa saboda jikinta baya barinta ta
wala yadda take so. Tana isa bakin kofar dakinta ta kai hannu ta tura kofar dakin
zata shiga sai ta ji kamar an turata haka ta tafi suuuuu ta fadi kasa ridd rub da
ciki.

“Subhanallahi”

Ta fada sannan ta yunkura ta tashi zaune tana jan kafa ta isa bakin gadonta ta
zauna ta daga zane ta duba kafar dake mata mugun ciwo.

“Ya haka abu dai kamar an turo ni”

Ta latsa cinyarta dake cike da tsokar nama tana runtse ido saboda zafin da yake
mata. Karar wayarta ne ya dago hankalinta ta kai dubanta gurin da wayar take Hajiya
Fatee ce a line hannu ta kai ta dauka ta danna picking ta saka a hands-free ta aje
wayar saman gado.

HURRIYA POV.

Tun da suka fita daga gidan idonta na gurin titi da motocin dake ta zirga zirga,
Fadeel ma be ce mata komai ba kwarjininta ya cika masa ido ta yadda har ya kasa
tambayarta gurin da zai kaita. Kallonta ma sai yayi da gaske yake yi, shi ma kasa
kasa, yayi kanwa ta hudu da ita amman ya samu kansa da jin nauyinta, maybe because
tana so Innocent ne kuma saboda tana kyau ne irin mai cika idon nan da haifar da
natsuwa, or maybe kuma saboda tana karama ne she's too young yaja ta da hira. Ganin
suna ta dawowa the same road da suke tafiya ya saka ta dago ta kalleta sai yayi
mata dan murmushi kadan.

“Ban san even center din da za'ayi party ba”

“K_Candy Event Center”

Muryar ta fito between her two soft lips.

“Okay....”

Ya cigaba da tukin, after like ten minutes ya sake yin magana ba tare da ya kalleta
ba.

“Yaushe za'ayi naki birthday”

Ta yi shiru kamar bata ji shi ba.

“Ko an yi?”

“Ba ayi ba, amman ya wuce”

“How old are you?”

Uffan bata ce masa ba har suka isa gurin ya faka motarsa ta bude zata fita sannan
ta ce.

“19...”

Ya bita da kallo har ta fice.

“Thank You”

Ta rufe masa motar a hankali sannan ta nufi hanyar shiga tana tafiya kamar mai
tausayin kasa.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

𝐏𝐚𝐠𝐞8⃣

Tana isa gurin masu aikin tsaron kofar suka tareta.

“Ina zuwa?”

“Ciki”

“Ina katinki?”

Sai a lokacin ta tuna ta ji Khairi da kawayenta suna maganar gate pass amman bata
maida hankali ta karba ba ganin ita din ta gida ce.

“Yayata ce take yin biki ciki, ba na bukatar gate pass”

“Gaskiya ba zaki ita wucewa ciki ba sai da gate pass”

“Toh ko zaka taimaka ka kira min ita dan Allah”

“Ki kirata da wayarki mana”

“Ba ni da waya, amman zaka iya ara min taka”

Har yayi kamar zai hanata sai kuma ya ciro karamar wayar ya mika mata. Number Ya
Yasir ta saka ta kira shi few rings ya daga.

“Hello Yayana”

Yana jin kalmar Yayana ya san cewa Hurriya ce.

“Hurriya waya waye wannan”

“Na wani ne, na zo gurin birthday din Yaya Khairi ne, kuma ba ni da gate pass shi
ne suka hana ni shiga”

“Kin fada musu ke kanwarsu ce? Ya aka yi ma baku shiga tare da su ba”

“Eh na fada musu, sun riga ni zuwa ne na ji muryar Namra tana min magana ko da na
fito ita ma ta wuce, sai wannan dan Hajiya Fatee ne ya kawo ni”

“Zan kirata ta fito ta shiga da ke”

“Toh Yayana na gode”

Ta katse kiran ta mika masa wayarsa.

“Na gode Allah ya saka da alheri”


“Amin”

Ya amsa sannan ya maida wayar aljihu. Rumgume hannayenta ta dan ja baya kadan tana
kallon kofar. Wani matashin saurayi ne ya fito yana tambayar masu gadin ina wadda
ke tsaye.

“Gata can”

“Ku barta ta shigo”

Hurriya na jin haka ta nufi gurin, guy ya kalleta sama da kasa.

“Shigo”

Ta cira kafa ta fara takawa ta shiga ciki, dim Light ne ko'ina sai sauti ke tashi,
tun daga yanayin samari da yan matan da aka tara a gurin zaka fahimci ba biki ne na
masu mutunci da sanin ciwon kai ba. Kusan ita kadai ce take sanye da abaya dukan
nin kawayen Khairi suna sanye da English wears, wasu ma kansu babu dankwali tsabar
wayewa da rashin tarbiya.

“Ga Khairi can”

Gayen dake take mata baya ya nuna mata yayarta. Hurriya ta daga kai ta kalleta tana
sanye da wata riga kamar yar bayahuda, kanta babu dankwali kanta ya sha gyara an
zuba mata attachments din har gadon bayanta, makeup din da aka yi mata ta kara mata
kyau gaba daya ta canja kamar ba ita ba. Mamaki ya saka Hurriya bude baki tana
kallonta bata sanin wayewar Khairi ta kai haka ba, aranta take ayyana yadda Yasir
zai ci ubanta idan ace yana gurin.

“Muje ki ganta”

Ta juyo ta kalli gayen. Ta san idan ta je ba mutunta Khairi zata yi ba, wata kila
ma zata gwatsale ta ne a gaban mutane.

“Aa ba sai na je ba”

“Okay to muje ki zauna”

Ta kalleshi kamin ta kalli gurin da ya nuna mata. Sannan ta fara takawa da kansa
yaja mata kujera ta zauna ta dan jin kunya abun ka da wanda be saba ba, not like
bata saba zuwa birthday ba she used to amman ba irin wannan ba, kuma wani namiji be
taba ja mata kujera ta zauna ba.

“Thank you”

“You're welcome kyakkyawa, kina son shan wani abu?”

“Aa na gode”

Ta dauke kai tana kallon yadda kawayen Khairi suke ta takawa MC sai zuba mata
kirari yake kamar wata amarya.

“Me yasa kika saka Abaya baki san birthday za'ayi ba?”

Ta juyo ta kalli abayarta.

“Na sani”
“To why do you wear abaya?”

Ta yi masa shiru kamar bata gurin, idonsa na kan wuyanta zuwa kirjinta domin wuyan
abayar mai yankan V ne dake bayyana kasan wuyan mutum, wani abokinsa ne ya kai masa
duka yana dariya.

“Shegen kaya ashe nan ka boye who's this?”

Gayen ya kalleshi yana murmushi.

“My new friend i think kawar Khary ce”

“Her Blood Sister”

Hurriya ta amsa masa da kanta sannan ta tashi ta bar taburin ta nufi wanda babu
kowa a kai ta zauna tana bawa idonta abinci. Bata ankara ba ta ji ana mata magana
dama da ita.

“Sai kuma kika gudu? Tsoron mutane kike ne? Na ga kin kasa sakewa ma what's wrong”

Ta kalleshi ta dauke kai ba tare da tace komai ba, hannunsa ta ji a fuskarta yana
kokarin juyowa da ita, da sauri ta buge hannu ta mike tsaye.

“Miye haka? Akan me zaka taba min fuska?”

Ya daga kafadunsa.

“Fuska ce fa kawai”

Kwafa ta yi ta juya zata bar gurin sai yayi dariya ya mike tsaye da gangan ya riko
hannunta, shi dai kam ta masa kyau and as she know friend dinsa Khairy ba zai yarda
duk wanda ya zo party ta a yau yace ba a saba rika hannunsa ba, domin kusan rabin
yan bikin duka suna rike da hannayen juna ne, saboda wasu are in relationships wasu
a dating wasu kuma a new friends to them hugging ko rike hannu is nothing in their
team.

“Ya kike yanga yan mata saboda kina da kyau ne?”

Jin ta yi kamar ta tsinka masa mari sai kuma ta ji bata da wannan kuzarin.

“Karka sake taba ni, ni ba irin sauran matan da suke nan ba ne”

“Miya banbanta ki da su? Saboda kina da kyau?”

Ta masa banza, a abu mai muhimmanci ma Hurriya bata cika son amsawa ba balle na
banza. Ya dan cize baki yayi murmushi.

“Shikenan zauna ba zan sake ba”

Bata zauna ba ta bar masa gurin tana rabon ido ko zata hango wanda ta sani ta zauna
a kusa da shi.

“Wani kike nema?”

Wani ne kuma dabam yayi mata magana har kara wacan gayen da wannan domin wannan
kansa ma wani kalar aski ne na yan iska. Shi ma dai bata ce masa na ta nufi gaba
gaba ta inda Khairi zata hangota ko zata samu su daga mata kafa. Wani gurin ta nufa
ta zauna tana kallon yadda yar'uwarta take rangaji kamar ta sha kwaya, gayen da ya
fara yi mata iso ta hango ya isa gurin Khairi yana mata magana a kunne, kamin ya
nuna gurin da take zaune har Khairiya ta kalleta ita ma ta mayar masa da maganar a
kunne. Sannan ya sauko daga gurin ya nufi gurin MC, before she know sunanta ya cika
gaba daya hall din.

“Ina Gimbiyar take, Hurriya ki fito kin yi farar tafiya daya daga cikin kananan
matasan mu masu ji da kudi dan gidan Alhaji Buba Sarauta yana nemanki ya ce a kira
masa kanwar Hajiyar ta mu wato Khairy domin ta taya yayarta murnar wannan birthday
da take da kuma na graduation dinta”

Kowa sai ya fara rabon ido ana ta ga wayw Hurriya wacece Hurriya, Khairi kuma ta
kasa boye mamakin dake fuskarsa, tambayarta sunan kanwarta da yayi ta fada masa
bayan ya nuna mata ita bata dauka abun da zai yi kenan nan ba. Gaban Hurriya kamar
zai fado tsabar bugawar da yake domin bata saba ba, irin haka ma be taba faruwa da
ita ba. Kasa tashi ta yi ta rasa me zata yi ba zata iya zuwa gurin da aka bukace
ba, bata san ma'anarsa na yin haka ba, so she decided to hide herself, tana kokarin
janye kujerar ta boya karkashin teburin, gayen ya nufo inda take MC na biye da shi,
hakan ya hanata boya sai kallonsa take ta cikin gilashinta tana jin ta ga abun da
zai mata, gaba daya sai hankali ya dawo gurinta ita kanta Khairy sai ta sakar musu
ido tana son ganin me ke shirin faruwa. Tun kamin ta karaso gurin da Hurriya take
zaune ya cire rapper dollars ya fara bararwar har ya isa gurin da take ya tsaya
akanta yana ta zuba mata dollars, idan suka kare sai ya dauko wata a aljihunsa ya
cigaba da zuba mata, a take gurin ya dauki ihu aka fara daukarsu da manyan wayoyi
wasu yan matan da suke crushing akansa kuma suka kasa boye kishinsu. Gaba daya
mantawa aka yi da wani birthday party sai ihu ake ana daukar Hurriya, da gayen dake
zuba mata kudin kamar be san zafinsu ba. Hurriya ta mike tsaye da sauri tana kallon
Namra da sai a lokacin suka ga juna, bata tsaya komai ba ya nufi kofar fita ta fice
daga gurin da gudunta, abun da ta yi ya bawa kowa a gurin mamaki domin at first
wasu sun dauka ko budurwarsa ce, sai dai guduwar da tayi ya saka shakku a zukatan
mutane. Khairy kan ta cika har tana kusan fashewa domin ta san saboda ita ya zo
birthday even though ba saurayinta ba ne he's just her friend amman ta san kudin da
ya zo da su ita ya kamata yayi ma kari da su gashi be yi ba ya karar da su gurin
kanwarta.

Hurriya ta fito da sauri ta biyo hanya tsoro duk ya gama cika ta gaba daya ma a
firgice take, hankalinta be kara tashi ba sai da ta iso titi, ko'ina tsit yake
kamar babu mutane, arzikinta daya rana ce ba dare ba, wannan ya saka ta dan ji
sauki. Juyawa ta yi kamar zata koma sai kuma ta ga ba mafita ba ce, tafiya ta fara
yi tana rumgume da hannayenta sai ta ji an mata horn, juyowa ta yi ta kalli motar
da bakin gilashi ya hana a ga wanda ke ciki. Ta juya ta cigaba da tafiya kamin ta
tsake tsayawa kamakon fakawar da mai motar yayi gefenta ya sauke gilashin motar.

“Saboda na miki karin kudi zaki gudu? Idan ni ne ki koma ba zan sake ba”

Ta kalleta ta dauke kai ta cigaba da tafiya, shi ma tafiyar yake slowly cikin motar
yana kallonta..

“Idan kuma gida kike son zuwa shigo na kai ki, you're not safe hare”

Kalmarsa ta karshe ta saka tsoron dake cikinta ya karu, ta dan karkato kadan ta
kalleshi sai ya kai hannu ya bude mata front seat. Tsayawa ta yi kamar mai tunani
shi ma sai ya tsaya daidai ita.

“Gida zan kai ki, shigo”

Ta kalli abun da ke aje a kasan inda mutum zai dora kafafuwansa idan ya shiga, sai
yayi saurin kai hannu ya dauke ya jefata baya.

“Shisha ce please shigo”


Ita dai tun da take bata taba ganin tukunyar shisha a fili ba sai yau, tana dai
ganinta a fina fina kuma ta san abun da ake yi da ita domin wadanda ake nunawa rike
da ita sha suke suna fitar da hayaki.

“I'm Adam by name, please ki shigo mana Hurriya”

“Na gode zan kira yayana ya zo ya kai ni gida”

“So you get phone please saka min number ki a nan”

Yayi picking latest IPhone dinsa dake cikin motar ya cire key ya mika mata. Ta
kalli wayar ta sake kallo sannan ta kai hannu ta karba without saying anything ta
saka number yayanta daman daga numbersa sai ta Appa da Ammanta ta haddace a kai.
Kara wayar ta yi a kunne

“Hello Yayana.. Ka zo ka dauke ni please ina jin tsoro kuma ina bakin titin gurin
Event din ba kowa”

“Me ya fito dake to?”

“Ni na gaji ne bana son zama ciki gida nake so, kuma su ba su gama bikin ba babu
wanda zai kawo ni”

“Okay ki koma ciki gani nan zuwa”

“Toh Yayana ka yi sauri ance I'm not safe here”

“Waya ce haka?”

Ta kalli mutumen dake jiran ta ba shi wayarta.

“Adam”

“Wane Adam”

“Ni ma ban san shi ba, yanzu na hadu da shi”

“Okay ina kusa da gurin koma ciki zan zo na dauke ki”

“Toh”

Ya kashe ya mika masa wayarsa.

“Thank You”

Ta juya ta cigaba da tafiyarta har ta koma ciki, wannan karon masu gadin ba su
hanata ba domin sun gane ita ce ta dazun. Ciki ta koma ta samu gurin inda ba za a
ganta ba ta zauna ta zubawa kofar shigowa ido Yayanta kawai take son gani. Tana
hango Adam ya shigo ta kara boya kamar ta san ita zai fara nema, sai ko ya hau
rabon ido yana neman inda zai ganta, gaba daya ta tafi da shi, a gurinsa duk abun
da take tana masa yanga ne saboda ta ga tana da kyau. Ta yi rabin awa a gurin
sannan ta tashi ta nufi kofa kamar mai shirin sata ta fice tana duddubawa ko
Yayanta ya zo, aikuwa ta yi sa'a tana fitowa motarsa na shigowa harabar da sauri ta
nufi shi yana fakawa ta bude front seat ta shiga.

“A tsorace kike Hurriya me ya faru?”

Ya tambaya yana kokarin kashe motar.


“Ba komai ni gida nake so”

“Ina Khairi ita da waye a gurin cikin yan gida?”

“Yaya Namra kawai na gani, sauran duk kawayenta ne ban sansu ba”

Ya duba agogo hannunsa.

“Su ma ai ya kamata ace kowa ya tafi gida yanzu, Je ki kirata”

“Yaya ba zata fito ba, kuma zata ce na bata mata birthday fa”

Ta saka mishi kuka domin ta san halin Khairy ko a banza ta dora mata laifi balle
kuma da dalili.

“Karki ce ni nake kiranta, ki ce wani ne yake kiranta, idan ba haka ke ma sai na


bata miki rai”

Ta fita motar ba dan ta so ba sai dan Yasir yayi mata dole, ciki ta koma ta isa har
gurin da Khairi take tana rawa ana zuba mata kudi ta rikota ta kai bakinta kunneta.

“Wani yana kiranki a waje”

“Waye?”

“Ban san shi ba”

“Je ki ce masa ya shigo ciki”

Hurriya ta juyo, ita dai bata san yadda aka yi masu gadin suka bar Yasir ya shigo
ba, sai hangon shi ta yi ya kankance ido yana kallon mutanen dake ta kai da kawo a
gurin. Ta nufi shi ma ya nufo gurin Khairy da bata san me ke faruwa ba sai rawarta
take ana zuba mata kudi. Galala Hurriya ta yi tana kallonsa ganin ya wuce ta ya
nufi gurin Yayarta, yana isa be tsaya komai ba ya dauke Khairy da mari ya fara
dukanta kamar an zugoshi.

“Wannan iskacin ne birthday? Kin mai da kanki kamar yar kafirai? Babu mutum daya
mai mutumci a nan kim hada maza da mata ana shashanci ki cw birthday? Daman sai na
hana Hajiya ta ce sai an yi saboda kawai ku ja mana zagi”

Dukanta yake ta ko'ina wadanda suka san yayanta suka fara ficewa da sauri, wasu
suka suka fara kai mata dauki ciki har da ma'aikatan gurin.

HAJIYA KALTUME.

“Hello”

Hajiya Fatee ta amsa daga dayan bangaren.

“Hajiya ina ta kira baki daga ba”

“Yanzu na shigo dakin, kin gan ni garin sauri har faduwa na yi kamar an turo ni”

“Subhanallahi, sannu daman ina ta kira na ce miki Fadeel zai zo”


“Ya ma zo har ya tafi, ya ce wai kin ce ya zo ya kai Khairi bata samu mota ba”

“Eh haka na ce masa saboda na samu ya zo, wato Hajiya akwai abun da nake tunani sai
dai gan gama yanke shawara ba sai kin zo, shiyasa da kika fada min zata birthday na
fara da wannan”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi tana murza kafarta dake zogi.

“Toh Hajiya Fatee kenan wato idan hagu ta ki a koma dama”

“Kwarai kuwa, idan ba zai iya rabuwa da wacan bakar karyar ba da ta dafa ta ba shi
ya shanye, to ya karo wata idan ya auro wanda nake so ko da bakinciki ai sai ta bar
gidan”

“Wato Hajiya Fatee magana nan ba ta waya ba ce, bari dai sai na zo kawai ko kuma
idan kin shigo”

“Toh shikenan Hajiya sai mun hadu”

Ta sauke wayar tana murmushin jindadi, domin an yi tsara akan gaba Khairy ta
kamalla karatu daman kuma can tana sha'awar hada jini da aminiyarta ko dan karfafa
zumuncinsu.

**** **** ****

Hajiya Fatee ma da murmushi ta sauke wayar, sannan ta fito falo ta zauna tana ta
sake saken yadda zata kara bullowa lamarin. Domin ta san ba karamar wahala zata sha
ba kamin ta samu kan danta Fadeel ya yarda zai aure, a ganinta mallakar da Afrah ta
yi masa ba karama ba ce ta yadda ta hana idonaa ganin ko wace mace sai ita kadai.

“Sallamu Alaikum”

Ta dago tana amsa masa.

“Wa'alaikassalam har ka dawo?”

“Eh ko da na je Already ta wuce ma”

Ta yi tusar baki tana jin rashin dadin bw tarardar Khairy ba.

“Aikin banza, zuwan kawai ka yi kenan”

Ya yi dariya yana saka keys din hannunsa ya taba kunnensa.

“No na sauke kanwarta yar farar nan ita ce bata samu mota ba, sai na kaita”

“Oh yar makauniya? Ko yar wajen Hajiya Nafisa?”

“Tana gani Hajiya fa”

“Amman sai da gilashi ai, ita da makafi duk daya, Allah yasa dai ka shiga ciki”

Ya yi fuskar mamaki.

“No why would i?”

“To wish her happy birthday mana, kuma Allah yasa dai baka je mata hannu sake ba”
Ya zauna yana dariya.

“Hajiya Khairi kanwata ce fa, kuma ban ma san tana birthday ba, sai da kika kira ni
kika fada min naje na daukota, ban shirya komai ba”

“Toh sai ka shirya wani abun ka kai nata daga baya, ko tana kanwarka ai tana sin
kyautatawa”

“Yanzu kuma ai ya wuce, sai da mu hari gaba kuma”

Ya mike tsaye yana cigaba da wasa da keys din hannunsa.

“Bari na tafi na bar aiki a office”

“Wane irin aiki yanzu da yamma, wai shike nan ba dama na zauna na yi hira da kai
sai ka ji kamar kama kan kaya, yar hirar ma sai a hana ka?”

“Waye zai hana ni hira dake duk duniyar nan Hajiya?”

Ta tabe baki ta dauke kai.

“Dan Allah karki ce Afrah bata ma san na zo nan ba, ki daina dora mata laifi kina
daukar alhakinta ne kawai”

“Kullum ai ni mai daukar alhakinta ce, daman ta ina Afrah zata yi laifi a gurinka?
Yar zinari, ina dai son ka sani ni uwarka ce ko kana so ko baka so, matarka bata fi
ni matsayi ba”

“Ai ba za a ma hada ba, babu mai matsayin uwa a duk duniyar nan Hajiya, amman duk
da haka tana da nata iyaka mata ma tana da muhallinta, ban san miyasa kika tsani
mutanen Afrah ba, yarinyar nan tana mutuntatako daidai gwargwado tana miki biyayya”

“Na ji dan Allah kama hanya ka tafi Allah ya bada sa'ar aiki”

Rokonsa take har da hade hannaye. Ya sauke ajiyar zuciya cikin yanayi na damuwa ya
koma ya zauna domin ba zai iya barin gidan ran mahaifiyarsa a bace ba.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
“Ka tashi ka yi tafiyarka bana bukatar zaman ka daman ai bana da muhimmanci a
gurinka, da ina da muhimmanci ba zaka wulakanta ni ba”

Maganarta ta sake sukarsa gaba daya sai mood dinsa ya sake sauyawa. Sometime baya
ganewa rikicin Hajiya Fatee gashi bata yi tsufan da zai ce ya kai ace bata gane
wasu abubuwan amman sau ta rika furta kalama anyhow.

“Hajiya yanzu laifina na rashin bawa Khairi kyauta ne? Zan je na siye na kai mata
shi ke nan”

Ta yi kamar bata ji ba har ya mike tsaye ya fara tafiya sai kuma ya juyo yana
kallonta domin a lokacin ne wani tunani ya zo masa.

“Hajiya me yasa kika damu da zancen siyawa Khairi gift?”

Ya tambaya with little confused domin shi be ma tana jin ta yi maganar birthday
Khairi ba sai yau kuma ta nuna damuwarta akai sosai.

“Dalili ba na birthday ne ba kawai, ina ta karkata ha hankalinka ka gagara fahimta,


saboda hankalin gaba daya yana can gurin matarka”

Ya koma ya zauna yana cigaba da kallonta irin kallon nan dake nuna karin bayani
yake nema.

“To me nene dalilin Hajiya?”

Ta juyo ta fuskance shi.

“Magana muka yi da Hajiya Kaltume ganin Khairi ta gama makaranta yanzu, kuma ba
wani tsayaye take da shi ba zamu hadaku domin aminci na da Hajiya Kaltume ya kamata
ace akwai auratayya a tsakaninmu ya kamata ace tarayyar ta wuce abokanta”

Wani kalar faduwar gaba ne ya same shi, jin yadda Hajiya Fatee ta gabato masa da
maganar aure kai tsaye abun da be yi tsammani ba, domin ba shi da ra'ayin aure mace
fiye da daya.

“Amma....Hajiya....”

Kamin ya furta ta tari numfashinsa.

“Aha... Ai sai ni ita da yake tana da yar albarka tana mata magana ta amince ita da
take mace balle kuma ni da nake da ďan namiji, amman gashi nan zaka fara musamin
gashi nan tun ba aje ko'ina ba zaka fara cewa ba haka ba”

Ya saka hannu daya ya shafa kansa gaba daya sai ta ruda masa tunani ya rasa ta ina
ma zai bullowa lamarin.

“Ai na sani yanzu zaka fara lissafa min cewar baka da ra'ayin aure mace fiye da
daya ko?”

Ya dago ya kalleta yana shafa fuskarsa sai dai be ce mata komai ba ya mike tsaye.

“Hajiya zan tafi gida”

“Toh a gaishe da sarauniya daman ai karshe na san haka za a rabu”

Ya sake kallonta cikin yanayi na damuwa sannan ya fice daga falon. Kamar marar
lafiya haka ya isa gurin motarsa ya bude ya shiga, yayi zaman minti goma a ciki
sannan ya murza key ya juya motar ya fice daga gidan. Kamar baya son driving haka
yake tuka motar a madadin ya karasa gurin aiki sai ya koma gida, domin gaba daya
jin yake jikinsa ma babu dadi. Tun daga kofar falon ya jiyo sautin muryar Afrah
tana rera karatun qur'ane, a fakin ta zauna kan cushion ya dafa kansa gaba daya
Hajiya Fatee ta gama ruda masa tunani, shi ko aure zai kara Khairi bata cikin irin
matan da yake so, balle ma ba shi da burin na auren mace fiye da daya. Matarsa tana
da duk wasu qualities da yake so a jikin mace, kuma suna zamansu lafiya tana masa
biyayya daidai gwargwado gata da addini, why Hajiya zata rikita masa lissafi yanzu
da wani zancen aure, sanannen abu ne Hajiya bata son matarsa kuma babu wani abu da
zai iya yi akan haka sai hakuri.

“Rabin raina?”

Ya dago ya kalleta murmushin da yayi arba da shi a fuskarta ya saka shi jin sanyi,
daman a duk lokacin da zuciya ta yi arba da wanda take so, idan ta kalleshi
farinciki take ji. Kusa da shi ta zauna ta kai hannu ta shafa kansa zuwa bayansa.

“Yau kuma ta ina aka taba angona? Gurin aikin ne ko friends ko kuma a hanya”

“Ba ko daya kawai dai bana jindadi ne”

A take hankalinta ya tashi ta saka hannunta cikin rigarsa tana taba jikinsa.

“Me ya same ka? Fever ko headache?”

“Ba rashin lafiya ta jiki ba, rai na ne babu dadi”

Ta mike tsaye ta cire hijabin dake jikinta ta aje ta nufi kitchen sai ya bi
kyakkyawar surarta da kallo, skirt din da ta saka irin wannan ne mai bin jiki gashi
Allah ya hore mata baya. Tashi yayi ya bi bayanta tana kokarin dauko ruwa a fridge
ta ji ya shafa gurin da ya fi ko'ina daukar hankalinsa.

“Wannan kwalliya haka ai sai ki mantar da ni damuwata ma, ni yanzu kin kwashe min
tunani gaba daya kin bar kwakwalwar fanko”

Ta saka dariya tare da rufe fridge din.

“Kai da ba wani nan wayo ne dan kar na tambaye damuwar kuma sai na tambaya”

Ya juyo da ita ya rika bayanta yana kankance idonsa.

“To ai na manta, kin taba ganin an bada abun da babu?”

Da sauri ta ja baya shi kuma ya cire hannunsa a jikinsa sakamakon jin motsin
yaransu da suka yi, ta nufi gurin cups shi kuma ya juya ya tarbeshi yana murmushi.

“Daddy...”

Ya daga ta farin din sannan ya daga mai binta ya aje ya sake daga na ukun da yake
namiji ya aje.

“Daddy sannu da zuwa”

“Yauwa ashe kuna cikin gidan ko? Da na shigo ban ji motsin yarana ba”

“Daddy baka duba dakin mu ba da zaka gan mu ai, Aiman ne ya leka windows ya ce
Daddy sai muka gano ka dawo”

Babbar data fi su wayo ta fada, ya rage tsawo ya shafa kansu yana murmushi.

“Na manta ai ban duba dakin ba, laifin Momy ne ita ce ta dauke min hankali”

Ya dago ya kalleta yayinda take mika masa kofin ruwa sai ya kashe mata ido yayi
mata alama da bayanta ba tare da yaran sun gani ba. Dariya ta yi
“Allah ya shirya min mijina”

Daga yaran har shi suka amsa da Ameen ya ba su hannu suka tana sannan ya sanye
ruwan ya rika hannunsu suka fice daga kitchen din.

KHAIRI POV.

Hajiya Kaltume ta sauko da saurinta cike da karfin hali domin har yanzu kafarta
ciwo take. Cikin tashin hankali ta kalli Khairi da Yasir ya gama kumbura mata
fuska.

“Lafiya wannan kuka kamar an yi mutuwa?”

“Da mutuwa da abun da Khairi ta yi yau duk daya Hajiya. Akan wane dalili zata saka
tufafi jiki duk a waje da sunan birthday, daman sai da na ce kar ta yi party nan a
waje amman kika goya mata baya, gashi nan na je na ga babu kowa a gurin sai tarin
yan iska marasa sanin darajar kai, ita kuma ta saka tufafi kamar wata karuwa”

“Haba Yasir haba Yasir saboda wannan sai ka nemi raunata nata mata jiki? Idan ma
bata yi daidai ba ne kamata ka mata duka har haka ba”

Da mugun mamaki Yasir yake kallon Hajiya Kaltume, ganin tana kokarin kare Khairi
instead of ta yi mata fada.

“Hajiya kin san abun da wannan abun zai janyo? Idan hotunan birthday nan suka yi
yawo mutumcin Appa da naki duk zai zube a idon mutane, wannan abubuwa da Khairi
take yi kina kyaleta ba tarbiya ba ne, tun abun nan yana ga kawayen banza har ta
kai ita da kanta yanzu ta fara kwaikwayon rayuwarsu”

Hajiya Kaltume ta nufi Khairi dake ta kuka ta dagota tana duba fuskarta.

“To sai ka zo ka nuna min yadda zan yi tarbiyar, idan tarbiya ce ban iya ba, kai ya
taka take? An fada maka doka na gyara tarbiya ne? Fisabilillahi ko da Khairi ta yi
ba daidai ba fada ba zai isa ba sai ka sauya mata fuska haka ko'ina jini kamar mai
fada da sa'ansa? Bana goyon bayan ta aikata abun da zai zubar mana da mutumci amman
wannan hukuncin naka ba zan lamunta da shi ba, wata kila ma cikin mutane ka rufe ta
da dukan”

Dubanta yayi irin duban da magana ta makale masa a makoshi yake ganin kamar furta
ma ba shi da amfani, ya kalli Khairi da har lokacin take zaune a inda ya wurgar da
ita tana kuka ya dauke kai ya fice daga falon.

“Oh ni wannan Yasir sai zuciya ta yi ta dibansa yana kai miki hannu kamar wanda ta
kashe masa wani”

Cikin kuka Khairi ta ce.

“Hajiya ba laifinsa ba ne, Hurriya ce ta fada masa yana shigowa dakin taron ya hau
ni da duka a gaban mutane sannan ya fito da ni ya saka ni a mota yana ta zagina”

Hajiya ta zauna a kujera tana hade fuska.

“Ja'irar yarinya wato ita nan har ta iya munafurci, to yayi kyau zata ko ci ubanta
a gidan nan, ke ma kuma da laifinki miye na zuwa ki yi wannan shigar rabin jikinki
duk a waje, Fisabilillahi Khairi wani mutumen kwarai ne zai so ganinki haka? Dan
Allah ku rika kiyayewa mana muna fa cikin makiya da basa son cigaban mu, abu kadan
dariya za'ayi mana a ji dadi”

“Wallahi Hajiya ba ni kadai nake jan abun magana ba, Hurriya ma baki ga mutanen da
suke mata magana ba a gurin, babu wanda be san Adam ba dan gidan Alhaji Buba
Sarauta yaron da yayi kaurin suna gurin iskanci amman haka ta zauna yana ta zuba
mata dollars har daukarta yayi suka fita ya dawo da ita, amman da yake makira ce
shi ne ta kira Yaya ta fada masa ya zo ya tarwatsa min taro”

Ta karasa tana jin wani irin bakinciki ko cake din birthday da ta kashewa kudi mai
yawa bata ci ba. Gashi kuma Yayanta ya ci mutuncinta a gaban friends dinta on a
special day like this one zai zame mata abun magana.

“To an yi mugun gado, indai shigewa maza ne Hurriya ta fara yi to gurin uwarta ta
gado, ba yau aka fara ba a nono ta sha, ba haka ta yi har ta aure min miji ba, ai
barewa ba zata yi gudu danta yayi rarrafe ba, kamar kumbo kamar kurensa. Tashi ki
saka rufafin kwarai mu tafi asibiti a duba fuskar nan taki kar ta kwana tana miki
zogi”

Ta tashi daker tana kuka sosai ta nufi stairs sai a lokacin suka lura da Ruma dake
tsaye a stairs din tana kallonsu ita bata sauko ba kuma ita bata koma ba.

“Toh lafiya? Kin san yanzu kin zama aljanna ni tsoronki ma nake, kin zama wata
halittar ta dabam a cikinmu”

Hajiya ta fada tana nuna Ruma da har lokacin bata ce komai ba, sai ma juyawa da ta
yi ta koma sama, gaba daya ta canja tun bayan da ta dawo daga hannun masu garkuwa
da mutane ta tsani gidan da mutanen cikinsa, ba kasafai zaka ganta a wani abu da
kowa yake tarayya ba, wannan dalilin ya hanata zuwa birthday din Khairi kuwa da
kusanci na kasancewarta yar'uwarta. Hajiya kamar wata gurguwa haka ta hau sama
daker ta shiga nata dakin ta dauko mayafinta da jakarta sannan ta kira direba ta
fasa masa ya kunna mota za su fita. Sai da ya shiga dakin Khairi sai ta same ta har
lokacin kuka take tana zaune a kasa.

“Ba zaki je ba na tafi? Ba saboda zuwanki ne kadai ba ina son na kai kafar nan a
duba min”

Cikin kuka Khairi ta kalleta ta ce

“Hajiya ba ki ga wulakanci da Hurriya taja aka yi min ba Wallahi, Yaya ya wulakanta


ni gaban friends dina”

“Toh ya zaki yi sai ki yi hakuri munafurci daman ai ya cikawa Hurriya ciki, ganewa
ne ba a yi sai yanzu amman na san maganinta ai, ke ma kuma fa baki kyauta ba ni
Allah yasa dai Fadeel be ganki da wannan shigar ba, abu kamar karuwar Lagos haba
Khairi”

Ta tashi tana kuka ta nufi gurin da tufafinta suke ta bude, cikin kuka ta canja
tufafin sannan ta biyo bayan Hajiya Kaltume da tuni ta sauka kasa.

HURRIYA POV.

Tana tsaye a waje har Yasir ya fito ransa a bace ya sake shiga motarsa da kallo ta
bishi har ya fice sannan ta dan leka bangaren Hajiya Kaltume kamar zata shiga wai
dan ta wanke kanta ta fadawa Khairi da Hajiya Kaltume ba ita ta zugo shi ya shigo
gurin ba, sanin ba za su kwashe da dadi ba ya saka ta juya ta fice daga bangaren ta
nufi bangaren Momy. A hankali ta tura kofar falon ta shiga tsoron dake cikin
cikinta ya hanata sallama har ta isa tsakiyar falon.

“Salon labe ne ko kuma rainin wayo? Zaki shigo min falo babu sallama?”

“Yi hakuri Momy mantawa na yi”

Ta fada da muryarta da bata gama fita ba.

“Daga ina kika?”

“Gurin Birthday din Yaya Khairi”

Momy ta dauke kai ta cigaba da latsa wayarta, Hurriya na ganin haka ta raba ta haye
sama ta shiga dakinta. Sai kusan magariba Namra ta dawo gidan, tufafinta kawai ta
cire ta shiga dakin Momy tana bata labarin abun da ya faru ita kanta ta cika da
mamaki irin shigar da Khairi ta yi ga kuma wasu watsassun kawayenta da bata san a
ina ta samo su ba.

“To ke me kike baki dawo gida da tun dazun ba?”

“Momy ina can ina jiran wanda zai dauko ni fa, gaba daya a hargitse aka watse taron
saboda Yaya Yasir ni ma ba dan na boya ba Allah kadai ya san kalar dukan da zai
min”

“Ya dokeki saboda shi ya haifa ki? Ai ba zan dauki wannan ba, ya taba dinka kala
daya ya kawo miki? Sai yanzu da girmanki zai ce ya saka miki hannu ya dakeki saboda
bikin da kanwarsa ta shirya?”

“Momy dan baki ga bikin ba ne, bari na nuna miki dress din Khairi kamar ba yar
gidan nan ba”

Ta shiga gallery wayarta ta kama hotunan da ta yi ma Khairi tana nunawa Momy.

“Momy kalli fa, ni ma raina ya bace da abun da ta yi Wallahi, ai na jidadi da


Hurriya ta fadawa Yaya Yasir ya zo ya watse taron nan”

“Au Hurriyar ce ma ta fada masa abun da ake yi? Ina ta ganshi to?”

“Oho mu ma kamar daga sama muka ganshi ina ganin ya fada jibgar Khairi na boya ban
bari na gan ni ba”
“Ikon Allah yaushe kuma Hurriya ta fara zama munafuka? Hada yaya da kanwa? Wannan
kam ba shi da kyau ai, ko bata fada masa ba ai ya san kanwarsa zata aikata yadda
take jin ita sa'ar kowa ce kawaye babu na albarka ai dole ma ta aikata, kuma Alhaji
ba zai ce komai ba duk abun da Kaltume ta yi ai shi ne daidai a gidan nan ita da
yaranta yanzu basa laifi”

“Gaskiya Momy kawayenta gaba daya babu na gari, wani dayan frind dinta ya zo yana
yi ma Hurriya liki da dollars”

“Rawa ta yi”

“Aa Momy kin san ai ba zata yi rawa ba, Momy kin san shi ma Adam ne fa, dan gidan
Sarauta”

“Ba dai dan Hajiya Nana ba?”

“Shi fa, yaron nan yana wasa da kudi”

“A ina ta san shi?”


“Ni ma ban sani ba, bari ma na tafi na tambayeta”

Ta tashi da saurinta ta bar wayar a gurin ta fice daga dakin Momy bata zame ko'ina
ba sai dakin Hurriya. Cikin natsuwa irin na masu son gulma ta tura kofar dakin ta
shiga, Hurriya na tsaye jikin windows, dan kwalin abayarta ya sauko saman wuyanta
hannunta kuma yana wuyanta tana shafawa zuciyarta kuma ta tafi wata duniyar karatu.

“Hurriya...”

Ta juyo ta kalli yayarta, Namra ta maida kofar ta rufe ta nufi gurin da Hurriya
take tsaye.

“Me kike yi”

“Ba komai kawai ina tunanin Hamad ne”

Ta fada tana sauke idonta kasa.

“Ke dai kin saka Hamad a ranki Hurriya, idan yana raye Allah ya bayyana shi idan
kuma ya mutu Allah ya jikansa da Rahma”

“Amin”

Hawaye ya sauko mata.

“Da ace yana nan kusa da mu, wata kila da yanzu muna son junanmu ba kamar baya ba,
wani lokacin ina jin bukatar abokin tattaunawa, har yanzu na kasa sabawa da
rashinsa ina jin kadaici sosai”

“Ki yi ta addu'a abun zai cire miki In Shaa Allah, amman shiga damuwar da kike ina
tunanin shi ne silar daya kara jefa Amma cikin damuwa”

“Ina kokari Yaya Namra bana bari ta gane ina cikin damuwa”

“Haka na da kyau, yauwa Hurriya kin san wannan wanda yayi miki karin kudi dazu?”

Ta share hawayenta da gefen hannun rigar abayar.

“Aa ban san shi ba, dazun ne ma na fara ganinsa”

“Toh amman kuma yake miki karin kudin haka nan kawai?”

“Ni ma abun ya ba ni mamaki sunana ma ban san inda ya ji ba”

“Maybe ko ya sanki wani gurin ke ce baki san shi ba”

“Ni da ba fita nake ba, amman ni ma mamaki nake”

“Toh ki yi hankali da shi yaron nan dan shaye shaye ne”

Ta amsa mata kai kamin ta ce.

“Yaya Namra dan Allah zaki taimaka min na fadawa Hajiya ba ni na kira Ya Yasir ya
shiga ciki ba?”

“To waya kira shi?”

“Ni amman na ce masa ya zo ya dauke ni ne kawai saboda wannan saurayin ya takura


min kuma ba ni da wanda zai kai ni gida, amman WallahI ban ce ya shiga ciki ba”

“To ai ke kika yi kuskuren Hurriya kema kin san dole zai shiga ai, kuma yanzu babu
mai wanke ki a gurin Hajiya”

“Ba Hajiya kadai nake tsoro ba, har da Yaya Khairi na san ni zata dorawa laifin”

“To kije ki ba su hakuri mana”

“Zan yi haka”

Ta fada cikin yanayin damuwa wasu hawayen na kara cika idonta. Namra ta fice tare
da ja mata kofa. Hurriya ta kai hannu ta taba hancinta kamin ta dago ta sake juyawa
top side view ta rumgume hannayenta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Misalin tara da rabi Hurriya na zaune dakinta ta ji an kwankwasa kofa, tana jin
haka ta san wanda be saba shigowa dakin ba ne domin Momy ko Namra basa kwankwasa
mata kofa balle kuma Miwan da Musib da basa gidan ma. Ta tashi da saurinta ta nufi
kofar ta bude sai ta yi arba da Ruma.

“Appa na kiranki”

“Ni”

Ta nuna kanta, Ruma ta daga mata kai.

“Eh”

Ta juya ta bar kofar ta fara sauka kasa, Hurriya bata tsaya komai ba ta bi bayanta
tana sanye da kayan bachi kanta sanye da hular saka. Ruma na gaba Hurriya na
bayanta tana jin kamar ta tambaye ta me ya faru kuma dai bata tambaya ba. Cikin
tsoro da fargaba ta shiga falon na Hajiya Kaltume gabanta na faduwa. Hankalinta be
kara tashi ba sai da ta yi arba da fuskar mahaifinta dake hade babu annuri a tare
da shi, bata yarda ta karasa cikin falon ba ta tsaya daga jikin kofa cike da ladabi
ta ce

“Appa ga ni”

“Okay tasowa zan yi na iskoki can kenan? Ni zan same ki a inda kike na yi magana da
ke ko?”
“Aa Appa ka yi hakuri dan Allah”

Ta taso ta karaso kusa da shi, ba duka take tsoro ba domin be taba dukanta ba,
fadansa take tsoro tun daga lokacin da ya canja mata sai ya zame mata abun tsoro
bata ma son zuwa kusa da shi sai da dalili domin ta lura baya bukatar ganinta.

“Appa gani”

Ta durkusa gabansa tana kallonsa ta cikin gilashin idonta, Yasir na tsaye gefen
Hajiya Kaltume dake zaune kusa da Appa, Khairi kuma na zaune a dayar kujerar tana
shafa man zafi.

“Miye wannan?”

Appa ya nuna mata video karin kudin da aka yi mata. Sai ta saka hannu biyu ta karba
tana kallo jikinta na rawa kamar yadda bakinta ma yake rawa domin bata san me zata
ce ba.

“Wace ce a nan?”

“Ni ce Appa”

Ta amsa da sauri.

“Waye wannan da yake miki liki”

“Ban san shi ba Appa Wallahi”

Tana rufe baki Hajiya Kaltume ta kai mata duka a bakin da mugun karfi.

“Baki san shi ba zai zo yana zuba miki dollars haka?”

Apoa ya kalli Hajiya cikin yanayi na rashin jindadin kai hannu da ta yi ta daki
Hurriya.

“Ba sai kin dake ta ba, magana ma ta isa a yanzu shata nata line zan yi”

“Ai idan ba a dake ta ba, ba zata san Annabi ya faku ba, karya da munafurci babu
kalar wanda bata iya ba, ka duba yadda ta zuga Yasir ya fasawa Khairi jiki”

Appa ya daka mata tsawa da ta saka ta fashe da kuka ta ja baya tana girgiza kai.

“Waye wannan mutumen na ce?”

“Ban san shi ba Appa Wallahi ni ma yau na fara ganinsa?”

“Karya take yi Wallahi Alhaji bata san shi ba”

Hajiya ta kai kafa ta halba mata wani shuri, kamin ta janye da sauri saboda ciwon
da kafar take mata har yanzu.

“Karya take munafuka baki san shi ba zai zuba miki kudi haka kuma kina zaune gashi
har sunanki ake fada”

Yasir dai yana tsaye sai kallo yake baya son yayi magana Hajiya Kaltume ta rufe shi
da fada, bayan kuma ga wanda ya kamata a rufe da fada nan wato Khairi.

“Ku dai duk abun da zai zubar min da mutunci ko kima a idon duniya shi kuke kokarin
aikatawa? Ko soyayya zaki yi me zaki yi da mashayi? Kaltume ta fada min yaron nan
yayi kaurin suna gurin iskanci da shaye shaye”

Hurriya ta saka hannu ta rufe bakinta, ta san duk wani abu da zata fada ba zai
wanke ta ba, ita kan da ta sani ma ba zata tafi bikin ba.

“Sannan kuma ka ja mata kunne akan munafurci abun da take ba shi da kyau, kina hada
yan'uwa fada kina sa a ciya daya mutumci a cikin mutane”

Sai a lokacin Yasir ya saka baki.

“Ni ba ita ta fada min Khairi tana wani abu a gurin ba, daukarwa kawai naje yi sai
kuma na yi decide na shiga ciki, kuma idan ma Hurriya tana da laifi to laifin
Khairi ne, domin ita ta shirya biki kuma Appa da ka ga irin shigar da ta yi da irin
mutanen da ta tara a gurin sai ranka ya bace”

Hajiya Kaltume ta watsa masa harara.

“Ita Khairi da ka raina ba, ita meye laifinta? Birthday kawai ta yi fa, kuma ina ce
Hurriya ce silar kowa ya fara yin birthday a gidan nan amman ba ayi mata fada ba
sai Khairi”

Appa ya mike tsaye.

“Ban shigo nan dan ku rufe ni da ka ce na ce ba, and Hurriya ina jan kunnenki idan
wani abu makamancin wannan ya sake faruwa sai na baki mamaki”

Yana kaiwa nan ya fisge wayarsa da Hajiya Kaltume ta tura masa video ya fice daga
falon. Hurriya ban da aikin kuka babu abun da take yi, ta rasa ta ina zata fara
wanke kanta.

“Munafuka sahibar kuka, ki yi ta rerawa mutane kuka saboda a tausaya miki a kyale
ki ko? To yanzu dai kin ji abun da Alhaji ya fada idan zaki kama kanki gurin yan
iskan samarin nan ki kama, idan kuma ba zaki yi ba yi, ga ki ga guri duniya ce”

“Wallahi Hajiya ban san shi ba, ni ban taba ganinsa ba”

Ba dan Yasir na tsaye gurin ba da babu abun da zai hana Khairi saka baki, sai dai
tana tsoron ta yi magana ya sake rufeta da duka. Dan haka ta ja bakinta ta yi shiru
sai kallonsu take, Hajiya Kaltume kuma ta rufe Hurriya da fata ta inda take shiga
ba ta nan take fita ba, sai balbale Hurriya take da bala'i ta ko'ina kamar ita ce
ta aikata abun da Khairi ta aikata. Sallama aka yi sai suka dago baga dayansu suka
kalli kofar amman aka rasa wanda zai amsawa Rukayya sai Yasir dake kokarin sakin
fuska.

“Rukayya”

“Na'am Yasir ya gd”

“Lafiya kalau”

Hurriyya ta tashi da sauri ta nufi kanwar mahaifiyarta ta rumgume ta da sauri tana


kuka.

“Mama Rukayya kara da kika zo”

“Idan ta zo magani zata miki? Idan dai zaki canja hali ki canja domin hanyar da
kika daukarwa kanki yanzu ba mai daurewa ba ce”
Hajiya Kaltume tana fada tana tabe baki, Rukayya da ke rumgume da Hurriya ta kalli
Hajiya ta ce.

“Ba zan mata magani ba, amman Allah zai mata”

Yasir yayi sauri cire hannayensa aljihu.

“Rukky Please aa karki fara abun da ba halin ba”

Ta kalli Yasir sai kuma ta dauke kai ta rika hannun Hurriya suka fice daga falon,
Hajiya ta bita da harara da maganganun kala kala.

“A dare kamar wannan yarinya budurwa ace bata gidansu, kuma ta shigo nan tana neman
fada min magana ita marar tarbiya”

“Haba Hajiya Rukayya tana da tarbiya Wallahi dan Allah ki daina fadar haka, kuma
baki san abun da ya kawota ba, be kamata ku samu tsabani da ita ba, ni zaku haifar
da matsala”

Yana magana fuskarsa a raunace kamar zai yi kuka. Sannan ya bi bayansu yana jin
Hajiya na jan tsaki.

A waje Hurriya sai rantsuwa take yi ma Rukayya na cewar bata san yaron ba, amman
saboda shi Appa ya rufeta da fada.

“To miyasa ba zaki bude baki yi magana ba, idan kina irin wannan zaman sai kin
cutar da kanki, ba zaki bude baki ki yi magana ba sai ki zauna kina kuka, ko da
kina da gaskiya a rashin gaskiyar za a baki”

“Basa bari na yi magana kuma idan na fada basa yarda”

“Amman duk abun da ba halinki ba ai an san ba halinki ba ne”

“Toh sarkin masifa me kike karanta mata?”

Rukayya ta juyo ta kalli Yasir da isowarsa kenan gurin, shi ma kansa yau sai ya
bata haushi saboda abun da mahaifiyarsa ta yi. Bata ce masa komai ba ta kalli
Hurriya

“Daman na fito daga gidan Anty Hauwa ne na ce mai napep ya biyo ta nan zan duba ki”

Hurriya ta rike hannunta tana jin kamar ta bita amman ba hali.

“Zan sallami mai napep din sai na sauke ki gida”

“Aa na gode yanzu zan tafi”

Ta saki hannu Hurriya ta fara tafiya sai ya kirata.

“Rukky”

Ta juyo ta kalleshi.

“Na ce zan sallami mai napep zamu sauke ki gida tare da hurriya daga nan ta duba
Amma”

Bata son tace masa no, kuma ta san Hurriya zata so ganin Amma domin ta dauki lokaci
bata saka ta a ido ba, ko da tace zata je sai Appa ya hana saboda Hajiya Kaltume
tace zuwan da take tana tafiya ne dan ta fadi karya da gaskiya.
“Tahm”

“Hurriya shiga ki dauko Hijabinki”


Ya fada sannan ya nufi gurin motarsa ya ja motar ya iso har gurin da Rukkaya take
tsaye, bata shiga motar ba sai da Hurriya ta fito sanye da dogon hijab dinta har
kasa, sannan ta bude ta shiga front seat Hurriya ta shiga baya, ya fara driving
suka fito gate a nan ya sallami mai Napep din sannan ya ja motar suka kama hanya.

“Rukky please bana son wani abu marar dadi yana shiga tsakaninki da Hajiyata, idan
ma ta fada miki wani abu marar dadi ko ta yi miki abun da bw dace ba, ki danne ina
son ki dauke ta kamar mahaifiyarki, saboda ni kuma ina tunanin ina da alfarmar da
zaki yi haka a gareni”

Ta hade yawu can cikin ranta take cewa Allah ya tsare ta Hajiya Kaltume ta zama
uwarta.

“In Shaa Allah”

Ya kalleta yana murmushi.

“Thank you”

Ita ma ta mayar masa da murmushin daga haka be sake cewa komai ba ita ma kuma bata
sake cewawa har suka isa gidan. Hurriya ce ta fara budewa ta fita motar Rukayya na
kokarin fita Yasir ya shigo ya dakatarda ita.

“Ina zaki je?”

Ta masa kallon rashin fahimta.

“Gida mana...”

“Ni kuma sai ki bar ni a nan?”

Ta yi dariya.

“To ka fito mu shiga gidan bakonka ne?”

“Ki dai tsaya mu yi hira ko raina zai saki ni raina ma duk a bace yake”

“Waya bata maka rai Hurriya?”

“Idan kina son jin labari zauna”

Ta yi murmushi sannan ta dawo ta zauna ba tare da ta kalleshi ba.

Hurriya na shiga cikin gidan ta fada dakin Gwaggo da sallama da muryar dake nuna
alamar kuka ta yi. Amma na jingine jikin kujera ita kadai a falon tana fuskantar tv
dake falon, ta dan karkato kadan ta kalli Hurriya. Hurriya ta isa gurin sai ta
kwanta saman jikinta ta fara hawaye, bata son ta fada mata abun da ya faru saboda
kar ranta ya bace gashi ba magana take ba balle ta bata shawara.

“Amma na Allah ya baki lafiya, Allah ya tashi kafadunki”

Ta cikin Amma ta iya amsawa da ameen ta kwanto da kanta saman kan Hurriya ta rufe
ido. Gwaggo ta fito daga dakinta tana mata maraba.
“Yau Hurriya ce a gidan nan kuma da dare, amman dai Alhaji be san kin zo nan ba
ko?”

Hurriya ta dago hawaye shakaf a fuskarta ta kalli Gwaggo.

“Be sani ba, Ya Yasir na biyo zamu kawo Rukayya ne”

“Daman tace sai ta biyo ta ganki, na dauka ma can zata kawana gidan Hauwa, saboda
na ga dare yayi sosai”

“Tana waje ita da Yaya Yasir, Gwaggo zo”

Hurriya ta kama hannunta suka koma cikin dakin, ta zauna bakin gado Gwaggo ma ta
zauna daman tana ganin ruwa hawaye a fuskarta ta san akwai abun da ya faru.

“Wani abu aka yi Hurriya?”

“Sheri aka yi min Gwaggo.... ”

Ta labarta mata abun da ya faru, sannan ta dora da abun da mahaifinta yayi mata
recently before birthday Khairi.

“Appa ya siyawa kowa sabon kaya na birthday din Yaya Khairi amman ni Hajiya tace
kar ya siya min ina da kaya da yawa, na masa magana sai yayi min fada, Gwaggo yanzu
Appa baya so na ko kadan idan na matsa kusa da shi sai yayi ta min fada, zaman
gidan ba ya min dadi kowa tsarguwata yake”

“Ki yi hakuri Hurriya zalinci be taba doreba, kuma komai yana da iyaka wata rana
sai labari, ke dai ki yi ta addu'a ki yi ta fadawa Allah matsalarki zai magance
miki ita, mu ma muna nan muna yi kuma akwai wani littafi da na siya miki na
addu'o'i mantawa na yi ban bawa Rukayya ta kai miki ba”

Gwaggo ta tashi ta nufi gurin da ta aje littafin husnul muslim ta dauko ta mika
mata.

“Addu'o'i ne da suka zo daga bakin Annabi Muhammad, karki yi wasa da su, domin ba
mu san me za a sake jifanke ko mahaifiyarki da shi ba, kuma duk abun da zaki ci ki
yi bismillah, sannan kar tsoro ya saka a baki wani abun da aka san an cutarwa ne ki
ci ko ki aikata, yanzu girma kike yi ya kamata ace kina kara wayo”

Ta share hawayenta

“Na gode Gwaggo”

“Ba komai Allah dai ya tsareki, kuma ina kara gargadinki ban da sakaci da addu'a,
kin ga rashin daukar addu'a da muhimmanci ne ya jefa Iyami a halin da take yau,
sannan kuma zan karbo miki maganin tsari akwai wani mai bada taimako na yi magana
da shi ya ce sai an ba shi 150k sannan zai fara yi na Iyami aiki, ya fada mana jefa
ce aka yi mata mai hatsarin gaske, kuma idan ba mu yi fa gaske ba zamu rasata”

“To yanzu ina za'a samu 150k Gwaggo?”

“Ina nan ina ta kokari Hurriya, idan kuma haka bw samu ba dole gidan nan zamu siyar
mu nemi karamin wannan mu siya sauran kudin sai mu yi maganin da su domin lafiyarta
ta fi mana komai”

“Amman idan aka yi zata warke Gwaggo? Kin san ana ta yi amman babu wani sauyi”

“Muna fatan haka, shi dai mutane da dama sun karba kuma an dace, mu ma muna fatar
mu dace wannan ciwon nata ya isheni Allah kadai ya san abun da take ji a ranta, ina
fatar na ga ta warke kamin na mutu”

Cikin kuka Gwaggo ta karaso maganar ita kanta a yanzu bata da wata damuwa da ta
wuce ta Iyami. Hurriya ta tashi rike da littafin ta fito sai ta tsaya daga bakin
kofar dakin tana kallon Amma dake kallon kofar dakin tun da suka shiga ciki, wasu
hawayen ne suka subuce mata sai ta fashe da kuka. Amma ta girgiza mata kai tana jin
kamar ta yi mata magana a dama, shigowar Rukayya ne ya saka Hurriya boye fuskarta
Gwaggo kuma ta taso ta fito daga dakin tana fada.

“Wane irin abu ne zaki je ki zauna har dare haka Rukayya”

Yasir dake bayanta yana sallama yayi saurin tare mata fadan.

“Tun isha'i take nan kofar gida Gwaggo laifina ne ni na tsayar da ita, ayi hakuri
dan Allah”

Rukayya ta juya ta kalleshi shi kuma yaki yarda au hada ido sai hakikancewa yake
yana ba Gwaggo hakuri kamar shi yayi laifin. Ya zauna saman kujerar da Amma take
jingine yana mata ya jiki.

“Amma ya jikin?”

Ta amsa murmushi kadan alamar jikin Alhamdulillah. Gwaggo kuma ta amsa masa.

“Jikin sai Godiya”

“Allah ya kara sauki”

Ya kalli Hurriya dake labe jikin curtains din dakin.

“Muje Hurriya kar Appa ya fara neman mu”

Hijabin ta janyo ya sauko ya rufe mata fuska sannan ta tako ta iso gurin Amma ta
kwanta jikinta ba tare da tace komai ba ta mike tsaye, Amma ta bita da kallo har
suka fice. Har sun isa gurin mota ta tuna bata shiga ta duba kanenta ba.

“Yaya dan Allah minti daya zan koma na duba Twins”

“Karki dade”

“Toh”

Ta koma cikin gidan da gudunta ta duba su ta fito ta shiga motar, sai da suka kama
hanyar gida sannan Yasir ya kalleta ya ce.

“Hurriya da gaske baki san yaron nan ba?”

“Wallahi ban san shi ba Yaya”

“To ya aka yi yanzu ya kira ni wai yana neman Hurriya na tambayi sunansa ya ce
sunansa Adam Sarauta ina ya samu number ta?”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi.

“Ni kuma? Wallahi ban bashi ba ko sunana ni ban san inda ya ji ba”

“Bana son ki min karya, kuma bana son ki aikata wani abin da zai zubar miki da kima
ko gidanmu, saboda haka ki kiyaye karki wani abu ya sake hadaki da shi, na san
gayen nan na yaron kwarai ba ne, idan ba haka ba ni ma zan saba miki”

“Toh Yaya amman Wallahi ban san shi ba”

“To ya aka yi ya sami number ta?”

Har zata ce bata sani ba, sai kuma tuna da ta karbi wayarsa ta kira Yasir.

“Da wayarsa na kiraka, lokaci da yace na saka masa number ta sai na kiraka na ce ka
zo ka dauke ni, ai har na fada maka Adam yace I'm not safe here”

“Na tuna, zan ja masa kunne”

“Toh Yaya”

Ta amsa tana gyara zaman littafin da Gwaggo ta bata a hannunta.

_________________
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo...

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

1️⃣
1️⃣ 1️⃣
1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 1️⃣

Hajiya Kaltume na tsaye rumgume da Hanayenta Yasir ya faka motarsa ya fito, sannan
Hurriya ma ta fito sau daya ta kalli gurin da Hajiya take ta dauke kai ta fice daga
apartment din ta nufi na Momy, wata kalar harara Hajiya take watsawa Yasir har ya
iso.

“Ina ka fito?”

Ya juya ya kalli Hurriya da tuni ta fice daga bangaren sannan ya kalli


mahaifiyarsa.

“Mun sauke Rukayya ne”

“Kun sauke Rukayya kamar ya?”

“Hajiya dare yayi shiyasa na kaita gida a mota, daga can Hurriya ta duba Amma”

“Ita bata san dare yayi ba ta kama hanya ta zo? Kasan ma a ina ta fito? Wace
yarinya mai tarbiya ce zata fita yawon dare?”

“Hajiya Stop...”

Ya fada yana kokarin danne bacin ransa.

“Ba sai ka min turanci ba, daman yaran zamani ne ku ai, sai ka zage ni ban sani ba,
amman dai bari ka ji na fada maka ka fitar sapgar Rukayyar nan ba yarinyar kirki ba
ce”

“Hajiya please karki munanawa Rukayya zato, yarinyar nan tana da hankali da
tarbiya, na san wacece ita, saboda ta yi dare baki san dalilin da ya saka ra yi
haka ba, ki daina fadar bata da tarbiya bata min rai kike, yanzu da wani yayi abun
da Khairi ta yi da yanzu kin zage shi, amman kin tsallaketa kina ganin laifin yar
wasu, dan Allah wannan ya zama na karshe da zaki fadi wata magana marar dadi akan
Rukayya”

Yana gama fadar haka be tsaya jin abun da zata fada ba ya wuce ciki ya barta a
gurin tsaye da mamaki.

“Ikon Allah baka son a fadi wata magana marar dadi akan Rukayya saboda Rukayya
kanwar uwarka ce? Anya dai Iyami bata Zuba maka ka sha ba, kai duk wani abu da ya
shafeta sonshi kake, daga kan Hurriya har Iyami yanzu kuma abun ya koma kan
kanwarta, eh lallai tun da ka ga farar fata, to Wallahi baka isa ba ba Rukayya ba
ko keya ce sai na ga bayanta, wato ma wani abu ne a cikin zuciyarka da har idan an
fadi sunanta da mugun abu ranka yake ba ci, har da wani tashi ka kaita gida kai ga
Sharukhan baban Soyayya, to da ni kake zancen”

Ta juya ta bi bayansa tana masifa, a falo ta zame shi zaune yana lasa wayarsa yana
ganinta yayi saurin tashi ya nufi stairs dan ya san fada zata masa, da kallo da
bishi har ya haye sama.

“Ba shakka, wato ubanka ya dandana nan bakin cikin Iyami shi ne kai ma zaka gwada
naka ko? Dadin abu kai haihuwar ka na yi ba aure ba, baka da ikon kanka sai ikon da
ake da shi akanka”

Ta zauna a inda ya tashi tana jin zuciyarta na wani irin zafi, domin bata da makiya
a yanzu kamar Iyami da iyalinta...

HURRIYA POV.

Da sallama ta shiga falon Momy ta dago ta kalleta ta dauke kai, Namra kuma dake
kwance cinyar Momy labarin da take da Momy ya hanata amsa mata.

“Ni Wallahi tausayi yake ba ni gaba daya ya koma kamar ba shi ba, dan murmushin da
yake da yanzu duk ya daina”

Momy ta shafa goshinta.

“Fadan kuma ya karu ba, sai bakar zuciya da ganin laifin kowa”

“Ai dole”

Hurriya ta risina tana yi ma Momy sannu da dare.

“Ina kika fito?”

“Tare da Yaya muka fita ya aje Mama Rukayya a gida ne, ni kuma na duba Amma”

Hurriya ta amsa tana jin kamar ace ita ce take kwance a cinyar Amma, Amma na shafa
kanta yadda ta shigo falon ta tararda Momy da Namra abun ya burgeta sai ya kara
mata kewar mahaifiyarta sosai. Namra ta tashi zaune

“Wayyo ban sani ba da naje dubata ya jikanta Hurriya”

“Da sauki”

“Allah ya kara sauki”

Hurriya ta amsa da amin sannan ta mike tsaye ta, Momy ta bita da wani kallo kamar
na tuhuma tana tsire baki. Hurriya ta shiga dakinta ta cire hijabin jikinta ta nufi
gaban madubi ta zauna tana kallon kanta, sai hawaye suka fara zubo mata. A take ta
sauke kanta kasa tana kallon hannayenta.
Rayuwar baya take tunawa lokacin da take cikin farinciki, Amma na kusa da ita Appa
yana kaunarta ga dan'uwanta abokin fadanta kuma mai tare mata fada. Ta tashi kamar
marar lafiya ta nufi gadonta ta zauna sannan ta cire gilashin idonta ta kwanta.
Bata farka ba sai asuba, bata fito dakinta ba sai 12pm shi ma kuma saboda yunwa ta
matsa mata lamba ne daman bata son fita ko'ina sai idan tana bukatar abinci, yanzu
ba irin da ba ne da take zuwa makaranta balle fita ta zame mata dole, tun bayan da
ta kammala Secondary school ta samu yancin zama a gida domin Appa be yi making wani
effort da zai nuna yana son ta cigaba da karatu ba. Ita kuma tana tsoron yi masa
magana sai dai ta yi ma yayanta shi kuma idan ya tunkari Appa da maganar sai yace
masa akwai abun da yake jira. Daga Momy har Hajiya Kaltume kuma babu wanda ya damu
da karatunta da ta yi da kar ta yi duk daya suke a gurinsu, Momy da yaranta take da
kanta daman rayuwar wani bata dame ta ba, Hajiya Kaltume kuma bata son Hurriya da
alheri ta ina zata damu da karatunta.
A hankali ta sauko kasa tana sanye da doguwar riga kanta babu dankwali, gashin
kanta a dan yamutse saboda rashin gyara shi da bata yi ba after ta yi wanka.

“Yauwa Hurriya dan Allah ki shirya anjima kadan zaki raka ni Mall na siye wani abu”
Ta juya ta kalli saitin gurin da Namra take zaune tana shafa abu a fuskarta.

“Toh Yaya Namra”

Sannan ta juya ta shiga Kitchen din ta hada tea ta fito ta nufi dining ta zuba abun
da zata iya ci ta dauka ta sake dawowa dakinta ta zauna a kasa ta nade kafafuwanta
ta fara ci, bata wani ci sosai ba ta fi ta koshi sai ta ja komai gefe ta aje. Tana
zauna a gurin har aka yi azahar, bata sake fitowa dakin ba sai da Namra ta tura
kofar ta leka ta.

“Kin shirya kuwa?”

Sai ta sauko saman gadon ta nufi gurin madubi ta dauka ta gyara kanta ta saka
ribbon ta dauki mayafin abayar ta rufa.

“Eh mu tafi yanzu”

Namra ta yi dariya ta girgiza kai sannan ta juya ta fita tana fadin.

“Shiyasa lokacin zuwa makaranta kike late ba zaki shirya ba sai a lokacin da ake
jiranki”

Murmushi kawai ta yi ta jira tare da Namra suna sauka tare, Hurriya na ganin Momy
ta yi saurin risinawa kamar yadda ta saba gaishe da manya.

“Momy barka da yamma”

Momy ta watsa mata harara.

“Sai yanzu kika ga damar gaishe ni, ba kin san ina cikin gidan ba? Me yasa baki
gaishe ni ba sai yanzu”

Ta yi shiru ba dan bata da abun fada ba, sai dan ta san tana fadar wani abu Momy
zata iya tsinka mata mari, kamar yadda bata isa ta shiga dakinta da sunan ta zo
gaishe ta, sai dai ta tsaya jiranta idan ta fito ta gaisheta kamar wata yar aiki,
wannan ne abin da Hurriya ta kasa yi, Momy kuma take jin haushinta.

“Momy mu dai mun tafi”

A take murmushi ya cika fuskarta tana kallon yar gudaliyar yarta mace daya tak data
haifa.

“Allah ya tsare, ya dawo lafiya yar Auta”

Ta yi murmushi sannan ta yi ma Hurriya alama da ta tashi su tafi, Hurriya ta tashi


suka fice tare. A tare suka shiga motar Namra na tuki Hurriya na zaune gaba tana
sauraren sautin da Namra ta kure a motar idanuwanta kuma suna kallon wani gurin
dabam har suka isa Sarauta Mall. A harabar Namra ta faka ta fito sannan Hurriya,
after ta rufe motar suka nufi cikin Mall din tana fadawa Hurriya abubuwan da take
son siya.

“Zaki iya daukar wani abu da kika ga kina so amman fa kar ya wuce 20k”

Fuskar Hurriya ta cika da murmushi.

“Na gode Yaya Namra amman ni ki ba ni kudin akwai abun da zan yi da su”

Da mamaki Namra ta kalleta tana kokarin kai hannu ta dauki turare.


“Me zaki yi?”

“Wani abu dai bana son na fada, amman yana da muhimmanci sosai”

“Shi ke nan to idan mun koma ki turo min account dinki sai na miki transfer”

Take a gurin Hurriya ta rumgume ta.

“Na gode Yaya Namra ke ma kina so na kamar Yaya Yasir”

Namra ta yi murnushi suka ci gaba da siyayyar after sun gama suka nufi gurin biya,
Namra ta bude jakarta ta dauko cart dinta ta mika.

“Aa an biya muku Hajiya”

“An biya kuma?”

“Eh ba na yau kadai ba har ma da wanda zaku sake zuwa nan gaba ko da kuwa za ku
yaye shagon nan ne gaba daya”

“Waya biya? Wanene wanda baya son kudinsa haka?”

“Gashi can bayanku”

Daga Hurriya har Namra juyawa suka yi kallon mai neman barar da kudi saboda be san
kimarsu ba. Suna hada ido kowanensu ya gane waye. Shi kuma ya nufo inda suke idonsa
na kan Hurriya.

“Kai ka biya kudi?”

Namra ta tambaya tana hade masa rai.

“Eh”

“Saboda me?”

Ya kalli Hurriya dake tsaye tana kallon ikon Allah.

“Saboda Hurriya”

“Miye tsakaninka da ita? Kuna da wata alaka ne?”

“Alakar dai nake kokarin kullawa, waye ke?”

Wannan karon Hurriya ce da kanta ta tari numfashin yayarta ta amsa masa rai a bace.

“Yayata ce, kuma daga yau karka sake nuna ka san ni domin ni ba yarka ba ce, kuma
karka sake kiran Yayana a waya kana cewa a hada ka da ni”

Adam yayi murmushi.

“Ya fada miki kenan? Na kira Khairi ta ki hada ni da ke, the last kiran da na yi ma
yayanki ma be saurare ni ba ya rufe ni da fada, Na gode Allah ma da na ganki a nan”

“Eh saboda basa son kana kirana kuma karka sake, sunana ya fita daga bakinka, mu
tafi Yaya Namra”

Namra ta bita da kallo she never thought Hurriya zata iya bude baki ta yi masifa
haka. Shi ma kallonta yake domin bata yi kama da irin yan matan nan masu masifa ba.
Adam ya maida dubansa gurin Namra da ta mika hannu ta dauki ledar kayanta.

“Khairiyya ce ta ce muku ni dan'iska ne?”

Namra ta kalleshi sama da kasa at his age ba zai wuce 25-26 ba that's mean ya bata
shekara daya kenan ko biyu.

“Malam Hurriya ba irin matan nan ba ne, dan Allah ka kama gabanka”

Ta dauki ledarta ta nufi kofar fita, suka bar shi a gurin kunya kunya ma'aikatan
gurin na kallonsa. Ko da Namra ta isa gurin motar Hurriya na tsaye ta hade rai ya
rungume hannayenta tana jiran fitowarta.

“Ashe kin iya fada”

“Ya bata min rai fa, jiya saboda shi Appa kamar zai dake ni, Kuma Yaya yayi ta fada
sosai”

Ta fada ba tare da ta kalleta ba.

“Shiga muje”

Hurriya ta bude motar ta shiga, Namra ta fara tukawa. A motar Namra sai zaginsa
take yana tsine masa tare da fadar daman irin samarin nan haka suke.

“Ni da na sani ma ba zan birthday din ba”

“Abun yar'uwa ace ba za aje ba? Ai dole ka je Khairy dai ta zama wata kalar mace
daman tun kamin ta kare karatun na wata friend dinta ke fada mana tana shan shisha,
kamar kar ta fara sami'ar nan sai ta hadu da friends din banza suka canja mata
rayuwa gaba daya ta canja”

Tana maganar tana kokarin kwaucewa motar take gabansu. Overtaking take son yi amman
mai motar ya hanata hanya, kasancewar titi express ne idan ta yi dama sai ya koma
can idan ta yi hagu sai yayi hagu. Horn ta danna da karfi shi ma ya mayar mata, at
first ranta ya baci har ta yi kamar ta bugu motar dake gabansu sai kuma ta danne
zuciyarta.

“Mai motar nan lafiya yake kuwa?”

“Ko yayi shaye shaye”

“Maybe”

Namra ta rage gudun motar shi ma sai ya rage, the second thing she did was laugh
irin abun yanzu kuma ya zama out of sence. Ta dan gwada kara gudun shi ma sai ya
kara, ta sake raguwa sai ya rage. Tana samun sa'a ta yi overtaking ta wuce da gudu,
shi ma sai ya danna a guje ya wuce, wannan karon har da Hurriya sai da ta yi
dariya, Namra ta sake yin gaba ta wuce shi sai ta sauya hanya, ga mamakinta sai ya
biyota a baya ya wuce, daga lokacin ne suka fara tseren gudu ita da shi ba dan sun
san waye a motar ba. Ita dai daman gilashin motarta a bude yake daga ita har
Hurriya ana kallon yadda suke shakar dariya su ne basa iya ganin wanda ke cikin
motar. Da gangan Namra ta sake sauya hanya tana dariya tana kallon nearby mirror
bata ga ya biyo ba, sai da suka kusa isa karshen Titi sai gashi ya bullo ta
gabansu.

“Mun shiga uku Hurriya waye mutumen nan?”

Hurriya dariya kawai take ta kasa cewa komai, domin a gurinta abun is so funny ita
bata tsorata kamar yadda Namra ta fara tsorata yanzu ba. Namra ta rage gudun
motarta ta sauka gefen titi shi ma sai ya rage gudun ya sauka gefen titi ya faka
gabansu.

“Ki daina dariya what if he want to kidnap us? Ko kuma wannan saurayin ne na dazu?”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi a take ta daina dariyar, A daidai lokacin da aka bude
motar wani matashin saurayi ya fito sanye da black T-shirt da wandon soja haka ma
kafarsa na sanye da black shoes. Murmushin da suka gani a fuskarsa ne ya dan
sanyaya musu zuciya domin alama da yanayin jikinsa be yi kama da masu aikata
mummunan aiki ba. Ya iso gurinta ya duko yana kallon fuskokinsu ko wannensu da
tsoro a idonsa.

“Nice race”

Namra ta dan yi murmushin karfin yana kallonsa, daga fuskarsa har hasken fatarsa be
yi kama da dan nigeria ba rigar soja dake jikinsa da kuma wandon. Sai dai kafarta
na kan burki jiran kawai take ta ga wani abu ba daidai ba ta taka burkin da karfi.

“Na zo na bi ku har gida sai kuma na yi gudun kar na tsorata ku”

“Yanzu ma a tsorace muke”

Yayi murmushi sosai ya shafa kansa.

“Na gani ai a idon wannan”

Ya nuna Hurriya.

“But i like it, tun da kuka fito Mall nake binku shiyasa na so na bi ku har gida in
case of na yi mussing race sai na biyo na kwankwasa muku”

Namra ta yi murmushi, Hurriya kam har lokacin a tsorace take. Hannu ya saka Aljihu
ya ciro karamin kati ya aje mata.

“Here is my cart duk lokacin da kika yi marmarin race just give me a call I'm Salim
Sarauta aka Ethiopian nice to meet you All”

Still idonsa ya kan Hurriya da tsoro ya gama bayyana a fuskarta, ya juya ta nufi
gurin motarsa ya shiga ya yi reverse ya hau titi, sai da ya kawo saiti mn gurin da
Hurriya take sannan ya danna horn sau biyu. Namra ta danna ta masa sau daya
murmushi yayi ya dauke kai yaja motarsa, Namra ta bi motar da kallo ta mirror ta
kai hannu ta dauki katin tana dubawa kamin ta kai babban yatsanta ta shafa. It take
her some minutes tana kallon katin sannan ta ja motar suka cigaba da tafiya, bata
yarda baya binsu ba sai da suka isa ta faka motarta.

“Yaya Namra na fada miki account din a yanzu”

“Bari sai mun shiga ciki na huta”

“Toh”

Ta bude motar ta fita tare da ledar da suka yi siyayya, har ta isa bakin kofar
falon ta tura ta shiga Namra na zaune a motar bata zare key ba sai kallon katin
take, har yanzu zuciyarta bata gama yarda mutumen kwarai ne ko na banza ba, and ta
kasa zaba mata tsakanin jefar da katin da kuma barinsa...
•••••
•••••
•••••

khairi ta tashi zaune da sauri tana kallon Hajiya Kaltume dake yakar hakora tana
murmushi.

“Haba Hajiya ni dai gaskiya”

Sai kuma ta yi shiru.

“Ke dai gaskiya me? Kin san dai tarenmu da Hajiya Fatee ko wani dabam ta dauko ta
ce ki aura ba zaki ce aa ba balle kuma danta, yaro kuma yana da nasa rufin asiri
daidai gwargwado”

“Amman yana da mata fa Hajiya”

“Ina ruwanki da matarsa? Matar da uwarsa ma ba sonta take ba, kuma saboda ita ne
ake son hada aurenku”

“Ni gaskiya ba zan auri mai mata ba da kurciyata haka nan, kuma yana da yara fa,
Hajiya kin fa san sha'anin kishiya yadda yake”

“Ko rabuwa suka yi ba hannunki yaran zasu zauna ba, kuma muna fatar kamin ki shiga
ma ita ta fita kin ga shi kenan an huta”

Ta bata fuska sosai kamar zata yi kuka.

“Gaskiya Hajiya ina da sauran time yanzu fa na gama makaranta kuma nake rayuwa”

“Matsalata dake wani lokacin baki da wayo Wallahi gaba Khairi”

Ran Hajiya ya fara baci ganin tana kokarin taro yarta tana kaucewa.

“Tashi dauko min wayata tana ringing”

Ta tashi yana turo baki gaba domin ta ko'ina bata ganin ta dace da aure a yanzu da
take cikin cin lokacinta.

“Maama ce”

Ta fada tana juyowa tare da picking din call din.

“Innalillahi”

Ta yi saurin mikawa Hajiya Kaltume jin yayarta tana kuka. Hajiya Kaltume ta karba
ta kai a kunne gabanta na faduwa.

“Subhanallahi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, abun har ya kai haka? Wai anya
Rilwan yana da hankali kuwa? Be san waye ubanki ba a garin nan da zai saka hannu ya
dake ki”

“Duka...!”

Khairi ta amsa da karfi tana kai hannu a gaba da mugun mamaki.

“Shi kenan gani nan zuwa, ki fada masa sai ya san ya saka miki hannu, ni da nake
uwarki ban doke ki ba sai shi da ya ganki da hakoranki talatin da 2”
Ta sauke wayar tana masifa

“Ni da na san haka yaron nan yake Wallahi ba za'ayi auren nan ba, tun da aka yi
auren nan kullum cikin tashin hankali nake, shiyasa idan na ga kiranta gabana har
faduwa yake, yanzu abun ya kai har da duka da zagin iyaye”

Khairi ta tabe baki.

“Wannan mijin nata fa dan shaye shaye ne Wallahi komai zai iya aikatawa”

“Wane irin shaye shaye halinsa ne, tun tana amarya yake mata wannan iskanci yanzu
kuma abun ya fara wuce gona da iri, yau shekara uku da aure nan amman kullum cikin
fitina ake ita ba kishiya ba balle ace asiri ake mata”

“Amman dai ai yana neman mata kuma yana shaye shaye”

“Ta ina kika sani kin jiki da zancen banza, ke ba zako iya shaidar mutane da abun
kirki ba sai na banza”

“Ni Wallahi na san abun da yake nan Hajiya ke ce baki wayanci duniya ba”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye daker tana latsa kafarta dake ciwon tun faduwar da
tayi.

“Ina jin ciwon kafar nan haka dole zan tafi, wannan wane irin tashin hankali ne, ga
mu cikin makiya yaro yana son kwance mana zane a kasuwa”

Ta nufi gurin da tufafinta suke ta shirya ta dauki jakarta tana tafiya kamar zata
yi gurmanta saboda zugin da kafar take mata duk kuwa da zuwan da ta yi asibiti jiya
ta kai kafar. Rai a bace ta shiga mota direba ya ja motar suka fice. Shekara uku
kenan da auren babbar yarta da ke bin Yasir wato Maama amman ta kasa samun
kwanciyar hankali irin na uwayen da suka aurar da yaransa, kusan duk wani kira da
Maama zata mata daya gaisuwa daya kuma na karar mijinta ne ko kuma shi ya zo har
gidansu ya kawo kararta.

__________

A gafarce ni please Wallahi uzuri ya rike ni. Amman In Shaa Allah ba zan sake post
late ba, idan na sake ku ce min Hajiya Kaltume 🌚🥺

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

1️⃣
2️⃣ 2️⃣
1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 2️⃣

Tun daga falo Hajiya Kaltume take jin kukan Maama, hankalinta be kara tashi ba sai
da ta shiga cikin dakin ta ga halin da yarta take ciki.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Maama? Haka Rilwan yayi miki da jiki?”

Maama ta kara narkewa da kuka tana daga idonta da yayi ja ta kalli Hajiya.

“Hajiya Rilwan kashe ni zai yi, Hajiya makure ni yayi Wallahi, yau babu kalar zagin
da be yi min ba”

“Saboda me? Me kika masa? Wai me ya dauki kansa ne? Ko an fada masa baiwa aka kawo
a gidan?”

Maama ta rike kafar Hajiya da sauri tana kuka.

“Hajiya ki kai ni asibiti kar idona ya siyaye”

“Haba idon yayi? Wai me kika masa ne?”

Kasa magana ta yi sai kuka take sosai tana taba jikinta, kana ganinta zaka san an
doketa amman ba irin dukan dake bayyana jini ko fatar mutum a waje ba, ma'ana be
fasa mata fata ba amman yayi nasarar kumbura mata jiki, idon kuma yayi ja sosai
saboda kuka da kuma dukan idon da yayi. Cikin takaici da bacin rai Hajiya ta daga
wayarta ta kira Yasir ta fada masa halin da ake ciki, sannan ta rika Maama suka
fita daga gidan suka nufi asibiti.
Duk wata kulawa da ya kamata a bata likitocin sun bata, bayan an yi mata allura
suka rubuta mata magani, a asibitin Yasir ya same su shi ya karbi takardar maganin
ya siyo sannan suka dawo gida. Zama kawai ta yi Yasir be jira ta huta ba ya fara
tambayar ta abun da ya hadata da mijinta.

“Maama me ya hada ku?”

Kasa kallonshi ta yi balle har ta amsa mata, ko kadan bata son bude dalilin
fadansu, domin ta san yadda ransu zai bace idan ta fada, gashi mijin nata ba shi fa
hakuri bata san iya inda yamutsin zai kai ba.

“Ba magana yake miki ba?”

Hajiya ta saka bakinta.

“Hajiya tsabani ne kawai irin na mata da miji”

“Tsabani dai amman sai yayi miki wannan dukan? Kullum da kalar matsalar da ake fama
yanzu kuma abun ya kai ga duka”

“Ai har da zagin iyaye dazun da ta kira wayata ce min ta yi ya doke ta ya zageta,
amman yanzu ta kasa fadar komai, idan mu baki fada mana ba ai dole shi mahaifinki
ki fada masa”

Ta sauko kan kujerar da take zaune da sauri.

“Hajiya dan Allah karki fadawa Appa, dan Allah wannan abun ya tsaya iya nan?”

Yasir yayi mata kallon mamaki, Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Yau na ga abu, Maama wane iri son kike yi ma bawan Allah nan ne? Mutum ya cutar da
kai ka kasa fada saboda a daukar masa mataki kuma yanzu zaki ce kar a fadawa
mahaifinki? To idan ya ganki me zaki ce?”

“Zan koma anjima Hajiya bana son Appa ya sani please bana son kowa ma ya sani,
laifina na duk abun da ya faru amman na miki alkawari daga wannan ba za a sake ba”

Cikin kuka sosai take maganar tana hade hannayenta.

“Kin sha fadar haka, amman babu wani canji gashi nan duk ki bi kin rame saboda
tashin hankali, lokacin da kike gida ma kin fi kiba, an yi aure dan huta amman
hutun ya gagara”

Yasir ya mike tsaye.

“Hajiya tana da gaskiya, akwai abubuwa da yawa ba be zama dole iyaye su ji ba, kuma
tun da har ta fadi cewar laifinta ne sai a barta ta gyara”

Hajiya Kaltume ta dube shi.

“Yasir ba yau aka saba irin tashin hankalin nan ba, kuma yanzu tun da ya fara gwada
mata da duka ba raga mata zai yi ba, musamman ma idan ya ga an kyaleshi”

“Toh ya zamu yi Hajiya, kina jin abun da take fada da bakinta fa, kuma daman ko
wane gidan aure da kalar tashi jarrabawar maybe tata ke nan, kuma tun da har bata
son mu ji sai mu daga mata kafa”

Maama ta lumshe ido hawaye na sauko mata ita kadai ta san yadda take ji a zuciyarta
haka zalika ita kadai ta san kalar zaman auren da take da mijinta, abubuwa da yawa
ta kan rufewa iyayenta da kawayenta saboda kar ran mijinta ya bace, ta wani
bangaren kuma tana gudun haka ya zama silar lalacewar aurenta da mutumen da take
jin idan baya tare da ita zata iya mutuwa.

“Shi ke nan, Allah ya kyauta idan ya san wata ai be san wata ba, zan tashi tsaye da
rokon Allah ya kawo miki kwanciyar hankali a gidan mijinki, kuma za'ayi nasara”

Hajiya ta fada ita kanta Maama ta san Hajiya na fada ne kawai saboda Yasir yana
zaune a gurin, amman ba rokon Allah take nufi ba. Yasir ya nufi dakinsa be dade ba
ya sauko ya fice daga gidan gaba daya, Hajiya Kaltume ta mikawa Maama hannu alamar
ta dawo kusa da ita, haka kuwa aka ayi Maama ta bar kujerar da take ta dawo ta
zauna ta kusa da Hajiya Kaltume.

“Sha kuruminki, ko yanzu zamu sake Zub kudi da yardar Allah sai mun mallake shi,
sai na saka an yi masa aikin da sai ya dawo karkashin kafarki yana tsoronki, yadda
nake iya juya mijina a yanzu yadda nake so ke ma haka zaki juya naki mijin, ki
kwantar da hankalinki komai zai wuce”
Ta share hawayenta, ba dan ta gamsu ba, domin sun sha gwada yi amman shiru ko abun
yayi kamar zai kama shi sai ya kuma ya watse. Ta daga kai ta kalli Khairi wanda ta
shigo rai a bace hannunta rike da waya. Ta nufi yar'uwarta da sauri hankali a
tashe.

“Innalillahi Maama ji fuskarki”

Wani hawaye ya sakd taruwa a idon Maama.

“Wai ke ba zaki iya rabuwa da wannan azzalumin mutunen ba? Ba haihu kika yi da shi
ba balle ko ace saboda Yaya”

Maama ta rike hannunta sosai ta jimke.

“Khairy ba zaki gane ba, duk wani abun da kike ganin zaki iya yi ko kin iya a waje
ne, da zarar an yi aure labari ya sauya, kuma ki roki Allah kar ya dora miki
jarabawar son namiji fiye da yadda yake sonki”

Daga Hajiya har Khairi tausaya mata suka yi, domin su duk yan kallo ne babu wanda
ya san abun da take going though sai idan ta fada ko kuma shi ya fada. Khairi bata
tada balli ba sai da dare yayi ta ga Maama ta shirya Yasir zai maida ita gida, a
lokacin ta fara fada tana ganin be dace abar Maama ta koma ba bayan duk abun da
yayi mata, ba a kira shi an masa gargadi ba.

“Ni ma dai haka na gani, abun ya fara kaiwa ga duka ya kamata ai iyaye su shigo
ciki, ko da baki fadi abun da ya hada ku ba sai ayi masa gargadi”

Ta girgiza ma Hajiya Kaltume kai tana fashewa da kuka.

“Aa Hajiya dan Allah, bana son kowa ya ji, kuma abun be kai ace za a saka iyayensa
ba, duk abun da ya faru laifina na na fada muku”

“Toh Allah ya kyauta gaba, tashi ku tafi”

Khairi ta bita da kallo baki sake tana ayyana idan ita ce ba zata iya daukar wannan
iskancin ba. A mota babu kalar nasiha da jan kunnen da Yasir be mata ba, bayan ya
yaba mata na boye sirrinta da ta yi.

“Sai dai ba komai yake bukatar boya ba, wani abun idan yayi yawa yana da kyau iyaye
su ji saboda a dauki mataki”

“Na gode Yaya kuma In sha Allah zan dauki shawarka”

“Allah ya sauwake kuma ya kawo kwanciyar hankali a tsakaninku”

“Ameen”

Ta bude motar ta fita kamar ba ita ba, aure mai saka ladabo in ji hausawa. Tsayawa
ta yi a gurin har sai da yayi reverse mai gadi ya bude masa gate ya fice sannan ta
juyo ta shigo ciki.

HURRIYA POV.

Hurriya ta shiga dakinta ta aje mata siyayyar da suka yi sannan fito ta shige
dakinta. Namra kam ta dade a motar tana sannan ta fito ta rufe ta shiga cikin
gidan. Ko'ina na falon kamshi yake alamar an sauke abincin dare tun kamin magariba,
tun kamin ta haura sama ta cire mayafinta ta shiga dakinta, saman gadonta ta aje
mayafin kuma a saman dai ta zauna tana duba kayan shower gel ne da perfume. Bandaki
ta nufa ta fara jera gel din sannan ta fito ta jera turaren ta dauki daya ta nufi
dakin Hurriya, ko da ta shiga Hurriya na tsaye jikin windows rumgume da hannayenta
tana kallon waje.

“Hurriya”

Ta juyo ta kalleta

“Ga turare daya ki yi amfani da shi, kuma ki tura min account din sai na saka miki
kudin, amman dan Allah me zaki yi da su?”

“Wani abu ne na sirrina Yaya Namra karki takura please”

“Shikenan i trust you na san ba zaki yi wani abu marar kyau da har za ace waya baki
kudin ba? You're not a bad girl”

Namra na magana tana kai hannu ta ja naman fuskarta cikin salon wasa. Hurriya ta yi
murmushi ta sauke kanta kasa. Namra ta aje mata turaren saman gado ta fice zuwa
dakin Momy. Ta tura kofar dakin tana sosa kanta.

“Momy wai ni kam Sarauta nan suna da Family da yawa ne?”

Momy dake kokarin cire sarkar zinarin dake wuyanta ta kalleta.

“Sarauta sunan kakansu sai ya zama yaya da jikoki suna amfani da shi, me ya faru”

“Ba komai kawai ina mamaki ne, wani muka ji ana fadarsa wai Sarauta”

“Sunan da suke bearing ne, kuma ba laifi suna da kudi kamar dai mu, yanzu kuka
dawo?”

“Eh na ji gidan sai kamshi yake an sauke girki”

Momy ta yi murmushi ta mike tsaye, ta nufi bathroom Namra kuma ta kwanta a gurin ta
dauki wayar Momy tana tabawa.

After fitar Namra Hurriya ta nufi gurin da turaren yake ta kai hannu ta dauka ta
bude kamin ta shinshina kamshinsa Khairi ta turo kofar dakin ta shigo a kufule,
waya a hannunta ba tare da ta ce komai ba ta mikawa Hurriya wayar. Sai da Hurriya
ta fara kallon wayar sannan ta kalleta. Khairi ta daka mata tsawa.

“Ki karba mana”

Ta karba da sauri ta kai kunnenta ba tare da sanin waye ba.

“Hurriya i wanted to talk to you so badly duk wani abun da kika ji akaina karya ne,
kawai Khairi tana fadar son ranta ne”

Hurriya kallon Khairi kawai take wayar a kunnenta ta kasa cewa komai.

“Hello... Are you there”

Ta sauke wayar ta mikawa Khairi ba tare da tace komai ba, Khairi ta karbi wayar ta
kai kunnenta.

“Bata son magana da kai ya kamata ka gane mana”


“Yeah that's because you told I'm a bad person, dazun nan babu kalar maganar da
bata fada min ba a gaban mutane kuma duk laifinki ne”

“Ta ina abun kuma ya zama laifina Adam? Ni ban fadi wata magana marar kyau akanka
ba, idan ma zan bata ka ko na zage ka ai kamar na yi ma kaina ne”

Cikin fushi ya tsinke kiran ba tare da ya sake cewa komai ba, ita kuma ta kalli
Hurriya daman kowa da wanda ya raina.

“Cikin mutane kika ci masa mutumci? Kuma kika ce masa na ce yana shaye shaye?”

“Ni ban ce kin ce ba”

“Amman dai kin masa cin mutunci a gaban mutane ko?”

Ta yi shiru, a take Khairi ta kai mata duka a baki daman tana da haushinta, tana
ganin saboda ita Yayanta yaya mata duka ya ci mutuncinta a gaban friends dinta,
yanzu kuma saboda ita Adam ya kira yana fada mata magana son ransa.

“Haba Yaya Khairi”

“Au haba ne? Ni banza kika saka aka yi min duka? Munafuka yar kasan wuta, haka
kawai kika ja min cin mutunci da duka a gaban jama'a”

Ta kai mata duka a fuska, Hurriya ta matsa baya ganin tana son yi mata illa.

“Wallahi tallahi sai na miki fiye da abun da kika min Hurriya, sai na dandana miki
bakinciki”

Hurriya dai bata ce mata komai ba sai kallonta take, Khairi ta yi kwafa ta juya ta
fita daga dakin, sai kuma ta dawo da sauri ta nuna da yatsa.

“Sauran kuma ki fadawa Yaya Adam ya kira na kawo miki waya, ki ga yadda zan taka
wuyanki wannan kassan na jikinki duk sai na karya su”

Ta yi kwafa a karo na biyu sannan ta fice, Hurriya ta zauna bakin gadonta tana taba
bakinta dake mata zugi...

“Allah ya saka min in one way or the other”

Ta fada idonta na cika da hawaye, sai da ta gama taba bakin sannan ta tashi ta
dauko pen ta dubuta account dinta ta fice daga dakin, kofar dakin Namra ta fara
turawa ganin bata ciki ya saka ta aje mata takardar a kan gadonta juyo ta fito.
Dakinta ta sake komawa ta dauki littafin da Gwaggo ta bata na addu'o'in ta sauko,
Garden ta nufa sai da ta zauna sannan ta bude ta fara karanta addu'o'in yamma.

HAJIYA KALTUME.

A waya ta labartawa Malaminta abun da ya faru, tana hada masa da magiya tare da
alkawarin yi masa duk abun da yake so matukar ya taimaka mata Maama ta samu kan
mijinta.

“Haba Malam kai da ka ra kwafar min da Alhaji, kuma ga Iyami ma sai labari za ace
wannan ya gagareka”

“Ba gagarata yayi ba Hajiya, wato yaron nan iyayensa suna tsaye akansa, duk lokacin
da zamu yi aiki ba ma samunsa ko da ma ya kama zaki ga abin ya bi ruwa, amman duk
da haka zamu kokarta zam sake yi masa aiki mai karfi”

“Dan Allah a taimaka Wallahi yanzu ba ni da tashin hankali sai na yarinyar nan,
kasan yadda uwa take jin idan ta aurar yarta a gidan tashin hankali, burina ace
tana zaune da mijinta lafiya kamar yadda nake da nawa”

“Karki damu zamu yi haka, yau da daren nan akwai wuridin da zan yi mata, komai zai
wuce”

“Toh shikenan zan sako mata na goro yanzu a account in Shaa Allah”

“Hajiya kenan toh sai na ga sakonki”

Daga haka suka yi sallama, bata aje wayar ba ta kira aminiyarta, sai da ta fara
shimfida mata halin da suka sami Maama sannan na Malam ya biyo baya.

“Oh wannan yaro dai ya zama butulu, an yi aure lafiya lafiya ashe mugu ne”

“Ai ni da na san haka yake Wallahi ba zan yarda ta aure shi, daman can ni be wani
kwanta min ba”

“To yaran zamani ne ko kin hana ta ai ba zata hanu ba saboda tana son shi, kuma
wani ba za a gane halinsa ba sai an yi auren ba”

“Amman dai Malam yace min zai yi aiki yanzu”

“Ai haka yafi, ni wasu mamaki suke ba ni fa ki duba ko yarinyar nan Afrah yadda
aiki be kamata, da yana kamata da yanzu ta bar gidan nan amman sai kashe kudi nake
a banza ko gezau”

“Shi ma yace iyayensa suna tsaye a kansa, amman duk da haka na san ba zai gagara
ba, karki so ganin yadda Maama ta lalace kamar marar lafiya saboda babu kwanciyar
hankali a gidan miji”

“Ai kam dole a tashi mata tsaye, ni ma na kiransa domin ina jin alamar motsi a
cikina”

Hajiya Kaltume ta zare ido kamar kawarta na gabanta

“Motsi kuma?”

“Wallahi, na fada masa sai yace na bashi lokaci zai bincika yake ga me kenan a jiya
na fara jin abun”

“Haba Hajiya Fatee kuma kike magana kamar kina kalau? Ai zama be gan mu ba, kira
shi yanzu nan idan ma zuwa ya kamata yayi sai ya zo ayi abun da ya dace, an samu
danne abu shekara uku yanzu kuma ace Labari ya canja, ai yanzu ne zamu fi shiga
tashin hankali ma fiye da baya”

“Ni ma ai hankalin nawa ba a kwance yake ba, ina jiran na ji daga gareshi ne”

“Muna aje waya yanzu nan ki kira shi, har sai kin jira ya kira ai mai nema bi yake,
kira shi yanzu nan”

“Toh Hajiya”

Hajiya Fatee ta katse kiran, ta shiga contact dinta ta nemo number sa da ta yi


saving da Yaya Malam saboda badda kama. Fuskarta shimfide da damuwa ta kara wayar a
kunne, sai dai har kiran ya katse ba daga ba, ta sake kiransa ya sake katsewa ba
daga ba sai a na biyar a lokacin da hankalinta yayi kololuwar tashi. Yana daga
kiran sai da ta sauke ajiyar zuciya tana jin wata rahma na sauko mata.

“Salamu alaikum Malam ina ta kira baka daga wayata ba lafiya”

“Toh Hajiya gani dai Alhamdulillah”

Tana kokarin karantar damuwar dake son aika mata ta sautin muryarsa ta ce.

“Ba lafiya ba Malam, me ya faru? Akwai wata matsala ne?”

“Babba ba karama ba, shi ya hana ni daukar wayarki, ni kaina ina cikin tashin
hankali”

Ta mike tsaye sai kuma ta koma ta zauna.

“Malam fada min me ya faru”

Malam yayi shiru kamar baya gurin can kuma ya numfasa ya ce.

“Wato Hajiya cikin nan ne ya sake tashi”

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, garin ya Malam? Ya aka yi haka ta faru”

“Ni kaina abun ya ba ni mamaki, shiyasa na ce ki ba ni dama na yi bincike kuma da


na yi bincike na gane yadda matsalar take, sai dai maganinta ne da wuya”

“Kamar ya Malam na shiga uku”

Ta mike tsaye again ta fara safa da marwa tana kuka da babu hawaye mai cike da
tashin hankali.

“Ba ki shiga uku ba, indai zaki iya domin wannan mafitar da na samu na sha wahala
kam amman kuma karshe ce”

“Malam fada min kai tsaye dan Allah ka saka ni cikin rudani”

“Wato Aljannun da muka saka suka yi aikin nan, su suka warware shi, kuma suka
waiwayo suna bukatar wani abu a gurinki mai girma....”

Hajiya Fatee bata san lokacin da gumi ya karyo mata ba, ta ji kamar ta dora hannu
akai.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to
08036126660

1️⃣
3⃣ 3⃣1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 3⃣

“Fada min Malam na ji idan abun da zan iya ne, kana ta kara jefani cikin tashin
hankali”

“Wato Hajiya maganar ce da nauyi, sai dai ya zama dole a fada, Hajiya Aljannuna nan
suna bukatar kwanciya dake”

Hajiya Fatee ta dora hannu saman kai ta matsa baya.

“Ni kuma? Ina Aljanni ina mutum Malam”

Yayi dariya dake kara tabbatar da gaskiyar abun da yake fada.

“Hajiya kenan ai suma suna son mata sosai fiye da yadda maza bil'adam suke son
mata, shiyasa suke auren matan hausawa”

A take hankalin Hajiya Fatee ya kara tashi.

“Malam ni ai ka kara firgita ni, ni ba yarinya ba balle ace sun ga wani abu a
jikina ya burgesu”

“Ko tsohuwa ce ke babu ruwansu matukar kin yi musu, balle ke Hajiya jikinki ma ba
za'ace kin yi shekarunki ba ga ki fara kin san aljannu suna son farar mace, dan
haka ki natsu ki yi shawara da zuciyarki, kuma karki kuskura ki fadawa kowa domin
suna nan tare da ke kuma sun ce basa son magana, saboda haka ki yi shawara da
zuciyarki duk abun da ta yanke miki sai ki yi amfani da shi, amman lallai kin ji
abun da suke bukata”

“Amman Malam ba za'a iya ba su wani abun ba su hakura?”

“Babu wani abu da suke so sai abun da na gabatar miki, wato abun da baki sani ba
shi ne, kamin na same ki da maganar nan sai da na yi ta lallaba su amman ina suka
ki yarda, dama na san zaki tsorata ai amman ina son ki kwantar da hankalinki ba wai
zai zo miki a mutum ba ne, a cikin jikina zai shiga, kuma babu wani abu nawa da
zaki ga ya canja, ni zaki gani a zahiri amman a badini ba ni ba ne Aljanine”

“Shi ke nan Malam zan yi shawara”

Ta sauke wayar cikin tashin hankali, ta rasa ta ina ma zata fara tunani, anya
aljannu ke bukatar haka ko kuma Malam? Ta ina aljannu zasu ce sai sun shiga a jikin
wani za su kwanta da ita, har ta fara lalaben number Hajiya Kaltume sai kuma ta
tuna ya ce mata aljannun sun ce basa son magana.

“Kai.... Kai.... Kai... Wannan bala'i da me yayi kama? Wannan tashin hankali duk na
minene? Abun da ban yi kurciya ba zan yi yanzu? Haka ina ji ina gani yara kanana
suka keya min rigar mutunci, yanzu kuma ga wata sabuwar matsalar ta fuskanto ni,
karshenta kuma idan ban amince ba zai ce cikin nan bayyana zai yi idan kuma haka ta
faru ya zan yi da duniya”

Ta fashe da kuka sosai ta sauko kasa ta zauna tana kuka har wani gurnanin ke fita.

“Wanna yarinya Afrah kin cuceni ba dan ke ba da ban san kofar gidan ko wane malami
ba, da yanzu duk wannan bala'in be same ni, saboda ke dan abun da Alhaji ya bar min
duk ya kare, kuma ban samu biyan bukata ba, ko da Matsalar ba taki ce ke kadai ba,
tun da zuwan na Kaltume ne, kuma ita ba a mata komai ba, gashi ta samu biyan bukata
ni kuma ina cikin bala'i”

Kuka take sosai tana kara jin tsanar surukarta a cikin ranta, kuka ta yi sosai har
sai da idonta ya kumbura bakinciki ya hade mata, idan cikin bayyana babu wanda zai
yarda a daji ta samo shi, domin shekara uku yanzu da faruwar abun, sannan kuma bata
san abun da zata fadawa danta da yan'uwanta ba, gashi kuma ba zata iya amincewa da
bukatar Aljannu Malam ba, idan ta tuna da fason dake kafarsa ma sai ta ji kamar
zata yi amai balle kuma ace ta kwanta gado daya da shi, bakauyen da gora ya gama yi
ma fenti a hakora, mutumen da be wuce zama mai gadin gidanta ba. Har aka kira
Isha'i kuka take ko da ta hakura idan ta tuna sai ta ji kukan ya dawo mata, ita ba
da samun nasara ba ita da kwasar ciki ga kuma bukatar Malam a yanzu, da zuciyarta
take shawara ko dai ta kyaleshi ta nemi wani Malamin ne, ta wani bangaren kuma tana
ganin kamar kamin ta samu Malamin da zai iya kwantar mata da cikin kamar yadda
wannan yayi abu ne mai wahala kuma bata san sherin da zai iya binta da shi ba, ta
kuma san cikin ba zai cire a yanzu ba a lokacin da yake wata uku ma aka fada mata
akwai matsala a zubarwa bayan kuma ta sha magani be zube ba balle kuma yanzu da
ciki ya sha kwanci shekara uku. Carbin dake hannunta kawai take ja ta rasa ma ta
ina zata fara, salati zata yi ko tasbihi ko istigifara gaba daya ta rasa abun
kamawa sai kuka kawai take tana juya carbin.

“Sallamu Alaikum”

Ta yi gaggawar kawar da fuskarta ba tare da ta amsa sallamar ba, sai dai haka be
hana danta Fadeel fahimtar kuka take ba, ya fahimci fushi take dashi domin dazun da
ya shigo gaisheta da safe bata amsa masa ba.

“Subhanallahi Hajiya Lafiya”

Ya fada bayan ya zauna a gefenta yana kallonta damuwar dake tattare da shi ta
gagara boyuwa. Kamar mai nema sai kawai ta fashe da kuka, abun yana cinta a rai
kuma bata isa ta yi labarin da kowa ba, domin babu wanda ya san komai sai
aminiyarta Kaltume, ko da zata fadawa kowa a duniya ba zata yi gangancin fadawa
Fadeel ba, tana jin kamar ace abun da zata iya fitarwa ne ta tattauna amman babu
hali.

“Allah yasa ba ni ne silar zubar hawayen nan ba Hajiya”

Ta kara kawar da kai ta tsakaiga kukan ta share hawayenta, sai dai bata yarda ta
kalli gefen da yake ba ma, hakan kuma sai ya kara daga masa hankali.

“Hajiya... Ki yi hakuri dan Allah idan ni na bata miki”

“Fadi ba shi da amfani domin na sha fada babu abun da ya canja, amman dai zan baka
zabi uku a yanzu, Fadeel ko dai ka saki Afrah, ko ka kara aure, ko kuma na yafeka
yafewa ta har abada...!”

Be san lokacin da jikinsa ya saki ba yayi nauyi a gurin.


“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Hajiya ta tabbata dai saboda da ni kike zubar
da hawayen nan. Hajiya ina son matata sosai domin ina jindadin zama da ita, amman
Wallahi zan iya rabuwa da Afrah matukar hakan ne burinki, kuma zan kara aure idan
har hakan zai saka ki farinciki, amman ba zan iya hakura da ke ba, ba zan yarda ki
yafe ni ba, ba nida wani abu da ya fi ki muhimmanci a duniyar nan, gaisuwar da na
yi miki dazun ma na tafi baki amsa min ba, ban wuni cikin farinciki ba”

Ya sauke ajiyar zuciya ya sauke kansa kasa.

“Na ji dadin da kika saukaka min kika ba ni zabi har uku, kuma na zabi na uku zan
kara aure kuma na miki alkawari matar da kike so ita zan aura, Allah ya huci
zuciyarki”

Ya mike tsaye yana fadin.

“Zan tafi Allah ya tashe mu lafiya”

Har ya fice bata juya ta kalli inda yake ba, bata jin tana da wata makiyiya a yanzu
fiye da Afrah, saboda tana ganin saboda ita danta baya mata biyayya kuma ya canja
mata. Ada can baya kamin Fadeel yayi aure shi din Mommy's Boy ne kullum yana gida
ba shi da abokin hira sai ita, komai zai yi sai ya fada mata tufafi ma ita take
bashi shawarar wadanda zai saka, a gidanta yake zaune. Sai dai yana haduwa ya Afrah
sai ya fara canja mata, bayan kuma ya guji matar da ta so ya aura da farko, har ta
kai ya kasa zama a gidan kamar yadda ta bukata saboda Afrah ta nuna masa ta fi
sha'awar zama a gidanta ita kadai ba dole sai a gidan mahaifinsa ba kamar yadda
Hajiya Fatee take so, shi ma kuma da yayi tunani sai ya yarda da shawararta, yana
yin auren sai rayuwarsa ta koma gaba daya a gidan matarsa, zabin tufafinbda zai
saka wasa da dariya ko wani abun na rayuwa da matarsa yake ba da ita ba, idan ma
zai nemi shawararta sai idan wani abun ne da ya shafeta ko kuma yake da muhimmanci
sosai, idan zai siya mata tufafi zai dauki Afrah su tafi tare Afrah ta zaba mata
tufafi mai kyau mai tsada su kawo mata, sai dai hakan baya kara komai sai wutar
kiyayyar Afrah a zuciyarta, duk kuwa da kasancewar tana kyautata mata. Wannan ya
saka ta fara zagon kasa tana son ya saki matarsa shi kuma ya nuna mata yana sonta
sosai, kuma idan ya rabu da ita ba shi da mai rike masa yaransa.

Cikin matukar damuwa Fadeel ya isa gidansa, ya samu kansa da zama a cikin motar ya
kasa budewa ya fita, shi dai a ra'ayin kansa ba shi da burin aure mace fiye da daya
saboda baya son tashin hankali kuma yana son matarsa tana sonsa, ya yanzu ma yana
cikin tashin hankalin rashin jituwar da suke samu da Hajiyarsa ina ga ya kara aure,
and all this love da biyayya da Afrah take masa ya rasa da me zai saka mata sai
kishiya. Jin yayi ana kwankwasa kofar motar yana daga kai sai yayi arba da annurin
zuciyarsa tana aiko masa da murmushi. Ta tsaba ado kamar Sequence Wax din da ya
siya mata a gurin Khadeeja Candy ta karbi jikinta sai kyali take kamar an wantsa
mata gold. Ya sauke gilashin motar

“Madam”

“Yallabai yau lafiya kake kuwa”

Ya sauke ajiyar zuciya sannan ya bude motar ya fito ya rufe.

“Habibina fada min me yake damunka daman tun jiya na lura da haka, me ke damunka?”

Sai da ya kasa bakinsa sau biyu sannan ya iya aje numfashi a muhallinsa.

“Afrah yau na ga Hajiya a cikin wani hali da ban taba ganinta ba, ban san wata rana
da Hajiya ta zubar da hawaye saboda da ni ba, sai na ranar da aka daura aurena shi
amman na farinciki ne yau kuma akasinsa ne”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, me ka aikata haka wanda ya bata mata rai Abban
Aiman?”

Yayi shiru yana kallonta ba tare da ya amsa mata ba, tana ganin haka ta san inda
matsalar take kuma bata bukatar karin bayani, a take zuciyarta ta fara bugawa.

“Cewa ta yi ka rabu da ni? Hajiya ta ce ka sake ni ne? Dan Allah karka kara minti
daya a gidan nan baka aikata abun da mahaifiyarka ta bukata ba, akwai pen da
takarda a cikin motar nan dan girman Allah ka dauko ka rubuta min matukar haka ne
silar zubar hawayenta”

“Ba saboda haka ba ne”

Ya amsata still yana kallonta.

“To minene?”

“Aure take son na kara....”

Bugun zuciyar da ta ji a yanzu da ya fada mata bukatar Hajiya ya dara wanda ta ji a


lokacin da take zargin sakinta Hajiya ta ce yayi. Sai dai ko kadan bata yarda ta
nuna masa ba, sai ma dariya data fara yi dariya sosai har sai da mai gadinsu ya
juyo ya kalli gurin da suke tsaye.

“Shi ne kawai? Oh Ya Rabbi ai Hajiya ta yi min da sauki, ni a yanzu ba ni da tashin


hankali kamar na rabuwa da kai, ko da raina Hajiya zata ce ka cire ka kawo mata duk
mai sauki ne matukar bata ce na rayu babu kai ba”

Ta mamaki yake kallonta babu alamar tashin hankali a tare da ita sai ma farinciki.

“Afrah you're joking?”

Ta ware hannayenta ta rika hannunsa suka nufi cikin gidan, sai da ta raka shi har
dakinsa ta taimaka masa ya fara cire tufafinsa sannan ta ce.

“Yallabai ko da ka auro ni fa, mahaifina mace uku yake aure, na bude ido a gidan mu
na ga mahaifiyata da abokan zama ba ita kadai ba”

“I know amman na san kina hakan ne just to support me amman ku mata baku son
kishiya ai”

“Abban Aiman idan ban taimaka maka ka yi ma Hajiya biyayya ba ni da kai duk a wuta
zamu tashi, karka manta ni fa yar gidan Malamai ce, an karantar da ni ni ma na
karantar, na san hakki uwa akan yaya ta ina zan yarda Hajiya ta sake zubar da
hawaye saboda mu? Dan Allah karka fara tunanin wani abu ko ka damu, kuma wanda
Hajiya take so zaka aura”

Ta fada tana lakatar hancinsa tana dariya as normal yadda ta saba kamar be fada
mata komai ba.

“Shiga ka yi wanka ka fito bari na shirya abinci, kuma sauran idan ka fito ka manta
baka yaba kwalliyar da na yi maka ba”

Ta bukata sannan ta fice tana dariya, shi dai mamakin karfin halinta ya hana shi
motsawa daga inda yake ma. Tana fita dakin ta nufi kitchen dinta kofar kitchen din
ta fara rikewa ta kai hannu ta dafa zuciyarta dayan hannun kuma ta rike kofar
kitchen din kamin ta saki ta nufi sink ta dora hannayenta hawaye suka fara
floating.
HURRIYA POV.

Sai da aka fara kiran Magariba sannan ta fito daga Garden din ta dawo cikin falon,
dakinta ta shiga ta yi alwala ta yi sallah sannan ta sauko Namra na yi mata magana.

“Na tura miki kudin”

Ta dauri ta nufi gurin da take zaune ta rumgume ta.

“Na gode sosai Yaya Namra”

“Never mind yar kanwata”

Namra ta amsa mata tana dariya, Hurriya ta zauna kusa da ita tana matsar yatsun
hannunta.

“Yaya Namra”

Ta dago ta dubeta.

“Ina son na tafi gidansu Husna dan Allah”

“Yanzu?”

“Eh ba zan dade ba”

“Okay sai kin dawo”

“Amman Momy bata sani ba, kar ta zo duba ni, kuma kin san bata son a shiga dakinta
balle na fada mata”

“tafi zan fada mata”

Ta tashi cikin jindadi da murmushi a fuskarta ta sake haurawa sama ta shiga


dakinta, jakarta ta bude ta dauko ATM dinta ta boye a cikin rigarta sannan ta dauko
hijab ta saka ta sake saukowa ta fice. Tafiya take kamar ana dagata sama saboda
sauri tsoronta kar wani ya fito daga yaran Hajiya Kaltume su hanata fita ko kuma
Appa ya dawo a daidai lokacin ta san shi ma ba zai barta ta fita ba. Kamar an
korota haka ta rika knocking gate din gidansu kawarta kuma Neighbor dinsu a house
four ne tsakaninsu. Mai gadin na bude gate din ta fada da sauri.

“Ina wuni Baba”

“Lafiya Kalau Hurriya ce”

“Ni ce Baba sannu da aiki”

“Yauwa”

Ta nufi main door din tana tafiya a hankali saboda ta shigo cikin gidan. A falo ta
samu kawarta da sisters dinta suna hira, Husna na ganinta ta tashi da sauri ta
rumgume ta

“Oyoyo Hurry”

Hurriya ta yi dariya, sai da ta gaishesu gaba daya sannan suka shiga dakin Husna.
ATM dinta ne first abun da ta fara danka mata.

“Me zan yi da Atm”

“Ba ke na bawa ba, dan Allah taimako na ke son ki yi min Husna kin ga ke ana
barinki fita, dan Allah ki kaiwa Amma akwai kudi a ciki 20k dazun Yaya Namra ta
saka min, kin ga ni ba school nake zuwa ba yanzu balle na biya, kuma idan na ce zan
je Hajiya ba zata bari ba, Appa ma fada yake yi”

“In Shaa Allah zan kai mata, Hurriya wai ya zancen makarantar ki, an kusa rufe
siyar da form fa, kin ga da kina zuwa makaranta irin wannan duk ba zai gagara ba
sai ki yi satar hanyar kawai ki tafi”

“Ban sani ba Husna, ba ni zan saka kaina makaranta ba Appa kuma be yi wani motsi
ba, sun kyale ni haka nan zama kawai nake, gidan ma babu dadi”

Ta sauke kanta kasa hawaye suka fara sauko mata.

“Husna I'm lonely, komai baya min dadi yanzu i miss those old days da zan zauna na
yi hira da Appana yana dariya, na yi marmari jin muryar Amma, na yi marmarin
ganinmu a inuwa daya, na yi marmarin Hamad fadan da muke ma na yi marmarinsa, Husna
kowa yana da uwa a gidan yana da abokin hira ni kuma ba ni da shi, idan suna
bukatar abu kowa zai je gurin mahaifiyarsa ta yi masa ko Appa ni kuma ba ni da uwa
a gidan, idan kuma na kusanci gurin da Appa yake sai ya rufe ni da fada, baya ma
son ganina”

Husna ta dafa kafarta tana jin tausayinta.

“Ki yi hakuri Hurriya, wata rana komai zai wuce ya zama tarihi”

Hurriya ta kalleta hawaye na mata sallama.

“Hakan na nufin Appa ba zai sake so na kamar da ba kenan? Hamad ba zai dawo ba?”

“Ba haka nake nufi ba, ina nufin wata rana rayuwar farinciki zata dawo komai zai
wuce, dazun ma sai da muka yi hirarki da Umma ita ma take tambayata maganar
karatunki, tace kina bata tausayi sosai saboda halin da kike ciki”

“Husna ina cikin kunci ina jin rashin sakewa sai na ji kamar a wani guri nake rabe
ba a gidan mahaifina ba”

“Komai zai wuce Hurriya, ki yi hakuri, me Amma zata yi da wannan kudin?”

Ta share hawayenta.

“Gwaggo ta fada min an kai Amma gurin magani kuma mutumen yace sai an bashi 150k
shi ne dazun da Yaya Namra zata siya min abu na ce bana so ta ba ni kudin kawai zan
bawa Amma, saboda Gwaggo ta ce basu da kudi yanzu duk sun kashe kudin da ya rage
musu gidan da suke ciki za a siyar ni kuma bana son a siyar da gidan, kuma ban isa
na tunkari Appa na ce ina son kudi ba, sai ya fara min fada ni tsoron ganinsa ma
nake yanzu”

“Innalillahi Abun har ya kai haka? Wallahi duk wanda ya raba ki da mahaifinki ya
ci amanarki Hurriya, da a baya ne ko miliyan kika ce kina so Appa zai baki. Ya
Allah ka dubi Amma ka bata lafiya, zan fadawa Umma in Shaa Allah zata cika kudin”

Hurriya ta rumgume ta da sauri.

“Na gode Husna, na gode Allah ya saka miki da alheri”


“Ba komai, Allah ya kawo miki sauki”

“Ameen, zan tafi kar a fara nema bana kusa”

“Okay muje ki gaishe da Umma sai na raka ki”

Sun tashi a tare Husna ta saka Hijab dinta suka fito daga dakin, Husna ce ta yi
mata jagora zuwa dakin Ummanta not because of gidan yana bakonta sai dan zata fi
sakewa idan Husna ta shiga gaba. Mahaifiyar Husna ta amsa da far'a tana sakawa
Hurriya Albarka sannan ta kara ja mata kunne akan addu'a da kuma hakuri.

“Karki yi wasa da addu'a kina ganin yadda aka maida mahaifiyarki bayan an cireta a
gidan ubanki, ke ma kuma an shata muku layi, ki yi ta fadawa Allah matsalarki,
sannan ki kara hakuri ki yi da hakuri Hurriya komai zai wuce”

“In Shaa Allahu Umma na gode”

Ta tashi ta fito, suka jero da Husna a harabar gidan suna tafi suna hira, sam bata
lura da Yayan Husna dake tsaye can gefe dare da Abokinsa yana hira ba har sai da
abokin ya kirata.

“Hey Young Lady...”

A tare suka juya suna hada ido sai ya sakar mata mata murmushi ita ma ta dan yi
masa murmushinta mai tsada kadan ta gaishe su.

“Ina wuninku”

Mutumen ya tako ta karaso gurin da suke tsaye tare da Yayan Husna, still tufafin da
ta fara ganinshi da su ne sanye a jikinsa wato wando sojoji da bakar rigarsu T-
shirt.

“Kin gane ni”

Ta daga kai kadan sai yayi murmushi.

“Ina kawarki?”

“Yayata ce”

“Amma fa ta iya driving, kun ba ni wahala dazun fa, but still i enjoyed it, it was
fantastic”

Bata ce masa komai ba har ya sake wata tambayar.

“Nan unguwar kuke”

Nan ma bata amsa masa ba, Yayan Husna ya tambaye shi.

“Ka santa ne Ethiopian?”

“Yeah i meet them today at Sarauta's Mall”

Ta juya zata fara tafiya.

“Please ki kirata mu gaisa idan kusa ne, or invite me na je na gaishe da Yayarmu”

“Zan fada mata”


Ta fada ba tare da ta juyo ba.

“Okay ina nan ina jira”

As always bata ce masa uffan ba, sai kallon juna da suka yi da Husna, sannan ta
shiga fadawa Husna yadda suka hadu...

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘 08036126660

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

1️⃣
4️⃣ 4️⃣
1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 4️⃣

Har bakin gate din gidansu Husna ta rakota sannan suka yi sallama ta shigo ciki
Husna kuma ta juya ta koma. Hanayenta nade cikin hijab ta shiga falon Momy, Namra
na zaune a gurin da ta barta tana operating wayarta, Momy kuma na zaune gefenta a
dayar kujerar tana cin abinci. Hurriya ta fara isa gurin Momy ta risina ta
gaisheta.

“Momy sannu da gida”

“Ina kika fito”

Namra ta yi karaf ta ce

“Ta fada min da zata fita”

Momy ta dauke kai ba tare da ta saks cewa komai ba. Hurriya ta tashi ta nufi gurin
da Namra take zaune ta kai bakinta saitin kunnenta.

“Yaya Namra wannan mutumen da muka gani dazun yayi tsere da ke har kika karbi
katinsa, na ganshi yanzu a gidansu Husna tare da Yayanta kuma ya ce a kira ki ku
gaisa”

Namra ta wara ido tana kallonta da dan mamaki. Like really. Hurriya ta daga mata
kai.

“Yace ba zai tafi yana can yana jiranki sai kin zo”

“Ya akayi ya ganeki?”

Namra ta tambaya kadan kadan tana dan murmushi, Hurriya ta daga kafadunta alamar
bata sani ba.

“Okay zan je”

Hurriya ta yi murmushi tana amsa mata da kai sannan ta daga ta nufi dakinta. After
ta maida kofar ta rufe ta cire hijab dinta ta zauna bakin gadonta ta dauko Qur'anen
ta bude tana karatu, bata daga ba sai da aka kira sallah Isha'i sannan ta aje ta
dauki hijab din ta saka ta gabatar da Sallah Isha'i. Tana sallamewa Namra ta turo
kofar dakin ta shigo tana murmushi.
“Na je mun gaisa, amman ya tambaya wai ko ni na hana mi dawowa”

Hurriya ta yi murmushi tana karanta addu'o'in sallame sallah. Namra ta zauna bakin
gadon Hurriya.

“Yana da ban dariya, he's nice na yi mamaki yadda ya gane ki”

Hurriya ta shafa addu'ar da take ta mike tsaye tana kallon Namra irin duban nan na
tuhuma (Zargi)

“Yaya Namra.... ”

“What? Nonono please daga haduwa da mutum? Don't please”

Ta tashi da sauri ta fice tana dariya, Namra ma dariyar ta yi ta hau saman gadonta
ta kwanta, zuciyarta cike da farinciki alkwarin da Husna ta yi mata domin ta san
zata cika. Washe gari da yamma Husna ta dawo mata da martanin cewar ta fadawa
Ummarta kuma ta cika kudin and the most beautiful thing is ta tafi ta kaiwa Gwaggo
kudin har suna saka mata albarka suna godewa Umma. Hurriya ta rumgume ta da sauri
tana murna.

“Na gode sosai Husna”

“Ba komai tarenmu y wuce haka, and Umma ma na ji tana magana akan makarantarki
domin ta nuna damuwarta sosai akai gaskiya”

“Ni ma abun yana damuna, ina son na yi ma Yayana magana shi zai iya magana da Appa
ko Allah zai saka ya tuna da ni ya saka ni”

“Hurriya da neman magana waya ce miki Appa ya manta da ke?”

Ta yi dariya.

“Haka dai nake gani”

“kin ga bari na tashi ke ma haka kike da kin zo gidanmu baki wani dadewa sai ki
fara cewa zaki tafi”

“Laaaa ai to ni kin san yadda gidanmu yake ba ni da freedom ne, amman ke ba a miki
tsananin da ake min, dan Allah ki zauna Husna na jidadin zuwanki”

“Ba zan zauna ba, muje ki rakani”

“Idan naje zan sake dadewa”

“Naki wayon zan tafi idan ba zaki rakani ba”

Hurriya ta tashi da sauri ta dauki Hijab dinta ta saka, sannan ta bi bayan kawarta
da tuni ta fice daga dakin, a tare suka daga kai suna kallon Ruma dake isar da
sakon Hajiya Kaltume ga Hurriya.

“Ni kuma? Me na yi to Hajiya take nema na?”

“Sako aka kawo miki”

Gaban Hurriya ya fadi ita da Husna suka kalli juna kamin su kalli Ruma da tuni ta
wuce abunta ta barsu a stairs din tsaye.
“Kin yi da wani za'a kawo miki sako?”

“Aa Wallahi ni wa nake da shi da zai kawo min sako? Kuma idan za a kawo sako da
sanina ai ba za a kai bangaren Hajiya ba sai dai nan da nake zaune ko?”

“Haka ne kuma, to sakon miye”

“Ban sani ba”

“Allah yasa ba wani sherin aka kulla miki ba”

“Amin, bari na tafi kar na dade na yi laifi”

Husna ta dafata.

“Na rakaki?”

“Aa dan Allah ki tafi, idan Hajiya ta lura da yawan zuwan da kike zata iya bata
alakarmu, ni kuma bana son haka”

“Shi ke nan”

Tare suka sauko Masu aikin Momy suka gaishe da bakuwar Hurriya duk da kasancewar ta
yarinya ta amsa cikin Ladabi domin bata hadu da su lokacin da ta shigo falon ba,
sai yanzu da zata fita.
A karamin gate suka rabu Husna ta nufi babban gate din fita gidan, Hurriya kuma ta
nufi bangaren Hajiya Kaltume gabanta na faduwa domin ta san ita kullum mai laifi ce
a gurin Hajiya. Cikin tsoro da fargaba ta shiga falon kana kallon idanuwanta dake
cikin gilashi zaka san babu kwanciyar hankali a tare da ita. Nesa da Hajiya Kaltume
ta tsaya ta risina

“Hajiya ga ni”

“Sako ne aka aiko miki, wannan dan iskan yaron da mahaifinki ya rabaki da shi wato
baki ji ba ko?”

Ta girgiza kai da sauri.

“Wallahi na kyale shi Hajiya, daman ni ban san shi ba sai a bikin Yaya Khairi”

“Amman mai gadin daya karbo sakon ai cewa yayi yace ga sakon da yace zai aiko miki
nan”

“Ban yi da shi zai aiko min da sako ba, Wallahi Allah Hajiya”

Khairi ya yamutsa fuska tana jan tsaki.

“Karya kike munafuka, baki hadu da shi a Mall ba, jiya ai sai da kika saka yayi ta
min masifa sai da na kai miki waya kuka gaisa, amman yanzu kin wani narke kina
rantsuwa kamar gaske, sannu kitse”

“Ni ba wani abu zan ce miki ba, zo ki dauki kayanki kamin Mahaifinki ma ya gani ace
na hadaku”

“Ko dai yayi mistake ne, Wallahi ban yi da shi za a kawo min komai ba, Hajiya ki
yarda da ni”

Khairi ta taba hannu.


“Yau ina Yaya yake ya zo ya ga abun da salihar nan take aikatawa ana ganin kamar
sai mu kadai ne zamu aikata, gashi nan kin aikata fiye da na mu ma”

Hawaye ya fara saukowa Hurriya jikinta ya hau rawa, domin bata san yadda zata wanke
kanta ba idan maganar ta kai ga Yayanta ko Appanta da take tsoro yanzu kamar
mutuwa.

“Yaya Namra ma tana tsaye a gurin a kira ta a tambayeta”

Hajiya ta tabe baki.

“Ita da Yasir ai ko rai kika kashe ba zasu fada ba, saboda kin iya kirsa da
munafurci da kalailayar mai rai kin bi kin lafe a jikinsu uwa macijiya, ni ba wani
abun zan fada ba dauki kayanki ki tafi”

“Aa ni ba nawa ba ne”

“Daukar shi ne rufin asirinki Malam domin Wallahi idan baki dauka ba, Yaya na
shigowa zan nuna masa su”

Hurriya ta mike tsaye ta iso gurin ta saka hannu ta dauki kwaton kwalin da aka yi
ma kwalliya aka rubuta. From Adam to Hurriya in stylish way. Kuka be kamata ba sai
da ta fita daga bangaren na Hajiya Kaltume sai ta zauna a balcony ta fara kuka
marar sauti saboda ta san daukar ma zai zame mata laifi ne. Ta yi minti talatin a
gurin sannan ta tashi ta nufi bangaren Momy, a bude ta samu kofar falon, a lokacin
da ta shiga babu kowa a cikin falon, sai ta maida kofar ta rufe, ta nufi stairs
tana jin kamar ace Adam din yana kusa da ita ya yakuta masa fuska ta yaga tufafinsa
ta watsa masa ruwa da yawu a jiki da fuska, tana tunanin haka ne iya karshen
wulakanci. Maida kofar dakinta ta yi ta rufe ta zauna bakin kofar ta fashe da kuka
kuka sosai mai sauti, domin gaba daya ta rasa ma ya zata yi, ta kira Yayanta ta
fada masa kamin Hajiya ko Khairi su fada masa ko kuma ta samu Appa da kanta ta yi
masa bayani, ko kuma dai ta zauna a gurin har sai an nemeta. Sai da ta ci kukanta
ta koshi sannan ta ďa ga daga ta tura kwalin karkashin gadonta bata ma tsaya duba
meye a cikinta. Ta shiga bathroom ta wanke fuskarsa ta fito ta kwanta saman
gadonta, ana daf da kiran sallah Magariba Momy da Khairi suka dawo gidan, ita dai
tana dakinta bata leko ba, abun duniya ya isheta, saurare kawai take ta ji an aiko
cewar Appa ko Yayanta yana kiranta.
Immediately after gama Sallah Magariba tana zaune saman carpet din da ta yi
sallah, Namra ta turo kofar dakin ta shigo cikin yanayin damuwa.

“Hurriya wa kika bari ya shiga dakin Momy da nawa?”

Hurriya ta dago ta dubeta ta cikin gilashinta.

“Babu wanda ya shiga”

“Tuna dai ko wani shiga?”

“Babu wanda ya shiga Yaya Namra me ya faru?”

Kamin Namra ta amsa mata Momy ta shigo dakin a kufule fuska kamar bakin hadari, ta
nufi wardrobe dinta ta fara watsa tufafi tana zubarwa a kasa, kamin ta juyo ta yi
gurin gadonta ta daga Bedsheet din, sai kuma ta juyo ta kalli Namra.

“Ke sauka ki kira min masu aikin nan”

Namra da rashin jindadin abun da Momy take yi ya bayyana a fuskarta ta ce.

“Momy dan Allah mu bi abun nan a hankali”


“Zaki sauka ki kira su ko sai na bata miki rai?”

Namra ta juya da sauri, domin ta fi kowa sanin yadda Momy take idan ranta ya bace.
Hurriya dai na zaune a gurin da ta yi Sallah faduwar gabanta a yanzu ya fi na
kallum, duk wani sake sake da take a ranta na dalilin shigowar Momy a dakin da kuma
tambayar da Namra take mata be kawo mata cewar zarginta ake da abun da bata taba
aikatawa ba ko a mafarki, har sai da masu aikin har uku suka shigo dakin.

“Ku bincika min ko'ina na dakin nan, ku duba min sarkar Namra da tawa da kuma
kudin”

Hurriya ta mike tsaye da sauri irin mikewar nan kamar wanda aka lakawa wutar nepa.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, ni kuma? Momy ni...? Momy ban taba ba, Wallahi
ban dauka ba, Momy ban zan miki haka ba”

“To waya aikata? Da zan fita waye na bari a bangaren? Waya shigo ya dauka?”

Hawaye ya fara mata zuba.

“Ban sani ba Wallahi amman ban dauka ba, ban taba sata ba Momy ko tsintuwa ban taba
yi ba, balle har na shiga dakinki na dauki kudi ko sarkar zinari, dan Allah karku
min haka, idan baku son zama na a gidan nan ku kure ni amman dan Allah karku laka
min abun da ban yi ba”

Namra ta ta yi saurin rika Hurriya dake kuka kamar zata narke.

“Momy da dai an zafafa bincike Hurriya bata taba daukar abu ba, kuma a jininmu babu
barawo”

“To waya dauka? Shekarata nawa da masu aikin nan balle har ace su suka yi”

“Haba Momy taya zaki shaidi bari ki bar na gida, Wallahi Hurriya ba zata dauka ba”

“Ke fice ki ba ni guri, ba ke da bakinki kika fada min Hurriya ta tambaye ki kudi
ba? Kuma su ma sai na saka an duba dakunansu ai sai an bincika ko'ina na gidan nan”

“Eh amman bana jin Hurriya zata aikata haka Wallahi, kuma wannan ai na dabam ne, a
maganar da na yi miki na ni na fi zaton ko zata siye anko ne ko wani abu dabam”

Momy ta watsawa Namra wata kalar harara da ke karantar da ita ranta yayi kololuwar
baci, ita kuma zata iya bata nata rai a take. Ganin haka ya saka Namra sauka ta
kira masu aikin, Momy na tsaye aka fara binciken dakin Hurriya tana ta kuka, sai da
aka daga komai aka bincike har kwalin da Adam ya kawo mata sai da aka bude ba aga
kudi ko sarka ba.

“Wato har da soyayya kike da wani a boye ko?”

“Aa aa aa sako ya kawo min, na je bangaren Hajiya na karbo kuma ban san zai aiko da
sakon ba”

Ta amsa daker tana kuka sosai.

“Oh to ke kika bar min kofar daki a bude kenan aka dauka min sata, ko kuma kika
sata”

“Na ga kofar a bude lokacin da na dawo kuma ban ga kowa a falon ba, amman Wallahi
ban dauka ba”
Still Momy bata yarda da ita ba saboda tana ganin ita ma ai talaka ce kuma
mabukaciya saboda halin da Amma take ciki, kuma gashi Appa ya daina kula da ita.

*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma
zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba,
na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba
tare da biya ba na barku da Allah...!*

Yadda Momy ta saka aka bincike dakin Hurriya haka ta saka aka bincike, dakunan masu
aikinta, a nan ma ba a samu sarka ba, ba a samu kudi ba. Daga nan kuma sai labari
ya canja Momy ta fara zargi ko Hajiya Kaltume ce ta aiko aka shigar mata daki
saboda ta aiko kiran Hurriya, a karfin hali da nuna isa irin na Momy ta aika da
masu aikinta kai tsaye a bangaren Hajiya Kaltume wai su bincike mata komai na
bangaren saboda an dauke mata sarkar zinari mai tsada da kudi mai kauri, a nan
Hajiya Kaltume ta fara nata masifar ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, ita
da Khairi, har Yasir abun be masa dadi ba ganin an lakawa mahaifiyarsa sata. All
this while kuma Hurriya na dakinta tana rusar kuka abun ya zame mata biyu ta rasa
gurin jin sanyi, domin ta san a yadda mahaifinsa ya tsane ta yanzu zai iya yarda ta
dauki kudin, gashi bata san yadda zata yi ta fidda kanta ba, secondly ga gift din
da Adam ya aiko mata ta san Khairi sai ta fadawa Appanta. Kuka take sosai kamar
ranta zai fita gaba daya ta gama fita daga hayyacinta tunani ma ta rasa wanne zata
yi.

9:30pm Appa ya aiko kiranta bayan kowa ya hallara a falonsa, cikin matukar tsoro da
firgici ta fito daga bangaren Momy tana tafiya kafafuwanta na yin kamar za su
zameta. Hankalinta be kara tashi ba sai da ta shiga falon ta ga kowa yana nan ciki
har da Yayanta da Hajiya Kaltume mai karawa miya gishiri, ga kuma Momy da ta
rumgume hannaye ta hakimce babu alamar sassauci a tare da ita, sanin kanta ne a
yanzu babu wanda zai wanketa domin babu mai kaunarta a gidan, kuma bata da tabbacin
za su shaideta, dan haka ta bi shawarar dake karya mata zuciya. Idonta yana a gurin
mahaifinta tana kallonsa zuciyarta na rawa kalaman da za su fito daga bakinsa kawai
take saurare. Sai da ta zauna kusa da Ruma sannan Appa ya dubeta duba na tsanaki ya
ce.

“Hurriya ina son ki fada min gaskiya, na san baki taba min karya ba, kin shiga
dakin Nafisa a lokacin da ta fita ko dakin Namra”

“App...”

Ta kasa karasa furta sunansa ma saboda kukan da ya ci karfinta, hawaye kam ko kai
waye sai ka tausaya mata yadda take zubar da su.

“Kin shiga”

“Ta girgiza kai”

Sai Hajiya Kaltume ta kada baki ta ce.

“Ai fa akwai iya kukan kamar yar drama, ba a dai taba sata a gidan nan ba sai
yanzu, kuma babu wanda yake bangaren nan sai ke, sai dai kuwa masu aiki, ko da yake
bari na rufe bakina ai ita wannan yar karuna ba a mata gwaninta, ni ma bata raga
min ba ni din ma da na fi karfin shekara biyu rabona da kofar falonta”

Momy ta dago tana harar Hajiya Kaltume ta ce.

“Kwarai kuwa, a gidan nan ba a shaidar kowa, domin kowa shegen kansa ne, rufin
asirin da Allah yayi min na san ai tsonewa wasu ido”
Hajiya Kaltume ta nunata da hannu.

“Ina arziki yake? Me kike da shi Nafisa? Babu abun da Allah ya baki wanda be bani
ba, zan iya siye abun da kike siye to miye zai saka ma na aika a dauko min wani abu
dakinki saboda gaki diyar Bill Gates ko?”

“Karya kike yi Wallahi, ki ce me nake da shi, ai ke kin san na fi karfinki sai gani
sai hange, ni ba irin Iyami ba ce, ahe”

Appa ya daka musu tsawa rai a bace.

“Miye haka wai? Na taraku a nan ne saboda ku fara sa'insa? Musamman ma ke Nafisa
kin fi kowa fitina a gidan nan, na fara gajiya da matsalalolinki”

“Allah ya raba ni da matsala, ka ga Matsala can”

Ta nuna Hajiya Kaltume sannan ta cigaba.

“Kuma daman ai dole ka ce ni ce mai fitina saboda ita wa'eh ta mallakeka baka ganin
kowa sai bakar kaza, daman idan ta shiga akurki bata barin kowa ya shiga, idan ka
gaji da matsalolina sai ka san yadda zaka yi da ni, amman ina mai tabbatar maka
zama daram dam dam dam, domin babu inda zan tafi na barwa wata makira yar kasan
wuta ta samin hannu a yaya”

Khairi ce ta yi karaf ta ce.

“Momy ba dai Hajiyarmu ce yar kasan wuta ba Wallahi sai idan ke”

Tana rufe baki Namra ta mayar mata da martanin.

“Ba dai Momy ba, sai dai ke Khairi yar shaye shaye kawai mai banzayen abokai”

Appa step on his feet ya sake daka musu tsawa sai da falon yayi tsif.

“Ku tashi gaba daya ku fice min daga falo, saboda kun raina ni, ku yi sa'insa a
gabana yaranku ma su yi ko? Toh wannan ya zama na karshe, kuma daga yau sai yau kar
wanda ya sake dorawa yata sata, ni na haifi Hurriya ko mahaifiyarta bata fini sanin
halinta ba, Hurriya ba zata yi sata ba, Nafisa ki tafi can ki nemi wanda ya shiga
dakinki ya dauki sarka da kudi, ki bincike masu aikinki amman Hurriya ba zata
aikata haka ba, duk abun da nake yi ma Hurriya ina mata ne ba dan bana kaunarta ba,
kuma haka ba yana nufin kowa ya kwaso shararsa ya watsa mata ba”

Ya kalli Hurriyya With Angry face.

“Hurriya tashi ki yi tafiyarki”

Hurriya bata san lokacin da wani sanyi ya ziyarci zuciyarta ba, hawayen da suka
banbanta da na dazun suka zubo mata. A nan kam ta samu courage din yin magana.

“Na gode Appa”

“Ba zata zauna a bangarena ba”

Momy ta fada cikin zafin rai da daga murya. Appa ya watsa mata harara.

“To sai ki hada komai na ki ki bar mata bangaren, domin duk wanda ke gidan nan yana
karkashin iko na ne”

Hurriya ta mike tsaye tana share hawayenta ta fice daga bangaren tana jin kamar an
watsa mata ruwan kankara a kunar da zuciyarta take mata.

_____________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

*HURIYYA*

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

1️⃣
5️⃣ 5️⃣
1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 5️⃣

“Sam Sam Sam ni hukuncin da Alhaji yayi a gidan nan be yi min ba”

Cewar Hajiya Kaltume da shigowarta falonta kenan. Khairi ta yi karaf ta ce.

“Ba ke kadai ba Hajiya, ni Wallahi na dauka ma korar Hurriya zai yi, domin zata iya
satar kudin nan”

Hajiya Kaltume ta zauna tana fadin.

“Ai ba nata ne ya ban mamaki ba, na Nafisa ne, yadda ta ci mutunci na ta dora min
sata ban ji ba ban gani ba, amman ace Alhaji ya kyaleta ba tare da yi mata wani
hukunci ba? Ni wane irin rashin godiyar Allah ne zai saka ni sata a bangarenta, ni
ban ma san ta fita bangaren ba, amman da yake ta raina ni haka ta laka min sata,
saboda bata da ta ido har da wani aiko masu aiki wai su zo duba mata bangarena,
haka fa matar ta taba dora min laifin fasa tayar bakinta, ta maida ni kamar wata
karamar yarinya”

“Wallahi Hajiya abun da Momy take yi a gidan yana wuce gona da iri, da zarar an
taba ta sai tace ita mai kudi ce, mu gaba daya ganinmu take kamar wasu awaki ita
kadai ce mutum”

Hajiya ta kara kashe ido domin laka mata sata da Momy ta yi da kuma kyalewar da
Appa yayi be yi komai ba ya fi komai bakanta mata rai.

“To wai waye zan tura ya shiga ya dauki kudin a bangarenta, idan ma ba wanda yake
bangaren ba waye zai san gurin da take aje kudinta, da sarka har a dauka, ko dai
masu aikinta ko kuma ita wannan mai siffar macizan ce”

“Ni fa zuciyata ta fi yarda ma ita ce, amman kin ga yadda ta wani sha jinin jikinta
sai kuka take ita munafuka, har Appa ya tausaya mata, wannan yarinyar da film take
da ta kwashi kudi dominbta iya acting”

“Bar shi ai sai na masa magana akan haka, dan yau yaushe za a shaideshi ne, har da
wani cewa wai duk abun da yake mata ba sonta ne ba shi ba, kin ji min wata maganar
banza”

Sai da Khairi ta kalli kofa domin tabbatar da babu wanda zai shigo sannan ta kalli
Hajiya Kaltume ta ce.

“Ya Yasir ma da wani ne sai yayi masa dukan mutuwa kamin ma a gane gaskiya, amman
kin ga da yake Hurriya ce uffan be ce ba, balle har ta kai ga ya doketa, ai Wallahi
Salma ta huta da tafi yin masters dinta a waje, Maama kuma ta yi aure babu mai shan
wahakarsa sai ni, daman ni ya tsaneni a gidan nan”

Hajiya Kaltume ta daga mata hannu.

“Ni yanzu ba ta Yasir nake ba, maganar nan ba zan bari ta wuce ba, ba a dora min
sata da kurciyata ba yanzu da yayana ba za a dora min sata na kyale ba, kuma
Wallahi sai na bawa Nafisa mamaki sai na maidata abar tausayi”

Khairy ta dan kalli wayarta da sakwannin ke appearing saman screen din wayarta, ta
dan bata fuska kadan da alamar damuwa sannan ta fara taba wayar tana reply kaminnta
mike tsaye ta nufi dakinta. Hajiya Kaltume kamar tashinta take jira sai ta tashi
ita ma ya nufi nata dakin ta dauki wayarta ta kira aminiyarta da bata iya boyewa
komai, sai dai ga mamakinta sai da wayar ta yanke har sau biyu ana uku Hajiya Fatee
ta amsa cikin wata murya dake bayyana damuwarta.

“Toh sawun giwa ya take na rakumi aka ce na kira na fada miki damuwata kuma na jiki
a cikin wata damuwar lafiya Hajiya Fatee”

“Ina lafiya anje gyaran kai an kare wuya, Hajiya Kaltume ina nan cikin matsalar
cikin nan, jiya da shekaranjiya ko bachi ban iya yi ba, na rasa madafa”

“Subhanallahi, baki sake kiran Malam ba? Ba na ce ki kira shi ba?”

“Na...”

Har zata yi subutar baki ta fada ma Hajiya Kaltume yadda suka yi da Malam sai kuma
ta tuna gargadin da yayi mata.

“Toh zan kira shi, ni tsoron kiransa nake kar ya fada min wani abun da zai daga
hankali na, domin na lura kamar akwai matsala”

“Aa ki kwantar da hankalinki Hajiya Fatee, kuma ki nuna masa damuwarki, kuma ki bi
duk wani abu da zai fada miki, na san ba zai wuce kudi ba, ko kuma ya ce sai kin
siya mishi wani abu, komai dai minene karki yarda cikin nan ya bayyana Hajiya Fatee
domin bayyanar cikin nan matsala ce da ko mun mutu sai mun bar abun fada, duk
tsanani karki yarda sirrinki ya bayyana”

Shiru Hajiya Fatee ta yi na dan lokaci kamin ta amsa.

“Toh Hajiya Kaltume, abun kunya ne kam sosai amman kuma idan ya fada min wani abun
da ba zan iya yi ba fa?”

“Kamar ya? Haba ta wajena karki karyar da zuciyarki mana karki yarda ta fada miki
akasin abin da na fada miki, yo Allah na tuna ko cewa yayi sai kin bashi kanki ko
kin bashi jini ko rabin dukiyarki ai kya aikata saboda rufin asirinmu”

Hajiya Fatee ta yi murmushin takaici mai sauti.

“Hajiya Kaltume ni yanzu me nake da shi? Wannan bakar matar da Fadeel ya auro ai
duk ta ga bayan komai nawa, duk wani boko ko malami da kika sani a garin nan babu
wanda be ci kudina ba, saboda wannan bakar yarinyar kuma kudi ba kadan suke karba
ba, amman babu biyan bukata ni na rasa gane wani irin abu ne wannan, shiyasa na
fara yakin yanzu da bakina”

“Waya san da me ta mallake miki da, ai wasu yayan dangin maguzawa ne Hajiya Fatee,
kuma su ma fa Malam nan sun iya tsibbo sosai, suka yi ma wasu ma balle yaransu,
zata iya yiyu mahaifinta ne ya tsaya mata, kuma yayi mata wani abun da za a lalata
duk wani shiri nake”

“Toh yanzu idan magani be yi ba, zan yi yaki da halshena, shiyasa na fada masa ya
zaba ko dai kara aure ko sakinta ko kuma na yafe shi har abada kuma Wallahi zan iya
saboda kura ta kai bango ba da ita da Iyami su suka ja mana shiga wahala, kara ma
Iyami tana san tana amsar nata hukuncin amman ita wannan sai kara samun gurin zama
take”

“Toh amman Hajiya wannan hukuncin be yi tsauri ba? Kina ganin zai iya aikata daya
daga ciki? Matar nan fa ba karamar mallaka ta yi masa ba”

“Dole ya zama ba, kuma zan fada masa Khairi nake son ya aura domin ita kadai zata
share min hawaye na”

Hajiya Kaltume ta yi murmushin jindadi.

“Da yardar Allah kuwa, daman duk cikin yayana babu mai halina irin Khairi ta fisu
fahimtar duniya ta san ciwon kanta sosai”

“Na lura da haka ai, sai dai kuma ki ja mata kunne ta jajirce gurin jan hankalinsa
sosai saboda ta dauke hankalinsa daga gurin wacan tun kamin ma ta shiga”

“Haka za'ayi, Allah dai ya hada kansu ya ba mu nasarar wannan aikin jihadi da zamu
yi”

“Ameen”

Daga haka suka yi sallama kowacce ta sauke waya da tunani na dabam, musamman ma
Hajiya Kaltume da take jin idan har Khairi ta auri Fadeel ta yi sa'a domin namiji
ne mai kyau ga hankali ga kudi ga iya kula da gidansa, musamman ma idan aka kure
matarsa yaransa kuma a maida su hannun uwarsu ko Hajiya Fatee gida ya zama na yarta
ita kadai.

“Matukar kika auri Fadeel Khairi kin yi dace, amman na lura ke ma kamar kina son
raba min hankali biyu toh ba zan dauka ba”

Magana take da kanta, ta sake daukar wayarta ta kira Malaminta ta fada masa abun da
ya faru har tana zargin ko aikinsu ya fara karyewa ne, sai ya bukaci ta bashi minti
goma zai sake kiranta, after ten minutes ya kira yana fada mata abun da ya faru.

“Daman na san ba zai karye ba, ai ba karamin aiki na yi ba, haba Hajiya duk bayan
sakamakon da kika min ga kudi ga Makka da kika kai ni, sai kuma na bari ki ji
kunya? Sam ai ba zan yarda ba, kawai dai abun yana dan fisgo masa ne, kin san fa ya
fi son yarinyar nan fiye da sauran yayansa domin na duba na ga haka a zuciyarsa
musamnan ma yanzu da abubuwan nan suke faruwa, kawai dai mun danne son ne a
zuciyarsa ba zai iya nunawa, kuma muka kawo tsana muka saka a tsakaninsu”

Hajiya Kaltume ta ji dadi sosai.

“Haka nake son ji, amman Malam ta bangaren Nafisa fa Malam, matar nan ta zame min
karfen kafa, na rasa ya zan yi da ita, amman maganar gaskiya tana jefani a damuwa
sosai, ka duba ka gani kirikiri an mata sata amman sai ni ta dorawa, kai ba dan
gidan nan ba ne ai sai na yi kararta”

“Karki damu, ita ma zamu maida hankali a gurinta, kuma zamu zafafa na Alhaji ta
yadda ba zai iya yanke shawarar komai ba, sai dake, kuma zan saka masa tsananin
tsoronki sannan mu cire Nafisar a zuciyarsa kamar yadda muka cire iyami”

“Haka nake so Malam, anjima kadan zaka ji sako mai nauyi”

Ya amsa da dariya.

“To Maa Shaa Allahu, sai dai kuma ina son na fada miki ki maida hankali gurin
Hurriya, domin yanzu haka da na duba matsalalolin gidan na duba na duba na kasa
ganin komai ta bangarenta”

“Kamar ya Malam?”

“Idan na je gurin bincikenta sai wani haske ya zo ya tare yadda ba zan iya ganin
komai ba sai ma na yi saurin kawar da ido saboda kar ya illata ni, kuma na duba na
ga ko ta can bangaren mahaifiyarta ake mata wani abu ban ga sun mata komai ba, wata
kila wannan haske ne ma ya hana Mijinki hukunta ta, na rasa gane ko minene Wallahi”

“Toh Malam ko wani lakani ta samu kuma? Shiyasa ta fara sata? Zan saka a bincike
min dakinta tsab a duba ko'ina idan ma wani abun ne ta yi a dauke shi”

“Ba ita ta yi sata ba, a cikin masu aikinta ne wata ta dauka, wata yar guntuwa baka
mai jiki ita ta sata, kudin da sarkar suna nan bayan dakunansu ta boye a cikin
itacen fulawa”

Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Lallai Malam ka kai Malam wannan da kudi na ne sai kawai na je na dauko kuma na
kori mai aiki, amman ina.... Sai dai ma na yi addu'ar Allah ya kara bata sa'ar
daukar wasu”

Malam yayi dariya yana jinjina muguntar Kaltume.

“Hajiya na lura ke ma ba ƙyale ba ce”

“Malam mutane ai sai da haka, na gode sosai sai ka ga sakona”

“Toh shikenan Hajiya sai na jiki”

Ta sauke wayar da mamaki a ranta, me Hurriya ta yi? Gashi yarinya ce balle tace ta
fara shige shige kuma gashi Malam yace ba Iyami ce ta bata komai ba.
“Toh minene? Bari Khairy ta zo zan saka bincika min yarinyar nan, ni kam na san ba
a banza ba Alhaji ya wanke ta a gaban mutane”

Ya cije baki ta kashe ido tana motsa kafa.

HURRIYA POV.

Tana shiga dakinta ta kalli gabas ta fadi ta yi sujadar godiya ga Allah na abun da
Appa yayi mata a yau, domin ta gama katsewa ta dauka zai yarda ta aikata ne har ma
yayi mata hukunci, amman sai gashi yayi abun da ba ta zata ba a yanzu. Rumgume
hannayenta ta yi tana jin kamar ace Amma ko Appan Hamad suna kusa ya rumgume wani
saboda jindadi. Cikin kuzari ta tashi ta fara gyara dakinta da aka yamutsa tana
maida komai a yadda yake. Har ta zo kan box din da aka hargitsa da Adam ya kawo
mata, takardar ciki ta fara dauka ta warware tana dubawa.

_Hey Beautiful... How are you? You're doing good i guess. Na aiko miki da wannan
sakon ne just to say sorry for what happen at Mall na lura kamar baki ji dadin haka
ba, i promise you ba zai sake faruwa ba matukar baki so. And duk lokacin da zaki
gama karanta sakon nan ina nan waje harabar gidanku a cikin mota ba zan tafi ba ko
da kuwa ko wa zai zo ya ganni_

Ta yi saurin daga kai a lokacin da ta kai gabar da yake fadar haka, sai ta nufi
windows dinta gabanta na faduwa da sauri ta daga curtains din tana rike da takardar
ta bude window tana kallon Motocin Momy dake gurin bata ga wata bakuwar mota ba. Ta
sake maida idonta gurin takardar

_Oops... Sorry wasa nake miki na san yanzu gabanki yana nan yana faduwa, relax take
a deep breath_

Ta yi taking deep breaths din kamar yadda ya bukata tana daga kanta sama ta sauke.
Sannan ta sake maida idonta gurin takarsar mai kyalli da zanen heart.

_Na san kin je kin duba ko zaki ganki i fooling you_

Ta yi murmushi kadan..

_You're Smile_

Sai ta saka dariya mai sauti mai dadi.

_And you're laughing_

Ta daga kanta sama gaba daya tana dariya tare da mamakin yadda aka yi ya sani.

“Oh my God, ya aka yi ya sani?”

Ta duba karshen sakon.

_Daman muradina kenan ki yi murmushi, i just want you to be happy and healthy...
Have a nice Day, ki boye teddy nan da kyau and spray that perfume, till the bottle
cried out for help, and also the chocolate can't wait to be on your soft mouth_

_Adam_

“Adam”
Ta maimaita sunan kamar yadda ya ke rubuce a jikin kakardar sannan ta kalli white
teddy din dake kasa, ta kalli kwalin turare da chocolate dake kasa at the same
time. Gurin ta nufa ta zauna ta dauki chocolate din ta fara ci, sai gata tana
lumashe ido saboda dadinsa. Ta dauki turaren ta bude ta fesa kadan tana jin
kamshinsa. And his words keep rolling in her head wani be taba mata haka ba, ita da
bata ma taba tsayawa da wani da sunan hira ba. Kamar an jefo mata tsawa haka
gargadin Appa da yayanta ya dawo mata a rai da kuma maganar da aka fada akansa
cewar ba yaron kirki ba ne. Cikin sauri ta maida komai cikin box din ta rufe ta
saka shi karkashin gado.
*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma
zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba,
na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba
tare da biya ba na barku da Allah...!*

Bayan Sallah Isha'i tana kwamce dakinta, Namra ta turo kofar dakin ta shigo,
Hurriya ta tashi zaune da sauri tana jiran jin abun da zata karanta mata.

“Hurriya yau ba zaki ci abinci dare ba hala?”

Ta yi shiru ta sauke kanta kasa.

“Baki jin yunwa ne?”

“Ina ji i thought kun tsane ni ne”

Ta fada shagwabe, Namra ta yi murmushi ta karasa kusa da ita ta zauna.

“Why zamu tsane ki, ko da gaske ce kina sata Hurriya ke fa jinina ce dole haka zan
so ki, balle ma ba halinki ba ne daman ni ban yarda kin aikata ba, baki jidadin da
naji ba a lokacin da Appa ya wanke ki, ni nafi kyautata zaton masu aikin Momy ne
suka dauka ko kuma wasu daga cikin gidan nan, amman ke da ake fadar kin fi mu kyau
hali a gidan nan ai ba zan yarda kin aikata ba, besides Momy tace ba zata bari ga
Allah ba kin ga ko waye zai bayyana kansa, ki daina damuwa tashi muje mu ci abincin
dare”

Hurriya ta sauko ganin Namra ta mike tsaye suka fita tare, suka sauka kasa a plate
daya Namra ta saka musu tuwon semu da miyar yauki ta saka manshanu sosai, ta dauko
ruwa ta zauna a kasa.

“Sauko mu ci”

Hurriya ta tashi ta shiga Kitchen ta wanke hannunta ta fito ta zauna kusa da Namra,
a madadin ta ci abincin kai tsaye sai ta kwantar da kanta jikin Namra.

“Yaya Namra na gode, ke da Yayana kawai kuke so na a gidan nan”

Namra ta yi murmushi.

“Ba komai yar kanwata, ni wannan abun da ake cewa yan ubanci bana miki kallon haka,
ina kallonki ne kamar uwa daya uba daya muke, tashi ki ci abinci”

Ta tashi ta gyara zamanta sai dai kamin ta kai hannunta cikin abinci Khairy ta
shigo sanye da karamin mayafinta wayarta a hannunta, is like kamar an mata dole
haka ta tsaya bakin kofar falon babu ko sallama.

“Hurriya taso muje”

Hurriya ta kalleta.
“Ina?”

“Ki taso idan zaki taso Malama”

Namra ta daga kai ta kalli Khairy da duba na wulakancin.

“Ba zata tashi ba abinci zata ci”

“Okay sannu uwarta, bari naje na fadawa Yaya uwarta ta hanata zuwa, ita ma kuma ta
ce ba zata je ba”

Hurriya na jin kiran na Yayanta ta tashi tsaye da sauri zata nufi kofar.

“Dauko mayafinki Hajiya”

Ta juya ta dauko mayafin kamar yadda Khairy ta bukata, sannan ta bi bayanta suka
fice, at first ta yi zaton bangaren Hajiya Kaltume za su nufa sai kuma ta ga ta
nufi gate.

“Ba yaya kika ce yana kirana ba?”

“Yana waje”

Huriyya ta bi bayanta suka fita gate, close to gate din wata mota ce fake da ba ta
gidan ba. Gurin motar suka nufa ta bude ma Hurriya baya.

“Shiga”

“Amman wannan ba motar Yayana ba ce... ”

“Zaki shiga ko sai ya fito ya mareki? Ba shi ya ce mu jira shi a mota ba”

Hurriya ta shiga da sauri, Khairy ta rufe bayan sannan ta bude front seat ta shiga
ta zauna tana taba wayarta. After like five minutes aka bude motar ta Driver seat
aka shigo, tana leken fuskarsa yana juyo ya kalleta wa zata gani ba Adam ba.

“Thank you Khary”

“This should be the last time sa zaka cilasta min fitowa da yarinyar nan”

Ta fada a kufule. Hurriya ta kalleta fuska kamar zata fashe da kuka, murya kamar a
shagwabe ta ce.

“Amman yaya Khairy kin san me Appa yace ko kuma kin san Yayana zai yi fada idan ya
sani”

Adam yayi saurin tarar numfashinta.

“Ba dadewa zamu yi ba Hurriya, kawai ina son na ganki ne kuma na baki hakuri abun
da ya faru, and na aiko da box an baki?”

Khairy ta watsa masa wani kallo.

“Okay ni zan hana mata box din kenan?”

“Waya sani, tun da har kika iya bata ni a gurinta ai zaki iya hana ta ganin box
din”
“Ni ban bata ka ba”

“And why take min kallon mutumen banza? Ni ba iskanci ne ya kawo ni gurinta ba, ki
daina fada mata bad things about me, na ga ai natsantsiya ce not like you that's
why i like her”

With shock Khairy take kallonsa.

“Adam what's the meaning of all this?”

“Sonta nake yi, and I'm ready to prove it, i want to talk to her parents da duk
wani mai son hana alakata da ita tafiya I'm serious”

Khairy ta tsaya kallonsa for some seconds kamin ta dauke kai ta bude motar, Hurriya
ma ta bude motar zata fita.

“Fita zata yi idan kika fita, ki zauna sai na gama magana da ita”

Ya fada da kamar fada yana kallon Khairy da bata fita motar ba, jin haka ya saka ta
fasa fitar ta rufe motar, Hurriya kam bata tsaya ba ta fice ta tana ganin Adam ya
bude motar ta ranta a na kare ta shige gida da sauri, a fusace ya dawo motar ya
rufe Khairy da fada

“Kin ga abun da kike ja ko? Kin dauki tsanata kin sakawa yarinyar har guduna take”

“Toh wai kai Adam duk yan matan duniya ka rasa wa zaka so sai Hurriya? Yarinyar da
ko jami'a bata fara ba”

“Ba ruwanki”

Ya bude gurin da yake ajiyar kudi ya dauko rafar dubu daya ya mika mata

“Je ki gyara abun da kika bata ina son yarinyar nan ta so ni”

Khairy ta kalli kudin ta kalleshi, kamar ta yi magana sai kuma ta saka hannu ta
karba ta bude motar ta fita.

“Why Adam why...”

Ta fada cikin yanayin damuwa da gajiyawa tana tafiya ba tare da ta juyo ba.
_____________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

1️⃣
6⃣ 6⃣1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 6⃣

Sai da Hurriya ta shigo gidan sannan ta daina gudu, sai dai hango Hajiya Kaltume
tsaye a karamin gate din part dinta ya kara daga mata hankali sosai domin irin
tsayin da Hajiya ta yi ya nuna kamar ita take jira. Rage tafiyar da take ta yi
gabanta na faduwa tana ta sake sake domin ta san halin Hajiya Kaltume da ma Khairy
din za su iya wanke kansu ita su jefata a ruwa. Tana daf da shigewa bangaren Momy
Hajiya Kaltume ta yi kiranta da hannu, a lokacin ne tsoro ya kara cika zuciyar
Hurriya, haka dai ta daure ta karasa gurin da take tsaye.

“Hajiya gani”

“Ina kika fito?”

“Yaya Khairy na raka waje gurin Saurayinta”

Hajiya Kaltume ta yi fuskar mamaki.

“Saurayinta kuma? Waye?”

“Ban san shi ba ni ma”

“Okay. Je ki BQ din Nafisa ki kira min Kulu, kuma ban ce ki fadawa Nafisa ba,
sannan ki fada mata ta same ni bangarena magana ce mai muhimmanci ki kirata dabam
ki fada mata ba a cikin mutane ba”

“To Hajiya”

Ta mike tsaye tana jin sanyi a ranta, na rashin zafafa bincike ko binta da zagi da
Hajiya Kaltume bata yi a yau. Tana shiga gate din da nufi BQ din Momy har karamar
kofar bangaren masu aikin ta fara budewa ta shiga ciki, dukansu suna waje suna hira
har da dare dare.

“Mama Kulu ina wuninku”

Ta gaishesu, duk suka amsa mata har Kulu, sannan Hurriya ta ce.

“Mama Kulu wai ki zo”

“Ni”

Ta nuna kanta.

“Eh”

“In ji wa?”
Dayar dake zaune kusa da ita ta saka dariya.

“Ke ma dai da neman tsawaita zance kike, waye zai kiraki duk gidan nan ban da Momy?
Kuma tun da kika ga Hurriya a kin san ita take nemanki”

Hurriya dai bata ce komai ba ta juyo ta fara tafiya, a bakin kofar ta tsaya har sai
da Kulu ta fito sannan ta tare tace.

“Ba Momy ke nemanki ba, Hajiya”

“Hajiya kuma?”

She asked with shock.

“Eh nima na dawo daga waje na ganta tsaye tace na kiraki kuma kar na bari kowa ya
ji, ta ce ki same ta bangarenta magana ce mai muhimmanci”

“Toh... Allah yasa dai lafiya”

Hurriya dai ban da kallonta babu abun da ta yi, domin ita ma bata san dalilin kiran
ba balle ta fada mata ita kuma bata daina faduwar gaba ba har ta isa bangaren na
Hajiya Kaltume. Daman Hurriya tana isar mata da sako ta shiga bangaren Momy ta bar
a guri..

Cikin tsoro ta shiga falon da Momy tana sallama. Ruma ce kadai zaune a falon tana
cin abinci, hannu ta sauke ta aje plate a kasa bayan ta amsa sallamar Kulu, ita
kanta mamakin ganinta a bangaren take.

“Hajiya na ciki ta ce tana son ganin”

“Eh tana ciki bari na kirata”

Ta mike tsaye tana tsude hannu ta nufi stairs, slowly ta tura kofar dakin Hajiya ta
lake.

“Hajiya ga Kulu mai aikin Momy a kasa tana nemanki”

“Je ki ce mata ta shigo”

“Nan eh?”

“Eh”

Ta juya ta koma, tun kamin ta karasa saukowa ta fadawa Kulu sakon Hajiya Kaltume.

“Ta ce ki shigo”

“Na shigo kuma?”

Ruma ta daga mata kai, Kulu ta daga kai ta kalli stairs din da bata taba hawa ba,
tun zuwanta gidan, shigarta bangaren Hajiya Kaltume ma za a iya kidayashi domin
bata zuwa sai idan Momy ta aikota, kuma ba kasafai Momy take haka ba. Da tsoro Kulu
ta taka ta hau stairs sai ta rasa wane daki zata shiga domin duka dakunan a rufe
suke kuma bata taba kaiwa gun ba balle ta gane wanene dakin Hajiya Kaltume.
Kwatantawa ta yi da dakin Momy sai ta isa bakin kofar dakin ta yi sallama ta
kwankwasa.

“Shigo”
Ta murda kofar ta shiga idonta na bayyana tsoronta a fili domin bata san dalilin
kiran ba, gashi ance mata magana ce mao muhimmanci kuma har ba a son kowa ya ji.
Kusa da kofar ta tsaya ta rigina tana zuba gaisuwa.

“Hajiya ina wuni”

“Rufe kofar ki matso nan”

Ta juya ta kalli kofar sannan ta saka hannu biyu ta rufe ta, ta matsa kusa da
Hajiya ta zauna a kasa.

“In ce dai ba wani laifin na yi ba”

Hajiya Kaltume ta kalleta tana murmushi.

“Aa ba ki yi laifi ba for now, na ma kiraki ne na yaba miki, sai dai nan gaba ban
sani ba ko zaki yi laifin idan kika biyewa sherin zuciya”

“Hajiya kin saka ni a hudu me ya faru?”

Hajiya Kaltume ta gyara ta kalleta da kyau irin duban nan dake nuna babu alamar
wasa a zancenta.

“Ke kika dauki kudin da yake uwar dakinki Nafisa, da sarkokinta da kuma sarkar
Namra ko ba haka ba?”

Hausawa suka ce marar gaskiya ko a ruwa gumi yake. A take gumi ya karyowa Kulu ta
fara hadeye yawu tare da dora hannu akai tana zaro ido.

“Ni Kuma? Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un Allah Wallahi Hajiya... ”

Hajiya ta daga mata hannu.

“Ban ce ki rantse min ba, abun da na sani ne nake fada miki, kuma bana bukatar ki
jadadamin, idan kuma kin yi musu zan mu iya zuwa ni da ke da Nafisa da kowa ma na
gidan na nuna gurin da kika boye kudin, bayan dakunanku cikin itacen fulawa”

Jikin Kulu ya fara rawa irin rawar nan dake kara bayyana rashin gasjiyarta.

“Kin ga daga nan sai Alhaji ya koreki, daman kuma ita Nafisa na san ba zata kyaleki
ba sai ta hadaki da Police, baki ga aikinki ba ki ga kudin da kika sata, kuma ga
zubewar mutumci da zuwa gurin yan sanda”

“Hajiya ki rufa min asiri dan girman Allah ki yafe min, ki dubi girman Allah ki
rufa min asiri, Wallahi zan maida duk abun da na dauka, dole ce ta saka na sata,
shekarata nawa a gidan nan amman ban tana daukar ko akaifa ba balle kudi”

Ta karasa da kuka sosai ko'ina na jikinta yana rawa, ta dayan bangaren kuma tana
mamakin ta ina Hajiya ta san da wannan bayan bata fadawa kowa ba, kuma babu wanda
ya san gurin da ta binne kudin.

“Ban ce ki maida kudi ba, da ki maida kudi da karki maida kudi duk daya ne a
gurina, ni ina ma jinjina miki da kika aikata hakan, domin Nafisa ban da bakar rowa
da wulakanci bata aje komai ba, na kira ki a nan saboda na fada miki cewar na sani,
kuma na jidadi da baki wahalar da kanki gurin bayyana gaskiya ba, ni nan da kika
ganina har duniya ta nade ba zan taba fadawa kowa cewar ke kika saci kudin Nafisa
ba ko sarkarta”

“Hajiya ina kika ji wannan magana?”


“Da wa kika yi maganar?”

Ta daga hannayenta sama.

“Wallahi ban yi da kowa ba.. ”

“Karki damu da inda naji, ba wani ya fada min ba, abun da nake son ki damu da shi
ne, abun da zan fada miki yanzu”

Ta kara gyara zama tana hade yawu da karfi.

“Toh Hajiya”

“Daga yanzu ina son ki zama karkashin ikona ba ikon Nafisa ba, ita kike yi ma aiki
amman ni nake da iko dake, ina son ki saka min ido sosai akan uwar dakinki, kuma
nan gaba duk abun da na ce ki aikata zaki aikata shi”

“An gama Hajiya Wallahi an gama.. Komai kike so shi za'ayi”

“Yayi kyau, ke kuma asirinki zai yi ta rufuwa har ki mutu, kuma zan cigaba da
biyanki bayan biyan da Nafisa take miki”

“Hajiya ni ba sai kin ba ni komai ba, kawai dai ki rufa min asiri idan kika min
haka kin biya ni”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi ta dauke fuskarta ta dauki wayarta tana latsawa, haka
ta kyale Kulu a gurin tana ta share gumi har na kusan minti biyar sannan ta kalleta
ta ce.

“Wake share dakin Hurriya?”

“Ni ce Hajiya ni nake sharewa na yi mopping ko'ina na saka turare”

“Yayi kyau da ba ke ba ce zan ce ki karba ki share saboda, aikin da nake son ki


fara min a yanzu shi ne, ki shiga dakin Hurriya ki bincike min komai na dakinki
idan kika ga wata laya ko wani kullin magani ko wani abun na dabam ki dauko min
shi”

“Toh Hajiya amman sai gobe, saboda dare ne yanzu, kuma Momy bata son kowa ya shiga
bangarenta idan tana nan”

“Ni ma ban ce ki yi yanzu ba, amman dai ki tabbatar kin samo wani abu karki zo min
hannu sake, domin ni na san akwai abu a dakin shiyasa na ce miki ki dauko, kamar
yadda na san ke kika yi sata kuma na san gurin da kika boye kudin”

“Toh Hajiya, Wallahi zan yi”

“Shi ke nan tashi ki tafi”

“To na gode Hajiya na gode Allah ya saka da alheri Allah ya rufa mana asiri, Allah
ya kareki daga duk shari”

Hajiya Kaltume bata ji zata iya amsa addu'ar ba dan haka bata amsa ba, sai kawai ta
daga mata hannu. Kulu ta tashi ta fice rike da zanen da ya kwance kuma ta kasa
daurawa sai rike shi da ta yi a jikinta ta sauka haka. Hajiya Kaltume bata sake
fitowa dakin ba sai da ta auna lokacin da ya kamata ace Khairy ta dawo cikin gidan
sannan ta fito dakinta ta nufi dakin Khairy, sai ta same ta kwance ruf da ciki
bandir din 1k a gafenta wayarta ma a gafenta aje. Sai da Hajiya ta gama kallon
komai sannan ta zauna kusa da ita ta kai hannu ta taba ta

“Ke Lafiya kike?”

Khairy ta bude ido.

“Lafiya kalau”

“Waye ya zo gurinki?”

“Waya fada miki wani ya zo gurina?”

“Na ga Hurriya na tambaye ta ina ta fito tace min ke ta raka gurin saurayinki, waye
wannan?”

Khairy bata son jin magana dan haka ta ce.

“Baki san shi ba”

“Hakan yayi, danan bana son saninsa, domin bana son ganin kowa a tare da ke sai
Fadeel”

Da far'a Hajiya Kaltume ta fadi haka tana kai hannu ta shafa bayan yarta irin na
uwa mai alfahari. Sai a lokacin Khairy ta zabura ta tashi zaune ta kalli Hajiya
Kaltume.

“Wane Fadeel kuma Hajiya?”

“Fadeel dai, dan wajen Hahiya Fatee yayanki”

Khairy ta lumshe ido ta bude alamar gajiyawa.

“Hajiya ina tunanin na nuna miki tun ranar da kika min maganar nan cewar Fadeel
baya a cikin tsarina, namiji mai mata da yara uku me zan yi da shi?”
*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma
zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba,
na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba
tare da biya ba na barku da Allah...!*
Hajiya Kaltume ta juyo da kyau ta fuskance ta tana kokarin lurar da ita duniya.

“Irinsu ai sun fi rikon aure, balle kuma shi da muka san halinsa ciki da waje? Baki
ga yadda yake zaune da matarsa ba? Sannan yayansa ai ba ke zaki rika su ba ko da ya
rabu da matar, sannan yaron nan yana da kyau ga kudi, irin sa mata suke rubibi fa
amman ke Allah ya kawo miki shi a arha”

“Ko duniya yake da ita, ni baya cikin tsarina bana sonsa, ina da wanda nake so...
Saurayi matashi be taba aure ba kuma shi ma mai kudi ne dan masu kudi da baya jin
zafin kashe naira”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi.

“Yaro yaro ne, ke Khairy ban da yarinta irin naki, har akwai saurayin da zai fi
Fadeel a garin nan? Ke dai ki bude idonki kuma ki ba zuciyarki hadin kai nan da nan
zaki ji kina sonsa, kuma ki duba ko amincin dake tsakanina da mahaifiyarsa”

A karo na biyu Khairy ta runtse ido ta bude da karfi, cikin ihu ta ce.

“Hajiya bana son Fadeel kuma ba zan so shi ba, baya cikin mazanjen da nake so, ni
ina da wanda nake so”
“Khairy lafiyarki kuwa? Ni kike yi ma magana da daga murya haka?”

“Toh Hajiya kina son cilasta ni auren wanda bana so, na fada miki bana ra'ayin
Fadeel, ba a auren dole yanzu”

Rai a bace Hajiya Kaltume ta mike tsaye tana nuna Khairy da wayarta a hannu

“Baki isa ba, shi da yake namiji be bijirewa mahaifiyarsa ba balle ke da kike mace,
kuma duk samarinki nan naki na banza ba, domin babu wanda ya nuna alamar da gaske
yake har kika gama karatunki, kowa na ganki da shi sai ki ce abokinki ne, sai yanzu
da na gabatar miki da wanda nake son ki aura mutumen kwarai wanda zai rike ki da
gaske sai ki gabatar min da wata maganar banza, to baki isa ba dole ne ki bi
zabina, ni na haife ki ba ke kika haife ni ba”

Fuuu Hajiya Kaltume ta fice daga dakin kamar walkiya rai a matukar bace. Khairy ta
fashe da kuka gaba daya Hajiya tana son rikita mata lissafi bayan wanda Adam yayi
mata. Kuka ta yi sosai sannan ta shiga bathroom dinta ta yi alwala ta fito ta
gabatar da sallah Isha'i tana gamawa ta nufi jakarta ta bude ta dauko kwayar magani
ta balla ta jefa a baki, sai da ta fara taunawa sannan ta kora da ruwan bandaki ta
hade ta hau gado ta kwanta.

Some weeks Later....

Hurriya tana zaune rike da kofin ruwa tana kallon MBC 4 Namra ta fito zauna kusa da
ita tana murmushi.

“Hurriya dan gidanki kullum sai yace na gaisheki, kuma ya ce yau zai shigo mu gaisa
saboda an ki gayyatarsa gurin gatsar tsire”

Hurriya ta dago ta kalleta da alamar tunani domin bata gane wa take nufi ba.

“Dan gidana kuma?”

“Yeah Ethiopian...”

“Oh... Hmmmm Yaya Namra ashe yau akwai daukar wanka?”

Namra ta harareta hana dariya.

“What do you mean?”

“Yaya Namra na ga taku ta zo daya fa, all my life a yanzu babu wanda nake son ganin
aurensa ko partner dinsa kamar ke da Yayana”

“Shi ke nan sai kuma aka ce miki wani abu ne tsakanina da shi?”

“Hmmmm ai yau idan ya zo fita zan yi na tsareku da ido har na gane komai”

“Okay ai tare zamu tafi, daman yace yau sai ya ga kanwata da nake ta masa rowa, but
bari na fada miki Gaskiya babu komai tsakaninmu fa, gaisawa kawai muke shikenan”

“Hmmm Yaya Namra i can read your eyes fa, shi ma alamunsa suna nuna akwai abu a
zuciyarsa fa”

Namra ta watsa ido da mamaki.


“Ke Hurriya yaushe kika zama haka? Wato ko kunyata baki ji kai tsaye kike fadar
haka”

Hurriya ta saka dariya sosai, sannan ta matsa kusa da Namra.

“Yaya Namra maganar Allah mutumen be miki ba?”

Namra ta yi shiru tana murmushi.

“Yaya, amman ba abun da kike tunani ne ba”

“Zai zama abun da nake tunani soon Yaya Namra, daga ganinshi mutumen kirki ne dan
Allah idan ya ce yana sonki karki ce aa”

Namra ta girgiza kai tana dariya ganin Hurriya ba zata barta da zancen ba, ta dauki
filo ta rumgume.

“Kyaji da shi ke dai”

Hurriya ta yi murmushi. Haka Hurriya ta saka mata ido har yamma tana lure da yadda
ta shirya turaren ma na musamman ta saka ta feshe jikinta ta ko'ina kamshi take.
Ana gama Sallah Magariba before Isha'i Namra ta sauko tana sanye da wata Egyptian
Abaya ko ina kyalli take gashi ta sha kamshi kamar wata amarya. Kusan wannan ne
karon farko da wani ya ziyarci gidansu da sunan ganinta kuma shi ba dan
makarantarsu ba kuma ba dan'uwanta ba. Har ta fita sai kuma ta dawo ta shiga dakin
Hurriya dake kwance tana karatun Qur'ane.

“Hurriya ta so mu je”

Hurriya ta juyo ta kalleta.

“Ya zo”

Namra ta daga mata kai tana murmushi fuskarta har annuri take. Hurriya ta aje
kur'anen ta dauko ta nufi Hijab dinta ta dauka ta saka.

“Amman Yaya Namra ki fadawa Momy? Kar ta fito nemanki ko nemana ba mu kusa”

“Ban fada mata ba, dadina dake akwai zurfin tunani, bari na fada mata sai na sameki
kasa”

“Okay”

Ta juya ta fita daga dakin ta nufi dakin Momy, daga bakin kofar dakin ta tsaya ta
fada mata tana da bako a waje zata je su gaisa, a take Momy ta yanke wayar da take
fuskarta ta cika da annuri.

“Maa Shaa Allah, haka nake son ji a gaishe shi”

Ta yi murmushi ta yi baya ta ja mata kofar, kasa ta sauko ta samu Hurriya tsaye


tana jiranta. Hannunta ta kama suka fita tare. Sai da Namra ta yi ta rabon ido
kamin ta hango shi tsaye can gurin gate din gidan.

“Laa har can ya faka?”

Hurriya ta fada tana ganin kamar ya tsananta ma kansa fakawa a nesa da apartment
din Momy. Tun kamin su karaso ya bude motar ya fito, farar shadda ce a jikinsa da
hula shi ma sai kamshi yake zubawa irin na manyan samarin nan dake gasar nuna ado a
gurin yan matansu. Haka nan Namra ta samu kanta da kunyar kallonsa har suka karasa
gurin.

“Salam”

“Salam...”

Ya amsa musu yana kallon Hurriya da murmushi a fuskarsa.

“finally yau dai an fito min da kanwar nan da ake ta min rowa”

Namra da Hurriya suka yi dariya kusan lokaci daya.

“Ba rowarta nake maka ba, kai ne baka bukaci gaisawa da ita ba”

“To ai tsoro nake ji, kar ki ce min na karya doka kuma kin san mai nema taka
tsantsan yake”

“Haka ne”

Hurriya ta kalleshi ta ce.

“Barka da dare”

“Hey Young Lady”

“Lafiya Kalau”

“Maa Shaa Allah, yau dai na ce zan zo na dubaki, even though dai aiki yana min yawa
amman Yayanki tana min rowarki kullum idan ina cewa ina gaisheki bata ce min kina
amsawa sai dai tace min zaki ji kina ji kuwa”

Hurriya ta yi dariya tana kallon Namra dake girgiza kai tana murmushi kawai yadda
yake da son ban dariya abun yana burgeta.

“Tana fada min, kuma ina amsawa”

“Good”

Ya fada still yana kallonta. Namra ta kalleshi kadan ta ce

“Ka shigo ciki”

“No nan ma ya isa, kawai dai ki kawo min kujera na zauna”

Hurriya ta wara hannunta

“Bari naje na dauko...”

“No bari na dauko”

Kamin Hurriya ta sake cewa komai ta juya ta nufi cikin gidan. Hurriya ta juya zata
bi bayanta sai ya kirata.

“Ina zaki je?”

“Zan taya ta daukowa ne”

“Hmmm baki son yayarki ta wahala kenan, ni kuwa na saba bata wahala kullum saboda
sai na ce ina gaisheki”
Hurriya ta yi murmushi ta bi bayan Namra, a tare suka dauko kujerun biyu ta nufi
bangaren da Motar Momy take suka aje a gurin, yana ganin haka ya san baya bukatar
ace masa ya karaso ya zauna, dan haka ya cira kafarsa ya gurin ya zauna a kujerar
da Hurriya ya aje. Namra kuma ta zauna a dayar, sannan Hurriya ta koma ciki ta
dauko musu ruwa da cups ta aje a gabansu.

“Ke ina taki kujerar?”

Hurriya na kallon Namra sai suka yi ma juna murmushi saboda tunawa da ta yi da


cewar ta fada cewar zata tsaresu da ido har sai ta gano komai.

“Tana falo tana jirana, a sha ruwa lafiya”

Ta bar shi a gurin ta wuce, sai ya bita da ido har sai da ta kauce daga ganinsa
sannan ya juya ya kalli Namra.

“Kanwarki nan tana da kirki, kuma tana da kyau ba zan yi karya ba”

“Yeah haka ake yawan fada duk ta fimu kyau, kuma maganar gaskiya ta fi mu kirki,
Hurriya tana da kirki sosai”

“Maa Shaa Allahu haka ake so, ina take karatu?”

“Tukuna nan dai bata fara jami'a ba”

“Why? Takardunta ba su fito ba ne?”

“Sun fito kuma sun yi kyau domin tana da kokari sosai, akwai abun da Appanmu yake
jira ne shiyasa be saka ta ba”

“Ko aure za'ayi mata?”

Ta yi dariya.

“Mu ma da muka gama jami'a muke maganar zuwa NYSC ba a yi mana aure ba balle ita,
ita ce karama a gidanmu yanzu”

“Oh... Na tambaya da tsoro fa, i thought answer ki would be yes”

Ta yi murmushi mai alamar tambaya.

“She's too shy bata son tsayawa ma, tana son saka glasses kuma yana mata kyau”

“That's because of her illness bata gani sai da gilashi”

“Whoo..what... Wow...”

Ya juya ya kalli part din Momy kamar zai ganta tsaye a gurin.

“Wow...”

“Wow... ”

He said for the third time.

“You make me like her more.. Gaskiya duk wanda ya samu yarinyar nan ya dace, and i
think I'm the luckiest guy”
Namra ta kalleshi tana murmushi da ya zame mata kamar na dole ne.

“Hmmm”

“The true is i like your Sister so much Namra, kuma na zo nan ne saboda na yi
magana da ita, amman na ga tana da kunya sosai ko tsoron mutane take ne i don't
know”

Namra ta sauke idonta kasa zuciyarta ta fara bugawa da mugun karfi, but she
managing to wear her light smile on her face. Ya mike tsaye ya nufi gurin motarsa
sai ta bishi da kallo har ya isa ya bude ya dauko abun da zai dauko ya kamo hanyar
dawowa. Sai da ya kusa isowa sannan ta share hawayenta, not because of tana sonshi
but because of disappointed, all her life ta dauka ita yake so ba Hurriya ba, yawan
tambayarta Hurriya da yake ba saka ta kawo a ranta son Hurriya yake ba. A gurin da
ya da ya tashi ya zauna ya mika mata ledar farko kamin ya mika mata ta biyu

“This one is for you, wannan kuma na Young Lady ne, last time i asked for her
contact kika ce bata da waya, so na saka mata waya a ciki, ban sani ba ko za a
barta ta yi amfani da ita, idan ma ba a barta ba, ba ki iya amfani da ita, ni dai
abun da kawai nake bukata ta fahimci me yake tafe da ni, kuma ta tsaya ta
saurareni, ta nan zamu fahimci juna da ita kamin iyaye su shigo ciki, idan Allah
yayi, amman kna son ta san cewa ba da wasa nake ba, so ina ganin ke zaki min wannan
kokari ki fahimtar da ita”

Ta amsa mishi da kai sannan ta mike tsaye rike da ledodin ta fara tafiya.

“Sai da safe...?”

Ya fada. Sai ta mayar masa ba tare da ta juyo ta kalleshi.

“Sai da safe”

Tun da ta saka gaba bata juyo ba har ta shige falon Momy. Tsaye ta yi da ledodin a
falo not knowing what to say or do, Hurriya dake kokarin mikewa tsaye ta amsawa
Momy dake fadawa Appanta yana nemanta a bangaren Hajiya Kaltume, ta kalleta ta yi
murmushi irin murmushin nan na zolaya.

Namra ta kasa mayar mata da murmushi kuma ta kasa barin kofar falon da take tsaye,
Momy ma dake tsaye stairs kallonta take kamar mai karantarta. Hurriya dake sanye da
Hijab dinta ta nufi kofar falon ta bude ta fita ba damar ta tambayi yayarta me ke
faruwa saboda Momy tana stairs tana kallonsu. Sai da ta fita daga bangaren Momy
sannan hankalinta ya koma gurin kiran da Appa yake mata, tana ta tunanin laifin me
ta yi?

“Hurriya...”

Ta juyo ta sauri ta kalli bakuwar motar dake fake kusa da motocin da suke bangaren
Hajiya Kaltume.

“Na'am”

Ta amsa ba dan ta fa mai kiranta ba, sai Khairy da ta gani tsaye ta daure fuska ta
rumgume hannayenta kamar an mata dole ta tsaya a gurin. Fadeel ya bude motar ya
fito ya tsaya kusa da Khairy, Hurriya a ganinsa ta matsa ta gaisheshi.

“Barka da dare”

“Sannu Hurriya, ya kike?”


“Lafiya Kalau”

“Dan samo min ruwa ciki na sha”

Ta kalli Khairy kamar ta ce wani abu sai kuma ta ji ba zata iya ba, ta juya ta nufi
bangaren Hajiya Kaltume ta shiga, babu kowa falon dan haka ta wuce Kitchen kai
tsaye ta dauko ruwa da cup ta dawo ta mika masa da hannu biyu. Ruwa ya fara karba
ya bude sannan ya ta rika masa cup din ya zuba ruwan ya ya mika mata da dayan
hannunta ya karbi ruwan ya sha ya mika mata Empty cup.

‘Dama ace... Ke ce..., da raina ba zai ba ce ba, kuma zuciya ba zata ki yarda ba’

A ransa yake maganar yana binta da kallo bayan ta isa kofar falon surukarsa Hajiya
Kaltume. A dinning ta aje cup din da bottle water ta nufi upstairs gabanta na
faduwa domin yanzu ta san abu ne mai wahala Appa ya kirata akan wani abun alheri
balle kuma a bangaren Hajiya Kaltume, waya sani ko wani sherin suka kulla mata.
Cikin tsoro da fargaba ta tura kofar dakin ta shiga.
After Hurriya ta wuce, Fadeel ya sauke ajiyar zuciya ya kalli Khairy dake tsaye
kamar an sassaka itace ya ce

“Ni zan koma”

“Toh a gaishe da gida”

Ta fara tafiya sai ya tsayar da ita, ya bude Motarsa ya dauko leda ya mika mata.

“Thank You”

Ta furta sannan ta wuce ta yi gaba, shi kuma ya shuga motarsa ya zauna, har sai da
ta shige ciki sannan ya yi ma motar key ya juya. Har ya isa gidan Hajiya Fatee be
daina tunanin yadda za'ayi su yi rayuwa haka da Khairy ba tun a waje balle kuma ace
ya aureta, tun ba yau ba ya lura ita ma bata ra'ayinsa kamar yadda baya ra'ayinta.
Domin wannan ne zuwa na biyar da yayi a gurinta idan suka gaisa baya sake cewa
komai ko da ya gwada ma sai ya ji baya iyawa ita ma kuma bata cewa kuma bata
sakewa, haka za su yi ta zama kamar wasu hotuna. Be kashe motar ba ya fita domin ba
dadewa yake son yi a gidan ba so kawai yake yayi magana da Hajiyarsa. One step
forward a falon Hajiya Fatee yayi arba da bako da ya fito daga dakinta sanye da
shadda ruwan kasa, kana ganinsa ka ga bakauye, and instead of ya karasa fitowar sai
ya juya da sauri ya koma cikin dakin na Hajiya. Fadeel yayi tsaye a falon yana
kallon kofar dakinta with curious face, sai ga Hajiya Fatee ta fito tana ganin
Fadeel ne ta saki fuska.

“Ashe ma Fadeel ne, yaya Malam fito ai danka ne”

Fadeel dai kallonta kawai yake.

“Waye wannan?”

“Kawuka ne na kauye, zauna sai ya fito ku gaisawa, yau ya zo nan zai kwana yanzu
haka ma zancenka muke sai gashi ka zo, Yaya Malam fito mana ku gaisa da Fadeel”

Fadeel ya zauna yana kallon kofar dakin da Yaya Malam ya ki fitowa.

_____________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

1️⃣
7⃣ 7⃣1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 7⃣

“Be taba zuwa nan ba sai yau, kakaninmu ne guda da shi, amman su a nijar suke, sai
bana Allah ya kawo shi”

Hajiya Fatee ta fada tana ta yan kama kame. Fadeel ya motsa hannunsa sai kuma ya
mike tsaye ba tare da tunanin komai a ransa ba ya ce.

“Maybe da safe zamu gaisa, ni ma gida zanje yanzu, daman na fito gurin Khairy ne na
biyo nan saboda akwai maganar da na so mu yi, amman zamu yi da safe”

Hajiya Fatee ta kalleshi tana murmushi.

“Okay Allah ya maka albarka”

“Sai da safe Hajiya”

“Allah tashemu lafiya”

Ya nufi kofar fita ta bude ya fice, sai da Hajiya ta leka ta ga motarsa ta bar
gurin sannan ta tashi a fusace ta shiga dakinta.

“Haba Malam haba na fada maka kwana gidan nan ba zai yiyu ba, ka ce dole sai an yi
haka saboda Aljanin da dare zai zo, kuma na fada maka karka fita daga dakin nan
idan kana neman wani abu ka fada min zan dauko maka, saboda gudun irin haka, kullum
dana sai ya zo da safe ko dare ya gaishe ni, yanzu ba dan yana da zuciya mai kyau
ba ai sai ya wani tunanin ya zo masa”

Malam yayi yar dariya mai cike da tsoro abun ka da bakauye.

“Hajiya ban san cewa danki zai zo ba, ni ma kawai na so na fita na dan zagaya ta
can baya ne akwai abubuwan da zan karanta saboda kiran rauhanai”

“Kuma ina ta kiranka ka fito mu gaisa baka fito ba, bayan na masa karyar cewa kai
dan'uwana ne”

“Akwai dalilin da ya saka, amman karki damu danki ai wata rana zai ganin har sai ya
gaji da gani na”

Kallon rashin fahimta ta yi masa.

“Kamar ya? Ai bana fatar haka, Malam bayan wannan za su sake neman wani abu ne?”

“Aa ba za su sake neman komai ba, yanzu din ma, ai shegen kwadayi ne da son mata
irin na manyan aljannu, kin san yadda farar mace take da daukar ido ko tsohuwa ce
balle ke da ba za ace kin yi shekarunki ba, shiyasa kullum ake fada muku ku rika
rufe jikinku amman baku ji”

Ta sauke ajiyar zuciya, ranta bakikirin kamar an mata bushara da mutuwa.

“Abubuwan sun yi yawa Malam, bana fatan sake aikata komai bayan wannan, tun bayan
rabuwata da miji wani abu be sake shiga tsakanina da kowa ba, sai da kaddara nan ta
fada min yara kanana suka ci mutunci, duk shi ne silar wannan bakincikin”

“Karki damu Hajiya, daman tuntuna saboda kin dauki lokaci ne da tuni ma an wuce
gurin, gashi har cikin ya kara satika, amman har yanzu ba mu makara ba. Amman
Hajiya na yi miki wata tambaya mana, miye sa ba zaki yi aure ba, wato a lokacin da
ina zurfafa bincike a kanki sai na hango maza da yawa da suke kaunarki, kina da
wannan kwarjin na hallita”

A kaikaice ta kalleshi kallon da ya fi kama da harara.

“Miya kawo wannan maganar Malam? Ina ruwanka da rayuwata ko aurena? Samun gurin har
ya kai haka?”

“Karki manta dai da Malam kike magana, kuma ina son na fada miki babu mai iya miki
irin aikin da zan miki duk garin nan, ki ga aiki kamar yankan wuka, ai kin yi ta
sake sake shi ya dauke ki lokaci, da kika ga babu mafita ne kika kirana kika ce kin
amince, ina bibiyar duk wanda nake yi ma aiki, ina ganin duk halin da suke ciki”

Ta rufe zancen da rufe kwalbar turare mai tsananin karfi, irin mai hawan kanka ya
tashi mai aljannu. Hajiya Fatee ta mike tsaye daga kan gadonta da take zaune ta
kalli Malam dake zaune a kasa ta ce.

“Malam ina ganin kamata yayi ka koma dakin baki dake waje, idan dare ya kara yi zan
zo da kaina, daman saboda gudun dana ko masu aikin gidan su ganka ne, kuma yanzu na
samu mafitar hakan tun da har na yi ma dana karyar kai dan'uwana ne”

“Hajiya ai duk yadda kika ce haka za'ayi, rufin asirin na ki ne ba nawa ba”

Ya mike tsaye.

“Sai ki min jagora zuwa dakin bakin, ni ma hankalina zai fi kwanciya da haka”

Komawa ta yi ta zauna yayinda yake tsaye yana jiran ta wuce gaba ta nuna masa
dakin, sai ta dafe kanta tana jin kamar ta fashe da kuka, abun duniya duk ua
isheta, idan tace zata bar cikin,tonuwar asirinta ne gashi har ya fara tasowa dan
lokacin data dauka bata mayar masa da amsar ta aminci ko akasin haka ba.
HURRIYA POV.

Kallo daya ta yi ma Appa ta san ba lafiya ba, domin fuskarsa a hade take kamar be
taba dariya ba.

“Appa barka da dare”

Appa ya duba duban dake kara bayyana bacin ransa.

“Karata kika kao Hurriya?”

Ta nuna kamta.

“Ni...”

Hajiya Kaltume ta yi karaf ta ce.

“Aa ba ke ba shi.. Tun da kin raina mutane”

Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume da sauri domin kalamanta suna kara rudata ne kawai.

“Tafiya kike gida gida kina fadar na ki na saka ki makaranta?”

Ta fiddo ido kamar za su fasa gilashin dake fuskarta su fito.

“Ni Appa Wallahi ban yi haka ba, ya za'ayi na yi haka?”

“Toh waya je ya fada? Da Magariba nan Alhaji Garba ya same ni da zancen yana neman
izini yana son ya nema miki makaranta, na gaza ne Hurriya?”

Tana jin Alhaji Garba ta san makocinsu ne kuma mahaifin kawarta Husna. A take
idonta ya cika da kwalla.

“Wallahi Appa, ban ce ka gaza ba, ban fada mata cewar ka ce ba zaka saka ni
makaranta ba, ni ban yi magana da Babanta ko mamanta ba, Appa Wallahi ban kai
kararka gurin kowa ba”

Appa ya zaburo mata kamar zai kai mata duka.

“Idan baki fada ta ina suka ji cewar baki zuwa makaranta? Har zai same ni da zancen
wai yana son ya sakaki makaranta baya bukatar sisina umarni kawai yake so, idan ba
kin je ki fadi wani abun ba ta ina zai sameni da wannan maganar? Dukan sauran yaran
babu wanda yayi wannan sai ke Hurriya?”

Hajiya Kaltume ta tabe baki.

“Ai ita dai Hurriya kamar tafiyar Iyami take jira, duk ta bi ta lalace abubuwa take
marasa kan gado, Allah ya tsaremu karki kwaso mana abun magana nan gaba”

Cikin kuka Hurriya ta girgiza kai.

“Appa ka ce ka san halina, ba zan aikata maka irin wannan ba, ni dai na san na yi
hira da Husna kawai akan karatuna, kuma ban ce mata ka kasa sakani makaranta ba,
Wallahi Appa ban fada ba”

“Kullum ana fada min abubuwan da kike yi Hurriya, yaron nan ma da na rabaki da shi
baki ji ba, an fada min har kyauta yake kawo miki, kuma yana zuwa kina fita hira da
shi, yanzu kuma abun ya fara tsallakawa makota, to sai ki tashi ki tafi can gidan
kawar ta ki ya hada ke da ita ya rike, makaranta kuma ba zan saka ki ba, ke da
karatu har abada, sai dai ki ganina gurin wasu, sannan ban yarda kowa ya saka ki,
sai na gani idan da karfi zaki yi karatu, babu wanda zai saka ki makaranta da yawun
bakina, idan ke zaki saka kanki Bismillahi”

Hurriya ta tashi da sauri ta isa har gurin da Appa yake zaune ta rike kafarsa tana
kuka.

“Appa ba ni da gata a duniyar nan sai Allah sai kai, na karbi laifina dan Allah ka
yi hakuri”

“O tooo kin aikata kenan, daman na san kin yi ai, domin babu wanda zai fitar da
sirrin gidan nan sai ke, kullum kina can gurin wannan Husnar ana zagina da yayana
ana fadar cin amanarki matan ubanki suke, Momy ma da take rike dake bata tsira ba,
balle kuma ni da kika maida abokiyar gabarki, ban da rashin hankali da tunani irin
naki ta ina zaki zauna kina zagin ubanki da kawarki har mahaifinta yayi tsaurin ido
ya tinkari Alhaji da wannan maganar”

Hajiya Kaltume ta fada, Hurriya ta girgiza kai da sauri, amman ta kasa magana.
Kalamanta sai suka kara tunzara Appa ransa ya kara baci.

“Na fada miki, ki hada komai baki ki koma can gidansu ki zauna”

Hajiya Kaltume ta daga masa hannu.

“aa Alhaji ba za'ayi haka ba, ai sai ka kasa su kara zaginka kuma, mu ma kuma ace
muna gani aka koreta, daman dai ta bata maka suna a unguwar nan, kai ne dai baka
sani ba saboda sai yau Alhaji Garba ya same ka da wannan maganar, amman zance kala
kala ni na ji, Nafisa ma ta ji, kawai dai muna shakkar fada maka ne saboda baka
yarda da komai aka fada maka na Hurriya, duk da haka dai ba zan ce ka koreta ba
domin bata gidan da ya fi wannan”

Hurriya ta kalleta tana kuka.

“Haba Hajiya ki ji tsoron Allah ki rika fadar gaskiya, bana zuwa ko'ina sai gidansu
Husna ita ma ba kullum ba, Wallahi ban taba zaunawa wani guri na zagi Appana ba...”

Hajiya Kaltume ta rufe baki.

“Laa ke ni da nake miki yaki saboda kar ya koreki, shi ne zaki dubi idona ki ce na
ji tsoron Allah na fadi gaskiya, to da can tsoronki nake ji ne? Alhaji ka ji min
wata magana?”

Appa ya mike tsaye yana kokarin fisge kafarsa, domin ransa a matukar bace yake,
Hurriya kuma ta kara rike kafar har sai da ya dago fuskarta ya dauketa da mari.

“Ba zaki sake min kafa ba, ki tafi can gurin wanda kika dauka ubanki ki zauna a
gidansa, kuma daga yau sai yau ban yafe miki ba idan kika sake furta wata kalma
marar dadi akan Hajiya”

“Ba zan saka bakina ba, kar ki rufe ni da duka”

Hurriya ta fashe da sabon kuka mai tsuma zuciya ta kwanta a gurin tana ta bawa Appa
hakuri amman be saurare ba ya yayi ficewarsa.

“Toh sai ki tashi ki koma gidansu kawar taki da kuke munafurcin tare, daman Allah
kadai ya san zagin da kuka min, uwarta ma ai yar gidan Iyami ce kin ga zata fi
jindadin rike ki”

Hurriya ta dago ta hade hannayenta.


“Dan Allah ki yi hakuri, ki bawa Appa hakuri Wallahi ban kai kararku ko'ina ba,
kuma ban zauna na zageku da kowa ba”

“Yanzu dai ki tashi ga kofa can ki fice min daga daki, kuma idan ba kina son fushin
Appanki ya karu ba ne zai fi miki kyau ki bar gidan, idan ma gurin kawar zaki koma
sai ki koma, idan kuma kina son kara janyowa kanki wata matsalar ne ga fili ga
doki”

Ta karasa tana nuna mata kofa. Hurriya ta mike tsaye ta fice daga dakin tana kuka
sosai, downstairs ta sauko ta a nan ta hadu da Khairy dake zaune ta hade rai.

“Yaya Khairy dan Allah ki bawa Appa hakuri, dan Allah Wallahi ban kai kararsa
ko'ina ba”

Khairy ta fisge hannunta.

“Wannan ya zama karon na karshe da Fadeel zai ce ki dauko masa wani ki dauko, banza
mai zubin karuwai ko wane namiji sai kin san yadda kika yi kika ja hankalinsa
gareki”

Ta tashi daga gurin ta nufi hanyar stairs, Hurriya ta bita da kallo hawaye dake
mata zuba suna kokarin katsewa, ita kuma yanzu kishi take da ita ko minene? Beside
ita da uwarta su suka shirya mata duk wani kulle kulle a gidan. Juyawa ta yi ta
fuskanci kofa ta fara takawa har ta fice, bangarensu Namra ta nufa, ko da ta shiga
falon babu hawaye a idonta dan haka babu mai sanin ta yi kuka sai idan an kalli
idonta da kyau. Ba tare da ta tsaya kula da kowa na falon ba ta nufi stairs sai
Momy ta kirata.

“Hurriya”

Ta juyo sai dai bata daga kai ta kalleta ba.

“Me yasa kika kai karar bakinga gurin mahaifinsu Husna?”

“Ko da na fada be zama lallai ku yarda ba, amman ni ban kai karar Appa ba, ban san
dalilin mahaifinta na samun Appa da maganar karatuna ba”

“Allah kyauta, iya baki dai yana da kyau muma Allah kadai ya san irin zagin da zaki
jan mana”

Hurriya ta juya ta ta cigaba da tafiyarta, sai da ta isa bakin kofar dakinta sannan
hawaye suka zubo mata. Ta murda kofar ta bude ta shiga, sai ta samu kanta tsaye
tana fuskantar madubin dake gabanta, wata macen mai kama da ita take gani, mai
tsananin rauni da damuwa, cikin zuciyarta take hangowa mai cike da kunci da
bakinciki. Takawa ta yi kamar mai koyon tatata ta isa gaban madubin dake dakin tana
kallon Innocent face dinta.

“Rarrashi nake so, babu mai yi min, gata nake nema na rasa shi ta ko'ina, rayuwa a
gidan da babu uwa akwai wahala ko da tana raye, farinciki neman gagarata yake yi,
me na tare musu ne? Wane laifi na aikata wa kowa yake ta tsanata? Dan wannan abun
har ya kai Appa ya koreni? Kuma babu wanda zai bashi hakuri?”

Magana take da kanta tana kallon kyakkyawar fuskarta dake zube a jikin madubin.

‘Ba komai yake bukatar kuka ba Hurriya, wani abun jajircewa yake bukata, ki
karfafawa kanki guiwa, ki goyi bayan kanki, sannan kuma ki saurari zuciyarki, idan
babu mai kaunarki ki kaunaci kanki, nuna musu zaki iya karki yi kasa a guiwa, wata
rana ke uwa ce, irin wannan matsalolin ke zaki magancewa yayanki...’
Wani ne ya kamata ace ya tsaya a gafenta ya fada mata wannan, akasin haka zuciyarta
ce ke karanta mata karantun da a yanzu ta shirya daukarsa, domin a yanzu ne idonta
ya bude zuciyarta kuma take kokarin waraka da rauni. Hannu ta saka ta share
hawayenta na dama zuwa hagu, sannan ta yi murmushi ta juya cikin kuzari ta fara
hada kayanta. Abubuwan da ta san zata fi bukata ta hada a luggage ta ta dauki
Qur'anenta ta fito daga dakin, ta fara saukowa a hankali sai da ta sauko falo
sannan ta kalli Momy ta ce.

“Momy zan tafi?”

“Ina?”

Momy ta duba ta da mamaki.

“Ina?”

“Appa ya ce na bar masa gidansa”

“Saboda wannan abun?”

Hurriya ta yi shiru bata ce komai ba. Momy ta tashi tsaye.

“Ina zuwa, ki bar gidan ki tafi ina?”

Ta nufi hanyar da zata sadata da bangaren Appa, kamin ta karasa Hurriya ta ce.

“Momy ko kin tafi ba zai hakura ba, ransa ya bace sosai”

Momy ta juyo.

“Daman na san za a rina, yadda Kaltume ta kori uwarki wata rana sai ta koreki a
gidan nan, ke ma kuma baki jin magana tun da kin san halin mahaifinki a yanzu ai ya
kamata ki kiyaye, miye na zuwa ki yi tseguminsa da kawarki har magana ta dawo
kunnensa”

Hurriya ta sauke kanta kasa, ita kanta bata san yadda zata warware wannan abun ba,
balle kuma su da suke kallonta a munafuka. Namra ta sauko rike da leda ta mikawa
Hurriya dake tsaye.

“Gashi Ethiopian ya ce a baki”

Hurriya ta kalleta, tana tsammanin zata taya ta jimamin korar da Appa yayi mata ko
ta tausayawa mata amman bata ga alamar ko daya a fuskarta ba.

“Ki rike na bar miki”

Ta juya ta ja Luggage dinta ta cigaba da tafiyarta, sai da ta fice daga bangaren na


Momy sannan ta ci hawaye ya cika idonta duk yadda ta so ta hana su zubowa abun sai
ya gagareta, domin bata iko da hawayenta a yanzu hasalima su suke da iko da ita.
Har ta isa gate masu gadin suka bude mata suna tambayarta lafiya, bata hararo
babban dalilin Appa na korarta a gidan ba. Idan ma mahaifin Husna ya same shi da
zancen, be kamata ya koreta saboda wannan ba. Tana tafiya tana karfafawa kanta
guiwa hawaye na zubo mata, har ta isa babban titin dake sokoto gusau road, a gurin
ta tari napep ta hau zuciyarta bata raya mata zuwa ko'ina ba sai gidan kakarta mai
kaunarta Hajiya Binta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

1️⃣
8⃣ 8⃣1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 8⃣

Hajiya Binta dake aikin dama shuwaka ta dago ya kalli Hurriya wanda shigowarta
kenan da kaya niki niki.

“Subhanallahi Hurriya lafiya”

“Appa ya koreni Hajiya”

“Kora? Kora fa kika ce Hurriya”

Ta daga kai idonta na zubar da hawayen da bata son zubarsu, sai dai kuma bata isa
ta hana su zuba ba.

“Me kika masa?”

“Kawata ce ta yi”

“Kuma a gidan aka rasa wanda zai yi wani abu har kika fito?”

“Hajiya Mai Napep yana waje yana jira”

Hajiya ta sauke ajiyar zuciya.

“Shiga dakins ki dauko kudi a jaka ki ba shi”

Hurriya ta nufi dakin, bata dade ba ta fito rike da one thousand ta fice ta sallami
mai Napep din sannan ta dawo ta zauna kusa da Hajiya Binta.
“Hajiya yanzu kowa baya so na gidan nan, ban san me na yi ba, kowa ya tsane ni”

Hajiya Binta ta bude robar gishi ta diba kadan ta zuba a cikin shuwakar data dama
ta dauka ta sha sannan ta kalli Hurriya ta ce.

“Nasara ce take tare da ke jikata, duk gurin da kika ga tsanani yayi yawa, to wani
alherin ne babba zai taho, wata kila nan gaba sai kin zama wata abar kwatance a
cikin familynku, duk sai kin fi su daukaka da nasarar rayuwa Hurriya karki ji komai
a ranki, kar wannan abun ya dame ki”

A lokacin ne wani kukan shagwaba ya rufe Hurriya ta tabe baki tana kallon kakarta
abar kaunarta.

“Hajiya ai yace ba zan yi karatu ba, wai ba da yawun bakinsa ba”

“Idan yana takamar haihuwarki yayi shi ma ai haihuwarsa aka yi! Kuma wanda ya haife
shi yana raye, kina can ma nake miki yaki balle kin dawo gurina? Ba dan yana gidan
mahaifinki ba ai da sai na ce haka ya fi, daman na yi nayi ya bar min ku na rike ke
da Hamad ya ki, yanzu kuma kin ga ya koreki da kansa”

Hurriya ta kwanta jikin Hajiya tana zuba shagwaba kamar ba ita ba.

“Cewa yayi wai na tafi gidansu baban kawata na zauna saboda ...”

Hajiya Binta ta girgiza kai cike da takaicin bayan ta gama sauraren dalilin korar
da aka yi ma Hurriya.

“Kin yi tunani da baki tafi gidan Iyami a wannan yanayin ba, sai abun ya kara mata
yawa a zuciya, idan ma zaki fada mata sai ki ce mata ni na dawo da ke nan gurina”

“Shiyasa na taho nan ai”

“Kim kyauta daman ina neman abokiyar zama, shi kuma Allah ya warware masa duk wani
abu da yake cikin kansa, gaba daya an juye masa hankali ya canja kamar ba shi ba,
gidan nan ma sai ya dauki wata uku biyu be zo ba, kiran waya kuma sai idan na kira
shi, babu ruwansa da kowa sai Kaltume, gaba daya ta dauke masa hankali sai abun da
tace yake yi”

“Kuma ni ban ce Babanta yayi masa magana ba fa Hajiya, ni ban yadda aka yi ma
Babanta ya ji ba”

“Wata kila tana tausaya miki ne, sai ta aika hakan da kyakkyawar niya, shi kuma ya
kasa fahimtar abun, daman kowaye zai ji haushi amman be kamata idonsa ya rufe har
haka ba, maraicinki ya kamata ya duba, yanzu da baki da ni ko baki da uwa a raye
sai dai ki koma wani gurin rabe gurin yan'uwa ko kuma wadanda baki hada komai da su
ba?”

Ta kara gyara kwanciyarta jikin Hajiya.

“Allah ma yasa ina da ke”

Hajiya Binta ta yi murmushin dake kara bayyana tsufanta, ta shafa kan Hurriya.

“Kar Allah ya raba mu har sai na damkaki ga miji mai amana Hurriya”

“Ameen”

Ta amsa tare da rufe idonta tana dariya.


“Ja'irar yarinya wato har da cewa Amin ko?”

Ta saka dariya sosai sannan ta tashi ta dauke kayan ta shiga da su dakin Hajiya.

“Aa daki dabam zamu yi, wake zama da kishiya daki daya”

“Dole ne ki yi hakuri da ni Hajiya daki daya zamu zauna”

“Toh aje kayan ki fito ki ci abinci, na san cikin nan naki yana nan dauke da yunwa”

Kusa da gadon Hajiya Binta Hurriya ta aje luggage dinta sannan ta cire hijab dinta
ta jefa saman gado ta juyo ta fito.

“Hajiya me aka dafa miki?”

“Zai wuce tuwo ne Hurriya kin san abincin tsufi ai ba kamar ku ba, idan ma baki son
tuwon ki shiga Kitchen ki dafa indomie”

“Toh”

Ta amsa sannan ta nufi hanyar Kitchen din, tun da ta shiga bata fito ba har sai da
Indomie dinta ta dahu ta zuba a plate ta dauko ta fito. Aje plate dinta yayi daidai
da shigowar Yasir falon hankalinsa a tashe yana ganinta ya dafa zuciyarsa ya nemi
guri ya zauna.

“Kin daga mana hankali, na je gidan Amma baki can, na dawo gidansu Husna aka ce
baki zo ba, na dauka wani gurin kika tafi”

“Allah yasa dai baka dagawa Iyami hankali ba, domin ba su san abun da ya faru ba”

“No naje gurin ne in a code way, ban fada musu abun da ya faru ba”

“Dadina da kai ai akwai hankali, ka kyauta”

Hurriya ta dube shi.

“Yaya ina wuni?”

“lafiya kalau shi ne kika kama hanya kika taho a madadin ki kirani”

“Yaya ko na kiraka Appa ba zai saurara ba saboda ransa ya bace sosai, kuma ba ni da
wayar da zan kiraka ma”

“Duk gidan nan ki rasa wayar da zaki dauka ki kirani?”

Hajiya Binta ta shiga tsakani ganin kamar Yasir yana neman mada abun fitina.

“Aa ba haka ba ne, ita kanta bata cikin hayyacinta a lokacin da ta baro gidan
saboda tashin hankali, ta ina zata tsaya neman wayarka ma, kuma kana jin tana fadar
cewar yayi fushi ba zai saurara ba”

“Tsohuwa kokari kareta kawai kike yi, amman da ta kira ni ai ba zata baro gidan
ba, yanzu da wani abun ya sameta fa”

“Laifin waye ba na mahaifinka ba? Akan me zai korota a dare yace ta tafi ta bar
masa gida kamar wadda ta yi cikin shege”

“Ita ma tana da laifi ai, Hajiya ta fada min duk abun da ya faru ba zai yiyu ka
zauna ka yi ta fadawa kawa karya da gaskiya ba, gashi yanzu har mahaifinta ta dauko
kafa ya zo ma Appa da wani zancen banza”

Hajiya ta tabe baki.

“Uwarka kuma dai ai ba zata fada maka gaskiya ba, karya da gaskiya zata hada ta
fada maka saboda ka yarda da ita ta karyarta Hurriya ka san sai ba son Hurriya suke
ba”

“Haba Hajiya wace irin magana ce wannan? Wannan ai hadin fada ne, sai ki hada
Hurriya da Hajiya ta dauka ko gaske ne”

“Yasir kai ma kasani da Khairiyyah ce ko Salma ko Rumana aka kora a gidan nan kana
ganin Kaltume zata yarda ta fito a dare kamar wannan?”

“Sai da na yi mata magana tace min ita ma bata san fitar Hurriya ba”

Hajiya ta tabe baki, Hurriya kuma tana cin indomie ziri ziri. Yasir ya mike tsaye
ko da ace Hajiya Kaltume karya ta fada masa ba zai so ya zauna a gurin da ake zagin
mahaifiytarsa ba, domin komai lalacewarta mahaifiyarsa ce.

“Alhamdulillah tun da tana nan, ni zan tafi idan Appa ya huce sai na dawo na
dauketa”

“Toh a gaishe da gida”

Hajiya Binta ta fada tana raka shi da kallo, Hurriya ma ta dago kai ta kalleshi.

“Yaya sai da safe”

“Sai da safe”

Ya amsa ba tare da ya juyo ba.

“Ina zata fada maka gaskiya, wannan Kaltume ba baki na yi mata ba, amman da wahala
ta gama lafiya”

Hajiya ta fada bayan ya fice. Hurriya dai bata ce komai ba, ta cire hannunta daga
taliyar tana kallon wani gafen na dabam, zuciyarta na raya mata yayanta ma yayi
fushi da ita a yanzu.

WASHE GARI....

_Barka da safiya Namra, fatar kin tashi lafiya ya su Mama da Daddy, And my
beautiful Young Lady, hope kowa yana kalau, a mika min gaisuwa gurin gimbiyar
please_

Ta aje wayar a hankali bayan ta gama karanta sakon ta manhajar whatsapp dinta, sai
ta nufi windows dinta ta bude curtains din tana kallon kasan bene zuciyarta na
gabato mata da wani abu na rashin dadi da bata san dalilinsa ba.
Me yasa zata ji haka, shi ne abun da ya fara zuwa mata a rai, daman ai be ce yana
sonta ba balle har tace ya koma gurin kanwarta ne. But at first alamunsa sun nuna
ni yake so. Wata zuciyar ta fada mata. Ta kai hannunta tana taba karamar sarkar
dake wuyanta.
Yana yawan tambayar Hurriya, amman ban yi zaton ita yake so ba, ko kuma dai ya juya
kanta ne saboda ya ga ta fini kyau. Sai kuma ta juyo tana kallon dakin kamar wani
bakonta sai sake sake take a ranta, wai it's normal ya so Hurriya domin be furta
mata so kai tsaye ba, but why take jin babu dadi so disappointed? It's because of
ta fara sabawa da shi kwana biyu, the way he approached her gashi da saka nishadi
da iya kula da aika ko kuma saboda tana tsamanin ita zai ce yana so.

Ta bar jikin windows din ta nufi gurin da ta aje ledar da ya kawo ma Hurriya ta
bude ledar ta ciro waya tana dubawa irin wyar Momy ce sak daga kala har model. Ta
sake saka hannu cikin ledar ta ciro Perfume set masu kamshi sosai. Sai da ta shaka
turare sannan ya maida komai yadda yake, ta nufi wayarta ta dauka. Ta rubuta masa.
_Bata karbi komai ba, na yi try bata karba ba, tace na aje maka_

After ta yi sending sakon sai kuma ta ga kamar be dace ta yi haka ba, but me zata
yi? Ta karba da sunan Hurriya ta karba, yayi ta jiran kiran Hurriya ya ga shiru, ai
kara ta fada masa gaskiya, ta jefar da wayar a kan gado tsakanin faduwar wayar da
shigowar kiran Salim ba za a iya fadar wanda ya riga wani ba. Hannu ta kai ta dauka
ta danna picking

“Are you free mu yi magana?”

Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta amsa masa.

“Eh ina jinka”

“Me yasa bata karba ba?”

Ta daga kafadunta kamar ance nata yana tsaye gabanta yana kallonta.

“Ban sani ba, maybe she's not interested, kuma bata shirya ma hakan ba, domin wani
be taba nuna yana som Hurriya ba, so ina tunanin ba abu ne mai sauki ta karbi abun
ba, saboda tana da banbanci da mu, tana ganin abubuwan differently”

“Amman da kika fada mata ya kika ga reaction dinta?”

“Not good... Not Bad...”

“How do you think zan iya shawo kanta”

Ta taka zuwa gaba tana shafa goshinta.

“Ina ganin kamar ba a takurawa mutum akan soyayya she's 19yrs idan tana ra'ayinka
zata sani”

“Or Maybe i can talk to her by myself? Ya kika gani na fahimtar da ita abun da ke
zuciyata kuma na nuna mata ba da wasa na zo nan ba, ko kuma kina ganin sai mun fara
daukar permission gurin iyaye? Maybe ita ma zata fi yarda da ni”

Ta yi shiru kamar mai tunani.

“Karka yi saurin tafiya gurin iyaye, ka fara magana da ita ka ji ta bakinta, domin
Appanmu baya daukar komai da wasa”

“Okay zan yi haka, zan shigo yau da dare ko na zo yanzu”

Ya lumshe ido ta bude jin yadda yake rawar jiki.

“Da dare zai fi sirri, domin bata nan jiya ta koma gurin kakarmu da zama, zan
kwatanta maka gurin”

“Zan fi jin natsuwa idan muka tafi tare, and Kakarta ma zata fi daukar abun da
muhimmanci, idan kina ganin babu matsala zan fara zuwa na dauke ki sai mu tafi
tare”
Samun kanta ta yi ta saka bijirewa rokonsa, duk kuwa da zuciyarta ta raya mata
haka, domin tana son ta cire kanta ne daga duk wani abu da ya shafe shi a yanzu
saboda ya nuna ba ita yake ra'ayi ba.

“Shikenan Allah ya kaimu”

“Ameen thank you”

Ta sauke wayar tana kallon kiransa har sai da ya yanke sannan ta dauke fuskarta
tare da ajiyar zuciya. Bata kara raina kanta ba sai bayan Sallah Isha'i a lokacin
da ya kira wayarta ya sanar mata yana waje yana jiranta, sanin ba dan ita ya zo ba,
ya saka bata cilastawa kanta shafa ko da hoda ba, balle kuma ta canja tufafi ko
saka turare. Tun bayan wanda ta saka sa rana bata sake saka wani ba, mayafi kawai
ta dauka ta yafa a saman gowns din atamfar dake jikin sannan ta saka shoes din da
suka yi shige da atamfar. Sannan ta fito dakinta ta nufi dakin Momy, kamar jiya yau
ma waya ta same ta tana yi. Daga bakin kofar dakin ta tsaya rike da kofar

“Momy zan leka waje ina da bako?”

Wani kasaitaccen murmushi ya bayyana a fuskarsa Momy, ba tare da ya yanke kiran ba


ta ce.

“Haka nake so, na jiya ne ko wani dabam?”

“Shi ne na jiya”

“Yayi kyau, amman ki sake fuskar mana, ki yi far'a ba fuskar damuwa ba”

Ta amsawa Momy da kai, Momy ta kara mata da cewar.

“Make sure kuma wanda ya cancanta ne, kin san dai waye iyayenki”

Nan da kai ta amsa mata, sannan ta juya ta fice idonta na cika da hawaye a karo na
biyu. A jiya ta kwadaita ma Momy cewar gurinta aka zo, saboda zatonta ne, yanzu
kuma Momy ta sake zaton hakan a karon kanta. Har ta fito falon rike da wayarta a
hannu bata daina fadawa kanta ajinta ya wuce ta tsaya irin wannan tunanin da
damuwar akan namijin da ba shi ne autan maza ba, kuma ba ita ce a gabansa ba. A
kokarinsa na karramata ya fito daga motarsa ya zagaya ya bude mata front seat, tana
kusantar gurin da motar take buri na kusantota. Bude mata motar kawai da yayi kamin
ta karaso wani abu ne da ba a taba yi mata ba, and to her wani abu ne dake bayyana
halinsa na kula da mace yadda ya kamata.

“Barka da dare”

Kamar wanda ta fado daga wata duniyar haka ta farko daga duniyar tunaninta ta dan
kalleshi and a lokacin ne ta fahimci ta karaso kusa da shi.

“Barka dai”

Ta amsa a takaice fuska ba yabo ba fallasa sannan ta shiga motar ta zauna, shi kuma
ya rufe murfin motar gently, sannan ya zagaya ga shiga bangarensa, ya kalleta bayan
ya rufe bangarensa yana tunanin ko zata masa wani karin bayani ko shawar before su
tafi.

“Za mu oya tafiya?”

‘Da gaske umarni na yake jira? Wai duk wannan na miye ne? Meye haka? Why why?’
Ta tambayi kanta, a zahiri kuma sai ta amsa masa ba tare da ta yarda ta kalleshi
ba.

“Yea...”

Yayi baya da motar tare da juya kanta sannan suka fice daga gidan.

HURRIYA POV.

Hurriya na kwance jikin Hajiya Binta tana game da keypad dinta, Hajiya ta ce.

“Wato da wani gurin kika fada shi ke nan babu wanda zai biyo bayanki ya binciki
lafiyarki, shi sun rufe masa ido su kuma babu wanda Allah yake ranta kowace daga
ita sai Yayanta take hange”

“Haka kwanan baya suka laka min sata, Momy ta ce na sace mata sarka da kudi, kuma
ban dauka ba, amman Hajiya ma cewa ta yi wai zan iya yi saboda na canja hali, Appa
ne kawai ya wanke ni, da Allah kadai ya san dukan da zan sha a gurin Yayana tun da
shi ne mai hukunta mutane, kuma da kowa sai ya rika kallo a matsayin barauniya”

Hajiya Binta ta daki kirjinta.

“Sata Hurriya? Sata dai sata? Ke Nafisa ta zarga da sata?”

Hurriya ta tashi zaune tare da amsa mata da kai.

“Har da cewa ta yi ba zata bari da Allah ba, amman ni dai har yanzu ban ji ance an
gane barawo ba”

“lallai rashin uwa a gida kukumi ne, saboda suna ganin baki da kowa shi ne suke
kwaso sharar sai ya sauke kanki, ai baki gadi sata ba Hurriya uwa da uba, yanzu da
uwarki bata da rai haka mutanen nan zasu rika ki? Ke ta ce kin satar mata?”

“Sakar zinari da kudi mai yawa, har da sarkar Yaya Namra kuma ban shiga dakin kowa
ba... ”

Ta fadawa Hajiya yadda komai ya faru, idon Hajiya Binta ya cika da kwalla.

“Ashe haka kike ta rayuwa cikin matsuwa a gidan nan? Duk fadin gidan nan da
ma'aikatan cikinsa a rasa waye za a zarga sai ke?”

“Ai Appa ya wanke ni yace ni ba barauniya ba ce”

“Me yasa baki fada min ba? Amman ko yanzu bata bace ba”

Hurriya ta kalleta da sauri.

“Hajiya ai ya wuce”

“Be wuce ba, uwarki bata min komai ba sai alheri, Allah ya mata albarka ya bata
lafiya, ta kula da ni kamar ni na haifeta, ba zan taba bari yayanta su wulakanta
ba, ba zancen sata kadai ba ko wannan korar da aka yi miki ba zan kyale ba, domin
idan aka kyalesu nan gaba za su aikata wanda ya fi wannan ma, gobe zan yafa
mayafina na tafi duk sai na ci musu mutunci”

Hurriya ta fasa kuka da yafi kama da shagwaba.


“Hajiya Wallahi zaki ja min ne kawai ace na zo na yi minahicci”

“Uwarki bata min komai ba sai alheri, matukar ina raye ita ko yayanta ba za su
wulakanta ba”

“Aa Hajiya ni dai dan Allah kar ki yi”

“Ba gidan zaki koma ba balle su ganki su wulakantaki, nan zaki zauna kuma yadda
wannan abun ya tsaya min a rai idan ba amayar da shi ba ba ni da kwanciyar hankali”

Duk yadda Hurriya ta so lallaba Hajiya Binta ta hakura da maganar, bata saureta ba.

“Ni da na sani ba zan fada miki ba Hajiya”

“Ai shi yake cutarki, ta nan kika sha banban da dan'uwanki, Hamad komai aka yi masa
sai ya rama kuma sai ya fada min, bawan Allah Allah ya masa rahma”

“Ameen”

Hurriya ta amsa cikin rashin ji dadi tare da daga kai ta kalli kofar falon da Namra
ta turo ta shigo da Sallama.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

1️⃣
9⃣ 9⃣1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞1️⃣ 9⃣

“Yau Namra ce a gidan na mu”


Hajiya ta fada tana kallonta, cikin karfin hali Namra ta yi murmushi ta nemi guri
ta zauna. This is the first time da ta ji bata sha'awar hada ido da Hurriya.

“Hajiya barka da dare”

“Barka, yau na ci arzikin Hurriya kin zo gidan nan kenan”

“Haba Hajiya daman can na kan zo na duba ki fa, karki ce saboda Hurriya na zo”

“To ssboda wa kika zo tsakaninki da Allah?”

“Sabosa Hurriya”

Cewar Namra tana dariya, Hurriya kuma dadi ya cika ranta jin cewar yar'uwarta ta
biyo sawunta, sai dai abun da bata sani ba shi ne ba tafiyace ta zuwa gurinta kai
tsaye ba tafiya ce ta Salim ba dan ita ba.

“Yaya Namra ina wuni”

“Lafiya Kalau Hurriya”

Ta amsa tana murmushin da ya fi kama da an mata dole.

“Ato ke dai kin kyauta da kika biyo sawu, daman ke kin fita dabam ba da yan'uwanki,
amman Nafisa kam da Kaltume rayuwarsu tana ba ni mamaki, yanzu Hurriya ta gama
karanta min abun da ya faru, ashe abun har ya kai a laka mata sata Namra?”

Namra ta kalli Hurriya ba tare da tace komai ba ta dauke ido.

“Ban yi zaton zamu yi ma yarinyar nan haka ba, saboda kawai bata da uwa cikin gida
sai ta zama abar wulakantawa, ban jidadi ba, yanzu ko korar nan da aka yi mata da
ke ce ko Khairy ai babu wanda uwarta zata yarda ta bar gidan, da bata da ni ya
rayuwa zata zame mata? Ke kuma ya kamata ace kuna nunawa iyayenku wasu abubuwa be
kamata su yi ba, wani abun ba za su lura ba sai an lurar da su”

Hurriya dai kanta na kasa tana jin kamar ta rufe bakin Hajiya Binta. A kokarin
Namra na kawar da maganar ta kalli Hurriya tana jin wani abu a zuciyarta game da
Hurriya ta ce.

“Da bako nake fa, kuma ke yake jira magana ya zo yi da ke?”

Hurriya ta dago ta kalleta. Hajiya kuma ta tambaya.

“Wane bako kuma?”

“Ita tasan wa nake nufi, ya zo ne yayi magana da ita sai mu tafi”

“Waye ne ban san waye ba?”

“Salim Sarauta... Yana waje”

Namra ta amsawa Hurriya kai tsaye kamar yadda ta bukata. Hajiya Binta kuma ta kalli
Hurriya ta ce.

“Saurayinki ne?”

“Aa Saurayin Yaya Namra ne, yana yawan tambaya ne, maybe ko yana son mu gaisa ne”

“To tashi ki tafi, idan kun gaisa sai ki dawo”


“Toh”

Ta amsa umarni, Hajiya ta tashi ta shiga dakin ta dauko hijabinta ta saka sannan ta
fito ta fice daga falon. Tana fita Hajiya Binta ta fara karantawa Namra sakon da
zata bawa Momy da Hajiya Kaltume. Cikin natsuwa Hurriya ta fita harabar gidan, sai
da ta gama kallon ko'ina sannan ta nufo gate domin bata ga bakuwar mota a gidan ba
bayan motocin da Appa ya ajewa Hajiyarsa guda biyu. Sai da ta fita gate din gaba
daya sannan ta yi arba da motar dake fake gefen gate din gidan, tun kamin ta fito
zuciyarta ta raya mata a waje ya aje motar ganin babu bakuwar mota a harabar gidan
Hajiya Binta. Kamin ta karaso ya bude motar ya fito yana taba wayar hannunsa, da
alama wani abun yake typing amman idonsa yana kanta har ta iso, cikin far'a da
sakin fuska ta yi masa sallama da muryarsa mai dadin sauraro.

“Wa'alaikissalam Young Lady”

“Sannu da zuwa barka da dare”

“Barka dai, fatar na same ki lafiya”

“Lafiya Kalau”

“Maa Shaa Allah”

Ya fada yana raba ido, ko za su samu gurin da za su zauna.

“Ko zamu iya rabawa daga can kar na aje ki yi ta tsayuwa, saboda ina da tarin
maganganu buhu buhu”

“Allah yasa ba laifi na yi ba, Yaya Namra tace min zamu gaisa ne”

“Laifi kika babba kuwa, kusa kisan kai ma”

Ta zaro ido hankalinta ya fara tashi.

“Ni...”

“Ke fa, amman yanzu mu fara zama tukuna”

“Nan ma ya isa ka fada min laifina ni hankalina har ya tashi”

Yadda take da kin sakin jiki zuciyarsa ta raya masa idan ya bukaci su shiga motar
su zauna ba zata yarda ba, ba kuma zai iya forcing dinta suje cikin gidan su zauna
ba. Dan haka ya bude mata mota ta gefen da yake ya matsa baya.

“Zauna nan, ni sai na tsaya zan yi magana da ke ne”

Bata son ta musa masa a karo na uku, haka kuma sanin cewar shi din masoyin Namra ne
yasa bata son ta aikata abun da zai fusata yar'uwarta. Juyawa ta yi ta kalli gate
din gidan. Kamar ya san abun da take sakawa a ranta kamin ta juyo ta tsinkaye shi
yana fadar.

“Karki damu, babu wanda zai fito har sai mun gama maganar da zamu yi”

“Ni fa zan iya tsayuwa ko na awa nawa ne”

“Shiyasa Namra ta kasa shawo min kanki, da alama dai kina da kafiya Hurriya kamar
zan sha wahala, please ki zauna zaki fi fahimtar magana ta idan kina zauna”
Ta taka ta zauna cikin motar kafafuwanta da fuskarta duka suna waje suna fuskar
gurin da Salim yake tsaye. Wayar dake hannunsa ya duba sai ya amsa kira da sauri.

“Ka iso?”

Ya juya bayansa.

“Oh na ganka”

Ya fada tana daga hannu ya tare fuskarsa daga haske motar dake haske fuskarsa.
Sauke wayar yayi ya saka aljihunsa.

“Ina zuwa Young Lady bari na mikawa wani, sako”

Ya zagaya da sauri dayan side din, hakan ya bawa motar mai tsananin haske haske
fuskar Hurriya har sai da ta saka hannu ta tare idonta da ba lafiyayyen ba. Gammm
ta ji an rufe mota sai dai ba zata iya fadar motar da aka rufe ba, ta Salim ce dake
neman sako kamar yadda ya fada mata ko kuma ta wanda za a bawa sakon ne? Ganin
Hasken dake hasketa ya dauke yasa ta janye hannunta daga idonta sai ta yi arba da
mutum tsaye a gabanta nesa kadan da gurin da Salim ya tsaya a dazun, kasansa ta
fara kallo har ta daga kanta sama ta kalli fuskarsa, akwai hasken wutar gidan dake
haska ko'ina ta bawa kowa damar ganin abun da yake wakana a harabar, sai dai hasken
be kai ya tantance mata fuskar waye tsaye a gabanta ba, saboda lafiyar idonta, sai
dai tabbas zata iya shaidar wani abu da ba zata kira da shi tsoro ba, kuma ba
fargaba ba ce, wani abu ne da ya cika idonta ya aikawa zuciyarta da sako ta fara
bugawa da karfi, a rashin zato da tsammani ta samu kanta a tsaye gabansa
numfashinta na kokarin sarkewa.

“Me kike yi a nan?”

Muryarta ta daki dodon kunnensa, a nan ta gane duk wani abu da ta ji gabanin fitar
sautin muryarsa shimfida ce.

“Ka santa ne?”

Salim ya tambaya yana rufe motar ta dayan bagaren sannan ya zagoyo.

“Ba nan ne gidansu ba, me take yi a nan?”

Ta daga kai da zimmar tantance waye tsaye a gabanta jin furta cewar ba nan ne
gidansu ba, wannan abun dai irin na dazun ya sake tare idonta daga kallon fuskarsa
idanuwanta suka shammaceta ta sauke su a fadaddan kirjinsa mai matukar fadi da
yalwatacce damtse, cikin wani yanayi da yafi kama da sihiri jikinta ya fara kyarma
kadan ta kasa tsayar da idanuwanta guri daya.

“Ba magana nake miki ba?”

Muryarsa bata yi kama da muryar da ta taba ji ba, idan ma ta taba to ta manta,


balle kuma fuskarsa da kwarjinsa be bari ta kalleta da kyau ba balle ta tantance
waye shi.

“Ni na sallamota magana zan yi da ita”

Salim ya fada yana kallon Saurayin dake gabansa da ba zai wuce sa'ansa ba.

“I said ba nan ne gidansu ba”

“Eh amman ta dawo nan a yadda na ji Namra ta fada?”


Mutumen ya kalleshi da kamar mamaki.

“Namra?”

“Ita ma ka santa kenan?”

“Cousin dita ce”

“Wow baka taba fada min ba”

“Dole ne sai na fada maka alakata da kowa? Ina tarkadun?”

“Shikenan kuma ka dawo ba zama lafiya, sai bakar magana kamar dan kishiya, ga su”

Ya mika masa takardun dake hannunsa.

“Tun da ka dawo ba mu samu zama ba, gashi ni kuma an min transfer”

Be ce da shi komai ba har ya gama duba takardun sannan ya juya. Salim ya bishi da
kallo yana fadin.

“Ajiyarka ta nan Captain, he's living healthy amman...”

Ya juyo da karfi ya kalleshi fuska babu annuri.

“Ban tambaye ka wani abu game da haka ba, idan ina bukatar sani wani abu game da
haka ni zan tuntuba watch your mouth Ethiopian...”

“Akwai maganar da nake son mu yi ne, akwai abun da ya kamata ka sani”

“Ba a nan ba”

Ya nuna gurin da ya tsansa, sai da ya kalli Hurriya sannan ya dauke idonsa ya juya
ya cigaba da tafiyarsa. Hurriya ta daga hannunta da sauri saboda haske motar da ya
dawo yana haska idonta, sai da ya ja motarsa ya bar gurin sannan Hurriya ta sauke
hannunta.

“Sorry na bata miki lokaci, wasu takardun ne na bashi na aikin mu”

Ita dai bata ce uffan ba sai mamakin inda ya santa take.

“Ashe ya sanki, he's very good friend of mine, yana da kirki sosai sai dai akwai
zuciya abu kadan ya bata masa rai, yana gaba da ni a aiki amman dai abokina ne
sosai”

Ta dauke idonta daga dayan gefen ta kalli kasa.

“Zauna please”

Ta girgiza masa kai alamar ba zata zauna ba, ga bakin nata yayi gum kamar an daure
mata shi. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali sannan ya ce.

“Okay, back to our business, Hurriya ina son ki saurare ni da kyau ne, na zo nan ne
saboda ina son mu fahimci juna da ke”

Ta kalleshi kai tsaye jin kamar yana kokarin kauce hanya.

“Fahimtar da nake nufi shi ne, ki fahimce manufata da abun da yake tafe da ni, na
san Namra ta yi magana da ke jiya, and ta fada min cewar baki karbi sakon da na
aiko miki ba, sai dai ban dauke shi a komai ba, maybe saboda baki gama sanina ba ne
ko kuma saboda ba wasu dokokin gidanku ne”

Ya gyara tsayuwarsa yana aika mata da kalamai cikin natsuwa.

“Hurriya ba na zo nan ne saboda na bata miki lokaci ko tarbiya ba, Allah ya san
abun da yake zuciyata son gaskiya nake miki babu wasa a ciki... ”

“So kuma...”

Ta amsa da karfi with confused.

“Eh na fara sonki ne tun a ranar da na fara ganinki, a Sarauta Mall, shiyasa na
biyo motar yayarki, kuma na gwada wasa da ku and...”

Ta daga masa hannu tana jin kamar kalaman sun mata girma.

“Wait... Yaya Namra fa?”

“Ban gane ba?”

A cikin rashin fahimta yayi tambayar ba tare da ya amsa mata nata tambayar ba.

“Yayata fa kake so take sonka, why are you here kana fada min magana haka?”

“Ni... Aa Wallahi ba Namra nake so ba, ke nake so ke na biyo ba ita ba, kawai na
lura da ke baki son magana ne ya saka na raba ta hannunta saboda na samu isowa
gareki, ita kanta ta san da wannan ai”

Hurriya ta girgiza kai.

“Bata sani ba, ni da ita mun gina fahimtar mu ne akan ita kake so ba ni ba, dan
Allah karka saka yar'uwata ta tsane ni, ita ce ta dace da kai ba ni ba, ita ce aka
shirya yi ma aure a yanzu ba ni ba, ni ce auta yanzu a gidanmu idan ka cire kane na
da baya nan, ina yayyu hudu mata, ban da maza uku ba za a tsallake su ayi min aure
ba”

Ya matsa kusa da ita da sauri.

“Zan jira Hurriya zan jira har zuwa lokacin da za'ayi miki aure...”

“Aa ni wani be ma taba cewa yana so na ba, ni ba aure ko soyayya ne a gabana ba,
akwai kalubalen da yawa da yake fuskatata su ya kamata na fara samun mafitarsu ba
soyayya ba I'm just 19yrs old”

“Yes but you're not a baby, wasu guraren ma wadda bata kai ki ba za a iya mata
aure, and zan jira ki Hurriya har zuwa lokacin da kika tashi ko iyayenki suka
tashi”

“Aa ka rushe duk wani gini na soyayyata da ka yi a zuciyarka, ka gina na yar'uwata


don't break her heart, Hurriya babu kowa yanzu a gabanta, bata taba son kowa ba,
kuma ba ta shirya son kowa ba, kai ba ma zata taba son kowa ba har abada... Sai an
jima”

Ta raba gefensa ta wuce ta bar shi a gurin tsaye speechless... Tana isa gate din ta
tura ta shiga, a yayinda Namra kuma ta fito falon Hajiya Binta ranta a bace har
wani halkalo take, a tsakiyar harabar gidan suka hadu da Hurriya, Hurriya ta tsaya
ita ma ta tsaya suka kalli juna, Hurriya ta dan yi murmushi kadan zata yi magana
Namra ta tari numfashinta.
“Zaki yi dariya mana, tun da kin zama munafuka munafurcin da kike yi a gidansu
Husna har yayi sanadin Appa ya koreki shi kika zo kina yi a nan ko? Kina son hada
Hajiya da Momy kuma kina son Hajiya ta yi fushi da Appa, kin kyauta idan halin da
kike yi abun kwarai ne ki cigaba, Hajiya ta fada min baki, ja, da yello na sakon da
zan fadawa Momy da Hajiya, kuma zan fada musu...”

Ta dauke kai ta nufi gate.. Mamaki da fargaba ya hana Hurriya cewa komai sai binta
da ta yi da kallo har ta fice. Tsaye Namra ta samu Salim a gurin da Hurriya ta bar
shi

“Lafiya?”

Ta tambaya ganin yanayin dake nuna kamar ba su rabu da dadi ba. Ya juyo ya kalleta

“Ba komai, zagaya ki shiga mu tafi”

Ya shiga side din da Hurriya ta zauna wanda shi ne side din mai tukin mota, Namra
kuma ta zagaya ta shiga front seat, tun da suka kama hanya bata ce masa komai ba,
shi ma kuma be ce mata ba, be kuma kalli inda take ba gaba daya yanayinsa ya sauya,
ta lura da hakan ta hanyar satar kallonsa da take time to time har suka isa. A
gurin da ya faka dazun ya sake fakawa ba tare da ya ce da ita komai ba.

“Anya dai lafiya ko wani abun ta yi maka ne?”

“Zamu yi waya”

Ya fada a takaice, sai ta bude motar ta fita ta rufe kuma ta tsaya a gurin tana
kallon motar har yayi reverse ya isa babban gate aka bude masa ya fita. Ita dai
mamaki da tunani ya hana ta tsinkayo abun da ya faru, bata amsa masa ba ne ta biyo
shi da bakar magana ko kuma dai wani abun ya faru, to amman ai ta ga Hurriya ta
shigo normal har tana mata murmushi, ita har tana zaton murmushin jindadi ne. Tana
tafiya tana tunani kamin ta waiga, to amman me yasa ta ganshi a wannan yanayin?
Idonta ya sauka a wata sabuwar motar da zata iya shaidar ta waye ba. Ta isa kofar
dakin ta murda ta tura ta shiga, tana yin arba da Captain dake zaune a cushion
hannunsa rike da takardu ta sake fuska ta karasa gurinsa da far'a.

“Captain sannu da zuwa”

Ya dago ya dubeta cikin wani yanayi da ba na wasa ba ya nuna ta da yatsa ya ce.

“Idan kika sake kai yaron nan gurin Hurriya sai na ci ubanki....”

Namra ta tsaya a gurin kamar hoto ta kalli Momy da ita ma kallonta take tana kuma
kallon Captain ta gafen ido.

“Momy zan samu?”

Momy ta kalleshi.

“Yanzu na fada maka duk abun da ya faru fa Captain!”

Ya kalli Momy ya ce.

“Ko zina take yi be kamata a koreta daga gidan ubanta ba, kuma yanzu kika gama fada
min cewar mahaifiyarta bata da lafiya ko magana bata iya yi, to yanzu waye zai kula
da ita idan bata gidan nan?”

“Gurin da ka ganta hannun kakarta ne mahaifiyart Appanta”


“Ba zata iya riketa yadda ya kamata ba, tarbiyarta zata iya tabuwa, dan Allah Momy
dan ni ki bawa mahaifinta hakuri ki yi duk yadda zaki iya yarinyar nan ta dawo
gidan nan.. ”

Namra ta yi katsalanta ta ce.

“Momy ta fada maka abun da ta yi...”

Captain ya mike tsaye ya daka mata tsawa, har sai da matsa baya da sauri gabanta na
bugawa da karfi.

“One word from your mouth sai na cika miki baki da jini, baki ji kunya ba kina
gidan ubanki zaune yar'uwarki jininki tana wani gurin da sunan mahaifinta ya
koreta? Baku san darajar jini ba saboda kina da yan'uwa da yawa, ni da aka haifa ni
kadai a cikin uwata, kuma ni kadai a gurin ubana na fi ki sanin darajar yan'uwa,
dan'uwa da kuka hada uba ko uwa shi ne ďan'uwa na jini makusanci, the rest are red
oil”

Ya wuce yana taka kasa da karfi kamar wata giwa, Momy da Namra suka bishi da kallo
har ya fice.

“Yaushe ya dawo?”

Namra ta tambaya, Momy ta kalleta ta ce.

“Ni ma yanzu ya shigo min, ina kika je? Da waye ya ganki?”

Namra ta nufi gurin da ya tashi ta zauna yana yawo da idonta tunani kala kala a
ranta.

“Gidan Hajiya na je, amman ni be gan ni ba sai dai idan Hurriya ce ta yi wani
munafurci, shiyasa na ga ran Salim ya bace, ita kuma ta shigo tana murmushi... To
me ma ya kai shi gurin ina ta san shi, shi ina ya san Salim?”

“Ni ba gane wannan shabbatun baki zan yi ba, ki yi min bayani kawai na fahimta”

Sai a lokacin Namra ta kalli Momy ta fara fada mata dalilin zuwanta gidan Kakarta
Hajiya Binta daga karshe ta rufe da sakon da Hajiya Binta ta bata ta fada musu.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

2⃣0⃣ 2⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞2⃣0⃣ 0⃣

“A haka Captain yake cewa na bada hakuri na dawo da ita, be san halin yarinyar nan
ba makira ce”

Namra ta ce.

“Ni ma sai yanzu nake gane halinta Momy, kuma na yarda ita taje ta yo munafurcin a
gidan su Husna wata kila tana yin haka ne saboda a tausaya mata”

“Bata daukarwa kanta hanya mai bullewa ba kuwa, kuma ni ba zan bada Appanku hakuri
akan dawowarta ba, ni ko kaunar ganinta ma bana yi a yanzu”

“Ni ma shi ne, gata da fuskar tausayi da iya makirci, ban san me ta fadawa Captain
na har yake son a dawo da ita, ko cewa ta yi mu muka koreta kuma? Har da wani cewa
idan na sake kai Salim gidan sai na ci ubana, waya sani ko cewa ta yi na kawo mata
dan'iska kuma”

Momy ta sauke ajiyar zuciya.

“Shiyasa tun farko ban so zaunawarta a bangarena ba, saboda bana son ganin dan kowa
a nan sai nawa, gashi nan kuma ta zo tana neman hanani zaman lafiya”

Namra ta cige baki, gaba daya yau Hurriya ta yi ruining din day dinta, daman jiya
ta gama sanin Salim ba ita yake so ba, yau kuma ta hada mahaifiyarta da Hajiya, ga
kuma Captain da ta saka ya zage ta kuma ya zargeta da abun da bata san kuskure a
cikin aikata shi ba.

“Wai yaushe ma ya dawo?”

Namra ta sake tambaya.

“Ni kaina ban sani ba shekaranjiya ma na yi waya da Hajiya Turai amman bata fada
min Captain zai zo, amman dai da alama yau ya shigo garin nan, duk dai zuwan nasa
ba sani ake ba”

“To yanzu ya zaki ce masa?”

“Cewa zan yi na yi magana da mahaifinta yace be yarda ta dawo ba, ban da ma


daukarwa rai ya cusa kansa a wannan rigimar”

“Kika san abun da ta fada masa”

“To ina ta san shi ma yaushe rabonsa da gidan nan”

“Zata iya ganeshi ai, kin san ya taba marinta, tawun motarsa ma da aka fasa kika ce
Hajiya ce ba Hajiya bace ita ta zuga Hamad ya zo ya fasa masa tawun mota”

Momy ta watsa mata wani kallo

“Ke tsaya... Kina nufin tayun da aka taba fashewa na Captain Hamad ne?”

“Wallahi shi ne”

“Oh yara dai sun zame mana masifa”

Namra ta tabe baki tare da duba wayarta sannan ta tashi tsaye ta nufi stairs, kamar
wanda ta yi mantuwa sai ta dawo ta nufi kofa.

“Ina zaki je?”

“Sakon Hajiya Binta zan isarwa Hajiya”

“Dawo kyaleta idan ta matsu ta fada mata da kanta ai tana da wayarta ta kira
wayarta ta fada mata mana”

“Momy kara na isar mata ai, kar ni ma na yi laifin gurin Hajiya kin san bata hada
Hurriya da kowa ba a gidan a nan”

Momy ta dauke kai ba tare da tace komai ba, wanda ke nuna alamar ta aminta Namra ta
tafi kenan sai dai ba dan ranta ya zo haka ba. Namra ya fice tana juya yawarta a
hannun har lokacin sake saken yadda Hurriya ta shirya komai take, me ta fadawa
Captain kuma me ya sa ran Salim ya bace shi ya fi tsaya mata a rai, har ta yi kamar
ta kira shi sai kuma ta fasa ganin shi ma kamar baya son ta sani, kuma ita Yaya ce
be kamata ta shige masa ba. Sai da ta kalli Khairy dake ta fito falon sannan ta
dauke kai ta shiga, daman ita da Khairy yanzu babu mai yi na wani magana tun a
lokacin da sa'insa ta shiga tsakaninsu saboda iyayensu. Sai da Namra ta shige
sannan Khairy ta dauke idonta daga kofar falon Hajiya ta nufi gate, tana ficewa a
karamin gate ta nufi babban masu gadin suka bude mata ta fita. Tafiya mai nisa ta
yi sannan ta isa gaban wata mota, sai da ta fara kwankwasawa ya sauke gilashin
sannan ta bude ta shiga baya ta zauna.

“Yarinyar nan fa bata nan amman baka yarda ba”

“Ba zaki iya fitowa da ita ba shi ne kawai”

“Wallahi bata nan, Appamu ya koreta ta koma gidan Kakarmu da zama”

Ya juyo ya kalleta.

“Saboda me?”

“Mumafurci ta yi shi kuma da ya ji ya koreta”

“Munafurcin me ye?”

“Ba abu ne da ya shafe ka ba, magana ce ta cikin gida, ni dai yanzu mu kare abun da
zamu yi ina son na koma kar Yayana ya dawo ya nemi ni bana cikin gida”

Ya daga kafadunsa.

“Kin san abun da ya kawo ni ai”

“Ni ba zan iya maka magani ba Adam, kullum kana damuna da maganar yarinyar nan, ni
fa ina da damuwa baka san abun da yake damuna ba”
“Duk wata damuwa taki mai sauki ce saboda na san ba zata wuce ta kudi ba, amman ni
kin san kudi ba za su magance matsala ta da yarinyar nan ba saboda kin bata komai”

Cikin matukar damuwa da gundira da dora mata laifi da yake ta ce.

“Yanzu me kake so na yi? Ni ban bata ka ba Adam, kuma ba a saka soyayya da karfi ai
da ka sakawa kanka ko?”

“So nake ki gyara, ki gyara duk wani abu da na bata yarinyar nan ta dawo tana kula
ni”

“Ban san yadda zan yi haka ba Adam, kuma kai kanka ka san ba auren yarinyar zaka yi
ba, ita kuma tana da wahalar sha'ani ba irin mu ba ce”

“Ta ina kika karanta cewar ba aurenta zan yi ba? Ina aka rubuta hakan a goshina?
Kin gani ko ke kika kara bata abubuwa”

“Kai baka san yadda zaka yi ta so ka ba ne Adam, kai ba namiji ba ne, ka dame ni da
zancen yarinyar kamar ita kadai ce mace a garin nan”

“Ba ita kadai ba ce, amman ita nake so yanzu kuma kin san yadda zuciya ke hana
mutum zaman lafiya idan be bata abun da take so ba”

“Adam akwai matan da suka fi Hurriya kyau a duniyar nan, kuma babu wanda zaka ce
kana so bata amsa maka ba, ita Hurriyar nan fa makauniya ce, bata gani sai da
gilashi”

“Ko gurguwa ce haka nake sonta...”

Ya mika hannunsa a front seat daga kasa ya dauko wata ledar ta mika mata.

“Kudi ba matsala ba ce, zan iya biyanki ko nawa ni dai ina son ki ja hankalin
yarinyar ya dawo gareni, kin san yadda nake daga hankali idan ina son abu”

Ta mika hannu ta karba ta bude kudi da ba zata iya fadar adadinsu a yanzu, kudi ne
mai yawan gaske kuma bata yi mamaki ba, daman cikin familynsu ya fi kowa wasa da
kudi, wannan ya saka yan mata da yawa suke lake masa. Ta daga kai ta kalleshi

“Adam.. Me Hurriya take da shi da ya fi na sauran matan duniyar nan?”

“Tana da kyau, tana da jiki da sifar da nake so a jikin mace, kuma babu ruwanta da
magana ina son mace haka, and zan iya nuna ta a ko'ina as my girlfriend kowa ya
gani ya san ya zabo mai kyau”

“Ba zan iya sakawa Hurriya ta so ka ba Adam, ko da kuwa duniyar nan da abun da yake
cikinta ka mallaka min, ba zan iya cusa soyayyarka a zuciyarta ba saboda tana da
wahalar sha'ani kuma tana da tsoro, kuma ta riga ta san waye kai, ko dan gudun
gargadin da Appa yayi nata da kuma Yaya Yasir dole ta guje maka”

Ya jinginar da kansa yana busar da numfashi.

“But zan iya maka taimakonka ta wata hanyar idan hakan zai wadatarta kuma idan
hakan zai saka ka daina dora min laifi”

Ya juyo ya kalleta.

“Wane irin taimako? Ni bana da burin da ya wuce yarinyar nan ta so, abun da kika
kasa fahimta shi ne yarinyar tana da karfin jini jan hankalin mutum, kuma idan ta
shiga zuciyarsa tana da wuyar mantawa abun daga jini ne, baki san iya yadda na yi
kokarin cire yarinyar a zuciyata ba amman sai kara shiga take har mafarkinta nake
Khairy”

“Ba zaka ki wannan shawarar tawa ba, amman ba yanzu za mu yi maganar ba sai idan na
shiga gida sai mu yi waya”

“Zamu iya maganar a yanzu ai, zai fi saboda gani ga ki”

“Yayana zai iya dawowa ya nemi ne, idan kuma ya gano ina nan zamu shiga matsala
daga ni har kai”

“Ki fada min a nan zai fi”

“Matsala ta da kai kenan Adam, ba ka daukar shawara kuma baka yi ma mutum izuri,
kanka kawai ka sani ni ina kokarin ganin na cireka a matsala kai kuma kana son
jefani, ba abu ne na tashin hankalin ba na ce ka bari na tafi gida idan na natsu
sai mu yi magana kamin lokaci ma wata kila na kara samun mafita”

Ba dan ransa ya so ba ya sauke ajiyar zuciya ya daga mata kai.

“Shikenan, amman zan fada miki gaskiya idan kika ci wannan kudin ban samu abun da
nake so ba”

Ya tsaya tare da busar da iskar bakinsa.

“Ba zan duba abotar mu ba, kuma kar yi mamakim duk abin da zan miki”

“Hakan ma ba zata faru ba”

“Okay”

Ta bude motar ta fita sannan ta miko hannu ta dauki kudin, be bar gurin ba sai da
ta shige cikin gida. Sai da Khairy ta nemi guri ta boye kudin a Garden saboda tana
tsoron Hajiya ko Yayanta ya ganta da kudi mai yawa haka a leda, tsayawa ta yi ta
natsu sannan ta dawo ta nufi kofar falon.

Ruma na zaune tana kallon Hajiya Kaltume dake ta zuba ruwan bala'i na sakon da
Namra ta isar na Hajiya Binta, ji take kamar ace mahaifiyar mijin nata tana kusa da
ita ta amsa mata daidai da abun da ta aiko aka fada mata.

“Wato ta koma can zata fara hada mu da Hajiya ko? Ita dai Iyami ta kawo mana bala'i
kawai a cikin gidan nan ta hana mu zama lafiya, na kashe maciji amman ban tare kai
ba shi ne a nan, yar guda guda ta zame mana fitina a gida”

Ruma ta kalli Hajiya Kaltume cikin yanayin bakinciki har idonta na cika da kwalla
ta ce.

“Haba Hajiya yanzu kuma me ye laifin Hurriya a nan, fadan da Hajiya Binta take yi
saboda abun da kuke mata ne, kuma gaskiya ta fada, da ni ce ko Khairy ba zako bari
wani na tafi ba, ita ma Momy da Namra ce ba zata bari ta tafi ba, amman kalli yadda
Appa ya koreta kamar wata bare, Hajiya komai sai kin dorawa Amma laifi matar nan
bata lafiya magana ma wannan bata iya, shin ya kuke son Hurriya ta yi? Ta rasa
dan'uwa mahaifiyarta babu lafiya yanzu kuma Appa ya koreta kuma still ita kike
dorawa laifi”

Hajiya Kaltume dake jin kamar ya janyo Ruma ta rufe da duka ta shiga fada a tsawa.

“Da uwarta bata zo ta aurar min miji ba duk zamu san da wannan matsalar ne? Da
yanzu za a haifi Hurriya har ta fara hada munafurci ne? Da take kwance bata da
lafiya ni na saka mata ne? Mugun bakin kwadayinta ne ya ja mata”

“Momy ma Appa take aure, amman baki mata masifa kamar yadda kike yi ma Amma, Amma
tana son mu tana nuna mana kulawa tsabanin Momy da ko bangarenta bata son mu shiga,
kuma idan har suna da laifi to duk laifinsu daya ne domin Appa suka aura”

“Ke yarinya ki iya bakinki, idan baki san gari ba saurari daka, banbancin Iyami da
Nafisa ai a bayyane yake, Nafisa a can ya ganta ya auro, Iyami kuma sai da ta gama
cin duduniyata ta san sirrin gidana da na mijina sannan ta kulla min gadar zare ta
zubar da ni a kasa, ke ba zaki gane abun da ake ji ba, saboda ke yarinya ce baki
san me duniya take ciki ba sai nan gaba”

“Ko da hakan ta kasance a gareni, ba zan tsaneta kamar yadda kika tsani Amma da
Hurriya ba, da ina ganin kamar ke ce mao gaskiya amman daga lokacin da aka kashe
Hamad, sai tunani ya canja wane irin tsana ce zata saka a kashe rai? Idan Amma tana
da laifi Hamad fa? Me ya aikata? Yaron nan yana kuka yana kiran sunan Appa da
mahaifiyarsa suka fitar da shi, kansa na jini yana ihu yana fadar ayi hakuri yana
rike kansa dake jini yana kiran sunan Hurriya daga karshe ma sunana ya koma yana
kira, Hajiya na kasa manta wannan duk lokacin da na kalleki wannan abun nake gani,
amman ni cewa kika kar a taba ni saboda ina yarki wace irin zuciyata ce wannan?”

Hajiya Kaltume na mikewa tsaye Khairy na turo kofar falon ta shigo da sallama.
Hajiya ta yi saurin kallon kofar idonta kamar za su fado saboda razana.

“Wa'alaikussalam”

Ta amsa mata muryarta na yin kamar zata yi rawa. Khairy ta karaso cikin falon tana
musu kallon tuhuma domin jiki da fuskar Hajiya Kaltume ya nuna alamar ba lafiya ba,
ga Ruma sai kuka take sosai.

“Lafiya?”

“Lafiya Kalau”

Hajiya ta amsa mata da sauri, Ruma ta tashi tana kuka ta nufi stairs, Khairy ta
bita da kallo har ta haye sannan ta kalli Hajiya da hantar cikinta ke kadawa ta ce.

“Me ya faru take kuka?”

Abun ka da makiri kuma wanda karya bata yi ma wahala a take Hajiya ta juye abun
domin bata son kowa ya ji.

“Munafurcin da Hurriya ta yi ne ya taba ta”

“Munafurci?”

A tsaye Hajiya Kaltume ta zubewa yarta komai da Namra ta fada har ma da wanda bata
fada ba, daman ai ba zata bar miya haka nan ba sai ta kara mata gishi da magi.

“Wallahi kawai ki fadawa Appa shi zai yi maganinta idan ba haka ba, shi ma kansa
sai ta hada shi da Hajiya, waya sani ma ko ta zugota ta zo tace ba ta yafe masa ba,
ko kuma ta rantse sai ya sake ki, daman tana da haushin barin gidan nan da uwarta
ta yi, shiyasa ni gaba daya fa bana kaunar yarinyar nan, ga iya jan hankalin maza
na bala'i kamar wata rikakkar karuwa”

“Wannan kuma ba banza ba, ai kin san uwarta sai ta wanke ta bata sha, kamar yadda
ta sha ta dauke hankalin Alhaji har ya aureta”
“Gaskiya ni ma i doubt wannan farin jini da jan hankalin ba banza ba ne, ba zai
yuyi ace kowane namiji farar mace mai kyau yake so ba, to mu ayi yaya da mu
bakake?”

Tana fada tana bata rai kamar ta ci magani.

“Ba farin ne kawai ba, har da asiri”

“Daga gani ma ba banza ba, Hajiya tafi ki fadawa Appa ya daukar mata mataki tun
wuri”

Ta zauna saman kujera tana ta fushi kamar an mata wani abu, kamin ta shiga Gallary
wayarta ta kamo hoton Hurriya ta kura ido tana son tantance abun da Adam ya gani a
fuskarta da jikinta da ya nace sai ita, ga Fadeel ma ko a jiya da ya zo sai da ya
nemi yin magana da ita.
Hajiya Kaltume da har lokacin a tsaye take ta juya ta nufi kofar dake gefen dinning
wanda zata sadata da bangaren Appa, zuciyarta fal da tsoro na maganar Ruma, yanzu
ba kisan ne abun da ke ranta ba, fallasar asirinta ne abun da yafi damunta, shekara
uku amman Ruma ta kasa mantawa ta saka sakewa gaba daya ta canja tun a lokacin da
wannan abun ya faru, idan kuma har zata rika sakin baki haka wata rana dole
asirinta zai tonu, ita ta san har ga Allah bata ce a kashe Hamad ba, ba saka an
dauke shi dan a kashe shi ba, hasalima ba shi aka je dauka ba, Hurriya ta ce a
dauka, tsaitsayi ya biyo ta kan Hamad ashe da rabon ya bar mata baya da kura. Bata
san ta isa bangaren Appa ba sai da ta ji ta bugi kofar shiga, a nan ta sauke ajiyar
zuciya ta rufe ido ta dafe kanta da hannu daya.

_Kai wayyo Allah... Da na sani ban aikata wannan abun ba, da ma ta asiri na bi
kamar yadda na yi ma Iyami, duk gajin hakuri ne ya ja min, yanzu ko yaran nan aka
kama suka fadi sunana ai na shiga uku sunana zai bace a duniya, yarana su ji kunya
musamman ma matan nan_

A ranta take ta sake sake rashin natsuwa da tashin hankali na kara kusantar ta, ta
sauke ajiyar zuciya ya kai sau takwas sannan ta sauke hannunta ta murda kofar ta
shiga, babu kowa falon dan haka ta nufi karamin falon Appa da ya fi yawan zama.
Yana ganinta yayi saurin sauke wayar da yake ya yanke kiran murmushin dake fuskarsa
ya bace.

“Hajiya”

Ta zauna kusa da shi tana fada.

“Na'am Alhaji a nan ake hutawa, Nafisa bata shigo ba?”

“Ina tunanin sai an jima kadan zata shigo”

Yayi saurin rejecting kiran dake shigo masa ya saka wayar silent ya aje ta a gafe.

“Toh bari na yi magana ta kamin ta shigo, wata kila ma ita ce take kiranka kasan
sarauniya ce wani lokacin sai dai ta kira ta tambaya abun da kake so ta zo maka da
shi, ba kamar mu da bama raina lada ba”

“Aa ba ita take kira ba, wani.... Sakatarenmu ne... ”

Ya amsa kamar marar gaskiya. Cikin rashin kuzari na abun da ya faru ta kora masa da
bayanin abun da Hurriya ta yi har Hajiya Binta ta aiko musu da sako. A take Appa ya
hade fuska ya bata rai sosai daman a yanzu baya ganin farin Hurriya sai bakinta.

“Wai yarinyar nan me take son zama ne?”


“Toh ka gani dai idan baka daukar mata mataki ba, sai ta lalace kuma nan gaba ba a
san me zata yi ba, kai kanka idan baka dauki mataki ba sai ta hada ka da Hajiya,
kara tun wuri ka rabata da gidan Hajiya ka maida ita can gurin uwarta ko kuma ka
dawo da ita nan din, domin ni dai ina jin tsoron shairin yarinyar nan, kara nan
tana karkashin kulawarka zaka saka mata ido”

“Bana bukatar Hurriya a gidana”

Appa ya fada a fusace.

“To ya muka iya da abun da ya fi karfin wuta, in ji kishiyar konanniya, hakuri zaka
yi tun da hannunka baya rubewa ka yanke ka yar kar dai ta zauna gurin uwarta ko
gidan nan, nan din ma zai fi saboda Hajiya zata iya cewa ba zata zauna gurin uwarta
ba, kuma idan ma ta zauna can zata iya sulalawa ta koma gidan Hajiyar ba tare da
saninka, kara tana gabanka kana ganinta, albashi ka samu ko masinja ne cikin
ma'aikanta ka aura masa ita mu huta...”

Uffan Appa be sake cewa ba ya bata rai sosai, domin sam maganar da Hajiya ta fada
masa na abun da Hurriya ta yi be masa dadi ba.
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

2⃣1️⃣ 2⃣1️⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞2⃣1️⃣

Appa be raba dayan biyu ba Momy ta turo kofar dalon ta shigo, yadda ta tararda Appa
da Hajiya Kaltume a kujera daya ya saka ta daure fuska ta fara wani kallo na uku
saura kwata.

“Miye haka Alhaji? Ina ce yau dai girkina ne, ko kuma irin abun da ake yi ma Iyami
shi za'ayi min?”

Hajiya Kaltume ta tabe baki, har ta juyar da fuska sai kuma ta juyo ta kalli Momy.

“Magana ce ta kawo ni, maganar da zata taimake ke ki ta taimake ni kuma ta taimaki


wanda muke neman aljanna karkashin kafarsa, magana ce akan Hurriya kuma yarki aka
aiko da sakon shi nake fadawa Alhaji”

Momy dake tsaye ta dauke kai domin haka be gamsar da ita ba, cikinsu babu wanda
yake son ganin abokin zamansa a bangaren mijinsa idan ba girkinsu ba ne, sai dai
Iyami suna mata haka, su kam shiga su yi magana da Appa ko da tana ciki wani
lokacin har sai Appa da kansa ya nuna musu baya so, ita kuma tana kiyaye yin haka
idan ba girkinta ba ne.

“Toh tun da kin fada ai sai ki kama hanya ko kuma maganat bata kare ba ne”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi kamar ba ita ba.

“Nafisa... Hajiya Nafisa... Ya fa kamata ace mun aje kishi a yanzu, ya kamata ace
mun san girma ya kama mu a yanzu, ni idan ma kina son kwanan idan girkina ya zagayo
ai sai na yafe miki, ni dai ina neman mafita ne acikin lamarin nan, domin Hurriya
ba ni kadai ta sako a gaba ba har da ke.. Da kuma mahaifinta, wata kila nan gaba
kadan idan tana zaune a gidan Hajiya zata iya sakawa ta tsine mana gaba daya, ko
kuma ta cilastawa Alhaji rabuwa da mu”

Appa yayi karaf ya ce.

“Aa Hajiya ai tana da hankali da tunani, ba zata yi haka ba”

“Baka da tabbaci kai kanka idan aka fada maka Hurriya zata aikata abun da zai saka
ka koreta a gidan nan zaka yarda? Amman da yake butuluce kamar uwarta ai gashi nan
ta je ta zage ka a wani gurin ta saka makota suna maka kallon azzalumi, nan gaba
kadan kuma baka san abun da zai biyo daga gurin Hajiya ba, kasan dai yadda take son
Hurriya take daukar shawararta”

Sai a lokacin Momy ta kai zaune, bayan Hajiya Kaltume ta gama rattaba bayannanta.

“Ni abun da nake gani kawai ka yi hakuri ka dawo da ita gidan nan, idan ba haka ba
ma zata iya lalacewa”

Momy ta dubi Hajiya Kaltume ta ce.

“To miye amfanin korarta da Alhaji yayi? Ai sai ta dawo ta cigaba daga inda ta
tsaya tana hada mutane”

“To ai mun san halinta yanzu, ko da ta fada ba zamu yarda kuma dole a ja mata
kunne”

“To sai dai idan bangarenki zata zauna, ni dai na gaji da zamanta a gurina, balle
kuma yanzu”

“Aa ni da take kallon a matsayin makiyiyarta, ta ina ma zata yarda ta zauna a


gurina”

Appa ya gyara zama ya kallesu one after the other ya ce

“Kar wanda ya sake bani shawara ko zabin gurin da Hurriya zata zauna, idan har zan
dawo da ita cikin gidan nan a inda nake son ta zauna zata zauna, daga gidan har ku
da yayanku a karkashin ikona kuke, musamman ke Nafisa na lura da bakinki ba shi da
linzami akan irin wannan maganar, kai tsaye kike furtawa, na yi miki kashedi amman
baki ji ba, wata kila sai kin ga zahiri... ”

Da mamaki Momy ta kalleshi bakinta a sake ta ce.

“Allah da iko yake, in ba dan ana son a maida laifi gareni ni da aka raina ba, ai
Kaltume ma ta yi maganar ba zata zauna a bangarenta ba, amman sai ni kake yi ma
radda wato ga ni itace mai dadin hawa, to Allah ya baka hakuri ta zo ta zauna,
daman korar ai ba ta Allah da Annabi ba ce, tun da ga shi har kuna son a dawo da
ita”

Appa ya dakawa Momy tsawa domin ita kadai ce yake yi ma fada a yanzu, Hajiya
Kaltume kuma an saka masa tsoronta ko da ta yi ba daidai ba ba zai iya magana ba,
and ba zai iya bijirewa umarninta ba.

“Nafisa... Akan yayana zaki iya janyo wa kanki masifar da zata daukeki daga gidana,
bana son ana aibanta min yaya dukansu, ki sani Hurriya ko kisan kai ta aikata
Hurriya Haruna Mai Yadi haka za a kirata babu wanda ya isa ya kankare wannan, kin
fara kai min hanci kuma ina daf da fyatoki, idan baki rike rike girmaki ba, baki
dauke idonki akan Yayana ba za ki sha mamaki”
Hajiya Kaltume dake murmushi cikin rai, ta kalli Appa da ciki wani yanayi dake nuna
da gaske take yi ta ce

“Haba Alhaji yanzu saboda Hurriya sai ka ce zaka fadi wani abu marar dadi akan
Nafisa, adai yi hakuri shekara nawa ana tare, yanzu ga yaya sun girma ana zancen
aure kuma zaka bari shaidan yayi tasiri akanka? Kara dai ayi hakuri duniyar ma duka
duka nawa take? Ni ko Iyami ban jidadin rabuwa da ita ba, tun da ga yaya biyu ko da
yake yanzu Hurriya ce kadai ta rage, amman dai ba dadi ai, da yanzu tana nan da duk
ba zamu samu wannan tsabanin ba, tun da yarta taba hannunta”

Cikin fushi Appa ya ce


“Ko yanzu ai zan iya kai mata ita, ba dole sai ta zauna nan gidan ba”

“Aa kara dai ta dawo nan din, can ga uwa tana jinya abun ai sai ya taru ya zama
biyu, wahalar ta yi musu yawa, kana ganin wannan halin da hurriya ta fara idan ba a
nan take ba ai kara baci zata yi, ni da kaina zan shirya mu tafi tare a daukota
daga gidan Hajiya, ko yanzu ai ta horu”

Momy dai bata sake cewa komai ba, domin bata son Appa ya sake furta mata wata
maganar marar dadi a gaban Hajiya Kaltume.

“Ni zan tafi bangarena sai da safe...”

Appa ya mike tsaye ya nufi dakinsa, kama yadda Hajiya Kaltume ma ta fice daga falon
bayan ta yi musu sallama. Duk wani damuwa da tunanin tonuwar asirinta ya gushe a
zuciyarta saboda farincikin ganin fadan Appa da Momy. Da murmushi ta shigo
bangarenta tana maida kofar dakin ta rufe Kulu ta mike tsaye hannunta biyu a hade
tana murzawa.

“Hajiya an fito, na ga ita ma Momyn ta fita shiyasa na zo da sauri, sai kuma aka ce
min kin shiga bangaren Alhaji shi ne na ce bari na jiraki”

Hajiya Kaltume ta dan yamutsa fuska yayinda ta kawo gurin da Kulu take tsaye da
daurin zanenta irin na masu siyar da ganye.

“Zuwanki ai ba shi da wani amfani kulu, kullum babu wani abun da kike kawo wa, tun
lokacin da na saka binciken dakin Hurriya baki kawo min komai ba”

Kulu ta shiga rantsuwa.

“Wallahi Hajiya na bincike dakin Hurriya kaf har kayanta sai da na duba amman ban
samu komai ba, kin ga kuma dole na fada miki gaskiya ba zan miki karya ba”

“To yanzu me ya kawo ki?”

“Dazun ne ina cikin Kitchen ina wanke kayan da suka ci abinci, kin san Momy bata
son a bar kaya ya kwana ba a wanke ba, to ina cikin wankewa sai ga wani bakon Momyn
ya shigo, yana ta masifar wai an kori Hurriya Momy bata yi komai ba, har umarni
yake bata wai ta dawo da ita, ita kanta Namra da ta saka baki a maganar sai da yayi
kamar zai mareta”

“To waye shi?”

“Ina tunanin dan yayanta domin can da yana zuwa gidan sosai kuma danta take kiransa
tana nuna masa so sosai, haka suke ce masa kefin”

“Miye alakarsa da Hurriya?”


“Toh nima shi ne ya ba ni mamaki ai, na ce ko sonta yake yi, ya ma daina zuwa an fi
shekara uku yanzu sai yanzu ya dawo, amman ita ma kanta Momy da Namra ina jin suna
tsinewa Hurriyar suna cewa bata da albarka”

“Ai dole, tun da ta fara hada munafurci, amman duk da haka ni da kaina zan tafi na
dawo da ita gobe, sai na nuna mata hankalin Babba dabam dana yaro, kuma idan za a
asake korarta sai daia yi nata korar da zata tafi nesa da garin nan gaba daya, ba
wai ta tsaya a kusa da Hajiya ta hada mu ko kuma Appanta ba”

“Shi ke nan Hajiya, daman na ce bari na fada miki ne abun da na ji”

“Kin kyauta kuma ina son cigaba da abun da kike yi, da zarar kin ji kyas ki zo ki
fada min, tun daga kan Hurriya har Nafisa da kasuwancinta”

“Toh Hajiya na gode mu kwana lafiya”

Hajiya Kaltume ta daga mata kai, sannan ta bita da kallo tana tauna maganar da ta
fada mata a ranta. Waye yaje yana masifar a dawo da Hurriya? Sonta yake ko kuma me?
Waya sani ma ko kanta take bashi ko yake neman samu saboda ta zama marar aji yanzu,
tun da uwarta ta bar gidan, kuma gashi har wani dan iskan ma Adam ya ce yana sonta.

“Hajiya...”

Ta juyo ta kalli Yasir dake saukowa yana sanye da jallabiyar da ya siye a Khadeeja
Candy Store, sai shinning take kamar an zuba mata mai.

“Yasir ka dawo?”

“Eh, na shigo ai baki dakinki Khairy tace kin tafi bangaren Appa”

“Eh na je na yi magana da shi ne akan Hurriya, kasan kai baka son laifinta shiyasa
ban fada maka abun da ta yi ba”

“Kararta kika kai gurin Appa kuma? Haba Hajiya? Duk bayan wannan abun?”

“Aa ba kararta na kai ba, sako Hajiya ta aiko mana wai muna takurawa Hurriya magana
dai babu dadi ji, ni kuma na je na samu Appanku na bashi shawarar dawowa da Hurriya
a gidan nan zai fi, ka ga mun guje bacin ran Hajiya kuma mun shirya ta da
mahaifinta”

Yasir yayi murmushi dake fitowa har daga zuciyarsa.

“Haka na ke son ki zama Hajiya, kuma na ji dadin haka Allah ya saka miki da alheri”

“Amin”

Ta kalleshi sama da kasa.

“Yau ka dawo da wuri baka tafi gurin hirar ba ne”

Ya dan yi murmushin kunya ya shafa kansa, tare da cira kafa ya nufi dinning, Hajiya
ta bishi da kallo na kauna da alfahari.

“Wai ni kam wace yarinya ce wannan mai tsada, har yau baka kawo min ita mun gaisa
ba, kamar fa baka daukar komai naka da muhimmanci, ni bana son Miwan da Musib su
rigaka aure, ka san kuwa suna dawowa kasar nan babu abun da za su yi sai aure”

Kai ya rankwafar alamar damuwa kadan na bayyana a fuskarsa.


“Hajiya, su dabam ni dabam idan ma sun riga ni aure miye a ciki? Komai fa lokaci
ne, ni ma kuma yanzu yarinyar da nake jira ta kare karatu kuma ina son na maida
hankali gurin gini na da hada kayan lefe, sai dai ni da ita muna tsoron yadda
iyayenmu za su karbi abun ne, musamman ma ta bangaren iyayenta”

Hajiya ta Kaltume ta nufi gurin da yake

“Miye abun tsoro, ka tafi kanka tsaye ka fada musu waye ubanka a garin nan, dole a
karba maka uwarka ma nan gaba kadan za a fara sakawa da ita cikin manya mata yan
kasuwa na garin nan ko ma na ce na arewa gaba daya”

Ta karasa yayinda ta dora hannunta a kan kujerar da yake zaune. Juyowa yayi ya
kalleta da murmushi a fuskarsa.

“Kasuwanci zaki fara Hajiya”

“Sosai kuwa, ina son na bude shagunan tufafi masu kyau da tsada, kuma zan bude
gidan mai ba da jimawa ba”

“Kuma Appa zai yarda?”

“Me zao hana shi yarda? Nafisa ma ba kasuwancin take ba? Ina ce nan take siyar da
sinari a shagonta ga kuma shagon aski da na gyaran jiki da na cin abinci da take da
shi a garin nan, babu mai kalar shagunanta, sai kuma yace zai hana ni? Ai ba zata
sabu ba”

“Toh Allah yasa albarka kuma ya hadaki da mutane na gari, amman ki kula sosai da
wanda zai kula miki da abubuwanki”

“Amin, ai kai nake son ka zama shugaba”

“No ba zan iya ba, harkar kasuwanci ai sai Appa, ni ko zan iya sai nan gaba, yanzu
akwai abubuwan da suke gabana?”

“Aure? Tun da na san ka gama karatu kuma kana aiki”

Ya daga mata kai.

“Aure Hajiyata”

“Wacece to? Da har kake tsoron iyayenta su ki karbarka? Ai babu yarinyar da zaka so
a garin nan ita ko iyayenta su ce maka a'a”

Ya karkato ya fuskance da kyau.

“Har da Rukayya?”

“Ko Wacece kuwa, amman wace Rukayyar?”

Sai da yaja dogon numfashi ya aje ya sauke idonta saka dan kar ya hada ido da
Hajiya Kaltume sannan ya bata amsar tambayarta

“Rukayya yar wajen Bappa”

“Ka kara batar da ni a duhu”

“Yar wajen Gwaggo, kanwar Amma, little mom din Hurriya...”

“Eeeehhh..... ”
Hajiya Kaltume ta dage hannunta da sauri matsa can baya kama wanda ta ga abun
tsoro.

“Ba a gidana ba, da yardar Allah ba a gidana ba, duk wani sihiri da suka ma
mahaifinka ya kama shi har Iyami ta aure kai kam ba zai kama ka ba, Innalillahi
Wa'inna Ilaihiraji'un, yau na ga bala'i ganin ido... Rukayya kuma yarinyar da ta fi
Iyami rashin mutunci da raina mutane? Haba Yasir duk matan duniya ka rasa waye zaka
so sai jinin Iyami?”

Yasir ya mike tsaye.

“Jinin Amma me ye matsakarsu? Suna da tarbiya suna duk wani abu da ake nema a gidan
mutunci, meye matsalar Rukayya”

“Bana sonta Yasir, ni da jinin iyami har abada, Hurriya ma rokon nake Allah ya raba
ni da ita balle kuma ka dauko min wasu yan baki gida, ba ni ba yan baki gida har
abada, kai kanka ba a banza suka barka ba”

“Komai dai na magani ne a gurinki Hajiya, kin ce Amma ta mallake Appa da mallaka ce
me zai saka ya saketa? Ni dai In son Rukayya kuma ita za aura, matsalata a yanzu na
yadda iyayenta za su karbe ni ba, ba kuma saboda kowa mai sai dan ke Hajiya”

Ya bar dinning din ya nufi stairs ransa a bace, sometimes ya kan gane kan
mahaifiyarsa, ita kam binsa kawai ta yi da kallo zuciyarta na karanta mata cewar ba
a hayyacinsa yake wannan maganar ba. Irin abun da aka yi ma Appa ne aka yi masa,
wato son suke ta ko'ina su mallake mata da da miji. A ranar da tunani ta kwana
washe gari Sallah asuba kawai ta yi ta dauki wayarta ta kira Hajiya Fatee ta fada
mata abun da ya faru, kamin ta kira Malaminta ta gabatar masa da bukatar.

HURRIYA POV.

Kafafuwanta a nade fuskarta kuma dauke da kayataccen murmushi take kallon Amma dake
cin abinci da kanta, duk kuwa da kasancewar hannun nata rawa yake rabin abincin na
zubewa, abun da bata iyawa tun a lokacin da ciwon ya same ta, gaba ta tisa Amma
tana ta kallonta kamar zata cinyeta tsabar murnar mahaifiyarta ta fara samun sauki.
Bayan Amma ta gama, Hurriya ta dauke plate din da cup din ruwa ta fitar sannan ta
dawo ta zauna kusa da Amma.

“Allah na gode maka da ka fara bawa Ammata lafiya”

Amma ta yi murmushi domin shi ne kadai abun da take iya yi Idan farinciki ya same
ta, idan kuma damuwa ce sai dai ta yi kuka, saboda bata iya magana, tana da abubuwa
da yawa a zuciyarta da take son ta tambayi Hurriya amman babu baki, ita kuma
Hurriya bata yarda ta yi hirar gidansu da ita, domin ba abubuwa masu dadi ne zata
fada ba, ko da Gwaggo ta tambaye ta, ba zata fada ba sai dai tace tana zaune kalau.
Cikin wani yanayi na tausayi da kauna da soyayya irin ta uwa zuwa ga yarta Amma ta
mika hannunta dake rawa ta kama hannun Hurriya idonta na cika da hawaye..

“Minene Amma? Bana cikin damuwa a yanzu, Appa ya maida ni gurin Hajiya Binta, kin
san yadda take so na ai, ita tace min na shirya na zo nan na wuni, saboda na kwana
biyu ban zo ba, ashe zan zo na farar da farinciki ne, gashi na ganki Amma kina cin
abinci”

Tana maganar tana sharewa mahaifiyarta hawaye a idonta. Twins din Amma suka zo da
gudu suka kwanta jikinta suna ta son yin fitina, da Amma ta kallesu sai ta ga sun
hadu su uku babu daya, da Hamad yana raye da yanzu yayanta sun cika hudu cif.

“Hurriya yau ji take kamar ta cinye Amma saboda murna?”

Hurriya ta saka dariya tana kallon Rukayya dake taje kanta.

“Mama Rukayya da kun fada min Amma ta fara motsa hannunta da sai na saci hanya na
zo”

“Shiyasa ai ba a fada miki ba, ki saci hanya ki zo nan wannan Kalwar ta hada ki da
Appanki, kin ga wannan mai fuskar yan wuta kiris ya rage ta shigeta, na tsani kamar
nan kamar mutuwata”

“Yanzu ai bana gidanta na koma gidan Hajiya, kin ga zan samu sauki, Hajiya bata
hana ni zuwa ko'ina balle ma kuma idan nan ne”

“To ya aka yi kika koma wai?”

“Ita ta rarrashi Appa kuma ya yarda”

“Wata kila ta ga wahalar da kike sha a gidan ta miki yawa ne”

Hurriya dai ta yi murmushi bata sake cewa komai ba, domin bata son a zafafa a
maganar. Bayan sun yi Sallah la'asar ta fito tsakar gidan ta zauna tare da Amma,
twins kuma suna ta wasansu kamin ta su fado kanta saboda tsokarnasu da take, sai
aka jone ita da su aka rasa waye karami, ita da kurciyarta bata gama fita jikinta
ko kuma su da a yanzu suke tasowa. Ana daf da fara kiran Sallah Magariba, Hurriya
ta shiga ta dauko hijabinta da jakarta domin sun yi da Hajiya Binta zata wuni a nan
ammam ba zata kai dare ba.

“Gwaggo zan tafi, Hajiya ta ce kar na yi dare”

“Toh kin koshi dai ko? Idan kuma kina son dan'waken ki tafi da shi”

“Aa na koshi a bawa yan biyu a ciki”

Sai suka saka dariya yana mulmula kan katuwar tabarmar da Gwaggo ta shimfida.
Hurriya ta kai kasa tare da kai bakinta a goshin Amma ta sumbanci, goshinta ta
sumbanci gefen fuskarta dama da hagu.

“Ina sonki Ammana Allah ya baki lafiya”

Amma ta yi murmushi tana binta da kallon da raunataccin idanuwanta. Gwaggo ta kalli


Rukayya dake hankalinta ke kan waya ta ce

“Ba zaki rakata ba? Ke dai kullum kina nan a waya, sai ta saka ki hauka idan baki
yi hankali ba”

Rukkaya ta kyalkyale da dariya.

“Gwaggo littafi ne nake karantawa na Khadeeja Candy, mai suna Mairo wai an bata
apple ta ce a kara mata gorar binni, wai yan binnni gorabar taushi ne da ita”

“Kyaje can ta shirmenki, kullum ai cikin karatun littafi kike, tashi ki karata ta
samu Napep”

Rukayya ta mike tsaye har lokacin dariya take, sai da ta shiga ta aje wayar ta sako
hijabinta sannan ta fito tana gyara talkamin kafarta.
“Mu tafi yar gidan Gwaggo, ke ko kishinki bata yi sai fada take min ban raka
kishiyarta ba”

“To idan ma ba yar wuta ba, wace kishiyar ce zata yi kishi da Hurriya baiwar Allah,
kifi musulmin nama”

Hurriya ta yi dariya, ita kanta Gwaggo dake maganar dariyar ta yi, kamin ta raka da
addu'a, Amma kuma ta bita da kallo tana dan murmushi kadan. Tare suka isa da
Rukayya har titi suna tafe suna hira, Rukayya sai tambayarta take wai halin Hajiya
Kaltume na nan ko ta daina.

“Me zata daina kuwa Mama Rukayya ni dai arzikina, daya bana gidan yanzu duk wani
abun da zata fada ko ta yi ba zai shafe ni ba”

“Wallahi kin huta, ai kara da Hajiya Binta ta dauke ki, kika rabu da wannan bakar
kalwal mai bakar zuciya”

Hurriya ta kalleta tana murmushi.

“Amman dai Mama Rukayya wasa kike so? Hajiya fa mahaifiyar Yaya Yasir ce”

“And so what? Ke baki ga yadda ta maida Amma ba? Ta mallake Appanku baya jin
maganar kowa sai nata? Ni fa da zan samu sa'arta sai na dauko fansar duk abun da ta
yi mana, saboda tana tsaye nan a makoshi?”

“Toh kuma ki yi Yaya da Yaya Yasir?”

“Wai ke ina ruwanki da Yasir din ne? Ke fa wata rana kamar munafuka haka kike”

Hurriya bata san lokacin da dariya ta subuce mata ba.

“Mama Rukayya ke dai yi a hankali, dan kin san Yayana fa, shi yake zane mu idan
muka yi laifi”

“To ni sai ya dake ni? Ke yarinya kama kanki, ai ko kirana yayi ban daga ba sai kin
ga yadda hankalinsa yake tashi, idan kuma ya zo ya karbi wayata ko ya gan ni da
wani ya fara kishi kenan, ni Rukayya i no dey carry last, haba ni ba halin Amma ne
da ni ba, kowa ya ce min kule chasss zan ce masa”

A karo na barkatai Hurriya ta yi murmushi, ta tsayar da mai napep ta shiga bayan ta


fada masa unguwar da zai kaita.

“Toh Allah ya tsare, damo sarkin hakuri”

“Amin Mama Rukayya na gode”

Mai napep yaja suka dauki hanya. A bakin gate ya sauke ta ta ba shi kudinsa sannan
ta shiga cikin gidan, tana yin arba da daya daga cikin motocin da mahaifinta ya fi
yawan hawa gabanta ya yanke ya fadi, tun a nan ta fara rage tafiyarta, hakalimlnta
be tashin ba sai da ta kunna kai cikin falon ta yi arba da Hajiya Kaltume da
Appanta, Hajiya Binta kuma tana zaune saman kujera.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

2⃣2⃣ 2⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞2⃣2⃣ 2⃣

“Hurriya an dawo”

Far'ar da Hurriya ta gani a fuskar Hajiya Kaltume lokacin da take fadar haka ya fi
daga mata hankali fiye da ganinsu da ta yi a gidan. Cikin rashin kuzari da faduwar
gaba ta karasa kusa da Hajiya Binta ta zauna a kasa, sannan ta mikawa Appa gaisuwa.

“Lafiya Kalau”

Ya amsa ba tare da ya kalleta ba, Hajiya Kaltume na murmushi tana kallon Hurriya
irin murmushi na murnar ganinta, bayan kuma a kasan zuciyarta ba haka ba ne.

“Hajiya Ina wuni?”

“Lafiya Kalau mutan aljanna, an dawo? Tun dazun muke nan ai, Hajiya ta ce kin tafi
duba Iyami ya jikin nata”

“Tana jin sauki?”

“Sosai?”

“Eh”

“Maa Shaa Allah...”

Ta kasa cewa Allah ya bata lafiya, saboda hausawa suna cewa addu'ar fatan alheri ta
makiyi karbabbiya ce, wai idan yayi maka sai an karba. Hurriya ta juya a hankali ta
kalli Hajiya Binta dake zaune fuska ba yabo ba fallasa.

“Hurriya an dawo?”
“Eh Hajiya sannu da gida”

“Sannu dai yar Albarka, kin yi Sallah?”

“Aa ina tahowa ne aka yi kira”

“To tashi ki shiga ciki ki yi Sallah ki”

Hajiya Kaltume ta ce

“Ai da ta bari sai mun tafi sai ta yi sallah a can”

“Babu inda Hurriya zata tafi, ai na fada miki tun da ya koreta ta dawo nan kenan
idan kika ga ta bar gidan nan to bana raye ne”

A take Hajiya Kaltume ta saka kukan munafurci.

“Haba Hajiya yanzu duk hakurin da muka yi ta baki baki hakura ba, ita dai Hurriya
na san bata da matsalar komai kuma ko yanzu zata so komawa gidan ubanta domin babu
kamar gidan uba a duniyar nan”

“Nan da take ai daji ne, da bata da alaka da kowa, ke ni kar nake ganinki, halinki
babu wanda ban sani ba Kaltume, tun kina da kurciyarki har yanzu da kika yi yaya,
saboda na aika muku da shi ne kika taso mijinki gaba kuka ta so wai azo a kalailaye
ni da dadin baki a tafi da Hurriya ku karasa kasheta a can ko?”

“Wallahi ba manufata kenan ba, ni taya zan ce na kashe rai balle kuma Hurriya haba
Hajiyaba zan iya aikata haka ba, kawai maganar da kika fada mana ne, na lura da
haka ya kamata na yi kasancewa uwa, a wacan lokacin idona ya rufe ne ni da Alhaji
shiyasa har ya koreta, ni kuma na kasa dakatar da abin amman na bashi hakuri
Hajiya, ita kanta da zata fadi gaskiya ta sani”

Cikin kuka Hajiya Kaltume take maganar da hawaye shabe shabe a fuskarta. Kukanta ya
bata ran Appa har yayi sanadin da ya watsawa Hurriya wani kallo daya saka ta sauke
idonta kasa da sauri.

“Hajiya, ki yi hakuri haka ba zai sake faruwa ba”

“Ba fa zata koma ba, daman can ni bana son zamanta a gidan nan, ba za a kula da ita
ba yadda ya dace, gashi ba iya magana take ba fa ma Hamad ne shi ne mai iya magana
da fadar abun da aka yi har ma ya rama, amman ita ba zata fadi komai ba, ko a
lokacin da aka ce taje ta yi gulmarka a wani guri ai be kamata ka yarda ba, domin
idan akwai wanda ya san halin Hurriya ciki da waje a duniyar nan kai ne, yadda ta
shaku da kai bata shaku da mahaifiyarta haka ba”

Appa ya sauke kansa kasa har lokacin hakuri yake badawa yana neman yafiyar Hajiya.

“Ni na yafe maka amman tabbas da baka zo ba kam, ina nan rike da wannan abun a
raina kuma ba zai maka dadi ba saboda ni uwa ce, ko ban fada ba idan raina ya bace
zaka iya gani a al'amurranka ko a jikinka ma”

“Toh a yafe min Hajiya hakan ba zai sake faruwa ba, kuma dan Allah ki bar mu mu
tafi da Hurriya”

“Ba za a tafi da Hurriya ba, idan ka ga ta bar gidan nan to a dayan biyu ko dai ta
yi aure ko kuma na mutu”

Hajiya ta sake fashewa da kuka, ita kanta Hurriya ta tsorata da yadda Hajiya take
son komawarta a gidan har da hawayenta. Cikin kukan Hajiya Kaltume ta kalli Hurriya
data kasa tashi a gurin da take zaune ta ce.

“Subhanallahi, ki yi hakuri dan Allah, kuma ki sak baki Hajiya ta hakura ita ma,
wannan maida magana baya da ake ba shi da dadi, takas mahaifinki ya zo saboda ya
tafi da ke, dan Allah ki yi hakuri Hurriya”

Hajiya Binta ta yamutse baki.

“Hurriya bata da ikon kanta, ikonta yana gurin mahaifinta da mahaifiyarta sai kuma
ni, dan haka ki daina saka Hurriya a cikin maganar nan”

Hajiya na fadar haka Appa yayi karaf ya kalli Hurriya ya ce.

“To idan haka ne, Hurriya ina baki umarni a matsayina na mahaifinki ki koma gida
cikin yan'uwanki, idan ba haka ba zaki yi mamakin abun da zai biyo baya...”

Appa na gama fadar hakan ya kalli Hajiya Kaltume ya ce.

“Tashi mu tafi”

Sannan ya mike tsaye, Hurriya ma ta mike tsaye da sauri, cikin karfin hali na tsufa
Hajiya Binta ma ta mike tsaye ta rike hannun Hurriya.

“Hurriya ba zata koma ba, gaba daya ka canja tsoho ta ya zan yi umarni kuma ka yi
kokarin karya wannan umarni? Anya kana cikin hayyacin Tsoho?''

Ya kada kansa kasa.

“Hajiya ba umarninki nake kokarin karyawa ba, bana son zaman Hurriya a ko'ina sai a
gida, sanin kanki ne tun kamin yau kin ce na baki ita ban baki ba, saboda bana son
kowa ya rika min da”

Hajiya Binta ta masa wani kallo na tsanaki, shi kuma ya ki yarda ya daga kansa ya
kalleta sai yawo yake da idon a kasa. Tun tashinsa har girmansa bata ba shi umarni
ya tsaba sai a yanzu, ba kuma yanzu ta yau ba, yanzu da girma ya cin masa ita kuma
take gangarawa. Ko a lokacin da ya saki Iyami babu yadda bata so ya dawo da ita ba
yaki, yanzu kuma saboda Hajiya Kaltume ta sako shi a gaba ya zo a maida Hurriya
yake wannan bubutan.

“Kai ma haihuwarka aka yi, kamar yadda ka haifi Hurriya idan baka yi hankali ba,
kai ma sai na baka umarnin da idan ka saba ba zaka ga da kyau ba”

Hajiya Kaltume ta kama gafen mayafinta tana share hawaye tare da mikewa tsaye domin
ta lura ran Appa ya bace kamar yadda na Hajiya Binta ma ya bace har ta fusata.

“Ba za'ayi haka ba, ba ta kai ga haka ba, Alhaji mu tafi, tun da Hajiya na zon
zaman Hurriya a nan ka barta ta zauna Allah ya bada hakurin zama”

Appa ya kalli Hurriya sai da hantar cikinta ta kada ta fara kokarin zare hannun
Hajiya Binta a hannunta, ba kuma dan komai ba sai dan saboda Hajiya Kaltume, sannan
ya dan risina ya ce.

“A tashi lafiya Hajiya”

Hajiya bata amsa masa ba bata ce masa komai ba har ya fice, kana ita ma Kaltume ta
yi ma Hajiya sai da safe ka roki gafararta sannan ta fice. Sai a lokacin Hajiya
Binta ta zauna ranta a jagule.
“Hajiya dan Allah ki yi hakuri ki bar na tafi, kar na kawo rudani tsakaninki da
Appa, ko kuma Appa yayi fushi da ni kamar yadda ya fada”

Hajiya bata kula hawayen Hurriya dake saukowa ba ta daka mata tsawa.

“Ke rufe min baki nemi guri ki zauna babu inda zaki je, gaba daya sun canja masa
kwakwalwarsa, idan yace ya yafe ke ni ma sai na yafe ki, idan takamar yana da kudi
yana kula da ni, ai ai ba haka ya tashi yana ciyar da ni ba, Allah ke min komai”

Hurriya ta duka tana kallon Hajiya bi ta data koma ta zauna.

“Idan kika samu tsabani da Appa saboda ni, zai kara wutar kiyayyata a zuciyarsa ne,
kuma zai tsine min domin baya a cikin hayyacinsa a yanzu, da ba ke ma ba zai tsaba
umarninki ba, idan kika yi fushi da shi ba zai ga da kyau ba, idan kuma hakan ta
faru da shi, ke da mu abun zai shafa, domin ke uwarsa ce babu yadda zaki da danki
sai hakuri, mu kuma yayansa har kasa ta hade bamu da wanda ya fi shi, amman matansa
za su iya gina kansu har su manta da shi, wuya bata kisa Hajiya, kuma duk yadda
suke nufina da sheri Allah zai kareni, ina jin tsoron fushin iyayena akaina, yardar
Allah tana tare da yardar iyaye, mahaifiyata bata da lafiya kuma bana kusa da ita,
ki fahimta Hajiya su suke su raba ni da Appa, dan Allah karki bari haka ta faru, ki
yafe mishi ki sauko daga fushin ki yi hakuri na koma...”

Hawaye ya zubo a idon Hajiya Binta, kalaman Hurriya na hankali sun ratsa
kwakwalwarta, sai ta saka hannunta biyu da tsufa ya canja musu halittar fata ta
rike fuskar Hurriya.

“Ke yata ce ta gari Hurriya, kuma kamar kore kamar kumbonsa, barewabata gudu danta
yayi rarrafe, kin fi duka Yaya da Tsoho ya haifa hankali da hangen nesa, karamar
yarinya mai kwakwalwar manya, Allah ya miki albarka, na barki na barki ki koma
gidan ki zauna, zalinci baya dorewa kuma da yardar Allah sai kin fi su albarka, sai
sun koma karkashinki sai rayuwarki ta dawo tana burgesu, ki shirya gobe zan saka
direba ya kai ki, kuma zan biki da addu'a, zan rika zuwa ina dubaki”

Hurriya ta lumshe ido tana kwantar da kanta a hannun Hajiya binta hawayenta na
sauka a tafin hannun kakarta. Ita kanta bata son komawarma amman ta lura kamar wani
abu suke shirya mata kuma suke son hada mata ita da mahaifinta shiyasa suka har
Hajiya Kaltume ta nace sai an koma da ita.

“Kin fadi gaskiya, Tsoho be taba musa ba sai a yanzu ta aka cire masa kowa a
zuciyarsa, yau a gaban matarsa nake cewa ba za'ayi ba yace za'ayi Allah mai girma”

Hajiya Binta ta sake fada tana hawaye. Hurriya ta bude ido ta kalleta

“Daman na yi tunanin haka Hajiya, saboda kin fadawa Yaya Namra sakon da zata fada
musu, suna ganin kamar kin zafafa sona ne akan na kowa, ita kanta Yaya Namra ta
fada min bakar magana, gaba daya a munafuka suke kallona ganin suke kamar zan iya
hada ki da Appa ne, Allah kadai ya san fushi da Appa zai yi da ni akan wannan, ni
kaina ina tunanin zafafan da Appa yayi ne a kaina ya saka suka raba ni da shi,
hawayen nan kuma Hajiya dan Allah ki share su kar wani abu ya sami Appana”

“kin yi tunani kuma na yaba da hankalinki, daman ina masa addu'a kuma zan kara, zan
dage, ke ma kuma zan cigaba da yi min kuma ba zan zauna haka nan sai na nemi
maganin tsari kala kala na baki, daga kuma karki sake wasa da addu'a Allah ya miki
albarka”

Hajiya Binta ta share hawayenta, tare da bawa zuciyarta.

*** *** ***


A mota babu kalar wutar da Hajiya Kaltume bata hurawa Appa a zuciyata akan Hurriya,
har tana fadar Hurriya ta hada shi da Hajiya gashi nan har ta yi fushi gashi kuma
ta hana Hurriyar komawa.

“Ni daman abun da nake ta ji ma tsoro kenan, nan gaba kuma ba san me zata kulla ba,
yarinya karama ta zama munafuka. Ko yanzu karka yarda ka barta a can idan ba haka
ba, Hajiya sai ta tsine maka nan gaba, amman karka sake waiwayar gidan sai idan ta
huce”

Kwafa kawai Appa yayi be ce komai ba har suka isa gida.

WASHE GARI.

I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma
zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba,
na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba
tare da biya ba na barku da Allah...!

Misalin karfe goma sha biyu na rana 12:00pm Captain ya shigo gidan, ya bude
tsadadiyar motarsa ya fito ipod a kunnesa yana magana cike da gadata, shi alaka
dole ga soja, kuma jinin sarauta ga kuma naira, shigar kananan kaya ce a jikinsa
kamar yadda ya saba, domin abu ne mai wahala ka ga Captain Da Shadda sai idan wani
abun ya taso. With little strong ya hau entrance din ya murda kofar falon Momy ya
shiga, hakan nan dai ya ji yau baya ra'ayin yin sallama even though ba fushi yake
ko bacin rai ba, haka kuma ba cikin farinciki yake ba, not happy not sad. Kulu na
ganinsa ta mike tsaye ta sauri tana kallonsa bakinta da jikinta suna rawa saboda
kwarjinsa, abu mai wahala ka yi arba da shi baka ji tsoro da fargaba ba, musamnan
idan haduwar farko ce, ba kuma tsoro na wanda zai maka wani abu, kwarjini da yake
da shi da murufa ta tsananin mazantaka da zakantaka ya wuce ka lalleshi baka ji
kwarjinsa ba, balle kuma ace ka san yadda yake da saurin fushi da tsananin fada
kamar gawurtaccen zaki.

“Sannu da zuwa Sannu da zuwa...”

“Yauwa sannu ya gida ya aiki?”

“Lafiya Kalau Yallabai”

Ya dan juyarta da kai yana kokarin yin murmushi

“No ki kira ni da Captain ko Jameel that's my name, amman wani Yallabai Yaya ko
ranka da ya dade old fashion ne, bana so. Ina Momy?”

“Toh toh na tuba, carpet bari a kirata tana sama”

Ya runtse ido saboda yadda ta sauya masa suna saboda rashin iya pronouncing din. Ta
haura sama da sauri, sanin kanta ne ba a shiga dakin Momy kai tsaye idan ba ita ta
kira mutum ba, musamman masu aiki, dan haka ta fara ya da zango a dakin Namra ta
sanar mata domin ita kuma ta sanar da Momy. Sannan ta sauko da saurinta kamar zata
fadi.

“Na fadawa Namra zata fada mata yanzu”

“Na gode”

Ta fice da sauri tana amsawa da babu komai, ai aikinta ne. Namra ce ta fara sauko
da far'a jin cewar dan'uwanta ya dawo kamin Momy ta biyo bayansa tana masa lale
marhabun.
“Yau kuma an sake ziyararmu, sannu da zuwa dana”

Sai a lokacin ya zauna yana murmushi da murna arba da yar'uwar mahaifinsa kuma mace
mai tsakanin kaunarsa fiye da kowa a familynsu.

“Momy ya gida”

“Lafiya kalau, yanzu ka dauki wata bakar dabi'a da ba zaka fada min yaushe zaka zo
ba sai dai na gane ka kawai ko? Balle na shirya maka wani abu”

“Ni kaina bana sanin zan biyo ta nan sai dai na biyo kawai, kuma idan ina ra'ayin
wani abu ai zan iya kira na fada miki”

“Captain sannu da zuwa”

Namra ta fada sannan ta nufi kitchen.

“Ya aikin? Yanzu ka dawo nan kenan? Yaushe ka dawo kasar wai?”

“Just two days ba, shi ne suka sake kawo ni nan na yi wata biyu zuwa uku sannan na
koma gida”

“Kaduna za a maida kai kenan?”

“Yeah na dade ina yawo, so yanzu fitar da na yi waje da kuma sa hannun Daddy, za a
bar ni Kaduna na zauna a nan, amman idan aikin ya taso na wasu garuruwa zan tafi mu
yi, akwai aikin da ban karasa ba nan Gusau kuma kin san tana ta kokarin a magance
matsalar tsaron nan shiyasa aka dage sai na dawo”

“Maa Shaa Allah, Allah ya taimaka gashi nan ka yi Fresh ka kara samun lafiya”

Yayi murmushi tare da kallon Namra data aje masa abun tabawa a mini center table
dake gefen kujerar daya zauna.

“Maganar aure dai shi ke nan ka watsar da ita Captain”

“Zan yi aure Momy dolena”

“To na tsorata da lamarinka fa, wacan ma ana daf da daura aure komai ya lalace kuma
tun daga lokacin baka sake gabatar mana da kowa ba”

“Bata min rai ta yi da yawa, taya ana daf da daura aurena zaki yi chat da wani
saurayi har ya daukeki ku fita, ni fa ina da mugun kishi da zai iya sakawa na kashe
mutum, bana iya daukar irin wadannan abubuwan, idan ina son mace ko kallonta bana
son ayi”

Ya aje ayar maganar tare da daukar lemun da Namra ta aje masa ta sha. Momy ta yi
murmushi.

“Toh Allah ya bada ta gari, yasa kamin ka bar garin nan ka samu wanda kake so, kuma
ya rage maka wannan fushi idan ba haka ba zaka yi wahalar zaman aure”

“Amin”

Ya amsa yana dauke fuskarsa da murmushi tare da shan lemun a hankali. Namra ma ta
yi murmushi tana taba wayar hannunta kamin ya dago ta kalleshi.

“Yauwa Captain wai a ina ka san Salim?”


Ya juyo ya kalleta.

“Salim Sarauta, abokina ne sosai tun a jami'a muke tare, ke ina kika san shi?”

Ya daga kafada tana dan zare ido kadan kamar wanda ta rasa abun cewa.

“A hanya muka hadu, ya nuna yana so na daga baya kuma ya koma gurin Hurriya,
shiyasa na kai shi gidan ma har ka ganshi, amman ban san me ka fada masa ba na ga
yanayinsa ya canja kuma har yau be sake kirana ba”

Captain yayi murmushi kasaita murmushin dake kara masa kyauta da haiba

“Ban fada masa komai ba, maybe dai ita ta bata masa rai, na je karbar abu ne na
gansu tare, amman karki sake kai shi gurinta, haka yake duk garin da yaje sai yayi
budurwa, musamman idan ya ga mai kyau ce just like your sister....”

“Hum himm”

Ya dan kalli Momy kamin ta sake kallonsa dan amsa masa tambayarta.

“Ina yarinyar take ta dawo?”

Momy zata yi magana Namra ta yi karaf ta tari numfashinta ta ce.

“Eh tana dakinta”

Ya maida dubansa gurin Momy fukarsa shimfide da murmushi yayi mata godiya.

“Thank You Momy, ko wace mace ta fi daraja da martaba a gidan iyayenta ko mijinta,
kuma a matsayinki na uwa daman haka ya kamata ki yi”

Ya dubansa gurin tsadaden agogon hannunsa sannan ya mike tsaye.

“Ya kamata na tafi kar na bata lokaci”

Momy dake mamaki yadda Namra ta yi masa karya ta ce.

“Nan da nan, baka wani dadewa”

“Yanayin aikin ne a haka, wai Musib har yanzu ba su dawo ba?”

“Suna da daf da dawowa, muna waya da su ai”

“Good”

Ya nufi kofar fita falon, Momyda Namra suka mike tsaye domin yi masa rakiya. Yana
bude kofar da zimmar fita Hurriya ta dake rike da kofar tana murdawa da zimmar
shigowa, dayan hannunta kuma yana rike da luggage ta sake naushin kirjinsa da kanta
daidai saitin zuciyarsa, a karo na biyu by mistake. A take daga hannun sama saitin
fuskarta. Kamin hannun ya kai fuskarta ta yi saurin lumshe idanuwanta dake cike da
yalwatacce gashin ido ga kuma na gira da ya kara masa kyau a sama, ta dauke
numfashinta tana jiran jin tafin hannunsa a fuskarta.

“Yarinyar bata da hankali komai a haukace take yinsa”

Kalaman Momy da kuma jin shiru babu mari babu alamarsa a fuskarta ya saka ta bude
ido a hankali pink lips dinta suna motsawa kamar zata ce wani abu. Hannu ta gani a
tsaye saitin fuskarta ba tare da ya kai hannun a fuskarta ya mareta, kuma be sauke
hannun ba, haka zalika be dauke idonsa daga kallonta ba, kamar yadda fuskarsa take
daure saboda abun da ta yi masa. Da sauri ta duke kasa ta ratsa gefenta ta shige
falon har Luggage dinsa na dukan kafarsa, abun da ya kara bata masa rai. A lokacin
ne ta tuna cewar shi ne mutumen da ya taba marinta.

“Yi hakuri”

Ya ta fada tana kara matsawa baya da sauri domin jin take kamar zai iya rikota yayi
mata hukunci ne, gashi babu Hamad mai rama mata. Ya sauke hannu ya juyo sai dai ba
ita ya kalla ba, Namra ya kalla.

“Why do you lie?”

Ta dan yi baya kadan ta rasa yadda zata wanke kanta, Momy ta kalleta sannan ta
kalli Captain ta already ya fice har yana kokarin rufe kofar. Sannan ta juyo ta
watsawa Hurriya harara

“Kin dawo ko? To shiga ciki ki zauna, gida kam na ubanki ne amman ikonsa nawa ne
domin bangarena ne”

Hurriya ta sauke kanta ta juya tare da taja kayanta ta haye sama. After ta shige
Momy ta kalli Namra ta ce.

“Me yasa kika yi haka? Namra ki daina yin abun da zai saka Captain ya tsaneki fa”

Ta dan cize baki cikin yanayin damuwa ta ce.

“Ban dauka zata shigo yanzu”

“Ki kiyaye next, domin ni ban ki kum fahimci junanku ba har ya kai ku ga aure, ko
ranar da ya bar gidan nan sai da muka yi magana da Ammy, akan ke da shi, amman
saboda lura da hankalinku baya kan juna ya saka ba ma son matsawa, kuma ko da babu
irin wannan be kamata kina haka ba be careful...”

“I will...”

Ta amsa tare da kallon kofar kamar mai tunani, tare da saka hannunta tana taba
wuyanta. Momy kuma ta nufi upstairs cikin matukar bacin rai.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

2⃣3⃣ 2⃣
𝐏𝐚𝐠𝐞2⃣3⃣ 3⃣

Tana tsaka da cire tufafinta a luggage Momy ta turo kofar dakin ta tsaya daga wajr
tana kallonta.

“Mun ga sakon da Hajiya da ta aiko mana akanki, kuma mun gode ke ma kuma zaki ga
irin nawa sakon, mahaifinki yayi gaskiya gidansa ni da ke duk muna karkashin
ikonsa, amman nan bangarena ne ina da nawa rules and regulations, dole kuma ki
kiyaye domin ba bangaren Iyami ba ne”

Hurriya ta sauke kanta ba tare da ta cewa Momy komai ba, ganin haka ya saka Momy ta
bar kofar a bude ta nufi nata dakin. Ajiyar zuciya Hurriya ta sauke ta dafa
goshinta.

“Allah ka kara min hakura zama a gidan nan, kowa da kallar tsanar da yake min”

Ta sake aje numfashi mai karfi sannan ta cigaba da cire tufafin ta jera a closet ta
aje luggage din gefe ta cire hijab dinta ta saka talkaminta ta fito daga dakin. Ko
da ta sauko babu kowa a falon kai tsaye ta nufi kofa ta bude ta fita. By this time
ta san cewa mahaifinta baya a gidan sai idan wani abu ya dawo da shi ko kuma ya
hana shi fita, dan haka Hajiya Kaltume uwargida, nan ma sai da ya ki bacin ranta da
take ganin za a cusa mata, ta bawa zuciyarta hakuri ta danne duk wani abu da zata
ji tun gabanin su fada mata, sannan ta tura kofar ta shiga. Sukan na su falon a
cike yake suna ta murnar dawowar Salma, sai dai ganin Hurriya ya saka sun tsaya cak
suna kallonta kamar irin wanda aka jefo daga sama daga gabansu.

“Hurriya”

Hajiya Kaltume ta fada da mamakinta karara a fuskarta.

“Na'am Hajiya ina wuni, Yaya Khairy Yayana, ina wuni yaya Salma sannu da zuwa”

Salma ta amsa tana kokarin boye munafurcinta a cikinta.

“Lfy kalau”

Yasir kuma ya ce.

“Lafiya Kalau kanwata, na jidadin da kika dawo, Hajiya kin yi abun da ya dace”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi, wani abun da ya bawa kowa dake falon mamaki ciki har
da Hajiya Kaltume da ita kanta Hurriya shi ne tashin da Khairy ta yi ta koma kusa
da ita ta rumgumeta tana far'a.

“Alhamdulillah, Allah ya kawar da bacin rana na jidadin da kika dawo, I'm so happy”

Hurriya ta kalleta har tana rasa abun furtawa, mamaki ya lake mata a zuciya.

“Ina taje ne ake ta murnar dawowarta?”

“Abubuwa da yawa suka faru Salma sai kin zauna zaki sha labari”
Khairy ta amsa bayan ta saki Hurriya.

“Ni ma fa ina da labarin da zan baku, kuma dukansu sai mamaki ya kama ku”

“Mamaki zai wuce ki ce kin samu wanda kike so zaku yi aure soon bla bla bla ni ma
aurar da ni Hajiya take kokarin yi fa, ga Fadeel kin san shi ai dan Hajiya Fatee”

A yanzu ma Khairy ce ke amsawa Salma tana dorawa da zancen auren dake ci mata rai.
Da mamaki Salma ta kalli Hajiya ta ce.

“Da gaske Hajiya? Fadeel ba yana da mata ba?”

Hajiya ta daga mata kai.

“Yana da mata amman kirkinsa ne ya saka nake son ba shi auren saboda ya nuna yana
son Khairy”

Yasir ya mike tsaye daman shi ba gwani ne na sauraren irin wadannan maganganun na
mata ba, dan haka ya kalli Hurriya.

“Muje waje Hurriya ina son magana dake”

Hurriya ta juya ta nufi kofa, tana gaba daya bayanta, sai da suka fice sannan Salma
ta kalli Hajiya Kaltume ta ce.

“Har yanzu yaya ganin mutuncin yarinyar yake yi?”

Khairy ta tabe baki.

“Hmmm me za'a fasa kwanan baya saboda yarinyar nan ya lalata min birthday”

“Amman hugging dinta kika yi yanzu fa, kina murna dawowarta”

“Toh ai Salma idan baka iya kama barawo ba sai barawo ya kama ka, kara ina haka
idan ba haka ba wani abun na samunta nan gaba za a iya cewa ni ce”

“Nikam i can't fake love, shiyasa wannan kawar tawa ma na ja mata kunne”

“Wace kawa wai?”

Salma ta gyara zama tana kara fitar da sauti saboda labarta musu abun da ta kumso.

“Hmmm Appa be fada muku zai kara aure ba?”

Sai a nan Hajiya Kaltume ta yi murmushi mai sauti ta ce.

“Ya ma isa Salma? Duk bayan wahalar da muka sha, ga tarin tashin hankali da
munafurci da ba mu gama fuskantarsa ba saboda Nafisa da Iyami? A yanzu kuma da ya
kamata ace ina da ikon gida ya tunkare da zancen aure? Haba wa..... Ba dai shi ba
sai idan wani kuma ko kuma idan na mutu”

“Hajiya wannan fa ba wasa ba ne, abu ne da na gani da idona, and she's my friend
muna daf da kare karatun nan take suka hadu, tana da va ni labarinsa but ban dauka
Appa ba ne sai yau da muka sauka airport”

Hajiya Kaltume ta karkata da kyau tana kallon Salma dake magana with full
confidence.
“Motar da ta dauke ta ma daga Airport ta kaita gida, Appa ya kawo, ban kara yarsa
shi din ba ne har sai yau da ta fada min cewar shi ne mamallakin Yadi's Motors”

“Ho... How... How... Comes....”

Cewar Khairy tana kallon yar'uwarta.

“Boye min ta yi, amman ta fada min cewar yana da mata biyu ya saki 3rd wife dinsa
yana da yaya maza hudu dayan ya rasu, yana da yan mata bakwai, amman na zama wata
sakarai da ban gane ba har sai a yau da ta fada min wai sunan wanda take son ta
aura Alhaji Haruna Mai Yadi, and she was telling me shi ya aiko da motar nan a
dauke ta”

“Amman baki mareta ba? Ta fa san mahaifinki ne?”

“Ban mareta ba, amman na fada mata zata jefa kanta a matsala ne kawai dan haka ta
rabu da mahaifina tun wuri, ni babu abun da ya fi bata min rai ma kamar yadda na
zama sha sha ban fahimci mahaifina ba ne har sai da ta fada min, bayan kuma ita din
ta sam cewa mahaifina ne domin sunana Salma Haruna Mai Yadi, and the most annoying
part is yarinya ce kamar ni sai barikin tsiya”

Hajiya Kaltume ta girgiza kai.

“Aa ni dai ban yarda da wannan ba, ko dai akasi aka samu ko kuma wani abun ya hada
su take zaton sonta yake, amman ni na san dalilin da ya saka mahaifinku ba zai kara
aure ba, kuma idan har zai kara din zan riga kowa sani”

Salma ta yi dariya.

“Okay idan baki yarda ba, zan baki duka nunbers dinta ki saka a wayar Appa, ko kuma
ki kawo ni na saka ko Khairy ko kuma ki yi wata dabara mu duba Instagram chat dinsa
dan na fi kyautata zaton nan suka hadu”

Khairy taja tsaki.

“Ni Wallahi wannan auren auren na Appa yana damuna, daman tun da na ga gidan nan da
part hudu na san yana da burin karo wata, kuma yanzu Fisabilillahi ace sa'ar yarsa
kawarta ma? Haba...!”

“Wannan burin ada ne ba, ba yanzu ba duk wacan rayuwar ta kau, ku kwantar da
hankalinku babu wani aure da zai kara, ni ban ma yarda zancen aure ne tsakaninsu ba
ko soyayya”

Cewar Hajiya Kaltume tana murmushi, sannan ta mike tsaye yana fadar.

“Yanzu dai an huta yar'uwar shawara ta dawo, sai ku shirya duk abun da kuke ganin
ya dace, zan sanarwa Appanku kamin Iyayen Fadeel din su zo”

“Hajiya Fadeel dai? Yana da mata fa? Kuma kin san yadda sherin kishiyoyi suke tun
da muna cikinki”

Taku kadan Hajiya Kaltume ta yi ta dafa kafardar Salma fuskarta da murmushi.

“Kyakkyawar makoma ake buri, bana fatar kowa ya sake yin irin auren da Maama ta yi,
tana can yana gana mata azaba, matarsa ba matsala ba ce domin Hajiya Fatee bata
sonta, kuma saboda matarsa take son ya auri Khairiya saboda Khairiyyah ta share
mata hawayenta, fata muke kamin ma ta shiga cikin gidan matarsa ta fice”

“Idan ta fita kina ganin Khairy zata iya rainon yayanta? Kuma yadda Hajiya Fatee ta
tsani matarsa zata iya juyowa ta tsani Khairy fa...”

Khairy ta kada kai kamar kadangaruwa domin an taba mota gurin da yake mata
kaikaiyi.

“Shi nake kokarin nunawa Hajiya ta gagara ganewa, ni har yanzu Fadeel din nan be
kwanta min a rai ba”

“Ku yara ne ba zaku gane ba, gaba nake hango muku Hajiya Fatee kuma bata isa ta
tsani Khairy ba har abada, kar ta san kar ne ni da ita, kuma ba ido zan zuba mata
ba, tun kamin a tafi ake shiri ba sai an dawo ba, dan haka ki kwantar da hankalinki
Khairy ki saki jiki ki saka kaunar Fadeel a ranki”

Salma da Khairy suka kalli juna kamin su kalli Hajiya su saka dariya, ita kuma ta
yi murmushi ta fice ta bar musu falon, su suna dariyar ta kasa fahimtarsu kuma duk
yadda take ganin abun zai zo da sauki ba zai zo, ita kuma tana murmushin abun da
take hango ma Khairy wanda ta kasa ganewa.

“Hajiya ba zata gane ba”

Salma da har lokacin dariya take ta ce.

“Ina fa, kin ga ko maganar Appa musawa take yi, kuma Wallahi gaskiya ne, haka ta yi
a auren Maama tana cewa tana hango mata jindadi ne saboda yana da kudi gashi nan
yanzu kullum da kalar azabar da yake nuna mata, last week na muna chat take fada
min yanzu har mata yake kawo mata a gida idan ta fita”

“Kullum fa iskancinsa gaba yake, ni ba zan ma iya daukar wannan iskancin da yake
mata ba, ita kuma kamar an mata magani ta kasa rabuwa da shi”

“Ni kaina ba zan iya ba, kuma wai Hajiya ta kyaleta sai iskanci yake ma mutane
yadda ya ga dama”

“To ya za'ayi idan ace za a masa magana ita take shiga ta tare, kar a taba mijinta
wata kila sai da ya mallaketa sannan ya aureta”

Salma ta tabe baki ta sauka daga kan kujerar ta zauna a kasa.

“Ke ba ni labari ya aka yi Hurriya ta bar gidan?”

Sai da Khairy ta kalli kofar falon dan tabbatar da Yayansu ba zai shigo ba sannan
ta fara bata labaran abubuwan da aka yi bata gidan.

HURRIYA POV.

Jerowa suka yi suna tafiya yana ta yi mata nasiha a matsayinsa na yayanta.

“Wallahi Yaya duk yadda kuke tunanin abun yake ba haka ba ne, ni bana munafurci ko
zancen Abban su Husna ni da ita kawai na san na yi magana kuma maganar karatu kawai
muka yi sai take ce min lokaci yana kurea na fada mata Appa nake jira, ban san
yadda aka canja zancen ba abun har ya kai mahaifinta ya samu Appa da maganar”

“Wacan ya wuce, komai ya wuce yanzu kawai ina jan hankalinki ne akan rayuwa, duk
wani abun da kika san zai janyo miki magana ko ya bata tsakaninki da mutane ki
daina kuma ki gujeshi, ina yabonki Hurriya shiyasa idan aka fadi cewar kin yi wani
abu nake musawa ko na yi mamaki saboda na san ba halinki ba ne, dan Allah ki natsu
ki daina duk wani abu da be dace ba”

“Ba zan sake ba Yaya ba zaka sake jin an fadi wani marar dadi kaina ba na maka
alkawari”

“Yayi kyau, in kin shiga ciki ki ce ina gaishe da Momy”

“Toh Yayana na gode”

Ta wuce ciki shi kuma ya juyo ya dawo bangarensu sai dai be shiga ciki ba ya shiga
motarsa ya bar gidan. Sai da Hurriya ta maida kofar falon ta rufe sannan ta lura da
Husna dake zaune akan sofa tana sanye da farar abaya. Da gangan Hurriya ta dauke
mata kai zata wuce Husna ta yi saurin riketa tana dariya.

“Fushi kike yi da ni saboda ban zo ba kwana biyu?”

Hurriya ta cire hannunta daga jikinta fuska a daure ta ce.

“Ba saboda haka nake fushi dake ba, ina fushi da ke ne saboda kin hada ni da
iyayena, abun da kike yi sam be dace ba Husna saboda na yarda dake na saka nake
fada miki sirrina ashe fitarwa kike gashi nan kin yi sanadinyar da Appa ya koreni a
gidan nan yau na dawo, kuma kowa a gidan nan yanzu ya tsane ni yana min kallo da
munafuka”

“Innalillahi ni kuma, dan Allah ki tsaya mu yi magana ta fahimta Wallahi ban yi


miki wani sherin ba, kuma mahaifina be zo gidan nan da wata manufa ba, dan Allah mu
tafi dakinki mu yi magana...”

Hurriya ta tsaya kallonta kamin ta gyara tsayuwar gilashin idonta ta nufi stairs,
Husna ta rufa mata baya, dakin suka shiga suka rufe sai after sun zauna Hurriya ta
fada mata abun da ya faru.

“Innalillahi, Wallahi Hurriya ba ma ni na fadawa mahaifinmu ba, Umma ce ta fada


masa kuma ita ma ta yi hakan ne saboda tana tausayinki, su a nufinsu idan Appa ya
amince sai su dauki nauyin karatun har ki kallama ganin kamar ba a son ki yi
karatun, ni ma kuma ban san suna da wannan manufar ba sai bayan sun aikata Umma
take fada min wai Abba ya samu Appanku da maganar be amince ba, sun ma yi rabuwa
marar dadi, dan Allah ki yi hakuri kar ki mi dawowa fahimta baibai, ban shigo ba
shiyasa ban san abubuwan da suka faru ba”

Hurriya ta sauke ajiyar zuciya, daman ta raya a zuciyarta cewar kawarta ba zata
aikata mata wani abun da zai jefata a damuwa ba da ganganci.

“Amman Hurriya ke da kika samu komawa gidan Hajiya meyasa kika dawo nan?”

Nan ma sai da Hurriya ta fada mata abun da ya faru, ciki kuwa har da rumgumar da
Khairy ta yi mata a yau.

“Eh gaskiya kara da kika dawo, kuma ko yanzu ki yi taka tsantsan, saboda su ya saka
bana son yawaita shigowa gidan nan, yanzu kuma gashi kin fada min abun da ake
kallonki da shi kuma na san ni za a kalla a matsayin mai tayaki”

“Su suka sani, ai Allah yana shaidata”

“Haka ne, kin ma san abun da ya kawo ni wai?”

Hurriya ta girgiza kai tana kallon Husna.

“Wani abokin yaya ne yace kin san shi sunansa Salim ya ce min har kun yi magana
amman ya rasa ya zai shawo kanki, shi ne ya zo jiya saboda ya gan mu tare lokacin
da kika je gidan kuma ya tambayi Yayana ya fada masa ni kawarki ce sosai, tare da
Yaya ma suka saka ni a gaba wai yana son na lallabaki na karkarto da hankalinki ki
fahimce shi, shi ba da yaudara ya zo ba...”

Hurriya ta mike tsaye ta dafe kanta tana yawuta a dakin.

“Ni kam na shiga uku, mutumen so yake ya ballo min wasu ruwan kuma? Yaushe na samu
na rabu da Adam shi kuma ya kuso yana son haddasa min fitina, na yi magana da shi
na fada masa cewar ni bana sonsa kuma fa ma Yaya Namra yake so daga baya ne ya dawo
guna”

“Duk ya fada min, amman yace ke ce baki fahimta ba, ko kuma yayarki ce take son
bata lamarin amman shi tun farko ke yake so, kuma Hurriya ni fa ina ganin idan da
gaske yake kuma aka bincika yana da halin kwarai sannan aka dace kina sonsa kawai
ki aure shi ki huta da wannan gidan, albashi idan zaku yi aure sai ya miki
alkawarin zai barki ki yi karatu”

Hurriya ta dawo ta zauna.

“Ni be min ba, kuma na fada masa gaskiya wata kila ma saboda shi ne na ga Yaya
Namra ta canja min, sai ta yi zaton ko ina kokarin kwace mata saurayi ne, kuma fa
tana son shi, ni gaskiya bana sonsa ni babu ma wanda nake so yanzu”

“Shi kuma yana sonki sosai Hurriya da ace zaki ba shi dama dai zaki saurareshi, ya
ce min ma zai zo gobe”

“Dan Allah kar ya zo kar ya hada ni da mutane, ki fada masa kar ya zo dan Allah,
Husna kin san halin da nake ciki ki fahimtar da shi mana”

Ta karasa tana cikin son yin kuka idonta na tara ruwan hawaye.

“Zan yi magana da shi, zan fada masa yadda zai fahimta, yanzu ya maganar karatunki”

“Ni dai yanzu ki tashi ki tafi kar ace na shigo da ke a daki muna gulma”

Husna bata da wani aiki a yanzu da ya wuce ta taimaki kawarta dan haka ta mike
tsaye ta yi mata sallama, cikin tsoro Hurriya ta raka falo, hankalinta be kwanta ba
har sai da Husna ta fice. Sannan ta dafa zuciyarta kamin ta sauke hannun ta koma
dakinta, sallah ta yi ta fito falon ta zuba abincin rana ta ci.

**** **** ****

Karamin filo ne a hannunta ta rumgume shi sosai a kirjinta, kalaman da Momy ta fada
mata dazun take tunanin, suna kokarin dorata a wani tsani da bata taba hawa ba,
zancen ana son su fahimci juna ita da Captain ta tsaya mata a rai. Yana da kyau da
za a so shi, yana da cikar halitta da duk wani abu da ake so a jikin namiji, sai
dai ganin yadda tsarin rayuwarsa yake ya saka bata taba ayyana ma kanta kaunarsa ko
sau daya a zuciyarta ba. Ta dago ta kalli wayarta dake ringing ganin sunan Salim ya
saka ta dan yamutsa fuska kamar ba zata daga ba, can kuma ta kai hannu ta dauka.

“Hello”

“Namra ya gida, ko da yake yayarmu ya kamata na ce”

“Haka fa, lafiya kalau ya aiki?”

“Alhamdulillah, alfarma na kira na roka kamar yadda na saba yi, kanwar nan taki dai
na kasa hakura da ita, na gwada ko zan iya amman na kasa”

“Toh yanzu kuma me zan yi?”


“Lallaba min ita zaki yi, yau ma zan shigo gidan kuma tare da dan'uwanki In Sha
Allah”

Har zata tambaya ta ce wani dan'uwanta sai kuma ta ji bata bukatar hakan, domin ya
nuna ba ita yake ra'ayi ba, dan haka be kamata ace ta shiga hancinsa ba.

“Okay zan yi kokari, amman daga wannan ba zan sake ba gaskiya, baka fada min ya
kuka kare ba a wacan karon”

“Idan na zo zamu yi maganar”

“Okay”

“Thanks”

Ta cire wayar kunnenta tana hautsina fuska, kamar zata ji haushinsa kuma sai take
ganin babu dalilin haka. Aje fillon tayi ta sauko saman gadon,

‘Babu wani lalaba ta da zan yi, yarinya ta nuna vata yinka dole ne, ai maganin
namiji mai shegen ruwan ido kenan da son mata’

Ta fada a ranta kamin wasu zantunka su fara zagayar kwakwalwarta, yanzu da Momy ta
fada mata kudirin da suke da shi akansu ita da Captain sai take ganin wata kila
canja mata ne Allah zai yi da son Salim da ta fara, ya bata wanda ya fi shi komai,
dan murmushi mai kyau ne ya kawata fuskarta, ta mike tsaye ta nufi kofar dakinta ta
bude sai da ta shiga dakin Momy ta duba bata ciki sannan ta sauko kasa domin ta san
idan bata dakinta to tana kasa ko bangaren mahaifinsu ko kuma ta fita daga gidan.
Tun kamin ta karasa saukowa stairs ta ji fadan da Momy take yi ma Hurriya har da
rantse rantsen abun da zata mata idan ta sake zuwa kai tsaye ta bude mata kuloli ta
zuba abinci.

“An gama abinci ban zubawa mijina ba, ni ban zuba ba sai ke ki zuba ke gaki
issashiya ko? To ba zan daukar miki wannan ba, daga yau sai yau karki sake bude min
kula ki zuba abinci ki jira sai na diba, ai na fada miki nan ba bangaren Iyami ne
ba, wannan rashin tarbiyar da kuke ni ba zan dauke shi ba”

“Ki yi hakuri Momy, hakan ba zai sake faruwa ba”

Hurriya ta fada cikin muryarta mai sanyi, dake nuna tsantsar nadamarta. Momy ta
sake daka mata tsawa.

“Idan ma ya faru ke ce a matsala domin kanki zaki jawa bala'i”

Hurriya ta ji kamar ace zata iya gyara komai kamar bata taba ba, amman ba dama
domin mai afkuwa ta afku, cikin tsananin damuwa ta nufi stairs tana tambayar kanta.

‘Wai haka ko wace ya take fuskarta matsala a gurin kishiyoyin uwa, ko kuma ita ce
ta fita dabam?’

Bata da mai amsa mata tambayarta kamar yadda ita ma bata san amsar ta ba. Namra ta
bita da kallo har ta haye sannan ta sauko.

“Abinci ta zuba?”

“Eh saboda iskanci da rainin wayo, ni kaina ban zuba ba amman ta zo ta bude warmers
ta zuba abinci”

“Wani sabon iskanci ne ta kirkiro kuma yanzu?”


“Oho mata ita zata sha wahala ai”

Momy taja kujera ta zauna, Namra ma ta ja nata kujerar ta zauna, sannan Momy ta
fara zuba abincin.

A bangaren Hajiya Kaltume kuwa tana shiga dakinta ta dauki wayarta ta kira, Malam
rashin samun wayarsa ya saka ta kira kawarta.

“Ikon Allah, hausawa suka ce dan halak kaki ambato, yanzu fa nake son kiranki na
tambaya size din Khairy na talkami”

Hajiya Fatee ta fada daga dayan bangaren bayan ta amsa wayar kawarta Hajiya
Kaltume.

“Hmmm ai ni wani abun ne na ji da ya so daga min hankali, kuma dai be daga ba


shiyasa na kiraki”

“Me ya faru?”

“Wai anya baki tunanin Malamin nan yana tayar da aikin da muke ba shi ne saboda ya
bukaci wani abu?”

“Ah touh Hajiya na ga cikin nan naki fa an kwantar kuma ya kwanta daga baya abu ya
tashi, har kika ce ya bukaci wani abu agareki, ni na ma manta ban tambayeki me ya
bukata ba”

“Hmmm wannan maganar kuma ai ta wuce Hajiya Kaltume ciki kuma ya koma ya kwanta
yadda ake bukata, ke dai yanzu me sa kika kira ni kuma me ya daga miki hankali
tukuna bari mu ji na ki”

“Salma ce ta dawo dazun, bayan ta huta take min hirar wai mahaifinta yana son
kawarta”

“Maa Shaa Allah Salma an dawo? Hajiya miye abun mamaki a maganar? Maza ko uwarki
aka ce su aura ai aurenta za su yi, balle kuma kawar yarsu, ke maza fa ba su da
kunya, ina ce Iyami ma ai yarinya ce kuma ya aureta ko kin manta”

“Amman ke Hajiya baki yi mamaki ace Alhaji yana zancen aure a wannan lokacin?”

“Daman namiji mai son aure aure ai ba zaka iya hana shi ba, halinsa ne ke dai yanzu
ba kin mallake shi ba ai duk wanda ta ji zata iya kawai ta zo”

“Aa, ina tunanin na gama da komai sai kuma wannan ya taso, na bar shi yayi aure ya
kwaso mana wata ita ma ta zo ta hana mu zaman lafiya? Kuma tace zata zuba nata
yaya? Ai kara ma Iyami da wannan yarinyar da take karama sa'ar Salma fa kuma
kawarta, ni ban gama yarda ba shiyasa hankali yake kwantawa wani bangare, kuma na
kira Malam wayarsa bata shiga ba, sai dai kuma ina mamaki idan har gaskiya me yasa
Malam be fada min ba? Bayan kuma yace duka aikin da yayi yana bibiyarsa duk lokaci?
Ko dai ya kwance kullin ne shiyasa har haka take shirin faruwa”

“Hajiya ki kwantar da hankalinki, idan ma ya kwance aiki wata kila akwai abun da
yake bukata ne kamar yadda yayi min, sai ki ba shi karki zo ganin yadda yake min
aiki a yanzu, ko jiya sai da ya bani maganin da zan saka a nama yanka tara na bawa
Fadeel ya ci, kuma tun kwanan baya da ya fara min aikin nan Wallahi na fara ganin
gaske, domin yanzu gidana yake cin abincin dare, na safe kawai yake ci a can shi ma
kuma na san ya kusa dainawa, ga maganar auren nan har zumudi yake a yanzu ba kamar
da ba”

“Idan kuwa haka ne, ai babu adalci a ciki, bayan ya fada min yanzu babu kowa a
zuciyar mijina sai ni, sai kuma ace ya kwance aiki, idan ma wani abun yake so sai
ya fada kai tsaye ba sai ya kwance ba”

“Ina ganin zai fi kyau ku yi magana da shi ki ji koma minene, ni kam Wallahi sai
sam barka, yanzu har jinsa nake kamar wani dan'uwana”

“Zan yi magana da shi”

“Okay, kamin ki manta minene size Khairy”

“Hajiya zan saka ta turo miki daga baya, yanzu kam bana iya gane komai”

“Kar fa ki saka kanki a damuwa, komai zai warware”

“Ina fatar haka...”

Ta sauke wayar da tunanina kala kala a ranta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Tun da Hurriya ta shige dakinta bata fito ba, har Magariba, bata son Momy tace ta
mata wani abun ba daidai ba dan haka ta kebance kanta a dakinta, da dare ma bata ci
abincin dare ba saboda bata fito ba, ta inda ta samu sa'a abincin da ta ci na rana
be yi saurin narkewa ba, dan haka bata kwana da yunwar rashin cin abincin dare ba.
Da asubar fari ta farka ta yi sallah sannan ta dora da karatun kur'ane har sai da
rana ta fito sannan ta yi azakar ta hau gadonta ta koma bachi.

Tara da rabi ta sake farkawa, a kasale ta sauka saman gadon ta shiga bandaki ta
wanke bakinta ta yi wanka sannan ta fito ta shirya cikin bakar atamfa mai ratsin
blue. Ta dora dankwalin a kan gado ta zauna gaban madubi ta gyara gashin kanta ta
yi farkin dinsa a baya, sannan ta shafa hoto kadan abun da ba al'adarta mai ma dan
ya zame mata dole ne take shafawa, amman a yau da yake ranar jumma'a ce ta ji tana
bukatar yin kwalliya. Ta dauki turare ta mai kamshi ta fesa, sannan ta dauki man
baki zata shafa sai ta tuna karyawa zata yi, hakan ya saka ta mayar ta aje ta koma
saman gadonta ta kwanta tana duba agogo dakin dake nuna karfe goma daidai. Sai dai
duk da haka bata son fita ta karya a yanzu ba dan bata jin yunwa ba sai dan bata
son tsaba dokar Momy, sanin kanta ne Momy bata karyawa da wuri idan ta fita ta
taba abun da Momy ta aje ba tare da Momy ta ci ba bata san iya hukuncin da zai biyo
baya, dan haka ta kara minti talatin akai sannan ta fito kanta a sake babu dankwali
gashin kanta sai sheki yake. Masu aikin Momy kawai ta samu a falon dayar na kallo
dayar kuma na saka turaren wuta.

“Dan Allah Momy ta gama breakfast dinta?”

“Wane breakfast kuma Hurriya breakfast tun yaushe har an wanke komai, na rana ma
kadan ya rage a gama”

Hurriya ta ji babu dadi.

“Dan Allah Inna Shatu idan kuka gama abinci ku rika zuba min nawa dabam, ba sai an
hade da na gida ba”

“Toh Hurriya”

“Yauwa na gode”

Ta nufi hanyar Kitchen kamin ta karasa ta ji muryar Namra a stairs tana kiranta.

“Me zaki yi a Kitchen Hurriya?”

“Tea zan hada”

“Saboda jindadi ko saboda me?”

“Ban samu breakfast ba, shi ne zan hada tea”

“To ki jira abincin rana ya kusa karasawa ai, idan yayi sai ki ci, kin san baki
karya ba kika je kika kwanta kina ta bachi any how”

Namra ta karasa tare da isowa daidai gurin da Hurriya take tsaye. Hurriya ta sauke
kanta ta juya domin barin kofar kitchen din.

“By the way Momy tace karki sake shigar mata kitchen idan kina bukatar wani abu ki
yi magana, ba wai ki shiga Kitchen haka kawai dan jindadi ki ce zaki hada tea ba”

Hurriya ta juyo ta kalleta ta cikin gilashinta duba mai kyau.

“Amman Yaya Namra nan gidan ubana ne, ina da iko da komai kamar yadda kike da shi,
me yasa kuke kyarata ne? Me na yi muku?”

Mamaki ya saka Namra rike baki.

“Ni kike fadawa wannan maganar?”

“To ya kuke son na yi ne? Na zuba abinci a jiya Momy tace kar na sake zuba abinci
idan bata ci ba, yau ina jin yunwa amman haka na wuni a daki saboda kar na fito na
tararda bata gama karyawa ba, yanzu kuma na fito Inna Shatu tace an wanke komai,
yanzu kuma zan hada tea ki ce ba haka ba, ko dan saboda jindadi zan iya hada tea
Yaya Namra balle kuma ban karya ba”

Tana maganar hawaye na sauko mata. Inna Shatu ta aje kaskon wutar dake hannunta
tana fadin.

“Abun be kai haka ba, tafi dakinki bari na hada miko tea din, ai da magana kika min
sai na hada miki ma ba sai kin shiga ba”
A take Namra ta tsaka rantsuwa.

“Wallahi tallahi ba zata sha tea din nan ba, ke har kin isa? Ki fada min magana?
Ina yayarki? Okay yanzu da kika dawo wani sabon rashin kunyar ne kike dawo da shi
ko? Har kina wani tutuyar gidan ubanki, uban da baya sonki? Uban da be damu dake
ba, uban da ke da banza duk daya a gurinsa?”

“Kamin nan na yi gatan da wata ya a gidan nan bata yi ba, mahaifina ya so ni fiye
da kowa a gidan nan, rayuwa ce ta sauya saboda bata tafiyarwa kowa a yadda ta saba
ba, kamar yadda bata tafi min a yadda na taso ba? Sai aka sauya min da wata
kaddarar mai daci, kuma hakan ba yana nufin zan tabbata a ciki ba, kar wannan ya
zama abun gori a gurinki Yaya Namra, domin ke ma baki san a ina rayuwa zata kai ki
ba, babu wanda ya san gobensa, kamar yadda ni ma ban san ya GOBENA zata kasance ba,
dukanmu muna tafiya ne akan RAI BIYU ran farinciki da kishiyarsa, a WANI GARI
rayuwa kaddara zata sauke mu na gaba? Babu wanda ya sani, na sani ni a yanzu tawa
kaddara baka ce kamar BAKAR WASIKA, amman ba zan dauwama a haka ba...”

Bata daina kuka ba kuma bakinta be yi burki ba har sai da ta fashe kurjin dake mata
ruwa a zuciya, sannan ta juya ta nufi stairs, har ta shige dakinta Namra bata gama
mamakin inda ta samo baki haka ba.

“Amman zata aikata tun da ta iya munafurci zata iya aikata wannan ma ba mamaki, tab
aiko kin dauko tuwa dafa kanki”

Ta shiga Kitchen ta dauko plantain, har ta yi aikin soyawa ta gama bata daina
mamakin yadda Hurriya ta fada mata magana kao tsaye ba.

“Ji take ta yi sa'a da ni, saboda ya girma kuma Salim ya nuna yana sona ya koma
gurinta, sai take jin ita ma ta kai mace.. To yarinya da sauran kuma na gode Allah
da zai musanya min da ni, domin da ace CIWON SO ya kama ni na wannan Salim din da
Allah kadai ya san yadda zata kalleni ma”

“Wacece ke da ya kamata ki maida hankali ki yo ki gama, kina nan kina shiririta ko?
Kuma kin fi kowa sanin halin Captain zai iya fushi yace ba zai ci ba, balle ma ya
fada min da bako zai zo gidan nan”

Momy ta tambaya tana tsaye kofar kitchen din, mundayen zinarin dake wuyan hannunta
suna amo. Namta ta juyo ta kalleta.

“Bako kuma?”

“Haka yace amman be fada min ko waye ba”

Namra ta dan kalli gafe tana tunawa da maganarsu da Salim a jiya, and if she guess
it right Salim ne bakon kenan, domin Captain ya fada mata alakarsa da shi.

“Uhmmmm wahalalle”

“Wa...?”

A tsawace Momy ta tambaya tana mata wani kallo sakaka. And that's was the moment da
ta yi realize bata fayyace ko waye ba.

“Wani tunanin nake yi dabam ba Momy ba Captain ba, na isa? Haba ko hauka nake ai ba
zan fara ce masa haka ba”

“Good”

Sai a lokacin Momy ta numfasa kamin ta bi miyar da Inna Shatu ke zubawa a karamin
kula.

“Wa kike zubawa miya Shatu? Ko kun fara satar nin har da abinci kuma?”

“Subhanallahi, Wallahi ban taba ba, Hurriya ce idan zan zuba abinci na zuba mata
nata dabam”

“Saboda me?”

“Toh Hajiya yanzu kuma ni na ce wani abu? Sai dai ki tambaye ta”

“Karki sake raba abincin mu da ita, salon da saka mana wani abu a abinci ko kuma
saboda ita ta fi wani neda za a ware mata abinci, ban da ma rainin wayo idan
Hurriya ta fada miki abu sai ki yi? Waya dauke ku aiki? Babu sisin mahaifinta a
cikin biyan masu aikin gidana, juye miyar nan tun wuri”

“Toh Hajiya”

Ta juye miyar ta aje kular ta fice. Anan ne Namra take bata labarin abun da ya faru
tsakaninta da Hurriya.

HURRIYA POV.

Yadda ta yi spending Night and Morning dinta a dakinta haka ta zauna a dakinta har
la'asar, saboda tana gudun ta sake fitowa ta sake yin arba da wani abun bakinciki,
kukan kan ta sha shi kamar shi ne last hope dinta. Ta rumgume yunwa, bakiniki kuma
yayi mata rumfa a zuciya, bata ji zata iya fita ba har sai da yunwa ta yi ta kawo
mata farmaki ta hana ta shakat ta hana ta zaman lafiya balle kwanciyar gado lafiya.

Sai da ta hada da karfin hali sannan ta iya Sallah la'asar saboda jikin nata babu
kwari ko kadan, tana sallamewa ta dauko kur'ane ta karanta suratul Kahafi ta yi
addu'a ta maida kur'anen a muhallinsa sannan ta dawo gaban madubi ta zauna tana
kallon kanta, fuskarta har ta yi rama saboda azumin dole da ya kamata tun jiya har
yau da yamma.

Siraran hawayen da suka zubo mata ta share sannan ta dauko hoto ta shafa a fuskarsa
saboda boye abokin rayuwarta wato kuka, sannan ta ta shafa man lebe kadan, ta tashi
ta dauko dankwalinta ta daura daidai yadda zai tsaya akanta ta karya karin
dankwalin da kyau irin daurin Zarah Buhari, ta sako gashin kanta data daure ya
sauko a gadon bayanta hakan kuma ba karamin karawa daurin nata kyau yayi ba, ta
gyara gilashinta, ba dan komai ta yi haka ba sai dan karawa kanta courage, and tana
jin she deserves to live a happy life kamar sauran sa'aninta balle kuma a yau da
yake rana ta musamman wato jumma'ah even though zuciyarta na cike da damuwa da
kunci, kuma kwalliyarta zata boye kukan da ta yi. Bata saka talkamin da suka saba
sakawa idan za su saka kasa ba a haka ta nufi kofar dakinta ta bude idonta cike da
tsoron arba da Momy ko Namra, ba dan tana jin yunwa sosai ba ba zata sauko ba sai
dai bata da wani zabi da ya wuce ta bawa cikinta da jikinta abun da suke bukata.

Ta dan rika skirt dinta ta dage shi kadan saboda ta samu sauka stairs din cikin
jindadi, hakan kuwa sai ya bawa kyawawan kafafuwanta kuma farare fes damar bayyana.
Tana hango falon da mutane gabanta ya buga da karfi, maza ne biyu da bata ga
fuskokinsu ba, sai Momy da Namra dake falon, ganin babu sarki sai Allah ya saka ta
cigaba da takawar without making any sound domin babu talkamin a kafarta, hakan
kuma sai ya taimaka mata babu wanda ya lura da saukowarta har sai da ya rage sauran
taku biyar ta sauka.

Kusan a tare Captain da Salim suka dago suka kalli stairs din dake hagu da inda
suke zaune, sai dai sun samu tsabanin aje idonuwansu a mabanbanta muhalli a jikin
Hurriya, Salim ya tafi kai tsaye gurin fuskarta, yayinda Captain ya fara sauko
idonsa a kan zarazaran yastun kafarta sirara masu matukar kyau zuwa leg dinta
slowly ya bi kasanta da kallo zuwa gurin da Salim ya dade da yada zango wato
fuskarta, Subhanallahi ba zai ce be taba ganin mata masu kyau ba a duniya but
Hurriya is different tana da wani sirritacce kyau mai jam hankali maza zuwa gareta,
wato kwarjini yana fisgar zuciyar wanda duk yayi arba da Innocent face dinta, tun
daga kan daurin dankwalinta har bakar atamfar dake da ratsin blue, zuwa gashin
kanta da ya bayyana, da yadda gilashin idonta ya daidaita a fuskarta, kaf babu abun
da bata yi masa kyau ba.

(Mace mai sirhirtaccen kyau ba ana nufin sai mai kyau ba, aa wasu ma ba su suka
kyau ba amman Allah yayi musu kwarjinin da maza suke sonsu, balle kuma ayi sa'a
kwarjin ya hadu da dan'uwansa kyau, ko kuma kudi, ko farinjini, sai namiji yayi
kamar zai haukace akanki yayi ta nan da nan da ke, abu ne mai wahala ko a taron
mutane ka ga an wulakanta mace mai kwarjini, ba kuma dole sai mai kudi ba, wani ko
talaka ne zaku ganshi da kwarjini, wani kuma an hada masa duka, kudi, kyau,
farinjini, kwarjini)

Salim ya mike tsaye yana kallonta.

“Sauko mana Hurriya”

Momy da Namra suka dago su ma dan bawa idanuwansu abincin. A take zuciyar Hurriya
ta raya mata saboda ita ya zo, ko kuma saboda Yayarta Namra amman yanzu da ya ganta
yake kokarin bata shirinsa, ga kuma mutumen dake kuss da shi mutumen nan ne da ta
bugewa kirji a jiya har ya so ya mareta, daman kuma ya taba dandana mata zafin
hannunsa dan haka bata manta ba, ga kuma Momy da Namra da bata san iya hukuncin da
zata karba a gurinsu ba idan wani abun ya faru. Juyawa ta yi da sauri ta koma tana
hada taku biyu uku na stairs din duk wani rashin karfi da yunwa sai suka kau a
lokacin, a tafiyar da za a iya kiranta da gudu ta haye sama ta shige dakinta ta
rufe ta saka key.

*** *** ***

“Salim zauna mana”

Kamar mai jiran umarnin Captain sai ya koma ya zauna ya maida idonsa a kasa.

“Yarinyar nan fa bata shirya magana da kai ko saurarenka ba, jiya babu yadda ban
lallabata ma amman sam bata ba ma saurareni ba balle har ta fahimci me nake fada”

Namra ta fada tana kallon yana yanayinsa ya can sauya duk kuwa da irin kokarin da
yake na ganin ya boye damuwarsa.

Captain ya kallesa ya fara magana calmly.

“Ita soyayya ba a mata dole, idan bata ra'ayinka karka ce sai ka cusa kanka da
karfi a gurinta, kuma ni ban ga wani dalili na son a biyo mace ama lallabata ta so
mutum ba, ni dai har ga Allah ban ga yarinyar da zan iya yi ma wannan ba, kuma ba
zan taba ganin ta ba har abada, yanzu ma saboda ka fada min da gaske kake yi kuma
kana sonta sosai shiyasa har na yarda muka zo tare, amman dan ina da alaka da ita
ko ba zan iya saka wani abun ba ko na hanata”

“Allah ma ya tsareka da hada alaka da wacan yarinyar”

Daga Salim har Captain kallon Momy suka yi sai dai babu wanda ya ce komai. Momy ce
ta fara mikewa tsaye.

“Bari mu baku guri ku ci abinci”


Namra ta bi bayanta suka haura sama, haka Salim ya bi abincin da aka jera musu ga
kuma plate din plantain da Captain ya saka hannu ya dauki daya.

“Ni zan tafi Captain, bana jin zan iya cin komai kuma sai da na ci abinci sannan na
fito, ya kamata na tafi”

Ya mike tsaye tare da kallon ledodin dake gefen kujerar da suka zauna.

“Ka shigar mata da wannan”

Captain ya dan motsa baki irin na wanda ya rasa abin cewa, ya bi Captain da kallo
kamin ta mike tsaye ya bi bayansa.

HURRIYA POV.

Kofar windows dakinta ta tsaya tana kallon kasa, har lokacin gabanta be daina
faduwa ba arba da ta yi da Salim da kuma mutumen da har yanzu bata san sunansa ba.
Each seconds sai ta juya ta kalli kofar dakinta tana jiran ta ji ko za a kwankwaso
mata ace ta fito, gashi idan Momy ce ba ta isa ta ki fitowarba, hankalinta be
kwanta ba sai da ta hango fitowar Salim, ta yi baya baya kadan daga windows din
gudun kar ya ganta, sai kuma ta ga mutumen da yake tare da shi a dazun ma ya fito.
Da sauri ta bar jikin window din ta cire dankwalin kanta ta jefar a gado ta bude
kofar ta sauka kasa ita a nufinta ta samu abun da zata sakawa cikinta kamin ta su
dawo ko kuma a cilasta mata fitowa a dakin da take da niyar shiga ta rufe kanta.
Ganin babu kowa falon ya saka ta taka a hankali ta leka Kitchen nan ma babu kowa,
ta dawo dinning har ta fara bude warmers sai kuma wata zuciyar ta raya mata cewar
za a iya ganewa ita ta ci abincin ganin ba a taba shi ba, a take ta rufe ta dauki
plate daya ta nufi abincin da aka jerawa baki ta zuba white rice ce da ta ji green
beans da carrots sai pepper soup din hanta da aka yanka kanana kuma aka saka kaza
sai kamshi take, ga plantain da aka soya. Komai sai da ta zuna, Jin kamar motsi a
sama wato stairs ya saka ta dauke plate din tana kallon stairs din ta watsa da gudu
kitchen ta rufo kofar.

Ta aje plate din a tana auna abincin da hannu biyu, idan ta ci da dama sai ta ci da
haka bata ma tsayawa ta tauna burinta kawai ya kai ga cikinta kamin asirinta ya
tsonu. Wani irin kuka ne ya tunkaro da ya fi karfin duk wani kokari nata na son
hana kanta kukan saboda tausayin kanta, a take ta fashe da kukan marar sauti hawaye
shar kamar magudanar ruwa. Kamar daga sama ta ji an bude kofar kitchen din tana
kallon kofar suka yi ido hudu da Captain da shigo a zatonsa Momy ko Namra ce a ciki
saboda ya ji karar rufe kofar a daidai lokacin da ya dawo falon.

Baya baya ta yi shimkafa a duka hannayenta guda biyu ga kuma bakinta ma cike da
wata shimkafar ga fuskarta da ruwan hawaye suka yi mata ado, ka a ganinta ka san a
firgice take. Be plate din da be gama zaunawa ba ne ya fado kasa saboda jikinta ya
tana plate din kadan a lokacin da take yin baya baya, a take plate din ya fado ya
fashe a kasa..

“Waye a kitchen waya fasa plate....?”

Namra dake saukowa ta tambaya domin ta ji karar faduwar plate din na Momy mai
tsada. Hurriya ta dauke numfashi da mugun karfi saboda tsoro. Captain yayi baya
kadan ya leka falon ya amsawa Namra.

“Ni na fasa”

“Subhanallahi Allah yasa baka ji ciwo ba?”

Ta sauko da sauri, sai amsa kamar yadda ya saba amsawa mutane magana wani lokacin
da bakar magana musamman idan baya son a shigar masa sabga.

“Na ji ciwo kin san ai yaro ne ni...”

Tana jin haka bata karasa gurin ba, sai kawai ta yi murmushi tana masa wani kallo
har lumshe ido take.

“Allah ya baka hakuri”

Ta juya ta fara hawa sama domin sanar da Momy abokinsa ya tafi Captain ne kawai.
Sai da ta haye sama sannan ya juyo ya kalli Hurriya a take ta hade sai ta zubar da
shimkafar a kasa ta hade hannayenta biyu waje daya ta daga su tana masa godiya tana
kukan da ba shi da sauti sai hawaye. Kamin ta duka zata fara kwashe breaking plate
din.

“Zo ki wuce”

Ya fada yana matsa daga jikin kofar ta yadda zata samu hanya. Ta dago ta kalleshi
ta girgiza kai

“Idan Momy ta gan ni a kitchen dinta sai ta kusa kasheni tace kar na sake shiga”

Tana fadar haka ta mike tsaye ta nufi kofar baya ta bude ta fice. Juyawa yayi ya
fice daga kitchen din kai tsaye ya nufi stairs ta nufi dakin Momy direct, yana dora
hannunsa a jikin kofar zai murda kunnuwansa suka jiyo masa wani sauti na Momy da
Namra yana fita.

“Wani sabon iskanci ya taso mata ba? Ai Wallahi sai na hanata numfashi a idan nan,
saboda tana ganin tana da kyau dole maza su fara binta ganin take yi tana daidai da
ni yanzu”

“Daman laifin na waye ne Namra ba naki ba, ki rika jan yarinya a jiki matsayinku ma
ba daya ba, uba kawai kuka hada balle kuma yanzu da take munafurci, gashi har ta
samu bakin fada miki magana, da yaran Kaltume me da yanzu ba su sumar da ita ba,
shiyasa ai bata yarda ta zauna a bangaren Kaltume ta shan wuyar da take sha a
hannunsu”

Cewar Momy tana mikewa tsaye. Namra ta ce

“Ko a nan sai na zahira ya fita jindadi, ai na riga da na gane halinta a yanzu”

Slowly Captain ya dauke hannunsa a kofar ya juya ta fara sauka ba dan ya gama jin
komai ba, sai dan baya bukatar jin wasu abubuwa da yawa a yanzu, daman he just want
to talk to her akan Hurriya ya ji ko laifi ta yi Momy take mata hukunci da wannan.
Be karasa sauka ba Momy ta bude kofar dakinta ta fara saukowa Namra na bayanta.

“Captain...”

Ta kira sunansa da mamaki ganin ya rage few steps ya sauka. Sai ya juyo ya kalleta.

“Haurowa ka yi? Wani abun kake bukata ne?”

“No da zan shigo ne sai kuma na ce bari dai na tafi kawai”

“Sorry Namra ta fada min kana falo ban fito da wuri ba, abokin naka ya tafi?”

“Yea ya tafi”

Ya sauka ya tsaya a daidai inda suka zauna dazun tare da Salim, Momy ma ta sauko
tana fadin.

“Ai da ma zaka ba shi shawara ya fita safgar yarinyar nan, wani rashin mutunci ne
take ji yanzu, ko da yake ni ban ki ta samu miji an mata aure ta bar bangaren nan
ba”

Kamin Captain yace wani daman kuma ba shi da niyar fadar wani abu akan maganar.
Hurriya ta turo kofa ta shigo falonta ta kofar da ake shigowa, bayan ta bata lokaci
a Garden ta wanke hannunta a fanfo da fuskarta. Gaba dayansu dubansu ya koma kanta,
tana isowa tsakiyar falon ta kalli Momy sai kuma ta yi saurin kauke kai kasa ta
nufi hanyar stairs.

“Ke zo ki dauki abincin nan idan zaki ci”

Captain ya fada in a game way, yana binta da kallo, ita ma juyowa ta yi ta kalleshi
kamin ta kalli Momy dake kallonta.

“Zo ki dauka mana”

Ya saka fada ganin tana jiran umarnin Momy, Namra ta yi karaf ta ce.

“Domin ku fa aka yi?”

“To ai shi ya tafi be ci ba, kuma ni ma a koshe nake maybe next time”

Hurriya na jin haka ta dawo ta duka a gurin ta dauki plate ta zuba rice din sai
karamin bowl ta zuba miyar sai da tsame rabin naman kazar dake ciki miyar sannan ta
dauki cup ta zuba fresh apple juice da Namra ta hada ta dauki wani plate din ta
zuba plantain duk abun da ta zuba wanda ta san zai isheta ne har anjima, sannan ta
dauka ta mike tsaye.

“Na gode”

Ta furta with sweet voice dinta tana musa laɓɓanta masu kyau. Sannan ta nufi stairs
sai da ta kusa haye sannan ta juyo ta kalleshi ta juya ta cigaba da tafiyarta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
“Baka dai ci abincin ba”

Ya kalli Momy yana saka hananyensa aljihu.


“Abokina ya tafi ransa a bace, taya zan zauna ni na ci abinci? Maybe next”

Ya kalli Namra dake tsaye ya kira sunanta. ”Namra”

“Hmmm”

“Be a good girl please”

Ta yi murmushi mai kyau.

“I will as always”

Ya mayar mata da murmushi sannan ya juya ya nufi kofa, da kansa ya bude ya fita
Momy ta take masa baya ita da yarta. Momy na nade hannayenta ta aika masa tambaya.

“Sai yaushe kuma Captain”

“Anytime kina iya ganina ma anjima, ai yanzu ina garin nan har na tsawon wata uku
kuma ina tunanin wannan ne best place da zan iya zuwa na yi yadda nake so, ba kamar
a bariki ba”

“Me yasa ba zaka dawo nan gaba daya ba?”

“Ban sani ba ko za a su bar ni zan gwada haka”

Ya bude motarsa bayan ya amsawa Namra sannan ya shiga yayi mata key, Momy na daga
masa hannu Namra kuma ta bishi da kallo da murmushi har ya fice. Momy ta juyo ta
kalleta.

“Wata kila ya jidadin yadda kika karbi bakonsa a yau”

“Ni ma na ga alama”

“Yayi kyau”

Momy ta fada tana murmushi sannan ta sauke kai kasa ta juyo cikin tafiyar kasaita
ta shiga falonta. Namra ta dade a gurin tana ta karatun wasikar jaki kamin ita ma
ta juya ta koma ciki. Hurriya ta ci abincinta yadda take so, sauran ta saka dayan
plate din ta rufe domin idan ta tashi ci anjima ba ta nema ba, kusan ita da
marainiya duk daya agidan, wata kila ma marainiya ta fita gata da samun kulawa.
Hakan ya taimaka mata bata fito neman abincin dare, shimkafar ta sake ci da dare ta
kwanta abunta. Da safe ma bata fito gudun kar ta yi wani laifin ko kuma Momy ta
rufe ta fada saboda ta zuba abinci da yawa ta kwashe nama, tana zaune a dakin har
karfe goma na safe, tana unkurin tashi ta yi wanka aka turo kofar falon aka shiga,
da sauri ta kalli kofar tana zaton ganin Momy ko Namra ga mamaki sai ta yi arba da
Khairy.

“Yaya Khairy”

“Na'am Hurriya yanzu kika tashi?”

“Tun dazun amman ban sauko ba sai yanzu”

“Kin yi breakfast?”

“Aa”

“Ni ma ban karya ba, zo muje mu karya bangarenmu, idan mun gama ina son ki rakani
wani gurin kin ji”

Ta dan yi shiru kamar mai tunanin yadda zata amsa mata kamin ta daga mata kai.

“Okay”

Ita kam gaba da ta kai ta ko ba komai zata karya, ba kamar jiya ba, already ta san
Momy ko masu aikinta za su ce mata abincin safe ya kare kamar jiya, gashi kuma bata
isa ta ce zata shiga kitchen ta girka ba ko ta saka a girka mata. Dan haka ta sauko
saman gadon suka fice a dakin tare da Khairy, kamin su isa bangaren Hajiya Kaltume
Khairy ta kama hannunta ta rike tana bata labarin guraren da za su da kawayenta da
ta kwana biyu bata hadu da su ba. A dinning suka zauna ita Khairy da kanta ta
hadawa Hurriya tea ta zuba mata komai na karyawa. Hurriya na tauna wainar kwai
zuciyarta na raya mata akwai abun da Khairy take shirya mata, domin a iya saninta
Khairy bata tana sonta ba ko na rana daya, idan ma kowa zai raga mata a gidan ban
da Khairy amman me yasa take nuna mata kulawa tana janta a jiki yanzu? Anya ba wani
abu take shirya mata ba? Ta mike tsaye sai Khairy ta kalleta da sauri.

“Ya aka yi baki sha tea ba fa?”

“Ruwa zan dauko a kitchen”

“Zauna bari na dauko miki”

Ta mike tsaye, Hurriya kuma ta koma ta zauna tana kallonta, Khairy na shiga kitchen
ta dauko ruwan da cup ta fito, sai mamaki ya kara rafe Hurriya. Haka dai ta karya
ba dan zuciyarta natsu da yadda Khairy take mata ba.

“Yaya Khairy saboda Adam ne?”

Khairy ta kalleta

“Ban gane ba?”

“Kike min haka kuma kike son na rakaki mu fita”

“Haba Hurriya Adam din da Appa yace kar ya sake ganinki da shi, kuma yaya ma yayi
gargadi akan haka, shi ne zan hadaku? Na rantse miki da Allah indai ni ce ba zaki
taba ganin na kawo miki Adam da idonki biyu ba, haba Hurriya kawai ina kokarin
ganin na kyautata miki ne, ni yar'uwarki ce be kamata ace muna samun tsabani ba,
kin ga yanzu ni aure zan yi, duk kuwa da ba a saka rana ba, amman ban san ya
rayuwata zata zama a gidan auren ba, kuma hausawa suna cewa idan kana son gani da
kyau to ka aikata mai kyau, and trust me daga yanzu an fara kenan har gaban abada
da yardar Allah sai kin ji cewar baki da wata yar'uwa kamar ni a duniyar nan”

Hurriya ta dan yi murmushi ba dan ta yarda ba.

“Amman ina tsoron wani abun da zai saka Appa yayi fushi ko yayi fada, musamman ma
ni na batawa Appa rai da yawa idan an sake ban san abun da zai biyo baya ba”

“Hakan ba na fatan ya faru, komai zai zama labari Hurriya, tashi ki shirya da wuri
dan bana son mu yi latti”

“Tou”

Ta tashi cikin sanyi jiki ta fice daga falon, ko da ta dawo bangaren Momy mai aikin
gyara dakuna ta gyara mata dakinta ta fitar da plate din da ta ci abinci. Tufafinta
kawai ta cire ta fada bandaki ta dauki lokaci a bandakin dakin tana Khairy, bata
son zafafawa akan negative mind, dan haka take kyautatawa yar'uwarta zato. Ko da
fito wanka wani bachi mai dadi ke ziyartarta haka dai ta murje ido ta hana kanta
bachin ta shirya cikin ready-made bata damu da daukar jaka ba ganin bata da kudi ko
wayar da zata saka a ciki, ta fito tana tafiya a hankali har ta sauko falon. Gaban
Momy dake zaune a falon ta fara risinawa ta gaisheta.

“Momy ina kwana?”

“Lafiya kalau”

Ta amsa mata a takaice.

“Zamu fita da Khairy tace na rakata wani gurin”

Nan kam Momy bata ce mata je ko karki je ba, balle ta tambayi inda za su je, a
lokacin da Hurriya ta gaji sai ta mike tsaye ta fice daga falon ga bachi ga hawayen
da suka cika idonta suna son zubo mata, ba dan komai ba sai dan abin da Momy ta yi
mata, ta tabbatar da uwarta ce ba zata bari ta fita ba ba tare da ta tambaye ta me
za su je yi ina za su je yaushe za su dawo, ko ma ta hana ta zuwa gaba daya. Amman
bata yi ba saboda ita din ba uwarta ba ce

“Na yi marmarinki Amma”

Ta fada tana tsayawa ta kalli bangaren da mahaifinyarta dake zama a da.

“Na yi marmarin rayuwarmu ta baya, a lokacin da kike nan kuma kike cikin koshin
lafiya da farinciki, Hamad ma yake nan”

Ta sauke ajiyar zuciya tare da saka hannunsa ta share hawayen da suka zubo mata,
sannan ta dauke kai ta shiga bangaren Hajiya Kaltume kamin ta karasa kofar falon
Khairy ta bude kofar ta fito da nata shirin tana rike da keys din mota.

“Oh yanzu fa nake cewa zan biya na kiraki na ga kin dade ga garin da hadari”

Hurriya ta daga kai ta kalli sama dake cike da hadari da alama za a iya sako ruwa
at any time kuma za a iya yaye hadarin duk cikin ikon Allah ne da abun da ya zo. Ta
sauke kai tana hamma.

“Bachi ma nake ji?”

“Bachi yanzu? Ko zaki koma ki kwanta next time sai mu tafi”

“No mu tafi kawai zai sake ni ai”

“Okay”

Suka nufi motar Khairy sai da ta fara shiga ta yi mata key ta juya motar sannan
Hurriya ta shiga suka kama hanya. At first Hurriya ta saka ido ne kawai tana
sauraren inda Khairy zata kaita duk wani labari da take bata, bata yarda ya dauke
mata hankali ba har suka isa gidan dake cike da yan mata suna ganin Khairy suka hau
ihu ana rumgume juna irin an dade ba a hadu ba din nan, babu bata lokaci Khairy ta
gabatar musu da Hurriya a matsayin kanwarta, Hurriya ta gaishe su sannan ta zauna.
Aka kawo abubuwan tabawa ana ci ana hira, ita dai bata yarda ta ci komai ba domin
zuciyarta bata natsu da gidan ba, kamar yadda bata gama yarda Khairy ba da sheri
take bibiyarta. Tun suna abu tana binsu da kallo har ta kai ta kan yi dariya ko
murmushi idan suka fadi wani abun ko suka yi wani abun, daya daga cikin kawayen
Khairy ne ta dauko chewing gum ta mikawa kowa ciko har da Hurriya kowa ya karba ya
ci, har dayar tana fadar a karo mata daya ba zai isheta ba.

“Zo ki karba idan kina da karfi, daman ke komai aka baki sai kin raina”
“Ni zaki cewa haka kam bala'i”

Suka fara kokawa da juna, Hurriya dai ta yi murmushi sauran kuma suna ta dariya,
tana ta kallonsu gwanin burgewa rayuwarsu da alama babu mai wata damuwa a cikinsu
sai nishadi suke ba kamar ita ba, tana tunani tana binsu da kallom sai hamma take
har bacin ya fara fisgarta tun tana iya daga ido ta kallesu tana jin hayaniyarsu
can cikin kamta har bachi ya sace ta gaba daya ta manta da wace duniyar take ma.
Bachin da bata farka ba sai La'arsar shi ma kuma Khairy ce ta tashe ta saboda
hadarin da ake da iska ruwan zai iya dadewa gashi basa gida.

“Kina ta bachi tashi mu tafi gida an fara ruwa”

Ta mitsintsika idonta kamin ta cire gilashin ta murza idon ta maida.

“Karfe nawa?”

Khairy ta duba agogo hannunta, Hurriya ma ta duba nata sai suka furta a tare.

“4:30pm”

Hurriya ta yunkura da karfi zata tashi sai ta ji jikinta da dan nauyi saboda ta
dade kwance gashin kanta ma duk ya sha birjice saboda ta sha murja akan gadon
saboda nauyin bachin da ta yi, har zuwa yanzu kuma be gama sakinta ba. Khairy ta
mike tsaye tana laka jakarta

“Ya aka yi? Ko zaki ci abinci?”

Hurriya dake mika yana jin kamar ta kara yin bachi ta ce.

“Jikina yayi tsami”

“Taimaka mata ta tashi mana wanda ya dade kwance ai dole zai ji dabam”

Wata kawar Khairy dake daga zaune kan sofa tana kallon Hurriya da Khairy dake gurin
bed ta fada. Khairy ta rika Hurriya ta mike tsaye.

“Baki tashe ni na yi sallah ba”

Ta fada har lokacin tana hamma.

“Bachi naki ne ya ga yayi nauyi shiyasa hala baki yi bachi jiya ba?”

“Na yi”

Ta fara takawa tana jin jikinta kamar ba nata saboda nauyin da yayi mata na bachin
da ta sha.

“Kowa fa ya wuce mu kadai muka rage, ita wannan yar iskar gidansu ne bata da
matsala”

Budurwa da Khairy ta fadawa haka ta mike tsaye tana dariya.

“Dan Allah yaushe zaku dawo?”

“Wa zai dawo nan yanzu kam ai sai dai a hadu a gidansu wata kuma, Hurriya cira kafa
kar ruwan yayi karfi sosai da alama fa zai kai magariba ana yi”

“Eh gaskiya, tun dazun fa hadarin nan yake na dauka ma ma da rana za ayi ruwan”
“Eh Wallahi”

Kawar ta rakosu har Balcony, Khairy ta juya ta kalleta.

“Toh mu kam idan Momy ta zo ki ce muna gaisheta”

“Zata ji, Allah ya kiyaye sai mun yi waya”

Ta koma ciki su kuma suka nufi motarsu, Khairy na hadawa da gudu dan kar ruwan ya
jikata Hurriya kam ta tsaya tana tafiyarta a hankali, wata zuciyar na raya abun da
be zo mata a rai ba sai yanzu, why take ta jin bachi bayan kuma ita ta san jiya ta
yi bachi ko da ma ace bata yi ba chi ba ai be kamata ta rika irin wannan mashalon
da nauyin bachin just because of bata ta yi bachi ba na rana daya, balle ma ta yi.
Kamin ta shiga motar ta raya ma zuciyarta cewar ba zata sake yarda ta sake raka
Khairy wani gurin ba, domin idan wani abun be faru a yau ba, zai iya faruwa wata
rana, kuma ta fi kyautata zaton wata kila kwaya ta saka mata ta yi bachi, waya sani
ma ko so take ta koya mata shan wani abu, daman ana kishen kishen tana sha kuma ta
lura da hakan domin ta ga tarin mutanen da ta tara a birthday ta babu na kwarai,
gashi kuma Adam din da ya nuna yana sonta shi ma yana shan shisha.

A ranta take ta sake sake bayan ta daukarwa kanta alkawarin ba zata sake rakata
ko'ina ba ko da kuwa ta yi mata magijiya haka kuma ba zata sake cin wani abu da
zata janyota ta ci su ci ba, ko da kuwa yunwa zata kasheta, domin mutum ba zai ƙi
ka da da maraice da dare ya ce yana kaunarka ba, idan bata da masu mata fada su
nuna mata mata daidai da kuskure, ya takama ta fadawa kanta.

“Kina bachi wata kawarmu ta zo na so kin ganta”

Khairy na tuki tana bata labarin abubuwan da suka faru kuma tana tambayarta wai
bata ji lokacin da aka yi kaza da kaza ba.

“Ban ji ba, na yi bachi ne sosai”

“Ai na ga alama kam, shiyasa na ce ki koma ki kwanta baki yarda ba, Allah yasa jibi
idan zamu fita kar ki yi irin haka, dan Allah ki rika yin bachin dare Hurriya ki
daina sakawa kanki damuwa ta hana ki bachi, na san ba zai wuce tunanin Amma ba ko
Appa, Amma zata samu sauki da yardar Allah”

“Amin”

Hurriya ta amsa a takaice, hakan ya saka Khairy ta kalleta jin ta katse mata magana
ba tare da ta kare ba, kuma ta amsa da Amin. Sai kuma ta dauke kai ta cigana ta
tukin ba, bata sake cewa wani abu ba har suka isa gida by that time ruwan yayi
karfi sosai. A gaban gate din Momy Khairy ta faka Hurriya ta bude ta fita ta rufe
mata motar sannan ta yi baya kadan ta nufo gate dinsu. Da tafiyar da ta fi kama da
kasaita ko kuma ace tausayin kasa Hurriya ta rika takawa ruwan saman dake sauka da
karfi suka ce me suke jira da ita ba su jikata ba. Tun da ta hango mota fake a
harabar dake kusa kusa da Entrance din Momy ta san suna bako ko bakuwa a gidan
domin ba motar da ta sani ba ce. Tana isa daf da motar aka bude farar motar mai
farin gilashi Captain ya fito rike da System dake cikin jakarta da wasu takardu, da
kuma wata yar jakar karama a hannunsa, shi kan da gudu ya rufe motar ya haye
Entrance din. Gudun kar ta isa gurin Momy ko Namra su zo bude masa kofa su disgata
gabanshi ya saka ta sauya hanya ta nufi hanyar da zata kai ta bayan dakunan
bangaren na Momy. Sai da ta kusa shigewa sannan Captain ya juya ya bita da kallo
yana kai hannunsa yayi knocking din kofar falon, ya hada da taba bell. Mai aikin
Momy ce ta bude kofar tana zaton ma ko Hurriya ce ta dawo domin sun san bata gidan.

“Sannu da zuwa Yallabai”


Ya amsa mata da kai.

“Momy fa?”

Ya tambaya yana cire talkaminsa

“Sun fita da yamman nan ita da Namra”

“Okay”

Ta mika hannu zata karbi kayan da suke hannunsa sai ya hanata.

“No bari na shiga dasu ciki”

Ya karasa shiga cikin falon sannan ya nufi stairs, dakin Miwan ya bude ya shiga,
yadda dakin yake a gyare yana kamshi sa ka rantse da Allah ana zama a ciki ne
ko'ina clean an gyara komai tsaba. Saman gado ya fara zuba kayan da ya shigo da su,
sannan ta shiga bandaki ya kama ruwa ya fito ta nufi kusa da windows yana cire
safarsa, sai da ya jefa safar a cikin kwandon dake gurin sannan daga curtains din
Windows yana kallon yadda ruwa ke sauka a itacen gidan, ba ruwan ko itacen yake son
gani ba dan haka yayi kasa da idonsa zuwa inda zuciyarsa take muradin gani.
Hurriya ce kwance daidai tsakiyar filin, ta ware hannayenta fuskarta da cikinta
suna fuskantar sama ruwan yana sauka a kanta, be san dalilinta na yin haka ba amman
sai iya fadar akwai natsuwa da nishadi a cikin wasa da ruwan sama a lokacin da suke
yara, kamin girma yayi talking over. Tana ganin anyi walkiya ta tashi zaune da
sauri ta rufe kunnenta, tsawa na biyo baya jikinta ya fara rawa sai ta tashi gaba
da sauri ta koma gefe ta tsaya. Sai da aka gama ta sake dawowa cikin ruwa tana
ganin wata walkiya ta sake komawa da gudu kamar wata yar yarinya, da ta ji ba ayi
tsawa ba ta sake shiga cikin ruwa, this time around jumping take tana ajijiya cikin
ruwa. Murmushi ya samu kansa da yi, he miss alot daga kurciyarsa zuwa yau, and
wanka a ruwan sama are one of his childhood memories.

Fararen curtains din ya saki ya saka hannunsa aljihu ya pistol ya bude jakar dake
ka yi gado ya sakata a ciki, sannan ya dauki jakar System din da takardun ya saka
talkamin Musib da suke dakin ya nufi kofar fita ya bude ya fito yaja kofar a
hankali. One after the other ya rika bin dakunan da suke gefen dakin da Namra take
yana budewa har ya ci karo da wanda yake kyautata zaton an Hurriya ne, tsaye yayi
yana kallon dakin kamar mai nadar bayanai sannan ya ja kofar ya rufe ba tare da
bari ta yi kara ba. Downstairs ya sauko ya zauna a sofa ya ja wani karamin tebur
gabansa ya bude system dinsa ya aje a kai, takardunsa da wayarsa kuma ya da wallet
dinsa da pistol ya dora sama gefen kujerar da yake zaune.

“Ranka ya dade kana bukatar wani abu?”

Inna Shatu ta tambaya tana mikewa tsaye.

“Aa na gode”

Ya amsa ba tare da ya kalleta ba.

“Toh”

Ta nufi kitchen domin ba zata iya fita cikin ruwa ba balle ta tafi gurin da suke
zama, kuma ta san Momy tana hana su zama a falonta idan tana ciki ko bakinta suna
nan. System din ya bude ya fara tabawa, yana tsaka da typing kofar falon da yi kara
alamar da mutum a waje. Inna Shatu ta fito daga kitchen da saurin da nufin zata
tafi ta bude.
“Lemme Handel it bari na bude”

“Tou”

Ta juya ta koma. Dauke hannunsa yayi daga typing din ya mike tsaye ya nufi kofar ya
bude. He thought Hurriya zai gani domin ita ya san da shigowarta gidan, sai kuma
yayi arba da Momy da Namra rike da umbrella suna mamakin ganinsa.

“Captain kai ne kuma?”

“Eh na zo baku nan ai”

Ya matsa jikin kofar suka shigo.

“Ka dade a nan?”

“Aa ban jima ba, Momy sannu da zuwa”

“Yauwa, ya aikin?”

“Alhamdulillah shi na zo na yi a nan ai”

“Captain sannu”

“Sannu Namra”

“Bari naje na canja”

“Okay”

Ya amsa mata ta siga biyu amfani da kai, da kuma furtawa. Momy ma ta bi bayanta
tana fadin.

“Ai da na san zaka zo ba zan fita ba ma, gashi nan ruwa duk ya jika mu”

“Be kamata ai ka ki fita saboda ni ba”

“Babu wani abun da ya fi uwa ta saka danta a gaban ta yi ta kallo, da ka san irin
dadin da nake ji idan ka zo gidan nan wata kila da kullum sai ka zo”

Murmushi kawai yayi ya bi su da kallo har suka haye stairs din. A madadin ya rufe
kofar falon ya samu kansa ta takawa ya fita tare da janyo kofar ya rufe daga waje,
balcony ya tsaya yana kallon yadda ni'imar Allah ke sauka ko'ina a gidan tana jika
gidan. Dan matsawa yayi kadan yana takawa a hankali har ya isa gurin da ruwan yake
zuba ya tara jikinsa ya saka hannunsa aljihu ya lumshe ido yana maida numfashi a
hankali, sanyin ruwan saman dake sauka a kansa suna ratsa zuciyarsa da ilahirin
jikinsa, da abun ya masa dadi sai ya daga kansa sama daga tsayen da yake ruwan na
sauka a fuskarsa and the thing is so funny kana jin ruwa na sauka a fuskarka kamar
an watsa maka wani abu. Haka ya jike kansa shakaf da ruwan saman hannayensa biyu
duka cikin zube cikin aljihu daga ipod din dake kunnesa da wristwatch da wallet
dinsa babu abun da be jike ba, shi ma ba wai ya shirya hakan ba ne, zuciyarsa ce ta
ingiza shi har ya samun kansa da bukatar aikata abun da ya ga wata ta yi. Is he a
teenager like her ya tambayi kansa kamin ya juyo ya kalli Namra dake masa magana...

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

HURRIYA POV.

“Assalamu Alaikum Warahamatullah


Assalamu Alaikum Warahamatullah”

Ta sallame sallah magariba ta karo da azkar din sallah, sannan ta daga hannunta ta
yi addu'a kusan rabin kowace addu'arta Amma ce, burinta Allah ya bata lafiya ta
tare kamar da, sauran addu'o'in bukatu na rayuwa suna biyo baya ne bayan ta yi ma
mahaifinta. Daf da zata shafa addu'ar Namra ta shigo dakin, saman gadonta ta jefa
mata ledar dake hannunta kana ganinta kasan Hurriya ta shigar mata hanci da yawa.

“Na gaji da ajiyar wayar nan, idan ma baki bukata ki jefar ko ki kyautar, bana
bukatar wani abu naki ko na Salim”

Ta juya tana jan kofar dakin da karfe Kamar zata ballata. Hurriya ta juya ta kalli
ledar sannan ta mike tsaye ta nade carpet din ta zauna a bakin gadonta ta dauki
ledar tana dubawa. Babbar waya ce har da sabon line da chocolate sai turare mai
kamshi. Komai sai da ta bude ta gani musamman ma wayar da take jin kamar ta yi
amfani da ita, sai dai tana tsoron kar Yayanta yayi magana domin bata taba rike
waya ba, kuma kowa zai tambaye ta ina ta samu, idan ta amsa da cewar Salim ya bata
za a tambaye ta miye alakarta da shi, to me zata ce? Wannan tunanin ne ya saka ta
maida wayar a ledar ta cire chocolate din da turare ta janyo kwalin da Adam ya bata
ta saka wayar a ciki, turaren kuma ta dora a mirror tare da sauran turarukanta da
suke gurin. Sannan ta hau gado ta dauki chocolate ta fasa ta fara ci tana lumshe
ido, daman ta san dadinsa domin Appa na siya mata lokacin da Amma take gidan, Amma
ma da kanta takan siya mata ko ta bata kudi ta siya wani lokacin amman ban da
wannan lokacin da komai ya canja. Knocked din kofar dakin aka yi, ta tashi da sauri
tana cin chocolate din, kamar zata tambaya ta ce waye sai kuma wata zuciyar tace
tashi ki duba mana, ta sauka saman gadon ta nufi kofar ta bude, Khairy ce tsaye
tana lasa wayarta suna hada ido ta sakar mata murmushi ta kunno kai cikin dakin.

“Hurriya ruwa be saka ki zazzabi ba?”

“Aa”

Ta juyo tana amsa mata. Khairy ta kalli bakinta da hannunta.

“Me kike ci?”

“Chocolate”
“Eyyyy yar gayu, wannan mutumen da na gani a falo ya kawo miki?”

Tambayarta take irin tambayar nan mai halshen damo, tana wani murmushi ta kalailaye
ido ita ga mai wayo. Ita kam Hurriya sai ta ji cewar ta samu mafita ai daman bata
san ya amsawa mata ga wanda ya bata ba dan haka ta amsa mata da.

“Eh shi ya ba ni”

Khairy ta kama hannunta suka zauna bakin gado.

“Ba ni labari shi ma sonki yake?”

“Aa ni aa”

“To ai kin san ke din mai kyau ce ga farinjini, tsaraba ce?”

“Haka nan dai ya ba mu”

Hurriya ta amsa tana jin kanta guilty saboda ta yi karya, abun da ba halinta ba.

“Dan'uwan Momy ne ko, ina yawan ganinshi ai ance dan yayanta ne”

“Eh”

Ta amsa tana daukar dayan chocolate din ta mika mata, a nan Khairy ta juya ta kalli
bayanta, Chocolate ta gani ba daya ba ba biyu ba uku ba zai kai 12 kala dabam dabam
kuma duk masu tsada.

“Kin ce ba sonki yake ba, amman ya kawo miki chocolate haka, maybe dai baki son na
sani ne ko? Haba Hurriya ki dauke ni kamar kawarki mana, ko da yake dai be kamata
na takuraki ba”

Ta mike tsaye.

“Daman Hajiya ce ta ce na kiraki”

“Ni kuma? Me na yi to?”

“Sai kin yi laifi za a kiraki? Haba Hurriya karki ma Hajiya wannan kallon mana”

Hurriya ta hade yawu tare da sauran chocolate din dake makoshinta, gabanta ya shiga
faduwa ita dai ta san alheri baya sakawa Hajiya Kaltume ta kirata, sai da ta wuce
gaba sannan Hurriya ta bi bayanta gaba daya ta saka mata tunani cewar Hajiya
Kaltume tana nemanta sai ta fara tunanin ko fitar da suka yi ne a dazun, ko dai
wani abun aka shirya mata? Ko Hajiya Binta ta sake yi ma Hajiya Kaltume wata
maganar ne? Da tambayoyi kala kala ta sauko stairs din, a daidai lokacin da Captain
yake hada takardunsa Namra na saka masa laptop din a jakarta. Sai da ta fara kallon
Khairy kamin ya kalli Hurriya dake biye da ita a baya, a shi da alaka ta Hurriya
dan haka ba shi da hurumin tambayar ta ina zata je ko kuma da waye take tare. Sai
da suka fice sannan ya kalli Namra ya ce.

“Amman wannan yarinyar tana shaye shaye ko?”

“Me ka gani?”

“Fada min kika yi?”

Ya jefa mata bakar magana kamar yadda ya saba.


“Allah ya baka hakuri, tambaya ce kawai”

“Ni m amsa na bayar, ke ma idan kika fara yi zan gane”

Namra ta yi murmushi tana mamakin yadda yayi saurin ganewa bayan kuma bata fada
masa ba.

“Amman ba a tabbatar ba, haka dai ake zargi saboda friends dinta wasu daga ciki
suna yi”

Be ce mata komai ba ya daga kansa ya kalli Momy ya kalli agogonta.

“Tun dazun ake ta kirana Momy sai gobe idan na dawo”

“Zaka dawo”

Ta tambaya daga inda ta tsaya ganin kamar yana sauri, ya daga mata kai.

“Kullum zaku rika ganina har na gama watannin da zan yi In Shaa Allah”

“Haka nake so, Allah ya taimaka ya maka albarka Jameel”

“Ameen”

Ya amsa suna hada baki da Namra, sannan ya karbi Laptop dinsa.

“Dauko min wasu kayan da suke dakin Musib”

“Okay”

Ya fita Momy na binsa da kallo, Namra kuma ta nufi stairs domin dauko masa sauran
kayansa. Dan lokaci da ta bata kamin ta kawo masa jakarsa da ipod da agogon daya
cire a dazun, har ya fusace ransa gaba daya bace, tana bude kofar falon ya ja
motarsa ya barta nan tsaye rike da kayan tana kallonsa.

“Kuma har ka yi fushi?”

Ta juya ta koma cikin falon.

“Be karba ba?”

Momy ta tambaya tana operating remote ganinta da rike da jakar ga kuma fuska na
bayyana labarin zuciya.

“Wata kila cewa zai yi na bata lokaci, wai har yayi fushi”

“Ya kamata ki saba, ki lura da duk wasu abubuwan da baya so ki rika kiyayewa, kin
ga yanzu hankalinsa ya dawo gidan nan wata kila ma saboda ke ne, kuma kin san halin
Captain ba sai an fada miki ba shi da fushi da zuciya da saurin kai hannu ba su da
maraba”

“Amman Momy wani lokacin abun sa ya kan yi yawa, dauko kaya kawai sai ya zama
laifi?”

“Toh haka Allah yayi dan'uwanki ya zaki yi? Je ki aje kayan amman make sure kin
kira shi a waya kin bashi hakuri”

Ta lumshe ido ta bude alamar damuwa.


“Shiyasa ya kasa zama da budurwa, komai aka yi masa bacin rai ne”

Momy bata bi ta kanta ba ta cigaba da kallon tv ba. Namra ta yi wuce da kayan ta


fara taka stairs.

HURRIYA POV.

Da tsoro ta shiga bangaren na Hajiya Kaltume, da farko ta ji tsoro ganin Yayanta da


Salma a falon sai ta yi zaton za ace ta yi wani abun ne, cikin karfin hali ta
gaishe shi ta gaishe da Salma, yanayin yadda ya amsa mata ya fahimtar da ita bata
da laifi a gurinsa. Khairy ta zauna kusa da shi.

“Wai yau na gaji da yawa, ina yin Sallah Ishan'i zan sha magani na kwanata”

Yasir ya dubeta

“Maganin me? Aikin me kika yi kika gaji?”

“Pain killer nake son cewa, zan shafa a kafa driving na yi yau mun yi yawa sosai”

“Good shiyasa na yi ta shigowa ina ganin kowa ban da ke, ke kawai kin fi son
rayuwar waje, ki je yi ta abubuwan da kike so babu mai ce miki uffan, kawaye ma
idan an rabaki da wannan gobe da wata za'a ganki? Khairy abun da kike yi fa ba shi
da kyau, kuma ina miki fada ne ki gyara ba dan ni kadai ba sai dan ke kanki da
future dinki, idan kika dauko wani abun magana ko, mutane za su zageki kuma kimar
gidan nan zata zube, amman ke da Hajiya kun kasa gane haka”

Salma ta ce.

“An kusa aurar da ita Yaya ka kusa hutawa”

“Mtscheeeeee”

Tsaki Khairy ta yi ta mike tsaye, ita dai har yanzu ba wani son auren take ba,
ganin take gana cikin cin lokacin ta ne za a yanke mata, ko da wani ne balle Fadeel
da ke da mata kuma da dukan alamu ba zai dauki irin rayuwar nan ta barin mace ta yi
wasu abubuwan da suka tsabawa dokar Musulimci da al'adar Malam Bahaushe ba.

“Hurriya shiga ciki Hajiya na kiranki”

“Toh”

Hurriya ta nufi stairs din tana jin cewar idan dai ba mahaifinta zata tarar a dakin
ba irin wacan karon da aka koreta, to komai mai sauki ne domin zagi da wulakanci na
Hajiya Kaltume ta saba da shi dan haka be daga mata hankali. Sai da Hurriya ta haye
sama sannan Khairy ta kalli Yayanta cikin sifar magiya da lalama ta ce.

“Yaya dan Allah ka daina irin fadan nan a gaban Hurriya”

“Hurriyar bakuwarki ce? Ko kuma ita wata bare ce da ba zan miki fada a gabanta ba?
Kuma da kin zama yadda nake so zan miki magana ne? And Salma was right idan an miki
aure dole ai ki tsanu, and wannan ya zama na karshe da zaki fita ba tare da kowa ya
san gun da zaki tafi ba! Dazun na tambayi Hajiya tace min baki fada mata gurin waye
zaki je ba, ki daina wannan dabi'ar tun a yanzu”

“Zan daina Yaya ba zan sake fita ba tare da na fada”


“Ya fi miki, ai saboda kun samu Appa yana musu sauki ne yanzu, ace kamar baya ne da
yake daukar zafi baku isa duk ku yi wannan ba, kuma ko. Yanzu idan kika sake irin
haka sai na fasa miki jiki”

Ya mike tsaye.

“Yaya, ka yi hakuri dan Allah ba zan sake ba, ko dazun ma fa ba ni kadai na fita
ba, tare muka fita da Hurriya ita tace gidan so boring shiyasa muka dan fita ta
samu ta sake ita ma”

“Ki dai koya mata fitar kike so, shekara nawa tana zaune a gida bata gidan so
boring sai a yanzu, ita ma ta fara raina wayon mutane, wata fadawa da zata fita?”

“Ita ai bangaren Momy take laifin ba na Hajiya ba ne”

“Shiyasa kullum Rukayya ke fadar na kula mata da Hurriya, wani lokacin sai a rasa
ta ina ma za'a fara controlling dinku Mtscheeeeee”

Ya karasa yana jan saki, Khairy da Salma suka kalli juna a gurin da Yasir yake
ambatar sunan Rukayya. Sai dai babu wanda ta isa tace wani abu domin sun san halin
yayan na su. Sai da ya fice sannan ya Khairy ta koma kusa da yar'uwarta suka tasa
gulmarsa da na Rukkayya.

HURRIYA POV.

Ta shiga dakin na Hajiya da Sallama ta zauna a kasa tana gaisheta, Hajiya Kaltume
ta amsa irin amsawar nan kamar ta dole fuska babu yabo ba fallasa, idan ta kalli
Hurriya wani kololin bakinciki ke taso mata saboda tuna Iyami da take yi.

“Lafiya Kalau, ya jikin Iyami? ”

“Ta ji sauki”

“Eh”

Ta daure ta kirkiro murmushin yaƙe.

“Maa Shaa Allah, haka ake so ai, Allah ya kara rikawa yanzu tana tafiya ko?”

“Aa bata tafiya”

“Ah ah kuma kika ce ta ji sauki?”

Hurriya ta yi shiru idonta da kanta a kasa kana ganinta ka ga natsantsiyar yarinya.

“Tana iya tashi zaune da kanta?”

Huriyya ta yi shiru na dakiku kamin ta girgiza kai.

“Ashha dai, Allah yasa jinya ta zama kaffara, ni fa ina son naje na dubata amman
ina gudun ka ce na ce, idan kin je dai ki gaisheta”

“Toh Hajiya”

Hajiya Kaltume ta dauko wayarta ta bude Gallary ta kama hoton wani farin lace ta
mikawa Hurriya wayar.
“Duba ki gani, daman wani Lace ne nake son na siya muku”

Bata yarda ta karbi wayar ba, a madadin haka ma sai ta bi Hajiya da wani kalami.

“Aa Hajiya na gode”

“Toh har da kyautar Iyami ta hanaki karba?”

“Aa Hajiya ai Amma bata iya magana, bata ce min kar na ki karbar kyautar kowa ba,
ni ce dai ban karba a karan kaina”

“Toh tashi ki kara gaba, daman duk yadda aka muku mutuncin sai kun ce ba ayi ba, an
riga an gado bakin hali, daman ni ai ba so na zaku yi har abada”

Hajiya Kaltume kamar wanda ta zare haka ta rika fadawa Hurriya kalamai marar dadi,
Hurriya dai bata dauki ko daya a nan gurin da ta fada mata su a nan ta bar su, ta
fice daga dakin. Fitar Hurriya da kamar minti goma Kulu ta shigo dakin ta zube kasa
tana dagawa Hajiya hannu kamar wata sarauniya ko matar sarki.

“Ranki ya dade gani, Khairiya ta fada mjn ina nema ma na fito har na kusa sai na
hango ta doso nan tare da Hurriya shiyasa na koma”

Hajiya Kaltume ta yi kamar bata ji ba ta shiga wani bangaren na wayarta, kamin ta


kara wayar a kunnenta.

“Yasir kana kusa?”

Yasir ya amsa a dayan bangaren.

“Eh ina nan waje, muna tare da Kamal ne”

“Asibiti nake son mu tafi idan ka gama”

“Waye ba lafiya”

“Ni ce, amman dai da sauki, ka bari sai ka gama ni ma akwai abun da zan yi yanzu”

“Toh”

Ta sauke wayar ta kalli Kulu, sai a lokacin take amsa mata maganar da ta yi.

“Ai kara da kika yi haka, saboda kaucewa ido”

“Duk wani abun da zai saka Momy ta ji ko ta gane akwai alaka a tsakaninmu ina
kokarin ganin na gujewa haka”

“Kin kyauta, dabam na ce a kira min ke ne, saboda mu yi wata magana da ke, kamin
nan tashi ki tura kofar dakin”

Kulu ta kike tsaye ta nufi kofa da ta bari a bude ta rufe, sannan ta dawo ta zauna
ta natsu sosai tana sauraren matar da ta fi tsoronta a yanzu fiye da uwar dakinta.

“Aminci ne ya saka na nake tambayarki abu ko na saka ki yi, na san ba dan kin dauki
sarka da kudi ba, wata kila ba zamu san juna ba, amman bana son kina kallon wannan
a yanzu, ni daman tuni na tattara wannan abun na aje a gefe daya”

“Hajiya ai ba dan karki ce na yi karya ba, nikam da nace satar nan ta zame min
alheri domin sanadinta na hadu dake”
Hajiya Kaltume ta sauke ajiyar zuciya ta marairaice fuska.

“Kulu ke da yar'uwata duk daya a yanzu, shiyasa har na kira ki nake son na fada
miki damuwata, kuma neman samun mafita a gareki”

“Hajiya tafi kanki tsaye, duk wani abun da kike so zan miki shi, yadda kika rufa
min ba ni da kamar ke a duniyar nan”

Dogon numfashi Hajiya Kaltume taja ta sauke sannan ta furta.

“Kulu ina cikin damuwa da matsala kala kala, amman wanda ta fi min yawa, ita ce
ciwon kafar nan dake damuna, yanzu haka kiran da kika ga nayi ma Yasir ita zan kai
asibiti, na dade ina ciwon nan amman har yanzu babu sauki babu alamarsa, tun ina
barin ciwon a cikina abun ya fara min yawa, to yanzu kuma sai abin da biyo har da
mafarkai da ba su dace ba, kuma ciwon nan sai cigaba yake, abun ya ba ni tsoro, ga
maganin asibitin nan yi ake amman a banza”

Kulu ta dukufa a tunani har wani kada ido take tana jinjina kai.

“Hajiya ba zaki gwada na hausa ba? Ko Allah zai saka a dace?”

Kamar an yi ma Hajiya Kaltume albishir haka ta ji, saboda Kulu ta sosa mata gurin
dake mata kaikaiyi.

“Shiyasa na kiraki ai, kin san ku ne mutanen kauye, kun fi sanin irin abubuwan nan,
wata kila ba zaki rasa sanin masu irin aikin ba”

“Akwai su Hajiya kala kala, akwai wata mai aljannu tana bada taimako sosai, kuma
akwai namiji ma yana yi”

“Yauwa namijin dai zai fi, ni ban cika son mata masu aljanu ba, na fi son inda zan
tafi a fada min ko minene, jifa ce ko kuma ciwo ne ko iska ne”

“Aiko kina tafi gurin Malam na gangare zai fada miki ko menene, domin shi baya son
ma ka fada masa abin da ya kawo ka shi zai baki labarin komai, har abun da baki
sani ba, da madubi yake aikinsa yana kallo madubi ya fadi magana ta tabbata, kuma
ko minene a take zai rabaki da shi, idan jifa aka yi miki ko turbuda a take ma zai
ciro shi”

Hajiya Kaltume ta dauki filo ta dora a cinyarta ta kwantar da hannayenta akai tana
gyada kai.

“Yauwa irin su nake so masu aiki kamar yankan wuka masu zafi”

“To idan kika kai gareshi magana ta kare, domin shi ko mutum kika ce ya kashe miki
zai kashe”

“Irinsa ya dace, kin ga ko minene a take zai fada maka kuma ya karya shi, a ina
hake Kulu?”

“A kauye uku yake, dake nan cikin bunguɗu”

“Babu nisa sai dai ban san yanayin hanyar ba?”

“Hanya lafiya kalau take, ai garin mu babu irin bata gari, su kansu suna tsoron
mutanen yankin”

“Maa Sha Allahu, sai dai kuma tafiyarmu kamar ba zata yi a tare ba, saboda uwar
dakinki Nafisa ba zata bari ba nake gani”
“Wannan ba matsala ba ne Hajiya, kina shiga garin Bunguďu ki dauke hanyar kauye
uku, da kin isa ki ce gidan Malam Ashiru mai Yasin da Allon karfe kike nema, ko
karamin yaron zai kai ki, idan kuma kina jin ba zaki iya haka ba ke nemi gidan su
Kulu taroro kina shiga gidan ki ce ni na aiko ki gurin Malam Ashiru za a kai ki,
zaki iya ma kira na yi magana da su”

“Allah dai ya saka miki da alheri Kulu, ina ganin ma ba zan tafi asibitin nan ba,
gobe ina gama karyawa zan kama hanyar garin, zan iya tafiya da direba na ma ya kai
ni garin”

“Daman Hajiya tafiya da daren ba ai ya fi sirrin da sauki”

“Haka zan yi, zan fara zuwa gidan na ku sai na kira na ba su ku gaisa idan ya so
sai kun iso gurin Malamin zai fi sauki”

“Toh Hajiya, Allah ya bada lafiya”

“Amin”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye daker tana cige baki kafar kuma kamar zata yi gurmanta
da ita haka ta taka ta isa gurin kayanta ta bude wardrobe ta dauko wani lace da ba
a dinka ba ta jefawa Kulu.

“Ahhhhh Kai Hajiya duk ni kadai? Alhamdulillah Hajiya na gode na gode, Allah ya
kara rufa asiri ya biya bukata, Allah ya kara lafiya ya tsare ki daga duk wani
sheri”

“Amin, wani abun kulu ai sai na samu lafiya ma, da yardar Allah idan bukata ta biya
zan kyautata miki, ta shi ki tafi kamin Yasir ya shigo”

“Toh Hajiya, amman zan bar leshin a nan saboda idon mutane, sai idan na ga sarari
zan zo na karba”

“Dadina da ke wayo Kulu kin iya sirri”

“Gidan na mu ne Hajiya sai da haka, kamin a fara fadar ana ganina bangarenki ”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi. Ita kuma ta mike tsaye ta yi mata sallama.

“Mu kwana lafiya”

Kamin ta isa kofar dakin ta bude Yasir ya bude sai dai be shigo ba ya bata hanya ta
fita yana amsa gaisuwar da take masa.

“Me ta zo yi nan?”

Hajiya ta nuna masa lace din dake kasa

“Nafisa ta aiko min da lace?”

“Ke kuma?”

Ya tambaya kamar mai shakku, Hajiya dai bata sake ce masa komai ba ta nufi gurin da
ta tashi ta zauna da tafiyar nan nata kamar zata yi dingishi.

“A kafa kike jin ciwon ne?”

“Eh gurin da na taba jin ciwo kwanan baya, a nan na sake jin ciwo haka nan kawai
sai na ji kamar an tureni na fadi kasa”

“Ko santsin gurinki ne ke janki”

Ya soma duba kafar da ta dan dago masa tana jin kamar ana yanka gurin sai sululi
yake mata kamar an watsa ruwan zafi.

“Aa ba wani tsantsi shekara nawa ina gidan nan da can tsantsin be ja ni ba sai
yanzu? Turo ni ake yi fa”

“To wa yake turoki Hajiya”

“Yo ina zan sani tun da abu ne na aljanu, amman tabbas ba faduwa ce zallar faduwa
ba, turo ni aka yi”

Yasir yayi murmushi tare da kai hannu ya latsa gurin.

“Ban san me yasa ku mata kuke yarda da irin abubuwan nan ba, haka Last week Rukayya
take ce min wai ance aljannu ne a jikin Amma, ku dai komai kun fi son ace aljannu
ne, wani abun fa daga Allah yake kai tsaye idan ana na asibiti zaki ga an dace, ita
kanta Amma da za a fitar da ita waje a dubata duba mai kyau za a gane Matsalarta”

Hajiya ta janye kafarta da sauri saboda lasa gurin da Yasir yake yi.

“Ku kuma ba ku yarda da aljannu ba ko?”

“Mun yarda da su mana, amman ba lallai komai ace su ba, kin ga kafar nan take da
zaki iya daurewa mu bari sai da safe mu tafi asibitin, hoto za su miki su duba
matsalar”

“Eh haka zan yi, mu hakura da tafiya asibitin nan sai gobe da safe”

“Ba sosai kafar take damunki ba”

“Yanzu dai ta min sauki ba kamaf dazun ba, kai Allah sarki na tausaya wa Iyami
gaskiya, a kafa kawai ina jin ciwon nan kamar zan mutu balle ita da ta ke kwance
bata iya komai shekara da shekaru, wai har yanzu bata iya tashi da kanta?”

“Rukayya ta ce min tana tashi da kanta yanzu, kuma da kanta take cin abinci,
rayuwar Amma akwai ban tausayi sosai, gashi ba wani karfi yanzu sosai ”

‘Munafuka Hurriya wato kin iya kini bibi ko? Ni zaki yi ma karya?’

Ta fada a ranta tana wani kashe ido, a zahiri kuma sai ta ce.

“Allah ka raba mu da wahalar duniya, wato Yasir yanzu ka zama dan gidan ka san ciki
da waje”

Murmushi yayi ya mike tsaye.

“Daman can ai dan gida ne ni, ba wai sai saboda Rukayya ba”

“Haka ne, Allah ya zaba abun da ya fi zama alheri amman dai ina son ka sani ba zan
taba yarda ka dauko yar'uwar makiyiyata uwa daya uba daya ka kawo a gidanka ba da
sunan mata”

“Hajiya Amma ce makiyiyar? Idan ma kuna kallon junanku da wannan ne ban isa na
canja ba, amman matsalarku dabam be kamata ta shafe mu ba, musamman ma ita Rukayya
meye nata a ciki?”
“Wai dan Allah duk matan garin Gusau ka rasa wanda zaka so sai ita? Me ta fi mata
da shi ne?”

“Hajiya ni dai ita nake so kuma ita zan aura da yardar Allah”

Hajiya ta daure fuska sosai tana watsa masa danta da be kishinta harara.

“Ina fada maka bana bukatarta a matsayin suruka kana karanta min ita zaka aura,
saboda kai ne uba ni ce ya ko? To mu zuba ni da kai shege ka fasa, ko saboda ka ga
wacan karon ka min magana na maka sanyi? Ina duba gudun ruwanka ne? Amman Wallahi
ko Rukayya ita kadai ta rage a duniya ba zaka aureta ba”

Gudun sa'insa da ita ya saka shi ficewa daga dakin ba tare da ya ce mata komai ba,
sai dai kana kallon fuskarsa zaka san kalaman na Hajiya Kaltume ba su masa dadi ba.

“Wallahi ba zaka aureta ba, ni gaba daya ma kamar an canja min kai, kai kenan
namiji Allah ya ba ni amman baka min biyaya, idan ina kiyayya da mutum kai sai ka
dauke shi masoyi, haka kake rawar jiki akan Hurriya sai ka ce ni na haifi yarinyar
nan”

Ta yi ƙwafa, kamin ta juyar da fadan gurin Hurriya da bata san tana yi ba.

“Ita kuma tsohuwar makira wai ita nan har ta iya canja labari ta fada min Iyami
bata ji sauki ba, wannan yarinyar da wata babbar mace ce da ni zata yi kishi nan
gaba, amman zan maganinku duka”

Ta mike tsaye tana daga kafar ta nufi bandakinta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Ita ke da girki yau, amman sai ta saka Khairy ta kai ma Appa komai a bangarensa,
saboda ba zata iya zirga zirga da kafar ba, daman kuma tana jin wani abu mai kamar
haushin Appa a ranta yanzu. Dan haka bata leka bangaren ba sai after goma da wani
abu, sannan ta saka kayan bachinta ta dora bakar abaya a sama, yau kam bata damu da
yi ma mijinta ado ba, daman kuma ba wani yabawa hake idan ta yi ba, bata sani ba ko
dan bata da kyau ne ko kuma saboda an dade tare da juna, amman ta tabbatar idan
Iyami ce ba zai kyale ba, tun asali can Appa irin mutunen nan ne dake da rayuwar
da, wani abun zuwan Amma ne ta canja shi, wani kuma Momy ce ta yi sauya mata ta
karfi da yaji.
Bata bar annuri da fuskarta ba saboda damuwa ta mata yawa yanzu, har ta rasa ina
zata kama, haka ta shiga barayar mijinta ba tare da sallama ba, Appa ya aje wayar
dake hannunta yana kallonta da yanayinta, a gaban gadon ta zauna cikin wata muryar
dake kara bayyana fushinta ta ce.

“Sannu da zuwa?”

“Yauwa, amman yau lafiya kike kuwa?”

“Me ka gani?”

Ya gyara zamansa yana kallonta irin kallon nan na mazan da suka kwashe shekaru a
duniya kuma suka fahimci rayuwa.

“Na ga yau Ummul Khairi ce ta kawo abinci, kuma kin shigo babu wani walwala a tare
da ke, kayan bachi da kika saba sakawa a nan ma yau can kika saka kika zo da su?”

Ta dan tabe baki.

“Ashe kana lura da al'amurrana”

Appa yayi dariya irin ta can cikin makoshin nan ya dubeta a natse ya ce

“Shekara nawa ana tare Kaltume? Uwargida ran gida? Uwargida sarautar mata? Kuma sai
ace ban lura da yanayinki ba? Ai shi miji kamar....”

Ya ja zaren furucin yana sosa gafen idonsa tare da aje wayar hannunsa.

“....Uba yake wani lokacin duk wani abun da mace take yi yana lura da shi, ita kuma
mace kamar gidan uba take a karkashin miji, wani ikon ma har ya fi na uba, shiyasa
Allah yake cewa ku tsiratarta iyalanku daga wuta, wanda makamashinta su ne Mutane
duwatsu, ku ai kuyo ne a gurinmu, dole sai muna kiyayewa, kuma kuna taya mu idan ba
haka ba abubuwan sai su mana, a duk lokacin da na tuna cewa zan tsaya a gaban Allah
amsa tambayarsa sai hankalina ya tashi matuka”

Ta juyo ta kalleshi a tsanake.

“Saboda me?”

“Alhamdulillah dukiyata halak dina ne, kuma ta hanyar da ya dace nake tafiyar da
ita, amman duk da haka sai na amsa hanyar da na sameta da hanyar da na kasheta, za
a tambaye ni kam ibada a gangaro kan iyali wannan abun yana daga min hankali, ko a
gaban alkali ka tsaya ya tambaye ka ina ka samu kudin jiya da yau ina ka kashe su,
ya ka yi ibadarka ta yau da jiya, ya ka tarbiyarta iyalinka ai akwai tashin hankali
balle Allah abun akwai ban tsoro Kaltume, a dalci ma a tsakanin yaya dole ne ka
tsayar da shi, kuma ka kula da tarbiyarsu, wani abun da idona yake rufewa na aikata
Kaltume yana damuna matuka, amman na rasa gane ina matsalar take, ga yarki Ummu
Khairy abubuwan da take yi bana jindadinsu, Yasir yana yawan kawo min kararta amman
ina bashi hakuri na daga mata kafa saboda ke, idan ba haka ba kin san gidana ba a
wasu abubuwan”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta yaya rigar after dress dake saman kayan bachinta
tana fadin.

“Duk kasan da wannan kuma kana tsoro amman kake ta karma karmar waso mata? Idan ma
ni ban wadace ka ba, ga Nafisa ka hada matanka biyu fara da baka amman duk haka be
maka ba sai da ka dauko mana macijiya gashi nan ta haifa ta bar mana bala'i a cikin
gida”
Appa yayi murmushi mai sauki.

“Iyami baiwar Allah, matar nan bata da matsala ko kadan, kawai dai anyi daidai da
wa'adin auren ya kare ne”

“Bayan ita yanzu ba wata zaka dauko ba”

Ya kalleta da kamar zai yi mamaki sai kuma ya tuna alakar dake tsakanin yarinyar da
yarsa Salma.

“Ina kika samu labarin nan Kaltume?”

“Abun duniya ai ba boyuwa yake yi ba, daman komai yayi tsami jinsa ake yi, yaushe
Iyami ta rafi mun samu wata firinar ta laba yanzu kuma zaka kwaso mana wata? Haba
Alhaji dan Allah kar rashin iyami yasa ka kara aure”

“Aa ko kadan, karin aure al'adarta ce, kamar yadda take al'adar Malam Bahaushe kuma
Sunna, ko da iyami tana cikin gidan nan zan kara aure, shiyasa na yi bangare hudu
ba biyu ko uku ba, ko Iyami na nan ko bata nan wannan abu ne da zan yi kuma ba dan
kun gaza a komai ba”

Ta saka kuka.

“Amman Fisabilillahi ka rasa wa zaka aura sai karamar yarinyar sa'ar Salma? Ko
kunya ba zaka shi ai sai mutane su ce maka mai budurwar zuciya, haka ka yi min daga
kawo Iyami aiki a gidan nan ka yalla ido ka aureta, ka saka a unguwa da dangi sai
labarina ake yi”

“A cikin mutanen da zasu zage ni, akwai mai ba ni naira biyar na kara gurin aikin?
Ko akwai wanda na tafi neman abun da zan ciyar da Iyalina a gurinsa? Kaltume wannan
kishin fa ba naki ba ne, ina ce idan za'ayi ta uku ta biyu aka yi ma, idan za'ayi
ta hudu ta uku aka yi ma, ki bar Nafisa ta yi wannan fadan, kuma aure fa ba zan
fasa ba, burina ne aurin mace hudu kuma sai na cija wannan burin da yardar Allah”

“Alhaji dawo zaka yi da Iyami kenan? Kuma ka kara aure?”

A take Appa ya fusata a yanzu kam ta kai shi kul.

“Idan zan dawo da ita akwai wanda zai hana ne? Me ye matsalarki da Iyami ne wai? Ta
bar gidan amman bata fita a bakinki ba? Ban san wani abun da ta yi miki ba bayan
alheri, amman kin dauki karan tsana kin dora mata, matar da lafiyar jikinta ma bata
wadace ta ba, ba a aure aka haife mu? Ko kuma ba a aure ni na aureki? Kina da yaya
shekararmu nawa tare da ke, to miye matsalarki da karin aure, idan mata dari zan
aura miye matsalarki da hakan? Akwai abun da na rage ki da shi? Ko kuma da kudinki
zan kara auren? Ke ce babba amman kullum ke ce mai fitina ta, na fara gajiya da
hallayenki nan Kaltume na fara gajiya, daga ke har Nafisa idan ba zaku gyara ba to
ko tabbas abun da ya ci Iyami zai ci ku, ita din ma da bata min komai ba balle ku
da kuke neman haddasa min fitina”

Ya sauke kafafuwansa ya saka talkaminsa cikin bacin rai ya nufi bandakinsa.


Kallonsa ma Hajiya Kaltume bata yarda ta sake yi ba, balle ta furta masa wani abu,
gaba daya jikinta yayi la'sar, a take ta shiga sake-saken zuci tana neman bakin
zaren lamarin.

‘Yau ni Alhaji yake fadawa haka? An samu matsala kenan, wata kila Malam ya fara
karya aikinsa ne shiyasa Iyami ta fara tashi? Kuma Alhaji ya fara son wata bayan ya
min alkawarin babu waa a zuciyarsa da yake so yake jin tsoron bacin ransa fiye da
na uwarsa kamar ni? Saboda yana somu yi min milkin mallaka irin na Hajiya fatee, ni
ko ba zan yarda ba, wata kila kuma Iyamin ce ta dukufa a wasu safgogin tun da gashi
har yana tunanin dawowa da ita, ko kuma dai wannan fitinannniyar yarinyar ce da zai
aura ce ta fi ni iya shiga da fita? Shiyasa har Malam ya ce ta gagareshi sai an
tafi gurin Malaminsa? Zata iya mallake Alhaji ta karya duk wani abu da na yi? Waya
ni m ko ita take aiko min da faduwa so take na fadi na mutu, ko ma Iyami? Kai
Nafisa ma zata iya shiga nata tsabgar fa? Gaskiya zama be gan ni ba, idan ban motsa
da wuri ba, za a min Zagon Kasa a lalata min tsari’

Haka ta raya dare da tunani kala kala, idan ta yi wannan sashen ta fado wani, ta
rasa wa zata zarga da karya mata aiki ko kuma kokarin rabata da mijinta, kamin
safiya ta waye har ta tsuma saboda burin da take da shi na tafiya kai kukenta ga
wanin Allah. Da asubar fari ta baro bangare Appa sallah ma a bangarenta ta yi, kana
ganin idonta ka san bachin da ta yi kadan ne, ga ciwon kafa na damunta. Tana
sallame Allah ta dauki wayarta ta kira Khairy bata daga ba, ta kira Salma bata daga
ba, ta kira wayar Ruma ita ma duk daya. Bata aje wayar ba ta kira Yasir shi kadai
ya dauka

“Yasir”

“Hajiya ina kwana?”

“Lafiya Kalau dan Allah ka tashi yan'uwanka su shirya mana abun karyawa ina son na
fita da wuri”

“Okay”

Ta aje wayar a kusa da ita ta cigaba da jan carbinta abubuwan da suka gudana
tsakaninta da Appa na musayar yawu suna dawo mata yau da asubar nan, har yanzu
mamaki take waya saka ta gaba. Ta aje carbin ta rafka uban tagumi kusan bata taba
shiga damuwa irin yau ba, ga aure Appa zai kara gashi yana kokarin juya mata baya
har yana ikirarin abun da ya sami Iyami zai iya samunta.

“Sallamu Alaiku Hajiya”

Ya juya ta kalli kofar dakin tana samawa Yasir

“Ya jikin Hajiya?”

“Alhamdulillah”

“Zan shirya da wuri sai mu tafi asibitin”

“Aa na hutar da kai tare da Khairy zan tafi”

“Hajiya saboda abun da ya faru jiya ne?”

“Ke nan dai kasan abun da kake kokarin aikatawa ba abu ne mai kyau ba”

“Miye abun rashin kyau a ciki Hajiya? Idan ma akwai wani abu tsakaninki da Amma ita
Rukayya meye nata a ciki?”

“Ai tun da sonta kake yi ba zaka gani ba, ni dai ko tsumma ne wannan tsumma na
Iyami ba zan taba sonshi ba, daga Iyami har yayanta har wani abun da yake da alaka
da ita ba zan taba son shi ba”

Ya mike tsaye ba tare da ya sake cewa komai ba ya fice daga dakin.

HURRIYA POV.

Bata yi irin saka ci da ta yi jiya ba, sai yau ta hana kanta bachi ta fito da wuri
ta zauna falo, kusan ita da masu aikon gidan duk daya, domin sai da Momy ta gama
karyawa sannan ta nufi dinning ta zauna ta zuba nata abincin ta fara ci, sosai ta
cika cikinta sanin cewar da rana ba lallai ne ta samu na damar ci kamar haka ba. Ta
dawo falo ta zauna a nan bachi yayi gaba da ita bata farka ba sai sha daya da rabi,
shi ma sanadin tashinta da Namra ta yi ne.

“Idan bachi zaki yi ki shiga dakinki mana, kin fi kowa sanin Momy bata son ana nata
bachi a falo”

Mika ta yi ta mike tsaye tana hamma, tukuna ta fara tafiya, har ta haye stairs din
bata juyo ba, kai tsaye ta zarce bandakinta ta yi wanka ta fito daure da tawul ta
tsaya gaban madubi tana kallon yadda kashin wuya ke mata ado kamar sarka, ta cikin
madubin ta hango Hajiya Binta dake sanye da onion Hijab dinta hakoranta na makka
guda suna kyalli a tsakanin hakoranta na gaba. Hurriya ta juya tare da zubawa da
gudu ta rumgume Hajiya Binta.

“Hajiya yanzu kika zo”

Har Hajiya Binta ta zauna Hurriya bata sake ta ba, tana rike da ita kamar zata
shige jikinki.

“Hurriya yanzu nake tafe Hurriya kuma tafiyar taki ce ke kadai”

Ta dafa kirjinta dake bugawa saboda murnar ganin Hajiya da ta yi.

“Ni kuma Hajiya? Allah yasa ba fada kika zo yi ba, ki ja min wata rigimar kuma”

“Sarkin tsoro tashi ki tura kofar ni ba shi ya kawo kawo ni ba”

Sai a lokacin Hurriya ta saki Hajiya ta nufi kofar dakin ta rufe ta dawo ta zauna
dafe da Hajiya dake bude hand bag dinta, gorar ruwan sai dai wannan ba ruwa ne a
ciki ba rubutu ne cike da gorar ta mikawa Hurriya.

“Hajiya menene?”

“Sha zaki yi, ki kasa uku a rana, kuma na kwana uku ne, wannan kuma da nono zaki
sha, idan zaki sha safe da maraice, kuma idan zaki sha ki hau kan gadonki ki tsaya
a tsaye sannan ki sha tare da bismillah”

Ta mika mata dayan maganin da yake kulle a bakar leda, sannan ta dauko mata nono.

“Na san samun nonon zai miki wahala shiyasa na nemo miki tun a can, ki rika amfani
da shi kina sha”

Ta saka hannu ta karba ta dora maganin a bedside drawer dinta ban da corar nono da
ta bari a hannunta ta fara budewa.

“Kuma ban da wasa, ban ce kuma ki aje shi a fili idan aka zo aka gani ki ce ni na
baki ba, addu'o'i ma mi rike Hurriya, kana idan kika yi sallah ki roki Allah bawa
mahaifiyarki lafiya, ya karkato da hankalin mahaifinki a gareku”

Hurriya ta daga ta kai bakinta tana sha.

“Ke ba fa Nonon zaki shanye haka nan shi kadai ba, sai da magani”

Hurriya ta saka dariya.

“Na sani ai Hajiya”


“Toh na san halinki fa, kar na tambaye ki ce kin manta ba ki sha ba, baki san nawa
na biya aka karbo min maganin tsarin nan ba, kuma ta tabbatar min idai Malami zai
zauna a kan ruwa be nutse ba, to sannan zai miki aiki ya kamaki, shi ma Tsoho sake
na yi ban kula da ba shi irin wannan ba, shi kuma be kula da addu'a ba, ai ko ba
dan abokan kasuwanci ya kamata ya nemawa kansa gambun karfe, amman be kula da ko
daya ba, wata kila da duk wannan abubuwan ba su faru ba”

“Kaddara ta riga fata Hajiya, haka Allah ya tsara”

“Haka ne”

Hajiya ta amsa sannan ta sauke ajiyar zuciya.

“Ina saka ran zuwa Umara ma wannan wata, da na ce zan daga sai wata na gaba amman
ina son tafiyar a yanzu, ko dan na yi muku addu'a, a zan zan roko miki na gari”

Ta karashe maganar tana jan kumatun Hurriya, Hurriya ta yi murmushi mai sauki.

“Allah ya kaiki lafiya Hajiya, ya karbi ibada, Hajiya karki manta da Amma”

“Ina zan manta da ita kuwa? Zan mata addu'a kuma zata samu sauki da yardar Allah”

“Allah ya sa Hajiya, Hajiya tashi mu tafi falo kar Momy tace kin shigo nan kin
zauna”

“Hurriya”

Hajiya ta kirata, sai ta amsa ta dago ta kalleta.

“Ummm”

“Nafisa matar ďana ce, ba uwata ba, ni nake a matsayin uwa a gareta, kuma na shigo
gidan nan ne saboda ke, ba saboda matar da bata dauke ni a matsayin uwa ba, matar
da bata san ta taka gidana ba sai idan wani abun ya faru, shiyasa da na shigo na
cewa mai aikin ta nuna min dakinki kai tsaye”

“Haka ne, amman dai tashi mua tafi falo Hajiya”

Ita tsoron take ace ta saka Hajiya Binta a daki ta kulla mata munafurci na gaskiya
da karya. Closet ta nufa ta dauko doguwar riga ta zuba ta dauki dankwali ta daura,
sannan ta dawo gurin gadon ta kama hannun Hajiya alamar tana son ta tashi su tafi.
Murmushi kawai Hajiya Binta ta yi ta mike tsaye domin ta san babba baya biyewa yaro
ayi ta jayayya balle kuma Hurriya da bata son musu. Suna fara sauko stairs din Momy
da Namra suka dago suna kallonsa a takr Hurriya ta ji wani iri ta kasa daga ido ta
kalli kowa har suka sauka.

“Hajiya sannu da zuwa”

Momy ta fada dan babu yadda ta iya, if not ba zata gaishe da surukarta ba saboda
bata zauna a falon ba, bata jira an kira mata kowa ba ta shige dakin Hurriya.

“Sannu da gida Nafisa, ya yaran?”

“Lafiya Kalau, ya tsufa”

“Gashi nan muna ja”

Namra ta gaisheta cikin muryar da ke nuna an mata dole.


“Hajiya ina wuni”

“Lafiya Kalau”

Ta amsa sannan ta zauna. Namra ta tashi ta shiga Kitchen ta dauko mata lemu da ruwa
da dan abun tabawa ta aje mata. Ruwan kawai Hajiya ta sha shi ma dan kar Momy ta ce
bata sha komai na ta ba. Bata wuce minti talatin a falon ba ta ce zata tafi.

“Da wuri haka Hajiya, na dauka nan zaki wuni, na ga idan kin zo har yamma kike
kaiwa”

“Irin wacan tafiyar kai tsaye daga gida nake fitowa zuwa nan, amman ta yau daga
wani gurin an fito sai na biyo nan na duba ku”

Duk suka mike tsaye ganin Hajiyar na ta mike tsaye.

“Allah ya saka da alheri mun gode ai a haka ma, bari na kira Alhaji a waya ina jin
be san da zuwanki ba”

“Aa ba bukata na fada miki ba zuwan da na saba ba ne, ko bangaren Kaltume ma ba zan
biya ba, sai dai wani lokacin”

Ta kalli Namra
“Namra an kammala karatu kuma sai mu ji shiru”

“Sauran Service, mun kusa zuwa”

“Aure nake magana, ga Khairiyyah ana ta maganar duk dai be turo ba amman ke mun ji
shiru”

“Ni ma ina kusa Hajiya”

“Toh Allah ya nuna mana, kuna da labarin Musib da Miwan”

Wannan karon Momy ce ta amsa mata da kanta.

“Eh muna waya da su, suna kusan dawowa shi dayan ya gama nasa karatun ma, dayan ne
ya rage”

“Allah ya taimaka ya sa a ci amfani”

“Amin”

Ta wuce gaba suna mata Allah ya tsare hanya, Hurriya ta biyota har gurin motarta ta
direba ke ja ya kai ta duk inda take son zuwa. Kamin ta shiga motar ta juyo ta
kalli Hurriya

“Karki yi wasa da abun da na kawo miki, kuma ki cigaba da hakuri Allah ya miki
albarka”

“Amin Hajiya, na gode”

Ta shiga motar Hurriya ta rufe mata motar tana daga mata hannu har suka fice, sai
da ta juyo zata shigo falon sannan gabanta ya fadi.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ta furta domin faduwar gaba ne da bata saba jin irinsa ba, kuma na zata iya fadar
dalilinta na faduwar gaban ba, sai da ta ja dogon Numfashi ta sauke sannan ta shiga
falon, kallo daya ta yi ma Momy da Namra ta maida kanta kasa bata sake kallonsu ba
har ta haye sama ta shige dakinta.
Namra taja tsaki tana wani hura hanci.

“Gaba daya yarinyar nan ta fita raina, Allah kadai ya san me ta fadawa Hajiya yanzu
kin ga tana zuwa bata ko tsaya an kiraki ba ta shige dakinta, ta sauko tana min
maganar yaushe zan yi aure wata kila ta fada mata karyar ina mata wani abun shiyasa
har take tambayar yaushe zan yi aure”

Momy ta tabe baki.

“Komai zata yi, su je su yi ta yi, gida ne dai ba a isa a kore ni ba, ni har wata
magana na ji a gurin Hajiya Mardiya”

“Wace Hajiya Mardiya?”

“Matar Alhaji Shamsu dan masanin tsafe, wai Alhaji zai hada shi da Kaltume tana son
ya fara sana'ar crude oil”

Namra ta daki kirji.

“What? Hajiyar?”

“Ita fa, ni ma nace ko dai ba ita ba tace min ita ce fa, wai har sun fara maganar
ma, ita ma mijinta ne ya fada mata”

Dariya ta subucewa Namra irin dariyar nan dake dauke da mamaki.

“Hajiya so take sai ta take ki Momy, saboda yanzu daga ke sai ita yanzu, Amma bata
nan ganin take kishi ya koma tsakaninku”

“Ai ba zai daure ba, ni fa ina da degree a fannin kasuwanci, ita kuma ko primary
bata yi ba, kin tana ganin mace da irin wannan kuma tace zata fi ni? Sannan ni
arziki na na ubana ne da na gada da kuma nawa da na nema tun yana da rai har bayan
ransa, ita kuma yar talakawa ce kamar Iyami, duk arzikin da zata samu ba zai kaiwa
ba, domin ita zata samu ne ta karkashin Alhaji ni fa? Kuma kin ga karatun da na
Musib ya tafi yi a waje saboda na saka shi cikin ragamar kasuwancina ne, domin idan
mu ne yau gobe ba mu ba ne, ita kuma yanzu zata fara kuma dan ta be sha'awar
kasuwanci, dana kuma yana da gogewar hakan”

“Ita ma Hajiya ina zata iya da kasuwancin Crude oil? Tana mace kuma ita da bata yi
karatu ba?”

“Ai a duniya yanzu babu kasuwanci dake saurin kawo kudi kamar crude oil shiyasa
take son ta fara, amman ina nan dake sai ta koma ko abun da zata daura ya gagareta,
ai Iyami ma yanzu ishara ce agareta, ciwon na kwantar da ita ta rasa komai daman
can da Alhaji ake tutiya yanzu kuma ba a tare, shiyasa rayuwar talauci bata yi ba
Wallahi, ke yanzu kina ganin idan ace Iyami wata shegiyar attajira ce a gidan nan
akwai wanda ya isa ya wulakanta mata ya? Kuma kin ga wannan abun da mahaifiyarta
akatau a duk lokacin da na kalli yarinyar can ko uwarta na tuna da wannan sai
kimarsu ta kara raguwa a idona..”

Bata kai zaren zancen ba ta yanke saboda kukan wayarta ta ji, ta juya ta dauki
wayarta dake gefe tana ringing, ganin number da ta yi appearing a gaban gilashin
wayar ya saka ta yi murmushi

“Captain”

Ta yi shiru still tana murmushi kamin ta sake fadar.


“Alhamdulillah, Okay maybe ta jefa wayar wani gurin ne”

Cire wayar ta yi a kunneta ta mikawa Namra.

“Karbi Captain yana son magana dake”

Namra ta mika hannu ta kara ta kara wayar a kunnenta.

“Hello”

“Ina wayarki”

Ta juya ta kalli stairs.

“Tana daki”

“Me ye amfanin waya idan ba zaki yi yawo da ita ba?”

“Sorry”

Yayi shiru kamar ba zai ce komai ba, sai kokarin sauke fushinsa yake yana kass da
numfashinta ya daidaita bugun zuciyarsa.

“Ki shirya yanzu ki tafi Mall ki samo min wasu abubuwan i will send you the list”

“Okay”

Ta cire wayar a kunnenta tana murmushi, ta mikawa Momy.

“Wato idan kana son ka ga tashin hankali a duniyar nan ka batawa Captain rai, wai
ya kira ni be samu ba, kuma fa ba zai wuce one missing call ba, shi da baya jera
mutum kira ma, amman a wayar nan ina jin yadda yake ta huci”

“Wani lokacin kuma fa, idan namiji yana son mace, idan ta bata masa rai ya fi
fusata fiye da kowa, ya kamata ki fara sabawa ai, iyayensa ma hakuri suke da shi ta
wani bangaren ina ganin kamar har da laifinsu fa, saboda tun yana karami sun nuna
masa basa son bacin ransa, shiyasa idan ransa ya bace abun yake masa zafi sosai
saboda be san bacin rai ba, ko kuma ki ga abun kadan ya taba shi, su kuma
hankalinsu duk ya tashi”

“Akwai haka amman Momy na fi yarda da abun har da hallita, duba ki ga yadda Hamad
ma yake yi a da”

“Haka ne kuma, to sai ko hanzarta kar ki kara bata masa ran domin na lura kwana
biyu nan hankalinsa yana karkata a kanki”

Namra ta yi murmushi ta nufi saying

“Ke dai Momy kina son canja manufar komai”

“Saboda ina fatar manufar tawa ta faru ba”

Ita ma dai da murmushin kasaita ta yi ta kana ta amsa wata wayar.

“Wa'alaikussalam”
*** *** ***

Sanin halin dan'uwanta ya saka bata wani ɓata lokaci ba shirya ta dauki jakarta,
atm wayarta da kuma key mota ta fice. Lafiyarta da kamar minti ashirin da biyar
Captain ya sake kiran Momy.

“Captain ta dauki wayar ya dai kuma ta tafi”

Momy ta bashi amsar tambayar da take kyautata zaton zai tambayeta.

“Eh mun yi waya da ita ai, an gama abincin rana”

“Ina tunanin an gama kam, ban leka Kitchen din ba, amman na san an isa gamawa zaka
zo ne?”

“Aa ina da aiki da yawa ba zan iya zuwa ba, amman zan aiko mota yanzu a karba min a
zuba a kula a bawa Hurriya zan turo wanda zai dauketa”

“Direba zai iya kai maka ai ba dole sai ita ba”

“Momy we have trust issues here, shiyasa ba ko'ina muka cin abincin ba, sai inda
muka yarda, kin ga wanda zan aiko ma ban yarda da shi ba, amman idan tare da na
gida ne i know I'm safe”

“Okay ka aiko shi yanzu”

“Okay Thank you”

Momy ta mike tsaye tana kiran masu aikinta dake kitchen, sai da suka shirya komai
aka zuba masa a coolers masu kyau ta saka plate da spoon a karamin kwado. Hurriya
na zaune dakinta mai aikin Momy ta shiga kiranta.

“Momy tace ki shirya ki fito yanzu nan da mayafinki zata aike ki”

Huriyya ta sauko daga kan gadonta ta nufi gurin da dogon hijab dinta yake ta dauka
ta saka ta cire flat shoes ta saka ta bi bayan mai aikin da ta dade ta sauka masa.
Ko da ta sauka Momy na tsaye dinning sai wani sham kamshi take tana yi ma masu
aikinta fada. Hurriya ta tsaya a daga gefe sai da Momy ta gama fadan ta juyo sannan
ta yi magana.

“Momy gani, Inna Shatu tace zaki aike ni”

“Ga abinci nan da zaki kaiwa Captain, ki jira direbansa ya iso, sauran kuma idan
kika tafi ki yi karabanin bata masa rai ki dawo ki ga yadda zan ci ubanki na yi
kasa kasa dake a gidan nan”

‘Shi dai wannan mutum suna jinsa kamar wani sarki’

Ta fada a ransa a zahiri kuma sai ta amsa da toh, ta nemi guri ta zauna har sai da
direban ya iso, sannan mai aikin ta daukar mata kayan aka saka a motarsa. Mutumen
da ya bude mata gidan baya ta shiga Soja ne dake sanye da uniform dinsa Complete,
tana zaune cikin motar shiru tana kallon titi har suka isa. Tun a bakin gate din
gabanta ya fara faduwa sakamakon arba da ta da fara da soldiers rike da makamansu,
tafiya suka yi sosai ciki sannan suka isa wani bangere da aka ware dabam da sauran
bangarori, daman gurin part part ne, a gurin da take ma part part ne. Fitowa yayi
ya bude mata motar after ya faka, ta sauko kafafuwanta ta fito ta dauki kwandon shi
kuma ya rika coolers din ya wuce gaba ta bi bayansa, gabanta sai faduwa yake saboda
tsaron dake gurin, kusan wannan shi ne karo na farko da ta taba arba da sojoji da
yawa haka. Wani gurin ya zagaya da ita dake bayan wasu manyan gine gine dake gurin
suka isa wani part da aka kawata da furannin daga gaba. A nan din ma akwai masu
tsaron wasu kuma suna ta aikin da takardu wasu da system. Can ciki aka wuce da ita
ya lasa wani gurin kofa ta bude sannan ya matsa baya yayi mata alama da ta shiga.

Captain ne zaune a kujera cikin katon office din yana mikawa wani files din dake
hannunsa. Mutumen ya karba ya tsare masa sannan ya juya ya fice, shi ma wanda ya
riko mata cooler sai da ya tsare masa sannan ya aje, da zai fita kuma ya sake sare
masa, yana fita kofar ta rufe kansa. Hurriya ta dago idonta kadan ta kalleshi sai
ta yi sa'a ita yake kallo daga inda yake zaune sanye da uniform dinsa complete abun
da bata taba gani ba, ita bata ma taba sanin soja ne ba sai yau. Da sauri ta maida
idon har da dan rufesu kwarjininsa na yau ya fi na kullum wata kila saboda yau yana
sanye da kakin na soja ne, dake karawa ko wane namiji kawarjini balle shi da Allah
ya wadata da six-packs.

“Baki iya sallama ba? Baki iya gaisuwa ba?”

“Assalamu Alaikum ina wuni”

Ta hade sallamar da gaisuwar a lokaci daya ta fada da sauri, har lokacin tana rike
da basket din ne tun da be bukaci ta aje ba. Ya aje pen din hannunsa ya mike tsaye
ya zagaya ya fito daga gurin table din ya nufi wasu kujeru da suke can gefe
visitors chair ya ware daya ya ja baya.

“Zo nan ki zauna ki ci”

Ta fara tafiya tana rike da basket din, ta ci? Ita? Ko kuma dai bata ji daidai ba?
Maybe nufin yake ta aje. Dan haka da ta aje basket din ta ta dauko coolers din ta
kai gurin ta aje.

“Na kai”

Ta fada, ba tare da bari sun hada ido ba. Ya mata banza ya cigaba da aikin da yake.
A nan ta soma fahimtar manufar.

“Ni fa na ci abinci”

Ta fada kamar a shagwabe.

“Saboda ke na saka a kawo abinci nan, ina nan aikin ya min yawa kowa aiki yake yau,
amman my mind was telling me kina can baki ci abinci ba you must eat...!”

Ya karasa a tsawace domin tana kokarin bata masa rai ne kawai, matsawa ta yi baya a
zarane ta dan saci kallonsa tana bata fuska ita dai ta san yana neman ja mata
matsala ne kawai a gurin Momy, kamar zata yi kuka ta ce.

“Na ci abinci fa”

Ya tsaya cak daga aikin da yake, ya dubeta. Kamin ya saka hannunsa aljihu ya ciro
pistol dinsa ya aje kan table.

“Bana maimaita magana, kina cikin headquarter soliders ne you should be careful...”

Yana aje bindigar ya mike tsaye ita kuma ta fadi zaune jikinta na rawa kamar
mazari, ta bude cooler ta fara zuba abincin wani na zubewa saboda tsoro. Ficewa
yayi daga office din ya barta daga ita sai bindigarsa dake kan teburin aikinsa. Ta
daga plate din ta dora a cinyarsa tana ci tana kallon bindigar, daman tana jin ana
fadar soja basu da imani yau ta tabbatar. Captain be dawo Office din ba sai da ya
dauki lokacin da yake kyautata zaton ta isa cinye abincin. Ta mike tsaye da sauri.
“Na cinye”

Ya kalli plate din sannan ya kalleta. Yanayinta so innocent da raunin dake tattare
cikin kyawawan idanuwanta, suka saukar masa da tausayinta, fiye da wanda ya ji a
lokacin da ya mareta Namra ta fada masa makauniya, fiye da wanda ya ji a lokacin da
aka dauke dan'uwanta, fiye da wanda ya ji a lokacin da ya same ta tana cin abinci a
kitchen din Momy irin cin yan yunwa tana kuka, fiye da tausayinta da ya ji a
lokacin da ya ji maganar Momy da Namra akanta.
Dauke kai yayi ya nufi teburinsa ya bude wani guri daga kasa ya dauko box din
gilashin da ya taba bata a lokacin da ya fasa na ta, a yanzu yana son ya bata
gilashin ne da ya siya da hard earned money, da hannunsa a England, as an apology
na marin da yayi mata a lokacin da yayi zaton tana sane ta bugu kirjinsa.

“Cire gilashin idonki”

Cikin wata muryar data fi kama da shagwaba da kuka ta ce

“Idan na cire hudu zan gani, bana gani komai sai da shi”

Kansa ya daga sama, yana addu'a a zuciya, na neman Allah ya kara masa hakuri da
juriyar iya controlling kansa, domin babu abun da ya tsana a duniyar nan kamar
musu. Hannunta ta kai ta cire gilashin ganin kamar zata bata masa rai a rashin
aikata hakan, bayan kuma Momy ta gargadeta, a take kuwa ta ganin komai da kyau
hudun da take tsoro ya mamaye idonta, da can tana ganin dishe-dishe idan ta cire
gilashin sai dai bayan tafiyar da dan'uwanta daya tilo yayi ya barta sai idanuwan
suka kara lalacewa saboda kukan da ta sha, da kunnuwanta take auna sautin takunsa
har kwakwalwarta ta sanar mata yana tsaye a gabanta. Tsakiyar cikin kwayar idonta
yake kallo, ya sani ko da zai saka wuka ya barka cikinta, ko ya dora mata bindigar
da take tsoro a kai ko yayi mata dariya ba zata shaidar abun da ta gani ba, domin
ita ta rasa wannan ni'imar. Kansa ya sauke kasa ya busar da iska bakinsa a hankali.

“Alhamdulillah”

Ya furta da nuryar da shi kadai sai muhallinsa za su ji, domin shi ya samu abun da
Hurriya ta rasa, daman kuma hausawa sun ce mutum dan tara ne be cika goma ba, Allah
ya mata gomai ya rage da ido, shi ne kadai tawaya a gurinta. Kamar an kunna wuta
haka jijiyoyin idanuwanta suka sanar da kwakwalwarta dake raba sako, ta karbi sakon
hoton fuskar Captain dake tsaye a gabanta hannayensa kuma suka zagaye tsakanin dama
da hagu na kyakkyawar fuskarta. Dauke hannunsa yayi bayan ya saka mata gilashin
sannan ya karbi na hannunta a lokacin da hawaye suka sauko a idonta irin saukowar
da wanda yayi arba da su a fuskarta zai tausaya mata. Ya nade gilashin ya dora a
kan teburinsa ba tare da ya kalli hawayen da suka zubo mata ba.

“Direba yana waje yana jiranki”

Daga haka be kara cewa komai ba ya fice daga office din, gafen hijabinta ta saka ta
share hawayenta, sannan ta nufi gilashinta ta dauka ta cire wanda ya saka mata ta
maida nata sannan ta nufi kofar ta bude. Taku daya biyu kamin ta yi na uku wanda ya
kawo ta ya nuna mata hanyar da za su ba, ba wanda suka zo dazun ba. Ba musu ta bi
bayansa har suka isa gurin motar ya bude mata ta shiga ta zauna, shi kuma ya shiga
mazaunin tuki yayi ma motar key, amman shiru shiru ta ji yaja motar sun kama hanya
ba, bata ankaro ba aka bude back seat inda take zaune, Captain ne ya shigo cikin
motar ya zauna, tana kallonsa ta yi saurin maida idonta kasa, sai ya kai hannu ya
dago fuskarta ya cire gilashin idonta ya saka masa nasan data cire ta aje masa a
office, sannan ya bude motar ya fita da nata ya rufe motar.
Damdamdam.. Ya buga bayan motar sai sojan yaja motar suka fara tafiya.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Sai da suka wuce sannan ya dawo office dinsa, yana shiga ya aje gilashin na Hurriya
a saman teburinsa ya zagaya ya zauna ya cigaba da aikin da yake. Few minutes Namra
ta kira wayarsa dake gaban teburin sai ya amsa ta bluetooth din dake kunnensa yana
duba wasu takardun.

“Ni fa na zagaye garin nan kaf duk inda nake saka ran samu wannan turaren Kapter
Bokur Perfume ance min babu shi, wasu sunce sai Abuja da Kaduna ake samunsa ko
Kano, wasu ma cewa suke ba su sanshi ba”

Ya dago daga aikin da yake yana murmushi ya jingina da kujerar da yake zaune yana
lilo, shi kanshi daman ya san ba za a samu turare ba domin abun da babu ne be ya
fada mata, shi ya hada sunan turare and ya san babu turaren dake da exiting mai
irin sunan.

“Okay, na baki zabi ki zabo min turare mai kamshi”

“Aa ka fada dai, kar sai na dauko maka turare ka zo kana min fada ko ka ce mai
warin albasa ne, kasan wata rana ba a maka daidai, garin gwaninta sai a bata maka
rai”

“Ssi ka ce ni nafi kowa muguwar zuciyar? Please select ina jiranki”

“Toh”

Ta kashe wayar, sai ya juyo kansa a hankali ya kalli gurin da Hurriya ta zauna,
rabin abincin da ta zuba a duk a kasa yake garin sauri ta zuba kuma ta ci.

“Mtscheeeeee”

Yaja tsaki ya tsani guri da datti ko kadan ne balle kuma na abinci, telephone dinsa
yayi using ya kira aka shigo aka gyara gurin aka maida komai gafe daya, bayan kamar
awa daya Namra ta kira sai ya fada mata inda zata zo ta same shi, a lokacin da ta
iso gurin ita kanta sai ta tsoro ya kama ta even though ta taba zuwa amman yadda
aka gyara gurin aka canja komai da tsaurara tsaro ya fi na da, arzikinta daya ya
aiko aka shiga da ita har ciki. Tana shigowa Office din ya dauke hannayensa daga
aikin da yake yana murmushi.

“Allah yasa kin zabo mai kamshi”

“I try my best na ga na samu mai kamshi kuma mai dadi, shiyasa na siyo kala biyar
ba daya ba”
Ta matso kusa da teburin ta dora bag din da turaren yake ciki ta fara cirowa tana
nuna masa. Ba laifi duka suna da dadi kuma duka na maza ne, amman babu kalar nasa a
ciki, haka yayi mata godiya ya karba ya aje, a lokacin da take kokarin dauke idonta
daga teburin idanuwan nata suka yi arba da gilashin Hurriya dake kan teburin a take
ta kai hannu ta dauka tana dubawa.

“Kamar gilashin Hurriya”

“Nata ne”

Ya amsa mata kai tsaye ba tare da tunanin komai ba.

Ta juya ta karewa ko'ina na office din kallo sai ta dora hasashenta akan abinci ta
kawo masa saboda kulolin Momy da ta gani.

“Abinci ta kawo”

Ashe kuwa ta yi hasashenta daidaita, sai dai wani abun ne ya tsaya mata a rai da ta
kasa hadewa har sai da ta tambaya.

“Me ya kawo gilashinta a nan?”

“Sato shi na yi kin san ni barawo ni”

Ta dan yi murmushi.

“Ni ban ce ba, na san bata gani sai da gilashin ne shiyasa”

“Na bata wani, ki zauna mana”

Ta zauna tana jin numashinta kamar zai shake zuciyarta na bugawa da mugun karfi.

“Kuma ta karba?”

“Da na yi mata ta karfi ba, kin san kanwar nan taki akwai musu da kafiya, amman
kuma tana samun sa'a na duk fushin nan nawa na kanyi kokarin controlling kaina na
daga mata kafa saboda kawai lalaurar da take tare da ita”

Yana aikin yana amsa nata da babu alamar wasa ko second thought a tare da shi.

“Ka taba bata wani abu kamin yau ta bata karba ba?”

Yayi shiru na wasu mintuna sannan ya amsa mata.

“Na taba bata kyautar gilashi a gabanki bata karba kin tuna? Kanenta ya hanata
karba saboda ya fi ni iya fitina”

Ta yi murmushin karfin hali.


“Hamad din ne ya fika fitina? Anya akwai wanda ya fika fitina Captain”

“Yep ai shi yaro ne yake da wannan fitinar, yayarsa ce fa amman tsoronsa take”

“Kai ma ai kowa tsoronka yake saboda fitinarka Captain, gaskiya bana jin akwai
wanda ya fi ka saurin fusata, fadar bakar magana, da kuma fitina”

Ya tsaya ya dubeta.
“Ashe haka kuke kallona, zan baku mamaki wata rana”

“Babu wannan ranar ai”


“Deal”

“Deal”

Ta amsa tana dariya, sai ya lumashe ido ya bude ya girgiza kai.

“Ki wuce da kulolin Momy, kuma ki fada mata na gode sosai”

Tana jin haka ta san ya sallame ta kenan, that's means yana bukatar ta tashi ta
tafi.

“Okay”

Ta mike tsaye ta nufi gurin da kulolin suke ta dauki wadanda zata iya ta fara kaiwa
a mota sannan ta dawo ta dauki sauran.

“Zaka shigo anjima?”

“No maybe gobe shi ma maybe”

“Okay sai anjima, a sha aikin lafiya”

“Thank you Sis, be a good girl please”

“I will.... See you soon”

Ta ja kofar ta rufe masa, tare da rakiyar wani sojan ta fita gurin zancen gilashin
da ya bawa Hurriya ya tsaya mata a rai, kuma yana kokarin gushe mata duk wani
farinciki da take ji na sakata neman turare da yayi. Amman what if shi ba da wata
manufa yayi ba? Balle ma yadda yake da halinsa anya zai iya da tafiya da Hurriya?

“Yarinyar nan tana da shegen kyau zata iya jan hankalinsa kamar yadda ta ja
hankalin Salim, gashi har yana fadar wai ta yi sa'a yana iya controlling kansa”

Ta amsawa kanta da kanta tana juya sitiyarin motar, zuciyarta na raya mata karya da
gaskiya deep down inside her ta san she feels jealous why zai bata gilashi bayan ta
ki farko few years back, and why ma zai ce ta kawo masa abinci?

“Saboda kin tafi siyo masa turare Namra, shi ma abun alfahari ne zai saka turaren
da kika siya masa so wannan ma ba wani abun daga hankali ba ne”

Ta bawa kanta amsa a daidai lokacin da masu gadin gidan suka bude mata gate.
Misalin karfe 8:30pm Hurriya na dakinta kwance ta soma jin kara kamar ana jifan
gilashin windows dinta, bata saka ran wani zai yi haka, wannan ya sska bata damu ta
tashi ta duba ba, har sai da ta ji jifan yayi yawa, sannan ta sauka daga kan gadon
ta nufi windows, curtains din ta fara dagewa ta leka waje mutum ya hango sanye da
kananan kaya komai fari, ta bude window tana kallon Captain dake kasa, sai ya jefar
da dutsen dake hannunsa ya dago dayan hannunsa dake rike da karamin bokitin roba ya
nuna mata sannan ya aje a kasa, ya nufi hanyar da kofar falon Momy yake, ta nan kam
ba zaka iya hango wanda zai fito ko ya shiga falon na Momy ba. Kamar yadda wanda ke
tsaye a bakin kofar baya iya ganin wanda ke sama har sai ya fito daga gurin. A bude
ta bar window ta juyo da sauri ta bude karamin teburinta dake gurin ta dauko
takardar da pen ta yi rubutu a jiki da girma yadda zai gani sannan ta nade takardar
a hannunta ta nufi kofar fita ta bude ta sauka falon. Ko da wasa be kalli inda take
ba yana ta magana da Momy dake tambayarta ya aiki.

“Aiki kam akwai shi kwana biyu nan, yanzu haka a gajiye nake i need to rest gobe ma
da wuri zamu fara”
“Namra ta fada min ta same ka kana ta aiki dazun, daman kuna haka ne”

“Yeah idan ana karshen shekara da kuma canjin duty ana samun irin haka, lafiya
kalau”

Ya karashe tare da amsa gaisuwar da Hurriya take masa, sai a lokacin ya kalleta ya
dauke idonsa.

“Ina Namra?”

“Tana bangaren mahaifinta ko a kira ta?”

“No, ni ma wucewa zan yi”

“Yanzu? Na dauka abincin dare zaka ci”

“No na ci abinci Wallahi, har fa na shiga gida na tuna ban siye abu ba dole na
fito, shiyasa na biyo nan”

Hurriya ta fice daga falon har da hadawa da sauri ta nufi gurin da ya aje mata
karamin bokitin, sai da ta fara daga bokitin ta cire karamin tawul din dake sama
sai ta yi arba da bakar leda da kuma fara har ta yi kamar zata bude wata zuciyar ta
raya mata Momy ko Namra za su iya tararda ita a gurin dan haka ta aje masa takadar
da ta rubuto tun a dakinta ta dauki bokitin ta juyo ta dawo cikin falon a daidai
lokacin da Captain ya mike tsaye. Momy na ganinta ta fara masifa

“Kin fa san bana son tsautsauniya, miye haka”

“Abun da na shanya dazun ne”

Ta amsa da sauri tana wucewa, Captain ya kalleta irin kallon nan na ashe ita ma ta
iya karya, ita dai bata juyo ba har ta shige dakinta. Har bakin kofar falo Momy ta
rakoshi kamar yadda ta saba, shi kuma ya gangara ya fara sauka yana duban gurin ya
hango takarda a aje, kai tsaye ya nufi gurin ya dauki takardar Momy na can tsaye
kofar falon tana son sai ta ga wucewarsa sannan ta koma ciki.

‘Ba zan iya amfani da wannan gilashin ba, saboda Hamad ya hanani karba, idan ina
amfani da shi zan ji kamar na aikata laifi ne, yana tuna min da dan'uwana dan Allah
ka ba ni nawa please’

Shi ne rubuce a jikin takardar, kansa ya daga sama ya kalli window dake bude amman
be ganta ba, daman ai ba zata bari ya ganta ba saboda ta san ta aje masa sako.

“Wani abun ne?”

Momy ta tambaya.

“Aa takardar dana fito da ita ce dazun ta fadi”

Sannan ya juya ya nufi motarsa.

“Momy da kin koma ciki akwai aikin da zan karasa a mota kamin na tafi”

“Toh shikenan Captain Allah ya tsare hanya sai da safe”

“Sai da safe Momy”

Ya bude motar ya shiga ciki ya zauna ita kuma ta koma ciki, a lokacin ne Hurriya ta
samu dagowa ta leko window kadan ta yi saurin labewa tana lekonsa ya dade a cikin
motar sannan ya fito ya aje mata takardar a daidai inda ta aje masa, sannan ya koma
cikin motarsa yayi mata key ya juyata ya bar gidan, sai ta ga fitarsa sannan ta
fito dakin da sauri ta sauko falon, samun falon babu kowa ya saka ta ji kamar ta
zuba ruwa a kasa ta sha, sub sub sub ta fice kamar wanda zata yi sata ta dauko
takardar bata tsaya dubawa a can ba ya dawo falon tana hadawa da gudu, domin yanzu
idan Momy ta tambaye me take yi ma yawo bata san me zata ce ba, da sauri ta shige
dakinta ta rufe kofar ta nufi window dinta ta rufe ta saki curtains din sannan ta
zauna ta duba takardar, ganin rubutun dake jikin takardar wanda ta ba shi ne ya
saka ta mamaki, ta juya baya me zata gani zanen bindiga ne pistol da karamin
harsashe, (Albarushi) a jiki. Wani irin faduwa gabanta yayi sai ta ji kamar
bindigar ce ya aje mata ba zane ba, daga saka kuma hannunsa ne. Ta aje takadarda
tana jin kamar ta yi kuka, ta janyo sabon bikitin ta cire tawul din ciki ta dauko
ledodi, leda ta farko ice cream ne da youghurt ga wata madara mai sanyi, leda ta
biyu kuma cake ne da gas meat. Sai gata ta sauko kasa ta zauna ta bude gas meat din
tana hadeye yawu, ta manta when last ta ci gas meat not because of babu kudin siye
a gidansu, sai dan babu wanda yake damuwa ya siya mata wani abun da take so, kuma
mahaifiyarta bata gidan balle ta fada mata tana son kaza da kaza. Har ta fara ci ta
tuna wani abu ta yi saurin tashi ta sakawa kofar dakinta key ta dawo ta zauna ta
bude Fresh milk din mai sanyi ta sha, sanyin ya ratsata har ciki zuciyarta, sai
gata tana murmushi daman bakin Hurriya ya san dadi.

“Yana da kirki wannan Captain din, even though ya mareni, amma kowa yana da good
and bad side right? But me yasa yake min dole? Har da bazarana da bindiga, ni dai
ba zan sake yi masa magana ba maybe next time zai iya dora min ita a kai, aiko zan
iya suma ma”

Ta kai naman a bakinta tana taunawa dadin naman har kwakwalwarta yake kaiwa ziyara.

“Tsorata musulmi dai haramun ne”

Ta fada tana turo baki. (Ni ko na ce Hurriya manya amman ba shi kayan dadi halak ne
ko 😁) sai ta ci naman ta koshi sannan ta rufe sauran tana jin kamar ace ita ma tana
da karamin freezer kamar Yayarta Namra da yanzu sai ta saka komai a ciki ta aje.
Cake din ta janyo ta bude ta gutsuri kadan ta ci, da dadin yayi mata yawa sai a
tsikaro mata wani tunanin, ta tashi da sauri ta dauko takardar da yayi mata zanen
bindiga ta bude gurin ajiyarta ta dauko karamin katin da wani ya bata a lokacin da
aka dauke Hamad ta dauko ta hada su guri daya tana duba yanayin rubutun sa hannun
hannun da handwriting din duk kala daya ne.

“Laa shi ne mutumen da ya ba ni abun nan?”

Ta fada tana tuna lokacin da ta shigo falon har ta tambaye shi waye ya ce mata soja
ne, ta ce yayi mata alkwarin zai taimaka ya dawo mata da dan'uwanta kuma yayi mata,
mamaki ya kara cikata, har tana jin kamar ace tana da wani abokin tattaunawa ta
fada masa. Da mamaki ta kwanta kamin tunanin dan'uwanta ya biyo baya, ita dai kam
ta san ta yi marmarin dan'uwanta sosai, fadan da suke be hana su yin hira ko gulmar
wani a tare da juna, shi zai daketa amman idan wani ya taba ta sai inda karfinsa ya
kare da yana nan a yanzu ta san wasu abubuwa za su zo mata da sauki. Hawayen da ya
zubo mata ne ya share ta sauko saman gadon ta nufi kofar dakin ta bude ta sauka
kasa, a falo ta hadu da Namra tana cin abincin dare, ta kalli abinci ta dauke kai
domin a koshe take but da ace bata ci ba babu wanda zai ce Hurriya sauko ki ci
abincin, kuma idan ta zo cin zai iya zame mata matsala ace ta yi wani abu ba daidai
ba. Ficewa ta yi tana daga kai ta kalli hadarin dake haduwa a sama iska ya kadawa
kamar zai taso. Bangaren Hajiya Kaltume ta nufa ta shiga falon, sai da ta fara
gaishe da Khairy da wata Cousin dinta ta bangaren Hajiya Kaltume da ta zo gidan,
sannan ta gaishe da Salma dake playing game da Ruma.

“Kamar kin san ina nemanki, daman na ce akwai birthday wata friend dinmu da za ayi
gobe zaki je?”

Khairy ta fada cikin far'a. Sai Hurriya ta bata red card.

“Aa”

“Why? Ki rika fita cikin mutane mana kina hutawa kina bude ido ya fi miki zama
kullum a gida kuma ba school kike zuwa ba”

“Ni dai na fi son zama a gida, bana jin fita gobe”

“To jibi zaki je? Za a yi wani jibi ma, kuma wannan ma ina jin kamar tace zata daga
zuwa jibi”

Hurriya ta kalleta tana mamakin yadda take son cilasta mata fita a gobe ko jibi.

“Aa Yaya Khairy idan kika ga na fita gidan nan to wani babban abu ne ya fitar da
ni, kamar duniya ko ciwo ko aika, amman ba fita haka nan kawai dan na shakata ba”

“Toh.... Kika gane? Aiko zaki takura yarinyar kara ma ki sake jikinki ki yi yawa,
shiyasa ko kawaye baki da idan an tashi aurenki ban san ya zaki yi ba, ke gaba daya
baki son shiga cikin mutane kamar wata kura”

“Ina jin dadin yin haka, na saba ne. Yayana yana ciki gurinsa na zo”

Daga karshe ta tambayi abun da ya fi mata muhimmancin bayan ta bata amsa, daman
saboda ta yi magana da shi ta zo bangaren.

“Eh yana dakinsa”

Ta nufi stairs Khairy ta bita da harara tana yatsina fuska.

“Wannan yarinyar akwai shegen taurin kai”

Jannat kalleta.

“To ke dole sai kin tafi da ita? Sai ki kyaleta mana, ni fa bana ma son shiga da
kanena cikin kawayena Wallahi”

“Ni ma ai dole ce ta saka akwai dalili, if not ta isa ma na tsaya ina lallabata
Mtcheeee”

Taja wani guntun tsaki. Hurriya da bata san wainar da ake toyawa ba haye sama ta
shiga dakin dayanta bayan ta yi knocking bata ji an amsa mata ba. Babu kowa dakin
sai dai tana jin motsin ruwa a bandaki tana gane yana ciki dan haka ta nufi gefen
gadonsa ta zauna kusa da wayarsa, karanbani ya saka ta dauki wayarsa tana tabawa ta
kawo haske amman bata bude ba sai an saka password, kamar zata cinye wayar haka ta
kurawa screen din wayar ido tana kallon hoton Mama Rukayya dake jikin screen din ta
yi masifar kyau ta sha makeup din zamani.

“Ke me kike yi da wayata?”

Ta dago da sauri ta dubi kofar bandakin sai kuma ta yi murmushi.

“Yayana hoton Mama Rukky ne a wayarka”

“To ya aka yi?”

“Ba ayi komai ba”


“Me ya kawo ki dakina? Gulma kika zo yi min?”

Ta washe hakora gaba daya ta manta da me kawo ta ma.

“Get out”

Ta mike tsaye tana dariya zata fice, sannan ta tuna dalilinta na zuwa ya juyo da ta
dawo.

“Yauwa Yayana na tuna abun da ya kawo ni ma”

“Minene?”

“Gilashina da yake hannunka wanda na baka ajiya, tun da dadewa ka tuna?”

“Na tuna, ya aka yi?”

“Daya zaka ba ni please”

“Why”

“Zan saka ne”

“Wannan da yake idonki fa?”

“Shi ai shi ba wanda Appa ya siya min ba ne”

“Waya siya miki”

“Ni dai ka ba ni zan yi amfani da daya”

“Wallahi ba duba tun a lokacin da aka taba fasa miki gialshin na bincika ko'ina ban
ganshi ba, ban san ya aka yi ya bata ba”

“Yaya ka sake dubawa idan ka gani ka ba ni”

“Okay”

“Toh, Yaya yau ka je gurin Mama Rukayya? Ko zaka je?”

Ya watsa mata wata kalar harara.

“Hurriya yaushe na fara wasa da ke?”

Ta fice da sauri tana dariya, a yanzu kam ta tabbatar Yayanta yana son kanwar
mahaifiyarta, idan haka kuma ya kasance zata fi kowa farincikin domin dukansu tana
sonsu. Bangaren Momy ta dawo ta shiga dakinta ta yi wanka sannan ta saka kayan
bachi ta yi addu'a ta yi karatun suratul milk sannan ta kwanta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

HAJIYA KALTUME POV.

Kai ta daga sama tana karewa dakin kallo wanda ya kasance na kasa ne ko'ina sai
kulli kullin yawu da aka sarkafa, sai mayan allunan karfe da madubai ga kuma ruwa a
kasko da karya ga kwalabe ta ko'ina kana shiga gurin zaka fahimci wane irin mutum
ne, balle kuma hancin mutum yayi arba da gawurtaccen kamshi turaren aljannu dake
tashi har wani juyin kai yake sakawa. Cikin hikima Hajiya Kaltume ta jinjina kai
tana jin dadi, ganin take kamar ciwonta ya warke ma gaba daya. Yana shigowa cikin
dakin ta gyara zamanta ta matsa baya tana kallonsa.

“Malam an shigo”

Ya zauna yana fadin.

“Da dai zaki kirani da Dan masani, ko na gangare zai fi Hajiya”

“Toh dan masani, sannu da kokari”

“Yauwa sannu dai Hajiya”

“Ya gidan ya iyali da komai”

“Komai lafiya kalau, Hajiya”

Ta dauko katon madubi ya dora a cinyarsa.

“Daman... ”

Zata fara bayani ya daga mata hannu, ya dangwalo yawun bakinsa yayi rubutu da shi,
sannan ya kalleta ya girgiza kai ya maida idonsa a gurin madubin, ya fi karfin
minti ashirin a haka sannan ya dago ya kalleta ya ce.

“Kanwar Kulu ta kawo ki nan ko?”

“Eh haka ne, can gidansu na fara zuwa sannan aka kawo ni nan”

“Na gani ai, kuma kin zo nan ne saboda mijinki zai kara aure, gashi kuma ya canja
miki, ga danki yana son auren yar kishiyarki da ta fita, kuma kina fargabar kar
ciwon da kika aika mata ya karya ta tashi mijinki ya ce zai dawo da ita, sannan
kina yawan faduwa har ki ji ciwo a kafa har kika tsoron ko an miki ture ne”

Ta daga masa kai.

“Hakkun babu musu a maganarka take”

Yayi dariya.

“An fada mana komai ai”

“Haka nake so, yanzu so nake a hana ďana auren yar iskar yarinyar, kuma a hana
mijina aure, sannan a dauke hankalinsa daga gurin kowa sai ni, idan da hali ma
wannan matar da take tare da shi abokiyar zamana ita ma a koreta, sannan bana son
mijina ya dawo da Iyami, kuma ciwon kafar nan ba turo min aka yi? Ni har tsoron
faduwar nake ji kar naje na fada a inda be kamata ba kafar ta cire ko ta karye na
shiga uku”

“Duk za'ayi Hajiya, amman sai kin daure kuma kin shirya domin ni bana aiki da wasa,
ciwon kafarki kuma babu wani ture babu aljannu babu komai, daga Allah ne”

“Toh Alhamdulillah yanzu hankali ya dan kwanta, kuma daman ni ai haka nake so,
yanzu miye abun yi?”

Ya aje madubin dake jikinsa gefe daya ya dubeta.

“Ina mai tabbatar miki da wani abu, tabbas mijinki zai dawo da abokiyar zamanki da
kike tsoron ya dawo da ita, matukar baki tashi tsaye ba”

Hajiya Kaltume ta dora hannu a kai tana jin wani karin tashin hankali na kusantota.

“Shiyasa na zo gurinka ai, dan Allah a hana ya maido da ita”

“Za'a iya hakan ne kadai idan zaki iya daukar nauyin jini, amman muddin matar nan
tana raye babu makawa sai ta dawo gidanki”

“Dan masani me kake nufi kenan?”

“Ni matsala ta bana boyo kuma duk abun da na gani ina fadawa mutum gaskiya, amman
ina aiki na gaskiya, abun da ya fi kawai mu yi ma matar nan halbin kasko domin
matukar tana raye Wallahi ina mai tabbatar miki mijinki sai ya sake zaman aure da
ita”

“Dan masani babu wata hanyar sai kisa? Kar abun yayi min yawa?”

Yayi dariya.

“Ashe baki shirya kenan kika zo, baki shirya mallakar mijinki ba, kuma baki shirya
hana kishiyarki dawawa ba, gaskiya ban ga wata mafita a nan ba bayan wannan, domin
madubin nan baya kara kuma ya nuna min akwai sauran zama a tsakaninsu”

Hajiya Kaltume ta yi shiru na wasu dakiku sannan ta sauke ajiyar zuciya ta ce.

“To maganar mallakar Alhaji fa? Da kuma hana dana aure”

“Za a yi miki na mallaka zaki mallake Alhaji ki koma kamar uwarsa, karki damu da
wannan amman fa zaki zuba kudi”

“Kamar nawa Malam?”

“A kalla za a kashe 50k”

Ta yi murmushi 50k abu ne mai sauki idan dai zata samu biyan bukata.

“50k ma matsala ba ne, zan bada fiye da haka ma, amman a duba idan akwai wani aiki
mai sauki da ba sai kisa ba sai ayi”

“Bari kiji na fada miki, matar nan ma tana nan ta fara tashi domin wanda kika saka
yayi miki aikin nan ya fara karya aikin, tabbas kuwa zata dawo cikin gidanki, kuma
dawowarta yana nufin fitarki”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, fita ta kuma? Ai ni shi ne tashin hankalina, ta
zauna ma ya na kare balle ita tana ciki ni ina waje?”

Gaba daya sai hankalinta ya tashi ta ji wani gumi na keto mata.

“Amman kana ganin idan an aikata aikin zai yiyu?”

“Me zai hana? Saboda hasarin halbin kasko idan be sameta zai iya fadawa akan
jininta shakiki kamar danta ko yarta”

Hajiya Kaltume ta taba hannu biyu.

“Shikenan ma daman yarta ta isheni a duniyar nan, a aikata mata kawai ka ga aikata
mata zai saka su ji tsoro su hana Yasir Rukayya, kuma zan huta nima hankali ya
kwanta, amman ina lafiya idan aka ce zata dawo kuma ni na fita”

“Idan aka yi haka babu ita babu mijinki har abada”

“Toh yanzu yaushe za'ayi aikin”

“A yanzu ma idan kika bada kudi, sai a dauko kayan hadi a kira aljannu, cikin dare
za'ayi halbi kin ga ruwan da yake cikin kaskoncan? A cikinsa za a halba idan aka
gabatar da aiki aka yi halbi da dare kamin safe sako ya isar mata, amman fa tabbas
idan be sameta ba zai fada akan yarta balle ma ita muke fatan ya samu”

“Akan samu irin haka ne, ayi ma mutum aiki kuma ya zama be fada kansa ba?”

“Ban taba samun irin haka ba, gaskiya wani lokacin ma akan fada ma mutum biyu da
uwa da jininta, kawai ina tabbatar miki karfin aikin ne”

“Zan biya kudin, zan bada 200k gaba daya, ina son a hana dana aure kuma a janyo
hankalin mijina a gareni sannan kuma a hana shi aure wacan yarinyar da yake
hasashen aure a yi musu farraqu”

Dan masani na jin 200k ya ji ransa yayi wasai kudin wata gona da wani gidan kauye
har da fili ma.

“Hajiya ni ko ina tabbatar miki, kuma na miki alkawari tsakanin yau zuwa gobe zaki
tashi da labari mai dadi akan kishiyarki, na mallaka kuma akwai aikin da zan hana
sai ki aiko ko kuma ki zo da kanki jibi ki karba, da zarar ya ci an gama da shi, a
game da auren da zai kara kuma wannan ni an san aikin da zan yi, mai irin sunan
yarinyar ma ba zai sake sha'awa ba”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi ya jinjina kai

“Haka nake so, so nake na mallake komai a gidan nan, ya zama be ganin kowa sai ni
da Yayana, Hurriya ma ina son a cire masa ita a rai kwatakwata”

Ta saka hannunta a jaka ta dauko 200k ta aje masa.

“Idan bukata ta biya zan baka ninkin wannan, ni dai burina ayi aiki yayi”

“Aiki kam ya gama, tashi ki yi tafiyarki”

“Na Gode dan masani”

Ta mike tsaye tana jin kamar an yaye mata damuwarta gaba daya, tunanin kar ta
daukarwa kanta hakki da yawa duk ya kau saboda ta ji ance zata fiya Iyami ta dawo.
Bata bar garin ba sai da ta sake komawa gidansu Kulu ta yi musu alheri kowa ta
bishi da 1k sannan ta shiga motarta direbanta ya kama hanya, suna mata addu'a bayan
sun gama murna da jindadin kyautar da ta yi musu. Ta isa gida cikin farinciki kamar
wata wanda ta aikin jihadi, tana shiga bangarenta ta yi wanka ta yi sallah sannan
ta fito ta shiga Kitchen da taimakon Salma da Khairy suka gama girkin dare, sannan
ta koma dakinta su kuma zauna a falo. Bayan gama sallah magariba ne yar yayarta ta
shigo gidan daman ta kan zo jefi jefi idan an yi hutu. Hajiya Kaltume ta yi murna
da zuwanta sosai daman suka sha hira a dakin kamin ta shiga da kayanta a dakin
Khairy. Misalin karfe tara daidai Hajiya ta dauki abinci mijinta ta shiga
bangarensada kanta ta kai masa, so take ta dawo da al'adarta ta kai masa abinci da
kanta saboda ta samu damar tsare shi kuma ta tabbatar ya ci abincin idan ya saka
maganin da bokanta dan masani zai bata. Sai dai gaba daya ya lura da yanayinta be
sauko ba daga tsabanin da suka samu jiya, har yanzu fuska a daure take kuma tun
bayan da ta gaishe shi ya amsa be sake ce mata komai ba, ita kuma bata yi yunkurin
wani abu ba, har sai da ya fara cin abinci, sannan ta dawo gabansa ta zauna ta zuba
masa ruwa.

“Wai Alhaji yanzu saboda dan tsabanin da muka samu jiya shi ne kake ta wannan
fushin? Yaushe rabon da ka yi fushi da ni haka?”

Yayi kamar be ji ta ba ya cigaba da cin abincinsa.

“Ayi hakuri ranka ya dade a gafarci Kaltume, ban san abun zai zama haka ba, idan
aure ne ayi ta yi kai zaka zauna da su ba ni ba, ita m Iyami Allah ya bata lafiya
ka dawo da ita ta rike yaranta”

“Ameen”

Ya amsa ba tare da ya kalleta ba, sai ta ji kamar ta dauki murfin kular da yake cin
abinci ta buga masa a kai saboda bakincikin amsawa da yayi da amin. Sai dai tuna
abun da ta taka ya saka ta yi murmushi ta kawar da duk wani bacin rai daga
zuciyarta... Sai da ya gama cin abinci ya sha ruwa sannan Namra ta kwankwasa kofar
karamin falon nasa.

“Waye?”

Hajiya ya tambaya tana harara kofar a zatonta ma yar makiyiyarta ce.

“Shigo”

Appa ya amsa mata da kansa yana gyara, ta turo kofar falon ta shigo, ganin Hajiya
Kaltume ya saka ta ji babu dadi domin tana son magana da Appanta private ne. Ta
zauna kusa Hajiya Kaltume dake kallonta tana raya abubuwan da za su faru nan da yan
kwanaki kadan idan ta mallake mijinta.

“Appa barka da dare”

“Barka dai Namra, ya kike?”

“Lafiya Kalau Appa”

Sai ta yi shiru.

“Akwai wata matsala ne?”

Ta dan kalli Hajiya Kaltume ta kalli Appa.

“Daman ina son magana da kai ne, amman zan bari sai da safe sai mu yi maganar kamin
ka fita”
“Privacy kike so?”

Ta daga kai. Appa ya kalli Hajiya Kaltume kai tsaye yace.

“Kaltume mu shiga bedroom mu bar miki nan ko kuma ke zaki shiga”

Hajiya Kaltume ta dubi Appa da mamaki sai dai bata ce komai ba ta yi murmushi.

“Aa bari ni na shiga, Namra a kebe lafiya”

Ta yunkura ta tashi tsaye ta nufi bedroom din Appa ta shiga ta rufe dakin, a nan ta
samu damar yin kwafa ta cize baki.

“Nan da dan lokaci komai zai canja, ke ma idan baki yi hankali ba sai kin fi
Hurriya shiga matsala ke da uwarki duk sai kun zama abun tausayi”

Ta zauna kan sofa tana matsa kafarta dake dake gwada son yi mata ciwo kamar jiya.

“Wai ni Alhaji zai cewa na ba shi guri zai yi magana da Namra, da dane ko fadar
haka da ta yi ai sai yayi mata fada, amman ba komai duk a tafin hannuna zaku dawo
sai na juya ku kamar waina”

Sai da Appa ya gama maganar da zai yi da yarsa sannan ya shigo dakin cikin wani
yanayi na rashin yabo da fallasa ya zauna bakin gadonsa yana kasa wayar hannunsa,
kamin ya dago ya kalli Hajiya Kaltume ya ce.

“Tun shekaranjiya nake wani tunani”

“Kamar na me Alhaji?”

Ya sauke ajiyar zuciya.

“Ina tunanin yaran nan ne da Iyami ta haifa, twins Hamid da little Hamad, tun da
aka haifi yaran nan ban taba zuwa dubasu ba a matsayina an ubansu”

Hajiya Kaltume ta ji gabanta ya fadi irin faduwar da be taba yi ba, yau Appa ya
fadi abun da bata kawo ran faruwar sa a nan kusa ba, lallai a yanzu ta yarda
Malamin da yayi mata aikin ya fara karya shi saboda yana son ta ba shi kudi mai
yawa ya mallaketa kamar yadda ya mallake Hajiya Fateee da bata ma son a fadi
laifinsa. Babu wani abin da zata yi a yanzu da ya wuce ta boye komaia kasan
zuciyarta, dan haka ta yi karfin halin murmushin da za a iya cewa ya zame mata na
dole ne kawai ta ce.

“Toh Alhaji ai za a iya zuwa ka dubasu ai yaranka ne, ni zan iya raka ma sai mu
tafi tare, ba wani abu ba ne”

Wannan karon ajiyar zuciyar da Appa ya sauke mai nauyi ce sosai.

“Ina jin nauyin hakan, saboda na juyawa yaran nan baya na ci amanarsu ba tare da
sun min komai ba, ina tunanin zan dauko su amman me zan ce idan zan aika a dauko
su? Kai....”

Ya busar da iskar data cika masa baki sannan ya tattare girarsa guri daya yana jin
rashin dadin a abun da yayi ma yaran nasa da suka kasance jininsa.

“To ai ba abin kunya ba ne Alhaji, yaranka ne kuma idan acan baya ka yi kurkure
yanzu ai gyara kake kokarin yi, karka dauki wannan a matsayin matsala dan Allah
shirya ka je ka duba su ko kuma a dauko maka su”
“Ban gama yanke shawara ba tukuna, zan yi tunanin abun da ya kamata na yi”

Ya amsa mata sannan ya aje wayar ya hau saman gadon, ita kuma ta juyar da fuskarsa
a dayan gefen tana kashe ido wani bakin kishi na cizon zuciyarta, sai a yanzu take
jin ta yi daidai ta ya yarda a ayi ma Iyami halbin kasko domin bata san da wane
irin zata sake dawowa gidan ta ba idan Appa ya maida ita gidan.
Kamin safiya ta waye Hajiya Kaltume ta matso saboda bokanta ya fada mata cewar idan
yayi aikin da dare ya halba mata kamin safe bukata ta biya kuma ita ta yarda da
hakan, sai da ta baro bangaren Appa ta dawo bangarenta take cin ciwon rashin karbo
number wayar dan masani da bata yi ba, da yanzu sai ta tambaye shi ya samu yin
aikin ko be samu ba. Kitchen din ta ta shiga ita da Ruma suna shrya abun karyawa,
Khairy da Salma kam ana can wata duniya ana sharar bachi musamman ma Khairy da bata
kwantawa sai ta sha abun da zai jefata a bachi mai nisa. Ita ma Ruma bata saba
tashi da wuri ba saboda uwarsu bata koya musu tashin da wuri, sai dai yau ta tashi
saboda tana da lecture 8 na safe. Suna shirya abun karyawar Hajiya Kaltume na
tunanin kalaman da Dan masani yayi mata, kuma yanzu ta fara tabbatar da haka, domin
a yanzu ta lura idan ta yarda ta fadi wata maganar akan Iyami Appa zai iya bata
nata rai, balle kuma ace ya dawo, wata kila milkin da zata yi a yanzu zai fi an can
baya, gashi yanzu ta haifi yara biyu maza ita kuma tana da daya ga son da yake yi
ma Hurriya zai dawo, su ma kananan yaran zai fara nuna musu gata, sannan kanwarta
ta aure danta dadi kan dadi, ga kuma wani auren da zai kara, above all ita ya
saketa.

“Kam uban can kai....Gwuttt”

Ta yi kwafa har sai da Ruma ta kalleta.

“Hajiya lafiya?”

“Lafiya kalau je ki taso yan'uwanki su tashi haka mana, wata kila ma ko sallah ba
su yi ba”

Ta juya ta fice daga kitchen din. Hajiya Kaltume ta bita da kallo tana tunanin
zuci.

“Hmmm wato ya sake ni ko? Ai kara ma a kasheta idan aka kasheta iyayenta ma za su
yi hankali tun da na gane kwadayi yayi musu yawa har suna son daukar wata yar au
aurawa Yasir, zan koya musu hankali”

Tana maganar tana wani huci kamar macijiya, sanin mijinta baya karyawa da wuri a
weekend days kuma today Saturday ya saka ta shiga dakinta dan ta kishingida, sai
dai me tunanin yadda abubuwan suka soma sauyawa mata a lokaci daya ya saka ta kasa
bachin na safe, ta dayan bangaren kuma idan ta tuna matakin data fara dauka sai ta
ji ranta yayi fari. Kadan kadan bachi ya fara fisgarta saboda bata samun yin na
dare ba yadda ta saba saboda tunani ganin take komai kamar mafarki ne.

“Hajiya ni kam na wuce”

Ta zabura ta bude idon da sauri sakamakon maganar da Ruma ta yi mata, tana cikin
shirinta na na fita ta goya teddy bag dinta a baya.

“Kin yi breakfast?”

“Eh na yi”

“Khairy sun tashi?”

“Na tasheta daker ta tashi ita Kuma Salma na ta tashinta ta ki tashi”


“Toh Allah ya kiyaye”

“Amin”

Taja mata kofar dakin, kamin ta rufe Yasir ya turo kofar dakin ya shigo.

“Hajiya Ina kwana?”

“Idan ban kwana ba zaka gan ki, Alhaji Yasir mijin Rukayya”

Kalaminta be masa dadi ba ko kadan, fushin da ta yi da yi da shi da safe ma be


jidadin haka ba balle kuma yanzu da abun ya biyo har da bakar magana.

“Ayi hakuri Hajiya”

“Hakuri daya ne, ka hakura da abun da uwarka bata so, shi ne mafita agareka, idan
ba haka ba zaka janyowa kanka abun da ba zaka iya dauka ba”

“Toh Hajiya”

Ya mike tsaye ya fice daga dakin. Hajiya Kaltume ta taja uban tsaki.

“Idan ban tashi tsaye ba wai sai su kasheni wadannan, gaba daya basa tausayina daga
shi har ubansa”

Ta juya kwanciyarta, sai kuma ta ji bachin baya mata dadi ta tashi zaune.

“Har neman hanani bachi suke saboda tashin hankali”

Ta mike tsaye ta shiga bandaki, sai da ta yi wanka sannan ta fito ta shirya cikin
Holland wax ta saka turare ta fito daga dakinta ta shiga dakin Khairy, saman carpet
ta sameta zaune da alama sai a lokacin ta yi Sallah.

“Khairy sak yanzu kika yi sallah asuba?”

Khairy ta juyo ta kalleta.

“Bachi na yi da yawa shiyasa”

“Wallahi ku daina wasa da sallah, duk wani abun da zaka aikata idan Sallah ka yayi
kyau to komai zai zo da sauki”

“Toh Hajiya zan kiyaye next time”

“Haka kike cewa kullum, idan kin yi breakfast ki gyara gidan zan shiga bangaren
mahaifinku, ita Salma ta tashi?”

“Ban sani ba, tana dakinta”

“Ina Jannat?”

“Ta sauka kasa tana falo ko dinning”

Tana amsawa mahaifiyarta tana hamma domin har lokacin bachin be gama da ita ba.
Hajiya ta ja mata kofar ta nufi dakin Salma dake leke da na Khairy ta tura sai ta
hangota kwance kan gado, ta baya kofar dakin baya tana fuskarta windows.

“Umm Salma.... Umm Salma..”


Haka Hajiya ta yi ta kiranta tana fadan ba su san su tashi da asuba su yi sallah ba
kullum sai an tashesu. A dolenta ta daure ta shiga ciki ta kai hannu ta taba
jikinta tana bugawa.

“Umm Salma...”

Nan ma bata amsa ba bata motsa ba, Hajiya ta juyo sai ta juyo kamar wanda ta
sankare. Fuskar mamaki da tsoro Hajiya Kaltume ta yi, ta kama hannunta ta rika sai
ta ji yayi sanyi kuma ya saki.

“Salma... ”

Ta kirata da karfi, ta kai hannu ta taba zuciyarta, sannan ta zauna ta mirginota,


ta kwantar da kanta a kirjinta bata ji zuciyar na bugawa ba, jiki na rawa ta saka
hannu a hancinta nan ma dai bata ji numfashinta ba, ta kai hannu biyu ta daga
idonta sai ta gansu a kafe babu alamar Salma ta san inda take. Duk wani nauyin jiki
da kiba haka ta manta da su ta yi wani tsalle daga bakin gadon zuwa baki kofar
dakin.

“Khairy.... Yasir ku zo ku duba yar'uwarku....”

Ta fice da gudu kamar zata fadi tsabar tashin hankali har jin take kamar babu
zuciya a kirjinta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Cikin tsananin tashin hankali aka kwashi Salma zuwa asibitin, duk kuwa da
kasancewar alamun tafiyar da babu dawowa ya bayyana a jikinta amman Hajiya Kaltume
bata yarda yarta ta mutu ba sai da likitoci suka tabbatar da haka. Tun a asibitin
Hajiya Kaltume take kirewa tana faduwa ta tashi tana kuka irin na tashin hankalin
da ba a saka masa rana, Appa ma duk juriyarsa sai da ya zubar da hawaye a cikin
asibitin, dominta abun tausayi ne, yarinyar data kare makaranta few weeks ta dawo
gida cikin aminci da koshin lafiya, babu ciwo babu komai an wayi gari babu ita a
yau.
Hauka ne kawai Hajiya Kaltume bata yi ba a lokacin da aka iso da gawar yarta gida,
Khairy ma idonta har ya canja kala, Ruma ma da kuka ta baro makaranta ta dawo gida,
Namra da Hurriya ma duk sai da suka zubar da hawaye na tashin hankali da mamakin
mutuwarta, abun ya taba kowa balle kuma Yasir da ya dauke ya kaita asibiti.
Da azahar aka yi mata sallah, a lokacin gidan na cike da jama'a domin wannan ne
karo na biyu da Appa yayi rashi mai girma bayan na Hamad. Hankalin Hurriya ya tashi
sosai a lokacin da ta yi arba da gawar Salma da aka daga aka saka a mota, kuma aka
ja motar aka fita da ita wasu jama'ar na yi mata rakiya a cikin har da mahaifinta
da dan'uwanta da kuma wasu daga cikin familynta na kusa da na nesa, ta tabbatar a
yanzu Salma ta yi bankwana da kowa kenan har abada, lallai mutuwa akwai tashin
hankali da bakinciki da kuma ban tsoro. Ana tafiya da ita sai ta dawo daki ta zauna
gaba daya tsoro ya kamata kusan wannan ne karo na farko da ta yi arba da gawa ganin
idonta. Ganin da ta yi mata jiya da dare a lokacin da ta shiga ta yi magana da
Yasir kawai take tunawa. Misalin karfe biyu da mintuna tana dakinta kwance Inna
Shatu ta shigo kiranta, sai a lokacin ta taso ta fito duk hayaniyar mutane da take
ji na yan'uwan Momy wandanda suke kusa suna zuwa yi ma Appa da Hajiya Kaltume
gaisuwa ba saka Hurriya lekowa ta ga ko su waye ba. Tana fara saukowa stairs din ta
hango Mama Rukayya sai idonta ya cika da hawaye bata kula da kowa ba sai bayan da
ta fada jikin uwar tata tana kuka domin mutuwar ta taba matuka.

“Mama Rukayya kin ji Yaya Salma ta rasu”

“Gaisuwarta na zo, kowa baya wuce lokacinsa Hurriya, yanzu tsakaninku da ita sai
addu'a”

Tana fada tana sharewa Hurriya hawayenta. Sai a lokacin Hurriya ta lura da wasu
daga cikin yan'uwan Momy da suke falon, ba kowa ta sani ba amman haka ta bisu daya
bayan daya tana gaida su, wasu su amsa mata kai tsaye wasu kuma sai sun gama yanga
saboda sun san wacece ita da matsayinta a gurin Momy.

“Ina wuni”

Ta fada a lokacin da kai gurin Captain dake zaune kusa da wata matar mai kama da
Momy sai dai ita yarinya ce sosai da bata kai ace ta haife shi. Da kai ya amsa yana
kallon idonta dake cikin gilashi
Hurriya ta juya gurin Rukayya.

“Mama Rukayya mu tafi daki”

“Muje ki rakani gaisuwa tukuna”

Rukayya dake fada ta mike tsaye suka jera da Hurriya suka fice daga falon. Sai da
suka kusa fita harabar gidan sannan Rukayya ta kama hannun Hurriya ta tsayar da ita
daga tafiyar da suke.

“Ni fa ban so zuwa gaisuwar nan ba”

“Saboda me?”

“Saboda Hajiya Kaltume kin san matar nan ba wani kirki ne da ita ba, zata ma iya
cewa dadi muka ji, Yasir ne ya takura sai na zo, na fada masa bana son Hajiya
Kaltume ta yi wata magana yace min babu abun da zai faru”

“Ba zata yi komai ba, Mama Rukayya baki ga yadda ta yi kuka ba idonta ya kumbura
sosai ni tausayi ma take ba ni”

“Ke kiji tausayin kanki, ita ma ta dandana yadda muka ji lokacin da Hamad ya rasu,
ni da na sani ma wata zan janyo ta rakoni ko ma na saka mask, ina gudun Gwaggo ta
sani ne shiyasa na janyo twins na ce mata gidan kawata zan tafi, ba su san da
maganar mutuwar ba, da Yasir ya fada min ban fada musu ba, saboda na san Gwaggo
zata iya hanani zuwa amman ita ta zo, kuma Yasir ba zai jidadi ba idan ban zo ba,
sai na koma na fada musu”
Hurriya ta fara waige waige.

“Ina twins din suke?”

“Suna can tare da Yasir, suna ganinshi suka bishi, muje ki raka ni na yi gaisuwar
na koma”

Hurriya ta bita suka taka har bangaren Hajiya Kaltume dake cike da mutane ta ko'ina
domin wannan ne karo na farko da aka yi mata mutuwa mai nauyi, yan'uwa har nasa sun
zo saboda sun san mai hali take aure kowa binta yake sau da kafa a familynsu.
Hurriya bata san Hajiya Binta ta zo ba sai da ta shiga bangaren na Hajiya Kaltume,
da sauri Hurriya ta karasa kusa da ita ta zauna tana gaisheta. Hajiya ta amsa da
dan murmushi kadan.

“Hurriya tun dazun nake dubawa ban ganki, na ce kina can kin boya ko sarkin tsoron
mutane”

Hurriya ta share hawayen da suka zubo mata ta ce.

“Hajiya Salma ta tafi”

“To ya aka iya, sai hakuri haka rayuwarma zata kare, shiyasa ake son mutum ya ji
tsoron Allah ya bawa kansa lafiya, duniya ba gurin zama ba”

Yan'uwan Appa dake kusa da ita suka amsa da cewar haka ne, suna dorawa da nasu
sannan suka yi ma Hurriya ya hakuri ta amsa tana kuka kai kace Salma wani kaunarta
take. Rukkayya ma ta gaishe da Hajiya Binta sannan suka haura sama tare da Hurriya
suka shiga har cikin dakin Hajiya Kaltume, zaune suka sameta kan karamin Carpet
Khairy na kwance a cinyarta, kallo daya zaka yi mata ka san mutuwar nan ta taba ba,
ba karamin tabawa ba, domin ta fada a take ga ido ya kumbura kamar ya silala, har
bata iya daga ta duba mutane da kyau, Khairy ma nata idon ba baya ba domin ta sha
kukan da bata taba yi ba, Maama na zaune kan gadon Hajiya Kaltume ita ma kana ganin
nata idon zaka san an yi rashi a familyn.
Rukayyah ta mika gaisuwa aka rasa mai amsa mata daga Hajiyar har Maama da Khairy,
sai wasu yan'uwan Hajiyar ne suka amsa ta fara gaisuwa tana Allah ya jikanta suna
amsawa da Ameen. Hajiya Kaltume ta dago wasu hawayen na zubo mata bakincikin rasa
yarta na dawo mata farko, ganin Rukayya da ta yi, da yanzu su ne da kuka ba ita ba,
amman gashi nan reshe ya juye da mujiya.

“Rukkaya karki sake shigowa gidan nan, munafurci ya kawo ki saboda ki zo ki ga zan
yi tun da na rasa yata, kun jidadi ko? Azzaluman mutane, tun da Iyami ta auri
Alhaji ba ni da kwanciyar hankali, kum bi kun hanani zaman lafiya, kuma Wallahi
babu ke babu dana, ko mata sun kare a duniya Yasir ba zai auri karuwa yar iska
irinki ba, kuma Wallahi ke da yayarki sai mugun abun ku ya koma kanku, sai kum ga
abun da ba ku so, Allah ya isa”

A nan jama'a suka shiga bata hakuri, Hajiya Fatee na fitowa daga bandaki ta dorawa
Rukkaya da nata.

“Daman ban da iskanci da tsaurin ido, ke har kin isa ki taso tsugudi dake wai kin
zo gaisuwa, wato ke yar iska yar daukar rahoto, to sai kije ki fada musu yadda kika
tararda mu, mutuwa dai ta san gidan kowa”

Wata yayar Hajiya Kaltume ta shiga yi musu fada tana tsawarta a matsayinta na
babbar duk kuwa da bata san me yake faruwa ba amman zata iya auna wasu abubuwan a
kalaman da Hajiya Kaltume ta fada cewar ko mata sun kare ba zai auri Rukayya ba, a
lokacin ne suka gane cewar ita din kanwar Iyami ce. A fusace Rukkaya ta mike tsaye
“Ni ma zan tabbatar miki da wani abu yau, ko maza sun yi karamci a duniya ba zan
auri Yasir ba, amman gida kam idan kika ga na daina shigowa, to babu Hurriya a
cikinsa”

Tana kawai ta juya, Maama da Khairy suka taso zasu yi kanta, sai da aka rike su.
Hurriya ta kasa cewa komai ita dai sai mamakin yadda Hajiya Kaltume take tsanar
mahaifiyarta da duk wani abu dake da alaka da mahaifiyarta take, me ye laifin
Rukayya dan ta zo gaisuwa, wanda aka yi ma rasuwa da ya kamata ace ya natsu ya koma
ga Allah shi ne suke haka, kamar Rukkaya ce ta yi sanadin mutuwarta. Ko da ta fito
daga dakin ta sauko kasa har Rukkayya ta fice daga gidan gaba daya. A lokacin da ta
fito ta duba ko'ina bata ganta ba sai ta koma bangaren Momy ta shige dakinta tana
ta mamakin, ta ya Hajiya zata ce sun jidadi waye yake farinciki da mutuwar wani? Ko
da kuwa nesa ne balle na kusa.
Bayan Sallah magariba Yasir ya shigo dakin nata shi ma kana ganinsa zaka san
mutuwar ta taba shi, domin ya dan yi rama ga idonsa yayi ja alamar bacin rai da
damuwa.

“Yayana”

Ya maida kofar dakin ya rufe.

“Hurriya, Rukkaya ta tafi?”

“Wani abu ya faru ne? Ta bar twins bata koma da su ba, kuma na kira wayarta bata
daga ba sai text ta yi min yanzu wai na aiko da twins ana mata fada a gida”

“Ina suke?”

“Suna kasa, me ya faru?”

Ta yi shiru kamar ba zata fada ba gudun kar ace ta yi munafurci ko gulma.

“Hajiya ta yi mata fada, ta ce wai ta jidadin an yi mata mutuwa ai ta zo daukar


rahoto ne, har tana cewa ko ita kadai ta rage ba saka aureta ba, kuma ta daina zuwa
gidan nan”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ta furta da murya can kasa irin mai bayyana damuwa, sannan ya zauna gefeb gadon
Hurriya ya dafe goshinsa.

“Ana cikin wannan halin na mutuwa me ya kawo magana irin wannan kuma? Daman sai da
tace min bata son Hajiya ta yi mata wani kallo na ce ba za'ayi ba”

Ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayarsa ya mikawa Hurriya.

“Kira Amma idan Gwaggo ta daga ki ce mata twins za su kwana a gurinki”

“Tou”

Ta karbi wayar bayan ya cire mata password ta saka number Amma dake haddace a kanta
ta kira, Gwaggo na dagawa suka gaisa ta fadawa Gwaggo kannenta za su kwana a
gurinta.

“Aa ki zo ki kawo su yanzu”

“Gwaggo dan Allah, haba Gwaggo ba su tana kwana a nan ba, zan jidadi idan suka
kwana za su rage min kewarku”
“Shikenan gobe amman su dawo gida, kuma ki kula da su”

“Toh Gwaggo na gode sai da safe”

Ta kashe wayar ta mika masa, ya karba ba tare da ya sake cewa komai ba ya nufi
kofar dakin ya bude, ita ma ta sauko daga kan gadon ta bi bayansa tana jin
farinciki kanenta za su kwana a tare da ita. Ko da suka sauko falon babu kowa sai
Momy, yan'uwanta da suka zo gaisuwa sun tafi tun dazun. Hamid Momy na ke yi ma fada
wai yana ta yi mata kiriniya a kitchen ya ki ya natsu. Yasir ko kallonsu be yi ba
ya fice domin ta shi ta isheshi ga rashin yar'uwa ga damuwar abun da ya ji Hajiya
Kaltume ta yi ma Rukayya, ga fadan da Rukkayya ta rubuto masa ana yi mata a
gidansu, goma ta hade masa da ashirin.

“Momy ai dole su yi, saboda ba su saba ba, gidansu ko rabin kyau wannan be yi ba,
kuma ba a saba ganin kayan dadi ba, sai bude fridge yake yana rufewa kamar wani
tsohon bakauye”

Cewar Namra dake zaune dinning tana lasa wayarta. Maganar ta soki Hurriya irin
tsokar da take jin bata zata iya mata kara ba, domin ita ma bata ti mata ba.

“Can inda suke zaune ba gidan mahaifinsu ba ne, gidan kakarsu ne, nan din dai shi
ne gidan mahaifinsu”

Hurriya ya rufe na rufe baki, Momy ta matsa ta wanke mata fuska da mari.

“Dan Ubanki Namra ba yayarki ba ce kike fada mata magana any how?”

Hurriya ta dafe kuncinta ta fashe da kuka.

“Amman Momy baki ji me take fada ba? Gidan uwata take kushewa”

“Karya ta fada? Kuna da irin wannan daular a gidan uwar taku ne? Da yara sun saba
da jindadi za su zo suna wannan rashin natsuwar ne? Me kuke da shi a gidan uwar
taki?”

Cikin kuka Hurriya ta matsa ta rika hannun kanenta zata ja su zuwa sama sai duk
suka bata fuska ganin an daki Hurriya har tana kuka, dayan ya ware hannunsa ya daga
sama alamar zai daki Momy saboda ta doki Hurriya, Namra na ganin haka ta bar
dinning din ta nufo inda suka ta yi masa dudu a baya.

“Marar kunyar yaro, Momy zaka daka”

Dayan ta doka kamin ta dauke hannunsa Hamad ya fashe da kuka ya zageta da hannu,
shi ma ta rikoshi zata dunduma masa dudu a baya, Hurriya na ganin hakan ta shiga
tsakani ta tare shi, sai fadan ya koma tsakaninta da Namra.

“Okay hana ni zaki yi na dake shi? Ko baki ga zagina yayi ba?”

“He's just a child, daukar alhaki ne kawai Yaya Namra”

“Okay to bari ke na dauki alhakinki na lura ganin kike kamar ni din nan sa'arki ce
ko?”

Namra ta kama wuyan rigar Hurriya ta shaketa har sai da ta fada baya kan kujera,
Hurriya na kokarin kwantar kanta tana kuka saboda karfi ba daya ba
Momy kuma na tsaye ta ki ta raba sai zuga Namra take wai idan ba duka ta yi mata
ba zata daina raina ta ba. Hamid da Hamad kuma suka hau kuka suna dukan Namra ta
bayanta, dayan ya dauko remote din dake Center table ya jefi Namra da shi.
“Kin ga wadanan berayen babu tarbiya a tare da su sam... ban san me ya saka Yasir
ya shigo min da su nan ba”

A tsakanin rufe bakin Momy da turo kofar falon da Captain yayi ba a iya shaidar
wanda ya riga wani ba, shigowa yayi cikin falon ya bayan ya rufe kofar yana kallon
Namra da ta danne Hurriya har a ganinta.

“Me yake faruwa?”

“Captain”

Momy ta fada, sai Namra ta dago da sauri ta juya ta kalli kofar, hakan ya bawa
Hurriya damar silalowa kasa tana tari kamar zata mutu, ba karamin shaka Namra ta yi
mata ba, a kokarin ganin ta kece rainin a tsakaninsu ta kusan aikata lahira ba da
niya ba. Captain na hango Hurriya ya nufi gurin ya saka hannunsa ya dago kafadunta
sai nishi take daker tana tari hawaye na fitowa a idon da bata iya shaidar waye a
gabanta saboda babu gilashi a idon nata. Hamid ya dawo gurinsa yana dukansa yana
kuka a zatonsa shi ma wani abun zai mata. Captain ya juyo ya kalli Momy.

“Momy kina kallo ana kokarin yin kisan kai?”

“Hurriyar ce bata jin magana Captain rashin kunya take yi ma Namra kamar ba yayarta
ba, saboda yaran nan ta kama Namra da kokawa”

Ya saketa ya mike tsaye ransa a bace.

“That's mean wani abun aka yi da ya kufular da yarinyar nan, idan ba haka ba babu
yadda za'ayi ta kama Namra da kokawa, yarinyar da ko yatsa aka saka mata a baki ba
zata ciza ba, ban san me ya faru ba amman zan iya shaidar ita ke da gaskiya”

“Captain baka san me ya faru ba, be kamata... ”

Tasss ya wanke fuskar Namra da mari tun kamin ta karasa furucinta. Ya nunata da
yatsa wani abu na fisgeshi yana kokarin ninka masa bacin ransa.

“Idan kika sake kai hannunki a jikin yarinyar nan....!”

Sai kuma yayi shiru be karasa ba sai wani mugun kallo yake watsa mata. Namra ta
rike fuska daga ita har Momy mamaki ya hana su sake cewa komai. Ya juya ta nufi
gurin da gilashin Hurriya yake ya dauka ya kama hannunta da take lalabe da shi ya
danka mata gilashin. Sai ta karba ta saka ta kalleshi.

“Na gode, na gode da ka zo...”

Ta furta wasu hawayen na sauko mata, ta san ba dan ya zo in time ba wata kila da
yanzu an yi gawa ta biyu a gidan.

“Me ya faru?”

A madadin ta yi magana sai kawai ta fashe da kuka, daman haka take ko a can da idan
suka yi fada da Hamad bata iya maida magana saboda kuka, Hurriya irin yaran nan ne
da idan aka yi fada basa iya bitar abun da ya faru ko da kuwa su suke da gaskiya
saboda kuka. Tausayinta sai ya kara kama shi, daman zuciyarsa ta raya masa tana nan
bata ci abincin dare ba, wata kila ma har da rana domin ya lura da yanayinta a
dazun shiyasa har ya dawo gidan da dare, ashe da rabon ya tararda wannan fadan ne.
Namra ta lumshe ido sai a lokacin kuka ya zo mata, Momy ta kama hannunta suka nufi
stairs tana kuka, Momy kuma rai bace an taba mata yar gudaliya gashi babu halin ta
yi magana saboda Captain ne, ta san idan ta yi magana zai iya cewa saboda ba ita ta
haife shi ba shiyasa ta yi magana dan yi mari Namra, wata kila ma yayi fushi, kuma
idan abu yayi zurfi ba zai tsaya iya tsakaninsu ba.
Hurriya ta mike tsaye ta share hawayenta, ta kama hannun kanenta.

“Su waye wadanan?”

“Kanena ne”

Ta amsa tana jansu, shi ma dai ya tambaya ne saboda confirmation amman ya ga


kamanin a fuskarsu ai. Hurriya ta haura sama da yaran ta shiga dakinta ta saka
Hijab dinta ta sauko tare da su, a lokacin Captain na zaune a sofa yana kallonta
har ta sauko tare da su.

“Ina zaki je?”

“Gida zan kai su”

“Cikin dare?”

“Daman Gwaggo bata so su kwana a nan ba, ni ce na takura su kwana a nan, kuma gashi
yanzu saboda su ana yin fitina”

“Je dakinki ki kwanta”

Ya bata umarni kai tsaye.

“Daman Amma bata son...”

Bata karasa ba ya daka mata tsawa.

“I thought na fada miki bana maimaita magana”

Ta juya da sauri jikinta na rawa ta nufi stairs, daman tsoronsa take balle yanzu da
ya mari Namra a gabanta. Twins na ganin ta nufi stairs suka fashe da kuka suka bi
bayanta, Captain ya kallesu.

“Dawo ki zauna a nan”

Kamar umarni take jira ta juyo da sauri ta dawo ta zauna sai suka nufeta suna zauna
suma kusa da ita suna kuka.

“Ki rarrashe su mana, ki zubo abinci ku ci”

Ta mike tsaye ta nufi dinning tana waigensa, daman dai bata isa tace masa Momy ta
hana ta taba abinci idan bata ci ba, kar yayi mata fada, babba plate ta dauka ta
zuba abincin ta dawo tsakiyar falon, ta koma ga dauko ruwa sannan ta zauna ita da
kanenta suka fara cin abincin kamar wasu marayu. Hamid sai kallon Captain yake abun
da Hurriya ta kasa yi gaba daya tsoronsa ya cika mata zuciya, hantar cikinta sai
kadawa take.

“Wuta....”

Little Hamad ya fada yana nuna kitchen din. Gaba dayansu suka dago suka kalli kofar
kitchen dake cikin da hayaki, Captain ya mike tsaye da sauri ya nufi kitchen din,
hankalin Hurriya ma ya tashi ita ma ta bi bayansa kamin su karasa suka ji ihun
Namra, Hurriya ta yi zaton wutar kitchen din ce ta fito da ita daga dakinta har
take ihu.

“Kunamu a dakina sun cijeni akan gadona suka har uku wayyo Allah na....”
Sai suka ji wani abun na dabam, sai kuka take tana sosa bayan rigarta kamar zata
fita daga hayyacin, har wani tsalle take tana saukowa kai kace ma fadowa zata yi a
stairs din. Captain ya kalli Twins din dake ta cin abincinsu, dayan yana kallon
Captain dayan kuma yana kallon Namra dake mirgina a stairs tana kiran Momy.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Ya dauke idonsa daga barin kallon yaran ya kalli Hurriya dake tsaye a rikice.

“Hurriya zauna ki rarrashi yaran nan”

“Ba kuka suke yi ba”

Ya watsa mata wani kallo irin na karki bari na maimaita kaina. Ta koma ta zauna ta
dafa su.

“Ku yi shiru ku yi hakuri ku yi shiru”

Tana yi tana kallonsa a ranta tana mamakin hikimarsa ta yin haka bayan yaran ba
kuka suke ba cin abincin suke yi. Shi kuma ya nufi kitchen din gaba daya hayaki ya
cika ko'ina, gurin da wutar take ya nufa electric kettle din Momy ce ta kama da
wuta, haka ya lalaba ya kai hannunsa ya taba socket din da niyar kashewa sai ya ji
a kashe, hakan yana nufin wutar ma a kashe take amman a haka sai da ya kama da
wuta. Abubuwa yayi ta budewa har ya samo mociya ya dauko ya bugawa kettle din ta
zubo da ita kasa amman wutar bata daina ci a jikin butar ba. Tab ya kunna ya rika
watsa ruwa a banza, da gudu ya fito daga kitchen din yana tare.

“Baka yi komai ba, Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, bari a kira fire service”

Momy ta fada hankalinta a tashe.

“Baku da fire-extinguisher a nan ne?”

“Akwai yana nan ta baya”

Momy ta wuce gaba da gudu kai kace ta kwashe kibar ne ta watsar, ta nuna masa gurin
ya dauko ya dawo kitchen din ya fesa, amman wutar taki mutuwa, sai ya sake fita ya
samo bargo ya jika shi da ruwa ya lulluba saman wutar, tana mutuwa wata ta kama
jikim gas a nan fa hankalin Captain ya tashi ya san gas ba shi da wasa. Ya fito da
sauri daga kitchen already Momy ta yi waya a kawo fire service, masu aikin Momy da
duk sun shigo falon suna kallon wutar har da masu aikim gida, wasu suka fara zuba
ruwa a gas.

“Nono ku daina zuba ruwa, wacan ma dan na sauke ta kasa ne ya sa na zuba ruwa”

Ya hana masu zuba ruwan sannan ya kalli Hurriya.

“Ya sunan wannan?”

“Little Hamad”

Ya kama hannunsa.

“Zo muje mu kashe wuta”

Hurriya na jin haka ta yi hanzarin riko kanenta tana shi bayanta.

“Karamin yaro ba zai iya kashe wuta ba”

“Zan mareki Hurriya, idan ba su suka kashe wutar nan ba ba zata mutu ba, saboda an
bata musu rai ne duk silar abun”

Ya nufeta yana matsawa baya ya riko Little Hamad din ya dagashi sama yana masa wasa
domin ya san ba zai iya sakawa su yi da karfi ba. Ya nufi kitchen da shi daga bakin
kofar ya tsaya ya bashi fire-extinguisher din suka rika su biyu suka hura iskar
zuwa inda wutar take amman bata mutu ba, ya dawo da shi ya dauki Hamid yayi masa
kwatankwacin yadda yayi ma Little Hamad, sai a ga wutar ta mutu a take kamar an
taketa. Captain yayi murmushi mai sauti ya sumbance shi a kumatu.

“That's my boy”

Ya aje abun ya juyo ya fito da shi falon yana dagashi sama ya jefa ya cha, yaron
sai dariya yake sosai, dayan ma ya zo da gudu ayi masa daman ko a gidan Amma haka
suke idan aka yi daya abu sai an yi ma daya, idan ba haka ba babu zaman lafiya, ga
su so friendly da kowa basa bakunta kuma basa fasa kiriniya a ko'ina.

“Wutar ta mutu kuwa ikon Allah”

Momy ta fada tana leka Kitchen din, bayan Captain ya aje su ya dubi Momy.

“Ba dole ba, wannan shi ne me wutar wacan kuma ina jin shi ne mai kunamar, ko kuma
duka Hamid din ne”

“To akan me? Ina mafari ina dalili? Daga zuwa bakunta sai su haddasawa mutane
gobara da kunamu? Na ga kunama ni ma daya a dakina ta shige under bed na fito na
fada kenan na zo na tararda wuta”

Captain yayi saurin girgiza mata kai.

“Momy karki ja su kara yin abun da ya fi wannan, ba a bata musu rai, ina tunanin ko
dai kin musu fada ko kuma taba Hurriya da kuka yi ne ransu ya bace, Ke ma idan kina
son zaman lafiya ki ba su hakuri”

Ya karasa yana magana da Namra da ke zaune a kasa tana rusar kuka har lokacin tana
lalaba bayanta, gaba daya ta cire zip din rigar amman zabin da take ji sai take jin
kamar kunamar tana nan bayanta, tun da ta zo duniya kunama bata taba cizonta ba,
sai yau.

“Ya zan yi na ba su hakuri ya ake bada hakuri, dan Allah ku yi hakuri ku yafe
min...”
Tana kuka tana rokonsa har da hade hannayenta guri daya. Hurriya bata san lokacin
da dariya ta subuce mata ba sai ta yi saurin rufe bakinta ta juya baya. Kowa sai da
ya kalleta Momy ta yi kamar ta yi mata fada saboda ta yi dariyar Namra, sai kuma ta
tuna ta kalli twins din ta shanye maganarta. Captain ya sauke kansa kasa a hankali
yana murmushi dariyarta is something else da ya daukeshi ya jefa shi wata duniyar
ta nishadi, sautin giggles laugh dinta na ta maimaita kansa a kunnunsa.

“Shatu shiga ki dauko mata hijab dinta mu tafi asibiti”

Momy ta fada cikin bacin rai, ba dan tana gudun ran yaran ya kara baci wata
Matsalar ta sake afkuwa ba da sai ta yi ma yaran duka kuma ta ci uban Hurriya
saboda dariyar da ta yi. Tare da Shatu suka haura sama ita ta shiga dakinta ta
dauko keys din mota Shatu kuma ta dauko Hijab din Namra, Momy ta sauka Shatu ta
saka ma Namra Hijab din ta rikata ta mike tsaye tana kuka. Momy ta yi zaton Captain
zai ce ya kai Namra Asibitin amman be yi wani unkurin ba har direbanta ya shigo ya
karbi keys din suka fice. Inna Kulu da Shatu ma suka fice daga falon, aka bar
Hurriya daga ita sai kanenta da Captain. Sai a lokacin Hurriya ta samu natsuwar
kwashe abincin da twins suka zubar ta zuba a plate ta dauke komai ta nufi kitchen
tana aje plate din ta kunna tap ta wanke hannunta, sai ta ji magana a bayanta.

“Kin iya dariyar keta ko?”

Me zata yi idan ba dariyar ba, ta sake kyalkyalewa da dariya irin dariyar nan da
baka iya controlling, idan ta tuna yadda Namra ta yi a dazun sai ta kasa rike
kanta, ta juyo tana fadar

“I wish ni ma twins ce da an bata min rai... ”

Ta kasa karasa a yayinda ta kalli fuskarsa, tunawa da shi din ba abokin hirarta ba
ne kuma ba yayanta ba, hasalima bata da wata alaka da shi, sai dai kuma murmushin
da ta yi arba da shi a fuskarsa ya saka ta dan ji sakewa fiye da yadda take ji idan
ta kalleshi a baya.

‘I'm your twinned, duk wanda ya taba ki, will see my reaction Immediately, trust me
Hurriya i hear the whole story, i know the pain behind this precious smile of
yours’

Magana yake daga zuciyarsa zuwa ga Hurriya dake tsaye gabansa yayin da yake rike da
murfin fridge.

“Zaki iya haihuwar twins ai, yawanci gadonsu ake, idan kika yi aure zaki iya
haifawa mijinki twins ko Tripple, i love twins too”

Ta kara fadada light smile dake fuskarsa kamin ta sauke kanta kasa ta fice daga
kitchen din, ba tare da ta sake cewa komai ba. Ya dan daga girarsa kadan ya kai
hannunsa ya dauko lemun kwalba ya bude sannan ya rufe fridge din, ya dawo bakin
kofar kitchen din ya tsaya shi baya cikin falon shi baya cikin kitchen din ya
jingina yana kallon Hurriya dake haurawa stairs tare da twins dinta gwanin sha'awa.
Sai da ta haye gaba daya sannan ta juyo ta kalli kofar kitchen din, daman jikinta
ya raya mata akwai idon wani a akanta, lemun dake hannunsa ya daga mata yana
murmushi, ita ma ta yi murmushi kadan sannan ta dauke kai ta karasa saman ta isa
bakin kofar dakinta, ta nan kam baya iya hangota ita ma bata iya ganin wanda ke
falon. Dakinta ta tura sai da yaran suka shiga sannan ta shiga ta rufe kofar, kan
gadonta dayan ya fada, dayan kuma ya nufi gurin da madubinta yake ya fara yi mata
tabe tabe.

“Hamid bari mana, zo ga chocolate”


Ta dauko ragowar chocolate dinta ta mikawa musu. Ko da su Momy suka dawo Captain ya
bar gidan, a daren Namra bata yarda ta kwana dakinta ba dakin Momy ta kwana saboda
tsoro, washe gari da safe Momy ta kira masu kula da fulawa suka bincike dakin na
Namra babu kunama babu alamarta, dakin Momy ma da aka daga gadon ba a ga komai ba.

Misalin karfe goma sha biyu na rana Maryam da wata yar'uwarta suka sauka airport
din sokoto, Appa ya aika da mota a sirrance aka daukosu tun daga sokoto har garin
Gusau, bata samu isowa gidan sai karfe biyu da rabi, saboda yanayin tafiya. Ko da
ta shigo gidan yana cike da mutane kamar jiya, masu zuwa gaisuwa da gaske da kuma
masu zuwa cin abinci, ta fito motar tana sanye da mask sai doguwar rigar Abaya da
ta rufe jikinta kovina ruf. Cousin dinta ta ma ta fito motar kowacensu tana rike da
jaka, suka shiga bangaren na Hajiya Kaltume, tun a waje suka gaisawa da mutane suna
musu ya hakuri har suka shiga can ciki gurin Hajiya Kaltume dake kwance a kan gado
zazzabin na dawainiya da ita. Sosai Maryam ta yaba halin kawarta na kirki tana
kukan rashinta, ita kanta mutuwar ta taba ba kuma ta zo mata bagatatan a lokacin da
ba ta yi tsammani ba, na ita kadai ba mutuwar Salma ta bawa kowa mamaki, ko da yake
ba a mamakin ikon Allah, sai dai jin cewar tana lafiya kalau gashi bata dade da
gama karatu ba, ya saka kowa tausaya mata. Bayan Maryam ta yi gaisuwa sai kuma ta
yi kuskuren gabatar da kanta a gurin Hajiya Kaltume saboda ta san wacece ita, ba
dan tana son auren mijinta ba sai dan abotar dake tsakaninsu da Salma.

Hajiya Kaltume dake kwance ta tashi zaune ta gyara hijabinta tana kallon fuskar
Maryam.

‘“Daman ke ce yarinyar?”’

Maryam ta dago ta kalleta, ba ta yi zaton Appa ya fada ma Hajiya komai a game da


maganar aurensu ba, domin shi da kansa ya bukaci su bar maganar a sirrance har sai
idan an daura aure sannan kowa ya ji, ta dayan bangaren kuma bata zaton Salma zata
boyewa mahaifiyarta wacece ita saboda ta gargade tun a ranar da suka yi bankwana a
airport.

“Ke ce yarinyar da kika haddasa mata bakinciki?”

Maryam ta maida kanta kansa tana jin kunya na rufeta. Hajiya Kaltume ta fashe da
kuka tana jin kamar da wuka a kusa da cakawa Maryam ta kasheta.

“Ke ce fitsarriyar yarinyar da kika hakikance sai kin auri ubanta? Duk saboda ku
yata ta mutu, ke da Iyami ba za ku gama da duniya lafiya ba, Allah ya tsine muku
albarka”

Maryam ta san wacece Iyami domin tana labarin yadda gidan Appa yake ciki da waje,
ba ta gurinsa ta ji ba ta gurin bincikar yadda rayuwar gidansa take ta ji.

“Shi ne saboda baki da kunya kika dauko kafa kika zo yin murna ko?”

Maryam ta dago da sauri.

“Subhanallahi wake murnar mutuwa? Ni kawar Salma ce ba makiyiyarta ba”

“Kawarta ba zata ce zata auri ubanta ba, mugun kwadayi da dogon buri ya saka zaki
auri ubanta tsohon da ya isa haihuwarki, kin ji kunya yarinyar kin ji kunya
rayuwarki zata lalace nan gaba, na rantse da Allah sai kin wulakanta”

Fada sosai Hajiya Kaltume take yi, ta inda take shiga ba ta nan take fita ba ana
riketa ana rufe mata baki amman ta kasa daina saboda zafin mutuwar yarta da take
ji, ga kuma silar komai a gabanta tana gani ita tana raye. Hajiya Fatee dake waje
ta taso ta shigo cikin dakin ta ita da mutanen dake waje ciki har da Hajiya Binta.
A fusace Maryam ta mike tsaye cikin masifa ta ce
“Miye laifina dan na zo gaisuwar yarki? Tun daga garin Naija na taso na zo garin
nan saboda gaisuwar Salma, akan wane dalili zaki tara min mutane, to bari jiki na
fada miki kanki kika tonawa asiri, domin wanda be san mijinki zai kara aure ba yau
ya sani, kin kunyata kanki da mijinki”

Tana aje aya Maama ta dauke ta mari, ta kai hannu zata rama Khairy ta rike suka
fara dukanta, cikin karfin hali ta fara ramawa ita da cousin dinta aka hau rabasu
daker aka kwaci Maryam hannun Maama da Khairy. Hajiya Binta ta dakawa Hajiya
Kaltume tsawa

“Wai ke kan kanki farau aure? Wane irin mugun kishi ne yake damunki? Kina babba
amman baki san ki tsawatarwa yayanki ba sai dai ki bude musu kofa?”

“Hajiya Karki kara min bacin rai, daman kullum goyon bayan dakinki kike baki tana
ganin farina ba, ai ni ba wani abun na yi miki ba amman kika dauki tsana da kiyayar
duniya kika dora min, ko wani abun na tare miki?”

“Magana kike ta rashin hankali da tunani Kaltume, ashe mutuwar Salma bata isheki
ishara ba? Girma kike kina cin kasa? Jiya ma danki sai da ya kuka min akan abun da
kika yi ma Rukayya, yaro yana son yarinya amman kina neman shiga tsakaninsu saboda
bakin kishi da ba zai haifar miki da komai ba? Yanzu kuma kin zo gaban mutane kina
kunyata mijinki akan abun da baki da tabbaci? Kuma ko da kina da tabbaci ya kamata
ki ci mutuncin yarinyar da ta dauko kafa daga nesa ta zo miki gaisuwa? Kim kunyata
kanki kin kunyata mijinki. Shiyasa kullum nake yabon Iyami kun fita shekaru amman
ta fi ku hankali, wannan abun da kike yi hauka ne?”

“Hauka ne Hajiya, idan kina da magani sai ki ba ni, na gaji da abun da kike min, ba
ba ku san me nake ji a zuciyata ba, ba kussn yadda yata ta rasa rayuwarta kun saka
ni gaba kuna kunna min wata wutar, na yi kishin kishin halak ne, ni na auri Haruna
tun ba shi da komai har ya zama komai, ni nasan fadi tashin da muka yi na rayuwa”

Hajiya Binta ta nunata da tsaya rai a bace.

“Karya kike ki fada min wannan, tun kamin a haifeki na ke kula da dana, ni na san
fadi tashinsa ba ke ba, ke kullun kara hauka kike ba hankali ba yayanki ma gasu nan
kin fara koya musu irin tarbiyarki”

Hajiya Kaltume zata sake yin magana wata yayarta ta rufe mata baki, tana bawa
Hajiya Binta hakuri.

“Babba babba ne ko yayane, dan Allah Hajiya ki yi hakuri, wani lokacin Kaltume bata
iya rike halshe, kar idonki ya rufe Hajiya ayi babu dadi a nan?”

“Babu dadi na nawa kuma? Ita da yarta ta mutu idonta be bude ta yi hankali ta natsu
ba? Me ye bata fada min ba? Ai wannan yar bata da albarka sam...”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta daki kirjinta dake mata zafi da ciwo a lokaci daya
tana kuka mai karfi ta ce

“Ba yar albarka ba ce ni Hajiya Binta, ki aura masa yar albarka ki kawo, ni kuma ki
saka bindiga ki halbeni ni da yayana”

Hajiya Binta ta kashe ido tana kallon surukar dake mata rashin albarka ta ce.

“Idan kin kwana da aure yau Kaltume na kwana a mace...! Sai na nuna miki ruwan nono
ya fi karfin wulakantawar”

Hajiya Binta ta kalli Maryam da ke tsaye gefe daya tana karewa Khairy da Maama
kallon daukar fansa ta ce.

“Wuce mu tafi yarinya...”

Maryam ta juya ta fice tare da Cousin dinta, Khairy da Maama kuma suna jin kamar su
rufe Hajiya Binta da duka babu hali, Ruma ce kadai ke rusar kuka saboda abun da ke
faruwa baya mata dadi sam. Hajiya Fatee da wasu yan'uwan Hajiya Kaltume suka bita
suna bawa Hajiya Binta hakuri amman ba ta sauraresu ba ta fice. Yayarta ce ta dawo
dakin tana fadar.

“To yanzu me ye amfanin haka? Jiya kin ci mutuncin yarinya yau kin ci ta wannan
yarinyar kuma abun be tsaya iya kansu ba sai da ya kai ga uwar miji? Haba Kaltume,
mutuwa tana saka mutane natsuwa amman ke kamar ana turaki?”

“Anty Hauwa ki bar ni da bakincikin da yake cikin raina, ni na san me nake ciki, ni
na san irin halin da nake ciki”

Ta fashe da kuka mai karfi. Maama da Khairy ma sai da suka yi kuka saboda ganin
mahaifiyarsu na kuka, daman kuma zafin mutuwar yar'uwarsu be isa barin zuciyarsu
ba. Sai bayan Sallah La'asar lokacin mutane sun dan fara ragewa, daman wasu sai dai
su zo su yi gaisuwa su tafi, Appa ya aiko ya aiko kiran Hajiya Kaltume tare da
Khairy da Maama da Ruma, suna jin haka suka san ba dalilin kiran, Hajiya Kaltume
gabanta ko faduwa baya yi saboda zuciyarta ta riga da dake, yadda abubuwa suka
riccabe mata bata fargabar faruwar komai a yanzu. Can cikin uwar dakin Appa suka
shiga, Appa yana zaune kana ganin fuskarka kasan ransa a nace yake. A kasa Maama da
Khairy har Ruma suka zauna, Hajiya Kaltume ta zauna a kujerar sofa daya dake dakin
idonta a kumbure ga wani ja da suka yi tsabar kuka da bakinciki da suka rumgume.

“Akan wani dalili yarinya zata zo tun daga nesa ki ci mutuncinta ke da yayanki?”

“Me yasa zata zo? Ba abun kunya ba ne dubi kamar kai ace zaka auri kawar yarka?
Wato Hajiya ta zo ta tsara maka maka komai, so ake a hada min zafi ta ko'ina kamar
ni na haifowa duniya bakin duhu”

Ta fara kuka da karfi. Appa ya maida dubansa gurin Khairy da Maama.

“An fada min abun da kuka yi, kuma abun da kuka yi ba kowa kuka yi ma sai ni, ni
kuka ciwa mutunci ni kuka wulakanta, sannan kun bar magana a bakin kowa, yar'uwarku
ta mutu yau kwana daya amman wuni na buyu amman kuna dukan kawarta saboda ta zo
gaisuwa, jiya ma ance kun yi ma Rukayya saboda rashin hankali da kikanci irin naku,
to daga sai yau ko kare na kawo kuka tsallaka shi sai na yi muku abun da ba ku taba
mafarkin ba, idan ita uwarku kishi take ku me kuke yi? Kar wanda ta sake tunkarata
da wata bukata tata na yanke, du wata dawaniniya da nake da ku daga yau ta kare,
idan har baku san darajata ba babu amfanin cigaba da yi muku komai, ke Maama ki
tattara ki koma gidan mijinki zaman gaisuwa na kashe daga yau, domin gobe ban san
abun da za su sake yi ba, ke kuma Khairy ki sani nan da kwanaki kadan zan aurar
dake, ke tafi can gidan mijin ki yi hankali”

“Appa....”

Khairy zata yi magana ya daka mata tsawa.

“Shut up ku tashi ku ba ni guri”

Suka tashi jiki na rawa suka fice daga dakin suna kuka. A lokacin ne Appa ya kalli
Hajiya Kaltume ya ce.

“Ke kuma ki yi zaman ƴaƴanki, kin ci mutuncina kin ci mutuncin kanki, kin ci
mutuncin yayanki duk haka be miki ba sai da kika tsallaka kika ci mutuncin
Hajiyata, matar da ta yi silar zuwana duniya, matar da ta rumgume tun bana iya
tsayawa da kafafuwana, to kin kai karshe, ko da ace Hajiya bata ba ni umarnin
aikata abun da na aikata a yanzu ba, zan aikata a karan kaina jin abun da kika yi
mata Hallayenki sun isheni Kaltume, kin kawo min nan”

Ya kama makogaronsa da hannuna yana nunawa.

“Dan haka na iyankance alakata da ke a yau Kaltume, NA SAKE KI SAKI DAYA....”

Hajiya Kaltume ta sauko daga kam kujera tana taba kirjinta.

“Ka sake ke ni Alhaji? Ni Kaltume yau ni ka saka? Ehhhhhhh ehhhhhhh ehhhhhhh


hmmmmmmmm”

Ta dora hannu akai tana dukan kanta kamar wata bayarabe.

“Ehhhooooooooo ehhhhwoooooooo hoooooo ni niiiiiiii hmmmmm kilkilkil ni aka saka?


Lallai wani bakincikin sai namiji, bani bakin cikin sai namiji, yata ta mutu kuma
ka sake ni, namiji dan kunama Haruna mai siyar da yadi ka ji kunya ka yi abun
kunya, yau kam na tabbatar Binta bata kaunata yau na tabbatar da waye kai Haruna
mai yadi, Mai yadi Haruna, tun baka da taro da sisi nake tare da kai, tun aka siyar
da yadin uku da sisin kwabo, tun kana siyar da yadin mutuwa yadin likkafani nake
tare da kai Haruna, yau ni ka saka saboda zaka auri yarinya sa'ar yarka? Lallai
namiji ba dan goyo ba ne, namiji dan kunama, duk macen da ta ce namiji uba ne sai
ta kwana marainiya”

Babu kalar gorin da bata yi ba Appa ba, dan Alhaji ma da take masa alkunya yau bata
saka ba saboda bakar zuciyarta ta mutanen farko ta tashi, halin na mata masu bakin
kishi da bakar zuciya ya motsa, tana murzar kafa a kasa tana kuka tana ihu
arzikinsa daya dakinsa ba mai daukar magana ba ne sai an bude. Appa ya mike tsaye
sai ta matsa da jan jiki ta riko rigarsa tana zuba masa rashin mutuncin.

“Ka tsaya mana mai abun kunya, saboda kana takama da arziki, arzikinka na banza,
saboda kana takamar kana da kudi sai ka aure yar aiki yanzu kuma zaka auro kawar
yarka, kuma duk a ni Kaltume bakincikin zai kare, ni zaka nunawa bakinciki? Allah
ya saka ka auro mai farar kafa, idan arzikin ya kare sai ka ga zata zauna da kai ko
kuma sai Hajiya Kaltume mai zuciyar karfe? Wallahi sai ka yi nadamar sakin da Binta
ta saka ka yi min yau Haruna mai yadi”

Appa ya buge hannunta ya fisge rigarsa.

“Albakarcin fadin sunan uwata da kika sake yi da kuma addu'ar da kika yi, na kara
miki saki daya, dazun saki daya na yi miki yanzu kuma na kara miki daya, Kaltume NA
SAKE KI SAKI BIYU”

Hajiya Kaltume ta fadi kwance kasa tana burzar da yawu tana ware hannaye sama kamar
wata mai aljannu.

“Shi ke nan na mutun yau an dandana min bakinciki ďa namiji yau an dandana
bakinciki, so ake na mutu gaba daya”

Appa ya kabe mata rigarsa ya fice daga dakin yana jin kamar ya kara mata wani
sakin, daman abun haka yake idan mace ta yi magani duk ranar da abun ya karye
namiji zai tsaneta irin tsanar da be taba yi ba. Ficewa yayi daga bangare gaba daya
domin baya son sauraren kalamanta da kukanta dake kara masa bacin rai, kuma baya
son hankalin mutanen dake waje ya kai garesu. Yana tafiya hannayensa a baya yana
tuna lokacin da ya saki Iyami, yarinya a cikin matansa amman bata yi wannan haukan
da cin mutuncin da Kaltume ta yi masa da uwarsa ba, yana tuna lokacin da ya bata
takardar sakinta a rubuce ta karba, har ta yi masa addu'ar Allah yasa hakan shi ne
mafi alheri kuma ya ba shi ikom kula da Hurriya da Hamad. A yanzu yake tambayar
kansa me yasa ya saketa? Why? Me ta yi masa? Me yasa ya rabu da matarsa abar
kaunarsa? Har ya isa bangaren na Momy be samu amsar tambayarsa ba. Cikin yanayin
damuwa da ya kasa boyuwa a fuskarsa ya murda kofar dakin ya tura ya shiga, ba zai
iya fadar abun da ya kawo shi bangaren ba, kawai dai ya baro na shi bangaren ne
saboda Hajiya Kaltume, ba zai iya barin gidan a yanzu da ake amsar gaisuwar yarsa
ba, sai dai arba da tawayensa dake wasa a falon Momy suna mata tsalla akan kujeru
Hurriya na kokarin hanasu sannan na fahimci kewar yaran da ya kasa zuwa ganinsu ya
kasa karbarsu ya rumgume su a lokacin da aka haife su ce take kiransa.

“Salamu Alaikum”

Yayi sallama muryarsa na isar da rauninsa dake idonsa na arba da yaransa kanana da
yayi, sai kuma ya samu kansa da kunyarsu damuwar abun da yayi musu ta yi kamar zata
fadar da shi a tsakar falon. Hurriya da Namra suka amsa masa Namra na murmushi
Hurriya kuma na faduwar gaba, tana addu'ar Allah yasa ba wani abun aka cewa Appa ta
yi ba. Ya zauna kan kujera yana kiran Hamid dake tsalle yana rike da kwalbar lemu.

“Husaini baka tsoron ka fasa kwalbar ka ji ciwo”

Hurriya ta kalli mahaifinta da saurin jin da ganin yadda ya nunawa kanenta kulawa,
Namra kuma ta dan hararesu ta ce.

“Tun dazun haka yake, idan aka hana shi kuma yace zai turowa mutane kunamu, shiyasa
ban ma masa magana ba”

Appa yayi murmushi yaran suna nufar gurin da yake kamar wadanda suka saba da shi.
Ya kama su ya dora dayan a cinyarsa dayan ma ya dora shi a cinyarsa yana kallonsu.

“Husaini...”

Wanda aka kira da Husaini ya nuna kansa yana gyara masa sunan domin ba su saba jin
ana kiransu da haka ba.

“Hamid”

“Oh Hamid... Haka Hamid.. To ai kai ne Husaini... ”

Appa ya fadi hakan ne saboda Hasan da Husaini shi mutanen da suka saba da shi, kuma
shi zai fi musu dadin fada.

“Appa Little Hamad shi ne Husani, Hamid Hassan ne”

Hurriya ta fada masa domin banbantawa, Appa ya hade wani abu mai karfi na
bakincikin rashin sanin yaransa da iya banbance a rashin dalili, yana cewa Hamid
Husaini ne saboda shi ne mai karamin jiki, Little Hamad kuma shi ne mai jikin
Hamad, a can baya har wasu suke daukar shi ne Yayan Hurriya saboda girman jikinsa.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Appa sai kallonsu yake yana shafasu idonsa a raunace kamar mai shirin yin kuka, sai
dai be bar hawaye ko alamarsu a idonsa kasancewarsa namiji kuma Uba. Abun da
Hurriya ta kasa yi ita kan sai da nata hawayen na farincikin suka zubo, yaran da ba
su taba rabar gurin da mahaifinsu yake ba suka ji dumin jikinsa. Yau gasu zaune a
cinyarsa yana shafa su. Kusan a lokaci daya kowa ya kalli kofar falon da aka bude
har Appa. Captain ne ya shigo cikin shiga ta kananan kaya kamar kullum yana rike da
keys dinsa dayan hannunsa kuma yana rike da wani kwali da aka yi rapping. Saitin
gurin da Hurriya take tsaye tana share hawaye ya fi maida hankali, kamin ya kalli
gurin da Appa yake zaune tare da yaransa yana amsa sallamarsa.

“Sannu da zuwa Captain”

Namra ta fada cikin murna da farinciki ganinsa tare da kyakkyawar tarba kamar
kullum, Captain ya aje kayan dake hannunsa a mini glass table dake kusa da inda
yake tsaye ya karasa gurin Appa ya risina har kasa ya mika masa hannu biyu ya rika
hannun Appa daya.

“Barka da yamma Appa”

“Barka dai yaro ya aikin?”

“Alhamdulillah, ya hakuri Allah yayi mata rahama, mun yi gaisuwa a waje amman ban
samu gani ka ba”

“Alhamdulillah, Ameen ya Allah. Ba komai Allah ya bada lada”

Appa ya amsa kana ya kalli Namra dake gabatar masa da Captain.

“Wannan ne ďan Yayan Momy Jameel”

“Na wayance shi ai, Nafisa tana yawan nuna min hotonsa da labarinta, wannan ne karo
na uku da muka gaisa i think”

Captain ya amsa da auri.

“Haka ne ranka ya dade”

“Allah ya taimaka”

“Ameen na gode”

Ya amsa yana rankwafawa alamar girmamawa da kunyar da be san ta ina take fito masa
ba. Appa ya sauke twins ya mike tsaye ya rika hannunsu ya nufi stairs, sai da ya
haura ya shige dakin Momy sannan Captain ya kalli Hurriya da yake zaton ko an kai
kararta a gurin Appa ne ya shigo yayi mata fada har take kuka.

“Why are you crying?”

Ya tambaya me take yi ma kuka in a sign language, sai ta girgiza kai ta sauke


idonta kasa, ko da wani abun aka yi mata ta ina zata iya fada a gaban idon Namra,
ta sake dago kai zulum ta zurma su a idon Captain dake kallonta kamar babu gobe,
wannan karon da girar idonsa yake tambayarta.

“Me ya faru?”

Ita kuma da yake bata iya munafurci ba sai ta amsa masa da kai cewar babu komai ta
kalli Namra ta yi saurin sauke idonta kasa.

“Na dauka zaka ce ya jikina Captain”

Namra ta tambaya tana kokarin kawarta abun da idanuwanta suke dauka.

“Baki da lafiya ne?”

Ita yake tambaya amman idonsa suna gurin Hurriya dake motsa siraran yatsun
hannunta.

“Cizon da kunamu suka min jiya”

Sai a lokacin ya kalleta yayin da yake kokarin rage tsawonsa.

“Oh gaba daya na manta Wallahi, hankalina yana gurin yarinyar nan na shigo na ga
tana hawaye na dauka wani abun ne ya faru”

Namra ta kalleshi irin kallon nan na yadda ya fada mata haka kai tsaye ba tare da
tsoro ko jin nauyi ba. Shi kuma be yi hakan da wata manufa fa face gaskiya, domin
ya ji duk wani takurawa da suke son su yi ma Hurriya, kuma ya ga wasu a idonsa,
jiya ma ya shigo ya tarar tana kokarin kasheta, hakan sai ya kara masa tausayinta
da kuma son ya taimaka mata.

“Me yasa kake damuwa da abun da ya shafi Hurriya Captain?”

Tambayar ta kutso ta huda makogaronta ta lakanci halshenta ta fito ta bakinta ba


tare da ita kanta ta shiryawa hakan ba, sai dan mamakin jin furucin da bata
tsammaci jinsa daga bakinsa ba. Sai da ya kalli Hurriya dake kallon Namra sannan ya
aika mata da tambaya ba tare da ya amsa tata tambayar ba.

“Saboda Uwata ce. Me ye matsakarki da hakan?”

Ta kalli Hurriya har zata yi doguwar magana sai kuma ta takaita ma kanta wahala.

“Babu”

Ta mike tsaye ta aje remote din hannunta ta nufi stairs har ta haura ta shige
dakinta bata juyo ba. Hurriya na ganin haka ita ma ta mike tsaye domin barin falon
kamar daga sama ta ji yana bata umarni.

“Shiga Kitchen ki dauko min ruwa”

Ba tare da tace komai ba, ta juya alakar tafiyarta zuwa hanyar Kitchen din gabanta
na faduwa, saboda hukuncin da Namra ko Momy za su yi mata na abun da ya faru yau
idan Captain baya gidan yana kusantota tun kamin ta san sakamakonta. Ta bude
refrigerator din mai kofa biyu ta dauko ruwan dake gefensa murfin ta dago ta rufe
sai ta ga mutum tsaye jikin dayan kofar refrigerator din yana hade hannayensa yana
kallonta. Ta dan ja baya kamar ta tsorata sai kuma ta nufi kofar fita daga kitchen
din tana rike da gorar ruwan.

“Wa zaki kaiwa ruwan?”

Ta juyo ta dawo ta tsaya gabansa ta mika masa ruwan, gaba daya kwarjininsa ya
rikitar da ita. Be karba kuma be fasa son sanin dalilin zubar hawayenta ba, ji yake
kamar ba shi da natsuwa da sukuni idan be zama silar yayewar damuwarta ba a
koyaushe, zuwansa ma a yau na tabbatar da ta ci abinci ne.

“Me kike yi ma kuka?”

Banbancin tambayar dazun da ta yanzu, furuci kawai, dazun yana mata ne in a code
way a yanzu kuma kai tsaye ya tambaya, yana kallon da ya fi kama da an hallito
idonsa ne domin kyakkyawar fuskarta. Ta karantu kuma ta haddace cewar baya son
maimaita tambayar, baya bada umarni sau biyu, gashi fa saurin bacin rai wata kila
ma yar karamar bindigarsa nan tana nan tare da shi, wata kila kuma idan bata amsa
masa tambayarsa a wannan karon ba zai barta ta fice daga gurin ba.

“Kawai na jidadin yadda Appa yake kula da twins ne ya dora su a jikinsa yana wasa
da su, abu ne da be taba yi ba, Twins ba su taba zuwa gidan nan ba sai jiya, ba su
taba rike hannun Appa ba, ba su taba zama a jikinsa sai yau shi ne abun ya saka ni
farinciki, har na yi hawaye”

_Me yasa ba su taba zuwa gidan ba? Su ba yayansa ba ne? Me yasa be taba wasa da su
ba? Me ya faru?_ kusan lokaci daya wadannan tambayoyin suka jero masa, and then he
realized be kamata ya tambayeta any of those questions ba, be ma kamata ya wuce
gona da iri ba.

“Kwalin dake falo na ki ne ke da twins, kin ci abinci?”

Ta daga masa kai, sannan ta juya zata fice har ta isa kofar kitchen din sai kuma ta
juyo, tana tunanin da wani suna zata kirashi, yadda Momy da Namra suke kiransa, a
gudun bata masa rai ko rage masa girma ya saka ta raba sunan da sunan da take ganin
ya dace.

“Yaya Captain...”

Ya kalleta yana hade ruwan da ya cika bakinsa da su, be amsa ba be kuma fasa kallon
idonta da ta kasa dagowa ta kalleshi ba.

“Removed the last sentence”

Ta dago cikin hankali da natsuwa irin nata, ta kalleshi ta cikin gilashin idonta
irin kallon dake kashe zuciyar namiji, da muryar dake narkar da zuciyar mai
saurarenta ta ce.

“...Ya... Ya... ”

Al'adarsa duk wani wani suna da za a kira shi, idan ya wuce Captain da Jameel
kauyanci ne, kalmar Yaya bata masa dadi ko kadan saboda haka ya hana kowa a
familynsa yi masa inkiya da Yaya. Sai dai wacan karatun nasa ya kau, dokokin da ya
gidanya sun rushe a lokacin da kunnuwansa suka yi kicibus da sautin da ya fito daga
bakin Hurriya, she pronounce it so right, so different, so unique, so sweet.

“Say that again”

A wani yanayi da ya fi kama da rauni da tausasa halshe ta maimaita.

“...Ya.. Ya...”

In a gentle way ya shigar da lip dinsa na kasa a bakinsa ya jika shi da yawunsa,
yadda take furta kalmar YAYA ya san he missed alot, me yasa ba zai so ta kira shi
da Yayanba? Ita din ba kamar yar'uwarsa ba ce?
“Repeat it...”

“...Yaya.... ”

Ta sake fada da sanyin murya irin mai tsoro aikata kuskure, har tana tambayar kanta
ko dai bata furta daidai ba? Ko kuma dai yana son ta yi ta fada ne har ya fusata
bayan ta san baya maimaita kansa.

_Miracle_

Ya furta a ransa yana kallon idanuwanta da farin yayi fari kamar watsa ruwan madara
a ciki.

“Uhmm mmm”

Ya amsa irin amsar dake nuna ta fito ne daga kasan zuciyarsa.

“Ina son na tambayi wani abu...”

Wani shaukin kallonta ne ya daukeshi ya lulashi a wata duniyar da ya haddasa


bugawar zuciyarsa a mabanbantan dakiku, natsuwarta na neman bukata a gurinsa ya
saukar masa nishadi da ya samu kansa da lumshe ido ya bude yana kallonta kamar mai
jin bachi.

“Name what ever you want girl...”

Ta hade hannayenta biyu guri daya ta rankwafar da kai, a wata murya da ta fi kama
da tausayi da shagwaba ta ce.

“Kai ne ka ba ni wata takardar ranar da Hamad ya bata? Har ka yi min alkawari zaka
dawo min da shi?”

“Me yasa baki manta ba?”

Kwaryar ididonta ya fara tara ruwan da aka sirka da gishiri.

“Har yanzu ziciyata ta kasa amsar cewar Hamad ba zai dawo ba”

Ta tako ta matso kusa da ita yana kallonta

“Ni ma zuciyata ta kasa karya alkawarin da na daukar miki...”

Ya kara motsawa dap da ita ya rage tsawonsa har tana jin saukar numfashinsa.

“Wata kila zai dawo...!”

Zuciyarta da mugun karfi, ta bude baki saboda numfashin dake fita ta hancinta na
kokarin karewa.

“Ina fatar haka...”

Ta furta muryarta can kasa sosai. Shi ma sai ya bata amsa da muryar mai dadi da ta
fi kama da rada ya ce

“Idan wannan ne farincikinki... Ni ma ina fatan haka Hurriya... Duk wani abun da
zai yaye miki damuwa ya sakaki a cikin farinciki ina fatan ki same shi”

“Kana da kirki kana damuwa da ni, thank you for understanding me”
Kamar wata kwarariya haka ta yi masa magana muryarta a kasa fiye da yadda ta muryar
shi take a lokacin da yayi mata magana.

“We all need that someone who get us like no one else, a right when we needed the
most, you need shoulder to cry on...”

hura mata iskar bakinsa mai kamshi a fuskarta, atak, sai ta lumshe ido, murmushi ya
fadada fuskarta hawayen bakinciki da suka rikide mata zuwa farinciki suka kawata
kyauta. Kamar wanda ta tuna wani abu murmushin fuskarta ya bace bat, sai ta matsa
baya da sauri ta bude idonta ta juya da fice daga kitchen din. Murmushi yayi ya
taka backwards yana shafa kansa, ya daga gorar ya sha ya aje, sannan ya kai
hannunsa saitin da aka aka yi gurbin zuciyarsa.

“Ajiya ce wannan, please ki ba ni hadin kai, saurin fushi breaking up with so many
girls wannan duk na yafe miki, karki raba ni da wannan she's special na gane haka
from DAY 1 na san ke ma kin san haka... ”

Ya rufe idonsa ya sauke dogon numfashi, ya kai ma zuciyarsa duka a hankali yana aje
mata sako.

“Idan kika raba ni wannan ni da ke duka zamu cutu, wata kila mu salwanta in one way
or the other, so try to be strong please, ki ba ni hadin kai i hope you understand
me”

Zuciyarsa ta buga da karfi tana raba sakon da yayi aika mata ga sauran sassan
jikinsa da suka kasance mukarraban aikinta. Ya bude idon yana murmushi, sai
farinciki yake kamar wani sabon ango, ba shi da kwashe kwashen mata, amman idan ya
ga wanda hankalinsa ya kwanta da ita ya kan tallata mata soyayyarsa, sau uku ya
taba yin haka, sau biyu aka yi nasarar saka ranar aurensa aka fasa saboda rashin
hadin kan da zuciyarsa take ba shi. Falo ya fito ya zauna yana kallon tv sai dai
gaba daya hankalinsa ba a gurin tv yake ba. Ya kusan minti goma shabiyar da zama
sannan Appa ya sauko Momy na bayansa waya a kunnesa.

“Gani nan zuwa”

Ya fice tare da twins dinsa, sai jan rigarsa suke. Momy ta zauna tana mamakin ganin
Captain domin Appa be fada mata tana da bako ba, ko da yake ba zata kira shi da
bako ba a yanzu daman tuni ya zama dan gida. Namra ma da ta haura sama da bacin rai
bata fada mata Captain ya zo ba.

“Ban san ka zo ba?”

“Saboda Appa yana nan ne, tun dazun na zo ai”

“Maa Shaa Allah yau dai na san babu aiki yau Sunday, kuma na ga farinciki a
fuskarka a yau fiye da ko yaushe, kana albishir ne?”

Yayi murmushi shi kansa ya san fitowarsa daga kitchen zuwa zamansa a falon nan ya
banbanta da kullum, and baya bukatar wani ya fada masa yana farinciki ya fahimci
haka tun a lokacin da sexy voice din Hurriya ya huda kuunnesa har ya karya
dokokinsa, ga kuma numfashinta da ke masa yawo a saman hanci har yanzu.

“Wata kila nan gaba kadan na yi albishir, farincikin kuma ina fatan ya daure har
abada”

“Allah ya tabbatar maka da shi”

“Ameen Momyna that's why i love you kina son farincikina”


“Kai dan gatan family mu ne Captain, idan wani be so farincikinka ba, to be so
Familynmu ba”

Ya bude baki ya rufe yana murmushin gefen baki. Daga bisani ya kalli Momy ya aika
mata da tambayar abin da ya tsaya masa a rai.

“Momy me yasa kannen Hurriya ba su taba zuwa gidan nan ba sai yau?”

Momy ta dan tabe baki.

“Alhaji ya juya musu baya tun da aka haifesu, ni kaina na yi mamakin yadda yau ya
shigo min da su dakina ya dorasu har kan gadona yana wasa da su”

“Why?”

“To Allah masani Captain, wata kila shiga tsakani ne”

“Kuma mahaifiyarsu ba ta yi tunanin ta kawo su ba?”

“Ta ina? Ka manta na fada maka bata da lafiya? Aiko hannu bata iya dagawa, bata
magana bata iya komai nan gaba kadan ma wata kila bara zata koma, domin dai ance
duk abun da take da shi ya kare, daman talakawa talas shiyasa kwadayi ya ja ta auri
Alhaji, yanzu kuma ta auren ya kare sai ta koma babu komai, ita fa wannan Hurriya
kaskantacci ne uwarta ga aiki ta yi, ta zo gidan ta bangare Kaltume daga aiki ta
aure Alhaji shiyasa Kaltume bata kaunarsu ko kadan ai, kara ni ina da zuciyar imani
ina ragama mata amman can ba ta sha da dadi ai”

“Mahaifinta mai kudi ne i guess to me ya kawo zancen kaskanci?”

“Ai wannan talauci da uwarta take ciki ba zai taba gogewa ba a ido, kuma ba zai
taba barin mutane irina su ga kimarta ba, ba gashi nan ta koma a kwance ba, da ynzu
tana da arziki zata tsaya jinya haka ne? Shekara hudu yanzu ana fama da abu daya,
ko Kaduna ba su taba kaita ba balle a fitar da ita, kuma wani lokacin da tana da
kudi ai ba za'ayi ma yarta ko ita ba, yanzu ka hada ta ni? Ko ka hada Hurriya da
Namra? Ai ba za su tana haduwa ba har abada, ka ga fa gidan nan kowa yana karatu
wasu sun kare amman ita tun da ta gama SSCE ubanta ya aje ta gefe ko kallonta baya
son yi, ya ki sakata makaranta da uwar tana da kudi ai ba za a yi ma yarta haka ba,
ko kuma ta dauki matakin shari'a ta karbe yarta ta saka ta makaranta mai kyau”

Jawabin da Momy ta kora masa, be kara masa komai ba sai tausayin Hurriya, bayan
kalubalen da take fuskanta a gidan ga damuwa na rashin uwa da dan'uwa a kusa, ga
kuma rashin lafiyar ido, yanzu kuma ya kara jin halin da mahaifiyarta take ciki,
talaucin da ya hana su ganin kimarta a gidan, ya kara mata martaba da tausayi a
idonsa.

HURRIYA POV.

Ta rufe fuskarta da tafi hannayenta har lokacin kamshin iskar bakin Captain da ya
hura mata be bar hancinta ba, bata taba samun kanta a yanayi kamamancin wannan ba,
murmushi take kamar wata sabuwar mahaukaciya a rufaffun idanuwanta bata ganin komai
sai fuskar Captain, all the good things da yayi mata suna ta dawo mata, bata da
wani abun fada akansa sai khairy yana da kyakkyawar zuciya da tausayi ba kamar
yadda ta ke tunani a baya ba. Bude ido ta yi ta sauko kasa ta zauna ta bude kwalin
da ta dauko a falo tana duba abubuwan ciki, chocolate ne da sweet candy mai dadin
nan, sai kuma gasashen kifi dake ta kamshi, tashi ta yi ta wanke hannunta sannan ta
dawo ta zauna ta bude kifin ta fara ci. Bata fito dakin ba sai da dare shi ma
saboda Yayanta Yasir ya shigo dakin ne ya bukaci ta fito su tafi kai Twins gida
saboda Rukkaya ta matsa masa ya kawo yaran Gwaggo ma sai da ta kira da kanta,
tsoronta duk be wuce na irin wulakanci da musgunawar da za'ayi ma yaran a gidan ba,
ta fito tana sanye da green hijab dinta ta kama hannun yaran dake falo ta fice da
su. Sai da suka isa bangaren Hajiya Kaltume sannan suka shiga motar Yasir yayi mata
key ya fice daga gidan suka dauki hanyar gidan Gwaggo.

“Hurriya”

“Na'am”

“Dan Allah ki bawa Rukayya hakuri, kuma ki lallaba Gwaggo kar ta yo fushi, ni kaina
ban jidadin abun da ya faru ba, gaba daya na rasa gane abun da ke min dadi gidan
nan ya rikice, mun rasa Salma, Hajiya ba zata karbi soyayya ta Rukayya ba, Hajiya
kuma tana asibiti yanzu haka? Gaba dayana rasa ina zan saka kaina na ji sanyi”

“Asibiti bata da lafiya?”

“Suma ta yi, amman da sauki gobe ma Appa yace ba za'ayi zaman gaisuwa ba, shiyasa
aka yi addu'a uku a yau”

An yi addu'an uku kuma bata sani ba? Ta tambayi kanta.

“Ban san an yi ba, kuma ban san an kai Hajiya asibiti ba”

“Kina cikin daki koda yaushe Hurriya ya za'ayi ki sani, kin zaman dabam”

“Bana jindadin shiga cikin mutane ne, wani lokacin ina tsarguwa”

Ta dora hannunsa biyu a sitiyarin motar.

“I understand your situation now...”

Daga haka be kara cewa komai ba, har suka isa gidan.

“Ki aje su ki dawo na maida ke”

“Toh”

Ta amsa sai a lokacin ta tuna da siyayyar da Captain yayi musu bata ba su ba, kuma
bata isa tace Yasir ya koma su dauko ba. Haka ta shiga cikin gidan tare da yaran ta
mika su hannun Gwaggo tana fada mata abun da Appa yayi musu a jiya, Amma ta kalleta
yanayin fuskarta ya nuna akwai damuwa da magana mai yawa a tare da ita amman babu
bakin fada.

“A da yardar Allah komai zai warware, sai ta ga Iyami ta tashi da idonta, amman
zaman aure kam ko da ya dawo yace zai maida Iyami ba zan yarda ba, aure ya kare
kenan Allah ya bata na gari, wannan wahala da ta sha ta isa haka, amman wai duk
wannan abun Rukayya bata gani ba saboda rashin hankali da tunani take kokarin
daukar kanta ta jefa a gurin Kaltume? Me ake da Kaltume me ake da jininta? Har
abada ko ba ni da rayuwa Rukayya ba zaki auri Yasir ba, sai dai ki mutu babu aure,
na Iyami ma kaddara ce da ba mu isa mu kauce mata ba”

Rukayya ta mike tsaye ta fice daga falon gudun hawayen da suka tarar mata kar su
zubar mata a gaban Gwaggo ta sha fada, daman tun jiya take mata masifa har yau da
dare. Hurriya ta kalli Gwaggo cikin yanayin rashin dadi ta ce.

“Gwaggo ko da tana son komawa? Yanzu idan Appa ya zo yace ta yi hakuri ta dawo ba
zata dawo ba?”

“Bata ma so! Auren babanki da Iyami rabuwa ce ta har abada”


Hurriya bata saurari maganar Gwaggo ba, ta matsa kusa da Iyami ta kama hannunta ta
rike.

“Amma wai baki son komawa ki zauna tare da mu? Idan kika ji sauki? Kowa yana da uwa
a gidan mu kadai ne ba mu da”

Amma bata ce mata komai ba, daman kuma ba zata ce ba domin bata iya magana a yanzu.

“Amma ki matsa hannuna sau daya idan zaki koma, idan ba zaki koma ba ki matsa
hannuna sau biyu”

Babu bata lokaci Amma ta matsa hannunta sau biyu ta girgiza mata kai. Gwaggo ta ce.

“To ki cire rai daga yau, ki dai fatan uwarki ta samu lafiya, kuma ta samu talaka
irinta mai mutunci ta aura, kishi da Kaltume kam an gama har abada, miji dai take
tutiya, to an bar mata shi ta dafa ta ci, wannan bakin kishin ya isa haka akan
ƴata, tsabar hauka har Rukayya take son jajibo mana wani aiki, sakaryar yarinyar
kawai”

Hurriya ta mike tsaye tana jin kamar ta fashe da kuka ta fice daga falon ba tare da
tayi musu sallama ba. A lokacin da ta fito cikin gidan sai tausayinta ya kama Yasir
ba dan ya san abun da ya gudana a tsakaninsu ba, sai dan a yanzu ya san yadda zafin
rabuwar auren iyaye yake, saboda abun da ya faru tsakanin Appa da Hajiya Kaltume a
yau, shi da yake babba kenan balle kuma ita da abun da ya faru tana karama, a yanzu
ya kara yarda idan iyaye suka samu tsabani har ta kai ga rabuwa yara yake taɓawa
fiye da yadda yake taɓa iyayen, ya ga halin da kanensa suka shiga da kuma
mahaifiyarsa ga shi shi kansa abun ya haifar masa da damuwa balle kuma Hurriya da
take karama da kanenta da su ma a yanzu suke tasowa.
Ta bude motar ta shiga ta rufe motar tana jin kamar ta fashe da kuka. Be mata uffan
ba shi ma ta shi damuwar ta isheshi baya son ya tambaya ta fada masa Gwaggo ta fadi
wata magana akansa ko ga Rukayya ko kuma ta mata fada saboda shi.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

After ya rufe motarsa ya bude back seat ya dauko katuwar ledar ya rufe motar ya
nufi falon Momy. Sai da ya fara danna door bell sannan ya murda kofar ya shiga.
Momy na zaune falon Namra ma kwance a doguwar kujera suna zancen Hajiya Kaltume,
sai dai shigowar Captain ya saka duk suka yi shiru, Namra ta tashi zaune tana masa
sannu da zuwa, but still yana jin babu dadi a yadda ya nunawa Hurriya kulawa a
dazun.

“Captain yanzu ake tafe”

Momy ta fada, sai ya dora ledar a kujera yana daga tsaye yana murmushi ya amsa
mata.

“Ni ma ban sa ran zan dawo yanzu ba, tafiya ce ta kama ni gobe da safe zan bar
garin nan?”

“Lafiya dai?”

“Yanayin aikin ne, zan yi 1 week a Kaduna”

“Da sauki ai, gida zaka je”

“Da can nafi son Kaduna, yanzu kuma na fi son nan”

Namra ta yi murmushi.

“Gashi kuma ka kusan gama aikinka na nan ai, ka koma KD gaba daya”

“Ina tunanin Daddy zan yi ma magana, a san yadda za'ayi a bar ni garin nan, domin
idan na koma Kaduna ba zan samu zuwa nan ba. Ina Hurriya?”

Momy ta sake dubansa bayan kallon da take masa da dan mamaki ta ce.

“Hurriya kuma?”

“Yea na siyawa twins dinta abu ne, kin san yadda nake son yara”

Ya amsa yana murmushi acting like bakin gaskiyarsa yaran ya kawo wa.

“Yaran ma ta tafi ta kai gida ai, ba nan suke zama ba”

“I know tsaraba ce bari na aje a dakinta”

Ya dauki ledar sai Namra ta mike tsaye.

“Let me help you”

“No please ajewa kawai zan yi na fito”

“To ai bata nan kuma yaran sun riga sun tafi”

Cewar Namra tana kallonsa da shakku a idonta. A take ransa ya bace ganin tana
kokarin kure shi.
“That's right idan ta dawo sai ta zuba ashara”

Ya dauke kansa ya nufi stairs rike da ledar, har dakinta ya shiga ya aje mata ledar
kan gado ya juyo zai fito sai kuma ya juya yana karewa dakin kallo, karamin gado ne
daidai ita sai mirror da closet dinta daga gefe. Ya taka ya isa closet din ya bude
yana kallo, can kuma ya rufe ya dawo gurin mirror yana duba kalolin mai da turare
dake gurin, ya kai hannunsa ya bude durowar dake jikin mirror a nan kuma yan kunne
da sarka ne sai agogo daga kasa kuma hotuna ne. Hotunan ya dauka ya shiga dubawa,
wani gurin ita da Hamad ne wani da Amma wani kuma family pictures ne su hudu, wani
kuma ita da Appa babu wanda take ita kadai sai wanda take karama, inda take rarrafe
wani kuma ta fara tashi dayan lokacin da ta kare primary. Murmushi yayi ya juya ya
kalli kofar dakin dake bude sannan ya dawo da idonsa gurin mirror ya sake dauko
wasu hotunan dake aje gefe daya, su kan nata ne inda take ita kadai sai kuma
wandanda ta yi ranar birthday ta sun yi kyau sosai ko'ina kuma tana sanye da abokin
rayuwarta ne wato glasses. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya dora hotunan
yana ta dauka hoto sai da ya gama sannan ya maida su a muhallinsu ya dauko
awarwaronta ya duba ya dauki zoben dake tare da sarka ya duba sannan ya aje ya rufe
mata gurin ya maida wayarsa aljihu ya fice daga dakin ya ja mata kofa. Da sassarfa
ya sauko stairs din kana ganinsa ka san a hanzarce yake.

“Momy zan tafi sai mun yi waya, sauri nake akwai mai jirana”

Mamaki ya hana Momy ce masa komai har ya fice. Namra ta daki hannun kujerar.

“Me na gama fada miki yanzu Momy? Kin ga gani ko?”

“Toh ni ma dai abun ya daure min kai, amman kin san Captain yana da son yara fa”

“Maganar ba ta son yara ba ce kawai, ko last time da ya aike ni siyo masa a Mall na
je office dinsa na samu glass din Hurriya and he was telling me wai ya bata wani
gilashin ne, kin tuna ko ranar da ya saka ta girki, and dazu da safe karki ga yadda
ya damu saboda ya same ta tana kuka”

“Kuka me?”

“Na munafurci da neman jan hankali mana, ni ma ban san dalilin kukan ba kuma kin ga
ko lokacin da ya tarar ina fada da yarinyar ita ya goyawa baya, saboda ita har
marina yayi fa”

Momy ta dan yi dariya kamin ta yi murmushi sai kuma ta sake yin murmushi abun kamar
zai kama kanta sai kuma ta ji be kama kanta ba.

“Amman Captain yafi karfin wannan yarinyar ai, beside idan ma zai so wata a gidan
nan ai ke ce kuma ina jiyo kamshin hakan”

“Babu macen da tafi karfin namiji Momy, yarinyar ta san yadda take ta sace zuciyar
maza, haka ta yi min a Salim har yanzu idan na tuna sai na ji wani iri, and now
Captain”

“Idan ma haka ne ke kike yin saka, kuma idan har ta dauki hankalin Salim ba zata
sami Captain ba”

“Na yi sake? Momy ni fa mace ce i don't run after a men, idan su ba su nuna suna
ra'ayi ba, ni ba zan iya zubar da ajina na yi kasuwanci kamar yadda take ba”

Namra na rufe baki Hurriya ta turo kofar falon ta shigo cikin yanayi na damuwa
sallamarta ma can ciki ta yi, Momy da Namra kuma babu wanda ya amsa mata, ta iso
kusa da Momy ta risina.
“Momy sannu da gida”

Ta mike tsaye sai Momy ta bita da kallo kamin ta ce.

“Ke...”

Hurriya ta kalleta tare da amsawa a hankali

“Na'am”

“Tafi ki dauko min ruwa a kitchen”

“Toh”

Ta juya sai Momy ta ce.

“Cire hijab din ki aje a nan”

Ba musu ta cire hijab din ta aje ta nufi hanyar Kitchen, Momy ta bita da kallo da
ta fito ma Momy kare mata kallo take tsab sannan ta karbi ruwa.

“Toh tafi dakinki”

Hurriya ta dauki Hijab dinta ta nufi hanyar stairs, sai da ta haye sama gaba daya
sannan Momy ta kalli Namra ta ce.

“Na ga dai idan farin nan ne ke ma kina da shi, kuma ko mazaunai kin fita ban san
wani abun ja mata hankali a jikinta ba”

“Tana da kyau Momy kuma munafuka ce ta iya kisisina kala kala”

“Ko dai minene ki cire wannan a ranki, ni da Hajiya Turai babu wanda muke so
Captain ya aura sai ke, idan ma be aureki ba ai ba zan bari ya auri yarinyar da ba
ajinsa ba irin Hurriya”

Namra ta mike tsaye tana rike da wayarta.

“That's mean idan Hurriya tana gidan nan wani ba zai taba cewa yana so na ba”

“Ki bude idonki Namra yanzu lokaci ya wuce da zaki ce sai anyi yaki a same ki, idan
kina son Captain to ki takawa yarinyar nan birki, ko da ma baki son shi ya kamata
ki hana alakarsu ko dan abun da ta yi miki amman idan kika kyale kin bata dama
kenan, sannan ni da ke mun san Captain ya fi karfin yarinyar nan waya sani ma nan
gaba kadan zata iya makancewa gaba daya, kuma yadda uwarta ta zo ta yi mana milki a
gida yarta ma tace zata auri Captain ta yi yadda take so, abu ne da ba zan dauka
ba, idan Khairy ce ko wata a cikin yayan Kaltume kina ganin zata kyale Hurriya ne?”

Fada sosai Momy take ta wani bangaren tana ganin kamar har fa laifin Namra na saken
da take yi har Hurriya take son damar yi mata. Namra ta sauke ajiyar zuciya ya nufi
stairs ta sani tana son Captain fiye da yadda ta ji tana son Salim da farko, har
tana murna tana ganin kamar sauyi ne Allah yayi mata saboda ta rasa Salim yanzu
kuma Hurriya na son sake jefata a cikin wata damuwar, idan har bata auri Captain ba
to be kamata ace ya auri kowa daga familynsu ba sai dai daga wajen familynsu balle
kuma ace cikin gidansu kuma kanwarta da suka hada jini daya. Ko da soyayya ce kadai
be kamata Hurriya ta yi da Captain ba balle aure, sai dai yadda ta san halin
Captain wata kila ko da wata alakarce ba zata dade ba saboda yanayin fushinsa da
saurin daukar zafi kamar kofin tasa, sai dai duk da haka Momy tana da gaskiya be
kamata ta zuba ido Captain yayi soyayya da Hurriya ba ko da be aure ta ba, hakan
zai lalata alakarsa da gidan idan suka samu tsabani kuma zai juya mata baya ba zai
yi tunanin ya aureta ba. Jingina ta yi da kofar dakinta bayan ta rufe, abu ne mai
zafi da ba zata iya rike hawayenta ba, ko da tafiya kuke a hanya wani yace yana son
kawarta ba ita ba zata ji babu dadi balle kuma ace cikin gidansu. Bayan kuma duka
mazajen nan biyu sun nuna ita suke so amman gashi yanzu Hurriya tana dauke
hankalinsu, ta saka hannunta a baki tana ciza kumbarta, gaba daya ta ma rasa me
zata yi, ta wank bangaren tana ganin kamar yunkurin yin wani abu zubar da kimarta
da martabarta ne ne mace.

“Amman Ina son Captain, Hurriya me yasa kike min haka? Why?”

Ta fadawa kanta kamin tambayar karshe ta biyo baya. Ajiyar zuciya ta sauke ta share
hawayenta ta nufi gadonta ta zauna tana busar da iskar bakinta, zuciyarta na mugun
zafi wani fitinannen kishi take ji marar misaltuwa, kamar an fisgeta haka ta tashi
ta fice daga dakin.

A kasale Hurriyya ta shiga dakinta bata lura da ledar dake kan gadonta ba saboda
hankalinta gaba daya ba a gurin yake ba, ya tafi gurin tunanin rayuwarta ta baya,
alamar da Amma ta bar mata na cewar ba zata dawo gidan ba ya saka ta kewar lokacin
da take gidan, tana ayyana yadda zata cigaba da fuskantar wahala da kalubale na
rashin Amma a gidan. Daf da zata zauna ta yi arba da bakar ledar daman hausawa sun
ce hankali ke gani ba ido ba. Hannu ta saka ta lalaba ta juya ta kalli kofar dakin
dake rufe tana mamakin waya kawo ledar a dakin. Zaunawa ta yi sannan ta saka hannu
biyu ta bude ledar wani dan karamin kati ne a sama dauke da wasu takaitattu
kalmomin.

_Tafiya ta kama ni yau din nan, kuma zan yi sati a KD, na san kuma ba ki samu
abinci in time na siya miki wannan i hope zai taimaka, karki ci da yawa so that
yayi miki sati lol_

_Yaya_

Tana gama karanta sai ta ji kamar an cire mata damuwanta gaba daya, sai murmushi
take tana sake karantawa, and the part da yace kar ta ci da yawa ya saka ta
nishadi. Ta aje takardar a gefe ta shiga ciro kayan, kwalin dabino ne uku sai
chocolate da kilishi da aka busar tare da biscuits kala kala da kuma karamin kwalin
cornflakes da madara cube sugar and different varieties of sweet Candy. Chocolate
daya ta dauka ta bude ta fara ci tana tuna abun da ya faru a dazun tsakaninsu
murmushinta ne ya fadada zuciyarta kuma ta shiga bugawa da mugun karfi kamar zata
fasa kirjinta ta fito, numfashinta yana yin sama kamar yadda ta samu kanta a
lokacin da ya matso daf da ita yana mata magana.

“Hurriya?”

Ta kalli kofar dakin a zarane tana amsawa Namra dake tsaye rike da kofar.

“Na'am”

“Ina fatan dai ba rokon Captain kika yi ya siya miki wani abu ba?”

Ta girgiza mata kai.

“Good saboda wannan iskancin da karuwanci da kika rika yi ma Salim be kamata ki


koma gurin abokinsa ba bayan kuma kin nuna masa baki sonshi, sannan Captain ba
sa'arki ba ne zaren ba kalar yadin ba ne, yana da kyau ki yi hankali tun wuri, bana
son kina shige masa, karki sake yi masa magana daga yau, saboda ni yake zuwa gidan
nan so daga yau bana son na sake ganinki idan yana nan, ban ma rashin hankali irin
na ki me Captain zai yi da makauniya”

A nan sai Hurriya ta kasa hade maganar da Namra ta jefe ta da ita.


“Zan kiyaye, ni daman ba ni nake mishi magana ba ni babu wata alaka a tsakanina da
shi, wata kila ba ki fahimta ba ne, zancen makanta kuma wannan ba da ni kike ba, da
mahallice ma kike ke ma kuma ba ki wuce ya dora miki ba”

“Idan be dora min ba, ke ai zai ki zo ki dora min shashasha kawai”

Taja tsaki sannan ta ja kofar dakin ta rufe da karfi. Hurriya ta ja dogon numfashi
ta sauke.

“A haka Amma kike cewa ba zaki dawo ba? Haka zan yi ta zama a gidan nan ina ganin
wulakanci kala kala? Idan wannan ya wuce wani zai zo? Tun da kika bar gidan nan ban
sake farinciki ba, na koma kamar wata bare kowa taka ni yake yadda ya so”

Ta share hawayenta, ta sake daukar takardar ta karanta, this time around sai ta ji
karatun be mata dadi ba kamar dazun ya manta da ita damuwarta ya sauya shafin
bakincikin zuwa fari ba, mikewa ta yi tsaye ta nufi gurin da wadacan takardun da ya
bata suke ta saka wannan a ciki. Sannan ta dawo ta sauke kayan daga kan gadon ta
jerasu a closet dinta ta dawo ta kwanta saman gadon feeling so boring ba tare da
dalili ba.

A WEEK LATER.....

Khairy ta cije baki tana jin kamar ta buga wayar a kasa kuma babu dama.

“Haba Adam wani irin careless ne wannan? Na fada maka yau aka sallamo Hajiyata daga
asibiti fa, kuma yar'uwata ta rasu ko sati biyu ba ayi ba amman ka kasa daga min
kafa wani irin abu ne wannan?”

“Look Khairy na daga miki kafa fa, ki duba tun lokacin da na baki kudin nan, kuma
na fada miki nan da 3 weeks zan bar kasar nan, idan na tafi ban samu yarinyar nan
ba kin san halin da zan shiga”

“Babu halin da zaka shiga tun da ba tare aka haifo ku ba, kuma ba Hurriya ce kadai
yarinya ba, so nawa mutum ke son abu be samu ba kuma ya hakura ni kaina wanda zan
aura yanzu ba wani son shi nake yi ba, amman a haka na hakura ba dole abun da mutum
ke so yake samu ba”

“Ke dabam ni dabam, and ban ce dole sai na aureta ba since bata so na amman i have
to teach her a little lesson ko dan gaba, kuma ki kika kawo wannan bad idea din sai
after na saka rai sai kuma ki fara min yawo da hankali”

Ta daga kafadunta kamar yana tsaye a gabanta.

“Amman ai yi aikina na baka kai ya kamata ka yi amfani da damarka ka yi abun da ya


dace?”

Ya amsa da karfi.

“How? A kankanen lokaci? Bayan kuma kin san babu yadda za'ayi na iya contacting
yarinyar nan”

“Adam ba zaka zo ka tsare ni da fada kamar ubana akan kudin da na fi karfinsa a


gidan mu ba, ina cikin nawa tashin hankali da damuwa karka takura min mana idan
kudi ne ka zo ka karbi abun ka na huta kai ma ka huta, just because of na kawo idea
cewa ba dole sai ka aureta ba zaka iya biyan bukatarka ai na maka hanyar da ya dace
ko?”

“Hanyar da kika kawo mummunar hanya ce da zata tana mutunci ni ma, kuma na jawa
iyayena zagi, babu wani amfani da za su min”

“Kuma ka yarda ka dauka?”

“Saboda na dauka shawara ce mai kyau da farko, later on kuma na gane bata lokaci ne
kawai, yadda zan yi samu magana da ita ma aiki ne”

“Zaka iya zuwa ka saka a sallamo maka ita ka mana ka yi magana da ita”

“Idan kuma na yi haka daga karshe ban zamu biyan bukata ba fa? And i told you ki
dauko yarinyar nan ku fito tare kin ki”

“Bata yarda ta fita da ni yanzu, kuma ba zan iya mata dole ba, sannan kuma idan
wani abu ya faru a lokacin da muka fita tare ai za a gane cewar ni ce”

“Daman ke kika lalata komai tun farko, kika ce mata ni ba mutumen kirki ba ne and
trust me you will regret this Khairy”

“Ka yi duk abun da zaka iya Adam karka fasa, kuma karka sake kirana matukar ba
kudinka zaka karba ba”

“Khairy ni zaki fadawa haka?”

Taja tsaki ta yanke wayar ta jefata a kan kujera, cikin wani irin fushi da bacin
rai ta ce.

“Hurriya kin haddasa min fitina, ke da uwarki kun hana mu jindadin rayuwar duniya,
ban gayyace ki bikin birthday na ba kika je duk shi ne silar, shi kuma ya bi ya
haukace sai ka ce ita kadai ce mace a duniya”

Ta zauna da karfi kamar an mata da dole tana jin kamar Hurriya tana kusa da ita ta
yi mata shegen duka ko ta rage wannan bacin rai.

“Ban san me yasa ma na karbi kudinsa tun farko ba? Ko zuciyar imani ba shi da ita
ji yadda yake takura min kamar be san ayi min mutuwa ba”

Ta sake jan tsaye sai a lokacin tuna da kiran da Hajiya Kaltume take mata, mikewa
ta yi tsaye tana fadin

“Gaba daya ya hargitsa min tunani”

Ficewa ta yi daga dakinta nufi dakin mahaifiyarta, ta shiga dakin cikin bacin ran
da ya gaga boyuwa a fuskarta.

“Lafiya kike?”

Hajiya Kaltume ta tambaya cikin wani yanayi na rashin kuzari, ta rame kamar ba ita
ba bakin fatarka ta karu har ya mata yawa tsabar bakinciki da damuwa. Hajiya Fatee
dake zaune gefenta ta tabe baki.

“Ke ma dai Hajiya har kya tambaya? Yayanki a gidan nan waye ransa ba a bace ba?
Waye be shiga damuwa ba? Ai ko cewar da yayi ba zai sake musu komai ba ya isa ya
saka su shiga damuwa balle kuma ya hada miki da saki, goma ta hadu da ashirin, ga
kuma aure da zai kara kin ji ishirin ta hadu da talatin kenan, wannan abu ai ya
miki yawa”
A take Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.

“Ni yanzu ganin make kamar ba gaske ba, ashe rana zata zo da Alhaji zai iya sakina?
Kuma ya ce min zai karo aure? Wai saboda an doki matar da zai aura har ya ce babu
ruwansa da yarana? Ki duba Hajiya Fatee satina daya a asibiti amman ko waya be daga
ya kira ya ji ya jikina ba? Hajiya Binta ma ko a leke bata leko ta duba ni ba? Sai
kace makikiyarsu”

“Ita dai Hajiya Binta ai bata ki kin mutu ba, shi ma kuma namiji ina ruwansa zai
kara aure kuma ya dawo da Iyami? Wannan abu na ku fa shiga tsakani ne kawai, waya
sani ma ko gurin bokanta kika je shi ne ya samu sa'a yayi mata aiki cikin sauki”

Hajiya Kaltume ta dan saci kallon Khairy dake zaune gafenta.

“Khairy dauki atm dina ki tafi ki yi transfer Hajiya Fatee zata baki account”

Khairy ta share hawayen da suka cika idonta na tausayin mahaifiyarta ta mike tsaye
tana amsawa.

“Toh”

Ta karbi account din a hannun Hajiya Fatee sannan ta dauki Atm din ta fice. Sai
after ta fice sannan Hajiya Kaltume ta kalli Hajiya Fatee ta ce.

“Bana ma son sun san cewar sanadina Salma ta rasu, wannan magana a tsakanina da ke
ne kawai Hajiya Fatee”

“In Shaa Allah babu wanda zai ji, daman ba komai ake fadawa yara ba, amman dai tun
farko ke kika yi sake Hajiya ga wanda ya saba miki aiki kika tsallake kika tafi
gidan malaminta”

“Kina da gaskiya wata kila malaminta ne, ko kuma malamin Nafisa ba, ita yar aikin
ta hada kai a cutar da ni, aiko sai na ci ubanta idan abubuwa suka daidaita, dan
Allah ki kara ba shi hakuri ga kudin nan za a tura masa a account ayi aikin da yace
duk abun da ya dace ayi”

“Da kaina zan yi magana da shi kamar yadda na yo yanzu, kuma ina tabbatar miki
Alhaji a haukace zai zo ya maida ke kuma ya gyara duk kuskurensa, aure kuma ba
za'ayi ba Iyami da yayanta kuma sai labari a gidan nan”

“Haka nake so, Allah ya bar kawancen mu har aljanna”

Cikin yanayin damuwa da muryar rashin lafiya Hajiya Kaltume take karfin hali tana
amsawa Hajiya Fatee.

“Ameen Ameen ai komai zai daidaita, bari dai Malam ya fara aiki ki gani ke ma ai
kin san irin aikinsa”

“Na sani kaddara ce ta kai ni gurin bokan Iyami, ko na Nafisa, wannan aure aure na
Alhaji yana haifar min da masifa, kuma har yake son dauko wata saboda rashin tunani
irin an namiji, su da sun ji suna da kudi ba zama lafiya sai aure, dan Allah ki ce
Malam ya daure shi daga aure nan a hana shi aure ko bayan na mutum...”

“Haka za'ayi, domin wannan yarinyar da yake son daukowa ma daga ganinta ita ma a
tsaye take, kara a hana ta shigowa tun wuri”

“Hmmmmm Alhaji ya ba ni mamaki”

Cewar Hajiya Kaltume tana girgiza kai...


Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Hajiya Fatee bata bar gidan ba sai da Khairy ta dawo daga bank ta tabbatar mata da
cewar ta yi transfer kudin zuwa asusun Malam.

“Toh Allah ya miki albarka, ku kwantar da hankalinku da yardar Allah komai zai
wuce”

“Ameen Hajiya”

Ta amsa sannan ta mike tsaye ta fice bayan ta ajewa Hajiya Kaltume ATM dinta a kan
gado. Hajiya Fatee ta dauki Hijab dinta ta saka ta mike tsaye tana rike da jakarta.

“Ina isa gida zan kira na fada masa an saka masa kudin, kuma yace da zarar ya saka
hannu aka fara aikin nan da kwana uku komai zai daidaita”

“Allah ya nufa Hajiya, wannan bakincikin kar ya kai ni”

“Komai dai wuce, bari na tafi kar yamma yayi”

“Toh na gode Allah ya bar zumunci”

“Ameen Allah kara lafiya”

Ta fice daga dakin, Hajiya Kaltume ta gyara zamanta zuciyarta na mata mugun ciwon,
idan ta tuna yadda Appa ya wulakanta sai ta ji kamar ya hade zuciya ta mutu, idan
har bata hana auren nan ba kuma ta hana Amma da dawowa gidan tabbas ita din ba
mutum ba ce, sanadin su komai ya faru, bayan rasa yarta ga kuma saki da Appa ya
dankara mata sai kuma wulakanci ya biyo baya,ya kwatanta mata irin abun da yayi ma
Iyami lokacin da ta haifi yan biyu. Cikin tsananin damuwa ta dago ta kalli kofar
dakin da aka bude, Ruma ce ta shigo tana rike fa plate din abincin da take ci.

“Hajiya ga Momy nan da bakuwarta...”

Rufe bakinta yayi daidai da shigowar Momy tare da Hajiya Turai a dakin. Hajiya
Kaltume ta gyara zamanta da sauri tana jin kunya na rufeta, kunyar sakin da Appa
yayi mata bayan ta gama nuna karfin iko da isa a gidan, ga kuma jinyar da ta yi
asibiti be je ba Hajiya Binta bata je ba haka ma Momy bata leka ta ba, har wata
zuciyar na raya mata da ganganci suka shigo. Daga bakin kofa suka tsaya Hajiya
Turai kamar mai kyamar dakin har da dage riga.

“Sannu da jiki Kaltume, Hajiya Nafiss ta ce min kwanan baya ma yarki ta rasu,
sannun Allah ya mata rahama”

Hajiya Kaltume ta kalleta ta san wacece ita, yanayinta tufafin jikinta da gwagwalan
dake wuyanta da hannunta sun wuce ta yi mata irin haukar da ta yi ma Maryam da
Rukayya, hausawa suka ce wasa guri take samu. Dan haka ta amsa mata da lalama sai
dai babu sakewar fuska.

“Amin na gode”

Hajiya Turai ta juya ta fara fita sannan Nafisa ta bi bayanta daman ita tun da aka
shigo uffan bata cewa Hajiya Kaltume ba.

“Samun guri, wato kawota kika yi ta gan ni ko? Saboda yanzu ke ce kadai matar gida,
ai Wallahi ko da ace Alhaji ba zai maida ni ba to sai dai duk abun da na tara ya
kare shi kuma ba zai sake zama da mata ba har abada”

Tana maganar wani mugun abun zuciya na taso mata bakinciki yana neman yi mata yawa.

“Ita ma wannan Nafisar ba kaunata take ba, ko a leke bata leka ta duba ni a asibiti
ba, ko da yake uban gayyar be tafi ba ita yar rakiya ya za'ayi ta tafi”

Ta yi kwafa ta girgiza kai.

“Tabbas na yi sake, da na san haka zai faru da ban tafi gurin wannan bakin bokan
ba, gashi Iyami bata mutu ba yata ta mutu Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Allah
sarki Salma”

Ta fashe da kuka mai karfi tana jin kamar ace zata iya dawowa da ita. Momy ta jero
tare da matar Yayanta Hajiya Turai suka nufo bangarenta, Hajiya Turai dake
murmushin kasaita ta ce.

“Sakin daya ma ta ya rage zai karasa mata shi nan kusa ki koma ke kadai, ban da
rashin sanin darajar kai har yaushe namiji zai sake ka zauna a gidansa wai zaman
yaya? Ba sai ta tattara ta koma gidanta ba ta tare, idan ma yana da ra'ayin maida
aurensa sai ya same ta a can”

“Ah to ke ma dai kya fada, ai haka na fada ni ma yaya dai da wayonsu ta bar su a
gidan ubansu ko ta tafi da su duk daya, ni dai ba zan sake yarda a dauko wahala a
kawo min ba, ga Hurriya nan har yanzu ban haife cikin bakincikinta ba”

Hajiya Turai ta dafa Momy.

“Ai kin yi kokari, ni zan iya rika kowa ban da yaran miji, shiyasa kullum nake
godewa Allah da ya miji ba mutum ne mai aure aure ba, kin ga da mai wannan
kwashekwashen ne da yanzu ya karo aure ko dan haihuwar nan da ta tsaya mana, amman
duk be kula wannan ba, gashi yanzu girma har ya kama”
“Wallahi kin huta, daman zuri'ar duk ba mu da wannan rayuwar ta son aure auren
mata”

“Allah yasa yaran mu su gado mu”

“Amin, da alama kam Captain ma ba zai yi irin wannan rayuwar ba”

Hajiya Turai ta yi murmushi masu nairori.

“Captain wanda auren farko ma ya gagareshi, ina maganar kari?”

“Na farko ma yana kusa, domin yanzu na lura kamar hankalinsa ya karkata gurin Namra
kuma sai dai mu saka musu ido mu ga gudun ruwansu kamin mu ga abun da Allah zai yi”

“Oh yanzu na gane dalilin da yake fada min cewar na kusa samun suruka, amman be
fada min ko wacece ba, har nake ce masa ko da ka jitu da ita ai abun baya daurewa,
sai ya ce min wannan kam idan har na ga be aureta ba to baya raye, amman ko naman
jikinsa take yanka ba zai rabu da ita ba”

Momy ta yi murmushi zuciyarta na kara jaddada mata Namra ce.

“Toh Allah yasa, zaman da yake a garin nan yanzu gaba daya hankalinsa yana gidan
nan komai aiki yayi masa yawa sai ya leko gidan nan”

“Aiko zan jidadi idan haka ta faru, daman abun da muke fata kenan, wata kila idan
ya dawo daga tafiyar nan zai gabatar min da ita”

“Tafiya yayi?”

“Eh tun last week yace zai tafi Abuja?”

“Oh Allah sarki daga Kaduna ya wuce Abuja? Aikin na su ne ba zama”

“Aa be zo Kaduna ba, daga nan Gusau ya wuce yace min sati daya zai yi”

Momy ta jingina jikin Range Rover din aka tuko Hajiya Turai tana mamaki.

“Ni kuwa ce min yayi Kaduna zai tafi”

“Aa gaskiya Abuja yace min, tun last week jiya ma da muke chat da shi yake ce min
ya kusa dawowa”

“Wata kila kuma ban ji daidai ba, ko kuma an canja tafiyar tasa ce daga Kaduna zuwa
Abuja”

“Maybe”

Daga haka suka yi sallama da Momy, Dreban ya bude mata mota sai ta shiga ta zauna
ya rufe Momy ta daga mata hannu ya ja motar. Momya ta shigo falonta ta samu masu
aikinta na kwashe kayan da suka ajewa Hajiya Turai bata taba ko daya ba.

“Kar a taba komai aje su a kitchen”

Kulu ta amsa da sauri.

“Toh Hajiya”

Momy ta haura stairs ta shiga dakinta, wayarta ta dauka tana murmushi maganar da
Hajiya Turai ta fada mata cewar yace ta samu suruka ya faranta mata rai. Akan haka
ne ta gwada kiransa ta ji lafiyarsa a yau domin tun da ya tafi bata kira shi ba,
sai dai tana magana da shi ta chat kamar yadda mahaifiyarsa ma tace. Sai da tana
kiran sunan sai kiran ya yanke alamar ba za a iya samunsa ba.

“Wata kila yana gurin da babu network ne”

Ta furta kana ta bude data ta shiga whatsapp dinta ta duba last chat dinsu two days
sai ta aje masa sako tana murmushi.

“My Son, ya aikin na ku? Hajiya Turai tace min Abuja aka kai ku ashe, amman baka
fada min ba, Allah ya tsare ya dawo da kai lafiya”

Tana kokarin aje wayar reply dinsa ya shigo bata san yana online ba sai a lokacin.

“Amin Momy na kusa dawowa jibi nan, Ammy ta zo kenan?”

“Eh kasan idan ta shigo Family House bata barin garin nan sai ta biyo gurina, ta
fada min albishir din da aka yi mata muna fatan jin labari mai dadi”

Ya turo mata emoji din murmushi sannan ya aiko mata da sako.

“Za ku ji ba da jimawa ba Momy. Hurriya tana lafiya Momy?”

“Hurriya???”

“Na dauka zaka tambayi Namra ne”

Ya turo mata murmushi shi dai yana kokarin isar mata da sakon zuciyarsa cikin
hikima tun da har ta fada masa Ammynsa ta tsegunta mata wani abu a kansa.

“Duka daya ne Momy”

“Aa ba daya ba ne, Namra yar 'uwarka ce jininka zaka iya juyata yadda ka ga dama
ka tambaye ta ko ka saka ta yin wani abu, amman Hurriya baka da alaka da ita”

“Alakar musulumci ta fi ta jini”

Momy ta kashe data ta aje wayar da mugun mamaki a fuskarta. Kar dai ace abun da
Namra yake hasashe ya tabbata kar dai ace Hurriya yake nufi da yarinyar? Idan ba
haka ba me ya kawo zancenta a yanzu. Ta sake daukar wayarta ta bude data ta masa
reply.

“Haka ne, amman ina son ka sani babu wata alaka tsakaninka da Hurriya, ya kamata ka
sani matsayinku ba daya ba”

Wannan karon bayan ya karanta be sake ce mata komai ba har ta gaji ta aje wayar ta
mike tsaye fice daga dakinta. Dakin Namra ta shiga sai ta same ta kwance kan gado
tana waya.

“Aje wayar nan ina son magana da ke Namra”

Namra ta tashi zaune tana kallon Momy da already ta zauna gefen gadonta.

“Me ya faru Momy?”

“Tafiyar da Hajiya Turai ta yi a yanzu ta fada min wata magana da Captain ya fada
mata, na yi zaton da ke yake, sai dai a yanzu da na ke chat da shi sai ya ke
tambayata ina Hurriya?”
Namra ta yi murmushi.

“Ai na fada miki Momy baki yarda ba”

“Ba wai yarda ne ban yi ba, ina ganin dai kamar Captain ba zai tsaya kula yarinya
irin Hurriya ba”

“Saboda me? Ga alama ya bar mana kamin ya tafi? Kuma shi Captain ba irin rayuwarku
ce da shi ba, be cika duba arzikin gidansu ba”

“Ba zan bar wannan ba”

“To ya zaki yi Momy? Ba ayi ma Captain dole kuma iyayensa suna son farincikinsa
fiye da na su babu wani abin da zamu iya yi”

“Iyayensa sun fi ni kyamar talaka, kuma Hajiya Turai ta san yadda nake da Hurriya
dan haka ba zata yarda danta ya aure ta ba, bana ma tunanin auren zai yiyu domin
Captain baya iya jure komai, daga yanzu ina son ki yi duk wani abun da zaki dauki
hankalinsa ki kwantar masa da hankali ita kuma zan yi maganinta na san yadda zan yi
da ita”

“Momy ni fa ba zan cusa kaina a gurin namiji ba, idan har zan yi haka miye amfanin
amsa suna na mace? Idan yana ra'ayi shi zai kawo akansa a gareni, ba wai na shige
masa na nuna masa so ba?”

“Baki son sa ne? Ko kin manta burin da muke da shi akanku? Yanzu ma sai da
mahaifiyarsa ta ce zata fi kowa farinciki idan hakan ta faru tsakaninku, haka kika
yi saka har ta yi nasarar raba ki da Salim yanzu kuma haka zaki zuba mata ido ta
rabaki da Captain? Karamar yarinya kamar Hurriya?”

Namra ta sauke ajiyar zuciya.

“Momy idan yana ra'ayina shi zai kusanto da kansa a gareni kamar yadda yake
kusantar da kansa gurin Hurriya”

“Take dai jan hankalinsa, saboda ta fiki wayo da iya kisisina, ki zauna nan kina
tunaninki na banza da shirme”

A fucewa Momy ta mike tsaye ta fice daga dakin, cikin kufula da fusata ta tura
kofar dakin Hurriya ta shiga.

“Ke...!”

Hurriya ta tashi gaban madubin da take ta juyo ta kalli Momy dake kallonta kamar
maciji yayi arba da kyanwa.

“Daga yau babu ke babu Captain, kar wata magana ta sake shiga tsakaninki da shi,
kuma ko kallonsa kika sake yi sai kusa kasheki... Na fada miki”

Hurriya ta daga kanta da sauri, Momy ta ja kofar dakin ta fice, Hurriya ta dafa
zuciyarta domin ba kadan Momy ta tsorata ba.

“All because of Captain? Ya Allah.... Kamar za su cinye ni ni miye nawa a ciki?


Saboda kawai yana kula ni, su basa kaunar wani ya nuna min tausayi”

Ta koma ta zauna tana busar da iskar bakinta, gaba daya ma sai ta ji gidan ya fita
ranta. A karo na biyu ta mike tsaye sai dai banbancin wannan tsayin da na farkon
wacan na shigor da Momy ta yi ne a birkice tana mata masifa wannan kuma na neman
barin gidan dakin ne. Green hijabi dinta ta dauka ta saka ta saka shoes dinta ta
fice daga dakin, ta san ba ta isa ta tambayi Momy permission din fita daga gidan ba
daman babu ruwanta da ita ko da zata fita ta dade a waje balle kuma yanzu da take
jin haushinta. Haka ma ba zata tunkari Hajiya Kaltume tace mata zata fita ba daman
ba bangarenta take ba, kuma duka duka yau ta dawo daga gidan bayan shafi sati daya
da ta yi a asibitin. Tana fita harabar gidan na Momy ta isa gate dinta sai yaja ta
tsaya tana tunanin ta saci kafa ta tafi gidansu Husna ko kuma dai ta hakura ta koma
a gidan da baya mata dadin zama a yanzu? Jingina da ta yi da gate din tana kallon
Babban gate din gidan da masu gadi suka bude. Ganin Motar Appa ya kara karya mata
guiwa daman shi baya son fitarta tun tana da gata a gurinsa balle kuma bayan da ya
saka mata takunkumin zama gida da hana ta zuwa gurin Amma ba tare da dalili ba. A
madadin direbansa ya nufi bangarensa sai ta ga akalar motar ta nufo gurin da take
tsaye wato bangaren Momy, Hurriya ta bar jikin gate din da sauri ta juyo zata dawo
ciki gabanta na faduwa zuciyarta na raya mata Momy ta hada ta Appa ne wata kila
saboda Captain shiyasa har ya dawo yanzu kuma ya nufo bangaren yayi mata fada. Sai
dai horn din da ta ji anyi ya katse hanzarinta na guduwa ta koma bangaren na Momy,
a lokacin da ta juyo sai ta an faka motar daidai gate din Momy, an sake danna horn.
Cikin karfin hali da hararon laifinta ta nufo motar ta mahaifinta da be cika hawa
ba sai lokaci zuwa lokaci, daman haka yake idan ya hau wannan gobe zai iya hawan
wata. Daidai gurin gilashin motarsa dake back seat ta tsaya domin ta san bangaren
da mahaifinta yake zama a duk lokacin da direba yake tuka shi. Appa ya sauke
gilashin motar ya kalli yarsa.

“Hurriya na ganki tsaye a nan kamar cikin damuwa, na saka direba na zo kuma sai
kika gudu?”

“Na dauka fada zaka min”

Ta fada a shagwabe tana taba yatsun hannunta.

“Fada me kika yi?”

Ta yi shiru tana kallon kasa, sai tausayinta ya kama shi, soyayyar da yake mata
irin ta uba da ƴa tana ta dawo masa a hankali.

“Shigo mota”

Ta daga kai ta kalleshi sannan ta zagaya ta shiga ta dayan side din, direban yayi
baya kadan ya canja akalar motar suka nufi bangaren Appa.

“Wani abun aka miki ne?”

Ta kalli Appa tana mai mamakin yadda yake son ya ji damuwarta a yau, abun da aka
haka rame aka binne shekaru hudu da suka wuce. Ta girgiza kai

“Aa”

“To ya na ga duk kin bata rai? Wani abu kike so?”

Ta sake dubansa neman sanin damuwarta da yake kokarin yi a yanzu ya fi komai


faranta mata rai.

“Ina son na tafi na duba Amma ne!”

Ta furta abun da ba da shi ta fito bangaren Momy ba, farko fitowarta na neman son
tafiya gidansu Husna ne, sai dai kuma bata san kalma da zata fito a bakin Appa ba
idan tace masa gidansu kawarta Husna zata ce bayan sun yi baran-baran da mahaifinta
saboda munafurcin da aka mata sherin cewar ta kulla.

“Ki saki ranki, daman takardu na dawo na dauka ki jira ni a mota yanzu idan na fito
sai mu sauke ki a can na wuce, amman karki kai dare”

“Ba zan kai dare ba Appa”

Ta amsa muryarta na karkarwa saboda kokarin danne kukanta da take. Ta manta when
last ta shiga mota daya da mahaifinta, ta manta when last mahaifinta ya nuna damuwa
da ita, ta manta rabon da magana mai taushi mai dadi ta shiga tsakaninta da
mahaifinta. Ta zauna a motar na tsawon lokacin da ya fita ya shiga bangarensa ya
dauko abin da zai dauko ya fita ya dawo cikin motar. A lokacin da ya dawo cikin
motar sai ta karkarta idonta tana kallon mahaifinta irin kallon da an shafe mata
yinsa a rayuwarta. Direba na tuki Appa yana duba takardun da ya dauko ita kuma tana
kallonsa idan hawaye suka sauko mata sai ta share cikin hikima ba tare da ya gani
ba, lallai a yau ta kara yarda da tabbatar da ko wace ƴa a duniya gatanta uba ne,
ko magana yake maka mai dadi zaka ji ka fi kowa rabo da dace a duniya.

“Hurriya ina tunanin dawowa da yaran nan a gidan nan, saboda ita can ba lafiya ta
wadace ba, kuma ni ba wani sanina suka yi sosai ba, yadda nake rayuwa da duk yarana
su ban yi rayuwa da su a haka ba, ya kamata su dawo nan ni daman bana son rikon
ƴaƴa a gurin kowa, na fi son yarana suna hannuna, ballantana kuma su da suke
kanana, yanzu suke bukatar gata”

Da gaske Appa ne yake wannan maganar ko kuma dai mafarki take yi? Shawararta yake
nema ko kuma fada mata ne yake abun da zai faru? Ta juyar da fuskarta ta matse
kwalla sannan ta juyo ta ce.

“Za su fi jindadin zama a can Appa saboda Amma tana can kuma Gwaggo zata kula da su
sosai”

Sai a lokacin Appa ya dago ya kalleta.

“Ga ki zaki iya kula da kanenki ai kamin a sama miki admission, kuma za a iya
daukar mai aiki ta kula da su, amman maganar gaske ni bana son zaman yarana a ko'in
sai a gidana”

Tabbas haka ne, ba ita kadai ba kowa ya shaida hakan a familynsu Appa baya bada
rikon yayansa ga kowa ko da kuwa Hajiya Binta ce da ta kasance mahaifiyarsa,
shiyasa a lokacin da aka haifi yaran be je duba su ba kuma be je duba mahaifiyarsu
ba ya baya kowa mamaki, sannan ya kyale su be tana cewa bari ya dauko su ko shi ya
tafi ya gansu ba. Wani mamakin be kamata ba sai da Appa ya katse mata hanzarin
tunanin da take ta hanyar aje mata kudi mai kauri a dan space din dake tsakaninsa
da yarsa.

“Ki bawa Hassan da Husaini wannan, kuma ki musu magana ina son zan shigo mu gaisa
da yarana”

“Toh Appa”

Wannan karon bata iya taimako kanta ba har sai da hawayen suka zubo mata, ta dauki
kudin ta bude motar ta fita ta shiga cikin gidan. Appa na zaune a motar yana kallon
kofar gidan ya takure fuskarsa a yanayin damuwa kamar mai tunanin wani abu, can
kuma ya sauke ajiyar zuciya.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Allah ka raba mu da aikin dana sani”

Ya fada yana kallon twins din da Hurriya ta fito tana rike da su ta nufo motarsa.
Bude gefensa yayi sai suka zo da gudu kamar wasu wadanda suka saba rayuwa da shi,
suka shige motar suna murna. Jinin alakar uba da ƴaƴa ya saka sun wayanci shi din
ubansu ne tun a ranar da Rukayya ta tafi da su har suka kwana a gidan, daman kuma
Gwaggo na nuna musu hoton mahaifinsu a wayar Rukayya saboda su san shi ko da ba su
rabe shi ba.

“Gwaggo tace na kawo maka su ka gansu”

Hurriya ta fada cikin rashin jindadi domin bata so Gwaggo ta hana shi shiga gidan
ba. Appa yayi murmushi domin shi ba yaro ba ne ya gama fahimtar komai a kawo masa
yaran da aka yi a waje.

“A haka ma na gode, na jikin Iyami?”

“Da sauki....”

“Me yake damunta?”

Hurriya ta yi hankali da wayon sanin ba komai zata fadawa mahaifinta ba dan haka ta
ce

“Ba wanda ya sani har yanzu”

“An bincika komai nata lafiya kalau?”

“An bincika amman yawanci suna cewa hawan jini ne, ya saka jikinta yayi haka, tana
shan magani kullum sai dai har yanzu babu sauyi”

Appa yayi shiru ya sauke ajiyar zuciya.

_Hawan jini? Wata kila saboda ni ne_ ya fada a ransa feeling guilty. Kadan ya taba
wasa da yaran ya sauke su a motar saboda jiran da ake masa gurin kasuwancinsa.

“Hurriya ki yi magana da Gwaggo, idan ta aminta an ba ni dama sai mu fitar da ita


waje ko za a dace”

“Appa da gaske?”

Hurriya ta amsa da karfi, sai ya daga mata kai da dan damuwa a fuskarsa. Da sauri
ta saki hannun yaran ta fada motar ta rumgume shi ta fashe da kuka.

“Appa na gode, Alhamdulillah Appa na gode da ka sake nuna mana kulawa, kada Allah
ya kawo wani abun da zai tare idonka daga son farincikinmu....”

Kuka take sosai da ya saka zuciyar Appa karaya, Direban ya juyo ya kallesu kadan
yana jin tausayinta, daman ya dade yana tausayin Hurriyya da halin da yake ganin
tana ciki.

“Hakkina ne Hurriya, abun da ya kamata na yi ne tuntuni, kuma In Shaa Allahu zan


yi”

Ta dago daga jikinsa.

“Na gode Appa”

Ta fita daga motar ta rufe masa, direbansa ya juya motar suka bar unguwar.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Hindu ta rike haba tana mamaki.

“Shi da kansa?”

Gwaggo ta amsa mata

“Ni ma abun ya ba ni mamaki, sai dai ba a mamakin ikon Allah, kuma daman shi
maganin dan kwana arba'in ne, idan ba a zafafa ba to sanyi yake daga nan har ya
karye”

Hindu ta taba hannu.

“Hmmm a haka ma mun gode Allah mutunen nan ya fara dawowa hankalinsa mugun abun ta
na magani ne ya koma mata”

“Ya fa koma, yanzu haka saki biyu yayi mata kuma idan na yanzu aka sallame ta ba
tana can asibiti kuma an ce be je ba”

Hindu ta daki kirjin idonta a waje tsabar mamaki har da su gyara zama.

“Ya saki Kaltume fa kika ce Gwaggo?”

“Wallahi”

Hindu ya daga hannu sama.

”Allah na gode maka da baka kashe ni ba sai da na ga wannan ranar, sai ta dandana
ta ji idan akwai dadi, wulakancin da ta saka aka yi ma Iyami yau an mata shi,
Allahu Akbar Allah baka da dole, Allah na gode maka”

“Ni ma dai haka na ce, kuma karshenta ba zai yi kyau ba domin ba, domin hakkin
Iyami ba zamu yafe ba kuma ga Hamad ma zai bibiyeta”

“Shiyasa aka ce idan zaka haka ramen mugunta ka gina gajere, ba a farinciki da
mutuwar aure amman na jidadin mutuwar na Kaltume, saboda ta san yadda ake ji yanzu,
dazun da ya zo har fadar yake wai a min magana yana son ya fitar da ita waje”

Hindu ta kara girmaman lamarin Ubangijina.


“Tabbas wanda ya aje kayansa a gurin Allah baya kunya, kuma mai hakuri mawadaci,
gashi nan Alhaji ya fara dawowa hayyacinta, Allah mai iko, ai tun da kika ce yace a
kawo masa yara su gaisa na san asiri ya fara karyewa”

“Hurriya tace ya fada mata zai dauke yaransa ya maida su gurinsa, ni kam ba zan
yarda ba aje a musu wani sherin kuma karshen daga haka zai iya cewa saboda Iyami ta
koma”

“Ah.. Gwaggo to ai abun da muke nema kenan, Iyami ta koma gidan Mijinta ta rumgume
yayanta ta haifo masa wasu, idan bata koma ba ai bukatar Kaltume ta biya ta samu
abun da take so kenan!”

Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya ta girgiza kai.

“Hindu ba zan iya da sha'anin magani ba, mace idan aka ce miki tsafi take a gidan
mijinta to zaman aure baya dadi ga abokan zama, kuma ba fasawa zata yi ba”

“Yanzu kuma Gwaggo ai ba zata iya komai ba, daman can rashin kula da addu'a ne da
kuma tsarin jini, amman yanzu babu wannan sakakacen duk abun da zata yi kanta zai
koma, wannan sakin da aka mata ma kar ki yi mamaki ace wani sharin ne ta dauko ya
koma mata, Dan Allah Gwaggo karki hana Alhaji maida matarsa idan ya bukata, ita
kanta Iyami da yayanta za su fi samun hankali idan suna guri daya, ba baki nake ba
amman da zarar shi kansa maganin ya sake shi ba zai barku ku zauna lafiya ba sai an
maida masa da natarsa ai yana kaunarta sosai shiyasa aka raba su, ba zai taba
barinta a gidan nan ba”

Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya.

“Ni kam da na tsorata sosai, har ina cewa ko da wani auren zata sake yi ba zan bari
ta auri ta auri mai mata ba, wai wanda matarsa ta mutu ko kuma ba shi da auren gaba
daya, ina ganin kishi kala kala amman na Kaltume ya tsorata ni sosai, mata babu
tsoron Allah a ranta”

“Karki ji komai, da yardar Allah karshenta ne ya zo, ni akwai wani Malami ma da na


ji yana bada taimako kuma ana dacewa gashi babu wani kashe kudi da za'a gwada na
Iyami ko Allah zai saka a dace”

“Shi kuma a ina yake? Lamarin maganin ne yi ake kamar ba 'ayi, sai an yi kamar za a
samu sauki sai kuma ki ga abun be yi ba, kin ga ko wanda muka gwada kwanan baya har
ta fara samun sauki tana daga hannun sai kuma abu ya zo yayi mana shiru”

“Komai ai sai Allah ya yarda Gwaggo kuma shi magani dace, abun da be yi ma wani ba
sai ki ga yayi ma wani, ba san inda dacen yake ba shiyasa ba a gajiya da yi, balle
ma wannan baya karbar kudi mai yawa”

“A ina yake? Kuma ina fatar ba irin masu tsafin nan ba ne”

“Aa babu tsafi a lamarinsa magani ne zallar magani kuma babu kashe kudi, ba zai
wuce ka biya dubu biyar ba shi bakwai takwas zuwa goma, idan mai jinya ya ji sauki
shi ne zai fada maka tukaicinsa sai ka biyashi, kuma yana bada maganin tsari ma
idan Allah yasa yayi maya na warakar ta ji sauki sai ya bata na tsarin jikinta,
kuma ga addu'a tana yi shikenan”

“A wane gari yake?”

“A Neja yake mazauni cibiyarsa na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin
ruwa kusa da dan gandu rice. kuma ya bada number wayarsa ma ba dole sai mutum ya
tafi ba, za'a iya masa magana ta Whatsapp ko a kira zai aiko da magani a duk garin
da kake”

“Toh Maa Shaa Allah, hakan ya fi ai, domin daukar marar lafiya zuwa wani gari akam
ai ya zama aiki sai dole musamman garin da ba kusa ba, kamata yayi ki kira shi ki
yi magana da shi sai mu ji yadda za'ayi”

“Toh daman dai na ce bari na fara fada miki kamin na yi karanbani kin san ni ba
zuciya ce da ni ba, Iyami ta watsa min kasa a ido tun a can baya amman dai ban
daddara ba”

Gwaggo ta yi dariya.

“Ba a biye Iyami ai, ita kanta yanzu ai ta ji jiki gobe ba sai an bata shawara ba”

Hindu ta yi dariya ta ciro wayarta ta kama number wayar da ta ji ana sanarwa a


gidan radio ta dauka. Sai da tabbatar number ce sannan ta kira ta saka a speaker,
bayan ya daga suka yi magana ya ta fada masa yadda ciwon Amma yake da abubuwan da
ake zaton asiri ne.... Ya ba su amsa daidai gwargwadon abun da ya fahimta sannan ya
fada musu yadda maganinsa yake da kuma kudin da za su biya, Gwaggo was shock ta ji
kudin da be wuce 6k amman wasu guraren sai an karbi kudi mai yawa ake ba su magani.
Suna gama waya da Hindu ta tura masa kudin har da doriya, sannan ta kira ta fada
masa ta saka kudi, shi kuma ya fada musu ranar da zai aiko musu da magani tun daga
Neja har garin Gusau.

“Kin ga ai haka ya fi ba sai mutum yaje ba, kuma kina ji yace idan ta samu lafiya
aka biyasa hakkinsa zai bata na tsarin jiki wanda zata yi amfani da shi ita da
yaranta gaba daya, Allah dai yasa karshen wahalar ne ya zo, a huta ba ma sai an
fitar da ita waje ba”

Hindu ta yi murmushi tana amsawa da Ameen.

“Ameen Gwaggo, daman ciwon ba na asibiti ba ne, irin ciwon nan ne da ake aikowa
mace duk abun da ta tara sai ya kare, ta ma yi arziki da ba a haukatata ba, wasu
haukata su ake ko ma a kashesu gaba daya”

“Allah ne ya tsare ita ma ai haukar aka so ta yi, kuma da abun da muke da shi duk
ya kare me ya rage mana? Allah dai ya bata lafiya kuma ya isar mata”

“Ameen bari na duba Iyamin tana ciki?”

“Eh tana dakinta, Allah ya saka miki da alheri Hindu ke ma kin yi kokari”

Hindu ta mike tsaye tana fadin.

“Haba Gwaggo taren mu da Iyami ai ya wuce haka, miye Iyami bata min ba? Babu kalar
arzikin da ban ci ba a lokacin da take gidan Alhaji kuma tun kamin nan Iyami mutum
ce har da rabin mutum”

Gwaggo ta yi murmushi tana kallon aminiyar yarta, Hindu na fitowa daga dakin Gwaggo
ta shiga dakin da Iyami take da sallama. Hurriya da Rukayya da suke rike da qur'ane
suna karanta mata suratul Bakara suka amsa suna rufe qu'anen.

“Aa ku cigaba mana, wannan ayar Allah shi yake kareta daga duk wani sheri”

“Mun gama ne ai Anty Hindu, sannu da zuwa”

Rukayya ta fada sannan ta mike tsaye ta fice, Hurriya ta bi bayanta bayan ta gaisa
da kawar mahaifiyarta. Hindu ta zauna kamar yadda ta saba tana ta hira da Iyami,
sai dai kai kawai Amma take iya daga mata ko da girgiza ko ta tabe baki, wani zubin
kuma ta yi hawaye, sai dai bata iya cewa komai saboda an rike maganar. Hurriya bata
bari Magariba ta yi mata ba ta yi ma Amma sallama da Gwaggo, Rukayya ta rakota har
bakin Titi ta samu abun hawa ta hau ya kawo ta gida, a ranar Hurriya bata gwada cin
abincin dare ba domin ta san za su iya samun matsala da Momy ko Namra ganin yadda
kowa ya kullace akan Captain, daman kuma kamin ta fito gidan Gwaggo sai da ta ci
abinci, a daki kuma sai ta dora da dan abun tabawar da Captain ya bata da be kare
ba har lokacin.

*** *** ***

Ranar Friday Misalin karfe goma sha daya daya da rabi, Hurriya ta fito wanka tana
daure da tawul ta tsaya gaban madubi tana tattara kitson dake kanta ta daure da
ribbon sannan ta ya dauki tissue ta cire gilashinta ta goge sannan ta zauna ta fara
shafa mai, slowly ta ji an bude kofar dakin, ta cikin madubi ta hango Captain tsaye
yana kallonta immediately ta mike tsaye ta juyo ta kalleshi, facing cap din dake
kansa ya cire da hannunsa na hagu ya rike yana kallonta, da sauri ta nufi gurin da
Hijanbinta yake ta dauka sai a lokacin ya kawar da idonsa.

“Subhanallahi what is happening here”

Da sauri Hurriya ta nufo kofar dakin dake bude ta rufe sannan ta dawo gabansa cikin
tashin hankali.

“Me kake yi nan?”

Ya kalleta sai yayi murmushi sai kuma ya nufi gadonta ya dora karamin kwalin dake
hannunsa, daga bisani ya saka dayan hannunsa aljihu ya ciro wani box.

“Wannan zan baki”

“Minene?”

Ya bude box din ya ciro wani abun hannu na azurfa ya duka ya aje kwalin.

“Kawo hannunki”

“Yaya bana so dan Allah”

Ya daga kansa sama ya rufe ido. A take ta fara masa kukan tsoro da shagwaba a
lokaci daya.

“Ina bindigarka take?”

“Tana mota”

Ya amsa ba tare da ya bude idon ba, domin kokarin kwantar da fushinsa yake that's
why ya amsa mata kai tsaye, if not dauke ta zai yi da mari a gurin kuma bata isa ya
tsaya yana neman ta yi abu tana masa wasa ba.

“Na san baka maimaita magana amman idan Momy ko Yaya Namra suka ga wannan abun a
hannuna zai iya zame min matsala”

Ya bude idonsa ya kalleta.

“Baki murna da dawowarta Hurriya? Baki min sannu da zuwa ba, ban ga shaukin murnar
dawowa ta a fuskarki ba why? A madadin haka sai tambayar kike me ya kawo ni dakin
nan?”
“Baka saba shigowa nan ba, be kamata ka shigo ba idan Momy ta gani zata min fada,
kuma Yaya Namra zata ji babu dadi kuma ko wacece ba zata jidadi ba ace saurayinta
yana kula wata”

“Saurayinta...!?”

Ya fada as question as surprised.

“Ita tace miki ni saurayinta ne?”

Hurriya ta sauke idonta kasa.

“Na gane”

Ya fada yana dan hade rai, domin ya fahimci idan yana yi mata magana da sakewar
fuska ba zata amsa masa yadda ya kamata ba.

“Ba ni hannunki”

A take ta fara masa kuka.

“Zata yi fada idan ta gani”

“Ba ni na baki ba? Wallahi wannan ba daga ni ba ne?”

“Waya ba ni Salim?”

“Come-on ya za'ayi Salim ya ba ni abu ya ce na baki kuma na baki har na bukaci ki


saka”

“To ya ba ni”

Har yayi kamar zai yafa mata bakar magana sai kuma ya ji ba zai iya ba.

“Wani ne ya ce na baki, na ba shi labarinki yadda kike da kirki da tarbiya da


kokari, sai ya yaba halinki kuma ya bukaci na baki wannan as gift kuma yace na
gaishe ki”

“Ban san shi ba....”

“Ba dole sai kin san kowa ba....”

Ya daka mata tsawa.. Sai ta matsa baya ta fashe da kuka. Hannu ya kai ya dafe
kansa.

“Please please ki daina min musu, idan ni na baki abu ba zan ji kunya ko tsoron
fada miki ba, kuma ba zan miki karya ba”

Hannu ta miko masa, ba dan tana so ba sai dan tana tsoron wani ya tarar da shi a
dakin. Matsawa yayi ya bude abun hannun ya saka mata ya rufe da abun rufewarsa. Ta
kai dayan hannunta ta taba awarwaron da aka rubutawa sister a jiki, ta ji gabanta
ya fadi wani tsumayi ya saukar mata.

“Na gode”

Domin al'adarta ce yin godiya a duk lokacin da aka yi mata wani abun alheri.

“It's my pleasure... Daga Ethiopia na zo miki da shi”


Kallonta yake kamar zai fada cikin idonta, tana jin kamar motsi a jikin kofar dakin
sai ta dago da sauri ta kalleshi a razane.

“Wani zai shigo”

Tsoron kar Momy ko Namra ta shigo dakin su ganshi ya manta ita haramci da halarcin
taba jiki ko hannun da ba muharraminta ba, bata san lokacin da ta kama hannunsa da
sauri taja shi zuwa bandakinta ba, shi kuma ya bita kamar wani hoto, hannu biyu ta
saka ta turashi ciki ta rufe bandaki, ta dawo da sauri zuciyarta na rawa ta bude
kofar dakin ta leka, ganin babu kowa ya saka ta rufe kofar dakin ta dawo ta bude
kofar bandakin.

“Fito babu kowa”

Ya fito kamar yadda ta bukata sai ta rufe kofar bathroom din ta kalleshi a kunyace.

“I'm sorry bana son wani ya same ka a dakin ne”

“Okay”

He said sannan ya nufi kofar fita sai kuma ta yi saurin dakatar da shi.

“Aa karka fita karka fita”

Ya juyo ya dawo ya tsaya gabanta yana kallonta, hakan sai ya kara tsanananta
bugawar da zuciyarta ke yi fiye da kima, musamman da ta daga kai ta kalleshi sai
idanuwansa dake kanta suka fada a cikin nata idon. Ta dan matsa baya shi kuma ya
nufi gadonta ya zauna yana kallonta

“Aa karka zauna idan wani ya same ka a nan na shiga uku”

Ta fashe da kuka sai ya mike tsaye ya nufo kofar fita, sai ta kara sautin kukan da
take wanda ya fi kama da shagwaba har da buga kafa a kasa, ba kuma ta yi dan
shagwabar ba sai dan ta rasa yadda zata yi.

“Karka fita”

Ya juyo ya kalleta.

“Ya kike son na yi? Kin ce kar na zauna kuma yanzu kin ce kar na fita what do you
want to do?”

Ta share hawayen ta nufo kofa.

“Ka tsaya a nan zan sauka falo na duba idan babu kowa sai ka sauko”

Samun kansa yayi da amsa masa.

“Okay...”

Ta nufi kofar ta bude sai kuma ta juyo ta kalleshi.

“Karka sake shigowa nan dan Allah, idan ba haka ba zaka saka ni a matsala”

A nan kam be ce mata komai ba kallonta kawai yake.

“Idan ka ji na yo tafi sai ka fito”

Nan ma be ce komai ba, ita bata jira abun da zai ce ba ta fara lekon waje tana
takawa a hankali kamar wanda zata yi sata, murmushi yayi ya bi bayanta. A hankali
ta fara saukowa stairs tana karewa falon kallo tana duba Dinning sai ta hango Momy
da Namra zaune suna kallonta, juyawa ta yi da sauri sai ta bugu kirjin Captain dake
bayanta ba tare da ta sani ba, kamar a rikice haka ta juyo da sauri ta sauko stairs
din gaba daya, shi ma ya biyo bayanta ya sauko. Ta dago ta kalleshi kadan ganin
hawaye ya taru a idonta ya saka shi juyawa zai taka stairs din ya koma tun da bata
bashi umarnin saukowa ba ya biyo bayanta gashi kuma yanzu zata yi kuka.

“Captain....”

Momy ta kira shi sai ya juyo amman ba Momy ya kalla ba Hurriya yake kallo. Hurriya
ta kalli Momy da sauri hawayena sauko mata ta ce.

“Daman dakin Yaya Namra yake nema sai ya fada dakina”

“Kamar ya Namra nake nema na fada dakinki? Sai ka ce wani kwarto ko dan'iska?
Already sun san zan shiga dakinki ai, yau na dawo na kawo musu tsabarsu na tambaye
ina kike aka ce kina dakinki shi ne na shiga na kai miki taki tsabar dakinki da
kaina, you can't lie”

A take ta fashe masa da kuka domin dai yaja mata fitina a gurin Momy kuma yanzu ya
saka ta yi karya a gabansu.

“Yaya miye haka? Ba kyau me yasa ka bari na yi karya?”

Ta nufi stairs din tana kuka sosai domin bata shiryawa tashin hankalin Momy da
Yayarta Namra ba. Binta yayi da kallo yana jin kamar ya bi bayanta ya rumgume ta
rarrasheta. Momy ta taso daga dinning din da take zaune ta nufo da mamaki karara a
fuskarta.

“Yaya? Na dauka baka son kowa ya kira da wannan sunan?”

Ya juyo ya kalleta.

“Ita ai bata sani ba, shiyasa da ta kirani da Yaya ban hana ta ba”

“Abun da mamaki, yarinya har ta samu damar tambayarka me yasa ka bari ta yi karya?
Tun yaushe wannan abun ya fara?”

“Ni ma ban sani ba Momy kawai tsintar kaina a duniyar”

Ya sauke ajiyar zuciya ya nufi cushion ya zauna.

“To ya zama na karshe daga yau, karka sake shiga sha'anin Hurriya, ba tsaraba ba ko
kallonta bana son ka sake yi?”

“Saboda ita nake yawan zuwa gidan nan Momy? Me ye illar kula Hurriya?”

“Saboda ita din ba ajinka ba ce, bata kai macen da za mu bari ka so ba balle kuma
har ka aura idan ma wannan abun kake tunani to ka farka tun wuri”

Da mamaki yake kallon Momy da ranta a bace har wani cika take tana kallonsa kamar
wani wanda ya aikata abun kunya

“Tana da kyau ai”

“Ba daga hallita ba ne”

Ya rausayar da kai sai kuma ya sake kallonta


“Tana da tarbiya”

“Ba daga tushe ba ne”

“Tana da mutunci da kamun kai, ta san ya kama”

“Ba daga martaba ba ne”

Da kakkausar murya take amsa masa tana jin bacin rai akansa wanda bata taba ji ba.

“To daga minene Momy? Miye illa idan na ce ina son Hurriya”

“Idan babu wanda kake so a Familynmu, ba za'arasa a wajen jininka ba, amman ban da
wanda bata kai matsayinka ba”

“Bana son auren zumunci, shiyasa wata bata taba burgeni daga cikin family mu ba”

Momy ta taka ta isa inda yake zaune ta kai hannunta ta dafa kafadarsa.

“To ka so kowa Captain amman ban da Hurriya, ba zan taba bari hakan ta faru ba, ka
fita tsabgar yarinyar nan idan ba haka ba, wahala kawai zaka ja mata, ni kaina bana
da alaka da ita balle kuma kai, Namra ce kawai zata iya ikirarin wannan amman ba ni
ko kai ba, know your limit....”

Ta juya ta barshi a gurin zaune da mamaki, Namra na ganin Momy ta haye sama ita ma
ta bar dinning din, sai da ta kawo kusa da gurin da Captain yake zaune sannan ya
mike tsaye yana mata kallon takaici ya ce.

“Ke kika cewa Hurriya ni saurayinki ne? Is that what you told Momy? Shiyasa take ta
masifa saboda na nuna ina son Hurriya?”

“Haka Hurriya ta shirya maka? Daman ta saba munafurci ai”

Ya watsa mata harara irin wanda ta dace da ita.

“Ni na shirya, tare da ni take munafurcin”

Fuuuu ya fice daga falon kamar walkiya, Namra ta rufe ido hawaye na sauko mata,
bata taba sanin tana son Captain ba sai a yanzu da ya fitar da abun da ke ransa, na
kudirinsa akan yar'uwarta ba ita ba. A gurin da ya tashi ta zauna ta dafe kanta
tana hawaye kurjin dake mata ruwa wanda Salim ya bar mata sai ya fashe a yau saboda
Captain ma ya juya mata baya....
Yana fitowa falon ya nufi motarsa sai da ya bude motar sannan ya dago ya kalli
windows din dakin Hurriya, sai ko ya hangota tsaye tana hawaye, kuma ita ma shi
take kallo da alama ta dade a gurin tsaye tana jiran fitowarsa. Gambun motar ya
saki ya kama kunnensa da hannu biyu ya rike duk da fuskarsa babu komai sai bacin
rai haka dai yake kokarin ganin ya bata hakuri na fitowar da yayi dazun ba tare da
ta ba shi izini ba, and be fada mata Momy ta san da zuwansa dakin ba ya barta tana
ta wahala. Hannu ta saka ta share hawayenta tana cigaba da kallonsa tana murza
awarwaron da ya bata. Da hannu yayi mata alama da ta yi murmushi shi ma yana
kirkiron murmushin da kallonta ke kwararo masa shi yana wanke masa bacin rai, and
she can't help it but to smile kamar yadda ya bukata, and this is the first time da
take jin wani abu na dabam akan Captain. Daga inda yake tsaye yayi mata thumb up
sannan ya shiga motarsa yayi reverse tana kallonsa har ya fice.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

CAPTAIN POV.

Da hannu daya yake tuki dayan hannunsa kuma yana amsa wayar da Salim yake masa.

“Matsalata da kai naci, tun muna Ethiopia kake damuna da maganar yarinyar nan,
Salim ba zan iya forcing dinta ta soka ba, ya kamata ka hakura tun da har ta nuna
maka bata kaunarka”

“Ba wacan maganar ba ce Captain wannan mai girma ce, ba maganar soyayya bace, and
yanzu na fahimci yarinyar nan bata cancance ni ba, kuma Alhamdulillah da bata yarda
ta amince da soyyayata ba”

Captain yayi dariyar da bata da sauti. Good Boy yanzu ka gane kenan. Ya fada a
ransa a fili kuma sai ya amsa masa da.

“To akan me ne?”

“Abun ba zai fadu ba, na kira Namra ina son ta sada ni da Hurriya na yi magana da
ita bata amsa min wayar ba, kuma ina son naje gidansu ina tunanin kamar ba za a
bari Hurriya ta fito ba”

“Yanzu kana ina?”

“Ina gida”

Captain ya kalli agogon hannunsa.

“Masallaci zan je yanzu, idan mun fito Jumma'at zan kiraka”

“Na so ka zo yanzu Captain wani abu ne da ba shi da kyau gani, ko na zo na same


ka?”

“What so ever it's, sai na fara gabatar da Sallah zan fuskance shi, so ka jirana
idan na fito zamu yi waya”

Be jira abun da Salim zai sake cewa ba ya kashe wayar, ya aje a cikin motar ya
cigaba da tukunsa, a babban Masallacin kan wurin Sarki dake garin Gusau yayi Sallah
Jumma'a sannan ya kira Salim at that Salim yana mosque domin ba masallaci daya suke
sallah ba, and akwai banbancin lokacin sallah Jumma'a a Masallacin Sheik Umar
Kanoma da na kan wuri. A kokarinsa na martaba lokaci ya nufo gidansu Salim din kai
tsaye, a harabar gidan ya shiga ya faka sannan ya aika masa da sako.

“Idan ka gama ina harabar gidanku”

Ya aje wayar ya bude gurin da yake cewa ajiye pistol dinsa ya dauka ya saka a
jikinsa sannan ya dauki counter dinsa dake cikin motar ya laka a yatsansa yana
tannawa, ya san yau ranar jumma'a ce ranar da aka ce a ninka salati ga Annabi
Muhammad S A W, idan kuma baka yi ka yi domin shi salati haske ne a duniya da
kiyama. Ya kusan minti talatin a gurin sannan reply din Salim ya shigo wayarsa.

“On my way”

Ya karanta sakon ya sake maida wayar ya saka aljihu ya cigaba da salatin, yana
kallon harabar gidan iyakarta rabin na su harabar dake Kaduna. Tsaki ya dan ja ya
duba agogon hannunsa, wata zuciyar na ce masa ya kira Salim ya fada masa idan sun
hadu a gurin aiki za su yi magana domin baya son bata lokaci a gurin, kamin ya kira
motar Salim ya shigo harabar gidan ya faka daidai gurin da motar Captain take,
kusan a tare suka bude motocin kowa ya fito, but jin kai irin na Captain ya hana
shi isa gurin Salim sai da Salim din ya karaso gurinsa ya jingina jikin motarsa.

“Minene?”

Captain ya tambaya ganin seriousness a fuskar Salim. Karamar ajiyar zuciya Salim ya
sauke sannan ya fara taba wayarsa dake hannunsa.

“Ina dawowa na tararda wani labari marar dadi a gidan nan”

Captain ya dauke kai.

“Kan da son jan zance, kai ba mace ba balle ace zan bika ina lallabaka, tun a mota
ma ya kamata ka fada min ko minene amman baka yi ba yanzu kuma na zo kana abu kamar
mai rubuta littafi, and you know bana son wannan bata lokaci”

“Akan Hurriya ne, wani abu ta aikata ita da Cousin dina, so abun ya daure min kai
na tura maka hotunan yanzu ta whatsapp ka duba”

“Ba zan duba ba idan ba zaka fada ba zan tafi”

“Tana mu'alama da cousin dina, ina tunanin shi ne reason din da ya hana ta amsar
soyayya ta, and Alhamdulillah na jidadin haka”

Captain ya tsaya cak yana kallonsa with so many questions zuciyarsa ta soma zafi
kamin ta tafasa, idonsa na kokarin sauyawa, the word mu'alama kowa ya ji ya san bad
thing ake nufi kalma ce ba mai kyau ba. Salim ya mika masa wayarsa

“Duba wannan”

Captain ya karbi wayar ya sauke idonsa akan mugun abun da he wish be kalla ba,
hotunan Hurriya ne a sirara tare da mutumen da yake ganin idan ya zo gurin Salim,
wani gurin suna kwance a gado daya, wani gurin kuma ta kwanto jikinsa wani kuma ta
yana kissing dinta ya tallabo kanta da hannunsa dake cikin gashin kanta, na karshen
ne hannunsa yake kan kirjinta and duka hotunan daga ita har shi babu mai tufafi a
jikinsu.

“Wannan ba Hurriya ba ce”

“Ni ma hala na fada da farko domin yadda take da tarbiya da mutumci ba zaka yi
zaton ta aikata ba”

Captain ya dago ya kalleshi naman fuskarsa na rawa cikin wata kalar murya mai fita
da sauti ya ce

“Waya turo maka wannan?”

“Cousin dina ne fa, yanzu haka case din da na zo gida na tarar ana yi kenan, i was
shocked da na ga abu kuma na yi magana da shi ya fada min gaskiyar itace amman be
san ya aka yi hotunan suka fita ba”

Captain ya hade yawun bakinsa sannan ya nuna wayar Salim dake hannunsa da yatsansa
na hadu.

“Ina yaron nan yake Salim? I need to talk to him...”

“Yana ciki bari na kira shi...”

Salim ya nufi main house din da saurinsa shi kansa mamakin abun yake ta wani
bangaren kuma yana gode Allah da be yi soyayya da Hurriya ba. Captain ya juya ya
kife kansa jikin motar zuciyarsa na bugawa da karfi, wani numfashi mai zafi yana
fita a hancinsa da bakinsa, wani irin kuna zuciyarsa take tana isarwa har cikin
kansa. Can kuma ya juyo ya jingina da motar, kamin ya daga ya fara zagaya motar
hannayensa nade a baya rike da wayar ta Salim.

“Hurriya....?”

Ya furta mamakin zayyane a fuskarsa, juyowa yayi ya dawo gurin da Salim ya bar shi
ya tsaya ya rumgume hannayensa yana kallon Salim din da ya fito tare da Adam, kamin
su karaso Captain ya nufi gurinsu suka hadu a tsakiyar gidan.

“Abun da Salim ya nuna yanzu nake son na tambaye ka it's real or fake?”

Adam ya kalli Salim ya sake kallon Captain.

“Wane irin tambaya ne wannan”

Captain ya kawar da fuska yayi murmushi, Salim ya kalli Adam.

“Just answer him”

“It's real”

Captain ya kara matsawa kusa da Adam yana wasa kafafuwansa kamar wanda yayi shekara
a tsaye.

“When how? Where?”

“A inda muka saba haduwa?”

“Da saninta ka dauki hotunan?”

“Aa ba da saninta ba, kuma ban san ya aka yi hotunan suka fita ba”
Captain ya juya baya ya busar da iskar bakinsa ya juyo ya kalleshi.

“Adam idan wani ya saka ka yi wannan abun i cam pay you fiye da abin da aka biyaka”

Adam ya girgiza kai.

“Babu wanda ya biyani, kamar baka san waye ni ba? Wa zai biyani na yi wannan abun?”

Captain ya kalli Salim, Salim ma ya kalleshi kamin ya kalli Adam a karo na biyu.

“Ina kuke haduwa da ita?”

“Tudun wada low-cost”

“Why not gidansu?”

“Saboda iyayenta basa so na”

“Ya aka yi ka san yarinyar nan ina ka santa?”

“Hurriya...? Na hadu da ita a bikin birthday din yayarta Khairy daga lokacin muka
fara soyayya sai kuma iyayenta suka fara nuna basa son alakata da ita, daga lokacin
sai muka yanke gurin haduwa daga nan dai sai shedan ya shiga tsakaninmu”

Captain ya maida dubansa gurin Salim cikin kalar yanayi dake sauya kyau fuskarsa da
raunin idonsa.

“Idan kana son Hurriya bata so ka ba, wannan normal ne an saba haka, amman kokarin
aikata wani abu, martabarta da ta gidansu kake tabawa”

Ya matsa kusa da Salim irin matsawar da yan dambe suke yi idan suka kullace mutum a
zuciya.

“Ba zan bar wannan ba, ba zan kyale kowa da hannu a lamarin nan ba”

“What do you mean? Ni zan saka kanena ya aikata haka? Shi ma an taba martabarsa da
ta gidanmu ko ka gane?”

“I don't care shi namiji ne zai iya haka, ko kai ka saka shi ko kuma yana sonta a
karan kansa zai iya haka? Hurriya ba zata aikata wannan abun ba ba zata yi hakan a
cikin hayyacinta ba”

“Saboda yana wearing innocent face tana nuna ita ta kwarai ce? Baka da wannan
tabbacin Captain, miye alakarka da ita wai da kake ta wannan kokarin”

Captain ya matsa baya ya watse wayar Salim dake hannunsa cikin daga murya da ya
hankalonta da idon kowa a harabar zuwa garesu ya ce.

“Ubanta ne ni Salim.... Haka kake son ji?”

Cikin zafin nama ya riko hannun Adam ya lankwashe hannun hoton da ya gani na
hannuns aa kirjin Hurriya kawai yake ta gani a idonsa har yanzu. Salim yayi
hanzarin rike Captain

“No no no no... Captain..”

Captain ya fisge hannunsa ya rika hannun Adam dake ihu da hannu biyu ya daga
kafarsa ya karya hannun Adam, da mutane suka yo kansu kamin su kawo ya dunkula
hannunsa ya kai a bakin Adam a take ya barar masa da hakora daya jini ya wanke
baki, Salim ya rike Captain da karfi amman hakan be hana Captain shimfidawa Adam
duka a kirjin da ya kwantar da kan Hurriya ba. Mutanen suka rike Adam dake ihu
kamar za a cire masa rai. Salim ya sake shi da karfi ya dawo gabansa ya tsaya

“Captain miye haka? Miye alakarka da ita? Dan me zaka rasa control akan wannan
abun?”

Sai kuma ya juya da sauri ya tare wani yayan Adam din dake son kaiwa Captain duka.

“Aa please matsala ce da za a iya magancewa dan Allah Kabir ka bar wannan abun a
hannu”

“Bar shi ya taba Captain din soja ya jawa kansa bala'i”

Salim ya juyo gurin Captain dake maganar ya kalleshi ganin yana kokarin ballo masa
wasu ruwan ballo masa ruwa a lokacin da yake son toshe wata hanyar, kowa dake gidan
sai yayi ma Captain uzuri saboda suna zaton yayan Hurriya ne, shi kansu abun ya
taba su balle kuma shi da yake da kanwa mace. Captain ya bude motarsa ya shiga ya
bar Salim a tsaye yana bawa Yayan Adam din hakuri domin yau jumma'a wasu yan'uwa
duk ba su dawo daga gurin Sallah ba, masu aikin gidan ne kawai sai wannan yayan
nasa da kuma mahaifiyar Adam din wacce ta fito tana kuka tana fadin ba zata bar
Captain ba.

“Yadda abun ya taba martabar gidansu haka ya tana martaba mu, kuma ai tare suka
hadu suka aikata saboda me zai fadawa dana?”

“Ba kyale maganar za'ayi ba, dole za a bi kadi ai, yanzu dai abun da ya fi a dauki
Adam din a kai shi asibiti”

Su biyu suka kama shi, Salim da yayansa Kabir suka saka shi a motar Salim din suka
nufi asibiti da shi. Suna isa Emergency Salim be tsaya an karbi Adam ba ya bar
Kabir da Adam din a gurin ya juyo da motarsa ya bi bayan Captain ya san ba zai wuce
ya tafi gidansu Hurriya ba.

Kamin Captain ya iso gidansu Hurriya ya kusa balla sitiyarin motar saboda yadda
yake dukansa da mugun karfi yana fisgarsa, gaba daya ya rasa ta ina zai fara
tunani. Yana yin fakin be tsaya kashe motar ba ya bude ya fita ya bar motar a bude,
yadda ya tura kofar falon Momy da a rufe take zai iya ballata. Hurriya dake tsaye a
dinning rike da plate ta juyo cikin tsoro ta kalli kofar falon, domin yadda ya turo
kofar falon ya shigo ya firgitata even though bata san waye ba har sai da ta kalli
kofar. Kai tsaye ya nufeta daman zuwan domin ita ne!

“Waye Adam.....!”

Ta daga kai ta dubeshi gaba daya muryarsa ta cika dodon kunnenta ta cika falon
tsayen da yayi a gabanta kuma ya cika duniyar idonta. Sai tsaya baya da sauri at
that time ne ya fisge plate din hannunta ya bugashi a kasa.

“Waye Adam....!!”

Ta yunkura zata ranta ana kare, ya rikota kamar wata bulala haka ya jujjuyata ya
jefar a gefen kujera ta fadi kasa tana kwala ihu.

“Subhanallahi? Captain Lafiya?”

Amadadin ya amsawa Momy dake saukowa tana tambayarsa tare da Namra sai ya nufi
gurin da Hurriya take kwance ya mikar da ita tsaye ya dauketa mari.

“Waye Adam?”
Ta kai hannu zata taba fuskar ya wanke mata fuska ta dayan gefen sai ta fasa taba
fuskar yawu da jini suka gangaro mata lokaci daya, yadda yake daka mata tsawa gurin
tambayarta da kuma marin da yayi mata a yanzu ya mantar da ita Adam, domin ta dade
ta tattara lamarinsa ta aje a gefe daya tun da dadewa. Momy ta iso da sauri ta rika
Captain ta matsar da shi gefe ta kalli Hurriya.

“Me kika masa?”

Hurriya kallon Momy ta yi ta fashe da kuka domin ba zata iya fadar abun da ta yi
ba, tambayarta yake wanda bata sani ba. At that time ne Captain ya samu damar
runtse ido ya bude ya zauna a kujera ya kasa cewa komai, zuciyarsa na masa wani
irin bala'in zafi.

“Wai me ya faru ne can anyone explain?”

Momy ta tambaya a tsawace tana kallon Captain kamin ta juyo gurin Hurriya.

“Me kika yi?”

Hurriya ta girgiza kai. Captain ya dago daker ta danna wutae da yake ji ya kalli
Momy yana nuna Hurriya.

“Waye saurayin yarinyar nan Momy?”

Momy ta daga kafadunta.

“I don't know, waye saurayinki? Miye matsalarka da saurayinta? What's going on


here?”

“Ba ni da saurayi Wallahi Allah”

Hurriya ta amsa cikin kuka, Captain ya daka mata tsawa.

“Karya kike yi waye Adam?”

Namra dake saukowa stairs ta amsa masa.

“Adam Sarauta? Wanda yayi miki ruwan kudi a birthday Khairy ina tunanin shi yake
nufi”

Captain ya kalli Namra yana kara tabbatar da zancen da Adam din ya fada masa cewar
a birthday yayarta suka hadu.

“Ba sarauyina ba ne....”

Ta amsa cikin kuka bakinta na mata mugun ciwo yana zubar da jini, kana ta kai hannu
ta rike rigar Momy ganin Salim ya shigo cikin falon sai zuciyarta ta raya mata
taruwa za su yi su duketa. Momy ta juyo ta kalli Salim Namra ma da mamaki take
kallom yadda ya shigo falon dake bude babu sallama babu neman izini, hakan kuma
yana karantar da ita akwai abun da yake faruwa.

“Ita ma ka fasa mata baki ko Captain? Wai duk na minene? My mind is telling me son
yarinyar nan kake a boye Captain? Is that the reason da yasa idan na yi maka
maganarta kake fushin dina away? Ba abun kunya ba ne a gareki ka yi soyayya da
yarinyar da ni na fara? You betrayed me Captain....”

Salim ya juya gurin Hurriya dake tsaye ya kalleta.


“Thank you da kika rufe kofafin soyayyarki a gareni, na gode da baki ba ni damar
dandana bakinciki da yanzu ya zame min abun kunya ba, ashe kin san tarayya kike da
cousin dina Adam shiyasa baki karbi soyayya ta ba, tir da ke babu uban da zai so
mace mai two face irinki green snake under green grass, kowa ya san wacece ke
yanzu”

Duk wata kalma da Salim ya fadawa Captain be dago ya kalleshi ba har sai da ya kai
ga taba Hurriya. At that time Captain ya kalleshi sai kuma ya daga kansa sama ya
kyalkyale da dariya ya daga kafarsa sama ya buga a kasa.

“Hahahahaha Salim.. Haba Salim....”

Ya sauke kan ya kalli Salim kamar bakin maciji da ke shirin yin sara. In less than
second Captain ya mike tsaye ya cire bindigar jikinsa ya taka ta isa gurin Salim ta
dora masa bindigar a kasan makoshi ya daga kansa kasa.

“One bad word for her, sai na tashi kanka sai dai ni ma a kashe ni, and you know i
can do it...”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Namra ta dora hannu akai, Momy kuma ta fashe da kuka ta nufi Captain ta rike shi ta
ja shi baya, tsoro take ayi kisan kai a gidanta.

“Ba ni ba kai Jamal daga yau... Kuma duk wani abun da yake da alaka da kai na
datseshi daga yau ba nan nigeria ba har wanda yake Ethiopia...”

“What are you waiting for?”

Captain ya furta a kakkausar muryar as his responsed ga Salim. Salim ya kalli Namra
ya kalli Captain yayi murmushi sannan ya fice daga falon.

“Na rasa gane me yake faruwa? Me kika aikata wai?”

Hurriya na jin tambayar da ta fito daga bakin Momy ta san fadan gurinta zai dawo,
sai ta juya zata bar gurin Captain ya ware kafarsa yaja yayi hanzarin rikota ya
jefar da ita kan kujera.

“Ban aikata komai ba Wallahi ni ban yi soyayya da Adam ba...”

Captain ya ciro wayarsa ya kunna data ta sauke hotunan da Salim ya turo masa ya
jefawa Hurriya wayar. Hurriya ta dauki wayar da sauri ta duba, duban da take da ma
ace idonta ya rufe gaba daya bata ga komai ba, wani tashin hankali da gurbacewar
rayuwa a hango a cikin wayar, idanuwanta suka yi arba da makwafin mutuwarta, da
gaske ita ce din ko mai kama da ita? Adam take gani Adam din da ya zame mata fitina
a rayuwarta, yaushe ta dauki hoto da shi? A ina? Da yaushe? A lailai a yau ta gane
wani garin ya fi gaban kuku, domin kuka ko kadan be kusanto idonta ba hawayen da
yake ma a yanzu sai suka tsaya cak.... Tun tana ganin hotuna daidai har suka koma
mata biyu ta gizon yayi yawa suka rabu gida uku, ta dago kai sai ido ya mamaye
ilahirin idanuwanta bata iya jin sautin komai saboda an dauke jinta a lokacin,
wayar dake hannunta ce ta fara faduwa kasa sannan jikinta ya bi baya, daga Momy har
Namra da Captain suna kallonta har ta jikinta ya kai kasa kanta ya bugu numfashi
yayo halinsa, aka rasa mai riketa. Momy ta karasa ta dauki wayar ta duba

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Shi ne abun da ya fito daga bakinta tana rufe ido, Namra ta karaso gurin da sauri
ta karbi wayar ta duba, bata gama ta tantancewa ba Captain ya karbe wayar a hannun
Namra, ya duka ya kai yatsansa biyu ya taba wuyan Huriyy, sannan ya dago

“I will be very happy idan na samu babu hannun kowa a cikin nan”

Momy ta dauke shi da wani kallo.

“Baka ma yarda ta aikata ba kenan? Kuma idan sheri aka yi mata mu kake zargin mun
aikata mata right?”

“Wutar data halba a zuciyata ba zata bar ni na yarda ta aikata hakan ba, kuma kowa
abun zargi ne a gurina because kowa yana da target dinsa akan Hurriya, and the
innocent soul a saw in her ba zata aikata ba, akwai wanda ya shirya wannan abun..”

“Kuma wani nan kanwar ubanka ce uwa daya uba daya ko?”

Ya dafe kansa.

“Momy please...”

Kamar wanda magana ta karewa a baki haka ya yanke kalamansa ya kasa kara wani
furucin ya fice daga falon.

Momy ta juyo ta kalli Namra cikin tsananin takaici da bacin.

“Wai ni Captain zai zarga?”

Namra ta duka ta taba Hurriya dake kwance a suma kamar gawa tana fadin.

“Kamin mu yi tunanin abun da Captain yayi mu kai yarinyar nan asibiti bata motsi
fa”

“Ke da kika ji zaki iya sai ki yi, ni ko mutuwa ta yi a yanzu Alhamdulillah,


zamanta a nan be kara mjn komai ba sai bakinciki da damuwa, dramer queen”

Momy ta saka kafa ta take ta wuce Hurriya ta haye sama, Namra ta bita da kallo
kamin ta kalli Hurriya hankalinta a tashe. Da gudu ta nufi kitchen ta kunna tap ta
dauki roba ta zubo ruwa ta zo ta zubawa Hurriya ta girgiza ta amman shiru.

“Hurriya Hurriya...”

Ta kara mata ruwan ta sake girgiza ta nan ma shiru, tsoron kar ta mutu a gurin ya
saka ta tashi da gudu ta fice daga bangaren Momy zuwa bangaren Hajiya Kaltume, and
abun mamaki ta isa gurin a daidai lokacin da Khairy take nunawa Ruma hoton Hurriya.

“Ba sai kin fada mana ba, mu ma mun gani video ta is all over the internet...”

“Ba wannan ya kawo ni ba”

Namra ta kawar ma Khairy kai ta nufi stairs tana kiran sunan Yasir domin ta san shi
kadai zai iya taimaka mata a yanzu.

“Ya Yasir ya fita Yaya Namra”

Ta juyo ta sauko da sauri.

“Dan Allah zo ki kama min Hurriya mu kaita asibiti kar ta mutu, faduwa ta yi kuma
bata motsi”

Ruma ta mikawa Khairy wayar da sauri ta bi bayan Namra suka fice a falon cikin
tsananin tashin hankali. Khairy ta bi su da kallo then ta maida idonta kasa tana
kallon wayarta dake hannunta. Contact dinta ta shiga ta yi dialing number Adam sai
kuma ta yi saurin yanke kiran ta fadi zaune kan kujera kamar mai mamaki.

CAPTAIN JAMAL POV.

“Wasu hotuna zan turo maka yanzu, ina son ka yi aiki mai kyau akansu ka gano min
idan editing aka yi, kuma ina son ka bincika a ina aka dauki hoto nan kuma ka gano
ne waya watsa hotunan a media”

“Okay Sir”

Ya sauke wayar daga kunnensa ya shiga Whatsapp ya aika masa da hoton sannan ya goge
su a wayarsa, ya saka wayar aljihu ya nufi gaban teburinsa ya dafa teburin ya
rumtse ido....

Zuuuuuu zuuuuu wayarsa dake aljihunsa ta yi vibration alamar kira, ba tare da ya


bude idon ba ya saka hannunsa aljihun ya ciro wayar, bude idonsa ya kalli wayar shi
ne abu na biyu da yayi sannan ya kara wayar a kunnesa kansa ya mugun tsarawa har
yana jin jiri.

“Salam”

“Captain me ya hada ka da Momy?”

Ita ce tambayar da mahaifiyarsa Hajiya Turai ta fara yi masa a madadin amsa


sallamar da be karasa yi ba. Yana jin haka ya san Momy ta yi magana da mahaifiyarsa
kenan.

“Ammy ba zan iya miki bayani yanzu?”

“Why? And she told me to wannan yarinyar kake so is that right?”

“YES”

Ya amsa da manyan baki, sannan ya mike tsaye gaba daya ya nufi windows din office
din.

“I Love her unconditionally Ammy, ni ma ban sani ba sai yanzu ita ce haske
rayuwata! Amman wani yana kokarin shata layi mai hudu a tsakaninmu, and the most
painful thing is yarinyar tana shan wahala rayuwa, i just..... ”

Yayi shiru, sai Ammy ta karasa masa.

“You just want to marry her and make her a princess? Haka zaka fada min?”

Ya kalli green grass din dake harabar windows din ya girgiza kai.

“Not a princess but a QUEEN....”

“That's back then ban da yanzu, ko a da can idan ita ce ba zan yi farinciki ba, sai
dole, ka tafi ka bawa Momy hakuri kuma ka watsar da lamarin yarinyar nan? Is not
your type”

Ya kai hannunsa ya taba saitin zuciyarsa.


“Har yanzu tana nan cikin zuciyata Ammy, wutar son yarinyar nan sai ruruwa take a
zuciyata little bit confused little bit angry”

Daga can cikin wayar Ammy Ammy ta yi dariyar da ta fi kama da almara.

“Captain ka fara fita hayyacinka ne? Are you crazy?”

Yayi shiru for some seconds.

“Ammy zai fi idan ba mu maganar nan a yanzu ba”

“Why?”

“I'm felling dizzy...”

Ya rike haif curtains din dake jikin windows yana jingina kansa jikin glass
window...

“Where are you?”

Amsar da be samu bata ba kenan ya wayar hannunsa ta fadi kasa, ya rike curtains din
da karfi sosai yana runtse ido ya bude be daina gani dizzy ba, Curtains din cirewa
suka yi suka fado sai dai Captain ya rigasu isa Kasa...!

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/COM8NE7rDs8HAG0Oqfr9wm

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin
daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin
aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of
payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

Da sauri ya rikota tsoro ya cika zuciyarsa na abun da take kokarin aikatawa.

“Hurriya kashe kan ki zaki yi?”

Ta daga masa kai tana kuka.

“Mutuwa ta fi rayuwata a yanzu”

“Rayuwarki tana da amfani mana Hurriya karki kashe kanki”

Yayi saurin kankameta ya saka a kirjinsa.

“Ban Aikata ba Jamal ban aikata Wallahi ban aikata ba, ban aikata ba, ban aikata
ba”

Shi ne abun da take ta maimaita sai ya daga kansa sama yana kallon ruwan da aka
sako ba tare da hadari ba...

“Captain... Captain”

Ya bude idon a hankali har a lokacin dizzy yake gani kamin fuskar Momy ta fito masa
clear, duka hannayensa biyu suna rumgume a kirjinsa dayan mai drip dayan babu.

“Sannu...”

Ya kalli wata yar'uwar mahaifinsa dake tsaye a kansa, a lokacin ne ya gane mafarki
yake na rumgume Hurriya da kokarin hanata aikata kisan kan da take son yi. Maida
idon yayi ya rufe zuciyarsa na wani irin fisga. Momy ta kai hannu ta taba kansa

“Jikin nasa babu zafi kuma”

“To Doctor ya kamata a kira, sun ce idan ya farka a kira su”

Cewar kanwar Momy Hajiya Ikilima, Momy ta mike tsaye tana rike da wayarta dake
ringing.

“Namra ce”

Ta fada sannan ta amsa wayar

“Eh ya farka..”

“Ita ma sai yanzu ta farka”

“To yayi kyau sannu da kokari uwarta, ta farka ba dole sai kin sanar da ni ba”

Captain ya bude idon tun gabanin Momy ta yanke wayar.

“Bari na kira likita”

Momy ta fice da sauri domin kiran Likita, Hajiya Ikilima kuma ta zauna a gurin da
Momy ta tashi tana kallon Captain da ya tsayar da gudun ruwan ya cire drip din
hannunsa ya sauko da kafafuwansa.
“Ina zuwa? Kai da ka tashi yanzu? Hankalin kowa a tashe yake tun jiya baka farka ba
sai yanzu, saboda yana asibitin sojoji ne suka hana kowa shigowa sai ni da Alhaji
Usman suka bari sai kuma Hajiya Nafisa”

Be ce mata komai ba ya sauko daga kan gado sai ta mike tsaye ta rikoshi.

“Ina zaka je wai?”

Be samu amsa mata ba, Hajiya Turai ta turo kofar dakin ta shigo tare da Mijinta
Engr Aliyu Turaki, Ammy ta jefar da jakarta ta rumgume Captain da sauri tana kuka
sosai. Sai a lokacin ya samu kuzarin yin murmushi cikin nauyin baki ya ce

“Ammy I'm fine”

“You're not... Baka taba suma ba tun da na haife ka, kuma ka dauki lokaci baka
farka ba, na tsorata da na rasa ka ban san ya zan yi ba”

Cikin kuka take maganar tun a jiya da ya kasa amsa tambayarta take cikin tashin
hankali har zuwa yau da ta yi zuwan da bata shirya ba, ta dago tana shafa kansa ta
taba jikinsa.

“Me yake damunka? Me kake ji?”

Yayi baya baya ya zauna yana kallon mahaifinsa da ya kasa cewa komai sai damuwa da
tsantsar kulawa ke dawainiya da shi.

“Ya jikinka Jamal?”

“Na ji sauki Daddy, da ba ku zo ba ai Momy ta isa ga Momy Ikilima ma sun wadatar”

“Da ba mu zo ba, hankalinmu ba zai kwanta ba”

Daddy ya fada yana kai hannu ya taba kan Captain cikin tsananin so da kauna. Ammy
ta shafa kansa da fuska tana taba ko'ina na jikinsa hawaye na sauko mata.

“Na yi waya da Dr George na saka Mustapha yayi booking appointment tun a yau, ko da
ka farka ko baka farka ba zan mu fitar da kai England a duba lafiyarka”

“Ammy wannan duka na minenen? I'm”

Ta girgiza kai tana kuka sosai tana shafashi ji take kamar ta bude cikinta ta saka
shi ciki ta rufe, tsoro take kar ta rasa ďa ďaya tilo da Allah ya mallaka mata
iyakar zamanta a duniya.

“You're not sauran kadan ni ma na mutu a jiya, da na kira Momy ka ta zo kuma na


kira abokan aikinka suka shigo suka fada min ka suma, na fi son na tabbatar da
lafiyarka... ”

Yayi murmushi a kokarinsa na karfafawa iyayen nasa guiwa.

“Ba zai wuce stressed ba, kin san yanayin aikin Ammy babu hutu kullum”

“To zaka aje aikin da daga yau...”

Daddy ya fada kai tsaye da fuskar dake nuna ba da wasa yake ba, Captain yayi masa
kallon mamaki.

“Is this a joke?”


“No... I have alot of money, ina da arziki ina da dukiya ina da hannayen jari dabam
dabam, ina da Campany's ba daya ba, ina kasuwancin jiragen ruwa Alhamdullah... Ina
da komai Jamal kai ka zabawa kanka wannan aikin ba dan ka rasa komai ba, kuma ba
dan bana bukatarka a cikin kasuwanci na ba, ina da arzikin da har ka mutu ba zaka
iya cinyewa ba, har jikokinka sai sun gada, fada min akan wane dalili zaka wahalar
da kanka? Idan har wannan tarin duniyar bata hana ka gajiya ba da samun hutu miye
amfaninta?”

Wannan karon dariya yayi mai sauti ya kama hannayen mahaifiyarsa da suke fuskarsa
ya rike yana kallonta.

“Na musu alkawari ina lafiya, kuma zan kara samun wata lafiyar dan Allah ku kwantar
da hankalinku”

Ya rumgume mahaifiyarsa tana kuka har lokacin. Momy Ikilima dake kallonsu gwanin
sha'awa ta ce.

“Dole hankalinsu ya tashi, mu ma hankalin mu ya tashi balle kuma su? Kar ka ga


laifinsu”

Ya kalleta yana murmushi kamin ya kalli Momy wanda ta dawo dakin tare da Likita.

“Hajiya Turai ashe kun iso?”

Ammy ta dago ta kalleta fa jajayen idanuwanta tana share hawaye.

“Eh mun iso Sannu da Kokari Hajiya Nafisa”

“Haba dai? Sai ka ce wata bare?”

Cewar Momy sannan ta nufi gefen gadon tana yi ma Captain ya jiki. Likitan ya duba
shi da kyau sannan yayi masa sannu.

“Rashin hutu ne kawai yake damunsa, akwai bukatar ya samu ya huta kuma ya bi
dokokin maganin da zamu dora shi akai da kuma shawarwari”

“In Shaa Allahu zai bi mun gode Likita”

“Allah ya bada lafiya”

Cewar Likitan sannan ya nufi kofa, Captain ya kira sunansa.

“Dr Rafiq ko zaka taimaka ka ba ni sallama yau? Idan ba haka ba iyayen nawa ba za
su yarda stressed ne ba kawai, kuma ba za su bar ni na huta ba”

Likitan da aka kira da Dr Rafiq ya dawo ya dauki takardun Captain yayi rubutu akai
yana murmushi.

“Zai iya bari asibitin a duk lokacin da ya so”

Sai ya fice daga dakin sannan Ammy ta girgiza kai.

“Ni ban yarda da wannan asibitin ba, ba ayi wani gwaji ba'a duba komai ba kawai ya
ce ya sallameka kuma wai stressed ne, zaka je England a can za a duba lafiyarka da
kyau za su gano ko minene”

“Saboda stressed din ne Ammy ko a can ne haka za su fada, ni kaina na san bana
samun hutu, kuma wannan asibitin da kike gani asibiti ce mai kyau da akw kula da
marar lafiya kamar a waje, asibitin Barrack ce fa, Barrack din ma babba”
“Idan haka ne me yasa ya sallame ka a yanzu? Ko da stressed din ne ai ya kamata ya
rike a nan ka huta ko na kwana uku, ko dai suna son su kashe ka ne?”

“Da na musu me?”

Ya tambaya yana murmushi Momy Ikilima da Momy kuma suka yi dariya, daman sun san
Ammy duk wani abun da ya shafi danta bata daukarsa da sauki bata saka wasa a ciki.

“A gida zan fi samun hutu, yanzu zan tafi na rubuta musu takardar na hada da
shaidar takardun da za su tabbatar da ba ni da lafiya, na saka hannu na aje musu,
Idan suka yi bincike suka tabbatar da gaskiya za su daga min kafa na kwana uku ko
sati ko kuma wata, wata kila ma har shekara ya danganta da abun da likitan ya fada
musu da kuma yanayin ciwon nawa da yadda suka gamsu”

“Dole sai na yi haka? Kuma dole kai zaka yi?”

“Aikin Soja ba kamar sauran aiki bane Ammy, dole na bi dokoki da ka'idodin manya
kamar yadda na kasa da ni ma za su bi ni, zan iya tafi na yi yanzu?”

Permission kawai ya roka daga gurin Ammy sai ta kara masa da tukuici.

“I will escort you”

Duk yadda ya so ta zauna yaje yayi abun da ya kamata da akansa be samu haka ba, sai
da Ammy ta raka danta da kanta har gurin da ya kamata shi kadai ya shiga sai da ya
karya dokar ya shiga tare da ita. After ya dawo abokan aikinsa suka yi ta shigowa
suna masa ya jiki, ciki har da manyansu and da yawansu sun san Engr AA Turaki wato
mahaifinsa ba dan yana aikin sojan ba sai dan connection da kuma kudi mai sa asan
mutum dan dole. Wasu kuma suka shigowa ne saboda Captain jindadin aikin da suke da
shi da kuma kokarinsa. Momy bata bari sun fita a office din ba sai da Captain ya
wanke bakinsa ya yi breakfast sannan suka fito wasu sojojin na take masa baya har
gurin da aka faka manyan motocin gidansu, Daya ta Momy, daya wanda Ammy da Engr
suka shigo sai kuma dayar da bodyguards din mahaifinsa suke ciki, dayar kuma ta
Momy Ikilima ce. Captain ya kalli Mahaifiyarsa ba tare da fargabar komai ya ce.

“Kamin mu wuce Ammy ina son muje mu duba Hurriya asibiti....”

Ammy zata yi magana Engr yayi saurin girgiza mata kai alamar kar ta hana, sai kuma
ya tari numfashin mahaifiyarsa ya amsa masa.

“Okay zamu fara zuwa mu dubata tukuna sai mu tafi gida ko Family House?”

“Family House”

“Okay My Son”

Direban ya bude masa mota ya shiga baya, tare da iyayensa Ammy da Engr, wani Knight
ya shiga Front seat, Hajiya Nafisa wato Momy da Momy Ikilima ma a dole suka bi
Captain da iyayensa dake kokarin cika masa kudirinsa. A harabar Federal Medical
Center wato FMC suka faka, security dake gaban motar Engr ya bude motar da sauri
Captain ya fito tare da iyayensa, Bodyguards na take musu baya. Ko kadan Momy bata
so zuwa duba Hurriya a asibiti ba, ba dan Captain ya so haka ba kuma iyayensa suka
biye masa ba zata taba zuwa dubata ba, domin ta fi jin tsanar Hurriya a yanzu fiye
da koyaushe, sanadinta suka fara samun da Captain gashi kuma yanzu ta ja musu abun
kunya, sai dai babu yadda ta iya saboda ďan ďan'uwanta ya so haka. A dokar asibitin
lokacin da suka zo ba lokacin ganin marar lafiya ba ne, amman ba a hana su shiga ba
domin ko na goye ya san kura.
“Ina ne?”

Captain ya tambayi Momy ba dan ita ma ta sani ba, sai da ta sauke ajiyar zuciya ta
kalli yayanta sannan ta daga wayarta ta kira Namra.

“Gamu mun shigo asibitin, wane daki ne?”

Ta fada musu har da number dakin, a nan suka juya zuwa wani ward din da ba wannan
ba, ko'ina suka wulga sai ya kallesu kana ganinsu ka san ba kananan mutane ba ne. A
lokacin da suka isa dakin da Hurriya take sai Captain ya kalli iyayensa ya ce.

“Wata kila ba zata so ta gan mu tare da ku ba, zan fi jindadi idan na shiga ni
kadai, na san idan na ce ku zauna a mota na shigo ni kadai ba za su yarda ba
shiyasa ban yi magana ba”

A nan kam Momy kasa hadeye maganar ta yi cikin bacin rai ta ce.

“Mu iyayenka mu zamu jiraka har sai ka shiga duba wata banzar yarinya tukuna mu
tafi? Sai kace kai ka haife mu?”

“Idan hakan zai faranta ransa me ye a ciki? Shiga ka yi abun da zaka yi son zamu
jiraka a mota”

Daddy ya fada sannan ya kalli bodyguard dinsa daya.

“Ka tsaya a nan idan ya fito ku same mu a mota”

“Okay Sir”

Daddy ya juya tare da Ammy domin komawa gurin motarsu, Momy ma dole ta bi bayansu
iyayen yaro sun goyi bayansa ita a su ta ki bi, a nan ta samu damar karanta musu
kabli da ba'adi na Hurriya, tana ta kusheta. Sai da suka wuce sannan Captain ya
murda kofar dakin ya tura ya shiga, tana zaune saman gadon ta lankwashe kafafuwanta
tana fuskarta hadu da kofar dakin.

“Kai kuma kai ne wa?”

Gwaggo ta tambaya tana kallonsa. Sai a lokacin ya tuna be yi sallama ba. Dan haka
ya jadada sallamarsa sannan ya karasa cikin dakin yana gabatar da kansa.

“Sunana Jamal amman an fi sanina da Captain ni dan Momy dan yayanta...”

“Toh ko me ya sa ka zo?”

Ya kalli Hurriya da babu gilashi a idonta hawaye na zubo mata ya ce.

“Na zo na duba Hurriya ne? Namra ta fada mana tana nan”

“Namra ta tafi gida tun dazu, kuma dan Allah ba ma bukatar kowa, daga dangin Nafisa
har na Kaltume, wannan kiyayyar ta yi yawa, ba bar uwa ba a bar ya ba, babu kalar
azabar da ba a nunawa yarinyar nan ba yanzu abun ya wuce nan har sai a hada da
kazafi? Kazafin ma na zina? Ita da gidan ubanta amman bata da walwala? Bata da
jindadi? Akan me? Yanzu gashi nan kun yi sanadi idanuwan nata sun rufe gaba daya,
bata iya gani ko da gilashin, buri ya cika tun safe da ta farka bata cewa komai ba,
an kashe yarinya tana ji tana gani”

Gwaggo ta karashe fadan da kuka, Captain ya sauke idonsa kasa hawaye suka zubo
masa.
“Ina kyautata zaton ni ne mutum na farko da ban yarda Hurriya ta aikata wannan abun
ba, ban zo nan domin cin mutumcinta ba, ita ma ta sani kawai dai na kasa natsuwa ne
har sai na zo na dubata, ban san matsayinki a gurinta ba, amman dan Allah ina rokon
Alfarmar ki bar ni na ga Hurriya”

“Gata nan ka ganta, amman ba zan je ko'ina ba, kai ma ba zaka dauki hotonta ka
yadawa duniya ka bata mata suna ba, kuma ko waye da hannu a lamarin kada Allah ya
bar shi da salama, daga yaron har kowa”

“Ameen”

Ta saka yatsansa ya cire hawayen sannan ya karasa gaban gadon Hurriya saitin inda
take zaune ya tsaya yana kallon fuskarta. Hawaye take malalarwar irin malalar da
gulbi yake idan ya kawo, babu yankewa kuma babu fasa zuba, yanayin yadda take
kallon saitin da yake tsaye ya isa ya kara tabbatar masa da bata iya tantance fari
da ja a yanzu, sai bakin da ya rufe ganin idanuwanta.

“Hurriya...”

Bata amsa ba, motsa ba bata bar masa wata alama da zai gane tana jin muryarsa,
ibadarta kawai take ta kuka. Cikin kuka Gwaggo ta ce

“Bata cewa komai, kuma bata gani”

Captain ya hadeye yawu mai matukar ďaci fa maƙaƙi a maƙoshi.

“Likita ne ya ce bata gani ko kuma ke kika ga alamar bata ganin?”

“Na ga alama, sa safe da ta tashi zata shiga bandaki ga gilashi a idonta amman
lalabe take, na fada Likitan da ya shigo suka duba idon suka ce ua samu matsala,
shiyasa suka canja mana daki ai, yanzu ba maganar sumanta ake ba, maganar idonta
ake Likita biyu ya duba idon zamanmu a nan sun ce sai an yi aiki wai jijiyar dake
hada idonta da kwakwalwarta ta samu matsala”

Captain ya daga kansa sama kamar zai fashe da kuka.

“Ya Rahma....”

Ya ambacin mafi rahamar masu tausayi, sannan ya sauke kai ya kalleta pointing
finger dinsa ya kai saitin idonta kamar zai tsokale ido amman bata matsa ba, a nan
ya tabbatar da bata gani da gaske.

“Jiya kin zo min a suma, kin fada min baki aikata ba, kuma na yarda da ke. Yau kuma
ina tsaye a gabanki ne domin na fada miki wani abu, kowaye ya aikata miki wannan
abun Hurriya, ba zai sake samun farinciki ba a rayuwarsa, sai ya kunyata fiye da
yadda ya so ya kunyata ki, sai na sa duniya ta tsine masa irin tsinuwar da zai ce
ina ma be aikata ba”

Ya kama hannunta ya rike a gaban Gwaggo.

“Na miki wannan alkawarin Hurriya, kamar yadda na yi miki alkawarin dawo miki da
dan'uwanki, shi ma wannan ki rubuta ki aje nauyin yana kai na....”

Gwaggo ta share hawayenta ta taso daga inda take zaune da sauri tana fadin.

“Kai kai kai sake mata hannu, ban san sharin da ka zo da shi ba kai ma”

Captain ya sake mata hannun ya nufi kofa yana share hawaye, be ma kula maganar
Gwaggo ta halin da ya ga Hurriya da damuwar da yayi arba da ita a fuskarta ta tafi
da tunaninsa. Gwaggo ta kama hannun Hurriya ta shafe mata da hijabinta.

“Babu abokin yarda a cikinsu, ni da na san haka rayuwa zata miki Hurriya da ban
bari kin zauna a gurin Ubanki ba, ko da kuwa shari'a ce zan yi da shi...”

Wani irin numfashi Hurriya ta fara fitarwa da karfi, kamin ta daga kanta sama ta
kwala wani uban ihu....

“Gwaggo ban aikata ba....!”

Gwaggo ta rumgume ta da sauri tana kuka.

“Wallahi ban aikata ba....!”

“Na sani, babu wanda ya yarda kin aikata daga ni har Rukayya”

“Allah ka hana, wanda ya aikata min wannan abun farinciki, Allah ka hana shi
jindadi da kwanciyar hankali, Allah ka nisanta shi da natsuwa ka kusantar da shi ga
kunya da damuwa, fiye da yadda yayi min”

Cikin tsananin kuka Hurriya ta yi ma kanta addu'a tana fatar mahallincinta ya amsa
mata.

“Ameen Hurriya Ameen”

Gwaggo na amsawa Hajiya Binta ta turo kofar dakinta ta shigo da sallama. Hurriya na
jin muryarta ta juyo ta kai hannu tana lalaben inda take.

“Hajiya komai ya kare min, idanuwa sun tafi, mutuncina ya zube... Na barar da kimar
Appa da Ammana a idon duniya, komai ya kare yanzu babu abun da ya rage min, kullum
bakinciki ne yake kusanto ni yana nisanta ni da farinciki....”

“Share hawayenki yarinyar, farincikinki mai kyau shiyasa yake da tsada, duk mai
hassadarki yana son ganin bayanki sai ya dawo karkashinki, wannan alkawalin Allah
ne mai hakuri yana tare da riba Allah da kansa ya ce dukannin tsananin sauki yana
nan damansa, idanuwanki za su bude Hurriya, damuwa zata yaye farinciki sai ki samma
wani, karki damu da hotunanki sun shiga duniya, ko karuwanci zaki yi, ki je ki yi
ki dawo Hurriya ni FATIMA BINTA zan karbe ki... ”

Hajiya Binta ta fada tana dukan kirjinta da karfi, kana ganinta kasan tana cikin
bacin rai...
If you read my book ba tare da kin biya ba, indai hakkina ne Wallahi ban yafe ba,
ku kuma masu sharing Allah ya muku yadda kuke min. I rest my case 🙌

CAPTAIN POV.

Ko da suka isa Family House dinsu, gidan yana cike da mutane, abun ka dake mai
jama'a, daman sun tun a lokacin da yake asibitin suka tafi ganinsa aka hana su
shiga. Kowa sai murna ganin Captain yake kamar wani Sarki, domin kowa a familynsu
yana son Captain ko dan duniyar Ubansa da Hajiya Turai. Duba daya zaka yi ma
Captain ka fahimci baya cikin farinciki ko kadan, ya zama so silent daga lokacin da
ya baro asibitin da Hurriya take zuwa motar har kawowa gidansu. Wani abun da ya
bawa Ammy da Engr AA Turaki mamaki shi ne takardar sammacin kotu da suka tarar an
kawo a gidan. Engr ya karanta takardar ya sake karantawa ya dago ya kalli
yan'uwansa dake cike da katon falo na Mahaifinsa.

“Waya kawo takardar?”


“Ma'aikacin kotu?”

Wata kanwarsu dake zawarci a gidan ta amsa masa. Momy ta tabe baki.

“Daman na raya a raina na ce sai abun nan yayi tsananina, karya yaron mutane fa
Captain yayi kuma ya fasa masa hakora!”

Ammy ya kashe ido.

“Ashe kariya ce ma kawai shi nw za a kai ďana asibiti? Ko kashe shi Captain yayi ba
zan bari ya tafi kotu ba balle kuma karaya kawai da zubar da hakora”

Engr ya sauke ajiyar zuciya cikin takaici ya ce

“Anya Bashir Sarauta ya san Jamal ďana ne kuwa? Har zai yanko sammacin kotu ya aiko
a gidan nan? Kuma ďana yake kara? Ni Bashir Sarauta zai saka ďana kotu? Bashir
Sarauta talaka a cikin masu kudi? Bashir Sarauta da yake karkashin inuwar
dukiyata...! Ai wani sarkin kakan wani sarkin ne... Amman ya ba ni mamaki, ni ma
kuma zan ba shi mamaki”

Momy ta ce.

“Ai duk Hurriya ce sanadi, gashi masu arziki za su yi fada akanta, yarinyar da bata
kai ba”

Captain ya kalleta kamar daman jiran yake tace wani abu a kan Hurriya.

“That's it, Hurriya this Hurriya that... Komai Hurriya kike blaming, yarinyar da
bata isa ta daga idonki ta kalleki a matsayin uwa ba, yarinyar da bata isa ta shiga
dakinki ta rokeki wani gata ba, yarinyar da bata isa ta shiga Kitchen dinki ta zuba
abinci ta ci ba, yarinya kamara kun matsa mata kun firgita mata kwakwalwa, yanzu ga
wata bakin hayakin ya rufe ta amman still baki ji tausayinta ba?”

Ammy ta kalleshi tana kai hannu ta taba shi kuma ta kwantar masa da zuciyar dake
fisgar ďanta.

“Captain you can't talk to Momy this way... Haba.. ”

Cikin lalama take fada tana dan kallo Momy. Captain ya kalli Ammy.

“Kiyayyarta da yarinyar nan wani abun ne da ya shafe ta na dabam, babu ruwana a


ciki ni dai abun da na sani babu abin da zai hana ni auren Hurriya...”

“God forbid...”

Ammy ta dauke hannunta daga jikinsa da sauri kamar ta taba mugun abu.

“Yarinyar da duniya ta gama ganin tairaicinta? Yarinyar da bata da kamun kai?


Karuwa? Kuma makauniya? Ba zan karbe ta a matsayin suruka ba har abada”

“Enough....!”

Daddy ya daka mata tsawa, sannan ya kalli Captain ya ce.

“Tashi ka shiga ciki ka huta”

Captain ya mike tsaye ya kalli mahaifiyarsa hawaye na zubo masa.

“A halin yanzu, Wallahi duk duniya Ammy ke kadai kika kai ki kira Hurriya da
karuwa, na hade ban ce komai ba, kuma ban dauki mataki ba... Ki gafarce ni Ammy ni
dai kam ban taba jin tsananin son wata mace a zuciyata ba kamar yadda nake jin
Hurriya a yau, i love her more than life....”

Kowa kallon Captain yake domin yau yayi abun da be taba ba, fadar yana son wata a
gaban kowa, kuma har ya zubar da hawaye.

“Ko Aljana ka ce zaka aura Jamal zan aura maka ita matukar hakan ne farincikinka,
kuma zan raba ka da wanda baka so matukar hakan zai dada ranka... Ka bar wannan
maganar a hannuna tafi ka huta....”

Cewar Daddy yana nuna masa hanyar bedrooms din dake stairs... Captain ya nufi
bedrooms din yana jin kamar za'a raba kirjinsa gida biyu, Hurriya ce aka watsa
hotunanta amman shi da ita ne suke raba nauyin bakincikin.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Yana shiga dakin ya nufi wata kujera ya dafa kanta ya sauke kansa kasa ya rufe ido.
Kamar an tsikare shi ya bude idonsa ya juyo da sauri ya fito daga dakin, tafiya
yake mai kama da gudu ya sauko stairs din.

“Ina wayata?”

Ya tambayi Ammynsa sai Momy ta bude jakarta ta dauko ta mika masa tana hawaye. Ya
saka hannu biyu ya karba ya juya ya koma ciki.

“Yaya da gaske barinsa zaka yi ya auri yarinyar nan? Wallahi bata kai ba Yaya bata
yi matsayin da zata zama surukar mu ba”

“Idan aurenta ne abun da Captain yake so, zamu nemi aurenta kuma iyayenta za su ba
mu ita dan dole ko da bata so, Allah ba hallatawa iyayen autawa Yayansu wanda basa
so ba, ya dai mata ikon zaba musu na gari, kamar yadda ya hallata auren mazina idan
sun tuba”

Ammy ta dubi Engr

“Ni fa ban gane ba, da gaske zaka aura masa yarinyar nan kenan? Ni ba da yawun
bakina ba ba zan yarda Captain ya zauna da wannan yarinyar ba, ai abun kunya ne ace
wannan yarinyar ta zama surukar mu duk matan duniya a rasa wanda zai aura sai
karuwa?”
“Ina tunanin kin fi ni son farinciki Captain...”

Ta kawar da fuskarta ta fashe da kuka.

“Wannan goyon bayan da zaka ba shi be yi ba Yaya, be kamata ka biye masa ba shi fa
soyayya ce take dibansa lokacin da zata zubar da shi zai fada a mugun guri ne”

Wata kanwarsa ta fada. Engr ya mike tsaye rike da takardar sammacin ya ce.

“Idan har kuna ganin akwai rashin dacewa a auren yarinya to ku roki Allah ya sauya
masa da wanda ta dace, kuma ki kwantar masa da hankali ku nuna masa illar hakan,
idan ya sauya ra'ayinsa Falillahil-hamdu ”

Ya nufi kofar fita ya fice daga falon yana kiran wani Assistant manager. Sai da ya
fita sannan Momy ta dubi Hajiya Turai ta ce.

“Karki yarda Wallahi ta ya za'a kawo miki wannan yarinyar a matsayin suruka? Taya?
Ai da kunya ma”

“Wani gine ne Captain yake son na dora wanda ba zai iya karasa ba, ni dai kam ba
zan taba karbar yarinyar nan a matsayin suruka ba”

Ammy ta fada tana share hawayenta. Wata step Mother din Engr ta dubi Momy ta ce.

“Kuma da gaske yarinyar nan ta aikata abun nan?”

“Ba mu da tabbaci, ko da ace ba da gaske ba ne, ai be kamata ya aureta ba Hajiya,


saboda duniya ta gama ganinta”

“Idan shari aka yi mata bana ganin illar aurenta a gurin Jamal, illar kawai ace ta
aikata ne, shi ma kuma idan ta tuba Allah zai karbi tubanta kuma yayi mata sakamako
mai kyau, domin Allah yana son bayinsa masu komawa a gurinsa suna kuka suna rokon
ya yafe musu, shin idan hakan ya faru da yarki zaki so wani ya juya mata baya? Ku
yi tunani mana”

“Ko ma dai minene Hajiya ba zamu yarda Captain ya auri yarinyar nan ba”

Momy ta amsa mata kai a ranta tana cewa saboda ba jikanta ba ne take fadar haka.
Safa da marwa yake waya a kunnesa yana jiran wanda ya aikawa kiran ya amsa.

“Nafi'u ka duba hotunan kuwa?”

Ya gabatar masa da abun da yafi daukin ji fiye da gaisuwarsa da sallama.

“Sir barka da yamma, eh na duba”

“Ya ake ciki? Editing ne i know”

“I'm sorry Sir gaskiya ba editing ba ne, na duba na yi bincike ni da entire team
dina ba mu ga wata alama dake muna editing ba ne”

Captain ya kai hannu ya shafa kansa ya runtse ido sosai.

“Maybe baka iya aikinka ba, maybe baka duba inda ya kamata ka duba ba”

“Na iya aikina ranka ya dade kai ma ka sani, wata kila da wannan gaskiyar mai nauyi
ce shiyasa ka kasa karbarta, amman na gano wani abu”
Ya bude idon da sauri ya nufi bathroom ya bude ya shiga ba dan ya boyewa wani ba
sai dan rudewa da yayi jin abun da yake nema zai samu.

“Alamu ya nuna yarinyar nan bata cikin hayyacinta aka yi hotunan, ko kuma tana
cikin bachi mai nauyi domin jikinta ya saki sosai, yadda yake rikota da ace a
hayyacinta take ba ta yi yaukin jiki haka ba, kuma babu inda take shauki ko
murmushi shi ne kawai yake yi, shi ma kuma akwai alamar tsoro a tare da shi ko kuma
rashin kwanciyar hankali, yadda hannayensa ma suke a jikinta ya nuna shi yake rike
da ita”

Captain ya zauna a jikin bathtub yana murmushi.

“Thank You, Thank You... Ka gano wanda ya dora hotunan?”

“Shi ne ban gano ba, na yi bincike na biyeye abubuwan da suka kamata ban gane komai
ba, amman na bibiye wandanda na ga hotunan a account dinsu na Facebook wasu
unverified pages ne masu neman labari wasu kuma daidaikun mutane ne, sai da na
bibiye wanda aka fi sharing hotunan da ya rufe wasu bangarora na jikinta sai na
samu wani dan jarida ne a Kano, and na dauki wayarsa na fada masa daga ina nake
kiransa kuma na tambaye shi a ina ya samu hotunan sai ya ce min a wani account ne,
ya fara gani, dayan kuma a bauchi yake shi kuma yace min turo masa hotunan aka yi,
na bukaci ya fada min account din da na bincika sai na samu an goge account din”

“Kana aje wayar nan, ka duba list din mutanen da suka dora hotunan karka damu da
yawansu ka turo min su, tare da sunanyen gidanjen jaridun, ka hado min da account
number dinka”

“Okay Sir”

Ya sauke wayar.

“Za su san sun taba mai gata, na miki alkawarin farinciki Hurriya zan cika miki
shi... ”

Ya fada sannan ya nufi madubin dake bandaki ya dora wayar ya cire tufafinsa ya
sakarwa kansa shower. Ya bata minti arba'in a bandakin sannan ya fito yana rike da
wayarsa jikinsa kuma na daure da tawul.

“Good Nafi'u”

Yayi forwarding sakon zuwa mabanbanta gurare sannan yayi waya da mutane daban
daban. At the end ya kira Namra.

“Hello Captain”

“Wace asibiti aka kai Adam? Kanen Salim”

“Ban sani ba, ya jikanka?”

“Bincika min yanzu”

“Toh”

Ya aje wayar ya dauki wani tawul din ya goge jikinsa, sannan ya zauna gaban madubi
yana hararo abubuwa da yawa. After like one hour yana zaune kan carpet bayan ya
sallame sallah wani kiran ya shigo a wayarsa bayan na calls din dake ta shigo masa
na yan'uwa da abokan aiki masu son tambayar jikinsa. Amman be amsa kiran kowa ba
sai na Namra.
“Yana yana asibitin Yariman Bakura, layin ya hadurra”

“Good”

Ya yanke kiranta tun kamin ta kara cewa komai, ya shiga whatsapp dinsa ya sake
sauke hotunan da Salim ya turo masa, ya yanke iya gurin da fuskar Adam take ya
turawa wata number tare da address, sannan ya fito whatsapp din ya shiga contact
dinsa ya nemo number the same person da ya turawa sakon ta whatsapp.

“Hello Sir”

“Uzairu na turo maka hoto da addreshin wani dan'iskan yaro yanzu a whatsapp, ni ya
taba so the fight is between me and him.. Ka duba address din ka dauki mutanenka ki
shiga cikin asibiti ku dauko shi ku aje min shi wani gurin da babu haske kuma babu
rahma, ku masa doka irin dukan da idan na masa tambaya zai ba ni amsa a take amman
ban ce ku kashe shi ba, ku aje shi a gurin for 10 hours”

“Yes Sir... ”

Ya sauke wayar, sannan ya amsa dayan kiran daya fito daga bachi.

“Yeah good so nake ku kama mai gidan jaridar ku bincike shi a ina ya samu hotunan,
at the end ku sa ya rubuta cewar sheri aka yi mata kuma yana neman yafiyar Hurriya,
ku saka yayi hakan tun a cikin office din ku idan be yi haka ba ku karya kafarsa”

“Amman Captain me yayi maka?”

“Yarinyar da suka batawa suna yarinya ce mai tsada she is innocent, please karku
ragawa kowa a gurin”

“Subhanallahi, aiko za su ga aikin DSS”

“Thank You My friend”

Ya sauke wayar ya amsa wata wayar, haka yayi ta bata umarni a inda umarninsa suke
jira a inda alfarma yake nema sai ya roki ayi masa haka.

HURRIYA POV.

“Daure ki sha tea ne kuma ba mai yawa ba”

Hajiya Binta na lalabata tana hada mata tea. Gwaggo ta ce.

“Babu yadda ban yi da ita ba amman ta ki cin komai tun safe har yanzu”

“Bana iya cin komai ne, ko na ci bana iya hadewa”

“Hurriya wannan abun duk zai wuce, wata kila an buga an buga an ga babu sa'a ne shi
ne aka bullo ta nan, amman duk wanda ya sanki ya san ba zaki aikata ba, babu wanda
zai yarda kawai ana son a jefaki a damuwa ne, dan haka karki bari damuwar da suke
son jefaki ta tasirantu akanki karbi ki sha”

Ta mika hannu tana lalaben kofin ta karba ta kai bakinta ta kurba kadan sai ta
gagara hadewa.

“Hajiya bana iya hadewa”


Hajiya ta karbi kofin ta rike tana kallon jikarta cike da damuwa sosai a fuskarta.

“Jibi zan wuce Ummara zan miki addu'a mai karfi a can, da yardar Allah wanda ya
aikata miki haka ba zai sake sanin rahma a rayuwarsa ba”

“Amin Hajiya”

Gwaggo ta amsa, sannan suka daga kai gaban dayansu suka kalli kofar dakin da aka
turo. Cikin wani irin yanayi kamar na kunya kamar tsoro Yasir ya shigo dakin
fuskarsa a raunane.

“Yasir”

“Na'am Hajiya”

Hurriya ta sauke kanta kasa duk da kasancewar bata ganin kowa tana jin kunyar aga
fuskarta saboda an yada tsiraicinta. Yasir ya tsaya daga tsaye suka gaisa da Hajiya
da Gwaggo be ce da Hurriya komai ba ita ma bata iya dagowa ba balle tace masa wani
ba sai hawaye take.

“Appa ya ce na zo da Hurriya”

“Ka zo da ita kuma? Be san tana asibiti ba?”

“Ya sani, yace na yi magana da likitan ya bata sallama”

“Saboda me? Be san idonta ya samu matsala ba?”

“Ya sani Namra ta fada mana komai, Hajiya idan za ayi mata aikin idon a ba nan
za'ayi ba kuma abu ne da yake bukatar shiri da tantance inda ya kamata da kuma
likitan da ya dace”

Hajiya zata sake magana Gwaggo ta dakatar da ita

“Je ka karbo sallamar, zamu tafi da ita mu ga iya gudun ruwansa amman ba zan bar
Hurriya ta zauna a gidan nan ba har bada...!”

Yasir ya juya ya fita daga dakin ba tare da yace komai ba, Hajiya Binta kuma ta hau
masifa ta daga wayarta ta kira shi kiran be shiga ba. Misalin karfe biyar da
mintuna Yasir ya faka a harabar Appa, Gwaggo ta fara fita sannan ta fito da Hurriya
Hajiya Binta ma ta fito tana kara shiryawa duk wani abu da ďanta zai yi. Hurriya ta
kama hannun Gwaggo ta rike da karfi.

“Gwaggo tsoro yake kar Appa yace be yafe min ba”

“Ko da ya fada ba zai kama ki ba, domin ba ki aikata ba kuma Allah mai adalci ne”

Cikin karayar zuciya da duhun idanuwa Hurriya ya shiga bangaren na Appa Gwaggo tana
mata jagora komai bata iya banbance komai a yanzu. Yanayin yadda ta ji numfashi na
tashi ya karantar da ita falon cike da mutane da bata san su waye ba, yan gidansu
ne kadai ko kuma dai duka familynsu da suke garin. Me Appa zai fada akanta shi ne
abun da ya fi tsorata ta, da lalabe ta zauna a falon kusa da Gwaggo, hawaye na mata
zuba, ta wani bangaren tana gode Allah da bata iya ganin komai, a yanzu da bata san
da wane ido zata kalli Appanta ba.

“Hurriya...!!!”

Gabanta ta kasa amsa kiran da Appa yayi mata gabanta sai bugawa yake da karfi.
“Kina da wata hujja ta kare kanki akan abun da muka gani tsakanin jiya zuwa yau?”

Ta yi shiru, Gwaggo ta ce.

“Ka san dai ba zata aikata ba...”

“Gwaggo dan Allah ki yi hakuri ki bari ta amsa min”

Appa ya bukata cikin yanayi da ke nuna shi ma yana cikin damuwa kwatankwacin wanda
Hurriya take ciki.

“Appa akai ni na yi alwala”

Tana fada ta mike tsaye tana kuka.

“Ba sai kin rantse ba abun da duk ba halinki ba ba zaki aikata shi ba”

Hurriya ta girgiza ma Hajiya Binta kai ba dan tana ganinta ba.

“Idan ban rantse ba babu wanda zai yarda da ni, ni ma kuma ba zan samu sukuni ba,
dan Allah ku kai ni bandaki”

Yasir ya kalli Ruma.

“Tashi ki kaita”

Ruma ta tashi ta rika hannunta suka shiga bandakin dake cikin falon, Hurriya ta yi
alwala ta fito ta bukaci a bata kur'ane.

“Bari zaka yi ta yi rantsuwar nan Tsoho?”

Appa ya kasa amsawa mahaifiyarsa, shi ma ji yake kamar Hurriya ba zai aikata hakan
ba sai dai zuciyarsa ta kasa natsuwa. Yasir ya tashi da shiga bandakin da Hurriya
ta fito yayi alwala ya shiga bedroom din Appa ya dauko mata alkur'ane ya kama hannu
ya mika mata, shi kansa idan ta rantse zai fi jin natsuwa, domin ya shirya ui mata
mummunan hukuncin idan har ta tabbata ta aikata. Hurriya ta rike qur'anen da dayan
hannunta sai ta dora hannunta na dama a saman kur'ane ta dafa.

“Na rantse da littafin nan, abun da yake cikinsa da wanda ya aiko da shi ban aikata
ba Appa”

Ta karasa cikin kuka... Gwaggo ta saka kalma shahada.

“La'ilaha Illaha Muhammad Rasulullah”

Sai gaba daya falon ya amsa suka karasa a tare.

“Sallalahu Alaihi Wassalam...”

Appa ma ya sauke kansa kasa ya fashe da kuka, babu wanda be yi hawaye ba a falon
kuma babu wanda be tausaya mata ba ciki har da Momy. Yasir ya sa hannu ya karba
yana hawaye da murmushi a fuskarsa, yar'uwarsa ta tsarkake kanta a gaban kowa hakan
ya kwantar masa da hankali yanzu kam ya yarda hundred percent bata aikata ba.. Appa
ya dago hawaye na zubowa daga idonsa ya mika mata kamar ance masa tana ganinsa.

“Zo nan gareni yata, fada min wa kika tarewa farinciki ya aikata miki haka?”

Hurriya ta fara takawa ta inda take jiyo sautin muryarsa tana kuka tana lalaben
hanya, Yasir ya rika hannunta ya karasa ta ita gurin Appa, hannayensa ta fara
kamawa sannan ta zube kasa a gabansa ta kwantar da kanta a kafarsa.

“Allah ya tsinewa wanda ya aikata miki wannan abun Hurriya, ba zai gama lafiya ba,
bakinciki da ya saka mana da neman bata miki da sunan gidan nan Allah ya ninka masa
shi...”

Kowa ya amsa da Ameen ban da Khairy da Namra dake ta kuka kai ka rantse da Allah su
aka aikatawa haka ba Hurriya ba.

“Ba zan bar maganar nan ba, sai na yi shari'a da yaron nan, ya ci mutuncina ya ci
mutuncin ƴata ba zan kyale shi ba”

“Ni ma na yi wannan tunanin Appa, na kudirta a raina idan har ta tabbata Hurriya
bata aikata abun nan ba, ba zan kyale maganar nan ba”

Yasir na aje aya Hajiya Binta ta ce.

“Da kun kyauta daman be kamata a kyale ba”

Momy ta tashi ta fice ba tare da tace komai ba, Ruma ta bi bayanta. Gwaggo ma ta
mike tsaye fuska a daure ta ce.

“Zan tafi gida, kuma zan tafi tare da Hurriya saboda a can zata samu kulawa”

Appa be ce komai ba bayan shafa kan Hurriya da yake, har Gwaggo ta iso gurin ta
kama hannunta suka fice. Sai da suka kusa isa gate sannan Yasir ya cin musu da mota
ya bukaci su shigo ciki ya sauke su gida, Gwaggo kamar bata shiga ba saboda yana
dan Hajiya Kaltume sai kuma ya daure ta shiga saboda saukaka Hurriya wahalar fita
titi zuwa neman abun hawa. Back seat suka shiga ita da Hurriya har suka isa Yasir
be yi wata magana ba, balle kuma Gwaggo da ta matsu su sauka a motarsa. Har cikin
gidan ya faka ya fito ya budewa Gwaggo ta fito ita kuma ta riko Hurriya ta fito
suka shiga cikin gidan. Yasir ya bisu da kallo gaba daya Hurriya ta zama abun
tausayi a yanzu.

“Kina ganin jarabawa Hurriya”

Ya furta sannan ya sauke ajiyar zuciya ya bude motarsa ya shiga. Rukayya na ganin
Hurriya ta shigo falon tana lalabe sai ta fashe da kuka ta saki kofin kurar da zata
bawa Amma ta nufi Hurriya ta rumgume ta suna kuka. Gwaggo ta girgiza mata kai domin
bata son Amma ta sani, sai dai abin da bata sani ba Rukkaya ta fada ma Amma komai
bayan tafiyarta.
Jin kukan Hurriya sai ya saka Amma ma ta fashe da kuka, kukan da ta shekara hudu
bata yi irinsa ba, kukan da tun da ciwon ya kamata bata taba kuka anji muryarta ba
sai yau. Hurriya na jin sautin kukan Amma ta saki Rukkayya ta fara lalaben gurin da
Amma take, Amma ta rika fuskarta ta saka hannunta ta bude cikin idonta tana kuka.

“Bana gani Amma bana ina ganin komai....”

Amman ta girgiza kai ta fashe da wani idin kuka mai taba zuciya.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un...”

Amma ta furta da wani irin karfi irin an mai kwancen murya. Rukkayya ta kalleta da
sauri ta rufe baki tana kuka, Gwaggo kuma ta zauna kusa da ita ta fadata.

“Iyami... Allahu Akbar....”

“Na jefaki a halaka Hurriya na je kaina, sun kashe min Hamad ke ma kuma so suke su
ga bayanki, da na san haka GOBENA zata kasance da ban auri Alhaji Haruna ba, na yi
nadamar wannan aure na kaddara.... ”

Da in'in'ina take maganar muryarta na rawa as well as bakinta saboda dadewar da ta


yi ba ta yi maganar ba, Twins dinta suka zo a guje suka tsaya suna kallonta, abu ne
da ba su tana gani ba, tun da aka haife su suka yi wayo Amma bata tana magana ba,
ba su taba jin sautin muryar uwarsu ba, bata taba kiran sunansu sun ji da kunnensu
ba.

“Amma... Amma... Ammma. Muryarki ya bude Alhamdulillah Ala kulli halin,


Alhamdulillahi hamdam kasiram”

Hurriya ta fada tana kuka tana dariya a lokaci daya sai kuma ta rumgume Amma. Gaba
daya sai falon ya karade da sautin kuka, Amma kuka, Gwaggo kuka, Rukayya kuka. Su
ma Twins sai suka fashe da kuka ganin Amman da Hurriya na kuka.

HAJIYA KALTUME POV.

“Kuma be ce zai dauki wani mataki ba?”

Khairy ta girgiza kai.

“Yace zai dauki mataki na wanda ya aikata mata haka, Ya Yasir ma yace zai dauki
mataki akai”

“Dan'iya daman idan be dauka ba ai be cika Yasir ba, amman na yi mamakin ace Alhaji
be mata komai ba, da ada ne Wallahi korarta zai yi”

“Kuka ma yayi sosai, Appa ya zubar da hawaye Hajiya kuma yayi tsinuwa akan duk
wanda ya aikatawa Hurriya wannan abun...”

Khairy ta fada cikin kuka.

“To ke miye naki a ciki? Har da wani kuka ni kowaye ya aikata haka ya biyani
Wallahi, dan Allah ni tashi ki ba ni guri zan yi waya”

Khairy ta mike tsaye ta fice daga dakin, Hajiya Kaltume kuma ta daga wayarta ta
kira Hajiya Fatee. Khairy ta shigo dakinta tana share hawaye ta nufi wayarta dake
aje ta dauka ta kira Adam.. Sai da kiran ya kusa yankewa sannan Adam ya daga.

“Adam ka ga abun da ka janyo ko?”

“Sai na kasheki Khairy sai na kasheki, ni zaki zaki yi betrayed? Sai na koya miki
hankali Khairy”

“Ban aikata komai ba, laifin ba nawa ba ne kana ne, kai ka lalata komai Adam... Na
yi nadamar saninka a rayuwata”

Ta dauke wayar a kunnenta tana kuka.......

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

A hankali ya maida fork a plate din kankanar dake gabansa ya kalli mahaifiyarsa
wacce ta tsare shi fa ido.

“Na koshi”

“Baka wani ci da yawa ba, kuma ka saka na yi cancelled tickets din da na siya, idan
na yi magana ka ce ka ji sauki”

“Na ji sauki mana Ammy baki gani ba?”

“Me kake son ci yanzu? Watermelon din nan kawai ka ci zuwanka gidan nan”

Ammy ta fada cikin yanayin damuwa. Ya duba wayarsa da sako ya shigo.

“Good... Ku turo location din gurin da kuka aje shi yanzu”

Ya masa reply sannan ya kalli mahaifiyarsa.

“Taliya nake son ci mai zafi sosai, and ke nake son ki girka min”

Ta kai hannu ta shafa fuska cikin tsananin so da kauna da kuma tausayinsa.

“Ko wani kake son na girkawa zan girka masa Captain balle kuma kai, zan girka maka
yanzu”

“Thank You”

Ta mike tsaye ta dauke plate din ta fice, binta yayi da kallo sai da ta rufo kofar
dakin sannan yayi rejecting kiran Salim dake shigowa wayarsa. Ya mike tsaye ya nufi
kofar ya bude ya sauko a hankali ya shiga falon Kakarsa domin ita a kasa aka yi
mata nata bangaren saboda kafafuwa da take fama da su, karamin falon ya fara shiga
sannan ya karasa bakin kofar dakinta. Daga bakin kofar dakin ya tsaya yana
kallonta.

“Nene.. ”

Tsohuwar dake rike da carbi ta dube shi da murmushin a fuskarta ta ce.

“Ango ya karfin jiki?”

“Alhamdulillah, Nene key motarki zaki ara min”

“Ina zaka je? Kai da baka da lafiya?”

Yayi mata alama da ta yi shiru.

“Ba sai kin fada kowa ya ji ba, Ammy zata iya hanani fita kuma abu mai muhimmanci
daga office ne”

“Ba a aiki da dare ai”

“Aikin mu ba shi da hutu, zaki ba ni key din ko na je gurin Hajiyar Maru na karba?”

Ta dan yi shiru kamin ta amsa masa.

“Yana nan cikin drawer, amman dai idan turaki ya san ka fita zai yi fada”

“Ba za su sani ba”

Ya nufi gurin da keys din suke ya dauka ya fice daga dakin, sai da ya fara bude
falon ya leka ya ga babu kowa a babban falon sannan ya fito ya rufe kofar ba tare
da ya bari ta yi motsi ba, ya fice salin alim, hankalinsa be kwanta ba har sai da
ya fice daga gidan. Har ya isa asibitin FMC Salim be daina kiran wayarsa ba, shi
kuma be amsa ba kuma ba zai amsa ba domin ya san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki.
Kai tsaye ya nufi ward din da Hurriya take, sai fa ga fara knocked sannan ya tura
dakin ya shiga to his greatest surprise sai ya samu wasu ne a dakin ba ita ba,
gaishe yayi sannan yayi musu bayanin wanda yake nema.

“Wata kila an sallame ta mu ma yau aka kawo mu”

“Okay Allah ya bada lafiya”

Ya juyo ya fito, har ya koma motarsa kiran Salim da na wasu new numbers be fasa
shigowa wayarsa, sai da ya shiga motarsa sannan ya kashe wayar gaba daya. Daga
asibiti ya nufi gidansu Momy, ya san ganin Hurriya a wannan daren a bangaren Momy
ba abu ne mai sauki a gareshi ba, bayan sun samu misunderstanding a dazun, and idan
tace kar ya shiga dakin Hurriya ko kar a kirata be isa ya ce ba haka ba. Sai dai ya
san karfin son ganin Hurriya saboda duba lafiyarta ba zai bar shi ya huta ba har
sai ya ganta, shi be ma ga dalilin dauketa daga asibitin a yanzu ba a dawo da ita
gida, ko dai daki aka canja mata, wata zuciyar ta hararo. A kokarinsa na neman amsa
ya karfafaf kansa guiwa ya bude motar ya fito yana kallon windows din dakin na
Hurriya. Tunawa da bata iya ganin komai a yanzu ya saka shi kara jin tausayinta.
Hannayesa ya saka a aljhun wandonsa sannan ya taka ya isa gurin kofar dakin ta Momy
ya danna door bell. Namra ta bude kofar falon, ganin Captain ya sakata mamaki sosai
domin ta san ba shi da lafiya me zai zo yi a gidan by this time. Ta ja baya tana
kallonsa without saying anything kamar ta yi arba da wani bako, Momy dake da remote
ta aje remote din tana kallonsa.

“Wata fitinar ce kuma ta taso?”

Yayi murmushi ya sauke kansa kasa.

“Na je asibiti duba Hurriya ban same ta a can ba”

Momy ta dauke kai ta maida gurin Tv kamar bata san abin da ke fitowa daga bakinsa.
Namra ta kalli Momy kana ta nufi kujera ta zauna.

“Hurriya bata asibiti if case you didn't know”

Ya maimaita yana kallonsu domin zuciyarsa na raya masa, wani abu akan rashin
ganinta be yi ba a yanzu.

“She's not here either”

Ya kalli Namra gabansa na tsananta faduwa.


“Wani abun ya faru? Mahaifinta ya koreta ko kuma yaya?”

“Tana gidan Mahaifiyarta”

“Ina ne?”

Momy ta kalli Namra dake kallonta sannan ta kalli Captain ta amsa masa.

“Ban san gidan ba”

Ya kalleta da kyau sannan yayi murmushi ya ce.

“Zo muje waje ki ji”

Momy ta kalleshi cike da fusata ta ce.

“Babu inda zata je, ku fita waje ka tirsasa mata abun da bata sani ba? Ko kuma ka
ce zaka daketa?”

Yayi murmushi

“Sai da safe Momy”

Ya juya ya fice ba tare da ya kara cewa komai ba, Namra ta bishi da kallon mamaki.

“Da ada ne zai yi kamar zai tashi gidan nan saboda bacin rai, amman ji yadda ya
fita har murmushi yake”

“Ai dole yayi murmushi mana saboda ya san ya kulla min bakinciki da bacin rai, ba
rantsuwa Hurriya zata yi ba ko kur'ane ta hade ba zai aureta ba”

“Amman Momy bata aikata ba fa sheri ne”

“Okay wannan ya wadatar dake kenan kin hakura da shi? Fine”

Momy ta jefar da remote din ta mike tsaye ta nufi hanyar stairs tana jan tsaki.
Namra ya bita da kallo kamar na rashin fahimta kamar mamaki.

Ya dade a cikin motar sannan ya yi mata key ya fice daga gidan yana tunanin yadda
za'ayi ya samu ganin Hurriya, da farko yana son na duba lafiyarta ne yanzu kuma
yana sso sanin halin da take ciki jin cewar tana gurin mahaifiyarta, korarta
mahaifinta yayi ko kuma wani abun ne ya faru...! Ya kunna wayarsa ya duba location
din da aka turo masa, kamin ya kashe wayar kiran Ammy ya shigo masa amman ya ki ya
daga already ya san dalilin kiran nata. Tafiya yayi mai nisa ta kusan barin garin
Gusau sannan ya isa Lalan, ya kutsa cikin wata unguwa dake gurin ya shiga can ciki
har ya isa gidan. Horn yayi wani soja ya fito rike da bindigarsa ya duba motar
Captain ya sauke gilashin motar Soja ya sara masa sannan ya koma da gudu ya rika
gate din shi da wani suka bude. Captain ya fito matarsa suka sake sare masa sannan
dayan ya ba shi labarin yadda suka dauko Adam abun da ya motsa asibitin gaba daya
domin sun tabka rashin mutunci a kokarinsu na cika umarnin shugaban na su.

“Ina yake?”

“Yana ciki gaba daya a firgice yake”

Captain ya wuce gaba suka take masa baya, a yayinda ya isa gurin kofar da aka saka
Adam kuma sai dayan ya bude masa ya sare masa. Captain ya shiga dakin da shi kadai
ne be da haske a duka dakunan da suke gidan. Sojan ya haska Adam dake zaune a kasa
daga shi sai gundun wando idonsa daya a kumbure hancinsa na jini sai nishi yake
kamar na mutuwa. Captain ya karasa ya duka a gabansa ya karbi wayar ya haska Adam
da kyau sannan ya haska kanshi

“Ka gane ni?”

Adam ya kalleshi da ido daya ya kasa cewa komai, sai Captain ya kama hannunsa da ya
rumgume a shimfida a kasa ya mike tsaye ya daga kafarsa zai taka hannun.

“Dan.... Allah.... Dan Allah.... Karka taka karaya ce a jiki dan Allah ka yi
hakuri....”

“Na sani ai, ba ni na karya hannun ba? Kuma ga dauri a jiki na gani”

Captain ya kai kafarsa ya taka hannun mai karaya na Adam ya murza, sai da Adam ya
kwala wani irin ihu ya kwanta a gurin kamar zai mutu. Captain ya dauke kafarsa ya
duka saitin da fuskar Adam take yana kallonsa ya ce.

“Soja be san tausayi ga azzalumi ba Adam, wannan kadan ne daga bangaren aikin mu,
na ce a aje min kai a nan na tsawon awa goma, kuma a gana maka azaba kala kala, sai
dai ka ci albarka na fito duba Hurriya sai na yanke shawarar kawo maka ziyara”

“Dan Allah ka yi hakuri... Dan Allah ka yafe min.. Ka yi hakuri... Wayyo Allah
mutuwa zan yi”

“Mutuwar ai nake son ka yi shiyasa na ce a dauko criminal irinka daga asibiti a


kawo ka nan, ka ga babu wanda ya san gurin da kake a yanzu, idan na ga dama zan iya
kashe ka a nan, na aje maka bindiga nace tare kake da yan ta'adda, idan na ga dama
kuma sai na aje maka bindiga b tare da na kashe ka ba, na ce mum daukoka daga
asibiti ne muka kawo ka nan saboda ka nuna mana sauran yan'uwan ta'adancinka, ko a
hukunmance babu wanda zai tuhume mu, kaga na lalata maka rayuwa zama gidan kaso
kuma ya kama ka, ko da ka fito rayuwa bata da amfani a gurinka”

“Me na maka? Me na maka? Ni fa Adam ne Adam Sarauta”

“Ni kuma Ni kuma Captain Jamal AA Turaki ne, sai yaya? Wannan be ji wuta ba ku gasa
min shi da safe zan dawo”

Captain ya mike tsaye, Adam ya yunkuro yana kuka zai rike Captain ya kasa saboda
azabar da yake ji a hannunsa.

“Ka yo hakuri dan Allah, me na yi?”

Captain ya juyo ya kai masa duka a baki.

“Mai tsada ka taba, ba ka ce kai dan'iska ba ne? Zan nuna maka na fika zama shege”

“Wallahi Wallahi ban mata komai ba”

Captain ya daga gira daya, sannan ya kunna wayarsa ya saka ta a plane mode, ya
shiga camera ya kunna video.

“Me saka ka yi min karya to? Me yasa ka ce min tare kuke haduwa?”

“Na yi hakan ne saboda kar laifin ya shafe ni kadai”

“Ya aka yi hannunka ya kai ga jikinta? Har aka yi muku hotuna?”

“Hotunan an dauke su ne a lokacin da Hurriya takw bachi bata cikin hayyacinta, bata
san an yi ba”
“Saboda me?”

“Magani aka saka mata”

“Kai ka saka mata maganin kenan?”

“Ba ni na saka ba, Khairy ta saka mata, ban san yadda aka yi Khairy ta saka maganin
ba, ni dai ta kira ni kawai ta ce min na zo gata nan”

“Sai kuma ka zo?”

“Eh saboda mun shirya hakan da ita?”

“Saboda ka lalatawa Hurriya suna?”

“Aa ba dan a bata sunanta ba ne, ni ina son Hurriya ne tun farko, sai dai Khairy ta
bata min suna a gurinta da iyayenta shiyasa sai ta ki saurarena, ni kuma na kasa
hakura Khairy ce ta kawo shawarar na yi amfani da Hurriya kawai a wuce gurin, ta
karbi kudi mai yawa a hannuna saboda ta samonin kan Hurriya, amman ban samu yadda
nake so ba, ni kuma na biye mata ne saboda ina ganin kamar wannan ce kadai damar da
nake da ita, shiyasa ta hada plan aka zo da Hurriya a gidansu Zuhura ta kira ni
tace na zo, ko da na zo har sun cire nata tufafi, ni kwantawa kawai na yi aka yi
mana hoto”

“Saboda me ka yi hotunan?”

“Saboda na yi amfani da su na yi ma Hurriyya barazana ta amince da ni, saboda


Khairy ba zata iya kawo min ita na yi amfani da ita ba, tana tsoron ace ta yi hanya
ayi ma Hurriya Fyade idan asiri ya tonu zata ji kunya”

Captain ya kai masa duka akai kamar wani criminal.

“Ka ji Jarumi yarinya tace bata yinka sai ka koma ta bayan gida kai dole sai ka yi
amfani da ita ko? Ashe ma fyade ka tashi yi mata!”

“Saboda na rasa yadda zan yi ne, kuma ya nuna min bata so na kirikiri”

“Me ya hana ka? Ashe baka kai dan'iska ba”

“Babu yadda zan yi na samu kan Hurriya ne saboda bata saurare balle na fita da ita
ko na ja ta wani gurin, Khairy kuma tana tsoro, shiyasa ta shirya wannan abun,
bayan mun dauki hotunan sai kuma yadda zan yi amfani da su ya zama aiki, saboda
Khairy bata son ace da wayar na yi amfani na yi barazana a gurin Hurriya ba, saboda
tana jin tsoro”

Adam na kuka irin na karti da majina shabe shabe ya ke fadar hakan yana rike da
hannunsa mai karaya.

”Nii kuma ba zan iya tunkararta kai tsaye ba, saboda ina tsoron kai ta fada a
gidansu, gashi ban samu yadda zan yi magana da Hurriya ba, a lokacin ne na gane
kamar wayo Khairy ta yi min, sai fadan ya koma tsakaninmu, na kasa daga nata kafa
saboda zan bar kasa na tafi gurin masters sanadin haka mu ka yi fada, washe garin
ranar da muka yi fadan na kirata na bata hakuri muka hadu a wani gurin and.... I...
Rape her there.... ”

Captain be san lokacin da ya bude baki ba.

“Wait... Wa ka yi raping?”
“Khairy saboda ta ci kudina kuma ta kasa ba ni abun da nake so, sai fadan min take
na yi amfani da hotunan, ni kuma hotunan ba su da amfani a gurina saboda ban samu
damar kebewa da Hurriya ba, kuma ban san ya hakan zai faru ba”

Captain ya mike tsaye yana jinjina lamarin Ubangiji, bahaushe ya ce wanda Allah ke
yi ma fada baya fada, all this plan akan Hurriya amman Allah ya kareta sherin da
suka kulla be same ta ba.

“Wacece Khairy ma?”

Ya sake tambaya domin tabbatarwa.

“Yayarta ce, mahaifinsu daya a gurin Birthday Khairy muka hadu da Hurriya, saboda
Khairy ce friend dita”

“To me yasa ka hadawa hotunan? Bayan ka samu abun da kake so a gurin Khairy? Akan
me zaka cutar da Hurriya meye nata a ciki?”

“Ba ni na yada hotunan ba Wallahi, ban san waye ya yada ba, wata kila Khairy ce
saboda ta ji haushi abun da muka yi mata, ta ce min sai ta dauki fansa, wata kila
ita da yada hotunan”

“Me yasa ka amsa cewar tare kake da Hurriya? Why? Idan ma an yada me ye ribarka na
amsawa”

Ya kasa magana sai wayyo wayyo yake yana kuka. Captain ya kama hannun ya murza.

“Ba tambayarka nake ba?”

“Wayyo....wayyo.... Wayyoooo..... Na yi hakan ne saboda kar nawa sunan na bace ni


kadai, dan Allah ka sa a maida ni gida dan Allah”

“Za a maid kai, na samu abun da nake so ai ka saukakawa kanka, amman still zaka
fuskanci hukunci...”

Captain ya tsayar da video ya mike tsaye ya fice daga dakin da Adam ke ta ihu yana
neman ceto.

“Ku bar shi a nan DSS za su zo su dauke shi, ku babu hannunku a ciki, ko a office
kar wanda ya amsa cewar kun je dauko yaron nan”

“Yes Sir”

Ya sara masa, sauran soldera din da suke waje mota biyu duka suka sara masa, sannan
ya bude masa motarsa ya shiga ya rufe motar ya sake sara masa. Captain ya cire
plane mode din ya shiga contact dinsa ya nemo wata number ya kira, after sun gaisa
ya ce

“Mubarrak akwai wata yarinya da aka batawa suna, kuma abun ne da ku ya kamata ace
kun yi Handel a yanzu, Lawyer na zai shigar da kara a gurinku cikin dare nan,
please ina son ka tashi yaranka a location din da zan turo maka yanzu su dauki
yaron, already na saka an dauko shi daga asibiti na san be kamata na yi haka ba
amman na kasa hakuri ne”

“Me yaron ya aikata....”

Captain ya labarwa abokinsa abun da ya faru a takaice, sannan ya dora da cewar.


“Already babansa ya kai case din kotu saboda na karya masa hannu, na zubar masa da
hakora so now i want you to cover me up...”

“Karka damu I know my job, ka turo Lawyer ka ya saka kara a gurin mu yanzu nan”

“Thank you”

Yana sauke wayar ya kira Lawyer sa Barrister Hauwa Zamau. Yana tukin motar yana
fada mata abun da ya faru har ya isa gida.

“To a matsayin wa zamu shigar da karar?”

Yayi shiru yana kallon harabar gidan kakan nasa.

“A matsayin wanda zata aura, ina neman hakkin cin zafinta da yayi, abu ne kika sani
duk wanda ya yi ta’adi ko kuma ya buga hotuna ko bidiyon tsiraici na mutum a yanar
gizo ba tare da izinin mutum ba, to lallai irin wannan mutumin ya aikata laifi, and
can be punished for Cyberstalking under S.24 of Cybercrimes (Prohibition,
Prevention, etc.) Act 2015 of Nigeria or any law being in force in Nigeria..”

“Amman a yadda ka fada min ya amsa maka cewar ba shi ya yada hotunan ba”

“Wannan zai zo daga baya, a iya yanzu shi kadai muka sani da hotunan dan haka shi
muke zargi, shiyasa muka shigar da karr gurin DSS saboda fadada bincike”

“Good point, i hope iyayenta ba za su ba mu matsala ba”

“I will fix that later... Ki aiko min da account number dinki yanzu nan”

“An gama ranka ya dade”

Ya katse kiran ya sauke wayarsa. Gallary dinsa ya shiga ya kama hoton Hurriya da ya
dauka a dakinta ya duba.

“Mai tsada... Kin rike mutumcinki gashi abun da suke shirya miki ya koma kansu,
ashe kaddarar mai yawa ce Allah ya takaita a haka, pretty girl with golden
Heart...”

Magana yake da hotonta dake cikin wayar yana murmushi kamar ance masa tana
saurarensa, kaunarta ta karu a zuciyarsa, a yanzu ya kara tabbatarwa ita din tabbas
mai tsada ce...
Sai da ya turawa Barrister alert mai kauri tare da Nafi'u sannan ya fito motar, sai
a lokacin ya lura bakin motoci dake gidan, kamin yayi wani motsi kira ya shigo
wayarsa wannan karon Daddysa ne ya kira, ya amsa kiran da girmama da ladabi.

“Hello Daddy”

“Jamal kai ka aika aka dauki yaron nan daga asibiti?”

“Wane yaro?”

“Dan gidan Bashir Sarauta”

“Cewa suka yi na dauka?”

“Ka amsa min kawai ka dauke shi ko aa? Me ya fitar da gidan?”

“Na dauke shi, amman na yi covering case din yana hannun DSS yanzu”
“Why? Fadan nan ba naka ne kai kadai ba so ka cire hannunka a ciki ka bar ni da
mahaifin yaron nan, ka zo gida yanzu nan”

Daddy ya katse wayar a take. Captain ya karasa ya shiga cikin falon, ga mamakinsa
sai ya samu Salim a falon tare da wasu mata biyu, sau daya ya kalli gurin da Salim
yakw zaune ya dauke kai zai wuce gurin Ammynsa dake tsaye tana kallonsa da waya a
hannunta.

“Jamal.... Ina Adam...?”

Captain ya juyo ya kalleshi.

“Jamal....? How dare you call your boss like that?”

“Ba a office muke ba, baka da wannan ikon a nan, ina Adam?”

“Na dafa shi an cinye ka san ni maye ne”

“Kai ka aika da boys aka dauko yaron nan ina ka kai shi?”

“Taya ka san ni na aika aka dauko shi? Ka gan ni a gurin ne?”

“Mahaifiyarsa ta fada min yadda komai ya faru? Taya zaka aikata hakan Jamal? Ina
hankalinka ya tafi?”

Captain ya taka ta isa inda yake tsaye, cikin wani irin isa da izza Captain ya ce.

“Bari na kira headquarter na fada musu Salim Sarauta ya shigo har cikin gidanmu ba
tare da uniform ba, yana tukumar ogansa da sace wani wanda ban san da wanzuwarsa a
kasar nan ba, kuma ka kira sunana kai tsaye with full of disrespectful, and you
know yadda wannan abun zai taba aikinka”

Captain ya kara matsawa kusa da shi sosai.

“Ka san yadda Power take da karfi a Familymu, zan yi duk yadda zan iya na ga an
cire uniform a jikinka, lastly ka san yadda bad ending yake karewa korarren ko da
karami ne balle kai, and you know i can do it, so respect yourself....”

“YES SIR...”

Salim ya amsa masa dan dole yana kamewa guri daya, sannan ya hade yawu ya juya ya
kalli matar da hankalinta yake a tashe ya ce.

“Mu tafi Anty Nabila”

“Mu tafi? Bayan ba mu san inda yaro yake ba? An zo an dauki yaro cikin asibitin
yana cikin tsananin ciwo sannan ka ce min mu yafi? Mu koma mu yi me?”

Cikin kuka matar take magana, sai dayar dake gafenta ya amsa waya sannan ta kama
hannunta

“Mu tafi Anty Nabila”

Sai da suka wuce sannan Salim ya kalli Captain ya juya ya fice daga falon cikin
tsananin takaici.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

“Ban zan iya fadar wata rana da ka samu matsala da abokinka ba sai yau, duk wannan
akan yarinyar da bata kai ta kawo ba ne? Kana kokarin fita hayyacinka, duk wasu
abubuw ada ba dabi'unka ba su kake aro ka yafe yanzu! Idan idonka ya rufe ni nawa
be rufe ba, ba zan taba karbar yarinyar da duniya ta gama ganin tsiraicin a
matsayin suruka ba...”

Be ji zai iya musu da mahaifiyarsa ba, saboda haka ya karasa gurin da take tsaye ya
kama hannayenta ya sumbanta yana murmushi.

“Zaki so ta Ammy saboda kina son farincikina, kuma a yanzu farincikina yana tare da
yarinyar nan, ba ni da wani buri a yanzu da ya wuce na ga na tsamota daga kogin da
aka jefata”

“Wai me yarinyar take da shi ne da babu a sauran mata?”

“Na so wasu matan kamin ita Ammy kin tuna? Har an min baiko da wasu, duka baki ce
komai ba ga wannan? Wanda ta fisu komai?”

“Babu wani abun da ta fi su sai tallata tsiraici”

“The more da kike zaginta the more da nake jin kaunarta na karuwa a zuciya, zagin
da kike mata ya kara bude min hanyar son taimaka mata”

Kallon rashin fahimtar inda ďanta ya dosa Ammy take masa, cikin bacin rai da daga
muryar ta ce.

“Zamu wuce Kaduna gobe”

“Ban samu amincewa daga gurin aikin mu ba”

“I don't care zamu tafi Kaduna gobe idan hutun da ka rubuta ya kare sai ka dawo”

Yayi murmushi sannan ya wuce ciki, da kallo Ammy ta bi danta, kiyayyar da take yi
ma Hurriya a yanzu ba dan tana talaka ne kawai ba, har dan hotunanta sun fita a
duniya ne, taya zaka kalli kazantacciya yarinya irin Hurriya a matsayin matar danta
guda daya tilo? Duk shekarun nan da ta dade tana jiran zuwan wannan ranar? Ace daga
karshe Hurriya ce? Duk matsayinta a idon duniya da yadda mutane suke kallon
mahaifinsa? Wai ina kishin danta ne? Taya ya barar da komai idonsa ya rufe akan
yarinyar nan? A yanzu ne take ganin ya dace ta yi wani abu saboda haka ta bi
bayansa ta shiga dakin da yake, sai ta same shi yana canja riga.
“Captain... We need to talk”

Ya karasa jan rigar kasa ya nufi gefen gadonsa ya zauna yana kallonta. Ta daure ta
zauna tana aje numfashi a gurin da ba muhallinsa ba, daga bisani ta saita fushin
zuciyarta.

“Magana ce da nake son ka ba ni aron hankalinka kuma ka bude zuciyarka ka karbi


abun da nake son fada maka”

Ya daga mata kai yana kara tattara hankalinsa gareta.

“Ba zan hana ka taimakawa yarinyar nan ba idan taimaka mata kake son yi, abu mai
kyau amman kar hakan ya saka na manta waye kai, Captain ya kamata ka dawo cikin
hayyacinka, ka tsaya ka yi tunani mai kyau yarinyar nan bata dace da kai ba, future
dinta ya lalace sanadin haka zai iya taba naka rayuwar, taya zaka shiga taron
mutane da fuskar yarinyar da duniya ta gama kallon tsiraicinta? Ni ma ta ya zan
kalli kawaye na gabatar musu ita a matsayin suruka?”

Yayi murmushi yana saka hannunsa na dama cikin kishiyarsa wato na hagu.

“Ammy kina so?”

“Wane irin magana ne wannan? Taya zaka tambayi uwa tana son danta musamman uwa irin
ni?”

“Dan Allah kin amsa min”

“Ina sonka irin son da babu uwar dake yi ma danta shi”

“Toh dan Allah ki so Hurriya, duk mai so na, kamata yayi ya so abun da nake so, duk
wani illarta da zaki ina min a yanzu ba zan gani ba, wata kila sai nan gaba shi ma
kuma bana fata”

“Ta ya soyayya zata rufe maka ido, ka kasa yin biyaya ga mahaifiyarka Jamal? Akan
yarinyar daka hadu da ita da girmanka? Ka bijirewa mahaifiyar fa ta haife ka ta yi
wahala da kai? Ko dan saboda kai kadai Allah ya ba ni shiyasa kake min haka?”

Ta karashe maganar idonta na cika da kwalla. Ya kalleta da fuskar da babu wasa a


cikinta.

“Zan hakura da Hurriya Ammy, matukar hakan shi ne zai faranta ranki, na hakura da
ita Ammy, soyayya ta yi kadan ta yi min irin wannan rufin, zan hakura da nawa
farinciki”

Ta share hawayenta tana murmushi ta dafa shi.

“Allah ya maka albarka, ba zaka gane amfanin abun da na yi maka ba sai nan gaba,
yarinyar ba ta dace da kai ba, be kamata ta zo a matsayin surukar mu ba”

Ya daga mata kai yana murmushi kadan, sannan ya sauka daga kan gadon ya zauna a
kasa ya kama kafarta ya rike.

“Ina rokon alfarmar ki bar ni na karasa aikin da na dauko, na yi ma yarinyar nan


alkwarin zan gyara mata komai, shi wannan karki hana ni Ammy”

Ta kama hannunaa da sauri cikin farinciki.

“Ba zan hana ka ba, na amince ka taimake ta, matukar ba zaka auro min ita a
matsayin mata”

“Na gode”

Yayi mata godiya ransa babu dadi, domin a iya gaskiyarsa yayi mata alkawarin hakura
da Hurriya saboda bata sonta, ba zai zabi farincikinsa sama da na mahaifiyarsa ba,
sai dai yayi ma kansa wani alkawari daya zai taimaki Hurriya zai cireta a damuwa
kamar yadda ya fada.

“Daddy yana nema na bari na shiga dakinsa”

“Yana can bangaren mahaifiyarsa, dazun sau biyu Bashir Sarauta na aiko masa da
mutane yana neman ka ba shi dansa”

Be ce komai ba ya dauki wayarsa da keys din Nene dake kan gado ya fice daga dakin,
gaba daya sai yanayinsa ya sauya, rashin kuzari da walwala sun tattara a fuskarsa
da jikinsa. Kamar wanda aka yi ma mutuwa haka ya shiga bangaren kakarsa dake cike
da mutane a falon da yaranta da jikokinta cikin ƴaƴanta har da Daddy dake zaune
kusa da ita. Kowa zai iya shaidar Captain baya cikin farinciki domin abun a bayyane
yake a fuskarsa balle kuma mahaifinsa da ya fi kowa sonsa.

“Ina makullin motata? Ashe fitina zaka je ka tayar shi ne ka karbi motata?”

Nene tana maganar tana kallonsa, sai ya karaso ya mika mata key motar ba tare da
yace komai ba, sannan ya nemi gurin ya zauna yana mamakin kansa da ada ne idan aka
bata masa rai kadan sai yayi kamar zai tashin kowa balle kuma babban abu kamar
wannan, amman a yanzu ya kasa yin komai sai ma sauyin yanayi da ya zo masa.

“Jamal.... Lafiya?”

Nene ta tambaya mahaifinsa kuma sai kallonsa yake yana karantar damuwarsa. Captain
ya kalli Nene ya kalli kowa dake falon sannan ya mike tsaye

“Ba komai, Daddy ka ce kana son ganina?”

Momy Ikilima ta ce.

“Captain akwai wata matsala ne?”

Ya girgiza mata kai alamar babu. Daddynsa ya sauke ajiyar zuciya cike da kulawa ya
ce

“Shiga ka jirani a falon Hajiyar Maru”

Ya amsawa Daddy da kai sannan ya fice daga dakin.

“Baka tambaye shi ina ya kai yaron mutane ba? Kuma na ga yanayinsa kamar da
matsala, Allah yasa ba kashe shi suka yi ba, kasan zuciyar Captain fa idan abun ya
motsa baya iya rike kansa”

“Zan yi magana da shi Hajiya zan ji ko minene”

Daddy ya mike tsaye ya fice daga falon, kowa sai mamakin yadda yanayin Captain ya
canja. A falon Hajiyar Maru wato step mother dinsa Daddy ya samu Captain zaune ya
soke kai kasa yana jiransa.

“Karantawa min abun da ya saka ka cikin damuwa?”

Daddy ya tambaya tun kamin ya zauna. Captain ya dago ya kalli Daddy ya fara magana
da muryar da ke kara bayyana damuwarsa.

“Ammy ce....”

Ya fada masa abun da ya faru tsakaninsu ya kuma jadda masa cewar ya hakura da
Hurriya saboda mahaifiyarsa. Daddy yayi murmushi ya kawar da kai kamin ya juyo ya
dauko masa zancen daukar Adam da aka yi, a nan ma Captain be boyewa mahaifinsa
komai ba, har video da ya dauka na Adam sai da ya nuna masa.

“Samarin yanzu hauka tana damunsu, idan yarinya tace bata sonka sai ka koma bibiyar
bayanta kuma? Da alama dai ba son gaskiya yake mata ba shiyasa ya koma bibiyar
rayuwarta”

“Ni ma haka na ce”

Captain ya fada babu kuzari babu nishadi da jindadin da ya shigo da shi. Daddy ya
ce.

“Amman Barrister tana da gaskiya, mahaifin yarinyar ba zai kawo matsala ba, ka san
wasu iyayen basa son bibiyar irin wannan lamarin”

“An abun haushi ma mahaifinta be san ina son yarinyar ba, be san na dauki wannan
matakin ba, na shigar da karar ne a matsayin wanda zai aureta ba tare da tunanin
wata matsala zata biyo baya ba, amman yanzu ina tunanin zan yi magana da Barrister
na fada mata a canja abun”

“Saboda me?”

“Ammy bata so kuma. Na fada mata na hakura Daddy”

“Hakan yana da kyau, amman ka bari mu yi magana da mahaifinta mu sanar masa halin
da ake ciki idan ya aminta sai a sauya labarin daga kai zuwa mahaifinta kai tsaye,
a matsayin mahaifinta ya shigar da karar ba kai ba, daman hakan zai fi mutuncin
saboda kai ba aurenta ka yi ba, da ace kai mijinta ne kana da full hujja”

“Okay, Daddy amman idan ka tafi please ka lurar da shi wasu abubuwan na rayuwa, na
tafi asibitin ban ga yarinyar ba kuma na tafi gurin Momy tace min yarinyar tana
gurin mahaifiyarta, ina tunanin korarta yayi gashi bata gani kuma mahaifiyarta bata
da lafiya bakinciki sai yayi mata yawa”

Daddy ya ji tausayin Hurriya ya kama shi.

“Amman me zai hana a nunawa mahaifinta video nan maybe zai sauko ya yafewa yarsa
laifin da bata aikata ba”

“Aa bana son nuna masa shi a yanzu, already case din yana hannun DSS idan aka fitar
da video lauyoyin Adam zai su iya cewa an masa cin zafi ne an masa da karfi ya fadi
abun da ba ayi ba, kuma na yi ikirarin ban dauke shi ba fitar da video zai rushe
wacan ikirarin nawa, and Salim zai iya samun kofar shigar da koke a kaina, bana son
ya samu wannan damar, amman idan aka je kotun shi da kansa zai sallamo yarinyar ai
kuma dole kowa ya san me suka shirya kuma na saka a bincika mutanen da suka yada
hotunan kowa zai fadi inda ya samu ai daga nan gaskiya zata fito”

“So shari'a biyu za'ayi kenan?”

“Yeah... Yarinyar nan mai tsada ce Daddy, su sun shigar da ni saboda na karya ma
dansu hannu, mu kuma mun shigar saboda dansu ya ci mutuncin Hurriya, and na yi
alkawari kowa sai ya karbi kasonsa sai na kunyata su kamar yadda suka kunyata
yarinyar nan”
Yana fada yana jaddawa jikinsa na rawa yana matse hannunsa.

“Allah kadai ya san halin da take ciki yanzu, sanadinsu ta rasa idonta gaba daya
daman ba lafiya ta wadace ta ba”

Daddy dai sai kallonsa yake da yanayin.

“Zan tare da mutane a gobe zan jajanta masa abun da ya faru kuma na fada masa
matakin da ka dauka, idan ya ba mu hadin kai shi ke nan idan kuma be aminta ba dole
mu yi aje case din”

“Daddy please ba zamu aje case din ba, na mata alkawari ko da ba zan aureta ba be
kamata na kasa cika alkwarin da na yi mata ba”

Daddy be sake cewa komai ba, ya ciro wayarsa dake aljihu yayi yana tabawa. Can ya
dago ya kalli Captain yana murmushi.

“Lawyer na ne ya aiko min sako, wai Bashir Sarauta yace ba a janye case din a gobe,
wata kila yana tunanin saboda an kai case din dukan da ka yi masa a kotu ne ya saka
ka sake daukeshi”

“Ya zo nan ne?”

“Ya zo nan amman ban yi magana da shi ba na fada masa be kai wannan matsayin ba a
yanzu, da kam ina ganin mutuncinsa amman ban da yanzu, kuma na fada masa idan ya
sake zargin ďa na da daukar yaronsa sai na shigar da kara a kansa”

Captain yayi murmushi da be wadaci fuskarsa ba.

“Daddy wannan ai shi ake cewa fin karfi”

Daddy ma yayi murmushi mai sauti irin na masu dollars and pounds.

“I have to do the needful kamin na bar garin nan, gobe da yamma zan koma Kaduna ban
sani ba ko Ammynka zata bi ni ko kuma zata tsaya jinyar ďanta ne”

Captain yayi murmushin da ya kusan za a iya cewa ya zame masa dole ne kawai, sannan
ya mike tsaye yayi ma mahaifinsa sai da safe ya fice.

HAJIYA KALTUME POV.

“Tun jiya da muka yi waya da ke baki sake kirana ba, abun har ya soma ba ni tsoro,
da na shirya zuwa gidanki a yau”

Hajiya Fatee ta yi murmushi.

“Ai ni dole na zo na same ki Hajiya Kaltume shiyasa da Fadeel na kira cikin na ce


ya zo ya kawo ni gidan nan, amman Hajiya gajin hakuri kika yi ne har kika aikata
mata haka?”

“Ina fa wai ni? Wannan ai can ya fito tsakaninta da dan'iskan saurayinta, wata kila
matsala suka samu shiyasa ya watsa hotunan, ai ni ya biya ya hutar da ni wannan
kadai ya isa ya hana Hurriya aure, domin babu wanda zai daukarwa yayansa uwa irin
wannan? Sai dai a samu dan baro can ko masu gyaran talkama a hada su, idan ma ta
samu domin babu mai auren makauniya”
“Kuma kika ce ta rantse da kur'ane?”

“Haka Khairy tace, wata kila kuma wani ne acan waje yake taya mu fadan, kuma shi ma
yaron nan ta yi masa wulakanci ba, kuma abun da zai baki mamakin idan ba su saba
haduwa ba a ina ya samu hotunanta”

Hajiya Fatee ta kyalkyale da dariya ta bawa Hajiya Kaltume hannu suka tabe.

“Ai wannan abun yayi dadi Wallahi ana ganin yarinya kamar ta kirki ashe ita ma yar
banza ce”

“To kin gani dai gashi Allah ya tona asirinta, ko uwarta ai zaman banza ta so samu
gurin Alhaji shi kuma da yake ba dan'iska ba ne sai ya bijiro mata da aure”

“Amman ni abun ya ba ni mamaki da kika ce Alhaji be koreta ba, ga irinsu nan da


yawa ana kora da ya korata da mun huta ma”

“Ni ma abun da yasa na kira na tambaye ki kenan ko dai Malam be fara aikin nan ba
har yanzu? Kin ga shiru fa ina zaune a gidan nan amman Alhaji be yi wani unkuri na
maida aurensa da ni ba, jiya kuma Khairy ta fada min kuka yayi ta yi yana tsinewa
wanda yayi abun nan”

“Zai yi wahala ace ba a fara ba, ya kamata dai mu kara hakuri kar mu yi gaggawa,
domin tun ranar da aka tura kudin na kira shi na fada masa an tura kudin kuma yace
min sun shiga ya gani, har na yace min anjima kadan zai shirya ya tafi gurin
Malamin nasa ya kai masa kudin, tun daga ranar ban sake jin wayarsa ba, ko yanzu na
kira bata shiga ba”

Ta sake gwada kiransa a gaban Hajiya Kaltume aka ce wayar a kashe take.

“Kin ji ko? Ina tunanin ko dai wayar tasa ta fadi ne, har wadda ta hada mu da shi
na kirata tace ita ma bata samun wayarsa a yanzu”

Da mamaki Hajiya Kaltume ta ce.

“To kuma be siye wata ba? Ni fa jikina ya fara sanyi Hajiya Fatee”

“Karki ji komai, ni na yarda da Malamin nan dari bisa dari, mu kara hakuri idan aka
kara kwana biyu ba mu ji komai ba ni zan shirya da kaina na tafi kauyen na bincika
na ji”

“Allah yasa dai yayi mana aikin mai zafi, so nake Alhaji ya zo jiki na rawa ya roki
yafiyata kuma ya maida aurensa, sannan a shafe masa Hurriya da uwarta a ransa kuma
a hana shi auren nan da zai kara a mallaka min shi na juya shi yadda nake so”

“Wannan ai a rubuce yake, daman ya fada miki irin aikin zai yi kuma zaki gani, ke
dai ki kwantar da hankalinki ba gashi kin fara gani ba, wata kila aikin ne ma ya
saka hotunan nata suka yadu”

Hajiya Kaltume ta rike baki tana mamaki da dariya.

“Haka fa.. Kin ga gaba kenan sai kora, kuma da yardar Allah sai Hurriya da uwarta
sun koma bara, tun da idon ya rufe ba zan bar Alhaji ya nema mata magani ba kuma ba
zan bari ya maida uwarta ba, kin ga rayuwa ta kare musu kenan, daman na fada mata
sai na dandana mata bakinciki kuma sai ta gani, ba za a ci amanata a zauna lafiya
ba”

“Wani abun ma sai nan gaba”


Suka bushe da dariya, Hajiya Fatee ta mike tsaye ta dauki hijab dinta ta saka.

“Bari na tafi kar na batawa Fadeel lokaci aiki zai je na ce ya kawo ni na ganki ya
maida ni direba na yayi tafiya”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta yi mata rakiya suka sauko kasa suna hirar, bacin
rai dake zuciyar Hajiya Kaltume tuni ya yaye saboda kawarta ta karafafa mata guiwa
kuma ta kwantar mata da hankali. Ganin Khairy zaune a falon ya ba wa Hajiiya Fatee
mamaki

“Ah... Na yi zaton kina waje? Tare da Fadeel muke fa”

“Na sani bana jindadi ne shiyasa”

Ta amsa a kasalance tana sauke ido kasa kamar munafuka. Hajiya Kaltume ta ce.

“Wai ke kam me yake damunki? Tun jiya kike wani laude laude kamar kazar da kwai ya
fashewa a ciki”

Sai Hajiya Fatee ta daga hannu tana fadin.

“Wata kila abun yar'uwar ne ya shafeta kin san abun da ya taba gira shi ya kai ga
ido har ya taba hanci, idan abun da ta yi karki saka kanki a damuwa kwana nawa ya
rage miki ki har gidan ma, kuma wannan ai abun farinciki a gurinku, kowa be lalace
ba sai Hurriya na tabbatar da Iyami tana lafiya ace wani ne a cikin yaran Hajiya
Kaltume yayi haka farinciki zata yi ”

“Kwarai kuwa shiyasa ni ma bana fatan alheri ya same ta sai sheri”

Hajiya Fatee ta wuce gaba suka jera da Kaltume har wajen gidan, kamin Fadeel ya
juya motarsa suka nufi karamin gate din gidan na bangaren Hajiya Kaltume. Daga inda
suke tsaye suka hango shigowar manyan motocin na alfarma har hudu cikin gidan, duka
motocin aka nufi bangaren Momy da su.

“To baki kuka yi kuma?”

“Ta yi dai ita yar karyar arziki, ita din ma ba barinta zan yi ba Wallahi”

“Aifa ki bari aikin Malam ya fara kawai sai wanda kika so zai zauna a gidan nan, ni
na manta ban fada miki ba Afrah fa tana gidansu yaran suna gidana shi kanshi jiya
gida ya kwana”

Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Ki ce Allah”

“Ba kina wasa da lamarin Malam ba? Hmmmm”

Hajiya Kaltume ta jinjina kai tana kara ganin girman Malamin da kwarewar aikinsa,
Afrah da ta gagari Hajiya Fatee yau ace Fadeel ya kora Afrah gida. Babu halin yin
wata doguwar magana saboda Fadeel ya faka mota a gabansu ya budewa mahaifiyarsa.

“Hajiya Fatee zamu yi waya”

Hajiya Fatee bata sake furta wani abu ba saboda Fadeel yana gurin sai dai ta yi
murmushi mai sauti ta shiga motar, Fadeel ya ja bayan yayi ma surukarsa to be
sallama.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Da tunani kala kala Momy ta sauko falon Namra na bayanta.

“Yaya yau kai ne a cikin gidana?”

Daddy dake zaune akan kujera tare da sauran yan'uwansa yayye da kanne yayi
murmushi.

“Nafisa mamakin zuwana kike ne?”

“Kwarai kuwa, Yaya tun da aka kawo ni gidan nan sau daya ka taba zuwa gidan nan fa,
da Hajiya Turai ce ba zan yi mamaki ba, amman ganinka ya saka ni a fargaba Allah
yasa ba Captain ya ce na yi masa wani abu ba?”

Alhaji Munzali yayi dariya, Daddy ma dariyar yayi ya ce.

“Saboda ba ni da kunya zai na taso na kawo miki takakka har gida?”

Ta yi dariya.

“Namra duk a firgicce take ita ma ta dauka Captain ya turoka, saboda jiya ya zo nan
yana neman a kai shi gidansu Hurriya na hana Namra, wata kila hakan ya fusata shi
ya kai karata a gurinka”

“Hakan da kika yi ai kin yi daidai, Ammy sa ma ta yi masa magana be so ma amman


daga karshe dai ya fahimta kuma yace ya hakura”

Momy ta zaro ido tana dukan kirjinta.

“Ya hakura yaya? Amman ya kyautawa kansa daman can yarinyar bata dace da shi ba
Wallahi, ni daman na san Hajiya Turai ba zata yarda danta ya auri yarinyar nan ba”

Daddy ya gyara babbar rigarsa yana kallon Namra dake jera musu abun karyawa.

“So jiya mun yi magana da Captain saboda ya shigar da kara DSS yanzu kuma yana son
ya janye karar ne a hannata komai a gurin mahaifinta, ni kuma yau zan koma Kaduna,
shiyasa na zo yanzu na san be isa fita ba ina son na yi magana da shi mu kai
karshe”

“Hakan yayi, ban da Abin Captain na son wahalar da kai miye na wani shigar da kara,
yarinyar nan fa makauniya ce ma idon za su bude ba za su bude ba Allah masani amman
ya tsoma kansa a damuwarta har da ikirarin aurenta kamar wanda baya cikin
hayyacinsa”

“Wannan maganar kuma ina tunanin ta wuce Nafisa, ki sallamawa mai gidanki zan yi
magana da shi”

“Toh Yaya”

Ta tashi jikina na rawa ta nufi bangaren Appa, a nan Daddy ya samu gaisawa da Namra
yana tambayarta ya karatu.

“Ai na kare, next week zan tafi service Kaduna In Sha Allah”

“Abu yayi kyau, muna da bakuwa kenan”

Daddy ya fada sai ta yi murmushi tana jin farinciki jin cewar Captain ya hakura da
auren Hurriya. Kamar yayan mahaifiyarta Alhaji Munzali ya san dalilin farincikinta
sai ya bijiro mata da makamanciyar maganar.

“Aure fa Namra?”

Ta yi shiru ta noce kai kasa, Daddy yayi murmushi ya amsawa Alhaji Munzali yana
kare yarsa.

“Za'ayi a daga mana kafa mana Alhaji, komai ai lokaci ne za ayi babu jimawa In Shaa
Allah”

Yanayin yadda Daddy ya bada amsar sai ta ji kamar yana mata inkiya da auren Captain
ne, hakan ya kara fadada farincikinta.

“Alhaji Rufa'i ku taba wani abu mana, kamin nan da wasu shekaru Nafisa ta mana
gorin mun shago gidanta ba mu ci komai ba, kasan Nafisa akwai rike abu ga iya gori”

Sai duk suka saka dariya har Daddy da yayi maganar. Daddy ya dauki ruwa ya sha ya
ci yankan cake daya sauran kuma kowa ya ci abun da yake sha'awa even though ba san
da zuwansu ba abun da yake gidan na tabawa ne Namra ta kawo. Appa ne ya shigo dakin
yana sanye da Babbar riga irin ta Malam Bahaushe sky blue shaddar dake jikinsa har
wani kara take tsabar sabun taka, be zauna ba sai da ya mikawa Alhaji Aliyu Turaki
hannu biyu suka gaisa yana masa maraba da zuwa.

“Yau Yaya da kansa a gidanmu”

“To kai ma gorin zaka min kenan, daman ance idan zama yayi dadi miji yana daukar
dabi'un mata, mata ma tana daukar dabi'un miji”

Momy ta yi dariya tana zaunawa, Appa ma dariyar yayi ya mikawa sauran hannu suka
gaisa, sannan ya zauna.

“Toh Allah yasa ba laifi muka yi ba”

Appa ya fada, sai Daddy ya kalli Alhaji Sadiq ya ce.

“Ka gani ko? Ita ma haka ta ce mana”

Sai duk suka saka dariya har Namra, sai suka natsu sannan Daddy ya kalli Namra da
Momy ya ce.

“To Nafisa ke da Namra ku ba mu guri zamu yi magana”


Momy ta tashi ta wuce sama ranta fes, Namra ma ba laifi ta ji farincikin fasa auren
da Captain yayi a yanzu kuma ba zata iya fadar dalili ba. Sai da suka haye sama
gaba daya sannan Daddy ya kalli Appa ya ce.

“A cikin mu nan babu mai bukatar gabatar da kansa, musamman ma ni na san ni na baka
auren Nafisa da hannuna, domin ni mahaifinmu ya wakilta na bada aurenta a
madadinsa”

“Haka ne ranka ya dade”

Appa ya fada cikin girmama, domin bayan alakar auratayya Appa ya san waye Engr A A
Turaki a fannin naira da kasuwanci.

“Toh da farko dai na zo nan ne saboda na jajanta maka abun da ya faru da yarka, ba
abu mai dadi ba muna jajanta maka”

Appa ya sauke ajiyar zuciya ransa yayi masa babu dadi.

“Wani ne yake kokarin ganin ya mutuncina, domin wannan abun ni aka taba ba wai
Hurriya ba, kuma yarinyar nan ta da kur'ane a gaban yan'uwanta a gabana ta ce bata
aikata ba, sheri ne kawai na makiya, ba kuma zan bar maganar ba yanzu haka mun yi
da Lawyer na zai zo ya same ni yau mu tatauna matakin da ya kamata mu dauka”

Daddy yayi murmushi

“Wani suruki da baka san da zamansa ba har ya dauki matakin kai yaron DSS, ya riga
ka daukar mataki ina zaton be san ma Hurriya ta yi rantsuwa ba amman yana gaba gaba
gurin yarda da cewar bata aikata ba, kusan shi ne silar zuwana nan hankalinsa ya
tashi har yana zaton ko ka kore Hurriya ne?”

Appa yayi ma Daddy kallon rashin fahimta

“Aa ban koreta ba, Gwaggonta ta tafi da ita zata fi samun kulawa a can saboda
bakinciki abun da aka yi mata, ya taba ta sosai har ya zama jijiyar dake aika sako
a idonta zuwa kwakwalwarta ta tabu, idon ya rufe gaba daya”

“Duka sukurinka ya fada mana haka, babu kalar haukar da be mana ba akan Hurriya”

Wannan karon Alhaji Munzali ne yayi magabar. Appa ya kalli Daddy ya ce.

“Ranka ya dade ban gane inda ka dosa ba, Wallahi”

Daddy yayi murmushi ya sake yin murmushi sannan ya dora.

“Mun zo jaje ne da rokon iri, na baka auren kanwata yau kuma ina zaune a gidanka
ina nemawa ďana Captain Jamal auren yarka Hurriya.... ”

“Ranka ya dade Hurriya?.... Dan ka ranka ya dade..... Danka....”

Appa ya saka kalmar shahada yana jin abun wani iri a lokacin da be saka ran faruwar
hakan ba.

“Ranka ya dade Huriyya dai ko wata dabam a cikin yayana”

“Hurriya dai Alhaji Haruna...”

Daddy ya nanata masa, a gudun kuskure ko samun akasi Appa ya sake share gafe ya
shimfida musu abun da ya faru.
“Ita ce yarinyar na da kake maganar an yada hotunan ta fa”

“Za mu hukunta wandanda suka yi haka fiye da yadda kai zaka yi, kuma ina tabbatar
maka zamu rike da mutunci da girmamawa”

“Ranka ya dade Hurriya bata gani sam a halin yanzu da nake maka magana”

“Za mu nema mata lafiya kuma za a dace da yardar Allah”

“Allahu Akbar....”

Idon Appa ya cika da kwalla, ba dan baya iya yin abun da Daddy yace za su yi na
Hurriya ba, sai dan gata da ya zo mata daga Allah na mallaka mata AA Turaki a
matsayin suruki, a lokacin da duniya take zaginta kuma ta rasa idonta, aka nemawa
yaron da ake ji da shi a Family su aurenta.

“Ranka ya dade na baka, na mallakawa Captain Hurriya Halak Malak”

Daddy yayi murmushi na musamman yana farinciki da farincikin ďansa.

“Alhamdulillah... Amman Alhaji Haruna baka yi gaggawa ba? Ya kamata mu ji ta bakin


yarinyar ko tana son ďana”

Appa ya saka hannu ya tsargar da hawayen da suka so zubo masa.

“Hurriya yarinya ce mai tsananin Biyayya ranka ya dade, tana da gudun bacin rai ba
zata ki zabin mahaifinta ba, kuma na san ban zaba mata mugun abu ba, na san waye
kai kuma na san waye Jamal, babu uban da ba zai so Jamal ya zo masa a matsayin
suruki ba”

“Maa Shaa Allah na yi farinciki da jin haka, daman kuma na yi tsammanin samun haka
a gurinka, halinka na kirki shiyasa mahaifinmu ya baka auren Nafisa kuma
Alhamdulillah aure yayi albarka”

Appa yayi murmushi jindadi marar misaltuwa.

“Ranka ya dade idan ba zaka damu ba, zan yi ma ďana Yasir magana sai a daura auren
yanzu a nan”

Appa yayi hakan ne saboda yana ganin kamar labari zai iha canja ko kuma shedan ya
shiga ciki daga baya..

“Toh ka yi mana irin abun nan na iyayen zamani, hakan zai saka ďana a farinciki
sosai gashi kuma ba mu zo da sadaki ba, kuma ba a yanka mana”

“A biya sadakin daga baya”

Alhaji Sadiq ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin 100k ya aje.

“Wannan yayi?”

“Aa Jamal yace min yarinyar mai tsada ce, ya kamata mu siye ta da Ƙima, je ka yi
magana da ďanka, ni ma zan yi magana da Nafisa”

Appa ya tashi yana sauri ya fice daga falon cikin zumudi da murna. Daddy ya kalli
kanensa

“Alhaji Munzali a fita a samo mana goro da Dabino ko?”


“Toh Alhaji”

Alhaji Munzali ya tashi ya fice, Daddy ya daga wayarsa ya kira Momy, sai gata ta
sauko da far'arta domin zuwansa ya faranta ranta.

“Yaya har kun kare”

“Aa tukuna dai, Nafisa a cikin sarkokinki an zinarina wacece ta fi tsada?”

“Wanda na siye 50 million, ban taba saka ya na siye na aje ne dai kawai a matsayin
kaddara”

“Dauko min ita yanzu nan?”

Har ta yi kamar ta tambaya dalili sai kuma wata zuciyar ta nuna mata idan ta yi
haka bata kyauta ko ma minene ai zata ji daga baya. Sama ta koma ta shiga dakinta
ta bude akwaitin sirrinta da take aje yi kudi ta dauko sarkar dake cikin wani box
da shi kanshi abun kallo ne, tare da receipt dinta ta sauko ta aje ma Yayanta.

“Gata yaya”

“Shiga ciki zan kira ki idan na gama”

“Toh”

Ta juya cikin rashin natsuwa da tunani ta koma dakinta. Daddy na zaune a gurin Appa
ya shigo falon da saurinsa.

“Ranka ya dade Bismillah ga shimfida na yi a waje”

Daddy da kansa dauki sarkar ya miki tsaye tare da yan'uwansa suka fice daga falon,
babbar harabar gidan Appa ya shimfida Carpet, sai da Daddy ya fara zaunawa sannan
sauran suka zauna. Yasir ya ba su hannu suka gaisa daya bayan dayan sannan shi ma
ya samu guri ya zauna, Appa ya gayyato har da masu aikin gidan domin shaidar daurin
auren Hurriya a gurin aka daura auren, Daddy ya wakilta Alhaji Sadiq a matsayin
wanda zai karbawa Captain aure, Appa kuma da kansa ya bada auren Hurriya, bayan ya
karbi zinarin a matsayin sadakin Hurriya. Bayan an daura auren ne Alhaji Munzali ya
dawo gidan, ya fito mota ya bude bayan motarsa Appa ya saka masu aikin suka kwaso
goro da dabino, Daddy ya sa an fasa goro da dabino ya cire dabino uku da goro daya
ya saka aljihunsa, sannan yayi musahaba da Appa yan'uwansa ma suka yi.

“Ba sai mun koma ciki ba, rigimar Nafisa ba zan iya da ita ba a yanzu, zata ce an
yi komai ba tare da ta sani ba, ka sanar mata a madadina”

“Ranka ya dade na gode, Allah ya baka danka ikon riketa amana”

Appa yana rike da hannun Daddy yake fadar hakan.

“Ameen, babu kai babu mugun suruki da yardar Allah Jamal zai rike yarinyar nan fiye
da yadda kake fata”

Daddy ya kara tabbatar masa da yarsa bata shiga mugun hannu ba. Appa ya takasu tare
da Yasir har gurin motarsu suka shiga sannan ya koma ya cire dabino da goro ya nufi
bangaren Momy yana murmushi kana ganinsa ka san yana cikin farincikin da ya dade be
yi ba. Yasir ne ya rabawa mutanen da suka shaidin daurin auren a gurin sannan ya
dauki sarkar Zinarin da Appa ya ba shi riko ya shiga bangaren mahaifinyarsa yana
murna. A falo ya tararda Hajiya Kaltume da Khairy zaune a kujera daya.
“Hajiya kina nan har yanzu”

“Wallahi kuwa, ka ga tun da na raka Hajiya Fatee nake zaune a nan muna hira da
Khairy, wai kiran me mahaifinka ya shigo yana maka a gaggauce?”

Ya zauna saman kujera yana rike da kwatin na zinari.

“Auren Hurriya aka daura...”

Khairy da Hajiya Kaltume suka kalleshi jin abin banbaragwai.

“Baka da hankali wane irin aure kuma?”

Yasir yayi murmushi daman ya san ba lallai kowa ya ji ya yarda ba.

“Aure dai Hajiya, Wallahi aure aka daura mata yanzu nan, wasu ne suka zo tambayar
aurenta Appa ya ce ba za su tafi ba sai an daura auren”

“Allah sarki to su ba su da labarin abun da ta yi ne? Ko kuma yan'uwan Adam din ne


suke neman a rufawa juna asiri?”

“Ba su ba ne, yarinyar nan fa ta rantse Hajiya bata aikata ba, be kamata ki fadi
haka ba”

“To ko da bata aikata ba ai dai mutuncin ta ya zube, duk wanda ya aureta kila ba
zata wuce gobe ba zai sake ta, da alama ba su da labari ne, shiyasa suka zo shi
kuma Appanku yana neman a raba shi da abun kunya a dole ya rike su a daura auren a
gurin, ko dai shi yayi sadaka da ita? Wa ta aura dan baro ko dan shara? Ko cikin
masu ban ruwan fulawoyin gidan nan”

Yasir girgiza kai yana murmushi, ya bude akwatin zinari dake hannunsa.

“Wani ne mai daraja Hajiya, dan'uwan Momy ne da Zinari mahaifinshi yayi sadakinta,
na naira miliyan hansi...”

A take fitsari ďan tsirin ya kubucewa Hajiya Kaltume ta cire dankwalin kanta ta aje
a cinyar Khairy tana kallon zinarin kamar zata yaga ido....

**** **** **** ****

Bayan Daddy ya rufe motarsa, suka jero tare da yan'uwansa suna tafiya ya ce.

“Mahaifinta yayi dabara ni ma na jidadin haka, ka ga mun tsallake ma duk wani tarko
a yanzu, shi kan shi Jamal sau biyu ana saka ranar aurensa ana fasawa saboda fushi
da wasu hujjoji da ba su kai ba, mu kuma muna biye masa ne saboda farincikinsa muke
nema, amman yanzu ka ga wannan duk ya kau a yanzu”

“Gaskiya haka ya fi, ka ga an huta da fitinar Hajiya Turai”

“Daman fitinarta ai zan iya da ita, matata ce fa abun da dai nake tsoro ta canjawa
Jamal din ra'ayi gaba daya”

“Wannan gaskiya ne”

Cewar Alhaji Sadiq. A falon Nene suka zauna gaba dayansu, sai Daddy ya sa a kira
masa Captain dake dakin sama tun safe be fito ba, kamin ya fito Daddy ya kalli Momy
Ikilima ya ce.
“Ikilima ki shiga gurin Turai a cikin kayana akwai wata shadda irin wannan ta jiki
sabuwa ce a cikin leda, a dauko ta ta hado miki da sabuwar hula, da turaren da ba a
fasa ba”

“Toh Yaya”

Ta tashi ta fice, domin bangaren da Daddy yake sauka dabam idan ya zo gidan.
Fitarta da minti biyu Captain ya shigo falon, a kasa ya zauna ya gaishe da
iyayensa.

“Ya karfin jikin Captain”

“Alhamdulillah daman stress me kawai Abba na ji sauki”

Ya amsawa Alhaji Munzali, kamin ya daga kansa yana kallon dinkakkiyar Shaddar dake
Ikilima take mika masa, ya saka hannu biyu ya karba.

“Shiga ka yi wanka ka saka wannan shaddar ka feshe turaren nan gaba daya a jikinka”

“Daddy why?”

Ya tambaya da confused.

“Ina son ka raka ni airport ne kuma ina son mutane su ga yarona cikin mutunci, kuma
karka dade ka fito yanzu nan ina jiranka”

“Toh Daddy”

Captain ya mike tsaye ya fice daga falon na Nene. Dakin da ya zama masaukinsa ya
shiga ya cire tufafin jikinsa yayi wanka ya fito ya shafa mai ya saka shaddar ya
dauko turaren ya feshe jikinsa gaba daya sai da kwalbar turaren ta kai kasa sannan
ya dauki hula ya saka a kasan shi kansa, ya dubi kansa a jikin madubi shi kanshi ya
san yayi kyau abun da ake kira da kyau, farar shaddar ta haske shi matuka...
Wayarsa ya dauka ya saka aljihu da wallet dinsa sannan ya nufi kofar dakin ta bude
ya fita yana wani irin kamshi mai sanar da zuwansa tun kamin ya iso. Ga mamakinsa
sai ya samu babban falon na kakarsa a cike da mutane ciko har da mahaifiyarsa da
kakarsa da abokiyar zamanta da duka wanda yake gidan a lokacin. Da mamaki ya sauko
falon yana kallon kowa kowa kuma yana kallonsa...

“Zo nan Jamal...”

Daddy ya fada yana murmushi, Captain ya nufi gurinsa sai Daddy ya mike tsaye ya
saka hannunsa aljihu ya ciro goro da dabino ya ce.

“Bude min hannunka... ”

Captain ya bude tafin hannunsa na dama ya mikawa Daddy, sai Daddy ya zuba masa
dabino da goro dake hannunsa.

“Mun je jaje, kuma mun roki iri, kuma an ba mu, na nema maka auren Hurriya a yau,
kuma an daura mun bada zinari na miliyan 50, a matsayin sadakinta, saboda dka fada
mana mai tsada ce, shiyasa muka siye ta da kima, yau mai tsada ta zama mallakinka,
Hurriya ta zama matarka halak malak...”

Kamar an aje hoto haka falon yayi tsit kamar babu wani abu mai rai a ciki, daga
Captain har iyayensa babu mai motsi....
MASU KARATU BA BIYA A ZO A BIYANI HAKKINA A SAUKE NAUYI A HUTA

500 to Zenith Bank


Hadiza Abubakar
2451879008

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Da farinciki Appa ya shiga dakin Momy ya nufo inda take zaune fuskarsa da annuri ya
zauna gefen gado. Da mamaki yake kallonsa daman kam mamakin kiran da Daddy yayi
mata ya karbi sarka be gama fita mata ba.

“Alhamdulillahi”

“Allah abun godiya”

Ta amsa sannan ta kalli goro da dabinon da ya shigo da su gabanta na faduwa.

“So da yawa kanyi abu basan alherinsa ba sai a gaba, wani abun kuma Allah ya barwa
kansa sani, ban tana jin farinciki da alfahari da aurenki ba sai yau, Allah ua miki
albarka Nafisa sanadinki yau na fita bakinciki an shafe min duk wata damuwa da nake
jinta a raina saboda faruwar abubuwan nan”

Momy ta yi murmushin rashin gamsuwa.

“Daman ai Yaya akwai karanci, wani abun yayi maka ko?”

“Ďanki Jamal kuma dansa ya nemawa auren Hurriya, kuma be bar gidan nan ba sai da
aka daura auren”

Momy ta kyalkyale da dariya har da daga kafa sama da buga a kasa.

“Yau kuma ni ake yi ma zolaya, taya za'ayi daurin aure a cikin gida ba mu sani ba
kuma daga kai sai yan tairarun mutane? Kila dai aurenka ne za a daura ko kake min
kwano kwano”

Appa yayi murmushi mai kyau.

“Shi aure ai ba dole sai an tara mutane ba, amman amsu aikin gidan nan da yayanta
Yasir sun shaidin auren Hurriya aka daura da Jamal a yau, kuma yayanki ya bada
Zinari a matsayin sadaki”

Ya aje mata goro da dabino na daurin auren a gadonta.

“Kin ga goro da dabino nan!”

Ta kalli goron da dabino har lokacin dariya take domin maganar Appa ba magana ce
mai kama kai ba, sai dai kume? Appa ba zai mata wasa ba, ba zai ce anyi ba alhalin
ba ayi ba. A take dariyar ta bace mata bat ta daga kai ta kalli Appa.

“Da gaske Alhaji? Yayana ya zo gidan nan ya nemawa Captain auren Hurriya?”

“Har an daura, yace ba zai iya da rigimarki ba, dan haka ya wuce yace ni na sanar
miki....”

Momy ta mike tsaye wayar dake cinyarta ta fadi kasa.

“Aure Alhaji? Auren Hurriya aka daura da Captain?”

“Kwarai, kowa ya ji zai yi mamaki, kuma tabbas Alhaji Turaki ya kai mutumen kirki
har ya wuce, ya yaye min bakinciki kuma na yarda zai rike yata da amana”

Momy ta dafe zuciyarta.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un


La'ilaha Illallahu Muhammad Rasulullahi Sallalahu Alaihi Wassalam”

Appa ya bita da kallon al'ajabi ganin yadda ta yi kamar wadda aka fadawa mugun abu.

“Yanzu duk matan duniyar nan Captain ya rasa wa zai aura sai Hurriya? Yarinyar da
duniya ta gama ganin tsiraicinta? Yarinyar da ko ido bata shi a yanzu? Anya Captain
yana cikin hayyacinsa?”

“Ita Hurriya ba mace ba ce? Da kike fadar ya rasa wa zai aura sai ita? Wane irin
magana kike haka ne Nafisa?”

“Captain ya fi karfin Hurriya bata cancance shi ba, rantsuwa fa na yi cewar Captain
ba zai auri Hurriya ba, shi ne Yaya zai shammace ni? Kuma ya biya sadakinta da
zinarina da ban taba sakawa ba? Naira miliyan hansi akan makauniya yarinyar da
duniya ta gama da ita?”

Appa ya mike tsaye ya daga hannu kamar zai mari Momy sai kuma wata zuciyar ta hana
shi, a madadin haka ya nunata da yatsansa.

“Ki san abubuwa da kike fada akan Hurriya, kamar kin mace a gaban waye kike tsaye
ni fa na haifi Hurriya, a madadin ki yi farinciki jininki ya auri jini sai ya zama
abun bakinciki a gurinki”

“Idan kai ne mahaifin Hurriya sai me? Na yi farinciki ďan ďan'uwana ya dauko yar
kishiya ya kawo a matsayin suruka? Ya tsallake Namra ya tsallake duk yaran family
ya fada gurin Hurriya”

Appa yayi murmushi yayi girgiza kai.

“Yanzu na fahimci komai, Allah ya huci zuciyarki yara kuma Allah ua ba su zaman
lafiya... ”

Appa yayi dariya mai sauti ya fice daga dakin. Momy ta dora hannu a kai tana ta
rawa kamar mai jin sanyi.
“Daman wannan ne dalilin zuwa? Har kana fada min Captain ya hakura? Ni kake yi ma
wayon Yaya? Ko ba zai auri Namra ba me yasa zaka amince masa ya auri Hurriya? A
cikin falona za a nemi auren yar kishiyata ba yata ba, duk tarin dukiyar Yaya da ta
matarsa ďa ďaya da suke ji da shi ya rasa wa zai aura a duniya sai Hurriya?
Yarinyar ido ya rufe mata? Aka tallata tsiraicinta, yarinyar da uwarta ma ga aiki
ta yi, talakawa maskakanta, tarin dukiyar Yaya Yau Hurriya ce yarinyar da zata raba
a jiki a dukiyar gidanmu, kuma ta bangaren da ya fi gwabi”

Daki cinyarta tana jin kamar ta zaga tufafin jikinta, a matukar fucece ta fice daga
dakin ta shiga dakin Hurriya ta fara yaye Bedsheets dinta ta jefar tana debo
kayanta ta watsarwa abubuwan da ke fashewa kuma tana ta fashe su tana watsar tana
kuka.

“Ashe sheri ne ya kawo ki bangaren nan, ashe mugun abu na karba na aje gashi nan
kina bibiyata”

“Momy lafiya”

Namra ta tambaya tana kallon yadda ta watsar da kayan Hurriya ta fasa abubuwa. Momy
ta juyo a lokacin da ta kalli Namra sai tausayin yarta ya kamata.

“Yayana ya daureni ya ci amanata Namra, na ci mutunci na ya watsa min kasa a ido,


kuma ya nuna min ďansa ya fi yar'uwarsa”

“Momy dan Allah ki fada min me ya faru?”

“Auren Hurriya ya nema a gurin Appanku, Appanku kuma ya amince aka daura auren a
cikin gidan nan yanzu nan”

Namra ta ji kanta ya dara da karfi.

“Aure abun kamar yar tsana? Ban gane aka daura ba, an taba daura auren haka babu
kowa?”

“Daga mahaifinku sai Yayana da Yasir aka daura auren”

Wani abu ta ji mai sanyi ya ratsa kanta ya sauko har kafafuwanta.

“Momy da gaske...?”

“Me zai sa na miki karya.? Yaya yayi min abun da ban yi tsammani ba, da ace wani ne
yayi min ba yayana ba zan ji zafi haka ba, amman ba komai kowa yayi mai kyau zai
gani kuma Wallahi Hurriya ba zata sake zama bangaren nan ba”

Namra ta yi baya baya ta fice daga dakin daman a bakin kofa take tsaye. Dakinta ta
shiga ta rufe kofar ta zauna hawaye suka silala mata a hankali.

“Aure?”

Ya tambayi kanta abin dai kamar ba zata fahimta ba. Shi ke nan duk wani fata da
take da kuma wanda iyayensu suke yi ya tashi a banza yanzu? Hurriya ta shiga
tsakaninta da Salim yanzu kuma ta raba ta da Captain ta aureshi? Ta mike tsaye ta
isa gaban madubin dakinta ta zauna a stool tana kallon kanta, shi ita bata kai ba
ne da Captain be yi hauka a kanta ba? Taya idonsa zai rufe ya tsallake ta ya fada
kan yar'uwarta bayan duk abun da ya faru da Hurriya, to da bata aikata ba ai ta yi
abin kunya, ta yi abun da cikaken namiji mai aji irin Captain zai guje ta zama
matarsa ko dan saboda kunyar duniya. Salim ma ya kusa hauka akanta amman Captain ya
goge mata hadda, ta saka hannayenta ta share hawayenta har yanzu jin take kamar dai
ba gaske ba ne. Momy ta turo kofar dakin ta shigo ita ma tana kuka.

“Auren nan ba zai je ko'ina ba, Captain da yake da zuciya da saurin fushi kwana
biyu ne zata fita ransa, kuma na san Hajiya Turai ba zata yarda ďanta ya aikata
wannan abun kunyar ba, aure ba zai je ko'ina zai lalace”

Namra ta mike tsaye da sauri ta shige bandakinta domin bata son Momy ta ga kukanta,
ganin take bata cancanci zubar da hawaye akan namiji ba, sai dai wadannan sun zame
mata dole ne. Zaunawa ta yi a kasa bayan ta rufe bandakin tana kuka marar sauti.
Momy na ganin hakan ta san yar gudaliyar yarta kuka bakinciki take, ita ma sai
rauninta ya karu, jikin bandakin ta tsaya tana buga kofar.

“Namra bude kofar karki saka kanki a damuwa kinji, na san babu dadi amman ki yi
hakuri karki wa damuwa kofa dan Allah ki kwantar da hankalinki, ni kaina ba zan bar
maganar nan ba ba zan kyale lamarin nan ba”

Kalaman na Momy sai suka zama kamar makamashi mai hura wutar bakincikin dake
zuciyar Namra, sai dai hakan be saka ta bude kofar ba, har Momy ta gaji da tsayuwa
ta fice daga dakin, tana shiga dakinta mayafi ta dauka da key mota ko jaka bata
tsaya dauka ba ta nufi family house dinsu.

CAPTAIN JAMAL POV.

A hankali ya fara rankwafa yatsunsa har ya jimke dabinon dake hannunsa yana kallon
Daddynsa har lokacin an rasa mai cewa komai. Daddy yayi murmushi yana kallon dansa
cike da alfahari kamar yadda Captain din ma yake kallon mahaifinsa ya kasa gasgata
kalamansa.

“Da alama dai kuna bukatar na maimaita kaina, abun da nake nufi a nan.... ”

Ammy bata bari ya fadi ba ta mike tsaye cikin tsawa da hargagi ta ce.

“No bana bukatar ka maimaita mana sautin da fadij mutuwa ya fi shi dadin ji”

Ta tofar da yawu.

“Touf! Allah ya tsare gatari na da saran shuka, har abada ďana ya fi karfin
wulakantacciya yarinyar yar talaka kuma wanda duniya ta gama ganin tsiraicinta
Wallahi”

Alhaji Sadiq ya mike tsaye tana dagawa Ammy hannu.

“Hajiya Turai sai dai hakuri amman Wallahi an daura auren Jamal da Hurriya yau,
idan baki yarda ba ki kira Nafisa ki tambaye ta”

Ammy ta kalli Daddy da sauri tana son kara tabbatarwa. Captain yayi murmushi ya
rufe idonsa har lokacin hannunsa na rike da dabinon ya kasa maida hannun kuma ya
kasa sauke shi kasa.

“Munafuntata ka yi Captain? Ka ce min ka hakura kuma sai ka juya ka shirya wani


abun da mahaifinka?”

Cikin kuka Ammy take tambayarsa, sai ya bude idonsa da sauri ya kalleta raunace.

“Wallahi Allah ban san komai akai ba Ammy”

Hajiya Turai ta juyar da dubanta gurin Daddy.


“Saboda me? Saboda me zaka aura masa wannan yarinyar? Be fada maka ya hakura ba?
Baka duba illar hakan ba a cikin zuri'arka?”

Daddy ya daga mata tsaya uku yana nuna mata daya vayan daya.

“Saboda na isa! Saboda yana sonta!! Saboda Allah be haramta ba!!! Kin ga dalilin
nan uku su suka saka na je na nemi auren Hurriya a yau, mahaifinta kuma ya bukaci a
daura auren a yau”

“Ikon Allah abu dai kamar a shirin film?”

Cewar Nene, Momy Ikilima ta ce

“A littafi dai wannan ai ya fi karfin shirin film”

Ammy da idonsa ya cika da hawaye har wasu za su zubo ta hau masifa.

“Da alama baka yi bincike ba kamin ka aura masa yarinyar nan, mahaifiyarta aikin
gida ta yi fa!, ni ba zan iya karbar ta a matsayin suruka ba, ba zan ina nunawa
duniya yarinyar nan a matsayin matar Captain ba”

Daddy nade babbar rigarsa.

“Kin gani Turai ba a daura auren yarinyar da Jamal ba sai da na yi ma mahaifina


alkawarin zan rike yarsa da mutunci da amana, kuma a matsayinki na matata idan ba
ki taya ki cika alkwarin nan ba, to be kamata ki barar da shi ba, karki zuga kanki
da yawa ki kone kanki ta hanyar haramta abun da Allah ya halatta, hargaginki da
kumbar baki ba zai saka Jamal ya saki yarinyar nan ba, domin ba je na auro masa yar
mutune saboda ya zubar min da mutunci ba, ina ce Alhaji Haruna ma yana da kalar
nasa rufin asirin idan kuma kin raina arikin gidansu ne yanzu danki take aure make
her a billion naira”

“Wayyo Allah na wannan wane irin abun kunya abun bakinciki ne? Kenan duk abun da
Jamal yake so sai mu biye masa mu aikata ko da halaka ce? Yarinyar da kare da mage
suka maganin siraicinta, ita zaka hannu biyu mu karba a matsayin in-law?”

“Wannan kuma ďanki kike ci ma mutunci a gaban familynsa, ina jiye miki tsoron ranar
da zaki yi nadamar nuna son zuciya fiye da abun da danki yake so, ki shirya da wuri
karfe biyar jirgina zai tashi”

Daddy na kaiwa ya kabe rifarsa ya fice daga falon, Hajiya Turai ta kalli Nene da
kowa dake falon tana kuka.

“Nene kina gani? Babu wanda zai ce komai ni za a bari da fadan nan?”

“Hajiya Turai me kike son mu ce? Aure ne an riga da an daura, sakawa zamu yi
Captain ya sake ta ko kuma mijinki zamu rufe da fada, kowa a nan yayi mamaki amman
abun da kaddara ta aiko dole mu karba mu zuba ido mu ga abun da Allah zai yi a
gaba”

Cewar Alhaji Munzali, kamin ya mike tsaye ya fice daga falon. Alhaji Sadiq ne kadai
yake lallabata.

“Ki yi hakuri Hajiya Turai, ki bi abin da danki da mijinki suke so, ki zuba ido ba
fata muke ma amman idan akwai illa a cikin lamarin nan za su gani a gaba kuma su
gane sun aikata kuskure, Jamal dai shi yake auren yarinya shi yake jin zai iya
daukar komai da ya shafe ta to ke mike naki a ciki? Ki yi hakuri a matsayinki na
uwa ki danne duk abun da kike ji dan Allah”
“Ba zan iya ba Alhaji Sadiq, Engr ya nuna min ba ni da muhimmanci a rayuwarsa da ta
dansa, shiyasa be duba shawarata ko ra'ayina ba ya aikata abub da ya aikata”

Ta fice daga falon tana kuka, Hajiyar Maru wacce ta kasance abokiyar zaman Nene ta
bi bayanta tare da Momy Ikilima, Alhaji Sadiq da Alhaji ya dafa kafadar Captain
yace

“Ka dauko wani aiki mai nauyi Jamal, idan baka yi hakuri ka kai zuciya nesa ba ba
zaka iya karasa ba, ka bawa kowa hakkinsa matarka da mahaifiyarka, Allah ya bada
zaman lafiya ya hada kanku”

Ficewa suka yi daga falon sai ya rage daga Captain sai Nene a falon har jikokin
Nene yan matan da kanana duk babu ko daya.

“Ka yi hakuri Jamal kowa ya ce zai iya sai an gwada aka ko zai iya dauka saboda
haka ka saka kana'a a zuciyar.... ”

Sakin baki ta yi tana kallon ikon Allah ba tare da ta karasa maganar ba. Gira
Captain yake daga masa ya sumbanci goro da dabino da Daddy ya ba shi, sannan ya
zuba shi a alijihu ya bude babban rigarsa yana nufar ina da take da rawa. Nene ta
rike baki.

“Ah...ah... Ah... Ja'irin yaro? Wato ni ka raina ko? Kake min rawa me yasa baka yi
ba a gaban iyayenka”

“Su ai iyayena ne, ke kuma kakata ce my first wife my kalbi”

“Tsohon makiri, amman tsaye ka yi a gabansu ba wani murna ba komai kamar wanda aka
yi ma auren dole, ashe kana so....”

Ya kyalkyale da dariya ya sumbanci kumatunta.

“Nene na godiya da kika haifo min gwarzon namiji kamar Daddy, ba dan shi ba da
yanzu na rasa yarinyar nan”

Nene ta kai masa duka a fuska.

“ja'irin yaro, amman kai da gaske baka ganin illar abun da yarinyar nan ta yi?”

“Bata aikata ba sheri aka yi mata, kuma asiri zai tonu nan ba da jimawa ba, kowa be
wuce kaddara ba hakan zai iya faruwa da ni, ko da wani a cikin jikokinki sheri ne
aka yi mata saboda a lalata sunanta”

“Haka ne, abun kam babu dadin ji babu dadin fadi, amman na tausaya mata matuka”

Captain ya daga hannayensa sama fafaren hakoransa na bayyana yayi ma Allah godiya.

“Allah ka ba ni ikon kyautata ma yarinyar da daukar nauyinta yadda ya dace, ka ba


ni ikon faranta mata, ka taimaka min gurin tarbiyarta da na yaran da zamu haifa
Allah, ya Allah ka karkato da zuciyar mahaifiyata da hankalinta ta fahimce kuma ta
so abun da nake so, Allah ya ba mu zaman lafiya ka kawar da shaidan da mahassada a
wannan aure”

“Ameen”

Nene ta amsa masa tana kallonsa cike da burgewa.

“Kana da hankali matuka Jamal, ba dan kana jikana ba hakika wannan yarinyar ta yi
dacen miji, matukar ba zata fusata ka ba to zaku zauna lafiya da ita”

“In shaa Allah Nene”

Ya kara taka mata rawar sai a lokacin yake jin wani kalar farin ciki da be san a
muhalin da zai aje shi ba, a lokacin ne wani shaukin auren da annashuwa da zumudi
suka same shi. Hanyar da dakinsa yake ya nufa yana tafe yana gyara babbar rigar
abun ka da wanda be saba saka manya kaya irin wannan ba. Agaban madubi ya zauna
yana shafa fuskarsa ya dauki ragowar tutaren ya feshe a jikinsa, wani irin yanayi
yake jin kansa da be taba samun kansa a ciki ba, yanayi ne dabam da yake zuwa sau
daya a rayuwar ko wane saurayi fa budurwa, yanayin da kan canja yanayin ango da
Amarya tun daga yanayin gari har zuwa na hallita da mu'amala da kuma na iskar da
aka shaka. Hoton da ya dauka na Hurriya ya kama a wayarsa yana kallo yana shafa
screen din da hannunsa.

“You're the only thing i want touch.... Kin kawo ni a wata duniya da ban yi
mafarkin zuwanta a kusa ba, kin haska min abubuwa da yawa da duhun watan soyayyarki
bata bari na gani ba, zan baki kyauta duniyar dake cike da haske da farinciki sai
na dawo miki da abubuwan da kika rasa, bakinciki da kike ciki zan maye miki
gurbinsa da farinciki, zan canja shafin rayuwarki har ki bata damuwa baya, zaki
gode Allah ki yi alfahari da ya baki ni a matsayin miji.... QURRATUL AYN (meaning
Delights Of The Eye, Darling, sanyin idaniya...)”

Ya sumbanci hoton sannan ya dorashi a kirjinsa ya rumgume ya lumshe ido yana


murmushi, a zuciyarsa yake ayyana Hurriya tsaye a gabansa tana kallonsa da murmushi
a fuskarsa fararen tufafi sanye a jikinta.

“Ya... Ya... Ya... Na.. ”

Ya ji yana fitowa between her soft lips tana motsa halshenta a hankali.

“Uhmmm..... ”

Ya bude ido yana amsawa, a nan ya gane imagination ne yake ba gaskiya ba, murmushi
yayi mai sauti ya cige bakinsa ya maida idonsa ya rufe yana jin kamar ace yana da
damar ganin Hurriya a yanzu.

HAJIYA KALTUME POV.

“Hurriya fa ka ce Yasir ko dai zolayata kake?”

“Taya zan zolaye ki Hajiya? Ga abun da yake zahiri, goro da dabino suna waje, idan
baki yarda ba ki tambayi Appa ki ji”

Hajiya Kaltume ta juyo ta kalli Khairy da ke kallon sarkar kamar wanda ta yi arba
da wani abun tashin hankali.

“Da wannan sarkar aka biya sadakin Hurriya? Wanene? Be san abun da yake yawo a gari
ba ne Yaya?”

“Ba za su rasa sani ba, wata kila ma shi ne dalilin da yasa suka zo neman auren a
yanzu, kuma zai iya yiyu ba su sani ba din ko ma dai minene an riga da an daura
fatan mu Allah ya bada zama lafiya”

Ya karasa yama dauko wayarsa daya dake aljihu ya amsa kiran Appa.

“Hello Appa... Eh tana hannuna okay gani nan zuwa”


Ya mike tsaye ya rufe sarkar.

“Appa yake kirana, yace ma kawo masa sarkar”

Ya nufi kofa, Hajiya da Khairy suka bi shi da kallo kamar wasu kauyawa. Hajiya
Kaltume ta kalli Khairy

“Anya Nafisa ta sani kuwa? Sadaki da sarkar zinari?”

“Abun kamar hankali ba zai dauka ba Hajiya, duk wannan cecekucen da ake akan
Hurriya ace wani ya zo ya aureta a rana daya kuma ya biya sadaki mai yawa haka?”

“To ni ma mamakin abun nake, abun dai kamar a mafarki”

“Kuma Wallahi idan wanda nake zargi ne dan Alhaji Turaki Hurriya ta warke Hajiya,
kin san yan'uwan Momy babu talaka balle kuma AA Turaki”

“Shin waye be san ubansa a kasar nan ba? Wai ko mafarki na ke dai”

Ta mari kanta baren dama ta koma hagu ta mari kanta ya mursa idonta ta hade yawu.

“Kuma fa ta makance kuma ya yarda zai aureta ko dai asiri aka masa?”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta dauki dankwalinta a hannu, ta nufi sama. A gurin da
wayarta take aje ta dauka ta kira number Hajiya Fatee.

“Sallamu Alaikum”

“Ba sai na amsa sallamarki ba balle gaisuwa, Hajiya Fatee duniyar nan fa tana
shirin rikice min, wai ashe motocin da kika gani dazun sun shiga bangaren Nafisa
neman auren Hurriya aka zo?”

“Hurriya? Ko dai Namra?”

“Hurriya dai da kika sani yar wajen Iyami... Kuma Alhaji ya ba su ba su bar gidan
ba sai da aka daura auren”

“Ina na taba jin abu haka? A bada aure kuma a daura a take? Anya mutanen kwarai ne
kuwa ko da yake Mahaifinta yana neman a raba shi da abun kunya ba dole ya amince
ba”

“Ba auren ne abun mamaki ba, wanda ta aura ne da kuma wanda ya zo nemam auren ne
abun mamaki”

“Toh... Wata kila dan fashi ne ko ko kuma masu yankan kai, domin su ne kadai za su
iya runtse ido su auri Hurriya a yanzu, ganin manyan motoci ba shi ke nuna mai
daraja zata aura ba wata kila ma ba zai wuce mai sharar gidan masu arziki, ya
walkilta mai gidansa nema masa aurenta”

“Alhaji Aliyu Turaki ne fa Hajiya Fatee, Yayan Nafisa, ya zo neman aurenta.”

“Oh... To... Wata kila yaron gidansa ya yi ma kara ko kuma ubanta ya nemo mai raba
shi da abun kunya ayi hadaka, ke waya sani ma ko tsoho ne za a hada ta saboda su
basa kunyar auren ko wace mace Sugar daddys din nan da kike ji da gani”

“Wannan saurayi ne sabo dal a cikin kwali, ďan Alhaji Aliyu Turaki ne wanda yake
zuwa gurin Nafisa, ina kare miki zance da zinari aka yi sadakinta na naira na gugar
naira har naira miliyan hansi....”
Hajiya Fatee ta amsa da karfi.

“Ke.... Hajiya Kaltume... Hurriyar? Har kin sa cikina ya murda”

“Ai ni fitsari kubce min suka yi, yar Iyami? Sauran yaran gida ba a musu ba sai ita
da duniya ta gama wulakantawa? Zama be gan ni ba Hajiya Fatee wannan yakin ba na
uwar Hurriya kadai ba ne har da Hurriya, Wallahi ba zan yarda ta fi yayana more
rayuwa ba, bayan duk abun da uwarta ta yi min? Ta aure min miji ta zo ta yi miki a
gidana yanzu kuma ta tafi yarta zata taka nairar da ta fi ta ubanta, yar mai aiki?
Uwarta ta mallake min miji ta yi yadda take so ita kuma yanzu ta take mu koma
karkashin inuwar ta muna daga kai mu nunata?”

“Ke ni fa wani abun ma mamaki yake ba ni, anya zuri'arsu suna barin namiji a banza
kuwa? Idan yaron be da hankali kuma iyayensa sai suka yarda? Ko da ba yaron kwarai
ba ne?”

“Captain ne fa na Soja, Nafisa ma jinsa take ballw iyayensa, kuma ko bayan haka
idan ta aure shi ai ta take, nan gaba sai a fara lissafi da ita a cikin yara kanana
masu arziki, Hajiya Fatee bana son Iyami bana son zuri'arta dan haka bana fatan
wani abun farinciki ya same su”

“To yanzu me ye abun yi?”

“Abun yi ki shirya gobe a gidanki zan yi karin kumallo, mu kama hanyar kauyen nan
muje mu samu malamin nan da kanmu, idan be fara aiki ba ya tada idan kuma ya riga
da ya fara a kara fetur hayaki ya baibaiye ko'ina a rikita Iyami da iyalinta a
karkato da hankalin mijina gareni”

“Amman fa ina tsoron kauyen nan Hajiya Kaltume kin san fa irin wahalar da muka sha
wacan karon, mussamman ma ni da kanana yara suka haikewa har da guziri na yo, ko
dai aika zamu yi?”

“Wannan zuwa da kai ne ya fi aike, yadda hankalina yake a tashe idan ban je garin
nan na yi magana da Malam ba na hura masa wuta ba zan samu salama ba, duk wani
tsoro ya kau min a yanzu, ai sawun giwa ya zarce na rakumi, idan ma ba zaki je ba,
ni zan shirya ma tafi”

“Aa ba zan bari ki tafe ke kadai ba, idan kin zo zamu tafi tare”

“Sai na shigo”

Ya katse wayar tana daga zanenta ta duba fitsarin da ke bin kafarta har lokacin
mararta ta kasa rike su.

“Dole, wannan tashin hankali da me yayi kama? Ina ga Iyami ta dawo gidan nan kuma
yarta ta auri mai kudi? Goma ta hadu da ashiri, rayuwa ta samu kenan”

Ta jefar da wayar akan gado.

“Ba zan taba bari ba, ba za a mareni a tsinka min jaka ba... ”

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Hajiya Binta ya jinjina kai tana kara girmama labarin Allah, a duk lokacin da ake
son mutun ya kunyata idan Allah yana tare da bawa ba a taba ganin abun da ake
bukata, kariyace da sakamako mai kyau tare da kyau da kariya mai yawa daga Allah
zuwa ga bayinsa da suka rike shi kuma suka dogara a gareshi.

“Duk wanda ya aikata wannan abun ya aikata ne saboda ya ci mutuncin Hurriya ya ci


namu, ashe be sani ba yana kara kusance da mata da alheri ne”

Appa yayi murmushi a yayin da yake zaune a kasa rike da sarka ya kalli Yasir dake
gefensa ya mika masa sarka.

“Budewa Hajiya ta gani”

Yasir ya karba ya mike tsaye ya bude mata sarka, Hajiya Binta ta saka hannu ta
karba idonta na cika da hawaye.

“Allah na gode maka da ka nuna min wannan ranar, Allah ka sakawa wannan auren
Albarka, kuma ka nuna min na sauran yaran”

“Amin Hajiya Amin”

Appa ya amsa da kansa, fadar irin farinciki da yake ciki a yanzu bata lokaci ne,
farinciki da yake a yanzu ya fi wanda ya samu kansa a lokacin da aka haifo masa
ita.

“Be kamata mu zauna ba Tsoho tafiya zamu yi mu sanar gidan mahaifiyarta da kuma ita
yarinyar halin da ake ciki”

“Haka ne... ”

A nan kam sai yanayin Appa ya canja, ya sauke kai kasa damuwa na bayyana a
fuskarsa. Yasir ya aje sarkar zinarin dake hannunsa ya mike tsaye ya fice daga
dakin yana taba wayarsa. Appa ya bishi da kallo har ya fice sannan ya juyo da kansa
ta inda Hajiya Binta take zaune ya ce.

“Ina jin kunyar hada ido da mahaifiyar yarinyar Hajiya, abun da na yi mata ban kyau
ba, be kamata na aikata hakan ba, ban san me yasa na sake ta ba, kuma na kasa samun
dalilin har yanzu da muke maganar nan dake, Iyami bata min komai ba face biyayya da
kyautatawa, amman na saka mata da mafi munin sakamako na juya mata baya na
wulakanta yaran da ta haifa min”

Ya shigar da lips dinsa duka biyu a bakinsa ya rufe dantse bakin zuciyarsa na ƙuna
da abun da bakinsa yake furtawa.

“Alhamdulillah, ganin ka gane kuskure ni a gurina abun farinciki ne, babu daren da
bana addu'ar Allah ya baka ikon gane gaskiya, domin abun da ka aikata kamar baka
aikata shi cikin hayyacinka ba”

“Ban san me ya rufe min ido na aikata haka ba, ina jin nauyin iyayenta da ita kanta
Iyamin a yanzu”

“Ka kawar da komai a ranka, daman shi aure ya gaji haka, a tsaba kuma a shirya ko a
yanzu dare be maka ba, lokaci be kure ba zaka iya gyara inda ka yi kuskure ka share
inda ka bata, kar wannan jin nauyin ya hanaka sanar da yarka Hurriya cewar ka bada
aurenta a yau, kai da kanka nake son ka fada mata wannan”

Ya amsa mata da kai sannan ya mike tsaye yana hade rigarsa.

“Zamu jiraki a waje Hajiya sai ki shirya mu tafi”

“Toh...”

A waje suka jira Hajiya ta fito tana rike da sadakin jikarta, ta shiga baya Appa da
Yasir kuma suka shiga gaba. A motar Hajiya sai godiya take yi ma Allah na yadda ya
kawo auren Hurriya a kusa kuma da mutumen da ba ayi tsammani ba, Appa kuma fargaba
da kunya na lullube shi a yayin da Yasir yake kara kusanta gidansu Gwaggo.

“Ni na manta ban tambaya ba, yaron dai yana da kirki ko? Murna da farinciki sun
mantar da ni wannan”

“Ba shi matsala Hajiya na san shi, yana da kirki kuma babu wanda zai fadi sherinsa,
Hurriya ta yi dacen miji fatan mu dai Allah ya bata lafiya kuma ya basu zaman
lafiya”

Hajiya Binta farinciki sai ya kara ninkuwa, ta kara yi ma Allah godiya.

HURRIYA POV.

“Wannan jaraba da kuke ta fadawa Allah ya yaye muku, idan wannan ya wuce sai kuma
wani ya zo, ke kin tashi baki ya bude ita kuma ido ya rufe”

Gwaggo ta kalli Hindu wanda ke kallon Hurriya tana lalaben gini har ta iso gurin da
Amma take zaune tare da Gwaggo da kawar Amma wato Hindu ta zauna.

“Abun da Allah yayi annabi sai ceto, likitocin sun ce wai damuwarce ta taba mata
ido, amman ni ban yarda ba na fi zaton wani aikin ne aka yi mata idon ya rufe gaba
daya, gashi an yada hotunanta kin ga shikenan an gama da rayuwarta, ba ido balle ta
yi karatu ta gina kanta kuma babu wanda zai aureta a haka”

Hindu ta rafka uban tagumi.

“Oh Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, wannan mugun kishi da me yayi kama? To ko


ita ma za mu nema mata taimakon a gurin da aka nemawa Amma? Tun da gashi dai mun
fara ganin haske”

Amma ta kama Hurriya ta kwantar da ita a cinyarta hawaye na sauko mata.

“Mun dai ga haske Hindu, Wallahi ban dauka zan iya kara yin magana ba, na dauka
kalmaina sun kare a duniyar nan, ina kallon abu na zan iya cewa a bani ba, ina da
maganganu da yawa a bakina amman ba zan iya furta ko daya ba, bana iya motsa jiki
bana iya komai, amman ki duba yanzu magana fa nake yi, bana jin karfi a jikina
sosai amman Alhamdulillah na gode Allah”
“Shi ma duk zai bari da yardar Allah, lafiya daman da rarafe take shiga a jiki har
a tashi tsaye, ciwo ne yake jefar da mutum farat daya”

Cewar Hindu. Kamin su daga kansu gaba daya su kalli kofar gidan, Hajiya Binta ce ta
shigo Appa yana bayanta sai Yasir a bayan Appa.

“Sallamu Alaikum”

Gwaggo da Hindu suka amsa mata, Amma kuma ta sauke kai kasa tana nadamar kallon
Appa da ta yi kamar wanda ta yi arba da bakin maciji.

“Maa Shaa Allahu, Iyami ce a waje? Haka nake so lafiya ta samu”

“Alhamdulillah, Rukkaya dauko tabarma ki kawo ma baki”

Gwaggo ta amsa tana bawa Rukkaya umarni. Appa ya kasa daga ido ya kalli kowa kamar
wanda ya aikata abun kunya. Rukkaya ta fito rike da tabarmar ta shimfida kusa da
wanda Amma take zaune. Hajiya ta fara zaunawa sannan Appa Yasir, daman haka
tarbiyar take, sai iyayen sun fara zama ake zama, idan kuma suna zaune ba ka tsaya
a kansu ba sai dai rankwafa ko na zauna a kasa.

“Jama'a ina kwananku ko wuni zan ce domin dai yanzu ai 12pm ta yi”

“Lafiya Kalau Hajiya ya gidan”

Gwaggo ta amsa ba yabo ba fallasa. Appa ma ya mikawa Gwaggo gaisuwa, ba dan yana a
gaban Hajiya Binta ba da kuma tunanin dalilin zuwansa wata kila da ba zata amsa
gaisuwar Appa ba.

“Lafiya Kalau”

Amma ta daga kai ta kalli Rukayya dake zaune ta ce.

“Dauko min hijabina Rukayya”

A rude Appa ya dago kai ya kalli Amma, Hajiya Binta ma ta kalleta Yasir ma
kallonta, dukansu sun yi turus suna mamakin jin furuci ya fito daga bakinta.

“Iyami kina iya magana yanzu?”

“Allah ya nufa Hajiya”

Amma ta guntun murmushi tana amsawa Hajiya Binta dake rike da baki.

“Allah da iko kake, kai Alhamdulillah yau farinciki ya mana yawa”

“Amma....”

Yasir ya kirata sai ta kalleshi ta yi murmushi ta amsa.

“Na'am Yasir”

“Alhamdulillahi”

Wannan karon Appa ne ya jaddada godiyarsa ga Allah yana kallon Amma, irin kallon da
ya dauki shekaru be yi mata ba, nadama da damuwa bayyane a fuskarsa karara.
Rukkayya ta kawo Hijab ta mikawa Amma, sai Amman ta karba ta saka domin tana ganin
Appa da Yasir ba muharramanta ba ne a yanzu.
“Hurriya ta so mahaifinki na son magana da ke”

Hurriya ta amsa kiran da Hajiya Binta ta yi mata ta tashi zaune, sai ta lalaba ta
matsa gurin da Hajiya take ta zauna, Appa ya kai hannayensa ya kama nata hannayen
ya juyo da ita ta fuskance sai ta nade kafafuwanta irin zaman da musulunci ya koya
mana yayin da zamu ci abinci, wato ta nade kafafuwanta tana fuskantar mahaifinta.
A lokacin da Appa ya kalli yarsa sai tausayinta da kaunarta da kuma kunyarta a
lokaci daya mamayeshi. Ya sauke ajiyar zuciya sau uku sai a hudu ya samu damar hada
kalmomin da zai gamsar da yarsa da su ya hada guri daya ya fara magana.

“Hurriya na san kin san cewar ni mahaifinki ne, a cikin abubuwan da Allah ya dora
min nauyinsu akwai ciyar da ke da shayar da ke da tufatar da ke da halak, idan kuma
kin kai munzali Annabi yace na zaba miki mijin na kwarai wanda na yarda da addinsa
da dabi'arsa kuma mai abun yi. Ban sani ba ko na kokarta a tarbiyarki, wata kila na
yi jarumta a ciyar da ke da tufatarwa, ba zan gane hakan ba sai ranar alkiyama, a
cikin kokarin sauke nauyin da Allah ya dora min, na aiwatar da wani a yau. Yake
ƴata yau kina zaune a gabana ne a matsayin matar wani, wanda cin ki da sha da
tufatarwarki za su koma a kansa, a yau kin shiga sahun manyan mata, a yau kin tashi
daga budurwar kin zama matar aure, daga yau ladarki zata riɓanyya har zuwa lokacin
da za ki bar duniya, neman aljannarki a yau ya sauka daga kan kafata ya koma
karkashin kafar mijinki.... A yau na aurar da ke Hurriya...”

Ta daga kanta ta kalli gurin da take kyautata zaton fuskar Appa take, bata iya
ganin komai saboda rashin masoya biyu, wato idanuwa, amman a haka zuciyarta take
ayyana mata yadda fuskar mahaifinta take. Bata ganin komai sai duhu, sai dai
makanta bata hana idanuwanta suke zubar da hawayen da tun da Appa ya fara magana
suke mata zuba. Appa ya dauki sarkar dake gaban Hajiya Binta ya dora a cinyoyin
Hurriya.

“Wannan sadakinki ne... An umarci iyaye su bawa yarinya sadakinta domin nata ne...
Wannan naki ne Hurriya...”

Hurriya ta kasa cewa komai bata jin komai sai _A yau na aurar da ke Hurriya_ haka
kalmar ta yi ta maimaita kanta a kunnenta kwakwalwarta na juya kalamin.

“Aure....”

Amma ta tambaya domin Mamaki ya hana Gwaggo cewa komai.

“Hajiya ban fahimta ba, wane irin aure kuma? ”

“Ki kwantar da hankalinki zaki fahimta”

“Ban gane na kwantar da hankalina ba, taya zai shigo cikin gidanmu kai tsaye ya
fada mana ya aurar da Hurriya? Saboda ya mayar da mu talakawa? Ni ba ni da hakki
akan Hurriya kenan? Wane irin magana ne wannan?”

“Kin fini hakki akanta Iyami, Annabi ya ambaci uwa sau uku sannan ya ambaci Uba...
Ban aurar da ita yau saboda na wulakanta ki ba, ban aikata hakan da wata manufa ba
sai dan ina ganin hakan ne abun da ya cancanci ko wane uba na gari aikata, na aurar
da ita ne a inda nake kyautata zaton za mutunta a rike ta amana, Iyami ki yi hakuri
tabbas na yi kuskure ban nemi shawararki ba na aurar da Hurriya”

“Wa ka aurawa ita? Saboda abun kunyar da ya faru ne ka yanke shawarar aikata haka?”

Gwaggo ta tambaya a fusace. Appa ya tausasa murya ya ce.

“Aa Wallahi su suka zo neman aurenta da kansu, sunan yaron Jamal da ne ga Nafisa,
dan wajen Alhaji Aliyu Turaki...”

Hawaye ya subucewa Amma.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, me ya sa zaka aurar min da ya a inda ba a san


darajar mutane ba? Macen da bata son hada hanya da talaka? Zaka dauki Hurriya ka
jefa a cikin danginta? Yarinya karama ta kafa fuskantar irin bala'in da na fuskanta
a gidanka, da na san haka rayuwa zata zama gaba daya Wallahi da ban aureka ba,
amman kaddara ta yi min zanen da ban isa na goge ba”

“Subhanallahi Subhanallahi Subhanallahi”

Appa ya maimaita har sau uku sannan ya ce.

“Na san ban kyauta miki ba Iyami, amman ki tausasa ko dan yaran nan”

Amma ta masa wani kallo na takaici da bakinciki.

“Yara? Wadannan twins din da aka haifa ka kasa zuwa ka tara hannu ka karba? Ko kuma
ďan da aka kama ka ce ba zaka bada kudin fansar sa ba! Sai da na hada komai da na
mallaka na bada, sannan Hajiya Kaltume ta baka umarnin biya? Ko kuma Hurriyar da ka
juyawa baya?”

Appa ya kasa amsawa ya sauke kansa kasa yana mai jin kunya da nauyin abun da ya
aikata.

“Bari na fada maka da bakina ka ji, yata bata auru ba, ba zan bada ita a inda za a
wulakanta ta ba, abun kunyar da aka yi mata kazafin aikatawa ni zan iya rumgumarsa”

Ba tare da Appa ya dago kai ba ya ce.

“Iyami karki furta kalami cikin fushi”

“Irin kalamin da ka furta a lokacin da na ke cikin gidanka da cikin yayanka? Irin


zuwan da iyayena suka yi ka wulakanta su? Yata ba zata je ko'ina ba Haruna.... Ban
amince da wannan auren ba...”

Hajiya Binta ta ce.

“Adai hakuri Iyami a daina tuna baya, a bar baya ta wuce”

“Haka ne Hajiya, da dan yaran nan ba da be isa ya shigo cikin gidan nan ya zauna a
nan yana magana da ni ba”

Appa ya share hawayen da suke masa zuba.

“Na cancanci tozarci da wulakanci da rashin mutunci a gurinki Iyami, ban kyauta ba
na sani, kuma na karbi hakan”

Ya kalli Hurriya dake amayar da ruwan hawaye ya ce.

“Ba zaki ce komai ba Hurriya? Wata kila ban kyauta miki ba, domin ban tsaya na ji
ra'ayinki ba”

Hurriya ta mika hannayenta ta kama hannayen mahaifinta ta rike.

“Hakika kai uba ne na gari Appa, ba zaka aurar da ni a inda kake tunanin zan wahala
ba, ba zaka aurar da ni a inda za a musguna min ba, ko da ban gani a aikace ba na
san a cikin zuciyarka haka ne, Appa ko kare ka aura min a matsayin miji, Wallahi
zan karbe shi na zauna da shi, balle kuma mutumen da kake kyautatawa zato, na gode
da zabin da ka yi min. Ya Allah mahaifina na ciyar da ni da halak, Allah ka ciyar
da shi da abinci da ya fi ko wane abinci dadi a aljanna, mahaifina ya shayar da ni
da halak, Ya Allah ka shayar da shi da ruwan alkausara, ruwan da bayan su babu
sauran ƙishi bayan shansu, Mahaifina ya tufatar da ni da ni da Halak, Ya Allah ya
tufatar da shi da mafi kololuwar darajar tufafi a aljanna, Mahaifina ya sama min
muhalli, Ya Allah ka yi masa muhalli kusa da Annabi Muhammad S A W, Ya Allah ka
shaida a yau mahaifina ya sauke nauyi na zaba min mutumen da yake ganin ya dace da
ni, Ya Allah ka sauke masa nauyin zunubai, a saka a aljanna a saukake”

“Ameen, Allah ya miki albarka Hurriya”

Appa ya amsa yana kuka, sannan ya kalli Amma ya ce.

“Iyami na gode da kika haifa min ƴa mai tarbiya da sanin ya kamata a kananan
shekarunta, wannan ma kadai abun alfahari ne a gurin, ku yafe min a inda na yi ba
daidai ba, na barku lafiya”

Ya mike tsaye ya saka talkaminsa ya nufi kofar fita daga tsakar gidan, sai ga
yaransa yan tawaye sun shigo sanye da uniform din makaranta rike da lunch box, suna
ganinsa sai suka yi gurinsa suna murna kamar sun saba da shi.

“Appa...Appa.... Appa...”

Durkusawa yayi yana shafa kansu a madadin ya amsa sai ya fashe da kuka kamar ba shi
ba. Yasir mai ya sauke kansa kasa yana hawaye, Gwaggo ma hawayen take ita da Hindu,
Rukayya kuma ta koma kusa da Hurriya ta zauna ta rungume suna kuka. Cikin karfin
hali Appa ya mike tsaye ya kama hannun yaransa ya fice daga gidan, Yasir ya share
hawayensa ya kalli Amma.

“Amma...”

Sai ta daga mishi hannu tana hawaye.

“Dan Allah tashi ka bi mahaifinka”

Ya mike tsaye ya kalli kakarsa.

“Hajiya tashi mu tafi”

Hajiya ta yi murmushi.

“Zan tafi Iyami amman zan dawo idan kin huce”

Sannan ta mike tsaye suka fice tare da Yasir. Amma ta share hawayenta ta kalli
Hurriya dake kuka ta ce.

“Shikenan abun da zaki fadawa mahaifinki? Kin goyi bayan auren da yayi miki? Kin
san wacece Nafisa, kin kuwa san irin zabin da Alhaji yayi miki?”

Hurriya ta dago daga jikin Rukayya ta ce.

“Amma, mata da yawa iri na ba su san ubansu ba, saboda uban ya mutu a lokacin da
suke ciki ko suke da kurciya, da yawa iyayensu ba su ga ranar aurensu ba saboda
mutuwa ta yi katanga, suna da yawa wadanda iyayensu ba su samu damar zaba musu miji
ba, wasu kuma an fasa aurensu, saboda ba a san ubansu.... Shim ni a gareni, wannan
na gata ba ne?”

Amma ta kasa amsawa. Cikin kuka Hurriya ta cigaba.


“Amma..., baka sanin muhimmanci uba sai ranar da ka rasa shi, uba yana da ƙima,
shi uban bango ne majingina ko wace ƴa. Idan kana son ka san darajar uba tambaye
maraya, idan kana son sanin tsadar uba da halin da ƴa mace take shiga idan bata da
shi, tambayi Ƴar da aka haifa ta hanyar zina...”

Ta saka hannunta tana share hawayen da suka ki tsaya mata

“Ni dai kam na sani, dukan abun da zai zo daga gurin Ubangijina mai kyau ne, dan
haka zan tara hannu biyu na karba, ko da ba zai min dadi a yanzu ba, zai zama
daraja ce da nasara a gaba, shi dan'adam ba ya kauce kaddara, kaddara bata wuce
bawa, wannan ma daga gurin Allah ne....”

Amma ta girgiza kai tana kuka.

“Aa Hurriya ban yarda da wannan auren ba, ba zaki je ki sha wahalar da na sha a
gidan ubanki ba, na yi irin wannan wautar na ki a lokacin da nake da kurciya kamar
ke, amman yanzu me ya haifar min?”

“Nasara....”

Gwaggo ta amsa mata a tsawace.

“Nasara ya haifar miki Iyami, haihuwar da kika da Alhaji Haruna nasara ce..! Zaman
auren da kika yi a gidansa nasara ce...! Samun soyayyarsa da ta mahaifiyarsa nasara
ce....! Abun da kuma ya same ki yanzu jarabawa ce ni ma na gane...”

Amma ta runtse ido ta jingina da bangon gidan.

“Abun da ya gudana a yau din nan ma Nasara ce Gwaggo...”

Cewar Hindu tana murmushi. Gwaggo bata sake cewa komai ba ta mike tsaye ta shige
falonta, Hindu kuma ta dafa kafadar Amma tana bata magana, Rukkaya ta kama Hurriya
ta kwantar da ita a jikinta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

“Ni kaina ban yi farinciki da wannan auren ba, sai dai ba zaka iya nunawa Yaya ba
ya fada maka ba daidai ba ko ma yace ba ka yi tunani ba, amman yarinyar sam bata
dace da matar Jamal ba sam, sam sam”

Cewar Momy Ikilima a madadin ta kwantar da hankalin Ammy sai zugata take, Hajiyar
Maru ce ta kawar da maganar Momy Ikilima ta hanyar nunawa Ammy ta karbi wannan
kaddara ta so abun da danta yake so.

“Ba zan iya kallon yarinyar a matsayin surukata ba Hajiyar Maru, shi kansa zafin
soyayya ne da rashin tunani yake dawainiya da shi, amman da zarar ya dawo hayyacin
zai gane kuskure suka aikata shi da mahaifinsa”

“Kamin su gane hakan, sai ki zuba musu ido ki ga yadda abubuwan za su yi, kin san
dai ba zaki iya ja da mijinki ba ko?”

“Ba zan iya ja da shi ba Hajiya amman ba zan karbi yarinyar nan a matsayin sukura
ba”

Hajiyar Maru ta mike tsaye ganin ta yi iya nata ta fice ta bar ma Ammy dakin.
Hajiya Turai ta dafe kanta tana kiran kukan da baya kusa da idonta.

“Sallamu Alaikum, daman ni na san ba da saninki Yaya ya aikata wannan abun ba, abun
bakinciki abub takaici abun Allah wadai”

Momy ce take fadar hakan daga shigowarta dakin, Hajiya Turai ta dago ta dube.

“Ta ina zan yarda Captain ya auro yarinyar nan, Engr be yi shawara da ni ba, be
fada min ba kawai yaje ya aiwatar da abun da zuciyarsa take so”

“To wai haka kika hade hannaye suka zuba ido ba tare da daukar mataki ba?”

“Matakin me zan dauka Hajiya Nafisa? An riga an daura aure me zan yi? Kin san dai
Engr ba zai bari na cilastawa Captain sakin yarinyar a yanzu ba”

Momy ta zauna tana karkasa yadda bakincikin ya rabu mata gida gida. Har La'asar
Hajiya Turai da Momy suna cikin dakin suna ta juya zancen, bayan saukowa daga
sallah La'asar ne Daddy ya shigo dakin, Hajiya Turai ta dauke kai ta juya fuska sai
dai hakan be hana shi zama kusa da ita ba, sai ma dariya da yayi yana tsokanarta a
gaban Momy.

“Haba Turaita yar Baturiya yau kuma da Engr ake fushi?”

Momy ta kalli dan'uwanta cikin bacin rai ta ce.

“Dole Hajiya Turai ta yi fushi, abin nan ya wuce duk inda kake tunani Yaya, kuma ba
a kyauta mata ba, ni ma kuma ba a kyauta min ba, na aikata abu ba tare da tunanin
halin da zamu shiga ba, yanzu haka ko da na fito na bar Namra tana kuka saboda
bakin auren nan da aka daura a yau da bakar yarinyar can, Namra da Captain suna
kaunar junansu amman yanzu wannan auren da daura masa a yau ya lalata komai”

Da kamar mamaki Daddy yake kallon fitinanniyar kanwar tasa.

“Amman Jamal be taba gabatar min da wata magana makamancin haka ba a game da Namra,
kuma ni na aikata abun da na aikata ne a yau saboda na gama karantar abun da Jamal
yake so ne, sannan abun da kuke ta kushe yarinyar nan da shi koraren ne a gurin
wanda ya san gaskiya, ni dai na ga video kuma yanzu haka shigowar da na yi a nan na
zo ne da maganar Bashir Sarauta yana falo yana jirana yanzu haka”

“Ai dansa ne ma ya dace ya auri yarinyar tun da yar'uwar badalarce, amman be nema
nemawa dansa ba sai mu, kamar dai masu bakin uwa”

Daddy yayi murmushi yana kallon fuskar kyakkyawar matarsa take magana cikin kuka da
fushi.
“Sheri ne aka yi mata Turai bata aikata ba, kuma ko da ta aikata tun da har danki
yaji zai iya zama da ita a haka mu miye na mu a ciki?”

“Ni dai ba zan karbeta a matsayin suruka ba, kuma ba zan bari ayi bikin komai ba
domin ba za a yada hotunanta a matsayin matar Captain ba”

“Daman daura aure dai shi ne wajib, kuma an yi, wadanna abubuwa ne da al'ada ta
tana da, shi ma kuma idan bangaren yarinyar suka nuna sha'awar yin haka ba zamu
hana su ba, ke dai a bangarenki ne ba zaki yi haka ba, ni ba tsegumi ya kawo ni nan
ba, Bashir Sarauta ne ya zo tare da yan'uwansa da iyalinsa akan maganar yarinyar,
da yi tunanin ko zaki so saurare a matsayinki na mahaifiyar Captain ko ba komai
haka zai share zargi da rashin ganin kimar yarinyar nan da kike yi, amman yanzu na
fahimci baki bukatar hakan”

Ya kalli agogon dake daure a wuyan hannunsa.

“Ki shirya na fada miki jirgina zai tashi 5pm na yamma”

“Babu inda zan tafi na tafi na bar yarona a nan da wannan yarinyar nan, idan na bar
garin nan sai idan tare da amaryar ne”

Daddy yayi murmushi.

“Amaryar da kika ce baki so? Ayi haka?”

“An dai riga an daura aure yanzu a ba mu amaryarmu mu tafi da ita Kaduna?”

“Ina aka taba haka? Daga daura aure yau babu kintsawa babu komai sai mu tafi karbar
Amarya kuma mu wuce da ita Kaduna? A kaduna ina zata zauna ma? Ai dole mu ma muna
bukatar lokaci ba yanzu yanzu ba”

“Duk gidanjen da suke garin Kaduna ace ba a san wanda zata zauna ba? Kai kace wata
yar zinari?”

“Tarin gidaje ba shi ne mafitar ba, sai wanda mijinta yake sha'awar su zauna
tukuna, wannan ma na aikin mu ba ne, ta ina ma za a dauki amarya akai a Kd bayan
mijinta yana nan garin Gusau yana aiki, tare da mu zata zauna ni ba zan iya bari
saboda Captain yayi aure ya zauna a gida daban, shi kadai Allah ya ba ni ba zan
bari wata ta kwace min shi ba”

Daddy yayi murmushi ya dauke kai ya fice daga dakin, shi dai duk a tunaninsa Hajiya
Turai take tana yi ne saboda ranta a bace, idan aka bata kwana biyu zata sauko ta.

“Wallahi ba zan taba bari ayi zaman auren nan ba, ba zan bar garin nan ba sai da
yarinyar nan”

Bayan Daddy ya fice Ammy take fadar haka, Momy ta mata kallon rashin fahimta.

“To ai idan kika yi haka kin nuna kina sonta kenan, ai kamata yayi ki banza
ajiyarta ki share yar banza ta fahimci familyn nan ba gidan aurenta ba ne”

“Shiyasa zan yi haka ai, idan na barta a nan cikin satin nan zata iya tarewa, idan
kuma ta haihu da ďana ai zance ya kare, ina nan garin idan kuma ta tare sai dai ta
tare a gidana”

“Wannan ba mafita ba ne lokacin da zai saci kafa ya tafi mai nawa ko gani be yi ba,
ki dai canja shawara”

Ammy ta juyo ta kalli Momy kamar zata fasa kuka. Momy ta yi shiru domin ita ma bata
san abin yi ba a yanzu kanta a rufe yake.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un wannan abu da me yayi kama? Wane irin rayuwa ne
wannan? Ni na rasa ma me ye abun yi, babu abun da yafi min bakinciki kamar neman
auren yarinyar nan da aka yo a cikin falona kuma aka yo sadakinta da sinari”

“Zinarin ma mai tsada, yarinyar ko gani bata yi. Amman ni na san abun yi ni na
sani, ta yaro ai kyau take bata karko”

Ammy na maganar zuciyarta na kuna, kamin ta mike tsaye ta nufi bangaren da mijinta
yake sauka idan ya zo gidan.
Daddy yana fitowa daga dakin ya hau sama ya shiga dakin Captain kicibus suka yi da
Daddy shi zai fito Daddy kuma zai shiga dakin.

“Daddy”

Captain ya fada yana sauke idonsa saka haka nan dai yake jin kunyar Daddy a yau.

“Kai ba mace ba miye na rufe kai a daki? Ko Ammy kake yi ma boyo?”

Captain yayi murmushi yana sosa bayan kansa. Daddy ya ce.

“Mahaifin yaron nan ne Adam ya zo tare da Iyalinsa, ya fara koro min bayana na
takatarda shi saboda ina ganin kai da mahaifin yarinyar ne kuka dace da yin shawara
ko yanke hukunci”

A take bacin rai ya mamaye zuciyar Captain da tsananin fushi ya ce.

“Me suka zo yi Daddy?”

“Kamata yayi ka sauko mu ji, bana son bata lokaci 5pm zan wuce Kaduna”

Daddy ya karasa yana duba agogo hannunsa, a tare da Captain suka sauko, a tunaninsa
iyayen Adam din za su sake bukatar ya basu dansu ne ko kuma wani abun da ya shafi
karar da ya shiga a DSS. Captain be ji zai iya gaisawa da ko daya a cikin family ba
domin dan su ya janyo musu kallon marasa mutunci yake musu. Salim be kalli gurin da
Captain yake zaune ba domin kowa baya marmarin ganin abokinsa a yanzu.
Sai da Daddy ya kalli Captain da fuskarsa take a gintse sannan ya ce.

“Ina tunanin kun san Captain, ko da iyalanka ba su sani ba kai dai ka san da cewar
Jamal ďana ne, Salim zai iya fadar hakan, dalilin da ya saka na dakatar da kai daga
bayani saboda na kira shi ne, domin shi da mahaifinta suke masu hakkin akanta
yanzu, kasancewarsa mijinta an daura Aurenta da Jamal a yau...!”

Da matukar firgici Salim ya kalli Captain da goshinsa ke kyalli kana arba da shi
zaka san ango ne latest. Kallo kallo suke da Salim kowa ya kasa dauke idonsa.

“Maa Shaa Allah, abu yayi kyau Allah ya saka maka da alheri a wannan jihadin da ka
yi, kuma ya baka wuyan dauka”

Cewar Bashir Sarauta yana jinjina kokarin Captain na toshe kunnuwansa a wannan
mawuyancin yanayin da ba kowa zai iya ba. Salim ya dauke idonsa da mugun karfi ya
mike tsaye fuuu ya fice daga falon

“Zaka iya cigaba ko kuma ka fara daga farko saboda ya fahimci me ke tafe da ku”

Alhaji Bashir ya kalli Captain cikin yanayin damuwa ya ce

“Daman mun zo nan ne akan maganar abun da ya faru da ne yi ma kowa dadi ba, DSS sun
sanar mana su suka dauki Adam sakamakon karar da Captain ya shigar, sun ce sun
dauke shi ne saboda bincike yanzu haka dai sun dawo da shi yana asibiti domin sun
masa duka sosai daurin da aka yi masa ma likita yace sai an sake daura shi...
Dalilin da ya saka muka zo nan shi ne mun bincike Adam akan abun da ya faru daman
kuma tun farko an yi masa fada kuma mun tambaye shi taya hotunan suka fita, sai
yace mana be sani ba, kuma ya fada mana cewar tabbas yana tare da yarinyar ne...”

A wannan gabar ne Captain ya kasa jurewa ya kalli Daddynsa cikin yanayin bacin rai
domin baya bukatar a nanata masa abun da ya riga da haddasace.

“Daddy na dauka magana ce mai muhimmanci za su yi, amman wannan yana maida hannun
agogo ne baya”

Daddy ya kalli Captain with serious face domin ko da Alhaji Bashir Sarauta ba
abokin kasuwancin Daddy ba ne ta wata fuskar ya kai ya haifi Captain and duk wani
abu na nuna rashin mutunci ko rashin girmama na gaba Daddy baya lamuntar dansa
Jamal ya aikatawa kowa.

“Respect yourself ka saurare shi ka ji abun da yake tafe da shi”

Captain ya maida hankalinsa gurin Alhaji Bashir Sarauta ba dan ransa yana so ba,
dai dan bin umarnin Daddynsa.

“A yanzu maganar da nake da ku, yanzu haka Adam ya fada mana gaskiyar cewar kazafi
aka yi ma yarinyar nan!.. ”

Yadda ya fadawa Captain gaskiyar abun da ya faru haka iyayensa suka fada. Daddy ya
girgiza kai cike da takaici ya ce.

“Duniya ta lalace, mun zo wani zamani da bayan tarbiyar dole dai muna hadawa da
addu'a ga yaranmu, ban da abun zuciya da aikin shaidan miye abun chusa kai da
nemana halaka akan me zaka dage sai yarinya ta so ka, bayan hakan be samu ba kuma
sai ka ce sai ka nemi lalata rayuwarta? Yanzu ya bata sunansa ya bata nata da bata
gidansu ina amfanin haka?”

Alhaji Bashir Sarauta ya ce.

“Babu ai na fada masa da abu ne mai kyau da yanzu celebration muke muna murna amman
ga abun da ya janyo mana, ita kanta abokiyar shaidancin tasa gashi ita ma ta
janyowa kanta ta samu nata kaso”

Daddy ya girgiza kai.

“Dole ai zata samu haka ko ma fi, ko bare ka aikatawa haka ai ba zaka ga daidai ba
balle kuma yar'uwarka ta jini, sun jefa yarinya a damuwa ba tare da hakki ba”

“Shiyasa na zo na baka hakuri kuma na roki yafiyar abubuwan da suka faru, daman
aiko sammaci bana nan Iyalina suka yanki ticket suka aiko da sunana, gashi kuma
shari'ar ta zame mana biyu, sannan yaron nan gashi babu lafiya, dan Allah ayi
hakuri a janye karar nan da Captain ya saka gudun kar mu kara yin abin kunya, domin
idan aka ce za'ayi shari'a har wadanda ba su da waya da redio zansu iya jin wannan
abun kunyar, wani ma zai iya cewa da kai nake shari'a ranka ya dade ba domin canja
labari be da wahala a gurin mutanen mu yanzu...”

Daddy yayi jimmmm na dan lokaci, ya sauke dogon numfashi yana nazari, be kai ga
yanke hukunci ba ya kalli Captain dake karanta sakon taya murna da Salim ya aiko
masa ya ce.

“Captain yanzu meye abun yi me ye shawara, ko da yake ya kamata ace an ji ta bakin


mahaifinta ma?”

Ya dago kai ya kalli mahaifinsa.

“Daddy zan janye shari'a daman kuma yin haka ba abu ne mai wahala ba, zan yi hakan
on one condition Adam zai yi video ya fadawa duniya gaskiya kuma ya roki yafiyar
Hurriya if not na zan janye shari'ar nan ba kuma Monday nan zamu shiga Kotu, hakan
ne kadai zai wanke Hurriya a idon duniya kuma daman na mata wannan alkawarin”

Mahaifiyar Adam din ta dubi Captain ta ce.

“Haba ďana wannan matakin be yi tsauri ba? Zai iya bata hakuri a sirrance kuma ya
fada mata gaskiya, amman fitowa yayi video yaje viral sai kara lalata lamarinsa ne”

“Ita da take mace ya lalata mata rayuwa balle kuma namiji? Da be aikata ba wata
kila da duk hakan be faru ba”

Yan'uwan Alhaji Bashir ne suka shiga rarrashin Captain ko zai sauko daga wannan
hukuncin amman fir yace idan ba haka ba shi ba zai hakura ba. Alhaji Bashir ya dubi
Daddy ya ce.

“Ranka ya dade a taimaka a saka baki lamarin nan”

Daddy ya nuna Captain.

“Shi ne mijinta, kuma wannan case din a hannunsa yake, ina tunanin a yanzu ko
ubanta be kai shi iko da ita ba, kuma ya saukaka muku a haka din ma, ni ban yi
zaton zai yi saurin amincewa ba, yin haka zai wanke matarsa daga zargi da zagin da
danku ya ja mata, kuma idan ma ba ku aminta yaron ya bada hakuri ta wannan sigar ba
ko kotu aka je Kotu zata saka shi ya bada hakuri kuma ya fadawa duniya abun da ya
faru, daga karshe kuma ya fuskanci hukunci”

Mahaifiyar Adam ya fashe da kuka domin a gurinsu yin abun da Captain ya bukata ma
cin mutunci ne da kara zubewar kimarsu. Daddy ya mike tsaye ya kalli Captain

“Ina ganin shi kenan nan ai, idan sun zabi haka sai ku aiko mana da video idan kuma
kotun kuka zaba duk daya ne, akwai uzurin da zan yi kamin na bar garin yau zan wuce
Kaduna”

Captain ya mike tsaye sai suka fice tare da Daddy aka bar Alhaji Bashir Sarauta da
matarsa da yan'uwansa da suka rako shi a falon.

“Adam ne ya ja mana wannan wulakanci, ni ban ga dalilin ma da zai sa a nemi janye


shari'ar ba a bar shari'ar ba, da abar shi kotu ta koya masa hankali”

Cewar daya daga cikin kanen ubansa. Alhaji Bashir ya ce.

“Ba za'ayi haka ba, shi ma ai sai ya wahala kuma ko kotun muka je ba nasara zamu
yi, tun da kudi za su zuba kuma su suke da gaskiya”

Mahaifiyarsa ta kalleshi.

“Yanzu kenan Alhaji dole Adam sai yayi haka? Babu wani abun da zaka iya yi? Shi
Captain ba zai duba abotar dake tsakaninsa da Salim ba?”

“Kina kallo Salim din ya tashi ya fice be ma tsaya aka yi magana da sho ba, wata
kila sun samu matsala da Captain din akan haka, kuma shi Adam ai ya fada mana cewar
Captain ya masa video idan ma ba mu saka ya bada hakurin ba zai iya sakin video
kuma ga shari'a a kotu, yara ne idan za su yi abu basa tunani, yadda Alhaji Turaki
ya fice ya bar a falon nan ai kin san akwai abun da yake zuciyarsu da jira kawai
suke”

Cikin kuka Hajiyar ta mike tsaye ta fice daga falon sannan sauran ma suka mike
tsaye.

“Alhaji ka tashi mu tafi, babu amfanin zama ai domin ba saurarenmu za su yi ba”

Alhaji Bashir ya mike tsaye.

“Zan samu mahaifinta na yi magana da shi, zamu samu mafita a can”

Cikin rashin jindadi suka fice daga falon. Dayan falon Daddy ya shigo tare da dansa
sai suka samu Ammy zaune tana jiransu, fuskarta a hade kamar ba ita ba.

“Ina tunanin ya kamata kaje ka samu mahaifinta ku yi magana, domin za su iya bi ta


can su siye shi da kalamai ya yafe musu, bayan kuma ba su cancanci hakan ba matukar
ba su aikata abun da ka umarce su ba”

Kamin su zauna Daddy yake fadar haka, Captain ya rausayar da kai

“Okay Daddy”

“Daga yin aure matsalar har ta tattara ta dawo mana a gida? Mu miye na mu da za su
zo mana a nan?”

“Saboda danki ne ya shigar da karar kuma mijinta ne a yanzu, sannan lalama suke bi
suna neman yadda za a kashe wutar ne cikin ruwan sanyi”

“Idan wani abu ne da ya shafi Hurriya ko mahaifinta kai ya kamata ka yi magana da


shi kai tsaye, ba Captain ba yaron da lafiya ma bata wadace shi ba, tare da shi
zamu tafi kaduna a yau....”

Captain ya kalli Ammy da sauri, Daddy kuma yayi murmushi ya ciro wayarsa yana
lasawa.

“Kin kawo shawara mai kyau, haka ya kamata yi tafiyarka Jamal zan yi magana da
mahaifinta da kaina”

Ya amsa masa da kai sannan ya juya ya fice daga falon.

“Ba zan tafi Kaduna na bar ďana ba, ko dai na fasa tafiyar ko kuma ka fada masa ya
shirya mu tafi, kuma a fadawa iyayen Hurriya tun da an daura aure a ba mu amaryarmu
zata tare”

“Wannan hurumin iyayenta ne ba na mu ba, ki je ki same su ku daidaita idan sun saka


ranar da ta yi miki shi ke nan, amman dai ki sani duk wani abun na zubar da mutunci
ba zan bari ya faru ba”

Yana kaiwa nan ya mike tsaye ya shige bedroom ya barta a falon zaune kunshe da
bakincikinta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
HAJIYA KALTUME POV.

“Wai ni kam ya ma sunan addu'ar nan da ake idan za a bar gida, wanda aka ce idan ka
karanta babu abun da zai same ka har ka je ka dawo?”

Hajiya Fatee ta yi shiru alamar nazari tana kokarin tunanin addu'ar amman ta kasa.

“Akwai dai Bismillah a ciki, Bismilah da wani abu a ciki ni ma fa na manta addu'a”

“Kin ga da kin rike ai da mun karanta yanzu, mu tafi cikin kwanciyar hankali”

“Duk abun da za'ayi fa ba zan samu kwanciyar hankali ba, domin ba mu da shi a
yanzu, tafiyar nan dai ta zame mana dole ne kawai, domin ni ma ina son na san
lafiyar Malam”

“To kin gani, dole a haka zamu daure mu tafi, Allah dai ya kaimu lafiya, amman
tashin hankali da nake ciki a yanzu ai ya fi na yan kidnapping”

“Babu wanda ya di wani, fatan dai Allah ya kaimu lafiya”

Cikin tsoro suka shiga motar ta suka dauki shatarta tun daga tasha direban ya zo
gidan Hajiya Fatee ya dauke su. Hajiya Fatee ce mai rike carbi tana ja tana leka
lake waje, Hajiya Kaltume kuma shiru take sai da suka iss cikin garin sannan
hankalinsu ya kwananta Hajiya Fatee ce ta yi ta nuna ma direban hanyar gidan Malam
be sauke su ko'ina ba sai a kofar gidan da yayi baki kirin har wani bangare na
ginin ya zube. Hajiya Kaltume ta kalli kawarta.

“Anya akwai lafiya a gidan nan kuwa?”

“Ina lafiya kina kallon gida kamar an yi gobara”

“Ni ma abun da ya daure min kai kenan, amman dai bari mu shiga cikin gidan mu ji”

Hajiya Kaltume ta zagoyo ta gefen da Hajiya Fatee take suka jera suka nufi gidan da
kusan ma za'a iya cewa ya zama kango.

“Ke yaushe rabonki da nan?”

“Wai ni? Ai tun zuwan da muka yi tare da ke van sake zuwa ba, to me zai kawo ni
irin wannan gurin ma sai dole”

“Yanzu wai da gaske kike filaye da gonakin da kika ce mutumen nan ya siya miki duk
baki ga ko daya ba?”

“Ai yarda ce ta kawo haka, ni na yarda da ko ban zo na duba ba na san ba zai cuceni
ba”

A bakin kofar gidan da aka zagaye da ƙaya suka tsaya suna kallon yadda gaba daya
gidan yake kone kuma babu alamar ana rayuwa a cikinsa.

“Hajiya wannan gidan da kike gani gobara aka yi, kuma kina kallon gidan ya zan
kango babu kowa a ciki”

“Amman Hajiya Fatee ni da ke a nan muka san matan malam suna rayuwa?”

“Bari mu tambaya, ba mamaki ma ace ya tashi tun da yanzu linkafa ta yi gaba”

Juyowa suka yi suka fito daga zauren gidan suka yar tafiya sannan suka isa gida
daman makotansa suka yi sallama. Hajiya Fatee ta shiga ciki Kaltume kuma ta tsaya
daga waje tana waige waige kamar wanda bata yarda da garin ba.

“Sannu ina kwananku?”

“Sannu dai muna lafiya”

“Alhamdulillah dan Allah Malam muke tambaya ko ya tashi a nan ne shi da Iyalansa?
Mun shiga gidan babu kowa a ciki na ga kamar ma ginin ya fadi”

“Ayyah wai Malam? Malam ai yau kwanansa tara da kwanta dama, Malam ai lokaci yayi”

Hajiya Fatee ta dora hannunta akan tulun kirjinta ido a waje kamar za su yi magana.

“Malam kike nufin ya rasu?”

“Malam ya rasu lokaci yayi, gobara yayi cikin dare wutar ta ci shi ta cinye yaransa
biyu kuma bata bar komai da yake gidan ba, amman sauran yaransa da matansa sun fita
da rai suna nan lafiya kalau”

Hajiya Fatee ta kai zaune tana dafe da kirji.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, na shiga goma na lalace yau kashi na ya bushe,


Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un Wayyo Allah na ni....”

Kuka da ambaton Allah da take ne ya saka Hajiya Kaltume shigowa, sai kuma ta shigo
a sa'a, domin ta shigo ne a daidai lokacin da matar take kara radawa Hajiya Fatee
cewar.

“Matansa sunan na yamma da mu kadan, a sabon gidansa suke takaba, ai Malam ya kowa
ya ji mutuwarsa duk wanda ya zo nan kuma yake mana”

“Mutuwa? Malam din ne ya Mutu?”

Hajiya Kaltume ta amsa a razane da karfi tana kallon matar dake rike da tabarya
tana surfe.

“Yau kwana tara kuwa, gobara aka yi a gidan, komai ya kone, zane wannan na daura
sai da aka taimakawa matansa da shi a lokacin da lamarin ya faru”

“Shi nan na shiga uku, ni kam ta kare min.... Al'amurra sai kara rinchabe min
suke.... Yanzu Malam be tashi tafiya ba sai da wahala ta tunkaro ni gaba da yamma,
na shiga uku na lalace”

“Ba ke kika shiga uku ba Kaltume ni na shiga uku, wayyo Allah wayyo ni kaina”
“Sai hakuri haka mutane suke ta kuka idan suka zo, ai mutuwar Malam ta taba kowa
musamman customers dinsa”

Hajiya Kaltume ma ta kai kasa ta zauna kusa da kawarta suna kuka kowa da dalilin
kukansa kuma da abun da yake yi ma fargaba. Tun matar na ba su magana har ta gaji
ta zuba musu ido, domin ko da matansa ne iyakar kuka da bakinciki da za su yi
kenan.

“Ku yi hakuri bayin Allah mutuwa ai ta gaji haka shiyasa kullum ake son a shirya
mata, Salmanu tashi ka kai su gidan matan Malam”

Ta fadawa babban ďanta, domin kukan da suke ya fara yi mata yawa har makota na
lekowa ta katanga wasu kuma na shigo suna kallonsu. Hajiya Fatee ta mike tsaye rike
da jakarka ta tana kuka, taku daya ta yi kamin ta yi na biyu wani hudun zuciya da
ido ya rufeta ta saki jakar ta fado kan Hajiya Kaltume da ko alamar tashi bata yi
ba, domin jikinta ya mutu kamar an mata allurar kasala.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un idan kika mutar min a yanzu ai sai abun ya taru
yayi min yawa ku taimaka min jama'a”

Matan dake kofar gidan suka karasa shigowa suka rika Hajiya Fatee suka daga ta daga
jikin Kaltume, suka shimfidata a kasa wasu suka fara mata fifita matar idan kuma ta
tashi da gudunta ta debo ruwa aka kwarawa Hajiya Fatee. Sai gata ta farko tana
hakki.

“Malam ya mutu, Malam me yasa ka mutu a yanzu? Asirin an tonu na shiga uku wayyo
Allah, Malam ya mutu ya bar ni da wahala wayyo Allah na....”

Wani irin shidewa ta yi luuuuuuu jikinta ya sake saki, har sai da matan suka jin
tsoron wannan suman nata na biyu, Hajiya Kaltume kuma tana zaune a gurin ta kasa
aikata komai sai kuka take kamar ita kadai ta rasa Malam. Ruwan aka sake zuba mata
sannan ta farfado tana kallon matan karkarrar dake juya mata tana jin sannun da
suke mata kamar a mafarki, fada mata da matar ta yi cewar Malam ya rasu ma sai ta
ji abun shi ma kamar mafarki ne ba gaske ba.

“Abun da zai fi akaisu gidan Matan Malam ko kuma a kaita asiri”

Wata daga cikin matan dake rike da ita ta fada, Hajiya Kaltume ta kalleta da
jajayen idanuwanta ta ce.

“Ina ne gidan”

“Daga nan ne yamma kusa da kuka uku, Sslmanu wuce gaba ka kaisu”

Yaron da aka kira da Salmanu ya dauki tayarsa da karen kada tayar ya wuce gaba yana
zumuncin nuna musu hanya, ganin mutanen daga birni suka zo. Ba dan taimakon Allah
da rahmarsa ga bayinsa ba da Hajiya Kaltume bata kai kanta gurin motar da suka
shigo ba, domin gaba daya kafafuwan rike mata suka yi, Hajiya Fatee kam sai da aka
riko aka saka ta motar idonta sai juyawa yake kamar bata san inda take ba. Yaron ne
ya wuce gaba da tayarda yana turawa su kuma suna cikin motar zaune a baya, Hajiya
Kaltume ce kadai ke iya kuka a yanzu Hajiya Fatee kam kai kawai take juyawa kamar
mai kokarin fita daga hayyacinta, direbansu na biye da su har suka isa katon gidan
ginar bolu kana ganin gidan da ba'ayi ma filista ba ka san ba duk kauye ba, ko a
kauna sai wanda ya tsaya da kafafuwansa.

“Wai yanzu da gaske Malam ya mutu Hajiya Kaltume? Shikenan Malam yayi tafiyar da
babu dawowa? Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, shi ke nan ta kare min dari ta hade
min da dubu, Wallahi ganin nake kamar ba gaske ko dai mafarki nake Kaltume?”
Hajiya Kaltume kam kaddara ta riga fata, bata iya cewa Hajiya Fatee komai a yanzu
domin ita ma bata da wannan kwarin guiwar. Hajiya Fatee ta unkura zata fita ta kasa
saboda jiki yayi nauyi a zaunen da take ma jiri ke debanta yana zubarwa.

“Dukiyata.... Cikin nan..... Ga Afrah... Indai Malam ya mutu a yanzu Malam be kyau
min ba”

Direban motar ya juyo ya kalli Hajiya Fatee dake sabbatu tana wani mashalo kamar
mashayiya. Cikin gidan Hajiya Kaltume ta shiga babu ko sallama sai tafiya take a
gajiye, daga a tsakar gidan ta fadi zaune tana kallon matansa dake zaune da
kayaransa.

“Daga tsohon gidanku muke aka fada Malam ya rasu, dan Allah ku ce mana ba gaskiya
ba ne”

Karamar ta sauke kai kasa idonta na cika da kwalla, mai karfin halin ce fa amsawa
Hajiya Kaltume.

“Malam kam rai yayi halinsa ya riga mu gidan gaskiya, sai dai mu bishi da addu'a,
ba Malam kadai ba har da yara biyu”

Hajiya Kaltume ta rushe da kuka tana dora hannu akai tana ihu kamar zata tara musu
mutane.

“Kashi na ya bushe a yau, ashe shiyasa komai yaki daidai, na zuba kudi ina duban
Malam yana nan yana aiki ashe Malam yana barzahu, na kira waya shiru ashe babu
Malam”

Matan suka taso suka rika Hajiya Kaltume suna kuka domin ta tsikaro musu bakincikin
rasa mijinsu da suka yi. Hakuri suka rika bata sannan suka rikata suka zaunar da
ita a ciki barandar gidan (Balcony) dayar ta debo mata fridge ta aje mata sannan ta
zauna tana bata labarin abun da ya faru tana kuka.

“Kin ga gidan nan be dade da gama shi ba, ya saka komai a ciki tv da fridge irin na
yan birni ya saka mana, kayan daki ma masu kyau ya zuba mana, na dubu 70k, duk
kauyen nan sai labarin gidan nan yake ashe Allah be kaddara a koma tare da shi ba
sai bayan ransa”

Hajiya Kaltume ta sharce kwalla ta girgiza kai tana kuka, kai ka ce kukan rashin
Malam kawai take da gaske ba kukan neman mafitarta ba.

“Yaushe ya rasu?”

“Yau kwana tara, kuma mutuwarsa ta bawa kowa mamaki, shiyasa har wasu suke zargin
ko jifansa aka yi, domin Malamai suna haka, idan aka ga ka taso ana yi da kai a
gari sai hassada ta shiga ciki”

Dayar ta karba mata.

“Ai ba kama ba ce wannan abun jifa ce kawai, domin yana cikin aikinsa karfe daya na
dare sai wuta ta fara kamawa a dakin, ihunsa kawai muka ji muka fito aka yi ta
dukan kofar ta ki budewa sai da ta cinye shi tass, kuma wutar bata tsaya nan na
haka ta bi gidan nan ta cinye komai har da yarana biyu iro da dan inna, zane wannan
na daurawa ba mu fita da shi ba, sai da makota suka kawo mana Hijabai, bayan wutar
ta cinye komai ta kama ginin gidan ta kone kamar watsa fetur, wannan abun ya bawa
kowa mamaki bayan an yi masarar kashe wuta aka bude dakin wuta ta ci Malam abun
babu kyau gani, haka ma aka saka shi ba tare da an yi masa wanka ba sallah akwai
aka yi masa aka saka shi a rame, saboda jikin ya kone wanka ba zai yi ba”
Ta karasa cikin kuka.

“Dole ayi masa jefa mana, a kauye ne wane Malami ne yake irin aikinsa? Babu shi
kuma gashi Allah ya amince masa komai girman gona ko gida sai aji Malam be ya siye
va dole hankalinsu ya tashi ba, mota ma wannan wanda Malam yake hawa abar kallo ce”

Hajiya Kaltume ta Kalli babbar matarsa tace.

“Amman duk wanda ya aikata nasa wannan abun mu ya aikatawa ba Malam ba, mu ya jefa
a matsala”

“Haka kowa yake fada, ga Malam da mutane manyan mutane kala kala gari gari zuwa ake
saboda iya aikinsa, kowa ya zo cewa yake ba mu aka yi ma mutuwa ba su aka yi ma”

“Wannan abu be yi dadi ba, Kawata na kiran wayarsa a kashe kullum ina sauraren ko
zai kira amman shiru ashe wani labarin ake na dabam”

“Malam ai be fita da komai ba, wayarsa ko ganinta ba ayi ba”

Hajiya Kaltume ta sauke ajiyar zuciya, idanuwanta suntun suntu tsabar kukan da
tasha.

“Kuma be bar muku sakon komai ba?”

“Ina zancen barin sako a mutuwar da ba a san da zuwanta ba balle a shirya mata,
kuma ko da ya bar wani abu ai wuta ta kone komai ina za a gani ma”

“Ba shi nake nufi ba, sako haka ko na kalami cewar an turo masa kudi ko kuma kudin
da filin da yake guri kaza ba nasw ba ne? Ko gona?”

“Aa babu kayan kowa a hannun Malam, domin idan ya siye gida ko gona ko fili ya kan
kiramu ya fada mana cewar gidan da yake guri kaza ko fili ko gona sun zama
mallakinsa ya siye, har takardun da ake yi na shaida yana nuna mana, kuma yawanci
idan sai siya da aminsa yake zuwa Malam Musa, bayan rasuwarsa kuma Malam Musa ya
hannata mana komai na Malam kuma ya bi mutane da dan abun da yake hannun malam na
mutane aka biya, babu hakkin kowa a gurin Malam yanzu”

“Da dai zan samu ganin Malam Musa na yi magana da shi, saboda akwai mai yawa da na
turo masa a account da sunan zai tafi gurin Malaminsa yayi min aiki, kuma kawata ma
Hajiya Fatee ta bashi kudi mai yawa ya siya nata gona da fili a kauye, da zan ga
Malam Musa sai na tambaye shi ko ya san wani abu a kai”

“Gaskiya babu, kuma wani be taba zuwa mana da irin wannan maganar ba sai ke, amman
saboda kaucewa zargi, bari a kira Malam Musa sai ku yi magana da shi”

Amaryar ce ta aika yaro gurin da ta san aminin mijinta na zama aka kirashi, da ya
iso ya shigo cikin gidan suka gaisa da Hajiya Kaltume ta yi masa gaisuwa sannan ta
kora da bayani.

“Ni sunana Hajiya Kaltume akwai kawata Hajiya Fatee tana mota yanzu haka, mutuwar
ta taba ta sosai ba zata iya takowa nan ba, ni na tura masa kudi kwana goma da suka
wuce ko sha daya, kudi mai yawa akan cewar zai kawai Malaminsa ayi min aiki domin
wannan aikin ya fi karfinsa, yace Malaminsa zai siye rakumi da kayan aiki, shi ne
nake tambayar ko ka san wani abu akan haka”

Mutumen da ake kira da Malam Musa ya girgiza kai.

“Aa Wallahi be yi wata magana kamanciyar wannan ba, kuma Malam ai Malaminsa ya dade
da rasuwa shekara kusan goma sha wani abu yanzu”
Hajiya Kaltume ta yi tagume.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un...”

Tana jin wani sabon kuka na taso mata.

“Ita kawata dake mota har filaye take bashi kudi ya siya mata da gona ita be yi
maganarta ba ko? Ko kuma ya bar wata wasiya? Ko a cikin gidajen da yake siye yace
wannan na Hajiya Fatee ne ko na wata”

“Aa babu wannan, Malam be taba fada min haka ba, Maimuna a cikinku akwai wanda ta
taba jin magana makamanciyar wannan abakin Malam”

Uwar gidan ta girgiza kai.

“Aa ai na fada mata ba mu san wani abu da Malam ya siye ya ce na wani ne ba, sai
dai idan sheri za'ayi masa anji ya bar dukiya a haka kai da mutanen birni azo ace
za a kwace”

“Aiko ba zata sabu ba, komai ai sai da hujja ake yinsa, Malam yana kafa shaida idan
zai siye abu, har takardu ana yi sai dai wutar da ta kone komai yasa ba a tsira da
takardun ba, amman shaidu ai suna nan da ransu, babu wanda ya isa ya zo mana daga
wani guri da sunan dan boko ya karbi duniyar Malam, idan ma manufar ku kenan to tun
wuri ku tashi ku kama hanyar garinku ko na tara muku mutane yanzu nan”

Hajiya Kaltume ta daga kai ta kali mutumen da ya mike tsaye yana nuna mata kofar
fita bakinsa da asuwaki hannunsa kuma rike da carbi.

“Indai kai aminin Malam ne tabbas ka san gaskiya sai idan cinye dukiyar zaku yi,
zan tafi amman ba zamu kyale wannan maganar ba”

Ta dauki jakarta ta mike tsaye ta fice a gidan cikin bacin rai tsabanin shigowar da
ta yi da zullumi. A mota ta tararda Hajiya Fatee ta fito da kafafuwanta waje tana
zaune daga ciki ta jingina da motar.

“Malam ya mutu, kuma ta tafi da dukiyarmu amman na ke kin yi wauta Hajiya Fatee
kuma kin yi sakarci irin haka ake gudu daman, Malam be bar wata wasiya akan kudinki
ko gonakin da yake cewa ya siya miki ba, kuma babu wata shaida ke ma kuma baki nemi
ya baki shaidar komai ba lokacin da yake raye, yanzu ga irin ta nan nan ke baki ga
duniyarki ni kuma ba ni ga aiki ba kudin rakumi....!”

“Ni ai idai wannan abun ba zai tashi ba, kudin mai sauki ne indai wannan abin
kunyar ba zai bayyanar min ba to zan iya hakura da komai”

Direban ya kai dubansa garesu.

“Subhanallahi wai Malamin da kuka zo gurinsa ne ya rasu?”

“Ba a sani ba, ina ruwanka? Ka kama bakinka ka yi abun da ya kawo ka, ba gulma da
sa'ido ba”

“Ah Hajiya daga tambaya Allah ya baku hakuri, ba ni na kar zomon ba rataya aka ba
ni”

Ya bude da yake jingine ya shiga ya rufe.

“Shiga mota mu tafi Hajiya Kaltume, zancen gida da gona zamu yi tunanin abun da ya
kamata mu yi daga baya”
Hajiya Kaltume ta juya ta dayan bangaren ta shiga motar, tana kuka.

“Abubuwa duk sun lalace min, idan na taba nan wani gurin ne zai kwance, idan na
dawo ta nan wani gurin kuma sai ya balle, ina saka ran za'ayi min aiki na samu
sauki wannan rayuwa da nake ciki sai kuma mu zo mu tararda bakin labari wannan abu
da me yayi kama... ”

“Ke naki ai duk mai sauki ne, ni cw a ruwa tsundun kuma babu tudun dafawa”

Haka suka yi ta juya zancen suna bakinciki da kukan da ya mantar da su akwau


bandits a hanya, direban yana sauke su a gidan Hajiya Fatee yayi tafiyarsa. A bakin
kofar dakin Hajiya Kaltume ta zube zaune ta cire mayafi ta je jaka a gefe tana
kuka.

NAMRA POV.

Gaba daya ta jika screen din wayarta da hawayen dake zuba a idonta, hoton Captain
take kallona gurin da yake sanye da kayan sojoji yana daga tsaye aka dauke shi
hoto. Ta san ta yi rashi na har bada domin abu ne mai wahala a yanzu Captain yace
zai dawo ya aureta ko da kuwa ya rabu da Hurriya, ta san ba haramun ba ne amman ai
da kunya, ace miji ya saki kanwa ya auri yaya, kuma yadda ta san halin dan'uwanta
ba zai aminta ya aikata haka ba.

“Tun farkon zuwanki bangaren nan, ban miki komai ba sai alheri, ke kika saka na
canja ashe ma kara da na canja domin kin nuna min cewar ke ba halak ba ce mai
tausayi, kin raba ni da Salim na hakura ina murna Allah zai musanya min da ďan'uwan
sai kuma ki zo ki karbe min shi? Baki ji kunya ba? Kin raba yayarki da samari har
biyu?”

Ta runtse ido tana kuka.

“Ina sonka Captain ina sonka me yasa baka gane ba, duk zuwan da kake gidan nan baka
fahimci hakan ba? Ko kuma dai Hurriya ta dauke maka hankali ne saboda ta fi ni
kyau? Me ya rude ka ka auri yarinyar da ba ajinka ba, yarinyar da bata dace da kai
ba, irin wannan jihadin da ka yi a finafinai nake ganin yana faruwa, ko kuma a wasu
kasashen turawa amman ba gidab Malam Bahaushe ba, waya ce maka hakan zai baka
kwanciyar hankali? Me yasa zuciyarka bata shawarce karka aikata ba?”

A firgice ta bude ido ta kalli wayar da ke ringing, zuciyarta ta shiga shawarar ta


daga kiran na Salim ko kuma ta kyale shi. Bata gama yanke hukunci ba ta samu kanta
da amasa kiran.

“Hello”

“Namra... Ai da kin fada min dan'uwanki Captain zaku bawa auren Hurriya da ban
wahalar da kaina ina neman ta so ni ba”

Namra ta yi shiru hawaye na sauko mata.

“Na ji an daura aure a yau, ina taya ku murna, amman ki sani amana ba zata bar
dan'uwanki ba, ya ci amanata ya aikata abun kunya, ya aure budurwar abokinsa abokin
ma na kusa da shi, yanzu na gane dalilin da ya sa baya son ma na yi masa zancen
Hurriya ashe kansa yake yi ma campaign, kuma bukata ta biya tun da yayi nasara sai
dai ina son ku sani KARMA is real kuma kowa ya aikata mai kyau zai sani”
“Salim bana da masaniya akan komai, laifin ba na Captain ba ne na Hurriya ne, daga
mahaifiyarsa har mu ba musa san da zancen daura auren a yau ba, sai sanar mana aka
yi, wata kila ta yi magana da shi ne ta roki yayi mata haka, amman Captain ba zai
yarda a aikata hakan da son ransa ba, waye zai so ya auri Hurriya bayan duk abun da
ya faru a yanzu, kuma idonta ya rufe bata ganin komai a yanzu...”

“To me yasa ya aureta?”

“Shi ne abun da nake kokarin ganewa, ni kaina a rikice nake Salim...”

Be sake ce mata komai ba ya katse kiran, sai ya jefar da wayar a kasa ta fada a
gadonta tana kuka mai karfi, bata taba jin kaunar Captain ba irin yau bata taba
sanin tana sonsa so mai tsanani ba sai yau.

CAPTAIN JAMAL POV.

Babbar rigarsa ya cire ya juyo ya dauki wayarsa ya amsa kiran dake shigowa.

“Ranka ya dade barka da yamma”

“Barka dai Allah yasa akwai labari mai dadi”

“Akwai ranka ya dade, duk mutanen da ka aiko mana da sakon sunayensu mun kama wasu
mun bincike su wasu kuma mun musu barazana a waya sun goge posting din sun bada
hakuri, sai dai dukansu sun ga horunan ne a wani gurin ne suka kwafa suka yada
abun, su ma kuma duk mun bisu mun saka sun goge kuma sun bada hakuri, mutum daya ne
ya ce mana wani ya turo masa hotunan da bayani shi da aka turowa da kuma mu da ya
fadawa mun bincika account din sai muka samu an goge account din.

“Na gode sosai already a nan mun riga mun gane wanda ya aikata abun, daman dai
bukatar mu a batar da hotunan daga internet, thank you so much, zan tuntube anjima”

“Thank You Sir”

Ya sauke wayar Adaidaita lokacin da mahaifiyarsa ta biyo bayansa ta daga bangaren


Daddy. Kallonta yake yana rike da wayarsa har ta karaso inda yake tsaye tana
murmushin takaici.

“Congratulations ka yi aure Jamal, ka auri yarinyar da haukan ka yake nuna maka


kana sonta, alhalin kanka ka wulakanta, makiyi zasu mana dariya su maka, ka zama
abun kwatance a cikin sa'ainka da friends dinka, saboda ka auri makauniya kuma
yarinyar da a yau idan na bude data na zan iya ganin siraicinta, wani ya rigaka
taba jikinta, yarinyar da mahaifiyar da kuma kaf danginka ba a maraba sa zuwanta
amman a haka farinciki kake kana jindadin ka samu mata, a daura aurenka a cikin
gida, daga mahaifinka sai masu aikin gida sai uban yarinya, kai da ya kamata duniya
ta san ka yi aure labarin aurenka ya cika kafafen sada zumunta sai gashi ya kare a
karamin gida kamar wanda ya aikata sheri”

Ya rage tsawonsa ya zauna akan gado.

“Ammy na san baki son yarinyar nan, ba zan iya sakawa ki so ta ba, amman dai ina
son ki sani ni dai ina kaunar yarinyar nan irin kaunar da ban taba jin ina yi ma
wata mace ba, kuma jifanta da kike da kalamai marasa dadi ni kike gogawa bakinciki
domin ita din matata ce a yanzu”
Ta kara yin murmushi tana daga gira.

“Haka ne Romeo uban soyayya, matar ka ce tabbas babu wanda ya isa ya goge wannan,
ni kuma uwarka ce na fi matarka karfin ikonka a kanka, kuma har abada ba zan taba
karbar Hurriya a matsayin suruka ba, ba zan taba sonta ba”

Har ta juya sai kuma ta juyo ta kalleshi ta nuna shi da yatsa.

“Jamal ni na haifeka ka nuna min karfin soyayya, mahaifinka kuma ya nuna min karfin
iko, ni kuma a yau zan nuna maka karfin hakki...”

Da kakkausar murya ta fada masa haka ta juya ta fice daga dakin. Captain ya soke
kai kasa damuwa na baibaiye shi.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Bayan kwana biyu....

After ya yanke kiran da ya shigo daga Ethiopia, cikin rashinya sauko da kafafuwansa
ya sauko daga kan gadon cikin rashin kuzari, ya saka bedroom slipper dinsa ya nufi
kofar falon ya bude ya fita. Downstairs ya sauko ya nufi falon kakarsa Hajiya Nene
ya zauna a kusa da kakarsa yana gaisheta. Sai ta kai hannu ta taba jikinsa ta amsa.

“Lafiya Kalau Jamal ya karfin jikin?”

“Alhamdulillah”

Ya kalli Ammynsa dake zaune sanye da doguwar rigar abaya kanta babu dankwali.

“Ammy ina kwana?”

“Lafiya Kalau, ka ci abinci?”

“No zan ci anjima”

“Haka ka sabawa kanka da wannan dabi'ar baka son cin abinci? Saboda ka daga min
hankali ne?”

Ya kasa daga ido ya kalleta.

“You fake it ko Captain? Tun ranar da mahaifinka ya bar garin nan baka sake sakin
jikin ba, abinci ma baka son ci”

Ko bata fada masa kai tsaye ba ya fahimci abun da take nufi.

“Ammy an faking ciwo ne? Bana yin komai saboda na daga miki hankali. Tashin
hankalin tashin hankalina ne”

Ya kalli wayar hannunsa ya mike tsaye.

“Bari na amsa wannan kiran”

Ya fice daga falon. Ammy ta bishi da kallo

“Da gangan yake wannan abun”

“Da gaske ba shi da lafiya, na taba jikinsa yanzu da zafi sosai, ki kalli
idanuwansa ki gani yaddda suka sauya alamar zazzafi yana damunsa sosai kuma ya rame
sukuninsa duk ya sauya, Turai karki zama irin sukunan mana masu kishi da matan
yayansu”

Ammy ta juyo ta kalli In-law dinta.

“Ba kishi nake da yarinyar ba, Allah ya tsare ni ba zan taba zama daya daga cikin
irin wadannan iyayen ba, kawai ba ma the same team ne, ke ma kuma kina goya masa
akan abun da kowa ya san ba daidai ba ne a gidan”

“Miye ba daidai ba? Goyo masa akan abun da addinin be haramta ba? Ko kuma son abun
da danki yake so? Ke ce ba daidai ba, tun a ranar da aka daura auren yaron nan baki
bar shi ya fita ko'ina ba, kin tsare shi a gida kamar mace gashi nan kin haifar
masa da damuwa”

“Idan ya fita ma babu inda zai je, already yayi received email daga gurin aikinsu
sun aminta sun ba shi sati biyu ya huta, to me zai fita yayi a waje?”

“Namiji ne shi fa, yana da abokai yana da guraren zuwa da yawa yarinyar nan ma tun
da aka daura aurensu ba ki barshi yaje ya ganta ba, Turai duk wanda zai so ďanki
yana bayanki ne, domin ke kika haife shi ke ya kamata ace kin fishi son abun da
yake so, ba shi kanwa ko yayar da zai ti shawara da ita akan Matsalar rayuwarsa ke
ce uwa da ke zai yi shawara a komai, yanzu kuma kin juya masa baya kika kokarin
cilasta masa ya zaba tsakanin rayuwa da mutuwa”

“Hajiya abun da yarinyar nan ta yi yayi tsauri da yawa, ko da kuma bata aikata ba
ni bana sonta bata cikin irin jerin matan da nake son Captain”

“Saboda dake za'a daura musu aure ko ba da Captain kuma ke zaki zauna da su ba
Captain ba, ko a gidan karuwai ya dauko ta tun da har ya nuna yana sonta ya kamata
ki so ta kema, balle kuma har igiyar aure ta shiga tsakaninsu ai zance ya kare,
tarewar ki a nan ba zai hana Jamal ya gana da matarsa ko ta tare a gidansa ba, na
san duk saboda shi ne kika aminta ki bi mijinki”

Ammy ta bata fuska sosai tana jin ta wani bangaren kamar bata kyautawa danta ba,
sai dai ita ma kuma ba su kyauta mata ba, sam bata son Hurriya a matsayin suruka.

“Ba gori nake miki ba, amman lokacin da Aliyu ya gabatar mana ke a matsayin matar
da zai aura, ba mu ce masa fa wanda muke so, sai kuma karba muna murna da addu'ar
alheri, mu dai muradin mu ya auri wanda yake so ba wanda mu muke so ba, so da yawa
mu kan ki abu ya zame mana alheri, kuma mu so abu ya zame mana sheri”

‘Gorin dai kike min Hajiya’


Ta fada a ransa a zahiri kuma sai ta mike tsaye ta dauki hijabinta dake gefen
kujera ta saka ta fice daga falon. Sama da haura zuwa dakin da Captain yake, tana
tura kofar dakin ta ji karar unkurin aman da yake daga bandakin dake bude, tsantsar
soyayya da kulawa irin na uwa sai ta karasa gurin da sauri hankalinta a tashe.

“Da gaske baka da lafiya ashe”

Ta taba wuyansa zuwa kansa ta ji shi da zafi sosai, da kanta ta kunna lap ta wanke
masa baki kamar wani karamin yaro.

“Mu je asibiti yanzu”

“Zan iya kira likita ya zo gida ya duba ni”

“Aa asibiti zamu tafi”

Ta cikin tsananin razani da tsoron kar wani abu ya samu danta. Sakinsa ta yi ta
fice daga bandaki da sauri. Tawul ya dauka ya goge fuskarsa idonsa har wani ja suka
yi alamar jikinsa ya saki saboda Fever, haka ya fito bandakin yana jin aman kamar
be gama yi ba, kofar bandakin ya rike yana jin yawun bakinsa na tsinkewa. Sai ga
Ammy ta shigo tare da Momy Ikilima

“Mu tafi ga direba can a waje”

“Ammy ba wani ciwo ba ne da zaka daga hankalinki ba”

“Ban taba baka umarni ka aikata a take ba tare da ka yi min musu ba, haka last time
na ce maka zamu tafi England a duba lafiyarka baka yarda”

Ammy kamar zata fashe da kuka take maganar. Ganin haka ya saka shi nufar gurin da
ya aje wayarsa ya nufi wayar ya dauka.

“Mu tafi”

Gaba ta saka shi, kamar wanda zai gudu sannan ta bi bayansa ita da kanwar mijin
nata.

“Zan iya tuki ba ni key”

Ya mikama Direban hannu, direban ya kalli Ammy. Sai ta girgiza masa kai.

“Ka bari ya kai mu ina zaka iya tuki yadda jikinka yake da zafi nan”

“Ammy ciwon nan be kai yadda kike tunani ba, zan iya tukin nan da kaina”

Ya rufe baki yana karkata dubansa ga motar Salim da ya faka kusa da wata motar
gidan. Captain ya bude motar zai shiga Salim yayi hanzarin bude tasa motar ya fito.

“Captain...”

Be amsa shi ba kuma be fasa shiga motar ba. Ammy ta kalli Salim din ta kalli ďanta.

“Salim ne”

“Na san shi ne Ammy mu tafi”

Salim na isowa gurin ya gaishe da Ammy da yar kunyarsa kunshe a aljihu.


“Lafiya Kalau Salim”

“Fita zaku yi?”

“Eh Captain za mu kai asibiti”

“Ba shi da lafiya ne?”

“Eh”

Salim ya kalli Captain din da baya son kallon gurin da Salim din yake tsaye ya mika
masa hannu.

“Hi”

Captain ya kalli hannunsa ya kalli fuskarsa, sai ya amsa masa ba tare da ya mika
masa hannun ba.

“Hi”

“Come on mu bar abun da ya faru ya wuce mana, ba yara ba ne mu, mun samu rashin
fahimta kuma mun hau dokin zuciya, amman ba zan bari wannan abun ya lalata alakarmu
ba, we're friends for more than 15yrs now wannan dan karamin abun ba zai bata
alakarmu ba, na san na yi ba daidai ba a wani gurin kai ma kuma ka zafafa I'm
sorry”

Salim ya sake mika masa hannunsa a karo na biyu, sai dai wannan karon na neman
kawarda fadan dake tsakaninsu ne, ba irin na dazun ba da yake na gaisuwa. Wannan
karon ma sai da Captain ya dade yana kallonsa hannunsa sannan ya mika masa nashi
hannun ba tare da yace komai ba. Ammy ta yi murmushi.

“Ko ku fa, amman ace mace zata shiga tsakaninku kamar ba maza ba? Ban jidadin abun
da ya faru ba kuma daman ina da kudirin na shirya tsakaninku”

Still Captain be ce komai ba, Ammy ta bude baya ta shiga tare da Momy Ikilima dake
yaba yadda Salim ya fi karfin shaidan ya kawar da girma kai ya kawo kansa. Direban
ya ja motarsu zuwa asibiti Salim kuma ya shiga motarsa ya bi bayansu. Sai da aka
fara diban jininsa aka auna bayan likitan yayi masa tambayoyi sannan ya ba shi gado
domin har yanzu akwai gajiya a tare da shi kuma yanayin jikinsa ya tsananta sosai.
A take aka saka masa drip Ammy ta tare a dakin tareda Salim hankalinta a tashe ta
fita dakin tana sanar da Daddy. Momy Ikilima kuma ta koma gida dare da direba domin
sanar musu halin da ake ciki da kuma dauko wasu abubuwa da ake bukata. Sai dakin ya
zama daga Salim sai Captain da idonsa yake rufe hannunsa kuma yake sanye da
cannula.

“I'm so sorry akan abun da ya faru, gaskiya ta bayyana yanzu kuma za a yadawa
duniya cewar Hurriya bata aikata ba”

“Matsalata da kai ba akan Hurriya ta aikata ko bata aikata ba ne, so please sunanta
ya fita daga bakinka, matsalar sa muka samu saboda na karya hannun Adam ne so mu yi
magana akan haka kawai”

Salim yayi ya dan tabe baki.

“That's right... Adam yayi abun da kake bukata an turawa mahaifinka video kai ma
kuma na turo maka ka duba whatsapp dinka”

Captain ya bude idonsa ya kai hannunsa na hagu ya ciro wayarsa ya bude whatsapp
dinsa, suna ganin Salim ya fara budewa kamin ya sauke video kiran Daddy ya shigo
wayarsa ta whatsapp video.

“Daddy”

“Hi Jamal... Yanzu Ammynka take fada an baka gado a asibiti, haka ne... ”

“Eh amman da sauki ba yadda take daga hankalinta ba ne...”

Salim ya juya ya fice daga dakin, yana rufe kofar dakin Ammy na kawowa bakin kofar
dakin, ganin Salim sai ta fasa shiga ciki.

“Ina son magana da kai Salim”

“Okay Ammy, zamu iya yi a nan ko sai mun tsada”

“Idan muka matsa zai fi”

Ya fara takawa ita ma ta taka sai suka jera suna tafiya.

“Amman ina son na sake yaba maka ne akan kokarin da ka y na kawar da komai a ranka,
kuma ka bawa Captain hakuri duk da kasancewar ta wani bangaren ka fi shi gaskiya,
na jidadin haka domin idan baka yi ba na san Captain ba zai taba iya aikata abun da
ka aikata ba, ka san halin abokinka”

Salim yayi murmushi.

“Nasan halin kayana Ammy ba sai kin fada min ba, shiyasa ai na bada hakurin da
kaina, ni kuma na fahimci ban kyauta ba ta wani bangaren and be kamata na bar
yarinyar kamar Hurriya ta raba ni da Captain”

“Good na jidadin dawowarka sosai, daman ina neman wanda zai taya ni fadan nan domin
ni kadai nake yakin nan a gidana, Engr yana goyon bayan Captain yan'uwansa kuma
basa son fada masa gaskiya saboda Engr, yau ma Hajiya Nene fada ta yi min tana
ganin kamar kishi nake da yarinyar nan ni kuma ba kishi nake da ita ba i just can't
find any reason da zai saka na so ta, i know da cousin dinka aka aikata abun nan
amman ko da ba gaskiya ba ne ai wannan abun ba zai shafe a idon duniya ba”

Ya tsaya daga tafiyar da yake.

“Why are you telling me this Ammy?”

“Bari na tambaye ka tsakaninka da Allah... Shin zaka iya auren yarinyar nan a
lokacin nan?”

“Ba zan iya ba, ko a gaba balle a yanzu na jinjinawa Captain yayi kokari kuma yayi
jihadin da ba kowa sai iya ba”

“To me yasa ba zaka taya ni fada masa gaskiya ba? Ka lurar da shi ta wani gurin da
kurakurai suke mana”

“Idan na yi hakan zai bata alakarmu da shi ne akwai, ba zai fahimta ba kuma sai yi
tunanin na zo ne saboda na daga masa hankali na hana shi zaman lafiya da Hurriya ko
sonta yadda ya dace”

“Cikin Hikima zaka yi Salim, wannan taimako a gareni da kuma shi kansa abokinka,
Wallahi bana son auren”

“Amman an riga an daura ai Ammy meyasa baki hana ba kamin a daura”


“Babu wanda ya sanar min da cewar za'a daura, mahaifinsa ya shigo gida ne kamar
haka ya sanar mana sun je jaje kuma yin nemi aurenta an ba su har an daura,
yarinyar da bata gani ma amman idonsa ya rufe ya rantsa sai ya zauna da ita”

Salim ya sauke ajiyar zuciya ya saka hannayensa aljihu.

“Yarinyar nan bata cancanci Captain ba ko kadan ko da kuwa bata aikata ba, ya
kamata ya lura da yadda duniya take kallonta a yanzu, amman kin san Captain ba a
masa daidai, kawai dai mu saka masa ido zai fi”

“Kai ma dai ba zaka iya ba kenan...! Babu wanda yake iya fahimtata”

Ta cige baki tana kallon wani ward din dake facing dinsu, Salim ma gurin yake kallo
sai dai kowa da kalar tunaninsa. After Salim ya fice Captain ya tashi zaune

“Ina fatan dai ba wata matsala ta ja rashin lafiyarka ba?”

“Aa rashin lafiya ne kawai babu wata matsala Daddy”

“Ma Sha Allah, daman ina da niyar kira na maka albishir sai kuma Ammynka ta sanar
da ni ciwonka a take tawun giwa ya take na rakumi”

“Akan Adam ne?”

“Ka ga video ne?”

“Aa zan sauke kenan ka kira ni, amman Salim ya fada min Adam din ya aikata abun da
ake bukarta ya aikata”

“Ya aikata yayi kamar yadda muke bukata, mahaifinsa ya turo min da video, domin ya
kara kira bayan ya tafi gurin mahaifin yarinyar be yi nasara saboda na yi waya da
shi na fada masa duk irin magiyar da za su masa kar ya aminta da su, sai kuma ya
dawo ni ma yana rokona sai dai ban bashi wata amsa ba bayan wanda ka bashi, kuma na
tabbatar masa a jibi Monday za a shiga kotu, sai gashi yau ya turo min da video”

“Na jidadin hakan Daddy thank you very much, da goyon bayanka ne na samu wannan
nasarar, zan yada video, na san hakan zai wanke yarinyar nan ko da ba gaba daya ba,
zata yi farinciki idan ta ji i wish ni zan fada sanar mata ma saboda na mata wannan
alkawarin”

Daddy yayi murmushi.

“Yaron ma abun tausayi, kaddarori ne kawai da rashin tunani irin na yaran yanzu,
jiya ma na yi waya da Hajiya nake tambayarta zuwa yaushe ne ya kamata ace Hurriya
ta tare saboda damuwa a yanzu matsalar idonta ne, ina son ta dawo karkashin ikonmu
ne gaba daya sai a nema mata maganin hakan zai fi armashi da ace tana gidansu za'a
nema, sai dai Hajiya tace min mu daga kafa zuwa nan da kwana biyu zata tafi ita da
Hajiyar Maru sai su yi maganar tarewar domin abun ne da ya danganci mata, kuma na
bata sako ta fadawa iyayenta mu dai yarinya muka aura ita muke so, ba dan mun raina
arzikin ubanta ba, amman ba ma bukatar komai daga garesu zamu zuba komai daga nan
garin da zata zauna har zuwa inda aiki zai kaika”

“You're best Dad ever samun irinka Daddy sai an tona, Hurriya ta yi sa'ar samunka a
matsayin suruki”

“Akan kawo mana neman taimakon auren wasu ma mu yi balle kuma naka? Jamal ba dan
kana son yarinyar nan ba no a kashin kaina yarinyar ta ba ni tausayi na halin
rayuwar data samu kanta, ina tunanin idan da ace yata ce ya zan ji, yarinya karama
an bata mata rayuwa da suna akan abun da bata aikata ba”
“Akwai matukar tausayi Daddy, amman Ammy ta kasa gane haka”

“Zata gane Son.. Zata gane.. Matsalar da aka samu Ammynka mace ce mai matukar son
riya da alfahari ba irin wannan auren take son ayi ba, kuma su mata suna da wannan
dabi'ar da rike abu balle kuma bata son yarinyar, dole sai ka yi hakuri with time
zata fahimceka..”

“Ina fatan haka”

“Bari na barka ka huta, zan aikawa mahaifinta da video yanzu, na san ba zai masa
dadin kallo ba, amman ya kamata ya san gaskiya kuma ya san matakin da zai dauka ko
dan nan gaba, amman da zaka hakura da yadawar wata kila zai fi, ya zai ji idan aka
ce yarsa ce ta aikatawa yarsa haka?”

“Daddy idan video be fita ba taya za a wanke Hurriya? Cikin alkawarin da na yi mata
na fada mata cewar sai na yada wanda yayi mata wannan abun fiye da yadda aka yada
hotunanta”

“All the best... Get well soon”

“Thank you Daddy”

Ya fita daga video call din ya sauke video da Salim ya turo masa yana kalla, a take
ya ji kamar an yaye masa ciwon dake damunsa saboda farincikin yadda Adam ya bada
labarin komai a video kamar yadda ya fadawa Captain da iyayensa banbancin wacan
video da wannan, wannan video shi ya dora shi da kansa a shafinsa na tiktok kuma
yana sanye da tufafi na kamala har da hula kamar mutumen arziki. Bayan ya gama
kallo ya jira Ammy a wayar sai ta amsa tana shigo dakin domin tana daf da kofar
dakin ne a lokacin da ya kira wayarta.

“Lafiya? Allah yasa ba jikin ba ne”

Ta karaso gurinsa da sauri. Captain dake jin kamar yau ce ranar angoncinsa ya
mikawa Ammy wayar yana dariya.

“Ba shi ba ne, duba wannan ki gani”

Ta karbi wayar ta kunna video ta kalla, sai ta tabe baki ta zauna.

“Still dai ba zai goge hoton tsiraicin Hurriya da yake idanuwan mutane ba, kuma
hakan ba zai hana ace kasan yarinyar nan da aka yada hotunan ta da wani saurayi ba?
To Captain take auren yaron Engr A A Turaki ba”

Far'ar dake fuskar Captain sai ta soma disashewa, doman yayi tunanin hakan zai cire
wani abu daga tsanar da Ammy take ma Hurriya.

“Tun farko kina kiyayya da ita ne saboda kina taya Momy kishi ne kawai saboda tana
yar mijinta kuma Momy bata son Hurriya, Namra ma bata sonta, da kunnena na ji komai
Ammy, kiyayyar da kike yi ma Hurriya ba na abun da ya faru ba ne kawai idan saboda
shi ne ai kaddara ce da bata wuce kan kowa ba”

“Haka ne, shiyasa mahaifinka zai yi mata komai ai, da yar wani mai arzikin ka aura
kamar mahaifinka, ai ba zai yarda da wannan ba”

“Shi ma ai be riga ya yarda ba, domin ba a taya masa ba kuma babu tabbacin zai amsa
ko akasin haka shi ma yana son yarsa...”

Ya koma ya kwanta ya rufe idonsa...


*** *** ***

Cike da girmamawa Appa ya amsar wayar sukirinsa ta bangaren biyu, suka gaisa cikin
mutunci da far'a Daddy ya tambaye shi rayuwa da kuma kasuwa suka ya amsa masa da
hamdallar Allah.

“Daman na kira ne akan maganar Hurriya...”

Daddy ya dan yi shiru.

“Akan maganar tarewarta ne?”

“Eh to...ba makasudin kenan ba, amman saboda ka fadi hakan bari na ce har da shi da
na bar mata su yi wannan aikin ne”

Appa yayi murmushi.

“Daman ina da niyar na yi maka magana akan hakan, saboda ina neman Alfarmar ka daga
mana kafa har zuwa ta samu lafiya, yanzu haka na fara shirye shiryen abun da ya
dace ayi ne akan idonta, abun ba zai yi kyau ba amarya da makanta...”

Daddy yayi hanzarin tariyar numfashinsa.

“Ka kawar da wannan maganar, yanzu neman lafiyarta da cinta da shanta a abu ne da
ya rataya a wuyan mijinta, kusan shi ne makasudin da ya saka nake son ta tare ai,
saboda ya zama tana hannunmu mu zamu yi mata komai, ba lafiyarta kadai ba Alhaji
Haruna har wata hidima da zaka yi akan Hurriya tun daga kayan daki har koma mun
dauke maka”

“Aa aa aa sam ba zan karbi wannan ba, na san kan yi kokari amman wannan bangaren
kan a bar min shi, yarinyar tana daya daga cikin yaran da nake alfahari da su, kuma
idan ban sakawa Hurriya na yi mata hidima mai kyau ba da me zan saka mata? Ni zan
yi ma yata komai idan ka yi min haka ai kamar ka raina nawa arzikin ne ko kuma na
ganin zan gaza ni kuwa zan baka mamaki”

Daddy ya ce.

“Ba wannan ba ne duka na so na yi hakan ne saboda kyautatawa, amman ba zan hana ka


Allah yasa hakan ne mafi alheri”

“Ameen na gode sosai Allah ya bar zumunci”

“Ameen Ameen. Akwai video da zan aje maka a whatsapp yanzu, video ne da Adam yayi
yake ba da hakuri na abun da yayi kuma yake fadar gaskiyar abin da ya faru, wanke
Hurriya sosai a video”

“Maa Shaa Allahu Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Allah na gode maka


Alhamdulillah”

Appa yana ta maimaitawa cikin farinciki.

“Sai dai bana son Hurriya ta ji a yanzu, kuma ina rokon Alfarmar ka kai Hurriya a
asibiti yanzu ta duba mijinta ba shi da lafiya yana can kwance an saka masa drip”

“Subhanallahi, me yake damunsa”


“Ba wani serious ciwo ba ne fever ce kawai”

“Toh ranka ya dade zan yi hakan, kuma ni ma zan je na duba shi anjima”

“Na gode”

Daddy ya yanke jiran, Appa kuma ya shiga whatsapp dinsa ya kama number Daddy yana
ta jiran sakonsa. Dilll sakon ya fado a wayar video ya fara bude kansa, daga kasan
video kuma address din asibitin da Captain yake ne.

Natsuwa sosai Appa yayi yana kallon yadda Adam ya fara bada hakuri da neman yafiyar
Hurriya hannunsa da dauri, kana ganinsa ka san baya cikin farinciki kuma ya sha
wahala domin jikinsa ya nuna haka, daga bisani ya koro da bayanin yadda abubuwan
suka faru. Appa na zaune a office dinsa sai gashi a tsaye yana kallon video cikin
firgici da mamaki yana jin duniyar gaba daya kamar mafarki.

“Khairy... Umm Khairi... Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ya koma ya zauna, yana ta neman daukin Allah ta hanyar ambatonsa kamin ya sake
mikewa tsaye ya maida video baya ya kalla, ya sake kalla ya sake kalla.

“La'ilaha Illallahu... ”

Ya karasa a zuciyarsa domin bakinsa ya masa nauyi kirjinsa ya kau yaji, kansa yayi
nauyi har ya rasa abun da zai fara tunani. Ya aje wayar a tebur ya zauna yayi shiru
na wasu mintuna yana kallon wani gurin kamin ya soke kai kasa yana sauke ajiyar
zuciyar da ta ki sauka a zuciyarsa. Tunanin yake ta ina ya gaza a matsayinsa na
uba, ta ina ya kyautata ta ina ne be kyautata ba? Me ya kawo haka a cikin familynsa
ga yaran da suka shi ya haife su? Ya kai hannu ya dauki wayarsa ya shiga contact
dinsa ya nemo number da ya kwashe shekaru be ji daga gareta ya kira. Sai da jiran
ya yanke ya sake yin wani shi ma ya yanke a uku aka daga.

“Assalamu Alaikum”

Appa baya iya amsa sallama a yanzu dan haka be amsa ba, maganar ma kamar wanda aka
dannewa numfashi haka yake yinta.

“Zan aiko da mota yanzu, za a dauki Hurriya taje asibiti ta duba mijinta ba shi da
lafiya”

“Wane irin magana ne wannan? Tun da ace mana an daura auren nan yau kwana biyu
mutunen be zo ya ganta ba, fari ne ba ki ne mu ba mu san kamaninsa ba, sai kuma
yanzu ka ce zata je ta duba shi?”

Ya daga yatsansa yana nunawa kamar ance masa tana gabansa a zaune.

“Dan Allah Iyami karki musa min, karki kara min bakinciki da bacin da nake ciki a
yanzu, baki san halin da nake ciki ba matukar ba so kuke na fadi na mutu ku huta...

Jin wannan kalamin ya saka Amma bata sake cewa komai ba har Appa ya kashe wayar,
Direbansa dake gida ya kira ya fada masa yaje ua dauki Hurriya ya kaita asibitin,
sannan ya dayan direbansa ya fada masa ya kunna mota za su tafi gida yanzu nan.
Yasir ne last mutumen da ya kira ya fada masa ya same shi gida yanzu nan, sannan ya
mike tsaye cike da nauyin zuciya irin na uban da yake jin kamar ya gaza ta wani
bangaren ya fice daga office din.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Amma ta kalli Gwaggo mamakin bayyane a fuskarta.

“Alhaji ne, wai zai aiko da direba a dauki Hurriya ya kaita asibiti ta duba
mijinta”

Gwaggo ma mamakin ne fal a ranta.

“Ba shi da lafiya ne?”

“Da alama kam, amman Gwaggo ta ya zata tafi duba shi mutunen da be taba zuwa gidan
nan ba tun da aka daura musu aure ni ban san shi ba shi ma be san ni ba?”

“Ko dai shi ma baya son auren ne? Ko kuma marar lafiya ne aka aura mata?”

“Shi nake tunani Gwaggo, kar abun yayi ma Hurriya yawa, na ji mahaifinta ma kamar a
cikin damuwa”

“Allah dai ya kyauta, wannan abun da daure kai yake”

“Kuma kin ga Kaltume da Nafisa ba za su so Hurriya da alheri ba, za su iya zugawa


mahaifinta ya aura mata kowa saboda ta sha wahalar rayuwa”

“Amman a yanzu ina ganin kamar Alhaji ya fara dawowa hayyacinsa ai, Allah dai kadai
ya san me yake nan”

Amma ta fada tana aje kofin maganin dake hannunta sannan ta yunkura ta tashi tsaye
cikin rashin kuzari irin na wanda be gama warkewa daga ciwo ba ta taka ta fita daga
dakinta. Dakin Rukkayya ta nufa domin a can Hurriya take rayuwa a yanzu, lalulen
dakin Amma ta fara yayewa sannan ta shiga dakin, Hurriya na jin yanayin tafiyar ta
Amma da bata gama kwarewa ba ta tashi zaune idanuwanta cike da duhu tana kallon
saitin kofar. Amma ta zauna kusa da ita tana kallonta.

“Hurriya ina son ki ba ni aron hankalinki”

Hurriya ta juya ta gefen da take jin muryar Amma ta mika mata dukan natsuwarta.

“Ba dan kina yata ba, hakika ke yarinya ce mai hakuri da sanin ya kamata, kuma kin
hadu da kalubalen rayuwa da kananan shekaru daman haka tsarin rayuwa yake, wani da
dadi wani babu, eani kuma na sirka masa, dan haka ina son ki kara hakuri akan wanda
kike da shi kuma ki karbi kaddara a duk yadda ta zo miki, a matsayi na uwa zan yi
ina nawa kokarin na ga baki cutu ba a rayuwar gidan aurenki, sai dai kuma idan na
hango wata matsala ko wahala da zaki sha zan tare ko da bani da karfi haka zan ta
yaki har Allah ya mu nasara”

“Na gode Amma”

“Allah ya miki albarka, Hurriya kin san mutumen da mahaifinki ya aura miki? Kin
taba ganinsa ko da sau daya?”

Ta yi shiru na wasu dakiku kamin ta daga kai.

“Na san shi”

“Marar lafiya ne? Ko yana da wata nakasa ko aibu?”

“Ba shi da shi ko daya Amma, a lokacin da nake gidan idan Momy ta hanani abinci shi
yake kawo min wani abu na ci, ko lokacin da Namra ta shake ni shi ya mareta yana da
kirki, amman yana da saurin fushi da zuciya kamar Hamad”

Amma ta ji sanyi a ranta jin kadan daga hallaya da siffar mijin da yarta ta aura.
Zuciyarta kuma sai ta karkata akan furucin Hurriya cewar Namra ra makureta.

“Me kika yi ma Namra ta makureki?”

Hurriya ta bata labarin abun da ya faru, Amma ta girgiaza kai, ta sani daman
jininta ba zai sha da dadin a gidan Momy ko Hajiya Kaltume ba. Ajiyar zuciya ta
sauke

“Appanki ya kira yanzu, yace direba zai zo ya dauke ki ya kai ki asibiti ki duba
mijinki wai ba shi da lafiya, ki shirya Rukkayya zata rakaki”

“Toh Amma”

Amma ta tashi ta fice daga dakin, Hurriya ta kai hannu tana tana awarwaron da
Captain ya saka mata a hannu da sunan wani abokinsa ya bata, tana jin kamar babu
dadin jin cewar ba shi da lafiya, ko dai baya son auren ne dole aka masa? Ko kuma
wani abu ya faru? Kwantawa ta yi kan tana tunani kala kala a ranta, zuciyarta na
raya mata taya mutum kamar Captain zai yarda ya aureta bayan duk abun da ake cewa
ta yi? Kuma gashi bata gani a yanzu, wata kila dai dole aka yi masa, amman kuma
yadda Momy take jinsa anya zata masa dole? Bayan Namra ta mata gargadi akansa Momy
ma ta yi mata. Sai da direban ya shigo sannan Rukayya ta shigo dakin ta saka Hijab
dinta ta sakawa Hurriya ta kama hannunta suka fita Amma na Allah ya tsare, Gwaggo
kuma na fada mata idan ta shiga ta gaishe da kowa.

CAPTAIN POV.

Idanuwan da ya rufe ne ya sake budewa sakamakon bude kofar dakin da aka yi, Salim
ya sake dawowa hannunsa rike da leda ya nufi gurin da aka tana da ya aje ledar
sannan ya kalli Captain.

“Sannu Allah ya baka lafiya, ga apple nan na san kana son Apple na siyo a waje ne,
anjima zan dawo Allah ya kara afuwa”

Sannan ya kalli Ammy dake zaune.

“Ammy zan tafi sai anjima zan dawo Allah ya ba shi lafiya”
“Amin Salim an gode”

Har ya fice Captain be ce masa komai ba.

“Abun da kake yi wani lokacin baka kyautawa Captain, na san kana da fushi amman
danne zuciya ake, ko sai anjima baka cewa yaron nan ba, ba dan kana da aboki kamar
Salim ba da yanzu ba ku shirya ba, amman yana mutunkata yana sonka, duk abun da
kake masa baya dubawa yana nan tare da kai, duk da yana karkashinka yana baka girma
da kulawa na abokantaka ba na aiki ba”

Nan ma be ce komai ba, Ammy zata sake wata maganar wayarta ta yi ringing sai ta
mike tsaye ta fice daga dakin. Captain ya sauke ajiyar zuciya ya ya dan dago kadan,
ya sake bude wayarsa ya kunna video ya sake kallo.

“Ina fatan hakan ya saka ki farinciki Hurriya, and Sister nan da ta aikata miki
wannan abun i hope bakincikin da zata shiga zai ninka wanda ta saka ki”

Ya fita daga whatsapp din ya shiga contact dinsa ya kira Nafi'u. After sun gaisa ya
gabatar masa da bukatarsa.

“Asiri na tuno na abun da ya faru da yarinyar nan so zan turo maka video yanzu ina
son ka yadashi iya yadda zaka iya, ya karade ko'ina a kafofin sada zumunta Please”

“Za'ayi haka ranka ya dade ka aiko da video”

“Okay, ba zan baka komai ba a yanzu dai na ga yanayin aikinka, idan ka cancanci da
yawa zan baka”

“Zaka gani Sir”

Ya sauke wayar ya sake komawa Whatsapp dinsa yayi masa sharing din video. Ya sake
kiran wani yayi requesting irin abun da ya bukata a gurin Nafi'u shi ma ya tura
masa video sannan ya koma ya kwanta. Bayan kamar minti talatin ya ji an bude kofar
dakin sai ya sake bude idonsa Rukkaya ta fara daga kai ta kalli sake kallon kofar
dakin domin ta tabbatar nan din ne sannan ta kasara turo kofar dakin tana sallama.

“Sallamu Alaikum”

Be amsa mata ba domin be san ta ba, be kuma san manufar shigowarta ba har sai da
Hurriya ta bayyana a bayanta.

“Oh My god”

Ya tashi zaune da sauri farinciki ya cika fuskarsa, hannu ya saka ya kashe ruwan ya
cire a hannunsa ya rufe gurin da jinin zai iya biyowa sannan ya mike tsaye ya
gyara rigarsa kamar ance masa Hurriya tana ganinsa. A tsakiyar dakin Rukkayya ta ja
ta tsaya tana kallonsa.

“Direban Appan Hurriya ne ya ce mana nan zamu shigo, dan Allah ko kai ne Jamal?”

“Yes... Angon Hurriya”

Ya fada yana nufar Hurriyar dake bayanta tana rike da hannun Rukaiyah. Hannunsa ya
kai ya kama dantsen hannunta ya rikata yana kokarin fitowa da ita bayan Rukayya.

“Assalamu Alaikum”

Hurriya ta fada tana jin tsoron da wani yanayi na dabam, domin wani be taba kaiwa a
jikinta haka ba a take jikinta ya fara rawa. Murmushi Captain yayi Rukaiya ma ta yi
murmushi tana mamakin a yadda ta samu Captain domin dukansu ba su saka ran namiji
ne mai kyau da tsari da cikar kalama ne ba irin Captain.

“Ban san ya kike da Hurriya ba, dan Allah ce ta sake hannunki ko kuma ke ki sake
hannunta”

Ya bukaci haka ne saboda Hurriya ta ki yarda ta saki hannu Mama Rukaiya.

“Ni kanwar Mahaifiyarta ce”

“Oh Ashe mamanmu ce, sorry ban amsa sallamarki ba, a yafe min Momy”

Rakayya ta yi murmushi ta saki hannun Hurriya, Captain ya mika hannunsa ya rika


hannun da Rukkaya ta saki ya jata har gurin gadonsa ya zaunar da ita. Sannan ya
nunawa Rukkayya kujera.

“Bismillah”

Ta karasa ta zauna tana masa ya jiki.

“Alhamdulillah, ko da aka daura auren ba ni da lafiya shi ya hana ni fita ko'ina


balle na je na gaisa da ku mu san juna”

“Idan ka samu lafiya ai sai ka yi Allah ya kara afuwa”

“Amin thank you”

Ya zauna kusa da Hurriya yana kallonta. Baya bukatar tambaya ya san wannan duk
shirin mahaifinsa ne, dan haka ya dauki wayarsa yayi ma mahaifinsa text.

“Thank You, you're the best Dad in the whole world”

Ya aje wayar a gefensa ya maida hannunsa a gurin Hurriya dake matsawa a hankali
domin tana jinsa daf da ita.

“Ya jikin?”

A madadin ya amsa mata sai ya kalli dan space din dake tsakaninsu yayi murmushi,
wani kalar nishadi da farinciki ne zuciyarsa na ganin matarsa labarin zuciyaa
tambayi fuska in ji hausawa, sai yake jin ya warke daga fever ma. Rukayya ta mike
tsaye tana rike da wayarta.

“Bari na jira a waje”

“Dama dai kin wuce gida zai fi, domin Hurriya ba yanzu zata koma ba sai dare”

“Gwaggo bata ce na barta ba, cewa aka yi mu zo mu dubaka mu koma, direban ma yana
waje”

“Wacecw Gwaggo?”

“Kakar Hurriya mahaifiyata”

Captain ya dariya.

“Ashe ma kaka ce, idan kin koma ki fada mata mijinta ya riketa, daman ya fi Kaka
iko da ita”
“Zata min fada”

“Fada kadai zata miki ashe, Wallahi Hurriya ba zata koma yanzu ba, akwai maganar da
zan yi da ita so ki tafi kawai karamar uwa madaukar zunubi”

Babu yadda Rukayya ta iya bayan yi masa fatan samun lafiya ta fice daga dakin
Hurriya na ji kamar ya ce mata kar ki tafi. Captain ya matsa kusa da Hurriya
jikinsa na taba nasa daman ficewar Rykayya kawai yake jira.

“Ni kike gudu?”

Ta yi shiru tana jin kunya na rufe ta, sai ta ji dakin yayi mata girma daga ita sai
shi daman tana jin alamar kamar su kadai ne a ciki. Ya saka hannayensa biyu ya
zafaye ta ya dora wuyansa a kafadarsa.

“Fada min ya kike?”

“Lafiya kalau”

Ta amsa da sauri, tana kin bashi hadin kan tsuma yatsunsa a cikin nata. Ya sumbanci
kuncinta ya kalli gefen fuskarta yana kai dayan hannunsa ya taba Lips dinta

“Ki yi hakuri na mari dukiyata na fasa bakin nan da kaina, ban jidadi ba I'm sorry”

“Ba komai ya wuce”

Ta mike tsaye tana jin wani iri, ya sauke kansa kasa yana murmushi kamin ya mike
tsaye ya koma gabanta ya tsaya ya dafa kafadarta.

“Alhamdulillah komai ya wuce a yanzu ko?”

“Ya wuce a cikin gida, amman yana nan a duniya za'ayi ta kallona da abun ko da na
bar duniya”

Ya kura mata ido kamar mai kokarin kure kallonsa. A hankali ya zaunar da ita ya
zauna gefenta ya saka hannunsa a cikin nata ya kwantar da kanta a jikinsa.

“Abu mai muhimmanci a yanzu, mahaifinki be yarda kin aikata mahaifiyarki ma haka,
Ubangijinki ma ya san baki aikata ba, mijinki ma haka duk wanda zai zargeki a
bayansu ba shi da amfani”

“Kai ma ka yarda ban aikata ba?”

Yayi dariya marar sauti ya dagota daga jikinsa ya fuskance yana kallon kyakkyawar
fuskarta.

“Na yarda amman ban tabbatar ba”

“Zan iya rantse maka da kur'ane kamar yadda na yi ma Appa”

“Ban karyata ki ba ai, zan tabbatar da kaina, na gaba kadan”

“Yaushe? Me yasa ba saka tabbatar a yanzu ba?”

“Kin matsu ne?”

Ta daga mishi kai a bakin gaskiyarta, sai ya saki hannunsa ya mike tsaye yana
murmushi domin ya fahimcin bata gane dawon garin ba. Kofar dakin ya nufa ya bude ya
leka hagu da dama sannan ya dawo ya tsuguna a gabanta hananyensa a cinyarta yana
kallon fuskarta a dora, sai fara kokarin mikewa tsaye tana ture hannayensa.

“Babu wanda zai ce wani abu a nan, ni mijinki ne, halak malak, ni zan bawa duniya
shaidarki daga yanzu har karshen rayuwarki”

Ya kama yatsansa yana murzawa a hankali.

“Mai tsada na yi yadda zan iya na ga mutunci ya karu a idon duniya, na iya kokarina
na saka an goge hotunan wadanda suka wallafa hoton sun goge, sai dai wadanda ban
sani ba”

Ya sumbanci hannayenta duka biyu ya saka su a fuskarsa.

“I will fix what they broken, zan zama zama hasken da zai haska duhun dake
rayuwarki, zan yaye miki damuwarki, zan saka ki yi alhari da ni a matsayin miji, da
ace zan iya sauya lokaci na koma baya da na rayu da ke tun kurciya har tsufa,
saboda ina bukatarki a rayuwata, i will spend every hour of the day keeping you
safe Hurriya, na miki wannan alkawarin Hurriya, zan baki wata duniya mai cike
farinciki, duniyar da babu kuka babu damuwa babu tashin hankali babu tsana babu
kiyayya....”

Hawaye ke sauko mata jikinta yayi sanyi, ba a taba siyeta da kalamai masu dadin
irin na yau ba, wani be taba yi mata kalam kwantar da hankali kuma ta ji hankalinta
ya kwanta ta samu natsuwa irin yau ba.

“Is Okay is alright....”

Ya mike tsaye ya zauna kusa da ita ya share mata hawayenta.

“Ban taba fada miki wannan ba Hurriya, bari na fada miki yau.... I LOVE YOU... INA
KAUNARKI HURRIYA fiye da duk wani namiji da ya nuna miki soyayya a duniyar nan”

Wasu hawayen ne suka sake zubo mata, sai ya kai bakinsa ya sumbanci hawayen nata ya
hade goshinsa da nata yana goga mata hancinsa, numfashinsa da nata yana tarayya.

“Ina jin wannan din ma kamar mafarki ne”

Ta fada cikin sautin kuka, sai ya dora bakinsa akan nata ya rufe ido.

“Gaskiya ne... Zahiri ne wannan Hurriya... Lokacin da Daddy yace min mai tsada ta
zama taka sai na ji kamar ba a taba bani farinciki irin na ranar ba, saboda ke ce
Hurriya”

Yana maganar lips dinsa na taba nata, kamin ya bude idonsa yana kallon nata idon
dake rufe. Sannan ya sumbanci banki ya sumbanci hancin ya mike tsaye ya dauko
wayarsa ya dawo kusa da ita ya zauna.

“I have another surprise for you”

Ya kunna mata video sanin bata iya gani sai ya kara mata muryar a kunne. Kamin ta
gama saurare hawaye ya jika gaban hijabinta, sai ta kasa jin farinciki kuma ta kasa
jin bakinciki ta tsaya a tsakiya tana jin ba gaskiya ba ne.

“Taya yar'uwa ta jini da uba mai daraja ya hada su, zata aikatawa yar'uwarta wannan
abun? Ko dai sheri yake mata? Na san Yaya Khairy bata shiri da ni amman wannan yayi
muni, mai kiyayya da ta yi zurfi da kai ne kawai zai iya aikata wannan! Idan ma
bata raga dan ni ba ai ta rangwanta ko dan mutuncin gidanku, a karkashin inuwa daya
muke da ita wannan abun ya taba mutuncin kowa a gidan bata gane ba? Na ma kasa
yarda ita ce ta aikata haka”
Captain ya rumgume ta, domin kukanta a yanzu yana daga masa hankali.

“Zamu kara tabbatar da hakan nan gaba kadan, gaskiya zata kara bayyana”

Hurriya ya rushe da kuka a kirjin mijinta ta kamkame shi.

“Na tuna... Na tuna ranar da ta fita da ni... Ranar da tace na raka ta gidan
kawayenta, Yaya Khairy ta cuce ni yar'uwa ta cutar da yar'uwarta ta jini, me na
mata amman me na mata”

Captain ya dagota jikinsa da sauri ya rike fuskarta da hananyensa.

“I know this not easy, baki mata komai ba Hurriya, makiyinka baya bukatar ka yi
masa laifi sannan ya hukuntaka baki mata komai ba”

Ta saka hannu ta rufe bakinta tana girgiza kai, yayi mata nauyi yyi mata muni ace
yar'uwarta ce ta aikata haka. Ya sake rungume.

“Shiiiiiiiiiiiiiiiiiii wannan ya wuce yanzu, ita ya kamata ta yi kuka ba ke ba”

Be dagota daga jikinsa ba sai da ya tabbatar ta daina kukan. Sannan ya dagota daga
kirjinsa ya kalleta.

“Kin rame wannan abun ya saka miki damuwa sosai, yaushe rabon da ki ci abinci”

Ta kasa yin magana. Ya shafa fuskarta.

“Kina bukatar cin wani abu?”

Ta girgiza kai.

“Kwanta a nan ki huta”

Ya kwnatar da ita kan gadon na dora mata kafafuwanta sannan ya subancin fuskarta
goshinta da saman idanuwanta da suke rufe. A hankali ya sauke ajiyar zuciya ya
matso da kujera ya zauna yana kallon fuskarta, ya matsa da kujerar ya shafa
fuskarta zuwa hancinta yana gaba lips dinta. Can kuma ya matsa baya ya kalli drip
din da ya cire dazun, sai ya janyo karfen ya maida ruwan da kansa ya daidaita
komai a yadda yake, kana yayi relaxing akan kujerar yana kallon kyautar da Allah
yayi masa.

“Ajiyar da na baki ajiya ce ta har abada, na gode da kika ba ni hadin kai, lallai
kasancewa da Hurriya abu ne da kike muradi, akwai farinciki a auren matar da kake
so kake tausayi... Na ji hakan yau, na yarda na karba na aminta wannan din mai
tsada ce, ta canja min siffa, ta sauyan lissafina ta rike linzamina... I will take
every risk for her, i will bend the rules... Thank you.... She's my world... My
Hayatie... My Rayuwa.. Thank you for this cause I know you feel the same... ”

Yana maganar hannunsa dafe a saitin da zuciyarsa take aje, idanuwansa kuma suna ta
bawa abun da ruhi yake bukata... Mursa kofar dakin da aka yi ne ya saka shi juyo sa
kai ba dan ya gundura da kallon rayuwarsa ba ya kalli kofar. Daga Momy har Ammy
Momy Ikilima da Hajiyar Maru tsaye suka yi suka kallon ikon Allah, Hurriya na
kwance a kan gadonsa shi kuma yana zaune a kujera da drip a hannu.

“Minene haka? Me yarinyar nan take yi a nan? Waya kawo ta?”

Ammy ta tambaya a tsawa, Hajiya Maru ta yi hanzari tariyar numfashinta.


“Turai ki saurara mana”

“Hajiya haba mana? Yaron da bashi da lafiya aka kawo asibiti shi ne za a kawo ta?
Shi yana zaune a kujera da ruwa a hannu ita tana kwance a gadon asibiti? Makauniyar
me zata masa?”

Hurriya ta zabura ta tashi zaune da sauri sai kuma ta sauko ta yi tsaye gabanta na
bugawa da karfi, bata san su waye ba, bata ji muryar wadanda ta sani ba, gashi bata
gani balle ta matsa daga gurin. Captain ya mike tsaye ya kalli mahaifiyarsa cikin
damuwa.

“Haba Ammy kamar baki san wacece ita ba? Kin tsorata ta kuma ba laifin be laifina
ne... ”

“Really..... ”

Ammy ta furta tana masa kallon mamaki, sannan ta juyo ya kalli Captain din ta saki
jakar dake hannunta.

“The only thing you care about is her, baka yi tunanin ya zan ji idan na ganta ba?
To na bar mata sai ta yi jinyarka”

Ta juya ta fice, Hajiyar Maru ta bi bayanta tana kiranta, Momy kuma ta duka ta
dauki jakar da Ammy ta saki tana yi ma Captain mugun kallo sannan ta juya ta fice,
Momy Ikilima ce kadai ta iya karasowa ta aje kayan dake hannunta ta kalli Hurriya
ta kalli Captain sannan ta fice cike da takaici. Captain ya kama hannun Hurriya ya
rike

“Karki daga hankalinki da yawa Hurriya when i meet you i tell myself that i will
love you and protected you at any cost....”

Hurriya ta sake hannunsa ta dan matsa baya.

“Yaya... Ina son na tambayaka...”

“Ask me any question, zan amsa miki”

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Yayi murmushi ya matsa kusa da ita kadan.


“Babu ruwanki a wannan Ni kika aura kuma da ni zaki zauna karki saka damuwar kowa a
ranki”

Ta yi shiru.

“Zauna”

Ta kasa zaman kamar yadda ya bukata gashi bata gani balle tace zata tafi gida ita
kadai, gaba daya sai ta ji zaman a dakin ya gundireta.

“Dan Allah ko zaka kira a kai ni”

“Ba yanzu ba, nan zaki wuni sai dare zaki koma”

Ta yi shiru a karo na biyu bata son zaman kuma bata son musa masa, hakan kuma ta
kasa komawa ta zauna a gadon da Ammy ta tarardar da ita. Hankalinta be kara tashi
ba sai da Ammy ta dawo dakin tana ta masifa tareda Momy da Hajiyar Maru wadda ta yi
aikin bata hakuri har ta hakura ta dawo. Hurriya ta sauke kanta kasa duk da
kasancewar bata ganin komai.

“Ya jikan nata Jamal”

“Alhamdulillah”

Ya amsawa Hajiyar Maru.

“Allah ya kara sauki, zan tafi da amaryar taka sai mu sauke ta a gida”

Ya daga kai ya kalli matar da take zaman kakarsa.

“Hajiya bata dade da zuwa ba, Daddy ne ya saka aka daukota saboda ta dubani kuma mu
yi magana akan video da Adam ya saki na bada hakuri”

“Ko ma dai minene yayi wuri ace ta biyo sawunka, be kamata ace iyayenta sun barta
ta zo asibiti dubaka ba, makauniyace me zata yi a nan? Da iyeyenta sun san mutunci
ba za su yarda ta zo ba...”

Hajiyar Maru ta dakawa Ammy tsawa.

“Ba na ce ki cire bakinki ba? Ba na ce ki dauke kai daga wannan ba”

“Zan iya cire bakina amman ba zan iya dauke kai ba, ni dai bana maraba da auren nan
bana son yarinyar nan bata dace da ďana ba”

Furucin Ammy yayi daidai ta saukowar hawayen Hurriya sai ta kame jikinta sosai ta
natsu.

“Ai kara ta fada mata irin zaman da zata yi da uwar Captain tun a yanzu, gaba daya
gidan nan babu mai goyon bayan wannan bakin aure”

Momy ta dora da nata, tabbas da ba su suka fadi hakan ga Hurriya ba da sai gurin da
karfinsa ya kare amman ba zai iya musu da iyeyensa ba ba zai iya fada musu magana
marar dadi ba, saboda haka ya kalli Hajiyar Maru ya ce.

“Hajiya zan kira a dauketa”

Ya juyar da idonsa gurin Hurriya


“Kina da number wani da za a iya kira?”

Ta daga kai. Sai ya runtse ido ya bude hawayen dake mata zuba suna kona masa rai.

“Fada min...”

“08....0...”

Ta karanta masa number Amma sai ya kira kamin Ammy ta daga ya tambeyeta number waye
ta fada masa. Hakan ya saka shi natsuwa ya gaishe da Amma cikin mutunci da
girmamawa sannan ya ce.

“Hurriya ce ta bukaci gida, gashi kuma direban da ya kawo su ya tafi kuma wanda zai
kaita yanzu be san gurin ba, kuma kin ga akwai lalura a tare da ita ba zata iya
nuna masa hanya ba”

“Toh Rukayya zata zo ta tafi da ita yanzu”

“Toh na gode sai ta zo”

Ya sauke wayar, amman ya kasa daga kai ya kalli kowa. Ammy ta ce

“Ta jira wanda zai zo ya tafi da ita a waje ko kuma ni na fita na bar mata dakin
har sai ta tafi tukuna na dawo”

Sai Momy ta karbe mata.

“Aa ai ba ayi haka ba, ke da danki? Ita zata fita ta jira a wajen”

A nan ma Captain be dago kai ba kuma be ce komai ba, Hajiya Maru ta girgiza kai ta
isa gurin da Hurriya take ta kama hannunta ta fice da ita sai a lokacin Ammy ta
zauna.

“Duk abun da kuke yi ma Hurriya ni kuke yi ma ba ita ba, domin ni nake aurenta ba
zata iya kawo kanta dole a gareni ba, kuma da ban aureta ba ba zaku mata haka ba,
na gode da kalar soyayyarku na gode”

Ya fada yana taba wayarsa sannan ya dago ya kalli Momy ya ce.

“Momy ina son ki sani, ko da kaddarar mutuwa zata raba ni da Hurriya domin ita
kadai ce abun da zata raba mu a yanzu ba zan taba auren Namra ba, domin ban taba
sonta ba ban taba jin ina kaunarta ba, kuma abun da kike yi ma Hurriya ko kike ziga
Ammy ba zai canja komai ba, face kallon da nake miki na yar'uwa uba mai daraja zuwa
wani dabam, ina son Matata! Ni dai ina son ku san wannan”

Ammy ta saki baki tana kallonsa Momy kuma ta kasa rike zuciyarta.

“Namra ba kwantai ta yi Captain balle ka ce idan Hurriya ta mutu ba zaka aureta ba,
kuma da yardar Allah Namra sai ta samu mijin da ya fi ka a komai, ina da rai wata
rana sai ka zo kana fada min bakinciki da damar da ka yi na auren Hurriya, laifin
ai ba naka ne kadai ba har da na Yaya”

Ta juya a fusace ta fice daga dakin tana barin kofar dakin a bude.

“Miye amfanin haka? Saboda wata yar iska wata bare zaka batawa kanwar mahaifinka
rai? Matar da bata san gurin da zata aje ka ba saboda soyayya? Me ya shiga kanka ne
Captain? Anya kai ne?”

Ita kam be ce mata komai ba har ta ci ta cinye.


HAJIYA KALTUME POV.

“Ya jikin nata Hajiya?”

Khairy ta tambaya. Sau Hajiya Kaltume ta yaye mayafin dake jikinta ta aje jakarta
gefe.

“Jiki da godiya, amman kam Hajiya Fatee bata da lafiya sosai, yanzu ma daker ta
yarda muka dauke ta muka kaita asibiti muna zuwa suka ba mu gado, ni ma kadan ya
rage na fadi jiri sai kwasheni yake damuwa ce ta mana yawa Khairy ba ita ba ba ni
ba, kara ita ta wani bangare, duniyar nan bata da dadi a gurin kowa yanzu sai
azzaluma, tun da muka dawo kauyen nan Hajiya Fatee bata sake lafiya ba, sai kin ga
yadda hankalin Fadeel ya tashi”

Khairy ta kwanto a hannun kujerar dake falon na Hajiya Kaltume tana fadin.

“Ni kaina bana cikin jindadi a yanzu”

“Ba ki da lafiya ne?”

“Lafiya ta kalau kawai dai zuciyata bata min dadi”

“Wake da dadin zuciya a yanzu Khairy? Ai sai idan abubuwa sun daidaita, ni kaina
yanzu abincin kirki bana iya zaunawa na ci, abubuwa sun hade min? Ga sakin nan da
Alhaji yayi min ko waiwaye gefena be sake yi ba, kamar wanda ya aje kashi... Ga
Iyami a gafe damuwarta na son yi min yawa, yanzu ga Hurriya da gani magani suka yi
ma yaron nan suka aura mata shi, kauyen nan kuma mun je mun tararda bakin labari,
ban da ma karfin zuciya ai sai mutum yayi mutuwar tsaye ko ta gaba daya a take”

“Hajiya wannan duk saboda Amma ne, ita ta haifi Hurriya har ta kawo mana matsala a
gida”

Hajiya ta hade hannu biyu ta daga sama.

“Saboda ita ne kuwa saboda ita ne, ni ko mutuwar Salma ai bana raba dayan biyu da
laifinta a ciki, ga kamun da barayi suna yi mana shekarun baya saboda ita ne dai,
ni kam yau da zan ga Iyami ai da hannuna zan kashe ta, duba ki ga Hurriya waya auri
irin mijin da ta aura a yanzu? Duk cikin yayan Alhaji babu wanda yayi dacen miji
irinta duk bayan cin amanar da ta yi min”

Maganar take zuciyarta na zafi sosai saboda bakinciki, kamin su dago kai su kalli
juna jin tsayarwa mota har biyu a bangaren ana rufe gambun da karfi. Khairy ta
tashi ta leka windows din Falon dake bawa mutum damar hango abun da ke waje, a take
gabanta ya yanke ya fadi.

“Appa ne tare da Yaya kuma nan suka nufo?”

Ta saki curtains din ta dawo kusa da Hajiya Kaltume ta zauna zuciyarta da jikinta
na rawa, Hajiya Kaltume ta maida hankalinta gurin kofar tana tunanin abun da ta yi
domin a yanzu bata da tabbacin alheri zai kawo mijinta a bangarenta. Yasir ne ya
fara turo kofar falon ya shigo sannan Appa ya biyo bayansa. Daga Khairy har Hajiya
Kaltume faduwar gaba suka samu kansu har Appa ya zauna yadda Yasir yake karara
Khairy ita kanta ta san akwai wani abu a kasa. Hajiya na son tambayar lafiya tana
jin tsoron domin ta lura da yanayin Appa ba yanayi mai kyau ba, sai da ta dubi
Yasir sannan ta kalli Khairy da yake harara.
“Wani abun kika yi?”

Khairy ta yi shiru jikinta ya hau kyarma zuciyarta na zillo.

“Umm Khairy... Me kike aikatawa Hurriya?”

Ras ras ras gabanta ya fadi irin faduwar da be taba yi ba, sai ta kasa amsawa kuma
ta kasa daina kallon Appa fuskarta kuma ta kasa boye tsoronta.

“Me kike aikata ga Hurriya?”

Appa ya sake tambaya yana kallonta. Yasir ya mike tsaye zai nufi inda take sai Appa
ya dakatar da shi.

“Dakata, ba abu ne na duka ba, wannan abun mai muni duka ba zai canja komai ba, ni
kadai na san ya nake ji a raina, yaya ne dukansu ace ďaya ta aikatawa ďaya haka? Ya
kamata na tambayi kaina me na yi?”

“Baka yi komai ba Appa babu ta inda ka gaza, dan Allah karka sakawa kanka tunanin
wani abu”

Yasir yayi saurin fada yana kokarin kwnatarwa mahaifinsa da hankali. Hajiya Kaltume
ta kallesu ta sake duban Khairy sannan ta ce.

“Duk lokacin da za'ayi ma Khairy hukunci a gidan nan ko duka saboda Hurriya ake
mata shi yanzu kuma me aka ce ta yi?”

Yasir ya bude wayarsa ya kunna video ya mikawa Hajiya Kaltume, tana fara kallo
Khairy ta fara hawaye domin ita ma tana jin abun da ake fada, sai ga Hajiya Kaltume
rike da baki.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un sherin sa za'ayi ma Khairy kenan?”

Appa ya nuna ta da tsaya.

“Ban shigo nan falon na zauna dan na yi magana da ke ba, karki kuskura saka min
baki a magana, duk wata asalin kiyayya da tsana da neman ganin baya ko kunyata wani
daga gurinki ta samu asali, duk abun da Khairy ta aikatawa Hurriya a yau goyon
bayanki ne rainonki ne, ke kika bude musu hanya ke kika nuna mata hakan, kin tsani
yarinyar nan kin tsani uwarta, akan abun da Allah be haramta ba, kaina farau aure?
Da a gidana kawai za a samu wannan tashin hankali? Ke ya kamata ki hada kan yaya
matsayinki na uwar gida amman baki yi ba, sai dai ki nuna musu tsana da banbanci,
yau duk wannan abun ya faru saboda ke ne!”

Ya maida dubansa gurin Khairy dake kuka.

“So nake ki karya ki banranta kanki kamar yadda Hurriya ta yi min rantsuwa bata
aikata ba”

Ta girgiza kai tana saukowa daga kan kujera tana kuka. Yasir ta dafe kansa ya
runtse ido sosai.

“Tir da halinki...! Tir da haihuwar ƴa irin... Tir da ke Khairy ba zaki taba ganin
abun da kike so ba a rayuwarki.... Taya zaki hada kai da wani namijin a waje saboda
cin ma burinsa ga yar'uwarki ta jini? Ki taimaka masa ya gaya rigar mutuncinta? Ko
kawarki bata cancanci haka a gareki ba balle kuma Hurriya, karshenta gashi ya fadi
abun da yayi miki hakan kuma be miki ba sai da kika yada hotunanta a duniya...”
“Na ji... Ni na hada kai da shi aka dauki hotunanta... Wannan gaskiya ne amman
Wallahi Tallahi ba ni na yada ba, ban yadawa duniya hotunan Hurriya ba, Wallahi ban
saka hotunanta a internet ba, bayan Adam ban turawa kowa ba Wallahi, akan wannan
zan iya rantsuwa da kur'ane, sheri ne kawai yayi min”

“Amman kin karbi kudinsa da sunan zaki nema masa hadin kan Hurriya? Ta yadda zai
samu damar Lalata da ita?”

Appa ya tambaya hopping to hear NO from her. Ta hade hannayenta tana kuka sosai.

“Na aikata... Ka yafe min Appa ka yafe min dan Allah? Dan darajar Hajiya... Ban
aikata hakan saboda na kunyata ku ba, ban yada hotunan ba...”

“Lahaula wala kuwwata illabillah, Khairy karki kuskura ambatar sunana a gaban kowa
daga yau, kar wata matsala ko matsi da kunci ya saka ki tuna cewar ni mahaifinki
ne....”

Hajiya Kaltume ta saka Kalma shahada Yasir ya kalleshi da sauri Khairy kuma ta
fashe da kuka mai karfi ta je ta gudu ta kama kafar Appa da tuni ya mike tsaye ya
fara tafiya bayan ya fadi hakan.

“Appa ka yafe min dan Allah, na tuba ka yi hakuri dan Allah... Ka yafe min Appa”

Tsayawa yayi ya kasa tafiya kuma ya ji ba zai iya juyo ya kalleta ba saboda ta bata
masa rai matuka.

“Bana bukatar ganinki”

Ya fisge kafarsa ya fice daga falon ya barta a gurin tana rusar kuka. Ta juya gurin
Yayanta.

“Yaya Yayaya... Dan Allah ka bawa Appa hakuri dan Allah.... Wallahi Wallahi ba ni
na yada ba... Sheri yayi min saboda ya hada ni da mutane ba ni na yada ba”

“Ko sa yaushe idan na yi magana akan abun da yarinyar nan take yi cewa kike ina
matsawa yanzu ga abun da ta haifar, wani ya keta mutuncinki a banza kuma yanzu za a
yada hoton siraicinki... Kamin mu shigo nan Appa kuka yake da idonsa miye amfanin
ya ta saka ta mahaifinta kukan bakinciki? Miye ribar hakan?”

Yana kaiwa nan ya mike tsaye ya fice yana kuka. Hajiya Kaltume ta mike tsaye tana
kuka ta nufi gurin da yarta take kwance a kasa tana mulmula ta rikata cike da
tausayinta.

“Ya yanke hukunci ne cikin fushi, ki yi hakuri Khairy zai sauko...”

Ta fara share mata hawayenta tana nata kukan.

“Amman da gaske yaron nan yayi miki fyade?”

Khairy ta daga kai wani sabon kuka na zuwa mata.

“Shiya hana ni farinciki da sakewa tun daga ranar har yau... Hajiya ashe haka ake
ji idan aka yi ma mace fyade....? Bakincikin abun ya fi na mutuwa...”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un....”

Hajiya Kaltume ta fashe da kuka ta rumgune yarta.

“Ba a bar maganar nan ba, Allah ya isar miki ba zan kyale yaron nan ba...
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un wannan masifa ta mana yawa...!”

*** *** ***


Tsaye Appa yayi a dakinsa ya rumgume hannayensa a baya yana kallon sama. Fuskarsa
da zuciyarsa babu komai a cikinta sai tarin damuwa da bakinciki, kokarin yake ya
gano wani kuskuren da ya aikata har aka jarabce shi da wannan, wani abun kaddara ce
kai tsaye domin gwada imanin bawa da zuciyar ko tana iya dauka, wani abun kuma
ishara ce na wanin abun da aka aikata daidai ba ko kuma a can baya. Ya nemi guri ya
zauna sai kuma ya ji kamar ya zauna a ruwa saboda damuwar da yake ciki hakan ya
saka shi mikawa tsaye ya fara zagaya dakin. A yanzu ya gane tun farko yayi kuskure
be tsaya ya zabe uwar da ta dace da yayansa ba, be duba dabi'u da hallaya ba, be
duba mai addini ba kamar yadda Annabi ya koyar, duk ya tsallake wannan gashi yanzu
dafin abun ya bibiyeshi. A dakin yayi sallah Azahar saboda jikinsa da yake jin ya
sauya masa kamar ba na shi ba, wani abu mai kamar zazzabi yana rufe shi, zuciyarsa
na ciwo sosai. Bayan yayi Sallah ne ya dauki wayarsa ya kira direbansa ya fada masa
ya kimtsa mota za su fita yanzu, sai da ya mike tsaye sai jiri ya debi shi ya fadi
kasa zaune yana ambaton Allah, can kuma ya sake yunkurawa ya mike tsaye sai gabansa
ya rike kirjinsa yayi kamar an tokare shi da mashi, a nan sai da yayi ta addu'a
sannan ya samu abun ya sassauta masa, a lokacin da ya fito ya shiga motarsa sai ya
ji baya bukatar kallon bangaren Hajiya Kaltume domin ji yake kamar ita ta aikata
haka ba Khairy ba, wani bangaren kuma yana ganin kamar da hadin bakinta, a yanzu ne
yake mamakin kansa da be karasa mata igiyar da ta rage a tsakaninsu ba, ya kamata
ya kabe ta daga gidansa ma gaba daya, sai a yanzu ne yake kara jin tsanar ta irin
tsanar da be taba ji ba, nadamar shekarun da ya bata a tare da ita yake a yanzu,
arzikinta ďaya yaran dake tsakaninsu ba dan haka ba shi kam da ko sunanta a yanzu
ba zai sake son a ambata a gabansa ba. Har ya isa garin Maradum be ya tunanin komai
sai irin zaman rashin ji dadi da Hajiya Kaltume ta yi da uwargidansa wato matarsa
ta farko Maryamu uwar Sapna, an yi zaman da babu dadi ga fitina da tashin hankali
kuma mafi akasari daga gurin Kaltume yake tasowa, kasancewar Allah ya saka zaman ba
mai tsawo ba ne sai Maryamu ta bar mata duniyar.

“Ka nufi unguwar kuka tara...”

Ya fada kai tsaye domin a yau zuciyarsa yarta kadai take muradin gani, yar da ware
dabam saboda sherin Hajiya Kaltume, idan ta gabato da bukata Kaltume sai ta tare ko
yanke hanyar da za'ayi mata duka sai dai rabi. Yana daya daga cikin dalilin da ya
saka bata marmarin zuwa gurin ubanta duk kuwa da kasancewarsa mai arziki domin bata
jindadin gidan bata jindadin Hajiya Kaltume kuma bata jindadin yaranta, da ba su
dauke ta a matsayin yar'uwa ba, har mantawa suke da ita. Ta gaban gidan aka faka da
dalleliyar motar mai matukar kyau da daukar hankali, sannan direban ya fito ya bude
ma Appa mota. Cikin jin zafin rikewar da zuciyarsa take ya fito motar yana kallon
shagon dake facing din gidan sannan ya dauke kai ya nufi gurin da kofar gidan take.
Ba laifi gidane da aka yi ginar bulo ba na kasa ba, sai dai ginin ya ji jiki ya
goge saboda ya dade sumitin dake gidan ma duk ya fashe. Sapna na tsaka da surfen
masara ta ji sallamar Appa, sai ta cire tabarya ta aje tana murna da farinciki
ganin mutunen da shi kadai ya rage mata a duniyar nan.

“Laaaa Appa.... Appa kai ne yau....”

Appa yayi murmushi yana kallon yarsa dake daure da zanen da riga dabam. Ita ce
babbar yarsa ita ce yayar Yasir amman wahala ta saka ta zama kamar ita ce kanwarsa
ta biyu ma. Ta shiga dakinta da sauri ta dauko tabarma ta shimfida masa gindin
bishiya, sai kuma ta ga kamar hakan be dace ba.

“Appa ko dai ka shigo falo?”

Yayi murmushi yayi bayanta suka shiga falon da ruwa ya taba silin kujerunta suka
koɗe suka fara lalacewa.
“Tsaya Appa karka zauna”

ɗakinta ta shiga ta ɗauko zanen atamfarta ta kasan akwati ta shimfiɗa a kujerar a


ƙoƙarinta na karrama mahaifinta, sannan ya zauna dai ta kwance ƙullin dake gefen
zanenta ta cire dari biyu ta mikawa yaronta da ya shigo dauke da bokitin ruwa.

“Karbi Aliyu siyo ma Appa na ruwan gora a waje Appana baya shan ruwa sai na gora”

Yaron ya sauke ruwan da sauri ya leko dakin ya gaishe da kakansa yana murna sannan
ya karbi kudin ya fice da gudu. Sapna ta zauna a kasa tana gaishe shi.

“Appa sannu da zuwa sannu da zuwa Appa”

“Sannu Sapna surfe kike yi?”

Ta yi shiru tana kallon kasa, bata son yace bata gode da abun da yake mata ba.

“Appa abun da kake aiko mana ne baya wadatar da mu, kasan yanzu Iyali sun karu ba
kamar da ba, yanzu ba ni kadai nake ba ya kara aure ya aje can gumawa, gashi ba
wata sana'a yake a yanzu ba, shagon da yake tsaro mutumen ya rufe shagon, kuma
barayi sun hana noma, daman da shi ne muke samu muna karawa, shiyasa nake surfen
dab abun da na samu sai na hada da abun da ya ba ni mu ci ni da yara...”

Appa ya sauke kansa kasa yana jin rashin dadi ta rashin adalci.

“Me yasa baki fada min ba Sapna? Kina da wani wanda ya fi ni ne?”

Ta girgiza kai.

“Ba ni da shi Appa kai ne uwata kai ne ubana ba ni da gata sai na Allah sai kai”

“To me yasa baki fada min ba?”

Damuwar ta bayyana a fuskar Appa har ta saka idonsa cika da kwalla, irinta ce a
fuskar Sapna ita nata kwallar suna zuba.

“Gani na yi kamar ba a son zuwana gidan, bana jin dadin yadda ake banbanta ni ko
dan ni ina kauye su suna birni ban sani ba, kuma idan na bukaci abu wani lokacin
har sai na manta kake yi min Appa, duk da haka kana kokari da mu na aiko mana sa
abinci duk wata, gashi ni ba ni da halin da zan maka komai, kuma ba ni uwar da zata
maka godiya, wani lokacin ina kunyar bijiro maka da bukata nauyin ai sai yayi maka
yawa”

Appa ya dube ta da kyau ya jinjina kai.

“Gaskiya ne.... Ke din nan ke da Hurriya da Yasir bana da kamar ku a ƴaƴa Allah ya
muku albarka... Kuma da tsananin biyaya da tausayi a gareni”

“Amin...”

Ya amsa tana share hawayenta, Aliyu ya shigo tare da kanensa su shi da a falon suna
ta murnar ganin Appa yau a gidansu, daman rabonsa da garin tun kamin a haifi
Hamad...

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx

Appa ya maida ludayin furar ya matsar da shi gefensa ya gyara zamansa yana sauraren
Hajiya Binta.

“Na muku addu'a sosai daga kai har ƴaƴanka, kuma zan cigaba da yi har zuwa ranar da
za dawo da yardar Allah”

“Na gode sosai Hajiya, Allah ya karbi ibada yasa ayi Umara karbabbiya”

“Ameen, ina wajen su Hurriya Amarya?”

“Suna lafiya Hajiya, na bawa mahaifiyarta kudi mai yawa da bake kyautata zaton za
su wadace ta siye mata duk wani nau'i na kayan Kitchen, Furnitures kuma ni zan siye
mata da kai ne”

“Ka kyauta, haka nake son ji sai dai su ma kayan dakin da dama ai iyayen mata ka
barwa su zaba mata za su kyau, ko kuma mahaifiyarta idan da hali”

“Mahaifiyarta har yanzu bata son ganina Hajiya, kudin nan ma Gwaggo da Bappa na
hannatawa ita bata da son saurare ma”

“Fushi ta yi da yawa, sai ka sha wahala kamin ta sauko, kuma ina fatan idan ta
sauko abubuwa za su daidaita ko dan yaya”

“Daya daga cikin dalilin da ya saka nake son kyautata mata a yanzu fiye da kenan,
kuma ina tunanin jingine lamarin auren yarinyar nan ya kamata na kimtsa gidana
tukuna, Sapna ma ina ta shirye shiryen dawowa da ita a garin nan kusa da ni, domin
halin da na same ta last week da na je garin nan ban jidadi ba”

“Wannan ma wani abu ne da ya kamata ka yi tuntuni, ni har mantawa nake da kana sa


ya a kauye saboda dadewar da take bata zo ba, kuma mu ma ba ma zuwa amman idan a
nan ne ka ga tana kusa da mu, na jidadin kudurinka Tsoho Allah ya maka albarka ya
kara yaye damuwa ya haskaka rayuwa”

“Ameen Hajiya”

“Sai ka cigaba da rike addu'a, kuma idan da hali ita ma Kaltume ka dawo da ita
cikin yayanta, ta ci albarkacinsu”
Ajiyar zuciya Appa ya sauke yana jin kamar Hajiya Binta na matso masa da mutuwa
kusa.

“Wato Hajiya da dai za a kara daga min kafa wata kila a gaba zuciya ta raya min
haka, amman a halin yanzu matar nan bata gabana ko kadan, da ina tunanin idan ta
cika idda zan fada mata ta koma gidanta ko Family House dinsu, domin bana bukatar
zamanta a gidan nan da sunan zaman Yayanta”

“Ba saboda ita zaka yi ba Tsoho saboda yayanka zaka duba, Yasir da Ruma domin ba
zan saka da Khairy ba”

“Idan umarni ne Hajiya zan bi idan kuma shawara ce zan duba”

“Shawara ce, Iyami ma da take kyautata min nake kaunarta cilasta maka maida ita ba
balle Kaltume da ba dan darajar Yayanta ba da ko kallonta ba zan yi ba, babu kalar
cin mutuncin da bata yi min ba, amman shi babba ba ya zama kamar yaro kuma abun da
duk ka aikata mai kyau ko marar kyau zaka girbe shi a kusa ko a nesa, wannan fadin
Allah ne”

“Haka ne, Kuskuren kuma daga ni ne Hajiya ban tsaya na duba background din ba kamin
na dauko, kaddara ta riga fata”

“Wannan ma zai wuce tsoho, ka kyautata zamanka da Iyalinka gwargwadon yadda zaka
iya, kuma ka kwatanta adalci a tsakanin ƴaƴanka ita soyayya an sani Allah yake
sakata, amman sai mutum ya bar abun a zuciyarsa ba sai ya bayyana ba domin bayyana
ko nuna fifiko akan wani shi ke bude kofar abubuwa da yawa da baka yi tsammani ba”

“In Shaa Allahu Hajiya”

“Allah yayi taimako ya hada kan Iyalinka”

“Amin”

Ya amsa sannan suka yi sallama ya sauke wayar ya kalli ragowar furar da Sapna ta
daka masa da kanta ta aiko masa bayan dawowar daga kasar Maradum. A yanzu jin kansa
yake a free kamar wanda ya fito daga wani kangi ya samu yanci haka yake jin a
ransa, nishadinsa na da yadda tsarin rayuwarsa na baya a yanzu jinsa yake a normal
a yadda ya saba yi.
A yanzu din ne yake jin marmarin abokiyar rayuwarsa fiye da koyaushe be taba
bakincikin rabuwa da ita ba sai a yan kwanakin nan gaba daya ta shige masa a rai
wani sabon kaunar Amma yake ji a ransa, be tabbatar da ya tabka babban kuskure na
sakinta ba tare da ta yi masa laifi ba sai a yanzu bata kusa da shi, gashi idan ya
tuna da yaransa Hamad Hurriya da yan biyun da ta haifa masa sai ya ji tausayinta ya
kara kama shi.

Lokuta da dama ya kan nutsa a duniyar tunanin dalilin sakin nata sai ya rasa, gaba
rayuwar baya ta zame masa kamar mafarki yayi wasu abubuwan da yayi ma Amma da
Hurriya da kuma iyayenta idan ta tuna sai ya ji babu dadi, kuma ya rasa dalilin
haka, kamar yadda a yanzu ma ya rasa dalilin tsanar da yayi ma Hajiya Kaltume,
macen a da ko tari ta yi jikinsa rawa yake ya amsa mata, a yau ita ce yake jin baya
bukatar zamanta a gidansa ita ce a yau yake fatan ta gama zaman idda ta bar masa
gidansa, a yau ita ce macen da baya son kallon bangarenta idan zai fita.
Zancen da Hajiya Binta ta yi masa cewar mata ne suka dace da siyayyar kayan dakin
Hurriya ya saka shi kiran Number Amma, kamar wani yaro haka ya aje wayar a gabansa
ya dauke hannayensa yana kallon number tare da fatan Amma ta daga kiran amman bata
daga ba har kiran ya katse, ya sake gwada kiran a karo na biyu sai kuwa ta dauka
hannunsa ya kai ya taba speaker dake jikin wayar, sallamarta kadai nishadi take
kasa shi tana tuna masa da rayuwarsa da suka yi a baya.
“Wa'alaikissalam...Hajiya an wuni lafiya?”

“Alhamdulillahi”

“Maa Shaa Allah, Ina yarana duka suna lafiya”

“Lafiya kalau”

Ta amsa a takaice domin bata son wata maganar da ta wuce sha'anin yara ko gaisuwa
ya wuce tsakaninsu. Shiru ya dan yi na lokaci kamin ya ce.

“Yanzu na gama magana da Hajiya nake fada mata yadda muka yi da ke na siyayyar wasu
abubuwan na Hurriya, nake fada mata ina son siyayyar kayan dakinta da kaina kamar
yadda nake yi ma sauran Yaya Sapna da Maama, wai take cewa su ma siyen kayan daki
ai na uwa ne, iyaye mata ya kamata su yi”

“Haka ne”

“Shi ne na ce idan babu damuwa sai ki shirya tare da mutanenki mu tafi Kano a duba
mata kaya masu kyau wadanda hankalinku ya kwanta da su, da ice ita din babu lalura
a tare da ita da sai mu tafi tare da ita ta zaba da kanta kamar yadda sauran
yan'uwanta suka yi”

“Already mun yi order kayan Kitchen gurin Khadeeja Candy, zata saka a kawo mana
daga Kano har gida, kuma wasu abubuwan Gwaggo zata tafi tare da Hindu Lagos su
siyo”

(Duk mai bukatar kayan kitchen, Bedsheets da kayan kawata falo ko daya, akwaituna
da kayan lefe kamar su laces shadda atamfa materials da Shoes and bag, sarka
yan'kunne turareka zai samu a gurin Khadeeja Candy Store cikin sauki da rahusa,
muna aikawa ko'ina a fadin Nigeria da sakashen dake makota da mu kamar irin su
Nijar Togo da Ghana cikin aminci da yardar Allah, mai bukata sai ya tuntube ni a
business line dina kamar haka :- 080361266660)

Appa ya sauke ajiyar zuciya jin kamar Amma bata fahimci inda ya dosa ba ya ce.

“Kayan daki nake magana kamar gado da kujeru da sauran abubuwa na cin abinci,
gidansa da ke Kaduna za a iya siya a Kd a saka a can ko kuma a siya daga Kano a kai
can, da son samu ne ma a siyo mata komai a waje na fi aminta da kayan can fiyeda na
cikin gida”

“A Kanon ma babu kalar kayan da babu, suna dauko kayan waje domin saukakawa masu
gaggauwa ba sai an kashe kudin jirgi ba wata order ma sai ka yi bata iso da wuri
ba, zaka iya zuwa Kano ka duba mata”

“Da zamu tafi tare ai da zai fi domin ke ce idonta a yanzu, kuma duk yadda zan yi
zabe ba zai kai ga ke yadda zaki zaba ba”

“Babu wata hujja da zata saka na shirya baka tafiya da kao Alhaji ko dai ka manta
ni din nan ba matarka ba ce?”

“Ba daga ni sai ke nake nufin tafiyar ba tare da familynki, shiyasa zan baki dama
ki yi shawara da su daga nan zuwa gobe abun da kika yanke sai ki fada min”

“To shi ke nan mu kwana lafiya”

Yayi saurin dakatar ta ita daga kokarin yanke wayar da take.

“Idan ba zaki tsaya mu gaisa ba, toh ina yarana Hassan da Husaini?”
“Sun tafi Islamiya”

“Hurriya fa bata kusa?”

“Rukayya karbi mikawa Hurriya waya”

Amma ta cire wayar a kunnenta ta mikawa Rukayya da ta mike tsaye ta nufo gurin da
suke zaune ta karbi wayar ta fice daga dakin zuwa dakin Bappa da Hurriya ta shiga
dazun tana ganawa da kakanta.

“Ka ji min wata magana wai Hajiya Binta dake Saudi gurin Ummara ta ce masa zaben
kayan daki na mace ne”

Baaba Uwani wadda ta kasance kanwa ga Gwaggo ta bude hannayenta jin an sosa mata
gurin dake mata kaikayi.

“Daman ai na fada, dama nan ya bar zabin komai zai fi, domin dai zaben Kaltume ko
wannan Hajiya Nafisa ba za su zabo ma Hurriya abun kwarai ba”

“Daman ni ban saka ran da Kaltume za a je ba, domin babu aure yanzu tsakaninsu,
Nafisa nake saka ran zata taimaka masa gurin zaben kayan ita na san ba zata zabo
abun kirki ba domin ba son Hurriya take ba kuma tun da aka daura auren nan har yau
bata tako gidan nan ba”

Hindu dake bude giɗa ta ce

“Da gaske wai bata zo ba?”

Amma ta waiga ta kalli kawar da za'a iya cewa yanzu ta zama yar'uwarta ta ce.

“Wallahi bata tako ba, kuma kin ga ko cikin danginsa da suka zo bata biyo su ta zo
ba kuma bata zo ita kadai ba Namra ma bata da tako nan ba”

“Allah da iko yake, da alama ma fa ita ma bata son auren nan, ke bi ba dan na ga
yaron ba tubarkalla Maa Shaa Allah da shi da zan iya cewa aura mata shi aka yi
saboda sun ga ba mutunen kwarai ba ne, ina fatan dai an bincike halinsa ba shi da
wani nakassu”

Ta karasa zancen tana jefa giɗa abakinta. Amma ta ɗan taɓe baki.

“Bashi da shi gaskiya domin shekaran jiya kamiN Hajiya Binta ta wuce Ummara ta zo
gidan nan yi mana bankwana take fada mana Appan Hurriya yayi saka an masa bincike a
akan yaron ta hallayarsa ta zamankewa da mutane kuma ba su ji wani aibu ba, Allah
ne fa ya wanke Hurriya kuma yayi mata sakamako da wannan, ki duba ko video nan na
Khairy yanzu da ya cika gari Appanta yace shi ne ya shiga ya fita ya ga komai ya
warware, an goge hotunan Hurriya ta inda zai iya kuma ya saka suka bata hakuri,
kuma shi ya cilastawa yaron fadar gaskiyar abun da ya faru, kina jin yadda aka
daura auren nan da sadakin kin san abu ne kawai min indin Allahi, karki so ki ga
yadda ya zo gidan nan, baya ma iya daga ido ya kalleni, son kakarsa ma ta zo ita da
abokiyar zamanta da kanen mahaifinsa su biyu da yayar mahaifiyarsa dukansu kuma ban
ga wani abu a tare da su ba, idan ba dayar ba dake ta hankada tana harare-harare”

Gwaggo da ta gama sallame sallah a yanzu ta ce.

“Daman ai ba za a taru a dangi ace kowa sai ya so ka ba, dole za a samu wanda ba ya
ra'ayinka, balle dai yadda yaron nan yake ba za su rasa matar ba shi ba”

“Gwaggo ai gabanki Hurriya ta fada mana yadda Namra da Momy suka mata gargadi akan
yaron, ashe dai shi ne mijin ba su sani ba”

Amma ta fada tana mike kafarta da har yanzu bata gama warke mata ba, tana kallon
Gwaggo ta cire hijabinta tana fadar

“Ki kwantar da hankali ki cigaba da yi mata addu'a ita ma kuma ta cigaba da yi


domin ba bari abun da aka zaba za'ayi ba musamman Kaltume Allah kadai ya san
hassadarta akan auren nan, kuma kin ga Saurayi ne ba mai mata ba balle ki daga
hankalinki da tsoron abun da zai biyo baya”

“Ko mai mata ne ma Gwaggo ya zan yi tun da mahaifinta ya riga ya bada ita? Ai babu
yadda zan yi sai hakuri, dan yasan Hurriya ƴata ce ai ya saka shi yin haka, da Momy
ce ko Kaltume ba zai taba yi ma yaransu haka ba a daura aure ba tare saninsu ba,
kuma na ji dadin da be bawa kowa siyayyar kayan ba ya kawo kudin nan yace a siya
komai”

“Yanzu fa ya dawo hayyacinsa kina ganin yadda yake rawar jiki da yaran nan wai ni
me yace ma kiran da yayi yanzu na ji kina masa zancen ya siya can?”

Amma ta fadawa Gwaggo abun da ya bukata, Hindu ta kyalkyale da dariya, Gwaggo da


Baaba uwani suka yi murmushi.

“Ba wani nan shiri yake nema, yana son ya kyautata miki ne kuma ya samu kanki”

Amma ta tabe baki tana wofintar da zancen Hindu da be kama kanta ba.

“Hindu ke dai baki rabo da zance a bakinki, ni yanzu ina ni ina Alhaji Haruna?
Daman can kaddara yara ce ta kaini kuma an haifa, Wallahi yanzu ni baya gabana
gidansa be burge ni sam, ke ni fa auren ma ya fita a raina ma gaba daya na wasun
mazan ma, balle na Alhaji Haruna mai mata irin Kaltume ko makiyi ba zan so ya zauna
da kishiya irin Kaltume ba, kamar dai kun manta inda aka fito? Magana wannan ina
son na yi amman na kasa daga kwance sai kwance babu abun da zan iya kawarwa bayan
an raba ni da aurensa an juye kansa, hakan duk be wadata ba aka koma a gurin
yarana? Shi kuke gani da fatan zan iya komawa? Ai har abada...!”

“Allah dai ya zaba abun da ya fi alheri amma mace ai bata cewa ba zata sake aure
ba, kuma idan da yara ko an rabu kamar ba a rabu ba ne yanzu ba gashi ba? Kuma idan
baki koma ba ai ita Kaltume ta samu abun da take so kenan”

Cewar Gwaggo domin ita ma a yanzu ta gano zaman auren ya fi babu, ko da wani
namijin ne balle kuma uban yayanta da aureta tun tana budurwa gashi har an kai ga
aurar da ƴa.

“Ni dai na hakura da Alhaji Haruna, idan har auren alheri a gare ni a gaba Allah ya
kawo min wani mai mutunci da sanin ya kamata, kuma ya ba ni abokiyar zama ta gari”

“Amin, idan kuma akwai alheri Allah ya maidake dakinki Iyami, ko dan yaranki, nan
gaba kadan zai ce zai karbi yaran nan kuma idan baki a gidan ba za su jidadi ba, ni
dai a matsayina na mahaifiyarki ina rokon idan ya nemi maida aurensa karki juya
masa baya dan Allah”

Amma ta kalli Gwaggo idonta na cika da hawaye.

“Gwaggo ban manta wahala da azabar da na sha saboda auren bawan Allah nan ba, kuma
ke da kanki kika ce inda shi ne ba zan koma ba, ko da fari ku kuka karfafa min
guiwar aurensa kuma... ”

“Kuma hakan be haifar miki da komai ba sai alheri, ki rika duba wannan ina son ki
sani ita kaddara a rubuce take ko da Kaltume ko babu ita sai kin yi irin wannan
ciwon sai haka ta faru, ita dai ta zama sanadi ne kawai kuma yanzu gashi ai kin
samu sauki jinyar kuma ta zame miki ibada, bari na dubawa Hurriya maganin Infection
da muka siya gurin UMMU SA'ADA WOMEN'S SHOP 09160547983”

Gwaggo ta mike tsaye ta fice daga dakin tana amsawa Baaba Uwani dake yaba kyau
maganin na infection.

“Ai da yana da daci ko tsami ma Hurriya ba zata yarda ta sha ba, yadda na san
Hurriya da son zaki ba zata sha ba idan yana da daci”

Cewar Amma tana share hawaye Hindu ta ce.

“Shiyasa ai nake jindadin maganinta, ba shi da daci kuma baya saka zawo ko tashin
zuciya ki sha abinki kamar kina sha tea, ga aiki a jiki kuma gashi da saukin kudi
daga 500 yake farawa har zuwa sama za ki ga yadda wanke marar mutum ta yi tass
shiyasa aka ce kar mai ciki ta sha, gashi har kala biyu take yi da mai kamshin
takafarnuwa da wanda ba shi da shi, saboda wasu basa son masu warin tafarnuwa, kuma
zaka iya sha tare da miji da yara matukar sun haura shekara biyar”

“Gaskiya na ji ana yabon maganinta, mu ma dai mun fara ganin aikinsa a yanzu, Allah
dai ya sa a dace kawai”

“Amin”

Wannan karon Baaba Uwani ce ta amsa sannan ta mike tsaye ta bi bayan Gwaggo da ta
fice dakin. Hindu ta daki cinyar Amma.

“Ke Wallahi ki koma dakin mijinki wannan kame kamen da yake ba na komai ba ne sai
na neman aure, kin san yanzu aurensa ya koma kasa saboda kin cika idda dole shi ma
ya shiga cikin manema, iyaka a nemi tsari kuma ki rike addu'a ba dare ba rana, ni
kam da zaki bi yawa Wallahi Iyami karki bar mijinki, Gwaggo ma shi take so”

Amma ta kawar dai tana dauko wani zancen domin ita dai a yanzu har ga Allah bata
son komawa dakin gidan Appa ita kadai ta san halin da ta shiga kamin ta samu kanta
a yau. Kwana da yin haka Appa ya sauka gidan da kansa tare da wani dan'uwansa da
Momy ya so a zo gidan sai dai yadda ta juya masa baya a lamarin auren nan ne ya
saka dole ya aje lamarinta a gefe, Bappa da dake zaune a madaidaicin falo ya kalli
Alhaji Haruna a natse sannan ya fara magana.

“Akan maganar da ka yi ne, ita Iyami tace tana ganin a tafi da kanwar Gwaggon yara
wato Baaba Uwani da kuma kanwata Innar su Nasiru da Ibrahim dake can sokoto zan yi
waya da ita ta zo sai ayi tafiyar da ita, da kuma Hindu, sai su ku duba kayan a
tare da naka yan'uwan”

Appa ba haka ya so ji ba, domin ya so ayi tafiyar ne da Amma, kamar yadda yayi da
Kaltume a lokacin da za su zabawa Maama kayan daki.

“Hakan yayi Bappa na gode sosai Allah ya saka da alheri, hakan ma wata alfarma ce,
ina godiya Bappa kuma ina kara bada hakuri akan abubuwan da suka faru, ita kaddara
haka take a yadda aka rubuta haka take zuwa, wani lokacin sai ido ya rufe hankalin
ya gushe ka aikata abun da baka yi tunani ba, ba dan Allah ya rubuto haka ba
Wallahi ban yi tunanin rana zata zo irin wannan ina raye ace bana tare da
mahaifiyar Hurriya ba”

“Haba wacan maganar ai duk ta wuce, sai dai ayi fatan Allah ya tsare gaba”

“Amin Bappa”

Appa ya kalli dan'uwansa Alhaji Musa, Alhaji Muss na ganin kallon da Appa yayi masa
ya fahimci inda ya dosa sai yayi hanzarin cewar.

“Bappa idan da hali ai sai a kira mana ita Iyami, akwai maganar da zamu yi da ita
akan sha'anin bikin nan”

“Toh babu matsala zan turo ta yanzu”

Bappa ya tashi ya fice daga falon da aka gina daga waje domin baki. Cikin gidan
Bappa ya shigo ya zauna a kujerar roba dake aje kusa da Amma.

“Mun yi magana da shi na fada masa yadda muka yanke, yayi ta godiya kuma ya kara da
bada hakurin abubuwan da suka faru”

“A Duk lokacin da ya zo sai ya bada hakuri, shi kam ya fahimci mun hakura mana,
gashi ana abubuwa gwanin sha'awa ma”

“Ni ma dai shi na gani, daman shi aure ai ya gaji haka, tare da wani dan'uwansa ya
zo shi yace suna son ganin Iyami akan maganar Hurriya, na fada masa zan turo shi”

Amma ba zata iya cewa ba zata je ba, domin Bappa ne mai fadar ya fada musu zata zo,
ta ina zata ki umarnin mahaifinta, sai dai ita kam da za'abi ra'ayin zuciyarta sam
bata son kebewa da Alhaji Haruna a yanzu, ba dan ta tsane shi ba, sai dan ta san
maganar da zai fada ba zata wuce sake jaddada bada hakuri ba. Amma ta aje turen
farin waken dake jikinta ta yunkura ta tashi tsaye ta nufi daki, Babba Hijab ta
dauko ta saka ta fito ta saka talkamin ta kofar fita tsakar gidan sai kuma ta juyo
kamar zata kira yaranta su tafi tare, sai dai gudun abun da Gwaggo zata ce ya saka
ta juya ta cigaba da tafiyar.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx

Amma na yi sallama Appa ya mike tsaye yana amsawa kunyarta na rufe shi, ba yau ne
karon farko da ya ganta bayan rabuwarsu ba amman yau ta fi cika masa ido saboda ya
kebe ne daga shi sai ita sai kuma kanensa dake tare da shi a yanzu.

“Hajiya an wuni lafiya”


Iyamin da yake ce mata a da yanzu yayi masa nauyin furtawa duk da kasancewar ya
girmi Amma nesa ba kusa ba. Amma ta amsa tare da zaunawa ta mikawa Alhaji Musa tasa
gaisuwar.

“Lafiya Kalau Iyami ya hakuri? Ya gidan?”

“Alhamdulillah, ya wajen su Larai?”

“Lafiya Kalau suke, dan Allah Iyami a dai kara hakuri rayuwa sai da hakuri kullum
kalubale sabo yake zama”

“Babu komai Alhaji Musa an mun saba da jarabawa, Allah dai ya kara mana imani”

“Amin amin haka ake so, Alhaji bari na jira a waje”

Ya tashi ya fice daga falon Amma ta bishi da kallo tana mamakin yadda yawancin
yan'uwa suke goyon bayan hukuncin dan'uwansu a daidai ko kuskure, domin tun da suka
rabu da Appa bab da Hajiya Binta babu wanda ya taba takowa a cikin yan'uwnsa da
suna duba yaranta ko ita ko ya jajanta mata abun da ya faru, amman yanzu saboda
Appa ne yake son zuwa gurinta da kansa gashi Alhaji Musa ya rako shi babu ko kunya
ashe da rasuwa Appa yayi haka za su wofintar da Iyalinsa kenan! Bata samu amsar
tambayar da ta yi ma kanta ba ta tsinkayo Appa yana fadar.

“Fatar dai duk kuna lafiya”

Ta maida kanta kasa ta amsa a takaice.

“Ina Hurriya?”

“Tana can dakin Rukkayya kawarta Husna ce ta zo suna can tare”

Kallonta kawai yake sai a yau yake ganin ramarta, ta yi rama sosai tun daga lokacin
da ta bar gidansa damuwa ta saka ta a gaba ciwo kuma ya rufeta sai ya abun ya zame
mata biyu ga tunani ga ibadar ciwo. Sai dai ramar bata karawa Appa komai ba sai
tausayinta da kaunarta a ransa.

“Bappa ya fada min hukuncin da kika yanke, zan iya sanin dalilin da ya saka kika
cire kanki”

Tambaya yake kamar mai lallaba yaro.

“Babu komai daman ai abun da ya shafi ɗan fari ko ƴar fari wasu ne suke shiga gaba
su yi ba mu da muka haifeta ba, ni dai al'adar mu ta Fulani da Malam Bahaushe haka
na sani”

“Haka ne amman yanzu wannan ai duk ya kau Hajiyata, da dai za'ayi tafiyar nan dake
zan fi jindadi”

“Ba saboda kanmu zamu yi ba ai, ba dan jindadinmu ba, saboda yara zamu yi wanda su
ne silar da ya saka na zauna a nan saboda Bappa ya fada min cewar kana son magana
da ni akan Hurriya”

Appa yayi murmushi ya san halin kayansa ko a lokacin da take gidansa idan ta yi
fushi bata iya ba.

“Hajiyata kenan, yanzu miye laifi idan na kiraki mun gaisa? Na san ba zaki fito ba
ne sai da dabara shiyasa shi Alhaji Musa yayi haka, amman gaisuwa ce kawai”

“Toh na gode”
Ta yunkura zata mike tsaye sai ya saka hannunsa aljihu ya dauko daurin kudi ya
tashi a inda yake zaune ya isa gabanta ya aje kudin.

“Ki shigarwa Bappa da wannan”

“Aa Bappa...”

Be bari ta karasa ba ya tare numfashinta.

“Ba na ki bane, balle ki ce ba zaki karba ba, na Bappa ne dan haka karki saka kanki
a ciki idai ba kina jin wani abu a game da ni ba, Hajiyata a bar komai ya wuce
mana, baki san iya damuwar sa faruwar abun nan ya haifar min ba, yadda Hurriya da
yaran nan ma suke kallona wani abu ne da na kasa sauke nauyin da a yanzu nake
jinsa, ban tana tunanin zamu kai ga aurar Huriyya ba ma tare da juna ba, amman haka
aka rubuta mana dole haka din ne zai kasance”

“Komai ya wuce Alhaji, babu amfanin ka yi ta nanata hakuri a duk lokacin da ka zo,
ni na riga da na watsar da komai, daman shi aure ai kowa ya san Allah ya hallata
saki a cikinsa, Hurriya ma da ka batawa gashi yanzu kana ta gyarawa yaran ma kanana
ma yanzu kana jansu a jiki ai komai ya wuce”

“Fata ma nake nan da wani lokaci kankane su koma gida tare da ni”

“Na san kana da son yara Alhaji amman dai zaman a zai fi a kusa da ni ko Gwaggo”

“A can din ma ai kusa da ke ne ke zaki rike kayanki Hajiyata har ma da wasu yayan
idan Allah kaddara mana sai mu samu”

Amma na jin hakan ta fahimci gurin da Appa ya tafi ita bata je can ba, har a kasan
zuciyarta ta san ta yafewa Appa kuma ta kawar da komai, amman zancen komawa gida a
yanzu ko nan gaba ba abu ne da take da buri ba, domin ta dandana bata ji da dadi
ba.

“Bari na shiga ciki”

Ta duka ta dauki kudin.

“Hajiyata baki ce komai ba, ko da yake ya kamata na bari a gama Hidimar Hurriya
amman gajin hakuri da nadama sun hana yin haka, Wallahi yanzu ina da buri mai yawa
na son kyautata miki fiye da baya, ina son a saka ki alfahari da ni a matsayina na
uban yayanki Hajiyata”

“Wai ina ka bar Iyamin ne nikam Alhaji?”

Appa yayi murmushi ya aje numfashi cikin hikima da kwarewa ta magidanci mai Iyali.

“Yayi min nauyi a yanzu, wata kila dai zan iya fada a gaba, wata kila kuma zan
cigaba da fadar Hajiyar ne har zuwa bayan dawowarki Ummara ke da Gwaggo da Bappa”

Ya saka hannunaa aljihu ya ciro wasu takardu ya mika mata, Amma ta kurawa takardun
ido gabanta na faduwa, tana tuna wacan ranar da ya mallaka mata takardun gidan da
bata ci amfaninsa ba kuma takardar rabuwarsu.

“Ki karba mana Hajiya, dan Allah karki ce zaki maida wannan, shaidan kadai yake
maida hannun kyauta, kuma ba naki ne ke kadai ba har da na iyayenmu, ina son bayan
an gama hidimar bikin Hurriya ke da Hurriya ku tafi yi ma Allah ibada”

“Wannan duk an minene Alhaji? Na siye ne da iyayen ko miye?”


“Su dai iyaye na kyautatawa ne, ina ta tunanin abun da zan yi musu na kyautatawa
sai na ga babu abun da ya dace kamar wannan, ke kuma bana bukatar siyenki ai, yara
sun riga sun bude min hanya, ko ayi dan ni ba ayi dan yara, rokon yafiyar da nake
ma kawai ina son na kankare zunubi na ya yake gurinki kuma ya goge bakin fentin da
zuciyarki ta yi min, domin bana son wata rana idan mun koma ki kalleni a matsayin
Appan Hurriya kamar yadda kike kira a baya ki tuna cewar na yi miki wani abu ba
daidai ba, amman komawa kam wajib ce ko ki yarda ko karki yarda umarni ne zan yi
kuma dole ki bi”

Amma bata san lokacin da hawaye suka zubo idonta ba murmushi kuma ya cika fuskarsa,
yau Appa rayuwa yake aiwatar a gabanta irin yadda suka saba a baya kamin abubuwa su
chabe musu.

“Allah ya saka maka da aljanna ya rabaka da Hajiya Lafiya ya yafe zunubanka ita
kadai ce godiyar da zan iya maka a yanzu”

“Godiyar kenan, a daura auren ma idan tafi Ummara kina dawowa ki tare a dakinki
idan ma baki bukatar zama a wannan gidan ni zan iya gina miki sabo da irin samfurin
da kike so Hajiyata”

Amma ta rausayar da kai cikin yanayi na farinciki da damuwa domin a tsorace take
har gobe.

“Ya Salam Alhaji...”

“Ahhh to Hajiya a free zan baki kujerar Ummara ki tafi ki dawo ki auri wani? Saboda
ga Alhaji Haruna Mai Yadi Shashasha ko hmm?”

Dariya da kanta ta yi mazauni a hakoran Amma har sautinta ya fito tare da hawaye.
Farin cikin da ya kwana biyu be ziyarci zuciyar Appa ba ne ya ziyarce a yanzu
saboda ganin murmushin amaryarsa uwar yarsa Hurriya abar kaunarsa mai yawan biyayya
a gareshi.

“Haba ko ke fa, ni na san ban saba cewa eh ki ce a'a ba yana daga cikin abun da
nake yabonki da shi a kullum idan na tashi fada ko tuna, dan Allah karki fara a
yanzu, ba halin kirki ba ne, wannan kafewar ma ban san inda kika aro ba, domin ba
halinki ba ne baturiyata”

Amma ta saka hannu biyu ta karbi takardun ta koma ta zauna speechless tana
kallonsu. Appa kuma ya ciro wayarsa dake ringing ya amsar wayar yana mamaki kiran
da ya kwana biyu be shigo wayarsa ba sai yau.

“Wa'alaikussalam”

“Na'am Alhaji Hafeezu”

Appa yayi shiru na dan lokaci sannan ya ce.

“Aa ina wani guri mai muhimmanci amman dai yanzu zan tafi gida, mu hadu a can”

Ya katse wayar ya saka aljihun gaban rigarsa da babbar riga ta tare sannan ya kalli
Amma ya ce.

“Hajiya zan tafi gida yanzu, daya daga cikin iyayen maneman auren Khairy ne ya kira
ni a waya, ya ce yana bukatar ganin a zai same ni ni kuma na fada masa mu hadu a
gida zai fi, tun da ga Alhaji Musa ma a tare da ni sai mu ji ko minene”

“Allah yasa mu ji alheri”


“Amin, kuma dan Allah ki fadawa Bappa ba sai ayi min godiya ba, kar ya kira ni na
ki dagawa yayi zaton wani abu, Wallahi godiyar ce bana bukata, kuma ina jiran
kiranki idan an saka ranar tafiyar kar lokaci ta matse”

“In Shaa Allahu”

Amma ta amsa da murmushi, shi ma murmushin yayi.

“Na gode uwar biyu”

Ya fada sannan ya fice ransa fes buk'atarsa ta biya, hakarsa ta cin na ruwa. Daga
gidansu Amma kai tsaye gidansa ya nufa tare da Alhaji Musa yana bawa Alhaji Musa
labarin irin biyayyar da Iyami take masa wanda abu ne da duk wanda yake kusa da shi
ya sani. Yayi mamakin tarardar mutanen da ba zai iya kiransu da baki ba a gidan
domin shi da su suna kusan zama surukai ne a matsayinsu na iyayen Fadeel. Tun a
waje Appa ya gaisa da su sannan yayi musu iso suka shigo cikin falonsa suka zauna
tare da shi, ganin yanayin fuskarsu dake dauke da damuwa ya saka Appa be yi wata
hubbasa gurin ganin an kawo musu wani abun tabawa ba, domin alamu ya nuna ba
farinciki ne ya kawo su ba, sai kishiyarsa.

“Toh Allah dai ya sa lafiya, irin wannan ziyara da rana tsana ba tare da wani abu
ba”

Wanda ake kira da Alhaji Hafeezu ya yi gyaran murya ya kalli Appa cikin kyautata
ladabi ya ce.

“Alhaji lafiya amman ba lau ba, wato maganar ce da nauyi shiyasa na ce zamu sameka
a inda kake ban so mun zo nan gida ba sai dan ka bukaci hakan, domin ka yi mana
karamci da hallacin da be dace ace mun furta wata magana makamancinyar wannan ba a
gidanka”

Appa yayi murmushi mai cike da takaici.

“Karka damu Alhaji Hafeezu daman na saka tsammanin faruwar hakan, tun a lokacin da
abubuwa masara dadi suka faru a gidana, na shiryawa fuskarta ko wane kalar
kalubale, kuma na san zancenku ba zai wuce ku ce Fadeel ya janye daga zancen neman
auren Khairy ba?”

Sai duk suka kallo juna ganin yadda yayi saurin harbo jirginsu. Appa ya sake fadada
murmushinsa.

“Karku ji komai, yayi abun da ya dace kowa yana son auren yar kwarai, kuma ita
kanta Khairy ba wai bata da tarbiya ba ne, kaddara ce dai irin wanda ta saba fadawa
bawa, shi kuma yayi abun da yake ji ya natsu da shi ne, babu ta inda zai zama mai
laifi a gurin kowa, ni din nan ma mai shiga gaba ne a nema masa aure idan ya samu
wata yar da yake so”

Appa ne mai magana Alhaji Musa kuma ya fara fada yana ganin kamar hakan be dace ba,
Fadeel din be rumgumi kaddara ba.

“Kayya dai assha dai..! Ba haka aka so, amman yara ne basa jin shawara kuma basa
jin maganar manya na su hangen dabam yake, ya same mu sa zancen ne kuma yace shi ya
janye, mu kuma muka ta inda aka hau ice ta nan ake sauka, da ace ya janye jikinsa
kuma baka ji wani bayani daga garemu ba kamar hakan be dace ba, a matsayinmu na
iyaye”

Appa ya sauke ajiyar zuciya daman ya san za arina, sai dai kuma jin albishirin be
masa dadi ba, ko kadan domin yana neman mai kwashe masa Khairy ne a yanzu da shi
kansa baya sha'awar ganinta.

“Yaro yana da gaskiyarsa kowa yana aikata abun da yake jin natsuwa da shi ne, a
addini ma ance ka bar abun da kake kwankwato zuwa ga wanda baka yi, ba wani abu ba
ne”

“Mun gode Alhaji mun gode da Fahimta”

Alhaji Musa zai sake magana Appa ya dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu. Suka
tashi suka fice cikin kunyar sakon da suka isar.

“Alhaji be kamata ka yi haka ba, taya zasu same ka har gida da wannan maganar?”

“Sun yi abun da ya dace Alhaji Musa, haka ake son iyayen na gari su kasance sun
warware ne saboda su suka nema masa aure, to da ace anyi tsammanin shi zai aureta
ko kuma mu ji shiru a kara tun wuri su sanar mana, kuma yana da gaskiyarsa babu
namiji da zai son auren mace kamar Khairy saboda abubuwan da aka fada ta yi ma
yar'uwarta ta jini, balle kuma ga maganar Fyade ta shigo ciki kuma ka san yadda
society mu suke daukar abun da girma”

Cikin takaici da Allah wadai Alhaji Musa da ya kasance kane ga Alhaji Haruna ya ce.

“Ummu Khairy bata kyautawa kanta ba, bata kyauta ba ban jidadi ba ta bata maka suna
ta lalata rayuwarta ina amfani haka”

“Idan ma akwai amfani a yanzu ta gani idan ma babu kuma ta gani, Allah ya shirya
mana zuria”

“Amin, yaran ne yanzu hankalinsu da tunaninsu sai ka rasa ina yake zuwa, ita na
Hurriya saboda bata aikata ba ne Allah ya dubeta ya kawo mata wannan yaron ban da
haka ai da sun zame maka su biyu abun babu dadi”

“Ko su goma suka zama zan iya dauka Alhaji, yadda kaddara ta rubuta ai haka za a
wanke a sha, Allah baya aje kayansa ga wanda ba zai iya dauka ba, jarabawa ce ta
rayuwa Alhamdulillahi”

Appa ya fada cikin tsananin bakincikin da be isa ya boye a zuciyarsa kadai ba har
sai da fuskarsa ta bayyana.

CAPTAIN JAMAL POV.

“Akwai wani abun da zan iya taimaka maka da shi ne?”

Captain ya girgiza kai ya kwanta jikin kujera kamar mai jin bachi.

“Aa anyi komai, daman ba wata hidima za'ayi ba, Ammy ta hana taron biki ta hana
komai ka ga babu bukatar yin wani abu”

“Amman dazun ina jin ka a waya da Abdulkareem kake masa zancen gyaran gida”

Captain ya zaburo masa da fada ganin yana son matsa masa ya shigar masa hanci.

“Already ina da gidan a nan da Kaduna Salim ka sani, na hannata masa komai ne
saboda yayi kwangilar kula da komai idan akwai abubuwa da za a canja ko a saka yayi
saboda sabon gidaje ne, kai kuma ba sana'arka ba ce to miye abun takuwara dole sai
ka shiga ciki?”
“Babu Allah bada zaman lafiya”

Salim ya fada a fusace shi ma ya mike tsaye zai fice Ammy ta dakarta da shi.

“Salim karka fita dan Allah karka yi fushi, na san halin Captain ba tun yau ba, kar
abun da yake yi a yanzu ya dame ka, mu kan mu tarewar da muka yi a wannan gidan na
dole ne, na sani yaushe rabon d mu zo garin nan mu yi kwana uku ma amman gashi yau
har mun tare a gidan nan saboda wannan auren, ka sha kuruminka idan zaka zai yi
auren kwarai da za ayi taro ayi biki na gani na fada ku zaku yi komai”

Salim be fita ba, sai dai kuma be dawo ya zauna a inda ya tashi ba, yayi karfin
halin cika fuskarsa da murmushi.

“Ammy har yanzu kina kam bakinki dai?”

“Shiyasa ai ban gayyaci kowa ba, sai idan zai sake aure”

Captain ya karkato ya kalli Ammy yana murmushi.

“Allah Ammy?”

Ammy ta masa banza ta cigaba da magana da Salim.

“Karka biye masa, kai ma kasan wanda ya ke a cikin hankalinsa ya san me yake yi ba
zai auri yarinya irin Hurriya ba ko da kuwa an hada masa da buhun zinari da gidaje”

Salim ya saka hannunsa aljihu yana fadin.

“Gaskiya kam, Captain ka yi jihadi babba”

A take murmushin dake fuskarsa ya Captain ya gushe.

“Sosai kuwa, kuma kai har ka mutu ba zaka taba samu mace irin Hurriya ba, shiyasa
abun yake ba ni dariya idan Ammy tace zan kara aure bayan domin bana jin zan iya
ganin wata macen ta burge ni a yanzu, kuma ni ba zan auro macen da zata hana ni
zaman farincikid Hurriya ba”

“Baka ma bukatar kara aure Captain ko dan gudun a goranta mata, ni ma kuma bana
fatan samun Hurriya a yanzu na fi karfinta, kai ma kuma ba zaka iya nunawa duniya
ita a matsayin mata ba, ba zaka gane illar hakan ba sai nan gaba”

Captain ya mike tsaye anger na dibanshi.

“Hey Mr Salim daga yau na yanke duk wata alaka dake tsakanina da kai, kuma karka
kara fadar wata kalma marar dadi akan Matata, kawai kana kishi ne saboda ni na yi
dacen auren Hurriya ba kai ba, dan haka na datse alakarmu daga yau kar ma wata rana
ka ce zaka shiga gidana ka ga Matata”

Salim yayi murmushi mai sauti.

“Kishi? Shiga gidan ka na ga matarka? Macen da kowa ya gama ganin tsiraicinta kamin
ka gani? Ita kake cewa kar na shiga na gani?”

Captain ya saka hannayensa aljihu yana jin kamar ace da bindiga a ciki ya raba kam
Salim biyu a gurin.

“Gun?”

Salim ya saka hannunsa aljihu ya dauko bindigarsa ya aje kasa ya turowa Captain,
mai nema a duhu balle an haska masa Captain ya duka ya dauki bingidar ya saita
Salim da ita ya danna sai ta amsa da kettttt alamar babu albashiru a ciki. Ko da
acw akwai alhasashen harbawa Captain zai yi because he found it hard to control
hia anger. Ammy ta fasa ihu.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Jamal miye haka? Kisan kai zaka yi?”

Cikin takaici Salim ya kalli Captain ya ce.

“Da gaske zaka iya harbina idan akwai halsashe a ciki?”

Captain ya wurga masa gun din.

“Ga zahiri kana gani? And daga yau babu kai babu ni, and the rest ka jira na dawo
bakin aiki”

Salim ya duka ya dauki bindigar yana bakincikin da suka saka idonsa tara kwalla.

“Ban yi tsamman ni samun haka daga gareka ba Captain, wannan ne karo na biyu da ka
nuna ni da gum saboda Hurriya, soyayyar wata be kamata be kamata ya rufe maka ido
ba, har ka manta waye ni a gurinka, na gwada ne domin na ga idan zaka iya aikatawa
da gaske, kuma gashi na nuna, a yau ka nuna min tsantsar kiyayya Captain, daman na
lura da wannan babin tuna ranar da ka gane ina son Hurriya, amman karka manra har
yanzu ina da sauran amfani a gurinka, be kamata ka manta wannan ba”

Salim ya juya ya fice rike da bindigar. Captain da be karasa kawai kofar ya juyo ya
kalli Ammy yana huci.

“He even got lucky ban fasa bakinsa ba, kuma ba laifin kowa ba ne sai na ki Ammy ke
kika janyo har ya samu fuskar fada min magana haka kai tsaye”

Ammy da mamaki be gama fitarta ta janye hannunta a baki cikin tashin hankali ta ce.

“Kisan kai fa ke nan zaka aikata Captain?”

“Ammy idan idona ya rufe bana gane me zan aikata sai bayan sun bude nake ganin abun
da na aikata, kin san wannan tun ina karami kuma dan Allah ina rokon alfarmar karki
sake cewa zaki alakanta ni da Salim”

Yana kaiwa nan ya nufi hanyar dakinsa. Ammy ta bishi da kallon tsoro, har lokacin
jikinta rawa yake, bata tsamanin tsamanin fushin ďanta ya kai haka ba sai yau.

“Aikin soja ma be dace da kai ba, ba zan bari ka cigaba da aikin nan ba, idan ba
haka ba wata rana zaka kashe wani ka bar mu da aiki”

Ta juya ta dauki wayarta ta shiga kiran Daddy. Captain ya zauna a kujerar dakin
yake yana jin zafin kalaman Salim kuma yana mamakin kansa da be canja masa kamanin
ba. Ya mike tsaye ya halbi kujerar da kafa, ya cige bakinsa sosai yana jin kamar
ace Salim din ne a gurin. Ya nufi bandaki ya wanke fuskarsa ya fito sai ya fito
daga dakin gaba daya ya shiga kitchen ya bude fridge ya dauko ruwa ya zuba ya daga
cup din sama yana sha...

“Amman karka manra har yanzu ina da sauran amfani a gurinka, be kamata ka manta
wannan ba”

Kalaman Salim na karshe sun dawo masa, sai yayi sauri aje cup din ya lalaba
aljihunsa babu wayarsa da gudu ya fito Kitchen ya nufi wayarsa ya dauka ya kira
wata number.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

“Alhamdulillah Thank you so much i trust you”

Ya sauke wayar tare da ajiyar zuciya a lokaci daya. Kamin ya taba komai kiran Daddy
ya shigo wayarsa ya daga kira Daddy ya rufe da fada duk yadda Captain ya so ya
wanke kansa be samu haka ba a gurin Daddy domin be tsaya ya saurare shi ba.

“Amman Ammy bata fada maka abun da Salim yayi min?”

“Ko miye yayi maka be kamata ka nuna shi da bindiga ba, ran mutum ba abun wasa ba
ne kuma a yadda kake tare da Salim be kamata ace kana barin Sheidan ya shiga
tsakaninku ba, kana jami'in tsoro amman kake wasa da rayuwar wani wanin ma abokin
aikinki, da wani mugun mutum ne zai iya amfani da wannan damar yayi against dinka,
kuma idan ba zaka sauko daga wannan zuciyar ba ta ina zaka iya uba kuma mai gida?
Nan gaba matarka idan ta maka laifi sai ka ce zaka yi mata, ko kuwa ba zan lamunci
wannan ba, ban wahalar da mahaifiyarka ba zan yarda ďana ya auro yar mutane ya
wahalar da ita ba, dan haka tun yanzu ka zubar da hallayen nan naka bana son su”

“Zan kiyaye Daddy amman baka san Salim ba ne ya... ”

“I don't care what Salim did to you, ko zaginka yayi be kamata ka yi wasa da
rayuwarsa ba, be kamata ka nuna rayuwarsa bata da muhimmanci a gareshi ba, hankalin
mahaifiyarka ya tashi wane irin abu ne wannan?”

“Yi hakuri Daddy”

Yadda Daddy ya kashe wayar kadai ya isa ya bayyana maka har lokacin ransa a bace
yake, abun da Captain yayi kokarin aikata laifi ne babba a dokar kasa kuma laifi da
zai iya sakawa a hukunta mutum ko a koreshi daga aiki ma a dokar aikin soja, idan
ma ace ya aikata matsalar su zata fi shafa fiye da Captain din. Kansa ya dafa ya
runtse ido ya bude shi kansa yayi nisa abun da ya aikata a gaban mahaifiyarsa a
yau, be taba aikatawa wani haka ba sai Salim kuma shi ne karo na biyu, haka yake
jin kamar ba zai iya rike kansa ba a duk lokacin da wata magana marar dadi ta fito
daga bakin Salim zuwa kunnensa akan Hurriya. Tashi yayi ya nufi hanyar dakin da
mahaifiyarsa take sai ya same ta zaune ta kifa kai da guiwa tana kuka. A take
hankalinsa ya tashi daman kukan uwa shi ne tashin hankalin ko wane ďa na gari, ya
duka a kusa da ita yana kallonta idonsa har sun fada tsabar tsoron da ya kama shi.

“Ammy lafiya... Kuka kuma? Me ya faru?”


Ta dago ta kalleshi hawaye na zuba a idonta.

“Zuciyarka tana ba ni tsoro ni ba zuciya ba, mahaifinka ba zuciya ba kai ban san a
ina ka dauko wannan rayuwar ba, ban san me zaka aikata a gaba ba, idan babu kowa
wata rana zaka iya kashe wani, zuwanka garin nan ya bata abubuwa da yawa na
farinciki na Jamal, soyayyarka da yarinyar nan ya lalata akala da Hajiya Nafisa a
yanzu, saboda tana ganin zan iya cilasta ko kuma na yi fadi tashin hana tarewar nan
amman na gaza, Namra muka so ka aura Jamal ba Hurriya ba, idan ba zaka so ta gida
ba ka nemo ta waje mai mutunci mana ba wannan ba, yanzu kokarin tarewa kake da ita,
ka bata da abokinka kuma nuna shi da gun miye amfanin haka? Duk akan yarinyar nan
fa”

Zaunawa yayi a gurin ya nade kafafuwansa ya duba mahaifiyarsa duba na tsanaki.

“Mutum baya aure sai matarsa Ammy ya kamata ki gane wannan, Allah ya rubuta ni da
Hurriya zamu yi aure ko duk duniya za su taru ba za su iya tare wannan ba, zuwan da
nake a gurin Momy ban taba zuwa saboda wata rana rana na so Hurriyya ba, haduwata
da ita wani abu da Allah ya kaddara domin ban san da ita a gidan ba har sai da
Mahaifiyarta ta fita, na san akwai yayan mijinta amman ban rike fuskar ko daya ba,
Ammy ya kamata ki duba wani daura auren da aka yi ma bada sanina aka yi ba, amman
duka Allah ya rubuta faruwarsu, farkon haduwarmu da yarinyar mari ne, na mareta da
hannuna saboda ta taba ni ba ta gani ba, daga lokacin da Namra ta fada min bata iya
gani sai da gilashi sai ta ba ni tausayi, ban tabbatar da ina tausayin yarinyar nan
ba sai ranar da na je zan shiga dakin Momy da kunne na ji yadda take magana da
Hurriya akan cewa zata musgunawa yarinyar nan kuma ba tare da ta mata komai ba, su
kan hana ta abinci wani lokacin sai da taimakona take samu ta ci, kamin zuwa yanzu
mahaifinta ya tsane ta aka kashe dan'uwanta ta koma bata da kowa a gidan Allah, ga
mahaifiyarta ba lafiya, and now aka yi mata wannan abun yanzu a haka Ammy duk bata
ba ki tausayi ba?”

“Ta ba ni, amman ai bata dace da kai ba, ina magana ne akan dacewa”

“Ta ina kike ganin bata dace da ni ba?”

“Baka ga yadda hotunan suka yadu a duniya ba? Kuma bata gani”

“Rashin gani kar ya dame ki, ina da wani yakini cewar Allah ba zai kunyata bawansa
ba, da yardar Allah idon Hurriya zai bude, yada hotunanta kuma ba ita ta aikata ba
aikata mata aka yi saboda a bata mata suna, kuma an yi nasara tun da gashi matar da
ya kamata ace ta fi kowa kaunarta ta tsane ta, abun da zai baki mamaki ma
yar'uwarta ce ta aikata mata abun Ammy, hakan ya nuna yarinyar nan tana fuskantar
kalulabe na rayuwa kala kala, ke kuma kina kara taya Momy kishi ne kawai shiyasa
kike tsanar Hurriya da yawa, na tabbatar da Namra ce haka ta faru da ita Momy ba
zata so na guje mata ba haka ne?”

Ammy ta daga kai.

“Amman saboda Hurriya ba yarta ba ce shiyasa take fushi dake ni ma take yi da ni, a
gabanki ta fadi cewar laifi ba nawa ba ne ni kadai har da Daddy, saboda tana ganin
ya aura min yar kishiyarta ya bar yarta”

Captain yayi shiru na dan lokaci idonsa na cika da hawaye.

“Wallahi Wallahi Wallahi Ammy ban san dalilin da ya saka nake kaunar yarinyar nan
ba, ni dai kawai Allah ya saka min kaunarta, ina jin farinciki a tare da
farincikinta ina jin damuwa a tare da damuwarta, idan wani ya tsane ta ina jin
kamar ya tsani cigaba ne, ita kadai ce yarinyar da nake jin zan iya jure duk wani
abu da ya shafe ta, zan iya daukar duk wani zagi da suka a duniyar nan, ban sani ba
ko a nan gaba zan gane kuskuren hakan, amman a yanzu bana jin son kowa sai ita,
shiyasa na kan kasa auna abun idan an tuna duk kaunar da kike min matsayinki na uwa
kin tsani wandda nake so, to ina zan kama Ammy? Wani lokacin ina jin tsoron kar
yarinyar nan ta dawo a gidana matsayin matata ki musguna mata ko ki wulankatata,
kamar ni kika yi ma, na san ba zaki yi fatan danki ya wulakanta yar mutane ne balle
ke kanki ki wulakanta matata Ammy ban taba tunani ba, ko da ace Hurriya tana aibu
na yi tunanin zaki boye saboda kar na ji raina ya bace, amman ke da kanki Ammy kike
yakar yarinyar nan? Kina fadar yadda zaki yi idan aurena ya zo yau duk kin kawar da
wannan saboda Hurriya ce, a gabanki abokina yake zagin matata saboda ya samu fuska
a gurinki Ammy, kina fada min irin kaunar da kike min kina gudun bacin raina amman
yau babu wannan... ”

Tuni hawayen Ammy suka kafe a idonta ganin ďanta yana kuka, bakinsa na furta
kalaman dake kama kwakwalwarta.

“Kuka kake yi Jamal...? Hawaye kake zubarwa?”

Ya kawar da fuskarsa gefe.

“Ammy ya yadda kika san zuciyata, tun da kika ga na shanye duk abun da aka yi ma
Hurriya na kaunace ya kamata ki fahimci yadda tasirin sonta yake da karfi a zuciya,
Ammy a yau zan miki rantsuwa da Allah na tabbatar miki da abun da kike da muradi...
Wallahi Wallahi Wallahi Ammy idan fasa auren nan ne farincikinki, zan hakura da
Hurriya Wallahi ba zata tare a gidana ba a matsayin matata zan hakura da ita! Amman
tabbas zan roko Allah ya dauki rayuwata, na fi sha'awar mutuwa fiye da rayuwa babu
Hurriyya a matsayin Matata...! Ko da na mutu zan tafi da tunanin wannan abun... ”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Ammy ta furta tashin hankali na kwance a idonta ta rika fuskar Captain da duka
hannayenta sannan kamin ta tashi ta rumgume danta tilo daya tana hawaye.

“Abun be kai can ba, be kai can ba...”

Ta dago ta kalli fuskarsa ta sake rumgume danta.

“Wannan irin so da kake yi ma yarinyar Allah yasa ta zame mata ƴa, wannan son ya ba
ni tsoro”

Tsoro ba a furucinta kadai yake ba har a cikin zuciyarta yake, domin Captain be
taba zaunawa da ita gaba da gaba ya karabta mata soyayyar wata mace da karfi kamar
yadda ya yi mata a yau ba, a yadda zuciyarsa take idan ya rasa zai iya jefa kansa a
cikin wani hali wata kila fushinsa da zuciyarsa su karu har aikata abun daba shi ke
nan ba, wata kila kuma idan yayi addu'ar ya amsa masa ya tafi ya barta da
bakincikin rasa ďa ďaya tilo da Allah ya bata, da bakincikin kin abun da yake so,
idan kuma hakan ta faru ta san ba zata yafewa kanta ba, Daddy ma ba zai daina ganin
bakinta ba.

“Ni ban yi mata tsanar da zaka roki mutuwa akan rayuwarka ba, ni mai kaunar abun da
kake so ce kawai dai ina ganin rashin dacewa ne akwai, ni mahaifiyarka ce Jamal ba
makiyiyarka ba”

Captain yayi murmushi yana jin dadi a zuciyarsa, daman ya san Ammy ba zata iya
zabar mutuwarsa da rayuwarsa.

“Ina son ki Ammy ina sonki sosai, shiyasa yanzu da kika ji yarinyar nan farinciki
ya rage, saboda baki goyon bayana kuma babu wani annashuwa da murna da kike na
auren, wata kila ma jira kawai ake na yi auren a karbi rayuwata maybe shi ne last
abu da zan yi a rayuwata, wata kila zan tafi ne kawai na bar muku yarinyar nan, ko
yanayin aikin da nake ma rayuwata kullum a cikin hatsari take komai zai iya
faruwa....”

“Wane irin magana ne wannan?”

Ta daka mishi tsawa.

“Wane zance kake haka? Me yake damunka? Ina ce komai ya wuce ai, me kuma ya sake
dawo da zancen mutuwa?, bana son wannan maganar karka sake”

Ya amsa mata kai yana murmushi.

“Ba zan sake ba Ammy”

Ya kwanta a jikinta kamar yadda yake mata a lokacin da suke cikin Kaduna idan yana
gida tare da ita, babu ruwansa da girman da yayi kwantawa yake a jikinta yayi ta
zuba shagwaba, kamar wani yaro. Kansa ya shafa yana kallonsa ita kam ba zata iya
jurar rasa danta ba, zata haka for now domin ta san gaba ba zai dade ba, yadda yake
da fushi ma wata kila da kansa zai zo ya fada mata ya saki Hurriya wata rana, domin
zuciyarsa ba ko wace mace zata iya zama da shi ba, shi ma ba zai jure wani abun ba.
Dan haka zata aje makamanta a gefe ta saka musu ido, gudun kar ta rasa ďanta kuma
ya dauke ta a matsayin makiyiyarsa. Wannan ne abun da ta ayyana a ranta.

HAJIYA KALTUME POV.

“Daga min mana Ruma kafar nan ciwo fa take min amman sai ki rika dora min kanki nan
kamar baki tausayina, gashi idan ina tafiya kamar zan yi dingishi haka nake yi, ina
tunanin Egypt zan tafi a duba min ita, tun da nan sun gagara gane komai”

Ruma ta tashi daga kwancen da take a jikin Hajiya Kaltume ta kalli Khairy dake
zaune tana gyara akafaitar.

“Yau ke da kanki kike gyara kafarki?”

“To ya zan yi? Ni tsoron fita nake yanzu, mutane za su fara kallonka saboda video
nan da ya fita wata kila ma har a nuna ka ace ita ce”

Khairy ta fada kamar zata yi kuka. Hajiya Kaltume ta ce.

“Ke daina damar da kanki, abun ne dai kin riga min yi da kin yi shawara da ni da ba
zaki aikata ba, ku yara ne ba ku san bandar kasa ba, sai ku rika gaggawa kuna son
aikata abun da zai kaiku ya baro, gashi nan duk kin bi kin rame, kin tsallawa a
madadin ita aka yi ma ta shiga damuwa gashi nan ma shirye shiyen aurenta kawai ake
yi, ni damuwa ke damuwa abu ya taru yayi mana yawa, ni na rasa ina ma zan saka
kaina na ji sanyi”

Hawaye ya zubo a idon Khairy.

“Da na san haka abun nan zai zama Wallahi ba zan aikata ba, kuma Wallahi ba ni na
yada hotunan ba, ni dai kawai na nasa barazanar zan yada ne, shi ne yayi min shairi
yace ni na aikata, gashi ya fadi zancen fyaden nan kowa ya ji, na muzanta Hajiya na
ji kunyar duniya”

“Ba ke kadai ba, abun ya shafi kowa ai, da murna nake da Hurriya ce ta janyo sai
gashi reshe ya juye da mujiya, ga abokiyar taya ni yakin tana can babu lafiya, ni
na rasa ma ina zan kama, abubuwa sun tsaya min cak...! Ina tunanin shiryawa zan yi
na tafi gurin Yaya Altine...”
Bata rufe zancen ba Alhaji Musa ya turo kofar falon ya shigo da sallamar fuska kuma
babu annuri. Hajiya ta amsa Khairy ta sauke kai kasa tana jin kunyar hada ido da
kanen mahaifin nata, ruma kuma ta gyara zamanta tana masa sannu da zuwa sai ya amsa
yana zaunawa.

“Yauwa... Sannu dai Hajiya barka da gida”

Hajiya Kaltume dake jin kamar ya zo yayi mata albishir ne na ganin ya daidaita
tsakaninta da Appa ta amsa masa tana murmushin karfin hali.

“Lafiya Kalau Alhaji Musa ya yaran?”

“Alhamdulillahi...”

“Maa Sha Allah...”

Sai kuma shiru ya biyo baya tun bayan da Hajiya Kaltume ta yi magana ta karshe.
Khairy ta daga kai kadan ta kalleshi ta ga ita yake kallo sai gabanta ya fadi, ta
mike tsaye zata bar falon ya katse shirunsu ta hanyar dakatar da ita.

“Zauna Ummulkhar maganar ai duk a kanki ne... Wato Hajiya dazun ni da Yaya mun tafi
gidansu Hajiya Iyami, to ni ina daga waje saboda na dan ba su guri ne su gana, sai
gashi ya fito yana fada min iyayen yaron nan ne suke son ganinsa....”

Daki daki Alhaji Musa ya jera musu abun da ya faru har zuwa karshe.

“A takaice dai yanzu shi yaron yace baya ciki idan ta samu wani ta yi aurenta”

Khairy ta fashe da kuka mai karfi daman ta saka ran haka, ganin yadda yaki ya daga
wayarta tun daga lokacin da abun ya faru har zuwa yau da aiko musu da mummunan
sako, Ruma ma kallon Khairy take cike da tausayinta domin ta san abubuwan za su
mata yawa ne. Fasa auren na Khairy da aka yi ba daga hankalin Hajiya Kaltume ya
jefata a tunani ba kamar jin cewar Alhaji Musa ya bawa Appa da Amma guri domin su
gana sai ta ji kamar an watsa mata garwashi a zuciya.

‘Su gana kamar yaya? Daman ganawa suke a yanzu? Ko da yake ga zahiri tana ganin
shirye shiyen auren Hurriya da ake sai dai ta ji labari yadda aka yi ko za'ayi a
gurin ďanta Yasir idan ta shinshini gulma, be bawa Momy ta yi komai ba ita da take
karkashinsa a yanzu balle kuma Ita da igiyar aure ta raba, yanzu hankalin Appa ya
koma gurin Iyami kenan? Gashi har da zuwa da kanensa ko dai auren zai maida? Tun da
yanzu ta samu lafiya kamar yadda ďanta ya fada mata tun kwanakin baya? Ita kam
abubuwa sun ribchabe mata a yanzu komai ya shige mata hudu...’

Bata gama sakar zuci ba Alhaji Musa ya kira.

“Hajiya kin fahimce zancen nawa?”

Sai ta kalleshi kamar wata yar marainiya idonta na cika da hawaye, ta rasa laifin
me ta yi abubuwa suka zo mata a haka.

“Na fahimta Alhaji Musa, to me zan ce kaddarori ne gasu nan sun rufe mu..”

“Shiyasa aka ce idan zaka gina ramen mugunta ka gina gajere, yanzu gashi garin yi
ma yar'uwarki sharri kin kunyata kanki kin kunyatata kin bata sunan gidanku, ina
amfanin haka?”

Hajiya Kaltume ta dafe kanta.


“Yara ne sai ka rasa gane me ke cin zuciyarsu batsa tsayawa su yi tunani”

A nan ya samu zaren zancen ya rufe ta nasa fadan yana karanta mata inda yake ganin
abubuwan da yake yi ma yaran ba daidai ba ne.

“Komai dai aka yi uwa ake dorawa laifi, to na ji Allah ya yaye mana”

Ya tashi ya fice daga falon ba tare da sallama ba.

“Yanzu ni Hajiya Fatee zata yi wannan cin fuskar, ashe ko mutuwa na yi ita din ba
mai rufa asirin yaya ba ne? Har zata kyale Fadeel ya aiko wai ya fasa aurenki? Ita
Hurriya ba gata nan makauniya ba amman a haka da siraicinta da komai ta samu dan
manya mutane ya aureta?”

Ruma ta share hawayenta ta ce

“Hajiya Saboda Hurriya bata aikata ba ne aka yi nata sheri aka ce ta yi, shiyasa
Allah yayi mata wannan sakamakon, daman sakamakon masu hakuri mai girma ne, shiyasa
yake da kyau mu kiyayi iyakokin Allah domin ba za mu iya jurar radadin ukubar sa
ba, gashi yanzu tun ba ayi nisa ba ta fara ganin illar abun da ta aikata”

“Ke dalla can rufe mim baki, tun kamin a haife ki na san wannan! Tashi ki ba ni
guri, daman ke da Yasir haka kuke kamar ba ni na haife ku ba”

Ta lalabo wayarta dake hannun kujera ta shiga kiran Hajiya Fatee....


Fadeel ya gyara mata fillon dake bayanta ta jingina da fillon tana runtse ido, ta
cije baki alamar ba karamin ciwo take ji ba.

“Wayarki ce take ringing a miko miki?”

Ta daga mishi kai, sai ya tashi ya nufi gurin da wayar take ya dauko ya miko mata.

“Hajiya ce take kira”

Hajiya Fatee ta karbi wayar ta duba ta aje domin ba ta da kalaman wanke kanta a
gurin aminiyarta a yanzu, ita ma ta kanta take.

“Wata kila ta kira tayi maganar auren da na ce na yanje ne”

“Shi ne ma, da dai ka yi hakuri Fadeel ka rumgume kaddara kamar yadda mijin Hurriya
ya rumguma”

“Hajiya ko na auri yarinyar nan ba zan samu aminci da ita ba, daman can ba sonta
nake ba saboda ke na nake son na aureta shi na dan kin matsa, kuma yanzu kowa ya ga
abun da ya faru babu wanda zai so ta zama uwar yayansa fa, indai zata iya aikawa
yar'uwarta haka ina da sauran mutane ko abokiyar zama? Amma Hurriya kaddara ce ta
fada mata, ni Wallahi da wannan din ma be aureta zan iya aurenta yarinyar tana da
kirki ai”

Hajiya Fatee ta sauke ajiyar zuciya ya hade yawu.

“Yanzu dawowa zaka yi da Afrah kenan?”

“Haka nake tunani Hajiya saboda akwai yara a tsakaninmu, kuma daman bata min komai
ba haka nan kawai na turata gida ban san me ya zo kaina ba, yarinyar nan tana min
biyayya sosai ke ma kuma tana miki kawai dai kin dauki karan tsana kin dora mata ne
Hajiya”

“Tana yi fa, tana min biyayya gwargwadon hali, gashi nan ai na koma da ciwo, daman
wanda be gode Rahamar Allah ba zai gode azabarsa...”

Ta karashe zancen da kuka.

“Wannan kuma wata jarabawa ce ta Allah Hajiya, wannan ciwon ai ba san minene ba
ciki ya fara kumbura kuma kin ce ba ki son aje asibiti, gashi tun da muka dawo
ciwon zuciya be barki ba, ga cikin nan naki tsoro yake ba ni, idan na ce zan tafi
asibiti kuma ki ce ba haka ba, a nan gida kowa duk wanda ya zo ba hadin kai kike ba
su ba kuma basa gane komai”

“Zan tafi ba yanzu ba, Fadeel lokacin da zaka kai ni asibitin zai zo, yanzu na
hausa nake son gwadawa ina tunanin aikin jinnu ne, akwai inda Murja zata karbo min
magani na fara sha”

“Toh Allah ya sauwake”

Ya fada tare da damuwa sannan ya tashi ya fice falon zuwa gurin kanwarsa Zainab da
ta zo daga Neja take jinyar mahaifiyarta. Sai da ya fice sannan Hajiya Fatee ta
daga kiran Hajiya Kaltume dake shigowa a karo na barkatai.

“Wallahi Hajiya Fatee kin ba ni mamaki, yanzu kina raye zaki bari ďanki ya juya ma
Khairy baya? Kina raye Fadeel zai watsa min kasa ado? Ashe ke ba mai rike yarana ba
ne ko da bana raye?”

“Na ce kar yayi Hajiya Kaltume amman ya nuna min ba zai iya auren Khairy ba, kuma
kanen mahaifinsa ma da suka nema masa auren da kansu suka kira shi suka bashi
shawarar ya canja wata yarinyar”

“Amman ai kin isa da shi, sai ki nuna masa hakan ba daidai ba ne kuma ki ce ba zaki
yarda ya fasa auren nan ba, shi be san kaddara ba?”

“Ke kaddara kika sani ne? Na ce ke kaddara kika sani ne da zaki rufe ni da fada
kamar uwata? Ki bar ni na ji da damuwata mana, kin san halin da nake ciki amman
saboda rashin tausayi irin naki kike neman kara min wani”

Hajiya Kaltume ta nuna kanta.

“Ni ce marar tausayi yau Hajiya Fatee?”

“Idan ba rashin tausayi ba, miye na kira kina daga min hankali? Kaddara kowa ai
rumgumarta yake, ke yarda kika yi da kaddarar auren Iyami? Na ce yarda kika yi?
Gashi nan kin janyo min saboda ke zan mutu na barwa yaya abun kunya, saboda ke
komai ya lalace min, babu kalar karyar da ban yi ba akan cikin nan, kuma duk
sanadinki ne komai ya faru, ke da kike kishiyar ba a miki fyade ba sai ni yar
rakiya, kuma ke Malam be miki komai ba sai ni kujera mai dadi zama, yanzu wai har
kina da karfin halin kira kina min masifa, to ba zai aureta ba, kuma Wallahi ďana
ya fi karfinki magani ba zai masa komai ko bana raye, karki sake kirana da wani
zancen Khairy aure an fasa ba za'ayi ba, idan cilastawa gaskiya ki cilasta Alhaji
Haruna ya maida ke mana, ko ki cilasta Yasir ya nemo mai aurenta a cikin abokansa
sai ni da kika raina...”

Ta kashe wayar tana kuka sosai kamar ranta zai fita.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na
goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun
lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
“Wai yau ni zan kira Hajiya Fatee ta zage ni ta kashe min waya? Yau ni duniya ta yi
ma zafi haka? Ashe rana zata zo da aminiya ta zata watsa min kasa a ido? Ta fada
min ban yarda da kaddara ba? Yau ni Kaltume duniya ta yi ma daurin hohon goro?”

Rike take da bakinta tana maganar mamaki fal a zuciyarta, taya abubuwa suka zame
mata haka? Ga saki ga auren Hurriya ga auren tata ƴar an fasa yau kuma ta kira
kawarta ta fada mata magana marar dadi. Ruma ta kalleta kamar zata ce wani abu sai
dai kuma ta san mahaifiyarta ba mace ce mai fahimta ba, dan haka bata yi kokarin
furta komai ba, Khairy sai rusar kuka take kamar wanda aka yi ma mutuwa.! Ta sani
ba wani son Fadeel take ba amman tana hangosa a wani tsani da zata hau ta tsira
daga kallon da mutane suke mata kuma ta samu mafaka da zata fake daga zagi da
bakinciki zuciya. Sai dai kuma a yanzu ta rasa wannan saboda Fadeel ya juya mata
baya...!

“Da ma mutuwa na yi da ma ban kawo yau ba, rayuwa ta juya min Hajiya, yau ni ce aka
fasa aurena, ni ce Appa yake fushi da ni, yau ni ce video suke yawo jama'a na tsine
min, yau ni ce nake tsoron shiga cikin mutane, ni ma ni ce na mutu ba Salma ba?”

Hajiya Kaltume ta kalli yarta cike da tausayinta ta ce.

“Ki daina yi ma kanki fatan mutuwa Khairy fasa aure ba shi ne karshen duniya ba,
ita kanta da hotunanta suka yadu a duniya ba ta rasa mai aurenta ba balle kuma ke
da magana kawai aka fada akanki kuma ba kowa ya ga hotonki ba, abubuwa za su daidai
ta Khairy ki daina fatan mutuwa dan Allah”

“Ba zaki gane yadda nake ji ba Hajiya, ba zaki gane ba shiyasa kike fadar
hakan...!”

Hajiya ta daka mata tsawa kamar yadda take mata magana da daga murya saboda rashin
kunya da bakinciki.

“Ni kin san yadda nake ji ne? Kin san abun da yake raina? Ke aurenki kadai aka fasa
fa amman kike wannan haukar ni kuwa mahaifinku sakina yayi saki biyu, yanzu kuma me
kika gama jin Alhaji Musa ya fada? Cewar daga gidansu Iyami suke alamar zata iya
dawowa a koda yaushe kenan! Ga auren Hurriya babu wani shirye shirye da ake da ni,
sannan mahaifinku ya juya muku baya, da yanzu shi zai shigo ya sanar mana fasa
auren nan yana fada yana karawa amman ki duba ko shigowa nan baya son yi, rabuwata
da mahaifinku da cewar babu ruwansa da yarana dawaimiyarku akaina zata dawo dan
kasuwanci da na fara karyewa zai yi abun da na tara ya kare, kuma bakincikin bana
tare da mahaifinku ba zai bar ni na cigaba da rayuwa ba, amman a haka dauriya nake
so nake na rarrasheki kokarin kwantar miki da hankali nake”

Khairy ta tashi ta shige dakinta da gudu tana kuka, Hajiya Kaltume kuka take sosai
kamar yadda kukanta ya saka yar autarta Ruma kuka.
“Hajiya ko zaki ma su Baba Musa da Baba Lawal a bawa Appa hakuri”

“Babu wanda zan yi ma magana Ruma, babu wanda be san abun da ake ciki ba amman ba
su yi kokarin sasantawa ba, ba zan kai kukana a gurin kowa ba, Wallahi hakki ba zai
taba barin iyami ba ba zata taba ganin daidai a rayuwarta ba”

Ruma ta dubi Mahaifiyarta cikin rashin fahimta inda uwarta ta dora.

“Hajiya Amma bata gidan nan fa, taya wannan issues din ya zama laifinta? Wata kila
ma dai kisan da kika saka ka yi ma Hamad ne nake bibiyanmu...!”

Hajiya Kaltume ta kalleta ta sauri ta buge mata baki.

“Kul.... Kul... Kul... Kika sake furta magana irin wannan, kul... Zuciyarki ta sake
raya miki wani abu makamancin wannan... Ni ban kashe Hamad ba ban kuma ce a kashe
shi ba, su suka aikata a karan kanku dan haka babu zancen bibiyar hakki a nan,
Iyami kuma ita ce silar komai tun farko dole na fadi haka, ke yarinya ce ba zaki
gane abun da nake nufi ba, kuma ba zan bawa Alhaji Hakuri ba, ba kuma zan nemi kowa
ya shiga maganar aurenmu ba, da yardar Allah sai Alhaji ya kawo kansa yana kuka
yana rokon na yafe masa”

Ruma ta kalli Hajiya Kaltume domin ta gama fahimtar inda ta dosa, ta san kuma wanda
yayi nisa baya jin kira mahaifiyarta ba zata taba fahimtarta a yanzu ba, dan haka
ta share hawayenta ta tashi ta bi bayan yar'uwarta.

“Duk yadda za'ayi na gyara al'amurrana sai na yi sai dai na rasa komai amman ba zan
zauna na zuba ido ina kallon abubuwa suna tafiya ba daidai ba, ni da mijina shekara
da shekaru kuma ace ni zan koma baya?”.

Ta share hawayenta wasu na sauko mata, zuciyarta na da yakinin zata iya wannan
yakin kuma ta ci nasara, bin bokaye da yan bori ne take jin yanzu ta fara domin ta
gwada ta ga riba.

MOMY POV.

Miwan ya sauko hannunsa daya a aljihu dayan kuma yana rike da wayar da ake yayi yar
zamani, daga inda Momy take zaune ta dago kai ta kalli danta cike da farinciki da
kuma alfahari.

“Kamar jiya kuka bar kasar nan gashi yanzu har ka dawo Alhamdulillah”

Miwan ya zauna yana murmushi gashin kansa yayi tsiro kamar wani dan kwallo.

“Momy muma muna alhari da ke wannan duk jajircewarki ce, da mun bi ta Appa ba zamu
yi masters din nan ba, Namra ma ya kamata ta je ta yi, domin yanzu degree ya zama
ruwan dare masters ce ke dan karawa mutum girma”

“Ita ma zata yi ai In Shaa Allah, da zarar abubuwa sun daidaita zata yi”

“Wai me yake damunta ma? Tun da na dawo ban taba ganinta a falon nan ba ba”

Momy ta aje cup din lemu dake hannunta.

“Ina ce shekaranjiya ma mun yi maganar nan da kai?”

Ya dan daga kafadunsa.

“Na ji ni ma ban so Captain ya auri Hurriya ba, amman ya zamu yi? Tun da mai faruwa
ta faru? Kuma ba ga ta inda wannan abun zai zame mata abun damuwa ba har da su boye
kai a daki”

“Saurayi biyu Namra ta rasa saboda Hurriya, na farko be wani dame ni ba ni ban ma
wani san shi ba, amman Captain har yanzu zuciyata ďaci take saboda be auri Namra
ba”

“Amman ya nuna yana son Namra ne? Ko kuma dai ke kuke ta hasashenku ne? Wata kila
ku kuka saka mata rai ita din ba shi take ra'ayi ba, ko dai yaya ya kamata ta
hakura mana tun da mai faruwa ta faru”

“Daman ai dole hakura zamu yi, amman tabbas yayana da Captain sai sun yi nadamar
abun da suka aikata, ba dai dangin Iyami ba ne?”

“Ta ji sauki wai?”

“Waya san mata can ita ta sani, ni har yau ban leka gidan ba, ko last time da
mahaifinku zai tafi sai da ya ce min ko zan je na ce Allah ya tsare ni da zuwa
gidan Iyami, shekaranjiya ma ina jinsa yana zancen zai biya min ummara ni da Sapna
na san ba zai wuce dafe dafe ba daga karshe yace albishir din maida Iyami ne”

Miwan ya dan dago ya kalli Momy yana murmushi

“Ni Allah har mantawa nake ina da yar'uwa Sapna wai tana nan dama”

“Da ta mutu ai da ka sani kamar yadda ka sani a lokacin da Salma ta mutu”

“Haka ne kuma, mutuwar Salma ta ba ni mamaki Wallahi haka sidda”

“Babu yadsa mutuwa bata zuwa ga bawa ai, ba a mamakin mutuwa sai dai fatan
kyakkyawan karshe”

Ta tabe baki ya cigaba da taba wayarsa. Momy kuma ta kawar da fuska tana wani
tunanin na dabam.

CAPTAIN POV.

Abubuwa da yawa be saka ran Ammy zata yi ba zai a auren nan su take ta kokarin
shiryawa a kuraren lokaci ciki har da Walima da wanki ango da kamu, mutane da yawa
da ta Boyewa zancen auren yanzu su take aikawa da katin gayyata wasu kuma tana
sanar musu ta waya yadda za'ayi bikin, tana yin haka ne kawai saboda farinciki
danta, so take kallon da yake Mata na macen da bata son aurensa ya tashi zuwa mai
son cigabansa ba kuma dan tana son Hurriya ba sai dan haka ya zame mata dole ta
aikata a matsayinta na uwa.

Captain kawai ya zauna ne yana kallon yadda abubuwa suke gudana, wasu daga cikin
cousins dinsa da friends sai a yanzu suke kiransa suna taya shi murna da yawansu
sun fi tambayar yaushe ne dauren auren idan ya fada masu an daura sai su yi ta
mamaki wasu kuma su ce ya boye musu wasu su ce be gayyace su ba, haka dai yayi ta
fama wani gurin ya samu wanke kansa wani kuma sai dai ya kyalesu su yi ta complain.
Ran Momy be kara baci ba sai da ta ga mini iv da Ammy ta saka ayi mata ta raba na
gayyatar walima da wunin biki, bakinciki be bar Momy ta leka walima ba balle wunin
biki kirkiri ta fitar da hassadarta a fili, daman ta wani bangaren tana ganin kamar
har da laifin Ammy na bari Captain ya tare da Hurriya bata bude masa wuta ba, ta
bangaren Ammy kuma tana ganin kamar Momy ta zafafa da yawa domin ita ma da take uwa
ta hakura ta bar abun a zuciyarta balle Momy da take kanwar uba, a yanzu take kara
yarda da zancen Captain ba, Momy ba tana bakinciki auren ne saboda ba Namra ba ce
not just because of Hurriya tana yar mijinta.
A family House din Mijinta Ammy ta yi Walima da wunin, ba daga arewa kadai ba har
daga kudancin Nigeria da yan'uwanta da na mijinta da suke wajen kasar nan da wasu
daga matan abokan kasuwanci Mijinta sai da suka yanke uzuri suka halarci walimar da
wunin biki, saboda sun san daga Daddy har Ammy ďa ďaya suke da shi Captain balle su
ce idan ba su samu zuwa a wannan ba idan wani bikin ya tashi za su tafi. And ba su
taba aurar ba sai akan Captain saboda haka dole ayi musu kara.

Walima aka yi ta gani ta fada, idan baka da gate pass baka isa ka shiga ba, kana
shiga kuma za a bude bayan motarka ka a zuba maka gift din Walima da kaza daya da
aka soya aka yi package dinta da kyau, idan kuma baka da mota za a baka abun ka a
hannuna ne ta inda Ammy ta banbanta abun ta gurin raba abun da yake cikin jakar
kayan walimar ne, masu hannu da shuni ta saka musu manyan abubuwa na masu arziki,
wadanda aka raina capacity dinsu kuma sai ta saka musu na su kanana, Ammy da kanta
ta aika da motoci aka dauko Hurriya da yan gidansu, daman ta saka an sanar musu da
abubuwan da ta shirya tun gabani zuwan ranar, Ammy bata son kowa ya gane Hurriya
bata gani dan haka ta fada mata ta yi acting smart kar ace ďanta ya auri makauniya.
In a code way aka yi komai na walimar sai dai haka be hana wasu noticing something
is wrong with Hurriya ba saboda yadda bata respond ma mutane idan aka yi mata
murmushi, and bata iya daga kai ta kalli mutane da kyau, team babu ruwanmu da gulma
ba su kula ba har ayi aka gama.

Ranar wunin biki Hurriya ta chaba ado da farin lace da farin mayafi domin farar
rana ce da ko wace ƴa mace take fatan gani a rayuwarta, kallo daya zaka yi ma
Hurriya ka fahimci babu yaki babu ja Captain ya zabo daya a cikin dubu, innocent
face dinta ta sha light makeup, an gyara gashin kanta ya kwanta baya kamar ba a
taba kai masa hannu ba, farar kafarta ta sha jan lalle mai daga hankali kowa ne
jarumin namiji mai son ido da kwalliya, ga jiki ya sha dilka ta ko'ina kyali take
kamar tsadadden lace dake jikinta. Ya yadda mutane suke fada yadda ta yi kyau take
auna irin kyau da ta yi, domin a nan aba a lamunce mata da ga yadda kyauta yake a
fili ne. Duk shagalin da ake na bikinta bana ganin kowa sai dai ta yi saurare a nan
ma sai da yarda ta rasa wasu masoyan da Allah yayi alkawarin wanda ya rasa su kuma
yayi hakuri zai masa sakamako da Aljanna, wato masoya biyu idanuwa. Hurriya na
zaune dakin Gwaggo akan gadonta tare da Husna da wasu daga cikin kawayenta na
makarantar su da boko da islamiya da Husna ta gayyato Amma ta shigo dakin tana
sanye da lace mai tsada brown color ita ma ta sha nata lallen sai dai nata na hausa
ba yayi baki sosai yayi mata kyau.

“Husna ke da kawayenki ku dan ba ni guri zan yi magana da Hurriya”

Husna ta tashi tare da kawayen suka fice, zuwa falo wasu kuma suka fita harabar
gidan da Appa ya saka aka gyara ko'ina saboda Hurriya. Amma ta zauna tana kallon
yadda fuskar yarta ke sheken amarci.

“Kamar jiya aka haife ki, ina tunawa lokacin da mahaifinki ya shigo me ya Gwaggo ta
bari aka haife ki a gida, saboda baya son matansa na haihuwar gida, ya fi son a
tafi asibiti, sai Gwaggo tace ai na haihu lafiya kuma ya amsa ƴa mace,mahaifinki ya
shigo ya saka hannu biyu ya karbe ki, a take a gurin ya rada miki suna ba tare da
yayi shawara da ni ba, ya ce barka da zuwa Hurriya, Allah yayi miki albarka yasa ke
din mai amfanarmu ce, kuma ya nuna mana aurenki, ashe Allah ya amsa”

Amma ta sauke kai kasa tana taba akwatin sarkar zinarin dake hannunta.

“Ina cikin wani irin farinciki a yau marar misaltuwa, burin ko wace uwa ta ga auren
yarta, kuma da mijin da yarta take so yake da halin kwarai, Wallahi ban yi zaton
rayuwa zata ara min lokaci na kawo yau ba, ashe dai zan tashi zan yi magana zan
aurenki Hurriya”
Amma ta bude akwatin sarkar zinarin dake hannu ta dauko sarkar da take a matsayin
sadakin Hurriya ta yaye mayafinta ta saka mata a wuyanta.

“Ina miki murna ganin wannan rana mai daraja, Allah yasa ki shiga gidan aurenki a
sa'a kuma ya baki yaya masu yi Miki biyayya kamar yadda kika yi min, ina kaunarki
ƴata Allah ya bawa wannan yaron ikon yi miki adalci da kaunarki kauna ta hakika ta
har abada”

Hurriya ta rumgume Amma da sauri tana kuka irin yar da bata son rabuwa da uwarta.

“Allah na gode maka da ka nuna min wannan rana”

Amma ta yi ma Allah godiya tana kuka kamin ta dago Hurriya daga jikinta ta kama
hannayenta ta rike.

“Ban sani ba ko ba zan samu yin magana da ke na anjima ko kuma ya kasance cikin
mutane ne ba zan iya fadar wani abun ba, dan haka nake son baki wani sirrin zaman
aure a yanzu wadda uwata ta ba ni kuma shi ya taimaka min har ake ganin kamar na
mallake Appanku”

Hurriya ta natsu sosai ta mika hankalinta a gurin mahaifiyarta.

“Ki rike hakuri, hakuri wani abu ne mai wahala aiwatar ba, amman ba shi da wahala
ga wanda ya dauki rayuwa da sauki, da hakuri na mallake zuciyar Appanku, idan yana
magana ko yayi fushi bana katse shi, saurara nake na ji kalamansa kuma na yi hakuri
ko da kuwa sun bata min rai, idan ya ba ni rashin gaskiya karba nake na rike ko
kuwa ni ce mai gaskiyar, sai bayan ya huce sai na lurar da shi kuskuren inda aibu
yake, ko kuma na fada masa gaskiyar a inda take, idan na ga yana son abu ina
kokarin na ga na fi sonsa, shiyasa ban taba nunawa yayansa kiyayya ba, na rike
mahaifiyarsa kamar tawa ina kyautata mata ina mata biyayya kamar yadda nake yi ma
danta, ina sa yawan kyauta saboda dangin miji da makota basa son mace mai rowa ko
mai tsananin son abunta, idan na ga yayi wani kuskure ina nuna masa illar haka kuma
na nuna masa hanyar da ta fi saukin bi, ban taba nuna masa ina kishin Nafisa ko
Kaltume ba, kuma ba dan bana yi ba, sai dan na fi karfin zuciyata na boye abun a
raina, shiyasa baya taba yarda cewar bana son matansa saboda na iya takuna, kuma na
rike girki na iya tuka tuwo yayi kyau na yi dadddar miya Appanku da ku kanku kuna
ci suna santi, na rike tsabta na rike kamshi mahaifinki ya taba fada min idan ya ji
kamshi turaren da ba nawa sai ya ji a dabam, duk abun da na san mahaifinku zai
bukata kamin ya fada na aiwatar idan kuma na kyama ne ina gudun nake kauce masa, da
wannan na gagari matan ubanki har suke ganin kamar na mallake shi na masa magani,
idan girkina ya dawo da wuri Appanku yake dawowa gida, ke ma ai kin sani saboda ina
masa hira, ina ba shi labarai masu dadi, na yi masa hira mu tattauna abubuwa da
yawa na yadda rayuwa take ciki, ni ce radio sa ni ce tv sa idan ina kusa da shi
bana yarda hankalinsa ya tafi ko'ina zai a gurina, idan kuma ba girki ba ne ina
kokarin kiyayewa na ga ban shiga hakki abokan zamana ba, idan zai yi zabe ni nake
zaba masa komai, ban tana yarda Appanku ya saka kayan da yake ra'ayi ba a ranar
girkina, saboda kwalliyar tawa ce ba tashi ba, ni nake zaba masa kayan da zai saka,
sai kuma na yi sa'a shi din mutum ne mai tsananin so na mai saurarena mai gudun
bacin raina...”

Amma ta yi murmushi tana tuna baya.

“Idan Appanku ya ce Iyami kar ayi kaza, Wallahi bana aikatawa saboda ya ce kar ayi,
ina ba shi lokacina sosai ina jin maganarsa ina bin dokokinsa, saboda ni ce a kasa
shi ne a sama shi din jagorana ne, Allah ya riga ya ba shi wannan girma, ni kuma
dole na bi saboda na samu aljanna ta, kuma kar ki yarda wani ya fahimci irin zaman
auren da kike da mijinki ba mai dadi bane ko da kuwa kun samu tsabani, ki sama
ma'ajiyar sirrinsa mai rufe duk wani asirinsa, kuma ki rika lura wane hali miJinki
yake shiga idan yana ciki damuwa idan yana fada ya yake, idan yana farinciki ya
dabi'unsa yake, abun da duk kika ji zaki iya dauka ki nuna masa tun farkon zamanku,
wanda kuma ba zaki iya dauka ba ki fahimtar da shi da wuri ba sai daga baya ba,
karki yarda ki raina mijinki ko da kuwa shi din abun rainawa ne a gurin wasu
mutane, ki zama macen da idan ran mijinki ya bace ke zai rika tunanin ko ma ya
nufo saboda ke kike kwantar masa da hankali. Kin ga abubuwan nan da na fada miki,
wata rana sai kin zo kina fada min yan'uwan mijinki suna tunanin kin mallake shi,
kuma wata rana mijinki ko aure ya kara zai yi ta ganinki ne wata macen ta kasa
sarrafa shi saboda karatunki ya saba dauka, wani darasin zai masa wahalar zama a
kai, da haka na gaggara a gidan mijinki sirrin ba na iya kyau bane kawai har da na
iya zama, ai wata macen bata da kyau amman a haka mijinta yake sonta fiye da kyau,
karki yarda wata macen ta fi ki a gurin mijinki”

Amma ta saka hannu ta share hawayen Hurriya dake zuba tana murmushi.

“Allah ya miki albarka”

“Ameen Amma na gode”

Ta fada cikin kuka wasiyar Amma na ratsa jikinta. Rukayya ce ta shigo dakin tana
sanye da anko kamar sauran yan gidan, ta yi matukar kyau blue atamfar ta karbe ta
sosai.

“Amma gasu nan sun iso, tare da mai hoton amman Gwaggo tace a fara kai masa Hurriya
su gaisa kamin mu shirya a fito hoton”

Amma ta kalli yarta dake hawaye har lokacin tana murmushi.

“Amarya tashi tafi ki gaisa da angonki”

Hurriya ta ji gabanta ya fadi, irin faduwar gaban dake samun ko wace amarya a ranar
wunin aurenta, daman tun da aka daura auren har zuwa yau ganin take kamar mafarki
take ba gaske ba. Kamin ta yi wani yunkuri Gwaggo ta shigo daki tana masifa wai
fitowa da amarya ya gagara a bar ango a can yana jira.

“Ai dole ya jira Amaryar ta mu mai tsada ce Amma”

Rukayya ta fada, Gwaggo ta gwatsaleta.

“Dan Allah can rufe min baki marar kunya uwar kawai”

Gwaggo ta kama hannun Hurriya ta fice da ita daga dakin.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro
kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku
da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Yana jin kamshi ya doso bakin kofar falon da yake zaune yayi saurin rufe idonsa,
yana murmushi, sai da muryar Gwaggo dake rangwado sallama ta karya hanzarinta. A
dole ya bude ido daya.

“Haba dai ina zumudin fara ganin Matata sai kawai na yi arba da fuskar tsohuwa...”

Gwaggo ta yi dariya tana mamakinsa.

“Kai daga na maka abun arziki na kawo maka ita na rabaka da jira shi ne zaka watsa
min kasa a ido? Daman ai ni ce uwar gidan ba ita ba”

“Aa ni yarinya na aura ba tsohuwa ba”

Gwaggo ta girgiza kai. Ta matso da Hurriya ta gabanta.

“To gata yaran zamani marasa kunya”

Shi dai be ce mata komai ba sai kallon Hurriya yake, har Gwaggo ta fice daga dakin.
A inda yake kyautata zaton gabas ne ya maida gaba ya duka kasa yayi sujadar godiya
sannan ya dago ya daga kansa sama yana kallon Hurriya dake tsaye gefensa.

“Fatabarakkallahu ahsanal halikin... Tsarki ya tabbata ga ubangijin da ya mallaka


min Hurriya a matsayin mata”

Ya mike tsaye ya fuskance ya kama hannayenta masu taushi yana murzawa a hankali.

“My Angel rabin rayuwar Captain Jamal Aliyu Turaki, macen dake harba wuta a zuciyar
Captain, macen da zuciya takw muradi rayuwata take tsoron rasawa”

Ya hade goshinsa da nata yana kallon kwayar idon da ta rufe duk kuwa da kasancewar
bata iya ganin komai ba dan komai ba sai dan tsananin kunyar Captain da take ji a
yanzu. Shi ma rufe idon yayi suna ta musayar Numfashi, slowly ya saki hannunta ya
saka hannayensa ya zagaye kwankwasonta.

“Finally...”

Ya rada tare da sumbantar saman fatar bakinta. Ya dago hananyensa yayi sama dasu ya
kwantar da ita a kirjinsa dake cike da babbar riga.

“Ina da wata babbar kyau da zan miki, na zabi na fada miki a yau ne saboda yau din
nan rana ce ta musamman a garemu amman ba zan baki kyautar ba sai nan da wani dan
lokaci kankane, kuma karki tambaye ni minene zaki gani idan lokacin yayi, wannan
kyautar ita ce cikar farincikinki a tare da ni”

Ta yi shiru ya labe a jikinta fitinannen kamshin dake tashi a jikinsa yana ratsa
hancinta ya rikita lissafin kwakwalwarta.

“My Precious Pearl”

Ya furta mata yana kwanto da kansa kusa da saitin kunnensa. Ta kara lafewa a
jikinsa tana jin kamar ta fi ko wace mace sa'arta dacen mijin aure a yanzu.

“Yaya...”
“Uhmmm”

Ya amsa can kasan makoshinsa yana jan numfashi, ruwan turaren da ta yi wanka da su
kamshi na rikita masa lissafi.

“Kar wani ya shigo”

Rumgume ta ya yi yana lilo ya daga kansa sama idonsa suka cika da kwalla. yana
shakar kamshin dake jikinta.

“Ai ni halalinki ne Hurriya, daga ranar da aka daura mana aure aka musanya komai
bawa ya zama halalinki kuma na ki, naki kuma ya zama nawa, yau kin saka ni shiga
wani yanayi da ban taba jin kaina a ciki ba”

Wani shauki na angonci da farinciki yake jin kansa a ciki, tun da aka daura auren
be taba jin nauyin ya hau kansa ba sai a yau. Dagota yayi daga jikinsa ya daga
mayafinta ya sauke shi a bayanta yana kallonta. So now Hurriya dake tsaye a gabansa
matarsa ce.

“My dream Girl, i never knew you're the one waiting for me, Allah ya bar min ke i
see the future in you... My soul my heart my blood line my joy...”

Ya sumbanci goshinsa irin sumbantar da sai da yawun da ya jika goshinsa ya saka


tsigar jikinta tashi, ya sumbanci gefen fuskaerta hagu da dama sannan ya kwantar da
kansa a wuyanta hancinsa ya shakar kamshin dake tashi a gurin, har lumshe ido yake
yana jan numfashi.

“Ranar yau kamar mafarki baka ji haka ba?”

Ya bude idon ya kama fuskarta yana yawo da idonsa, ya sumbancin hancinta.

“Na ji, abun dai kamar wasa ace ni din ango ne, kuma angon ma na Hurriya...”

Ta bude idon tana kallon numfashinsa ke fita, sai ya hade goshinsu yana goga mata
hancinsa a hankali.

“Bana jin akwai wata macen da ta yi dacen, ango a yau kamar ni, ka kawar da duk
wani abu da ka ji, ka runtse ido daga komai ka tsaya ka dage sai ni, ban taba
hasahen wannan ba, farkon da ka fara dukana ina maka kallon azzalumin mutum ne
marar imani da tausayi ashe ban fahimce ka ba, kai zaka canja rayuwata...”

Yayi murmushi mai sauti.

“To ba dole ba, tun haduwarmu ta farko da kika buge kirjina kika guda zuciyata kika
shiga ciki kika zauna abunki, ban san kina ciki ba sai daga baya and i have faith
in what i see, a karo a biyu ma haka kika daki kirjina kika kusa kika shiga da
karfin tsiya kika yaki duk wata mace dake shirin shiga ciki kika zauna”

“I think i meet a angel in person, ka zama hasken rayuwata ba”

Ya saka hannunsa yaja lips dinta da sha man lebe a hankali yana kallonsa cike da
fitina.

“Tukuna dai... Yanzu din ne zan sama hasken rayuwa kuma sanyin idanuwanki Hurriya”

Ya hade bakinsu na wasu dakikun da suka suka kusa hada mintuna daya. Yadda jikinta
yake rawa ya kara tabbatar masa da ita din sabo shiga ce da bata saba da irin
abubuwan nan ba.
Sai da ya ji alamar shigowa mutana sannan ya natsu ya kyaleta, ba tare da ya dauke
ido akanta domin kallonta ne kadai abun da ke kwantar masa da hankali a yanzu,
daren ma ya karaga yayi matarsa ta kasance a gefensa. An yi hotuna kamar za a kure
camera duk wani hoton da aka dauka da Captain idan Hurriya tana ciki zaka tarar
yana satar kallonta ne ko ma yana kallonta gaba daya. A nan ya samu gaisawa da wasu
daga cikin yan'uwan Amma aka gabatar da shi a gurinsu suka ganshi shi ma ya gansu
sai yaba halinsa da hakittarsa suke suna fadar shi da Hurriya sun dace da juna.
A can gidansu ma hotunan aka sha kala kala daman amsu dauka hoton ba daya ba ne,
abinci ma sai kalar wanda kake ra'ayi zaka ci, abu daya ne ya rage armashin bikin
shi ne rawa da ba ayi ba, domin babu kamu babu dinner abun da mutane da yawa suka
saka ran za'ayi amman ba'ayi ba, saboda lalurar dake tare da Hurriya ta ido, idan
aka ce za'ayi zata wahala kuma mutane da yawa za su gane Amaryar makauniya ce.
Da yawa sun zo daga dangin Appa saboda ya sanar musu da kanshi, hakan ya nuna yana
son zuwansu bikin kenan, ciki har da Sapna da wasu daga cikin yayanta, amman daga
bangaren Hajiya Kaltume har Momy babu su babu yayansu haka kuma babu a wani na su
da ya zo. Amma ba ta yi mamaki ba daman ta san ba za su zo yarta ba, balle kuma
abun alheri ya sameta kamar wannan na aurar Hurriya da mutumen da kowa ke yaba
halinsa da na Iyayensa.

Misalin karfe takwas na dare aka jera manyan motoci na alfarma a kofar gidan Bappa
kai kana ganin motocin da manyan matan da suka zo bikon amarya ka san amaryar mai
tsada ce. Bappa ne ya fara yi mata nasiha sannan Gwaggo Hindu ma ta yi mata Amma
kam sai ta kasa cewa komai sai kuka take tana fada Hurriya ji take kamar ƴar zata
tafi ta barta ne tafoya ta har abada, ita kanta Hurriya bata iya rike kanta kuka
take.

“Ki yafe min Amma ki yafe min”

Shi ne abun da take ta fada ta rike Amma da karfi daker aka banbare hannunta, kusan
ta saka mutane da yawa kuka, 3M Nene wato kakar ango ta bada a yi bikon Amaryar sai
kuma akwati daya na manyan laces da atamfa da turare da Ammy ta hada na bikon
Amarya, haka suka aje kayan sannan suka dauki Hurriya. Husna na rike da hannun
kawarta har gaban mota sannan iyeye suka shiga tare da Hurriya Suna ta zauna daga
gaba aka ja motocin sai gidan Appanta. A babban falonsa aka shiga da Hurriya aka
zauna da ita tana sanye da lifaya an rufe kanta da fuskarta.

“Maraba Maraba Maraba”

Shi ne abun da Appa yake ta fada har ya zauna yana kallon inda yarsa take zaune a
natse.

“Ki ji tsoro Allah Hurriya akan dukan lamurranki, ki bi biyaya ga mijinki domin shi
ne abokin rayuwarki a yanzu kuma shi ne jigonki, ki bi shi sau da kafa neman
aljannarki ya tashi daga karkashin kafafuwanmu ya koma gurin mijinki, ki yi koyi da
mahaifiyarki mace ce mai tsananin biyayya agareki kuma mai son abun da nake so,
indai kin bi halin mahaifiyarki mijinki ba zai taba kuka dake ba”

Hurriya ta mike tsaye ta matsa kusa da inda take jin muryar mahaifinta sai wata
daga cikin kanen Appa ta kamata ta zaunar da ita gaban Appanta. Hurriya ta rike
kafafuwansa tana kuka.

“Na gode Appa, da yardar Allah ba zan saka ku ji kunya ba, Appa ka yafe min dan
Allah”

“Na yafe miki Hurriya baki min komai ba, ke yar albarka ce.”

Shigowar Yasir ne ya hana kwalla dake idon Appa zubowa domin ya shigo da zolaya ne.

“Wayo take Appa dan ta samu a yafe mata, ai ba mutuwa zaki yi ba aure ne dan haka
ki daina wani rokon gafara, ko Appa ya yafe idan ban saka baki ba ba ta yi ba”
Duk suka yi dariya har Hurriya da ta daga kai tana jin kamar ace zata iya ganin
yayan nata mai tsananin nuna kauna a agare tun kurciya har girmanta. Yasir ya daga
mayafinta ya dubi fuskarta.

“Kanwata, yau zaki tafi ki barmu ko? Rayuwarki zata koma wani gida tare da wasu
Iyali da ba mu ba, Allah ya baku zama lafiya, kuma zan jaddawa angon nan cewar
kanwata mai zurfin ciki ce ko da tana cikin damuwa bata fada dan haka ya rika kula”

Hurriya ta kwanto jikinsa tana kuka.

“Yayana yayan da ya fi na kowa”

“Ina alfahari da ke kanwata”

Appa da kansa ya bukaci a shiga da ita gurin yan'uwanta ta yi musu bankwana, haka
kuwa aka yi bangaren Hajiya Kaltume aka fara shiga da ita, aka zaunar da ita a
falon, Hajiya Kaltume ta fito ta tsaya daga sama bata sauko ba saboda bakinciki,
daga inda take tsaye ta yi Allah sanya alheri. Khairy kam saukowa ta yi tana kuka
sosai kamar ranta zai fita ta yi rama kamar ba ita ba, da kanta ta zauna a gaban
Hurriya ta kira sunanta da muryar kuka sai Hurriya ta kasa amsawa.

“Ki yafe min dan Allah... Na san na cutar da ke amman ki daure ki duba hakkin jinin
dakw tsakaninmu ki yi hakuri ki yafe min dan Allah...”

Rukayya Allah Allah kawai take kar Hurriya tace ya yafe mata, domin ta san halin
yarta da sanyin hali. Hajiya Kaltume dake tsaye can sama kuma tana jin kamar ta
sauko ta lakadawa Khairy shegen duka akan wannan abun kunyar da ta yi mata. Ruma ma
ta roki yafiyarta tana kuka ta rumgumeta, daga bangaren Hajiya Kaltume aka wuce da
ita bangaren Momy, a falo aka samu Momy tare da Namra suna zaune da Miwan. Hurriya
ta zauna kasa tana neman yafiyarki tana kuka.

“Babu wanda zai ce kin masa wani abu da saninki Hurriya, halinki mai kyau ne, ni na
yafe miki haka Allah ya kaddara haka ya so, Allah ya ba ku zaman lafiya”

Shi ne abun da Momy ta fada tana hawaye, domin a yanzu ta yarda babu sarki sai
Allah babu yadda zata yi da abun da Allah ya kaddara faruwarsa. Daga gidan Appa aka
wuce da ita family house din mijinta ta gaisa da su Nene da Hajiyar Maru, kanen
Mahaifin Captain da kanenen mahaifiyarsa da wasu daga cikin danginsa, babban
akwaiti aka bude mata kowa ya kawo nasa kyautar a zuba wasu tufafi wasu kudi. Da
aka kawo a gurin Ammy sai ta kama hannun Hurriya ta saka mata key mota.

“Barka da zuwa Turaki Family yarinya, ba dan Captain yana ďana ba, amman tabbas kin
yi dacen miji fatan ba zaki ba shi kunya ba”

A take falon ya dauki ihu kowa na murna da mamakin Ammy ta yi ma Hurriya kyautar
mota, a sabuwar motar aka saka Hurriya da masu kaita gidan mijinta suka kama hanya
zuwa gidan Captain. Kusan rabin unguwar Gidan dawa sai da suka san da Amarya a
unguwar saboda manyan motocin da suka rika ratsa titin suna shiga cikin unguwar.
Wani mamaken gidan da za a iya karamin gida hudu a ciki aka shiga da Hurriya, har
gaban babbar kofar falon aka faka motar, kan wani jan carpet da aka shimfida na
musamman domin Amarya Hurriya ta sauko da kafafuwanta tana lullube da fuskarta aka
shiga da ita gidanta mai cike da kamshi ga guďa na tashi ta ko'ina.. Dakin da aka
ware a matsayin na Captain a ciki dakuna biyar da Appa ya cika mata da kayan daki
aka zaunar da ita akan gadon na alfarma, kan lallausan zanen gadon da aka siya mata
gurin Khadeeja Candy. Iyaye suka sake yi mata nasiha sannan suka tafi, aka barta
da Husna sai yan matan Amarya. Ba dauki dagon lokaci ba aka shigo da ango yana
sanye da shaddarsa fara mai matukar kyau. Kana ganinsa ka ga ango baki baya rufuwa
fuska dauke da annuri. Kusa da matarsa kuma uwargidansa ya zauna abokansa na
zolayarsa shi dai be ce komai ba sai murmushi yake. Su ma abokansa da yan'uwa suka
yi ta su nasihar sannan su Husna suka kara da taku suna dariya domin babu mai aure
a cikinsu.

“Ba sai kun fada mana ba, angonta ya ta jadda mana amaryar mai tsada ce, dan haka
ba mu bukatar tayawa zamu bada abun da ba a isa a mayar mana ba... Ko wace mota da
zata yan matan amarya akwai jakar kawayen amarya a cewa kowa jaka tana dauke da
kyauta da kuma kudi na siyen bakin amarya”

Hakan da Cousin din Captain ya fada va karamin faranta ran amarya yayi ba, suka ji
dadi suka daga mazan har matan suka fice suna murna tare da addu'ar alheri ga
ma'auratan. Sai da kowa ya fice sannan Captain ya daga mayafin Amaryarsa ya leka
fuskarta ya kalli hawayen dake zubo mata.

“Mai tsada... Idan ba ni ba wa za a kawo wa Amarya tana kuka har yanzu?”

Ta yi murmushi cikin kukan ta ce.

“Idan ba kai ba, wa zai auri makauniyar amarya?”

Sai ya rumgumeta yana dariya.

“Ni ne idonki ai, na huta baki bukatar kallon kowa daman a yanzu”

Ta sauke ajiyar zuciyata tana lafewa a jikinsa kamar wata kyanwa. Ya kama hannunta
ya rike yana murza yatsun a hankali.

“Na gode Allah da ya nuna min wannan ranar Alhamdulillah, ban yi tsamanin abubuwa
za su zo mana haka da wuri ba, ko da yaushe tsarin Allah mai kyau ne”

Ita dai bata ce komai ba tana kirjinsa sai shakar dadaddan kamshinsa take. Ya dago
ya ssauke lifayar daga kanta zuwa wuyanta ya shafa kanta.

“Maa Shaa Allah, Amarya ta kyakkyawa son kowa kin wanda ya rasa, kin ga yadda kika
yi kyau yau kuwa?”

Ta girgiza kai alamar aa. Sai ya fara fada mata yadda komai yayi kyau a jikinta
yana tana hancinta da bakinta har sai da ta yi dariya.

“Taso mu yi alwala”

“Na yi a gida”

“Shi ne baki fada min ba na yi?”

Ya ja lebenta a hankali sannan ya sake ta ta tashi ta cire babbar rigarsa Falo ya


fara fita ta rufe musu kofar gidan sannan ya dawo ya shiga bandaki yayi alwala ya
fito ya shimfida musu carpet ya daga matarsa yana rike da ita ita ya tsayar sa ita
daga baya shi kuma ya matsa gaba kadan ya tsaya kabbatar sallar. Cikin natsuwa suka
yi sallah Nafisa yayi musu addu'a ya juyo ya kama goshinsa ya karanta addu'a sannan
ya kwanto da ita jikinsa.

“Yan mata na...”

Ta yi shiru tana jin wani bakon al'amari da bata saba ji ba, wani yanayi take ji na
dabam a tare da ita. Hannunsa ya saka aljihun rigarsa ya ciro dabinon da Daddy ya
damka masa ranar da aka daura aurensu ya saka a bakinsa ya tauna dabinon da yawunsa
sai da yayi taushi sannan ya saka hannunsa ya ciro ya kai mata saitin bakinta.
“Dabinon daurin aurenmu ne, ranar da Daddy ya ba ni a raina na ce zan aje sai kin
tare mu ci a tare”

Ta bude bakin da tunin yawunsa da ya tauna dabinon da su suka jika mata lebe, ya
saka mata a baki sannan ya lashe hannunsa, ya sake tauna wani har yayi taushi
sannan ya dago fuskarta ya hade bakinsu suka ci dabino a tare. Kamin ya cire
bakinsa ya kalli fuskarta yatsansa ya saka ya matsa hancinta har sai ta ta fara
masa kukan shagwaba.

“Da zafi”

“Uhmmm wannan kawai tukuna ma”

Ya tsakani idonta yana murmushi, kamin ya tashi ya dauko musu abun tabawa, sai da
ya fara ciyar da ita ta koshi sannan ya ci, daga bisani ya kawar da komai ya dauki
Amaryarsa cak sai kan gado. Wardrobe ya dauko musu kayan bachi, sai da ya saka nasa
sannan ya fara kokarin rabata da lifayar dake jikinta.

“Ke me yake zuciyarki? Hummm me kike tunani?”

Ya rada mata a kunnen kamin ya dago ya kalli fuskarta. Sai ta yi shiru domin bata
da abun fada, tun da ba wani abu yayi mata ko yace mata ba.

“Kayan bachi zan saka miki”

Ta kanne kafada.

“Aa da wannan zan kwanta”

“Hey don't try to act smart here”

Ta fara rare masa kuka a hankali, sai yayi murmushi yaje kayan bachin ya zauna kusa
da ita ya rumgumeta. A dole ya hakura ya kyaleta ta yi bachi da lifayar har safe.

HAJIYA KALTUME POV.

“Kin ba ni kunya Khairy ban yi zaton zaki iya haka a gaban mutane ba, idan ma neman
yafiyarta zaki yi ai sai ki yi daga ke sai ita a cikin mutane ba, yanzu ai ta ji
dadi ita da Iyami sai su ce gashi nan kina kuka kina neman yafiyarta”

“Hajiya wanda aka yada video shi a duniya kamar ni da yana da sauran jin kunya ne?
Ni fa yanzu rayuwata ta kare, da ina tunanin auren Fadeel zai rufe abubuwa da yawa
akaina kuma ya saka ni jin sanyi amman haka ya gagara, shi ma ya juya min baya”

Ruma ta kalli Hajiya cike da damuwa ta ce.

“Hakan da ta yi ba laifi ba ne Hajiya, idan ba irin yau ba yaushe zata roki


yafiyarta?”

Hajiya Kaltume ta ja tsaki, bakinciki ya zame mata kashi kashi. Khairy ta mike
tsaye tana kuka ta haura sama ta shiga dakinta sai ta kife akan gado ta fashe da
kuka.

“Ka cutar da ni Adam.. Ka gama da rayuwata ka ruguza shiri ka tarwatsa duniyata


wayyo Allah na...”

Kuka take sosai tana jin kamar ace adam din yana kusa da ita ta kashe shi ko ta
rage zafi, can kuma ta dago ta nufi wayarta ta dauka ta kama number Adam ta aika
masa da sako.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro
kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku
da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

*Shafin nan sadaukarwa ce gareki UMMU FAISAK my albasa my tomato my pepper, jikar
Iya kawar Amo da Hajiya Kaltume. Alherin Allah ya kai miki har a gadon baccinki*

*** *** ***

_Wallahi baka taba yin farinciki a rayuwarka ba Adam kamar yadda ni ma ba zan yi
ba, ba zaka taba ganin haske ba, sai na bayyanama duniya abun da kake boyewa sai na
hana ko wace mace aurenka, baka da zabin rayuwa daga yanzu har zuwa mutuwarka, idan
ban auru ba ba zaka auru ba Adam..._

Yana gama karanta sakon ya dan dago ya kalli mutanen dake falon sannan ya maida
kansa yayi mata reply.

_Mu zuba zuwa Khairy, ni da za a ga shege, kuma ni sai na auri macen da nake so
nake ra'ayi amman ke ba zaki taba auren mijin da kike so ba, saboda kowa ya san me
na yi miki kuma idan kika matsa asirin ba nawa kadai zai bayyana ba har da naki
domin ke ma yanzu ya shafe ki kin ga sai mu yi jinya tare_

Yana bata amsa ya aje wayar ya cigaba da kallon tv rai a bace, Salim ya taso daga
inda yake zaune ya nufo Adam.

“Ara min wayarka zan sauke app wayata ya ki sauke shi”

Without second though Adam ya mikawa Salim wayar ya tashi ya hanyar dakinsa. Salim
ya zauna a gurin da Adam ya tashi yana.

“Akwai pin a jiki”

Adam ya dawo ya cire masa pin sin sannan ya shige dakinsa. Kai tsaye a Salim ya
shiga whatsapp dinsa yana duba recent chat ne ga wani abun daga hankali ko bata rai
ba, yana kokarin fitowa daga whatsapp din sakon Khairy ya sake shigo ta SMS.

“Mu zuba zuwa ni da kai shege ka fasa Adam”

Ya haka ya samu bin sakon ya karanta har wadda ta aiko masa da farko. Salim ya dan
dago da mamaki kamin ya sake maida kansa, wannan ne karo na biyu da ya sake ganin
wani abu da ya daga masa hankali a wayar Adam. Da kansa ya shiga dakinsa ya mika
masa wayarsa sannan ya fito harabar gidan zuciyarsa na zafi. Domin ganin yakw yanzu
ya zama loser shi ya fara son Hurriya amman abokinsa yayi masa overtaking duk kuwa
da irin yadda aka bata sunan Hurriya, it pain him yadda abokinsa yayi betrayed
dinsa. Number Namra ya kira domin sauke mata haushin dake ransa.

Namra ta share hawayenta sannan ta kalli wayar dake gefenta ta dauka.

“Hello”

“Burinku ya cika? Kun nani Hurriya kun bawa wani?”

“Wane irin magana ne wannan? Wa yake murna da wannan auren ne? Kai kanka ka san
Hurriya bata dace da Captain”

“Bata dace da shi ba ta aure shi? Na yi zaton ma kina can gurin raka amarya ai”

“Zan aje wayar idan baka da wata magana mai muhimmanci, ina cikin damuwa ba zan
yarda ka kara min wata ba”

“Baki da matsala daman saboda ba ke kika rasa ba”

“Idan har da gaske kake kana kaunarta me ya hana ka fitowa ka aureta kamar yadda
Captain yayi?”

“Captain ne silar lalata komai, a duk lokacin da na yi masa maganar Hurriya ture
min maganar yake, saboda yana min kallon wani dan iska, daga baya na fahimci sonta
yake shiyasa kansa yake yi ma campaign”

“To kai miyasa baka kirkiri taka Jam'iyar ka yi takara da shi ba? Da ka yi hakan da
auren nan yanzu be faru ba”

“Ban yi tunanin zai yi jihadin aurenta a haka ba, na dauka zai hakura da ita ni da
shi duk mu rasa...kuma na yi tunanin da gaske din ta aikata sai bayan da gaskiya ta
bayyana abun ya zo min a wani iri”

“Ya fika kaunarta shiyasa ta tari yakin gaba da gaba, gashi kuma daga karshe
gaskiya ta bayyana cewar bata aikata ba, ka ga ya ci riba, kark sake kirana Salim”

“Ni zaki ce kar na sake kiranki?”

“Ubana ne kai? Alakar dake tsakanina da kai saboda Hurriya ne, yanzu kuma ta yi
aure dan haka babu sauran wata alaka tsakaninmu, gaskiya Captain ya fada kana wasa
da zuciyar mata shiyasa ko wace macen ka gani sai na nuna kana sonta, da farko ni
daga baya kuma ya koma gurin Hurriya, ai kara da ya hana ka aurenta hakan zai koya
maka darasi”

“Ko kuma ya koya masa darasi ba, idan har aboki zai iya cin amanar abokinsa na
kurciya ya karbe masa yarinyar da yake sannan ya datse alakarsu har ya nuna shi da
bindiga kuma yayi masa barazanar rasa aikinsa me kike tunani? Dole shi ma hakki zai
bibiye shi”

Namr taja tsaki ta yanke kiran. Daga ita har Salim Momy Hajiya Kaltume da kuma
Khairy kwanan bakinciki suka yi a ranar duk saboda bikin Hurriya.

WASHE GARI...

Misalin karfe goma na safe Hurriya na kwace jikin mijinta yana gyara mata baki
bayan sun gama cin abinci da breakfast da aka aiko musu daga Family house din su
Captain.

“Tashi mu zagaya na fada miki yadda gidanki da dakinki yake”

Ta dan dago kamar bata son motsi, cikin siffar shagwaba da son kuka ta ce.

“Ni dai da ka bar shi, ba amfani tun da ba gani zan yi ba”

“Zaki taba ai, kuma idan ya bude zaki gani”

“Wannan idon abu ne mai wahala ya bude, Appa ya kashe kudi mai yawa akan ido,
kullum kara rufewa yake ba budewa ba, yanzu kuma ya rufe gaba daya”

Ya dora gemunsa a saman kanta yana taba fuskarta.

“Zai bude Hurriya zai bude da yardar Allah... Ina ta shirye shirye akwai abun da
nake jira ina son nan da dan lokaci zamu tafi Ethiopia akwai wani asibiti ido mai
kyau zan saka a dubaki a can zasu Miki aiki kuma ina da yakinin Allah ba zai
kunyata mu idonki zai bude”

Ta yi shiru tana sauraren yadda yake gangarawa da hannunsa zuwa gurin da bata
tsammani.

“Idan kuma idon be budewa gaba daya fa?”

“Zai bude, ki daina fadar hakan ki yarda zai bude”

Ta zabura ta tashi zaune daidai da sauri ta ture hannunsa. Sai yayi murmushi ya
cige baki ya kashe mata ido kamar tana kallonsa.

“Iya daga kafar na yau ne kawai, you better get ready for tonight...”

Ya rada mata a kunne sannan ya mikar da ita tsaye tana bata fuska kamar zata yi
kuka, gaba daya sai ta ji tausayin kanta ya kamata.

“Kin tuna ranar da kike fada min na yarda dake na ce miki na yarda baki aikata ba,
amman ban tabbatar ba, to anjima zan tabbatar”

Ji ta yi kamar kasa ta bude ta shige ciki tsabar kunya a yanzu ta fahimci inda
zancensa ya dora tun a karon farko da yace mata zai tabbatar. Dariya yayi ya
rumgume ta ta baya tana takawa a hankali har suka fita dakin. Kitchen suka fara
yana fada mata abubuwan dake ciki wadanda aka siya gurin Khadeeja Candy, sannan
suka fito suka shiga dayan dakin nan ma ya fada mata abun da ke ciki idan ya fada
mata sai ya kai hannunta ta taba ta ji yadda yake da haka har suka fito harabar
gidan nan ma ya rika fada mata yadda tsarinsa yake.

“Amman wata zata zauna da ni ko? Idan ka fita”

“Saboda me?”

“Zan ji tsoro ni kadai ai, kuma ban zan iya komai ba ai”

“Baki bukatar yin komai for now, kuma idan zan fita zan tafi dake gida gurin Ammy
ki zauna idan zan dawo sai na dauko ki kamin su bar garin nan”

“Wani garin za su koma”

“Kaduna suke zama, ni ma ai da zarar lokacin da aka ba ni a nan ya kare can zan
koma a zamu zauna, amman kamin mu zauna can sai mun fara tafiya ayi miki aikin
idonki tukuna...”

“Da ace idon zai bude, kai nake son na fara gani Captain...”

Ya kwantar da kansa a kafadarta.

“Ba zan ce Aa ba, amman maybe zan zama mutum na biyu da zaki fara gani saboda iyaye
suna raye”

Ta juyo ta saka hannayenta ta lalaba inda saitin fuskarsa yake ta rike fuskar.

“Kana karfafa min guiwa, kai kake fara yarda da ni kamin kowa, na jihadin lokacin
da ka yarda ban aikata ba, kuma idan a rufe ido da kunnenka daga jin duk wani abun
da za a fada a kaina, har ranar yau ta kasance, duk wata macen mai dacen aure a
bayana take a yau...”

Ta yi dage ya duka mata da fuskarsa ta sumbanci shi a gurin hancinsa.

“We deserve each other shiyasa Allah ya hada mu a tare kuma ya tare duk wani abu da
zai shiga zuciyata ya bata zamanmu har yau ta kasance”

Hawaye ya sauko mata.

“Ina kaunarka Yaya”

“Yayanki yana gida wannan mijinki ne, My Baby Pearl...”

Ya kwantar da ita a kirjinsa yana shafa bayanta. Cikin gidan suka dawo duk yadda ta
so ta ki be barta ba sai da ya taimaka mata ta yi wanka, sannan shi ma yayi suka
fito ita da shi suna daure da tawul daya, ita tana ta gabansa shi kuma yayi mata
rumfa a baya, har gaban madubin dakin suka tsaya ya cire tawul din sai ta yi saurin
juyawa ta rike shi dariya ya sa domin shi ma babu tufafin a jikinsa.

“Idan ba ni ba wa za a kawo w tsaleliyar budurwa kamar wannan kuma ya kyaleta”

Ta saka mishi haka, hakan ya saka shi dauko mata tufafinta ya taimaka ta saka
sannan ya shafe mata jikinta da mai kyau ya saka nasa tufafin ya dauki hoda da
kansa ya shafa mata ya saka mata man lebe ya saka mata turare sannan wasan ya canja
salo. Be kyaleta ba sai da ya ga lokaci na tafiya tukuna ya shiga ya sake tsabtace
kansa ya fito ya sumbance ta.

“Zan tafi na gaishe da su Ammy na san yanzu wasu za su fara zuwa ganin amarya kar
ayi gulma da ni”

“Ni kadai zaka bari?”

Ya saka bakinsa cikin nata ya sake sumbanta tukuna ya sake ta.

“Mutane za su shigo yanzu ai”

Ya amsa ta sannan ya nufi wayarsa dake kara ya dauka ya duba mai kiran.

“Nafi'u...”

Ya furta sannan ya amsa kiran.

“Hello oga barka da safiya ya aikin”


“Sorry na kira ban sani ba ko kana cikin wani aiki”

“Go ahead”

“Hotunan nan ne aka sake yadawa tsakanin jiya da dare zuwa yau, kuma mun bibiye
account din sai kuma samu an goge na alhani amman mun samu information din dayan da
ya saka hotunan umarni kawai muke jira mu kama shi a Bincike ina ya samu hotunan”

“Irin wannan ma baku bukatar umarni na Nafi'u just do it ina yaron yake...”

“Kaduna... Ka yi duk yadda za'ayi ku kama shi please kuma ku bincike shi da kyau”

“Okay Sir”

Ya sauke wayar cike da mamakin mai kokarin hana su jindadin rayuwa a yanzu.

“Me ya faru?”

Ta tambaya domin jin yadda yake amsa wayar da kuma yadda yayi shiru bayan amsa
wayar ya tabbatar mata da ba kalau. Kallonta yayi sai yayi murmushi ya nufo inda
take ya saka zauna.

“Babu komai Babyna wani abun ne da ya shafi aikina”

“Ka tabbata?”

“In Shaa Allah”

Ya sumbanci gefen fuskarta yana kallonta wani irin sonta da son kwanciyar
hankalinta ke fisgarsa. Be bar gidan ba sai da mutane suka fara zuwa daga
yan'uwansa da na Appa da na Amma musamman wadanda ba garin suke ba.

CAPTAIN POV.

Ammy ta aje tea cup din dake hannunta tana kallon danta.

“To waye kuma da wannan aiki?”

“Za mu gane, kuma ko waye sai ya dandana kudarsa”

“Ko yar'uwarta ce?”

“Bana tunanin haka, saboda asirinta ya tonu, kuma bana jin Adam ne domin ya fada
cewar ba shi ba ne ko a yanzu!”

“Ko ma dai waye ya kamata a hukunta shi a yanzu, domin ya wuce gona da iri kuma ba
kai kadai ne da fadan ba har da na mu domin idan hotunan suka sake yaduwa har da mu
za a taba”

“Mutum daya nake zargi.”

“Waye”

“Bana son fada, amman gaskiya zata yi halinta, and if i find out shi din ne, zan
masa ba dadi”

“Zan yi magana da aka daddynka san fada masa a zafafa bincike ta bangarensa ma ko
zamu samu wani abu, and ka kula da gidanka domin wanda zai iya yi ma Iyalinka haka
zai iya neman rayuwarka ko ta matarka ko ma ya sake yin wani abun da zai zubar da
kimarka, gashi yarinyar ba gani take ba be ma kamata a barta ita kadai a gidan ba”

“Na barta ne just for today and tomorrow saboda masu zuwa, amman bayan nan idan zan
fita nan zan kawo ta sai idan na dawo sai na dauke ta mu wuce”

“A madadin haka ka rika kaita a gidansu mana ko kuma ka dauki mai kula da ita tun
da ka ji ka gani zaka iya”

Ya dan yi murmushi.

“Nan din ma gidansu ne ai saboda gidanmu ne, Ammy kina son yarinyar nan fa ki daina
boyewa”

“Au boyewa nake ma?”

“Idan ba shi ba, miye na danka mata key mota? Duk soyayya ta dake fa baki taba siye
min mota ba, amman ita gashi kin siya mata sabuwa, sannan kika bada kayan bikonta”

“To ya zan yi? Na yi abun da ya kamata uwa ta yi ne, ba ni da wani zabin ne”

Yayi dariya sosai yana kallon mahaifiyarsa cike da farinciki.

“Ni dai tarewar ne a haka be min dadi ba, da dai ka hakura har idon ya bude da abun
ya fi armashi gaskiya”

“A yanzu din ma babu abun da ya ragu Ammy, ina farinciki da matata kuma ba wai bana
son duba idonta din ne a yanzu ba, akwai planning din da nake, ina son nan da two
years....”

“What...! Baka da hankali ashe..!”

Ya dan bata fuska.

“Ammy ni?”

“Taya zaka auro yar mutane ka ajeta har nan da two yrs sannan a duba idonta? Wane
irin plan ne wannan? Hummm uhmm you better not, karka kuskura gwada wannan,
iyayenta ba za su yarda ba ai”

“Karkashin ikona take yanzu”

“Haka ake aure a garinku? Dan tana karkashin ikonka iyayenta ba za su yi mata abun
da ya dace ba, gaskiya be kyauta ka ajeta a haka har two yrs ba ai sai ta wahala
kara dai a gwada idan ma ba a dace ba ansa ba a dace ba ne amman ba wai haka nan
kawai ba”

Yayi murmushi ya taso daga inda yake zaune ya zauna kusa da uwarsa.

“Kin gani ko Ammy kina son yarinyar nan Wallahi gashi kin damu da ita...”

“Ni shawara ce kawai nake baka, idan ta ni ne ka barta har sai nan da shekara goma
ma babu abun da ya dame ni”

Side hug yayi mata yana dariya.

“Ammyna i love you so much...”

Ta yi murmushi kadan tana tabe baki.


“Ka ji da shi, ku yaran zamani sai dai abi yadda kuke so ba yadda iyaye suke so ba”

Ya sake yin dariya ya mike tsaye ya fice daga dakin, haka ya fito harabar gidan ya
gaisa da mutane cousin dinsa mata suna ta tsokanarsa. Sai da ya shiga motarsa
sannan ya kira Nafi'u ya aika masa da wata number.

“So nake ka yi min hacking din account din da yake jikin number nan, ka duba duk
wani abu da ke cikin chat din maybe zamu samu wani abu da muke nema, ka yi duk
yadda zak iya ka duba komai na account din”

“Okay ranka ya dade”

**** **** ****

A WEEK da bikin auren Hurriya Amma da Gwaggo suka tafi Ummara tafiyarsu da kwana
biyu Momy ta tafi tare da babbar ƴar Appa wato Sapna Momy kuma ta biyawa yarta
Namra suka tafi tare duk kuwa da kasancewar ta taba zuwa ba sau daya ko biyu ba.
Hakan kuma ba karamin taba ran Hajiya Kaltume yayi ba, a nan ta fara shige shigenta
ko zata samu kamin Momy da Amma su dawo Appa ya daura aure da ita kuma ya juyawa
Momy da Amma baya, amman yi take kamar tana shuka dusa, ga ciwon kafa ya sakata
gaba amman ta kasa tsayawa ta maida hankali gurin neman lafiyarta kokarinta na
yadda zata koma karkashin inuwar mijinta ne a yanzu. Bata da wani buri da ya wuce
wannan kuma duk inda zata saka kafa ta gabatar da bukatarta za su karbi kudinta su
ce za a mata aiki mai kyau kuma Appa zai juyo ya nemata haka ma aurensa da Amma ba
za a maida ba. Babu abun da ke daga mata hankali a ciwon kafarta nan kamar yadda
idan an bincika ake ce mata babu wani rauni ko wani ciwo a gurin amman kuma ita
tana jin azabar ciwon da ko tafiya bata iya yi daidai yanzu. Tana shan wahala sosai
gurin hawa da saukowa a stairs har bata son yin ko daya sai idan ya zame mata dole.
Yau ma kamar kullum ta sauko tana ta wai wai wai da kafar har ta zauna. Yasir yayi
saurin yanke wayar da yake ganin Hajiya ya aje wayar gefe ya maida hankalinsa gurin
tv.

“Me kake ayi nan? Yau baka da aiki ne?”

“Ina da aiki sosai ma Hajiya, gyaran gidan da Appa yace za'ayi ne mutanen nake jira
su iso”

Wani kallo Hajiya Kaltume ta yi masa na rashin zato balle tsammani.

“Gyaran gida za'ayi? Ba mu da labari”

“Ni ma ban sani ba, kawai ya kira ni yace min na jira kar na fita da wuri so that
idan sun zo na nuna musu lungu da sako na gidan”

“Ikon Allah to gyaran gida na minene? Na ga dai ko auren Hurriya ba'ayi gyaran
gidan nan ba, baka fada min shi yasa aka gyara gidansu Iyami ba? Amman ba a gyara
nan ba, to yanzu kuma gyara me za'ayi”

“Wallahi ban sani ba Hajiya, kin san ba komai ne Appa yake shawara da ni ko ya
sanar min ba, amman dai ko minene ai zamu ji”

Hajiya Kaltume ta sauke wani dogon numfashi tana jin wani sabo na tukare mata a
kahon zuciya.

“Ya kafar taki?”

“Da sauki”

Ta amsa irin amsawar dake nuna hankalinta baya gurinsa.


“Da dai kin daure kin fita a duba kafar nan kar abu ya zame miki babba fa, Appa ma
na ji yana zancen yana son fita a duba lafiyarsa shi da yake lafiya ma kenan balle
ke da ciwon kafa ya matsawa ya kamata a bincika ko minene”

“Zan yi Yasir akwai abun da yake gabana yanzu, ina son na gama da shi ne tukuna”

“Minene Hajiya?”

“Be shafe ka ba”

Ta mike tsaye cikin jan kafa da dingishi ta sake haurawa sama ta shiga dakinta
zuciyarta har rawa take kamar zata fado. Ta zauna bakin gadonta ta rasa me zata yi
kuka ba mafita ba ne, to miye mafita, yanzu tana ji tana gani Amma zata dawo gidan
nan? Ko kuma dai sabon aure Appa zai daura.

“Na shiga uku na lalace..”

Ta fashe da kuka. Ta lalabo wayarta ta kira Number sabuwar kawarta Hajiya Larai
dake ke karata gurin masu magani a yanzu.

“Subhanallahi Hajiya kamar fa kuka kike yi..”

“Ba dole na yi kuka ba, ciwo ya dame ni ga kuma auren nan Alhaji jin sa zai yi ko
kuma ya maida iyami abun duniya ya isheni Hajiya Larai, kullum sai ramewa nake ga
ciwo ga bakinciki”

“Komai zai warware Hajiya Kaltume karki damu kanki, kin ga duka malaman nan da na
kaiki gurinsu sun iya aiki babu wasa babu kama hannun yaro kuma tun da aka yi musu
biya mai kyau ki saka ido zaki ga yadda komai zai tafi daidai”

“To ai abun ne kullum shiru Hajiya Larai abu sai kara gaba yake, yanzu fa har
Alhaji ya saka ayi masa gyaran gida, ni dai ina tunanin ko zan bo ta bangaren
Hajiya Binta ne idan na je yi mata barka da dawo na bata hakuri ko abubuwa za su
daidaita, wani abun fa dole sai ana saka baki”

“Karki kuskura zubar da kimarki Hajiya Kaltume da yardar Allah sai Alhaji ya zo
yana kuka yana neman yafiyarki”

“Toh Allah yasa, da wacan Malamin ne da ya rasu da yanzu aiki ya fara amman su babu
wani motsi har yanzu”

“Gaggawa aikin shaidan ne ki saka hakuri sa sannu zaki ga aiki yayi, kuma yanzu ma
idan mun gama wayar nan zan sake shiryawa na tafi gurin Malam na gangare na sake
masa bayani”

“To sai na ji ki Allah ya taimake mu”

“Amin”

Ta kashe wayar tana sauke ajiyar zuciya.

*** **** *****


Ya shafa fuskarta sannan ya tsika ci abarba ya kai mata a baki, daker ta dago daga
kirjinsa ta bude baki ya saka mata.
“Tauna mana haba Baby, an fada min gida ma fa haka kike yi ba ki wani cin abinci,
shiyasa ko kibar amarci da kowa yake yi ke baki yi ba, sai dai ni na yi”

“Daman ni bana wani cin abinci”

“Ai mantawa na yi na ce Amma ta roka mana ki rika cin abinci tun da Hajiya ta dawo
balle na ce da ita”

Hurriya ta yi dariyarta mai kayatarwa.

“Har da cin abinci sai an roka”

Ya sumbance ta.

“Eh mana, yanzu ma ba mu yi latti ba, cikin week din nan za su dawo kamin su dawo
zan fada musu su roka miki cin abinci”

“Daman na sha addu'a a gurin Kakata Hajiya Binta tun tana Saudi gurin Ummara har ta
dawo addu'a take min, su Amma ma da suke can addu'ar suke ta mana Allah ya tsaremu
ya bani lafiyar ido ya sa a yi aikin cikin nasara da sa'a.”

“Amin ka ji yar gata, ta ko'ina roka miki ake”

Ta dago kamar tana ganinsa.

“Allah yasa kamin mu tafi aikin nan su dawo”

Ya kai mata kiss a goshi.

“Da wahala gaskiya, mu da zamu tafi jibi su kuma sao karshen satin nan za su dawo
ai”

Ta bata fuska.

“Ko ka daga har wani satin please”

Ya kwaikwayeta yana jan hancinta har ta turo baki gaba yadda ta yi.

“Ko ka daga har wani satin please”

Ta daga hannu zata dokeshi sai ya rike hannu ya matse har sai da ta yi kara sannan
ya sake ta yana dariya.

“Ke ba ganin kike ba sai fitina, ka ji min mata haka kika fitini zuciyata kina
dukan kirjina har sai da kika shige ciki...”

“Ba wani nan kai ne daga ganin yar yarinya kyakkyawa ka cusa kai har da wani ba ni
chocolate da gilashi kana saka ni cin abinci dole a office dinka”

Ya zaro ido yana dariya.

“Ta nan kika bullo kuma”

Ta nauyi cikinsa.

“Yanzu duk sai na rama abun da ka yi min har da marina da kai yi”

Ta lalaba fuskarsa ta kai ma kumatunsa cizo har sai da yayi ihu ya rumgumeta yana
dariya yana mata chakulkuli.
“Na daina... Na daina...”

Ta yi dariya sosai har da su dari.

“Ki biyani chocolate din da kika ci nawa, daman na rubuta duk abun da kashe miki ai
ba dan Allah na yi ba”

“Ka fadi ko nawa ne, idan Saurayi Captain ya zo zai biyaka, amman fa soja ne kana
yin wasa zai harbeka yana da fushi sosai”

Yayi dariya ya cigaba da tsakalar cikinta tana ihu da dariya a lokaci daya.

Two days later... Jirginsu ya tashi daga Abuja tafiyar awa hudu da mintuna 40 suka
yi sannan suka sauka Addis Ababa babban birnin Ethiopia. A Oasis hotel apartment
/Haya Hulet suka sauka Hotel ce mai kyau da aka wadata a abubuwan more rayuwa. Mama
Rukayya da ta kasance yar rakiya daga bangaren Hurriya sa kuma Momy Ikilima daga
bangaren Captain suka sauka a daki daya, Captain da matarsa kuma suka sauka a daki
daya, sai wanda suka zo da shi domin hidima shi ma aka ba shi nasa dakin dabam.
Kwana biyu a hotel din Hurriya na tafiya kwararrin likitocin da suke Bethel
Hospital, addis Ababa, Landmark General Hospital, Medical center hayat hospital
MCM suna duba idon, daga karshe dai aka yanke shawara yi mata aiki a Medical Center
Hayat Hospital MCM, saboda kwarewar aikinsu da kuma kyakkyawar alakar dake
tsakaminsu da wani na kusa da Hurriya.

Ana gobe za ayi mata aikin ta tsora sosai duk kuwa da irin karfafa guiwa da
tabbacin da likitocin suka bata cewar za'ayi nasara. Har yanzu zuciyarta bata yarsa
100% idonta zai bude ta samu lafiya kamar kowa ba, ganin tun haihuwa take da ciwo
har zuwa yanzu d ta girma.

“Baki yarda da ni ba? Baki yarda za'ayi nasara ba? Baki yarda Allah zai iya warkar
dake ba? Baki yarda Allah ya karbi addu'ar da ake ta yi miki ba?”

Ta kwantar da kanta a kirjinsa.

“Na yarda, kawai ina tunanin idan ba ba ayi nasara ba, zan tabbata a haka ne har
abada”

“Za'ayi nasara da yardar Allah”

Ya kwantar da ita kan gadon ya fara kissing din wuyanta, tana ta kokarin hana shi
amman be saurara mata ba sai da ya raya daren kamar darensu na farko har tana masa
kuka a yanzu din ma. Da asuba shi ya taimaka mata ta yi wanka suka yi sallah, ta
hau gado da niyar bachi kamin lokacin zuwa asibitinsu yayi, a nan ma be bar Hurriya
ta huta ba, sai da ya sake gajiyar da ita har tana masa miya. Misalin karfe daya na
rana suka isa asibitin aka wuce da ita dakin da aka ware mata na musamman sannan
aka fara yi mata wasu treatment din. Ba a shiga aikin da ita ba sai karfe bakwai na
yamma. And the most expensive news is anyi aikin cikin nasara sai dai babu tabbacin
ko zata gani daidai ko kuma irin na da ne ko ma idon be bude gaba daya ba sai idan
ta bude idon, hakan kuma ba zai samu ba sai nan da sati idan idonta ya warke. Daga
ranar da aka yi aikin suka saka mata dokokin na abun da zata ci ko ta sha da irin
motsi ko aikin da zata yi. Sun bada damar mayar da ita gida ayi jinyarta kamin
ranar da za a bude idon, sai dai Captain ya zabi ta zauna asibitin saboda ta fi
samun kula kuma ya san a gida ko a Hotel din da suka sauka zata iya karya dokarsu.

A asibitin Hurriya ta yi jinyar idonta for one week, ranar da za a bude idon ba ita
kadai ba har Captain da Rukayya da Iyayensu dake gida da fargaba suka wuni na
tsoron rashin nasarar aikin. A hankali aka fara warware daurin dake idonta har aka
cire, ita kanta ta ji alamar nasara a tare da aikin domin tana iya jin haske a
idonta dake rufe tun kamin ta bude.

“Hurriya can you open your eyes please....”

Ta fara motsa ido da take jin kamar ya like mata. Wani likitan an ganin haka ya
dauko wani magani ya diga mata a idon dake rufe.

“Open it slowly...”

Ta bude idon a hankali, sai dai bata iya daga shi sosai yayi mata kamar na masu
shan kwaya (Irin na Ummu Falsak) sai dai tana iya ganin abun da yake gabanta da
dishe dishe hakan kuma ya faranta ranta.

“Don't let tears drop”

Ta yi kokarin hade kukanta bayan dayan likitan ya bukaci haka. Sai ta sake maida
idon ta rufe sannan ta bude a hankali. Fuskar Captain ta fara cin karo da ita kamin
ta bi sauran Likitocin hudu da suke dakin da kallo dukansu farar fata ne kamar kasa
mijinta babu daya da ta sani.

“Alhamdulillah”

Captain ya fada yana durkusawa kasa yana kallonta tsabar farinciki.

“Congratulations”

Cewar Likitocin suna tabawa kansu kowa ne na gaisawa da dan'uwansa. Captain ya dago
ya rumgume ta yana farinciki.

“Ina gani yanzu ina gani ina gani Alhamdulillah”

“Daman na fada miki za'ayi nasara gashi kuma anyi”

Hawaye ya sauko mata tason ta share tana tsoron saka hannu a gurin, blink din sa
take da idonta ma ganin take kamar idan idon ya rufe ba zai bude ba. Captain ya
sumbance ta a gaban Likitocin sannan ya sake ta ya juyo.

“Dukansu sun yi kokari gurin aikin nan Baby Aisha Alhamdulillah, wannan shi ne Dr
Camil, sai a Dr Nille....”

Haka ya bi yana gabatar mata da Likitocin da suka yi nasarar yi mata aikin Maza uku
mace daya tana musu godiya.

“Bayan su akwai wani matashin yaro mai karatun Optometrist.. Wato likitan ido who
will perform medical and surgical treatment for eye condition, shi ma ya kamata a
gode masa, domin tare da shi aka yi aikin a kokarinsa da yake na koyon aikin kuma
duk saboda ke ne, ina da yakini Allah ba zai kunyata shi ba shiyasa na yarda 100%
idonki zai bude Babyna kuma saboda shi Muka zabi yin aikin a wannan asibitin da
yake karatu gashi kuma an yi nasara Alhamdulillah”

Hurriya ta kalli Captain tana murmushi kamin ta maida dubanta gurin kofar da Dr
Nyala ta bude. Wani matashin yaro ne ya shigo sanye da lab coat fuskarsa da idonsa
sun yi ja sosai kana ganinsa ka san ba karamin kuka ya sha ba, domin har a yanzu ma
hawaye zuba suke a idonsa. A take murmushin dake fuskar Hurriya ya gushe ta kalli
Captain da sauri ta sake duba yaron dake tsaye gabanta sai jikinta ya fara rawa
kamar zata kamkame guri daya ta rufe ido da sauri tana shisshika da karfi....
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo
sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka
kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar
aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin
jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da
yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun
mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin
ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki.
Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro
kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku
da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan
gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326.
Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da
maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku
tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

Captain yayi saurin rike matarsa da sauri yana leka fuskarta.

“Hurriya...”

Ta kama rigarshi da karfi ta rike har lokacin idonta a rufe yake jikinta kuma rawa
yake. Ta kasa yarda ba mafarki take ba, kamar yadda take jin kamar tsananin son
rayuwa da ďan uwanta yana neman haukata a yanzu da yake mata gizo, to amman kuma
kalaman da Captain ya furta fa? Wani hannun ta ji a jikinki wanda ya banbanta da na
mijinta, dumin hannun ya fahimtarta da alakar jininta da jinin mai taba ta, shi ma
dai sunanta yake kira kamar yadda Mijinta ma yake kiranta, wata kila ta yi dagon
zango ne ko kuma kokarin farkawa take da daddadan mafarki. Hakan ya kara mata
kuzarin bude idonsa sai ta sake arba da wani mai irin fuskar dan'uwanta mai irin
hanci da idonta mai hasken fata kamar nata, sai dai ya girmi Hamad fuskarsa ya
sauya sosai. Hannayenta sake rawa ta dago zata murza idonta Captain yayi karaf ya
rike

“Karki murza ido”

“Gizo suke min”

Ta amsa a cikin wani sauti mai kokarin gauraya da kukanta.

“Ba gizo ba ne, da gaske ne wannan ma...”

Ta sake bude idon a karo na uku ta kalli matashin yaron dake a yanzu yake dukushe
gaban gadon da take zaune yana kuka har lokacin hannunsa ya kan hannunta ya rike ta
gam. Ta kalli Captain hawaye na sauko mata.

“To waye wannan?”

Captain be ce komai ba sai da yayi magana da Doctors din suka fada masa dokokin
abubuwan da zata kiyaye da kuma abun da da zata ci sannan yayi musu godiya suka
fita.

“Hurriya...”

“Na'am”

Ta amsa da sauri domin amsarsa kawai take jira.


“Ba kin ke kika fada mim dan'uwanki yana raye ba? Shim ba ke kika kasa yarda cewar
Hamad ya tafi ya barku ba? Kowa ya karbi mutuwar Hamad amman ban da ke haka ne?”

Ta daga kai tana kuka ta kalli Hamad din da shi ma kuka yake sosai.

“Saboda jikinki yana baki dan'uwanki wadda ya fi kowa kusanci da ke yana raye,
jikinki be fada miki karya ba tabbas Hamad yana raye, kuma shi ne a gabanki yanzu”

“Taya wannan karyar zata zama gaskiya? Ji yanayin yau nake kamar ba ni ba, tsoro
nake kar na farka daga wannan bachi na ga komai ba gaske ba”

Hamad ya kalli Captain cikin wani yanayi marar misaltuwa da wata murya ta samari
masu tashen balaga ya ce.

“Me yasa ka yi min karya? Why? Ka ce min kowa ya mutu bana da kowa a yanzu why? Ko
kuma kowa ya mutu Hurriya ce kadai a raye?”

Cikin tashin hankali da ba a sakawa rana Hurriya ta dubi dan'uwanta muryarsa ta


sauya kamar yadda siffarsa ma ta sauya, ko a can baya daman wasu shi suke dauka
yayanta ita kanwa saboda girman jikinsa.

“Dan Allah ya zan yarda Hamad ne...? Ya zan yarda? Ki kira Amma.. Kira min Mama
Rukayya... Dan Allah”

Ta rike Captain da karfi kamar zai tsere mata, taya idanuwanta za su bude a yau
kuma ta yi arba da wani mai kama da Hamad yace mata Hamad din ne.

“Amma tana raye? Daman Amma tana raye?”

Hurriya ta kalleshi kamar yadda yake kallonta da tsananin mamaki da al'ajabi.

“Magana kake kamar ka san kowa...”

“Na san kowa mana Hurriya, Hamad ne Hamad dinki mai yawan dukanki mai yawam fada
dake mai saka ki kuka, Hamad yaron Amma da Appa ni ne Hurriya”

Hurriya ta rike baki tana kallonsa hawaye na sauko mata sharrr. Captain ya zauna
kusa da ita ya rumgumeta.

“Abu ne mai wahala dukanku ku yarda da wannan”

Ya dago hannun Hurriya ya nunawa Hamad.

“Awarwaron da ka taba bani as a gift ka ce na bawa budurwata, shi ne nan, Hurriya


kin tuna lokacin da na baki kyautar wannan na ce miki wani ne wanda ya dauke ki d
Ƴar'uwanki ya baki?”

Ta daga kai fuskarta na kirjin Captain tana kuka kamar ba gobe.

“Shi ne ya ba ni”

“Me yasa ka bar ni na yi rayuwa a cikin duhu? Why? Me yasa ka ce min kowa ya mutu?”

Hamad ya tambaya da karfi yana wani nishi sai kallon Captain yake cike da bakinciki
yana jin kamar ya shake shi.

“Na rayu da wasu mutanen da ba jinina ba, a kasar da ba tawa ba, na rayu akan cewar
kowa nawa baya raye, recently nan Salim take yake fada min cewar akwai gaskiyar da
kake boye min ashe da gaske kake”
“Shiyasa na saka aka canja maka gida ai, wata kila da ban maka wannan karyar ba da
baka samu lafiya ba, da ban maka wannan karyar ba da baka rayu ka kawo yau ba, da
ban maka wannan karyar ba da baka natsu ka yi wannan karatun ba, gashi kuma saboda
shi ka cika burinka tare da kai aka yi aikin idon da ka taba fada min cewar ka yi
yar'uwarka alkawari”

Hurriya ta dago ga kalli Hamad ta mika masa hannayenta so take ya taba ta a karo na
biyu ta ji idan da gaske dan'uwanta ne. Hamad ya kama hannun yar'uwarsa da ya fi
Marmari fiye da kowa ya rike. Sai ta fashe da sabon kuka.

“Ni dai ina so ko da waninka ne aka kawo min a matsayin kai, zan karba kai ne kadai
ka rage min farincikina ya cika, ni kadai ce na yarda baka mutu ba Hamad, amman duk
haka ganinsa nake kamar ba gaske ba”

“Tun a ranar da da Captain yace min za'ayi wani aiki da yake son ayi tare da ni
amman ba zai kawo aikin ba sai a lokacin da zan fara koyon aikin a wannan asibitin
sai na kagara na ga haka, da na zo na ga fuskarki sai na ji kamar wata rayuwa ce ta
same ni da ba zahiri ba, kuma ya hana ni magana a ranar har sai yau... Kuka nake
Captain ya cutar da ni”

“Ban cutar da kowa ba a nan, ni kawai taimako na yi, kuma ba zan amsawa kowa
tambaya ba sai a gaban iyaye”

Captain ya fadawa Hamad a tsawace, kamin ya rika fuskar Hurriya ya share mata
hawayenta.

“Ya isa haka, yau aka bude idonki i thought hakan zai saka farinciki ba kuka ba,
karki janyo min wata matsala please”

Ya rumgumeta a kirjinsa, ita kuma kamar ya karawa kukanta fetir haka ta ji sai ta
kara fashewa da kukan sosai.

“Ina son na tafi gida ina son na ga iyayena idan suna raye...”

“Hakan ba zai yiyu ba, sai an dauki permission daga makarantarka hakan kuma ba zai
yiyu ba sai da hujja, dole ka kwantar da hankali kamin mu yi tunanin abun da zai
fi”

“Ba zan kwantar da hankali ba, 8na bukatar ganin Amma, babu ruwanka da rayuwata you
lie to me azzalumi kawai, ka kira min Amma zan yi magana da ita”

Captain ya daka masa tsawa a karo na biyu.

“Ba zaka bar garin nan ba sai da izini, kuma ba zan kirata ba...! And control
yourself Hamad na hadeye ka a zuciya Wallahi”

Yadda Hamad din yake ta fada ya kara tabbatarwa da Hurriya lallai dan'uwanta sai
dai akwai abun da ita da shi ba su sani ba, waya kawo shi a garin nan? Meya saka ce
ya mutu? Ta ya ya hadu da Captain? Kuma me yasa Captain ya boye mata gskiyar har
zuwa yau? Ta dago kai ta kalleshi tana jin idonta yana wani dauri kamar zai like.

“Kira min Amma...”

“Toh zan kirata, amman yanzu ki min hakuri mu tafi masaukinmu kim ga Mama Rukayya
da Momy Ikilima ma suna waje suna jiranmu! Sai mu magana a masauki zai fi kin ji”

Magana yake mata ta siffar rarashi yana shafa gashinta, sai ta girgiza masa kai ta
lake kafadarta daya.

“Aa dan Allah ka kira Amma”

“Okay”

Ya ciro wayarsa ya danna number surukarsa ya aikata mata da kira. Wayar bata dade
tana ringing ba Amma ta dauka tana sallama sai da ya amsa sallamar ya gaisa da ita
sannan ya mikawa Hurriya wayar. Hurriya ta karba tana kuka

“Hello Amma...”

Hamad yayi saurin kara kunnensa a jikin wayar yana sauraren muryar mahaifiyarsa sai
ya fashe da kuka.

“Lafiya Hurriya idon be bude bane?”

“Amma wata gaskiya zan fada miki mai kama da karya, Amma Hamad ne yana raye yana
tsaye a gefena yanzu na yi magana da shi kuka ma yake yi Amma Hamad dinki yana
raye...”

Amma ta yi shiru for some seconds sannan ta amsa.

“To ba Jamal wayar...”

“Amma baki yarda da ni ba?”

“Na yarda ba shi wayar..”

Hurriya ta mikawa Captain wayar sai Hamad yayi karaf ya karbe ya kara a kunnensa.

“Amma... Amma.. Amma...”

Nan ma Amma bata ce komai ba, domin ba muryar Captain ta ji ba, kuma ba muryar
wanda ta sani ba ne, sai dai hankalinta ya tashi sosai tana jin kamar yarta ta samu
matsala ne.

“Amma ki ce wani abu dan Allah Hamad ne...”

“Ba Hamad ba dai.... Ko waye kai dan Allah ka bawa Jamal wayar...”

Hamad ya dauke wayar a kunnesa ya mikawa Captain sannan ya nufi kofa zai fice
hawaye na sauko masa, Hurriya ta yi saurin sakowa daga kan gadon tana kiranshi.

“Dan Allah karka tafi, dan Allah karka tafi Hamad inda da gaske kai din ne karka
tafi dan Allah...”

“Jamal matarka bata da lafiya ne?”

Amma ta tambaya Captain ya sauke ajiyar zuciya.

“Lafiyarta kalau, kuma an yi aikin idon ya bude Alhamdulillah an yi nasara”

“To me yasa take min zan cen Hamad? Ko idonta ya fara ganin fatalwa ne yanzu
kuma...”

“Da gaske ne Amma Hamad yana raye, akwai abun da baku sani ba, akwai abun da na
boye muku sai a yanxu nake jin lokaci yayi da ya kamata ku san komai...”
“Kai ma baka da hankali ko Jamal? Dana Hamad ya dade da rasuwa...”

“Be rasu ba Amma Hamad yana raye....”

Ta katse wayar ji take kamar wasa suke son yi da hankalinta ko kuma dukansu ba su
da lafiya ko kuma dai yana biyewa matarsa ne wata kila ta tabu.

“Ka ga abun da ka janyo ko? Ka kashe kowa a gurina kuma ka kashe a gurinsu...”

“Ban kasheka a gurinsu ba, ba ni na yi wannan ba step mother dinka ce ka tuna


wannan? Ban fadawa kowa kana raye ko a mace ba, amman kai na fada maka suna a mace
ne saboda ka rayu...”

Captain na kai aya kiran Appa ya shigo wayar Captain cikin girmamawa da mutuntawa
ya amsa kiran.

“Lafiya kalau ya matarka?”

“Alhamdulillah an yi aiki cikin nasara Appa ido ya bude...”

“Alhamdulillah maa sha Allah ina take bata wayar..”

A madadin ta karba sai Hamad ya sake karbewa.

“Appa...”

Appa yayi shiru kamin ya amsa.

“Na'am waye wannan...”

“Hamad ne Appa Hamad ne...”

“Hamad na mu?”

“Eh Wallahi ni ne Appa wallahi ni ne ba fatalwa ba ne ban mutu ba”

“Me ka fada min na yarda kai ne? A ina ka hadu da Hurriya? Ina ka san Captain...”

“Ina karkashin kulawarsa ne Appa, ina tare da Captain kusan ko da yaushe, amman ku
ya fada min kun mutu...”

“To ba shi wayar zan yi magana da shi....”

Hamad ya aje wayar akan gado domin bakin cikin abun da Captain yayi masa ba zai
barshi ya sake hada hannu da shi ba. Captain ya kalli wayar sannan ya danne
zuciyarsa domin ya san babba baya zama kamar yaro, kuma dole zai yi ma Hamad uzuri
na halin da yake ciki a yanzu.

“Hello Appa..”

Iyami ce ta kirani tana kuka tana fada min wata magana da bata kama hankalinta ba,
ni ma kuma bata kama nawa hankalin ba, shiyasa na kiraka sai kuma na ji makamancin
abun da take fada min me yake faruwa.

“Labari ne mai tsawo Appa ba zai yiyu a waya ba, dole sai an zauna hakan kuma ba
zai yiyu ba sai an dauki permission daga makarantarsu Hamad gudun lalacewar
karatunsa”

“Hamad kake kira fa Captain...”


“Hamad Appa Hamad yana raye... Amman yanzu kamin uzuri zan tafi masaukinmu idan
Hurriya ta natsu zamu yi magana... Zan kiraka na fada maka yadda komai zai gudana.”

Hankali namiji be taba zama iri daya da na mace ba hakan ya saka Appa ya saurare
shi.

“Toh ina jira..”

Captain ya kashe wayar ya kalli Hurriya dake kallon Hamad kamar zata cinye shi tana
hawaye.

“Kukan nan ya isa haka, ni da na san haka abun zai zama ba zan bayyana miki shi ba”

“Ni kuma sai na yi ta zama har zuwa lokacin da zaka bayyana ni bayan na ga
yar'uwarta?”

Hamad ya fada a tsawace, Captain ko gefe da yake be kalla ba ya kama matarsa.

“Mu tafi Mama Rukayya suna reception suna jiranmu, daga can zan yi clearing kudin
asibitin sai mu tafi masauki mu yi magana hakan yayi miki...”

Ta daga mishi kai.

“Hamad zai tafi tare da mu ko?”

Ya daga mata kai yana shafa fuskarta hawayen dake zubar mata yake jinsu har a
ransa.

“Toh...”

Ya dauki mayafinta ya rufe mata kai sannan ya kama hannunta suka fito daga dakin.

NIGERIA....

Appa ya saka hularsa yana amsawa Yasir.

“Eh can zan tafi gurin Iyami na yi magana da ita, saboda na ji tana ta kuka abun ne
da daure kai na rasa gane kan gadon labarin..”

“Ni ma na ji abun wani iri, maybe akwai abun da Captain din yake boyewa ko kuma
Hurriya ta samu matsala ne? Yake biye mata...”

Yasir ya fada with confused.

“Amman na ji wata murya yake cewa Appa ni ne Hamad ne har da rantsuwa ni abun ya
daure min kai... Shiyasa nake son na tafi gurin mahaifiyarta”

“Okay Aappa Allah ya tsare”

“Amin sai na dawo...”

A tare suka fito bangaren Appa ya shiga motarsa, Yasir kuma na nufi bangaren Hajiya
Kaltume domin labarta musu halin da ake ciki. Shigarsa bangaren ta yi daidai ta
cire mayafin da Hajiya Kaltume take tana sauke gajiya. Tana kallon fuskar danta ta
san ba kalau ba, domin mamaki ne da daure kai a fuskarsa sai dai bata ce masa komai
ba har sai da ya zauna.

“Lafiya.?”

“Wani abu ne mai daure kai Hajiya... Yanzu muna tare da Appa a gida muna duba
kasafin kudin da suka shiga da fita na wannan watan bangaren Motocin Appa, sai Amma
ta kira tana kuka wai Hurriya ta kirata da number Captain tana mata zancen Hamad,
Appa ma be gane kan maganar ba sai da ya kira Captain din da kanshi sai wani ya
karba yana cewa shi ne Hamad, Appa dai yayi magana da yaron kamin Captain ya karba
ya ce idan sun koma masauki zai kira Appa su yi magana kuma shi Captain din ya fada
ma Appa cewar Hamad ne, but labari mai dadi dai idon Hurriya ya bude”

“Hamad......!”

Hajiya Kaltume ta fada da karfi kamar zata rusa dakin.

“Karya ne ba dai Hamad ba, Hamad din da ya mutu? Hamad din da aka kashe? Yaushe zai
rayu? Wane irin Hamad kuma? Wannan karya ne, an riga da an kashe Hamad ba zai dawo
ba, wannan wai duk na minene Yasir? Duk na ganin bayana ne? Duk na son a ga
karshena ne? An hana ni zaman lafiya da mijina, an fitine ni har sai da Alhaji ya
sake ni, yanzu kuma zai maida Iyami, idon Hurriya ya bude, ta yi aure ta auri
babban mutum, sannan n fasa auren tawa yar, mahaifinku ya juya min baya, na gagara
neman lafiyata na gagara zaman dakina kullum bana gurin wannan boka bana gurin
wannan malamin, amman har yanzu shiru, yanzu fa na dawo daga wani gurin, sai kuma
ka zo min da labarin wai Hamad yana raye? Yaron sa aka kashe tuntuni? Yaushe zai
rayu? Hamad ya mutu wani ne dai ya dawo yana son a kai ni gidan yari, burin Iyami
ya cika... Shikenan tawa ta kare”

Cikin rashin fahimta da mamaki Yasir yake kallon mahaifiyarsa, be da dalilin daga
hankalinta saboda Hamad ya dawo ba har da zancen gidan yare, above all ta gama fada
masa tana bin malamai da bokaye.

“Ta ina dawowar Hamad zata saka a kaiki gidan yari idan ma gaskiya ne?”

Tana tambayarta ne a daidai lokacin da Ruma da Khairy suka sauko domin har
dakunansu suna jin muryar Hajiya Kaltume saboda yadda take daga murya.

“Saboda ni na saka aka sace Hamad... Ni na saka aka dauke shi tare da Umm Ruman,
Hurriya na ce su dauka sai aka yi kuskure aka dauki Hamad... Amman ban ce su kashe
shi ba, Danja ne ya aikata hakan ba da umarnina ba..?”

“Waye kuma Danja?”

“Wanda na saka ya sace Hamad, a gidan Hajiya Fatee na hadu da shi.. Ni na saka shi
aikin saboda ina son a karbe kudin Iyami ne da Alhaji ya bata lokacin da ya sake ta
ya damka mata kudi da gida ga sarkar zinari ya siyawa Hurriya wannan ya saka na
aikata... Iyami ta hana ni jindadi ta hana ni zaman lafiya ta saka na rasa komai
daga zuwa aiki ta aure min miji sanadinta na rasa Salma ni na kashe yata da
kaina... Iyami na ce a halbe sai aka halbe Salma ta cikin madunin Tsafi nan ma ni
na saka mai aikin Nafisa ta kai ni duk saboda Iyami ne... Shikenan na lalace rayuwa
ta ta kare...”

Kama ganin yadda take maganar yana murza jikinta zaka san bata a cikin hayyacinta.
Khairy da Yasir ne mamaki ya cika su, Ruma kam kuka ta fashe da shi domin ta san
asalin gaskiyar.

“Hajiya... Wannan maganar ba a cikin hayyacinki kike yinsu ba...”

Yasir ya fada tana tasowa daga inda yake zaune ya dafa mahaifiyarsa ta kai kasa
tana kokarin cire riga.

“Ni na saka aka dauke shi Wallahi... Ni na ce a sace Hurriya su kuma suka dauke shi
ina ta murna asirina yana rufe sai kuma ka ce min wai Hamad ya dawo? Gidan yari zan
tafi kenan? Gidan yari zani Yasir?”

Ya rike rigarta yana kuka, ya dago ya kalli kenansa.

“Akwai wanda ya san wani abu a cikinku...”

Cikin kuka Ruma ta ce.

“Eh gaskiya ta fada, ita ta saka aka sace Hamad, kuma Hamad da ni duk mun ji
muryarta lokacin da take magana da su, Har yake cewa Hajiya me na yi kika ce a kawo
mu nan? Idan na dawo sai na fadawa Appa, sai ta fara fada tana cewa ya ji muryarta
zai tona mata asiri, bayan ta kashe wayar ne suka buga mishi karfe akai kan ya
fashe yana ta jini, Hamad yana ta ihu yana kiran sunan mutane har da ni, suka fitar
da shi daga dakin suka bar ni daga nan ban san me ya faru ba...”

“Innalillahi Wa'inna'ilaihirraji'u ײ”

Yasir ya furta har sau biyu sannan ya mike tsaye ya rike bakinsa. Khairy kuma ta
fadi zaune tana kuka domin bata taba jin wannan ba sai yau. Hajiya Kaltume kuma
bata fasa tonawa kanta asirin abun da ta yi ba, tana ta firgar rigar jikinta da
zanenta.

“Hajiya me yasa baki ki tunanin makomarki ba da ta mu kamin ki aikata? Wane irin


abun kunya ne wannan? Har yaushe zuciya zata bushe ki aikata hakan ga dan mijinki
dan be miki komao ba, be tare miki komai ba? Idan ma kishi kike da mahaifiyarsa shi
meye nasa a ciki? Gashi har kina fadar sanadinki Salma ta mutu...”

Hajiya Kaltume ta kyalkyale da dariya ta buga kafa. Ta janyo jakarta ta ciro


maganin da ta dawo da shi ta zube a gurin.

“Ai ba Shikenan ba, ni na saka Khairy ta dauke gilasan da suke dakinka na Hurriya,
ni na yi ma Hurriya da Appanta farraqu, aka saka masa tsanar Hurriya, ni na saka
aka saki Iyami Yasir ni na yi mata wannan asirin kuma na ce a kwantar da ita ciwo,
kuma na ce ayi mata asiri kar wani ya ganta ya aureta, yanzu wannan maganin shi
kuma bokan ya fada min idan na yi amfani da shi Alhaji zai zo Jiki na rawa ya maida
aurensa, kuma Fadeel zai dawo ya auri Khairy... Kawata Hajiya Fatee ita take kai ni
ko'ina ita ma kuma tana can da ciki cikin haihuwa wanda ta saka malam ya danne, na
biyawa Malam makka saboda na jidadin aiki, na mallaka Alhaji sai abun da nace yake
min... Tabbas na aikata Hamad kuma ni na dauke shi ni ce nan na aikata, kuma na yi
shiga gaban Alhaji da Sapna na kawar masa da ita a zuciya ya fita maganarta na
shashantar da ita a zuciyarsa...”

Kusan duk wani abu da Hajiya Kaltume ta aikata tun cancan da har zuwa yau sai da ta
fadawa yaransa da wanda suka sani da wanda ba su sani ba. Yasir sai ambaton Allah
yake be taba tunanin mahaifiyarsa ta yi nisa haka ba sai yau be taba tunanin ita ce
sanadin barin Amma a gidan ba sai yau, be san ita ta shiga tsakanin Hurriya da Appa
ba sai yau, be san ita ta aikatawa Hamad haka ba sai yau. Ya rasa ta ina zai fara
ya rasa ina zai saka kansa ya samu sassaucin rayuwa.

“Ku shiga da ita cikin daki ku rufe karku bari ta fito”

Ya fada sannan ya share hawayensa yana jin kamar ace ya mutu kamin yau. Ruma ta
kalleshi tana kuka.
“Yaya yanzu idan da gaske Hamad ya dawo gidan yari za a kai Hajiya Kenan?”

Ya cije baki ya saka cewa komai sai hawaye ke sauko masa. Tashi yayi ya fice daga
falon ya nufo bangaren mahaifinsa ya zauna a gurin yana jin wani bala'in gabas da
na yamma yana hade masa, da ma ace wata ce daga cikin kannensa zai ji sauki amman
uwarsa? Abun yayi masa muni gaba daya ma sai ya rasa abun da zai yi, tun farko be
ga dalilin Hajiya na aikata hakan ba, domin bata rasa komai a gidan Appansa ba idan
ma ta tasa me yasa ba zata barwa Allah ba. Yanzu wa gari ya waya? Karshenta jifan
akan wa ya dawo? Waye yayi mummunan karshe? A yanzu ya kara jin kaunar Amma a ransa
domin ita da ta wakkala ga Allah gashi yayi mata mafita kuma yana kan mata, Hurriya
ma haka, Amman Khairy gashi ta girbi abun da ta shuka tun abun be yi nisa ba,
Hajiyarsa ga abun na kokarin taba hankalinta ko ma ya taba.

Allah kawai yake ambato ya rasa me zai yi, wa zai tunkara da maganar ya rasa ina
zai bullowa lamarin. Yana zaune a gurin har la'asar, sallamar ma yana yi ya sake
dawowa gurin ya zauna tunani yake amman tunanin ya ki tsaya masa ya tasa wanda zai
ba shi shawarar abun da ya dace ya aikata. Asibiti zai dauki Hajiya ya kaita? Ko
kuma dai ya sanar da Iyayenta da kanenta domin babu iyaye a yanzu, ko kuma dai ya
samu mahaifinsa da maganar. Daga balcony din da yake zaune ta bangaren Appa ya
hango shigowar motar Maama, hakan ya saka shi tashi ya nufi bangaren mahaifiyarsa,
a dakin ya sameta tare da sauran yan'uwanta Khairy da Ruma suna kuka har lokacin
Hajiya Kaltume bata daina tonawa kanta asiri ba.

“Ku kira su Hajiya Fanna da Mama Zainab ku fada musu halin da ake ciki, idan
asibiti za a kai ta sai mu tafi...”

Maama ta juya ta kalleshi tana hawaye

“Haka Jarabawar ta zo mana Yaya? Ni gidan aure babu dadi Hajiya kuma nata auren ya
kare, Khairy an fasa yanzu kuma wannan ya biyo baya?”

Yasir ya daka mata tsawa kamar zai daketa.

“Laifi duk na waye ba naku ba? Idan ta kauce ko zata aikata wani abun da ba daidai
ba kun fi kowa sani, me yasa ba zaku nuna mata illar hakan ba? Amman ke kuke zugata
kuna tayata kishi ku nuna abunda take daidai ne, ke Khairy lokacin da kika aikatawa
Hurriya haka bata ma sani ba, saboda zuciyarku babu kyau, ke kuma idan abun kwarai
ne gashi yanzu kin yi aure kin girba, kar wanda ya sake saka min baki akan lamarin
uwata kar wanda ya sake wata magana ku bar ni na ji da zafi daya”

Ya share hawayensa ya fice daga dakin, ya sauko kasa wayarsa tana ringing da ya
duba sai yayi arba da number Appa, and for the first time sai ya ji ba zai iya amsa
kiran ba, a yayinda wayar yake rike a hannunsa tana ringing. Ya jingina da kofar
falon ya cije bakinsa ya buga ginin ya girgiza kai. A karo na biyu wayarsa ta sake
yin ringing ya dago ya duba wayar Appa ya sake kira wannan ya dauka sai dai yana
kara wayar a kunnesa sai ya fashewa Appa da kuka kamar mace.

“Subhanallahi... Yasir.. Lafiya kana ina?”

“Ina gida Appa.. Amman ba lafiya, ji nake kamar na bar garin nan kamar na tafi a
inda babu kowa na rayu a yau, duk na ji duniya ta isheni”

“Toh gani nan zuwa gidan”

Appa ya sauke wayar yana jin karin wata damuwar, daman ya kira ya fada masa yadda
suka yi daman ya kira ne ya fada masa yadda suka yi da Amma da kuma Captain sai dai
jin halin da dansa yake cike har yana kuka ya saka shi jin babu dadi domin be san
Yasir da bayyana damuwa idan ma akwai.
Yasir ya share hawayensa yana kokarin ganin yayi halin maza wajen hana kansa kuka
da jin tsanar duniya da halin da yake ciki, ya nufi bangaren Appa, a Balcony ya
zauna kamar dai dazun yana jiran Appa, sai dai Yayyun Hajiya Kaltume da Maama ta
kira ta fada musu halin da ake ciki sun riga Appa zuwa, hakan kuma be saka Yasir
tashi ya koma bangaren ba, domin baya son ya sake kallon mahaifiyarsa a cikin
wannan halin. Direban Appa ya fakawa Yasir ya mike tsaye Appa kuma ya fito mota da
sauri yana kallon Yasir.

“Mu shiga ciki”

Yasir ya wuce gaba sannan Appa ya bi bayansa, a babban falonsa suka fara zaunawa
Appa ya dubi ďansa cike da damuwarsa ya ce.

“Lafiya Yasir? Me ya faru..?”

Nauyin furucin da kunyar abun da mahaifiyarsa ta aikata sai ya saka shi kasa furta
komai a gaban Appa.

“Yasir daga kanka ka kalleni mana fada min damuwarka ni kaina da nake mahaifinki
wani abun ai kai nake samu mu tattauna balle kuma kai da kake ďana me yake faruwa?”

“Appa a game da Hamad ne... Dazun ban mun gama magana da kai na shiga cikin gida na
fadawa Hajiya abun da ya faru...”

Ya kwashe abun da ya faru ya fadawa Appansa domin be san a inda zai bude damuwarsa
bayan nan ba. Appa ya mike tsaye yana ambaton Allah yana jin kamar duniya zata
rikito ta fado masa tsabar tsorata da abun da Hajiya Kaltume ta aikata.

“Yanzu da saka hannun Kaltume aka dauke ďana? Da sa hannunta a rabuwata da Iyami?
Me na... Me.. Mena rage ta da shi? Akwai ta inda na canja mata ne bayan auren nan?
Ba Iyami da yayanta kadai ba har da Sapna? Ita me ta yi mata? Wace irin mata ce
Kaltume? Me yake damunta? Innalillahi Wa'inna ilaihirraji'un”

Duk yadda Yasir yake tunanin abun ya gigita shi sai ya tarar ya gigita Appa fiye da
shi domin sai da ya tsorata da yadda Appa ya rike kirjinsa ya dafe saitin da
zuciyarsa take, tsoron rasa mahaifinsa ya saka shi nadamar sanar masa abun da yake
faruwa.

“Appa dan Allah ka zauna”

Yasir ya rika shi ya zauna yana girgiza mai shi ma abun ya daure masa kai, ya san
be rage Hajiya Kaltume da komai ba, akan wane dalili zata azantar da kanka ta
azabtar da shi kuma ta bi ta yayansa da matarsa? Ta wani bangaren kuma yana ganin
laifin ba nata ba ne nashi ne saboda be rike addu'a ba tun farko, kuma be tsaya ya
zabo mai addini ba da bata so ta masa wannan aika aikarba a gidansa. Hankalinsa be
kara tashi ba sai da ya shiga da kansa ya duba halin da Hajiya Kaltume take ciki, a
nan ya tabbatar da abun da dansa ya fada masa yan'uwanta kuma suka bukaci tafiya da
ita gida a tare da su, Appa ua daga hannunsa sama yace ba su bukatar umarninsa
domin ba aurenta yake a yanzu ba. Momy da Namra sai suka shigo suna kallonta a
lokacin da labarin ya isa kunensu, Momy wani sabon tsoron Allah ya kamata daman can
ta san Kaltume zata iya aikata fin haka ma, amman ba ta yi zaton da hannunta dumu
dumu a satar Hamad ba, a nan ta gane ita kanta Allah ne kadai ya tsare wata kila
ita din ma ta an sace mata Namra ko Miwan ko Musib.

Ta bangaren Iyami ma haka ta kasance cikin mamaki ta tashin hankali a lokacin da


Appa ya sanar mata halin da Kaltume take ciki, sai ta fashe da kuka tana mamakin
tsananin kiyayya da zafin kishi da zai saka mace aikata irin wadannan munanan
abubuwan, daman can sun yi tsammanin da hannu a cikin lamarin saboda yadda ta nuna
bata damu ba kuma yake nunawa yaran kiyaya ta zahiri. Hakan sai ya kara sanyaya
guiwar Amma dake shirye shiryen tarewa a gidan Appa, duk kuwa da ta ji cewar a
yanzu Hajiya Kaltume bata cikin hayyacinta, kuma ita ma ta rike addu'a da tsarin
jiki ba kamar da can ba, ta wani bangaren Gwaggo da Iyami suna ganin kamar Hajiya
Kaltume ta yi haukan karya ne saboda ta san asirinta yana daf da tonuwa. Faruwar
hakan ya sakawa Amma yarda cewar yaron da zai baro Ethiopia tare da Hurriya da
surukinta da kanwarta lallai danta ne wata kila Allah ya raya shi ne saboda zuwan
wannan ranar da asirin Kaltume zai tonu, domin wani abun tun a duniya yake bayyana.
Ba sai an je ba, lahira karbar sakamako ne kawai da sanin makoma.

HURRIYA POV.

Cikin tsoro Mama Rukayya take kallon Hamad da ke zaune a masaukinsu, Hurriya na
zaune a kusa da shi tana kuka shi kuma yana hawaye.

“Taya wai za ace wanna Hamad ne ni fa ban gane ba..”

“To ke da kika san kan labarin kenan balle ni da ban san komai akai ba”

Cewar Momy Ikilima. Captain ya dan dago ya kallesu kamin ya dauke kai ya cigaba da
amsa wayar Appa.

“Hakan nake tunanin zai fi, sai mu dunguma gaba daya mu dawo tare, saboda bana son
karatun nasa ya samu matsala ka san su nan sai da doka suke komai ba kamar kasarmu
ba”

“Shikenan za'ayi haka, zan kira ka duk yadda ake ciki”

“Na gode Appa...”

Ya sauke wayar ya kalli Hamad.

“Hawayenka su suke saka yar'uwarka kuka kuma kasan yadda idonta yake”

Hamad ya kalleta sai ya mike tsaye da sauri Hurriya ta rike hannunsa ganin take
kamar idan ya fita ba zai sake dawowa ba.

“Dan Allah karka tafi..”

“Hurriyana sake ki babu inda zai je tare zamu koma nigeria, na yi magana da Appa
zai yi magana da jami'an tsaron can a matsayinsa na Mahaifin Hamad sai su aiko da
takarda zuwa ga Ambassador Nigeria da yake nan shi kuma zai yi magana da makaranta
su ba mu aron Hamad mu tafi tare da shi a can za a warware komai”

Ta sake shi ba dan ta gamsu zai dawo ba idan ya fita sai dan babu yadda ta iya.

“Bana son ya sake tafiya ya bar ni..”

“As long as you're with me you're not alone, you will never be, babu sauran damuwa
Hamad ba zai sake tafiya ba..”

Captain ya fada mata yana kokarin kwantar mata da hankali. Hamad ya share hawayensa
ya ce.

“Idan ace Hajiya bata mutu ba, sai na kashe ta da hannuna...”

“Baka bukatar yin haka, jami'an tsaro da kotu zasu yi aikinsu”


Captain ya fada sannan ya karasa ya zauna kusa da matarsa ya kama hannunta ya rike
sai ta kwantar da kanta jikinsa.

“Da gaske wai Hamad din ne dai? Innalillahi Wa'inna'ilaihirraji'u, wannan wane irin
abu ne? Hamad...”

Mama Rukayya ta fada sannan ta nufe shi ta rumgume tana kuka sosai shi ma kuka yake
yana kewar kanwar mahaifiyarshi...

Sai da suka sake yin two days a garin saboda processing din da Appa ya bi na ganin
an samu dawowa tare da Hamad ba tare da wata matsala ba, a tsawon kwanan biyun nan
kullum Hurriya tana tare da Hamad sai idan ya bar hotel din zuwa school, idan ya
dawo Hurriya tana tare da shi tsawon wunin ranar tana labarta masa abubuwa da suka
faru bayan baya nan yadda rayuwa ta zame mata a gidan Appa bayan tafiyarsa har zuwa
aurenta da sherin da aka yi mata. Duk abun da suke Captain sai da yayi ta kallonsu
gwanin sha'awa domin shi dai be san dadin dan'uwa ba.

“Na yi kewarki sosai Hurriya na fi jin kewarki fiye da kowa, saboda ina yawan
dukanki ina zalintarki, da Captain ya fada min cewar bani da kowa a yanzu, sai na
tuna abubuwa da nake miki na ji kamar na akashe kaina abun yana ta damuna...”

Hurriya tana hawaye ta ce.

“Yanzu duk mun girma Hamad, daman can kurciya ce, kana da zafin zuciya ni kuma bana
iya raba kaina da kai, shiyasa har Amma ta yi maka takwara ban yarda ka mutu ba..”

Captain ya mika mata waya.

“Cry Cry Baby Ammy zata yi magana dake”

Ta karbi wayar ta kara a kunne.

“Hello Ammy ina wuni..?”

“Lafiya kalau, ya idon naki?”

“Alhamdulillahi ina ta samun sauki”

“Ya na ji muryarki wani iri? Ko Captain din ne yayi miki wani abun?”

“Aa ba shi ba ne”

“Ba shi wayar”

Hurriya ta mika masa wayar sai ya zauna kusa da ita ya kara wayar a kunne.

“Ammy”

“Wani abun ka yi mata ne? Na ji kamar tana kuka?”

“Ban mata komai ba, ya za'ayi na mata wani abu Ammy yaushe muka yi auren ma da
za'ace har mun fara samun tsabani?”

“To waye be san halin maza ba? me take yi ma kuka?”

“Tana tare da dan'uwanta ai na fada miki abun da ya faru, kuma idan suna tattauna
labarin baya tana yawan kuka shi ne kawai”

“Ayyah ba ka ce gobe za su dawo ba?”


“Eh in Sha Allah daman amincewar makaranta Muke jira kuma sun ba mu takardar a
rubuce za mu taso gobe da safe da yardar Allah”

“Allah kawo ku lafiya, ku kula da kanku”

“I will i love you Ammy”

Ta gwatsale shi.

“Dan Allah can ko kunya baka ji a gaban matarka da kanenta sai ka ce wani yaro”

Yayi dariya ya sauke wayar. Hamad ya kalleshi.

“Kai mutumen kirki ne Captain ka kula da ni yadda ya kamata, Hurriya ta ba ni


labarin yadda ka yi mata yaki, amman me yasa ka ce min kowa ya mutu?”

“Idan mun je zaka ji”

Captain ya juyo da fuskar Hurriya

“Mai tsada me za miki order?”

Ta juya ta kalli Hamad.

“Hamad me zaka ci?”

“Haba Baby ina lallabaki ki ci abinci ke kuma da wannan gwaskan kike? Babu inda be
sani ba a garin Addis Ababa ki daina damun kanki da cinsa”

“Ko a gida haka muke, inda har zan ci abinci to zan zuba masa ne ya ci, ka yi
hakuri

Yaja hancinta yana murmushi.

“Tsokanarki nake, tambaye me yake so sai na siyo muku”

Hamad yayi murmushi yana ganin kamar mafarki ne, wai yayarce da mijinta zaune tare
da shi a yau.

“Yayata mai kaunata yar'uwata abar alfaharina”

“Ba ka ce ni ba yayarka ba ce?”

Ta tambaya tana hawaye shi ma hawayen yake yana murmushi.

“Ada kenan yanzu na bar miki girman”

Ta yi murmushi cikin hawaye, Captain ma Murmushi yayi ya tashi ya fita.

Ya sake daukarsu awa biyar da mintuna kamin su iso Nigeria daga babban birnin
Ethiopia. A Abuja suka sauka, ba su tsaya komai ba suka sake booking flight from
Abuja to Kaduna, Ammy ta yi musu tarba ta musamman tana ta na'am na'am da matar
danta kamar daman can babu wani abun da ya taba shiga tsakaninsu. Sai da suka yi
wanka suka huta sannan suka hadu a teburin cin abinci da yake gidan. A nan Hurriya
ta gane ubanta Alhaji Haruna Mai Yadi karyar arziki yake domin falon Ammy ma ba
tile ba ne wani abun ne aka shimfida mai kamar ruwa, ga manyan kujerun da bata taba
ganin kalarsu ba a rayuwarta, dinning din ma wani abun kallo ne a gurinta balle
kuma dakin da suka sauka. Ko'ina na gidan kyalkyale ni kamar an watsa zinari.
Bakauya ta zama a gidan komai ta gani sabo yake zama mata, a nan ta yarda da Momy
take ganin kamar bata dace da auren Captain ta bangaren arziki. Masu aikin gidan ma
kansu abun kallo ne basa barin komai ya zuba a kasa da zarar an aje abu za su zo da
gudu su dauke.

Captain da kansa yaja mata kujera ta zauna, sannan ya zauna yana magana da
mahaifiyarsa da ta zabi serving din matarsa da kanta ba kamar Momy Ikilima da Mama
Rukayya da masu aiki suke zuba musu abinci ba, sai da ta fara ajewa Hurriya plate
din abinci sannan ta zubawa Captain ta aje masa warin kwai dake kan salad ya saka
shi jin tashi zuciya da sauri ya kawar da fuska yana yunkurin amai.

“Me ya faru wani abu ka gani a abinci?”

“No kwan ne na ji shi wani iri, bana son warinsa”

Ammy ta dauke plate din ta zuba masa wani abinci babu kwai har ya fara ci sai kuma
ya ji baya son abinci kawai wani abun kwadayi yake so.

“To ko dan kun yi tafiya a jirgi ne?”

“Ammy karki sa na ji kunya mana, yau na saba hawan jirgi?”

Hamad ya kalleshi.

“Ko dai baka da lafiya ne?”

“I think so, jikina ma yayi zafi, tun da muka je ba wani lafiya nake ji ba, kawai
dai ina daurewa ne saboda akwai abubuwa da yawa a gabana”

Ammy ta kalli Hamad.

“Wannan ne yaron? Shi da wanda kake yawan zuwa Ethiopia gurinsa daman? Da zarar ka
samu sarari sai ka tsallake ka tafi Ethiopia ashe duk saboda shi ne?”

“Wallahi kuwa Ammy”

“Bari na kira Family Doctor ya dubaka kamin ku tafi”

“Okay”

Ammy ta tashi ta bar dinning din, Captain ya kalli daya daga cikin masu aikin gidan
ya ce.

“Samo min wani abu mai ruwa ruwa na sha”

“To ranka ya dade”

Sai da Ammy ta kira likitansu na gida ya zo ya auna Captain ya duba shi ya fada
musu fever ne kawai yayi masa allura ya kuma dorashi akan magunguna sannan suka bar
garin Kaduna a business flight din Daddy da baya kasar domin ta waya ya gaisa da
Hurriya yayi mata maraba da zuwa gidansa kuma ya saka Ammy ta hada mata goma ta
arziki a madadinsa.
*A duk lokacin da nake littafi sai an tambaye ni minene POV saboda ina saka shi a
duka books dina, POV yana nufin POINT OF VIEW. idan wata ta sake tambayata sai na
cire mata hakorin gaba 🥴*

HAJIYA FATEE POV

“Hajiya jikin ne dai?”


Fadeel ya tambaya yana taba jikinta cike da damuwa Hajiya Fatee ya dago ta dubi
danta, cikin bakinciki da nadama ta ce.

“Ko da jikinki bana bukatar tafiya asibiti yanzu Fadeel, ku bar ni na yi abun
kunyana a nan idan ma kasheshi saku yi ku kashe, bayan na tafi”

Afrah ta girgiza kai.

“Haba Hajiya ki daina fadar hakan, abun da ya same ki kaddara ce daga Allah, kowa
da yadda Allah ya rubuta masa kaddararsa, zai iya samun kowa, Allah ya tsare mu da
kashe abun da kika haifa, ko me kika aikata muna son rayuwarki kuma ina sonki a
haka saboda kw mahaifiyar Fadeel ce ina son miJina ba zan taba tsanar mahaifiyarsa
ba”

“Na yi abun kunya, sanar matar ďana ina ta ganin kamar kin tare shi daga gareni
ashe sheidan ne yake ta min gizo da sake sake, dubi yadda na zama na janyo muku
abun kunya”

Fadeel ya sauke ajiyar zuciya, tabbas idan har duniya ta san halin da mahaifiyarsa
take ciki zai ji kunya ba karami ba, daga lokacin da na gane gaskiyar abun da take
boye masa har zuwa lokacin da ta bayyana masa gaskiyar komai da komai be sake
walwala ba, ba sake kwantawa bachi ya dauke shi ba, be sake kallon wani abu yayi
dariya ba gaba daya farinciki ya kaurace masa.

“Zan tafi na bar muku abun kunya Fadeel, dan Allah ka yafe min kuma ka kula da
yar'uwarta, ka fahimtar da ita ban kai aikata aka min cikin nan ba sai dan kaddara
ta biyo ta nan”

“Karki damu Hajiya, Zainab zata dauko kuma zaki samu sauki ki tashi da yardar
Allah, ko ma miya faru mu dai muna son rayuwarki”

“Mutuwata tafi rayuwata Fadeel bana fatan rayuwa idan ma na haihu lafiya, idan kuma
ban haihu ba, kun huta karku fadawa kowa abun da uwarku ta yi, Afrah ki yafe min
dan Alla..”

“Na yafe miki Hajiya Wallahi ni ban rike da komai ba”

“Allah ya muku albarka... Tashi ka tafi gurin aikinka, ga matarka nan ai ta isa
tana kula da ni”

“Toh Hajiya”

Ya mike tsaye ya fice daga dakin. Kusan tun da gaskiyar cikin ta bayyana shi da
yar'uwarsa suka ji cewar ba kari ba ne, cikin shege ne Hajiya Fatee ta yi Zainab ta
bar gidan ta koma gidan kanen mahaifinsu kuma ta kasa komawa gidan mijinta saboda
uwarta ta yi abun kunya, sai kulawar Hajiya Fatee ta dawo karkashin Matar Fadeel
wato Afrah wanda ya maida ita gidansa bayan fasa auren Khairy da yayi daman ba shi
da burin auren kawai yana biyayya ga cilastawar mahaifiyarsa ne. Matar da take zagi
take cewa ta mallake mata ďa matar da saboda ita wannan mummunan kaddara ta same ta
yau ita ce take kula da komai nata take mata komai kamar yarta, kusan a gidan ta
tare ita da yaranta saboda kula da uwar mijinta.
A ranar da Hajiya Fatee ta yi ma danta da matarsa wasiya kuma ta roki gafararsu
a ranar ta yi musu bankwana, a ranar ita da danta ba su kwana duniya ba, cikin dare
nakudar data shekara ashirin da wani abu rabon da ta yi kalarta ta taso mata, idan
Fadeel yayi yunkurin kiran wani ko kaita asibiti sai ta hana tana fadin ya barta ta
mutu cikin gidanta domin ta san cikin nan ba zai barta ba, daga karshe da ya ga
wahalar ta yi yawa sai ya dauko mota kamin ya saka ta ciki ta ce ga garinku ita da
danta. Rufin asirin da take rokon Allah yayi mata na mutuwa cikin gida ta samu
wannan an karba mata, kamin safe fuskar Fadeel da Afrah ta kumbura sosai saboda
kuka. Haka Afrah ta rinka rusa kuka kamar uwarta ce ta mutu tana matukar jin
tausayin mijinta da ya rasa uwa da kuma tausayin Hajiya Fateen. Sai yafiyar Allah
take roka mata, wani kukan ba tashi a gidan ba sai da yarta Zainab ta zo ta fara
nadamar tafiyar da ta yi ta bar mahaifiyarta cikin fushin abun da ta aikata musu
ashe ma ba mai dade bace a duniya, a yanzu kam sun zama ba su da kowa daman uban ya
dade ta rasuwa yanzu kuma uwa ta bi bayansa. Har aka yi amsar gaisuwa aka kare
Hajiya Kaltume bata zo gidan ba, sai da aka kara kwana sannan Yasir ya zo gaisuwa
gurin Fadeel Maama kuma ta shiga ciki ta yi ma matan. Yasir ya fada masa halin da
Hajiya Kaltume take ciki na rashin lafiya da ba zata ita zuwa gaisuwa ba, sai
Fadeel ya tausayawa mata duk da kasancewar Yasir din be fito fili wikiwiki ya fada
masa hauka take ba. Sai dai hakan be hana shi tausaya masa ba, domin daga ta shi
Hajiyar har Hajiya Kaltume bin bokaye da rashin yarda da kaddara be haifar musu da
ďan mai ido ba.

*** *** ***

Lokacin da Captain ya kira Appa ya fada masa sun kusa shigowa garin Gusau, sai Appa
ya fadawa Amma ita kuma ta kira mutanen gidansu ta fada musu sai duk suka taru a
gidan na Appa a bangaren Amma. Shi kan shi Appa sai ya dawo gida da wuri, kamin su
iso, Amma ta kasa zama ta kasa tsayuwa sai safe da marwa take ta kagara ta ga ďanta
shi din ne ko waninsa. Suna Haka Hajiya Binta ta iso daman tun da Appa ya fada mata
take ta mamaki kuma take daukin ganin jikan nata.

Duk yadda Appa ya so ta natsu sai ta kasa saboda abun da yake gabanta ma son ganin
Yarta da Ďanta. Daga Hurriya har Mama Rukayya babu wanda ya san da daurin auren
Alhaji Haruna da Iyami da aka sake daurawa bayan dawowarta saudi balle tarewar Amma
a gidan Appa sai da suka dira a gidan.

Motarsu na tsayawa Amma ta fito da sauri tana sanye da Hijab. Hindu, Gwaggo da Inna
Uwani suna bayanta Appa tare da Alhaji Musa da Malam Zakiyyu kanensa da Hajiya
Binta duk suna tare da shi, Yasir ma da a lokacin ya iso gidan ya fito motarsa da
sauri yana kallon Hamad da Hurriya da suka fito motar. Amma ta durkushe a kasa tana
rufe baki tana kuka, tabbas danta ne amman kamaninsa sun sauya yanzu girma ne yake
kamashi ya zama ba kamar lokacin da aka dauke shi ba, banbancin wacan ranar da Ruma
ta fito mota tana fada mata Hamad ya mutu da wannan shi ne wannan yana a raye ne,
amman kukan kusan daya ne, Appa ma hawaye yake kusan kowa kuka yake har shi kan shi
Hamad ne.

Amma ta dubi Hurriya dake kallonta garau tana gani babu gilashi ga kuma Hamad sai
ta juya baya tana kuka tana godiya a gurin Allah. Hamad ya nufi inda take da
gudunsa yana kuka kamar za a cire masa rai irin kukan da ya fi kama da rashi. Ya
rumgume Amma yana kiran sunanta jikinsa na rawa muryarsa na rawa Amma ma ta
rumgumeta danta tana kuka sosai. Hurriya ma kuka take Hajiya Binta, Rukayya Yasir
kusan kowa sai da yayi hawaye a gurin saboda tausayi. Amma ta taba fuskarsa ta taba
kunnesa ta lalaba jikinta ta shafa bayansa kamar wanda ta rude.

“Hamad... Hamad... Hamad.. Hamad... Allahu Akbar.. Hamad.. Da gaske ne ashe Hurriya
gaskiya ta fada maka mutu ba...”

Hamad ya dago ya rumgume Appa yana kuka.

“Na yi marmarinku Appa na yi kewarku, rayuwar da babu iyaye babu dadi no matter
what mutum zai samu a duniyar nan”

“Mun yi bakinciki rashinka Hamad ashe kana raye, Alhamdulillahi”


Appa ya share hawayensa sannan ya kalli yarsa yana murmushi.

“Hurriya an samu lafiya Alhamdulillahi”

Hurriya ta nufi mahaifinta ta rumgumeshi tana kuka.

“Kukan ya isa haka ku shiga ciki mana”

Hajiya Binta ta fada, sai da Hamad ya rumgume kowa a gurin sannan ya daga kansa
yana kallon gidan ta ko'ina.

“Ashe zan dawo na yi rayuwa a nan”

Ya fada yana tuna ranar da Amma ta shirya kayanta zata bar gidan, tana boye musu
sakin da Appa yayi mata, shi kuma a lokacin ya gama fahimtar komai saboda ya fi
Hurriya wayo da fahimtar abubuwa. Yasir kallonsa yake yana jin tausayin
mahaifiyarsa ita kawai yake tunawa halin da take ciki yanzu da kuma wanda zata
shiga a nan gaba.
A falon Amma suka zauna gaba dayansu, Hurriya na ganin yadda aka kawata falon aka
saka furniture da komai ta fahimci Mahaifiyarta ta dawo sai farinciki ya lullube ta
daman abun da take da burin gani tuntuni kenan dawowar mahaifiyarta a gidan.

Sai da suka yi sallah suka dan huta sannan suka sake haduwa a bangaren Appa har
Momy da yaranta Hamad ya ba su labarin yadda aka daukeshi zuwa lokacin da suka buga
masa karfe a kai suka fita da shi daga dakin be sake sanin inda yake ba sai da ya
farka ya ganshi a wata kasar tare da wasu mutanen da ba yarensa ba kabilarsa ba.

“A haka na yi ta rayuwa a cikinsu, sun suna min kauna sosai sun dauke ni kamar
ďansu ba su tana muna min banbanci ba, saboda mahaifiyar Salim mace ce mai son
mutane, musamman ni, tana yawan cewa tana ganina kamar ďanta Salim ne, tun daga
lokacin da Captain ya fada min cewar ba ni da kowa a duniyar nan, sai na rike su a
matsayin yan'uwa da iyaye amman babu daren da bana kewarku...”

Captain yaja numfashi ya sauke har lokacin yana jin fever dake tare da shi ya
kwadayin son abu mai ruwa be fita jikinsa ba.

“Wannan dalilin ne kadai ya saka na dagawa Salim kafa, ta bangaren nan yayi min
hallaci kuma mahaifiyarsa ta cancanci ko wane kalar tukuici daga gareni”

“Me yasa ka ce min kowa ya mutu?”

Hamad ya tambaya, sai dai Captain be kula tambayarsa ba ya dauko zaren labarin tun
daga tushe.

“A ranar da na zo gidan nan, na shiga bangaren Momy na samu Hurriya tana kuka ta
fada min cewar an dauke dan'uwanta, kamin ita Namra ta ba ni labarin abun da ya
faru saboda tana saka ran ko akwai hannuna a ciki ne saboda fasa min tayun mota da
Hamad yayi da kuma kyautar da na yi ma Hurriya a lokacin ta gilashi sai ta ki ta
karba, na ce mata sai na dauki mataki, a yanayin yadda aka ba ni labarin ma sai na
fahimci ba Hamad aka zo dauka ba Hurriya aka so sacewa da ba sameta ba ne aka dauke
Hamad, a ranar Hurriya ta roke ni wata alfarma ta tambayi sunana na ce mata ni Soja
ne sai tace Malam soja ka nemo min dan'uwana dan Allah, ni kuma na mata alkawarin
zan nemo mata shi har na yi mata rubuta a takardar na ranar da na dauki alkawarin
da sign na bata, tun daga lokacin sai na baza mutane na neman yaron sai dai ba a
same shi ba sai after an yi sanarwar cewar ya mutu a nan, sojojin da suke aiki a
hanyar sokoto suka samu gawarsa a cikin wata gona shi ma kuma saboda sun za su
shiga cikin kauyen dake gurin ne gurin kai farmaki, a take suka sanar da da
headquarters Mu cewar sun samu gawar yaron da na ba da cigiya na shigar da report
akansa, su kuma suka sanar min, a take na shirya ni da kaina na tafi gurin tare da
wasu soldiers daga headquarter saboda bincikar yadda komai ya faru, sai muka samu
har lokacin yana zubar da jini fresh blood ba daskarare ba irin na wanda ya mutu,
kuma da na taba shi sai na samu yana da rai amman baya numfashi, a take muka dauki
gawarsa zuwa asibitin tureta dake sokoto muka saka likitan gurin ya duba shi sai ya
fada mana cewar alama sun nuna yana raye, amman yayi nisan da abu ne mai wahala ya
iya tashi saboda ran sa yayi nisa kadan ya rage masa, i never give up na dauke shi
daga wannan asibitin zuwa asibitin dake cikin garin sokoto wato asibitin anan suka
karbe shi suka yi iya abun da za su iya kuma aka yi nasara numfashinsa ya dawo, sai
dai sun fada mana abun ya taba kwakwalwarsa, da ya fara jin sauki sai ya zama be
bude ido be cewa komai baya motsi numfashin ne kawai a duk tsawon lokacin nan yana
karkashin kulawata ne, ni da kaina na nemi Salim ya taimaka min na je da yaro a
kasar da mahaifiyarsa take, saboda mahaifinsa dan garin gusau ne, dan Sarauta
Family's, sai dai mahaifiyarsa yar kasar Ethiopia ce aiki ya kai mahaifinsa a can
ya aure suka haifi Salim da Ziaw sai suka rabu ya dawo nan Nigeria tare da Salim ya
bar nata Ziaw a can wannan dalilin ne ya saka ke kiran Salim da Ethiopian saboda
yana zuwa gurin mahaifiyarsa sosai yana zama a gurinta, be musa min ba ya amince
sai na nemi transfer daga asibitin zuwa asibitin Medical Center Hayat MCM, saboda
ina tunanin duk wanda zai saka ayi ma karamin yaro kamar Hamad haka zai iya kashe
shi idan ya san yana raye, kuma gashi mu ba mu da full evidence na wanda ya aikata
hakan balle mu kama shi, tun da ba mutanen aka kama ba gawarsa kawai aka samu, ko
ba komai a can kasar zai fi samun kulawa fiye da nan, da Salim muka shirya komai
bayan na fada masa halin da ake ciki shi kuma ya sanar da mahaifiyarsa sai ta yi
mana duk abun da ya kamata muna isa aka karbeshi a asibitin, kuma sai aka yi sa'a
yana ta samun sauki, sai dai hankalinsa ya tabu ya kan yi wasu abubuwan masara dadi
yana yawan firgita da kiran sunayen Iyayensa sai likitocin suka tabbatar min da
cewar matukar ba a sama masa abun da yake so ba zai iya haukacewa kuma zai yi
wahalar warkewa, wannan dalilin ya saka idan na kai masa ziyara ko Ziaw take ko
Mahaifiyar Salim mu kan cusa mata cewar bashi da kowa, na kan ce baka da kowa Hamad
kai kadai yake rayuwa ko bachi yake idan na fada masa haka sai ya zabura, na fada
masa kowa naka ya mutu a yanzu mu wasu Iyalin ne da ka samu wadanda ba ka sani ba,
a haka sai da Hamad ya kwashe shekara daya a asibitin sannan ya ji sauki har suka
sallame mu, sai na kai shi a gidansu Salim a gidan ya fara rayuwa kuma ya rayu da
karyar dana cusa masa cewar ba shi da kowa”

Captain yayi shiru yana jan numfashi kamin ya cigaba.

“Be cika damuwa ya bani labari ko yayi hirar rayuwarsa ta baya ba, wata kila saboda
na riga na fada masa cewar ya rasa kowa ba, wata rana ya taba tambaya ya aka yi ya
rasa kowa sai na fada masa, yadda na tsince shi, kuma a lokacin da yake nan asibiti
ma nemi iyayensa sai na samu bakincikin rashinsa ya kashe su, sai ya tambaye ni ina
da wata wata yar'uwa Hurriya ita baka ganta ba? Haka ne Hamad...?”

Captain ya tambaya sai Hamad ya daga masa kai yana tuna lokacin.

“Na ce mishi ita ma na yi mata irin yadda aka yi maka, shin kana sha'awar komawa
garin da babu kowa sai yace min aa, da haka na samu ya fuskanci rayuwarsa na saka
shi makaranta a can, saboda ya fada min lokacin da yayarsa yake raye yana da burin
zama likitan ido saboda ita, na karfafa masa guiwar yin karatun saboda ya cika
burinsa, har kai inda yake a yanzu, a lokacin da ya gama high school sai na nema
masa makaranta a kasar kuma muka nemi bangaren da yake aka ba mu, saboda sun yaba
da hazakarsa, a yau Hamad yana cikin best students na makaranta mai su kwazo da
maida hankali, na taba daukar hotunan Hurriya na tafi da su na zimmar nuna masa sai
kuma na kasa hakan, saboda ban san ta yadda zan amsa masa tambayar da zai min ba,
kuma a lokacin ba ni da kakkafar alaka da ku kamar haka, kuma na san mahaifiyarsa
ba zata iya daukar wani mataki ba, tun da ga Hurriya ma a lokacin ana musguna mata
babu wanda yace komai na san wanda ta aikata wannan zata samu wanke kanta cikin
ruwan sanyi ko ma ta sake kashe shi”

Captain yayi murmushi yana tuna bawa.


“Na bawa Hamad labarin sabuwar budurwar da na yi, har nace mishi ya dauketa a
matsayin yayarsa sai ya ba ni abun hannu a matsayin kyauta kuma na kawo miki
Hurriya gashi nan a hannunki”

Hurriya ta kalli abun hannun ta kalli Hamad Hamad ma ya kalli abun hannun da ya
taba bawa Captain.

“Ta yadda zan juyar da karyar da na yi ta zama gaskiya ne abu mai wahala a gareni,
shiyasa na bar abun a haka har zuwa lokacin da gaskiya zata yi halinta, kuma wannan
ne dalilin da ya saka na zabi zuwa Ethiopia aikin idon Hurriya fiye da ko wace
kasar, lokacin da na yi wacan lafiyar tare da Salim muka tafi a lokacin ya gane ina
son Hurriya hakan yasa har yanzu nake kyautata zaton shi ya yada hotunan Hurriya a
kafofin sada zumunta, kuma zatona ya tabbata domin hacking din da na saka ka yi min
da kuma bincike sirrin wanda na saka aikin ya fada min haka, sai dai yadda ya samu
hotunan ne abun da ya daure min kai, a lokacin da yayi min furucin cewar yana da
sauran amfani a gurina sai na saka aka dauke ka daga gidansu aka kama mata masauki
a makarantarku saboda gudun kar zuciya ta saka shi ya cutar da kai, na san akwai
tsaro a makarantar ta yadda ko da ya aikata maka hakan za gane ko waye...”

Sai a lokacin Hamad ya gane dalilin Captain na maida shi hostel din makarantar da
yayi.

“Wata kila ya samu hotunan ne ta hanyar Adam”

Hurriya ta fada, Captain ya daga mata kai.

“Ni ma haka nake zato, ko da sanin Adam ko kuma a sirrance domin dan'uwansa zai iya
fada masa matsalarsa shi kuma kishi da haddasar ni na same ki ba shi ba ya saka shi
aikata hakan....”

Amma ta share hawayenta tana taba Hamad dake zaune kusa da ita yan biyu suna zaune
a cinyarsa.

“Na dauka da gaske Hamad ya mutu, na karbi wannan kaddarar amman Hurriya ta ki ta
karbi wannan”

Hamad ya kalli Hurriya ta kalleshi. Captaim ya ce.

“Ya taba fada min cewar Yana fada yawan fada da yar'uwarsa yanzu kuma yana son
neman lafiyarta kuma gashi bata nan...”

Suka yi Murmushi. Yasir ne mutum na farko da ya fara mikewa tsaye ya fice daga
falon. Sai da ya dauki lokaci sannan Rukayya ta bayansa. Gingine ta same shi jikin
motarsa ya rike kansa ya rasa me ke masa dadi a duniyar nan.

“Yasir...”

Ya dago ya kalleta sai ya kawar da idonsa.

“Minene Rukayya?”

“Ya kake?”

“Lafiya kalau”

“Dan Allah karka boye min ya kake?”

Da ya dube ta sai ya ga hawaye take zubarwa shi ma sai na shi hawayen dake makale
suka zubo.

“Ban sani ba, ko za su zabi kai Hajiya gidan yare ko akasin haka, amman ba zan iya
zama garin nan matukar mahaifiyata ta kasance a gidan yari, ba ni da sauran
farinciki a yanzu. I respect your parents decision da suka hanani aurenki suna da
gaskiya”

“Yasir shin har yanzu kana so na?”

Ya dubeta da kyau sai yayi murmushi ya dago wayarsa ya nuna mata hotonsa da yake a
screen din wayar, sannan ya sauke ya tafi ya bar a gurin tsaye. Amma da yan'uwanta
suka koma bangarensu suna tattauna abun da ya dace Appa ma yana tattauna da nasa
yan'uwan. Captain kuma ya fito yana magana da Hurriya, so yake ya dauketa su je
family house dinsu su ganta even though Magariba ta gabato, ita kuma tana son
kasancewa da yan'uwanta a yanzu.

“Idan mun tafi can Nene zata iya cewa na kwana a can ai ko?”

“Ya za'ayi tace miki haka bayan kuma ta san kina da MiJinki?”

Ya duba yaga babu mai ganinsu sai ya kama fuskarta yana kallon kwayar idonta.

“Alhamdulillah you can see now my baby my heart my soul my duniyata”

Ta yunkura zata yi dariya sai amai ya cika mata baki, da sauri ta ja baya ta juya
ta fara kwarara amai a gurin kamar zata amayar da yan hanjinsa. Captain ya shiga
cikin ya dauko mata ruwa ya wanke mata bakinta sai da yayi da gaske sannan ya iya
danne zuciyarsa domin shi ma aman ya ji yana taso masa. Ya taba jikinta.

“Sannu kina jin rashin lafiya ne?”

“Aa amman kai jikinka da zafi, ko zaka tafi asibiti ne?”

“Maybe gobe, amman ba yau ba dare yayi, ki shiga ciki ki huta gobe zan tafi na kai
ki gurin su Nene”

“Toh.. Sai da safe..”

Har ta juya sai ta ji an riko hannunta an dawo da ita.

“Hurry na.. Me kika ci ya saka ki aman nan? Me yasa kika yi amai?”

“Ban sani ba”

Ta dan yamutsa fuska.

“Turarenka nan ne bana so yanzu”

Yayi murmushi ya rika hannunta ya nufi gurin motarsa.

“Me ye ina zamu je?”

“Asibiti”

“Babu asibiti da yamma fa..”

“Ta barrack zamu tafi likotocinsu kullum available”

“To ai ni lafiyata kalau”


“Ni zaki raka”

Ya bude motar ya saka ya zagaya ta dayan bangaren ya shiga yayi ma motar key.
Sannan ya kama hannunta daya ya rike yana tuka motar.

“Ban a kwashe aman ba, idan wani ya gani zai ji kazanta”

“Idan mun dawo sai ki fada a kwashe”

Be tsaya ko'ina ba sai asbitinsu na Barrack yana zuwa aka hau yi mata gwaje gwaje
mamaki ya hana ta magana bayan kuma yace shi zata raka, ba ayi taru ba sai a gurin
da za a debi jininta a auna, nan kam sai da ya zauna a kujera ya rumgume da karfe
ya rike hannun sannan aka dibi jinin. A nan ya barta ya tafi yayi sallah ya dawo
sannan ya karbi results. Be bude ba sai da suka isa gurin mota yana karantawa yana
murmushi.

“Me suka ce? Ka shafa min rashin lafiya ko? Kai ne fa mai ciwo”

“Baby na kin dai shafa min laulayi”

Ya kashe mata ido daya, sai ta yi fuskar rashin fahimta.

“Ban gane ba?”

“Minene Albarka aure?”

Ta dan yi shiru...

“Kwanciyar hankali da zaman lafiya”

Ya daga kansa sama yayi dariya sannan ya jata jikinaa ya rumgume yana jin wani irin
kaunarta a ransa.

“Silly Girl, albarka aure haihuwa”

Ta dago da sauri ta kalleshi tana kwalo ido baki sake, sai ya daga mata kai ya
sumbaci goshinta.

“Uhmmm”

Ya shiga sumbantar fuskarta ta ko'ina, kamar ba a public place suke ba, he just got
lucky inda suke babu kowa gurin aje motoci ne kuma ko akwai bariki babu ruwan kowa
da rayuwar kowa.

Ya bude Mota ya saka matarsa sai da ya sumbanci hannunta sannan ya rufe motar ya
zagaya dayan side din ya shiga ya sake sumbantar ya kama hannunta ya rike yana tuka
motar.
Wani irin farinciki yake ji marar misaltuwa a zuciyarsa, be taba tunanin haka ake
ji ba idan mace tana dauke da cikin ďan mijinta sai yau, baya iya bayyana yadda
yake ji a zuciyarsa son matarsa ya ninku a ruhinsa.

“Ki kula da kanki please”

Ya fada a lokacin da ya bude mota ta fito. Ya waiga ya ga idan babu mai kallonsu
sannan ya juyo ya rumgumeta ya sumbanci goshinta. Ya kama fuskarta ya aika mata da
wani killer look.
“I Love You so much sanyin idanuwana, thank you for this”

Ya taba cikinta. Hawaye ya zubo idonta ita kanta she can't believe ciki ne a
jikinta so she's going to be a Mother now..

“Ni ya kamata na gode maka, you came in to my life by accident sai kuma ka zama
cikar farincikina, abokin rayuwata, silar share hawayena, ka min alkawarin
kyakkyawar duniya mai ciki da farinciki kuma ka fara va ni tun a yanzu... Buri yana
ta cika saboda kana kusa da ni, ina matukar kaunarka Jamal duk mace da ta samu
namiji irinka a matsayin miji hakika ta dace da Abokin Rayuwa na gari mai son
farincikinta, kai din wata babbar kyauta ce da Allah yayi min ta inda ban yi zato
ba kuma a lokacin da ban yi zato ba...”

He weep her tears yana murmushi ya sumbanci bakinta ya latsa kasan lips din.

“My cute Baby my happiness, anything for this Girl”

Ta yi murmushi ta sauke hannunsa kasa.

“Kar wani ya gan mu fa...”

“Zaki kwana gidan nan ne just for today, i can't wait na bude ido gobe na gan ni a
kusa da ke, i love you”

Zata amsa masa da i love you too Hindu da Inna Uwani suka fito, sai ta yi saurin
juyawa daga fuskantarsa da take ta kallesu.

“Hurriya ke kika yi amai dazun? Twin yace mana ga aman nan a waje Rukayya ta kwashe
kuma sai ba mu ganku ba..”

“Eh Captain ne yayi ba shi da lafiya tun a gida shi ne yau sai yayi amai, yanzu ma
na raka shi asibiti ne aka ce malaria ce take damunsa”

Captain ya kalleta da sauri, jin yadda ta daure shi a take tace shi yayi mai kuma
shi ta raka asibiti.

“Subhanallahi... Jamal babu lafiya?”

Hindu ta tambaya, sai dan yi shiru kamar wanda ya rasa me zai ce.

“Eh...... Amman da sauki asibiti muka fito yanzu suka ce Hurriya...”

Ta kalleshi da sauri tana zare masa ido. Sai ya sauya maganar daman yayi haka ne
kawai saboda ya tsorata shi ba zai iya fadar tana da ciki ba a gurin yan'uwanta.

“Sai suka ce ma Hurriya ina dauke da malaria”

Ta daga mishi kai alamar haka ne daidai.

“Sannu har da gajiya ai, kana kokari sosai Wallahi....”

“Na gode zan tafi sai da safe...”

Ya musu sallama ya bude Motarsa ya shiga yana jin zazzabin da Hurriya ta kira masa
yana kara rufe shi. Hindu da Inna Uwani suka nufi gate Hurriya kuma ta shiga
bangaren mahaifiyarta tana jin komai kamar ba gaske ba. Ta daga kai tana kallon
bangaren bayyana yadda farinciki yake a gurinta yanzu abu mai wahala, mahaifiyarta
ta dawo a karkashin inuwar mahaifinta a yayinda ita kuma take karkashin kulawar
nata mijin, ga dan'uwanta a kusa da ita. To yanzu me ya rage mata? Mai hakuri
mawadaci wahala ko bakinciki basa taba daurewa a rayuwa, haka ma dade da farinciki
basa dauwama har abada, sai an bude ko wane shafi na rayuwa... Ta shafa cikinta
tana murmushi ta samu amincewar ubangiji zata iya ganin abun da ta haifa nan gaba.
Jin kukan Rukkaya ne ya kawar mata da duk wani tunani da take a lokacin sai ta yi
hanzarin shiga cikin falon dake dauke da mahaifiyarta, Gwaggo da kuma Rukayya.

“Ashe baki da hankali har yanzu? Ke yanzu duk wannan abun da ya faru har sha'awar
auren Yasir kike...”

“Allah yana fitar da mai kyau daga mummuna gwaggo kuma yana fitar da mummuna daga
mai kyau, ni ban ce sai na auri Yasir ba, ban zan iya auren mutumen da zuciyarku
bata gamsu da shi ba, amman dai na sani farinciki ko wane ďa yana tare da uwarsa,
idan aka kai Hajiya Gidan yari, Yasir ba zai sake farinciki ba, ni kuma nawa
farinciki yana tare da Yasir, dan Allah Yaya Iyami karki saka a rufe ta Allah ya
riga ya gama miki komai...”

Tassss Gwaggo ta wanke fuskar Rukayya da mari.

“Ke yanzu soyayya har ta isa ta rufe idonki ki ce kar a hukunta Kaltume akan abun
da ta yi?”

Amma ta bata rai sosai tana kallon Gwaggo da alamar dake nuna bata jidadin marin da
Gwaggo ta yi ma kanwarta ba.

“Da baki mareta ba Gwaggo, soyayya babu abun da bata sakawa, idan har so zai rufe
idon mutum kamar Jamal ya yarda da Hurriya ya aureta a lokacin da take cikin
tsananin rayuwa da damuwa, me zai hana so ya rufe idon Rukayya? Kuma gaskiya ta
fada, ni Allah ya gama min komai daman idan mutum ya cutar da kai karka ce sai ka
rama kawai ka bar shi da Allah sakamakon da yake zuwa daga gurin Ubangiji ga
azzaluman mutane mai tsanani ne, irin wanda ruhi baya iya jurewa. Kuma Yasir ya
cancanci ko wace kalar alfarma a gurina ko a gurin yayana, yana da kirki be taba
nuna min banbanci da mahaifiyarsa ba ko sau daya...”

“Ko ma dai minene ba za a kyale ta ba, tun da na gane hankalinki da nata ya zama
iri daya”

“Daman maganar ba a gurinmu take ba, tana gurin jami'an tsaro ne sai yadda suka
yanke..”

Gwaggo ta ja tsaki tana jin haushin yadda Amma take da sanyi a wannan bangaren.
Hurriya ta karasa ta zauna a kusa da Rukayya tana bata hakuri.

“Barta ta yi ta kukan, ta dade bata mutu ba yara ba su da kunya soyayya na rufe


musu ido su kasa ganin daidai”

Cewar Gwaggo cikin tsawa. Hurriya dai bata ce komai ba ya ta tashi ta fice daga
falon zuwa bangaren Hajiya Kaltume a nan ta samu kofar falon a bude bata yi tunanin
babu kowa a ciki ba sai da ta shiga, tun ranar da yan'uwan Hajiya Kaltume suka tafi
da ita suka tafi tare da Khairy da Ruma. Yayanta ta gani zaune ya hade kai da guiwa
yayi shiru gwanin tausayi. Ta matsa kusa da shi ta zauna a kasa sai ya dago ya
kalleta da karfin hali irin na maza sai ta yayi mata murmushi.

“Hurriya...”

“Yayana ka yi hakuri dan Allah na san baka cancanci haka ba..”

“Kaddara bata duba cancanta, hakuri kuma ya zame mana dole. Sai a yanzu nake kara
jinjina kokarinki a lokacin da Amma ta tafi ta barki, yau ji nake kamar ba ni da
kowa a duniyar nan, i Felt Empty, da zarar na tuna cewar Hajiya bata da lafiya sai
ta ji komai ya tsaya min cak, and ba ma wannan ba taya zamu kalli duniya da abun da
Hajiya ta aikata..?”

“Kowa yana kuskurea Yayana, na tabbatar da ace kana sane ba zaka bar Hajiya ta
aikata haka ba, komai ai kaddara ne ka fada, ya kamata idan ta same mu mu rumgume
ta da hannu biyu...”

“Haka ne Hurriya Allah ya ba mu ikon cinyeta...”

“Ameen”

Ta amsa tana kallonsa cike da tausayawa.

CAPTAIN POV.

Da zazzabi ya isa gidansa, har ya faka mota yana kokarin fita sai kuma ya tuna da
wani abun da ya kamata yayi, hakan ya saka shi komawa motar ya sake yi mata key mai
gadi ya sake bude masa gate. Unguwarsu Salim ya nufa ya shiga har cikin gidansu ya
aika a kira shi, mai aikan yaje ya dawo ya sanar masa da Salim baya gidan. Captain
ya sake juya kan motar yana tunanin a ina zai ga Salim a yanzu, ya kira shi a waya
ko kuma dai ya gwada ziyarar gurin da yake dan taba zuwa da dare. Da shawara ta
biyu zuciyarsa ta aminta dan haka ya nufi wani gurin da Salim yake yawan zuwa idan
yana free da dare.

Captain ya faka motarsa waje ya fito ya shiga gurin yana duddubawa sai kuwa ya ci
karo da Salim zaune shi kadai yana lasa wayarsa. Captain ya karasa gurin yaja
kujera ya zauna, Salim ya dago ya kalleshi gabanshi na dan faduwa.

“Na dauka ka ce babu ni babu kai, me ya kawo ka nan? Zuwa ka yi ka ci min mutunci a
gaban mutane?”

“Ba wannan ya kawo ni, zuwa na yi na buga maka warning na karshe, kuma na fada maka
abin da baka san na sani ba...”

Captain ya bude wayarsa ya nunawa Salim duk wani evidence da ke nuna shi ya aikata
abun da yake zarginsa.

“Ka cutar da Hurriya Salim, saboda bakar zuciyarka ka runtse ido ka yada ďan'uwanka
da yarinyar da baka isa ka hana ni sonta ba, hakan duk be maka ba sai da ka sake
aikata a karo na biyu bayan mun yi aure, wannan abun zai iya saka ka rasa aikinka
ba wannan aikin Soja ba har wani aiki a nan gaba ma, kuma zai iya daureka a gidan
kaso ka sani ko? Kuma zai iya lalata character dinta a idon duniya... Ina ka samu
hotunan?”

Yayi shiru zuciyarsa kamar zata cire sabisa yadda take bugawa da karfi.

“Wata rana ne na dauki wayar Adam zan tura abu, sai na ci karo da hotunan, abun ya
daga min hankali sosai kuma na yi mamaki amman a lokacin na yi tunanin da gaske
Hurriya ta aikata hakan da Adam ne, ban ce masa komai ba na tura hutunan da abun da
zan tura na goge na bashi wayarsa, har sai zuwa lokacin da muka tafi Ethiopia tare
na ganka kana kallon hotunanta da ban san a ina ka samu ba, sai ya fahimtar da ni
son Hurriya kake yi, kuma ka san ka yi betrayed dina tun da ka san ina son yarinyar
nan be kamata ka so ta ba...!”

“Saboda ubana ne kai? Kamin na nuna ina son Hurriya kai baka nuna ta nuna bata
bukatarka ba? And let me tell you something Wallahi ban fara tausayi Hurriya da
taimakonta saboda na fada soyayya da ita ba, ban kawa wannan a kusa ba, sai tsintar
kaina na yi abun kuma haka Allah ya tsara, me yasa baka karvi Kaddara ba ka hakura
sai ka zabi cin zafinta...”
“Na yi tunanin ta aikata da gaske ne, shiyasa tun muna Ethiopia na saka aka yada
hotunan, kuma na yi tunanin hakan zai canja alakarku”

“Ka bari zuciya ta yaudareka ka aikata amininka mummunan aiki na cin mutuncin
Iyakinsa, a yau da na gane gaskiya idan ina so zan iya hukunta ka Salim ta ko wace
siga, amman ba zan yi ba, kasan saboda me?”

Salim yayi shiru ya kasa cewa komai.

“Ba zan manta alherinka a gareni ba, kuma saboda mahaifiya zan daga maka kafa,
amman dai alaka da ni da kai na yankata har abada, and duk lokacin da ka sake
batawa Hurriya rai zaka rasa damar abubuwa da yawa”

Captain ya mike tsaye ya bar shi a gurin yana gumin tsoro da kunya a lokaci daya.
Misalin Tara da rabi na dare Hurriya na zaune tare da Hamad da Amma suna hira kiran
Captain ya shigo wayar Amma har ta yi kamar ta bawa Hurriya kai tsaye kuma ta amsa
suka gaisa sannan ya tambaye matarsa.

“Amma Hurriya na kusa zan yi magana da ita ne...”

“Eh”

“Hurriya ga mijinki zai yi magana da ke”

Hurriya ta tashi ta karbi wayar ta koma ta zauna.

“Ke shiga ciki mana idan magana ta sirrin yake son yi dake fa?”

Ta tashi ta nufi stairs domin cika umarnin Amma. Sai da ta shiga dakin sannan ta
rufe kofa sannan ta ce.

“My Noor ya jikin?”

“Ba dadi har yanzu zazzabi nake ji, i just call to say Hi and kin ci abinci?”

“Na ci, kai fa ka ci...”

“Na sha tea shi kadai na ji ina so, ya kike..?”

“Lafiya kalau”

“Ya Baby na?”

Ta bata rai kamar yana gabanta.

“Ba kyau ka daina”

“Me ye ba kyau? Tambayar babyn nawa?”

Ta masa banza sai yayi dariya.

“I miss you so much, ina jin kamar mun yi shekara ba mu hadu ba haka nake gani”

“Dazun fa kawai muka rabu”

“Yeah kin san na yi alkawari i will spend every hour keeping you safe kuma yau bana
tare da ke maybe that's why na kasa natsuwa”
“I'm safe My Noor baka bukatar ka damu”

“I love you”

“I love you more more more”

Yayi murmushi sannan ya ce.

“Wane hukunci Appa ya yanke? Akan Hamad? Na manta ban tambaya na yana lafiya?”

“Yeah... Amman har yanzu ba su yanke hukunci ba”

“Okay... Je ki kwanta kin ji mai tsada, sleep tight”

“I will i love you”

“Ki yi mafarki kin ji babyna”

Ta yi dariya ta kashe wayar, ta bude dakin ta fito a lokacin da ta sauko sai ta


samu Hamad da Amma suna hawaye little Hamad yana kan cinyar Hamad yana rike da
hannunsa.

“Me aka yi ma kuka kuma?”

“Farinciki, ban yi tsammanin rayuwa zata sake ara min lokaci na ga wannan ranar ba,
ban yi tsammanin dawowar Hamad ba, yanzu iyalina sun cika maza uku mace ta daya”

Hamad ya share hawayensa ya kalli Hurriya.

“Da ace da gaske kowa ya mutu, da ba zan sake farinciki ba, kullum ina tunanin
rayuwar baya, idan na tuna ni kadai ne a raye sai na ji na tsani kaina ina yawan
tuna gargadin da kike mana na zaman lafiya da juna ni da Hurriya, a lokacin da na
yi zaton bata raye my heart keep bleeding, kullum ina tunanin da ma ace ban yi ba”

Amma ta kalli Hurriya still tana hawaye.

“Jamal yaron kirki ne sosai, mai tunani da hangen nesa mai rikon amana mai tausayi
ba tare da duban mai zai samu a gaba ba, karki yarda ko da wasa ki batawa mijinki
rai Hurriya, ba ko wane namiji ba ne ďan kunama, Jamal namijin da ko wace mace zata
dauka uba ne har ta goya da zane, kar wata rana yayi miki wani abu ki manta duk
wannan, Allah baya son mai butulci”

“In Shaa Allahu Amma”

Ta maida kanta kasa tana kara godiya ga Allah, a yanzu kam abubuwa da yawa sun
daidaita a rayuwarta...

*** *** *** **** ****

BAYAN WAƊANSU SHEKARU....

Ruwa aka sheka yau a Calabar kama da bakin kwarya, sanyi ya sauko ta ko'ina ni'imar
Allah ce da rahma. Ko ina yayi tsit abubuwa da yawa sun tsaya saboda ruwan da aka
yi wasu na tuni suka shige gidajensu. Ta bangaren bangaren Hurriya ma haka
labarin yake daman ba sanin kowa ta yi a garin da aiki ya kawo mijinta ba, idan ma
ta sani ba barinta fita yake ba, ya saba mata da zaman katon gidan da sojoji suke
gadinsa by fire by force, tun tana complain har ta gaji ta karbi dokar ta zuba masa
ido.
Jamal ya fito bathroom yana daure da bathrobe ya nufi dansa dake kuka yana ta
masifa.

“Tun da na shiga wanka yaron nan yake kuka amman kin gagara rarrashinsa, saboda
kawai baki san zafin haihuwa ba”

“Shi din ne ya cika zuciya fa, wai idan ya fara kuka ba a kama shi ba shi ba zai
hakura ba, to ni za a nunawa zuciya ni da nake da Hamad da...”

Ya dora dansa a kafada sannan ya juyo ya kalleta.

“Da wa?”

“Da oga Jamal...”

“Wato idonki yayi kwari har wani kiran sunana kike kai tsaye ko?”

Ta kashe masa ido daya.

“Wayar kai tana ta ringing dazun”

“Waya kira?”

Ya nufi wayar ya dauka yana jijjiga dansa.

“Har five missing calls miyasa baki dauka ba?”

“Yaya Namra ce fa, ko na dauka idan ta ji ni ce ba zata yi magana ba, ka san ai ta


saba kira idan ta ji muryarna ba zata ce komai ba sai ta kashe waya”

“Amman ai wani baya zama daya da wani, idan ita tana yanke alaka dake ke sai ki
sada ai ke din jininta ce babu yadda zata yi”

“Amman dai Allah yana gani na yi iya yadda zan iya na janyo ta a jikina ta ki ba ni
hadin kai, idan na kirata da waya bata dagawa idan na mata magana bata amsa min,
haka haihuwar nan da ta yi ina shiga gidanta sai ta bata rai ta dauke min fuska to
ya zan yi?”

Ya zauna bakin gadonsa ya maida Aliyu a hannunsa.

“Zo ki ba shi nono, laifinki ne da kike bari yayi kukan ai baki kusa...”

“Ni yar aikinsa ce da zan rika zama kullum kusa da shi saboda kar yayi kuka?”

“To miye aikin ki a gidan idan ba kula da yarana ba? Kin ga ni Baby idan kika yi
wasa Allah zan ki sha wahala a garin nan kin san dai baki da kowa a nan sai Allah
ko? Ina Manal?”

“Na siyar da ita miliyan biyar na ci tsire”

Yayi dariya ya girgiza kai

“Wallahi da ke ma sai na siyar da ke, bukin nan na Musib da za mu je kawai Appa ya


ga babu ke...”

“Wallahi Appa ba zai barka ba, idan ya fara maka masifa sai ka rikice”

“Baki san Appa ya fi so na dake ba yanzu?”


“Ni kuma Daddy da Ammy sun fi ko da kai...”

“Aa aa dama dai jikokinsu kika ce sai na yarda amman ke din? Ta ina?”

Ta bude ido.

“Zan nuna maka kuwa, Allah ya kai mu Kaduna lafiya”

“Ameen bashi nono dan Allah kuma ki daina wofintar min da yaro dan Allah”

“Ban masa komai ba kawai zuciya ce fa, Ammy tace haka ka yi kana karami da an
kyaleka sai kuka sai fushi....”

“To miyasa za a aje ni din? Kuma Ammy ta daina zama da ke tana baki labarin
kurciyata haka kawai”

Ta ra kwafar da kai tana daga masa gira daya.

“To yaya?”

Yayi dariya yana mika mata Babanshi.

“Wato baki horu ba ko? Duk abun da na yi Miki jiya sai da kika samu baki fada min
magana yau har da su daga gira?”

Yana fadar haka sai murmushin dake fuskarta ya gushe ta bata fuskar.

“Na bari yi hakuri”

“Matsoraciya, babu abun da za a fasa yarinya, kara ma ki saba soja fa kika aura ai
sai hakuri kawai”

Ya sumbanci goshinta sannan ya mike tsaye yana dariyar keta ta fara shafa mai. Tana
rumgume da Haydar tana ba shi nono har ya gama shirinsa ya saka uniform sannan ya
zauna kusa da ita yana amsa kiran da Namra ta sake masa.

“Lafiya Kalau ya yaranki?”

“Lafiyarsu kalau, Ya Hurriya da su Manal? Da Daddy”

“Lafiya Kalau”

“Captain daman ni ce nake son na je Gusau yau kuma babu flight, shi ne nace bari na
tambaya ko zan samu ta bangarenka lefen Musib za a kai kuma bana son aje ba tare da
ni ba”

Captain ya daga hannunsa ya dafa matarsa.

“Wallahi Daddy ya karbe komai nasa a gurina, ya cire sunana a komai ba ni da ikon
komai nasa yanzu sai dai ki kira shi ki yi magana da shi”

“Me yasa?”

“Saboda na ki yarda na aje aiki na tsumduma a harkokinsa”

“Okay bari na kira Momy sai ta mishi magana ko Ammy”

“Okay ki gaishe da Sadiq”


Captain na sauke wayar Hurriya ta kalleshi sai ya sumbanci idonta

“Yaushe yayi haka?”

“An kwana biyu”

“Amman kansan baka kyauta masa ba ko? Be kamata ka yi haka ba”

“Babyna mutum be da ra'ayin kansa ne? Bana son kasuwanci Allah ya gani na fi
jindadin aikina”

“Haba Noor idan baka maka ba wa zai masa? Kai kadai yake da shi fa, kuma wani abun
ko bama so haka zamu daure mu aikata saboda iyaye”

“Baki fatan na kai Major General ne? Yanzu gashi an kara mukami kuma a haka sai na
bar aikina na koma ga wanda ban saba ba, ba wai ba zan yi ba ne gaba daya, zan yi
amman na hada biyu”

“Ni daman ba son aikin naka nake ba, kullum muna wannan garin gobe muna can ni dan
Allah ka aje ka ka bi abunda Daddy yake so if not...”

Ta aje masa babynsa ta mike tsaye sai yayi hanzarin mikewa ya rumgume ta ta baya.

“Me zai faru haba yan matana my one and only daga ke ba kari idan ina soja, idan na
zama dan kasuwa kuma... That's the whole different story”

Ta Bude baki ta juyo ta kalleshi.

“To me kake nufi”

Da dariya yayi ya rumgume ta yana sumbantarta.

“Uwargidata kuma amarya wasa nake, kar a hana ni abinci a yau”

Ta yi dariya tana lilo a jikinsa.

“Karamin aikina ne kuwa”

Ya shiga gyara mata girarta.

“Ai na sani, uwar Manal da Haidar sarakuwar AA Turaki in-law din Hajiya Turai, yar
gatan Jamal farincikin Amma, sanyin idon Appa, aminiyar Hamad”

Ya sumbanci bakinta yana shafa jikinsa kusan a kullum kamar amarya take a gurinsa,
saboda sonta da yake mata ya fi wanda take masa, ita kuma tana kokarin ganin ta
kyautata masa ta rike kambunta a gurin mijinta.

“Dadadadadada..”

Yana jin muryar Manal yayi hanzarin dauke bakinsa a na ta ya kauce daga shu'umin
rikon da yayi mata ya kalli kofar dakin da aka turo. Yarinya ce yar shekara biyar
rike da pen da ipad ya raba gashin kanta gida biyu an mata two babys da pink
ribbons. Kusan fuskarta gaba daya fuskar Captain ce kadan ta debo daga Hurriya.
Captain ya rage tsayu ya duka daidai yarsa yana gyara mata gashin kanta.

“Ammyna ina ta tambayarki...”

“Ina daki ina drawing, Dada na zana ka look”


Ta nuna mishi zanen dake ipad dinta sai ya karba yana yabawa.

“Wow Ammyna kin yi kokarin excellent”

Manal ta yi dariya ta yi tsalle tana jindadi. Captain ya sumbance ta sannan ya daga


ta sama ya dauke ta ya fice daga dakin.

*** *** ****

An yi bikin auren Musib da Ruma da aka hade lokaci daya, cikin jindadi da barin
naira, domin Musib shi ne dan Momy na karshe da zata aurar a yanzu, bayan Miwan da
ya auri wata Abokiyar karatunsa da kuma yar gudaliyarta Namra wadda ta auri Dr
Sadiq abokin Yayanta Miwan, hakan ya saka Momy ta fitar da kudi ta yi hidima sosai
kamar yadda ta yi a sauran bikin yayanta ko ma fi.

Amma ta zage dantse wajen ganin ta zamewa Ruma uwa duk kuwa da irin abubuwan da
Hajiya Kaltume ta yi mata a lokacin da take gidan, Amma bata duba wannan ba daman
hali ba daya ba, dan haka ta rike Ruma kamar yarta, duk wata siyayya da za'ayi ta
auren Amma ce ta yi domin Momy tana can tana fama da nata hidiman na auren danta.
Duk wata hidima da ya dace uwa ta yi Amma ce take yi, domin bayan komawar Ruma da
Khairy a gurin yan'uwan mahaifiyarsu sai zaman yake yi musu dadi, bakinciki sai ya
taru yayi musu yawa, suna kallon mahaifiyarsu da bata iya komai sai tona asirin
kanta har ta kai ana rufe ta a daki sai idan za a bata abinci ko abin sha ko gyara
mata jikinta sannan za a bude ta, ko kuma idan wani ya kawo mata ziyara. Gashi
kuma ba sa jindadin zaman gidan, Ruma da kanta ta zabi dawowa gidan mahaifinta a
karkashin kulawar Amma ta san ko ba komai zata fi rika ta da daraja fiye da Momy da
har yanzu take nuna musu banbanci. A lokacin da ta dawo sai Amma ta saka hannu biyu
ta karbe ta kamar komai be faru ba, har zuwa lokacin da ta kammala karatunta ta
samu Miji Amma ta yi mata komai da ya kamata tare da taimakon Sapna da Amma take
janyowa a duka al'amurran gidan kasancewarta babbar yar Appa gashi kuma yanzu ta
dawo kusa da su da zama saboda Appa ya siya mata gida a cikin garin Gusau.

An yi biki cikin farinciki da jindadin yan'uwa da yawa sun samu halarta ciki har da
matar Fadeel da zumunci ya daure tsakanin Yasir da Fadeel din kamar wasu
yan'uwansu, matansu ma suka kulla, waton matar Yasir Rukayya da ta zame ma Ruma,
kamar babban yaya gurin shawarwari da wasu abubuwan na rayuwa. Yasir ya tsaya kamar
Appa idan ana bukatar wani abun shi ake yi ma magana ba Appa ba domin ya dauko
girman ya rayata a wuyansa tun kamin yayi aure ma balle kuma yanzu da yake da yara
biyu da matarsa. Kusan kowa tambaya Khairy yake yaushe zata yi aure ganin ita ce
Babba amman shiru har yanzu ko mashinshi babu, Yayarta Maama ce take dan tare mata
wani lokacin tana cewa ai aure lokaci ne ita ma zata yi idan lokaci yayi, gashi
kanenta Hurriya da Ruma sun yi sun barta, abun ya taba ta sosai domin tambayar mace
yaushe zata yi aure ba abu ne mai dadi ba balle kuma ita da kaddara da fadawa. Har
aka ci aka shude bakin Namra be hadu da na Hurriya ba, har yanzu da kowace ta yi
aure take da Yaya Namra bata shiga safgar Hurriya ta riga ta tattara lamarinta ta
aje gefe daya.
Ko a lokacin bikin aurenta ma haka ta yi mata kamar ba yar'uwarta ba, zata yi
magana ko mu'amala da kowa ban da Hurriya da zarar sun gaisa bata sake tambayarta
komai. Tun abun yana damun Hurriya har ya daina domin ta san babu ta inda take da
laifi, abu ne da Allah ya riga sa ya tsara shi babu yadda za a canja.

Amaryar Musib ta tare a garin da mijinta yake wato a Zamfara, Ruma kuma ta tare a
gidan nata mijin dake Kano. Duk da rashin lokaci da takurarwa aiki da Captain yake
samu haka ya cije ya zo daurin auren na dan'uwansa da kuma yar'uwar matarsa. Sai da
Hurriya ta yi da gaske sannan ya barta ta fi kai Amarya Kano, daga can yayi mata
booking flight zuwa garin da yake aiki a yanzu. Sai bayan biki da kwana biyu sannan
Hamad ya shirya ya kai musu Manal da aka bari a gurin Amma, yayi kwana biyu a garin
sannan ya dawo gida.

*** *** ***

Manal na ganin Daddynta a kwance ta zo da gudu ta fada a faffadan kirjinsa ta


kwanta.

“Dada baka da lafiya”

Ya daga idonsa kadan ya kalleta.

“Yes Manal”

Hurriya ta kai hannu ta taba wuyansa.

“Jikinka yayi zafi, bari na kawo maka magani”

Ta mike tsaye ta fara tafiya kenan ta ji yayi mata wata magana da ta saka ta juyowa
da sauri tana tofar da yawu.

“Wata kila dai ba a banza nake fever nan ba, duk a karkare daga karshe ba zai wuce
ace akwai ajiya a cikinki ba”

“Allah ya kiyaye, yaushe aka haifi Haidar din ma to, yaron da yanzu yake koyon
zama”

“It doesn't matter, ni dai na san irin wannan fever dake sani kyamar abinci da
zafin jiki sosai bana yinta sai da dalili”

“Wallahi aa Allah ya tsare Malaria ce kawai, ko kuma gajiyar aiki”

“Zamu gani ai sai a gane mai gaskiya, ni na san yanayin da nake ji ba irin na
rashin lafiyar mutane ne ba ne”

Ta daga kafadunsa tana murde baki.

“To wata kila aljannu suka shafe ka”

Ya kyalkyale da dariya sosai kamar ba shi ba ya daga Manal daga jikinsa ya zauna ya
zaunar da ita. Hurriya kuma ta shiga ciki ta dauko masa magani da ruwa ta balla ta
ba shi ya sha.

“Thank You Allah ya miki albarka”

“Ameen Allah ya baka lafiya”

“Dada Allah ya baka lafiya”

Manal ma ta fada sai ya amsa da Ameen yana murmushi.

“My Ammy rabin raina”

Hurriya ta tabe baki.

“Hamad na yi aure zan bada ita”

Manal ta lake kafada kamar ta san abun da ake fada, Captain kuma yayi dariya mai
sauti.
“Da kin jawa janki wahala ko ya dauki yarana ai sai ya dawo da su zai samu salama,
ko da Nigeria ne kuwa balle wata kasar”

“Ni ma dai bana son zaman shi a can”

“To ya za'ayi tun da ya zabi cigaba da masters dinsa a can”

“Wallahi duk saboda yarinyar nan ne, ni bana son ma ya aureta saboda Salim”

“Ina ruwan Salim da soyayyarsu? Ita dai tace Hamad take so, shi ma kuma yana sonta
sai kawai a musu fatan alheri”

“Ai Amma ba zata bari ayi auren yanzu ba sai ya gama masters dinsa”

“Kamin lokacin ita ma ta gama makaranta ai, sai ayi daidai a dauko muku yar
Ethiopian amman al'adunsu daban da na mu”

“Wai Salim yana duniyar nan ma?”

“Yana nan mana, kin san an watsar da lamurransa shiyasa ba ni da labarinsa yanzu,
yayi ta kamun kafa a kamin yayi aure yana son dawowa gurin Namra ya nuna masa ba ma
bawa marar tunani da mutumci auren zuri'armu, yaje can ya samu daidai shi”

“Amman baka kyauta ba, ka sani ko tana sonshi har lokacin?”

“Ko tana son shi be cancanci aurenta ba, kuma ita ma bana jin zata iya aurensa
gaskiya, ke ce dai take ta kishi har yanzu ta bari shedan ya shiga gabanta”

“Ai na gani, shiyasa yanzu ni ma bake kama jikina, Momy ma bata nuna min komai
yanzu amman ita ta saka daina nuna min kyama”

“Zata daina with time, nan gaba zata gane kuskuren abun da take ta daina”

“Allah yasa”

“Ameen”

Ya mike tsaye.

“Ammyna Dada will take a little nap okay?”

“Okay Dada get well soon...”

“Ba dai Soon ba Ammyna, Mamanki ta riga ta shafa min ni ban san yadda aka yi ma
muke raba pain din nan ba”

Hurriya ta saka masa dariya sai ya kai mata rankwashi a kai ya nufi dakinsa. Tashi
ta yi ta bi bayansa sai ta samu har ya hau gado, remote ta dauka ta rage ac sannan
ta lullube shi sai ya saka hannunsa da karfinsa ya janyota ta fado kansa.

“Come here ni kike yi ma dariya dazun dan kin ga gaban Ammyna ne ko?”

Ya fara kokarin tsikararta yana hada mata da mitsika sai ihu take data dariya.

“Na bari Allah na bari Captain”

“Oh Really Captain kai tsaye?”


Ya ma tashi zaune gaba daya yana chakularta.

“Yayana haba Dada Manal, My Noor na bari Allah na daina kuwa, haba Sojana”

Ya sumbance ta ta daga blanket din ya saka ta ciki shi ma ya lulluba ya rumgume a


dolenta ta yi bachin da bata tashi yi ba har da su numshari.

*** *** *** **** ****

Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah. Godiya ta tabbata ga Allah da ya ba ni


ikon rubuta wannan littafin. Inda na yi kuskure Allah ya yafe min, darasin dake
ciki kuma Allah yasa ni da ku mu amfana da shi.
Haka kuma ina rokon yafiyar wadda duk na batawa rai cikin rashin sani ko ganganci
a yafe min da Allah, idan mu ne yau ba mu ne gobe ba. 🤲

Ba zan aje alkalamin ba har sai na yi godiya ga duk wanda ya siye littafin Hurriya
ma'ana yan paid group na Hurriya, da kuma yan Arewabooks. Na gode na gode na gode,
na san kauna ce sila. Allah ya bar min ku.

And to those that read my book without paying da wadanda suka yi forwarding, na bar
ku da Rabbi 🙌

Malam Mai Tawakkali ina godiya Allah ya kara budi ya karo wasu customers masu
yawa 🙏

Daga Marubuciyar.

ZAKI
FULANI
GOBENA
HAFSATU MANGA
RAI BIYU
DEENAH
BABBAN GORO
SALEENA
CIWON SO
BAKAR WASIKA
ZAGON KASA
ZABIN RAI
WANI GARI
HURRIYA

Ta ku har kullum🥰
KHADEEJA CANDY
(Oum Namra)
08036126660

You might also like