Download as doc, pdf, or txt
Download as doc, pdf, or txt
You are on page 1of 127

_~*BOSS LADIES WRITERS*~_

KE GABATAR MA KU👇

_🔥💫THE PRISONERS🔥💫_

~TAKUN🔥🔥🔥ƘARSHE~

Daga Alƙalamin Boss Bature

Dedicated To Aunty Kubra😍

_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty
❤._

_______________________

Bayan ƴan mintuna Pravin ya fito daga toilet fuskarshi a jiƙe da ruwa kamar wanda ya ɗauro alwala,
maimakon taga 6acin rai akan fuskarshi sai taga akasin hakan, wani irin shu'umin murmushi yake sakar
mata, hakan ba ƙaramin 6ata mata rai ba, ɗaure mashi fuska tayi haɗi da kau da idonta daga kan shi, taci
gaba da cin abincinta.

Gefen ta ya zauna"idan akwai wani punishment din daya fi wanda kika bani a yanzu, A shirye nake dana
kar6e shi, Ni dai buri na ki yafe min mu shirya tsakanin mu, My Sarah bazan juri fushin ki ba" daɗin baki
Pravin yaci gaba dayi mata, tun da ya fara magana Hajiya Saratu bata dube shi ba.

Abincin ta take ci, hannu takai zata ɗauki apple ciki Jerin kayan marmarin dake shaƙe a plate da sauri
Pravin ya ruƙe hannunta yana faɗin"Bai kamata kina share ni ba, tun ɗazu nake yi maki magana kinyi banza
kin ƙyaleni inata zuba kamar aku," a marairaice ya ƙare maganar, ranta ya 6aci ta tsani tana cin abinci a
takura mata, a harzuƙe ta fuskance shi da niyar ta 6al6aleshi da masifa sai dai kafin tayi hakan yai saurin
shammatarta ya haɗe bakinshi da nata, kafin tayi yunƙurin janye bakinta yayi saurin zagaye hannayenshi ya
ruƙe qugunta ruƙo bana wasa ba, still bata daina kiciniyar raba kanta dashi ba sai dai yaci ƙarfinta, lokaci
ɗaya ta soma jinta a yanayin da bata shirya kar6arshi ba, kissing ɗinta ya fara yi cikin ƙwarewa yake sarrafa
ta, har yayi nasarar zuge zip din rigarta slowly ya zame wuyan rigar har zuwa kan flat stomach dinta,
abunda ya jima bai samu damar yi da ita ba, numfashinshi har wani hauhawa ya ke yi kamar mayunwacin
zakin da yaga nama, zame tonge dinsa yai daga cikin bakinta ya shiga manna mana mayataccen kiss tun
daga kan wuyanta har izuwa saman big boobs dinta da suke acike fam, ƙoƙarin 6alle hannun bra din yayi
asusuce yakai hannu zai yi grabbing dinsu kamar daga saman Yaji ta bangaje shi da ƙarfin gaske har sai da
Ya faɗa kan mattress din, da sauri ta maida bra din ta gyara wuyan rigarta daya kwale mata, idanuwanta
sun kaɗa jawur sun ƙanƙance fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin sai faman huci take yi alamun 6acin
rai.

Lumshe idanuwansa yayi tsabar takaici da ƙululun baƙin cikin da yaji na katse mashi enjoyment dinsa da
ta yi ne yasa shi fitar da ruwan hawaye suka soma gangarowa saman kuncinsa, muryarshi ƙasa ƙasa ya
furta

"Meyasa za ki yi min haka? Kin hana ni jin daɗin rayuwata sai kace ba mijin ki ba, gaba ɗaya kin juya min
baya ta 6angaren bani hakkina, Saratu ba ki yi min adalci sai naci wahala kafin nake samu ki bani haɗin kai,
ada ba haka ki ke yi min ba kin canza, Idan laifi nayi maki ki faɗamin mana" zuciyarshi na tafarfasa ya ƙare
maganar.

Gaba ɗaya abincin Ya fita aranta, yunƙurin amai ta soma yi da gudu ta nufi toilet ta shiga, ranshi ya
6aci gani yake kamar don saboda kiss din da yayi matane yasa take yin amai saboda tana ƙyamar shi.

Daƙyar Ya iya miƙewa zaune ya jingina bayanshi da headboard idanuwanshi sun kaɗa jawur, Ya rasa gane
dalilin da yasa ya gaza haƙura da ita duk irin wulaƙancin da take yi mashi, ga dukkan alamu ya manta da
abun da ya kawo shi ɗakin.

Kusan mintuna biyar kafin Hajiya Saratu ta fito daga toilet, hannunta ɗaya dafe da saitin zuciyarta, Cak ta
tsaya da tafiya ta ɗaura idonta akanshi, kamar yadda take kallonshi haka shima ya ke kallonta, ba ta yi
mamakin ganin hawayen dake akan fuskarshi ba, aranta ta furta"jarababbe kawai" a fili kuma tace"dama
ka shigo ɗakin ne donka takura min da jarabarka ne"? Meyasa ita wadda ta taya ka kwana adaren jiya bata
biya maka buƙatarka ba? Kai ne fa da kanka ka faɗamin cewa tafi ni Iya tarairayar miji ko ba haka ba"? Ta
faɗa tana jifar da shi da harara.

Dafe kanshi yayi da hannu ɗaya, sai yanzu ya gane dalilin dayasa tayi mashi wulaƙancin nan, Kishi ne ke
damunta, duk da yasan bata gasgata abun da ya faɗa mata ba.

Cikin sanyin murya yace"kin 6ata min rai jiya shiyasa na faɗa maki hakan saboda kiji abunda naji, amma
ba dagaske nake ba, duk da baki ƙaunata ni bazan iya haɗaki da wata ƴa mace ba, saboda ke kaɗaice acikin
zuciyata har abada, shiyasa nake haƙuri dake duk wulakancin da zakiyi min bazan iya cin amanarki ba......."
Yana magana hawaye na cigaba da wanke fuskarshi.

Duk irin zafin da ta ɗauka sai taji jikinta yayi sanyi, lokaci ɗaya tafara sassauta fushin fuskarta, koda Pravin
Ya fahimci raunin da zuciyarta tayi sai yai amfani da wannan damar ya ƙara sanyaya muryar shi haɗi da
marairai ce mata fuska Yaci daga da cewa"bansan meyasa ki ke son 6ata min rai ba, burinki ki ƙuntata min,
bayan ba haka mu ka yi wa juna alƙawari ba, kada ki manta Saratu, ƙaunar da nake yi maki itace tasa nabar
dangina saboda kin nuna baki ra'ayin zama a india ahaka na amince na biyoki Nigeria, kuma na zauna a
family house dinku saboda kin buƙaci kinfi son zama tare da ƴan uwanki, babu irin gorin da ba'ayi min ba
akan ina zama gidan surukaina amma saboda son da nake yi maki yasa na jure duk wani wulaƙancin da
nake fuskanta, naci gaba da zamana, har muka tara zuri'a, ban ta6a buɗe baki na faɗa ma wani cewa bada
son raina nake zaune gidan surukaina, ke ce ki ka nuna kina so ni kuma saboda ƙaunar da nake yi maki yasa
nake yi maki biyayya" dakatawa ya ɗanyi da yin maganar yana binta da kallo, tsantsar nadama yake gani
akan fuskarta.

"Idan naga dama zan Iya sakin ki, In kama gabana saboda ni ban dogara dake ba, da Allah na dogara ki
daina tunanin dukiyarki take sanyawa ina atare dake ba haka bane ko ɗaya, Ni ƙaunarki nake yi don Allah
ba don wani ba in ba haka ba ai da tuni na koma ƙasarmu".
Ƙafafuwanta ne suka Gaza ɗaukarta, a daddafe ta nufi mirror chair ta zauna akai tana fuskantar shi.

"Saratu ki faɗamin kin daina sona ne"? Yanayin yadda yayi mata maganar, ba ƙaramin karya mata zuciya
yayi ba.

Runtse idanunta ta yi, ita kanta ta rasa gane meyasa take yi mashi haka? kuma a yadda ta ke jin shi babu
abun da ya canza na daga ƙaunar da take mashi.

Jin motsin shi yasa tayi saurin buɗe idanuwanta, saukowa yayi daga kan gadon ya nufi ƙofar fita daga
ɗakin Yana share hawayen shi da hanky.

Har ya ruƙo handle din ƙofar Aranshi yana Allah Allah ta dakatar dashi yaji ta ambaci sunanshi"Pravin"
shu'umin murmushine ya bayyana akan fuskarshi, a hankali take tafiya tana tunkararshi, da sauri ya 6oye
murmushin fuskarshi Ya juyo yana dubanta tamkar mai fama da ciwon ido, unexpected tayi hugging dinshi
ta zagayo da hannayenta saman bayanshi, muryarta ƙasa ƙasa ta furta"I'm really sorry, my hubby. I've
realized my mistake, and I won't hurt you any more"

Kwantar da kanshi yai kan kafaɗarta Ya zagayo da hands dinsa ya ruƙo waist dinta, yaushe rabon da yaji
ɗumin jikinta haka harya manta sosai yayi tighting ɗinta, Yana shaƙar ƙamshin turaren jikinta, bai ta6a
tsammanin zaiyi nasara akanta ba, sai gashi cikin sauƙi ya yaudareta da kalamansa.

"Ki yi min alƙawarin ba zaki ƙara 6ata min rai ba? sannan zaki dinga bani haƙƙina akai akai, duk time dana
buƙace ki" ya faɗa batare daya raba jikinshi daga nata ba.

"Bazan iya yi maka alƙawari ba, kasan ɗan adam ajizine, dole wata rana mu samu sa6ani bawai fatan
hakan nake yi mana ba, but in sha Allah zanyi ƙoƙarin ganin na kawar da duk wani abu da zai 6ata maka
rai"

Ƙara ƙanƙameta yayi, hada manna mata kiss kan kafaɗarta.

Tsawon mintuna kafin ya raba jikin shi daga nata, Ya ruƙo hannunta acikin nashi, fuskokinsu ɗauke da
murmushi.

"Ina fata kanka bai yi maka ciwo, naga idanunka sun kaɗa jawur"
"Kada ki damu, dama kece damuwata kuma Alhamdulillah yanzu komai ya wuce tun da kika kar6i laifin ki,
fatana shine Allah Ya dawwamar da zaman lafiya a tsakanin mu"

"Ameen my husband" daɗi yake wai yau shi hajiya saratu take kira da hubby da kuma sunan mijinta, Ya
manta when last yaji hakan daga gare ta.

Janyo hannunshi tayi"ka dawo mu zauna mu ci abinci a tare, nasan kana jin yunwa"

Girgiza mata kai yayi"no bana jin yunwa my wife" ya faɗi hakanne saboda cikinshi acike yake, Hajjaty ta
bata shi lafiyayyan abinci yaci ya ƙoshi babu yunwa atare dashi.

"Namanta ban faɗa maki ba" a hanzarce ta kalle shi tana jiran jin ƙarashen zancen
"Game da abun da ya faru jiya, dangane da shigowar maciji gidan nan........" a tsanake Pravin Ya labarta
mata komai, hatta ƙaryar da yayi masu Senate Lateef bai 6oye mata ba, a ƙarshe yace"na faɗi masu
hakanne donsu ɗauki abun serious, saboda bana son abunda zai cutar min dake da kuma ahlinki, shiyasa
nayi masu ƙaryar cewa kin kwana idonki biyu"
Tun da ya fara maganar, Yanayin fuskarta ya canza zuwa 6acin rai, a ruɗe ta furta"Wai kana nufin yaya
Hateem shi ya tura da jet aka dauko sheikh imam from sudan to Nigeria? Sannan shi macijin dama mutun
ne!? Kuma a gidan Owais dake acikin estate din nan Yake zaune....." Hankali amatuƙar tashe ta furta
maganar.

Jinjina kai pravin Yayi"ƙwarai kuwa duk abunda kika ji na faɗa maki dagaske ne, yakamata mu ɗauki
tsastsauran mataki idan ba haka ba owais da prime minister zasu ja mana bala'e garin son taimakonsu, In
ba haka ba taya zasu taimaki Yaron dake canza halitta Ya koma Maciji? Ni dai nafi tunanin wasu miyagunne
daga cikin abokan hamayyar Jam'iyar su baba Obie suka shirya maƙarƙashiya donsu kashe baba, shiyasa
macijin Ya faɗo gidan nan maimakon sauran gine ginen dake akusa da gidan owais din......" a firgice hajiya
Saratu take faman zazzare idanunta duk tabi ta ruɗe, maganganun da Pravin Ya faɗa mata sun yi matuƙar
yin tasiri Acikin Zuciyarta, Jiki na 6ari ta nufi ƙofa zata fuce don taje ɗakin baba obie, Ko mayafi babu
akanta, da sauri pravin ya ruƙo hannunta a haushine ta juyo tana kallonshi.

"Bari in ɗauko maki mayafi," ya faɗa tare da sakin hannunta, Ya juya cikin takun sauri ya nufi closet dinsu,
jim kaɗan Ya dawo hannunshi ruƙe da mayafinta Ya lullu6a mata shi akanta, da sauri ta fice daga ɗakin.

Fitarta keda wuya Pravin Ya tuntsire da wata irin mahaukaciyar dariya mai matuƙar razanarwa sautinta
tamkar ba daga bakin shi take fitowa ba.

Lokaci ɗaya ya haɗe fuskarshi tamkar bai ta6a yin dariya ba, Ya juya cikin ɗakin Ya nufi gaban mirror Ya
tsaya yana kallon fuskarshi, kafin Ya zura hannu ya zaro wayarshi daga aljihun suit dinsa.

Pressing dinta ya soma yi, kafin Ya kara wayar a kunne.

da kakkausar Murya Ya furta"mugun Bawa komai yana tafiya yadda muka tsara!!!

Yana ƙarasa faɗar hakan, Bai Jira amsar da mutumin zai bashi ba yai rejecting call din, akan mirror Ya
ɗaura wayar, ya juya da sauri ya fuce daga dakin yabi bayan hajiya Saratu.

*💋UNAISAH❤*

Idan muka koma 6angaren Unaisah tamkar mai gadi haka ta tsare Danish, duk wani motsinshi akan
idanunta, a yanzu haka tana daga kwance gefenshi ta ɗaura kanta saman chest dinshi, ta aza hannunta
saman flat stomach dinsa ta natsu tana shaƙar ƙamshinsa, sai faman lumshe idanunta take yi wani irin
bacci ne ke ƙoƙarin fisgarta, lokaci yana ta tafiya ba tare data ankare ba ko sallah bata yi ba, gaba ɗaya ta
shagala ta saki jikinta, ba zato ba tsammani tajiyo muryar babban mutun Yana faɗin"Allah Yasa ya farka"
rass taji gabanta ya faɗi, da ƙarfi ta ware manyan idanuwanta tare da yin wuff ta miƙe zaune tana kallon
glass door din a hankali ƙofar ta soma zugewa, a hanzarce ta rarrafa ta faɗo daga saman gadon ta shige
cikin labulan ɗakin ta la6e kamar wata 6arauniya, jikinta sai kerma yake yi kamar wadda tayi ma sarki
ƙarya.

Gaba ɗayan su ne suka shigo ɗakin tun daga kan Prime minister, sheikh Imam, chief owais, Big guy da
salsabeel sai Boss Man, a bakin gadon nashi suka dakata da yin tafiyar idanuwansu akan Danish dake a
kwance.

Unaisah dake a la6e bayan labule zuciyarta ce ta soma bugawa tunawa da ma6allin rigarshi data bari a
buɗe, tasan zasu iya gani kuma zasu gane wani ya shigo ɗakin, sai faman cizon yatsanta take yi, tayi
danasanin shigowa ɗakin.
"Har yanzu bai farka ba ko"? Prime minister ne yayi maganar Yana duban fuskar salsabeel.

"Eh Yalla6ai, amma idan kana buƙatar Ya farka sai atada maka shi, Inyaso daga baya sai ya koma baccin"

"A'a banaso na takura mashi, zan jira har zuwa lokacin da zai farka"

da mamaki akan fuskar Boss man yace"ya akai ma6allin rigarshi suka cire"? Sai da ya ambaci hakan su ka
yi saurin kai idanuwansu kan Ƙirjinshi dake a buɗe, lamarin Ya ɗaure masu kai.

"Ko Shi ya buɗe da kanshi? Ko wani ne Ya shigo" Prime minister ne yayi tambayar da alamun ruɗu akan
fuskarshi.

Sheikh Imam Yace"bana tunanin shi ya buɗe da kanshi, sai dai wani iko na Allah ko kuma wanine Ya shigo
ɗakin bayan fitar mu"

"Wanene zai shigo? Yaran gaba ɗaya na tattarasu a ɗakinsu Unaisah, Ummi tana aɗakinta, babu yadda
za'ai ma ta Iya ƙetare Iyakarta, Ƴan uwansu maza kuma tare dasu muka tafi masallaci balle ace ko sune
suka shigo" big guy ne ya kora jawabin.

Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba Chief owais da baice komai ba, A hankali yake bin ɗakin da kallo kafin
Ya sauke idanuwanshi kan bedsheet din gadon dake a yamutse alamar wani ya hau gadon.

"His bedsheet is squeezed. which means someone came into the room after we left," chief ne ya furta
maganar, nan take suka kai dubansu ga zanin gadon, Ya yamutse sosai.

"Amma wanene Ya shigo" Acewar Boss,"Karfa ace wani mugun abunne"


Damuwace ƙarara akan fuskar Prime minister, ya dubi Shiekh Imam dake a gefenshi"Ni dama hankalina
bai kwanta ba tun da muka tafi masallaci muka barshi shi kaɗai a ɗakin"

Cikin kwantar da murya sheikh Imam Yace"In sha Allah babu abunda ya faru dashi, Ina da tabbacin hakan"

Shiekh Na rufe baki Big guy yace"Sir, please give me a chance to check the CCTV footage, that way we'll be
able to find out if someone else entered the room.( Ka bani dama in bincika cctv footage, ta hakan zamu
Iya gane wanda ya shigo ɗakin idan har mutunne")

Shiru Chief Owais Ya ɗanyi har Ya buɗe baki zai bashi amsa karaf idanuwanshi suka sauka akan labulan
dake lilo Yana mutsi nan take Ya fahimci mutunne Ya la6e aciki

"There's no need to check the CCTV."

Ya faɗa tare da ɗaga Voice dinsa Ya furta"Come Out!"

Rass taji gabanta Ya faɗi, duk da ranta bai bata da ita Yake yin maganar ba.

"I'm commanding you to come out from behind the curtains. Don't make me repeat myself," babu wasa
akalamansa.

Jin wannan maganar yasa gaba ɗayansu su ka kalli direction din da chief owais Yake kallo, Tsantsar
mamaki ne akan fuskokinsu ganin labule Yana motsi.
"Amma koma wanene wannan jikinshi zai gaya mashi, kayi kuskuran shigowa ɗakin nan" big guy ne ya
furta maganar.

Prime minister kuwa Ya ƙura ido Yana jiran ganin wani me ƙarar kwanan ne.

Tsawa Boss man Ya daka da karfi tare da fadin"zaka fito ko sai mun harbe ka da harsashin bindiga"

Ƙiris Ya rage ta saki fitsari a wando, tuni ta haɗa uban gumi, jikinta ya hau yin kerma, ita da ba mai laifi ba
amma ta firgita kanta, hakanan ta tsinci kanta da jin faɗuwar gaba, gani take kamar in suka kamata a ɗakin
zasu zargi wani abu, kodan saboda ma6allin jallabiyarta data cire masa, zasu iya tsammanin da wata
manufar tayi hakan.

"Bawan Allah ka fito salin alin ka bayyana kanka tunkafin mu fusata" acewar big guy, shiru babu alamun
na cikin labulan zai motsa.

Moving quickly Chief Owais Ya nufi labulen yayin da yake nannaɗe hannun Rigar shi, har ya miƙa hannu zai
damƙi wuyan mutumin ta cikin labulen muryar Boss man ta dakatar da shi.

"Sir, Unaisah ce," cak Ya tsaya tare da juyawa yana kallon Boss, gaba ɗaya mutanan dake a ɗakin shi suke
kallon cike da mamakin taya akai yasan wanene.

"Raina ne ya bani itace, kuma ita kaɗaice zata Iya shigowa ɗakin nan don ta duba ɗan uwanta" Ya faɗa
tare da ɗaga muryarshi ya furta"Unaisah come out" A hankali kowan nan su Ya ɗaura idanuwanshi kan
labulen.

Janye labulen tayi ta fito tana faman zare gray eyes dinta, nauyin haɗa ido dasu taji da sauri ta duƙar da
kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.

"Jari mai kasada, da ace kinbari chief ya shaƙi wuyanki sai dai ki ganki a Emmergency room" Big guy ne
yai maganar da zolaya, gaba ɗayansu suka saki murmushi, prime minister yace"idan na fahimta wannan
itace Yarinyar nan ko" Ya faɗa idanuwanshi akan fuskarta, Boss Man yace"itace My daughter"

Sheikh Imam Yace"Tabarakallahu ahsanul khaliqin, zonan ƴata mu gaisah" yai maganar tare da miƙa mata
hannu.

ɗagowa ta ɗanyi ta kalli chief dake a gefenta, face mask din fuskarshi Ya hana ta ganshi da kyau, sai dai
kyawawan idanuwanshi.

Tana faman zazzare idanuwanta haɗi da ƙyafƙyaftasu ta nufi sheikh iman, ta ɗaura hannunta asaman
nashi daya miƙa mata.

"Unaisah ko"? Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh.

"Meyasa kina ji muna magana ki ka yi shiru baki tanka mana ba kamar wata mai laifi, ai ba wani abu bane
don kinzo duba ɗan uwanki"

Shiru tayi bata ce komai ba, duk ta kama kanta kamar wadda tayiwa sarki ƙarya.

"Zonan surukata" prime minister ne ya kirata, da sauri ta wurga eye balls dinta kan fuskarshi rass taji
gabanta Yai mugun faɗuwa, har saida ta zaro ido waje ta saki baki tana kallon ikon Allah, duk sun fahimci
dalilin ruɗawarta.

da sauri ta kalli Boss man ta kuma kalli Salsabeel dake atsaye fuskarshi ɗauke da murmushi
"Baki ji Yana magana ba? Kije ku gaisah" acewar Salsabeel
Zuwa tayi gaban prime minister ta tsaya muryarta adabarbarce ta furta"Ina kwana,"

Murmushi yasakar mata Ya ɗaura tafin hannunshi saman sumar kanta


"Ba ki yi breakfast bane? Ko baki duba time ba, Naji kina fadin Ina kwana bayan rana tayi" cikin kulawa
yayi mata maganar.

Muryarta kamar ta salihar baiwa ta furta"mantawa nayi,'

"Okey, surukata Ina fata kina lafiya"?

"Lafiyalou"

"Naji dadin haɗuwa dake, ke fa"?

Ɗaga mashi kai tayi"nima"

"Unaisah" Boss ne ya kira sunanta, ta juya tana kallonshi.

"Sunan shi prime minister, uncle na chief namu, kuma shine ya kira sheikh Imam don Ya duba lafiyar ɗan
uwanki"

Da sauri ta maida kallonta ga prime minister, farin cikin yasa taji hawaye sun cika mata idanuwanta,
miryarta na rawa ta furta.

"Mun.... gode, Ubangiji Allah yasaka maka da gidan Aljanna, kamar yadda ka sanya mu farin ciki kaima
Allah Ya faranta maka, In sha Allah duk idan nayi sallah zanyi maka addu'a'.

Murmushi kowan nan su yasaki, musamman prime minister har cikin ranshi yaji daɗin kalamanta.

"Nagode surukata,"
Juyawa tayi da sauri ta dubi sheikh imam.

"Baba mungode, Allah ya saka maka da mafificin Alkhairinsa" addu'o'i ta dinga yiwa sheikh imam,
Fuskarshi ɗauke da murmushi Ya shafa sumarta da hannun shi tare da cewa"Nagode da addu'arki agare ni,
kina da kaifin basira, kuma kina da hankali, Iyayenki sun baki Tarbiya, Allah yayi maki albarka tare da
sauran ƴan uwanki" amsa mashi tayi da ameen, haƙiƙa taji daɗin kalaman sheikh imam, ƴan hawayen da
take 6oyewa cikin idanuwanta tuni sun fara gangarowa kan kuncinta.

"Unaisah, saura chief namu, yakamata kiyi mashi godiya" Boss Man ne ya faɗa yana nuna mata shi,
tamkar mai jin shakkar shi ta juya tare da ɗaura idanuwanta kanshi, Yana daga tsaye ya goya hannayenshi
on his broad chest, harta ɗaga ƙafa zata nufe shi Big guy yai hanzarin dakatar da ita ta hanyar yi mata
Magana.

Nufota yayi adai dai bayan ta ya dakata tare da duƙo da kanshi saitin kafaɗarta Yayi mata raɗa.

"You don't need to thank him, saboda baya so, but be kind to him. If you give me the chance, I'll guide
you.

Cikin sanyin murya ta amsa amshi da toh.


"Good Girl," Ya ambaci hakan tare da ɗago da kanshi, babu wanda yaji me suke tattaunawa.
Boss Man Yace"Unaisah zoki wuce ki tafi ɗaki ki yi sallah, Yanzu za'a kawo maku lunch ɗinku" amsa
mashi tayi da toh, kafin ta nufi ƙofar room ɗin ta fuce da sauri.

Kafin wani ya kuma yin magana acikinsu, Danish dake akwance Yaja dogon Numfashi, Yatsun ƙafarshi
suka soma yin kerma da na hannayensa nan take suka fahimci ya farka daga bacci, wani irin annurin farin
cikine Ya bayyana akan fuskar prime minister.

Salsabeel Yace"Ya farka, Yakamata akawo mashi abincin Yanzun"

"Wani kalar abinci zai Iya ci"? big guy ne ya tambaya.

"Abinci mai ruwa zaifi yi mashi sauƙin wuce wa ta maƙoshi, don bazai Iya tauna abu mai tauri ba"

"Okey, bari naje na kawo mashi" big guy ya faɗa tare da juyawa a hanzarce ya fuce daga ɗakin.

Fitarshi keda wuya, Wayar Chief ta fara Ringing, gaba ɗaya suka ɗago suna kallon shi
Prime minister yace"Wanene ke kiranka"
Curo wayar yayi daga aljihu Ya duba screen din kafin Ya bashi amsa da cewa"Dad Lateef ne"

"Okey, idan kana buƙatar ka shirya kafin mu tafi can gidan ka tafi ɗaki, in sha Allah kafin ka dawo na
kammala bashi abincin mu sai mu fara zuwa gida"

Chief ya furta"okey," kafin ya juya ya nufi room door din, bayan fitarsa

Sheikh Imam Yace"atare zamu tafi gidan baban naku, Inason in gaishe da aminina da sauran mutanan
gidan"

Prime minister Yace"Toh,"

Shigowa ɗakin Big guy yai hannayen shi a ruƙe da tray madaidaici, kan carpet din gefen gadon Ya daurashi,
kafin Ya haye saman gadon Yayi ma salsabeel alamar yazo Ya taimaka mashi, atare suka ɗaɗɗago da Danish
suka jinginar da bayanshi jikin headboard din gadon bayan sun sanya mashi pillow, Yalwatacciyar sumar
kanshi ta sauko kan shoulders dinshi.

"Baba, ko zaku je gidana ka huta, kafin in kammala bashi abinci, in yaso daga baya zamu zo tare da Chief
owais, sai mu wuce gidan baban"

Jinjina kai Sheikh Imam Yayi, Hakan yayi nima inaso in canza kayan jikina, Wa zai kai ni gidan"?

Big guy yace"Aikina ne wannan" ya faɗa tare da saukowa daga kan gadon, Yace da sheikh su tafi Ya sauke
shi a mota, Sallama sheikh Yayi ma Prime minister kafin fitarshi saida Ya faɗa cewa idan sunga wani abu
badai dai ba dangane da Danish su kira shi awaya su sanar da shi.

Prime minister Ya amsa mashi da toh haɗi da yi mashi godiya, bayan fitarsu, wayar boss tayi ringing, da
sauri ya zaro daga aljihu, sunan chief ne ya bayyana akan screen din da sauri yai Ya kara wayar a kunnanshi.

Bayan sun kammala yin wayar Ya dubi Salsabeel.

"Chief Yace ka koma gida wurinsu khadeeja" Amsa mashi yayi da toh,
"Yalla6ai zan wuce, In sha zuwa gobe zan shigo in ƙara duba jikinshi" cikin girmamawa yayi maganar Yana
duban Prime minister
Fuskarshi asake yace"Allah yakaimu Lafiya, Amma nayi tunanin kaima agidan nan kake zaune"
Salsabeel Yace"a'a, gidanmu daban, Ina kula da sauran Ƴan uwanmu ne"
"Akwai sauran Yaran kenan bayan wanda ke acikin gidan nan"?
"Eh yalla6ai"
"Allah ya tayaku ruƙo, Sai Allah Yakaimu"

"Ameen" ya fada tare da kallon boss yayi mashi sallama.

"chief yayi magana da Jami'in da zai yi driving dinka, Yana awaje Yana jiranka"
Amsa yayi da toh, kafin Yasakai Ya fuce daga ɗakin.

Ya rage saura prime minister da Boss man sai Danish da ke asaman gadon.

"Yalla6ai zan taimaka maka mu bashi abincin"


Prime minister yace"Okey,"
Boss man ne ya ɗauki tray din abincin Ya ɗaura shi daga gefen gadon, Ya ɗauki robar madara Ya cire murfin
a cup ya tsiyaya madarar, kafin Ya miƙa ma prime minister yasa hannu ya kar6a haɗi da furta mashi thanks.

Abaki ya kanga ma Danish sai dai yaƙi buɗe bakin ya rufe shi gam.

Ajiye robar milk din boss yayi, tare dakai hannu ya ruƙo la66ansa ya buɗe mashi baki daƙyar, a hankali
milk din take shiga bakinshi hankalin prime minister ya kwanta ganin yana swallowing dinta, duka ya
shanye, murmushi yasaki yana kallon boss man yace"naji dadi daya sha, ka ƙara mashi da yogurt"

Martanin murmushin Boss yayi mashi kafin ya kar6i cup din ya zuba mashi yogurt ya miƙa ma hateem,
cikin ikon Allah danish ya shanye, sai da ya tabbatar daya cika mashi cikin shi tukunna yace.

"Bari nabarshi haka, kada naci ka mashi ciki," Hateem ne ya faɗi hakan idanunsa akan fuskar Danish wani
irin kallon so da ƙauna yake jefa mashi.

Sauke tray din boss yayi kan carpet, kafin ya ɗago yana kallon hateem daya ƙurawa danish ido kamar mai
karanto wani abu akan fuskarshi, tun ɗazu yake ta son ya tambayeshi wani abu sai dai ya kasa, gani yake
kamar raini ne yayi magana da mutun mai babban muƙami irin Hateem.

Daurewa yayi muryarshi da alamun jin shakkar furta maganar yace"yalla6ai..." kallon da prime minister
yayi mashi ne yasa shi saurin haɗiyar maganar.

Murmushi ya sakar mashi tare da cewa "I'm listening to you, and I heard you mention my name. Why did
you go silent? Is there something you want to tell me?"

Sunnar dakai ƙasa Tajo yayi"bakomai subul da baka nayi wurin furta sunan"

"Ban yarda ba, please tell me what you want to talk to me about. Kada kaji nauyin yi min magana, I'm a
human being like everyone else."

Da sauri boss ya ɗago da ido ya kalleshi, haƙiƙa yana matuƙar mamakin sauƙin kan prime minister Hateem,
tun da yake arayuwarshi bai ta6a tsammanin akwai wata rana wadda zato zo har ya sami damar ganawa da
shugaban ƙasar Nigeria sai gashi cikin ikon Allah ya haɗu da mutun bai ruƙe da babban muƙami na
shugaban ƙasar canada ƙasar da tana ɗaya cikin Manyan ƙasashen duniya da suke da tarin jama'a da
wadatar arziƙi...

Yayi zurfi acikin tunaninshi muryar prime minister ta katse shi"kayi shiru baka ce komai ba,"
Sosa ƙeya ya ɗanyi da hannunshi kafin ya furta"am....dama yalla6ai tambayace nakeso nayi maka idan ka
bani dama, amma dan Allah kada ka ɗauka da wata manufa"
Da fara'a akan fuskar Hateem Yace"kada hakan ya dame ka, Nifa ɗan siyasane, tambayoyi har marasa kan
gado ƴan jarida sunayi min kuma in basu amsa dai dai dasu, ballanta kuma kai dana yaba da hankalin ka,
duk mutumin da Owais ya yarda dashi toh nima na yarda dashi, don haka kada kaji komai na baka damar yi
min kowace irin tambaya ce"

Ajiyar zuciya boss man ya sauke, har cikin ranshi yaji dadin kalaman prime minister, kuma ya ƙara jin
ƙaunar mutumin aranshi.
Sai dai duk da haka nauyin shi yake yi, daƙyar ya iya buɗe baki yace"yalla6ai, naji kamar ance baka ta6a
haihuwar ɗa namiji ba, ƴa'ƴan biyu duka mata ne shin dagaske ne"? Boss Na ƙare maganar yayi saurin kau
da idonshi gefe ɗaya saboda kunyar tambayar da yayi mashi

Shiru prime minister ya ɗanyi, na ƴan mintuna yana maimaita maganar taj acikin zuciyarshi, yayin da yake
kallon fuskar danish

"Am sorry Sir, idan tambayata ta 6ata maka rai" acewar Tajj.

Calmly Hateem Ya soma magana ba tare da ya kau idon shi daga kan fuskar Danish ba.

"Ka fama min raunin da yake kwance acikin zuciyata, tsawon shekaru da suka gabata, bana son tuna
haukan da nayi, da hawayen dana zubar, da kuma ƙunci da raɗaɗin dana fuskanta saboda rashin da nayi na
abun da na ƙwallafawa rai........" tuni yanayin fuskarshi ya canza zuwa matsananciyar damuwa, yayin da
yake yin maganar farin ruwane kwance acikin fararen idanuwanshi.
Hatta tajj dake sauraronshi, Jikinshi yayi mugun yin sanyi tunkafin Ya ƙarasa jin zancen nashi
Numfasawa prime minister yayi before saying"I've lost so much that I still haven't forgotten him. I loved
him more than I love my children now, and I've never stopped missing him. I know if I tell you that, you'll
think it's crazy." He said it with a smile on his face.

("nayi babban rashi da har yau bana manta shi, inason shi fiye da ƴa'ƴan da nake dasu a yanzu, kuma har
yau ban ta6a cire shi araina ba, nasan idan na faɗa maka zaka ji abun wani iri" ya faɗa fuskarshi da
murmushi.)

"Bayan gimbiya mujeedat ta yi haihuwa ta biyu ta haifi Yazrin, a ƙalla ta ɗauki shekaru bata sake haihuwa
ba, tunda Allah ya bani ƴan mata har biyu, sai na ƙwallafa rai ga son samun ɗa Namiji har tsakar dare
inayin nafilfili akan Allah ya bani ɗa namiji, cikin ikon Allah a lokacin da banyi tsammani ba, Allah ya kar6i
addu'ata, Matata ta samu ciki a daren ranar ko runtsawa banyi ba.. though I wasn't sure if it was a girl or a
boy, nidai kawai nasanyawa raina namiji ne.." dakatawa yaɗan yi da yin maganar, tajj ya natsu yana
sauraronshi, tun yana daga tsaye har dai yakai ga janyo kujerar gaban mirror ya ajiyeta daga gefen gadon
ya zauna yana kallon prime minister.
Cigaba da magana yayi"tun kafin a haife shi na fidda mashi suna, na tsara mashi kalar rayuwar jin daɗin da
zaiyi, hatta makarantar da zan sanya shi da komai ma na rayuwarshi sai da na rubuta a diary din dana ajiye
domin shi kawai, ita kanta gimbiyata mamaki ta dinga yi ganin yadda na haukace akan son abunda ke
acikinta, har fadi take yi na fahimci kafi sonshi akan sauran yaran dana haifa maka, idan ta fadi hakan sai
dai nayi murmushi, ba ita kadai ba hatta family dina na Canada dana Nigeria sai da suka shaida ƙaunar
dana ke yi mashi, duk rana ta Allah saina kirasu awaya nace su tayani da addu'a Allah ya sauki matana
lafiya, saida na addabi kowa da zancen cikinta, mahaifina har tsakar dare nake tada shi daga bacci ince
mashi ya tashi yayi nafila ya taya matana da addu'a......" shiru ya ɗanyi idanuwanshi akan agogon
hannunshi.

Tajj duk ya ƙagara da sonjin ƙarashen zancen.

"Ban ta6a kawowa raina cewa yaron zaizo duniya amace ko zai mutu bayan an haife shi, kana Naka Allah
Yana nashi, sai gashi an haife shi babu rai, wallahi bazan iya misalta haukan da nayi ba a asibitin da ta
haihu, likitan daya fara furta mun zancen an haifi yarona babu rai da hannu biyu na cakumi wuyan rigarshi
na shaƙe shi tamkar zan kashe shi daƙyar dangina suka raba ni dashi, na dinga yi masu sambatu ina fadin
karya sukeyi min ni yarona bai mutu ba da ranshi, daga ni har mahaifiyarshi ba'a bari munganshi ba, ita
bata acikin hayyacinta bacci takeyi, ni kuma an hana in ganshi gudun kada in haukace masu saboda sun
fahimci na mutu akan ƙaunarsa, tun bayan 2 weeks da faruwar lamarin, Ina kwance gadon asibiti Ina jinyar
zuciyata, duk na fita hayyacina sai sambatu nake yi ina fadin ina yarona baba kana gani za'a raba ni dashi,
ni nasan ɗana bai mutu ba, baba ina jin bugun zuciyarshi acikin zuciyata, ire iren kalaman da nake fadi
masu ba ƙaramin raunata masu zuciya nayi ba, babu wanda bai zubar min da kwalla ba, haka suka dinga
lallashina sunayi min nasiha, daƙyar suka shawo kaina har suka samu na haƙura nabarma Allah komai sai
gashi yanzu tamkar ba'ayi ba" Prime minister Hateem ya ƙare maganar yayin da hawaye ke ƙoƙarin
gangarowa saman kuncinshi, da sauri boss man yayi saurin share mashi hawayen don bazai juri ganin
babban mutun kamar prime minister yana zubar da hawayensa akan idonsa.

"Nayi kuskure dana yi maka tambayar nan, ka gafarceni yalla6ai, ni kaina jikina yayi sanyi kuma banji daɗin
yanayin da na jefa ka ba, da ace nasan maganata zata fama maka raunin dake acikin zuciyarka wallahi
daban furtata ba" cikin sanyin murya murya Boss man Yayi maganar.

Cikin karyayyar murya yace"kada ka damu, ay yanzu komai ya riga daya wuce,"

Ƙarfin hali taj yayi wurin furta"yalla6ai ko zan Iya sanin sunan baby boy din da ka rasa"

He smiled a little before saying, "Sunanshi *OMAIR BIN HATEEM OBINNA* wannan shine sunan da nayi
niyar sanya mashi, Allah bai nufa ba"

Maimaita sunan taj yayi"suna mai daɗi, ubangiji Allah ya baka mafiyin abunda ka rasa, In sha Allah zan
tayaka da addu'a"
"Nagode sosai"

"Yalla6ai, zan fada maka wani abu, ni tunda nake arayuwata ban ta6a ganin mutun mai babban muƙami
mara girman kai irin ka, A yanzu haka da muke yin magana sai nake jin tamkar a mafarki ne

Murmushin gefen fuska prime minister ya saki jin abunda taj yace.

"Ba kai kaɗai ba, mutane dayawa suna mamakin halina, ni ta inda na banbanta da sauran, bani da girman
kai, kuma bana ɗaukar kaina wani, duk idan na tuna cewa mu dukkanmu bayin Allah ne, kuma babu wanda
yafi wani awurinshi sai wanda yafi jin tsoronshi sai in ƙara jin ni ba wani bane, idan na shiga cikin takalawa
sai in manta wanene ni, zan saki jiki dasu muyi mu'amala tamkar bani da ko sisi, haka zalika idan na shiga
cikin masu kuɗi sai inji dai dai nake da su, yanzu haka da nake atare dakai, kallon aboki nake yi maka" zaro
ido taj yayi fuskar shi da alamun mamaki.

"Ni kuma yalla6ai"

Ɗaga mashi kai hateem yayi alamar eh, wani irin farin cikine ya lullu6e Taj sai faman sakin murmushi yake
yi jin prime minister ya kira shi da sunan aboki.
A hankali Hateem Ya mayar da idanuwanshi kan fuskar Danish, ya miƙa hannu ya shafi gefen fuskarshi.

"Allah ya jarabceni da ƙaunarka, Ina fata ka zama alkhairi arayuwata, zan cigaba da yi maka addu'a Allah
Ya baka lafiya, bana so in koma ƙasar canada batare da ka buɗe idanuwanka kayi tozali dani ba" cikin
sanyin mirya ya ƙare maganar, ba zato ba tsammani yaji saukar yatsun hannun danish acikin nashi wata irin
cakuma yayi ma hannun prime minister ya ƙanƙame shi, hankalin Taj ba ƙaramin tashi yayi ba, har ya
yunƙura zai raba hannun Danish daga ruƙon da yayi ma Hateem, da sauri ya girgiza mashi kai alamar a'a,
komawa yayi ya zauna still hankalin shi bai kwanta ba, idanun shi akan hannayensu dake harɗe cikin na
juna, lamarin yayi mugun ɗaure mashi kai ganin mutumin da ko yatsan shi bai iya ɗagawa amma yayi ƙarfin
halin ruƙe hannun mai girma Hateem.

Tun da ya kafe hannun Danish dake a ruƙe da nashi da ido, bai ko ƙyafta ba, wani irin yanayi yake ji
atattare dashi mara misaltuwa, ga wani bugu da zuciyarshi take yi mashi, gaba ɗaya ya shagala da kallon
hannayensu na tsawon awa batare daya ankara da gudun da lokaci ke yi ba

Motsin buɗe ƙofar ɗakinne Yaja hankalin boss ga kallon mai shigowa, Chief Owais ne Yake nufo su cikin
shiga ta tsadaddun suit launin ash colour, wani irin sanyayyan ƙamshin turarene ke fita daga jikinsa,
tunkafin Ya ƙarasa garesu idanuwanshi suka sauka akan hannayen prime minister dake a ruƙe dana
Garkuwa, walking gently ya nufi bakin gadon ya ɗan dakata da yin tafiya, miƙewa Boss yayi tare da sarah
mashi.

"Uncle am ready, yakamata mu tafi suna jiran mu, tun ɗazu suke kira awaya" tamkar baisan furta
maganar yayi ta.

Shiru babu alamun prime minister zai amsa mashi.

Boss man ne yace"Sir, wani abu ne ya faru wanda ya ɗaure mana kai, yanzun nan kafin ka shigo Danish Ya
damƙi hannun prime minister Ya ruƙe shi sosai, ina da tabbacin shine dalilin dayasa ya shiga yanayin nan"

Ɗage girarsa yai alamar yaɗanyi mamaki kafin ya furta"Okey, kayi mashi magana ta yadda zai ji ka"

Boss ya amsa da toh, sannan ya je daga gefen prime minister yadan russina tare da cewa"Yalla6ai, Chief Ya
shigo Yana son yin magana dakai"
Tamakar bazai ɗago ba, A ƙalla sai da ya ƙara mintuna biyar cuf tukunna A hankali Ya dago da fararen
idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur da su tamkar mai fama da ciwon ido.

Zagayowa chief yayi ta 6angaren da prime minister yake a zaune Ya tsaya yana duban fuskarshi.

'Uncle are you okey," ya tambayane ganin yadda idanuwanshi suka yi ja.

Can ƙasan maƙoshi sound din muryarshi ke fita"Owais, kaga yadda ya ruƙe min hannuna? meaning, he
feels what I feel about him."

"Uncle, don't let that bother you, zamu dawo ne anjima sai ka ƙara duba shi.

Jinjina mashi kai yai ba tare daya furta komai ba, shi kanshi chief yana mai al'ajabin ƙaunar da Uncle
Hateem ya ke ma Danish.

Ganin yaƙi sakin hannun Danish, yasa shi sake furta"uncle, we ave to go" Magana chief yakeyi mashi
amma gaba ɗaya hankalinshi na akan danish, ganin babu alamun zai motsa yasa chief, ruƙo hannunshi
cikin kulawa yai mashi alamar ya tashi su tafi, yunƙura prime minister yayi da niyar ya miƙe daga saman
gadon sai dai wani iko na Allah Danish Yaƙi bari ya raba hannun shi da nashi.

Muryar mai girma Hateem na rawa ya furta"My son, Yaron nan Yaƙi sakin hannuna, baison in tafi nabar
shi"

"Uncle, kada hakan ya dame ka" chief ya faɗa, tare dakai hannu ya damƙi hanun danish daƙyar ya
6an6areshi daga ruƙon da yayi ma hannun hateem, shatun akaifun danish har saman fatar hannun prime
minister, wurin yayi ja.
Hakan ya sosa ran Chief Owais, baiji daɗin yakushin da Danish yayi mashi ba, shi kuwa Hateem ko kaɗan
baiji zafi ba, baima lura da yakushin ba.

Chief da boss ne suka kwantar da Danish, tare da lullu6a mashi bargo har saman ƙirjinshi, kafin suka bar
ɗakin, bawan Allah prime minister yana tafiya yana waiwayon ɗakin, gani yake kamar idan ya tafi bazai
ƙara ganin shi ba.

__________________________✍️

BARI MU ƊAN KOMA BAYA MUJI MEKE FARUWA A 6ANGAREN SU ARMY BOY DA TIGER.

Bayan Gari Ya waye suna akwance Saman Sofa, sun saki baki da hanci suna sharar bacci, ba zato ba
tsammani Muryar Khadeeja ta farkar da su, Daga can saman bene ta kware murya da ƙarfi tana
fadin"Wayyo Allah, Mayu sun kwanar mana agidanmu, wai ku ba zaku tafi gidan ubanku ba" A firgice Suka
farka suna faman mutsustsuke idanuwansu, kafin suka kalle ta, a lokacin harta nufi bene tana saukowa
down, Sumar kanta a hargitse babu kayan mutunci a jikinta Rigar baccin jiyace bata cire ta ba, dai dai
gwiwarta rigar ta tsaya mata, hannunta ɗaya ruƙe da qugunta, ta dambara janbaki saman la66anta har kan
kumatunta, ga wani man baki data shafa sai ƙyalli yake yi.

Kallon juna su ka yi fuskarsu babu walwala, Army boy yace"Allah ya wadaran naka Ya lalace wannan
masifaffiyar yarinyar Allah Yayi mana maganinta, saboda jaraba baccin ma bazata bari mu ƙarasa shi cikin
dadin rai ba, Ni dai harga Allah an takura min, yakamata sir ya bamu iznin komawa gida"

Takaici Ya hana Tiger cewa komai, Jira yake kawai Ta ƙaraso Yaji me zatace masu
Da gudu ƴan uwanta suka fito daga ɗakunansu, suka biyo bayanta,

A tsakankanin sofas din khadeeja ta dakata da yin tafiyar tana jifarsu da matsiyacin Kallo Tace"mayu masu
cinye ma mutane abincinsu, Yanzu sai ku girka mana abunda zamu ci" zaro ido su ka yi suna kallonta.

Mamaki take basu, A iya sanin su dayawa mata suna jin shakkar sojoji amma ita wannan mai kunnan
zoman babu alamun tsoronsu a fuskarta.

Tsawa Army boy Ya daka mata"ke karki kuskura ki ƙara kiran mu da sunan mayu idan ba haka ba zan harbe
ki da bindiga" maimakon taji tsoron maganarshi saita galla mashi harara tana fadin"Ai wallahi sai kun girka
mana abun da zamu ci, tunda kuka cinye mana sauran abincinmu na jiya"

Dafa kafadarta hawwa tayi"dan Allah ki ƙyalesu, Ki zo mu koma ɗaki, ki yi wanka ki canza kayan jikinki,"
murguɗa mata baki tayi"ni babu inda zanje, wallahi sai sun girka mana abincin da zamu ci, saboda Yunwa
nake ji"

Girgiza kai sojojin sukayi suna kallonta kafin suka kalli sauran ƴan uwan nata,
"Jiya bamu samu damar Yin magana daku ba, muna fata kun tashi lafiya"
Atare suka hada baki wurin amsa masu da lafiyalou"
Tiger Yace"Ku fada mana sunayenku muna son ji"

Namijin cikinsu ne Ya fara Yin magana.

"ni sunana MUBEEN" Jinjina kai tiger yayi"Ke fa" Ya nuna Macan dake a gefenshi, Fara ce sol tana da
kumatu da ƴar kiba
"RUBINA"
"Suna mai daɗi, Kefa mai idanuwan ƴan chaina, ya fada da zolaya yana nuna ta gefen rubina
"YASMIN SUNANA"
"Good Girl, and You " Da ido Ya nuna Ƴan matan dake ruke da hannun junansu ɗaya Doguwa ɗaya
madaidaiciya
"Ni sunana Hibba ita kuma Sarah"
"Masha Allah, Naji dadin haduwa daku, Allah yayi ma rayuwarku albarka" amsa mashi sukayi da ameen
Khadeeja masifaffiya tace"ƙwarama da baku tambaye ni sunana ba, don ba fada maku zanyi ba"
murmushi suka saki ba tare da sunce mata ƙala ba.

Bubbuga ƙafafuwanta tayi"ni dai yunwa nake ji, ku tashi ku shiga kitchen ku girka mana abinci"
Army yace"bamu Iya girki ba, Ko kin ganmu da zannuwane ɗaure a ƙugunmu?
Harara ta watsa mashi
Tiger yace"Yar uwa khadeeja, baku da maiyi baku girkine a gidan"?
Hawwa ce ta bashi amsa da cewa"yayanmu salsabeel shine yake girka mana abinci"

Zaro ido Tiger yayi"kina nufin wannan ƙaton mutumin"?

Ɗaga mashi kai tayi alamar eh


Sarah tace"ba koda yaushe yake girka mana abinci ba, yaya omar yana kawo mana daga gidan su," sun
gane wa take nufi, wato Big guy shi ne suke kira da Asalin sunan shi Umar.

Kallon agogo Army boy yai a lokacin ƙarfe goma sha biyu na safe.

"Da alama sun manta yau basu kawo maku abincin da wuri ba, Ya za'ai kenan"?

Da sauri Mubeen Yace'ai akwai yogurt da madara a frigde, hada bread a store, Idan muna jin yunwa kafin
akawo mana abinci su muke ɗauka mu ci,"

Ran khadeeja Ya gama 6aci, Bubbuga ƙafafuwanta tayi hankalinsu ya dawo kanta, idanuwanta rufe ta
soma zazzaga masu masifa tana fadin"ni wlh bazansha yogurt da bready ba, ai kune kuka cinye mana
sauran abincinmu a kitchen, wlh idan baku je kun girma min abunda nakeso ba zan kira yaya Omar awaya
in fada mashi kun ci mana abincin mu"
Aruɗe suka hada baki suna fadin"Me yai zafi, Kinji munce bazamu girka maki ba ne?

Nuna masu hanyar kitchen tayi da hannunta"ku tashi ku shiga ku dafa min abinci"

Agajiye suka miƙe tayi gaba suka bi bayanta sune har cikin kitchen.

Ƴan uwan dake a falo, saman sofa suka zauna, su kansu ba zasu Iya da rigimar khadeeja ba, Sara ce ta
ɗauko masu Robobin madara, Ta miƙa ma kowan nan su, suka zauna suna sha
Daga falo suna jiyo sautin muryar khadeeja dake acikin kitchen.

"wainar kwai zaku soya min" ta fada tare da buɗe kofar store ta dauko masu egg container ta kawo masu
shi akan Countertop ta daura shi.

Cikin kwantar da murya Tiger yace"khadeeja wannan kwan yayi maki yawa ina laifin a soya maki biyar"
harara ta galla mashi"ai bani kadai zanci ba, hada Ƴan uwana suma suna jin yunwar" roba ta ɗauko masu
inda zasu kaɗa kwan hada abun kaɗawar,
Kafin ta nufi freezer tana fadin"hada Chicken pepper soup zaku yi mana, Sannan Ku soya mana kifi mubeen
yana son ci" Bin ta da kallo su ka yi baku nan su a buɗe kamar sakarkaru haka suka bi ta da kallo.

Kaji ta ɗauko Guda Uku Manya manya masu tsokoki ajikinsu ta ajiye masu

Tace"chicken peper soup zakuyi mana, akwai kayan miya da kayan ƙamshi duk zan ɗauko maku su"
hankalinta kwance takeyi masu magana, har wani ƙyafkyafta masu idanu takeyi.
Daƙyar tiger ya iya bude baki yace"Yar uwa khadeeja, bakomai muka Iya girkawa ba, Kuma wannan
abincin yayi yawa, ga kwai ga kuma kaji"?

Zum6ura mashi baki tayi"wanda yasa kuka cinye mana abincin mu na jiya," ta faɗa tare da juya masu baya
ta nufi cikin store, gabansu har faɗuwa yake yi, Jim kaɗan ta dawo hannunta ruƙe da Manya manyan
doyoyi guda uku ta ajiye masu aƙasa tana faman yin nishi tace"idan kun gama girka wadannan saiku fere
doyar ku soya mana ita da kwai" Baki abuɗe suke sauraronta
Komawa cikin store tayi sai gata ta kuma dawowa hannunta ɗauke da ƙaramar roba, dankalin turawane
acikinta
"Chips zaku soya mana da shi" ta ajiye robar, har ta juya zata koma Army boy yayi saurin shan gabanta,
Muryarshi a tausashe Yace"khadeeja, Ya isa haka, wai ke meke damunki? Mu fa mazane ba mata ba, bamu
Iya girki ba, Bindigogi muka Iya ruƙewa, taya zaki kwaso wannan uban kayan abincin kice mu girka maki"?

Fashe mashi tayi da kuka tana bubbuga ƙafa tace"wallahi idan baku girka ba saina fada ma Yaya omar kun
cinye mana abinci, Kuma In ƙala maku sharrin kun ta6ani" Waro ido waje su kayi har saida gabansu Ya fadi
jin abunda tace, Ita kanta da tayi maganar bada wata manufa ta furta ta ba.

Lallashinta suka soma yi"shikenan, Munji zamu girka maki, Yanzu ki koma falo ki zauna, ashagwa6e tace
toh, kuma zan dinga leƙowa ina duba ku" amsa mata sukayi da toh
Bayan fitarta daga kitchen din tiger yace"Allahumma ajirni filmusibati wa aklikni khairan min ha, Yarinyar
nan ba ƙaramar makira bace"
Army boy yace'ai duk laifinka ne, kaine jiya kasa na kwaso masu abincinsu da duk hakan bata faru ba,
yanzu gashi ta daura mana wannan uban aikin"

"Idan laifina ne kaima hada laifinka ai, tunda atare muka cinye masu abincinsu"

Ran kowan nan su Ya 6aci, tamakar zasu rufe juna da bugu

"Faɗa ku ke yi ko"? Muryar Khadeeja ce ta fargar dasu, arude suka hada baki wurin fadin"A'a aunty, Muna
yanke shawarane akan meya kamata mu fara girkawa"

Murmushi ta saki har dimple dinta Ya lotsa, Hannunta ɗaya ruƙe da Robar milk da take sha.

"Idan ma faɗa ku ke yi ku kuka sani, Nidai ina jiran abinci, kuma wallahi Kafin In shanye madarar nan ku
gama min girki na, idan ba haka ba hmmmm kunsan sauran" Ta fada tare da juyawa ta fuce daga kitchen
din.

Army ya ɗaura hannayenshi biyu saman kanshi"mun shiga uku, wannan wata irin bakar rana ce"?

Tiger yace"Ba surutu Ya kamata mu tsaya muna yi ba, Mu fara mata girkin kada ta shanye madarar"

Tu6e rigunansu sukayi, Ya rage saura wandunan kakinsu a jikinsu, sham sun manta da bindigogin su da
suka ajiye afalo.

Kamar mata haka suka fara aikace aikace, wanke nama, Fere doya, Gyaran cefane, da yankan kayan lambu
suna haɗa uban gumi zufa ta ko'ina, da waya sukeyin amfani wurin yin browsing yadda akeyin chicken
paper soup da sauran abunda basu Iyaba, duk bayan ƴan mintuna sai khadeeja ta leƙo kitchen don taga
idan suna yin aikin yadda ya kamata, bayin Allah kamar ba sojoji ba, ta takura masu ta addabi rayuwarsu

Yayin da take zaune a falo cikin ƴan uwanta, Hawwa tace"khaeeja baki kyauta masu ba, dan Allah Ki yafe
masu aikin yayi masu yawa"
Gatsina mata hanci tayi batare da ta tanka mata ba
Sarah taja guntun tsoki tana kallonta tace"kinji haushin rayuwarki, kuma wallahi saina fada ma Yaya Jazz
abunda kika yi masu"
Banza tayi dasu tamkar bata ji me suke fadi ba,
Yasmin tace"please ku daina yi mata magana, Itama bayin kanta bane, Lalurace Yaya jazz fa yace mu
runka hakuri da yar uwarmu"
Hibba tace"duk da haka halintane, Deeja tafiye rashin jin magana, bata da haƙuri, saina fada ma Yaya
salsabeel"
Duk wanda yayi magana saita kalli la66ansa
Robar yogurt din dake a hannunta ta ajiye kan carpet, Ta yunƙura ta miƙe tana yin miƙa, duk suka bita da
ido, bindigar da ta gani sakon kujera takai hannu ta dauka ta saita su da ita tana fadin"wallahi dukan ku sai
kun mutu, banzaye kawai, Har ni zaku dinga yi ma faɗa"

Dariya suka saki gaba ɗayan su, saboda basu san meye amfanin bindigar ba.

Hawwa tace"dalla malama Ajiyeta a ƙasa, Kada ki lalata masu abunsu"

Harara ta watsa mata tana faman cije la66a tace"ta kanki zan fara hawwa Jiya Hada kulleni adaki don
kada In futo waje, yau idan na kashe ki bazaki sake Yi min haka ba
Tana ƙare maganar ta daddage ta ruƙe bindigar dakyau, Tana ƙoƙarin harbawa, Mubeen yayi saurin Janyo
Hawwa gefe daya, ba zato ba tsammani harsashin bindigar Ya harbi jikin kujarar inda Hawwa take zaune,
Wani irin Hayaƙi ya fita Wurin da bullet din ya shiga nan take ya fashe.(😳)

Nan fa ido Ya raina fata, Gaba ɗayansu sun rude sun gigice, Amatuƙar firgice suka mimmiƙe tsaye suna
faman zare idanuwansu
Dariya tasaki tana fadin"kunyi tunanin bansan yadda akeyin amfani da ita ba ko? To ai na ta6a ganin video
a wayar Ya omar, wasu suna kakkashe mugaye da ita, ɗaya bayan ɗaya kuma zan kashe ku yanzun nan" Ta
faɗa Tana saita su da ita, fashewa sukayi da kuka suna yi mata magiya, saboda rashin hankali Ta kara sakin
wani harsashin kaitsaye ya sauka a tsakankanin ƙafafuwan Rubina, Baiwar Allah Kuka hada majina, sauƙin
ma bai ta6a fatar ta ba.

Maza suna a kitchen suna girki, sun bar psycho afalo tana aiki, duk irin girman sautin harbin bindiga basu ji
ba, Mubeen Ne ya watso da gudu Ya shigo kitchen din ya ɗaga murya Yace"ga khadeeja can ta daukar
maku abunku tana harbin mu" gabansu ne yayi wani irin mugun faduwa, aguje suka fito daga kitchen din
adai dai lokaci ta saita kan Sarah jikinta sai kerma yakeyi

Tsawa Tiger Ya daka Mata, da sauri Ta juyo da bindigar ta saitasu tana dariya tace"Ajalin ku ne ya fito
daku daga kitchen, dama haushinku nake ji, Jiya kunkashe min jazz dina"
Hankalinsu idan yai dubu toh Ya tashi, Khadeeja ta saka su a tsaka Mai wuya, Ga girki sun baro a kitchen
Ga wani tashin hankalin dayafi gigitasu
Dole suka zube kan gwiwowinsu muryoyin su na rawa suke yi mata magiya"dan Allah Anty khadeeja ki
rufa mana asiri, wlh bamu kashe maki jazz dinki ba, Yana nan da ranshi, yaji sauƙi raunin jikinshi ya warke,
Ki taimaki rayuwarmu ki ajiye bindigarnan aƙasa....." tamkar zasu fashe da kuka haka suka dinga roƙonta,
zuciyarta kamar ta kafuran farko babu alamun sassauci tace
"Nafa san me nake Yi, baku isa ku raina min wayau ba, Idan dagaske Ya jazz bai mutu ba toh Yana ina"?
Fuska amarairaice Army boy yace"Yana asibiti, likitoci suna duba lafiyarshi,"
Ƙasa ƙasa da murya Tiger yai mashi raɗa"kai dole fa mu nemi mafita wallahi, Idan ba haka ba zata Iya
kashe mu ko ta kashe ƴan uwanta tun da ba hankali gareta ba, ga kuma Abinci mun bari kan gass"

Army boy yace"to ya zamuyi! Ni wallahi komai ya kwance min,"


"Gulmata kukeyi koh"? Ta fada tana jifarsu da harara
Atare suka girgiza mata kai alamar eh, tace"idan ma gulmata kukeyi daga yau Idan na kashe ku bazaku
sake yi ba"
"Ku lallashi yar uwarku, zata Iya ja mana bala'e daga mu har ku" Tiger ne yayi maganar Yana kallonsu
Hawwa.

Duk wanda yayi yunkurin buɗe baki zai bata haƙuri da bindiga take saita shi,
Kwatsam Wayar Tiger Ta soma Yin ringing, adabarbarce ya zura hannu ya zarota daga aljihun wandonshi,
duk sun rude, ganin sunan Major ya bayyana ne yasa hankalinsu Ya ɗan kwanta,
Picking call din yayi tare da kara wayar akunne
Ko sallamar major bai amsa ba, Ya furta"Jazz Ya Jikin Naka"? On the other hand Muryar Major da alamun
mamaki yace"Jazz Kuma? Baka ga sunan wanda Ya kira ka bane"?
Tiger bai kula maganarshi ba yaci gaba da fadin"Kamar ka sani tun safe khadeeja take son Yin magana
dakai, Ai saida na fada mata baka mutu ba lafiyarka ƙalou amma taki jin maganata"
Tun da ya ambaci sunan Jazz khadeeja ta jefar da bindigar kan carpet, ta nufe shi tana fadin"Bani shi muyi
magana" jiki na 6ari Army yayi saurin Miƙewa ya damƙi ƙeyarta yana fadin"bashi bane don ubanki, Har mu
zakija ma bala'e, masifaffiya kawai, Kin bi kin ƙuntata rayuwurmu kin hanamu sakat, wlh baki isa ba, Aɗaki
zan kulle ki," kuka tadinga yi mashi tana zagin shi, ɗaukarta yayi ya nufi saman bene da ita, Daki ya shigar
da ita ya kwantar saman gado, Ya fito da sauri yaja ƙofar Ya datse ta da mukullin daya gani ajikin ƙofar,
Ajiyar zuciya ya sauke kafin Ya nufi falon, A lokacin Tiger Ya kammala yin wayar da major, Ya miƙe dasauri
Yaje ya dauki bindigar ya hada da ɗayar da suka ajiye kan sofa, duka biyun Ya turasu karkashin dining table
Kallon sauran yaran su ka yi"ku koma ku zauna Yanzu zamu kawo maku abincin" amsa masu sukayi da toh,
Jiki asanyaye suka zauna duk basu ji dadin abunda khadeeja ta aikata ma sojojin ba
"Dan Allah kuyi hakuri Idan mun 6ata maku rai" sarah ce tayi masu maganar
Murmushin yaƙe suka sakar mata"kada ku damu, ai munyi maganinta yanzu" juyawa sukayi atare suka
nufi kitchen, abun da suka daura kan gass harya fara ƙonewa shaf shaf suka ƙarasa Yin girkin.

Khadeeja dake adaki, Sai kuka takeyi tana bubbuga ƙofa da hannunta kamar zata 6alleta, sumar kanta duk
ta rufe fuskarta
Gajiya tafara Yi da buga ƙofar, Ta Juya zata je ta kwanta karaf idanuwanta suka sauka akan Wayar dr jazz
da suka bari kasa, Ga kayanshi daya bari riga da wandon shadda, jiki na 6ari taje ta dauki wayar, duk da
bata Iya amfani da ita ba sai da tayi ƙoƙarin kunnata, saboda ta haddace Yadda jazz yake latsawa agabanta,
Cikin sa'a ta kunna wayar haskenta Ya kawo,
Gefen gado ta zauna tana yin shessheƙar kuka
Ta soma kacaccala mashi wayar, kasancewar babu password a wayar Yasa ta samu damar dannata son
ranta, batare da saninta ba ta shigar mashi contact dinsa adai dai kan sunan My Mom ta latsa Kira, Ringin
wayar ta fara Yi, Khadeeja ta natsu tana jiran jin wazai Yi magana kamar yadda taga Ana yin amfani da ita
ayi communicating

Kiran wayane Ya shigo layin Mom turai, a lokacin tana acikin bedroom dinta ita da sir mubarak akwance
saman gado, ita kadai ce idonta biyu, shi Sir mubarak Ramuwar baccin dabaiyi ba jiya yake Yi.
Jin wayarta na ruri ne Yasa ta sauko daga kan gado, taje gaban mirror ta duba sunan mai kiranta
Mamakin ƙarara akan fuskarta ganin sunan My Own Son Ya bayyana akan screen din wayarta
Murmushi tadan saki tana fadin"Allah Sarki My son, Ciwo Ya hana kazo inda nike shiyasa ka kirani awaya,
bari Naji me Yake buƙata" ta faɗa tare da ɗaga wayar ta kara a kunnanta, hada ƙoƙarin yin sallama.

Shessheƙar kukan Khadeeja ne Ya fara cika kunnanta, Zaro ido waje turai tayi muryarta da alamun ruɗani
ta furta"Wacece ke kuka"?

*Daga Alƙalamin Boss Bature🫶*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426
First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida*_~*✊💋BOSS
LADIES WRITERS✊💋✊*~_

_🔥💫THE PRISONERS🔥💫_

~TAKUN ƘARSHE~

Daga Alƙalamin Boss Bature

Dedicated To Aunty Kubra💋

_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty
❤._

_______________________✍️

Shessheƙar kukan Khadeeja ne Ya fara cika kunnanta, Zaro ido waje turai tayi muryarta da alamun ruɗani
ta furta"Wacece ke kuka"?

"Khadeeja ce, Ina Jazz ɗina Yake" kafin Turai ta bata amsa kiran Ya katse, abun ya ɗaure mata kai, Ya akai
wayar Jazz taje hannun mace? Maimaita sunan khadeeja tayi aranta kafin da sauri ta fito daga dakin ta nufi
bedroom dinsa.

A lokacin suna daga zaune gefen gadon shi, Shi da Ibad dake bashi abinci abaki, hannun ibad ruƙe da plate
with spoon, har yayi wanka ya sanya jallabiya a jikin shi.

Shigowa mom Turai tayi dakin gaba daya suka dago suna kallonta.

Ajiyar zuciya ta sauke fuskarta da fara'a ta ce"My son, how's your body? I hope you're getting better
now."

In a cool voice yace"Mom da sauki, ina samun kulawa a wurin ƴan uwana, yaya Zaki ma bai jima da fita
ba"

Murmushi tasaki tana kallon Ibad tace"our last born, Sannu da ƙoƙari, kana Ji da ɗan uwan nan naka"
Ta6e baki yayi kafin yace"to ya zanyi mommy, daddy ya 6allo mana aikin Jinya, Yana can kwance Kinyi
mashi wanka Yana bacci, Ya ya Zaki kuma ya gudu ya barni da aikin bashi abinci abaki"

Tuntsirewa tayi da dariya, shima jazz ɗin dariyar yake Yi, shi kuwa ko ajikin shi bilhakki dagaske Yake Yin
maganarshi.

Tsagaiwata tayi da yin dariyar tace"Ibad na fahimci maganata ta tsaya maka aranka, Nifa ba daddynku
nayi ma wanka ba, Taimaka mashi nayi ya rage kayan jikin shi, idan ba haka ba ni taya zan Iya yi ma shi
wanka ƙato dashi, Kallarni ka gani Ƴar ƙarama dani" hura mata hanci yayi batare da yace komai ba

"Jazz where's your phone"? Ta faɗa tana kallon shi.

He was silent for a while, Yana ƙoƙarin tuna inda Yabarta.

"Mom, kamar nabarta a gidan Yaran da nake Kula da lafiyarsu"

Miƙa mashi wayar tayi"Duba ka gani, wata yarinya ta kira da layinka, tana kuka, wai jazz dinta take nema"

Da mamaki akan fuskarshi Ya kar6i wayar, Yana duban Kiran da akayi da layinshi, tunkafin Ya danna kiran
ranshi ya bashi cewar Khadeeja ce.

Da sauri Ya kira layin, ringing uku ta ɗauko tana fadin"Ni ku ƙyale ni tun da ba zaku bani muyi magana da
Ya jazz ba, kun wani isheni da kira,"

Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarsa, jin muryar deejan sa, mom turai da Ibad sun tsareshi da ido suna
kallon fuskarshi.

"Khadeeja ni ne fa" a kwance take kan gado Jin muryarshi Yasa Ta yi zumbur ta miƙe zaune tana fadin"Ya
Jazz dama baka mutu ba"? da wani irin farin ciki ta furta maganar.

Murmushi ya saki tamkar yana a gabanta yace'ban mutu ba My deeja, lafiyata qalou, Yanzu haka ina
agida, wannan layin da kika kira, Na mom ɗina ne"

Shagwa6a ta sanya mashi" I hate U ya jazz, Shine ka manta dani, duk nabi na tashi hankalina akanka
ashema kana gida"

"No, it's not like that, Khadeeja. I miss you. I've been thinking about you tun time din dana dawo hayyaci
na"

Kallon juna mom Turai da Ibad su ka yi alokaci ɗaya, kafin suka maida dubansu gare shi.

"Faɗamin Kin yi breakast da safe kuma kin sha maganinki"?

"Ni ban sha uban komai ba, babu wanda ya bani, waɗancan ƙattan da aka bar mana agida jiya suka cinye
mana abincin mu, yau kuma na sanya su dole su girka mana, aiko suka shiga kitchen suna yi, basu sani ba
na ɗauki bindigarsu nadinga tsoratar dasu hawwa......." hankalinta kwance take kora mashi jawabi, a firgice
ya ɗago da ido yana kallon Mommyn su, ga dukkan alamu suna jin maganar da deeja take Yi mashi,"

Muryarshi a ruɗe ya furta"Dagaske kike ko wasa"?

Dariya tasaki kafin tace"Wallahi dagaske nake maka, don ma sun min wayau sun kulleni a ɗaki, ai da tuni
na kakkashe su"
Zaro Ido Ibad Yayi, Mom Turai tayi dariya, gani su ke yi kamar zolaya ne abun da yarinyar take faɗa ma jazz,
shi kuwa yasan zata aika, Fiye da haka ma shiyasa ya ɗauki maganar ta serious.

"Khadeeja, Ina fata baki raunata kowa acikinsu ba"

"Wlh ban kashe kowa ba, ai na faɗa maka sun ƙwace bindigar"

Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke


"Dan Allah My baby girl kada ki ƙara yunƙuri ɗaukar bindiga kinji ko?

"Toh,"

"Yawwa ai nasan kina jin magana ta, idan har kina so na zo gidan karki ƙara rashin ji," muryarta a ladab ce
tace"In sha Allah" kamar wata mai hankali

"Good Girl, Kafin nazo kiyi wanka, Kici abinci ki ƙoshi," tace "Toh"

"Namanta ban tambaye ki ba, Where did you find my phone?"

"Aɗaki kabarta saman kayanka, nan na ɗauke ta"

"Okey, pls Ki ajiye min inta, kada kice zaki yi wasa da ita"

"Toh, Idan kazo gida zaka gyara min gashin kaina kuma kayi min kalar kitson kalaban nan da ka ta6a yin
min"

Da sauri ya ɗago suka hada ido da mom Turai.

Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Eyyeh, Lallai ashe Jazz har kitso ka Iya yi ma mace, gama wayar ka bani
labari"

da zolaya ibad yace "mommy kin huta, da zuwa saloon, daga yanzu Jazz zai dinga yi maki gyaran gashi"
miƙa mashi hannu tayi suka tafa kamar wasu abokai.

Duƙar da kai Jazz yai"Khadeeja sai anjima, please take care of your self for me"
"You too," sallama su ka yi da ita.

Kunya duk ta kama shi, sai faman sunnar dakai ƙasa Yake Yi.

"Jazz kai muke sauraro ni da mommy" ibad ne yai maganar.

Fuskarshi a yamutse ya furta "Khadeeja ce yarinyar da daddy ya baku labarin ta, She's mentally ill. There's
no love between us. ina kula da ita ne saboda rashin lafiyarta"

mom turai da raha tace "Don't lie to me. I'm your mom and I understand you. Yarinyar nan dai sonta kake
Yi" shiru yayi bai ce komai ba, don yasan da wuya ta fahince shi, zolayar shi suka dinga yi tun yana ɗaure
fuska har yakai ga sakin dariya.

______________________✍️

A hankali Motar su Ta shigo gidan, bayan jami'in yayi parking, Salsabeel Ya fito daga ciki Yayi mashi sallama
kafin ya nufi ƙofar shiga falo.
Yana shiga falon ya hango su Hawwa zazzaune kan carpet, An jera masu kayan abinci saman Tray, komai da
Khadeeja ta ba sojojin Umarnin su girka masu saida suka girka shi, tun daga kan Chicken pepper soup, fried
fish, Chips, wainar kwai, Doya da kwai.

Gyaran murya yayi masu tare da buɗe baki Yayi sallama, A hanzarce suka ɗago suna kallonshi, aiko da sauri
suka miƙe da sauri hada gudu suka nufeshi, ɗaya bayan ɗaya yake rungumarsu a jikinshi.

"Ya salsabeel Ina kaje tun jiya baka dawo ba, Ka tafi kabar mu da kewarka"
Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Eyyah am sorry, nima nayi kewarku, ay min afwa wani uziri ne Ya ruƙe
ni, amma tunda na dawo yanzu komai ya wuce"
Yayi maganar idanuwanshi akan fuskokinsu
"Ina Khadeeja"?
Nan fa suka haɗa baki suna bashi Labarin Ta'asar da Khadeeja tayi ma sojojin da aka bar masu.

Hankalin shi ya ɗan tashi sai dai baiyi mamakin abun da Khadeeja ta aikata masu ba, ya riga daya san halin
kayanshi.

Jin motsin tafiyar mutane yasa shi saurin kai idonshi inda suke.

Fitowarsu kenan daga kitchen, wanke wanke Suka tsaya yi a kitchen din sun gyara komai da suka 6ata, har
sun maida suturarsu.

Wani ɗan iskan kallo suka watsa ma Salsabeel, Hakan Ya tabbatar mashi da ransu Ya 6aci sun harzuƙa.

Tamkar mai jin shakkarsu ya furta"Am...dan Allah Kuyi haƙuri, Yanzu na shigo gidan su Hawwa suke bani
labarin abun da khadeeja ta aikata maku, banji dadi ba, Yalla6ai ne bai bani damar dawowa da wuri ba, da
duk hakan bata faru ba....."

Fuskokin su babu annuri ko miskala zarratin


Tiger yace"malam bamu buƙatar Jin komai daga bakin ka, tun da ka dawo gidan falillahil hamdu, Ka ci
gaba da kula da ƴa'ƴanka, Mu kaga tafiyar mu sannan duk abun da ka gani badai dai ba kada ka tuhumi
kowa, Khadeeja ce sila" Rai a6ace Ya ƙare maganar, Ya nufi Dining table Ya duƙa ya dauko masu
bindigoginsu.

Army boy yace"Zan baka shawara, Yarinyar nan ku gaggauta kai ta Gidan Mahaukata, can ne Yafi dacewa
da ita, Idan ba haka ba wata rana zaku kuka da kanku, don wannan tafi bomb bala'e"

Army na kammala yin maganar suka nufi ƙofar fita daga falon, da sauri salsabeel Yabi bayansu yana basu
haƙuri.

"Dan Allah Ku tsaya, bai kamata muyi irin wannan rabuwar ba, nasan ban kyauta maku ba, amma dan
Allah kuyi hakuri kada ku ruƙe mu aranku"

Ta6e baki su ka yi, Tiger yace"hmmm bakasan masifar da yarinyar can taso taja mana ba, shiyasa har kake
da ƙwarin gwiwar Yi mana magana, Badan Allah Ya kawo mana mafita ba, da yau mu dukan mu zamu
baƙunci lahira"

Jiki asanyaye Salsabeel Yace"ina ƙara baku hakuri, Allah Ya huci zuciyarku"

"Dama ahuce take, bamu hanya mu wuce" matsa masu hanya yayi, duk bai ji ɗadin abun da ya faru da su
ba. har suka fuce bai daina bin bayansu da kallo ba.
Sai da yajiyo tashin motarsu, tukunna ya sauke ajiyar zuciya, Ya juya ya kalle su Hawwa.

"Awani ɗaki suka Kulle ta"? Sarah ce Ta nuna mashi kofar dakin, Azafafe Ya nufi upstairs, Yana isa bakin
ƙofar Ya sanya hannu ya murɗa key din.

Tsabar 6acin rai ko sallama baiyi ba ya faɗa ɗakin, a gaban mirror ya taras da ita zaune, ta sanya undy ta
jashi har saman kirjinta, ga dukkan alamu wanka tayi shine ta zauna tana gyara jikinta kamar wata mai
hankali.

Gyaran murya yayi mata, zumbur ta miƙe tana faman ƙyafƙyafta idanuwanta, hannayenta biyu ta ɗaura
asaman kanta kafin tace "sun faɗa maka abunda na aikata"?

Takaici ne Ya ishe shi wato har tasan ta aikata badai badai ba.

"Meyasa"! Aɗan tsawace Ya jefa mata tambayar, Ta6e mashi baki tafara yi alamar zata fashe mashi da
kuka da sauri Ya zare mata ido haɗi da cewa"Yi min shiru! kar in kuskura Inji kukan ki," da buɗar bakinta sai
cewa tayi"ai dama ba ka so na, Kafi son su hawwa, shiyasa kake min fada" sassauta fushin fuskarshi yayi
tunawa da karancin hankalinta

"Am sorry, raina ne Ya 6aci, bawai bana sonki ba, pls ki daina rashin ji dan Allah"

Washe mashi baki tayi "Nadaina, bari na ɗauko maka wayar Ya jazz, na kira shi har mun gaisa ashe bai
mutu ba Yana nan da ranshi" ta faɗa tana dariya ta juya ta nufi gado ta dauko wayar taje ta miƙa mashi
Yasa hannu Ya kar6a.

da mamaki yace "Taya akai ki ka yi waya dashi"? Watsa hannu tayi"nima bansani ba, na daddana saina
kira,"
Call log Ya shiga, numbar farko data bayyana ta Mom turai, Ya danna ma Kira, Bayan ta ɗaga wayar cikin
girmamawa salsabeel Ya gaishe da ita, daga bisani Ya tambayeta Ya jikin jazz, tace mashi da sauki, bata
tambayi wanene shi ba sai ta ba Jazz wayar suka cigaba da yin magana,

Hankalin shi ya kwanta Jin muryarshi raɗau tamkar bai ta6a yin ciwo ba, sun jima suna yin wayar har jazz
ya tuna mashi da maganin khadeeja kafin suka yi sallama Ya adana mashi wayar a hannun shi
Tattara Yaran yayi a falo, hada shi suka zauna suna kwasar girkin da Su Tiger suka Yi masu, dama da
yunwar shi Ya dawo, aikuwa dai sunyi kullu wash rabu hani'an, su mama Tiger An Iya girki, sai santi su ke yi,
musamman khadeeja, bakinta dama dama da maiƙo.

*🌹ZEENATU🌹*

Baiwar Allah, Ta hana zuciyarta sukuni, tun lokacin da tayi masu Benazir la6e a toilet, kunnuwanta suka jiyo
mata maganganun da suka tsaya mata aranta, haƙiƙa tayi danasanin sauraransu, don tun safe take faman
jinyar zuciyarta, kiri kiri taki cin breakfast dinta, har lunch bata ci ba, yini tayi a cikin bedroom dinta da
raɗaɗin abun azuciyarta, Tani tayi ƙoƙarin shawo kanta donta faɗa mata meke damunta taƙi ta sanar da ita,
ba irin lallashin da ba ta yi mata ba amma taƙi sakin jikinta.

A yanzu haka tana daga kwance saman prayer mat, ta lullu6e jikin ta da dogon hijabinta launin milk, daga
gaban dardumar qur'anic stand ne an bude shi alamar karatu take cikin yi bacci yayi awon gaba da ita.

Damuwar halin da take aciki Ya hana Tani samun sukuni, fargabanta kada ace wani abunne ke shirin faruwa
da ita shiyasa ta canza mata.
Shigowa ɗakin tayi domin gyara mata bedroom din, karaf idanuwanta suka sauka akan zeenatu dake
ƙudundune tana bacci.

Cikin takun sauri Tani ta nufi dardumar, aranta tana fadin'baiwar Allah, daɗina da ita duk halin da zata
shiga bata mantawa da yin ibadarta"

Zuƙunnawa tayi agaban prayer mat din, muryarta ƙasa kasa ta ambaci sunanta.

"Zeenatu! Zeenatu! Ki tashi ki koma kan gado ki kwanta, kwanciya kan prayer mat, bai da amfani jibi yadda
ki ka ƙudundune kanki duk kin takure kanki"

Tani sai zuba takeyi babu alamun zeenatu zata farka,


"Oh Oh ni wannan baccin naki bame ƙarewa bane da alama, dan Allah ki tashi" still bata tanka mata ba.

Hannu ta ɗaura saman jikin zeenatu ta bubbugata, nan ma taƙi farkawa, lokaci ɗaya Tani ta fara Jin
fargaba acikin zuciyarta, hankalinta yayi mugun tashi, a ruɗe ta ɗaga murya tana ƙwala mata kira da sauti
mai karfi"Zeenatu! Zeenatu! Nashiga uku, Wayyo Allahna, meke faruwa dake ne, Zeenatu dan Allah ki
tashi" jikinta na rawa ta soma kiciniyar tu6e mata hijabin data ƙudundu ne kanta aciki daƙyar ta samu ta
yakice hijabin ta nannaɗeta gefe daya kan darduma, koda Tani ta ɗaura idanuwanta akan jikin zeenatu
saida gabanta Ya faɗi, ganin wata irin zufa dake tsastsafo mata ta ko'ina, Rigar jikinta ta manne ma fatarta,
sumar kanta kuwa duk ta yamutse babu gyara, shafa wuyanta Tani tayi nan fa taji yaɗauki zafi sosai.

A gigice ta miƙe ta watso da gudu ta nufi babban falon gidan, a lokacin Dr shureim Yana daga zaune kan
Sofa, Benazir tana a gefenshi, fuskarta ɗauke da murmushi take kallon shureim dake bata labarin
ƙuruciyarta.

Kamar mahaukaci haka Tani ta nufo su ta zagayo ta gaban Sofas din, kusan atare suka dago suna kallonta
da alamun ruɗani akan faces dinsu
Dr shureim Yace"Tani! Lafiya? Meke faruwa"?

Sai faman yarfa hannu take yi duk tabi ta ruɗe.

"Pls ki buɗe baki kiyi mana magana" acewar Benazir, daƙyar ta iya tattara natsuwarta wuri guda, da karfin
hali ta furta"Zeenatu ba lafiya! Tana acan daki rai hannun Allah, kwata kwata bata motsi..." kafin ta ƙare
maganar, da gudu Dr shureim da Benazir suka nufi part dinta, tsabar sauri mayafin jallabiyar Benazir har
faɗuwa yake yi kan kafaɗarta da sauri take sanya hannu ta gyarashi, Tani tana abiye da bayansu.

Suna shiga ɗakin idanuwansu suka sauka akan zeenatu dake a kwance magashiyan tamkar bata numfashi.

Slowly dr shureim ya zube agabanta kan gwiwowinsa, ya sanya hannayenshi biyu ya tallabo da kanta ya
ɗaura saman laps dinsa, Benazir ta zuƙunna gefenshi, fuskokinsu da alamun ruɗu suk soma ambaton
sunanta"Zeenatu! Zeenatu"!

"Tani, bata da lafiya ne"? Benazir ce ta jefa mata tambayar


Muryar Tani tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi ban sani ba nima, yanzu nashigo ɗakin na taras da ita a
kwance, nayi tsammanin ko bacci ta ke yi, amma dana kira sunanta na bubbuga jikinta taƙi farkawa nan fa
na gane babu lafiya atare da ita"
A faɗa ce Benazir tace
"Tayaya za ki ce bakisan meke damunta ba? Bayan ke ce kike kula da bedroom dinta"
Tani dake kallon Benazir duk tasha jinin jikinta
"Bansan ya zanyi maki bayani ba, ba laifi na bane, tun safe nake fama da ita akan ta fadamin meke
damunta taƙi ta sanar dani, na rasa gane kanta ta ƙuntata kanta aɗaki, ta hana kanta sukuni yinin yau"
hawaye har sun fara sauka kan fuskar Tani.

Jiki asanyaye Benazir tace"bari naje na faɗa ma su Mommy abinda ke faruwa" A firgice Tani tayi hanzarin
dakatar da ita ta hanyar shan gabanta muryarta na rawa ta ke ambaton" inna lillahi wa inna ilaihirraji'un,
dan Allah ki rufa min asiri kada ki faɗa masu abunda ke faruwa, wlh zasu Iya korata daga gidan nan, ba
lallai su fahimce ni ba, Alhaji musa baya raga mana akan Zeenatu, Idan yaji wannan maganar babu makawa
zai kore ni ne"

Cikin rashin fahimtar kalaman Tani, Benazir tace"dan Allah malama ki bani hanya in wuce, kina ganin
yarinya babu numfashi sannan ki hana in fadama Iyayenta, hakan bazai yiwu ba dole suji ko dan akira
likitan ya duba ta" a tsiwace Benazir tayi maganar, tare da bi ta gefen Tani ta nufi ƙofar fita dakin.

Zubewa Tani tayi saman gwiwowinta hannayenta biyu asaman kanta, yayin da hawaye ke yin sintiri akan
kuncinta.

"Dr shureim nasan kai zaka fahimce ni, dan Allah ka hanata fita daga dakin nan, wallahi idan ta faɗa masu
halin da ake ciki, bani kadai zata ja ma bala'e ba, duka ma'aikatan gidan nan zata shafa"

Ɗagowa dr shureim yayi, launin idanuwanshi har sun canza kala, muryarshi adidashe Ya ambaci sunan
benazir, Harta ɗaga ƙafa zata ƙetare kofar ɗakin tayi saurin cin burki jin kiran shureim.

Juyowa tayi miryarta da faɗa tace"yaya shurem kada ka biyewa matar nan, akan me zata hana afada masu
halin da ƴarsu take aciki, so kike mu rufa maki asiri, mu zuba ido muna ganin yarinya bata motsi har wani
abin da ba'a fata ya faru da ita ko"?

Fashewa Tani tayi da kuka, abun duniya ya isheta.

Cikin sanyin murya dr shureim yace"Sister calm down ur mind, Zeenatu suma tayi ki miƙo mun ruwa in
yayyafa mata, sannan kada ki sanar da kowa, mu jira muga awani yanayi zata farka, Idan ba lafiya dole mu
sanar da mutanan gidan don akira mata doctor" amsa mashi tayi da toh, da sauri ta nufi ƙaramin fridge
dake a dakin ta buɗe ta ɗauko bottle water taje ta miƙa ma shureim yasa hannu ya kar6a.
Kowan nan su fargaba ce azuciyarsa, musamman Tani jikinta yaƙi daina yin kakarwa
Kusan sau uku dr shureim Yana yayyafa mata ruwa a fuskarta batare da ta motsa ba, Har sun fara fidda rai
a lokacin da ba su yi tsammani ba suka ga Taja dogon numfashi tare da sauke shi, da wata irin kasalalliyar
murya ta firta"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"

Atare suka hada baki suna ambaton sunanta"Zeenatu! Zeenat"


Firgigit ta ware blue eyes dinta akan fuskokinsu, launin farin idon ya canza sosai
Wata irin nauyayyar Ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke
"Zeenatu, fada min meke damunki"? Tani ce tayi maganar
Cikin kwantar da mirya Benazir tace"Sister ɗina, baki da lafiya"? Da ƙyar zeenatu take buɗe idanuwanta
sunyi mata nauyi saboda kukan da tasha, fuskarta tayi jawur.

"My zeenat" jin miryar dr shureim yasa tayi saurin wurga eye balls dinta akan fuskarshi, wani sabon kukan
ne ya kufce mata tamkar ranta zai fita, duk tabi ta rikitar da su.

Hada baki su ka yi wuri lallashinta da kwantar mata da hankali daƙyar su ka shawo kanta, tayi shiru tana
faman ƙyafƙyafta masu idanuwanta waɗanda ke ajiƙe sharkaf da ruwan hawaye.

"Please faɗa min meke maki ciwo"? Dr shureim ne yai maganar,


Duk sun tsareta da ido
Daƙyar ta iya buɗe baki ta furta"Yunwa nake ji" sunyi mamakin jin abunda ta fada masu badan sun yarda
da maganarta ba,
"Tani, dama zeenatu bata ci abinci ba? Shiru tani tayi tana faman zare idanuwanta, banezir ta jefa mata
kallon tuhuma kafin tace" Ɗazu da safe ke kika ce tace akai mata breakfast dinta a ɗaki Kenan baki kai
mata ba "?
Girgiza kai tayi Tani tayi"Na kawo mata abincin, Itace taƙi ci, ba yau ta fara yi min hakan ba, Idan wani abu
na damunta bata cin abinci, kona tursasa mata akan dole taci, sai tace min in tafi zata ci, da zarar nabar
ɗakin take daukar abincin ta shiga toilet da shi tayi flushing dinshi" har saida Dr shureim ya ɗan zaro ido jin
abunda Tani tace, Zeenatu ta haɗe fuska ga dukkan alamu bata da gaskiya, Miƙewa benazir tayi da sauri ta
nufi toilet jim kaɗan sai gata ta fito daga ciki fuskarta adaure babu walwala tace"Zeenatu baki kyauta mana
ba, Fisabilillah haka ake rayuwa? Don wani abu na damunka sai kaƙi cin abinci? Maimakon ma in ba ci
zakiyi ba ki bata ta mayar a kitchen sai ki zubda lafiyayyan abinci, kinsan fa ba kyau Almubazzaranci"

Rufe ido zeenatu tayi, har lokacin bata ɗago da kanta daga kan laps din dr shureim ba.

"Tani ki ci gaba da yin haƙuri da ita, In sha Allah zata daina very soon yanzu ki koma kitchen ki haɗa mata
wani abincin ni zan bata da kaina"

Muryar Tani asanyaye tace"To" kafin ta juya da sauri tabar dakin


"Sister, nabar wayata daki ko zaki dauko min"
Benazir ta amsa mashi da toh, kafin ta fuce daga dakin, Ya rage da ga shi sai zeenatu, dama da biyu ya
aiki benazir ta ɗauke mashi waya.

A hankali ya tallabo kanta ya ɗaura shi kan ƙirjin shi, tamkar ƴar baby haka ya ruƙe ta.

Wata irin kunyarshi ce ta kamata, taƙi bari su haɗa ido.

"My zeenat, haka za mu yi aure kina yin min rigima? Ya kikeso inyi da rayuwata idan baki gyara halin nan
naki ba"?

Turo mashi pink lips dinta tayi batare da tace komai ba, murmushi yasaki yana mai mamakin ƙuruciyar
zeenatu.

"Faɗa min waya ta6a min ke"? Daƙyar ta ɗan iya buɗe ido ta harare shi kafin tayi sauri kau da idonta gefe,
nan take ya fahimci wani abu.

"Hakan na nufin ni na 6ata maki rai? Ko kinji maganganun da muka tattauna nida sister benazir ɗazu da
safe"?

Muryarta da shagwa6a tace" I heard everything, ya Shuraim! I won't marry you, because you lied to me.
You told me that you had never been in love, bayan ba haka ba ne, sannan ka nuna min hotona amatsayin
hoton da ka ke yawan kallo a phone din ka, ashe ba haka bane hoton wata ne daban, Why ya shureim?
What did I do to deserve that?' she said, giving him a suspicious look.

Aranshi ya ayyana zeenatu matsala, tun yanzu ya fara jin shakkar kishinta .

"Ka tsare ni da ido baka ce komai ba Sannan har fadi kake yi wai ba zaka ta6a samun madadinta ba even if
u get married" ranta a6ace ta ƙare maganar hawaye nabin fuskarta, hannunta ɗaya dafe da saitin
zuciyarta.

Tun da take yin magana ya natsu yana bin fuskarta da kallo har saida ta gaji don kanta ta dakata da yin
maganar tukunna ya samu damar bata amsa
Calmly ya furta"My zeenat, baki fahimci kan zancen namu ba, shiyasa babu kyau yiwa mutun la6e, kalli
yadda kika takura kanki akan abunda baki da tabbaci kansa" harara ta jefa masa"yaya shureim ni fa ba
kurma bane, Ina ji ai," ta faɗa tana nuna mashi kunnanta da hannu.

Murmushi yayi mata, ita ko sai ƙara haɗe mashi fuska take yi.

"Bana son 6acin ranki zeenatu, don haka zan faɗa maki gaskiyar abunda na 6oye maki, saboda ina burin
na aureki duk wani sirrina ya kamata ki sani, amma bana so ki faɗa ma kowa"

Jinjina mashi kai tayi alamar Toh, shiru yai yana yanke shawara da zuciyarshi, ƙwara ya faɗa mata gaskiya
idan ba haka ba zata ci gaba da yi mashi kallon maƙaryaci kuma ba sonta ya ke yi ba tun da yana da wadda
yake kallon hotonta kullum bayan haka zata cigaba da yin jinyar zuciyartane tun da ita haka Allah ya halicce
ta da kishin tsiya.

"Dangane da hoton dana nuna maki naki, tabbas bashi nake kallo ba, hoton ƴata ne nake kallo....." tsabar
firgita da jin maganarshi yasa zeenatu ta zabura ta sauka daga jikinshi ta koma tana fuskantar shi,
idanuwanta azazzare, maganar ta daki kunnanta tamkar a mafarki taji ta.

"Yaya shurem na shiga uku, ƴa fa kace, dama ka ta6a yin aure hada baby"
Girgiza mata kai yayi"a'a, Ni ban ta6a yin aure ba, na samu yarinyar bata hanyar aure ba...." bai kai ga ƙare
maganar ba yaga ta ɗaura hannayenta biyu saman kanta alamar ta shiga uku.

"Ya shureim dama kai ɗan iskane" dafe kanshi yai da hannu ɗaya

"Idan ba zaki natsu ki saurare ni ba, zan tashi nabar ɗakin nan" da sauri taja baki tayi shiru.

Tuni yanayin fuskarshi ya canza sam baya son tuna abunda ya faru a rayuwar shi, tamkar yana faman
raunin dake a zuciyar shi ne

Numfasawa yai kafin ya ɗaura da cewa "Bayin kai na bane, zan Iya cewa ƙaddarace ta afka min har hakan
ya faru, a yanzu haka da nake baki labari, Yarinyar bata araye tun tana jaririya ta rasu, Tsakanina da
mahaifiyarta bamu ta6a yin soyayya ba, daga ni har ita ba mu ta6a tsammanin zamu yi mu'amala da junan
mu har takai mu ga aikata sa6on Allah, mun fuskanci matsanancin tashin hankali, abun da ya faru zeenatu
shine silar ƙuncin rayuwar da na shiga..... '

Duƙar da kanshi ƙasa yayi tamkar mai neman gafara, hawaye tuni sun cika idanuwanshi, sam bayason
tuna baya saboda tsohon raunin dake acikin zuciyarshi.

Jikin zeenatu yayi mugun yin sanyi, har cikin ranta ta yarda da maganar shi, ta kuma ji tausayin shi.

"Yaya shureim na yarda da kai, please forgive me for what I said. Rashin sani ne kuma nayi danasani, dan
Allah ka daina zubar da hawayen ka, I know it's hurting your heart, amma kayi haƙuri"

Matsawa tayi kusa dashi ta sanya tafin hannayenta biyu ta share mashi hawayen dake akan fuskarshi,
wani irin tausayinshi ne ya kamata, da sauri ta rungumoshi ya ɗaura kanshi saman kafaɗarta itama ta
ɗaura nata kan asaman tashi kafaɗar.

"Yaya shureim ita babyn taka an riga haihuwarta kafin Ni"?

Cikin rauni na murya ya furta"da ace tana araye da yanzu ta girmeki" cikin sigar lallashi take ɗan bubbuga
bayanshi da hannayenta, ba tare da sun raba jikinsu ba taci gaba da tambayarshi Ya sunanta"?

"*FATIMA*" atakaice Ya bata amsa


"Allah sarki Ƴar uwata fatima, Allah yajiƙanta"
"Ameen"
"Ita maman babyn naka, meye sunanta" shiru yayi don baison furta sunan.

Fahimtar hakan yasa tayi saurin canza akalar zancen nata

"Yaya shureim idan aunty benazir ta kawo maka wayarka zaka nuna min hotonta dan Allah"
"Zan nuna maki"
A hankali ta ɗago da fuskarta, haɗi da daura idanuwanta akan fuskarshi, ta dafe kafadunsa da hannayenta
Ido cikin ido suke kallon juna
"Idan mukayi aure nima zan haifa maka ɗiya, bama ɗaya ba Ƴan biyu zan haifa maka, sai mu sanya masu
sunan Fatimarka" tunkan ta ƙare maganar tayi saurin dukar da idonta ƙasa
Shi kanshi yayi mamakin maganar data furta mashi, saboda kunyar dake gareta amma ya fahimci tausayin
shi ne Ya kamata.

Shafa sumar kanta yai da hannun shi ɗaya"nagode da kulawarki agare ni,"
da buɗar bakinta sai cewa tayi"ya shureim pls ka sanar da daddyna da daddynka maganar auranmu, suyi
sauri su daura mana aure, don in haifa maka fatima"

Dariyace ta kubce mashi, cikin jin kunyarshi Zeenatu ta yi saurin miƙewa ta nufi gado ta haye ta kwantar da
kanta
Abun da basu sani ba, benazir tana la6e tana sauraronsu, hannayenta biyu ruƙe da Tray din abincin
zeenatu data kar6a a hannun Tani
Hankalinta idan yai dubu toh ya tashi, har sai da gabanta ya fadi, Jin zeenatu nayiwa shureim zancen aure,
aranta tace"taya ma haka zata yiwu? Soyayya tsakanin Ya shureim da zeenatu ƴar cikinsa? Anya kuwa
zeenatu tasan ainihin shekarun dr shureim? Lamarin ya ɗaure mata head.
Shiga dakin tayi da sallama abakinta, dr shurem ne ya amsa mata sallamar, ta ƙarasa kan carpet din gefen
gadon ta ɗaura mata tray din
Idanuwanta akan fuskar Dr shureim, ya lura da kallon da take yi mashi sai dai bai kawo komai aranshi ba
"Ina wayar"
Cikin aljihun jallabiyar jikinta ta zaro wayar ta miƙa mashi, Ya kar6a yana fadin"nagode sister,"
"Yayana, wani abu ya farune bayan fitana? Naga zeenatu a kwance kan gado"
"Taji sauƙin abunda ke damunta, dama ba wani ciwo bane" gyaɗa kai benazir tayi"Okey, mu taimaka mata
taci abincin"
Atare suka zauna da zeenatu suna bata abinci abaki, Hankalin benazir yaki kwanciya sai satar kallon dr
shureim da zeenatu takeyi afakaice batare da sun ankara ba, har wani kallon ƙauna taga suna jefawa
junansu, ita dai abun ya tsaya mata aranta, ya girmi tunaninta.......

*❤HAJIYA ADAMA🤍*

A zaune take kan mirror chair, ta ɗauki wankan riga da zane na zallar leshi launin ruwan toka rigar tayi
matuƙar yi mata kyau, ta ca6a adon zabba da awarwaro a hannunta, head dinta kala ɗayane da takalman
ƙafarta black colour, Hand bag ɗinta tana ajiye saman gadonta itama launin takalmanta ce.

A tsanake take shirya kanta, bayan ta gama shafe shafenta, ta kai hannu ta ɗauki turare tabi ko'ina na
jikinta ta feshe, miƙewa tayi ta nufi gadon inda ta ajiye mayafinta, ta ɗauka ta yafa shi a kafaɗa, kafin ta
ruƙo handbag din.
Tana ƙoƙarin juyawa Uncle abdallah Ya doko sallama hannunshi ɗauke da baby junaid sunyi shiga kala
ɗaya ta shadda blue sky.
Murmushi tasakar mashi, da fara'a akan fuskar uncle abdalla yace"madam shanyar da ki ka yi ta bushe
tun ɗazu ba ki je kin dubo ta ba"
Farfari tayi mashi da ido"am sorry my husband, nabarku kunata jirana awaje"
From head to toe yake binta da kallo har zuwa kan head din data ɗaura, komai nata burgeshi yake yi,
Hajiya adama ta Iya ɗaukar wanka.

Baby junaid sai faman lumshe idanunsa yakeyi sam baya fahintar komai biji biji yake ganinsu baccine ke
neman yaci ƙarfinsa
"Kullum ƙara kyau kike yi, faɗamin menene sirrin"?
Still fuskarta da murmushi tace"bani da wani sirri daya wuce kai, Mijina, saboda kulawar da kake bani da
tarairayata da kakeyi sune suke ƙaramin kwanciyar hankali da natsuwar da nake samu har kake ganin ina
ƙara kyau"

Lumshe idanuwanshi yayi tare da waresu kan fuskarta.

"Shiyasa nake ƙara ƙaunarki acikin zuciyata, samun mace irinki abune mai wuya a duniyar nan, kin haɗa
komai hajiyata, kyau, nasaba, ilmi, abu mafi jan hankali agare ki, tsaftarki, da Iya girkinki, idan nace zan
lissafa maki kyawawan ɗabi'unki da halayanki to kuwa zamu kwana batare dana kammala karanto maki
ba"
Tsabar jin dadin maganarshi ce tasata yin dariyar farin ciki
"Kana ƙara huramin kaina fa,"
"Ba hura maki kai nakeyi ba, Kin cancantane my wife"
"Thank u dear, for loving me and for everything" har cikin zuciyarta take fada mashi kalaman
"Yakamata mu tafi, baby junaid fushi yake yi damu, munƙi kai shi wurin mommynsa" ya fada yana dariya
Kallon fuskar baby junaid hajiya adama tayi, tuni bacci yai awon gaba dashi, Ya langwa6e kansa saman
chest din uncle abdallah.

"We will miss him. I love my grandson bana son rabuwa dashi sai dai ba yadda zanyi dole na maida ma
mamansa" yanayin fuskarta ne ya canza zuwa damuwa,
" jin kaina nakeyi tamkar ban ta6a haihuwa ba saboda rashin Uzair, abun yana ta6a min zuciyata, shi kaɗai
nake gani inji dadi, da kuma ɗan uwansa tajuddeen da baby angel dinmu Yanzu duk babu su ..." cikin jin
ƙunar rai ta furta maganar, jikin uncle abdallah yayi sanyi, Shi kanshi abun yana damunshi.

"Tunda na haifi uzair ban sake samun damar da zan haihu ba, saboda matsalar dana samu, mijina meyasa
ba zaka kar6i shawarata ba? Nifa inason ganin jininka" idanuwanta sun cika tab da ƙwalla.

Ɗaure fuska uncle abdalla yayi, tamkar bai ta6a yin dariya ba

"That's enough! Bana so kina min maganar nan! Stop trying to pressure me into getting married. I have no
intention of doing it, ke kaɗai kin ishe ni, kada na kuskura naji kin sake tada maganar," Yana ƙarasa
maganar ya juya da sauri ya fuce daga falon, Bin bayanshi tayi, a harabar ajiye motocinsu, ta same shi tsaye
ya jingina bayanshi jikin motar, harya kwantar da baby junaid, a back seat.

Agabanshi ta tsaya tana ƙoƙarin shanye damuwarta tace"am sorry, idan ranka ya 6aci, bazan ƙarayi maka
maganar ba,"
Batare dayace mata komai ba ya nuna mata murfin motar, buɗewa tayi ta zauna a front seat, Ya zagaya ta
other side ya zauna a driver's seat, key yayi ma motar, a hankali yayi reverse ya karya kwana ya fitar dasu
daga cikin gidan, tunda suka haura kan titi babu wanda yayima wani magana acikinsu, kowa da abunda
yake saƙawa aran shi, idanuwan hajiya adama sun kaɗa jawur dasu, jefi jefi takan kai idonta ta cikin mirror
din motar ta kalli baby junaid dake akwance yana sharar baccinsa, mutuwar son yaron takeyi, sam batason
rabuwa dashi sai dai ba yadda zatayi.
A hankali motarsu ta ƙaraso bakin gate din gidan Uncle ɗan Iya, Horn su ka yi Baba mai gadi Ya buɗe masu
ƙofar su ka shiga daga ciki, bayan uncle abdallah yayi parking din motar, cikin kulawa ya dubi fuskar Hajiya
adama
"My wife," kallon shi tayi fuskarta a yamutse babu walwala
"Kinsan ina sonki, and bana son 6acin ranki, zan Iya yin komai danganin na faranta maki rai, dalilin dayasa
bazan dauki shawararki ba saboda gudun in jefa rayuwarmu cikin hatsari, ke kanki kinsani samun mace
tagari wahala ne dashi a duniyar nan, ina jin tsoron in auro wadda zata yi silar tarwatsewar farin cikin mu,
ko in auro maki Yarinya da zata raina ki, Ina fata kin fahimce ni"?
Ajiyar zuciya ta ɗan sauke fuskarta ɗauke da murmushi tace"na fahimce ka, mu shiga daga ciki" ta fada
tare da buɗe murfin motar ta fito ta buɗe mazaunin baya ta ɗauko baby junaid ta rungume shi a kirjinta, ta
rufe kofar, atare da uncle abdallah suka nufi entry hall na shiga gidan Uncle abdallah

Tunkafin su ƙarasa Aneelerh da zahra suka fito fuskokinsu dauke da fara'a sun dauki wankan Atamfa riga da
skirt, ɗaurin ɗan kwalinsu kala ɗaya, Aneelerh ta yafa Mayafi akanta, yayin da zahra ta daura nata mayafin
kan kafaɗarta,
"sannunku da zuwa, Ina wuninku," zahra ce tayi maganar, Uncle abdallah Ya amsa mata da Lafiyalou,
Fatan mun same ku lafiya" ya faɗa yana kallonta tace"Lafiyalou,"
Kafin ta kar6i baby junaid daga hannun Hajiya adama, rungume juna sukayi ita da Aneelerh
"Mommy sannu da zuwa, nayi murnar ganinku," Aneelerh ta fada tana murmushi ta dago da kanta, Itama
hajiya adaman murmushin ta sakar mata
"Surukar arzuƙi, kullum ƙara kyau kike yi," cikin jin kunyarta ta dan dukar da kanta tana fadin"daddy Ina
wuni Ya gida Ya aiki"
Uncle Abdallah Yace"lafiyalou daughter, fushi nake yi dake, kinƙi zuwa kiga gidan mu"
"Naso zuwa mommy adama ce tace nabari zata zo kawo shi, badan haka ba ai dani zan zo dauko shi daga
nan ma har inga gidan, amma ay min afwa in sha Allah zan fidda lokaci ni da zahra mu shigo gidan" yaji
daɗin maganarta
Zahra tace"mu shiga daga ciki," ta fada tare da basu hanya suka nufi ciki,
A lokacin Mami tana cikin jera masu abinci a dining, Ummi kuma ta fito daga daki jikin ta sanye da hijabi,
tana ganinsu ta nufesu fuskarta dauke da annurin farin ciki, Itama mami ta ajiye jeran abincin da take yi ta
nufesu da fara'a suka gaisa da junansu, kafin suka zazzauna saman sofa, fira suka fara ta6awa a tsakaninsu,
Zahra da Aneelerh suka basu wuri, Ɗaki suka shiga a saman gado Zahra ta kwantar da baby junaid tana
fadin"Baby boy dinmu Yaji hutu, sati biyu kacal har ƙiba ya ƙara, fatarshi tayi kyau"
Aneelerh tace"ni kaina na lura da canzawar da yayi, gaskiya mommy adama ta iya raino, kalli kumatunsa
sunyi 6ul6ul da su" gaba daya suka sanya dariya
"nasan baby junaid ba ƙaramin ta'asa yayi masu ba, Allah kadai yasan adadin madarar da ya shanye masu"
cike da shakiyanci zahra tayi maganar tana jan kumatunsa da hannunta
Aneelerh tace"kamar wanda yasha ƙwaya sai bacci yake yi yaƙi farkawa duk surutun da muke yi, Allah na
gani nayi kewar babyna" daga gefen gadon suka zauna suna kallonshi kamar zasu hadiyeshi, farin cikin
ganin shi ne Ya cika su
"Auntyna bari naje kitchen in dauko mashi Cake dinsa nasan zai yi farin ciki idan Ya ganshi" Miƙewa zahra
tayi jiki na rawa ta fuce daga dakin.

Fitarta ɗakin keda wuya Baby junaid Ya fara mutsi mutsin farkawa daga bacci, tunkan Ya buɗe
idanuwanshi Ya fara yin sambatu yana fadin Ni wurin mommyn baby zanje, ni ku kaini gidan mamana"
Dariya Aneeerh tasaki batare da tace komai ba, ƙarasa buɗe idanuwanshi yayi Biji biji Ya fara ganinta kafin
ya ƙara ware idanuwan akan fuskarta, zazzaresu yayi tamkar yau ya fara ganinta, muryarsa da shagwa6a ya
furta"Mommyna, bacci nake yi ko mafarki" tuntsirewa tayi da dariya tare da sanya hannayenta biyu ta
daukoshi ta daura shi kan laps dinta haɗi da rungume kanshi saman kirjinta
"Baby mommy ni ce, ba mafarki kake Yi ba, mommy adama ta dawo mun dakai kana bacci"
Fashe mata yayi da kuka Ya ƙanƙameta da hannayensa biyu, Hankalinta atashe ta ke fadin"My baby boy
meyasa keke yin kuka? Maimakon kayi farin cikin ganina, ko ba ka so dawowo gida bane"?
Cikin shessheƙar kuka yace"mom..my wallahi bazan ƙara zuwa gidansu kwana ba, Ni bazan ƙara tafiya in
barki ba, duk inda zamuje sai dai mu tafi atare......" bata bari ya ƙare maganarba tai saurin toshe masa
bakinsa da tafin hannunta, gudun kada su Hajiya adama su jiyo sautin kukanshi da maganarshi
"sorry my baby boy, Nima bazan ƙara bari kayi nesa dani ba, kayi hakuri idan hakan ya 6ata maka rai"
dakyar ta lallasheshi Yadaina yin kukan
Shafa sumar kanshi tayi da hannunta"yanzu fada min me ya faru bayan zuwanka gidan" tamkar baison
furta maganar yace"Bakomai" dariya ta yi donta fahimce ranshi a6ace yake
"Tunda bazaka fadamin ba, Ni zan fada maka meya faru bayan tafiyarka" ƙura mata manyan idanuwanshi
yayi fuskarshi babu annuri
"Idan dare yayi bana Iya bacci saboda rashin ka atare dani, nayi maraicinka my baby boy, bani da aikinyi
sai tunaninka, dakai nake kwana dakai nake tashi, har mafarkinka nake yi, idan abun ya dame ni sosai, sai
in dauki pillow Ina kuka ina Kiran sunanka, wayyo Allah baby junaid dina ka tafi kabarni....." da wasa
takeyin maganar tana kwatanta mashi yadda ta ke yin kukan, Murmushi taga ya fara sakar mata hakan ba
ƙaramin dadi yai mata ba
"Mommy kema kinyi kuka da bana nan"
Ɗaga mashi gira tayi alamar eh, dariya yasaki har fararen haƙoranshi suka bayyana tar dasu
"Wallahi naji dadi, ke ma kinji abunda naji," wannan maganar da yayi mata ta bata dariya.

Shigowa ɗakin zahra tayi hannunta ɗauke da plate daga saman shi chocolate cake ne, an ajiye cake knife
daga gefe ɗaya.

Akan table zahra ta daura mashi cake dinshi, kafin ta zauna daga gefen Aneelerh
"Ashe Ya farka, rigimamme naga sai haɗe min fuska yakeyi, ko ba ka ji dadin ganina bane"?
Washe mata baki Yayi idanuwanshi akan cake din data kawo mashi yace"na wanene wannan"?
Aneelerh na murmushi tace"naka ne, aunty zahra ce ta haɗa maka"
Wani irin farin cikine ya bayyana akan fuskarshi, da sauri ya sauka daga kan laps din Aneelerh Ya rungume
Zahra yana fadin"I miss U sis zahra," dariya suka saki, Zahra tace"yau naci albarkacin cake, Har ana fadin
Anyi missing dina, toh nagode Nima nayi kewarka our baby boy," ta fada tana shafa sumar kanshi
"Ni zan yanka cake din" Ya fada Tare da raba jikinshi daga nata, da zumuɗi yakai hannu zai dauki wukar
aneelerh tayi saurin rigashi daukarta"Ni zan Yanka maka" ba musu ya amsa mata da toh
Zahra dake kallonsu gwanin ban sha'awa tace"Aunty Aneelerh ki cigaba da tayani addu'a Allah Ya bani miji
nagari inyi aure kafin in mutu, wallahi inason ƴa'ƴa idan ina kallonki ke da baby junaid sai inji dama ni"
Fuskar Aneelerh dauke da murmushi tace"in sha Allah zahra, zan cigaba da tayaki addu'a, very soon kema
zakiyi aure har ma ki haifa mana babies"

"Ameen Ya Allah Auntyna, Bari in dauko wayata Inyi maku hoto" acewar zahra, Ta miƙe da sauri ta fuce
daga dakin, har zata gifta ta falo tajiyo sallamar Abie da Uncle dan Iya, da sauri takai idonta kansu, atare
suka shigo fuskarsu dauke da fara'a suka nufi su uncle abdallah,
Kau da idonta tayi da sauri ta nufi bedroom dinta ta shiga, akan gado ta dauko wayarta, ta ɗan dakata tana
daddana wayar, wi-fi ta kunna ta shiga whatsapp dinta, messages ne suka fara shigowa ta ko'ina, wasu
sakonnin daga abokan aikinta wasu kuma daga mutanan da suke mutunci dasu,
Shagala tayi da karanta sakonnin mutane, har tazo kan sakon da Hajiya saratu ta tura mata tun jiya da
marace bata gani ba sai yanzu, Gajiyar aikin da su ka yi ne ya hanata hawa whatsapp din jiya.

Tsabar zumuɗi yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin buɗe chat dinsu
Unexpected Tayi tozali da hotunan da hajiya saratu ta tura mata, Na twins dinta, Sunyi matuƙar yin kyau
hotunan a ƙalla sunkai guda biyar, Hoto na farko a london suka yi shi, Hoto na biyu sunyi shi a ƙasar dubai,
sauran hotunan an dauke shi a dakin taron da aka gabatar da shagalin birthday din baba obie, Jiya kenan"
Abun kallo ya samu, Komawa zahra tayi gefen gadon ta ta zauna tana mai mamakin turo mata hotunansu
da hajiya saratu tayi? Takasa gane me take nufi da hakan.
Message ta gani daga ƙasan hoto na ƙarshw da sauri ta soma karanta shi kamar haka
*Daga Alƙalamin Boss Bature🫶*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida*[02/03, 6:31
PM] Anty Hajjo 2: ~TAKUN ƘARSHE~

_______________________Boss Bature✍️

Rubutun dake a ƙasan hoto na ƙarshe ta karanta kamar haka

_"If you had the chance to choose between them, which one would you like?"_

A ruɗe zahra take kallon screen din wayar, a ƙalla ta maimaita karanta sakon yafi sau a ƙirga, duk tabi ta
ruɗe ga wani farin ciki daya lullu6eta duk da bata gane me hajiya saratu take nufi ba.

Miƙewa tayi jiki na rawa ta fito ta nufi dakin Aneelerh.

Tana shiga ta taras da su suna Cin cake, Ita da baby junaid.

Jin motsin shigowarta yasa duk suka ɗago suna kallonta.

"Zahra, meye faru naga kina murmushi"?

"Aunty na, duba ki gani abun da hajiya saratu ta rubuta min" miƙa ma Aneelerh wayar tayi, bayan ta kar6a
ta soma duba hotunan, Baby junaid dake cin cake Ya ce"Aunty Zahra, Kin iya cake, Yayi daɗi, Idan Angel
dina ta dawo gida, zaki hada mata kalarshi"

ɗaga mashi kai zahra tayi"me zai hana my baby boy, ai dole baby Angel taci cake" Murmushi yasaki"thank
u sis zahra"

Ɗagowa Aneelerh tayi ta ɗaura idonta kan zahra dake atsaye tana kallonta.
"Na taya ki murna, wata'kil burinki ne zai cika, a fahimtana, Hajiya saratu tana son haɗa ki da ɗaya daga
cikin ƴa'ƴan ta shiyasa ta baki za6i"

Cike da kokwanton maganarta Zahra tace "Anya aunty Aneelerh? Gaskiya bana tunanin hakan, tayaya ma
zata hada ni da ɗanta? Ni da ba yar kowa ba, nifa nasan masu kudin nan basa auran bare sai dai yasu yasu
jinin arziƙi" cikin sanyin murya ta furta maganar"kuma ni waɗannan sunfi karfina wallahi, ko lokacin da
muke zuwa gidan yi masu hidima basu yi ma mutane magana suna da girman kai, idan muka gaishe dasu
da hannu suke amsawa, ko kallo ba mu ishe su ba"

Dariya Aneeleeh tayi"kin bani mamaki zahra, sai kace bake bace kike da burin auran Chief owais, sai gashi
yanzu kina maganar ƙannansa sun fi ƙarfin ki"

Dariya zahra tayi"ki gane mana, Chief Yafi ƙarfina nesa ba kusa ba, Haukana kawai nake Yi, daga baya
kuma na zauna nayi ma kaina karatun tanatsu, Na lallashi zuciyata na haƙura na barma Allah za6i"

Aneelerh na murmushi tace"Yanzu dai zoki zauna daga gefe na, In taya ki za6an wanda Ya dace dake, duk
da naga kamannin su ɗaya ban iya banbanta su"

Zama zahra tayi daga gefenta, hankalin baby junaid baya akansu, Ya samu cake sai ci yake yi duk ya 6ata
bakin shi.

Ƙura ma hotunan ido su ka yi"zahra idan hasashena ya zama gaskiya wani irin farin ciki za ki yi?

"Mara misaltuwa" amsar da zahra ta bata kenan.

"Za ki zama ɗaya daga cikin surukan Baba Obie, Uwa Uba ɗan gidan Hajiya saratu minister of health, gashi
itace autarsu, gaskiya zaki more wlh gata ta ko'ina zaki samu idan familyn suka kar6e ki hannu biyu" da
fara'a akan fuskarta ta yi magana.

Zahra bata ce komai ba, Ita dai gani ta ke kamar hakan ba mai yiwuwa bane

"A cikin su wanene ne yafi kwanta maki a rai"?

Aneelerh ta jefa mata tambayar

"Aunty aneelerh nabar maki za6i dan Allah, Ni kaina bana iya banbanta su, amma kamar wannan shine
Zayn idan kika kalli fuskarshi da kyau zaki fahimci yana da masifa" ta faɗa tana ɗaura yatsanta kan face din
Zayn.

Shi kuma wannan shine zaid a hasashena, Yafi zayn saukin kai.

Aneelerh tace ƙwara mai saukin kan, akan mai masifar, amma fa kamar yafi kyawun sura.

Zahra tace"Eh, hakane, zayn yafi zaid.

"Nidai nafi yi maki sha'awar zaid, indai yana da kyakkyawar zuciya"

Shiru zahra ta ɗan yi kafin tace"An ta6a faɗamin basa jin magana, kamar suna kula mata, Har page dinsu
na insta na ta6a shiga, suna yawan ɗaura hotunansu da matan banza masu bayyana tsiraicin su"

Yanayin fuskar Aneelerh ne Ya canza zuwa damuwa.

"Zahra kin tabbatar basu jin magana"?


Ɗaga mata kai zahra tayi alamar eh
Kwa6e fuska Aneelerh tayi"akwai matsala, but mommynsu tasan da hakan"?

"Bana tunanin ta sani, saboda mutane suna jin shakkar yi mata magana kinga kuwa babu wanda zai Iya
tunkararta da wannan maganar mara dadin ji"

"Banji dadi ba zahra, Har na fara yi maki murna amma yanzu sai naji abun ya fara fita raina, bazan hana ki
za6ar wanda kikeso ba acikinsu, Idan Allah yasa sanadin shiriyarshi ce sai kiga ya shiryu ta silarki, babbar
matsalar shine ace baya sonki, da ace idan ta haɗa kun zaku son juna har ma son shi ya rinja yi naki tabbas
zai Iya canza kanshi, amma idan ke ki ke son shi baya sonki baki Isa ki iya tanƙwarashi ba sai dai wani iko Na
Allah"

Jinjina kai zahra tayi ta gamsu da bayanin Aneelerh sai dai bata Jin zata Iya haƙura da damar da take da ita,
Allah na gani ta jima tana son Hajiya saratu da ya'yanta duk wani abu da zai hadasu son shi ta ke yi.

Cikin sanyin murya tace"Auntyna, addu'arki nake buƙata nima zan dage da addu'a, Idan Har dagaske zata
hadani da daya daga cikinsu toh Allah yasa ya zama alkhairi agare ni da kuma shi kanshi wanda zata haɗani
dashi din, Idan yana da kyan hali zanyi farin ciki, imma akasin hakan zan dauki hakan amatsayin ƙaddarar
rayuwata, Allah na gani Ni bazan Iya janye tayin da tayi min ba"

Dafa kafaɗarta Aneelerh tayi"Zahra, bana so ki jefa rayuwarki inda zaki ƙuntata, babban kuskure ne ki auri
miji mai neman mata, Ni nafison kiyi aure inda bazaki ta6a yin danasani ba, ko dan saboda Ƴa'ƴan da zaki
haifa yakamata kiyi nazari kafin ki yanke hukunci"

Damuwace ƙarara akan fuskar zahra, Ga samu ga rashi.

"Nagode da shawararki auntyna, but ni yanzu bansan wani amsa zan bata ba, gashi na riga da na bude
sakon zata ga alamar nagani"

Shiru Aneeleerh tayi naɗan wani lokaci kafin Ta furta"Ki bata amsa da sunan wanda ya birgeki, zamu jira
muga martanin da zata mayar mana"

Amsa mata tayi da toh, ta kar6i wayar daga hannun Aneelerh, sunan zaid ta rubuta ba tare data ankare ba
keyboard Ya canza mata sunan ya koma zayn, ahaka ta tura message din.

Bayan ta kammala ta soma daukarsu hotuna tare da baby junaid, sun dauki lokaci a dakin kafin suka fito
falo don ay fira dasu, Hajiya adama da uncle abdallah sun ji dadin tarbar da akayi masu, An mutuntasu an
kuma karramasu kamar kada su tafi, ga lafiyayyan abincin da su zahra suka girka masu, sunci sun ƙoshi sun
kuma sha fira, wuraren marece suka bar gidan.

*Shin Meke Faruwa A Obie Estate 🔥🔥🔥*

Bayan fitowar Chief owais da Prime minister Tare da Boss man, jami'ai suka yi gaggawar bude masu motar
da za su shiga.

Ta ƙofar baya suka bi wadda zata 6ular dasu zuwa cikin Obie estate, kasancewar Gidan Owais shine
ƙarshen ginin dake acan bayan estate din, Gate dinsa Biyu, akwai gate na gaba wanda zai fitar dakai titi,
Gate din baya kuma zai shigar dakai Cikin estate.

Prime minister Ne Ya buƙaci Yana son su fara zuwa gidanshi don su taho da sheikh imam kafin su wuce
gidan baba Obie.
Da matsakaicin gudu motocin suka ƙaraso babban katafaren entry na gidan prime minister dake a tsare da
jibga jibgan canadian polices da sojoji.

A harabar Ajiye motoci su ka Yi parking, A hanzarce Sojoji suka nufo motar, Tare da buɗe masu ƙofa.

Kusan atare suka fito, ba tare da bata lokaci ba, su ka ɗunguma zuwa babban falon gidan.

A lokacin Nazli tana zaune saman Sofa ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, Hankalinta na akan laptop dinta,
Yayin da Yazrin Take zaune a gefenta hannunta ruƙe da tsadaddiyar Wayarta.

Ba zato ba tsammani, sallamar su prime minister ta ratsa kunnuwansu.

Yazrin ce tayi saurin ɗagowa da idonta yayin da ita Nazli tayi tamkar bata ji sallamar su ba, dama
halintane idan tana aiki a laptop ba ƙaramin abu ke Iya dakatar da ita ba.

Tsantsar farin ciki ne akan fuskar Yazrin, da mamaki ta furta"Big Bro"! da sauri Ta miƙe ta nufe shi,
tunkafin ta ƙaraso Chief ya buɗe mata hannu alamar tazo gare shi, hartana tuntu6e garin sauri duk
zumuɗin ganin shi ne, prime minister Yace"bi a hankali daughter ba guduwa zaiyi ba" sai faman washe
mashi baki take Yi, hugging dinsa tayi, ya ɗaura hannayenshi biyu asaman Bayanta Yana ɗan bubbugashi
ahankali Ya furta"Long time no see, I missed You so much"

Ɗagowa tayi da kanta tana fadin"I miss you too, rabin raina You forgot about us, and you stopped coming
to Canada, ko kiran wayarka akayi baka picking" voice dinta tamkar zata fashe mashi da kuka Ta ƙare
maganar.

Ɗaura hannunsa yayi kan mayafinta"Am sorry, Kuna araina, aiki ne Ya 6oye ni, amma hakan ba yana nufin
aikina yafi ku mahimmanci ba, Ina fata kin fahimce ni" jinjina mashi kai tayi alamar eh.

Boss man Dake atsaye Yana kallonsu yayi mamakin yadda owais Yake Yi mata magana, bai ta6a ganin yana
sakar ma mace fuska haka ba sai Yau da Allah Ya kawo su gidan Prime minister, Hakiƙa Ya yaba da Haɗuwar
daular, sai yaji tamkar Yabar Nigeria ne, ga wani ni'imtaccen sanyin A.c mai ratsa hudojin fatar mutun, ya
yaba da kyawun Yazrin, Jefi jefi yakan dan saci kallon falon, badan Ya fito daga gidan chief Owais ba, da
Allah kadai Yasan ƙauyancin da taj zaiyi agidan prime minister.

"Mu shiga daga Ciki mutumina" Muryar prime minister ce ta fargar dashi daga tunanin da yake saƙawa
aranshi, Murmushi ya saki, Hateem Ya ruko hannunshi suka nufi jigunannun royal sofas din Falon masu
numfashi Ƴan ubansu afagen haɗuwa.

Yazrin ta ruƙe hannun chief Owais acikin nata, Har suka samu wuri suka zauna saman sofa, Lokacin da Taj
yai tozali da Nazli Har saida gabanshi Yadan fadi, aruɗe Yake kallonta sai ya dinga ganin fuskar Danish akan
fuskarta, Prime Minister ya lura da rudanin dake akan fuskarshi, gyaran muryar da yayi mashi ne yasa shi
yin saurin kallon shi, da ido yai mashi alamar ya yaganta, jinjina mashi kai Taj yayi, suka sakar ma juna
murmushi.

"Nazli" Prime minister ne Ya kira sunanta, A hankali Ta dago da fararen idanuwanta ta daurasu akan
fuskarshi.

"Dad, welcome back" ta fada ba tare da ta kau da idonta daka kallon shi ba.

"Yawwa, Baki ga mutanan da nazo da su ba" sai lokaci ta kalli Boss man tamkar bata son yin maganar ta
furta"Hey, How are you"

Fuskarshi da fara'a yace"lafiya lou fatan na same ki lafiya"


Amsa mashi tayi, harzata dukar da kanta Yazrin tayi saurin cewa"Sister, baki gaishe da big bro ba" ba tare
data kalle shi ba tace"Okey" Iya abunda ta furta kenan.

Tsantsar mamaki ne akan fuskar Boss man, ko a mafarki bai ta6a ganin mace mai izza irinta ba, bai ta6a
tunanin za'a Iya samun macen da zata kau da idonta daga kallon chief owais, sai akan Nazli.

Chief owais tamkar shima baisan da zamanta ba, hankalinshi na akan wayar hannunshi daya ruƙe Yana
daddanawa

"Nazli, ki gaishe da Yayanki" babu wasa akan fuskar Hateem Yayi mata maganar, tun daga kan Yanayin
yadda ya furta mata maganar zaka fahimci ranshi ya sosu da abunda Nazli tayi

Batare data dago ta kalli chief owais ba ta furta"ya kake"

Banza yayi da ita, har saida prime minister Ya ambaci sunanshi tukunna Yace"Uncle kada hakan Ya dame
ka, ka bar ni da ita, dai dai nake da ita" cikin nuna isa Yayi maganar.

Daure fuska Yazrin tayi, ranta ya 6aci bata ji dadin abunda Nazli tayiwa Chief fa, Kodan saboda baƙon da
suka zo dashi aganinta bai kamata tayi hakan ba.

Miƙewa tayi tare dakai hannu ta dauki laptop dinta, ko sallama babu ta nufi upstairs, sautin takalmanta
har cikin kunnuwan su.

Bayan tafiyar Nazli, Gimbiya Mujeedat ta sauko down cikin shiga ta alfarma, tunkafin ta ƙaraso take sakar
masu murmushi.

"Marhaban bika, My Son In-law, Long time bamu haɗu ba, dama kana a kasar," ta jefe mashi tambayar
tare da samun wuri ta zauna tana fuskatar su.
Ɗagowa chief Owais Yai tare da kallonta, da murmushin gefen fuska ya furta"ban jima da dawowa ƙasar
ba, nayi laifi ban leƙo mun gaisa ba, sai yau Allah Ya nufa" taj dake kallon gimbiya mujeedat afakaice Ya
jinjinawa haduwarta, mace kamar kanta aka fara tsara kyau ta haɗu ga Iya dattako.

"Sannu da dawowa Mijina, Ina fata anyi nasara"cikin kulawa tayi maganar tana kallon Hateem, lumshe
mata ido yai tare da ɗan jinjina mata kai alamar eh
Dauke idonta tayi daga kan fuskarshi ta dubi Taj, baiyi tsammani zata kula shi ba, amma sai yaga ta sakar
mashi murmushi tana fadin"barka da zuwa" yace mata yawwa.

"Mijina baka fadamin wanene wannan ba"?


"Sunanshi tajudeen, abokin aikin Owais ne"
"Masha Allah, malam Taj, naji dadin haduwa dakai, Ya aiki"?
Yace mata lafiyalou," sun ɗan ɗauki lokaci suna tattaunawa kafin daga bisani,
Prime minister Yace da ita"Sheikh Imam Yana aciki"?
"Eh, tun ɗazu daya zo, na kaishi masaukin da aka tanadar masa,"

"Okey, bari na shiga wurinshi" ya fada tare da miƙewa ya nufi Hanyar zuwa part din da shiekh Imam Yake.

Kafin dawowarshi, Biyu daga cikin masuyi masu hidima suka shigo falon, Hannayensu ruƙe da ƙayatattun
trays, daga saman an jera kayan abinci kala kala da drinks"

Cikin girmamawa suka gaishe da su tajudeen, kafin suka sauke farantan kan lallausan carpet din dake
awurin.
"Big bro, fadamin me kake son ci, zan zuba maka da kaina" yazrin ce tayi mashi maganar, girgiza mata kai
yai alamar a'a, zuciyarta ajagule tace"Pls, kada abunda sis nazli tayi maka Ya 6ata maka rai, kariga da kasan
halinta" calmly ya furta"okey" daga haka bata ƙara yi mashi magana ba, zuƙunna tayi batare da girman kai
ba tace da masu hidiman da suka kawo abincin ku tafi ni zan yi serving dinsu, tafiya sukayi, Ita kuma ta
zauna ta dauki lemu me sanyi ta tsiyaya shi a cup ta zuba ma Taj ta miƙa mashi.

Har cikin ranshi yaji dadin hakan, kuma ya yaba da hankalinta, tun anan Ya fahinci tafi sauƙin kai Akan Ƴar
uwarta Nazli, nan take Ya tuna da Halin Danish miskilancinshi sak kalar Na nazli ne, Aranshi yace Komai
nasu kala daya kamar ɗan uwanta"

"ya owais, zan je na dawo" yazrin ta fada Tana kallonshi, amsa mata yai da ok, da sauri ta nufi upstairs.

Bayan taj Ya kammala shan lemun, ya fara shan fresh fruit din da aka kawo masu.

Elevator Yazrin Ta hau, ta sauke ta a second floor, moving quickly Ta nufi ɗakin Nazli, a buɗe ta samu ƙofar,
zura ƙafarta keda Wuya ta fara Cin karo da takalman Nazli a tsakar daki, Ga mayafinta kan floor, Da sauri
takai idonta kan katafaren gadonta, tana daga kwance doguwar sumar kanta ta lullu6e mata bayanta.

Cikin sanyin murya Yazrin ta soma Yin magana tana tunkararta.

"Sister, Meyasa kika za6i ki ƙuntatawa zuciyarki? kina sonshi amma meyasa kike ja mashi aji"? Shiru Nazli
bata tanka mata ba, babu lamun zata motsa.

"Ni banga amfanin 6ata mashi rai da ki ke yi ba, da hankalinki da tunaninki, gaban baƙon daddy, kike nuna
ba'a isa dake ba, wannan ba ɗa'a bace, shi kanshi daddy ranshi ya 6aci da abunda kikayi," dakatawa ta
danyi da yin maganar tana kallon Nazli dake kwance tamkar maiyin bacci.

"Nasan kina jina, ban damu ba dan kin share ni, Nidai shawara nake baki a matsayina na ƴar uwarki mai
son farin cikinki, kada kiyi wasa da damarki, mata dayawa suna hauka akan son Ya owais, basu ta6a samun
damar yin tozali dashi ba, amma ke cikin sauƙi Kin same shi, Kina ƙoƙarin Yin watsi da damarki, bana son
kiyi danasani sister," har cikin zuciyarta take furta kalaman.

"I thought when you saw him, you would rush to hug him and tell him how much you missed him, but sai
naga akasin hakan, wai yaya owais kika share kamar wani tsaran wasan ki, ki daina ganinshi kamar wani
tsaranki, kafin a haife ki shi aka fara haihuwa"

Shiru Nazli bata motsa ba, Yazrin taci gaba da cewa"Ki cigaba da ja mashi aji, wata rana zakiyi danasani,
Allah yasa Ya auri wata bake ba...." kafin Ta ƙare maganar A fusace Nazli Ta yunƙura ta miƙe zaune Ta
rarumi laptop dinta dake agefenta, daga Inda take ta daddage ta wurga ma Yazrin ita, da sauri Yazrin Ta
tarbe laptop din da hannu biyu, fuskarta dauke da murmushi tace"kinji haushin magana ta ne"? Kaɗan kika
gani, sai ma ranar da za'a shafa fatihar auranshi, Haukan da za ki yi sai yafi wannan" wurga mata laptop din
Yazrin tayi kafin ta juya da gudu ta fuce daga dakin ganin yadda Nazli take huci.

A hankali ta ɗaura kanta saman pillow, haɗi da lumshe idanuwanta, red lips dinta sun ciza launinsu, ita
kadai tasan irin radadin da take ji aduk lokacin da tayi ma owais haka, ita aganinta batayi laifi ba, shi
yakamata yazo inda take don ya nemi afwarta akan tsawon lokacin daya ɗauka ba tare daya je canada ba,
Alƙawari ne ta ɗaukarwa kanta idan har baizo wurinta Ya wanke kanshi ba ita kuma har abada bazata ta6a
kula shi ba, koda an shafa fatihar auran su!!!
Don ita ba irin matan da namiji Yake juyawa bace, macace mai aji, mai kuma Ji da kanta, zata iya haƙura da
komai akan izzarta.

Idan muka koma Falo, Bayan ƴan mintuna, Prime Minister Ya shigo falon tare da Shieikh Imam, sai kuma
gimbiya Mujeedat, miƙewa Chief Owais Yai shima Taj Ya miƙe, suka yima Gimbiya mujeedat sallama kafin
suka dunguma zuwa harabar ajiye motocin gida, jami'ae suka buɗe masu ƙofa suka shiga, Ajere motocin
suka nufi gidan baba Obie.

*BABA OBIE*

Bai jima da farkawa daga bacci ba, jikin shi yayi tsauri, wani irin azababben zazza6i ne Ya lullube shi, har sai
da Senator Lateef ya kira family doctors din su, domin duba lafiyar mahaifinsu, a ƙalla likitocin sun ɗauki
tsawon mintuna talatin akan shi suna ƴan bincike binciken su, kafin daga bisani suka tabbatar masu da
cewa Firgici ne da tsoro ke damun shi, Idan Har ba'ayi gaggawar kawar mashi da abunda ke razanar da shi
ba, zuciyarshi zata Iya bugawa, Jin wannan maganar daga bakin likitocin yayi matuƙar ƙara ɗaga
hankulansu, musamman Hajiya saratu duk tabi ta ruɗe, hannayenta biyu asaman kanta take ambaton Inna
lillahi wa inna ilaihirraji'un, mun shiga Uku, Ƙiri kiri ana so aga bayan uban mu.

Bayan tafiyar Likitocin, gaba ɗayansu suna adakin Obinna, zuciyoyinsu cike da jimamin sakamakon ciwon
shi, ya kasa ta6uka komai, duk ya yamutse tsufanshi Ya ƙara bayyana, Senate lateef ne ya taimaka mashi ya
shiga bathroom yai wanka, ya fito ya canza suturar jikinshi, Kafin Ya shimfiɗa mashi darduma, acikin dakin
yai sallar da bai samu damar yi ba, sam babu natsuwa atattare da shi, bayan Ya kammala Yin sallar ne,
senate Ya ruƙo hannunshi, Ya zaunar dashi kan lallausan carpet, da sauri His excellency abdul razak Ya miƙe
daga kan arm chair din da Yake azaune Ya nufi Kayan abincin da Hajjaty ta kawo mashi, Ya sanya hannu
biyu ya ɗauko su yaje ya ajiye farantin gaban Baba obie.

Saukowa Hajiya saratu tayi daga gefen gadonshi, ta zauna gefenshi idanuwanta acike tab da hawaye take
yi mashi sannu.

"Babana Allah Ya baka Lafiya, Ka daure ka ci abinci, sai kasha maganin zazza6in da likita Ya bada abaka"
cikin kulawa tayi mashi maganar, a raunace ya ɗago da idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur dasu Ya
ɗaura su akan fuskar Saratu na tsawon mintuna biyu, kafin ya kau da idon Ya dubi Senate Lateef da ke
ƙoƙarin zama gefen gadonshi, A hankali Ya maida idonshi akan fuskar His excellency deen da Pravin
waɗanda ke A zaune kan carpet.

Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi, kafin ya ware su kan fuskar Twins dake zaune kan carpet kamar wasu
mutanan kirki, sun yi zaman cin tuwo kowa da abun da Yake saƙawa aranshi.

"Sannu baba, Allah Yabaka Lafiya," su twins ne sukayi mashi ya jiki, kafin sauran mutanan dake adakin
suma sukayi mashi Ya jiki, bai samu damar amsa masu ba, Sai dai bin dakin da yake yi da kallo.

Muryarshi adisashe Yace"Hateem baizo bane ko baku fada mashi halin da nake aciki ba"?

Shiru su ka yi jin, kowa yana jin fargaban fada mashi abunda Prime minister Yayi.

"Kunyi shiru bakuce komai ba! ina Owais? Yace min zaizo yau ya akai ban gan shi ba"? fuskarshi ɗauke da
matsananciyar damuwa Ya furta maganar.

Hajiya saratu ce tayi ƙarfin halin buɗe baki, ta labarta mashi abunda Pravin Ya fada mata dangane da tura
jirgi da hateem yayi zuwa Sudan dan adauko Sheikh imam Ya duba jikin Yaron daya rikiɗa Ya koma maciji.

Tsabar 6acin raine tsantsa akan fuskar Obie,

Senate Lateef yace"tun safe babu wanda ya kira awaya cikin su don ya tambayi ya ka kwana, Gaba ɗaya
sun ɗaura burin duniya akan Yaron da muke zargin Abokan hammayar mu ne suka turo shi donsu tarwatsa
zuri'armu" afaɗace senate Lateef Yayi maganar
His excellency deen Yace"gaskiya bamu ji daɗi ba, Hateem bai kyauta mana ba, yayi abu gamon kanshi
batare daya nemi sha'awar mu ba, ni narasa gane meke damunsu daga shi har Owais din idanuwansu sun
makance basa ji basa gani indai akan taimako ne, toh gashinan dai suna ƙoƙarin jefa rayuwar mahaifinmu
cikin matsala, Fisabilillahi Ina amfanin hakan"? Ya ƙare maganar tare da jan dogon tsoki.

Tun da suka fara magana, Pravin Yake ta tsuma, tsabar zumuɗun su ƙare maganarsu don ya samu damar
tunzura su, ganin Deen Ya dasa aya a maganarshine ya samu ƙwarin gwiwar cewa
"Yakamata ayi gaggawar ɗaukar mataki akan Yaya Hateem, Shina fi ji, duk da ba fata nake Yi ba, amma
idan wani abu Ya same shi, Ba iya family din mu Ya shafa ba, Nigeria gaba daya ya shafa, ƙasar da yake
mulka bazasu ta6a sassauta mana ba idan wani abu ya samu shugabansu, koda kuwa kwarzane ne Ya fito
akan fatarshi sai sunji ba'asi" maganar pravin ta ƙara ɗaga masu hankulansu, babu wanda yai wannan
tunanin saida Ya furta tukunna suka ankara da gangancin da suka Yi.

Ganin yadda suka ɗaga hankalinsune Yasa shi ƙara samun kwarin gwiwar cigaba dayin magana.

"Ga kuma mahaifinmu babu ƙoshin lafiya, ba zamu zuba ido muna ganin wani bakon abu na neman yi
mashi illa ba, dole mu dauki mataki, wallahi indai akan baba ne sai inda ƙarfin mu Ya ƙare, dole Yaron
Yabar estate din nan, ai nan ba gidan marayu bane" ya faɗa yana mai nuna 6acin ranshi
Senate Lateef Yace"Sannan, shi kanshi Owais din zamu Yanke alaƙarshi da Yaran! Babu shi babu su, shi
kuma Hateem tunkan Aje ko'ina, acikin satin da zamu shiga Ya tattara Ya koma canada, don ba zamu bari
Yaja mana bala'e ba, Idan muna son ganinshi koda duk weekend ne zamu iya zuwa canada wannan ba
damuwarmu bace, awurinmu tamkar zuwa kano ne"

Duk maganar da sukeyi akan kunnan Baba Obie, yayi shiru Yana sauraronsu, abincin ma Yagaza cin shi,
hajiya saratu sai lalla6a shi takeyi akan yaci amma Yaƙi Ya, Ranshi Ya 6aci matuƙa, bakomai yafi ƙona mashi
rai ba face rashin zuwan Hateem da Owais, bayan sunga halin daya shiga adaren Jiya, maimakon su mayar
da hankali wurin kwantar mashi da hankalinshi, sai suka ta'allaƙa wurin Kula da abun da Ya cutar da
rayuwarshi, me hakan Yake nufi?

"Baba dan Allah kaci abincin idan ba haka ba Hankalina bazai kwanta ba" hajiya saratu ce tayi mashi
maganar yayin da take miƙa mashi abincin data ɗebo a cokali, kawar da kanshi gefe ɗaya yai batare daya
furta mata magaba ba.

"Grandfa, please kaci abinci, gaba ɗaya mun damu da halin da kake aciki" zaid ne yayi maganar.
Kafin wani Ya kuma furta magana, Suka soma Jiyo dirar motoci acikin Estate din
"May be sune suka ƙaraso" Acewar His excellency abduk razak.

"Anya kuwa sune? Naji ɗazu Yaya deen ya kira Yaya sharafuddeen nafi tunanin shine Yazo" Pravin ne yai
maganar, dakatawa su ka yi da yin magana, gaba ɗaya hankalin su ya koma akan ƙofar dakin, sunyi matuƙar
ƙagara da son ganin wanene zai shigo.

Knocking ƙofar dakin Akayi, Pravin Ya ɗaga murya tare da cewa"ku shigo daga ciki"

Lokacin da ƙofar ɗakin ta buɗe, Prime Minister Hateem Ne Ya fara shigowa yana maiyi masu sallama, Chief
Owais Yana abiye da bayanshi, su kadai suka shigo, Boss man da sheikh Imam suna acan babban falon
gidan suka zauna saman sofa.

Tun da suka shigo dakin kowa yayi shiru yana binsu da kallo, su kansu sun fuskanci babu Lafiya, cikin
girmamawa Hateem yabi ƴan uwanshi ɗaya bayan ɗaya ya gaishe da su, fuskokinsu babu walwala suka
amsa mashi, chief Owais ma Haka yabi kowan nan su ya gaishe da shi, banda Pravin, baya acikin jerin
mutanan da suka kai matsayin da zai iya gaishe da su, tunfil azal basu jituwa, shiyasa hajiya saratu take
matuƙar jin haushin Owais, saboda ƙiyayyar da yake nunawa mijinta, ko yanzu daya gaishe da ita daƙyar ta
amsa mashi tana faman yamutsa fuska.
A hankali ya zauna daga gaban farantin kayan abincin baba Obie, wanda tun da suka shigo ɗakin
idanuwanshi suke akan fuskokinsu, Idan ya kalli prime minister sai Ya kalli Owais, har gaishe da shi su kayi
bai amsa masu ba, hakan ba ƙaramin ɗaga hankalin prime minister yayi ba, don wannan alama ce dake
nuna cewa mahaifinshi yana fushi da shi.

da sauri Zayn da zayn suka haɗa baki wurin gaishe da Prime minister, bayan ya amsa masu suka gaishe da
chief Owais, shima ya amsa masu fuskarshi babu walwala, daga haka babu wanda ya ƙara furta magana,
munafuki pravin a fakaice yake sakin shu'umin mirmushi, wato haƙarsa ta cimma ruwa

Baba Obie, Ya tsayar da idanuwanshi akan fuskar Owais, kamar yadda yake kallon shi shima haka yake
kallon shi

"Hateem, meyasa tun safe bakazo gida ka duba ni ba"? Baba obie ne Ya jefa mashi tambayar.

Daƙyar Ya iya buɗe baki Yace"Kana araina baba, nasan ban kyauta ba na rashin zuwana, ka gafarce ni"

"Baka fada min me ya dakatar dakai daga zuwa ba? Shi nake son ji"

Da sauri Zayn da zaid suka miƙe ganin irin kallon da hajiya saratu tayi masu alamar su tashi su tafi, salin
Alin suka fuce daga dakin

A tsanake Prime minister Ya labarta mashi abun da Ya faru.

"Saboda wa kazo ƙasar nan"?

Jim ya ɗanyi kafin Ya furta"saboda kai babana"

"Taya za'ai nayarda da maganar ka Hateem? Abun da Ya cutar dani daren Jiya shi ka tsaya taimako, tun
safe kana can kana yi mashi hidima, yayin da ni kuma nake kwance ba lafiya"

Tuni prime minister Yasha jinin jikinshi, duk sai yaji ba dadi, zuciyarshi ta karaya
"Baba bansan baka da lafiya ba, dan Allah kayi hakuri idan na 6ata maka rai, amma ka riga da kasan halina
kuma kaine kake ƙarfafa min gwiwa akan yin taimako, ka sha fada mana tun muna yara idan muka ga
mutun na buƙatar taimako to mu taimaka masa da abun da muke dashi, kada mubarshi hakanan, Yaran
nan bayin kanshi bane, ƙaddarace ta afka mashi, baida kowa marayane, Yana buƙatar waɗanda zasu tallafi
rayuwarshi.... "Kafin Ya ƙare maganar, Pravin yayi kuskuran katse shi da cewa "yaya kai ne baka fahimta
ba, Yaron nan maƙiya ne suka turo shi don su tarwatsa zuri'armu, idan ba haka ba ta ina mutun zai Iya
rikiɗa ya zama maciji? Sannan ya rasa inda zai faɗo duk gine ginen dake a estate din nan na kusa da gidan
Owais din bai shiga cikin su ba sai nan zai faɗo"? Daƙyar Ya ƙare maganar, ganin wani mugun kallo da chief
owais Ya watsa mashi, nan take Ya haɗiye yawu ya soma ƴan kame kame
Rai amatuƙar 6ace yace"malam, fuce kabar ɗakin nan, meye alaƙarka damu da har zaka katse Prime
minister Yana magana, wannan abune daya shafi dangin mu bana ka ba" Tsabar mamakin kalaman Owais
Yasa kowan nan su Ya dube shi, musamman Hajiya saratu ta muzanta da jin cin mutuncin da Owais Yayima
mijinta.

Babu kunya Pravin Yace"Owais kai har yanzu yarone, duk abunda zaka fada min ba zan ji haushi ba, Ina yi
maka uziri, kuma magana da kaga Inayi don in kare dangin ku ne saboda halaccin da kuka Yi min....."
Azafafe Owais Ya yunƙura Ya miƙe tsaye, Yana naɗe hannun rigarshi tamkar Mayun wacin zaki haka Ya
tunkari Pravin, An rasa wa zai dakatar dashi, kafin Owais ya ƙaraso Pravin yayi saurin nufar ƙofa ya buɗe ya
fuce yana huci Ya maida ƙofa Ya datse.

Juyawa owais yayi ya koma inda ya tashi ya zauna.


Da buɗar bakin Prime minister sai cewa yayi"My son ka yi abunda Ya dace" wannan maganar Ta hateem
ta ta6a zuciyar Hajiya saratu
Ranta a6ace tace"yaya hateem, kana goya mashi baya saboda Yaci mutuncin mijina"?

Prime minister bai tanka mata ba, bai kuma ɗago da ido Ya kalle ta ba. Hakan Ya ƙara 6ata mata rai,
harara tadinga jefawa Owais Ko kallo bata ishe shi ba, baima san tana yi ba.

Shi dai baba Obie, Ya zubawa sarautar Allah ido, don wannan fadan Yafi ƙarfin shi.
His excellency abdul Razak ne Yace"Owais, Kai muke sauraro muna son jin ƙarin bayani dangane da Yaron
daya rikiɗa da kuma Yarinyar dake atare da shi"

Kusan mintuna da Yin maganar abdul Razak Kafin Ya furta"Marayune su goma sha ɗaya nake ruƙo a
hannuna, dukansu agidana suke da zama, a ƙarƙashin kulawata," Iya abunda Ya furta mashi kenan
"A ina ka tsince su"? Shiru yayi bai bashi amsa ba Har saida His excellency abdul Razak Ya maimaita mashi
maganar a tunaninshi kobai ji mai yace bane
"Sojojin america ne suka tsince su A daji, shine suka damƙa case dinsu a hukumarmu, saboda Yaran sun
faɗi cewa Su Ƴan Nigeria ne, ɗaya daga cikin Yaran ma akwai mahaifinta mun same shi, muna zargin
masuyin garkuwa ne suka sace su daga Ahlin su, shi kuma yaron aljanune suka shige shi a dajin sune suke
canza mashi halitta, wannan shine Iya abunda nasani dangane da su" atakaice Ya ƙare bayanin.
Gyaran murya senate Lafeef Yayi kafin Ya soma magana
"Mun riga da mun Yanke hukunci, Bamu buƙatar Yaran su ci gaba da zama a estate dinmu! Saboda Lafiyar
mahaifinmu, sannan mun yanke alaƙarka da su, shi kuma prime minister zai koma canada adai dai date din
da aka bashi umarnin komawa, don ba zamu lamunci gangancinku na son taimako Ya jefa rayuwar Ahlinmu
cikin matsala ba, don ni har Yanzu ban yarda da Yaran ba, tunkafin ma in gansu Hankalina bai kwanta da su
ba, tayaya za'a tsinci Yara adaji sannan akawo su estate dinmu? Meyasa su sojojin american basu ruƙe su
ba a hannunsu ba? Saboda sunsan ba alkhairi bane shiyasa suka manna maku su" fuskar shi babu annuri
yayi maganar.
Hankalin prime Minister Ba ƙaramin tashi yayi ba Jin abunda suka ce, kasancewar shi mutunne mai
biyayya ga yayyan sa ko kara suka ajiye mashi bai iya ƙetare wa, mutun ɗaya ne zai Iya dakatar dasu wato
mahaifinsu sai dai ga dukkan alamu shima Yana goyan bayan hukuncin da suka Yanke,
Muryarshi asanyaye ya furta"kada kuyi min haka, saboda ku nazo ƙasar nan a ƙalla nakusa shekara ban
samu damar zuwa gida ba, Yanzu Idan na koma bansan ranar dawowa ba, Baba ka sanya baki a maganar
nan"

His excellency Deen dake zaune Yace"Idan saboda mu kazo ƙasar nan, kada ka damu, ka tafi kawai mu
zamu zo inda kake, idan ma takama duk sati zamu Iya shigowa Canada kasan bamu da matsalar abun
hawa" ya faɗa yana ƙara jaddada mashi"zamu Iya barin aikinmu mu ɗauki hutu saboda kai, munyi maka
alƙawarin hakan, zamanka a ƙasartamu ne bamu yarda da shi ba, don ba zamu yi gangancin da zaka cutu
ba har wani abun Ya same ka, Idan ka manta wanene kai bari in tuna maka, prime minister na ƙasar
canada" duƙar da kanshi ƙasa yai hawaye tuni sun cika idanuwanshi, bakomai yake jimawa ba face Yaron
daya ƙwallafa ran shi, yasan idan harya haura ƙafa yabar ƙasar nan da wuya su sake haɗuwa, watakil ma
daya daga cikinsu yabar duniyar batare da sun yi tozali da juna ba.

Jikin Chief owais yayi sanyi laƙwas, hankalinshi na akan prime minister, shi kadai Yasan damuwarshi

His excellency abdul Razak ya numfasa kafin ya ɗaura da cewa"kai kuma Owais, ba zamu hana Ka Yin aikin
ka ba, sai dai babu zancen Yara su cigaba da zama agidan nan, ka kaisu gidan marayu ka haɗa su da
wadanda zasu cigaba da rainonsu"

Takaici Ya hana Chief Owais furta masu komai, gaba ɗayansu hankalinsu ba akwance Yake ba.
A hankali Baba Obie Yake kallon fuskar Prime minister data Chief owais, ga dukkan alamu Ya fahince su
sai dai Yana jin tsoron wani abu Ya same su ta silar taimakon da suke Yi, shiyasa bai dakatar dasu senate
lateef ba.

"Baba, dan Allah kace wani abu, nasan zaka fahimce ni, wallahi Ina ƙaunar Yaron, baka ganshi ba Yana
kama dani da Nazli, komai namu iri ɗaya kamar ni na haife shi" muryarshi tamkar zai fashe da kuka yayi
maganar, basu ta6a ganin raunin prime minister ba sai Yau da Allah Ya jarabce shi da ƙaunar wani bare

"Hateem! Wannan bai shafe mu ba, kowani ɗan adam yana da masu kama dashi a duniyarnan, shi kuma
mugun mutun ba'a gane shi a suffar shi yakan shiga cikin mutanan da yake hari yayi rayuwa dasu na
tsawon lokaci Yana kyautata masu rana ɗaya yake tarwatsa su da makircin shi, na fadi wannan maganar ne
don ni har yanzu ban yarda da yaron ba, dashi da sauran ƴan uwanshi, mutanan da aka tsinta a daji, wama
yasani ko ƴa'ƴan aljanu ne kuka dauko mana" senate Lateef ne ya faɗa Yana watsa hannayen shi.

A hankali prime minister Ya zura hannu cikin aljihu ya ɗauko wayarshi, wadda tun safe rabon shi da ita, a
gida yabarta gudun kada atakura mashi da kiraye kirayen waya, sai ɗazu da suka shiga gidan Ya kar6eta
daga hannun gimbiya mujeedat.
Layin Sharufudeen Ya dannawa Kira, bugu uku Yai picking,
"Ina agida, dan Allah kazo, idan ba haka ba komai zai Iya faruwa"
On the other hand muryar sharafuddeen Ta amsa mashi da toh, gani nan zuwa, ka kula min da kanka"
amsa mashi yai da toh kafin yai rejecting kiran
"Meye amfanin Kiran Sharafudden da kayi? Dakai dashi duka a ƙarƙashin ikon mu kuke, mune agaba
daku" cikin nuna isa senate lateef Ya furta maganar
Cikin sanyin murya Hateem Yace"nasan da hakan Yaya, amma shi zai Iya fahimtar zuciyata fiye da kowa,
kuma zai kwantar min da hankalina"

"Kana nufin mu bamu Iya kwantar maka da hankalinka? Kodan saboda shine shaƙiƙinka"? A harzuƙe
senate Lateef Ya furta maganar
Da sauri Baba Obie Yai masu gyaran murya gudun kada su fara Yi mashi ƴan ubanci abun da Ya tsana
arayuwarshi.

Gaba ɗaya Hankalinsu ya dawo kanshi"Ya Isa Haka! ya Isa, bana son nasake Jin wani Ya furta magana
acikin ku" Shiru sukayi batare da wani ya kuma cewa Uffan ba
"Baba abincin fa Yana hucewa, Yakamata Kaci" hajiya saratu ce tayi maganar cikin nuna damuwarta
Kallon Owais yayi nan take Ya fahimci me Yake nufi
Hannu owais Ya sanya cikin plate din da hajiya saratu ta zuba mashi abinci

Ya soma ɗebowa Yana bashi abaki Yana ci,


Hakan Ya ƙara 6ata mata rai, wato ita ta bashi abinci da hannunta Yaƙi Ci sai Owais daya fi ƙauna, shi ya
za6a ya bashi abinci
Bazata juri kallon su ba, miƙewa tayi tana fadin"Baba Allah Ya ƙara Lafiya, Ni zan wuce ɗaki" bata jira
amsar da zai bata ba tayi saurin fucewa daga ɗakin.
Senate latef ma ranshi ya sosu, duk irin rashin ɗa'ar da Owais Yayi ma Pravin baba obie bai dakatar da shi
ba, after that Ya sanya shi bashi abinci abaki, bayan Hajiya saratu itace tafara Yunƙurin bashi amma Yaƙi
kar6a, ba tun yau ba ya saba nuna banbanci akan Sauran Jikokinshi da Owais, Hatta Ya'yan Hateem Yafi Ji
da su akan nasu me hakan ke nufi"? Aranshi ya saƙa maganar

(Nidai nace na shiga uku, Kada afara Ƴan uba A family Obinna, Rikicin zai haɗe mana)

Yayin da chief Owais Yake ba baba Obie abinci abaki, Ya tsare shi da ido Yana bin shi da kallon so da ƙauna
kamar zai haɗiye shi, Lemu mai sanyi ya zuba mashi a cup Ya miƙa mashi, Ya sanya hannu Ya kar6a Yana
sha, har cikin ranshi Yaji dadin hakan aduk lokacin da ranshi ya 6aci indai Owais Yana atare dashi wani irin
sanyi ne yake ratsa zuciyarshi tuni yake neman damuwar Ya rasata.
In a respectful voice Chief Ya soma yi mashi magana, ta yadda babu mai iya jin su.

"Kai kadai ne zaka Iya fahimtata, saboda kai ka raine ni tun ina ƙaramina, aduk lokacin da na sanya buri
akan abunda nakeson cimmawa kaine kake ƙarfafa min gwiwa don ganin nakai ga matakin nasara, babana
kada ka bari wannan karan in faɗi ƙasa, yakamata ka sanya baki awannan maganar, kasan bazan ta6a kawo
wani abu da zai cutar dakai ba, Haƙƙina ne in kareka daga dukkan wani abun farmaki, yaran nan mutanene
kamar kowa, basu da niyar cutar da kowa, saida na zurfafa bincike akansu na tabbatar da hakan tukunna
na kawosu cikin gidana, bazan Iya yin nesa da su ba, Kuma bazan Iya dakatar da hukuncin da iyayena suka
zartarba, amma kai zaka Iya dakatar da su,' cikin tausasa harshe Ya ƙare maganar tare da ruƙo hannayen
baba obie acikin nashi, Ya ruƙe su sosai.

"Baba, Yaran nan basu da kowa, suna buƙatar wadanda zasu tallafi rayuwar su, nasani ba dole saini zan
taimake su ba amma na riga dana daukarwa kaina alƙawarin bazan ta6a rabuwa dasu ba, A yau ina so ka
nuna min ƙaunar da kake Yi min, da goyan bayan da kake bani, baba kada ka bari arabani da yaran nan ko a
tursasamin akan in fitar da su daga gidana......." yanayin yadda owais yake yi mashi maganar yayi matuƙar
karya mashi zuciya, tuni jikinshi yayi sanyi laƙwas, launin idanuwanshi har sun ɗan canza kala.

Shi kadai Yake jin me owais Yake Fadi mashi, sauran saidai su bi da ido, prime minister dai tunda ya dukar
da kanshi kasa bai ƙara dagowa ba, shi kadai Yasan abunda ke damun shi, zuciyarshi tafarfasa take yi
tamkar ana rurata da garwashin wuta, Aranshi ya ayyana koda zai bar ƙasar bazai daina bin diddigin
rayuwar yaron ba, bazai ta6a bari Ya wulakanta ba.

Lumshe ido Obie Yai a hankali ya ware su kan fuskar Owais


"Zanyi tunani akai" atakaice Ya furta mashi maganar, ajiyar zuciya chief owais ya sauke, ya riga dayasan
ƙaunar da yake mashi bazai Iya jurar 6acin ranshi ba
"Allah ya ƙara maka lafiya kakana, da anjima kafin ka kwanta bacci zanyi maka tausarnan dana saba yi
maka duk idan nazo nigeria, nasan zaka ji daɗi"
Dariya baba Obie Yai har hakoransa suka bayyana fafare ƙyal da su
"Owais ka iya fadanci, kasan duk wata hanya da zaka faranta min, Allah yabarmin kai jikana" amsa mashi
yai da Ameen.

daga haka basu ƙara Yin magana ba, sai dai kallon juna da sukeyi jefi jefi, su sanate lateef sun zama Ƴan
kallo, kamar hotuna haka suka zauna zugudun suna kallon su.

Bayan wani lokaci Jiniyar Motoci ta karaɗe Estate din, nan take ransu Ya basu cewar Mai girma
sharafudeen ne Ya ƙaraso gidan, tun abakin entry hall din shiga falo, Security details dinshi suka dakata da
take mashi baya kamar yadda ya basu umarni, shi kadai Ya shiga Gidan Cikin shiga ta alfarma tsadaddiyar
shaddace a jikinshi launin kore, duk Inda Ya gifta masu aikin gidan a gaggauce suke russinawa su gaishe
dashi kamar zasuyi mashi sujjada, A main falo din gidan Yaci karo da sheikh Imam tare da Taj zaune saman
Royal sofa, Hankalinsu kwance suke tattauna fira atsakaninsu, sunyi jiran ganin mutanan gidan shiru basu
fito ba har sun fara tunanin kodai babu lafiyane? Musamman lokacin da pravin ya fito daga dakin baba
obie ko kallo basu ishe shi ba, har kallonsu yayi amma yaƙi tanka masu, hakan ya sosa zucuyarsu, haka
itama hajiya saratu tazo ta wuce ta falon bata bi takansu ba, har ƙwara su twins sun gaishe da sheikh
Imam, suka kuma gaida Taj kafin suka wuce.

Zuwan sharafudeen Obinna, Ya faranta masu rai, tunkafin Ya ƙaraso garesu Yake Fadin"wa nake gani kamar
babana Imam malik," miƙewa Imam yayi ya nufe shi suka rungume juna kafin suka raba jikinsu
"Ashe rai kanga Rai? Baba Imam sai yau zansa ka a idona? Gaskiya nayi fushi" Ya faɗa Yana haɗe fuskarshi
Dafe kafaɗarshi sheikh Imam Yayi"Masha Allah, Sharafuddeen Bana ƙasar, shiyasa baka ganina akai kai,
amma yanzu tunda nazo in sha Allah zan dinga shigowa Villa muna gaisawa'
Sharafudeen na murmushi Yace"Idan ma bakazo ba, Ni zanzo har inda kake, wallahi nayi farin cikin
ganinka, tun yaushe kazo ƙasar"
Shiekh Imam Yace"Yau da sassafe Nayi sammakon shigowa ƙasar, saboda kiran da ɗan uwanka yayi min"

"Masha Allah, Ina fata komai lafiya"


Sheikh Imam Yace"lafiyalou, Ga abokin Aikin Owais Ku gaisa da shi" Ya faɗa Yana nuna mashi tajudeen
dake azaune, kamar ya sanshi haka Ya nufe shi da fara'a, da sauri Taj Ya miƙe suka rungume juna, haƙiƙa
yasha ruwan mamaki, bai ta6a ganin mutane masu ruƙe da babban muƙami da suke da sauƙin kai irin
Hateem da ɗan uwansa sharafuddeen, yajima yana mamaki da al'ajabinsu, kowa nasu ne basu ɗauki
duniya da zafi ba.

Raba jikinsu yayi daga na juna"yalla6ai sannu da zuwa, Ina wuni, Ya hidima da jama'a, ubangiji Allah ya
taimaka"
"ameen mutumina, Ina fata na same ka Lafiya"da mamaki Taj yake kallonshi jin ya kira shi da sunan
mutumina kamar yadda yaji ɗazu Hateem Ya kira shi da sunan
Ganin alamun ruɗu akan fuskarshi yasa mai girman sharafudeen cewa"Owais Ya fada min komai dangane
dakai, ganinka ne kawai ban ta6a yi ba, nasan zakayi mamaki dana gane ka ba tare dana tambaya ba" ya
faɗa yana sakar mashi murmushi, shima taj din murmushin yayi har cikin ranshi ya ƙara ƙaunar Chief
owais.
"Babu isasshen lokaci, In sha Allah zan samu time din da zamu tattauna dakai" ya fada Yana bubbuga
kafaɗar taj da hannunshi.
"Toh Yalla6ai, nagode sosai" kallon shiekh Imam yai"baba mu shiga daga Ciki" yai maganar tare da ruƙo
hannunshi suka nufi part din baba obie,

Zama taj yayi akan sofa, fuskarshi ɗauke da murmushi, Ji yake tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha, acikin
ranshi ya furta"Allah nagode maka da haɗani da mutanan kirki acikin rayuwata"
Wayarshi Ya zaro daga aljihu ya soma tunanin Kiran Big guy don Yaji awani hali su Unaisah suke aciki sun
ci abinci ko kuwa.
Kiran na shiga big guy yayi picking
"Ya mutumina kana Ina ne? Na dawo gidan na taras baku nan"
"Mun shigo gidan baba Obie ne mu dukanmu muna anan"
"Okey, Ina fata komai na tafiya yadda yakamata"
"Taya zan sani, nifa ka ganni nan a falo, Ina zaman jiran fitowarsu, Allah yasa dai mu ji alkhairi, don kuwa
naga wannan ba'indiyan da kake bani labari sai mazurai yake yi, ko gaishe mu bai yi ba"
Sautin dariyar big guy ne Ya karaɗe kunnuwanshi
"Itama wannan matar, mai kama da su chief owais ta fito tagan mu bata gaishe damu ba"
"Dama ya za'ae ta gaishe dakai, taga baƙuwar fuska, matar da bata sakar ma bare fuska, sai dai shi sheikh
Imam din ne dai bata kyautaba tun da aminin baban su ne, wata'ƙilma bata ganku bane shiyasa bata
gaishe da shi ba"
Boss yace"nima nayi tunanin hakan"
"Shi kuma wannan gabjejen ƙaton dangin su kirishna, kabarshi kawai, mutumin banza, baida mutunci, shi
da yazo cin arziƙi yayi kane kane a dangi" da zolaya big guy yayi maganar, taj yayi dariya cike da nishaɗi
yake sauraron shi.

"Very soon zamu yi mashi korar kare daga family din, tun da ba gidan ubansa bane" acewar big guy gaba
ɗayansu suka tuntsire da dariya
Bayan sun tsagaita Boss man Yace"dama na kirane don inji lafiyar ƴa'ƴana"
"Kai dai fadi gaskiya, Ko dai ka Kira Kaji Lafiyar Jarin ka, Ifrituwar Yarinya wlh ɗazu data la6e a bayan labule,
naso ace ka bari chief Ya shaƙi wuyanta, Yasin sai tayi jinya a gadon asibiti, Yarinya sai ƙiriniya kamar
ansanya mata battery" fashewa taj yayi da dariya
"Cin mutuncin Ya isa haka, Na lura baƙin ciki kake Yi da ita shiyasa ka sanya mata ido, Ni dai yanzu fada
min suna ina.

Sai da Ya Mula Yasha Iska tukunna Yace"Sun ci sun ƙoshi, kowannansu Ya koma dakinsa, harma sunyi
wanka sun canza sutura, Na rakasu dakin Danish sun ganshi, Yanzu haka kowan nan su Ya koma dakin shi,"
Ajiyar zuciya Boss man ya sauke"Alhamdulillah, Naji dadin jin hakan, inataso in tambaye ka ka tuntu6i
6angarensu Salsabeel"?

"Bakasan meya faru ba" nan fa big guy ya kwashe duk abunda Ya faru Ya sanar dashi, hankalinshi Ya dan
tashi
"Bawan Allah jazz, abu baiyi dadi ba, Allah ya bashi Lafiya, In sha Allah zamu fidda lokaci muje duba shi,
Har Yanzu suna a asibitin ne"?

" Na kira Major Waya Ya fada min cewa An sallame su, Jikinshi yayi kyau da sauki, naso na kira jazz din
awaya ashe ya mantata acan gidan Yaran, sai dai muka gaisa da shi ta wayar Major har nayi mashi Ya jiki"
Boss Yace"ka kyauta, Nima zan kirashi zuwa anjima kafin muje gidan nasu, amma fa yakamata Yaran nan a
ƙara masu tsaro"
Big guy yace"Nima nayi tunanin hakan, Jira nake komai ya lafa Yaron nan Danish Yaji sauƙi kafin mu
tattauna akan yaran idan za'a haɗesu gida ɗayane ko kuma za abarsu acan din, but Yanzu zan tura da
jami'an da zasu basu tsaro in sha Allah"
Sunjima suna tattaunawa atsakaninsu daga bisani sukayi sallama da junansu.

________________________✍️

Gaba ɗaya Sun hallara, Bayan Shigar Mai girma sharafudeen da Sheikh Imam, Cikin girmamawa da
karramawa suka Yi mashi Kyakkyawar Tarba sanin matsayin shi awurin mahaifinsu Obie, kusan aminine shi,
Ya jima Yana yi masu hidima da ta shafi 6angaren addinin islama, shiyasa suke girmama shi suna ganin
ƙimar shi da darajar shi acikin idanuwansu, Baba Obie Yayi farin Cikin Ganin shiekh Imam har Yana fadin Ya
akai Prime minister bai shigo da shi ba, shiekh Imam Yace shi ne Ya buƙaci Zama a falo, Obie Duk da bai jin
dadin jikinshi sai da Ya miƙe adaddafe da taimakon chief owais daya ruƙo shi, ya samu damar rungume
imam malik, fuskokinsu ɗauke da matsanancin farin ciki sunyi matuƙar yin kewar Junansu, Mai girma
Sharufudden tuni ya nufi ƴan uwanshi tun daga kan senate lateef, duk wanda Ya miƙa ma hannu suka gaisa
daga bisani sai Ya yi hugging dinshi, Har yazo kan Hateem wata irin runguma yayi mashi tamkar zai maida
shi ciki, Hateem yayi murnar ganin ɗan uwan nashi yasan shi kadaine zai fahimci zuciyarshi ya kuma share
mashi hawayen shi, bayan sun kammala Ƴan gaishe gaishen nasu, Sheikh Imam malik ya fara Yi masu
addu'o'i kamar yadda yake yi masu duk inyazo gidan, hakan ba ƙaramin daɗi yake yi masu ba, amsa mashi
suka dinga yi da ameen ameen, har ya gama yin addu'o'in nashi, baba obie yace yaji dadin zuwanshi yana
da tabbacin zai taimaka mashi wurin warware matsalar data ke ƙoƙarin kunno kai a zuri'arshi, Imam Malik
yace shima yaji dadin zuwa Gidan kuma in sha Allah komai zai tafi dai dai, bi'iznillah, amma kafin su fara
zaman tattaunawar, duba da gabatowar sallar Magrib Yana ga su bari su yi salla, harma da Isha'i kafin su
dawo ayi zama na musamman don asamu maslaha, gaba ɗaya sunyi amanna da maganar Imam malik, ba
tare da 6ata lokaci ba, kowannansu ya dauro alwala, suka fito atare suka ɗunguma zuwa harabar ajiye
motocin gidan, sojojine suka take masu baya har zuwa masallaci, acan masallaci suka haɗu da Sir Mubarak
tare da Zaki sunji dadin ganin shi tun daren Jiya daya tafi suna tsaka da yin firar yaushe rabo sai yanzu Allah
Ya haɗa su dashi, bayan sun fito daga masallaci suka tsaya suna ƙara gaisawa, anan Sir mubarak Ya sanar
da su uzurinshi na rashin zuwa gidan, sai dai bai sanar dasu game da zargin jazz da yai har takai shi ga
bugunshi yadai ce masu Jazz Ba lafiya sun kwana asibiti Jiya sai Yau suka dawo, Hankalin baba Obie Ya tashi
jin cewa Jazz din shi baida lafiya, duk yabi ya rude, har saida Sir mubarak Ya kira mashi jazz a waya yaji
muryarshi da sauƙi har yana zolayar shi yayi missing din ganin gemun shi, shifa lafiyarshi qalou jinyace
tadan lokaci, kada yai tunanin zai riga shi mutuwane shima sai yaci zamaninshi ya tara ya'ya da jikoki,
dariya baba obie yayi sosai, sun ɗan jima suna yin wayar kafin Ya miƙa ma su hateem wayar duk suka yi
mashi ya jiki ya amsa masu da sauƙi, hatta imam malik saida yayi waya da jazz hakan ba ƙaramin daɗi yayi
ma Jazz ba ganin yadda suka nuna damuwarsu akanshi, bayan sun kammala yin wayar ne sir mubarak Ya
amshi phone dinsa Ya tura aljahu, ɗaya bayan ɗaya suka shiga motocinsu, a jere suka nufi Estate dinsu......
✍️
*❤UMMIN AMERICA❤*

Moving quickly yake tattaka stairs, tun kafin ya ƙarasa ƙofar room dinta, sautin daddaɗar Muryarta dake
yin qira'ar karatun alƙur'ni mai girma ya ratsa kunnuwanshi, har saida ya lumshe idanuwamshi saboda
yadda karatun nata ya ratsa zuciyarshi, sautun tamkar ana busa sarewa tsabar daɗinta, daƙyar ya samu
damar tattara natsuwarshi da kamalarshi ya nufi ƙofar, ya sanya hannu yaɗan yi knocking dinta, shiru babu
alamun zata dakata da yin karatun balle harya ya sanya ran zata bashi permission din shiga ciki, kusan sau
biyar yanayin knocking shiru taƙi tanka mashi, A ƙarshe ya yanke shawarar buɗe ƙofar da kanshi, A hankali
Ya zuge ta, tana ƙarasa buɗewa Ya haura ƙafarshi cikin ɗakin bakinshi ɗauke da sallama, yayin da
idanuwanshi ke kallonta, tana daga zaune saman darduma, dogon hijabin dake ajikinta launin maroon yayi
mata kyau, ya bayyana ainihin wacece Ita, bakomai ne ya karya mashi zuciyarshi ba face ruwan hawayen
da suka wanke fuskarta sharkaf, Eye lashes dinta sun cukurkuɗe dakyar take Iya kallon Qur'anin data buɗe
tana karantawa, duk da sanyin A.c na ɗakin hakan bai hana ta zubda gumi ba......

Ya fahimci batasan da shigowarshi ɗakin ba, hakan yasa shi ɗaga murya ya furta sunanta"UMMI!" Ras Taji
gabanta ya faɗi don sai taji tamkar muryar Sheikh Imam ce Ta ambaci sunanta, a wani irin firgice ta
yunƙura ta miƙe tare da yin saurin kai idanuwanta da suka kaɗa jawur kan fuskar shi, wata irin nauyayyar
ajiyar zuciya ta sauke ganin Big Guy ne , fuskarshi sanye da face mask.

Ganin irin kallon da yake yi matane yasa tayi saurin share hawayen fuskarta.

Wani irin tausayintane Ya kama shi, bai ta6a jin ta burge shi ba irin yau.

Calmy Ya furta"Am sorry, na shigo maki ɗakin without asking for ur permission, na kwankwasa ƙofar shiru
baki buɗe ba, shiyasa na yanke shawarar shigowa"

Shiru tayi bata ce mashi komai ba, aranta taɗanyi mamakin tausasa harshen da yayi wurin yi mata magana,
don tun ranar da suka fara haɗuwa ta fuskanci baida sauƙin kai, musamman jiya da ta ƙure ma su batul
sanyin A.c Ya rufe ta da faɗa kamar ubanta abun ya ƙona mata rai, ta kuma yi mamakin zafin kanshi don
tun da take arayuwarta wani namiji bai ta6a yi mata hakan ba saboda kyawun surarta da ke jan
hankalinsu..

"Kin yi shiru baki ce komai ba"? Muryarshi ce ta fargar da ita, adabarbarce ta furta"badamuwa"

Goya hannayensa yai kan chest dinsa Ya nufe ta har sai da yaje dab da ita tukunna ya dakata

"Dama kin iya karatul alƙur'ani? da sanya hijabi"?

"Kamar yadda ka gani" ta bashi amsa atakaice"

Lumshe idanunshi yadanyi before ya furta"kin kusa tafiya da imanina, inason mace me ilmin addini"

"Ni bani da ilmi, Idan ma abun da ke aranka kenan to ka daina, Ni karuwa ce, zaifi ka fuce min daga ɗaki
tun kafin in rinjayi zuciyarka" fuskarta adaure babu annuri ta furta maganar.

Dariya yai ta cikin face mask dinsa sautin ke fita,

"Da ace kinsan wanene Ni, da baki furta wannan maganar ba, domin kuwa ke bakomai bace akaina"
yanayin yadda ya furta maganar yaɗan so ya jefa ta aruɗani, sai taji Muryar tamkar ba ta shi ba.

tafin hannayensa biyu ya daura akan gefe da gefen fuskarta, nan taji wani irin abu ya ziyarci zuciyarta
"Na damu da halin da kike aciki, shiyasa nazo don na dubaki, ɗazu muna a falo, naga yanayin da kika
shiga ganin Imam malik, kin san shi ne"?
Aharzuƙe Ta janye hannayensa tana girgiza kai tace'bansan shi ba, Yau na fara ganin shi, Ni da ba'a Nigeria
nake ba taya zan san shi ma" ta faɗa tana haɗe fuskarta.
"Hakane, amma meyasa kika gudu kina kuka"?
Rai a6ace tace"Idan wannan ne ya kawo ka ɗakina, Dan Allah Ka fuce ka bani wuri,"
Gyaɗa kanshi yai"Shikenan, nadaina, am sorry idan na 6ata maki rai, kamar yadda na fada maki, Na damu
dake ne, wunin yau baki ci abinci ba, Kin hana kanki sakat, Ki faɗamin meke damunki"?
Yamutsa fuskarta tayi kafin tace"babu abun da ke damuna, kawai bana son kowa atare dani, bana son
takura, kuma bana jin yunwa shiyasa ban nemi abinci ba" atsiyace ta ƙare maganar, ya natsu yana kallon
small lips dinta tamkar na jinjiri
"Haƙƙin mu ne mu kula da cin ki, dan Haka dole ki ci abinci ko kina so ko bakya so," ya faɗa yana ɗaga
mata gira
Harara ta galla mashi"babu wanda ya isa yayi min dole, ciki dai nawa ne idan naga dama zanci abincin
basai an tursasa min ba"
"Kidaina yi min magana da tsawa, kodan saboda kinga na damu dake ne"?
Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh,
"Da zaka fuce ka barmin ɗakina da hankalina sai yafi kwanciya"
Shiru ya yi jimm tamkar baiji dadin maganarta ba, tayi tunanin zai tafi amma sai ta ga ya sanya hannun shi
na dama ya ruƙo face mask din fuskarshi, slowly ya zame shi
Wata irin furgita tayi lokacin da fuskarshi ta bayyana, Har saida ta ja da baya da baya ta kusa faɗawa
mirror chair ta dafe ta da hannu ɗaya, idanunta amatuƙar zazzare take kallon shi tamkar ƙwayar zasu faɗo
ƙasa la66anta na rawa ta furta"da.....ma kai ne? tayaya akai ka shigo gidan nan"?

Wani irin shu'umin murmushi ne ya bayyana akan fuskarshi, kalar na tantiran ƴan iska, waɗanda suka
shahara afagen iya shaidanci
Lokaci ɗaya suffarshi ta ƙara bayyana, faffadan kirjinshi Ya buɗe sosai.
Zame rigar jikinshi yayi, wani irin murɗaɗɗen damtsen hannu ne dashi, gaban kirjinshi kuwa da bayanshi
zanan tattoo ne 6aro 6aro, kai daga ganin wannan ko acikin shaidanun ibliss ne shi,
Lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai, ya gigitar da ita, jikinta ya soma yin kakarwa, duk tabi ta ruɗe,
asaman gadonta Ya jefar da long coat dinsa

Muryarshi tamkar ta mashayin giya ya furta"Kin tsorata ne"?


Sam takasa furta magana, tamkar an ɗaure maƙoshinta, yanayin yadda numfashinta ke fita da ƙarfi kirjinta
har sama da ƙasa yake yi,
Tuntsirewa ya kuma yi da dariya, haɗi da tausasa harshenshi Ya furta"ba fa yau kika saba gani na ba, ni ne
dai naki ɗin nan da kika sani"
Yawu ta haɗiya Kutt! Sautin Ya fita, daƙyar Ta Iya tattara kalmomin dake akan harshenta ta furta"tayaya
akai ka shigo gidan nan dake atsare da Jami'an isod, Bayan haka ko'ina akwai CCTv cameras saƙo da lungu,
dan Allah ka faɗamin ta wace ƙofa ka shigo, kuma ya akai ka sanya kalar kakinsu? sannan kayi min suffar
big guy" a razane take jefa mashi tambayoyin, abunne yafi karfin kwalwarta, mutun kamar aljani, takasa
yadda da cewa shine, gani takeyi kamar mafarkine takeyi
Cikin Takun Izza Ya nufeta, dab da ita ya tsaya, tare da ɗaura hannayenshi kan bayan kujerar da ta jingina
bayanta.

Can ƙasan maƙoshi Ya furta"Ummi, kinsan wanene ni, akan buƙatata zan iya yin komai, nagaza jurewa ne
shiyasa na tako da kaina nakawo kaina inda kike....." da ƙarfi ta furta"baka bani amsar tambayar da nayi
maka ba"?
"Kada ki ƙara yi min magana kina ɗaga min murya" atsorace ta jinjina mashi kai Alamar toh
Lumshe idonshi yadanyi na wani lokaci kafin ya furta"Idan kin yarda dani ki daina tambayata bana so, duk
abun da nayi nayine saboda ke" ajiyar zuciya ta sauke, lokaci ɗaya taji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarta,
kuma nan take taji ta aminta da kalamanshi, ɗaura hannayenta tayi saman kafaɗunshi, tana faman lumshe
idanu ta furta"'I'm glad to see you, My controller, saboda a ƙuntace nake, bana Iya fita koda kofar gate ne,
sun hana rayuwata sakat saboda aikin da nikeyi masu babu shige babu fuce, tamkar prison haka nake jin
kaina"
Shu'umin murmushin gefen fuska ya sakar mata, tare da kashe mata ido ɗaya, hakan ba ƙaramin jefa ta
yanayi yayi ba, A hankali Ya ruƙo ƙasan hijabin jikinta, ya yaye shi tare da jefar da shi kan gadonta, ruƙo
gaban jallabiyar jikinta yai da hannu biyu, tun daga sama ya direta ƙasa, batare daya zuge zip dinta ba, sai
da ya rage daga ita sai pant da bra tukunna Ya dakata, yana duban fuskarta, numfashinta harya fara
canzawa, da wani irin huci yake fita, baiyi mamakin ganin cukowar kirjinta ba, yana ɗaya daga cikin abunda
yake ƙara gigitar dashi akanta, idan zai shekara baya tare da ita, duk ranar da ya dawo gareta, baya ganin ci
baya sai dai ci gaba, dirin jikinta natural ne.
Ɗaura hannayenta tayi saman kafaɗunshi, yai saurin hade bakinsu wuri guda tamkar zasu cinye
harsunan junansu,
Dungurugum ya ɗauketa da hannayenshi, ya nufi toilet da ita, yana shiga ƙofar ta datse.
wani irin sautin gurnanine ya soma fitowa mai haɗe da nishinsu tamkar namun dawa suna fafatawa, kafin
wani lokaci sautin sambatun ummi ya karaɗe ɗakin haɗi da ƙarar da take saki tamkar zata fasa
bango............."

*Daga Alƙalamin Boss Bature✍️


*

Mu haɗu Jibi Idan Allah yakaimu da rai da Lafiya🌹

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida*
[02/03, 6:32 PM] Anty Hajjo 2: ~TAKUN ƘARSHE~

_______________________Boss Bature✍️

*😈PRAVIN😈*
A kwance Yake saman gadon Hajjaty, Idanuwanshi suna fuskantar Ceilling, tsantsar 6acin raine akan
fuskarshi, ranshi ya 6aci da korar karan da Chief Owais yayi mashi agaban su senate lateef, bakomai yafi
ƙona mashi rai ba face yadda suka gaza dakatar da shi, hakan ya ƙara tabbatar mashi da cewa shi bakowa
bane A family din, Kwandon shara yafi shi amfani, tsawon lokacin da yake akwance babu sallah babu salati,
Yana ji anata kiraye kirayen sallar magrib har aka fara na isha'i bai motsaba, yaci alwashin sai Ya tarwatsa
zuciyar owais, yajima yana da wannan burin Allah bai bashi ikon yin hakan ba, amma yanzu yafara tukfa da
warwara akan ta wace hanya zai 6ullo don ganin ya karya mashi zuciya"?

Miƙewa yayi daga kwancen da yake, ya jingina bayanshi da pillow, fuskarshi babu annuri ko misƙala
zarratin, tunani yaci gaba dayi akan ta wace hanya zai ta6a zuciyar chief owais ta yadda zai azabtar da
rayuwarshi, yayi zurfi acikin tunanin shi motsin buɗe ƙofar toilet ya fargar da shi, hajjaty ce ta fito sanye
cikin jallabiya ta ɗaure kanta da mayafi, alwala ta ɗauro, ganin shi azaune ne yasa tayi saurin furta"Pravin!
Me kake yi har yanzu baka tafi masallaci ba? Ai nayi tunanin zan fito na taras babu kai aɗakin" shiru yayi
bai tanka mata ba sai dai binta da yayi da idanu kamar wani mazuru.

"Magana nake yi maka, ko akwai wani abu ne dake damunka? Naga 6acin rai akan fuskarka"

Saukowa yayi daga saman gadon Ya nufe ta yana huci ya soma magana"Ni da wancan Uban ƴan Ji da
kan ne, Harni zai kora daga ɗaki agaban Iyayenshi ba tare da sun tsawatar mashi ba"? Adabarbarce ta
furta"bangane akan wa kake magana ba"
Dogon tsoki Yaja kafin Ya kwashe duk abunda Ya faru Ya sanar da ita....

Cikin sanyin murya tace"Owais bai kyauta ba, amma kaima da laifin ka pravin, meyasa kake son shisshige
masu ne? Tun da sun nuna basu so to ka daina mana, Ka tsaya A iya matsayinka na surukinsu......" wata irin
gigitacciyar tsawa Ya daka mata, Har saida taji gabanta ya fadi, ta shiga zazzare idanuwanta akan fuskarshi
Ya canza mata tamkar ba shi ba.

Nuna ta yayi da yatsan hannun shi"Idan ba zaki kwantar min da hankalina ba, toh kada ki kuskura Ki yi
abunda zai ƙara harzuƙa Ni" Muryarta Na rawa tace"Naji amma dole na fada maka gaskiya pravin, mu
dukan mu muna fuskantar wulakanci daga wurin waɗanda basa ƙaunar mu a family din nan, kuma ba
komai ya jawo hakan ba face zaman da kake Yi agidansu...." Idanuwanta acike tab da ƙwalla ta ƙare
maganar.

Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi na wani lokaci ba tare daya furta mata komai ba, har saida ta fidda rai da
zaiyi mata magana tukunna Taji Yace"Naji zanyi tunani akan maganar, Yanzu akwai wani taimako da nake
son Kiyi mini My wife," natsuwa tayi tana sauraron shi don jin me zaice mata.

"Kinga ni bani da halin da zan Iya shiga cikin su don jin me zasu tattauna atsakanin su tunda owais yana
nan bazai bari naje ba, Inaso kiyi min recording duk abun da zasu tattauna tun daga farko har ƙarshe"
tsantsar ruɗanine akan fuskarta.

"Akan wani dalili? Meye naka aciki da kake son jin sirrinsu"! Idanunta azare ta furta maganar.

Matsawa yayi dab da ita, da yake ɗan duniyane sai ya sassauta muryarshi ta yadda zai shawo kanta.

"My wife, mutanan sunyi mana halacci daga ni har ke, ba zamu so wani abu da zai cutar da su ba, ai kinga
abun da Ya faru Jiya" daga mashi kai tayi alamar eh.

"Maƙiyane suke ƙoƙarin halaka Baba Obinna, shiyasa suka Turo da macijin nan don Ya hakalar da shi" waro
idanuwa waje tayi tamkar kwayar zata faɗo ƙasa.

"Bashi kaɗai ba, Kowa Na family din nan zata shafa, abunda baki sani ba, Macijin Mutunne fa" dafe ƙirji
tayi da hannu ɗaya amatuƙar ruɗe take kallon shi.
Komai daya faru saida pravin Ya sanar da ita, hada maganar zuwan sheikh imam da canza halittar Danish,
baiwar Allah duk tabi ta ruɗe tasha jinin jikinta.

Muryarta na rawa ta furta"Inna lillahi Wa'inna Ilaihirraji'un,

Afakaice Pravin Yasaki shu'umin murmushi, ganin Ya fara Yin nasara akanta, Yaci gaba da cewa"abun da
nakeso na fahimtar dake, Ni ƙoƙari nake yi don ganin na taimaki rayuwar Ahlin nan, wallahi bana son abun
da zai cutar da su, shiyasa nake shisshige masu don jin meke faruwa a tsakaninsu ta hanyar hakan nake
taimaka masu wurin shawo matsalar dake addabarsu, ɗazu dana shiga dakin owais Ya hankaɗoni waje, zan
wuce ta falo naga sheikh imam da wani mutum ban kulasu ba, saboda shi kanshi sheikh Imam din Ina
zargin hada shi cikin masu shirya maƙarƙashiya a cikin family din nan"

Girgiza kai hajjaty tayi"a'a pravin, bana tunanin hakan, Ina kyautata mashi zato, saboda shi aminin obinna
ne, kuma yajima yanayi ma family din nan hidima, gaskiya Imam malik bazai iya yarda ahaɗa baki da shi
don cutar da familyn obinna ba"

Ta6e baki pravin yai kafin yace"hmm bakisan halin malaman nan ba, yawancin su fuska biyune dasu, A fili
musa a zuci fir'auna, duk wanda fa kika ga ya ra6i familyn obinna ba alkhairi bane ya kawo shi"

"Kana nufin hada mu kenan?" Hajjaty ta jefa mashi tambayar


da buɗar bakinsa sai cewa yai"ai mu mun riga da mun zama jini ɗaya da su, ina magana ne akan ire irensu
Imam malik masu zuwa kar6ar zakka"

Shiru hajjaty tayi tana nazarin maganar shi, kafin tace"yanzu shi yaron yana agidan owais, tare da sauran
yaran daka fada min"?

"Ƙwarai kuwa, Ya kawo mugun abu ya ajiye agidansa, babu fa wanda yasan yazo ƙasar nan, shigowar sirri
yayi, kedai kawai Allah ya shiga tsakanin mugu dana gari amma fa akwai matsala idan har basuyi gaggawar
ɗaukar mataki ba......" ya faɗa yana mai nuna damuwarshi.

Ruƙo hannayenta yai acikin nashi"My wife, Ki bani haɗin kai don ganin mun taimaki ahlin nan kodan
saboda halaccin da su ka yi mana, Inaso muyi masu gwanintar da zasu yi alfahari da mu wata rana" wasa
wasa pravin yadinga tunzurata har yasamu nasarar shawo kanta.

Cikin sanyin murya tace"In sha Allah, zan baka haɗin kai mijina, zamu haɗa hannu don ganin mun yaƙi duk
wani mugu dake da mummunar manufa akan zuri'ar baba Obie" da ƙwarin gwiwa ta furta maganar, babu
wasa a kalamanta.

Wani irin daɗine Ya ziyarci zuciyar pravin yayin da yake kallonta.

"Zan tayasu da addu'a, ubangiji Allah Ya kare su daga sharrin maƙiya da mahassada, Ya Allah duk wani mai
mugun nufi akan zuri'ar baba Obie, Ya Allah Ka toni asirinsa, ka hana shi zama Lafiya, Bayin Allahn nan ni
ban ta6a ganin mutane masu kyakkyawar zuciya irinsu ba, amma ahaka wasu bakin ciki su ke yi da ci
gabansu......" har cikin zuciyarta take furta maganar, don ita harga Allah tana ƙaunar familyn baba Obie,
tana matuƙar sonsu bata son duk wani abu da zai cutar dasu koda kuwa Hajiya saratu ce.

"Yanzu abunda za'ae, kiyi sauri Ki yi sallar, Idan Kika Kammala ki ɗauki wayarki ki tafi second falo, ina da
tabbacin acan zasu zauna suyi tattaunawar, ki riga su zuwa ki saƙa wayar inda ba zasu gani ba, bayan kin
danna recording, Inyaso daga baya idan suka tafi saiki koma falon ki ɗaukota ki kawo min, yaya
sharafuddeen ma Yazo gidan, naji jiniyar shigowar motocinsu, Har leƙawa nayi ta window naganshi"
Amsa mashi tayi da toh, ta nufi closet din kayanta ta dauko Hijab ta tura a jikinta, saida ta kabbara sallah
tukunna Pravin ya shiga toilet domin yin alwala, a ɗakin yai sallar magrib da isha'i kafin Ya gama sallar, tuni
hajjaty ta fuce daga ɗakin, zama yayi kan darduma yana ta yin saƙe saƙe acikin zuciyarshi,

Kamar yadda ya tsara mata haka ta aiwatar, tun kafin su shiga falon hajjaty ta riga su zuwa ta kunna
recording da dabara ta shiga falon kamar tana gyara shi, a hankali ta ajiye wayar a karkashin sofa table,
kafin ta fito daga falon ta nufi kitchen domin shirya masu abun da zasu sha.

Bayan tafiyar hajjaty, da ƴan mintuna Gaba ɗayan su suka shigo Second Falo din wanda ya kasance na
musamman dake A gidan Baba Obie, an wadata shi da Luxury Furniture ba kasafai suke amfani da shi ba,
sai Idan za su yi zaman tattaunawa tukunna ake buɗe shi, wani irin ni'imtaccen sanyin A.c ne ka ratsa
cikinsa, dare ne tamkar da rana saboda wadatattun Chandeliers masu haska ko'ina sako da Lungu, Idan ba
agogo Ka kalla ba ko sararin samaniya ba zaka ta6a gane dare ne ba a gidan baba Obie.

Bayan kowan nan su ya samu wuri ya zauna saman sofa, Sheikh Imam ya fara buɗe masu taron da addu'a,
kafin daga bisani, baba Obie yaba Owais damar yi masu bayani dangane da Yaran da yake ruƙo a hannun
shi.

A tsanake Ya labarta masu tun daga farkon zancen har zuwa karshe kamar yadda Ya fada masu ɗazu.

Mutum ɗaya ne baisan da zancen ba, Lokacin da abun ya faru baya agidan sai yanzu yake ji daga bakin
Owais.

"Owais dama bayan yaran dake acan gidan da Jazz yake Aiki Akwai wasu A gidan ka" Fuskar Sir mubarak da
alamun ruɗu ya furta maganar.

Jinjina mashi kai Owais Yai alamar Eh, nan take ya yanke shawarar sanar dasu dangane da abun da ya faru
tsakanin shi da jazz jin cewa sun san da zancen yaran, bayan ya labarta masu, kowan nan su ya jinjina ma
lamarin sai dai har yanzu mutun uku basu Goyi bayan zaman Yaran a estate din ba.

Sheikh Imam ya ɗaura da cewa"naji daɗin taruwar da mu ka yi anan kuma ina fata zamu samu maslaha, da
farko dai Yaran ba masu cutarwa bane, ba abun da ku ke tsammani bane, Ni shaida ne akan hakan, Mutane
ne su kamar kowa, hatta shi kan shi Yaron da yake rikiɗa cikakken mutunne, kamar yadda Owais ya faɗa
maku Ni da kaina na duba shi, kuma nayi magana da shaiɗanun jikin shi, wataƙil ko dan baku ta6a ganin
mutun ya rikiɗa bane akan idon ku, shiyasa abun Ya ruɗar daku, Amma Ni nasha gani akan idona mutun ya
rikiɗa Koya 6ace Idan muka ja mashi ayar Allah....." ya ɗan dakata da yin jawabin yana kallon su, Senate
Lateef ya haɗe fuskarshi babu annuri ko misƙala zarratin shi fa yana akan bakan shi.

Duk sun natsu suna sauraran sheikh Imam sai da yakai Aya tukunna Senate Ya fara magana rai a 6ace"Ni
bazan ta6a goyan bayan tsintattun Yaran su zauna a family din mu !! Bazai yiwu ba wallahi, Saboda Shi jiya
mahaifin mu ya kusa zaucewa adaren jiya bai runtsa ba, Da firgici Ya kwana, sannan itama saratu bata
runtsa ba a zaune ta kwana saboda gizan da macijin keyi mata, A haka akeson a Ƙaƙaba mana su a family?
ya jefa tambayar yana kallo su sheikh imam babu wanda yai yunƙurin dakatar da shi "Ai daga ji babu
Alkhairi Atattare da su yakamata aduba maganar“ ya faɗa yana mai ƙara jaddada maganar shi.

Gaba ɗaya idanuwansu akan shi, sai da ya ƙare maganar, His excellency abdul Razak Yace"Ni ban hana
ataimake su ba, Amma bazai yiwu su zauna mana a estate dinmu ba, tun da yaran basu da asali, me zai
hana a ɗauke su akaisu Orphanage home dinmu dake anan garin Abuja, In yaso sai mu dinga tallafa masu,
amma fa ban da wannan yaron mai fama da aljanu ba zamu lamunta da zaman shi agidan marayu ba, zai
iya cutar da mutane, kawai aware shi shi kaɗai yayi rayuwarshi har zuwa lokacin da zai samu warakar
lalurar shi"
Tun da suka fara magana Shiekh Imam da chief owais suke bin su da kallo, Shi dai Prime minister ya rasa ta
cewa ganin yadda suka haƙiƙance akan ƙin amincewa da zaman yaron, Mai girman sharafuddeen ma yana
sauraransu sai dai hankalin shi yafi karkata akan ɗan uwanshi, ya fahimci hankalin shi ba a kwance yake ba
dama shi tul fil azal bai cika son rikici ba mutunne ma'aboci son zaman lafiya bayason hayaniya.

Gyaran murya baba Obie Yai masu, hankalinsu ya dawo kanshi.

"Kun gama magana"? his excellency deen yace"Eh baba, mu kawai Yaron ke bamu son zaman shi acikin
estate dinmu, su sauran Yaran ni bani da ja akansu, tun da su lafiyarsu ƙalau suyi zamansu agidan owais din
ko akai su gidan marayun mu...." kafin Deen ya ƙare maganarshi, senate lateef yai hanzarin tarar
numfashinshi da cewa"bazai yiwu ba, Nifa ban lamunta da su zauna a estate din nan ba, sannan dole
ayanke alaƙar su da danginmu, idan taimakon nasu ya zama dole zamu haɗa masu kuɗin da zasu ishesu
suyi rayuwarsu, shi kuma Prime minister Hateem satin da zamu shiga ya hanzarta barin ƙasar nan, zaifi
mana kwanciyar hankali, tun da na fahimci idanuwanshi sun makance akan yaron da bai hada alaƙa da shi
ba"

ya faɗa fuskarshi aɗaure, yayin da yake kallon Prime minister Yaci gaba da cewa"Sarai kaga abunda ya faru
adaren jiya, amma ka kau da idonka, damuwarka akan yaron ce ba akan mahaifinmu ba, maimakon tun da
asussuba ka kamo hanya kazo gida donka duba shi ka ga ya yakwana jiya sai ba ka yi hakan ba duk kabi ka
zauce akan yaron da bakasan asalin shi ba...."

Tsabar yadda senate ke magana har wani gumi yake fitarta, duk da sanyin A.c na falon, Lamarin yayi
mugun ɗaurewa Sheikh Imam kai sai faman jinjina kai yake yi, maganganun senate ba ƙaramin fusata Chief
owais su ka yi ba, tun da ya duƙar da kanshi ƙasa bai ɗago da shi ba, ƙoƙari yake yi don ya lallashin
zuciyarshi idan ba haka ba komai zai Iya faruwa!!.

Senate yaci gaba da cewa"kai kuma Owais," ya faɗa yana nuna shi da hannu"ka 6ata min rai! Meyasa ka ke
yin komai gamon kan ka? ba tare da ka nemi shawarar mu ba? ko dawowarka Nigeria Yakamata ka sanar
damu, amma sai ba ka yi hakan ba kamar kai ke da kan ka, sannan ka kwaso mana wasu tarkace acikin
family batare da ka sanar damu ba, me hakan ke nufi? Bamu da amfani ne ko bamu isa dakai ba ne?" a
zafafe Senate Lateef yayi maganar yana duban chief owais, wanda yayi shiru yana sauraron shi batare daya
yi yunƙurin tanka ma shi ba.

"Allah Ya huci zuciyarku, Na fahimci gaba ɗaya ranku Ya 6aci dangane da abunda ya faru Jiya Ina mai baku
hakuri amadadin Owais" mai girma sharafuddeen ne yayi maganar yana mai tausasa harshen shi.

"Bai kamata kan wannan maganar mu ɗaga hankulanmu ba, Owais dai muke iko dashi, Sannan Kune
manyan Family duk abunda kuka zartar dolen mu ne muyi biyayya akai, ko munaso ko bamu so," Jin
maganar sharafuddeen yasa senate yafara sassauta fushin fuskarshi, hatta sauran sun ɗan samu natsuwa.

"Baba, Hukunci ya rage naka, Kai muke sauraro duk abunda ka zartar dangane da yaran nan wallahi
zamuyi maka biyayya" in a calm voice sharafuddeen ya faɗa yana duban baba obie.

Gaba ɗaya hankali ya dawo kan Baba Obinna, dake zaune kan sofa, sandar shi tana a jingine da sofa hand.

sun ƙagara da son jin amsarshi, saboda shi kaɗaine mai faɗa Aji.

"Mubarak!" da sauri sir Mubarak ya ɗago ya kalleshi cikin girmamawa ya amsa mashi da na'am baba.

"Banji kace komai ba"

Murmushin gefen fuska Sir mubarak ya yi kafin yace"Baba, ni bani da matsala wallahi, yaran nan ba akaina
zasu zauna ba, owais ne ke kula dasu akan me zan damu? Na yarda da shi kuma nasan bazai ta6a kawo
abunda zai cutar da zuri'armu ba, Ni dai inayi mashi fatan Alkhairi duk shawarar da ka yanke zamuyi
biyayya"

Chief yaji daɗin maganar sir mubarak, dama yasan bazai bashi matsala ba.

"Aminina, naji kayi shiru, inaso naji daga gare ka" baba obie ne ya faɗa yana duban Imam malik.

Murmushi ya saki, Yana mai fara'a yace"wannan abu na ku ne na Ƴan siyasa, Kun san yanda ake jefa
ƙuri'a waɗanda suka fi rinjayi, maganarsu yakamata aɗauka, Nidai anawa ganin kenan, Yaro dai bame
cutarwa bane, jarabtace ta ubangiji babu wanda yafi ƙarfin Allah ya jarabce shi acikin mu, shi kuma owais
Jinin ku ne Ku kan ku kun yaba da hankalinsa, ni banga wani abu da zaisa ace za'a yanke alaƙarshi da yaran
ba yakamata aduba maganar nan" cikin Hikma Imam malik yake yi masu magana, har cikin ranshi baison
yaji suna maganar korar yaran daga familyn Obie.

Jinjina kai Baba Obie yayi kafin ya kai dubanshi ga sharafuddeen.

"Meye ra'ayinka dangane da yaran"?

"Baba, Ni bani da matsala, kamar yadda yaya Mubarak Ya faɗi, Nima haka, Kafin mu yanke hukunci
yakamata mu yi wa kan mu adalci dasu kansu Yaran, Abun da Ya faru da ɗan uwansu bayin kanshi bane,
Allah ne yake jarabtarsa, gaba ɗayanmu musulmai ne kuma munyi imani da ƙaddara mai kyau ko mara
kyau, so yakamata mu kar6i yaran nan hannu biyu mu rungume su, Sannan Yaran nan fa ba muke ɗaukar
ɗawainiyarsu ba, ba agidan mu suke zaune ba, Agidan owais suke zaune shi ne ke kula dasu kuma shine ke
da alhakin duk wani abu da zai faru, babu yadda za'ai araba owais da yaran nan! Saboda Bincike su ke yi a
kansu, Hukumar Sojin america suna da sanya hannu akan case dinsu, bazai yiwu owais ya rabu da su ba...."
jin wannan maganar ta sharafudeen yasa senate ɗaure fuska, gani ya ke yi kamar hada baƙar magana
sharafudeen ya gaya mashi daya faɗi cewa agidan owais suke zaune kuma shi ke ɗaukar ɗawainiyar shi,
maganar ta sosa ran shi, Deen da abdul razak sun fara aminta da kalaman sharafudeen akan zaman yaran.

Bayan Sharafuddeen Ya kammala maganarshi, Baba Obie Ya ambaci sunan Hateem, A hankali ya ɗago da
idanunsa waɗanda suka kaɗa jawur da su, Muryarshi adisashe ya furta"Bani da abin cewa, duk hukuncin
da aka yanke baba zanyi biyayya"

Shiru su ka yi na wani lokaci babu wanda ya ƙara furta magana acikinsu falon yayi tsit kamar mutuwa ta
gifta.

Shigowa falon hajjaty tayi da sallama a bakinta, hannunta biyu ruƙe da faranti daga saman shi Tea pot ce
tare da cups, daga bayanta Abla ce tare da Sophia kowan nan su ya ruko tray na kayan abinci, Amsa masu
sallamar sukayi cikin girmamawa suka sauke trays din kafin suka gaishe da su sheikh Imam da sauran
mutanan falon, da fara'a suka amsa masu, kafin daga bisani suka fuce daga ɗakin.

Babu wanda yai yunƙurin ta6a kayan abincin, kowa kanshi ya ɗauki zafi.

"Aminina, bismillah" Obie ne ya furta hakan harya yunƙura da niyar ya zuba mashi Tea a cup da sauri
Imam malik yace"Alhamdulillah, kafin na baro gidan Hateem na cika cikina babu yunwa atare dani,"

Cikin kulawa obie yace"Ban yarda ba, amma tun da kace haka, Bari na zuba maka tea din kasha, nasan zaka
ji dadin shi, Hajjaty ce ta haɗa shi"

Sheikh Imam na murmushi yace"na fahimci ba ƙaramin ji kake da matar nan ba"
Murmushi obie yai batare dayace komai ba.
Owais ne ya miƙe ya nufi tray din ya dauki tea pot ya tsiyaya masu tea a cups din yabi kowan nan su Ya
miƙa mashi, ba tare da ya zuba nashi ba ya koma ya zauna.
"Ba za ka sha ba"? Hateem ne yai mashi maganar, Calmly ya furta"bani buƙata"
Bayan kowan nan su ya kur6i tea din, baba obie ya soma magana yana duban fuskokin su.

"Na yanke shawara....." bai ƙarasa maganar ba, ganin yadda suka ɗago suna kallonshi Ya fahimci sun ƙagara
da son jin mai zai ce ne.

"Dangane da abun da ya faru jiya, na ruɗe ne shiyasa harna firgice, amma yau da Owais ɗina yayi min
bayani na fahimce shi, na yarda yaron mutunne kuma ba mai cutarwa bane, tun time da abun ya faru har
ya shigo gida na, ya samu damar da zai iya cutar da mu amma bai yi hakan ba, sannan naga ƴar uwarshi
taje gare shi ta lullu6e shi da rigarta tana kuka tana rokon shi akan ya canza halittar shi ya zama mutun,
nayi mamaki ƙaramar yarinya bata ji tsoron tunkarar shi ba a suffar maciji, sannan baiyi yunƙurin sarar ta
ba, hakan ya ƙara tabbatar min da cewa mutunne da gaske......" wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar Owais
da Hateem da sauran masu goyan bayan zaman su, In ka cire Senate lateef donshi har ga Allah bai yarda da
yaran ba.

Numfasawa baba obie yai, kafin yaci gaba da yin maganar sai da ya fara kur6ar tea din hannun shi.

"Na amince su cigaba da zama a estate din mu"! A matuƙar ruɗe Senate lateef ke kallonshi da tsantsar
mamakin yadda ya amince da zaman tsintattu a zuri'ar su, zuciyar shi ta sosu sai dai bai yi kuskuran katse
mashi maganar shi ba, wani irin annurin farin ciki ne ya bayyana akan fuskar Hateem da sauran magoya
bayan zaman yaran a estate din.

"Amma abu ɗaya ne ban yarda da shi ba"!! ya faɗa Yana Shafa gemunshi da hannu ɗaya, yayin da
idanuwanshi ke akan fuskar Hateem da chief Owais, kamar yadda yake kallonsu haka suma suke kallon shi.

"Hateem, bana so wani abu Ya ƙara shiga tsakaninka da Yaron, babu kai babu shi, ban amince ka taka inda
yake ba Har ka koma Canada," Ras yaji gabanshi yai mugun faɗuwa, baisan sa'adda ya sauko daga saman
sofa ya dawo kan carpet ya zauna, motsa la66ansa ya soma yi da niyar yin magana da sauri sharafuddeen
Yai mashi gyaran murya nan take Ya fahimci me yake nufi, ƙoƙarin haɗiye damuwarshi yayi, In a cool Voice
yace"Shikenan baba, Na amince, amma dan Allah Ina neman alfarma awurinka" a marairai ce yayi mashi
maganar.

"Ina sauraronka"

"Nayi ma Gimbiya mujeedat alƙawarin zan kawo yaron gidana don ta ganshi....." da sauri senate ya katse
shi"mugun abun zaka kai gidanka? Inda iyalanka suke? Wannan wani irin gangancine"?

Deen yace"yakamata aduba lamarin nan fa, gaskiya ba zamu lamunta ba hauka kake yi da zaka ɗauki
mutun mai hatsari ka kai gidanka? What if something happens?" he said in a tense voice.

"In sha Allah Ba abun da zai Faru, Nidai kawai ay min alfarmar dana nema" ranshi aƙuntatace yayi
maganar.

"Hateem Kayi haƙuri, tunda Yaron baida lafiya, ba yadda za'ai ma ya Iya taka ƙafarshi balle har Yaje
gidanka, sai dai Idan Yaji sauki kafin lokacin da zaka koma canada" Imam Malik ne Yayi maganar yana
dubanshi

Jinjina kanshi ya ɗanyi, ba tare da ya ce komai ba.

Baba obie dake kallon shi ya fahimci babu nutsuwa atare dashi, cikin kwantar da murya yace"Hateem,
kada hakan ya dame ka, kasan ina son farin cikin kowan nan ku, ba zanso abun da zai 6ata maka rai ba,
dalilin dayasa na raba ka da yaron saboda lalurar dake atare da shi, bana so wani abu ya cutar min
dakai...." gyaɗa kai yai"bakomai baba nagode" cikin sanyin murya ya faɗi hakan.

Murmushi sheikh imam ya saki yana fadin"aminina yakamata kaga yaron nan da Hateem ya ƙwallafa rai
akai, dama sauran yaran, zaku sha mamakin kamanninshi da Hateem, daku kanku" ya faɗa yana nuna su
Deen, ba yabo ba fallasa suka dube shi batare da sun ce ƙala ba.
Baba obie ya ɗan yi jim na wani lokaci kafin yace"aminina, acigaba da bashi kulawa ta musamman, Idan
yaji sauƙi Allah ya raba shi da abun dake damun shi, in sha Allah zamu je mu duba shi, zamu taya shi da
addu'a, Allah ya yaye mashi abunda ke damun shi"

Sheikh imam ya amsa mashi da ameen aranshi yayi mamaki yadda suka nuna basu buƙatar ganin yaran
duk da ya fahimci kamar suna gudun haɗuwa da danish ne saboda lalurar shi.

Duba agogo sharafuddeen yayi"dare yana ƙara yi, Ina so zan wuce"

Baba obie ya dube shi"zaka iya tafiya tun da inada madadinka," ya faɗa yana nuna chief Owais da cup din
hannun shi
Murmushi sharafudeen yasaki tare da kallon Owais a fakai ce ya kashe mashi ido ɗaya, murmushin gefen
fuska chief ya saki ganin abunda daddynsa yayi masa, ba tun yau ba ya saba yi mashi hakan sometimes
tamkar aboki yake ɗaukar shi.

Gyaran murya Senate lateef yai hankalinsu ya dawo kanshi, fuskarshi babu walwala ya furta.

"Hateem, kada ka manta, akwai taron da zamuyi a National Assembly, domin gabatar da jawabi da kuma
ganawa da kakakin majalissar wakilai"

"Ina sane da wannan" atakaice Hateem ya furta hakan.

Sharafuddeen yace"bayan haka zamu ziyarci national Mosque, da kuma National Christian Centre, akwai
kuma ganawa ta musamman da zaka yi da sarakunan gargajiya daga sassan kasar mu, after that zaka
halarci State Dinner (Liyafar cin abincin dare) tare Ni A Villa"

Sheikah Imam yace"babu hutu kenan Hateem zai fara yawo, ko da yake haka ya dace tun da ba kowani
lokaci ake samun damar zuwa ƙasar ba, ƙwara ka za gaya gari nima dai hadani za'a je villa wurin liyafar ko
ba agayyace ni ba sai na je don nasan za'aci kaji" da zolaya sheikh imam ya fada yana murmushi

maganar shi ta ba su nishaɗi, gaba ɗayansu suka sanya dariya.

Sharafudeen yace"aikune kan gaba baba, kai zaka buɗe mana taro da addu'a" sheikh imam yace masha
Allah nagode da karramawarnan"
Baba obie yace"Idan da hali ma, yakamata ku leƙa masarautar yarbawa ku gaishe da dangin mariganya
ƙudirat, da kuma masarautar kano suma yakamata aje masu da Hateem, sannan zaka ziyarci National
museum dake a lagos, da kuma Yankari Game reserve.... "Tunkan baba obie ya ƙare maganar, Hateem ya
furta"baba duk ni zan halarci waɗannan wuraren daka lissafa? Bani da isasshen lokaci, On saturday next
week zan koma canada, ina buƙatar hutu" fuskarshi a yamutse yayi maganar.

Senate yace"dole ne kaje ko kana so ko baka so, mu zamu jagorance ka, Tun da ka shigo ƙasar tamu, dole
ka zaga dangi, ka kuma ziyarci wuraren buɗe ido,"

gyaɗa kanshi yai har cikin ranshi baison yawace yawacen nan badan komai ba sai don saboda Danish
baisan yayi nisa da estate din, duk da an yanke alakarshi da yaron zaifi mashi kwanciyar hankali idan har
yana akusa da inda yake rayuwa.
"On friday zamu shirya maka family dinner, na bankwana" acewar Deen.

Muryarshi asanyaye ya furta "Allah yakaimu lafiya" suka amsa mashi da ameen.

Sun dauki tsawon lokaci suna tattaunawa a tsakaninsu har wuraren ƙarfe sha ɗaya Na dare, Kafin daga
bisani sheikh Imam ya rufe masu taron da addu'a, daga nan su ka yi wa junansu sallama, Har bakin entry
Hall, Baba obie yayi masu rakiya, Hateem Ya shiga mota tare da sharafuddeen, Sheikh Imam tare da Boss
man suka shiga mota ɗaya, suma sauran kowa Ya nufi Gidan shi dake a estate din, banda chief Owais, baba
obie Ya ruƙe shi, yace shi zai taya shi kwana yau tunda shi yakawo abunda ya tsoratar da shi babu musu
owais ya amince mashi domin shima yayi kewar kakan nashi.

Tun acikin mota, Sharafuddeen yake tausar Hateem akan yayi haƙuri dangane da hukuncin da baba Obie ya
yanke mashi na raba shi da yaron, sannan ya kwantar da hankalin shi, ya yi mashi alƙawarin ko bayan baya
ƙasar zasu kula da rayuwar yaron, ba zasu ta6a bari ya wulaƙanta ba, kalamanshi sun tausasa zuciyar
Hateem, shi abinda yafi damunshi raba shi da akayi da yaron, yanzu shikenan bazai sake zuwa inda yake
ba, har ya koma canada , abun ya ta6a zuciyarshi baiso haka ba, har cikin gidanshi sharafuddeen ya shiga,
suka gaisa da gimbiya mujeedat, ita kadaice bata runtsa ba saboda rashin dawowar mijinta, Su Yazrin tuni
sun nutsa a baccin su, bayan sharafuddeen yayi masu sallama ya fito daga gidan security detail dinshi suka
buɗe mashi mota ya shiga, batare da 6ata lokaci ba, suka nufi Aso Villa domin komawa ga muhallinsa.

Bayan barin su gidan da kusan mintuna talatin, Hajjaty ta lalla6a taje ta ɗauko wayarta data ajiye ƙasan
table, jiki na rawa ta nufi dakin don ta kaima pravin, tana shiga ta taras da shi yanata faman yin zarya adaki
kamar mai fama da ɗan kanoma da basir, duk ya ƙagara da son jin abunda suke tattaunawa, jin sallamarta
yasa shi yin saurin tambayarta ina wayar, da sauri ta miƙa mashi, yasa hannu ya kar6a tare da kunna
recording din, ya soma sauraron tattaunarsu, hajjaty dake kallon shi, ganin yadda yake tsuma zufa ta
wanke fuskarshi yasa tace mashi lafiya, rai a6ace ya jefar da wayar saman gado yana fadin wannan wace
irin masiface? Wato dole dai sai yaran nan sun zauna a estate din nan, wallahi bazai yiwu ba, duk yadda
zanyi saina yi silar barin su, nasan owais ne ya tunzura obie har ya amince da zaman su, saboda ya
makance akan ƙaunar shi, Idan sunsan wata basu san wata ba....." yana huci yai maganar, hajjaty dake
kallon shi, tsantsar mamaki ne akan fuskanta, harta fara kokwanton anya pravin baida wata manufa akan
yaran? Meyasa ya tada hankalin shi akansu? Tayi zurfi a tunaninta taji ya buɗe kofar ɗakin Ya fuce waje, Jiki
asanyaye ta nufi gefen gadonta ta zauna tare da kwantar da kanta, tayi tsammanin zai dawo dakin amma
sai taji shiru, ranta ne ya bata cewar ko ya tafi dakin hajiya saratu ne hakan yasa ta ja bargo ta lullu6e
jikinta....

*❤EX-PRISONERS❤*

Bayan Sun kammala Cin dinner dinsu, sam sun kasa runtsawa saboda tunanin ɗan uwan su Danish, ɗazu
da marece sun je duba shi, Yanzu ma kuma Bayan sun sanya kayan bacci a jikin su sun yi shirin kwanciya,
ɗakin shi suka nufa, gaba ɗayan su ne a kawaye da gadon shi, sun yi tsaitsaye cirko cirko suna kallon shi.

Unaisah da Batool sun sanya kayan bacci kala ɗaya Riga da wando launin black gray, rigar tana da hula duk
sun lullu6e kawunansu da ita, Jemimah da Azeeza ma kalar nasu sleep dress din iri ɗaya ne Yar gown ce
dai dai gwiwa ta tsaya masu launin pink colour, sun daure kawunansu da head scarf, Praveen da Hanna
launin nasu farare ne riga da wando masu zanen flowers ajikinsu.

Hala zalika Mazan ma kowan nan su yana sanye da kayan baccin sa.
Tun suna daga tsaye har dai suka kaiga samun wuri gefe da gefen gadonshi suka zazzauna, banda Gabriel
dake atsaye ya goya Azeeza a bayan shi saboda makantar daren ta, duk da lalurar ta fara sauki yanzu, tana
gani ba laifi saboda hasken dake gauraye da gidan tamkar da rana, yana ƙara ƙarfafa mata ganinta sai dai
babu clear amma takan iya shaida fuskokin su, shiyasa bata damuwa yanzu bama kowa yasan tana da
lalurar ba sai ƴan uwanta.....

Fuskokinsu babu walwala, yayin da suke kallon shi, musamman Haris hawaye tuni sun jiƙe fuskarshi.

"Allah ya baka lafiya ɗan uwana rabin raina, Danish na tausaya maka, Ina jin raɗaɗin da ka ke ji acikin
zuciyarka, In sha Allah ƙarshen wahalarka ne Yazo"

murya arauna ce Haris Ya furta maganar, idanunsa akan fuskar Danish dake akwance tsakiyar gadon kamar
matacce.

"Danish, ban sani ba ko kana ji na, dan Allah ka kwantar da hankalinka, kada ka ta6a sanya damuwa akan
abunda ke faruwa dakai, ko jiya da muka guje ka don ba mu san kai bane, amma Yanzu mun riga da mun
sani, kuma in sha Allah, a kowani hali na rayuwa duk runtsi duk wuya muna a tare dakai, har ƙarshen
rayuwar mu" Batool na ƙarasa faɗar maganar ta fashe da kuka tamkar ranta zai fita, da sauri ta kifa kanta
saman mattress din daga gefen hannun shi, ta ɗaura nata hannun akan nashi.

"Batool ki daina yin kuka, zaki ƙara karya mashi zuciyarshi, saboda Ina ji araina yana sauraron mu ba bacci
yake yi ba" cikin kwantar da murya Unaisah ta furta maganar, idanuwanta akan Batool cikin shesshekar
kuka tace"ya wahala sosai, ko motsi bai iyayi, mu kallon shi kawai mu ke yi, shi ka ɗai yasan raɗaɗin da
yake ji acikin zuciyar shi, sai yaushe ne zaiji dadin rayuwarshi"? Cikin jin ƙunar rai ta furta maganar tare da
dago da kanta idanuwanta sun kaɗa jawur..

Fashewa da kuka Azeeza da jemimah su ka yi, sautin su ya karaɗe ɗakin, Naufal Yace"Dallah meye haka?
Kuka shi zai mana maganin damuwar ɗan uwan mu ne? Ku bar mu muji da abunda ke damunmu mana"
zuciyarshi a jagule yayi maganar,

Muryar Jemimah da shessheƙar kuka tace"Ni wallahi tausayinshi nake ji, bawan Allah, lokacin da muna a
daji bamu lafiya shi ya rinƙa ɗawainiya damu har muka ji sauƙi....." kafin ta ƙare maganar, parveen cikin
raunin murya ta katse ta da cewa"Idan muna jin yunwa shi yake sama mana abinci, sannan Ya hana idonshi
bacci duk don saboda mu, amma meyasa mu muka kasa taimaka mashi awannan halin"? Muryarta na
rawa ta jefa masu tambayar.

"Saboda bamu da yadda zamuyi Parveeen, addu'a ce kadai zamu Iya taimaka mashi da ita," acewar Javed
shima fuskarshi ayamutse take.

"Ba iya addu'a ba javed, Idan muka tona asirin miyagun mutanan can da suka ƙasƙantar da rayuwarmu,
Ina da tabbacin zamu Yi nasarar kawo ƙarshen matsalar Danish damu kan mu, don kuwa nasan har Yanzu
suna nan suna bibiyar rayuwarmu bazasu ta6a ƙyalemu ba kodan saboda kada mu tona masu asiri dole
subi diddiginmu" sajeed ne Yai maganar..

Unaisah ta natsu tana kallonsu, ba tare data tsoma baki ba, saboda ita a halin yanzu ta fahimci wani abu,
tun da har jami'an isod suka gano salsabeel to kuwa tana da tabbacin sun san komai game da rayuwarsu!!
Kallonsu kawai su ke yi.

"Ƙwara kowa yasan me suke aikatawa, mu faɗa masu kawai, su taimaka su rabamu da su, Su ƙyale ɗan
uwanmu yayi rayuwarshi cikin salama" Hanna ce ta faɗa tana faman tada jijiyoyin wuyanta.

Calmly Unaisah ta furta"ku daina surutu kuna hana shi natsuwa, yakamata mu je mu kwanta, tun da mun
ganshi inyaso gobe da safe sai mu dawo mu ƙara duba shi"
Shiru su ka yi, ba tare da sun motsa ba saboda basu sun yin nesa da shi, da da halima a ɗakin shi za su
kwana, yayin da su ke cigaba da kallon shi tamkar zasu haɗiye shi, tsananin tausayin shi suke ji ga wata irin
ƙaunarsa da su ke ji.

Parveen da Jamimah sai hamma su ke yi, ita jamimah hada gyangyaɗin bacci.

"Please ku tashi mu tafi ɗakunan mu" Nawfal ne yai maganar, tare da miƙewa ya zagaya ta 6angaren da
garkuwa yake akwance ya duƙar da kanshi ya manna mashi sumbata akan forahead dinsa, ganin hakan
yasa Jemimah yin sauri rarrafawa tsabar iyayi saman chest dinshi ta haye tukunna ta manna mashi
sumbata kan cheek dinsa har sau biyu, murmushi kowan nan su yasaki abun ya ƙayatar da su.

Ƙarasa hawayewa gadon Batool tayi har zuwa gefen Garkuwa in a cool voice ta furta"ɗan uwana rabin
raina, idan kana saurare ni, nayi kewarka sosai, Allah ya baka Lafiya sanyin idaniyata" gefen fuskarshi ta
manna ma kiss, kafin ta sauka daga kan gadon, da sauri Haris ya zagaya ta inda su nawfal suke a tsaye daga
gaban gadon ya russina tare da ruƙo hannun Danish ya buɗe tafin hannunsa A hankali ya sumbace shi kafin
Ya furta"ko ban faɗa maka ba, nasan kasan da irin ƙaunar da nake yi maka jinin jikina, Allah ya tashi
kafaɗunka" bayan Haris Ya saki hannun shi, Javed Ya miƙe ya nufi Side da danish yake, Ya manna mashi kiss
a forehead nashi.

"Big bro, our guardian, Allah ya baka lafiya" ya faɗa cikin nuna tausayawarshi.

Sajeed dake agoye da Azeeza, Ya matsa kusa da Danish,Ya sauketa daga gefen gadon, da rarrafe ta lalubo
Danish ta ɗaura fingers dinta saman fuskarshi ta shasshafa shi, duk suna ta kallonta.

Haris da zolaya yace"kada ki lashe mana ɗan uwa, Kiss ɗaya zaki manna mashi ya wadatar" kusan sau uku
ta sumbace shi, biyu kan cheek dinsa, ɗaya kan tsinin hancin shi, bayan ta gama nata, Sajeed ya ruƙo
Hannun shi kamar yadda Haris yayi, a hankali Ya sumbace shi gently ya furta"ka kula mana da kanka our
super star, zamu kwana da tunaninka, gobe da sassafe zamu zo duba lafiyarka, garkuwar mu"

Murmushi duk suka saki, wani irin daɗi suke ji, mayar da goyan Azeeza Sajeed yayi akan bayan shi.

Hanna ma ta sumbace shi, Ya rage saura Unaisah, dake zaune tayi zugudun kamar mai tunanin wani abu.

"Genie saura ke" acewar jemimah idanuwanta sunyi luhu luhu saboda baccin da take ji.

"Unaisah we are waiting for u, ki yi mashi kiss kamar yadda muka Yi mashi kafin mu tafi" Sajeed ne yai
maganar, tamkar bata ji me suke cewa ba, tayi kasaƙe tana faman wurwurga eye balls dinta.

Dafa shoulder dinta Batool tayi"Sister, Kin yi shiru, ki motsa mana, Ko kin manta abun da muka ce zamuyi
idan mun fita daga ɗakin Danish"

Haris Yace"menene za ku yi" da sauri tace"karatu ne zamu yi kafin mu kwanta bacci" Ya furta okey,

Jiki asanyaye Unaisah ta ƙarasa haurawa kan gadon, crowling slowly ta nufi Danish, koda ta ƙarasa inda
yake a kwance, saita sanya hannu ta zame hular kanta, nan take nannaɗaɗɗiyar sumar kanta ta warwaro ta
sauko kan kafaɗunta, rumfa tayi mashi da gashinta ta yadda ba zasu Iya ganin sumbatar da za ta yi mashi
ba.

Sajeed Ya buga ƙafa yace"ba mu yarda ba wlh, You are trying to be smart Unaisah, dole ki janye sumar
kanki mu gani da kyau" Ya faɗa yana sakin murmushi.

Haris yace"kiyi yadda kowa yayi" Batool da su javed sai murmushi suke saki, shiru tayi bata tanka masu ba.
Babu Mai Iya ganinta acikinsu, ɗaura tsinin hancinta tayi akan nashi, numfashinsu ya soma kokawa dana
juna, hatta bugun zuciyarshi saida ya canza, dogon wuyan shi ta fara manna ma sumbata har zuwa kan
chin dinsa ta sumbace shi a hankali kafin slowly ta ɗago da kanta, ta sumbaci forehead dinsa, ta dawo kan
eye lids dinsa ɗaya bayan ɗaya ta sumbace su, tana ƙoƙarin kai mashi sumbata kan soft lips dinsa ba zato
ba tsammani taji an damƙo sumar kanta, da ƙarfi ya ɗago da ita, A firgice ta juyo don ganin wanene Ya
katse ta......

Rass taji gabanta Ya faɗi ganin Big Guy, wata irin kunya ce ta rufeta, da sauri ta sanya tafukan hannayenta
ta rufe face dinta, su Haris dake atsaitsaye sai tiƙar dariya suke yi, ashe tunda ta dukufa tana sumbatar
danish suka jiyo motsin buɗe ƙofa, suna kallon shi yai masu alamar suyi shiru da bakinsu, nan fa kowan nan
su Yaja baki yai shiru, Lamarin ya ɗaure mashi kai, don bai fahimci me ta ke yi ma danish din ba, yadai ga
tayi mashi rumfa da sumar kanta, Cikin sanɗa yaje gaban gadon Ya daddage Ya damƙo gashinta kanta.

"Ki ji tsoron Allah Jari, Faɗa min kike Aikata ma bawan Allahn nan" fuskar shi ɗauke da murmushi yayi
maganar yana bin ta da kallon tuhuma, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi Ni ba ƴar iska
bace, ba abun da kake tunani bane, Ka tambaye su ka ji" ta faɗa tare da ɗago da kanta a lokacin ya sakar
mata gashin kanta, duk tabi ta ruɗe, gani ta ke yi kamar kallon ƴar iska yake yi mata, tun akan abun da Ya
faru ɗazu da suka kama ta a ɗakin Danish ta cire mashi ma6allin gaban rigarshi, shiyasa take fargaban kada
ace kallon yar iska yake yi mata.

Sunnar da kanta ƙasa tayi, fuskarta a tur6une babu annuri, sai faman ƙyafkyafta idanunta take Yi

"Ƴan uwan Jari, ku fada min me take aikatawa tunda ita bazata fadamin gaskiya ba" Ya fada Yana nuna su
Sajeed Da hannun shi
Har suna hada baki wurin maimaita sunan JARI,
da shagwa6a66iyar Murya Jemimah tace"Unaisa ɗin mu ce Jari"

Big guy yace"Yeah, Ita nake nufi, ko bakusan cewa ita ɗin Jari bace"? Da mamaki suka girgiza mashi kai
gami da tambayarshi ma'anar jari.

"Shi Jari wani abu ne da idan ka sanya shi zaka samu riba, yar uwarku jari ce gare mu baki ɗaya, tun da
muna ƙaruwa da ita, kamar dai yanzu da take koya mana wani baƙon abu...." tunkan ya ƙare maganar
Unaisah tai saurin furta"wlh bani na faraba ai, Naufal ne Ya fara Yi mashi kiss, kowa yayi nice ma ta ƙarshe,
Kuma ni bama kiss nake mashi ba, Falaƙi da nasi nake karanta mashi..." a shagwa6e ta ƙare maganar.

Dariya suka saki gaba ɗayansu, bayan sun lafa, Big guy yace Ku tashi muje in rakaku ɗakunan ku, Dare
Yayi sosai, Yakamata kuna bacci da wuri saboda karatun asubahi da ake koya maku" amsa mashi su ka yi da
toh, yakai hannu ya ɗauki Jemimah, kafin su bar ɗakin saida Kowan nan su yayi mashi addu'a suka tottofe
mashi jikinshi, har sun fita Unaisah ta dawo ɗakin da gudu ta lullu6e garkuwa da lallausar bargonsa, kafin
ta kashe switch din dakin yai duhu, ta kunna mashi bedside lamp, tamkar karta bar ɗakin haka take ji,
addu'o'i ta tottofa mashi tun daga ƙasa har sama kafin tabi bayan su suka nufi bedrooms din su.

Sai da big guy ya tabbatar kowan nan su Ya shiga dakin shi, tukunna Ya nufi hanyar da zata kaishi part din
da room dinsa Yake agidan.

Fitarshi keda Wuya, Unaisah da Batool, suka fito daga ɗakin su, Hannayen su ruƙe da plates sun rufe su,
abincin da suka ajiyema Ummi ne, tun ɗazu suka shirya zuwa dakinta don su kai mata abinci sun kasa
saboda fargabar awani hali zasu taras da ita, duba da yanayin da ta shiga ɗazu na ganin sheikh Imam,
Batool ce ta bada shawarar su ɗebi abinci su kai mata, tun lokacin da aka kawo masu dinner dinsu, Suka
ɗibar mata plate biyu na abinci, A ɗakinsu suke 6oye mata shi sai yanzu su ka samu damar fito da shi.
Cikin sanɗa suke yin tafiya suna ƴan waige waige kamar wasu munafukai, fargaban su kada wani ya gan su,
basu san cewa duk wani motsin su akan idon jami'an isod dake kula da CCTV room ɗin gidan.

A hankali suka haura second floor kaitsaye suka nufi ƙofar dakin ummi, cike da fargaba Batool take
zazzare ido, don har yanzu mugun jin tsoron ummi take yi, gashi ta damu da ita kamar yunwar cikinta.

"Sister, Ni zan jira ki awaje, ke sai ki fara shiga" cikin muryar raɗa batool tayi ma unaisa maganar.

Harara unaisah ta jefa mata" waye ya kawo shawarar mu kawo mata abincin"? Yamutsa fuska batool
tayi"Ni ce,"

"Don haka ke zaki fara shiga, Ni dama hankalina bai kwanta da mu zo kawo mata abinci ba, wata'ƙil ma
taci abincinta tun ɗazu, mu ne ba mu sani ba"

"Shikenan, Mu koma ɗaki sai mu cinye"

Dariya Unaisah tasaki tana kallon batool tace"ai wallahi yadda kikasa muka ajiye mata abincin nan sai mun
kai mata shi, Kuma ke zaki miƙa mata da hannunki" ta faɗa tana nuna ta da girar ta, jikin Batul harya fara
kerma tsabar tsoro, idanunta suka ciko da ƙwalla.

"Nidai mu koma ɗaki, sai in cinye abincin" a tsorace ta faɗa.

da zolaya Unaisah Tace"You are just a coward, ai na lura shakkar aunty ummi kike ji, gashi duk kin damu
da ita, Yinin yau tun bayan data shige daki kika ga bata fito ba shikenan kika addabe ni da tambayar Aunty
ummi, bata ci abinci ba, tana adaki, ko awani hali take aciki, ni narasa gane meyasata kuka, yen yen yen
haka kika isheni, shine yanzu kuma mun kawo abincin kike kokarin zillewa" murguɗa mata baki batool tayi
batare da tace mata ƙala ba.

Knocking ƙofar Unaisah tayi daga ciki suka jiyo Muryar Ummi ta furta"Come In"

Tura ƙofar Unaisah tayi kafin ta shiga da sallama abakinta, Batool tana abiye da ita sai fama 6oye kanta
take Yi.

Kusan atare suka ɗaura idanunsu akan shimfiɗeɗan gadonta, tana daga kwance ta ɗaura kanta saman
pillow, yayin da eyes dinta ke akan apple laptop dinta da ta ajiye saitin inda take fuskanta, wata yar gown
ce a jikinta, shara shara kana Iya hangen inners dinta, tsayin rigar bai wuci gwiwar ƙafarta ba, gashin kanta
a yamutse yake mai uban yawan gaske, ya cunkushe wuri guda, yanayinta da kasala a jikinta babu kuzari.

Kamar an danna masu full stop haka suka dakata da yin tafiyar suna faman binta da kallo, jin shiru sunyi
mata sallama basu shigo bane yasa taɗan ɗago da idanunta waɗanda suka rikiɗa suka koma launin Ja, Su
kansu da su ka yi tozali da idanunta saida suka sha jinin jikinsu, wani ɗan iskan murmushi tasakar masu
haɗi da ɗage masu gira ɗaya tace"meyasa ku ke kallona? Ba zaku shigo ciki bane"? Kallon juna su ka yi cike
da al'ajabin jin sautin muryarta tamkar ta gardin ƙato wanda yasha ya bugu da giya.

"Aunty Ummi baki da lafiya ne"? Unaisah ce ta furta maganar, a kasalance ta miƙe zaune haɗi da jingina
bayanta kan gadon, kafin ta furta"Lafiyana Lau, menene ku ka kawo min"

ta tambaya yayin da take kallon Batool data 6oye kanta bayan Unaisah.

"Abinci ne" buɗe ido ta yi alamar tadan yi mamaki .

"Wanene Yayi tunanin kawo min abinci acikin ku"? Ta faɗa tana nuna su da yatsanta.
Cikin muryar raɗa Batool tace"Dan Allah ki ce mata ke ce bani ba"

Murmushin mugunta Unaisah tayi jin abun da ta raɗa mata,

Da gangan tace "Batool ce, tun ɗazu da kika tafi ɗaki kina kuka ta hana kanta sukuni, ta dinga damuna da
tambaya akan Aunty ummi shiru bata fito taci abincin ta ba, ta tafi tana kuka bansan awani hali take ba, Pls
sister mu ajiye mata abinci mu kai mata"

Lumshe idanu ummi tayi, har cikin ranta taji dadin jin hakan.

"Ku shigo daga ciki," ta faɗa tana nuna masu gadonta da hannu, Unaisah ce tayi gaba Batool tana abiye da
bayanta kamar wata mara gaskiya, taji haushin faɗa matan da unaisah tayi

"Bani plates din" ta fada tare da mike masu hannu ta kar6i plate din hannun Unaisah, ta ajiye akan gadon,
ta kar6i na hannun batul ta ɗaura shi kan side drawer tana fadin"tun da kun kawo min abincin, ku zaku
bani a baki in ci"

duk idan tayi maganar sai sun kalli fuskarta, bakomai ne yake ɗaure masu kai ba, face sautin muryata daya
canza kamar na wadda tasha giya, ga idanuwanta sun yi ja.

"Aunty Ummi sautin voice dinki Ya canza, Idanunki ma suna yi ja sosai, ba ki jin daɗin jikin ki ne"? Cikin
kulawa Unaisah tayi mata tambayar, ƙamshin turaren ummi duk Ya buɗe ɗakin.

"Nothing is bothering me. Maybe it was my crying that made my voice change." She said, trying to bring
her voice back to normal.

"Meyasa ki kuka ɗazu da kika ga sheikh Imam"? unaisah ce ta ƙara jefa mata tambayar

da zolaya tace"Unaisah kin cika bin ƙwaƙƙwafi, Kina min tambaya kamar Ƴar jarida, Ku zo ku zauna Yau
muyi fira" ta faɗa tana nuna masu mattress.

Unaisah ce ta fara hawa gadon, Kafin Batool ta haye gadon tana mai jin shakkar haɗa ido da ummi, suna
fuskantar juna da ita, Batool tana agefen Unaisah, Ummi tana fuskantarsu.

ta lura kamar Aunty Ummi batason tambayar da take Yi mata dangane da sheikh Imam hakan yasa taja
baki shiru.

da fara'a akan fuskarta tace"Banyi tsammanin kun damu dani ba, har na fidda rai da zanci abinci, gashi
wata iri yunwa nake ji kamar inci ƴan hanjin cikina...." ta ƙare maganar tana ya mutsa fuska ta buɗe plate
din gabanta, ashaƙe yake da tsiran nama, yanka yanka yaji kayan haɗi sai maiƙo yake yi ga kayan lambun da
aka yayyanka mashi, sai ƙamshi yake yi, sun kura mata ido suna kallon ta.

"naji daɗin tsiran nan da ku ka kawo min, wa zai fara bani abaki" da sauri Unaisah tace"Batool" ta faɗa tare
da ruƙo hannun batool ta ɗaura shi kan plate din, Hankalin batool ba ƙaramin tashi yai ba, fuskarta duk ta
yamutse itafa atakura take jin kanta har yanzu bata manta abunda ya faru tsakaninta da ummi ba a daren
Jiya, gani takeyi kamar bata ƙaunarta.

"Babe, Ki bani tsiren miyau na Ya gwada" ta faɗa tana ɗage mata gira, hada sakar mata murmushin gefen
fuska
Daurewa batool tayi, ta ɗauki tsiran hannunta na kerma takai shi bakin ummi, Unaisah na dariya tace"wlh
batool tsoron ki take ji aunty ummi," ruƙo hannun batul ummi tayi ta ƙarasa tura naman abakinta, har
wani lumshe ido takeyi, tana taunarshi ta ce.
"Na lura da hakan, Amma kada ki damu zamu saba ne" Ummi ce tayi maganar, sanya hannu unaisah tayi
cikin plate din tsiren ta dauko ta tura ma ummi abaki, Idan batul ta bata ita ma sai ta bata abaki, wani irin
ƙaunarsu ce ta ɗarsu acikin zuciyarta, A hankali take satar kallonsu afakaice, don bata son su gane tana
kallonsu.

Bayan sun kammala bata tsiren suka buɗe dayan plate din me ɗauke da chips, shima suka bata har tana
tambayarsu sunci nasu abincin ne? Suka ce mata Eh sun ci, duk da haka saida ta ɗebi chips ta tura ma
kowan nan su abaki, Cike da nishadi suke tauna.
bayan sun gama, Unaisah ta ɗauko masu Juice me sanyi suka sha.

Ganin sun fara yunkurin tafiya ne Yasa tace"why baza ku tayani kwana ba"? Waro ido batul tayi tunawa
da abinda Ya faru Jiya, Murmushi Ummi ta sakar mata, Ta fahimci tsoro take ji kada ta ƙara Yi mata irin na
jiya hakan yasa tace

"Asaman gadona zamu kwana, kafin muyi bacci har kallo zan kunna mana a laptop," jin hakan yasa batul
taji hankalinta ya kwanta.

gaba ɗayan su suka haye gadonta, unaisah ta takura ma Ummi akan tana son ta gyara mata gashinta,
adole ummi ta ɗauko mata comb, da ita da batool suka kama gashin kanta suka dinga sharce shi bayan sun
kammala, ta basu ribbom babba suka ɗaure mata gashin daƙyar saboda yawanshi gashi taurine dashi
donma tana gyarashi da mayuka masu sanya laushin gashi.

Gefe da gefenta suka kwanta, ta kunna masu kallo a laptop, cikin nishadi su ke yi, da zarar anzo wurin da
za'ae kiss ko makancin hakan take yin saurin rufe masu idanuwansu da tafukan hannayenta, hakan ba
ƙaramin dariya yake basu ba, Saida dare Ya fara nutsawa ta kashe kallon, a lokacin bacci mai nauyi yai
awon gaba da su, ta sauko daga kan gadon ta kunna masu bedside lamp kafin taje ta kashe hasken ɗakin
ya rage saura na fitilun gefen gadon, ta dawo ta kwanta a tsakiyarsu.

A jiyar zuciya ta sauke, tare da ɗaura eye balls dinta tana kallon fuskar batool dake ta sharar baccinta, A
hankali ta daura hannunta kan hular batul ta zameta, gashin kanta ya bayyana, shafashi taci gaba dayi tana
binta da kallon ƙurulla, gani take kamar ta ta6a sanin mai kama da ita, sai dai ta gaza tuna wanene ko
wacece ke kamanceceniya da ita cikin mutanan da tayi tarayya da su.

Lumshe idanuwanta tayi yayin da ƙwalwarta ke tariyo mata wani abu can daya ta6a faruwa a
arayuwarta wanda yayi silar tarwatsewar Farin Cikinta, baƙin tarihin da har bada bazata ta6a mantawa da
shi ba, Ya lalata darajarta da ƙimarta Ya zubar mata da mutuncinta a idon jama'a, wasu kalmomi ne suka
soma yi mata yawo acikin kanta.

_Nayi danasanin kasancewarki Ƴata, wallahi da ace nasan da zuwan wannan ranar da tun kina acikin ciki
zanyi silar da za'a 6arar dake_

Tuna wannan maganar yasa ta fashe da wani irin matsanancin kuka tamkar ana zare ranta, sham ta manta
da su Unaisah dake bacci.

Cikin muryar bacci batul ta furta"aunty ummi kuka ki ke yi"? Da sauri ta haɗiye kukanta, Hannunta ɗaya
atoshe da bakinta, ta runtse idanuwanta.

Idanun batul biji biji ta buɗesu, akan fuskar ummi, hankalinta ya tashi matuƙa ganin yadda fuskarta ta jiƙe
da hawaye, muryarta na rawa ta furta"aunty.... ummi, baki da lafiya? Meke damunki"?

Daƙyar ta iya buɗe ido ta kalli batool dake kallonta batare da tace mata komai ba.
Duk da shakkarta da Batool take ji hakan bai hanata jin tausayinta ba, hankalin ta ya tashi matuƙa da
ganin yanayin da ummi take aciki.

Hannunta na kerma ta ɗaura shi saman fuskar ummi a hankali take share mata hawayen dake sintiri kan
kuncinta.

"Aunty ummi ki daina kuka dan Allah, bana son ganin ki cikin damuwa"

Muryarta adisashe ta furta"meyasa kika damu dani? Ko Kin manta abunda nayi maki jiya"?

"A'a ban manta ba, ni kawai ina ƙaunarki kuma bana son ganin kina kuka"

tayi mamakin abunda batul tace mata.

"Don't worry, I'm feeling better. Go back to sleep." ta faɗa tana ƙoƙarin danne damuwarta.

"Bazan Iya bacci ba, idan bakiyi ba," kalaman batul sun sanyaya mata zuciya.

"Ki sanyani inyi baccin" matsawa batul tayi dab da ita.

Da ƙarfin hali ta rungume ummi sosai tayi tighting dinta, ta daura hannayenta saman bayanta, itama ummi
ta daura nata hannun asaman bayan batool ta ƙanƙameta, wani irin yanayi ta soma ji mai wuyar fassaruwa
hatta bugun zuciyarta ya canza, ta rasa gane dalilin faruwar hakan, Yau ne karo na farko data fara rungume
Batool ajikinta amma wani iko na Allah sai ta dinga jin kamar ta ta6a rungumarta, ita kanta Batool din sai
da taji canzawar bugun zuciyarta daurewa kawai take yi amma sai take ji kamar su dawwama ahaka ita da
ummi batare da sun raba jikin su daga na juna ba.

Ƴan addu'o'in da Unaisah ta koya masu, ta soma karantowa tana tottofa ma ummi.

Wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, lokaci ɗaya ta nemi damuwarta tarasa, Ahaka bacci mai nauyi yayi
awon gaba da su rungume da juna kamar zasu koma mutun ɗaya.....

(Nima kuma na rungumi Alƙalamina)

Mu haɗu Gobe Idan Allah yakaimu da rai da Lafiya🌹

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida*[06/03, 6:46
PM] Anty Hajjo 2: ~TAKUN ƘARSHE~
_______________________Boss Bature✍️

*The Unexpected call📞📲*

*❤CHIEF OWAIS✊*

A tsaye yake a gaban dressing mirror, cikin shiga ta pajamas Maroon colour, yayin da baba obie dake zaune
saman gado ya ƙura mashi ido yana kallon shi, A hankali yakai hannu ya ruƙo roban massage oil Ya juya
suka haɗa ido da shi, murmushi baba obie ya sakar mashi yana fadin"sannu da ƙoƙarina, tun ɗazu nake
kallon ka, kanata laluban mai bayan ga abunan akusa dakai bansan me kake tunani ba daya ja hankalin ka.

Murmushin gefen fuska chief owais ya sakar mashi, kafin ya nufe shi yana fadin"grandpa, kaima kaso ka
wahalar dani, maimakon ka fadamin ka ganshi sai ka barni ina ta neman shi" dariya Obie yai cike da nishaɗi
yau jin shi yake tamkar wanda akayiwa albishir da gidan Aljanna saboda zuwan Owais Ya faranta zuciyansa.

Daga gefen shi chief owais Ya ɗaura Massage Oil din, Baba obie Ya juya mashi bayansa ta yadda zai ji
dadin yi mashi tausar dama daga shi sai short a jikin shi.

"My Grandpa, Ka tsufa sosai, bayanka yayi tamoji tamoji" da zolaya chief ya furta maganar.

"Ba dole na tsufa ba, shekaru sun ja Owais" in cool voice ya fada
A lokacin Owais Har Ya fara shafe mashi bayan shi da message oil din tare da yi mashi tausa, A hankali
yake matsa fatar bayan shi yana murzata Runtse idanunshi yai haɗi da cije la66ansa Chief har leƙen fuskar
baba obie yake yi, ya fahimci kamar yana jin zafin tausar da yake yi mashi ne.

"Wash! Allah na! Owais kabi A hankali, wannan hannaye naka kamar na samudawa, kana murza min
baya kamar yadda kake damƙar mugu idan ya aikata laifi" ƙumshe dariya chief yai jin sambatun da baba
obie Yake yi mashi.

"Baba, saboda lafiyarka nake yi maka hakan, naga kana runtsa ido kuma kana cizon la66anka, Hakan na
nufin kana jin zafin tausar, Amma idan na gama yi maka zaka ji daɗin jikin ka......" ɗaga muryarshi yayi da
ɗan ƙarfi ya furta"toh.. Toh.. Naji yanzu saura ƙafafuwan da ƙirjina amma dan Allah kabi a hankali kada ka
shaƙe min zuciyata, dama ya lafiyar gwiwa"

"Kana bani nishaɗi My Grandpa, Amma kayi min laifi...." kafin Ya ƙare maganar Baba Obie yace"Laifin me
kenan"? Ya fada tare da Juyawo Yana fuskantar shi, Ya ɗaura bayan shi kan pillow, tare da miƙe ƙafafuwan
shi yana duban Owais.
"Kafin In bar Nigeria ka yi min alƙawarin Zaka dinga kula Min da lafiyarka, Har family doctors din mu nayi
ma magana akan su dinga duba ka akai akai, dama tun time dana faɗa masu hakan sai da dr Alex Ya faɗa
min cewa kaine baka basu damar da za su duba ka, da zarar sunyi yunƙurin bincika lafiyarka sai kace masu
kashe ka suke son yi meyasa"?

Ya jefa mashi tambayar Yana bin shi da kallo, hands dinsa na akan ƙafafuwan baba obie da yake yima
tausa

Shiru yayi mashi batare da ya furta komai ba.

"Ba ka da abun cewa, shiyasa ka yi min shiru kana kallo na ko"? da zolaya yayi mashi maganar, baba obie
yai murmushi tare da hararar shi yace"Bawai na rasa abun cewa bane, kawai ina tunanin yadda kake nuna
damuwa akaina, Idan kaga na faɗa masu haka toh ni lafiyana ƙalou bana buƙatar a bincika ni," ya faɗa yana
shafa gemun shi da hannu ɗaya
Shiru Owais yayi mashi batare daya furta komai ba, ya maida hankali akan tausar da yake yi mashi.

"Nayi kewarka sosai, Meyasa ka yi nesa dani? Abun da baka ta6a yi min ba owais, ka riga da kasan yadda
na ƙwallafa rai akanka, sai da takai ga ko bacci nake yi ina sambatu a kan ka, ko na kira layin wayarka baka
ɗagawa meyasa Owais? Ko dan kaga na damu dakaine" ya faɗa yana kwa6e mashi fuska kamar zaiyi mashi
shagwa6a, chief owais dake kallon shi aranshi ya ayyana rigimar tsufa ta motsa, A fili kuma ya furta"Ba
haka bane, Kamar yadda ka damu dani nima haka na damu dakai, ko aiki nake yi kana arai na, Grandpa
kasan yanayin aikin mu ɗaga waya wuya yake min wasu lokuttan ma bana sanin an kira ni.... " bai kai
ƙarshen maganar ba ya dakata yana kallon ikon Allah ganin baba obie yana kwaikwayon maganar shi, gaba
ɗayansu suka sanya dariya.

"Are you making fun of me? I won't speak anymore" obie na dariya yace"ka yi haƙuri jikana, Muryarka ce
da daɗin sauraro, shiyasa ƴan mata suke haukan su kai kuma kana yi masu rowar kan ka, faɗa min menene
Sirrin ko akwai wani abu da kake sha wanda yake ƙara mata daɗi" calmly ya furta a'a, daga Allah ne"

"Amma kasan wani abu"? Girgiza mashi kai owais yai.

"Dawowar nan da kayi, Ka canza min Owais, Ka ƙara Girma kuma Ka ƙara Kyau"

"Shiyasa ka ƙura min ido Kana kallona ko"? fuskar Obie da murmushi Yace"ai ba laifi bane don na kalli
Jikana, kai ɗin mallakina ne, Halak malak, Mahaifinka ma ya sallama min kai tun kana ƙaraminka, Ni ke kula
da kai, gaskiya Owais Ka more ni sosai, komai nawa akanka Yake ƙarewa, duk inda zan taka tare dakai nake
zuwa.... " tun daya fara maganar, Chief ke sauraron shi, A lokacin Ya kammala Yi mashi tausar, Har ya
mayar da man kan mirror.
Hayewa yai saman gadon, Ya kasance Suna fuskantar Junansu.

"Ban taba tunanin zan kai wannan lokacin araye ba, bani da burin daya wuce inga girmanka, graduation
ɗin ka, harma da auran ka da ƴa'ƴan ka, Sai gashi cikin Ikon Allah da raina da lafiyana, Ka girma ka kammala
karatu harma kana aiki, sai dai auran ne har yanzu baka da niyar yin shi balle har in sanya rai da zan ga
jikokin da zaka sama min" ruƙo hannun shi chief yai acikin nashi ya ruƙe shi gam, kafin ya soma yin magana
a tsanake.

"Kada hakan Ya dame ka, in sha Allah nan bada jimawa ba, Mafarkin ka zai zama gaskiya, ko dan saboda
farin cikin ka zan yi ƙoƙarin yin hakan"
lumshe do baba obie yai wani irin farin ciki ne ke ratsa zuciyar shi.

"Allah Ya nuna mana lokacin, zanyi farin ciki mara misaltuwa, kuma za'ayi shagalin bikin da ba'a ta6a yin
makamancin shi ba,"
duba agogo Chief Yai"baba dare yayi sosai, Yakamata mu kwanta mu huta, Gobe da Safe In sha Allah zan
ƙara yi maka tausar, don kaji daɗin jikin ka" amsa mashi yayi da toh, kafin ya soma ƙoƙarin gyara kwanciyar
shi, saukowa owais yai daga kan gadon Yaje ya kashe switch din dakin, Ya dawo ya kunna masu fitilun gefen
gadon, daga bisani ya haye ya kwanta gefen baba obie, daga kwance suka cigaba da yin fira sama sama,
har bacci yafara daukar owais, Jin shiru yadaina magana yasa baba obie juyowa yana duban shi, shafa
gefen fuskarshi yayi tare da sumbatar shi kafin yayi mashi addu'a ya tofe shi, ya janyo masu lallausan duvet
Ya lullu6e rabin chest din su.........❤

*(After Some Days)*

Bayan wasu ƴan kwanaki, tun ranar da Baba obie ya yanke alakar Prime minister da Danish bai sake gigin
zuwa inda yake ba, Yabar komai a hannun sheikh Imam da chief Owais, saboda a halin yanzu baida lokaci,
ba azaune yake ba, ranar lahadi suka fara halartar National mosque tare da manya manyan malaman
addini suka gudanar da taro, aranar litinin kuma Ya ziyar ci majalissai dokoki ta Nigeria, sunyi zaman
tattaunawa da ƴan malissa a ƙarƙarshin jagorancin senate president lateef, tare da kakin majalissai wakilai,
sun karrama Hateem a matsayin babban baƙonsu, sunji dadin tattaunawar da sukayi dashi kasancewar shi
mutun daya iya mu'amala da mutane duk inda aka zauna dashi sai an ƙaru da baiwar da Allah yayi mashi
na iya tsara kalami, ga farin jinin dake gare shi, gidajen jaridu basu da abin yaɗawa daya wuce ziyartar
national assembly da prime minister yayi, komai daya tattauna da shawarwarin daya bama shuwagabannin
Nigeria, saida ƴan jarida suka yaɗa shi a social media, duk aranar ya ziyarci gidajen marayu da gidan Yari,
yayi masu kyaututtuka naban mamaki wanda ya gigita mutane zunzurun kuɗi ya bayar da za'a tallafi
rayuwarsu da shi, aranar talata yabar garin abuja shi da Iyalan shi da ƴan uwan shi tun daga kan senate
lateef his excellency deen and his excellency abdul razak tare da Sharafudden da hajiya saratu, Sir mubarak
da kuma muƙarrabansa na ƙasar canada, Chief of staff, national security advisor, 6angaren masu ba su
tsaro Royal canadian mounted polices and Nigerian Soldiers.

kasancewar A privet jet din mai girma sharafuddeen suka yi tafiyar basu jin wahalar zuwa ko'ina, arana
ɗaya sai suje har sama da gari uku, ƴan mintuna jirgin yake sauke su suje inda zasu je, kafin marece su lula
zuwa wani state din.

Wuri na farko da suka fara ziyarta bayan barin su abuja, masauratar yarbawan jihar lagos suka fara sauka
an mutuntasu an kuma karramasu sanin matsayinsu a ƙasar, kafin suka Wuce Garin Kano, anyi masu
kyakkyawar tarba, kwana ɗaya su ka yi awashe garin ranar da zasu baro garin saida suka biya kasuwannin
kano da gidajen tarihi da gidan gwamnati, daga bisani suka ziyarci jihar bauci, a katafaren wurin
shaƙatawar nan me suna Yankari anan suka yaɗa zango tare da gwamnan jihar, haƙiƙa Prime minister ya
mori lokacin shi a Nigeria, yaji dadin yawon buɗe idon da suka je tare da ƴan uwanshi, sai dai abu ɗayane
bai goge ba a tunanin shi wato Danish, da shi yake kwana da shi yake tashi, ko abinci zaici saiya tuna da shi,
aranshi ya ayyana inama ace hada shi suka taho yawon nan da Allah ne kaɗai yasan irin farin cikin da zai yi.

A ranar Alhamis suka dawo Birnin Abuja amatuƙar gajiye, friday za'a shirya mashi family dinner, Ranar
sataurday Hateem zai bar Nigeria agurguje zasu koma Canada.

____________________________✍️

Idan muka koma 6angaren su Unaisah cikin ƴan kwanakin nan wata irin shaƙuwace ta shiga tsakaninsu
da ummin america, musamman Batool sun kulle da ita, Har karatun kur'ani ta fara ƙoƙarin koya masu ranar
da suka ji ta yi masu ƙira'a tsantsan mamaki ne ya kama Unaisah, don ita bata ta6a tsammanin ummi ta iya
karatun kur'ani ba sai gashi tana yi mata ƙarin karatu cikin suratul baƙra, har tambayarta tayi aunty ummi
dama kin iya karatu, sai tayi dariya tace mata hadda gareta ai, tun tana ƴar shekara goma sha bakwai ta
haddace alkur'ani mai girma, Unaisah ta jinjina mata aranta ta ayyana amma ya akai take aikata sa6on
Allah bayan ita din mahaddaciyar alƙur'ani ce, wata kil kuma wata jarabtar ce ta ubangiji Allah wa'alamu.

Damuwarsu ɗaya ayanzu Ɗan uwansu Danish yaƙi dawowa dai dai, Har yau babu wani cigaba kamar
kullum yana akwance idanuwanshi arufe wanka da cin abinci su boss ne ke taimaka mashi, da kuma
salsabeel dake zuwa dubashi kusan kullum sai yazo, tare da shi ake ɗawainiyar kula da garkuwa, haka zalika
sheikh imam kusan agidan yake wuni, wurin yi mashi addu'o'in da zasu bashi kariya, Hatta Ƴan uwan shi su
Sajeed sai da Imam malik Ya koya masu addu'o'in da zasu dinga yi mashi hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu
ba, sau uku suke zuwa duba shi a ɗakin shi don suyi mashi addu'a safe rana da dare, Ita unaisah har tsakar
dare tana zuwa ɗakin shi ba tare da sanin kowa ba, duk ta ƙagara ya yadawo hayyacin shi, akwai abubuwa
da dama da take son yi mashi albishir, na farko tana so ta faɗa mashi dangane da prime minister Hateem
dake kama da shi na biyu abun arziƙin daya fara fito mata a ƙirji, ta riga ta yanke shawarar fada mashi idan
ya dawo normal, ta hana kowa yagansu a 6oye take ɗaure su da mayafi ta matse su don karsu bayyana
agani, abunda bata sani ba, batool tuni ta ganota duk in zata shiga toilet tsakar dare don tayi masu kallon
ƙurulla sai batool tayi mata la6e, ta dinga tiƙar dariya kamar cikinta zai ƙulle.

Tun ranar da ummi tayi tozali da sheikh imam bata ƙara bari sun haɗu ba, da zarar yazo gidan take komawa
ɗaki ta zauna ko bakin ƙofa bata fita har sai ta shaida tafiyar shi tukunna take saukowa down stairs.

A 6angaren su Benazir, since last week taso zuwa gidansu Aneelerh Allah bai nufa ba, saboda rashin samun
layin Abie din Aneelerh, Alhaji ubaid yayi trying layin shi baya shiga, kuma shi kaɗaine dama yake da
numbar shi, Adole Benazir ta haƙura da zuwa gidan su tun da bata da hanyar da zata samu address din su,
bata ji dadi ba gashi har Mamie tafara yi mata zancen komawarsu Jos, don ma alhaji ubaid yace ba yanzu
ba sai sun cike wata ɗaya ai da tuni sun jima da komawa, mamie bataso hakan ba, saboda ita bata son
suna zama gidan Alhaji musa, badan bata jin daɗin gidan nashi ba sai don saboda ranta dake raya mata
cewar ba don Allah yasanya suka zo gidan shi ba, don kawai yaji daɗin juyasu son ranshi shiyasa yake son
su zauna masa agida, taci alwashin indai Alhaji ubaid bai basu damar komawa joss ba cikin watan nan to
zata kama hanya ta tafi ne koda ita kadaine! Sauƙinta ɗaya Hajiya sarah tana janta ajiki matar tana da
mutunci duk in tadawo daga office sai ta ware masu lokaci sun shiga garden ita da mamie donsu tattauna
kan abunda ya shafi rayuwarsu da ta ƴa'ƴan su, ba ƙaramin ɗebe mata kewa take yi ba.

Haka Itama zeenatu bata da matsalar komai ayanzu, Benazir ta zama tamkar ƙawarta, har gyara mata gashi
takeyi tayi mata kwaliya, dr shureim ne yake daukarsu a motarshi su fita yawon shaƙatawa, kullum sai sun
fita yawo ko gajiya basayi. To meya fi ransu? Nima da zan samu mai fitar dani yawon binshi zanyi.

A 6angaren Pravin kuwa, Takaicin duniya Ya ishe shi, tun da yaji cewar baba obie ya amince yaran su cigaba
da zama a estate dinshi duk irin wahalar dayasha wurin ganin ya tunzurasu donsu ƙi amincewa da shi
amma abanza, baƙin ciki da hassada ne ke damun shi, Ranshi ya 6aci matuƙa ya kuma ci alwashin sai ya
raba alaƙar yaran da chief owais, burin shi kawai su bar estate din. Ko ita hajiya saratu a yanzu tadaina
damuwa da zancen yaran tun da taji hukuncin da baba obie ya yanke sai ta sanyama zuciyarta salama, idan
pravin yai yunƙurin tunzurata don taje ta tada maganar a wurin baba obie, sai tace mashi itafa yanzu bata
su take ba, tun da ba'a kanta suke zaune ba, Owais shi zai kula da komai.
Idan ta faɗi hakan sai yaji tamkar ya rufe ta da bugu.
Kullum tunaninshi ta wace hanya zai 6ullowa lamarin???

Alhamdulillah Jikin dr. Jazz yayi sauƙi, da taimakon ƴan uwanshi da suke bashi kulawa, har gida yake shiga
don ya gaishe da Baba Obie, sannan yaci gaba da zuwa gidan su khadeeja kamar yadda ya saba zuwa
domin duba lafiyarta.

Idan muka koma wurinsu Aneelerh, shiru har yau zahra tana zaman jiran sakon Hajiya saratu harta fara
tunanin kodai dama wasa take yi mata ne? Ko kuma tayi mistake ne wurin tura mata hotunansu twins don
ta za6i ɗaya? Tarasa ina zata tsoma ranta taji daɗi ta riga data ƙwallafa rai akan su twins shiyasa duk ta
damu kanta, kullum ne saita duba chat dinsu da hajiya saratu har tsakar dare duk don taga kota tura mata
amsar maganarta amma shiru kake ji har yau, ganin yadda ta ɗaga hankalintane yasa Aneelerh kwantar
mata da hankali tace taci gaba da addu'a idan rabonta ne zata samu, sannan tayi mata uziri watakil
tamantane ko kuma ta shiga busy a aiki shiyasa bata samu damar bata amsa ba,
Aneelerh Ba ta jima da fada mata hakan ba, Sai ga mahboob yazo masu da labarin tafiyar da sukayi zuwa
wasu states din nigeria, Jin hakan yasa taji sauƙi acikin zuciyarta.

Hajiya adama tun bayan da suka kawo baby junaid, kusan kullum saita kira donsu gaisa dashi har video call
suke yi, ta jima tana mamakin yadda junaid yake yi mata surutu idan ta kira shi awaya, amma lokacin da
aka kai masu shi kamar wani salihin bawa baya surutu sai in yana son cin wani abu tukunna yake buɗe baki
yace abashi, nan take ta fahimci yafi son zama wurin mommynsa, yanzu tasama ranta dangana bazata ƙara
raba shi da maman shi ba, idan tana son ganin shi ita za ta je gidan ko kuma ta gayyaci aneelerh tazo mata
da shi, yanzu haka Aneelerh ta fidda masu lokacin da zasu je gidan ita dasu mami da ummi hada su uncle
ɗan Iya gaba dayansu zasu je kai masu ziyara, tun da ta sanarma hajiya adama farin ciki kamar ta zuba
ruwa ƙasa tasha, taji dadin zancen zuwansu................

Atakaice kenan abubuwan da ke faruwa atsakanin family din kowani 6angare.

*💋BABE UNAISAH ANGEL❤*

fitowa tayi daga toilet, Jikinta asanye da bathrobe fara ƙal ta ɗaure igiyoyin rigar saitin waist din ta, fatar
jikin ta da alamun lemar ruwan wankan da tayo, A hankali take tafiya tana tunkarar Dressing Mirror, ta
wutsiyar ido take kallon Batool dake akwance saman gadon su, tana fuskantar ceilling tamkar maiyin bacci,
alhalin nan kuwa idonta biyu....

On mirror Chair Unaisah ta zauna, fuskarta babu annuri babu walwala, kamar bata da ƙoshin lafiya ko
wani abunne ke damunta wanda yayi silar canzawarta.

Body lotions din su ta ɗauko ta buɗe murfin, ta soma bin ko'ina na jikinta tana shafe shi da mai.

Bayan ta gama shafa man, ta feshe sako da lungu na jikinta da turare, ƙamshin shi ya buɗe room din, hatta
Batool sai da ƙamshin Ya ziyarci Hancinta.

Sumar kanta ta soma gyarawa, ta busar da ita tabi da smoothing serum ta cuccuɗata, tunkafin ta kammala
kunnuwanta suka Jiyo mata sautin knocking ƙofar room dinsu da ake Yi daga waje.

"Batool, nasan idonki biyu, je ki leƙa ki ga wanene ke yi mana knocking, may be ko aunty ummi ce,"

Fuskar Batool Ayamutse ta buɗe idanuwanta, ta sauko daga saman gadon tana miƙa haɗi da yin hamma
ta nufi ƙofar, ƴar rigar dake a jikinta bata wuce gwiwarta ba.

Buɗe ƙofar ɗakin tayi, tare da leƙawa ganin big guy ne yasa tayi saurin zuwa ta dauko Mayafi ta lullu6e
kanta kafin ta dawo bakin ƙofa ta kuma leƙawa tana fadin"Barka da safiya Ina kwana"

Kamar kullum da face mask a fuskarshi ya amsa mata da lafiyalou, yakike fatan na same ki lafiya' bayan
sun gama gaisawa yace"ina Jari "?

"Tana a ciki, Yanzu ta fito daga wanka, ko in kira maka ita"? Ɗaga mata gira yai alamar eh, juyawa tayi da
sauri ta shiga dakin, A lokacin Unaisah ta koma gaban Closet dinsu, tana laluban Suturar da zata sanya, Jin
motsin shigowar ta yasa ta juyo tana kallon Batool
"Wanene"?
"Big guy ne Yake son ganin ki"
"Ni kuma"? ta faɗa da alamun mamaki"ni nama yi tsammanin boss man ne, Ko me zai faɗa min bari dai
naje naji dame yazo"

Ta faɗa tare da ɗaukar Hijab ta zura ajikinta, Ta nufi ƙofar dakin cikin girmamawa ta gaishe da shi ya amsa
mata da fara'arsa
"Batool ta fada min kana nemana, gani toh" yadda tayi maganar taso ta bashi dariya.
"Kina wani abune"? Girgiza mashi kai tayi"a'a, ba abunda nake yi"
"Yawwa My baby Girl, Kin tuna maganar da muka ta6a yi dake last week"? Shiru tayi tana faman ƙyafta ido
a ƙoƙarinta nata tunano maganar da sukayi
"Namanta, ka tuna min mana"
Numfasa yai kafin yace"ba kince kinaso kiyi ma chief namu godiya ba game da alkhairin da yake yi ma ki"
murmushi tasaki tare da cewa na tuna.

"Good, Yanzu abun da nake so dake, Kinga ni ke ɗawainiyar kai mashi abinci har ma da gyara mashi room
din shi, saboda bai yarda da kowa ba Yana da wuyar sha'ani, Nima don ya aminta dani shiyasa ya yarda ina
masa aiki a part dinsa, abun da Yakamata Yanzu ke nakeso Ki cigaba da zuwa part dinsa kina yi masa
hidimar kai mashi abinci, breakfast lunch and dinner, sannan yana yawan shan coffee, a rana sau shida
nake kai mashi, gyaran daki kuma sau biyu ne safe da dare before ya kwanta bacci, sai kuma gyaran falo
dinsa da toilet dinsa da dressing room din shi hada gym room dinsa......" tunda yafara kora mata jawabi, ta
zaro mashi idanu waje tana kallon shi, ganin kamar ta ruɗene Yasa shi sassauta muryarshi yace"Ko ba ki Iya
aikin mata bane"? Murmushin yaƙe ta sakar mashi tare da cewa"Na Iya, amma naji kace Yana da wuyar
sha'ani kuma bai yarda da mutane, Tayaya zai yarda Ina zuwa part dinsa yi mashi aiki"? Ta jefa mashi
tambayar tana duban shi.

"Kada ki damu, zai yarda da ke, abun da yasa kika ga Na baki wannan aikin saboda ta hanyar kyautata
mashi ne kaɗai zaki Iya biyanshi da ɗawainiyar da yake yi maku, tun da shi ba'ayi mashi godiya baiso,"

Jinjina kai tayi kamar tana fahimtarshi,


"Shikenan, Yaushe zan fara zuwa yi mashi aikin"?
Murmushi yasaki jin ta amince fatan shi Allah yasa Chief Ya yarda da ita.
"Yanzun nan zaki fara aikin, Gyara mashi Room dinsa, baya aciki daga sallar asuba ya nufi gidan kakansu
Obie, kafin Ya dawo please ki tabbatar kin gyara mashi ko'ina na part dinsa, before ki gama ni kuma zan
kawo maki breakfast din shi, duk idan nakai mashi abinci sai na tsaya nayi serving nashi kema haka za ki yi,
nasan kina da natsuwa chief baison mutun mai ƙazanta yana son mai tsafta, kullum ki tsaftace jikinki da
suturar ki kafin ki shiga part dinsa.... " wani kallon take bin da shi a fakaice.

"Baka da matsala dani, In sha Allah zanyi komai yadda ya dace,"


Har cikin ranshi yaji daɗin maganar data furta mashi,
"Mu je in nuna maki ɗakin" da sauri tace"Ai ban gama shiryawa ba, ka bani mintuna yanzu zan dawo"
amsa mata yayi da toh, da sauri ta koma ɗakin a lokacin batool ta shige bathroom tana wanka.
Shaf shaf ta nufi glass wardrobe dinsu, ta shirya kanta cikin Turkish gown launin Yellow, rigar tayi mata
kyau ta kuma bi shape din jikinta, tana da belt a tsakiyar ta, tayi rolling mayafi akanta, kafin ta ɗauko
Cashmere slippers mai gashi gashi launin yellow ta zura a ƙafarta.

Bayan ta kammala kimtsawa, Ta fito daga ɗakin, Shi kanshi Big guy daya kalle ta sai da gabanshi Ya faɗi
ganin kyan da tayi, satar kallonta ya dinga yi batare data ankara ba.

Tafiya suka soma Yi, tana abiye da bayanshi, tayi tsammanin upstairs zasu hau amma sai taga Ya nufi
elevator, Zaro idanu tayi ganin inda zasu shiga, tunda take arayuwarta bata ta6a hawa elevator ba sai yau,
wani irin daɗi take ji, musamman da suka shiga daga ciki, tayi sama da su A hankali ta sauke su a second
floor, kofar ta zuge, fitowa yai daga ciki da sauri tabi bayanshi, abakin kofar ɗakin nan data ta6a zuwa
kwanaki taga wani mutun Yana motsa jiki nan yakaita nan take ta gane cewa shine ɗakin kuma mutumin
da tagani shine chief dinsu.

Abakin door room din suka dakata da yin tafiyar,


"Ƙofar tana da password, ba zaki Iya shiga ciki ba tare da kin sanya password din taba, sai kuma idan shine
ya baki iznin shiga" ɗaga mashi kai tayi alamar toh.
"Amma yanzu babu security din ƙofar zaki iya shiga, sai dai ki kula please banda 6arna" dariya tayi tana
fadin"6arna kuma sai kace wata ƙaramar Yarinyar"
"Nasan ki da ƙiriniya, shiyasa na faɗi hakan"
Yamutsa mashi fuska tayi batare da tace komai ba, Ya buɗe mata ɗakin Yace ta shiga ta fara aikin idan ta
kammala yana s falo Yana jiran ta" amsa mashi tayi da toh, sai da taga Ya bar part din tukunna tayi sallama
ta shiga daga ciki.
Kamar yau ta fara ganin dakin, dama time din farko data fara shiga bata samu damar ƙare mashi kallo ba,
har mamaki takeyi idan ta tuna mai rai ne ke rayuwa a dakin, Kamar baza'a mutu ba, komai ka kalla mai
tsadane da inganci furniture din dakin har daukar ido suke yi idan ka kalle su, tsabar haɗuwarsu.
Ga wani sanyin A.c mai haɗe da ƙamshin room freshner har cikin hancinta take shaƙar shi.

A ƙalla ta 6ata tsawon mintuna, kafin ta soma tambayar kanta, meya kawo ta dakin? Don ita bata ga abun
da zata gyaraba, babu datti ko kaɗan komai a gyare yake kamar yau aka fara amfani da ɗakin, har ƙwara
bedsheet dinsa Ya tattare alamar anyi amfani da shi.

Ɗaura idanunta tayi akan Toilet dinsa, daga inda take tana kallon komai dake aciki ta jikin glass din bangon
, atsaftace yake komai na cikinsa fari ne ƙal.

Ruƙe qugu tayi da hannu aranta tana fadin"Ikon Allah, To ni meye amfanin zuwana part dinsa? Me ake so
nayi! Bayan babu wani abu da zan gyara, ni wannan dakin ma in nawane ai say yayi sati kafin in gyara shi"

Ta jima atsaye ba tare da ta ta6uka komai ba, tunawa da big guy dake jiranta a falo, ne yasa tayi saurin
nufar gadon chief, Ta soma gyara shi, bayan ta gama ta koma tana jera mashi turarurrukansa da body
lotions dinsa da yayi amfani da su da safe, cikin ƙanƙanin lokaci ta gama gyara ko'ina na part dinsa..

Fitowa tayi daga part dinsa ta sauko down, Babu kowa A falon, Ƴan uwanta duka suna a bedrooms dinsu.

"Kin gama gyaran"? a hanzarce Ta juya Baya jin muryarsa, Big guy ne ya nufe ta hannun shi ruƙe da
haɗaɗden wooden tray madaidaici daga saman lafiyayyan breakfast ne.
"Na gama,"
"Madallah sannu da ƙoƙari" tace mashi yawwa,
"Yanzu ki biyo bayana muje dakin, inaso na gwada maki yadda za ki yi serving din shi abincin" amsa mashi
tayi da toh,
Sai da ya fara tafiya tukunna tabi bayanshi, har suka haura second floor, bayan sun shiga ɗakin ya ɗaura
tray din kan wani ƙayataccen table, kafin ya dube ta yana fadin"kin yi ƙoƙari Jari, haka kika Iya gyaran
ɗaki"? Murmushi tasaki jin ya yabe ta, aranta tace dama can a gyare yake.
Batare da 6ata lokaci ba, ya soma kwatanta mata yadda zata gaishe da chief da kuma yadda zata tambaye
shi me yake buƙata ta zuba mashi, hada yadda zata zuba mashi abincin duk sai da ya koya mata, ya yaba da
hankalin ta shiyasa bai kawo ma ranshi cewa zata yi mashi kwa6a ba.

"Zan tafi Jari, please Kada ki bani kunya, Kiyi komai awanyance, Inaso Chief ɗinmu Ya yaba dake" ya faɗa
yana kallonta,
"In sha Allah, zanyi ƙoƙari"
"Good Girl"
Juyawa yayi da sauri Ya nufi ƙofar fucewa daga falon, tsaye tayi tana yanke shawara da zuciyarta.
Maimakon tayi abunda yace mata, sai ta Fito cikin sanɗa kamar 6arauniya tana ƴan waige waige ganin
babu big guy ne yasa ta saki jiki, da sauri ta sauko down stairs ta nufi bedroom ɗin su, tunkafin ta shiga ta
soma kwalawa Batool kira.

Batool dake a zaune kan mirror chair, har tayi wanka ta sanya Pakistan ajikinta, Riga da wando, launin
blue sky, ta sauko da sumar kanta har tsakiyar bayanta masha Allah.

Jin kiran da Unaisah take ƙwala matane yasa tayi saurin miƙewa tare da juyawa tana kallonta da mamakin
ganin yadda take haƙi
"Lafiya"?
"Toilet zan shiga sister, uziri gare ni, gashi big guy ya sanya ni yin aiki a part din Chief dinsu, Dan Allah ki
taimaka ke ki yi aikin" tana magana haɗi da dafe cikinta.

Adabarbarce Batool tace"to ai ni bansan dakin shi ba, sai dai ki nuna min"

"Muje in nuna maki" ta faɗi tare da yin saurin zuwa gaban closet din kayansu ta ɗauko mata mayafin
pakistan dinta, sai da tayi mata rolling din shi tukunna ta Ruƙo Hannunta.

Gaba tayi Batool tabi bayanta suka shiga elevator, su batool basa banbana sai bin elevator din take Yi da
kallo
"Sister menene wannan?
"Sunanta Elevator, Na'ura ce dake ɗaukar mutun daga sama takai shi ƙasa ko daga ƙasa takai shi sama, tafi
sauƙi akan bene, Kin ga shi yana gajiyar da mutun amma ita wannan tsaye kawai zakiyi tayi sama dake, bari
na gwada maki yadda zakiyi amfani da buttons dinta, Nima a wurin big guy na gani da muka shiga atare" A
tsanake tayi mata bayanin yadda zata Yi amfani da ita.

Murmushi Batool tasaki"meyasa baki ta6a nuna min ba? Ai da bazan ƙara hawa bene ba, duk in zanje
dakin aunty ummi kona Danish, sai dai in hau elevator"
Unaisah tace"indai wannan ce har sai kin gaji da ita, don daga yau kece zaki dinga zuwa gyara ma chief
dakinsa sannan ki kai mashi abinci"

A matuƙar ruɗe Batool ta furta"Ni kuma"? Ta faɗa tana zare idanuwanta.

"Ƙwarai kuwa, big guy yace ta wannan hanyarce kadai zamu Iya biyanshi abunda yayi mana, wato mu
dinga kyautata mashi..... " cikin kwantar da murya tayi ma batool bayani.

Fuskar Batool da fara'a tace"indai wannan ne babu damuwa, zan dinga kai mashi abincin in gyara mashi
ɗaki kullum in sha Allah"

Murmushin gefen fuska Unaisah ta saki, Aranta taji daɗin amincewar da Batool tayi, Dama da biyu tayi
hakan, saboda batason tana kusanta kanta da wani Namiji, ta san halin mutuminta sarai, duk ranar da
Allah ya farfaɗo da shi ya risƙeta a ɗakin chief tabbas komai zai Iya faruwa.

Fitowa su ka yi daga elevator din, A bakin ƙofar ɗakin nashi, Unaisah ta sanya hannu ta buɗe, suka shiga
daga ciki, tun da Batool ta daura idanuwanta akan haɗuwar ɗakin nan fa tabi ta ruɗe ta rikice kamar
wuyanta zai balle saboda yadda take ƴan leƙe leƙe, tambayoyin tadinga jefa ma unaisah menene wannan?
Ya ake amfani da shi.

"Kinga kiyi abunda ya kawo ki, a sannu zanyi maki bayanin komai, Yanzu dai zan tafi in barki, ai na fada
maki toilet zan shiga, ki natsu ki saurare ni kada ki yi mashi kwa6a, mutunne mai son mace mai tsafta da
natsuwa, nasan duk kina da wannan, dan Allah kada ki bani kunya my sister,"
"In sha Allah"
"Yawwa My baby Girl, Idan chief din Ya shigo cikin girmamawa zaki gaishe da shi, kina ji na ko"? Ɗaga mata
kai tayi alamar eh, taci gaba da koya mata komai dangane da yarda zata yi serving din shi.

Daga bisani tace"toh, Sister ni zan tafi, ki yi zamanki ki sha A.c kafin chief Ya ƙaraso" tana fadin hakan tayi
saurin fuce wa daga dakin.

Batool ta samu abun kallo, haka ta dinga ƴan leƙe leƙe tana yi mashi yawo a ɗakin shi.

Bayan Unaisah ta sauko down stairs bedroom dinsu ta koma, fuskarta ɗauke da murmushi, har ta ƙagara
Batool ta kammala aikin ta dawo don taji meye faru bayan chief Ya shiga ɗakin? Abu ɗaya take zullumi
kada Batool tayi mashi kwa6a.

Tunani ta soma yi mai yakamata tayi yanzu? Ɗazu dai da asuba sunyi karatun alƙur'anin da ake koya masu
da wasu littattafan addini, sannan sunyi breakfast dinsu, shiyasa sauran duk basu fito daga ɗakin su ba,
saboda baccin da bai ishe su ba.

Lokaci ɗaya ta tuna da i phone ɗinta, Jiki na rawa ta nufi bedroom din su, tana shiga ta nufi inda ta ajiye
ta, ta ɗauko wayar tare da backpack ɗin Unaiza.

Saman gadonsu ta haye, ta sanya hannu ta zuge zip din jakar ta soma ƙoƙarin lalubo sim din, sam ta
manta inda boss man ya sanya mata shi, ranta ne ya bata cewar ta bincika littattafan dake abackpack din
wata'ƙil a tsakiyarsu ya zura sim din.

Nan take ta zazzago da Textbooks din Ciki, tare da Diary din Unaiza, buɗe su ta dinga yi tana neman sim
din har tazo kan Diary din Shafin farko data buɗe hoton Unaizah ne, Lokaci ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi
ganin fuskarta, tayi kyau a hoton kamar ka kira sunanta ta amsa maka.

Tunda ta ƙurama hoton ido ko ƙyaftawa batayi ba, A hankali ta daura hannu tana shafa fuskarta, yayin da
idanuwanta su ka cicciko tab da ƙwalla.
Taso ace zata Iya karanta labarinta data rubuta a diary din sai dai raunin zuciyarta bazai barta ta Iya
karantawa ba, A hankali Ta furta"I love You so much our lovely sister, Allah yaji ƙanki"

Tana ƙoƙarin rufe diary ɗin, Ba zato ba tsammani, Sajeed Ya faɗo dakin sam babu sutura a jikin shi sai ɗan
gajeran wando, sumar kanshi ta yamutse kamar yadda fuskarshi take a yamutse babu annuri babu walwala
ko sallama baiyi mata ba, Ita kanta data kalle shi sai da gabanta ya faɗi ganin yadda ya faɗo mata ɗaki da
short.

Muryarta na rawa ta furta"Sa... jeeed!? Lafiya ka shigo min daki babu sallama meke damunka!? ta jefa
mashi tambayar tana kallon shi, babu alamun zai amsa mata har saida ya haye kan gadonta Ya zauna Yana
fuskantar ta, la66ansa Na rawa Ya furta" I had a dream..." Ya faɗa yana ƙoƙarin tattara natsuwarshi
A matuƙar ƙagare tace"Wani irin Mafarki kayi ne daya rikitar dakai haka"
Ruƙo hannunta yayi acikin nashi ya matsa shi kafin cikin sanyin murya ya furta.

"TWIN SISTER ƊINA!!" Rass Taji gabanta yayi mugun faɗuwa tunkafin ma taji ƙarashen zancen.

"Sister tun bayan da muka baro prison muka tsinci kanmu a Daji, kafin Allah ya kawo mana ɗauki muka
bar dajin Zuwa america, ban ta6a yin mafarki da ita ba, tamkar ma namanta da itane don ko tunaninta
bana yi, amma Yau bayan mun kammala Yin breakfast, dama bacci bai isheni ba, na koma ɗakin na kwanta
cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awon gaba da ni, kwatsam nayi mummunan mafarkin duk da kin ta6a
fadamin babu kyau mutun yayi bad dream ya faɗa ma wani amma wannan mafarkin kamar wani tuni ne
da Allah yake yi min akan Ƴar uwata da kuma sauran yaran da ake azabtar da rayuwarsu a gidan kurkukun
ƙaddara....... " a yayin da yake yin maganar hawaye tuni sun wanke fuskarshi, Jikin unaisah sai tsume yake
yi
"Ina sauraronka, ka faɗamin me ka gani a cikin mafarkin naka"?

"Naga abun da ya fi ƙarfin idanuwana, saboda bala'e kukan da nikeyi acikin mafarkin har a zahiri sautin shi
yake fita batare da sanina ba, har sai da naufal ya farkar dani daga baccin ya ke faɗa min.... " shiru ya ɗanyi
na wani lokaci suna kallon juna idanunsu azazzare yayin da bugun zuciyarsu ke hauhawa.

"A Cikin mafarkin da nayi, naga sister dina GABRIELLA, tare da wasu Yara sanye cikin jajayen uniform kalar
namu, ko'ina na jikinsu Jiƙe Yake da Jini, Hannayensu da ƙafafuwansu a daure suke da igiyoyi, hatta
bakunansu an toshe su da jan ƙyalle, na dinga ihu ina kiran sunanta, bata iya yi min magana sai dai
hawayen jinin da ke fita acikin idanuwanta.... Sister bansan ya zanyi ba, Ni da farko na fidda rai da ita
amma a yanzu inason ganinta inason nasan awani hali take aciki, tana araye kota mutu? Duk da bana
kawowa raina cewa bata arai.... " daƙyar Ya ƙare maganar wani irin kukane yaci ƙarfinsa, da sauri ya kifa
kanshi saman kafaɗar Unaisah, Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, ta rasa gane meyasa har yanzu ba su yi
wani yunƙuri na ruguza kurkukun ƙaddara ba, tabbas sunyi ganganci saboda kowani ɗaƙiƙa ɗaya da suka
6ata barazana ce arayuwar sauran yaran dake a Prison.
A hankali ta daura hannunta saman bayanshi, Cikin sanyin murya tace"bansan ma me zance ba, ni kaina na
girgiza da jin mafarkin da kayi, amma abin da nakeso in tuna maka mafarki ba gaskiya bane, ba lallai bane
abunda ka gani ya zamana gaskiya, zaiyi wuya... " lallashin shi taci gaba dayi, Jikinshi duk ya saki babu
kuzari kamar wanda yayi ciwo, hada zazza6i ke kokarin kama shi.

ɗago da kanshi tayi daga kan kafaɗarta ta talla6o fuskarshi da hannayenta biyu, dakyar yake iya buɗe
runannun idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur da su.

"Dan Allah, ka daina kuka, bana son ganin ɗan uwana a wani hali na damuwa, bana jin daɗi"

Muryarshi na rawa yace"sister, ba zaki gane ba ni kadai nasan abunda nake ji, wannan mafarkin ina jin shi
dagaske ba wasa ba, ni dai kawai ki shirya mana abunda ya kamata muyi"

Shiru tayi tana tunani aranta na tsawon mintuna batare da ta kau da idonta daga nashi ba tace"Sajeed, ka
kwantar da hankalinka, In sha Allah komai yakusa zuwa ƙarshe, Yunƙurin da zamuyi zai zamanto TAKUN
ƘARSHE a tafiyar mu, A yanzu ba za mu Iya yin komai ba in har Danish bai samu Lafiya ba, Shine jagoranmu
kuma garkuwarmu, su kansu mutanan dake kula damu burinsu Danish Ya farfaɗo daga muguwar kasalar da
yake fama da ita...."
"Har yanzu bangane me kike nufi ba, shin mu ba zamu Iya tona masu asiri bane? Sai Danish"?

"Wani asiri Zamu Tona masu? Bayan sun riga da sunsan komai dangane da rayuwarmu!!" A firgice Sajeed
Yake dubanta da alamun mamaki Ya furta"ke kika faɗa masu"?

Girgiza mashi kai tayi"a'a bani na faɗa masu ba, amma ina da tabbacin sunsan komai, kuma akwai shirin
da suke Yi shiyasa suke buƙatar Danish.

Fuskarshi da alamun ruɗanin kalamanta yake kallonta.

Fahimtar hakan yasa tace mashi zan yi maka bayanin komai, Amma Ba yanzu ba, Ni dai burina ka kwantar
da hankalinka, Sister dinmu kuma zamu cigaba dayi mata addu'a, Har zuwa lokacin da zamu ɗauko ta"
Kwantar mashi da hankali taci gaba dayi har saida taga Ya samu nutsuwa tukunna tace

"Ka ta shi ka shiga toilet ka wanko fuskarka duk ta 6aci da hawaye" in a cool voice Ya amsa mata da toh, Ya
sauko daga kan gadon Ya nufi toilet din ɗakin su Ya shiga ciki.

Har saida taga Ya maida ƙofa Ya rufe sannan Ta kau da idonta, cigaba da neman sim din tayi, sai da ta
tarwatsa littattafan A ƙarshe ta gano shi cikin ƙaramin aljihun backpack din, Ajiyar zuciya ta sauke, kafin Ta
dauki wayar ta sanya sim din, power button ta danna nan take screen din wayar yayi haske.
Contact ta shiga anan taga phone numbers waɗanda dr laura ta yi mata saving akan waya, Murmushi
tasaki tana tunanin wani time yakamata ta kirata awaya su gaisa"? Kafin Ta yanke shawara, Sajeed Ya fito
daga Toilet fuskarshi da lemar ruwa ya nufe ta idanunsa akan wayar hannunta, tun kafin yayi magana ta
dago da wayar tana nuna mashi tace"Ka tuna wannan wayar"? fuskarshi babu walwala yace"Na tuna, Itace
Dr Laura ta america ta baki ko" daga mashi kai tayi"ina fata kanka baiyi maka ciwo"?

Cikin kulawa tayi mashi maganar, zama yayi daga gefen gadon kafin yace"yana yi min amma da sauƙi,"
"Ko in kar6o maka magani"? Girgiza mata kai yayi alamar a'a"basai nasha ba zanji sauƙi in sha Allah"

Diary din dake ajiye gefenta yakai hannu ya ɗauka, har zai buɗe shi tayi saurin fisge shi, Tamkar walkiya
wasu hotuna guda biyu ƙananu suka faɗo daga cikin diary din babu wanda Ya lura da su a tsakaninsu har
hotunan suka sulale kan floor.

"Bazan bari ka bude shi ba, saboda Zai Iya fama maka raunin dake a zuciyarka," ta faɗa tare da tattara
textbooks din da sauran kayan da ta fiddo daga jakar ta mayar da su ciki.
Miƙa mata hannu yayi"tun da kin hanani ganin diary din, Bani wayar Hannunki," babu musu ta miƙa
mashi.
Danna danne ya soma yi duk tana kallon shi.

"Unaisah, kinsan wani abu"? Da sauri tace A'a

"Ina ji araina na ta6a ruƙe waya, Kalar wannan, Kamar Mommyna ne ta siya mana nida twin sister dina"

Waro Idanu waje tayi jin abunda yace, Da mamaki tace"Sajeed, Zaka Iya tuna wani abu dangane da
rayuwarka? Naji kana fadin ka ta6a ruƙe waya kalar wannan mai tsada"?

Jinjina mata kai yayi"bakomai zan Iya tunawa ba, Yanzu ne naji abun Yanayi min yawo akaina, Amma
tabbas nima na ta6a mallakar I phone nawa nakaina hada Laptop, Sannan mahaifiyarmu Farace
daddynmu kuma kalar skin dinmu gare shi chocolate colour......" tunda yafara magana Take binshi da kallon
mamaki da al'ajabin ta yadda akai har ya fara tuna wani abu dangane da rayuwarshi, bayan ta ta6a
tambayar shi a lokacin suna a prison yace mata bazai iya tunawa ba, wata'kil Allah ne Ya nufa sihirin da
matsafan suka yi mashi zai warware shiyasa yafara tunanowa, Hankalin shi na akan wayarta yaci gaba
cewa"muna kama da daddynmu Ni da sister ɗina, Idan bazan manta ba, Mahaifin mu Attajirin mai
kuɗine... " muryarta a ruɗe tace"Zaka Iya Tuna sunan shi? Ko sunan Mommyn ku? Da sunan Country din da
kuke rayuwa? A ƙagare ta furta maganar.

Shiru ya danyi, Yana kallon Screen din wayarta da yake daddanawa.

"Bansan asalin sunan shi ba, amma kamar yana da nick name da ake kiran shi da shi, Ni kamar Big Boss
Ne Namanta, mommyn mu kuma sunanta umm......" duk yadda yaso ya tuna sunanta ya kasa.

Cike da zumuɗi ta dafe kafadarshi"bro, Kayi ƙoƙari ka tuna dan Allah, Koda bayanzu ba, waɗannan
bayanan da su zamuyi amfani wurin gano su wanene Azzaluman da suka sadaukar da mu" Jinjina mata kai
yayi"zanyi ƙoƙari na tuna, amma ko Yanzu naga daddyna wallahi zan gane shi saboda kamanninmu sun 6aci
da shi Yana da Kyau, hatta ƙirar jikina kalar nashi ne da sumar kaina, bani da banbanci da shi sai dai na
girman jiki da shekaru"

Ɗaga hannayenta sama tayi"Ya Allah Ka bayyana mana bayin Allah nan, Da mahaifin Unaizah Jan wuya, da
dukkan waɗanda suka sadaukar da mu, wallahi muna kwaɗayin Ganin su ko don mu tarwatsa zukatansu"
addu'o'i ta dinga yi yana amsa mata da ameen.
"Da ace zan Iya tuna Phone number din mommyna da mun jaraba kiranta, saboda na ta6a haddace
layukan wayarta dana Daddyna amma nasan zaiyi wuya mu same su.

Cikin sanyin Murya Ya ƙare maganar,


Unaisah tace"Sajeed, koda ka tuna layin wayarta wallahi ba lallai tana amfani da shi ba, tun da mugayene
babu Allah aransu, kamar yadda Iyayen Unaizah suka hana tasan komai nasu, kuma zai Iya kasancewa
Hakane"

"Kin faɗi gaskiya, amma duk da haka zan jaraba rubutawa mu gani," ya fada tare da daddana wayar Ya
rubuta number dayake tunanin ta mommynsa ce, duk suka ƙura ido suna jiran ganin in zata shiga, Muryar
na'ura ce ta sanar da su cewa Number da suke kokarin kira badaidai take ba, dafe kai yai da hannu
ɗaya"nayi mistake sister bazan iya tuna ainihin yanda number din yake ba" fuskarshi yamutse yayi
maganar.

Ganin Yana rubuta wata number ne yasa tace mashi"wannan fa"?


"Layin wayatane zan kira" natsuwa sukayi suna jiran jin in zai shiga, Har saida gabansu Ya faɗi Jin Wayar
Na yin ringing, duk da basu da tabbacin Idan Number dai dai Ya sanyata, kallon juna su ka yi da alamun
mamaki, Har kiran ya katse ba'a ɗaga shi ba, Suka sake kira nan ma ba'a yi picking ba....

"Mu bari zuwa Anjima sai Mu ƙara Kira, Allah yasa layin dai dai muka Kira," acewar Unaisah
Sajeed Ya amsa mata da ameen.

*❤MOM SARAH🤍*

Su biyu ne zaune Asaman wasu Hadaddun kujerun shaƙatawa dake a bakin Swimming pool Area na gidan,
Daga tsakiyar su table ne mai ɗauke da Mugs guda Biyu na coffee suna sha suna fira, Hajiya Layla ta sanya
arab gown ta yafa mayafi akanta, yayin da ita kuma Hajiya Sara ta dauki wankan kimono robe, babu mayafi
akanta zallar gashin kanta ne ta saki har saman gadon bayanta launin Ja.

"Har yau ina mamakin Yadda Kike rayuwa da Mijin ki, mutun babu fara'a babu annuri, gaskiya Ina jinjina
maki" Hajiya layla ce tayi maganar.

Murmushi hajiya sara tayi"bana damuwa da hakan, Saboda nature din shi ne, Sai ka Iya zama da shi zaka
gane wanene shi, Yana da sauƙin kai, fiye da tunaninki" ta6e baki Hajiya laila tayi"ahakan"? Jinjina mata kai
tayi"ƙwarai kuwa, saboda Yana kyautata min, kuma yana nuna min so, tun lokacin dana aure shi bai ta6a
canza min ba, nasan yana da wuyar sha'ani sai dai ba kamar yadda kika zata ba, ban ta6a neman abu a
wurin shi na rasa ba, ko baida shi zaiyi min ne balle ma Yana da shi din, Baya son 6acin raina, Sannan yana
bani kulawa, wani lokacin idan muna atare sai in dinga jin kamar ma bamu daɗe da yin aure ba saboda
yadda yake tarairata...."

tun da hajiya sarah tafara kora ma hajiya layla bayani take ta faman yamutsa fuska, ba haka taso taji daga
gare ta ba, tun ɗazu take ƙoƙarin bugun cikinta don taji ya take haƙurin zama da Alhaji musa sai dai wani
abu data fahinta dangane da Hajiya sarah irin matan nan ne masu shegen wayau, ba su bari aji sirrin mijin
su, baka ta6a jin aibun mijinta abakinta sai dai Alkhairinsa.

Mug din coffee ta dauka ta kur6a zuciyarta ajagule, bayan ta ajiye mug din tace"amma a ganinki
abunda Alhaji musa yake yima Mijina ya dace? A matsayin shi na yayanshi ya dinga juyashi son ranshi"?

Girgiza kai Hajiya sarah tayi"Ni kaina ban goyi bayan hakan ba, ko lokacin da ya bashi umarnin yazo daku
joss sai da nayi kokarin dakatar dashi sai yace min indaina sanya mashi baki akan abin da ya shafi
danginshi, gaskiya banji daɗi ba, amma abunda ke ɗaure min kai, meyasa shi Alhaji ubaid ɗin Yake yi mashi
biyayya? Bayan shine ke babba"?
Ɗaure fuska Hajiya layla tayi tamkar bazata tanka mata ba tace"may be ko dan arziƙin Shi bai kai na musan
ba shiyasa yake liƙe ma shi, kinsan idan mutun nada arziƙi ko shine ƙarami agida babba yake komawa"
"Bana tunanin haka, amma dan Allah ki yi haƙuri da halin mijina" ta faɗi hakanne don ta fahimci ran
Hajiya layla a6ace yake da abunda Alhaji musa yayi masu.
"Bazan 6oye maki ba, ina jin haushin Yadda Mijinki Yake juya mijina, wannan ba ɗabi'ar arziki bace, Yana
da girman kai da izza, nazo gidan nan ne bada son raina ba, Alhaji Ubaid shine Ya takura min akan muzo, da
wallahi ko ƙeyata bazaku gani ba" a fusace ta faɗa tana haɗe rai, jin wannan maganar yasa Hajiya sarah ta
sassauta muryarta"Allah Ya Huci zuciyarki, nasan bai kyautaba.... " Kwa6e fuska Layla tai batare da ta
kuma cewa komai ba.

"Na lura kamar ranki Ya 6aci" acewar Sarah,


Murmushin yaƙe Layla tasakar mata"komai ya wuce ai, Tun da na faɗi ta cikina, kinsan ni ban iya 6oye
damuwata ba"
Martananin murmushin sarah tayi mata, tsawon mintuna babu wanda ya ƙara yin magana acikinsu sai dai
su kalli juna suyi murmushi.
Sai daga bisani Layla tace"Inataso in tambayeki Omar Ɗin mu tsawon lokaci ban sanya shi a idanuwana
ba"
Hajiya sarah tace"Ni kaina bansan meya ruƙe shi A america ba, baya son zama nigeria saboda daddyn shi
da basa jituwa, Amma yana kokarin kirana awaya wannan karanne ma ya dau lokaci nima kona kira shi
bana samun shi, sai idan shine Ya tuntu6e ni"

Har layla ta buɗe baki zatayi magana Ta hango Zeenatu dake tunkarosu sai sauri take Yi, Riga da wandon
jean ne a jikinta, Kanta babu mayafi, Yau ne karo na farko Da hajiya layla tafara ganin zeenatu tana yawo
babu mayafi a jikinta.

"Dama zeenatu tana yawo babu hijab ba mayafi a jikinta" jin haka yasa sarah ta dubi inda hajiya layla take
kallo ita kanta mamakine Ya kamata.

"Sai dai idan wani abunne Yaja hankalinta har ta manta bata sanya mayafin ba"

Sai faman sakar masu murmushi take yi, Cikin girmamawa ta gaishe da su atare suka amsa mata.

Mom sara tace"daughter Kin dubi jikin ki kafin ki fito daga ɗaki"? da sauri takai hannu ta shafa kanta taji
babu mayafi, duk tabi ta ruɗe tana faman zazzare idanu, kunyar duniya ta kamata.
"Mom, wlh bansan babu mayafi ba, ashe haka na fito, namanta da hijab din saman gado, Bari na koma in
dauko"
Gaba ɗaya suka sanya dariya
Layla tace"Ki kwantar da hankalin ki, ai ba wani abu bane don kinyi yawo a cikin gidanku babu mayafi,
amma dai yakamata kina kulawa tunda kin girma" ta fada tana kallon kirjinta da suke aciki kamar zasu fasa
rigar, dukar dakai ƙasa zeenatu tayi wani irin kunyarsu take ji
"Bari na koma in dauko mayafin"
Har zata juya Mom sara tace"ke zonan" da sauri ta dubeta, Da ido hajiya sarah ta nuna mata wayar
hannunta"me kike yi da ita"?
"Oh namanta, Ita na kawo maki, Ana kirana da baƙuwar number a lokacin ina a toilet, ban samu damar
yin picking ba shine na kawo maki ki duba mai kiranki"
A ruɗe Sarah tace"kamar ya ana kirana? Wayar wacece"?
"Tawa ce"
"Sai kuma kice ni ake kira"!
"Mommy ai ni bana amfani da ita, tun da na kar6eta a hannun ki nace maki zan ba yaya shureim ya tura
min hutunan su to su kadai nake kallo, ni banma lura da sim awayar ba"
Miƙa mata hannu sarah tayi"bani wayar" bayan ta kar6a ta soma bincika layin dake akan wayar don ita
kanta batasan akwai sim ba, sai yanzu da zeenatu take fada mata.

"Layin Mtn ne akan wayar, amma wannan number da aka kira ki da ita bansan wanene ba, ki koma ciki,
Idan na shigo zan duba mai kiran naki"

Amsawa tayi da toh, da sauri ta juya ta nufi cikin gidan cike da fargaban kada Yaya shureim yaganta da
ƙananun kaya.

Har saida ta 6ace ma ganinsu tukunna suka kau da idanunsu daga kallonta.
"Zeenatu tana burgeni, Idan ina kallonta sai in runka tunawa da Yarinyar Benazir"
Sarah dake kallonta tace"yarinyar da baki damu da ita ba? A yadda naji labari baki ta6a ganinta ba saboda
baki zumunci dasu"
"Hakane, Amma ayanzu da zan ganta babu abun zai hana in rungumeta, saboda nayi danasanin watsin
danayi dasu"
Sarah tace"kinyi babban kuskure, Baki kyautaba, Sai kace ba jininki ba, Ai ni da jikatace wallahi koda ban
son mahaifinta saina ƙaunace ta, laifin wani baya shafar wani"

Shiru Layla tayi batare da ta sake cewa komai ba, Ita kadai tasan takaicin da take ji duk idan ta tuna yadda
taƙi Tajuddeen da Yarinyar shi......

Bayan zeenatu ta shiga gidan, Cikin sanɗa take tafiya gudun kada Dr shureim Yaganta ahaka, babu kowa
hanyar data biyo sai lalla6awa take yi kamar wata 6arauniya, adai dai lokacin dr shureim ya fito daga
bedroom din shi sanye da jallabiya, Babu rawanin larabawan da yake naɗawa akanshi zallar sumar
kanshice har saman wuyanshi ta nannaɗe gwanin ban sha'awa.

Tunda yayi tozali da bayanta Ya ƙura mata ido yana kallonta, kwata kwata ranshi bai bashi cewar zeenatu
ce ba, saboda bai ta6a ganinta da ƙananun kaya a jikinta ba, sun matseta duk da bata da ƙiba kayan sun
mata kyau.
Da sauri Yabi bayanta Kamar yadda take Yin tafiya cikin sanɗa shima haka Yabita da sanɗar har cimmata,
"Zeenatu"! Kaitsaye kiran ya daki kunnata, A firgice ta juyo idanuwanta azare take kallon shi, wata irin
zabura tayi da niyar ta watsa da gudu sai dai kafin tayi hakan yayi sauri ruƙo waist ɗinta ya dawo da ita jikin
bango, Ya dafe da hannu ɗaya yana binta da kallon mamaki.
Da sauri ta daddafe kirjinta da hannu biyu don kada yagan mata abunta, ta kasa jurar hada ido da shi,
Kunyar shi duk ta kamata, Juya mashi baya tayi tana fuskantar Bango, muryarta da shagwa6a ta furta"ni fa
bansan babu mayafi na fito ba,"
Koda tayi maganar hankalinshi na akan bayanta data juya mashi, sumar kanta yabi da kallo, ƙamshin
turarenta sai shigar mashi hanci yake yi
Jin yayi shiru bai tanka mata bane yasa ta juyo don ganin me yake yi, karaf suka haɗa ido cikin na juna,
kallon juna suka cigaba dayi kamar zasu haɗiye kawunansu tsabar so da ƙauna, Bai ta6a yi mata kyau irin
na yau ba saboda sumar kanshi daya bari babu Arab turban dinsa, haka shima tayi mashi kyau yau daya
ganta da ƙananun kaya.

daƙyar Ya iya tattara natsuwarshi Ya furta"Kin yi min kyau" murmushi tasaki tana faman ƙyafƙyafta mashi
blue eyes din ta.
Ɗaura hannun shi yayi saman sumar kanta, lallausar gaske Ya shafata a hankali har wani lumshe mashi ido
take Yi
Can ƙasan maƙoshi ya furta"na fara tunanin yi ma Uncle maganar auran mu saboda naƙosa na mallake ki,
ko dan ki haifa min fatima" shi kanshi baisan ya furta hakan ba, gaba daya yafara zaucewa da kyawun
zeenatu
Runtse idanunta tayi da sauri tare da ɗaura tafukan hannayenta ta rufe fuskarta alamar taji kunyar
kalamin shi
"Yaya shureim ni kunyarka nake ji, dan Allah kabarni in tafi ɗakina"
"Ki daina jin kunyata, Ni da nake burin ki zama abokiyar rayuwata" wani irin daɗine ya ziyarci zuciyarta jin
kalamin daya furta mata.
Tunda yafara kallonta bai bari ya daura idonshi akan dukiyar fulanin ta ba sai da taja numfashi suka
motsa tukunna hankalin shi ya karkata akan su.
Yajima yana mamakin cukowarsu kamar bana yarinya ba, jin numfashinshi saman fatar kirjinta yasa tayi
sauri buɗe fuskarta da idanunta gaba ɗaya lissafi na neman kwance mashi kamar zai cafko su haka yake ji
ya duƙufa yana kallonsu ko kyaftawa baiyi.
"Yaya shureim menene haka? Dan Allah ka daina kallona, Ka bari sai munyi aure" Ta fada tana bubbuga
mashi ƙafafuwanta, ɗagowa yai da idonshi ya kalleta launinsu harya fara canzawa
Matsar da fuskanshi yayi saitin tata ya daura tsinin hancin shi akan nata, nan take ta soma jin wani irin
yanayi atattare da ita, Numfashinta harya fara canzawa, Bugun zuciyarta ya ƙaru, duk ta ƙagara da son jin
shi a jikinta, tayi tunanin zaiyi mata irin abunda taga daddynta da mommynta sunayi wato kisssing din
junansu.

Kamar tasan abunda ya ke shirin yi mata kenan, saboda baya a hayyacinsa a buƙace yake da ita, Yana
kokarin haɗe bakinsu, Kwatsam Benazir Ta biyo hanyar da suke da sauri take Tafiya sautin takalmanta ne
suka ja hankulansu, a gigice Zeenatu ta bangaje dr shureim ta watsa da gudu ta nufi bedroom dinta.

"A'u'zu billahi minasshaidanirrajim"

acikin zuciyarshi ya furta hakan.

*Daga Alƙalamin Boss Bature✍️


*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida*
[06/03, 6:46 PM] Anty Hajjo 2: *Assalamu Alaikum*

_Bayan gaisuwa irin ta addinin musulunci tare da fatan kuna lafiya_

_dangane da maganar yin posting a watan ramadan, Ina mai bada hakurin canza shawarar da nayi, cos My
elders didn't approve of my decision to post during the fasting month, so I canceled the update until Eid.🙏_

_In Allah ya yarda hakan bazai canza komai ba In sha Allah, idan na samu time zancigaba da typing ina
tarawa zaifi min kwanciyar hankali✍️
_

_This week One page nayi posting, a barshi a matsayin na last week da nace zan biya bashi_

_Weekend din nan mai zuwa zan turo pages din wannan satin, saboda a halin yanzu bazan iya ba, ni kadai
nasan abunda nake ciki, Amma in sha Allah weekend za ku ji daga gare ni👏🤝👍_
*fatan za'a fahimce ni, a kuma yi min uzuri, Allah yakai mu da rai da Lafiya, Ubangiji Allah ya kawo mana
sauki cikin rayuwarmu, Allah ya yayema kowa abunda ke damun shi👌**Something Is About to Happen*
_______________________________✍️

jikin shi da kasala Ya juyo Yana duban Benazir dake tunkaro shi ga dukkan alamu bata ga Zeenatu ba.

"Yayana nakaina, me kake yi anan"? Tana murmushi tayi mashi maganar

Sam ya kasa buɗe baki Ya bata amsa, sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi.

"Lafiya? Ya akai naga idanunka sun yi ja"? Aruɗe ta jefa mashi tambayar tana duban shi.
Shafa sumar kanshi yai da hannu ɗaya kafin ya furta"bakomai, Yanzu na tashi daga bacci,"

"Amma dai daga gani baccin bai isheka ba, cos gaba ɗaya kamar ma baka a hayyacinka"

Ƙaƙaro murmushi yayi akan fuskarshi batare dayace mata komai ba.

"Yayana, Maganar zuwa gidan su Aneeleeh ne Ya kawo ni, wallahi duk na damu da rashin samun layin
Abie din su, har number dinsa na kar6a awurin daddy na jaraba kiran layin da wayar mom amma shiru ba'a
ɗagawa" muryarta tamkar zata fashe da kuka tayi maganar.

"Bana so mubar abuja batare da mun je gidan su ba"

"In sha Allah zamu je, Zanyi maki ƙoƙarin hakan, abun da yakamata mu yi shine mu tura mashi da text
message, may be layin nashi baya akan waya duk ranar da ya sanya shi zai ga sakon mu ne"

"Hakane, tun da akwai layin awayarka ka tura mashi da sakon"


Ba tare da 6ata lokaci ba, Dr. Shureim Ya zaro wayarshi, ya soma daddanata
"Me zan rubuta mashi"? Ya tambaya yana kallonta.
"Ka faɗa mashi Benazir ce Ƙawar Aneelerh, Matar Tajuddeen" Ya furta Okey, bayan ya gama rubutu text
din Ya turama masa, Kafin daga bisani ya ɗago da ido, Ganin takura mashi ido yasa shi yi mata gyaran
murya"lafiya kike kallona"? murmushi tasaki tare da fadin"yayana fada min gaskiya, meya jefa ka cikin
yanayin nan" ta fada tana ɗage mashi gira, nan take ya fahimci jikin shi ya nuna halin da yake aciki, shafa
kirjin shi yai da hannu tamkar zai gyara ma6allin gaban jallabiyarsa Duk yabi ya dabarbace wata irin kunya
ce ta kama shi.

"ina Zeenatu"? Ta jefa mashi tambayar tana bin shi da kallon ƙurulla.

Galla mata harara yayi"Bansani ba, Ƴar sa Ido, Kije dakinta ki neme ta, wato dai bazaki canza halinki ba,
Har yanzu kina nan da rashin jin maganarki, ' kafin ta kara furta mashi magana yayi saurin wuce ta Ya nufi
bedroom dinshi, Yana shiga ya jefar da wayarshi kan gado da wata irin kasala Ya faɗa saman gadon Yana
fuskantar ceilling, wani irin yanayi yake jin kanshi mara misaltuwa.

Lumshe idanunshi yayi yayin da acan cikin zuciyarshi yake tariyo wani abu daya ta6a faruwa arayuwarshi
Har abada bazai ta6a mantawa da wannan daren ba, wanda yake yi mashi laƙabi da DESTINED NIGHT,
abun da ya faru a daren Ya tsaya mashi aranshi Ya kafa tarihin da har abada bazai ta6a gogewa aranshi ba.

Ƙoƙarin canza akalar tunanin nashi yayi gudun kada ya fama raunin dake a zuciyarshi.

Sunan Allah yaci gaba da ambato har saida yaji zuciyarshi tayi mashi sanyi tukunna Ya samu damar
miƙewa Ya nufi toilet don Ya tsarkake jikin shi.
__________________Boss Bature

A hankali dankareriyar Motarsu Ta kunno kai ta cikin Katafaren Gate din shiga gidan dake a tsare da
Security Officers, motace Yar Ubansu mai numfashi tsadaddiyar Gaske, Su biyune a back seat Na motar,
Alhaji musa dake a hakimce Ya kishingiɗa saman seat din ta motar, Wankan boyal ne a jikin shi launin milk
sun zauna mashi, daga gefen shi Alhaji Ubaid ne Cikin shiga ta shadda fara, dawowarsu kenan daga taron
da suka halarta wanda akayi a head quarter na party din su.

Tun kafin Security guard din dake driving dinsu yayi parking, idanun Alhaji musa masu dauke da bacci suka
hango mashi Hajiya sarah da layla dake a gaban Swimming pool suna fira, ta cikin window din motar Yake
dubansu, Ranshi yayi mugun 6aci, dama fuskar babu annuri ko miskala zarratin.

Bayan motar tasu tayi parking a harabar Ajiye motocinsu, Bai jira Security guard din Ya buɗe mashi mota
ba, da kanshi Ya buɗe murfin Ya fito Yana faman haɗe rai, fitowa daga cikin motar Alhaji Ubaid Yai,
idanunsa akan Musa yace"wai meke damunka ne? Tun dazu da muka fita taron jam'iya babu annuri akan
fuskarka, mutane sai rububinka sukeyi amma kai ko kaɗan basu agaban ka, Ka haɗe rai kamar wanda aka
aiko ma sakon mutuwarsa... " kafin Alhaji Ubaid Ya ƙare maganar, Alhaji musa Ya ɗaga mashi hannu babu
mutunci Ya furta"Ya isa haka! Bana son jin maganar nan," da sauri Alhaji ubaid Yaja baki yayi shiru, Cikin
Takun Isa da izza Alhaji musa Ya haura ƙafa Ya nufi Cikin gidan.

Hajiya Layla dake hangen su Alhaji ubaid tun da suka fito daga mota, da zolaya tace ma mom sarah"Matar
so Ga mijin So can Ya dawo, Naga kamar ranshi a6ace Yake yakamata kije ki lallashe shi"

sai data furta maganar Hankalin Sarah Ya kakarta akan su, A lokacin Har Alhaji musa Ya shige Ciki, miƙewa
tayi da sauri tana fadin"Nasan bai wuci gajiya bace ta dameshi, dama da safe kafin ya fita Ya faɗa min baya
jin dadin jikin shi, " tana ƙare fadan hakan Tabi bayan Alhaji musa.

Bayan tafiyarta, Hajiya layla bata motsa daga inda take a zaune ba, Alhaji ubaid take Jira Ya ƙaraso inda
take ganin Yana tunkarota sai faman sakar mata murmushi Yake Yi, Ita ko ta haɗe mashi fuska, don ba
ƙaramin haushin shi take ji ba tunda yaƙi amincewa da zancen Komawarsu Joss.

Kujerarar dake fuskantarta Yaja ya zauna.


Fuskarshi da fara'a yace"uwargida ran gida, fatan na sameki Lafiya"
Banza tayi da shi batace komai ba, sai ma cup da ta dauka tana shan sauran coffee dinta
"Layla kina ji ina magana kinyi banza kin ƙyaleni, Ko sannu da dawowa babu"

Ta6e baki tayi tare da hararar shi tace"hmmmm, me kakeso nace"? Shiru yayi baice mata komai ba, sai dai
binta da idanu da yakeyi.

"Ka bani mamaki, nayi tunanin mijina Namiji ne, ashe ba haka bane nayi kuskure, Ka nuna min kai ba
komai bane wai ƙaninka shike juya ka son ranshi, baka jin maganar kowa In ba ta shi ba, kamar wani
ubanka" rai a6ace tayi maganar.

Tuni yanayin fuskar Alhaji ubaid ya canza zuwa matsananciyar damuwa, baya son mitar da Hajiya layla
take yi mashi kullum haka ya ke fama da ita.

"Layla bai kamata Kina gaya min magana ba, Har yanzu ni mijinki ne matsayina agareki bazai ta6a
canzawa ba... "
Murmushin takaici tasaki tana dubanshi tace"Ubaid! Duk abunda na faɗa maka Kaine kaja, wallahi ka 6ata
min rai, bana jin daɗin ƙasƙantar damu da ka ke yi awurin musa, baya ganin girman kowa daga kai har ni,
burinshi mu zama tamkar bayinshi shi kuma uban gidan mu, na rasa gane da wani yare zanyi maka magana
yadda zaka fahimce ni...." muryarta na rawa ta ƙare maganar, hawaye tuni sun cicciko idanunta.
Girgiza kai yai cikin sanyin murya yace"bani da amsar da zan baki, duk abunda kika faɗi gaskiya ne layla,
bawai bana fahimtar ki bane, sai dai bani da yadda zaniyi, yakamata kiyi min uziri, Ni ina girmama musa ne
saboda halaccin shi agareni, yayi min abubuwa da dama waɗanda bazan ta6a mantawa ba, duk wani
cigaba da kika ga na samu arayuwata musa shine sila....." kasa ƙarasa maganar yayi sakamakon dariyar da
layla ta saki tamkar wata zararra, jikinta har jijjiga yake yi.
da mamaki akan fuskarshi yace"meyasa kike min dariya? Kin maidani mahaukaci ko"?

Tsagaitawa tayi da yin dariyar ta soma yin magana.

"Mijina Ina tausayin rayuwarka, Sannan Ina jiye maka ranar da zaka yi danasanin yarda da kayi da ƙaninka
musa, saboda ya riga daya gama dakai! tarkon daya ɗana maka Yayi tasiri a zuciyarka, Wai kai baka amfani
da ƙwaƙwalwarka ne? Idan har don Allah yake kyautata maka meyasa baya yi maka biyayya amatsayin shi
na ƙaninka"!? A faɗace tayi maganar, Alhaji ubaid Yayi shiru Yana sauraronta, kalamanta sun yi mashi tsauri
suna neman ruguza mashi lissafin ƙwalwarsa.
"Kasan ni bana 6oye ta cikina! Idan abu yana damuna kai tsaye nake faɗi ma mutun koda kuwa bazata yi
mashi daɗi ba" Ta faɗa tana mai ƙara jaddada kalamanta.

"Yakamata ka farka daga baccin da ka ke yi, tunkafin lokaci Ya ƙure maka, Ni dai zan faɗamaka gaskiya
koda kuwa zaka ji haushina ne, Alhaji musa ƙaninka ba ƙaunarka yake yi ba dakai da iyalanka, Baya sonmu
ba don Allah Yake kyautata mana ba face sai don saboda wata manufa tashi, na faɗa maka hakanne bawai
don ina zargin shi da wani abu ba, sai don saboda babu gaskiya a lamarin shi!"

A zafafe Ta ƙarasa maganar, tare da kai hannu ta daki gaban table din, Bata jira amsar da zai bata ba tayi
saurin miƙewa zuciyarta na tafarfasa ta nufi cikin gidan ta shige.

Gaba ɗaya Alhaji Ubaid Ya rasa meke yi mashi daɗi a duniyar nan, Har cikin ranshi bayason 6acin ran
layla, A cikin ƴan kwanakin nan kusan kullum sai sun samu sa6ani da ita saboda Alhaji musa, baisan ya zai
yi da ita ba, a ganin shi itace ta tsani Alhaji musa shiyasa take neman 6ata mashi suna a wurinshi duk don
su bar gidansa.

Ya jima zaune kan kujera Hannin shi ɗaya dafe da kanshi sai daga bisani Ya miƙe Ya nufi cikin gidan.

*ALHAJI MUSA💪*

Bayan shigarshi bedroom dinsa, rage kayan Jikin shi yayi, ya rage saura farar shirt da short, Sai faman Cika
ya ke yi yana batsewa, zuciyarshi Ta kai maƙura awurin 6aci.

Hajiya sarah tana ƙoƙarin shigowa bedroom din nashi, ba zato ba tsammani taji Ya furta"Kada ki kuskura
ki shigo min nan!" Ras taji gabanta Ya faɗi, abakin kofar ta tsaya tana dubanshi Yana daga tsaye Ya dafe
sofa din dakin da hannayenshi.

"Meyasa zaka hanani shigowa"? Cikin kwantar da murya tayi mashi maganar
Tamkar bazai tanka mata ba yace"zonan"! Kamar wata ƙaramar yarinya haka ya kirata, bayan ta shiga
dakin daga gaban sofa din ta tsaya tana kallon shi.

Zagayowa yayi ta gabanta, ya sassauta fushin fuskarshi.

"Meya hana ki zuwa wurin Aiki yau"?


Cike da jin shakkar shi tace "Namanta ne ban faɗa maka ba, Jiya na ɗauki hutu saboda Hajiya layla inaso
muna samun lokacin da zamu dinga zama muna fira harma mu dinga fita" daƙyar ta ƙare maganar ganin
irin kallon da yake jefa mata, tuni tasha jinin jikinta.

"Saboda ita kawai kika ɗauki hutun aiki? Kin fara shaye shaye ne"? A ruɗe take kallon
"Kin ci sa'a bani da ɗabi'ar ta6a lafiyar mace, da kuwa yau saikin yaba ma aya zaƙinta, " mamakin
maganarshi ne yasa ta zaro idanunta waje har saida ta maimaita kalmar sai kin yaba ma aya zakinta.
Adabarbace ta furta"bangane me kake nufi ba"?

"Bani da lokacin Yi maki bayani, amma Inaso in ja maki kunne akan matar can, bana son ganin kina sakar
mata jiki kuna yin fira, wannan umarni ne daga gare ni, ban amince ki rinka ke6ance kanki da ita ba"!

ɗaure mashi fuska hajiya Sarah tayi"akan me zaka hana ni yin fira da ita? Haramunne yin hakan? Ko tayi
maka laifi ne? Ina buƙatar hujja.

Da kakkausar Murya Ya furta"Umarni nake baki ba shawara ba, ki koma aiki gobe sannan kada in ƙara
ganin kin ke6ance da ita" Ya faɗa yana furzar da huci ta hancin sa.

Ta fahimci bayason hajiya layla, ta daɗe da sanin rashin jituwarsu sai dai batayi tsammanin abun yakai
haka ba.
Ƙwara tabi Umarnin shi ta zauna lafiya idan ba haka ba, Ita zata jama kanta"
Yana ƙoƙarin juyawa tayi saurin ruƙo hannun shi acikin nata, kallo ya jefa mata mai kama da harara.

"Ka yi hakuri idan ranka ya 6aci, in sha Allah zanyi maka biyayya bazan ƙara zama yin fira da ita ba"
Lumshe idanunshi yayi kafin ya buɗe su Ahankali Ya furta"me kuke tattaunawa ne da ita"?
Tayi mamakin tambayar daya jefa mata, saboda tasan halin shi, mutunne da bai Iya shiga shirgin mutane
ba, idan yana zaune a wuri baka isa ka yi mashi gulmar wani ba, amma sai gashi yau yana neman ta fada
mashi abun da suke tattaunawa da Hajiya Layla.

Bayan ta kammala faɗa mashi calmly ya furta"bansan meyasa ta sanya min ido ba, bata son ganina kamar
na kashe mata wani"
Matsawa Sarah tayi dab da shi ta ɗaura hannayenta saman fadadan kafaɗunsa
"Kada hakan ya dame ka, ni dai shawarar da zan baka, dan Allah ka basu damar da zasu koma Joss,
saboda ta nuna batason zama a gidan nan" ta faɗa tana mai tausasa kalamanta.
Jinjina kanshi yayi"zanyi tunani akan hakan,"
Ya faɗa tare da juyawa Ya nufi Katafaren gadonsa, Ya haye ya kwanta idanunsa suna fuskantar ceilling.

Duk sai taji ba daɗi, ganin yanayin shi da damuwa akan fuskarshi, tasan bai wuci ƙiyayyar da hajiya layla
take nuna mashi bace tasa shi shiga yanayin.

"Babe, kana buƙatar wani abu ne In kawo maka"?

Batare daya kalleta ba Ya furta"Bana buƙatar komai, ki zo ki kwanta a gefe na" taji dadin maganar daya
furta mata da sauri ta nufi gadon tare da hayewa ta zauna kan mattress din, sai da tafara zage zip din
rigarta, ta cireta kafin ta kwanta saman kirjin shi, ya ruƙo waist dinta da hannun shi ɗaya, ɗagowa tayi da
blue eyes dinta tana kallon sajan fuskarshi.
"Bana gajiya dakai, banƙi mu kasance har Iya ƙarshen rayuwarmu atare da kai ba, Idanunsa dake a
lumshe yaɗan buɗe su A hankali yana duban fuskarta ba tare daya ware su ba.
Sumbatar cheek dinsa tayi, tamkar zaiyi murmushi sai dai bai bari Ya bayyana ba, ta fahimci yaji dadin
abunda tayi masa, kallon juna suka cigaba da yi, tunawa tayi da layin dake akan wayar Zeenatu, har ta
buɗe baki zata fada mashi kiran da akayi da bakuwar mumber da sauri ya ɗaura mata yatsa sama lips
dinta.

"Ina buƙatar hutu!" murmushi tasakar mashi, tare da rungumo shi suka ƙanƙame juna, cikin ƙanƙanin
lokaci bacci yayi awon gaba da shi.

Idan muka koma 6angaren Zeenatu tun da ta watsa da gudu ta nufi bedroom dinta, tana shiga ta haye
saman gado ta kwanta tare da rungumo pillow a ƙirjinta, fuskarta ɗauke da murmushi, wani irin so da
ƙaunar yaya shureim take ji, taso ace Benazir bata katse mashi hanzarin shi ba, da yau ta kar6i first kiss
dinta a wurin hubbinta, wani irin nishaɗi take ji kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, sai faman juyi take yi a
tsakiyar gadon kamar me fama da ciwon ciki.

Jefar da pillown hannun tayi tare da saukowa daga kan gadon ta shiga toilet, after some mins ta fito
fuskarta da alamun lemar ruwa ta nufi glass wardrobe dinta, suturar jikinta ta canza zuwa riga da skirt
launin dark brown, ta dawo gaban mirror ta zauna tana kiciniyar ɗaure gashin kanta da ribbom.

Jin motsin shigowar mutun ɗakinta ne yasa tayi sauri juyowa don ganin wanene
Benazir ce a tsaye ta goya hannayenta saman kirjinta,
Kamar mara gaskiya haka zeenatu take kallonta, duk tabi ta kame kanta wata irin kunyar Benazir ce ta
kamata gani take yi kamar taga abunda suke yi ita da dr. shureim.
Muryarta da in'ina ta furta"am.. um.. aunty Benazir kece" dariya Benazir tayi tare da shiga ciki tana
fadin"Zeenatu kenan, dole ki ruɗe babyn shureim"
Waro ido waje tayi jin ta kira ta da sunan babyn shureim hakan na nufin tagansu ɗazu, da sauri ta miƙe
daga kan mirror chair din tana faman duƙar dakai ƙasa
"Kin bani mamaki zeenatu, Ki rasa dawa zakiyi soyayya sai yaya shureim! Kamar kin makance, May be
bakisan shekarun shi ba, Ki daina ganin shi kyakkyawa kamar matashin saurayi, ya kusa sa'an daddynki... "
har saida gabanta ya fadi jin abunda Benazir ta faɗa mata.
Muryarta na rawa ta furta"am... aunty Benazir kina nufin yaya shureim da daddyna sa'annin juna ne"?

"Eh mana, kema in banda abunki taya zaki yi soyayya da wanda Ya girme maki? yafa haife ki" Da biyu
Benazir take fada matan hakan duk don tacanza mata ra'ayinta na son ya shureim, don ita aganinta bai
kamata yaso ƴar cikinsa ba, badan bata son shi da zeenatun ba, sai dai bata jin zata iya bari ya auri mace
mai ƙaramin shekaru amatsayinshi na tazurun daya daɗe baiyi aure ba, zaifi dacewa Ya auri babbar mace
wadda takai shekara talatin.

Bubbuga ƙafafu zeenatu tayi akan floor, voice dinta da shagwa6a tace.

"Aunty Benazir ai ba haramun bane, cos The Prophet Muhammad, peace be upon him, married Aisha
when she was very young," ta faɗa tare da sanya hannu ta rufe fuskarta cike da jin kunyarta.

Dariya Benazir tayi tana dubanta da mamaki wato bazata kar6i shawararta ba tafi son Sugar daddy irin Ya
shureim.
"Zeenatu Ki fahimce ni, Kinfi buƙatar saurayi wanda baifi shakara ashirin da bakwai ba, Ina zaki kai Ya
shureim"?

"Aunty benazir dan Allah kidaina fadin haka, wallahi bana so, Inason Ya shureim ɗina, koda tsohone shi"
tamkar zata fashe da kuka tayi maganar.

Gyaɗa kai benazir tayi"its Okey, babyn shureim, Naji nayi shiru bazan ƙara magana ba, hakan yayi maki"
Tana faman zumbura baki tace Eh, dariya Benazir tayi da zolaya take fadin"lallai ya shureim yayi kasuwa,
Irin wannan So haka? Ta fada tare da samun wuri gefen gadon zeenatu ta zauna.

"Ina wayarki take"?

"Nabarta A cikin wandon jean dina dana cire, Bari na dauko maki" da sauri ta juya ta nufi inda ta rataya
kayan.
Sai gata ta dawo hannunta ruƙe da wayar ta miƙa ma Benazir, bayan ta kar6a, zeenatu ta zauna agefenta.

Screen din wayar ta ƙurama ido hoton Fatiman shureim ne, nan take yanayin fuskarta ya canza, da sauri
ta furta"Zeenatu! Meyasa kika daura hoton nan a wallpaper dinki"?
"Saboda inason hoton ne, yaya shureim ne ya tura mun hotunanta"
Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, aranta ta ayyana bazai yiwu ba, dole in sa zeenatu ta sauke hoton
fateema daga wallpaper dinta.
"Aunty Benazir, Ɗazu An kirani da wata baƙuwar number lokacin na shiga toilet, bansan wanene ba, har
mommy nakaima wayar tace ita batasan ma da layi akan wayarba, Nima kuma bansan da layin ba"
Cikin kulawa Benazir tace"waye ya siya maki wayar ne"?
"Daddy ne Ya siya min, amma bani yaba ma ita ba, saboda bayason ina yawan amfani da waya zata Iya
ɗauke min hankali daga yin ibada, shine yaba mommy wayar, ita kuma ta ajiye min ita, dama ni ban damu
da ita ba, sai da naga hotunan fatiman ya shureim awayarsa shine naje nace ma mommy ta bani wayata
zan yi amfani da ita" tunda tafara yin maganar Benazir bata kau da ido daga kallon ta ba, tayi mamakin da
har shureim ya iya faɗama Zeenatu sirrin shi, hakan ya ƙara tabbatar mata da irin Ƙaunar da yake yima
zeenatu.

A hankali ta kau da idanunta daga kan Zeenatu, ta ɗaurasu kan screen din wayar, Call logs ta shiga, nan
take tayi tozali da bakuwar number da aka kira zeenatu da ita kusan 2 missed calls, Aranta ta ayyana Uncle
musa ne ya siya mata layin awaya ko kuwa tare da sim din aka siya mata wayar? Tayaya ma haka zata
yiwu? Idan shine ya sanya mata sim din meyasa bai sanarma mom sarah ko ita zeenatun da akwai sim a
wayar ba? Sannan babu yadda za'ai companyn da aka sayi waya su bada ita tare da sim"

Zeenatu dake kallonta ganin ta ƙurama screen din ido babu alamun zatayi magana ne yasa tace"ko dai in
kaima daddy wayar ya duba min mommy ma tace idan ta shigo gidan zata bibiyi layin"!

"A'a zeenatu, Kada ki kai mashi wayar, nafi tunanin shine ya sanya maki sim din aciki ba tare dasanin ki ba
may be ya manta bai faɗa maki ba, sannan layin da aka kira ki da shi ina da tabbacin wrong number ne
suka kira"

"Nima raina ya bani hakan, to ki goge min layin daga kan wayata"

Benazir tace"A'a, kada mu yi saurin goge number, Mu jaraba kira don mu faɗa ma mai layin wrong number
ne ya kira, Kinga ta hakanne zai iya gyara number din ya kira wanda yake son yin magana da shi"

Jinjina kai zeenatu tayi alamar gamsuwa da bayaninta.


"Yaushe zamu kira su"?
"Yanzu zan jaraba"
Danna kira Benazir tayi, duk sun ƙagara da son jin me layin ya ɗaga sai dai kash Kiran yaƙi shiga"
"Ki bar min wayar a hannuna, tunda ba amfani kikeyi da ita ba, Zuwa anjima zan jaraba kiran layin"
Amsa mata tayi da toh
"Amma idan mommy ta tambayeni ina wayar ya zan fada mata"?

"Sai kice mata ni na kar6a, ina wani amfani ne da ita" amsa mata tayi da toh.

"Namanta wayata a hannun mutumin da na zauna awurinshi can ƙasar Canada" benazir ce tayi maganar
Zeenatu tace"aunty dama a canada kika zauna? Ya sunan mutumin da kika zauna a wurin shi"?

Shiru ta yi tamkar bazata tanka mata ba tace"hakane a canada na zauna, mutumin daya ruƙe ni sunan shi
Zaki Mubarak Obinna, ɗan gidan chief of army staff bansan ko kin san shi ba"

Murmushi zeenatu tayi tare da cewa"nasan ƴan family din obinna sosai, tun kafin in mallaki hankali na
muna yawan zuwa estate dinsu nida mommy na, da yake suna mutunci da Hajiya saratu daga bayane
daddy ya hanata zuwa Yawo dani, tun da na kammala secondry school Ya garƙameni agida, bai bari tana
fita dani, har sai da Ya shureim Ya dawo da zama gidanmu sannan Ya kyaleni ina fita tare da shi.
Murmushi benazir tayi"Allah sarki, kada ki damu ai yanzu tunda ina nan zamu dinga zuwa yawo sosai,
Harma estate din nasu zamu Iya zuwa duk da bansan su ba amma indai na tuntu6i zaki mukayi magana da
shi nasan zai gayyace ni zuwa gidansu, ya jima yana da burin inje gidansu saboda ya nuna ma Iyayen shi ni,
Amma naƙi amince mashi saboda bana son zuwa nigeria a lokacin"

"Idan ma zaki gidansu ƙawarki Aneeleeh dan Allah ki tafi dani, nima inason zuwa, Naji kuna magana da su
mom layla akan zaku je gidan"

"In sha Allah, atare zamu tafi," taji dadin maganar Benazir fatan ta Allah yasa ta samu ƙawaye agidan kawar
Benazir, tana da burin ganin ta tara friends sai dai daddynta Ya hanata Yin kawaye, baison kowa ya rabeta.

*❤EX-PRISONERS🌹*

Shigowa ɗakin Naufal Yayi, fuskar shi babu walwala, shima babu suturar a jikinshi sai gajeran wando,
sumar kanshi duk ta yamutse har saman wuyan shi, Kunsan atare Unaisah Da Sajeed suka juyo suna kallon
shi
Harara ya watsa ma sajeed tare da cewa"Ɗan rainin wayau, ashe nan ka shigo, kasa inata nemanka,
Hankalina Yaƙi kwanciya ganin Halin da ka farka daga bacci"
Murmushi Sajeed Ya sakar mashi, tare da saukowa daga saman gadon unaisah bayan ya miƙa mata
wayarta ya nufi Naufal Ya rungumo shi Yana fadin"Sorry My baby Boy, Na tayar maka da hankali, ashe ka
damu dani har haka? Halan ma kuka kayi saboda rashin ganina da baka yi ba" ya fada da zolaya yana shafa
mashi fuskarshi.

Tsoki Naufal Yaja ba tare daya tanka mashi ba Ya dubi Unaisah


"Sister barka sannunki"
Murmushi tayi dimple dinta biyu suka lotsa
"Yawwa rabin raina, halan Sajeed ne Ya 6ata maka rai"?
Yamutsa fuska yayi kafin yace"eh mana, kawai Ina kwance Ina bacci na jiyo shessheƙar kukan shi ya cika
min kunne na, ba arziƙi na farka Hankali atashe na tada shi daga bacci ina tambayarshi lafiya yake kuka, Bai
tanka min ba kamar wani shashasha haka yabarni ya fito daga dakin, Ina ta neman shi ashe nan ya shigo"
Ya faɗa yana jifar Sajeed da harara"don yaga na damu da shi ne, Allah nan gaba idan Ya ƙara yi min haka,
Bulala zan sanya mashi"

Dariya su ka yi gaba ɗayansu, Sajeed yace"na fi ƙarfinka Naufal, mai buguna sai ruwan sama da rana," ya
fada yana nuna mashi faffadan kirjinshi da damtsen hannunshi.
Nannaɗe hannun riga Naufal yayi yana fadin"ba kai kaɗai Allah Yaba kirar karfin ba, Nima ina da ita, babu
abunda zaka nuna min in banda girman jiki"
Unaisah dake kallonsu kamar ta samu tv, Wayarta dake a hannunta ta danna ta shiga Camera, Ta saita su
tana ɗaukarsu Video batare da sanin su ba, saboda sunyi mata kyau, sai taji inama ace hada Danish dinta
da kuwa shi zai kar6i kambun faɗan nasu, domin kuwa Danish Yafi su tsayi da kuma kyawun Sura duk da
suma ɗin ba daga baya ba musamman Gabriel Namiji ne.

A yayin da take ɗaukarsu video, bakomai take tunawa ba face garkuwarsu, lokacin da ta risƙe shi a ɗakin
Gidan kurkukun ƙaddara Kwance Yana bacci da red shirt a jikin shi, yayi mata kyau fiye da tunanin mai
tunani, duk da a lokacin a matsayin giant yake saima ya ƙara yi mata kyau, tana matuƙar ƙaunar komai
nashi ta ƙosa ya dawo normal mutun kodan suci gaba da bama junansu kulawa.

Tayi zurfi acikin tunaninta, Shessheƙar kukan Azeeza Ya fargar da ita, da sauri ta janye wayar daga saitin
fuskarta, su Sajeed dake atsaye suna kokoyi shida Naufal jin kukun Azeeza ne Yasa suka dakata kusan atare
suka kalli ƙofar shigowa dakin.
Kamar Mahaukaciya Haka ta shigo sanye da ƴar gown wadda bata rufe gwiwar ƙafarta ba, fuskarta
sharkaf da hawaye tayi jawur da ita, rigar jikinta ta jiƙe da ruwa
daga bayanta Jamimah ce atsaye ta ruƙe rugu tana faman sakin murmushin mugunta.

da sauri Unaisah ta sauko daga saman gason, ta nufi Azeeza ta ruƙo hannunta tare da rungumeta tana
tambayar ta lafiya take kuka
Muryarta da shessheƙar kuka tace"jamimah ce ina bacci ta watsa min ruwa ajikina, shine wai take cewa
nayi fitsarin kwance bayan itane ta kwarara mun ruwa a kasan rigata.... " tunkafin Azeeza ta ƙarasa
maganar, Jemimah tayi saurin cewa"wallahi ƙarya take yi min, Fitsarin kwance ne tayi mana a ɗakin mu, Ni
bani na zuba mata ruwa ba" Ta faɗa tana faman gumtse dariya.

Cikin muryar Raɗa Naufal Yace da Sajeed"babynka tayi fitsarin kwance, Yakamata kaje ka wanke mata"
harara Sajeed Ya watsa mashi tare da ingije shi, Ya nufi Jemimah, ganin Yana tunkarota Yasa ta juya da
niyar ta gudu sai dai kafin ta fuce daga ɗakin, Yayi hanzarin cafkota da hannu biyu ya ɗaga ta sama yana
fadin"Mugunta ko? Ai ba ke kaɗai kika iyaba kowa ma Ya iya ta, rasa kunya 6eran tanka, da wasu
kunnuwanki kamar na zomanya, Jibi kumatunki duk kin shanye ma mutane madara da bonbita, Yau zanyi
maganinki" Ya fada tare da Juyawa ya nufi Toilet da ita, Kuka tadinga yi mashi tana kokarin kwacewa, da
gudu naufal yabi bayan shi yana fadin"please bro, Ka kyaleta yarinya ce bata da wayau" ko sauraron shi
baiyi ba yaja kofa Ya datse.

Azeeza dake kwance Jikin Unaisah sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi, Taji daɗi Sajeed zai rama mata
abunda Jemimah tayi mata, ba tun yau ba kusan kullum sai jamimah tayi mata mugunta don taga suna
kwana a ɗaki ɗaya.

"Ki yi haƙuri da sister dinki, nasan halinta bata jin magana, Kunnan ƙashi ne da ita, amma please ki daina
bari tana ganin kukanki, shiyasa take ƙara rainaki saboda tasaba sanyaki kuka... "
Cikin sanyin murya Azeeza tace"Toh, amma kiyi mata magana tadaina jana fada, har fadi takeyi wai ni ban
isa da ita Ba, maganarki kaɗai take Ji"
Murmushi unaisah tayi"zan yi mata magana idan ma bata daina ba zamu fara koya mata hankali ne"
Fitowa Sajeed Yayi daga cikin toilet Yana faman sauke ajiyar zuciya, fuskarshi ɗauke da murmushin
mugunta.
Naufal dake kallonshi yace"Mugu Ina ka baro mana jamimah"?
Harararshi yayi" ka shiga ka ɗaukota, wata'ƙil ƙafafuwanta baza su iya daukarta ba shiyasa ta kasa fitowa"

Ya faɗa tare da wucewa Ya nufi Azeeza, Ruƙo hannunta yayi Acikin nashi ya rabata daga jikin Unaisah
Ya zauna daga gefen gadon Yana fadin"Har nagaji da yi maki magana akan ki daina bari Waccan Ƙaramar
halittar tana sanyaki kuka, serious idan baki daina ba zamu 6ata" ya faɗa yana daure mata fuska.
Muryarta ƙasa ƙasa tace"zan daina"
Harara ya watsa mata"haka kullim kike fadamin, last warning zan baki daga yau idan na ƙara ganin hawaye
akan fuskarki da sunan jamimah ne tasa ki kuka Jikin kine zai gaya maki" yai maganar tare da kama
kunnanta yace"Idan kunne Yaji"? da sauri tace mashi Jiki Ya tsira"

Dariya ce ta kubce ma unaisah da naufal, shima sajeed din dariyarce tazo mashi sai dai Yaƙi barin ta kubce
mashi don baison raini ya fara shiga tsakanin shi da Azeezarsa, Yafi son tana jin shakkarshi.

"Jemimah!" Jamimah ta"! Naufal Ne ya kira sunanta, Shiru taki ta amsa mashi, Sajeed Yace"zuciyar ce ta
motsa, tana jin ka ƴar rainin wayau"
Miƙewa unaisah tayi da sauri ta nufi toilet din, tana shiga ta taras da jemimah zaune cikin kwamin wanka
da sajeed Ya cika da ruwan mai uban yawa, Rigar jikinta duk ta manne ma fatarta, ta ɗaure fuska sai
shessheƙar kuka take Yi kamar zata haɗiyi zuciya tsabar 6acin rai.
Ganin Unaisah yasa ta fashe da kuka rai a6ace ta dinga bugun ruwan da hannayenta tana fadin"wayyo
Allahna Anci mutuncina, Zuciyata tafarfasa take Yi min, Genie kinga abunda Sajeed Yayi min ko? Kina gani
baki hana shi ba, Saboda rashin mutunci ya jefa ni acikin ruwa"

Hatta su Sajeed dake adakin saida suka jiyo maganganun da Jemimah takeyi a toilet, gaba ɗayansu suka
sanya dariya hada Azeeza.

"Am sorry My Little sister, Sajeed bai kyau ta miki ba, Amma kiyi hakuri dan Allah" unaisah ce ta fada Cikin
lallashi da lallami Ta nufi jemimah, ta sanya hannu ta ɗaukota daga cikin ruwan,
"Kinyi wanka"? Idanunta na fitar da hawaye tace"a'a ni ban yi ba"
"Okey, Bari nayi maki wanka, Sai in ɗauko maki wasu kayan ki canza"
Ta fada tare da cire mata rigar, shaf shaf tayi mata wanka ta daure mata jikinta da towel, Asaman bayanta
ta goyo jemimah, suka fito daga toilet din, sai faman zumbura baki take Yi, Hada jifarsu Sajeed da harara.
"Azeeza mu tafi dakinku, Inaso Ku shirya in yi mana hotuna da wayata" amsa mata tayi da toh,
Sajeed yace"Mu ma bari muje mu shirya ayi mana hotunan, Ko mun samu na ajiyewa saboda tarihi"
Yayi maganar tare da miƙewa Ya dafa kafaɗar Naufal, suka fuce daga dakin.

*❤BATOOL🌹*

Kusan mintuna da tafiyar Unaisah, Chief Ya shigo dakin sanye cikin shiga ta white thobe launin Sky blue,
tabi shape din jikin shi, Hannun shi ɗaya ruke da wayar shi, Ya karata a kunnanshi ga dukkan alamu waya
yake yi.

"Yanzu na shigo gidan, In sha Allah Uncle Idan na shiga bedroom dinsa zan kira ka video call kaga
fuskarshi, nasan hakan zai kwantar maka da hankalin ka"

On the other hand, Prime minister yace"nagode my Son, bansan meyasa nakasa cire shi arai na ba, Na
ƙwallafa rai akan shi"

"Kada ka damu uncle, Nafi so ka kwantar da hankalin ka, baifi awanni daka dawo daga tafiya ba, nasan
kana bukatar hutu, Idan rabon ka ne shi watarana zaku gana"

"Ina fatan hakan, nagode da kulawarka, sai naji ka".

"Okey" ya ambaci hakan tare da zame wayar daga kan ear dinsa.

Yayin da yake tafiya A hankali yake bin ko'ina na room din shi da kallo, Kafin Ya sauke idon shi akan Glass
table din dake dauke da breakfast dinsa.

Ƙarasa shiga ciki Yayi, batare da 6ata lokaci ba, Ya zame jallabiyar jikin shi, Daga shi sai short Ya nufi toilet
Ya shiga domin yin wanka.
After 15 mins Ya fito Waist dinsa daure da white towel, a gaban dressing mirror ya tsaya da niyar ya gyara
jikin shi, kwatsam A lokacin da baiyi tsammani ba kunnuwansa suka jiyo mashi sautin motsin mutun a
bedroom dinsa.

A hanzarce ya ɗaura idanunsa kan madubin, ta ciki ya hangota ta fito daga hanyar zuwa Gym Room
dinsa kamar Aljanna, Hannunta ɗaya ruƙe da mayafinta, Ga wannan Uban gashin kan nata data ta saki
saman bayanta yayi mata tamkar hijabi, Lamarin ya ɗaure mashi kai ganin matashiyar mace a ɗakin
kwanansa, Wacece ita? Tayaya akai ta shigo mashi bedroom din sa? Da iznin wa"? Acikin zuciyarsa ya furta
hakan ba tare daya kau da ido daga kallon ta ba, ƙarfin halin ta yayi matuƙar bashi mamaki, tsawon lokacin
daya shigo dakin har ya shiga bathroom yayi wanka duk tana a ciki ko me take yi!?
Gaba ɗaya Hankalinta ba akanshi yake ba, batasan ma da zaman shi a dakin ba, har ta ƙaraso tsakiyar
dakin bata lura da chief Owais ba, idanunta ba su hango mata shi ba, Sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi
kamar wadda tasha gudu.

Ganin bata da alamun motsawa tabar mashi room dinsa ne yasa shi juyowa A hankali Ya nufe ta, sam
bata ji motsin takun shi ba, saboda Ta juya mashi baya sai ƴan waige waige take Yi, duk kallon da tayima
dakin nashi bai isheta ba.

A lokacin da batayi tsammani ba, Taji saukar hannun mutun saman sumar kanta, Kafin tayi wani yunƙuri
Ya damƙi gashinta, wata irin firgita Batool tayi, A gigice Ta fasa ƙara Sautin Ya cika kunnuwanshi dasauri ya
sakar mata gashi, hakan ya bata damar juyowa don ganin wanene.
Wani irin bugu zuciyarta tayi lokacin da idanunta suka sauka akan faffaɗan ƙirjinshi, da waɗannan Strong
arms din nashi, ta zazzaro mashi ido waje la66anta na kerma take ambaton"INNAHU MIN SULAIMAN
WAINNAHU BISMILLAH" adabarbarce ta furta hakan, kamar wadda taga wani mugun abu, Kallo ɗaya da
tayi ma fuskarshi har suka haɗa ido ba ƙaramin gigitar da ita yayi ba, duk tabi ta ruɗe, Mayafin hannunta
tuni ya jima da zamewa saman floor, juyawa tayi da gudu tana neman hanyar fita daga dakin sai dai takasa
gane ta ina ƙofar da suka shigo take, sai faman bin bango take yi, Jikinta ya hau yin kerma kamar wadda
Sanyi ya kama.

Chief dake atsaye yana dubanta, Kallon mahaukaciya Yake Yi mata saboda kalmar data furta mashi da
kuma firgitar da tayi kamar taga wani mugun abu, Ya rasa gane me ya ruɗar da itane, ta6e la66ansa yayi
kafin Ya juya ya nufi cikin ɗakin,
Batool dake ta neman kofar fita, tuni zufa ta jiƙeta yadda kasan babu A.c a dakin, Mugun tsoron shine Ya
kamata hada ƙarin babu sutura a jikin shi shiyasa ta rikice da ganin al'amurransa, towel din daya ɗaure
waist da shi ko gwiwarshi bai rufe ba.

Jin takun tafiyar Shi abayantane Yasa ta ƙara ruɗewa, A gigice Ta juyo tana duban shi, sumar kanta ta rufe
mata gefe da gefen fuskarta, har Ya sanya Short a jikin shi tare da singlet fara ƙal.

Fashe mashi tayi da kuka tana fadin"nashiga uku, dan Allah ka buɗe mun ƙofa in tafi ɗakin mu, wallahi ni
ba 6arawo bane, bada niyar wani abu na shigo maka ɗakinka ba.

Fuskarta sharkaf da hawaye tayi maganar tana faman jan majina.

Bai tanka mata ba, yama rasa bakin magana, mamakin ta ya gama kama shi, sai yanzu ya gane fuskarta a
cikin Yaran da suke kula da su.

Gently Ya juya Ya nufi gaban side drawer din shi, ya buɗe Ya dauko jotter da pen asaman drawer din Ya
ɗaura jotter, rubutu yayi mata bayan ya kammala ya cire paper din ya tunkari Batool Ya miƙa mata
takardar, gabanta na faduwa ta sanya hannunta dake kerma ta kar6a tana kallon abun da ya rubuta mata.

Muryarta da shessheƙar kuka Ta furta"ai..ai.. Ni Ban Iya karatu ba, sai dai in kaima Unaisah ta karanta min"

Wannan maganar da ta furta mashi ta ta6a zuciyar shi, har sai da ya ɗaura reddish eyes dinsa akan soft
brownish lips ɗinta da suka jike da ruwan hawayen ta, ga wani uban gumi da ta haɗa a jikin ta, shi abun da
ya ɗaure mashi kai ruɗewar da tayi kamar taga wani mugun abu, ita kanta Batool din tunfarko taso idan
suka haɗu ta natsu ta yi mashi bayanin abunda ya kawota dakinsa, sai dai dalilin shaƙar da yayi ma sumar
kanta ne, Yasa ta firgice mashi ta kuma fahimci bai san da maganar zuwan ta ɗakin shi yi mashi aiki ba!.

Taƙi Yarda ta ɗago su haɗa ido saboda ƙwarjinin da yayi mata, gani take yi kamar zai rufeta da bugune
yadda yayi mata rumfa da kirjinsa.
"Dan Allah ka buɗe min ƙofa in tafi daki, zan kai mata ta karanta min"

ba tare daya furta mata komai ba, Ya dafe Glass door din dakin nan take ƙofar ta soma zugewa a hankali,
Jikinta har rawa yake Yi wurin yin saurin fucewa daga dakin kamar za tayi tuntu6e.

Ta tafi tabar mashi Mayafinta akan floor, komawa yayi gefen gadonshi Ya zauna da sanyin jiki, wata irin
yunwa ce ke addabar shi, bazai juri jiran wani yayi serving na shi ba,
Da kanshi Yayi serving abunda zaici, Kakkauran tea ya zuba a cup Ya soma kur6an shi atsanake, Yayin da
brain dinshi ke tariyo mashi kalaman Batool
Ai ni ban Iya karatu ba, zan kaima unaisah ta karanta min, Abun Ya tsaya mashi aranshi, Duk da bai kalleta
dakyau ba, zai Iya bata shekaru goma sha bakwai zuwa sha takwas, a wannan shekarun bata Iya karatu ba?
Bai yi tsammanin abun yakai haka ba.

Bayan fitar batool daga dakin chief, nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, tana tafiya idanunta akan paper ɗin
daya bata, Har ta sauko down ta nufi dakin su.

Lokacin da ta shiga bata taras da kowa ba, yanke shawarar shiga toilet tayi don ta wanko fuskarta, asaman
gadon su ta ɗaura paper din, da sauri ta shiga toilet ta wanke fuskarta, fitowa tayi tareda nufar gado nasu,
isarta keda wuya ƙafarta dake sanye cikin wandon pakistan ta harba hotunan da suke yashe kan floor ba
tare data lura da su ba, nan take hotunan suka gangara ƙarƙashin gadon suka shiga ta yadda babu mai iya
ganin su.

Miƙa hannu Batool tayi ta ɗauki Paper din Ta juya da sauri ta fito daga dakin tana neman su Unaisah.

Sautin Muryoyin su Tajiyo A falo suna surutu cikin takun sauri ta nufe su, tun kafin ta ƙarasa ta hango su
tsaitsaye sun yima Unaisah rumfa hannunta ruƙe da waya tana yi masu hotuna, tun daga kan Haris, Naufal,
Javed, Sajeed, da su Azeeza jamimah, parveen and Hannah kowannansu ya sanya sutura mai kyau ajikin
shi, Unaisah ce tasa suka ɗauki wanka, don tayi masu hoto.

Babu wanda Ya lura da Batool acikin su, Camera taja hankulansu, har saida Ta furta Sunan Unaisah
tukunna suka ɗago da idanunsu akanta.
Kallo ɗaya da Unaisah tayi mata saida taji gabanta ya fadi ganin yadda kumatunta suka yi ja alamar tayi
kuka
Gaba ɗaya sun lura da yanayin Batool babu walwala,
Ruƙo hannunta Haris yai acikin nashi"Sister baki da lafiya ne"?
Shiru tayi batace mashi komai ba, Hankalinta na akan Unaisah
"Me akayi maki? Kuka ki ka yi"? parveen ce tayi mata tambayar, girgiza mata kai tayi alamar a'a.
hannah ta ruƙo hannunta tana fadin"Sis Batul ki zo ay mana hoto atare dake"
Fahimtar halin da take aciki ne Yasa Unaisah miƙa ma Sajeed wayar hannunta, bayan ya kar6a tace"ka
cigaba da yi maku hotunan, yanzu zan dawo"
Ta faɗa tare da ruƙe hannun batool, suka juya atare suka nufi ƙarshen falon inda babu mai jin su
Shafa gefen fuskarta tayi da hannu tana fadin"meya faru? Chief ɗin Ya dawo"?
Batare da batool ta furta kalma ba ta miƙa mata Paper din hannunta
da sauri Unaisah ta sanya hannu ta kar6a, A fili ta karanta.

"How did you get into my room? And why are you crying at me like I'm a monster? nayi maki wani abu
ne"?

Murmushin gefen fuska unaisah tayi"meyasa ki kuka? Faɗamin?


Tana faman jan numfashi tace"tsoro ya bani, ya damƙi gashin kaina da hannun shi kuma babu kaya a
jikinshi, short towel ya ɗaure a qugunsa.... " tun kafin ta ƙare maganar Unaisah ta tuntsire da dariya
Batool dake kallonta ganin tana yi mata dariyane yasa ta ji jikinta yayi sanyi laƙwas, in cool voice tace"Nayi
ƙauyanci"? tambayar da tasaba yi mata kenan a duk lokacin da take tunanin ta aikata ba dai dai
Dafa kafaɗarta Unaisah tayi fuskarta da murmushi tace"My own sis ba ki yi ƙauyanci ba,
"To meyasa kike min dariya"?
"Saboda kin bani dariya, meye nayi mashi kuka? Ba bugu ba zagi kin fashe da kuka kamar wata ƙaramar
yarinya ni danake so ki zama big girl, matar manya.

"Ni dai bazan ƙara komawa ɗakinsa ba, Tsoronsa nake ji sai dai ke ki je" ta faɗa tana nuna ta da hannu.
Maƙe kafaɗa Unaisah tayi"Batool ki fahimta ni bazan iya shiga dakin sa ba, bayason ana sharing aiki a part
dinsa, idan mutun ɗaya ya fara shi zai cigaba da yi har sai in shi yace ya gaji baya so, nima big guy ne ya
gaya min hakan.

Fuskarta ayamutse ta ƙare maganar tana dubanta, itama batool din kallon ta take yi, taƙi gane cewa
wayau Unaisah take yi mata.
"Ya zanyi? Ni wallahi tsoron shi nake ji, baki ga launin idanuwanshi ba kalar na danish ɗinmu, kuma ma
suna kama sosai don dai shi launin fatarshi chocolate ne"
ta fahimci Batool ta tsorata da chief, idan tana magana yatsun hannunta har kerma su ke Yi.
"A hankali zaki saba da shi, dan Allah ki daure Sister, za ki ji dadin yi mashi aiki" da wayau da dabara
Unaisah ta shawo kanta, har ta amince zata cigaba da zuwa.
"Yanzu idan kika koma ki fada mashi cewa, Big guy ne ya baki aikin kula da part dinsa, ke zaki cigaba da
daukar ɗawainiyarsa kina gyara mashi daki da kuma kai mashi abinci, haka zaki faɗa mashi,"
Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"amma ba yanzu zan koma ba ko"?
"Idan baki koma ba kayan abincin da kika bar mashi a ɗaki wazai kwashe su? Na fada maki bayason
kazanta, sannan bai saba da wahala ba komai yi mashi akeyi"
tana ƙarasa fadan hakan Taja hannun Batool suka nufi Hanyar zuwa Part dinsa, A bakin ƙofar shiga unaisah
ta saki hannunta.
Jiki na rawa Batool ta sanya hannu ta kwankwasa ƙofar,
A hankali Ta zuge, saida ta fara dadaita natsuwarta tukunna ta yi mashi sallama, shiru bai amsa mata ba, a
tsananin tsoro ce ta zura kafarta, a lokacin Harya kammala Yin breakfast dinsa, yana daga kwance saman
lallausar mattress dinsa, Ya ɗaura kanshi bisa pillow, Yayin da idanunsa ke akan Laptop dinsa da yake
operating
Yawu ta haɗiya Muryarta na rawa ta furta"am.. dama Big guy ne yace in dinga zuwa inayi maka aiki a part
dinka, kuka kuma da nayi kaine ka bani tsoro daka kama min gashin kaina"

Dakyar ta ƙare maganar, batare da ta motsa daga bakin ƙofar ɗakin ba, tamkar baisan tanayi ba, yayi shiru
yana sauraronta, babu alamun zai kalleta
Jin shiru bai tanka mata ba, yasa ta yanke shawarar shiga dakin donta kawar mashi da kayan abincin da ya
gama amfani da su.

Cikin sanɗa take yin tafiya kamar 6arauniya, duk a tunaninta bacci yake yi saboda idanunsa dake a lumshe
batasan cewa idonshi biyu ba kuma yana kallonta, yayi mata hakanne saboda baison Ya ƙara firgitar da ita,
tunda ya fahimci ruɗaɗɗiyace ita.

Tana ƙarasawa gaban table din tayi saurin kwashe kayan abincin, sam bata yi tunanin ɗaukar mayafinta
data gani akan pillow ba saboda saurin da take Yi, bayan ta fita abakin bene ta tarass da unaisah tana
jiranta.

Murmushi ta saki tare da nufarta tana fadin"Sister, nayi mashi bayani amma kamar bacci ma yake yi, ga
tray din abincin na dauko Ina zamu kai shi"?

"Nikaina bansan ina ne kitchen dinsu ba," unaisah ta fada tare da kar6ar tray din"bari naje na nemo
kitchen din, Ki tafi falo," amsa mata tayi da toh, da sauri Batool ta sauka daga kan benan ta nufi falo.
Unaisah tana cikin tafiya, Tajiyo motsin buɗe kofar Falon, su biyu suka shigo Boss man tare da Big guy,
wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta, Allah Ya taimaketa, Ta kar6i tray din daga hannun Batul da kuwa Big
guy saiya gane ba ita taje yima chief aiki ba.
Tunkararsu tayi fuskarta dauke da fara'a tace"Yalla6ai nagama yi mashi aikin, A ina zan ajiye tray din"
Big guy yaji dadin Jin hakan daga gareta, alamar jinjina yayi mata da yatsan hannun shi kafin Yace"ai
tunda naga kina yin fara'a raina ya bani cewar Kin samu kar6uwa awurin chief, bani labari daya ganki meya
ce maki"? boss man dake sauraronsu murmushi ne dauke akan fuskarshi dake asanye da facemask.
"Bayan na gaishe dashi Ya amsa min, sai nace mashi me yakeson ci in zuba mashi, to daya fada min saina
zuba mashi na tsaya har ya cinye na ƙara mashi wani, kusan fa plate uku ya cinye ya kuma sha Tea" da
mamaki Big guy ya maimaita kalmar plate uku!
"Kina nufin chief shi yaci abinci har plate uku"?
Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh, saboda karfin hali irin nata ko tsoron yace zai buɗe warmer din batayi ba
Boss man yace"wow, My daughter kin ciri tuta, ai ni tunda nake da chief bai ta6a yarda wata mace tayi
mashi aiki a part dinsa ba saboda bayaso"
Sai faman washe masu baki take Yi,
"Ga tray din abincin, Yanzu saura aikin kai mashi lunch ko"? Ta tambaya tana kallon big guy
Boss man yace"a'a, Sai kuma dinner, idan yakai Rana bai ci breakfast dinsa da wuriba to baya cin lunch na
safen daya ci ya ishe shi sai kuma Dinner dinsa.
Wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta"Allah Yakaimu daren Lafiya" suka amsa mata da ameen, daga bisani
big guy Ya kar6i tray din hannunta Yace tabiyo bayanshi zai nuna mata kitchen dinsu.

Atare suka tafi shi kuma boss Ya wuce dakin chief, Bayan Ya bashi iznin shiga, Yana zura kafarshi karaf
idanunsa suka sauka aka Mayafin dake yashe kan pillow, farat ɗaya ranshi ya bashi cewar Na unaisah ne da
ta shigo kawo mashi abincin, zuciyarshi ta musa da cewar ba mayafinta bane, saboda ita yaganta da mayafi
tayi rolling,! Kenan na wanene wannan"!
A hankali Yakai hannu Ya ruƙo mayafin Yana dubanshi Kafin Ya kalli chief dake a kwance Ya lumshe
idanunsa

"Yalla6ai barka da hutawa"

In a calm voice Ya amsa mashi yawwa


"Naga missed call dinka awayata ina fata lafiya"?

"Alright. I'm just reminding you about the plan we have for Hateem's farewell dinner tomorrow.

Murmushi Boss man Ya saki"Ina sane da komai Yalla6ai, Kuma in sha Allah babu wanda zaisan da zancen
zuwanmu tare da Yaran, ba zata zamuyi masu, Sai dai yalla6ai naso ace hada Danish zamuje, ko dan
saboda Prime minister Hateem, Ina so su gana da junansu, har magana nayi ma sheikh imam akan ko zamu
iya kaishi asibiti aduba lafiyarshi sai yace min babu abunda likitoci zasu Iya yi mashi a halin da yake aciki"
cikin sanyin murya ya kare maganar
A hankali chief Yaɗan ware idanunsa tare da cewa"nima nayi fatan hakan sai dai har yanzu babu wani
cigaba a lafiyarshi, Allah Ya bashi lafiya"
Boss ya amsa mashi da amen, kafin Ya fuce daga dakin hannun shi ruƙe da mayafin daya tsinta.

..shigar shi falo keda wuya, Idanunsa suka sauka akan Batool, dake sanye da Pakistan launin Mayafin
hannun shi, girgiza kai yayi don ya riga da ya gane itace taje dakin Chief Yi mashi aiki ba Unaisah ba, baiyi
mamakin hakan ba saboda Ya riga daya san halin kayansa, idan bata son yin abu babu wanda Ya isa ya
tursasa mata akan tayi shi, shiyasa da big guy ya bata aikin kula da part din chief sai ta tura Batool don tayi
a matsayin itane taje, dole ya ɗauki matakin akan hakan don bayason ya samu tangarɗa akan alƙawarin
daya daukarwa kanshi.
Batare da Batool Ta luraba, Ya daura mata mayafinta saman kanta, Kafin Ya nufi su sajeed dake ta faman
daukar hotuna Daya bayan ɗaya ya rungume su sai dadi suke Ji yazo, Nan fa suka fara daukar hoto tare da
shi.
*🌹ANEELARH❤*

A kwance take saman gado tana sharar baccinta, tun da ta sallami baby junaid ya tafi school ta koma kan
gado ta kwanta bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita,
Can cikin baccinta ta soma jin ana ƙwanƙwasa ƙofar dakinta, da wata irin kasala ta farka tana yin miƙa,
doguwar rigar jikinta duk ta yamutse, saukowa tayi daga saman gadon ta nufi ƙofar tana tanbayar wanene
Daga waje muryar Ana ta amsa mata da cewa"Aunty ni ce"
Buɗe ƙofar tayi tare da bata iznin shigowa daga ciki.
A hankali ta zuro kafarta Jikinta sam babu kuzari ta rame tayi duhu, v-neck shirt da pencil skirt ne ajikinta
black and white, ta daure guntun gashin kanta da ribbom.
"Aunty barka da safiya, Ina fata ban takura maki ba, Na katse maki baccin ki" ta fada tana faman duƙar da
kanta ƙasa
"Babu komai, Ina fata dai lafiya kike ko"? Cikin kulawa tayi maganar
"Lafiylou, dama nazo ne in ƙara yi maki godiya...." kafin ta ƙare maganar Aneelerh ta ɗaure mata fuska
tare da cewa"Ana bana son abunda kikeyi min, na fada maki bana son godiyar da kike yi min amma kinƙi ki
daina, "
Cikin sanyin Murya tace"kiyi hakuri Aunty idan na 6ata maki rai," dakyar ta ƙare maganar saboda kukan
daya ciyota nan take ta fashe mata da kuka.....

Lamarin ya ɗaurema Aneelerh kai Daga maganar batason godiya sai kuka? Anya kuwa ba wani abunne na
daban ke damun Ana ba?
Dafa kafaɗarta tayi da hannu daya"ya Isa haka, bana son kukan nan, Idan wani abu ke damunki dan Allah
ki fadamin kada ki ji komai, In sha Allah zan yi ƙoƙarin ganin na taimaka maki mun magance koma
menene".
Yayin da Ana ke kallonta idanunta sun kaɗa jawur, fuskarta ta jiƙe sharkaf da hawaye,
Muryarta na rawa ta furta"Aunty Aneelerh bakomai"
Girgiza kai Aneelerh tayi"wallahi ban yarda dake ba Ana! Nifa ba haihuwar yau bace, Duk wanda Ya kalleki
sai ya gane baki da koshin lafiya, kuma da akwai wani abu dake damunki, Don haka ki fada min kawai!
Rashin. fadamin shi zaija maki yin danasani"!
Su6ul da baka tayi wurin furta"kona faɗima babu wanda zai yarda dani, zai yi wuya afahimce ni"!! Rass
Aneelerh taji gabanta ya fadi, muryarta da alamun ruɗu ta furta"Meke nan"?
A firgice ta zare ido tare da yin saurin cewa"babu komai, babu komai! Na tafi sai anjima" juyawa tayi da
sauri ta nufi ƙofar dakin zata fuce, sai dai kafin ta haura kafarta Aneeleeh tayi saurin ruko hannunta ta juyo
da ita suna fuskantar juna
Wani irin kallon kallo suke jefa ma juna batare da sanin ma'anar hakan ba
"Ana! Ki faɗamin meke damunki? Menene kike son fadamin wanda kike tunanin babu wanda zai yarda
dake?dan Allah kada ki 6oye min, idan ma sirri ne nayi maki alƙawarin bazan fada ma kowa ba"
Numfashi Ana taja, gaba dayanta a tsoroce take babu kwanciyar hankali atare da ita
"Babu komai!Nabar Girkin dana daura a kitchen zanje na duba" tana karasa fadan hakan ta zame
hannunta daga ruƙon da Aneelerh tayi mata, da sauri ta fuce daga ɗakin.
Bayan fitarta, Hankalin Aneelerh Yaƙi kwanciya, Ta jefata a ruɗani, ga wani bugun zuciya da take ji a
kirjinta.
kalmar Da ana ta fadi ta tsaya mata aranta, da tace kota fadi babu wanda zai yarda da ita meke nan"?!
Tayi zurfi acikin tunaninta Wayarta dake ajiye kan side drawer ta soma ruri, a hanzarce ta juya ta nufi
drawer ta dauki wayar, sunan zahra ne ya bayyana akan screen din wayar,
Bayan ta ɗaga kiran ta kara a kunne
kafin tayi sallama Muryar Zahra ta katse mata hanzarinta
"Auntyna ya ki ke ya gida"?
"Lafiyalou Sister, Bakya a gidan ne"?
"Na tafi wurin aiki, har dakin ki na shigo don inyi maki sallama sai na tarar kina bacci, bana so na takura
maki shiyasa ban tada ki ba"
Shiru Aneelerh tayi tana sauraronta har ta ƙare maganar babu alamun zata tanka mata, Jin shiru yasa
zahra cewa"auntyna kodai baccin bai ishe ki bane? Naji kinyi shiru?
Numfasawa tayi tare da samun wuri gefen gado ta zauna tukunna ta samun natsuwar yi mata magana
"Ban jima da farkawa ba, Har yanzu kasalar baccin bata sake ni ba, shiyasa zaki ji ni wani iri"
"Kiyi wanka zaki ji dadin jikin ki" acewar zahra
"Zanyi in sha Allah, yanzu dai fada min meya faru ne kika kirani awaya? Naji muryarki kamar akwai farin
ciki atattare dake"? Ta fada tana murmushi tamkar suna atare da juna
"Kamar kin sani auntyna, shiyasa nake ƙara ƙaunarki saboda kina fahimtata fiye da kowa, abunda Ya faru
Ina awurin aiki, Hajiya sarah ta kirani awaya.... " a ƙagare Aneelerh tace"me tace maki"?
"Ta faɗamin suna buƙatar za'ayi masu decoration gobe friday, Za suyi Farewall dinner, Na bankwana da
prime minister Hateem, Jibi zai bar ƙasar tare da Iyalansa zasu koma Canada"

Wani irin farin cikine Ya bayyana akan fuskar Aneelerh"Zahra na tayaki murna, Alkhairi ne ke bibiyarki,
hajiya sarah bata manta dake ba, Ashe kina aranta"
Sautin murya zahra da annushuwa tace"bana tunanin zan iya runtsawa a daren yau, saboda farin cikin zan
halarci family dinner dinsu, wallahi aunty naso ace tare dake zamu je amma nasan bamai yiwu bane tunda
nima tace daƙyar tayi mana hanyar da zamu samu halartar taron, saboda tsaron da za'a sanyama Estate
din a goben"
"Kada ki damu zahra, Nima inason zuwa amma koda nasamu damar da zan biki bazan je ba, idan ma
kikaje kamar naje ne, bani da damuwa nasan zaki bani labarin komai daya faru a shagalin, Harma Ki dauko
min hotuna da videos don inga Ƴan family din Obinna"
Zahra tace"in sha Allah auntyna, yanzu zan koma bakin aikina, Sai na dawo gidan ki kula min da kanki,"
"Nima ki kula min da kanki sai anjima" baya sunyi sallama Aneelerh ta ajiye wayar saman pillow, ta miƙe
da sauri ta nufi toilet ta shiga ciki, after some minutes ta fito daga wanka, shaf shaf ta canza suturar jikinta,
ta sanya
Primcess vest tare da wrap skirt, ta ɗaure kanta da mayafi, da sauri ta fito daga dakin ta nufi bedroom din
mami.

Tunkafin ta shiga ta soma jiyo muryarta tanayin karatun kur'ani, da sallama ta shiga ciki, a zaune ta taras
da mamie saman darduma sanye da hijab, idanunta akan kur'anin da take karantawa, gefen gadonta ta
zauna tana jiran ta kai Aya.
"Aneelerh kin tashi daga baccin lalacin"? Mami ce ta faɗa tana dubanta
Murmushi tayi mata"mami bansan baccin ya ɗauke ni ba,"
"Na gaji da ganinki zaune a gida, zan tuna ma Abie dinki maganar aikin da Uncle ɗan Iya yace zai sama
maki a asibitin Obinna, Indai dagaske yake zai yi maki hanya"
"Mami nikaina nagaji da zama babu aikin, Dan Allah ki tuna mashi idan Ya dawo su yi magana asama min
aikin in fara zuwa"
"In sha Allah zanyi mashi magana, ai nafi son ganin cigaban ki"
Murmushi suka sakar ma juna
" shiru sukayi kowa da abunda yake saƙawa acikin zuciyarshi.

"Dama zuwa kikayi don kiyi ta kallona"? Mami ce tayi maganar fuskarta da murmushi.

"Dangane da Ana ne, mami Yarinyar nan akwai abunda ke damunta, taƙi ta sanar dani, ina ɗaki ta shigo
daga yi min godiya akan kudin da muka bata ni da zahra, sai nace mata bana so tana min godiya kawai sai
ta fashe mini da kuka.... " gaba ɗaya Aneelerh ta sanar da ita abunda Ya faru.

Mami ta jinjina kai tana dubanta tace"tuntuni fa na lura da canzawarta, tayi baƙi ta rame kamar bata da
koshin lafiyar, har tambayarta nayi meke damunta sai ce min tayi babu komai lafiyarta ƙalau Ni bansan ya
zamuyi da ita ba" Mami ce ta fada tana mai nuna damuwarta.
"Mami yakamata ki ja ta a jiki kiyi mata magana wata'ƙil ke ta faɗa miki tunda kin haifeta zata ji tamkar
mahaifiyarta ce keyi mata magana"
Shiru mami tayi na wani lokaci kafin tace"Toh, zan jaraba yi mata magana mu ji meke damunta"
"Tana a ina ne yanzu"?
"Ta fadamin zata je kitchen duba girkin da ta daura"
Mikewa mamie tayi"muje wurinta Inji" da sauri aneelerh ta miƙe ta dauki kur'anin mami da cazbaharta ta
ajiye su a ma'ajiyarsu, Kafin Tabi bayan ta suka fito daga dakin,

Adai dai Lokacin Ummi ta fito daga daki sanye da dogon Hijab taci karo da su atare
Fuskarta da fara'a tace"Uwa da ɗiya ina zuwane haka"
"Wurin Ana zamuje, Yarinya duk ta rame tayi baƙi, Taƙi fada ma mutane abundake damunta ko ke baki
Lura bane"?
Jim ummi tayi kafin tace"kamar kun shiga zuciyata, fitowar nan da nayi dakin ki nake shirin zuwa don inyi
maki magana game da ita, na jima da lura da hakan, duk ta canza ba kamar yadda nasanta ba farkon
zuwanku gidan nan, Yanzu tayi baki ta rame babu ƙugun nan nata da kirjinta duk sun zube kamar mai fama
da wata lalura,"
Aneelerh tace"abun da yafi ɗaure min kai da ita ummi, kwata kwata bata da natsuwa, ko magana take yi
yatsun hannayenta zaki ga suna kerma kamar wadda sanyi ya kama"
Ummi tace"Muje muji meke damunta," gaba dayansu suka nufi kitchen din gidan, Koda suka shiga basu
ganta ba, Har ta kamma aikace aikacen da take Yi, tayi wanke wanke tayi mopping dinsa.
Ummi tace"baiwar Allah gata da ƙoƙarin yin aiki, banji dadin halin da take aciki ba"
Fitowa sukayi daga kitchen din suka nufi bedroom din Ana.
Abakin Door room din Suka dakata da yin tafiyar, Aneelerh ta kwankwasa mata kofa, kusan sau uku Tana
buga kofar kafin suka jiyo motsinta ta cikin dakin, buɗe kofar tayi tare da leƙowa tana kallon su
Fuskarta a yamutse, idanunta sun yi jajir da su.
Murmushin yaƙe ta ƙaƙalo akan fuskarta, cikin girmamawa ta gaishe dasu tana ƙoƙarin 6oye damuwarta
"Wurin ki muka zo mu shiga daga ciki" mami ce tayi maganar, da sauri Ana ta matsa masu hanya suka
shiga dakin, Daga tsaye suka tsaya tace mashi su zauna saman gadonta
Ummi tace"ba zama ya kawo mu ba, zuwa mukayi don muji meke damunki Ana, meke faruwa dake ne?
Duk kin canza mana kin rame kinyi baƙi! Baki da lafiyane"?
La66anta na kerma ta furta"babu komai lafiyana lau madam, wallahi babu abun dake damuna"
Cikin kwantar da Murya mami tace"Kada ki 6oye mana komai, Ki ɗauke mu tamkar iyayenki, dan Allah ki
fada mana damuwarki, In sha Allah zamu share maki hawayenki,
Mami na rufe baki Aneelerh tace"Ana please kada ki bani kunya, Saboda mun ɗauke ki da daraja shiyasa
muka damu da damuwarki, Kina gani dai mami da ummi da kansu suka zo dakin ki yau duk don saboda sun
damu dake, Idan kika ce babu abunda ke damunki, kinyi mana karya saboda babu yadda za'ai ki rame
batare da ciwo ko wani abu ba, dole da akwai wani abu da baki son mu sani"

Gaba ɗaya sun ɗaga mata Hankalinta, Cikin kwantar da murya suke yi mata magana amma sai ta dinga
ganin kamar suna yi mata faɗane, Dafe kanta tayi da hannu biyu tana ambaton sunan Allah tamkar
musulma.
Muryarta na rawa take fadin"Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, na roƙe ku ku ƙyaleni, ku tafi kawai, nagode
da kulawarku agare ni,nagode"
Hankulansu atashe suke ambaton sunanta haɗi da tambayarta meke damunta.
Gaba ɗaya ta rikice masu, sai sambatu takeyi tana rokonsu akan su tafi subar dakinta, a karshe ta watsa da
gudu ta shige toilet taja ƙofa ta datse. 😳

Kallon juna suka somayi da tsantsar mamaki da rudani aka fuskokinsu,


..mami tace"to fa, Anya kuwa lafiya"?
Ummi tace"bafa lafiya, Ni dai inaga kamar hada aljanu ke damunta.
Jikin Aneelerh yayi sanyi, tun datake da ana bata ta6a ɗaga mata murya ba sai yau da ta rikice masu tana
korarsu daga dakinta, tabbas babu lafiya!
"Yanzu ya zamu yi da ita"? Mami ce tayi maganar,
Ummi tace"yakamata mu sanar da su Abie, dangane da halin da take aciki"
Sun jima a dakin Ana suna yi mata magiya akan ta fito daga toilet, amma taki fitowa a karshe dole suka
hakura suka bar mata dakinta..

*Daular Obie Estate*

Gaba ɗaya Manyan matan Family din sun hallara a gidan Hateem domin yi masu bangajiyar tafiyar da su ka
yi, musamman saboda zuwansu akayi masu shimfiɗa ta alfarma a katafaren Garden din gidan hateem,
garden ne na alfarma cike ya ke da tsiro da furanni launuka daban daban masu ban sha'awa, ga wata irin
ni'imtacciyar iska mai ratsa fatar jikin mutun, daga can cikin garden din akwai wani ƙaramin tafki wanda ke
acike da tsaftaccen ruwa launin blue sky, inda fararen agwagi suke shawagi acikin sa, an tsara komai da
kyau, a tsakiyar garden din akwai wani katafaren wurin zama, kewaye da ciyawar da aka yi wa ado,
Lallausar darduma ce mai wani irin laushi a jikinta irin ta sarakuna, An kewayeta da tuntuye, yayin da suke
a zaune kowaccensu ta ɗauki wanka na kece raini na mutunci, mata ne masu duniya, ajin farko, waɗanda
suka gaji arziƙi tun kaka da kakanni, wayayyune masu ji da ilmin da Allah ya basu, mace ta farko Gimbiya
mujeedat ce a kishingiɗe saman dardumar tayi shiga ta alfarma cikin tsadaddiyar Arab gown launin Ash
colour anyi mata adon sparkling stones, masu ɗaukar ido, ta yafa mayafin saman kafaɗarta, baƙar sumar
kanta ta sauko har saman dardumar da suke, daga gefenta First Lady ce Hajiya Malikat Sarauta ƴar sarkin
Yarbawa jihar Lagos, Mace mai ji da kanta, mahaifiyar Chief Owais, A launin fata chocolate colour ce, taji
hutu, bata da yawan fara'a, tana da ƙaramin baki ga dogon hanci, idanunta masu kyan gaske sunyi kama da
Asian eyes, kayan jikinta Na yarbawa ne, Wrap around skirt ta sanya tare da farar shirt, anyi mata naɗin
head akanta, tun daga kan wuyanta har hannayenta adone na zinarai, bayan Hajiya Malikat sai Hajiya
Laurat uwar ji da izza, ƙanwar Alhaji Musa, Idan ka gansu atare da Hajiya malikat baka ta6a gane cewa
kishiyoyine saboda kowaccensu bata ɗaukar raini, ita malikat arziki da sarauta ta gada, ita kuma Laurat
Arziƙine gare su na fitar shari'a, sai dai daga ganin fuskarta zatayi rashin mutunci idan aka ta6a, daga ka
kalli fuskarta zaka shaida ƙanwar Alhaji musa ce, Kamanninsu har sun 6aci da shi, hatta launin fatarsu kala
ɗaya ce, Hausa fulani ce, ta ɗauki wankan shadda launin dark brown anyi mata ado, Wuyanta na asanye da
sarƙar diamond, haka yatsun hannayenta zabban diamond ne masu kyalkyali da daukar ido.

Mace ta gaba, Hajiya Madina ce matar senate Lateef, barumaya ce, tana da hasken fata da tarin sumar kai,
hatta gefe da gefen fuskarta akwai tsagensu na rumawa, Tana da kyau iya gargado sutura tanayi mata
kyau, daga ganin fuskarta tana da kyakkyawar zuciya ko ba'a faɗa maka ba, Hadaddiyar atampa chiganvy
ce a jikinta tabi shape din jikinta, Itama ta dauki nata adon na zinarai.

Bayan Ita sai matar His excellency Deen, Hajiya Jamila, Bafullatanar usili ce, Ƴar sarkin Jihar adamawa
state, Fara ce jawur da ita, tsabar kyanta kamar ba'indiya.

Daga ita sai Matar Abdul Razak, Her excellency Muhibbat, Shuwa Arab ce ƴar mai duguri, fara doguwa ga
gashi har gadon baya, family dinsu sunyi ƙaurin suna a 6angaren Arziƙi, Mace ce mai ji da kyawu da
wadatar arziki, tana sanye cikin shiga ta bubu gown ta lace, ta kashe ɗaurin kallabi, awarwaron dake a
hannayenta na zallar zinari ne.

Mace ta karshe basai nayi maku bayaninta ba, Kun riga da kun santa, bakowa bace face Aunty Masifatu
Hajiya saratu, mutuniyar, wankan material ta ɗauka, gaba ɗaya ƙamshin turarensu Ya karaɗe iskar garden
din hakan ba ƙaramin ƙara ma yanayin ni'ima yayi ba.

Daga tsakiyarsu Katafaren Faranti ne na azurfa, mai girman gaske wanda masu hidima suka kawo masu shi,
An cika shi da Soyayyun Kaji jar suya, da kayan marmari nunannu, tare da juice masu sanyi.

Fira su ke yi atsakaninsu cikin harshen turanci tamkar ba su son furta magana.


"Naji daɗin ziyarar da kuka kawo min, kuma naji daɗin ganinku, Sai naji dama A ƙasar nan nake zaune,
saboda mu runƙa sada zumunci a tsakaninmu akai akai" gimbiya mujeedat ce tayi maganar tana binsu da
kallo ɗaya bayan ɗaya.
"Ni kaina naji dadin haɗuwar da mu ka yi, bazan Iya musalta farin cikin da nake a ciki ba, Allah Ya ƙara
Haɗa kawunanmu da zuri'armu" hajiya malika ce ta fada, tare da kai hannu ta ɗauki Yankan Tufa tana sha.
"Canada tamkar gida take awurina ina yawan zuwa saboda business din da nake yi Acan, In sha Allah zan
dinga zuwa Ina kawo maku ziyara, Har sai kun gaji da ganina" hajiya Laurat ce ta faɗa tana duban gimbiya
mujeedat, murmushin gefen fuska Mujeedat ta sakar mata tare da lumshe idanunta.
Hajiya Jamila tace"naji kamar kuna Bankwana, Tun Kafin jibin tayi ko kun manta da family dinner da zamu
Yi a gobe?
Hajiya saratu tace"Kamar kin shiga zuciyata, nima tun ɗazu maganar da nake ta so Inyi masu kenan, ai
gobe muna da gagarumin shagali In Allah yakaimu da rai da lafiya, dole kowa ya halarta" ta faɗa tare da kai
hannu cikin faranti Ta yago cinyar kaza ta tura abaki tana tauna
Hajiya jamila na dariya tace"daɗina dake saratu baki wasa da cikin ki, Zaman mu anan kin cinye fiye da
rabin kaza, shiyasa gaki nan kullim ƙara ƙiba kike yi,"
"Kinsama kanwar nan tawa ido" acewar Gimibiya mujeedat.
"Kibarni da ita aunty, da duk wani mai sanya min ido akan cin abincina, nasan maganinku, zanyima
yayyena magana su ƙara maku kishiyoyi, ƙwara ku lalla6ani ku dinga lallashina idan ba haka ba kun san
sauran" dariya su ka yi gaba dayansu,
"Meya yayi zafi, nayi shiru bazan ƙara tanka maki ba, Ci ki ƙoshi, Idan ma kina buƙatar ƙari zansa akawo
maki" hajiya jamila ce ta faɗa tana tura mata farantin agabanta, Hajiya sarah tayi dariya da zolaya tace"Bari
naja bakina nayi shiru, naga wasu sun fara haɗe min fuska saboda nayi maganar kishiya"
Murmushi kowannansu ya saki,
Gimbiya mujeedat tace"ko kaɗan banji fargababa, because I know who my husband is. He doesn't want to
remarry; I'm enough for him." She said proudly and gently.

Hajiya laurat tace"ai dama irinku ba'ayi maku kishiya, wane mutun, ballanta kuma mijinki da gaba ɗaya
rayuwarsa acikin turawa yayita, ba lallai Yana da wannan ra'ayin ba, tun da suma mace ɗaya su ke aure"
Her excellency Muhibbat ta murmusa tare da cewa"ni dai koban fada maku ba kun riga da kun sani,
ba'ayi mana kishiya, Mijina bai ta6a gigin kula wata ƴa mace ba"
Hajiya malikat dake sauraransu tace"nima nan bada jimawaba zansa mijina yayi waje da wata" ta faɗa da
zolaya tana kallon Hajiya laurat, dariya suka sanya gaba ɗayansu.
Hajiya Laurat tace"Ni da sharafudden mutu karaba takalmin kaza, badai mutun ba sai Allah, me raba ni
da shi sai mutuwa"
Yamutsa fuska Hajiya malikat tayi"alfarma fa nayi mashi ya aure ki, saboda yana jin shakkar tunkarata da
zancen auranki yasa shi ƙin sanar dani sai dai naji daga saman an shafa fatihar auranku, wato yanzu kin
samu wurin zama shiyasa har kike da bakin fadin mutu karaba takalmin kaza," cikin raha suke Yin firar tasu.
Hajiya Muhubbat tace"ai ni ina mamakin dauriyarku da har kuka Iya haɗa kanku, babu mai jin sirrinku,
Gaskiya kun burgeni, amma ni fa wallahi bana tunanin zan Iya zaman lafiya da kishiya, shiyasa tun kafin
abdul razak Ya aureni saida muka ƙulla yarjejeniyar bazai yi min kishiya ba, mahaifina ma saida Yaja mashi
kunne akan hakan"

Jinjina kai Hajiya madina tayi'lallai abun naki azimin ne, ni kuwa dai bana jin zan Iya hana Mijina Yin aure,
tun da Allah ya Halasta masu auren mata har huɗu, Idan Ya nuna yana so zan goyi bayanshi, kuma Idan Ya
aurota zamu yi zaman lafiya da ita idan har ba ita bace ta bijirema hakan ba"

Wani kallo her excellency Muhibbat Ta yi mata"babu zuciya a kirjinki, Shiyasa bakya kishin mijinki"
"Bawai don bani da kishi bane, nafiso idan ma kishin zanyi inyi irin na matan manzon Allah SAW, ni fa da
ace mijina Yana bin matan banza ƙwara ya auro mata uku a lokaci ɗaya, amma idan nace zan tauye mashi
hakkin shi in hana shi auran abunda yake so to fa zan jefa shi ga halaka ne, sannan ban Isa In hana
zuciyarshi son wata ƴa mace ba"
Jinjina kai su kayi jin bayanin Hajiya madina badan sun fahimce ta ba.
Hajiya Jamila tace"godiya yakamata muyiwa Allah daya bamu mazaje nagartattu, nagari masu ƙaunarmu
tsakani da Allah, Har Yau Ina alfahari da kasancewata ɗaya daga cikin surukan dattijon Arziƙi, Allah Ya saka
mashi da gidan Aljanna, Ya haifa mana zaratan maza sadaukai, Tsakaninmu dashi sai son barka" Murmushi
hajiya saratu tadinga saki jin ana yabon mahaifinsu, wani irin dadine Ya lullu6eta
Hajiya Muhibbat tace"Ai Zuri'ar Obi komai sun haɗa Allah Ya basu, kyau, nasaba, ilmi, wadatar arziƙi,
ƙawayena har tambayata sukeyi wai babu sauran ƴa'ƴan shi da suka rage? Don su aura suma su shigo daga
ciki, nace masu sai dai Jikokinsa ƴa'ƴan cikin su in suna so" dariya sukayi gaba ɗayansu.

Bayan sun lafa, kowaccensu Ta sanya hannu a faranti ta dauki abunda take son ci, wasu nama Wasu kayan
marmari wasu kuma lemu suke sha.

_______________________✍️

A hankali Motar Sir Mubarak Tashigo Gidan Hateem, A Harabar ajiye motoci yayi parking dinta, fitowa yayi
daga front seat ya zagaya ta back seat Ya bude ma mom turai kofa, A hankali ta fito ta sanya atampa riga da
skirt sunyi mata kyau, Ta yafa mayafi saman kafadarta, yayin dashi kuma yake asanye da Shadda.
Kallon juna sukayi, da sauri ta kau da idonta gefe, hannunta ruƙe da ƴar handbag dinta
Muryarta ƙasa ƙasa ta furta"dan Allah kabarni in koma gida, bansan meyasa ka tursasa min akan inzo
gurinsu ba, na faɗa maka basu ƙaunata, wallahi ci mun mutunci zasuyi"
Ɗaure mata fuska yayi"kar na kuskura nasake jin kin furta maganar nan! bana jin dadin yadda kike ware
kanki daga cikinsu! Dame suka fi ki? Tsoron su kike ji? Baki Iya mayar masu da martani in suka gaya maki
magana"?
Tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace"Ina da banbanci
dasu, Har Yau har gobe sunƙi mantawa da matsayina agidanku, Suna yi min kallon ƙasƙantacciya Ƴar aiki,
babu abunda Ya canza"

*DAGA ALƘALAMIN HAFSAT BATURE✍️


*_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_

‫🔥✊💋سجن القدر‬

~Takun Ƙarshe🔥~

‫😘💘💋قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة‬

An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘

Daga alƙalamin Boss Bature💋✊

__________________________✍️
Tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace"Ina da banbanci
dasu, Har Yau har gobe sunƙi mantawa da matsayina a gidan ku, Suna yi min kallon ƙasƙantacciya Ƴar aiki,
babu abunda Ya canza"

Ya fahimci baƙaramin jin shakkarsu ta ke yi ba, muryarshi a kausashe ya furta"kamar ba matar Sir
mubarak ba, kin bani kunya, wlh daga yau zan baki last warning, idan na kuskura na sake ganin kin zubda
hawayen ki ko kina jin tsoron wani acikin su, sai na sa6a maki" ƙiris ya rage ta fashe mashi da kuka, jin
yadda yake mata magana da faɗa.
Zare mata ido yayi"ina fata kin fahimce ni"? Muryarta na rawa furta"yea..h" ruƙo hannunta yayi acikin
nashi, yaja ta a hankali suka nufi katafaren falon gidan, ko da su ka shiga masu yi masu hidima suka taras
sai kai komo su ke yi a cikin falon, ganin sir mubarak yasa suka yi saurin gaishe su cikin girmamawa bayan
ya amsa masu ya tambayi ina gimbiya mujeedat.

Ɗaya daga cikin hadiman ce ta bashi amsa da cewa"su na a garden"

Damƙa mata hannun Turai yayi wadda tuni jikin ta yayi sanyi lakwas.

Cikin kuwala yace da hadimar "she's my wife, inaso ki rakata wurin su, ki bi min ita a hankali' murmushi
hadimar tayi aranta ba karamin burgeta yayi ba, daga gani yana daraja matarshi
"In sha Allah yalla6ai" ta faɗa tare da ruƙo hannun mom Turai suka nufi ƙofar fita daga falon, tana tafiya
tana waiwayon shi, kamar yadda shima yake kallon ta har sai da ta 6ace ma ganin shi kafin ya nufi ɗakin
prime minister.

Jin motsin shugowar Sir Mubarak ne Yasa shi Buɗe idanunsa Yana dubanshi
Daga gefen gadon shi Ya zauna Yana fadin"ƙanina Ya Gajiyar tafiya," miƙewa Hateem Yayi da wata irin
kasala Ya zauna Yana fuskantar Sir mubarak
"Gajiya tabi Jiki, yayana nakaina, kaima ya gajiyar taka"
Da zolaya Sir mubarak Yace"nifa Sojane tafiyar da mukayi bata isa ta gajiyar dani ba" murmushi Hateem Ya
sakar mashi
Cikin kulawa Sir mubarak Yace"Meke damunka? Naga yanayinka ya canza ko baka Jin dadine"?
Cikin sanyin Murya Yace"lafiyana lou" ya fada yana kokarin danne damuwarshi
"Nifa Yayanka ne Hateem, baka Isa ka 6oye min damuwarka ba, dan Allah ka faɗamin, Idan ba haka ba
hankalina bazai kwanta ba, na fahimci tun da kazo ƙasar nan ka canza gaba daya"
Ruƙo hannun sir mubarak Yayi acikin nashi ya damƙe shi sosai.
Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta"bansan ya zanyi ba da ƙaunar yaron nan na wurin Owais, shine silar duk
wani hali da nake aciki, Har mafarkin shi nake Yi" ya faɗa yana mai sanyaya muryarsa.

"Allah Ya jarabce ni da son shi, bani da alaƙa da shi amma sai nake jin kamar ni na haife sa, na faɗa maka
ne saboda kana ɗaya daga cikin waɗanda suke fahimtana"

Tun da ya fara magana Sir mubarak yake binshi da kallo mai nuni da tausayawarsa gare shi, yasan
bakomai ke damun shi ba face rashin samun ɗa namiji, shiyasa ya kwallafa rai akan yaron da owais ke ruƙo.

"Ban ta6a ganin shi ba, amma saboda kai In sha Allah zanje har gidan owais ɗin In ga Yaron zuwa Gobe In
Allah Yakaimu"

"Yana kama dani, tamkar Anyi photocopy din fuskana, hasken fatane kaɗai Ya banbanta mu da shi,
Fatarshi farace Sol, tamkar Nazli, Dalilin dayasa kaga nashiga halin nan, bana son inbar ƙasar nan batare da
yaji saukin lalurar shi ba, ina matuƙar son mu gana dashi, sai dai na rasa wannan damar da nake da ita,
baba ya hanani kusantar shi, Gidan Owais dinma An hanani zuwa saboda shi, dole In hakura" cikin
karyayyar murya ya faɗa yana faman sauke numfashi.
Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, yana neman rudar dashi, Aranshi Ya ayyana wannan wata irin
kaunace haka? Abu kamar aikin asiri Allah na tuba.

Lallashin shi ya somayi yana kwantar mashi da hankalin shi, Har saida Yaga yafara sakewa tukunna suka
cigaba da tattaunawa a tsakanin su.

__________________✍️

Lokacin Da Hajiya Turai, Ta shigo garden din tare da Hadimar data rakota, Tunkafin Ta ƙarasa inda su
Gimbiya mujeedat suke, Hajiya laurat ta rafka salati tana fadin"wa nake gani kamar Harriet ƴar aikin gidan
baba obie" ta kira ta ne da ainihin sunan ta, gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta, Hadimar data rakota Harta
Juya ta nufi hanyar komawa gidan, Jiki asanyaye turai take tafiya tana tunkarar su.

Wani irin Matsiyacin kallo Hajiya laurat da Hajiya saratu suke watsa mata.

Tuni tasha jinin jikinta, da hannu Hajiya laurat ta nunata"ke! meya kawo ki nan? Ko kinga sa'ar Yin ki ne"

Shiru tayi bata tanka mata ba, Hajiya saratu ta kwashe da dariya Tana fadin"shisshigine da kutsu irin na
ɗan talaka, malama wani tsautsayinne ya kawo ki wurinmu? Ko aiko ki akayi don ki yi mana hidima ne"?

Cike da shaƙiyanci her excellency Muhibbat tace"jibarta kamar wata mutuniyar kirki, ita kanta ta raina
kanta shiyasa take jin shakkar shiga cikin mu, Ni wlh bansan me mubarak Ya gani a jikinta da har Ya aureta
ba, in banda hasken fatarta da gashin da take da shi, Mace kullum kamar ana ɗibar namanta ana miya da
shi, babu ƙiba babu tsawo, Duk arziƙin da take ci," Dariya suka sanya, mutun ukune basu tanka mata ba,
Gimbiya mujeedat da hajiya malikat sai Hajiya madina. Sauran sune hatsabiban.
Hajiya Jamila tace"ai auran nata da yayi bana Allah da annabi bane wama yasani kota asirce shine,
saboda Sir mubarak yafi ƙarfinta nesa ba kusa ba, Babban gorone, Shiyasa ta nace mashi don aci arziƙi, don
Ma Allah Yasa bata ta6a haihuwa da shi ba, sai dai taci ta zubda.... " Hankalin turai ba ƙaramin tashi yayi
ba, Jin cin mutuncin da suke Yi mata, Tuni hawaye sun soma wanke fuskarta.
Hakan ba ƙaramin daɗi yayima hajiya laurat ba, Ita dama burinta takala Ya ƙuntata.

"Nifa Har yanzu ban daina zargin Yaron nan nata shege bane, tun da bashi da uba, ahaka tazo da shi aiki
gidanmu daga ƙasar england, matar nan muguwar munafuka ce, babu Allah aranta, Allah kadai Yasan
maƙarƙashiyar da take kulla mana" zaro ido waje Hajiya turai tayi jin abunda Saratu take fadi, Maganar ta
ƙona mata ranta, zuciyarta har wani tafarfasa take Yi sam takasa buɗe baki ta dakatar da su, sai dai binsu
da take Yi da idanu.

"Gobe kada in kuskura Inga ƙeyarki awurin taron shagalin dinner din da za'ayi na Hateem, Idan ba haka
ba agaban idon kowa zan watsa maki ruwan lemu akan fuskarki" Hajiya laurat ce ta fada tana nuna ta da
cup din hannunta.

"Dake da wannan ɗayar munafukan meye ma sunanta"? Da sauri hajiya saratu tace"hajjaty" hajiya laurat
tace"yawwa ita nake nufi, uwar iyayi, mai shafa turaren ƴan bori, ku biyun nan bamu buƙatarku a family
din nan don kawai ba yadda zamuyi daku ne amma very soon zamu yi maku korar kare" ta faɗa tana sakar
mata shu'umin murmushi.

Fashewa Turai tayi da kuka mai cin rai, kamar an ruƙe mata ƙafafuwanta takasa tafiya tabar wurin su.

Gyaran murya Gimbiya Malikat tayi masu, gaba ɗaya suka kalleta.

"Ba girmanku bane, kun bani Kunya, ni banga amfanin maganar da kuke gaya mata ba, ku kama mutunci
ku mana" rai 6ace ta furta maganar, babu wasa a fuskarta.
Sai lokacin Gimbiya Mujeedat ta buɗe baki cikin nutsastsiyar muryarta ta furta Sunan turai.

Baiwar Allah muryarta na rawa ta amsa mata da na'am.

"Zo ki zauna kusa dani" ta fada tana nuna mata gefenta.

rai a6ace Laurat da muhibbat suka miƙe tsaye suna fadin Allah Ya kiyaye su haɗa kafada da ita, Indai turai
zata zauna sai dai su su tafi" ko kallon su mujeedat batayi ba.
Muryar turai da shessheƙar kuka tace"bazan Iya zama ba Aunty mujeedat, bana so na shiga tsakaninku, ni
zan tafi kawai, dama yaya mubarak ne Yace in zo wurinki don inyi maki bangajiyar tafiyar da ku ka yi, don
haka zan tafi tun da naganki..... " tana ƙarasa maganar, ta juyawa da sauri ta nufi hanyar fita daga garden
din.

Zuciyar Gimbiya mujeedat ta sosu, ranta ya 6aci da kalaman da Su laurat sukayi ma Turai.
Yunƙurawa tayi tare da miƙewa tsaye tana gyara rigarta,
Har suna hada baki wurin tambayarta ina zataje?
Batare da dube su ba tace"zan shiga cikine, nagode da ziyara sai mun haɗu gobe idan Allah yakaimu" Ta
fada tare da kallon Gimbiya malikat tace"mu shiga daga ciki," miƙewa hajiya malika tayi suka ruƙe hannun
juna atare suka nufi cikin gidan.

Bayan tafiyar su, Tsoki Hajiya laurat taja tana fadin"wannan munafukar matar duk itace taja mana, Muna
zaman mu lafiya, ta tarwatsa mana farin cikin mu"
Hajiya Jamila tace"Halin talakan kenan, Yanzu gashi tasa Ran gimbiya mujeedat Ya 6aci"
Hajiya saratu tace"banji dadi ba wallahi, amma nasan ta inda zan rama, Allah yakaimu gobe lafiya, Idan
har matarcan ta kuskura ta zo dinner din ya hateem jikinta zai gaya mata sai nayi mata abun da bata ta6a
tsammani ba" ta faɗa tana faman haɗe fuskarta, Sun jima a garden din kafin daga bisani kowaccensu ta
shiga motarta suka nufi gidajensu.

Baiwar Allah Hajiya turai tana azaune cikin motar Sir mubarak, tasha kuka tamkar ranta zai fita tayi
danasanin zuwa gidan prime minister, kalaman su sun ƙona mata rai, musamman da hajiya saratu ta
ambaci jazz da sunan shegene, tayi alkawarin bazata fadama sir mubarak abunda suka gaya mata ba, don
kuwa idan yaji sai sun yabama aya zakinta.

_______________________✍️

Baka jin sautin komai a falon tamkar babu mutane acikinsa, alhalin nan kuwa Suna zaune kowa Ya hakimce
abun sa, tsabar miskilanci ne Yasa basa iya buɗe baki su tanka ma Junan su, Kowannan su da abunda Ya
ɗauke mashi hankali, fitowa Dr jazz yayi daga bedroom dinsa ya kimtsa kanshi cikin shadda launin blue sky
abunka ga farar fata ta ƙara fiddo mashi da hasken shi, ga wani daddaɗan ƙamshin turarensa dake fesowa,
Ya gyara sumar kanshi hannun shi ɗaya ruƙe da key din motarsa, wani irin annurin farin cikine akan
kyakkyawar fuskarshi ga dukkan alamu akwai wani abu daya faranta mashi rai.

kafin Ya ƙarasa cikin falon, Idanunsa suka hango ma sa Matasan Samarin Family din dake zaune saman
sofas Har sai da gabanshi Ya faɗi da idanunsa suka yi mashi tozali da su, Baisan da zuwansu ba, aranshi ya
ayyana to fa ashe yau muna da manyan baƙi a gidan na mu ba, meyasa Ibad bai faɗa min sunzo gidan nan
ba? Ya ƙarasa zancen zucin nashi cike da jin fagabar tunkararsu, Ya kasa motsa ƙafafuwanshi Ya tsaya
atsaye kamar wanda aka yi mashi Iyaka da shiga falon, ɗaya bayan ɗaya ya soma bin su da kallo, Zaki Yana
a azaune saman 2 seater Yayin da Apple Laptop dinsa ke akan Table din gabansa, Gaba ɗaya ya tattara
hankalin shi akanta yayin da yake operating dinta atsanake, Short ne a jikin shi tare da Denim shirt tabi
shape dinsa, Kau da idanunsa yai daga kan Zaki Ya mayar da su kan Wani Matashin saurayi fari Sol, fatarshi
ko ƙwarzane babu, Ga wata nannaɗaɗɗiyar sumar kai dark brown, kai daga ganinsa wani shege ne mai ji da
naira, Allah yayi shi da kyau mai jan Hankali, Jallabiya ce a jikin shi launin grey, ta zauna mashi sosai,
bakowa bane wannan face Captain YASEER ɗan gidan His Excellency Abdul Razak da Her Excellency
Muhibbat shuwa arab ne kamannin shi sak dana su Chief Owais, banbancin su launin fatane dana Ido,
hannun shi ruƙe da Expensive phone dinsa da yake daddanawa da zira ziran yatsun hannunsa, yayin da
Justice Nadeem ɗan gidan His excellency Deen Yake a kishingide kan doguwar Sofa, Ya zagayo da hannun
shi ɗaya saman forehead dinsa, idanunsa suna a lumshe tamkar mai yin bacci.

Ziyad ne kaɗai yake a zaune saman lallausan Carpet din dake a shimfiɗe tsakiyar Sofa set din falon,
faffaɗan farantin da aka kawo masu fresh fruit acikinsa ya tasa a gaba yana shan kayan marmari, duk acikin
su Ziyad yafi su sauƙin kai kasancewarshi ɗan jarida da son labari, A yanzu haka da yake a zaune cikinsu A
takure yake jin kanshi sunƙi sakar mashi fuska su yi fira kowa Ya kama harkar gabanshi shiyasa ya sauko kan
carpet yaci gaba da shan kayan marmari.

Ƙamshin turarensu Ya gauraye Falon, Jazz dake kallon su ba ƙaramin burge shi su ke yi ba, ba tun yau ba
Yana son Yaga jikokin Baba Obie sun haɗu suna sada zumunci aranshi sai yaji inama ace shima Jikan Baba
obie ne da Allah ne kaɗai Yasan irin Farin cikin da zaiyi a duniyar nan.

Ganin basu lura da shigowarshi falon bane yasa shi yin saurin tafiya cikin sanɗa Ya nufi ƙofa Ya fuce daga
ciki Yana faman sauke ajiyar zuciya, da sauri Ya nufi Harabar Ajiye motocinsu, Ya buɗe motarshi Ya shiga
daga Ciki, tare dayi mata key, zuciyarshi acike fal da tunaninta, fatan shi Allah yasa wannan karan ta kula
shi.
Yana driving fuskarshi dauke da annurin farin ciki, A haka Ya nufi Gidan baba obie.

Ganin shirun nasu bamai ƙarewa bane, Yasa shi miƙewa, Ya nufi Zaki Ya sanya hannu ya ɗauke laptop din
da yake dannawa, Ya juya Ya nufi Captain Yaseer Ya kar6e wayarshi, kafin Ya tunkari justice Nadeem Ya
sanya hannu Ya kamo Hancinshi Yaja Shi da karfi har sai da Justice Nadeem Ya buɗe idanunshi dake dauke
da bacci Fuskarshi adaure yake kallon Ziyad.

Harara Ziyad Ya watsa masu Ranshi a6ace yace"wai meke damunku ne? Kullum muka haɗu kamar wasu
kurame babu mai magana kowa ya kama harkar gabansa? Haka ake zumunci? Ni banga amfanin kirana
wurin nan donmu haɗu ba.... " gaba ɗaya sun ɗaura idanunsu kan fuskarshi babu alamun zasu tanka
mashi.

Guntun tsoki Yaja"kun wani zuba mun idanu kuna kallona wato ni ga shashasha"
Yamutsa fuska Zaki yayi tare da miƙa mashi hannu yace"Bani laptop dina ziyad"
"Ta ƙarfi ce zoka kwata" A faɗace Ya faɗa Yana haɗe mashi fuska.

Murmushi gefen fuska Zaki Ya sakar mashi.

"Meye damuwarka"? Ya tambaya yana faman lumshe idanunsa.

"Damuwata shine ku bani aron hankalin ku muyi fira kan abunda ya shafi rayuwarmu, daga gobe fa
shikenan kowannanku zai koma inda Yake rayuwarsa, yawanci ba akasar nan kuke zaune ba why ba zamu
kula juna yadda ya dace ba? Bamu da tabbacin ko zamu sake haduwa da junanmu"

Yanayin yadda yayi masu maganar Ya ta6a zuciyoyinsu,

In a calm voice Zaki Ya furta"In sha Allah zamu sake haɗuwa, Yanzu dai ka yi haƙuri, Ka zauna mu yi fira"

Ta6e baki Ziyad yayi, kafin Ya koma Ya zauna, Batare daya miƙa masu Kayansu daya kar6a ba.

"Bro, Ni bansan ta yadda zan fara firar bane, ko zaka taimaka mana da abun da zamu tattauna akai"?
Captain ne Ya faɗa Tamkar baison furta maganar, justice Nadeem dake a kishingiɗe tuni Ya gyara zama
saman Sofa Yana duban su
"Me zai hana Mu yi magana dangane da matayen da muke da burin aure"? Acewar ziyad.

kallon Harara Captain Ya watsa mashi"mu yi magana kan abu mai mahimmanci, Idan ba haka ba zan ja
baki na nayi shiru"!

"Aure shi yafi komai mahimmanci domin kuwa Sunna ce mai karfi ta Manzon Allah SAW, Allah Ya bamu
komai da zamu buƙata, Kowannanmu Yana da aikin yi, Aure shi ya rage mana yakamata ku yi tunani yanzu
fa lokaci ne da zamu more rayuwarmu, mu ma yi aure mu hayayyafa kamar yadda Iyayen mu suka yi.... "
Ziyad ne ya kora masu jawabi.

"Look, Ni aure baya a gabana yanzu, har yau banga macen data kwanta min arai na ba, tun lokacin dana
rasa wadda nake da burin aure naji matan ma sun fitarmin araina"

Justice Nadeem dake kallon Captain Ya saki murmushi tare da cewa"Ai ba ita kadai bace mace a family
dinmu ba, Kai ma kaso ka wahalar da kanka, Ai ni tun lokacin dana fahimci macace mai izza da ji da kai, na
sanyama zuciyata salama, saboda bana son macen da namiji bai isa yayi iko da ita ba, ba zata yi dadin
zaman aure ba, kwara wadda zaka Iya juyawa son ranka ba wadda zaka dinga jin fargaban tunkararta ba"

Ziyad yace"ka faɗi gaskiya mutumina, ita fa gaba ɗaya namiji ma baya agabanta, bata da burin yin aure,
kai ma mai yaja maka yin dakon soyayyarta? Bayan Ga matasan ƴan mata nan masu jini a jika a family
namu.... " kafin Ziyad ya ƙare maganar, Zaki yai gyaran murya tare da cewa"wai kuna Nufin Nazli"? Ɗaga
mashi gira Nadeem yai, matashin murmushi ya saki kafin yace"Kuna nufin bakusan alaƙar dake a
tsakaninta da chief Owais namu ba"? Atare suka haɗa baki wurin furta meke nan"?

Jim ya ɗanyi kafin Ya furta"Uncle Hateem, Ya riga daya mallaka mashi ita, bata da wani miji daya wuce shi
a duniyar nan, tun kafin tazo duniya, wannan alƙawarine dake atsakanin Uncle sharafudeen da uncle
Hateem, zasu haɗa auran ƴa'ƴansu... " da mamaki suke kallon shi
Ziyad yace"amma ni banta6a ganin alamun suna kula junansu da sunan soyayya ba, Ko ranar Birthday din
grandfa da suka haɗu ko kallo ba su wa junansu ba"
"Dama taya za'ai su kula juna?bayan kowannansu Yana ji da kanshi daga ita har shi Owais din, duk abunda
take taƙama da shi shima Yana da shi, gaskiya Uncle sharafudeen da Hateem basu yi tunani mai kyau ba,
bayan sanin cewa Izza A jinin su take, tayaya Nazli zata yi mashi biyayya amatsayin matarshi? Justice
Nadeem ne yayi maganar.

Captain da ke sauraransa fuskarshi babu annuri babu walwala ya furta"da ace nasan da zancen nan da
tuntuni na cireta araina, dama ni ba Iyawa zanyi da ita ba, owais din shi yafi dacewa da ita, suje can su
ƙarata," Ya faɗa tare da jingine kanshi jikin Sofa.

Shiru suka yi na ɗan wani lokaci, babu wanda Ya furta magana sai daga bisani Justice nadeem Ya
furta"Zaki Ina budurwarka ta Canada Kyakkyawar balarabiyar nan"

Da zolaya ya faɗa yana duban shi.


Kallo ya jefa mashi mai kama da harara kafin Ya furta"ta koma gidan su"
Zaro ido justice Nadeem yayi"me? Kana nufin tabar gidanka"
Ɗaga mashi gira yai alamar eh,
"But why"?
Bai cika son tada maganarta ba, saboda hakan Yana fama mashi raunin dake a zuciyarshi.
Cikin sanyin murya ya furta"bansan meyasa ba, rana ɗaya ta haukace min ta soma kokarin juya min ba,
badan naso ba nabarta ta dawo Nigeria"
Justice Yace"banji dadi ba, me zai hana ka nemi gidansu inyaso saika gabatar da kanka wurin Iyayenta"?
Murmushin takaicin Zaki yayi"tana da aure har da ƴarta, ban ta6a fada maka bane"
Jin wannan maganar Yasa Captain ware manyan idanunshi, hatta Ziyad dake sauraransu saida Ya zaro ido
da alamun mamakin kalaman Zaki
A ruɗe justice Nadeem ya maimaita maganarshi"tana da aure har da ƴa? Amma ta zauna a gidanka
tsawon shekaru tamkar ma'aurata? Kafin Ya ƙare maganar Captain Yace"tayaya hakan zai yiwu? Nima fa
nasan Matar duk lokacin da zanje canada a gidan ka nake taras da ita, nayi tsammanin Ƴar aikin ka ce,
shiyasa ban ta6a kawo ma raina wani abu ba,"

Girgiza kai Zaki yayi"ba ƴar aikina bace, Taimakon ta nayi, na ruƙe ta agidana saboda ta nuna min bata da
kowa bayan mun fara shaƙuwa take bani labarinta, Hankalina Ya tashi jin cewa tana da aure, amma
agidana mijinta ya tura mata da sakon saki, ganin hakan yasa muka cigaba da yin rayuwarmu, naso ta
amince min in aure ta saboda bani da burin daya wuce na mallake ta, nasan tana sona sai dai tafi ƙaunar
takomama mijinta saboda ƴarta da tabar mashi"

Gaba ɗaya sun lura da canzawarshi, hakan Ya ƙara tabbatar masu da irin kaunar da yake yi mata.

Miƙewa yayi da sauri Ya nufi bedroom dinshi, Da sauri justice Yabi bayanshi, Yana Shiga Ya zura
hannayenshi cikin aljihun short dinshi, Yayin da zuciyarshi ke cigaba da tafarfasa

"Bana so hakan Ya dame ka, Yarinyar nan ko tana so ko bata so, Kai ne mijinta, Saboda kafi cutuwa,
Tsawon shekara goma sha shidda kuna rayuwa agida ɗaya tamkar ma'aurata? Ka raineta ka kashe mata
maƙudan kudi, Idan har ta butulce maka Allah ma bazai barta ba"

Justice ne yayi maganar, yana daga tsaye abayanshi


"Duk abunda nayi mata nayi ne don Allah..." kafin Ya ƙare maganar justice yace"nasan don Allah kayi
mata amma wallahi bazan bari ta karya maka zuciya ba, tun da nake da kai baka ta6a nuna kana son wata
ƴa mace ba, sai akanta, don haka dole ta aure ka, shi kuma mijinta Ya haƙura ya nemi wata, nasan ma yayi
auranshi tun da jimawa"
Juyawo Zaki yayi idanunsa akan justice Yace"nagode da kulawarka agare ni, amma mubar maganar,
saboda hakan bamai yiwuwa bane, Ni bazan tursasa mata akan ta so ni ba, ta ɗauke ni tamkar yayanta
tana girmamani, tun da nake da ita ban ta6a nuna mata inasonta da aure ba itama haka "
"Ita ai ba makauniya bace, in ba kaiba wani namijine zai dauki dawainiyar baligar mace kamarta almost
16years, idan bazan manta ba, lokacin da naje gidanka a canada, ina lura da duk wani motsinku, Idan ka
shiga daki da dare zaka kwanta tana binka bata fitowa har saita tabbatar da kayi bacci take fitowa, kaima
kuma haka, sannan baka Iya cin abinci idan ba atare da ita ba, itama haka, kana nufin wani abu bai ta6a
shiga tsakaninku ba"? ya faɗa yana bin sa da kallon tuhuma.

"Nadeem, Ba abunda kake tunani bane, nasan nayi kuskure na ajiye macen da ba muharramata ba a
gidana, amma wallahi ban ta6a shigarta ba..... " muryarshi na rawa ya ƙare maganar, wani irin yanayi yake
jin kanshi tunawa da rayuwarshi da ita.

Numfashi yaja kafin yaci gaba dacewa"Ta saba min da kanta, komai ita take yi min, bansan menene so ba
sai akanta, ban fara muradin yin aure ba sai akanta, ashe ita din ba rabona bane...."

"Da ace kuɗi zasu Iya siyamin ita, wallahi har dukiyata zan iya salwantarwa saboda ita, bana tunanin zan
samu macen da zata Iya maye min gurbinta, Ni ita kadai nakeso Nadeem" kwallar dake taruwa a cikin
idanunsa har sun fara kokarin gangarowa saman kuncin sa.

Hankalin Justice Ba ƙaramin tashi yayi ba, ko a mafarki bai ta6a tunanin mace zata Iya tanƙwara zuciyar
Zaki ba.

Dafa kafadunsa yayi da hannayenshi


"Inaso ka faɗamin shi mijinta tsawon shekara nawa su ka yi atare"?
In a low voice zaki Ya furta"ƙasa da 2 years, ta faɗa min aranar data haifa mashi baby tabar gidan badan
bata son shi ba, kawai taji ya futar mata arantane"
"Kasan mijin nata"?
"Taya za'ai nasan shi? ni ko sunan shi ban ruƙe ba, saboda kishinta da nake ji"
Murmushi justice yayi tare da ruko hannun Zaki, suka zaune gefen gadon shi.

"Iyayenta masu hali ne"? ya jefa mashi tambayar.

"Yeah, mahaifinta ya ta6a ruke mukamin Governor a jihar joss, amma bai jima a mulkin ba ya sauka
sakamakon ciwon kafar dake damun shi, bayan haka Ƙanin Mahaifinta Former president ne Na nigeria,
Alhaji Musa wadata, Yayan Matar Uncle sharafudeen Hajiya Laurat, nima a wurin ta naji labarin ta" jinjina
kai justice yayi"Ƴar masu Hali ce, Alhaji musan nan Yana ɗaya daga cikin wadanda suka fi kowa kuɗi a africa
bayan family dinmu, amma nayi mamakin da har ta gudu tabar nigeria basu nemo ta ba, meyasa tabar
mijinta da ƴarta? Shine abun tambayar"
"Naikaina Labarinta Yajima Yana ɗaure min kaina, Sonta ne Ya makantar dani shiyasa ban mayar da ita ga
Iyayenta ba, saima na taimaka mata wurin 6oye kanta agidana, naci gaba da bata kulawa"

Justice ya ce Labarinta Akwai ruɗani Acikinsa, Ta fito daga babban family, ga ta kyakkyawa da ita amma
ahaka har ta gudu daga gidan mijinta? Akan wani dalili? Me ta nema tarasa?"
Ya faɗa yana kallon Zaki,
"Nayi kokarin nemanta don inji ya ta koma gidansu? Iyayenta sun kar6eta ko kuwa? Shine fargabana sai dai
bani da hanyar da zan Iya kiranta, tabar min wayarta a hannuna, bansan kowa nata ba, in ba hajiya Laurat
ba"
Numfasawa Justice yayi kafin yace"kada ka damu ɗan uwana, zan iya yin komai akanka, gobe Idan Allah
yakaimu a family dinner zanyi magana da hajiyar laurat din dangane da ita Yarinyar," har cikin ranshi yaji
dadin maganar justice, ya kwantar mashi da hankalin shi sosai harya fara tunanin yadda haduwarsu zata
kasance da ita, sun jima adakin suna tattaunawa daga bisani suka dawo falo wurin su Captain.

______________________✍️

A hankali Motar Dr Jazz Ta ƙaraso bakin Entry Hall na shiga gidan baba Obie, Bayan yai parking ɗinta ya fito
ya nufi cikin gidan, A katafaren Main Falo din gidan Ya taras da Twins zaune saman sofa tare da wani
matashin saurayi kyakkyawan gaske kallo ɗaya zaka yima fuskarshi ka shaida ɗan uwan Justice ne, gaba
ɗayan su wankan suit ne a jikin su, Cike da jin fargabansu Ya nufe su, Cikin sanyin murya yace"barkanku da
hutawa"
Ko kallo bai ishe su ba, Kamar Yayi magana da bango, kuma sun ganshi.
Kusan sau uku Yana maimaita maganar da yayi masu amma babu wanda Ya amsa mashi, hakan Yasa shi
yanke shawarar Tafiya yabar wurinsu Har Ya ɗaga ƙafa zai tafi muryar Zayn takatse shi.

"Kai zo nan"! da kakkausar Murya Ya faɗa tare da yafuto shi da hannu, Irin kiran da akeyima kananin Yara,
Jazz baiji komai aranshi ba Ya nufi Zayn.
Yamutsa fuska zayn yai yayin da yake binshi da kaskantaccen kallo Yace
"Kai makaho ne? Baka gan mu bane zaka wuce batare daka gaishe da mu ba"? Fuska adaure yayi mashi
maganar.
Cikin sanyin murya Jazz yace"Nayi maku magana kusan sau uku babu wanda Ya kula ni"
Harara Zayn ya watsa mashi, Dr. nawaz dake a kishingide yana duban su Yace"zayn dama har yanzu
wannan kwandon sharar Yana agidan nan? Nayi tsammanin Uncle Mubarak Ya saki babarsa sun koma
kasarsu"
Ta6e baki Zayn yayi"gayanan dai kana kallon shi, baida banbanci da masu gida, Har yafi mu jin daɗi, Uncle
Mubarak ya ɗaure mashi wurin zama"
Yamutsa fuska Dr.Nawaz Yai"Kaci sa'a ba'a ƙasar nake zaune ba, da tuni nasa anyi watsi dakai, donni bana
son bare ya ra6i Ahlinmu," Jazz dake atsaye yana sauraron Rashin mutuncin da suke yi mashi, tuni
idanunsa sun cicciko tab da kwalla.
"Ya isa haka!" Zaid ne Ya faɗa tare da kallon Jazz, Da hannu Yayi mashi alamar Ya tafi, bawan Allah Jiki
asanyaye ya nufi Hanyar kitchen din gidan, tunkafin Ya karasa Able ta fito daga ciki hannunta ruƙe da tray
na kayan marmari, ganin jazz yasa ta dakata da tafiya fuskarta da fara'a tace"Jazz Ya jikin naka"?
Fuskar shi babu walwala Yace"da sauki"
"Allah Ya kara lafiya" ya amsa mata da ameen, ganin Yana ƴan kalle kalle Ne yasa ta fahinci akwai wani abu
da yake nema don haka tace"ko akwai wani abu da kake bukata ne"?
Ɗaga mata kai Yai haɗi da cewa"Eh, Ina neman Faryat ne,"
"Muje na raka ka, Nima wurin su zanje kai masu Kayan marmari," amsa mata yayi da toh, ta yi gaba yabi
bayanta, aranta ta ayyana ko me zai kai shi wurin faryat? Tantiriyar Yarinyar nan da babu Allah aranta"
Upstairs suka hau, bayan sun sauka third floor, suka nufi Balcony dake acan sama,Tsayawa fasalta kyawun
wurin 6ata baki ne sai wanda Ya gani, tunkafin su karasa Jazz Ya hango Su zazzaune saman wasu hadaddun
Kujeru Bugun Dubai, Matasan Ƴan mata ne masu ji da kansu, A kalla sun kai su uku Kowaccensu Ta dauki
wanka na kece raini, Kamshin turarensu tuni Ya soma Cika mashi hancinshi.

Kaitsaye idanunsa suka sauka akan Faryat, wadda ke asanye da mini skirt ya matse jikinta, daƙyar skirt
din Ya wuce Ass dinta, Rigar jikinta kuwa Ko cibinta bata rufe ba, ta bayyana shape din kirjinta hatta nipples
dinta kana iya ganin tsininsu, babu mayafi akanta Kitson kalabar da akayi mata ne mai kyan gaske ansanya
mata sparkling stones masu jan hankali saman gashin kanta, yatsun hannunta yana asanye da gold knuckle
rings, Haka zalika Hancinta na amanne da nose ring, wata ziririyar sarka ce a kafarta, Yarinyar karshe ce
wurin Iya barikanci, Hatsabibiyar gaske bata jin magana ko miskala zarratin, sai dai fa akwai kyan sura,
komai nata irin na hajiya saratu ne banbancinsu girman jiki da shekaru.

Matashiyar dake a gefenta, Yusra ce Ƙanwar Yaseer, Kallo ɗaya zakai mata saika sake kallonta, Tsabar
haɗuwarta, itama fara ce sol, kamanninta sak dana mahaifiyarta Her excellency Muhibbat, gata doguwa
tubarkalla, bayan ita sai Zulaihat kanwar Ziyad Wankan tarwaɗa ce alaunin fata tana da saukin kai ko a
fuska ka kalle ta, babu wanda Ya lura da Jazz A cikinsu Hankalinsu na akan firar da suke Yi.

able ce tayi masu sallama, Tare da ajiye masu tray din kayan marmarin saman round table din dake a
tsakiyar kujerun su, juyawa tayi da sauri ta fuce tabar wurin.
Wani irin shakkar Yi masu magana Yake ji, Sai faman bin Faryat Yake Yi da kallon ƙurulla.

"Na jaraba kiran layin Sister Hindu bata yi picking ba, may be ko bata a kusa ne da wayar, ita dai Yazrin
nayi mata uziri, saboda tafiyar da suka sha nasan haryanzu gajiyar tafiya bata sakesu ba" Zalaihat ce tayi
maganar tare dakai hannu ta dauki tufa tana ci
"Ina ga mezai hana mu shiga gidan yi masu bangajiyar tafiya, Su mommy ma suna acan"
"Ni dai ba inda zanje, sai zuwa gobe idan mun haɗu wurin Dinner din daddy Hateem" Acewar Faryat Tana
faɗa tana farfari da idanunta.
"Gobe akwai shagali, zamu yi sharholiyarmu son ran mu, Har nakagara goben nan tayi," Yusra ce ta fada
tana karkaɗa kafarta.
Har Faryat Ta buɗe baki daniyar tayi magana, Sautin ringing din wayar Jazz Ya dakatar da ita, Kusan atare
suka wurga idanunsu kan fuskarshi, nan take yaji gabanshi ya faɗi rass saboda kwarjinin da suka yi mashi.

Yamutsa fuska Yusra tayi tare da kau da idonta


Zulaihat kuwa Murmushi tasakar mashi
"Dan uwa, Tun yaushe kazo wurin nan ne?
Yana faman Kame kansa Yace"tare da abla muka zo"
"Amma meyasa bakayi mana magana ba jazz," cikin kulawa ta fada tana dubanshi Ta fuskanci Hankalin
shi ba kwance yake ba
"Wa kake nema ne"?
Kallon Faryat da yayi ne yasa ta gane ita yake son gani"
Murmushi zulaihat tayi,
Faryat dake kallon shi, wani irin shu'umin murmushine akan fuskarta, yunƙurawa tayi ta miƙewa ta dubi su
Yusra"ni zan shiga ciki, bazan jima ba yanzu zan dawo" Yusra dake harararsa tace"faryat kin bani kunya, Ki
rasa wa zaki kula sai wannan halittar" ta fada tana nuna shi da yatsa
Zulaihat tace"Please Yusra, babu ruwanki da shiga sabgarsu" Ta6ebaki Yusra tayi
Ba tare daya ankare ba, Faryat ta ruƙo hannunsa tare da jan shi suka soma tafiya atare, wani sanyine yaji
ya ratsa zuciyarsa, duk da yasan ba lallai Faryat ta sassauta mashi ba, Ya riga daya san halin ta.
Kaitsaye suka nufi bedroom dinta dake a gidan, adai dai bakin kofar shiga Dr.Jazz Ya dakata da tafiya, da
sauri ta kalle shi hadi da kashe mashi ido ɗaya tace "my babe meyasa ka dakata da yin tafiya? Let's go
inside," ta fada tana matse hannunsa dake acikin nata, har cikin zuciyarshi yake jin matsar da take yi mashi.
Muryarshi ƙasa ƙasa Ya ce"basai na shiga ciki ba, mu koma falo mu yi magana"

Ɗaure mashi fuska tay "Jazz, you will lose your chance to talk to me if you don't go in," she warned. "If you
don't go in, don't expect to see me again"!

*Daga Alƙalamin Boss Bature✍️


*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan
layin 08169856268*_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_

‫🔥✊💋سجن القدر‬

~Takun Ƙarshe🔥~

‫😘💘💋قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة‬

An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘

Daga alƙalamin Boss Bature💋✊

__________________________✍️
Tana ƙarasa fadar hakan ta sanya hannu ta ture ƙofar ta shiga ciki, A ƙalla Yafi karfin mintuna biyar a bakin
kofar yana yanke shawara da zuciyarsa, haƙiƙa Yana matuƙar jin tsoron Allah, bayason zama daki ɗaya da
macen da ba muharramarsa ba, hakanan ba tare da wata lalura ba, balle kuma faryat da ta kasance
tantiriya, sai dai baya jin zai iya rasa wannan damar, Allah ya jarabce shi da tsananin ƙaunarta, Itace mace
ta farko da ya fara jin tsantsar sonta tun lokacin daya mallaki hankalinsa, ya mutu akan kaunar faryat yana
son yarinyar duk da kasancewarta mara jin magana.

Numfasawa yayi kafin ahankali ya tura kofar dakin nata ya shiga daga ciki, katafaren dakin kwana ne,
kamar na ƴar sarki, tsabar haduwar furniture din dakin, Komai na cikinsa Launin black pink ne.

Bayan shigarsa dakin, Sanyayyan sanyin A.c ne mai haɗe da daddaɗan kamshin turaren faryat ya ratsa
hancinsa da fatar jikinsa, Lumshe idanunsa yayi slowly ya buɗe su akan faryat dake a tsaye gaban dressing
mirror, ta juya baya kitson kalabar kanta ya sauko har mid back dinta, ta cikin madubin ta ke jifar shi da
shu'umin kallo.

Ganin yaƙi ƙarasowa gare ta, yasa ta juyo ta nufe shi, dab dashi ta ɗaya suka soma jefa wa junansu kallo.

Ba zai iya jurar shaƙar ƙamshin turarenta ba da kallon surar jikinta hakan ba ƙaramin jefa shi yanayi ya
ke yi ba, Muryarshi na rawa ya furta"Am.. umm.. tun da naganki zan tafi"

ba zato ba tsammani yaji ta ɗaura hannayenta saman kirjinshi, muryarta da shagwa6a ta furta"Ni ban gaji
da kallon ka ba, My honey, tsawon lokaci bansanya ka a idanuwana ba, nayi kewar komai naka jazz.. "
kafin ta ƙare maganar, jazz ya tari numfashinta da cewa"Faryat tayaya zan yarda da kalamanki? Bayan ke da
kanki kika faɗi cewa bazaki ta6a sona ba, kuma ba zaki iya aure na ba"

Juya mashi baya tayi haɗi da goya hannayenta saman kirjinta kafin ta soma magana.

"Jazz, I won't hide it from you. Nothing has changed. I love you, but I can't marry someone who has no
origin", (Jazz bazan 6oye maka ba, Har yanzu babu abun da ya canza, Inasonka amma bazan Iya auran
wanda bashi da asali ba,)" ta faɗa tana girgiza kanta, kafin ta ɗaura da cewa.

"kaima ka sani jazz mommyna da daddyna ba zasu ta6a yarda mukasance atare ba, jazz I come from a
wealthy family. How can I love someone like you who has no origin? What is your family status?" ta jefa
mashi tambaya ba tare da ta jira amsar shi ba taci gaba da magana

"Ta ya ya zan auri ɗan tsohuwar mai aikin gidan mu" tun da ta fara magana sai yanzu ta juyo ta fuskance
shi, Jikin shi yayi sanyi lakwas, hawaye tuni sun soma taruwa a cikin fararen idanuwansa, kalamanta sun
kashe mashi kwarin gwiwarshi, sai yajima gaba ɗaya ya tsani kan shi, ta fahimci halin da ya shiga sai dai ko
kaɗan bata ji tausayin shi ba.

"Jazz Hamshaƙan masu kuɗi suna rububi akaina, waɗanda duniya tasan da zamansu, How can I choose a
meaningless future for myself when I could have so much more?" a tsiwace ta faɗa tana zare mashi
kyawawan idanuwanta masu dauke da zira ziran eye lashes.

Hawayen da suka cika idanunsa tuni sun wanke fuskarshi

Cikin karyayyar murya yace"Nasan ni bakowa bane faryat, bani da asali, amma inaso ki sani, ina son ki
tsakani da Allah badan wani abu naki ba, ba lallai ki sami wanda zai so ki kamar yarda nike sonki ba, nayi
maki alkawarin zan baki kyakkyawar kulawa idan har kika amince da soyayya ta, ba zaki ta6a danasani ba
faryat"!
Shu'umin murmushin gefen fuska tasakar mashi, wani irin kyawuntane Ya kara bayyana.

Matsawa tayi tare da shige mashi, Har takaiga mumfashinsu na kokawar fitowa, hannayenta biyu ta
ɗaura saman waist dinsa, da sauri ya yi kokarin kwace kansa daga gareta sai dai taki bashi damar yin
hakan, gaba ɗaya ta kashe mashi jikin shi.

"Jazz ka daina wahalar da kanka akaina, cos I will never marry you. Owning me is not an easy thing, idan
mommy taji zancen kana neman soyayyata kai kasan me zai biyo baya, shiyasa nake rufa maka asiri,
saboda ina da buri akanka," lumshe idanunsa yayi cikin jin ƙunar rai, Allah ne kadai yasan Irin azabtuwar da
zuciyarsa take yi mashi akan soyayyar faryat, zai iya jure komai amma bazai juri ya rasa ta ba.

Jin motsin hannunta akan Trouser dinsa ne yasa shi yin saurin buɗe idanuwansa a hanzarce ya buge
hannunta Yana faman fitar da huci...

Kashe mashi ido ɗaya tayi tare da zuro harshenta waje ta lashe pink lower lips dinta, cikin jin shaukin shi ta
furta"jazz, har yanzu ban canza ra'ayina akanka ba, ka bani dama, in ɗebe maka kewa, kaga babu mai
kallon mu daga ni sai kai, zan faranta maka rai, sannan inyi maka abun da zai zautar dakai ya gigita ka" ta
faɗa cikin jin shauƙin shi tana kokarin tura mashi boobs ɗin ta da suke acike fam.

Jikin shine ya soma kakarwa a ruɗe ya furta"bani da wannan ƙazamin tunanin araina, dan Allah ki daina
fadamin kalaman nan, Hakan Yana karya min zuciyata, Ni tsakani da Allah nake sonki, Idan babu mai kallon
mu Allah Yana kallon mu faryat, Bazan bari mu sa6a mashi ba, "

Harara ta jefa mashi"matsalata dakai kenan, Har yanzu bakauyene kai, sai kace ba bature ba, sam baka
da wayewar nan irin ta zamani, Daga anyi magana sai ka ambaci sunan Allah kamar kafi kowa tsoronsa, Ay
Allah gafurirrahim ne, Idan mukayi sai mu roƙi rafiyarsa... " tunkafin taƙare maganar yace"Idan kuma muka
mutu muna cikin aikatawa fa"? Murguɗa mashi baki tayi"nima bansani ba, tun da baka buƙatana ka tafi
kawai, zan nemi wanda zamuyi da shi" ta fada tana ruƙe qugunta.
Wani irin kishine ya ziyarce shi, tamkar Ya haɗiyi zuciya haka yake ji
"Faryat ba ki jin kunyar fadin hakan agabana ba"? Ɗaga mashi gira tayi

"Yeah i can sleep with someone in front of you. tun da kai bazaka bani abun da nakeso ba, jazz bakason
farin cikina, na jima ina sha'awar son kasancewa dakai amma kaƙi bani haɗin kai" cikin rauni na murya
yace" idan kina son kasancewa dani ki aure ni mana, zan zama naki ke kadai, Mallakin ki, ko da yaushe kike
bukatana zan kasance atare dake",

Girgiza mashi kai tayi"A'a nidai kawai kayi min abun da nakeso, ay na fada maka bazan iya auranka ba, sai
dai mu kwanta in baka kaina" Lamarin faryat ba karamin mamaki yake bashi ba, A shekaru bazata wuce 22
Years ba, Mace har mace sai dai babu kunya ko kadan.

Ganin Ya tsareta da idanunsa ne yasa ta fara tunanin ko ya amince mata ne, ɗaura yatsun hannayenta tayi
akan wandonsa da niyar ta zame masa shi, A hanzarce Ya buge hannunta, da sauri jiki na rawa ya nufi kofar
dakin zai fuce, da gudu tabi bayanshi tayi hugging dinshi, ta soma raira mashi kukan shagwa6a, hakan
baƙaramin yanayi ya jefa shi ba, baisan da wani yare zaiyi mata magana ta fahince shi ba, ya riga daya gane
faryat tana sonshi, Rashin asalin shine yasa take gudin shi.

Muryarta da shessheƙar kukan ƙarya take fadin"Jazz, kada ka tafi kabarni, Ina buƙatarka Jazz, Ina son
kasancewa tare dakai, dan Allah ka amince min muyi nayi maka alkawarin bazan faɗama kowa ba, Idan ma
kana fargaban wani ya gan mu, sai mu je hotel in kama mana room, ko muyi a cikin motana" ta faɗa tana
murza mashi mararshi da hannayenta, gaba ɗaya tagama susutar dashi wata irin zuface tasoma wanko
fuskarshi
Muryarshi da matsananciyar kalasa sautinta ke fita
"Bazan iya sabama mahaliccina ba faryat, Ina jin tsoron Allah, kiyi haƙuri, Nima inajin abun da kike ji
amma bazan iya ba, Kina bani wahala faryat, kema kuma kina cutar dakanki, saboda kina sona, Kina son
kasancewa dani, amma kin haramta ma kanki aurena akan wani dalili naki mara ma'ana, Meyasa bazaki
tausaya mana ba daga ni har ke? Faryat ki cika mana burinmu na ganin mun raya soyayyarmu, kada ki bari
shaidan Yaci galaba akanki, ki fi karfin zuciyarki faryat, ki zauna kiyi tunani... " daƙyar ya ƙare maganar
muryarshi na sarƙewa ya daddage ya 6an6are hannayenta daga ruƙon da tayi mashi, da sauri ya ruƙo
handle din ƙofar ya fuce daga dakin

A jikin kofar Ya jingina kanshi hawaye masu ɗumi suka shiga zarya akan kuncinsa.

Sautin shessheƙar kukan faryat ne ya cika kunnuwansa, baisan ya zaiyi da ita ba, yasan da irin mugun
sha'awar dake gareta sai dai shi bazai amince mata su aikata sabo ba, saboda babu ɗa'a ga abokin halitta
wurin sa6ama mahalicci Allah! Bazai juri sauraron kukanta ba, zuciyarshi karaya take yi, da sauri Ya sauko
down stairs Cikin takun sauri Ya Nufi part din baba Obinna, zuciyarshi na cigaba da tafarfasa, Abakin kofar
dakinsa Ya tsaya da yin tafiyar Ya zaro hanky, Ya goge kwallarsa, Kafin ya daidaita nutsuwarsa, sallama yayi
mashi.

Daga Ciki Ya jiyo muryar baba obie

"Shigo daga ciki" Buɗe kofar yai tare da shiga Ciki, adai dai lokacin Baba Obie, Yana zaune saman darduma
hannun shi ruƙe da cazbaha.

Ba zato ba tsammani, Yaji saukar Jazz saman bayanshi, gaba ɗaya ya rungume shi tare da cusa fuskarshi
saitin kafadarsa, Hakan ba ƙaramin ɗaga mashi hankali yayi ba, saboda a duk lokacin da jazz yayi mashi irin
wannan rungumar to an 6ata masa raine," Yana Iya jiyo sautin fitar numfashinsa, dakatawa yayi da jan
cazbahar, Ya ruƙo hannun Jazz Ya zagayo da shi ta gabanshi, tare da rungume shi ya kwantar da kansa
saman kirjinsa tamkar ɗansa na cikinsa ko jikansa.

Cikin sigar lallashi yake bubbuga bayansa batare daya furta masa ƙala ba, har saida Yaji alamun Ya fara
samun nutsuwa tukunna Ya soma magana
"Waya ta6a min shalelena"? Muryarshi adisashe Ya furta"Baba ka ta ya ni da addu'a, ita kadai nake bukata
daga gare ka" ya fada batare daya raba jikin shi daga na Obie ba.

"Jazz kasan bana son damuwarka, Ka fada min koma menene nayi maka alkawarin indai baifi karfina ba
wallahi zanyi maka shi," babu wasa a kalamansa
Jazz yayi fatan ace zai iya fada mashi abunda ke damunshi amma bazai iyaba, Yasan muddin baba obie yaji
zancen Yana son faryat sai ya aura mashi ita, koda kuwa Iyayenta basa so, shi kuma abunda yake gudu tada
husuma, saboda ba lallai hajiya saratu da Pravin su amince mashi ya aureta ba, komai zai iya faru.

Shafa bayanshi baba obie yaci gaba dayi yana fadin"Ina sauraronka, Fadamin meke damunka rabin raina"

Ɗagowa yayi da fuskarshi wadda tuni ta jiƙe sharkar da hawaye, cikin rauni na murya yace"baba, Bana jin
daɗin yadda wasu suke guduna saboda rashin asalina, meyasa sauran mutane ba kamar kai da daddy
mubarak suke ba"? Zuciyar baba obie ba karamin karaya tayi ba, nan take ya gane gori akayi masa, bawan
Allah tsantsar tausayinsa ne yakama shi.

Cigaba da yin magana yayi"Na tsani kaina baba, Rashin asalina Yana neman Yaja min na rasa abunda
nakeso, kowa ya buɗi baki sai yace ni ɗan mai aikine bani da asali, Har shege ake kirana baba" daƙyar ya
kare maganar wani irin kukane Yaci karfinsa da sauri Baba obie Ya janyoshi zuwa jikinshi sosai Ya rungune
shi, Yana lallashin shi.

"Toh toh ya isa ka yi shiru, Bana son Kana sanya damuwa aranka, Kukan Ya isa haka, kowani ɗan adam da
ka gani a duniyar nan da irin tashi ƙaddarar, babu wanda Allah baya jarabta, inaso ka rungumi wannan
amatsayin ƙaddararka, Kada ka ta6a bari wani Yasa ka canza tunaninka, Allah Shi yake son ganin rayuwarka
haka, Kuma shine zai nema maka mafita" nasiha mai ratsa zuciya baba obie Yaci gaba dayi mashi har saida
yaji ya daina kukan tukunna Ya raba shi daga jikinshi
Cikin kulawa yace dashi"Yanzu fada min wanene Ya tsokane ka"?
Shiru yayi batare dayace komai ba, baba obie ya fahimci bayason ya sanar da shi, hakan yasanshi cewa"Ko
da yake basai ka fadamin ba, ni da kaina zan binciko wanene, kuma zan hukuntashi" ya fada yana daure
fuskarshi alamar ranshi ya 6aci.

"Baba," Kallon shi obie yayi ina sauraronka


"Kamar yadda nasaba fadamaka,Yau ma zan maimaita maka, Ni dai inason family ɗinka, Ina alfahari daku,
nayi fatan ace nima ina ɗaya daga cikin jikokin ka sai dai Allah bai nufa"

Wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskar baba obie.

"Jazz baka ɗauke ni kamar yadda na dauke ka ba, ko da yake ba laifinka bane, laifin wadanda suke yi maka
gorine, sune sukasa kake jin kanka bare afamily dina, amma inaso kasani, baba obie baya yi maka kallon
bare, inasonka jazz kamar yadda nakeson jikokina, Kamar yadda kake fatan ka zama daya daga zuri'ata
nima haka nake fatan ka kasance" yayin da baba obie ke yin maganar, wani irin sanyi da daɗi ne ke tsuma
zuciyar jazz, har abada bazai ta6a mantawa da halaccinsu agare shi ba.

Ganin Ya faranta masa raine yasa baba obie cewa"namanta ban tambayeka ba, Ya jikin naka"?

Fuskarshi dauke da murmushi Yace"naji sauki, nagode na kulawarka agareni"


Jinjina kai baba obie yai"gobe idan Allah yakaimu, Ina fata zaka halacci Dinner din Hateem"

Jim ya ɗanyi harga Allah baison zuwa kodan gudun a ci mutuncinsa, amma saboda yana son ya faranta ma
baba obie yasa shi cewa "In sha Allah tare dani za'a buɗe taro"

Murmushi baba obie yai masa"Naji dadin jin hakan rabin raina.

Jan shi da fira baba obie yai, kamar wani abokinsa, tuni jazz ya saki jikin shi.

*💋 UMMIN AMERICA❤*

Duk Yinin Yau Bata fito daga ɗaki ba, ta killace kanta tun safe bata jin daɗin zuciyarta, duk ta ƙuntata kanta,
tayi jiran zuwansu unaisah su shigo don su ɗe6e mata kewa sai dai shiru babu alamarsu, tuntana sa ran
ganin su har ta fidda ranta, ta ƙundundune kanta cikin lallausar bargonta, Sallah ce kaɗai take tada ta daga
saman gado
Har ta fara nutsawa cikin baccinta kwatsam wayarta dake ajiye kan nightstand ta soma yin ruri, da wata
irin kasala ta ɗago da kanta, sumar kanta duk ta hargitse babu gyara, laluba Hannu tayi ta kamo wayar
batare data duba sunan mai kiranta ba tayi picking tare da kara wayar a kunnanta.

Sautin Muryar NATASHA ne ya Daki Dodon Kunnanta"nayi fushi Kin manta dani ko"? ta faɗa cikin
harshen turan ci.

Muryarta da kasala Ta furta"ba haka bane Natasha, Kina araina, dake nake kwana dake nake tashi"

"Ban yarda da kalamanki ba Ummi, Idan Dagaske kinyi kewata meyasa baki kirani ba? Sai da na kira ki ni
da na damu dake ko"?
Shiru tayi na ɗan wani lokaci har sai da Natasha Ta furta Naji kinyi shiru tukunna taja numfashi tana
faman sauke ajiyar zuciya tace"bansan yadda zanyi maki bayani ba NATASHA, ni kaɗai nasan halin da nake
aciki, ina cikin damuwa, Ina cikin kaɗaici, Rayuwata a ƙuntace take natasha, bani da wani ƴan ci, ba wanda
Ya damu dani, tun safe bana jin daɗin jikina babu wanda ya leƙo ɗaki na don Yaga awani hali nake aciki....
"Muryarta na rawa ta ƙare maganar, tamkar zata fashe da kuka, hakan Ba ƙaramin ɗaga Hankalin Natasha
Yayi ba, Jin sautin miryar aminiyarta da alamun matsananciyar damuwa..
Cikin saurin mirya ta furta"Ummi, muyi magana ta video Call, Inason naganki ko hankalina Ya kwanta"

"Toh, amma kafin nan zan shiga toilet, Ƴan mintuna kaɗan Idan na fito zan kiraki" natasha ta amsa mata
da toh, bayan ta yi rejecting Kiran, ta daura wayar kan drawer, kafin Ta sanya hannu ta yaye bargon data
lullu6a da shi, Jallabiya ce a jikinta launin dark ash, saukowa tayi daga kan gadon ta nufi toilet, After Some
minutes ta fito fuskarta da alamun lemar ruwa, Laptop dinta dake ajiye kan desk ta dauko ta koma kan
gado ta zauna daga tsakiya ta ajiyeta agabanta, kafin ta buɗe ta soma sarrafata, Natasha ta kira video Call
nan take ta ɗaga, kallon juna suka soma yi tamkar suna a wuri ɗaya, Natasha tana a kishingiɗe saman
beach chair dake a ga6ar teku, babu suturar mutunci a jikinta, dama ita bata cika son sanya suturar da zata
rufe mata tsiraicinta ba, tafi sha'awar ta sanya pant da bra.

cikin harshen turanci suke yin magana.


"Yanayin fuskarki Ya tabbatarmin da bakyajin dadin Ummi, Ki faɗamin meke damunki? Waya ta6a min ke"?

Yamutsa fuska Ummi tayi tamkar batason furta maganar tace"kamar yadda na faɗa maki bana jin daɗin
jikina, narasa gane meke damuna, amma ina da tabbacin hada kaɗaici, ban ta6a ƙuntataba Irin na Yau, Jin
kaina nake tamkar Ina a prison"

Cikin kulawa Natasha tace"meyasa ba zaki janye aikin da Commender Ya baki ba? Ummi dama ni nasan
bazaki Iya jurewa ba, tuntuni naso In gargaɗeki saboda ba zaki Iya ba, mu da muka saba da yawo kullum sai
mun fita wurin abokan harkar mu, taya zaki Iya jure rayuwar kulle"? Ta faɗa tana mai dubanta,
Dafe kai Ummi tayi da hannu ɗaya"Har yanzu banyi danasanin kar6ar aikin kula da yaran nan ba, Saboda
Inaji araina akwai wani alkhairi atattare da zamana da su, shiyasa bana danasani, ni kawai abunda ke
damuna rayuwar kullance ke banaso, Yana ƙuntata Rayuwana, hada ƙarin Yaran da suke ɗebe min kewa
basu zo wurina ba yau, ni kuma nakasa tashi naje gare su" fuskarta a yamutse tayi maganar
"Har Yanzu ba zaki fahimce ni ba Ummi, Ni inaso na kwatarmaki ƴan cinki ne, Inason farin cikin ki, Kina
buƙatar abokan Harka, kefa ba irin matan da za'a ƙuntata ba ne...' tunkan Natasha ta ƙare maganarta,
ummi tayi saurin tarar numfashinta da cewa

"Akwai labari mai daɗi, nasan idan na fada maki zakiyi mamaki"

Ta faɗi hakan ne don batason Natasha taci gaba da yi mata zancen Ajiye aikin da take Yi.

"Naƙosa naji labarin nan fadamin mana" ta fada tana sakin murmushin shaƙiyanci.

"Mutumin Ya ziyarce ni Har cikin gidan da nake,"

Waro idanu waje natasha tayi da mamaki ta furta kina nufin Big Boss? Ya ziyarce ki? Ɗaga mata gira ummi
tayi alamar eh.

"Amma ya akai ya iya shigowa gidan Jami'an Isod, bayan kin faɗamin acikin sharuddan da suka baki, babu
shige babu fuce basu buƙatar wani naki yazo inda kike, har zuwa lokacin da kika kammala Yi masu aikin su"
ta faɗa a kagare da son jin ƙarashen xancen.
Dariyar shaƙiyancin Ummi tasaki tamkar babu damuwa aranta"kinsan mutumin na dabanne, ni kaina
bansan tayaya akai ya shigo gidan ba, Har tambayarshi nayi sai yace min idan na yarda dashi indaina
tambayarsa.... " dariya natasha tayi cike da nishaɗi tace"Namijin Duniya, Nayi kewarshi ummi, kullum cikin
begen ganinsa nake yi, yayi min nisa yanzu, ba kamar lokacin da nake yi mashi rainon babynsa Pretty ba,
tun da Ya kar6i Yarinyar sai nayi dagaske nake ganin shi, ko wayana baya picking... " kafin Natasha ta ƙare
maganar Ummi tayi hanzarin tarar numfashinta da cewa"wai ina yarinyar take ne? Na jima ina son na
tambayeki ita, nayi missing dinta, tun ranar dana fara Yin tozali da ita naji kaunarta ta shiga raina, duk da
bata jin magana amma tana da kyau"
Natasha tace"hmmm, Ummi Ya raba ni da ita, tsawon watanni, duk idan na tambayeshi ina baby Pretty na
sai yace min ya mayar da ita wurin mamanta, har alfarma na nema awurin shi akan ya amince min inbiyo
shi nigeria saboda ina son ganinta amma Ya hanani.... "muryarta na rawa ta ƙare maganar idanunta sun
cicciko tab da kwalla.

"Ummi Inason yarinyar nan, Ina ƙaunarta, nayi fatan ace ni na haifeta ko dan saboda mu kasance atare
har abada, mun shaƙu da juna, na saba da ita, Amma yayi min yankan ƙauna.... " tunda tafara magana
ummi ta natsu tana kallon fuskar Natasha ta cikin screen din laptop tamkar suna awuri ɗaya.

"Ummi nasan zaki Iya taimaka mani, tunda Yana kaunarki, Yasha fadamin ke kadaice kike Iya sarrafashi son
ranki, please kiyi amfani da damar da kika da ita, Ki lalla6a shi Ya dawo min da baby pretty" cikin sanyin
Murya ta ƙare maganar, Ummi dake kallonta tuni tausayinta Ya kamata, bata ta6a ganin Natasha tana
zubar da kwallarta akan wani ɗan adam ba sai akan babyn da take mutuwar so, tasan da irin kaunar da
take yima yarinyar a lokacin baya.

Cikin kwantar da murya ummi ta furta"Am sorry, Kinsan bana son ganin hawayenki, zan Iya yin komai
akanki, saboda halaccin ki agare ni, Kin wuce ƙawa a wurina sai dai ƴar uwa, saboda kin kaunace ni a
lokacin da kowa yake guduna, abun da nakeso dake ki kwantar da hankalin ki, zanyi kokarin ganin na
shawo kanshi don ya dawo maki da babyn ki"
Murmushin farin ciki natasha tasaki tana fadin"thank u ummi, nasan zaki iya yin komai saboda farin cikina,
shiyasa nake ƙara kaunarki, ina nan ina shirye shiryen zuwa Nigeria saboda ke"

Martanin murmushin ummi ta mayar mata,


"Ina handsome boy din nan, namanta ban tambaye ki shi ba"

"Bashi da lafiya, Yana a kwance"


Yamutsa fuska Natasha tayi"najiye mashi ba dadi, Allah Ya bashi lafiya, har yau ban manta da fuskar shi ba"
Murmushi Ummi tayi mata" dama ke ay bakya mantawa da abu mai kyau, naga kin kirani da layinki Na
england, hakan na nufin kin koma gidanki"?
Ɗaga mata gira tayi alamar eh. Jinjina kai ummi tayi, shiru sukayi na wani lokaci yayin da suke kallon juna
batare da ƙyaftawa ba.
"Kin tsareni da ido Kina kallona, Kamar akwai wani abu da kikeson fadamin" acewar natasha ta faɗa tana
ɗage mata gira.
Dariya Ummi tayi, Harta Buɗe baki da niyar furta magana, Sautin knocking ƙofar da akayine Yasa ta fasa yi
mata maganar,
"Zan Kiraki Anjima Ki kula min da kan ki"
"Bangaji da jin muryarki ba ummi, amma shikenan zan jira zuwa anjiman inma kin manta baki kirani ba, Ni
zan Kira ki, ki kula min da kanki and pls ki daina sanya damuwa aranki" a hankali ummi ta furta mata"toh,
nagode da kulawarki agare ni" bayan sunyi sallama, Ta kashe video Call din, ta sauko tare da laptop din a
hannunta, ta nufi desk ta ɗaurata, kafin ta shiga wurin closet dinta, mayafi ta daura akanta.

ɗaga Murya ta yi Wanene"?


Daga waje tajiyo Muryar Batool Tana fadin"aunty Ummi ni ce" wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta jin
muryar Batool.

"Ki shigo daga ciki," turo ƙofar batool tayi tare da shigowa ciki, tana bin dakin da kallo kafin ta ɗaura
idanunta akan fuskar Ummi, Murmushi suka sakarma juna
"Nayi fushi Batool, sai yanzu zaki tuna dani? Nayi tsammanin kece mutun na farko da zaki zo gare ni idan
kika ji shiru ban fito ba, amma sai naji shiru babu ke babu unaisah" tafaɗa tana haɗe mata fuska alamar
ranta Ya 6aci.
"Aunty ummi am sorry, Kina araina, tun ɗazu nake taso in shigo wurin ki'
Miƙa mata hannu Ummi tayi da sauri Batool ta ƙarasa gabanta tare da faɗawa kan chest dinta, sosai Ummi
tai hugging dinta.

"Nayi missing dinki My babe, kun barni a daki ni kaɗai inata kewarku, Ina unaisah ne"! Ta faɗa batare
data raba jikinta daga na batool ba.

"Nima bansan inda take ba, ɗazu muka rabu"


"Okey,ina fata kina lafiya, " ɗago dakai Batool tayi"Lafiyata lou, amma ke kamar baki da lafiya"
Shafa gefen fuskarta ummi tayi"bana jin dadi, amma kada hakan Ya dame ki, ganinki da nayi ya faranta
raina" ta ƙare maganar tare da ruƙo mayafin Pakistan din batool"kayan sunyi maki kyau sai naga kinyi min
kama da wata Old friend ɗina da muka rabu da dadaɗewa, kamar ita ta haifeki, Itama doguwace fara,
Mom dinta balarabiya ce"
Murmushi batool tayi"amma ni da Unaisah nake kama"

Girgiza kai Ummi tayi"No, baki kama da Unaisah kun dai yi yanayi da ita"

Kwa6e fuska Batool tayi saboda ita tafison ace tana kama da Unaisah, ummi ta fahimci hakan sai tayi
saurin cewa"wasa nake maki, dama don in ga reaction dinki ne, gaskiya kuna kama da ita sosaima kamar
twins" jin hakan yasa batool sakin dariyar farin ciki, ummi dake kallonta batayi mamakin hakan ba ta riga
data fahimci tsantsar ƙaunar da suke ma junansu.

"Mu zauna ki tayani fira, Ko baki gaji da tsayuwa bane"

"Aunty ummi, nasan kina jin yunwa, ki tafo muje falo zan sama maki abunda zaki ci" wani irin kallon ƙauna
ummi keyi mata ba ƙaramin dadi take ji ba idan Batool ta nuna damuwa akanta.
Ruƙo hannunta ummi tayi acikin nata atare suka fito daga dakin.

Sautin Muryoyinsu Naufal ne Yajawo Hankalin Ummi Ga kallon su, tun Dazu suna a falo, Tare da Boss Man,
Sun tasa shi gaba sai surutu suke zuba mashi.

Jin takun Takalmansu Yasa su dagowa suka kalli su Ummi dake saukowa down stairs, Har suna haɗa baki
wurin ambaton sunanta Aunty Ummi.
Saukowa Jamimah da azeeza su ka yi daga kan sofan da suke zaune, da gudu suka nufe ta, Hannah da
Parveen ma suke miƙe suka nufe, wani irin daɗi taji aranta,
Ɗaya bayan ɗaya ta soma rungumarsu a jikinta,
"Aunty Ummi, Yanzu kika tashi daga bacci"? Azeeza ce tayi mata tambayar
Girgiza mata kai tayi alamar a'a
Parveen tace"Ko dai baki lafiya" Harara Ummi ta jefa ma Parveen tare da cewa"kun damu dani ne? Meyasa
ba ku zo bedroom ɗina kun duba ni ba? Shiru sukayi sai jamimah ce tai kokarin cewa"mantawa mu ka yi"
Jan kumatunta Ummi tayi da hannu"Aku sarkin ɗumi, Na riga da nage baku kaunata, Shiyasa baku damu
dani ba" ta faɗa haɗi da marairaice masu fuska,
"Wallahi aunty Ummi Muna ƙaunarki, kuma mun damu dake" Hannah ce tayi maganar
"Ni dai Inasonki aunty Ummi, kiyi hakuri idan mun 6ata maki rai," murmushi ummi tasakar ma Azeeza da
tayi maganar.
Ruƙo hannunta Jemimah Tayi"Aunty ummi nima ina sonki"
"Naji na Yarda kuna sona, Yanzu mu shiga ciki," ta fada tare da Jan hannun Batool suka nufi ciki tare da su
Hannah
Tunkafin Su ƙaraso, Boss man Yake Kallon Ummi, sam ya manta da ita.
"Barka da hutawa Yalla6ai, Fatan ka wuni Lafiya, Ya iyali"
A hankali Ya furta"Lafiyalou Ummi, Ina fata kema haka"? Ɗaga mashi gira tai alamar eh, ta faɗa tare da
samun wuri saman Sofa ta zauna, suma sauran duk suka zauna.

hankalin Sajeed na akan screen din wayar Unaisah, Haris da javed suna zaune gefe da gefen shi tare da
naufal sai kallon Game din da Yake bugawa suke yi, baijima da sauke shi akan wayar ba.

Gyaran Murya Ummi tayi masu atare suka dago suna kallon ta.
"Sannunku, ba hello ba Hi kun samu Waya kunata danna waya baku ita ne"
"Ta Unaisah ce," Acewar Sajeed
Da mamaki Ummi tace"Unaisah ke da waya iphone15pro? Amma ban ta6a ganinta ba"
"Dr Laurace ta bata Kyautarta, ɗaya daga cikin Likitocin da suka yi jinyarsu a america"
Boss man ne Ya bata amsa, Jinjina kai tayi.
"Ina ita Unaisah dinne"? Tayi tambayar tana kallon su
Boss Yace"Bansan meya tsayar da ita ba, tunɗazu da muka shigo tare da big guy Ya tafi da ita zai nuna
mata kitchen din gidan nan ban ƙara ganin ta ba, ba mamaki ta tsaya taya masu aiki girkin dinner"

"Dan Allah ka nuna min kitchen din, Inaso In kar6o ma aunty Ummi abinci, Yunwa take ji" acewar Batool.
Murmushi boss man Yayi yana dubanta yace"kin damun da auntyn nan naki da alama, kada ki damu, bari
na kira big guy awaya, idan suna a kitchen din zansa akawo mata abincin.... " kafin Ya ƙare maganar,
Parveen tayi saurin cewa"Dan Allah Nima zanci" dariya sukayi gaba dayansu.
Ummi tace"foodie, Baki Gajiya da cin abinci, shiyasa kika fi sauran ƴan uwanki jiki"
Kwa6e fuska tai"ay bani kadai bace me cin abincin ba, Ki kalli kumatun jamimah sunyi manya manya da su"
maganarta ta basu dariya.
Harara jemimah ta watsa mata"ay dai ban kaiki Cin abinci dayawa ba, Ni madara da bonbita nake sha, Sai
dafaffan kwai da Fika fikin Kaza," boss dake kallonsu murmushine dauke akan fuskarshi, Firarsu ba karamin
nishadi take sanya shi ba
Wayarshi Ya zaro daga aljihu Ya danna ma Big guy kira, Bugu uku Yayi Picking

Miƙewa yai da sauri Ya nufi cikin falon nesa da su ya tsaya saboda hayaniyarsu.

"Malam Ina ka shiga ne? Ka tafin mun da rabin raina"

On the other hand sautin dariyar Big guy ta karaɗe Kunnuwansa,

"Nifa Yanzu Haka Ina daki kwance saman gadona"

"Bana son Iya shege, To ita ina kabarta?

"Ka riga da kasan Halin Jarin naka, yarinyarce da kiriniya, Tunfa dazu dana nuna mata kitchen din nace
mata ta dawo cikin yan uwanta, bayan na fada mata hakan na wuce room dina, yanzu haka bata wuce
kitchen din, Cikin kattai" ya karasa maganar Yana dariya.

Daure fuska boss yayi tamkar Yana agabanshi,


"Zamu hadu dakai ne, Allah idan wani abu Yasamu Yarinyar nan jikinka ne zai gaya maka dan rainin wayau"
ya fada tare da yin rejecting kiran,
Cikin takun sauri Ya nufi hanyar zuwa kitchen din, ba laifi akwai tazara tsakanin kitchen din da main falo,

Lokacin da Ya Isa katafaren kitchen din gidan tamkar a restaurant tsabar haɗuwarshi, kai kace ba wurin
Girka abinci bane saboda girman shi da ƙawatuwarshi, An zuba kayan aiki masu tsada da inganci, gaba
ɗaya masu girka abincin Gidan Jami'an Isod ne cikin chef'uniform, matasan samari masu jini a jika, daga
ganin Yadda suke aiki zaka shaida kwarewarsu a 6angaren catering, ko mace bazata nuna masu Iya sarrafa
abinci ba, A ƙalla sunkai su Bakwai, Babu wanda Ya lura da shigowar Taj acikinsu, Gaba ɗaya Hankalinsu na
akan Unaisah, dake agaban kitchen island tana Yanka masu kayan Lambu, abun da ya ɗaure ma taj kai,
ganin Yadda sukayi mata rumfa kamar zasu haɗiyeta tsabar yadda suke binta da mayataccen Kallo, Ta saki
baki sai Labari take basu su kuwa sun Kasa kunne suna sauraron daddaɗar muryarta, Tunda suka kafe ta da
idanunsu ko kyaftawa basa yi kamar zasu haɗiyeta.

Gyaran Muryar da Taj yayi masu ne Yaja Hankulansu ga dubanshi, kamar sunga wani mugun abu, A
gaggauce su kayi saurin barin Inda Take, kusan atare suka buga ƙafa Haɗi da sara mashi.
Kallon Harara Ya watsa masu, Cikin harshen turanci Ya furta"wannan wani irin gangancine zaku bar Yarinya
tana amfani da wuƙa? Kun wani tsareta da idanunku kamar zaku lashe ta" Sunnar dakai su kayi Suna faman
sosa keya suka hada baki wurin furta"sorry Sir, ba laifin mu bane, Itace ta buƙaci damu koya mata girki,
munyi kokarin Hanata amma saita sanya mana rigima"
Wurga eye balls dinsa Yayi akan Unaisah dake Kallon shi, Har ta ajiye wuƙar hannunta, nufo shi tayi
fuskarta da murmushin Yaƙe tace"ay ni nace su bani In tayasu aiki, Kuma dama Na iya ba yar koya bace" ta
fada tana ruƙe qugunta da hannu.
Wani kallo Ya jefa mata me kama da harara, bakomai Yake tunawa ba face lokacin da tana yar ƙaramarta,
ranar daya tafi aiki yabarta a gida tana jin yunwa taje ta kunna cooker gass da sunan zata yi girki, wuta ta
kama a gidan, wai yau itace take mashi kurin ta Iya girki ba yar koyo bace? Girgiza kai Yayi haɗi da yin
murmushi tacikin face mask dinshi
"Daughter, ƴan uwanki sunata nemanki, Yakamata Kizo Mu koma falo" maƙe mashi kafaɗa tayi"ay bamu
gama girkin ba"
"Bana son gaddama, zo ki wuce mu tafi"
Marairaice mashi fuska tai"dan Allah kabarni wallahi inason In Iya girki kala kala,"
"Kada Ki damu, zansa a koya maki amma ba yanzu ba, dokar Aikin mu ce mace bata shiga hurumin mu,
baki ga maza bane a kitchen din"? Cikin lallashi yayi mata maganar Yana nuna mata chefs din dake
tsaitsaye cirko cirko suna kallon su
"Yalla6ai, da dai anbarta ta koya tun da ta nuna tana so, kuma ni aganina maca ce ita, wata rana zataso tayi
ma mijinta.... "Tunkafin chef din daya dauko Maganar Ya karasa boss Yayi mashi wani kallo mai nuni da
kashedi, Hakan yasa shi yin saurin Katse maganar,
Janyo hannun Unaisah Yayi dakarfi Ya fito da ita daga kitchen din, Chefs din basu ji dadin zuwan Shi ba, Ya
raba su da Yarinyar data ɗe6e masu kewa yau, zuwanta Ya faranta masu rai, sunji dadin surutun da tadinga
yi masu, komai nata burgesu Yake yi.

Ranta Ya 6aci, Ganin yadda ya janyota daga kitchen din, da sauri ta fusge hannunta tana fadin"Ni ka ƙyale
ni, in tafi da kaina" Ta faɗa tana daure mashi fuska, Sam Yakasa ce mata komai sai dai kallonta da yake yi.

"Bansan meyasa ka takura rayuwata ba, girki fa kawai na roƙa kabarni In tayasu amma ka hanani, dan Allah
menene alaƙata dakai ne? Na lura so kake kana Yin iko dani, Idan don saboda taimakon da kukayi mana ne
ay dan Allah ku ka yi ko"? A fadace ta faɗa tana zare mashi gray eyes dinta tamkar zata rufe shi da bugu,
Har saida Yaji gabanshi Yaɗan fadi, sauƙinta ma yasan halinta,
"Meyasa ni kadai kake ma haka?
"Saboda ke jini na ce" a zuciyarshi Ya furta maganar
"Kiyi haƙuri Idan na 6ata maki rai, bana son 6acin ranki, Ƴan uwanki ne suke ta nemanki, bayan haka
kamar yarda na fada maki dokar aikin mu ce mace bata shiga hurumin mu, waɗannan chefs din da kike
gani dukansu a lokacin baya ba mutanan kirki bane, Dayawansu Ƴan shaye shaye ne da masu bin matan
banza, wasun su mugayen ƴan ta'adda ne wadanda suka gagari Iyayensu da hukuma, Ire iren su chief Yake
kamowa Ya koya masu hankali, Idan suka shiryu sai ya maida su Jami'an Isod..."

Waro ido waje tayi jin Ya ambaci mugayen ƴan ta'adda.

"Ba Zanso abun da zai cutar min dake ba, Haƙƙina ne kula da rayuwarki Unaisah dan Allah kada ki hanani
Yin aikin lada... " in cool voice ya faɗa...

Wani irin kallo yaga tana bin shi da shi, kamar akwai wani abu da take son ganowa
Muryarta na rawa ta furta"dan Allah ka cire min face mask din fuskarka inason ganinka"
Girgiza mata kai yayi"zaki ganni amma ba yanzu ba, amma meyasa kike son ganin fuskata"?
"Saboda muryarka, tayi min kama da ta daddyna wallah sai nake ji kamar daddyna ne kai, duk da nasan
ma ba shi bane, ina ji araina baya araye ma" idanunta har sun ciko da kwalla.
"Kina ji aranki ni daddyn ki ne" ɗaga mashi kai tayi alamar eh"
"Ki ƙaddara aranki cewa Ni ne" ya faɗa tare da ruƙo arm dinta, Ya janyota jikin shi, haɗi da kwantar mata
da kanta saman kirjinsa, wani irin sanyine taji ya ratsa zuciyarta, lumshe idanunsa yai a hankali ya sanya
hannu tare da zame face mask dinsa, Sumbatar head dinta yai, kafin da sauri ya maida mask din fuskarsa.
Tsawon mintuna biyar cuf suna manne da juna, sai daga bisani ya raba ta da jikin shi, baiwar Allah jikinta
yayi sanyi tamkar an watsa mata ruwan sanyi,
Shafa gefen fuskarta yayi da tafin hannunsa"Ina sonki my daughter" murmushi tayi mashi"Nima ina sonka
daddy na"

*Daga Alƙalamin Boss Bature✍️


*

*(Kaɗan daga cikin na sati mai zuwa idan Allah yakaimu da rai da lafiya, unaisah zatayi waya da Benazir😍
Garkuwa zaiyi tashin bazata, kada ku bari abaku labarin walimar hateem😂🤣 Ni kaina zumuɗin ta nake yi🔥🔥
🔥)*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan
layin 08169856268*_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_

‫🔥✊💋سجن القدر‬

~Takun Ƙarshe🔥~

‫😘💘💋قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة‬

An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘

Daga alƙalamin Boss Bature💋✊

__________________________✍️
Har Ya ruƙo hannunta za su shiga ciki sai kuma Ya dakata yana faɗin "Au namanta, Auntyn ku ummi tana
buƙatar abinci ban sani ba, ko akwai abunda chefs suka gama girkawa yanzu"? ya tambaya yana duban ta.

"Akwai naga sun kammala Rice and chicken stew tare da coleslaw hada zobo ma ... " kafin ta ƙarasa lissafa
mashi yace"Okey, Ki jira ni, bari na shiga ciki in kar6o mata" amsa mashi tayi da toh.

Bayan shigarsa kitchen din ta soma tunanin ko awani hali Garkuwarsu ya ke a ciki? ta yi matuƙar damuwa
da shi, ganin shi da take yi a mawuyacin hali ba karamin karya mata zuciya ya ke yi ba, rabon da ta
sanyashi a idanunta tun da asuba da su ka shiga yi mashi addu'a, da tunanin shi ta wuni ta bari sai da
anjima ta shiga duba shi.

"My babe, I'm back" Muryar Boss man ce ta fargar da ita, da sauri takai dubanta gare shi, Hannayen shi
ruƙe da handle din wooden tray mai faɗi, daga saman shi haɗaɗdun warmers ne babba da ƙarama tare da
plates da sauran tarkacen kayan abinci"

Miƙa mata yayi kar6i nan, ta sanya hannu ta kar6a cikin kitchen din Ya koma jim kaɗan Ya dawo hannayen
shi ruƙe da wani madaidaicin faranti mai ɗauke da mixed drinks masu sanyi.

Ganin tana kallon shi yasa shi kashe mata ido ɗaya, murmushi tasakar mashi, a tare suka jera zuwa cikin
falon.

Jikin Batool Har Kerma Yake Yi wurin mikewa da wani irin sauri ta nufi Unaisah zata rungumeta, ganin Tray
a hannunta yasa ta dakata tana faman ɗaure mata fuska tace"Ina kika shiga inata nemanki"

"Ina a kitchen fa, Girki Na tsaya taya masu aiki" ta faɗa tare da wucewa ta sauke tray din hannunta saman
Carpet, Parveen tun da tayi tozali da Abinci takasa samun sukuni, Tafi kowa zalama.

A Plate Batool ta zuba ma Ummi abincin ta hada mata da pineapple juice ta miƙa mata, fuskarta da fara'a
ta kar6a tana fadin nagode My babe," a tsanake ta soma Ci.

Ɗaya bayan ɗaya unaisah ta soma kasa masu abincin tana miƙa masu a plate, bayan ta gama da su itama
ta zuba nata tare da Boss man a plate ɗaya, suka zauna suna ci gwanin ban sha'awa, falon Yayi tsit baka jin
sautin komai saina taunar abincin da suke ci...

"Ummi Ina son Yin magana dake bayan sallar magrib" Boss ne yayi mata maganar, amsa mashi tayi da
toh.

"Amma wannan ɗin abincin daren mu ne"? Acewar Parveen, Harararta Naufal Yayi.

"Kusan ƙarfe shida na marece, A haka Har kike tambaya, toh abincin dare ne, mu da cin wani abincin sai
gobe da safe in Allah yakaimu" javed ne Ya bata amsa Yayin da yake kur6ar lemu me sanyi.

"Ba'a magana idan Ana cin abinci," Boss ne ya faɗa yana duban su.

"Dariya fa da murmushi suma ba'ayi"?

Jemimah ce ta jefa mashi tambayar yayin da take cunkusa abinci abaki tana tauna.
Dariya suka sanya gaba ɗayansu cikin raha.

"sajeed Ina wayata"

Dafe kai Yai da hannu ɗaya"Am sorry sister, Na cinye maki chargy, bansan ko kina da charger ba"

"Akwai charger bani wayar" da sauri ta miƙe taje gaban sofa din da yake a zaune, Wayar Ya zaro daga
trouser pocket nasa ya miƙa mata ita.

Tasa hannu ta kar6a, kafin ta nufi bedroom dinsu, shigarta keda wuya wayar hannunta ta soma ringing,
tana kokarin ɗaga Wayar ta kashe kanta kamar tayi hauka saboda ta gane number da suka kirane ita da
sajeed.'
Cikin takun sauri ta nufi backpack din su, ta buɗe ta dauko cazar wayar ta jona a socket, akan idonta wayar
tayi haske alamar ya ɗauka, lumshe idanunta tayi tare da jingina bayanta jikin gadon, zuciyarta a cike fal da
tunanin shi.

*💋NAZLI👑*

Sautin daddaɗan kiɗa ne da ke tashi a katafaren gym room (ɗakin motsa jiki) da ke a gidan prime minister,
an ƙawata shi da manyan injinan motsa jiki, a tsaye take saman thread mill tana gudu cikin shiga ta kayan
motsa jiki, sport bra tare da short launin black colour, sunyi bala'in yi mata kyau, sun bayyana farar fatarta
sol ko kwarzane babu, tamkar bata ta6a yin rarrafe ba arayuwarta saboda hasken fatarta harta gwiwar
ƙafarta tayi jawur da ita, dirar mace doguwa ga kyan sura, ta ɗaure lallausar baƙar sumar kanta sai salƙi
take yi da sheƙi ta sauko har saitin waist din ta, gaba ɗaya ta tattara nutsuwarta akan abun da take yi,
sautin music din ba ƙaramin ni'ima yake samar mata ba, kyawawan idanunta na akan tanƙameman
madubin dake manne da bango, zufa ce ta soma tsastsafo mata ta ko'ina ta jiƙe sharkaf da ita, babu
alamun gajiya atattare da ita, daga gani ta ƙware a 6angaren gym.

Bakomai ne acikin zuciyarta ba, face zallar begensa, duk yadda taso ta hana kanta tunawa da shi abun
yaci tura, tayi tunanin zata iya sarrafa zuciyarta wurin hana ta tunaninsa sai dai abun yaci tura, a kowani
daƙiƙa son shi ƙara ninkuwa yake yi a zuciyarta, ga dukkan alamu Nazli batasan menene So ba, ko da yake
girman kai da izza sun hana ta gane cutarwar da take yima kanta, shiyasa ta kasa miƙa wuya"

Tunanin shi ne ya haifar mata da jin Kasala, ba arziƙi ta dakata da motsa jikin, ta kai hannu ta ɗauki short
towel fari ƙal ta soma tsane jikin ta da shi, bayan ta kammala fitowa tayi daga gym room din ta nufi
bedroom dinta, kai tsaye ta shiga bathroom domin yin wanka.

Shigowa ɗakin Yazrin tayi cikin shiga ta riga da wando black and white, tayi rolling veil akanta, hannunta
ruƙe da wayarta.

Ganin babu ita a dakin yasa tayi tsammanin ko ta fita ne har zata juya ta juyo motsin ta a toilet da sauri
ta la6e a bayan labule.

Gently ta zuro ƙafafunta dake sanye cikin slippers, bathrobe ce a jikinta fara ƙyal, hannunta ɗaya ruƙe da
towel sai faman tsane sumar kanta take yi.

Yazrin dake a la6e bayan labule, wayarta ta danna ta shiga camera ta ɗage labulen a hankali ta soma
ɗaukar Nazli video batare da sanin ta ba.

Dressing mirror ta nufa cikin takun qasaita, wasu tsadaddun mayukan gyaran jiki ne asaman mirror din,
bayan ta zauna ta soma bin ko'ina tana shafe shi a tsanake, kafin ta dauko bakhhoor burner ( turaren wuta)
ta soma turara jikinta da sumar kanta, komai nata cikin aji take yin shi, Nazli macece mai tsafta ga son
gayu, kuma ma'abociya son ƙamshi.

Duk wani motsinta, Yazrin na kallonta ta cikin camera, bayan ta gama gyaran jikin nata, closet ta nufa jim
kaɗan ta fito, har ta canza kayan jikin ta zuwa kimono robe, yazrin da ke ta daukar ta video kayataccen
murmushi ne kan face dinta, aranta ta ayyana ukhty Nazli badai iya gayu ba, bata gama zancen zucin nata
ba, taga Nazli ta haye saman Royal bed dinta hannun ta ruƙe da wayarta, bakomai take kallo ba face
hotonsa, har zooming dinshi take yi da zira ziran yatsun hannunta, hoton da take kallo tsohuwar ajiyace a
kalla yakai shekara biyar, lokacin yakai masu ziraya a canada, ba tare da sanin shi ba ta dauki hotan, dama
duk in yaje basa jituwa da Nazli, har ya bar ƙasar basa sakarma juna fuska kai kace makiyane, Yazrin ce
kadai suke mutunci da juna, kuma a lokacin suna matuƙar ƙaunar junansu, amma izza ta hanasu bama juna
kulawa sai dai su yi magana ta text message, tamkar basa a gida ɗaya.

fita tai daga gallery ta shiga wurin messages dinsu


Har ta rubuta "I miss u.... ' sai kuma ta goge, zuciyarta na raya mata zubda aji ne ta nuna ta damu dashi,
shi ne yakamata yafara yi mata magana
Jefar da wayar tayi gefenta, tare da kai hannu taja lallausan duvet dinta ta lullu6e fuskanta, ganin hakan
yasa Yazrin fitowa daga bayan labulen cikin sanɗa ta nufi gadon, tare da hayewa ta janyo wayar Nazli cike
da fargaba cikin sa'a ta ɗauko ta batare da security din wayar ya shiga ba, hakan ba karamin dadi yayi mata
ba.

Whatsapp dinta taso ta shiga sai dai kash password Ya hanata, tunani ta soma yi me Nazli ta rubuta a
matsayin password dinta?

Gudun kada ta tayi mistake ta samu matsal


Zurfi tunani ta shiga, can zuciyarta ta raya mata cewar ta jaraba rubuta date of birth din Aki Owais saboda
ta ta6a ganin ta rubuta shi a diary din ta amatsayin rana mafi mahimmanci agare ta.

Wani irin tsalle ta daka ganin Ya buɗe, da sauri ta shiga nutsuwarta tana leƙen Nazli, wadda tuni bacci yayi
awon gaba da ita
Yazrin tayi mamakin ganin tsawon lokacin da suka dauka ba suyi magana wa junansu ba, Ranta ya sosu
bata ji daɗi ba, ji take kamar ta dauki pillow ta bubbuga mata akanta tsabar haushin da taji.
"Ƴar bakin ciki, In sha Allah baki da miji a duniyar nan daya wuce big bro, bazan zauna na zuba maki ido
kina cutar kanki ba, Akhi Owais shi ya dace ya mallake ki, nayi maki sha'awar auran shi saboda samun miji
nagari irin shi ba abu ne mai sauƙi ba, Ina son kiyi rayuwar farin ciki yar uwata, dole na shirya tsakaninku....
" acikin zuciyarta ta furta maganar tare da cigaba da danna wayar, daga wayarta ta tura video din data
dauka, kaitsaye ta yi mashi sending, shaf shaf ta rubuta mashi text message da harshen turanci kamar haka

_Nayi kewarka bugun zuciyata, ina mai baka haƙurin nuna halin ko'in kula da nayi, ba'asan raina ba, nayi
danasanin hakan don ba ƙaramin cutuwa nake yi ba na rashin jin ɗumin jikinka a kusa dani, ka duba
whatsapp in ka, na tura maka video dina don ya ɗebe maka kewar rashi na, nasan zaka ji dadin kallon shi_

fuskar yazrin dauke da murmushin mugunta ta tura mashi message din, bayan ta gama ta ajiye mata
wayarta, ta nufi kofar fita daga dakin tana faman sakin dariya, ta riga da tasan me zai biyo baya muddin
Nazli taga aika aikan da tayi mata ba ƙaramin husuma zata tada ba, zata ce ta zubda mata aji awurin chief
owais.

*A GIDAN UNCLE ƊAN IYA*

Kusan Atare Su ka yi Parking din motocin su, Mahboob ne Ya fara fitowa daga front seat hannun shi ɗaya
ruƙe da key din Motarshi, fuskarshi dauke da murmushi yake kallon Motar zahra.
"Sannu da dawowa Hajiya Zahra Surukar Kaka Obinna" Ya faɗa tare da buɗe Back Seat din Motar Shi Ya
duƙar da kai Yana leƙan Baby Junaid dake zaune Hannayenshi rungume da Food basket dinshi, Ga school
bag din shi a gefe, Sai faman ɗaure fuska Yake, Da alama rigimar tashi ce ta motsa.

"Ranka Shi daɗe, Mun ƙaraso gidan, zaka iya takawa da kafarka ne mu shiga ciki ko kuwa ni kake so In
goyaka"? Da zolaya mahboob yayi maganar yana dariya.
Yamutsa mashi fuska baby junaid yayi "ni ka goyani" Ya fada A kule.

Juya mashi baya Mahboob Yayi Ya ɗan zuƙunna Baby Junaid Ya Haye bayan nashi, Bayan Ya miƙe Ya ɗauko
mashi Backpack dinsa tare da kwandonsa

Adai dai Lokacin Zahra Ta fito daga motarta, tayi shiga cikin Lafaya, Hannunta ɗaya ruƙe da Ƴar purse dinta
Fuskarta da fara'a take duban Baby Junaid Da Mahboob
"yau wata rana mun dawo gida atare, baby junaid dina zo nan" ta faɗa tare da miƙa mashi hannu, babu
musu Ya soma kiciniyar saukowa daga saman bayan mahboob, daukarshi tayi Mahboob yace"Wato ni kake
gudu? Zamu hadune ɗan rainin wayau, tun da naje dauko shi Daga school Yake ta jin haushina saboda naje
amakare shi kaɗai Ya rage ba'aje daukarsa ba, baisan nima bada son raina ba, Motarce ta samu matasala
sai da nakaita gyara tukunna naje daukoshi da ita"
Dariya zahra tayi"Gaskiya baka kyauta ba, taya zaka bar mana Baby Shi kadai Ga yunwa, meyasa baka
kirani awaya naje daukosa ba"

"Banyi dabarar yin Hakan ba, Yanzu dai tun da mun dawo gida, gashi nan ki kaima jatumarsa, nagaji da
kallon kumburarran fuskarshi"

"Mahboob baka da mutunci, zamu rama ne" ta faɗa tana dariya, baby junaid kuwa Ya ɗaure fuska,
Kumatunshi sunyi jawur da su, da alama kuka Yake so yayi.

Atare suka nufi cikin gidan, tana agaba mahboob Yana abayanta
Bayan shigarsu Falo, Suka taras da mami da Ummi zaune suna kallo a plasma tv din falo, Cikin girmamawa
suka gaishe da su.

"Sannun ku da dawowa, Ya gajiyar aiki"? Cikin Kulawa mami tayi maganar, atare suka hada baki wurin
cewa"yawwa mami"
Ummi dake kallon Baby junaid tace"to fa, Me akayi masa ne naga yana ɗaure fuska"
Mahboob Na dariya Yace"wallahi Ummi Rigimarshi ce ta motsa, Kinsan Halin shi.

Zahra tace"bawani nan, shine Yaƙi zuwa ɗaukarshi da wuri, Yabar shi a school yana ta jira"

"Gaskiya mahboob Baka kyauta mana ba, saboda Allah, Haka akeyi? Sai kabar mana Yaro ga Yunwa"
Ummi ce ta faɗa tana satar kallon baby junaid duk don ta nuna mashi taji Haushi.

"Ay mashi uziri mana, hakanan dai Mahboob bazaiƙi zuwa ɗaukar baby junaid ba sai dai idan wani
uzirinne Ya ruƙe shi" mami na fadan hakan Mahboob Yace"ay har bayani nayi ma zahran, motana ne Ya
samu matsala sai da nakaita gyara, in sha Allah Hakan ma bazata ƙara faruwa ba zan dinga zuwa ina dauko
shi akan lokaci"
Ummi tace"haka Yakamata"
"Zonan babyn mommynsa" acewar Ummi ta fada tana miƙa mashi hannu, maƙe mata kafaɗa yayi alamar
bazaije ba, Saima Ya ƙara ƙanƙame Zahra, mami na dariya tace"In banda abunki sai kace bakisan halinsa ba
idan Yana fushi Yafi buƙatar jin ɗumin mommynsa,"
"Ina auntyn tawa take"?
"Tana a kitchen"
Maimaita kalmar kitchen Zahra tayi, aranta ta furta me kuma Aunty Aneelerh take yi a kicin"? Batayi Ƙasa a
gwiwa ba, Ta nufi kitchen din Mahboob Har Ya zauna kan sofa, sai kuma Ya miƙe Yabi bayan zahra.
Tunkafin su ƙarasa kitchen din suka hango Aneelerh ta haɗa uban gumi a kitchen tana girki, Ita kadai.
Sam bata Ji alamar shigowarsu ba, ta zage damtse sai motsa miya take Yi
"Aunty Aneelerh"? atare suka haɗa baki wurin kiran sunanta, da sauri Ta rufe soup pot din, Ta juyo tana
fuskantarsu, kafin ta ɗaura idanunta akan Baby Junaid,
Murmushi ta sakar masu "Sannunku da dawowa,"
"Yawww, Auntyna, Yau ke kike Aiki akitchen Ina Ana"? Zahra ce ta jefa mata tambayar, Mahboob
Yace"Allah yasa dai lafiya"
Girgiza kai tayi cikin sanyin murya ta soma magana"ba lafiya...." gaba ɗaya ta labarta masu abunda Ya faru
zuwansu dakin Ana tare da su mami, Hankalinsu Ba ƙaramin tashi yayi ba, Musamman Mahboob.

"Bansan Ya zanyi ba, Taƙi faɗa mana abun da ke damunta, Ni tsorona kada wani abu Ya faru da ita"
fuskarta da tsantsar damuwa ta furta maganar
"Nima hankalin bai kwanta da ita ba, dafarko nayi tsammanin Damuwar halin da ƴan uwanta suke aciki ne
ke damunta, ashe ba haka bane, daga gareta ne" Acewar Mahboob.
Kafin Zahra ta furta magana baby Junaid Ya fashe da kuka, Dama ranshi a6ace Yake, da sauri Aneelerh Ta
miƙa hannu ta kar6e shi cikin sigar lallashi take jijjiga shi tana fadin"Am sorry My baby boy, kayi hakuri
nasan nice na 6ata maka rai,' muryarshi da shessheƙar kuka Yace"wayyo Allah mommy, Kuna ta surutu Kin
ƙi kulani, baki missing ɗina ba" dariya zahra da mahboob su ka yi, hakan Ba ƙaramin 6ata mashi rai yai ba,
Hada Jifar Su da harara

Shafa sumar kanshi tayi"Na kar6i laifina, ay min afwa... " zumbura mata baki yayi,
Zahra tace"aunty Aneelerh, Ki tafi dashi ɗaki Ni zan ƙarasa girkin, Inyaso da anjima Sai mu ƙarasa
tattaunawa"

"Keda kika dawo daga aiki a gajiye kuma kike neman in bar maki girki, a'a gaskiya Ki bari na ƙarasa ai ba ni
kadai nake yi ba, Tare da Ummi muke Yi, bata jima da komawa falo ba.. "
Kafin Ta ƙare maganar, Mahboob Yace"tun da tace zatayi kibar mata kawai, Nima saina tayata, baby junaid
yana buƙatar kulawarki, Kije Ki lallashe shi"
Murmushi tasaki Tana kallonsu, Har cikin ranta take jin tsantsar kaunar Yan uwanta, Haɗin kansu Na
burgeta, fatanta Allah Ya dawwamar da farin ciki arayuwarsu, Hakika suna kyautata mata.
"Nagode, zahra, Mahboob, Allah Ya barmu mun ku,"
Amsa mata su ka yi da ameen
"Zan shiga ciki, pls zahra Ki dafa mashi indomie" amsa mata tayi da toh, Bayan fitar Aneeleeh daga kitchen
din, Mahboob Ya ajiye food basket din Junaid, Yabi bayan aneelerh hannun shi ruke da backpack din Baby
junaid,
Bayan Ya ajiye mashi adaki, Ya fito Ya nufi nashi room din, shaf shaf Yayi wanka Ya sanya gajeran wando da
ƴar singlet, Kafin Ya nufi kitchen don Ya taya zahra girki kamar wani mace, atare suka cigaba da kula da
girkin, suna tattauna fira dangane da matsalar Ana.
"Amma kai a tunaninka meke damunta"?
"Sister Ni kaina nakasa gane wani tunani zanyi dangane da matsalar Ana, sai dai kawai mubita da addu'a,
Allah ya yaye mata abunda ke damunta,'
"Ni aganina, Mu kar6i Contact din Ƴan uwanta , mu tuntu6esu may be sunsan meke damunta, tunda sunfi
kusa da ita"
"Nima nayi tunanin hakan, Yanzu dai mu jira, zuwa lokacin da su Abie zasu dawo gidan, nasan zasu Kirata
su tambayeta,"
"Hmm kana ganin zata Iya faɗa masu gaskiya? Bayan Aunty Aneeleeh tace tare da su mamie suka je dakin
nata amma taƙi fada masu, ai ni aganina idanma akwai wanda Ya dace ta fadamawa baiwuci su mami
dinba"

Jinjina kai Mahboob Yayi"kin fadi gaskiya,"


"Ni abunma Ya fara bani tsoro, da naji aunty aneeleeh tace Ana ta dinga kwala masu ihu tana fadin su fita
subar mata dakinta, Anya mahboob bata da matsalar kwalwa?
Mahboob Yace"Bana tunanin hakan, wata'kil Aljanune suka shige ta, mu cigaba da tayata addu'a Allah Ya
kawo mata saukin abunda ke damunta"

"In sha Allah zamuyi mata"


Daga haka basu ƙara magana ba, sun maida hankali akan Girkin da suke Yi.

Fitowa Aneelerh tayi daga Bathroom, Bayanta goye da baby junaid, tayi mashi wanka, sai faman hade mata
fuska Yake Yi, Riga da wando ta Dauko ta zura mashi ajikinshi, ta feshe shi da turare, zama tayi gefen
gadonta,ta ɗaura shi saman laps dinta, hannunta ɗaya dafe ta shi,tarasa meke yi mata daɗi, Ita dai
Hankalinta bai kwanta da halin da Ana take aciki ba, Ji take aranta kamar wani abunne Zai faru, zuciyarta
batayi mata daɗi, sam ta manta da baby junaid Tayi zurfi a tunaninta, Har Ya fara lumshe ido zaiyi bacci,
Muryar Zahra ta fargar da su,
hannunta biyu ruƙe da plate din indomie, Sai tiriri Take Yi, daga saman indomie din ta shimfiɗa mashi
Soyayyan kwai, Mahboob Yana abiye da bayanta, Hannun shi ruƙe da mugs biyu na kakkauran Tea.

"Sannunku da kokari, nasanya ku aiki ko hutawa ba ku yi ba"

"Pls ki daina fadin hakan, Mu yakamata mu Yi maki sannu, anbarki da girki a kitchen, Su mami suna a falo
fira tai dadi" Mahboob Ne yai maganar
Asaman Table zahra ta daura plate din, Mahboob Ma ya sauke nashi mugs din, atare suka fuce daga dakin.

Baby junaid tunda yayi tozali da indomi Ya soma sakin murmushin murna, Har wani lashe le6ensa Yake Yi
"Mommy da zafi, kuma ni Yunwa nake ji Allah" ashagwa6e Yayi maganar
"calm down Your Mind my baby boy, Ni zan baka da hannuna, kasan dai mommy bazata bar baby junaid
dinta Yaji zafi ba ko"? Ɗaga mata kai yai alamar"
"Yawwa my boy" ta faɗa tare dakai hannu ta dauki fork, ta soma nannaɗo taliyar tana hura mashi da baki
idan ta huce saita tura mashi abaki, kusan atare suka cinye indomie din dakwai, Kafin suka sha tea din su.
"Kada kayi bacci, Yanzu za'a fara kiran sallar magrib," ɗaga mata kai yai alamar toh, Janshi ta soma yi da
fira duk dan kada yayi bacci.

Bayan Kammala sallar Magbrib, A lokacin Abie da Uncle ɗan Iya sun shigo gidan, babu wanda Ya tuntu6esu
da maganar Ana, sun bari ne sai sun huce gajiyar da suka kwaso ,Har saida suka kammala cin abincinsu,
Tukunna Ummi ta sanar da su Halin da ake ciki, babu 6ata lokaci, Abie Yasa suka hallara A falon gidan gaba
ɗayansu, Ana ce kaɗai ke babu acikin su.

Aneelerh da zahra da Mahboob suna zazzaune kan Carpet, A lokacin baby junaid Ya jima da yin bacci, Yana
can kwance saman gado.
Abie da Uncle ɗan Iya suna a zaune saman Sofa mai mazaunin mutun uku, Abie Yana sanye da farar
jallabiya ya manna farin glass a idanunsa, Yayin da Uncle ɗan Iya yake asanye da Riga Yar shara ta farin
Yadi, daga ciki ya sanya gajeran wando baƙi.
Su Mamie da Ummi suna zaune saman Sofa mai mazaunin mutun biyu, dukansu Hijabai ne a jikin su.
tamkar mutuwa ta gifta babu mai magana acikinsu, Har na tsawon mintuna kafin daga bisani Uncle ɗan Iya
yayi masu gyaran murya, suka ɗago suna duban shi, da hannu Ya nuna Mahboob
"Je ka kira ta" Amsawa mahboob Yayi da toh, ya miƙe ya nufi bedroom din Ana, abakin ƙofar Ya tsaya tare
da kai hannu yayi knocking kofar kusan sau uku bata buɗe ba, Har ya fara tunanin ko bacci tayi ne sai kuma
Yajiyo mutsu mutsunta ta cikin ɗakin.
A hankali ta turo ƙofar ɗakin, tare da leƙo da kanta,
Ko da mahboob yai tozali da fuskarta sai da gabanshi ya faɗi ganin yadda ta kumbura suntum, idanuwanta
sun kaɗa jawur, daga gani kukan take cikin yi
In a calm voice Ya furta"ina fata ban katse maki baccin ki ba"
Muryarta adisashe tace"ban kaiga Yin baccin ba,"
Jinjina kai yayi"Uncle ne yace in kira ki, su na a falo shi da su mamie da abie"
Shiru tayi jimmm kamar bazata motsa ba, har saida ya maimaita mata maganar tukunna tace Toh, ka jirani
mu tafi atare"
"Okey"
Maida ƙofa tayi ta rufe ta, badajimawa ba sai gata ta fito sanye da doguwar riga, ta yafa mayafi akanta,
Jin ta ruƙo hannun shi acikin nata ne yasa shi saurin kallonta, sam hankalinta ba akwance Yake ba, bai yi
yunƙurin raba hannun shi daga nata ba, A haka suka nufi falon, sai da suka kusa isa yayi saurin zame
hannun shi daga nata, Takun tafiyarsu ne Yaja hankalinsu mami ga dubansu
Cikin girmamawa Ana ta gaishe da su, tare da samun wuri gefen Aneelerh ta zauna tana faman jan
numfashi, bayan mahboob Ya zauna.

Abie dake kallon Ana Ya soma Magana a tsanake

"Inaso ki natsu ki saurare ni," jinjina mashi kai tai alamar toh
"Ki ɗauka tamkar mahaifanki ne suke yi maki magana, kada ki ji shakkun faɗa mana abun da ke damunki,
saboda mu kaɗai ne makusantanki a yanzu, Haƙƙinmu ne mu kula da rayuwarki, Idan wani abu ya same ki
ba zamu ji daɗi ba" wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, haƙiƙa kalaman abie sun yi tasiri a zuciyarta.
Uncle ɗan Iya ya ɗaura da cewa"banji daɗin abun da Ummi ta fada min ba, baki kyauta mana ba, ashe
baki ɗauke mu yarda muka ɗauke ki ba, meyasa zaki zauna abu na damunki ki gaza gaya ma kowa? Meye
amfanin 6oye mana eye"? Muryarshi da faɗa yake yi mata magana, alamar ranshi ya 6aci.

Sunnar dakai ƙasa Ana tayi yayin da idanunta ke akan Yatsun hannayenta
"Meke damun ki ne, inaso ki faɗi mini gaskiya"? Ya jefa mata tambayar, Su Aneelerh da su mami sun
natsu suna kallon ta.
Numfashi taja tare da sauke shi A hankali ta furta"Idan na 6ata maku rai, dan Allah ku yafe ni, Aunty
Aneelerh, mami, ummi, Zahra, Mahboob, abie, uncle, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku, duk da kasancewata
yar aiki agidan nan, Sannan ba musulma ba amma kun daukeni tamkar jinin ku, ko dan saboda nuna
damuwar da ku ka yi akaina zan fada maku gaskiyar abun da ke damuna...." ta faɗa tana mai ƙanƙan da
kanta, gaba ɗaya duk sun ƙagara da suji meke damunta, musamman Mahboob Ya kasa ɗauke idanunsa
daga kan fuskarta, wani irin tsantsar sonta da ƙaunarta yake ji, ga matsanancin tausayinta dake addabar
zuciyarsa.
"Cikin kwanakin nan, Ina yawan yin mugayen mafarkai, waɗanda suke neman haukata ni, bansan meyasa
hakan yake faruwa dani ba, idanuwana suna gane min abunda yafi ƙarfin gani na wanda silar hakan yasa
nafara zaucewa, ni gani nake ma kamar mutuwa zanyi..... " muryarta na rawa ta ƙare maganar nan take ta
fashe da kuka mai sautin gaske, Hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba, Jikin kowannansu yayi sanyi
"Kiyi shiru, Kukan Ya isa haka, Ki faɗa mana me kike gani a cikin mafarkin naki"! Uncle ɗan Iya ne yai
maganar
Cikin shessheƙar kuka tace"wallahi duk yadda zanyi maku bayani ba lallai ku fahimce ni ba, ni kaɗai nasan
halin da nake aciki, ni kaɗai nasan bala'en da nake gani, Ba tun yanzu ba, tun ina ƙaramata idan nayi
mafarki mummuna yana zama dagaske, hatta rasuwar iyayenmu saida nafara yin mafarkin zasu yi hatsarin
mota, sai gashi ya tabbata, uncle ɗina ma ni nayi mafarkin mutuwarsa kuma ya tabbata, da wuya inyi
mafarki mummuna bai zamto gaske ba, ni damuwata mutanan da nake a tare da su bana son wani abu ya
sami wani daga cikin ku...." tashin hankalin da ba'a saka mashi date, A matuƙar ruɗe Zahra take kallon
Aneeleerh, Ummi ta kalli Mamie, Idanuwansu azare, mahboob kuwa kusan suman zaune yayi.

Shiru tayi Tana faman yin shessheƙar kuka,


Abie dake kallonta, nazarin maganarta yakeyi, yaso ace musulmace ita, kodan ya bata shawarar ta runƙa
yawaita yin azhkar, da sauran addu'o'in neman tsari.
Tsawon lokaci falon yayi tsit, babu mai magana acikinsu, sai kallon kallo da suke jefawa junansu.
Muryar Uncle ɗan Iya ce ta katse Shirun nasu
"Ki daina sanya damuwa aranki, Mafarki ba gaskiya bane, shaidan ne yake assasashi, Ki yawaita yin
addu'a, muma kuma zamu tayaki, Allah shi yake tsare bawansa, in sha Allah babu abun da zai same ki,
damu kanmu,"
Ajiyar zuciya ta sauke, Cikin sanyin murya tace"in sha Allah uncle, zanyi hakan"
"Aneelerh, Idan zata kwanta bacci ki rakata dakinta, Ki yi mata addu'a," Ya fada yana duban Aneeleerh,
Cikin girmamawa Ta amsa mashi da toh,
Kwantar mata da hankali suka cigaba dayi, Kowa sai da ya sanya bakin shi wurin Lallashinta da bata baki,
Har saida suka tabbatar Ta samu saukin damuwarta tukunna mamie tace"daga yau kada ki sake ware kanki
a daki! Kina jina ko"? Daga mata kai tayi toh
"Kidaina kuntata kanki adaki, ki dinga fitowa waje wurin su Aneelerh Kuna yin fira, hakan zai ɗebe maki
kewa don na fahimci hada kaɗaici ke damun ki" jinjina kai ana tayi alamar toh.
Gyaran murya abie yai tare da cewa"Idan kina buƙatar wani abu, Ki fadama Aneelerh ko zahra, su sanar
dani in sha Allah zamuyi maki shi, kada kiji komai ki dauka tamkar Iyayenki ne" wannan maganar da abie Ya
furta mata ba karamin ta6a zuciyarta yayi ba, nan take ta fashe masu da kuka mai tsuma zuciya, sautin
muryarta dakyar yake fita wurin yi masu godiya.
"Ku tashi ku rakata daki ta kwanta ta huta" Ummi ce tayi maganar tana nuna su zahra, ruƙo hannun Ana
Aneeleerh tayi atare suka miƙe, Zahra tabi bayansu, Har cikin dakinta suka kaita, Bayan ta kwanta Aneelerh
da zahra sukayi mata addu'o'i, Kafin daga bisani suka yi mata sallama, Kamar karsu barota haka suke ji,
bayan sun fito daga dakin sun kulle mata kofar, zahra ta kalli Aneelerh
"Nifa tsoro yakamani aunty na, tun da naji Ana tace mafarkinta yana zama gaskiya, wallahi bana so wani
abu ya samu ɗaya daga cikin mu"
Ita kanta Aneelerh hankalinta ba akwance yake ba, zuciyarta taki Aminta da kalaman ana, sai dai tayi
kokarin danne damuwarta wurin kwantar ma zara da hankalin ta

"Zahra kin riga kin sani, mafarki ba gaskiya bane, Ni ko kadan hankalina bai tashi ba, kema kuma inaso ki
kwantar da hankalinki, In sha Allah babu abun zai faru, face alkhairi"

Cikin sanyin murya zahra tace"Allah Yasa" Ta fada a yayin da suke shiga falon, komawa sukayi saman carpet
suka zauna kowa zuciyarsa da fargaban maganar Ana.

Idan muka koma 6angaren su Ummin america tun bayan kammala sallar magbrib, tayi wanka ta shirya
cikin Baƙar jallabiya, tayi rolling veil akanta, ta bi ko'ina na jikinta ta feshe da turare, bakomai take jira ba
face kiran Boss man, tun da ya fada mata yana son magana da ita gaba daya ta rasa sukuni ta kosa taji me
ya ke son faɗa mata, tana cikin yin safa da marwa a room dinta, wayarta tayi ringing a hazarce tayi picking
call din, muryar boss ce ta isar mata da sakon ta same shi a down, jiki na rawa ta fito daga dakin ta sauko
down stairs babu kowa a falon, duk suna a dakunansu

A falo ta same shi tsaye cikin shiga ta jallabiya, ya goya hannayensa akan kirjinsa, fuskarsa a sanye da face
mask.

Da fara'a ta nufe shi batare da 6ata lokaci ba, suka jera a tare suka nufi swimming area din gidan, ko'ina
ka kalla hasken fitilun lantarki ne tamkar da rana.

"ina sauraron ka Yalla6ai, tun da muka fito kayi shiru baka ce komai ba" ummi ce ta fada tana kallon Taj
dake a gefenta.

"ga dukkan alamu Kin ƙagara da kiji dalilin kiran da nayi maki"
Jinjina mashi kai tayi alamar Eh, A yayin da suke zama saman kujerun dake a bakin pool din masu kyan
gaske, suna fuskantar Junansu.

"Nasan zakiyi mamaki idan nace maki chief ne Ya bada Sako A fada maki"
A ruɗe tayi mashi farfari da idanunta cikin kagara ta furta"A message from the chief for me? Does he know
about me? So what did he say?

Calmly Boss Ya furta"Yeah Yasan da zaman ki fiye da tunaninki, chief da kike gani baya zama wuri ɗaya da
mutumin da baisan tarihin rayuwarsa ba," Wani irin bugu kirjinta yayi mata cike da fargaba ta furta.
"I don't understand what you mean! Chief ya san komai dangane da rayuwana! How is that possible?"

Dariya boss yayi ganin yadda ta shiga ruɗani


"Ki kwantar da hankalin ki Ummi, Amsarki tana atare dani, ki natsu ki saurari me zan fada maki" fuskarta a
yamutse ta amsa mashi da toh.
Numfasawa yayi kafin Yaci gaba da fadin"sakon da chief Yace A fada maki shi ne, Gobe Idan Allah ya
kaimu, zamu fita tare da Yaran nan zuwa cikin estate din su, muna so su halarci Farewell dinner din Uncle
ɗinsa Hateem, amma fa bama so kowa yasan da wannan zancen! Zuwan bazata zamuyi tare da su, ke
kuma abun da muke so daga gare ki, ki yi kokarin shirya mana su.... " kafin Ya kare Maganar tace"wai kana
nufin prime minister Hateem na canada ne za'ayiwa dinner din? ɗaga mata gira yai alamar eh, but amma
meyasa naji kace zuwan bazata za'ayi da yaran"? Ta faɗa tana mai neman ƙarin bayani.
Bai 6oye mata komai ba, dangane da budurin da aka sha lokacin da Danish ya rikiɗa, naƙin amincewa da
zaman su a family din"
Jikinta yai sanyi"Allah sarki, ashe abun da ya faru kenan, ko da yake dama zaiyi wuya su yarda da su, ni
kaina lokacin daya rikiɗa ba ƙaramin firgita nayi ba, saboda abu ne da ban ta6a gani ba, toh su kansu abun
da zai sa su ƙi yarda da zamansu kenan, bayan haka hukuncin da shi baba obie ya yanke na raba alaƙar
prime minister hateem da danish yayi dai dai, a fahimta na yayi hakan saboda gudun kada ɗansa ya cutu....
" jinjina kai taj yai alamar gamsuwa da bayanin ta, kafin wani ya qara magana a cikin su, sai ga jami'in isod
Ya fito daga ƙofar falo, hannun shi ruƙe da plate mai ɗauke da mugs biyu na coffee, akan table din dake a
tsakatsakiyarsu ya ajiye plate din kafin yabar wurin
Tura mata mug ɗaya taj yayi"kisha, ni nasa a kawo mana dan muji dadin tattaunawa' murmushi tayi har
cikin ranta taji dadin karamcinsa, A hankali ta ɗauki mug din ta soma kur6ar coffee din, shima ya dauki
nasa yana sha, bayan ta tsagaita da sha ne taci gaba da magana "kowani bawa da irin tashi jarabtar, Idan
kaji na wani kai naka ba komai ba, shiyasa a koda yaushe akeson bawa ya zamanto mai hakuri dakai zuciya
nesa, haƙiƙa ina tausayin wadannan bayin Allah, duk da ban kaiga jin tarihin rayuwarsu ba... ' murmushi taj
ya ɗanyi tare da cewa"kada ki damu, nan badajimawa ba zaki ji tarihin rayuwarsu, In sha Allah"

Gyaɗa kai tayi "A ina za'ayi dinner din sannan ƙarfe nawa ne zasu je can din"?

"A cikin Estate din nan, Bayan sallar la'asar"

Shiru tayi alamar tana nazarin wani abu, yayin da yake binta da kallo.

"Menene dress code din da za'a sanya a wurin dinner din"? ta tambaya tana kallon fuskarsa.

"abaya matan za su sanya, A cikin suturunsu mun sanya masu abaya na larabawa kala kala, A ciki za'a
daukar masu masu kyau na mutunci, sannan bama son suyi shigar da zata baiyana sumar kansu, a rufe
masu ko'ina na jikin su.

Gyaɗa kai tayi"okey, in sha Allah amma baza'ay masu make up ba"?

"Duk kyan da Allah yayi masu"? Ya faɗa da murmushi kan fuskanshi, Itama ummin murmushin takeyi"masu
kyaun ma su na yin make up, ko da yake naji ka ce arufe masu ko'ina na jikin su, ba buƙatar yin make up,
ɗaga mata gira yai alamar eh.

"Tare da ni zaku tafi ne"?


"Idan kina ra'ayin zuwa"
Girgiza kai tayi alamar a'a
"Meyasa"?
"Nafi so kubarni a gida, nasan Su Unaisah zasu bani labari, har ma su daukar min video na dinner din in
gani nima"
"Ban yarda ba, yakamata kema ki shirya mu tafi tare dake, zaki ji dadin shiga cikin family ɗin Obinna," jim
ta ɗanyi tana wani tunani aranta.

"Kinyi shiru baki ce komai ba"


Numfasawa tayi tare da cewa"ka yi hakuri amma zuwana ba lallai ya zama alkhairi agare ni da ku kan ku
ba, bana so na 6ata maku shagalin ku, nasan ka fahimce ni" jim ya ɗanyi yana jujjuya mug din hannunsa,
tabbas ya fahimci me take nufi,shi kanshi yasan ba lallai chief Ya amince su tafi da ita ba, yadai ɗan bugi
cikinta ne don yaji idan tana son zuwa sai kuma akaci sa'a bata ra'ayi.

"Alfarmar da nake nema a wurin ku, dan Allah ku barni in fita gobe, Inaso zan ziyarci gidan ƙawata dake
aure anan abuja"

"Bani da wannan hurumin, Amma in sha Allah zanyi kokarin nema maki alfarma wurin chief, but inaso
kisan da sani duk inda zaki je jami'in mu ne zai kai ki," har cikin ranta taji dadin maganarsa.

"Idan akwai abun da kike buƙata ki faɗa min" cikin kulawa yayi mata maganar yana dubanta.

"Dan Allah ka fadamin shin dagaske ne chief Yasan komai dangane da rayuwana"? Ta fada cike da fargaba.

Jim ya ɗanyi yana dubanta kafin Yace" "I'll give you an assignment. If you can find the answer, then I'll tell
you what you want to hear," A ƙagare ta ke kallon shi, A hankali Ya sanya yatsun hannayen shi tare da zame
mask din fuskarshi.

Wani irin kallo ummi ta soma binshi da shi, Yau ne karo na farko da ta fara Yin tozali da fuskar Boss man,
bata ta6a tsammanin Yana da kyawun fuska har haka ba.

"Dama haka kake da kyau"? da alamun mamaki ta furta maganar, Murmushin gefen fuska Ya sakar mata
har dimple dinsa ya lotsa, nan take ta soma kokarin tariyo inda tasan fuskarshi sai dai kash takasa tunawa
amma tabbas tana ji aranta ta ta6a sanin shi ko kuma wani ne me kama da shi.

"Ina da aure, Ki daina kallona, matana tana da kishi, zata iya yin komai akaina" da zolaya taj yayi maganar.
Ummi tace"tasan tana da kishi meyasa ta auri namiji mai kyan sura? Ay kamata yayi ta auri mummuna, ni
fa bazan 6oye maka ba, ka jima kana bani mamaki kai da abokin aikin ka big guy da chief din ku, tun da
nataso rayuwata da wuya a samu namijin zan gifta awuri batare daya bi ni da kallo ba harma ya neme ni,
amma ku sam babu wannan tunanin aranku, zuciyarki a tsarkake take, hakan ba karamin daure min kai
yake yi ba, shi chief mace ko kallo ma bata ishe shi ba, wata irin dakakkar zuciya ce da shi.

Ƙayataccen Murmushi Taj Ya sakar mata batare daya furta mata ƙala ba

"Wallahi nasan ka, sai dai bazan Iya tuna a ina nasan ka ba, ni hatta muryarka na jima ina son tuna ina na
son ta," still face dinsa da murmushi Yake dubanta.

"Amma meyasa kake yi min kama da Unaisah? Ko dai idanuwana ne suke nuna min badai dai ba"?

"Ba laifin idanuwanki bane, Unaisah Ƴata ce, Jini na ce, Ni mahaifinta ne, asalin sunana Tajuddeeen,"

"I can't believe it, Unaisa fara ce zan iya sanyata a jinsin larabawa, kai kuma daga ganin ka hausa fulani
ne"
"A salin sunana Zaheer Tajudeen, Zaheer sunan Mahaifina ne, Tajudden kuma sunana ne, Ki tambayi
Unaisah menene full name dinta zata fada maki da bakinta, Ita kanta ayanzu haka batasan cewa Ni
mahaifinta bane ƙaddara ce ta rabamu, sai gashi cikin ikon Allah mun sake haɗuwa," murmushi ummi
tayi"Allah sarki, Na tayaka Murna, amma mahaifiyarta wani jinsi ce"?
"Hausa Arab ce" Dariya Ummi tayi cikin raha ta furta"hausa arab! Bayan hausa fulani har Hausa rab ke da
akwai, ban ta6a ji ba sai akanka"
"Ina nufin Half cast ce, Mahaifinta hausa fulani ne, mahaifiyarta kuma Balarabi ce" gyaɗa kai tayi"masha
Allah, shiyasa yarinyar taka takasance fara sol, Ga gashi tubarkalla amma tsakanin kai da mahaifiyarta halin
wa ta ɗauko"? murmushi yasaki yana dubanta yace"meyasa kika tambaye ni"?
"Unaisah tana da faɗa, daga ka kalli idanunta zaka shaidan hakan, ga wayau da kaifin basiri Allah Ya bata
fiye da sauran ƴan uwanta" haƙiƙa Yaji daɗin Yabon da ummi tayi mata,
"Haka mutane suke cewa, shiyasa nima nake alfahari da ita, Inason Unaisah, fiye da yadda nakeson kaina,
A halin Yanzu bani da tamkarta a duniyarnan, Itace ta rage min wadda nake gani naji sanyi araina, silar
unaisah nasamu alheri da dama wadanda idan na fada maki su zakiyi mamaki, ɗaya daga ciki Unaisah itace
silar haɗuwana da Chief" da mamaki Ummi ta ɗan zaro mashi sexy idanunta haɗi da buɗe baki, Jinjina
mata kai yayi" Murmushin gefen fuska tasaki"Ina ƙara tayaka murna, Yarinyarka Jarinka ce, Allah Ya
albarkaci Rayuwarta" amsa mata yayi ameen, daga ita har shi sun ji daɗin zaman firar da su kayi, Haƙiƙa taj
ya ɗebe mata kewar kaɗaicin dake damunta, ta ƙara ganin mutuncinsa da ƙimarsa a idanunta, Sai dai
tarasa gane meyasa take jin kamar ta ta6a sanin shi? Musamman daya faɗa mata sunan shi sai yawo yake
mata akai.

Ni'imtacciyar Iskar dake kaɗawa ta ƙara masu ƙaimin firar ta su, kafin wani lokaci taj yace da ita"kada na
cika ki da surutu, ko zaki koma ciki ne"? Fuskarta da fara'a tace"no ko kusa, ni baka takuramin ba, saima
ɗebe min kewar da ka yi, naji dadi fiye da tunanin...... " bata ƙarasa maganarba sakamakon sautin dirar
motar daya ratsa kunnuwanta, kusan atare suka juyo suna duban motar.

Bayan sojan dake driving din motar yayi parking, Ya fito Ya zagaya ya buɗe mashi murfin back seat dinta,
Ƙafarshi kaɗai ya zuro waje Gaban ummi ya faɗi rasss, jikinta ya soma kakarwa, A hankali ya ƙarasa fitowa
daga cikin motar, kamar kullum cikin shiga ta malamai magadan annabawa, bai ɗaura idanunsa akan kowa
ba sai akan Ummin america, a sukwane ta miƙe tana gyara mayafin da tayi rolling, taj kuwa fuskarshi dauke
da murmushi ya nufi sheikh imam yana fadin"Ya sheikh Barka da zuwa tun ɗazu muke ta sa ran ganin ka"
Martanin murmushin Shiekh Imam ya mayar masa a yayin da yake kokarin kau da idanunsa daga na ummi
ya mayar da su akan fuskar taj, musabaha su ka yi shikeh imam yace"Ay min afwa, ban samu damar zuwa
duba mara lafiya na ba, wallahi yana araina da shi na wuni, wani uziri ne ya ruƙe ni"
Jiki na rawa Ummi ta juya ta nufi ƙofar shiga falo, Duk don kada su gaisa da sheikh imam, har ta kusa
kaiwa ga ƙofar muryar taj ya ratsa kunnanta
"Ummi, ki zo mana ku gaisa da sheikh imam" tamkar an dasa mata aya ta tsaya cak, tana mai mayar da
numfashi, Har cikin ranta bata ji daɗin dakatar da itan da yayi ba, sai dai bata jin zata iya watsa mashi ƙasa
a ido, musamman yau daya faranta mata rai.
Tunkafin ta juya ta soma jin takun tafiyarsu bayanta, jiki asanyaye ta waiwayo tana dubansu, lokacin da
suka ƙaraso da sauri ta sunnar da kanta ƙasa, muryarta na rawa ta furta"sannu da zuwa"
Cikin sanyin murya ya amsa mata da yawwa
Taj dake dubansu a fakaice yace"sheikh bari na gabatar maka da ummi,"jinjina mashi kai yai alamar toh
"Ummi Tamkar uwa take a wurin yaran da muke raino, ita ce take kula da su"
Fuskar sheikh babu annuri ya furta"anya kuwa sunyi dacen uwa"? Har sai da gaban ummi ya fadi rass jin
abun da yace, hatta shi kanshi taj aruɗe ya kalli fuskar shaikh imam

*Daga alkalamin Boss Bature✍️


*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki
tura*

3196407426

First bank
Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan
layin 08169856268, Ƴan Niger kuma su yi min magana ta layina 08103884440*

You might also like