Nihaad Complete

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 339

💖💖 *NIHAAD* 💖💖

By Khaleesat Haiydar📖
✍🏻

All thanks to Allah SWT for giving me the ability and privilege to present to you
this book. My mother Hajiya Hajarah Allah ya karo farin ciki da kwanciyar hankali
da arziki me amfani, Allah ya saka maki da gidan Aljanna, 👏🏻 my special greetings
to my own Barrister KH, Allah ya jibanci lamarinka, ya kara bude hanyoyin arzikin
da xa ayi ma addini hidima💖 and My lovely aunt Rukayya Allah ya raya su Lil
Khaleesat ya kara maki kwanciyar hankali.. And then my fans, i am who i am as a
result of u guys, i love you all for the support always, Allah ya baku farin cikin
duniya da na kiyama.... As usual support ur writer and may God bless u.

Tun da ta ji furucin wan Abbanta na karshe ta sakar masu kuka me karfin gaske, ta
kalli Mahaifiyarta dake goge hawayen dake sauka idonta, babu alamar dai xata ce
komai, Ta kalli Abba da fuskarsa ke hade tamkar hadari, shi ma bata samu courage
din ce masa komai ba, yayyinta maza biyu dake parlon babu wanda yace komai cikinsu,
ta dinga kuka da shesheka ta kalli Umma warce tayi tagumi, kallon Kakarta dake
girgiza kafa tayi cikin rawan murya ta kamo hannunta tace "Don girman Allah kice su
yi hakuri sharrin shaidan ne, don Allah kice su yafe min, ni ban san wanda yayi min
haka ba..." Kakar ta warce hannunta tace "Ja can, Ke har kinsan sharrin shaidan
alhalin kece shaidaniyar Nihad, ai kafin ki dauko mana abun kunya gwara tun wuri mu
kunyata ki, ki ce lalle ke sai kin xama mutuniyar banxa abinda kaf xuri'a babu? Me
yake burgeki da rayuwar 'ya yan iska har wannan abu ya same ki haka?" Kuka kakar ta
saki tace "Allah mun gode maka, ka haifi ɗa ne kawai baka haifi halinsa ba, yanxu
meye wannan kika mana Nihad" Mikewa Nihad tayi tana kuka sosai ta fice daga parlon,
direct dakinta ta nufa don tasan ko me xata ce a parlon nan babu wanda xae
saurareta, tunda har Umma ma ta ki cewa komai to babu wanda xai ce komai, bayan ta
shiga daki ta sa makulli ta fada kan gado tana rusa kuka kamar ranta xai fita, is
this actually happening to her? yanda ta ga rana haka ta ga dare, gashi ta kasa
sallah ko da raka'a daya ne, gaba daya ta fice hayyacinta, she wish all this is
nothing but a dream, she wish xata farka taga mummunan mafarki kawai take, da asuba
aka murda kofar dakin ta daga idonta da suka kumbura tana kallon kofar amma bata da
niyyar tashi ta bude, har aka gaji da Knocking aka bar wajen. Sai wajen karfe
takwas na safe tana xaune saman darduma ta jawo wayarta da kyar, rabonta da wayar
tun shekaranjiya, gaba daya bata son abinda xai hadata da wayar ma balle xuciyarta
ya kara rauni, yanxun ma da ta dauko sim card dinta take son cirewa ta karya,
missed calls da ta gani ya doshi hamsin, da messages da ya ninka calls din, ko wani
message xance daya ne content dinsa, "Is that you on social media Nihad?" "Nihad
what came over u?" "Nihad what is happening?" "Nihad something is wrong somewhere,
ur Video is all over the internet" Fita tayi daga Inbox din hawaye me xafi na sauka
idonta, ta bude WhatsApp shi ma dai duk messages din ne har da videos... Kashe
wayar tayi ta ciro sim card din ta karya kamar yanda tayi niyya sannan ta jefar da
wayar saman gado tana goge hawayen da ya ki tsaya mata, wayyo ina ka xata farka
taga mafarki kawai take da gaske, tun shekaranjiya take wish din nan, amma taki
farkawa wanda hakan ke kara tabbatar mata da gaske ne duk abinda ke faruwa, babu
wani xancen mafarki, Knocking din kofa aka yi, ta kalli kofar sai kuma ta mike a
hankali ta nufi kofar ta bude, Umma ta gani tsaye, nan da nan wasu sabbin hawayen
suka ciko idonta, Umma ta shigo dakin ta kulle kofar, Nihad ta bi ta da kallo har
ta xauna gefen gado, Nihad ta karasa inda take ta durkusa kasa cikin sanyin murya
tace "Umma don girman Allah ku rufa min asiri kar ayi min haka, wllh xan iya
mutuwa, talk to Abba plss" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "It's too late
Nihad, tun da har Alhaji Abubakar ne ya yanke hukuncin nan kema kinsan babu me ja
da wannan hukunci nasa, ke dai naki addu'a, mu ma kuma muna nan muna taya ki da
shi, it's okay to make mistakes as long as we learn from them, so ki kwantar da
hankalinki everything will be alright, kuma koma waye ya aikata maki haka sai dai
mu ce Allah ya shiryesa" Ta rushe da wani kuka cikin tashin hankali take cewa "Na
shiga uku Umma, yanxu baxa ki iya ce ma Abba komai ba? auren dole fa xa su min,
Umma ya xan yi da raina idan hakan ya faru, na shiga uku na..." Mikewa Umma tayi ta
nufi kofa ta fita ta kulle. Compound Umma ta fita ta tarda Abba dake xaune shi
kadai kana ganinsa kasan yayi nisa a tunanin da yake, ta nufesa ta ja daya daga
kujerun dake wajen ta xauna tana kallonsa da damuwa karara fuskarta, he looks so
disturbed also, ta kwantar da murya tace "Damuwa ba shi ne mafita ba Ranka shi
dade, kayi hakuri ka sa ma ranka salama, Allah ne ya tsara haka, sai mu gode masa
mu kara gode masa kawai" Abba ya numfasa yace "I think aurar da Nihad yanzu ba shi
ne mafita ba Sumayyah, amma Engineer da Hajiya baxa su fahimci hakan ba, she is
just 19, ga kuma wannan abu da ya faru, ta ina xata fara xaman aure bata gama
mallakan hankalin kanta ba? da xa su sake shawara da ni da na ce masu gwara kawai
ta tafi waje ta karasa karatun ta a can, ko da Uk ne...." Umma dake ta kallonsa
tace "Wannan gaskiya ne, aurar da Nihad is not a way out, amma ni dai shawarata kar
ka tofa naka a issue din nan Yallabai, duk yanda Yaya yayi da Nihad dai dai ne don
'er sa ce, kuma ran Hajiya xae 6aci idan ka bijiro da wannan batun na taje waje
tayi karatu, gani kawai xa su yi kana ma goyon bayanta ne, naka kawai ido sannan
kayi mata fatan alkhairi duk yanda suka yi da ita er su ce, kuma baxa su yi abinda
xai cuceta ba, tunda suka ce aure mu xuba masu ido duk yanda suka yi dai dai ne,
shawara ta biyu kuma kada ka kuskura Yaya yace xai hada Nihad da daya daga 'ya
yansa balle ma bana tunanin xa ayi hakan kawai in case xa a bijiro da wannan
gaskiya ka nuna a'a, don in har aka yi hakan zumunci xae tarwatse kasan su waye 'ya
yan nasa da iyayensu, yara ne masu ji da kansu wa enda ba sa rayuwa a kasar, don
haka kar ka soma yarda... don walakantattciya xasu mayar mana da er mu, ni yallabai
yanda video din nan nata ya tafi viral gwara kawai a samo wani da ba kowa ba, bawan
Allah wanda ba ma shi da abun duniya, shi kadai xai iya aurenta ya rufa mata asiri
su xauna lafiya ba tare da ya goranta mata wataran ba, bai kuma walakanta mana ita
ba, kyau ace ma a karkara yake rayuwarsa yallabai" Abba ya daga kai yana mata wani
kallo babu ko kiftawa, tace "Atoh Allah ya baka hakuri, ka samo wani d'an senator
ko Attajiri ka hadasu kawai, hakan ma dai dai ne...." Tana kai wa nan ta mike ta ce
"Allah ya rufa asiri, ya tsare yan baya" Daga haka ta bar wajen, Abba ya dafe
kansa. Umma ta saka Abba tunani iri iri bayan ta bar sa a wajen, ta wani bangaren
she is damn right, abinda ta fada gaskiya ne, babu wanda xai yi ma tayin Nihad ya
amsa da farin ciki ko dadin rai, Nihad is nothing but a disappointment to him, bai
taba xaton hakan daga gareta ba kuma yayi da ya sanin fifitata da yayi cikin duk
'ya yansa, yayi da ya sanin nuna mata so karara da yayi kan sauran 'ya yan sa, amma
Alhmdlh tunda abinda tayi ya tsaya iya haka, shawaran da Umma ta basa kuma shi xai
yi amfani da... Mai gadi ne ya bude gate jin ana horn, Abba ya bi motar da ta shigo
compound din da ido har yayi parking, yana xaune aka samesa cikin ladabi ya mika
masa ledan dake hannunsa yace "Ga aiken Alhaji" mikewa Abba yayi yace "Mu je can
parlor daga nan ka kwashi takalman da xa ayi min polish ka ba mai gadi" Abba na
gaba yana biye da shi a baya har suka shiga cikin babban parlon gidan, sannan main
parlor din Abba, Abba ya xauna yace "Ka ɗan jira xan yi waya, xan sake aikenka ne"
Mai gadi ne xaune a position dinsa tare da driver, mai gadin yayi kasa da murya
yace "Ka ko ji abinda ke faruwa kuwa??" Drivern yace "Me ke faruwa?" Mai gadi ya bi
compound din da ido kafin cikin rada yace "Daxu Saminu ya xo ya nuna min nima a
waya, wllh na gani.." Driver yace "Me ka ga?" Mai gadi ya kai baki kunnensa cikin
rada sosai yace "Wllh hoton tsaraicin fitsararriyar yarinyar nan ne duk ya baxu
yanar gizo, da idona na gani a wayar Saminu, kai baka ganin duk gidan kamar anyi
mutuwa ba, ai duk gidan alhini suke, Da yake baka da babban waya baxa ka gani ba"
Driver ya kallesa da kyau yace "Tsaraici?" Mai gadi ya kwashe da dariya yace "Yo
tsaraici mana, yar kamfai da rigar mama kawai ne a jikinta kuma hoto me motsi aka
mata, duk halittar jikinta babu wanda bai fito ba malam, abun dai ba a cewa komai,
ni Alhaji ne ma ke ban tausayi don ya shiga damuwa sosai" Yana kallon mai gadin
yace "Kai a ina ka gani??" Mai gadi yace "Toh jira ka ga ikon Allah" yana fadin
haka ya nufi boys quarters da sauri, ba a dau lkci ba sai gashi ya dawo rike da
wayar saminu, ya mika masa, amsa yayi ya danna play a video din, ko second goma bai
yi da kallon ba ya ajiye wayar gefensa yana kallon Mai gadin, Mai gadin ya kwashe
da dariya yace "Toh dada, muma duk haka muka gani, Allah kadai yasan iyakar inda
abun nan yaje, shi ma a wani gruf ya gani wai, har fesbook yace min ya gani, kaga
daga yanxu sai dai ta daga ma wasu kai ba mu ba kuma" Dariya mai gadin ya kyalkyale
da, Driver ya mike yace "Ga takalma in ji Alhaji a ba shoe shiner" Daga haka ya
tafi boys quarters. Nihad na kwance edge din gadonta ta kafa ma agogon dake manne
bangon dakinta ido, xuwa yanxu kam ta hakura da kukan da take, but she is so weak,
har ta mance rabonta da wani abinci, babu wanda ke bin ta kanta a gidan banda Umma
dake shigowa dakin nata lkci lkci, she still don't have the courage to go to her
mother, Bude kofar dakin aka yi ta daga kai da sauri, Husnah ce ta shigo dakin da
sallama fuskarta dauke da damuwa, ta karasa kusa da ita ta xauna gefen ta amma ta
kasa cewa komai, Nihad din ma dai bata ce mata komai ba, Husnah ta sauke ajiyar
xuciya tace "Kar ki sa ma kanki wani ciwon kawata, duk abinda ya faru da mutum a
rayuwa dama Allah ya tsara hakan, kiyi hakuri da kaddaranki, kiyi hakuri kiyi
accepting with good faith" Lkci daya hawaye ya kawo idon Nihad, Husnah da ita ma
har hawayen ya cika idonta tace "Pls have faith don Allah Nihad, koma waye yayi
maki wannan abun Allah baxai bar sa haka ba, tun a duniya Allah xai bi maki
hakkinki, ya saka maki" Nihad ta mike xaune ta fashe da kuka tace "Ji nake kamar in
kashe kaina Husnah" Husnah ta rufe bakinta da sauri tace "Kiyi istigifari, who are
u not to be tested by Allah?? Kar ki kuma fadin hakan, kowa da irin tasa kaddaran a
rayuwa, ki dau naki with good faith nace maki, in sha Allah xaki cinye wannan
jarabawan, muna nan muna maki addu'a, Allah
ya rufe abun cikin gaggawa a daina yawo da shi a media" Nihad ta share idonta a
hankali tace "How will i mend this damage?" Husnah tace "Allah will, ke dai ki ci
gaba da addu'a, wllh kawata tunda naga abun nan Allah ya sani baccin kirki for the
pass 3 days ban yi ba, amma koma waye yayi mana haka xai ga sakkaya daga wajen
Allah, sai Allah ya saka mana" Nihad ta sunkuyar da kai a hankali tace "Kuma fa wai
aure Uncle dina da Inna suka ce xa ayi min" Husnah ta xaro ido tace "What?? Aure??
Which of ur uncle are u talking about? Abbansu Hamid??" Nihad ta gyada mata kai,
Husnah ta rike ha6a tace "But sorry to say Nihad yanxu duk rashin jin da su Zeenat
da Pinky ke yi bai gani ba sai naki? Duk runz din da suke yi babu wanda ya hango
nasu sai naki? Lallai kam ance laifi tudu ne, Kawai sbda wani axxalumin yaje yayi
posting dinki halve naked shine xa ace xa a maki aure? Wa enda ma aka saki
hotunansu fully naked ba ace xa a masu aure ba sai ke da naki nafila ne, Tabdi...
to wai wa suka ce xa su aura maki?" Nihad tace "I don't even know, but i am
thinking of running away" Husnah tace "Nima nayi wannan tunanin, kada ki wani tsaya
a cuceki a...." Bude kofa aka yi duk suka yi shiru suka juya suna kallon kofar,
Yaya Farooq ne ya shigo dakin, Nihad sai da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta don
bata mance dukan tsiyan da yayi mata shekaranjiya ba, banda ma Umma ta masa jan ido
ta kwaceta a hannunsa, Ya wani murtuke fuska yana kallon Husnah cikin daga murya
yace "Ke, Uban wa ya baki permission din shigowa gidan nan, ta ina ma kika shigo
don uwarki??" Husnah ta mike tana sissinne kai jikinta na 6ari, Ita dai Nihad banda
faduwa babu abinda gabanta yake har ta fara kallon bandaki ko can xata shige ta
kulle, Ya daka ma Husnah wani raxanannen tsawa yace "Xo ki fita kar in karya ki in
karya banza" Jakarta ta dauka ta nufi kofa da sauri har tana tuntube, Tana fita ya
doka ma Nihad wata harara yace "Kin ga result din bin ire iren kawayen nan ai..."
Cikin rawar murya tace "Yaya ita Husnah ai babu ruwan..." Haureta ya kai kafa xai
yi ta kauce, ta fashe da matsanancin kuka dai dai shigowar Umma, Umma na ganinsa,
tana tafe hannu tace "Wato duk warning din da na maka bai isheka ba ko Farooq? Duk
jan kunnen da nayi maka kar ka sake dawowa hanyar dakin nan watsi kayi da shi sbda
ban isa ba ko?? To uban naku ma da ya ga abun nan ko nunata da yatsa bai yi ba
balle ya kai mata hannu, kai ko zagi bai hadasa da ita ba, to wai shin ma ina
ruwanka farooq? Meye naka? To wllh ka shiga hankalinka ka fita harkarta a gidan
nan, ka shiga hankalinka nace, Shi Usman da yake ba mahaukaci bane ai nasiha kadai
ya hadasa da ita, tun daga sannan ma a ina ta sake saka sa a ido, abun nan dai naga
ba yaki bane, kai iskancin da kake sani ake yi balle a tsawatar maka?? To ahir
dinka farooq kar ka kuskura in nuna maka bacin rai na wllh" Ita dai Nihad shessheka
kawai take, shi kam banda kallon mahaifiyarsa babu abinda yake, ji yake kamar ya
karya Nihad ko xai ji sauki a ransa, juyawa yayi ya fice daga dakin kamar xai tashi
sama, Umma ta bi sa da harara, sai kuma ta ja tsaki tace "Rabu da shi, ba kanki
farau ba ai" Daga haka ita ma ta fice daga dakin. Bayan magrib Nihad ta dake ta
fita dakinta for the first time tun da gari ya waye, part din mum dinta ta nufa,
duk gaba daya jikinta a sanyaye yake, ta bude kofar parlon a hankali Mumy na xaune
parlon da sisters dinta biyu, tun jiya suke gidan amma ko bin ta kanta su ma basa
yi, abun duniya duk ya ishesu barin da suka ga damuwar da yayarsu ta shiga, Nihad
dai tunda Umma ta kwace ta a hannun Aunty Jamila rabonta da su sai kuma yanxu,
banda faduwa babu abinda xuciyarta ke yi, Mumy ta nuna mata kofa alamar ta fita,
kuka ta sakar mata ta xube nan bakin kofar cikin rawan murya tace "Don Allah Mumy
kiyi hakuri ki yafe min, wllh i don't know how all this happen, i don't know who
did this to me, mumy ba halina bane don Allah ki saurareni" Mumy tace "Fita nace
Nihad" Kallon Aunties dinta tayi tana girgiza kai wasu sabbin hawayen na sauko mata
tace "Aunty Jamila don Allah ku ce Mumy ta yafe min" Ganin Mumy ta mike, ta tashi
da sauri ta fice daga parlon xuciyarta na bugawa, kuka take sosai bata da option ta
nufi dakin yayanta farooq, bata tadda shi a dakin ba ta rakube jikin kofa tana
shessheka, ba a dau lkci ba ya shigo dakin daga masallaci, yana kokarin kulle kofar
ya ganta, kan yace komai ta hade hannunta with tears tace "Ya farooq don Allah ka
saurareni, only u will understand and listen to me, wllh i knew nothing about that
video, ban san wa yayi min ba, ban san yaushe aka min ba, ban kuma san wanda ya
fitar ba" Kuka take sosai, ya daure fuska yace "Shaye shaye kika fara da har baki
san when and where aka maki video din ba Nihad??" tace "Believe me yaya Farooq,
wllh ban sani ba, yanda ku ka gansa haka nima na gansa" Yace "Na rabaki da bin
kawaye barkatai Nihad, na rabaki da yawace yawace da xuwa parties, har night party
nasan kina xuwa don Sadeeq saw u, na maki magana kika karyatasa kamar bai san me
yake ba, u are just different from every other child in this house, just look at
the disgrace u have caused to our family, u have tarnished the reputation of our
home, how will i face my frnds da suka sanki, my own blood with such act? Oh no,
Subhanallah" Ta dinga girgiza masa kai tace "Don Allah ku yi hakuri yaya, i wish my
life can end now because of all this, i regret everything" Xaunawa yayi gefen gado
ransa a dagule, ita dai ta dinga goge hawayen da ya ki tsaya mata tace "Yaya farooq
i need one favor from u plss" Yace "U don't deserve that favor Nihad" tace "Plss
yaya abu na karshe da xa ka iya min a rayuwa shine don Allah kar ka bari Abba su yi
min auren dole, wllh xan iya mutuwa kaga har na gaya maka" Yace "What did ur
boyfriend say about the video?" A hankali ta sunkuyar da kai tayi shiru, ya hade
rai yace "Tambayarki nake" Cikin rawan murya tace "Yayi blocking dina...." Farooq
ya gyada kai yace "Good" ta hade hannunta tace "Don Allah yaya, kasan consequences
din auren dole kar ku bari ayi min, na yarda a min ko wani hukunci amma banda auren
dole, idan ma xa a ce for the rest of my life baxan sake fita waje ba, sannan babu
ni babu karatu har abada i agree but kar ayi min auren dole sbda wannan mistake din
nawa, ka taimaka kayi ma Abba magana" Umma ce ta shigo dakin duk suka daga kai
suna kallonta, tace "So kike ki kara tunxura Abbanki Nihad? Duk shirun da yayi maki
bai isheki ba sai kin tunxurasa, Ba na baki shawaran kar ki ce komai a kan batun
auren nan ba, so kike ki fusatar da Abbanki yayi maki abinda bai ta6a maki ba?"
Faruq yace "Noo wannan ba magana bace Umma, we don't even know da wanda xa a
hadata, ko ma me tayi ai da gatanta and she still have her right, su gani suke
auren shine way out, whereas it's not" Umma tace "Toh tunda kai ka haifesu ai sai
ka gaya masu way out" Ya girgiza kai yace "Umma idan ma auren ne ba sai a bari
komai ya lafa ba, ta yaya abu na xafi xafi a shigo da maganar aure, waye xai
aureta? Noo bata yi deserving wannan auren ba gaskiya" Umma tace "Ko ma wa xai
aureta wannan ba damuwarka bane sai ka xuba ma iyayenka ido, su ai sun san abinda
ya kamata, ko so kake ka nuna masu goyan bayan abinda tayi kake?" Ya dinga kallon
Ummar tasa, Mikewa yayi ya fice daga dakin, ta bi bayansa, Nihad ta bi su da kallo,
sai da suka sauka stairs Umma tace "Farooq" ya juyo yana kallonta, tace "Naga kamar
so kake ka ja ma kanka bakin jini gun Kakarku da Engineer, sannan nima hakan ya
shafeni, kawai so kake ka ja min maganan da ba shi da ranan mutuwa gun tsohuwar
nan, don haka kar ka sake tofa komai a kan lamarin nan, ita kanta uwar da ta
haifeta taki cewa komai har yanzu, me magana dama daga ni sai kai, kuma a hakan ma
haushinmu ake, don Usman ma bai tsoma kansa ba balle a ga nasa, to ba Uba daya ba,
ko ciki daya ku ka fito da Nihad ni dai nace ka janye bakinka daga issue din nan
domin a samu masalha, daxu Abban naku ma ya kirani wai ya tafi karkara neman wanda
xai hadata da, to idan ana son asiri ya rufu ai sai dai hakan dama, to wa xai yarda
ya aureta a nan dai cikin gari? don haka nake kara gargadinka, kar ma ka fara cewa
a fasa aure" Faruq yace "Karkara kuma?" Umma tace "Ehh nan fa, ko ka ga alamar
Nihad xata samu miji cikin gari ba karkaran ba nace, da wannan mummunan abin da ta
aikata wa xae yarda nasa ya aureta?" Yace "Ah haba, karkara kuma, noo ba dai
karkara ba, waye ya ba Abba wnn muguwar shawaran? Karkara fa kike ce Umma" Strictly
Umma tace "Farooq" ya daga kai ya kalleta tace "I am giving u this serious warning,
kada ka kuskura ka sake tofa naka a wannan lamarin, kaji abinda nace maka??" Bai ce
mata komai ba, tace "To na dai gaya maka" daga haka ta bar wajen ya bi ta da ido.

💖 *Bitter Rivalries*💖

And i came really prepared...... 🤗

Contact me directly via👇🏻

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

By _Khaleesat Haiydar_✍🏻

~~

Dumbin gaisuwa da fatan alkhairi xuwa ga iyayen gidan Khaleesat's Palace, my die
hard fans🥰😍 Su Hajjaju Chamo me gwala-gwalai duk da jarin ya karye amma take ta
bobboye mana, Hajiya Aunty Zahra mai siyar da harawa, Hajiya Nafisa Mom twins, Su
Hajiya Aunty Maryam, Uwar Nabeela, Mrs Jay, Hajiya Inna, Hajiya Deejah, Hajiya
Zeenaru, Nanisa Zero Zero, Hajiya Bilkisu, Hajiya Rabia, Damsel, Uwar Yusrah, Ummu
Zainab, Uwar gidan Barrister wato Khaleesat me siyar da tayoyi, kai duk wanda bai
ga sunansa a nan ba ya biyo ni da sunan xai gansa a next page😜 amma fa ko kun ki ko
kun so sai nayi sharing link dinku, ku tanadar ma sabbin fans ruwa da cin cin ehe.🤓

Da daddare Abba na xaune parlonsa tare da Yayansa Alhaji Abubakar.... Alhaji


Abubakar yace "Ae duk ba sai ka sanar masu komai ba, kawai gobe idan an daura auren
kowa ma sai ya sani, i don't think u owe anybody explanation to this" Abba ya
numfasa yace "Toh shikenan" Alhaji Abubakar yace "Yea i think that's okay ba sai
kace ma kowa komai ba for now, a ina kace xa su xauna? I mean which of ur houses
are they staying?" Abba yace "I don't think i can keep her where she will in any
way feel comfy, i wish xai koma can karkarar tasu su xauna in basa enough jari,
idan noma xai yi ma yayi employing workers su yi masa a can ko ni xan dinga biya,
cause i want her to learn a bitter lesson of her life, ina son ta san wata rayuwar
bayan rayuwa cikin daula" Alhaji Abubakar ya girgiza kai yace "No... There is no
need for all that, duk abinda ya kamata kayi kar ka fasa, ka basu inda xa su xauna
comfortably" Bayan Alhaji Abubakar ya bar gidan, Umma ta shigo parlon Abba, ganin
basu ta6a abincin da ta ajiye masu ba tace "Haba yallabai, ko abincin baka ci ba
har yanxu?" Abba yace "Kawai ayi min black tea" Umma tace "Toh shkkn" Tashi tayi ta
dau abincin ta fita, ba a dau lkci da fitarta ba Farooq ya shigo parlon, waya ya
tadda Abbansa ke yi, wanda da jin yanda yake amsa wayar kasan magana ce aka kirasa
a kan Nihad kuma abokinsa ne me kiran nasa, Farooq ya sunkuyar da kansa duk jikinsa
yayi sanyi, har Abba ya gama wayar ya jinginar da kai da kujera bai ce masa komai
ba, a hankali Farooq ya dago yace "Barka da dare Abba" Abba ya amsa, Farooq yace
"Throughout ina ta kiranka but couldn't reach u on phone" Abba yace "Ehh wata er
tafiya nayi, is there any problem?" Farooq yace "Ya gajiyan hanya" Abba yace
"Alhamdulillah" Farooq yayi kasa da murya yace "Abba magana ce dama a kan Nihad?"
Dai dai nan Umma ta shigo da mug din black tea dake ta kamshi, Da hannu Abba yayi
masa alamar ya aka yi, Farooq yayi shiru, Abba yace "Maganar me a kan Nihad Umar?"
Farooq ya d'an fara kame kame, sai kuma dai kawai yace "Abba a kan auren nan da aka
ce ne, is it not better a yi hakuri a janye, idan ya so..." Dakatar da shi Abba
yayi yace "Idan wannan maganar ce ta kawo ka, ka je kawai i need rest Umar, kaga
ban dade da shigowa gidan ba" Umma dai na xaune kan one sitter, pleadingly Farooq
yace "Pls ka saurareni Abba" Abba yace "I said i need rest...." Umma tace "ka je
yace xai huta ko kuwa?" Mikewa Farooq yayi ya fice daga parlon, Umma ta kalli Abba
tace "Kayi hakuri Yallabai, xan so ka cire wannan damuwar a ranka, in sha Allah
everything will be alright, kar kaje ka sa ma kanka wani ciwon bayan hawan jinin da
kake fama da" Abba yayi sigh yana girgiza kai yace "A kalla ba a kirani a rana ba
xa a kirani sau goma a kan Nihad, the video is trending day by day.... Me yafi
wannan bakin ciki Sumayyah? A reputable person like me, noo Nihad tayi tarnishing
image din gida na" Da damuwa Umma tace "To ya xa ayi Yallabai haka Allah ya kaddaro
mana, sai dai kawai mu rungumi kaddara, amma akwai wani malami bawan Allah, tun
ranan da abun ya faru Hajiya Sukhaina tace ko shi xa ayi ma magana yayi addu'a
Allah ya kawo karshen trending din abun, shiru xaka ji kamar ba ayi ba wllh, neman
video din ma xa ayi a rasa" Abba ya mata wani kallo yace "Malami? Wani irin
malami?" Umma ta gyara xama tace "Ba boka fa nace ba Alhaji, amma dai shkkn kawai,
ina ce akwai malamai bayin Allah wa enda..." Mikewa Abba yayi bayan ya dau mug din
black tea dinsa ya wuce daki ya kulle kofa. Washegari friday ana sauka sallan
juma'a, Abba ya tafi tare da yayansa da cousins dinsa biyu xuwa garin da aka daura
ma Nihad aure, a kan sadaki dubu hamsin wanda shi ya bayar. Sai kusan la'asar suka
dawo gida, nan kuma ya sanar ma Umma su fara shirye shiryen kai ta, Umma tayi shiru
cike da jimami, sai kuma ta sauke ajiyar xuciya tace "To wani gidan kenan xa a kai
ta yallabai?" Abba yace "Wannan gidan da aka gama na Rijiyar zaki, it's already
furnished" Umma tace "Allah sarki, ina laifin wannan gidan na kusa da mu yallabai,
ai xa su fi sakewa a nan..." Abba yace "Ban yi niyya ba" Umma tace "Rijiyar zakin
ma yayi ai, Allah ya saka da alkhairi" mikewa tayi ta fita don xuwa sanar ma Mum
din Nihad da Yan uwanta dake can bangarenta abinda Abba ya ce, nata side din ta
fara shiga, first daughter dinta Kamila na xaune parlon sai second daughter dinta
Amina, sannan kanninta mata biyu da suka xo daga Jigawa daxu, Umma tace "To duk ku
shirya kai amarya an daura mata auren yau dai" Kamila ta riƙe ha6a tace "Har an
daura?? yanxu Umma Abba bai fada maku da wa aka yi auren ba, ni kawai sai xuciyata
ke bani Hamid ne ko Saif" Umma ta saki baki tace "Hamid? Ita uwar Hamid din karen
hauka ya cijeta xata yarda a hada shi da Nihad? Ko kuma shi Hamid din mahaukaciya
ne da zai amince da auren Nihad, Kai har shi Uban Hamid din da ya kirkiro auren ba
yarda xai yi ayi auren da ɗan sa ba karewa kenan, haka ita ma Innar, wani can dai
Abban naku ya samo a karkara, hakan kuma kadai ne rufin asirinta a dai abin nan da
ya faru" Amina ta mika ma Umma wayarta dake ring, Umma ta amsa ganin autarta ce ke
kira ta daga ta kai kunne da murmushi tace "Hello auta, duk yau kin ji ni shiru ko"
lkci daya ta hade rai tace "Ki zo kiyi me kina karatun ki Nihal? A kan wani dalili
xaki taho kuna tsaka da karatu? To wllh kar ki fara idan ba haka ba yanxun nan in
kira Farooq in gaya masa, me xuwanki xai sa a fasa, bayan har an daura auren ma,
duk sanda ku ka yi hutu idan kin dawo sai kije ki ga dakin er uwar taki ba shikenan
ba, amma ki wani ce xaki kamo hanya kamar ana yaki" a kufule Umma da ta gama
sauraronta tace "To wai uban meye na wannan kukan da kike, so kike ki ja ma kanki
wani ciwo ne ko ko? Bata da waya yanxu a hannu, idan na fita yanxu xan bata sai ku
yi magana, amma ta ina xaki baro Zaria da yamman nan ba hutu ku ka yi ba, kuma dama
kin ta6a dawowa gida ke kadai ne banda gulma da daura ma kai wahala Nihal?? Ni dai
sai anjima ban san shashanci" Katse wayar Umma tayi, Aunty Laraba tace "Wai tahowa
xata yi daga Zarian?" Umma tace "Ehh wai, kinji wata gulma dai, ko uban me xata xo
tayi oho" Aunty Laraba tace "To wai ita tace ma Abban nasu bata son Maryam Abatcan
da er uwar ke xuwa ne?" Umma tayi murmushi tace "Aa haka dai yayi niyya ita ya
turata federal dai dai ita, ita kuma Nihad dama Private ne dai dai da ita inji
uban, wato Maryam Abatcha, option ma ya bata ta xabi Private uni da take so shine
ta xabi Maryam Abatcha" Aunty Maimuna tace "Ai ko ga Maryam Abatcha ana ta gani a
soshiyal media" Umma dai bata ce komai ba, sai kuma tace "Allah dai ya shirya mana
zuri'a kawai" daga haka ta fita xuwa bangaren mum din Nihad, a corridor ta hadu da
matan Alhaji Abubakar su biyu sun shigo gidan, suka gaisa da fara'a ana kara
jajanta lamarin da ya faru, Hajiya fatima tace "Daxu Abbansu Hamid ya dawo gida
yake sanar mana ai har an daura aure, nace shine babu labari ko daga gare ku
Hajiya" Umma tace "Wllh abun ne ya xo a haka Hajajju, kinsan muna ta tunanin xa su
hakura a fasa auren a nemo wani solution, to kin san halin mazan namu da kafiya,
wllh sun ki, kawai fatan Allah ya basu xaman lafiya da ko ma waye mijin" Hajiya
Zuwaira tace "Shikenan addu'ar, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi a gareta,
Allah kuma ya duba yan baya" Duk suka amsa da Ameen, Umma tace "Mu je dama bangaren
Maryam din xan je" a tare suka tafi part din Mumy, bayan an gaisa an kara
jajantawa, Mumy dai bin su kawai take da kallo bata cewa komai, Umma ta sanar mata
abinda Abba yace sannan ta fita daga dakin. Bayan magrib xa a kai Nihad, kafin
Magrib din Abba ya tara gaba daya matan nasa da 'ya yansa, Usman, Farooq, Kamila,
Amina, Nihal ce kawai bata nan a yaran Umma, yaran Mumy kuwa Nihad da kanninta biyu
wa enda duk maza ne, daya me shekara tara da kuma me shekara shidda duk basa
parlon, Bayan duk sun hallara a parlon Abba ya nisa yace "Ina fatan duk kun ga
abinda ya faru da yar uwarku Nihad, Nihad is nothing but a disappointment to the
family, kar ku ga Nihad tayi wannan mummunan laifin na bada ita ga wanda nayi niyya
without bothering ko ya cancanceta ko bai yi ba, to wllh wllh if anything of such
should happen again in my family infact ko wanda bai yi kusa da hakan ba idan ya
faru a family dina wllh i will prefer to shoot that person" Umma ta sauke ajiyar
xuciya tace "Allah Ubangiji ya tsare, ya kare mana zuri'a Alhaji" Abba ya kalli
Mumy da bata cewa komai tun faruwan abun, amma kana ganinta kasan she is
heartbroken, her first child, habaa ko bacci bata iya yi tunda wannan lamari ya
faru, da tasan Nihad xata girma ta yi irin wnn rashin jin da Allah bai raya mata
ita ba, tun faruwan hakan ita ma ta kashe wayarta sbda kiran yan uwa da abokan
arziki da suka san Nihad, Abba yayi gyaran murya yace "Ban ga laifinki ba Maryam
don ni nasan kinyi iya bakin kokarin ki na ganin kin ba ma Nihad tarbiya yanda ya
kamata, u tried ur best, matsalar kawai u didn't make Nihad ur frnd aside mothering
her, amma dai babu komai, kawai dai kafin Nihad ta dauko mana abinda xuciyarmu xai
kasa dauka nan gaba tun wuri ni da yayana da yan uwana mun mikata, kusan xance na
bada sadakarta" Abba na fadin haka ya ciro sadakinta dake aljihunsa ya mika ma Umma
yace "Sai ki damka mata ku da xa ku kai ta" Umma ta amsa cikin sanyin murya tace
"Yanxu Yallabai mun yi deserving a bada er mu ba tare da mun san wanda aka ba ma
ba? Ai hankalinmu baxai taba kwanciya ba, tun jiya nake bin ka kaki gaya min, ai
yana da kyau a sanar mana mu sani don muna da hakkin sani, idan ma ni bani da
hakkin in sani mahaifiyarta fa?" Abba ya ɗan yi shiru, sai kuma ya dau wayarsa yayi
dialing number snn ya kai kunne, ana dagawa yace "Ka shigo nan parlor ka sameni
yanzu" daga haka ya katse wayar, duk kowa yayi shiru ya xuba ido ya ga wanda xai
shigo parlon barin Farooq da Umma. Da sallama ya bude kofar parlon, ganin su Umma
ya dakata daga bakin kofar bai shigo ba, Abba na kallonsa yace "Karaso" ya karasa
shiga cikin parlon kansa a kasa, duk occupant din parlon
kallonsa suke with full shock, Abba ya nunasa yace "Shi na ba auren Nihad, shine
mijinta" Mikewa Farooq yayi yana kallon Abba baki bude, Mumy ta hadiyi wani kullutu
da taji ya tokareta a makogwaro, Umma kuwa sae kallonsa take daga sama har kasa
babu ko kiftawa, ta ma rasa yanayin da take ciki ita, Kowa na parlon ya kasa cewa
komai, tsabar silence din parlon da allura xai fadi xa a ji karar faduwarsa, shi
kam dai yana ta tsaye ya sunkui da kai har sannan, Abba yayi breaking silent din
yace "Je ka" Juyawa yayi ya fita daga parlon, Usman ya kalli Abba yace "Haba Dad?
Yanxu shi ka aura ma Nihad?" Farooq yace "No Abba, u should have given her a
choice, bata yi deserving ayi mata dole ba sbda wannan kaddarar tata, but Abba...."
Kasa cewa komai yayi ya koma ya xauna, shi ma ya rasa yanayin da yake ciki, but he
don't think it's still bad after all, just dat.... Girgiza kai kawai yayi, Umma
tace "Haba Alhaji...." Abba ya mike yana bin kowa da kallo yace "No one have the
right to query my authority" Yana fadin haka ya bar masu parlon ya shiga bedroom
dinsa, suka dinga kallon kallo a tsakaninsu a parlon, Usman ne ya fara mikewa ya
fice daga parlon, Mumy ta mike ta bi bayansa ita ma tana share idonta, Umma ta
sauke ajiyar xuciya tana kallon Farooq, ita gaba daya ma kanta fa ya kulle, Abba
really took them unaware, jinginar da kanta tayi da kujera Farooq ya mike ya fice
daga parlon shi ma. Ana idar da magrib yan kai amarya suka fara shirye shiryen kai
ta, Nihad bata ta6a shiga irin tashin hankalin da take ciki ba a wannan moment din,
ko video dinta bai tada hankalinta kamar yanxu ba, gashi nobody is there to console
her, Nihal na schl, Husnah kuma taki xuwa gidan sbda Farooq, gashi bata da numberta
a kai balle ta amshi wayar wani ta kirata, su kamila da Amina tamkar ma farin ciki
da abinda ya sameta suke don uban kwalliya suka ci har da kashe dauri Hajiya
Zuwaira ce ta kai ta gun Mumy tayi mata fada ta sa mata albarka, sbda takaici da
bakin ciki Mumy ta ki cewa komai daga karshe da aka tilastata sae cewa tayi Allah
ya tsare, Alhaji Abubakar ne kawai yayi mata fada, Abba kuwa tun da aka idar da
magrib ya ki shigowa gidan dama, a haka dai aka tattara ta da akwatunan kayanta uku
wanda Umma da Kamila suka hada mata wasu kayayyakinta a ciki, kuka take kamar xata
shide, har addu'a ta dinga yi Allah ya dau ranta kafin a karasa da ita gidan, tana
ganin an shiga gidan ta kara sautin kukan da take a haka har aka shigar da ita
daki, gida ne bungalow madaidaici me dakuna uku, ko wani daki da bandaki, sae
bandakin dake parlor sai kitchen, anyi furnishing gidan babu laifi sai dai
furnitures din ba masu tsada bane, Nihad ta dinga kuka tana cewa ta shiga uku, masu
bata bakin ma har sun gaji sun daina, karfe tara saura suka fara shirin tafiya,
Nihad ta rike hannun Kamila cikin kuka tace "Aunty ynxu tafiya xa ku yi ku bar ni,
don Allah kar kuyi min haka..." Kamila tayi dariya tace "Ae ko dole xa mu yi maki
haka tunda mun kawo ki gidan mijinki kinga ni ynxu sae na koma xan dau jakata inyi
driving xuwa gida, kawai kiyi hakuri ki bi mijinki ku xauna lafiya ko hakan xai
goge wannan ta6on da kika ma kanki" Daga haka ta fice daga dakin don dama ita ce
karshen fita, Nihad ta silalo kasa ta xauna tana kukan takaici, tana jin duk suka
fice daga gidan ta daina jin hayaniyar kowa, nan kuma tunanin ta ya tafi gun wanda
xata gani a matsayin mijinta, tsoho ne, yaro ne, baki ne, fari ne, kato ne, siriri
ne, mummuna ne, kyakkyawa ne, infact duk wannan tunanin ne suka baibaye ranta
gabanta ya dinga faduwa hankalinta ya kara tashi, daga karshe ma daina kukan tayi
banda bugawa babu abinda xuciyarta yake, ta fi minti ashirin a haka taji an bude
gate, da sauri ta mike ta tafi gun window ta bude labule amma sai taga ba ta nan
gate din ma yake ba balle taga me shigowa, komawa tayi ta xauna can karshen gado
tana jin yanda kirjinta ke heaving, to waye wannan da ko mota ba shi da, bayan wasu
mintuna taji an shigo parlor, daga karshe ta ji kamar an bude wani daki an shiga,
mikewa tayi ta jingina da window with so much fear, har ta gaji da tsayuwa bata ga
alamar xa a shigo dakin ba, komawa tayi ta xauna gefen gado, a kan idonta karfe sha
daya tayi, bacci take ji amma taki kwanciya sbda fargaba, kafin sha biyu bacci
barawo ya saceta. Ba ita ta bude ido ba sae da hasken rana ya sauka saman fuskarta
washegari da safe, a firgice ta mike xaune, sae kuma ta sauka daga saman gadon ta
shige bandaki da sauri, bayan ta idar da sallah ta mike a hankali ta nufi kofar
dakin ta bude ta fita xuwa parlor, ta dinga bin ko ina da kallo xuciyarta na
bugawa, kofar da take tunanin kitchen ne ta nufa ta bude kofar a hankali, wani kara
ta saki ba tare da ta shirya ba ganin mutum a tsaye yayi backing kofar kitchen din
ga ruwa ya daura saman gas, juyowa yayi suka yi ido hudu da ita, wani irin shock ne
ya bayyana a fuskarta ta dinga komawa baya tana kallonsa bakinta ya kasa furta
komai, can ta nunasa da yatsa nan ma words suka yi failing dinta, juyawa yayi ya
kashe gas din don ruwan ya fara tafasa ya juye cikin mug sannan ya bi gefenta ya
fice daga kitchen din ba tare da ya sake kallonta ba, makalkalewa tayi jikin kofa
jikinta na 6ari tana ganin abun kamar a mafarki, sae a sannan bakinta ya bude ta
fasa wani raxanannen ihu, sai kuma ta fara ganin kitchen din na juya mata lkci daya
ta sulale kasa....
_8 months earlier_

Contact me directly via👇🏻 to gain access to the book

07087865788 ✍🏻 NIHAAD💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

~~~

Gaisuwa da fatan alkhairi xuwa ga sauran membobi yan gurmin Khaleesats Palace, don
gurminsu ya hana in saka sunansu jiya inga ta tsiya, Su Hajiya Aisha Bela, Hajiya
Suwaiba, Hajiya Safiyya Usman😂 Hajiya Mardiyya mandy rice😜, Hajiya Sadiya uwar
Hanan, Uwar Sa'eed, Hajiya Farida me kayan en gayu, Amzaj, Hajiya Zaarah, Wata ana
ce mata me kayi nayi, Hajiya Aisha Macika, Hajiya Billy, Uwar Habee, har dai da
wata me gawayin dare, duk na gaisheku kyauta... Sauran da basu ga sunansu ba a
tsakiyar rubutu xa su gani😁

8months earlier...

Zaune yake saman farar kujera dake kusa da dakin mai gadi, ya fi awa daya xaune
wajen, lkci lkci yake goge zufan fuskarsa da handkerchief din hannunsa, karamar
waya ya fiddo aljihunsa yana duba agogo dake nuni da karfe biyar da rabi, ya juya
ya kalli mai gadi dake xaune gefensa da radionsa a hannu, xai yi magana aka danna
horn, da sauri mai gadin ya ajiye radion ya mike ya isa bakin gate din gidan ya
bude, wata rantsantsiyar mota ce ta shigo compound din, mutumin dake xaune ya bi
motar da ido har ta isa kantamemen space da aka tanadar don parking a compound din,
mai gadin ya dawo bayan ya maida gate din ya rufe yace "Bari in sanar masa kana ta
jira kar ya shige ciki kuma" Daga haka ya nufi parking lot din ya jira har dattijon
dake cikin motar ya sauko yana gyara babban rigar jikinsa, da ladabi me gadin ya
risina yace "Barka da isowa Alhaji" Alhaji Ibrahim yace "Yauwa Aminu... " Mai gadin
yace "Alhaji dama Habibu ya taho da baƙon tun daxu, shi har ya ma tafi yace yau xai
koma, baƙon kuma gashi can yana jiranka tun karfe biyu" Alhaji Ibrahim ya kulle
motar tasa yace "Ohk, to ya karaso" Mai gadi ya koma gun mutumin dake xaune saman
farar kujera da sauri yace "Kaje nayi masa magana" Tashi mutumin yayi ya nufi
parking space din, yana isa ya duka har kasa yana kallon Alhaji Ibrahim yace "Barka
da yamma Alhaji" Alhaji Ibrahim na kallonsa yace "Yauwa kai ne wanda Habibun ya
kawo kenan?" Mutumin yace "Eh ni ne" Alhaji yace "Ya sunanka?" Mutumin ya sauke
idonsa daga kallonsa yace "Sunana Ibrahim" Alhaji Ibrahim ya jinjina kai yace "To
madallah, amma ya ku ke da Habibun?" Mutumin yace "Garinmu daya da shi, ga gidanmu
ga gidansu, babana aminin mahaifinsa ne" Alhaji Ibrahim yace "To ba laifi, ai har
garin naku naje watanni da suka wuce" Shi dai mutumin bai ce komai ba, Alhaji
Ibrahim yace "Shkkn babu damuwa, amma kayi karatu ne?" Mutumin ya girgiza kai yace
"Aa iyakata sakandari, shi ma ban zana waec ba" Alhaji Ibrahim ya daga kafada yace
"Ohk, xuwa kake ganin xaka dinga yi kullum ko kuma yaya tsarin naka yake?" yayi
kasa da kai yace "Duk yanda ka tsara haka xa ayi Alhaji" Alhaji Ibrahim yace "Kaje
dai gobe da safe ka dawo, ni yanxu xan shiga ciki in huta ne, dawowata daga aiki
kenan..." yace "Toh nagode kwarai Alhaji, Allah ya kara girma" Tuni Alhaji Ibrahim
ya nufi main entrance din shiga gidan nasa, ya mike ya bi sa da kallo, sannan ya
kalli building din gidan wanda duplex ce gari guda, juyawa yayi ya koma gun mai
gadi, mai gadin na ganinsa yace "Ya ake ciki?" yace "Yace in dawo da safe" Mai gadi
yace "Ahaf ai ka ma samu, tunda ta hannun Habibu ka biyo, ai Alhaji sun fi shekara
goma sha biyar da Habibu, har kauyensu ya je daurin aurensa kwanaki, in dai baka da
rawan kai sannan uwa uba ace kana da nutsuwa gun aikinka to wllh tuni Alhaji xai ja
ka jiki ka xama kamar d'an gida, ba ga mu ba duk mun dawo kamar yan gidan banda dai
ba halinsu daya da wasu daga ahalin gidan nasa ba, to ya sunan naka?" Mutumin yace
"Sunana Ibrahim" Mai gadi ya rufe baki yace "Yo ai sunan Alhajin kenan" yace "Allah
sarki, Sai goben in sha Allah, xan tafi ynxu" Mai gadi yace "Allah ya kai mu" Gate
ya nufa ya fita daga gidan. Alhaji Ibrahim ne xaune parlonsa, daga gefensa matarsa
kuma amaryarsa Hajiya Maryam, Wasu yan mata ne biyu xaune daga kasa saman lallausan
carpet dake malale parlon, Hajiya Maryam tace "Ayi hakuri Alhaji in sha Allah hakan
ma baxai sake faruwa ba, ita ma Hajiya nasan bata fahimce su bane, amma xa su je su
bata hakuri" Alhaji Ibrahim na kallon yan matan yace "Ku tashi ku bani waje" Duk a
tare suka ce kayi hakuri Abba, yace "Ku fita nace..." Mikewa suka yi a tare suka
fita daga parlon, daya daga cikin yan matan tace "Gaskiya ni ki daina ja min Nihad,
ko me kika yi sai a hada mu a mana fada, da na sani da ban biki ba jiya, haba don
Allah" Tsaki er uwar tayi mata ta bi wani corridor tayi gaba abunta irin ko damunta
abun bai yi ba. Wata mata ce da baxata haura hamsin da bakwai ba xaune wani
lafiyayyen parlor da ba a cika da kaya masu hayaniya ba, cike da ɓacin rai tace
"Toh banda ma fitina da neman magana irin naku dole ne sai kun je? Me yasa baxa ku
xauna inda Allah ya ijiye ku ba, maganinku kenan" Nihad tace "Ae wllh daga yau ko
Abban ne yace mu je ni dai sai dai in fita inyi using opportunity din in xaga gari
in sha iska in dawo abu na, i don't care... baxan sake xuwa ba gaskiya" tana kai wa
nan ta mike ta dau wayarta dake caji ta fita daga parlon, Hajiya Sumayyah tace
"Atoh dai, da ya fi maku, don dama magana ta ce kawai bakwa ji banda haka na hanaku
xuwa tun ba yau ba" Ita dai er uwar Nihad na kwance saman kujera bata ce komai ba,
Hajiya Sumayyah ta bude kofar bedroom dinta ta shiga ta kulle. Washegari asabar
kasancewar yan matan gidan basu da lectures duk suka yi shirin tafiya islamiyya
amma banda Nihad dake kwance parlon step mum dinta tana aikin danna waya, Hajiya
Sumayyah da suke kira da Umma da tace "Ke Nihad kina kallon lkci kuwa, ko baxa ki
islamiyyan bane yau ma?" Nihad tace "Umma sai gobe i have something important to
do" Umma tace "To ita Nihal ma cewa tayi ba xata ba?" Bata rufe baki ba sai ga
Nihal ta shigo har ta gama shiryawa, Umma ta kalli Nihad bata dae ce komai ba ta ci
gaba da abinda take, Nihal tace "Hope u are been cautious of time Nihad?" Tashi
Nihad tayi ta fita daga parlon tana cewa "Ni sai gobe" Mai gadi ne tsaye tare da
mutumin da ya xo jiya, bayan sun gaisa mai gadin yace "Yanxu xaka ga Alhajin ya
fito xai tafi gun motsa jiki, don ma yau bai fito da wuri ba, amma dai bari in
sanar masu a ciki kar kuma ka yi ta jira haka babu dadi" mutumin yace "To nagode"
Xaunawa yayi kan farar kujera yana bin compound din da kallo don ya kayatu da
kyawawan shukoki na flowers har ma da artificial flowers, daga can wani gefe wani
karamin water fall ne me ban sha'awa ruwa na ta xuba ga artificial crocodiles da
kifaye a ciki, ba a dau lkci ba mai gadin ya dawo yace "Ka ga wancan yar barandar?"
ya kalli inda yake nuna masa yace "Eh na gani" Mai gadin yace "Toh kaje can kayi
jiran alhajin, akwai kujeru ma a wajen" Tashi yayi ya tafi wajen yana bin ko ina da
kallo, bayan kujeru masu kyau har da carpet grass malale a kasa daga gefe, ga
artificial flowers da ya kawata wajen, ya xauna saman daya daga kujerun wajen
surveying everywhere with his eyes, bayan kusan minti sha biyar aka bude kofar
parlon, tsaye tayi tana kallonsa daga sama har kasa a bit flabbergasted, ya kalleta
yayi kasa da kai yace "Ina kwana" tace "Wa kake nema Malam? Daga ina haka?" Yace
"Mai gidan nake jira" ta fi minti daya tana masa kallon sama har kasa, ta ma rasa
me xata ce, sai kuma ta sauka kasa xuwa compound din ta tafi gun mai gadi da sauri,
yana gaisheta ta ki amsawa tace "Aminu waye wancan aka bar sa xaune a kofar shiga
parlor? Waye wannan?" Yace "Ranki shi dade baƙon Alhaji ne wanda Habibu ya kawo
jiya, shine sabon...." Ta gwalo ido ta dakatar da shi da sauri tace "Haba Aminu,
Haba Aminu, yanxu kai rashin hankalin naka ya kai haka, a tunaninka ya kamata a bar
sa yaje har can ya jira Abbanmu, privacy din mu ne can din fa? ga dai kujeru a
compound amma har sai yaje balcony kamar xai shiga parlor, a ina aka ta6a haka?"
Aminu yayi kasa da murya yace "Wannan gaskiya ne Hajiya, ayi hakuri anyi kuskure
kam, ayi hakuri" Tace "To tun wuri ka tafi kace ya dawo nan kusa da kai ya xauna ya
jira Abban" Aminu yace "Toh Hajiya" tabe baki tace "Ni dama tambayarka xanyi hope
jiya baku mance feeding din tsuntsaye na ba?" Ya washe baki yace "Haba dai Hajiya,
ai kullum safe rana da dare sai Saminu ya basu, yau ma da asuba ina kallo yaje ya
xuba masu" tace "Yauwa toh nagode, bari in je in duba su, shekaranjiya da jiya duk
bama nan ban gansu ba" Yace "Da yake sai dare ku ka dawo jiya din ma" Tace "Eh fa"
daga haka ta wuce ta xaga ta inda tsuntsayen suke a backyard din gidan wanda nan
dinma duk shuke shuke ne, ta fi minti bakwai tana kallon kyawawan tsadaddun birds
din nata ko wani breeds a cage dinsu daban, birds din iri hudu ne ko wanne me kyau
har kuma da Aku a ciki, ta tafi gun akun da aka yi Seperating da sauran tace "Hello
cutie" The bird was only chirping and flying around the little cage alamar he
appreciates seeing her, bayan wani lkci ta bar wajen xata koma cikin gida, tsaye
taga Abba a balcony bakon nasa kuma ya sauka daga saman kujera ya durkusa kasa yana
sauraren Abba, kallonta kawai Abba yake da mamaki yace "Nihad ke baxa ki islamiyyan
bane?" Tayi gathering courage tayi kasa da murya tace "Abba assignment nake typing
anjima xan yi submitting via...." Abba ya dakatar da ita yace "Why are u skipping
Islamiyya this days Nihad, last week ma na ga baki je ba ko, hakan ba dai dai bane
dear" Sunkuyar da kanta tayi bayan few seconds ta dago, kallon mutumin dake
kallonsu ita da Abba tayi, ta wani daure fuska wondering why he was looking at
them, tana tafiya a hankali ta shiga parlor ta kullo kofar, bayan minti shidda aka
sake bude kofar, har sannan Abba na tsaye speaking with the man, su uku ne duk
sanye da hijab din islamiyya har kasa, Abba ya kallesu, sai kuma yace "Ke xaki yi
driving din?" Tace "Eh Abba ga makullin" Amsa yayi ya mika ma mutumin dake durkushe
gabansa yace "Ka ajiyesu a makaranta, xan jira ka har ka dawo" Ya amsa da ladabi
yace "Toh Alhaji" shi ya fara sauka Balcony din, Autan Mumyn Nihad da ake kira da
Sudais yace "Abba is he our new driver" Abba yace "Yes he is sweetheart" Duk suka
yi ma Abbansu sallama suka sauka xuwa parking lot, sai da suka tsaya dai dai motar
xuwa makarantarsu sannan drivern ya nufi motar shi ma, bayan ya bude duk suka shiga
back seat, ya shiga ya tada motar yana warming, shi dai Abba na tsaye balcony har
sannan yana kallonsu, Drivern na warming motar yaji ance "Ina kwana" ya daga kai
yana kallonta ta madubi da mamaki, sai kuma yace "Ina kwana" Bayan wasu yan mintuna
ya ja motar suka bar gidan xuwa islamiyyan nasu with Fadil and Sudais directing
him. Parking yayi bakin gate din islamiyyan, Nihal ta bude motar ta sauka su Fadil
ma duk suka sauka, bayan ta kulle motar ta kallesa tace "Sai anjima" Yace "Sai
anjima Hajiya" Suka shiga makarantar, reverse yayi ya bar wajen har sannan bai
daina mamaki ba. Yana isa gidan bayan mai gadi ya bude masa gate ya shiga yayi
parking ya kashe motar ya sauka, gun mai gadin ya nufa ya xauna, Mai gadin yace
"Inji ka yi kumallo dai?" Driver yace "Aa" Mai gadin yace "Toh bari inyi ma mai
aikin gidan magana in amso maka" Daga haka ya nufi backyard din gidan xuwa kofar
kitchen dake baya, Drivern dai na xaune yana ta juya makullin motar hannunsa sai ga
mai gadin ya dawo da plate din dankali da kwai da kofin shayi, ya amsa yace "Nagode
sosai" slice din bread ne biyar a gefen irish din da kwai wanda aka matsa ketchup a
gefe shi ma, irish din ya fara ci yana dangwalawa da ketchup din, Mai gadi yace
"Amma xaka dinga tafiya ne da daddare ka dawo da safe ko gidan nan xaka tsaya?" ya
kallesa yace "A ina xan tsaya a nan din?" Mai gadi yace "Ka ji ka, Yo ai har Habibu
ya gama yayinsa a gidan nan kafin Alhaji ya bude masa shagon da ya bude masa na
tayoyi a gidan nan yake komai nasa, duk tare muke, ga can boyis kwata, su Saminu da
Shafi'u masu gyaran pulawa da sharan tsakar gida da Isiya me wanki da guga ai a nan
suke duk" ya dau cup din shayin ya kurba yace "Dakin babba ne?" Mai gadin yayi
dariya yace "Wai daki, to har parlor akwai a ginin, sannan dakuna uku ne ko wanne
da bandaki, kai har ma da kitchen a nan din" yace "To shikenan" Aminu mai gadi yace
"Kai ma kayi xamanka kawai a nan xa ka fi gane kan albashin naka, kaga babu xancen
kashe kudin abun hawa xuwa da tafiya sannan xa a ciyar da kai a nan ba sae ka siya
komai da neran ka ba, duk abinda yan gida suka ci a nan shi mu ma muke ci" Shi dai
bai ce komai ba ya gama cinye irish din tass sannan yace "Toh xan xauna nan din in
sha Allah, nagode da kulawa" Ganin ya ajiye plate din Aminu yace "Ya haka, naga
baka ci kwan ba? Yanxun nan fa ta soya maka" Ya girgiza kai yace "Bana so" Aminu ya
dau plate din yana kokarin cin kwan yace "Allah sarki, wasu haka suke basa cin kwai
sai suce yana masu karni, mu dai kam ko danyensa ne baxa mu ki ci sha ba, wa yaƙi
dadi" Sai da Aminu ya cinye kwan ya mike yace "Mu je ka ga Boyis kwatan" shi ma ya
tashi, yana biye da shi, suka tafi far end of the main building in which stood a
Beautiful Chalet, mai gadi ne ya fara shiga, shi ma ya cire takalminsa bakin kofar
shiga Chalet din kamar yanda mai gadin yayi sannan ya shiga ciki, ba laifi parlon
na da girma, sannan ga kujeru har ma da tv, kaya ne ko ta ina a parlon ga wani
tashi da parlon yake, everywhere looks very untidy, isiya ne tsaye parlon yana ta
faman guga a ironing board, Aminu yace "Ashe kana ta guga shi yasa baka fito ba,
ina Saminu?" Isiya dake ta kallon wanda Mai gadin ya shigo da yace "Suna can daki"
Aminu yace "To ga bako, kun samu karuwa a nan, shine ya maye madadin Habibu a gidan
nan yanxu" Mutumin ya gaida isiya, isiya ya amsa yana ci gaba da gugansa, Aminu na
kallonsa yace "Mu je ka xabi dakin da xaka xauna ko" Isiya yace "Ka dai san dakin
dake daga dama ni ne a ciki, na hagu kuma Saminu, wanda ke jikin na hagun Shafi'u
ne a ciki" Shi dai kallonsa kawai mutumin yake, Aminu dake kallon Isiya shi ma yace
"To ya xa ayi kenan" Saminu da Shafi'u ne suka fito daga dakunan su, Isiya yace
"Toh ai parlon ma na da girma sai kawai ya maida nan din wajen kwanansa ko" mutumin
ya gyada kai yace "Ohk to shikenan" Isiya yace "Yauwa" Aminu ya kalli su Saminu
yace "Sabon direban gidan ne shi ma kuma nan xai xauna, sunansa Ibrahim kun ga
sunan Alhaji ne...." Saminu yace "To sannun sa da xuwa" Tuni ya juya ya fita daga
parlon ya bar mai gadi, Aminu na ganin haka ya bi bayansa da sauri... Suna tafe mai
gadi yace "Amma kasan da nauyi mu dinga kiran sunan Alhaji gatsau, baka da wani
sunan ko inkiya da xa mu iya dinga kiranka da?" kallonsa yayi yace "Khalil
Mahaifiyata ke kirana" Aminu yace "Allah sarki, to ai mu ma sai mu ce khalil din,
suna me dadi kamar na larabawa wllh" Bayan sun koma mazaunin mai gadi sun zauna,
Mai gadin ya kallesa yace "Yanxu kawai kayayyakin ka xaka je gida ka debo, aikin
naka ma fa ba wani me wahala bane, kaga yan makaranta motar makaranta ce ke xuwa
daukansu da safe, Yan matan nan biyu kuma daya a zaria ma take karatu, dayar ce ke
karatu a nan, ita warce ke karatu a nan din sai ta kai karfe biyu ma bata tafi
makarantar ba, Alhaji kadai xaka ajiye karfe tara gun aikinsa, ban ki ba dae Nihad
don gantali gareta kamar ta ci kafar kare, kuma sae ta fake da makaranta, a takaice
dai kai Alhaji wajen aikinsa da safe shine ainahin aikinka sauran duk masu sauki
ne" Khalil da har ya gaji da surutun Aminu ya gyada masa kai kawai, for the next
30mins Aminu bai yi shiru ba, Khalil har ya daina tanka masa don ya ma yi nisa a
tunanin da yake, dai dai nan Alhaji ya fito, Mai gadi yayi kasa da murya yace "Da
alama yau baxai je motsa jikin ba kenan tunda har gashi sha daya ta yi" Sai kuma ya
mike, Khalil ma ya mike yana kallon Alhajin a bit surprised at who is standing next
to him, Khalil yayi kasa da murya yace "Yan makarantar har sun taso ne?" Mai gadi
ya kalli Khalil da sauri yace "Ka je yana maka magana ne" Khalill ya nufi Alhajin
da hanzari, Alhaji yace "Mu je xaka ajiye mu 3 streets away from this" Khalil yace
"Toh" Motar da yayi parking bayan ya ajiye yan makaranta ya nufa, Abba yace "Wancan
motar ba wannan ba" Khalil ya tafi gun motar da Abba ya nuna masa, Bayan sun fita
gidan Mai gadi ya kulle gate, driving Khalil yake a hankali, lkci lkci yake kallon
Nihad dake zaune bayan mota da Abbanta tana danna wayarta. Ganin Khalil a layin da
Alhajin yace ya ajiye su, Alhaji Ibrahim yayi mamaki sosai, don shi ya ma mance ba
Habibu bane ke jan sa, bai yi masa kwatancen inda xai kai su ba ya dai ce masa 3
streets.... Ganin yayi slow down Alhaji Ibrahim yace "Noo ci gaba da tafiya, gida
na uku xaka tsaya" Dai dai gidan Khalil yayi parking, Alhaji yace "Kayi horn kawai"
yana yin horn mai gadi ya leko ganin motar ya koma ya bude gate din da sauri,
Khalil ya shiga ciki ya samu waje yayi parking , Alhaji Ibrahim yace "Maa sha
Allah, kayi jirana har in fito" Khalil yace "To Alhaji" Nihad ta sauka ta daya side
din wayarta kare a kunnenta, Alhaji Ibrahim ya sauka ya nufi entrance din gidan, Ta
side mirror Khalil ke kallonta amma sai yaga kamar wannan fara ce ai, Nihad dake ta
xagaye da waya a kunnenta da sunan she is making call, whereas she is not kawai
bata son Abba yace su shiga ciki tare ne, tana ganin Abban nata ya shiga gidan ta
turo baki ta tafi can karkashin wani Thatch dake compound din wanda aim dinsa wajen
shan iska, xaunawa tayi a wajen. Khalil ya sauka daga cikin motar ya tafi gun mai
gadin gidan suka gaisa, Mai gadin na kallonsa yace "Ko kai ne madadin Habibu"
Khalil yace "Eh nine" Mai gadin yace "Maa sha Allah" Xaunawa khalil yayi yana bin
compound din da kallo, wanda shi ma yayi haduwan karshe, ya d'an juya ya kalli Side
din da Nihad take, she was so engrossed with what she is doing on her phone....

U can contact me directly via👇🏻

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

~~~~

Gaisuwa da fatan alkhairi xuwa ga manya manyan fans dina irinsu.. Fatima Arebia,
Aisha Abubakar, Maman Shukrah (Banatsapparel and more) Khadijah Dutse, mu'azatu😂,
infact da duk wani member na Khaleesats palace da ban ambato ba a nan ku sani ina
son ku har raina, ina yin ku, ina maku fatan alkhairi Allah ya dafa maku a duk
lamuranku, My respect to many of my fans da suka fara patronizing Nihad without
even waiting for the end of free pages, yawancin ku ba biyan littafin ku ka yi ba
kyauta ce kawai kuke min, kuma ina alfahari da ku, ina maku fatan alkhairi da
Zuri'a dayyiba. Allah ya bar xuminci, ya saka da Alkhairi ya karo maku yalwataccen
arxiki, na kuma sadaukar da page din nan gare ku.

Bayan minti talatin da biyar Nihad ta gaji da jiran Abbanta don har sannan bai fito
daga gidan ba, ga kiran da Husnah ke ta yi mata taki dagawa don bata son tace mata
bata gida tasan baxata jira ta ba, kallon agogon dake makale hannunta tayi ganin
sha biyu har da minti goma ta tashi daga kan kujerar da take ta nufi khalil, Babu
yabo babu fallasa tace "Hey xan koma gida kayi dropping dina yanxu" Sai da ya fara
kallon mai gadi dake gefensa kamar dai da mai gadin take, ta daure fuska tace
"Malam da kai fa nake?" Sai a sannan ya kalleta ya d'an kara kunnensa gaba yace
"Na'am" Rasa ma me zata ce masa tayi saboda bakin ciki, har sannan fuskarta a daure
tace "Ina ga dai kana da matsalar ji, dalla malam ka tashi ka maida ni gida" Yace
"Naga ai Alhajin bai fito ba" Tana masa wani kallo tace "Eh na fi ka sanin bai fito
ba" Yace "To kar ya fito ya tarar bana nan" Ta rike kugu cike da masifa tace "Sai
ka maida ni, idan ka maida ni xaka iya dawowa idan ka ga dama" Ya dauke kai yayi
shiru bai ce komai ba, shi dai mai gadi sai mazurai yake da ido babu damar ya kwaba
ma khalil, shi tsoronsa ma kada wnn ɗan abin ya sa ya rasa aikinsa, yana ga kamar
Khalil bai ta6a aiki gidan masu hannu da shuni bane shi yasa har ya tsaya suna ja
in ja da Hajiya karama banda haka ina shi ina biyeta, ai duk abinda tace haka xa
ayi, tsawar Nihad ne ya dawo da mai gadin reality don sai da ya tsorata, "Dalla
Malam kana bata min lkci, are you even okay, how dare u query my order? Ko dai kana
shaye shaye ne???" Khalil ya ɗan kalleta, sae kuma ya mike ya nufi motar, ta ja
wani dogon tsaki ta bi bayansa kamar xata tashi sama tana harararsa, duk sai taji
ranta yayi mugun baci, bayan mota ta bude ta shiga, tuni mai gadi har ya wangale
gate yana daga mata hannu alamar Allah ya tsare, Khalil yayi reverse ya fita daga
compound din, cikin mintuna kadan ya isa gida da ita, yana parking dai dai gate ta
ja tsaki ta bude motar ta fice without closing the door, da ido ya bi ta har ta
shiga gate din gidan, ya fi minti biyar tsaye da motar, daga bisanni ya sauka ya
kulle door din motar, sannan ya shiga yyi reverse ya bar layin ya koma can gidan da
Abba yake. Nihad na shiga gida bangaren Umma ta nufa, jefar da jakarta tayi saman
kujeran parlon tana kallon Umma tace "Umma wani irin driver ne wannan Abba yayi
employing, who even linked them? wllh yaron bai da kunya ko kadan Umma, kinga
abinda yayi min kuwa??" Umma ta ajiye kayan hannunta tana kallonta tace "Me yayi
maki?" Nihad tace "Wllh rashin kunya yayi min, ni babu wani wanda ya ta6a min haka
ma tun da nake, wai yaron ya maida ni gida yaki fa" Umma tace "Aa abu me sauki sae
ayi ma Abban naku magana ya sallamesa, halan d'an kauye ne?" Nihad tace "Toh ae
dama su ne masu wannan tsagerancin da rashin ta idon, wllh Umma wannan idan yayi
wata daya a gidan nan daina kai mu duk inda xa mu xae yi, Allah cewa xai dinga yi
baxae je ba kansa tsaye idan ma bai hada mana da zagi ba, gwara kawai Abba ya dawo
ya sallamesa a samo wani dama ni bai min ba from the start, irinsu ne idan an shigo
da su inuwa su maida mutum rana, wai kinga me yayi min ne, jayayya fa muka tsaya
muna yi da shi" Daga haka ta fice daga parlon ta tafi dakinta don ta shirya xuwa
inda xa su hadu da Husnah, sae dae tana tsaka da shiryawa ta dinga kiran wayar
Husnah ta ji a kashe, lkci daya ranta ya baci, kaddai har tayi tafiyarta, ta zauna
gefen gado tana ta trying din layin amma ya ki connecting. Ana kiran sllhn Azahar
Abba ya fito daga gidan tare da wata tsohuwa, Khalil ya mike tsaye ganinsu, suna
karasowa inda yake Abba yace "Sabon drivern da na dauka kenan Hajiya, yau ya fara
aiki..." Tsohuwar ta kallesa daga sama har kasa tace "To ba laifi, kuma da ganinsa
xae fi Habibu kwazo duba da halittarsa, kawai dae sai mu yi fatan Allah ya sa ya fi
Habibu nutsuwa, don Habibu ni kadai nasan ɗan iska" Khalil yayi kasa da kai tare da
risinawa yace "Ina yini Hajiya" da fara'a tace "Lafiya lau, amma kai buzu ne koh?"
Ya murmusa yana girgiza kai, Tsohuwar tace "Toh a dai kula da dukiyar mutane ka ji,
kai ma sai kaga Allah ya kula da kai, baka ga motar da Habibu ya ajiye kafin ya
tafi ba, duk ta fita hayyacinta daga karshe konden konden aka siyar ma, su ma din
dai a walakance suka siya, ya sunanka?" Yace "Ibrahim" Buda baki tayi tace "Ikon
Allah, Kai ae kawai ka zama d'an gida abun ka daga yau ka ji, babu me raina ka ko
waye shi, kanka tsaye kar ka yarda da hakan, ae sunan Uban gidan naka kenan, kuma
ni na haifesa, Allah yayi maku albarka gaba daya" yana murmushi yace "Ameen" Abba
yace "Toh ki koma haka Hajiya, ni xan tafi" Tace "To Allah ya tsare, idan Habubakar
din ya dawo xan tattauna da shi" Yace "Ba laifi, sae anjima" daga haka ya nufi
motar, Khalil na biye da shi a baya. Yana ajiye Abba a gida, Abba yace "Ka tafi
islamiyya ka dauko yara nasan sun tashi ynxu" Khalil yace "Toh in sha Allah" hanyar
makarantar ya nufa, yana parking bakin gate sae ga Nihal, sannan Fadil da Sudais,
Amina ce karshen fitowa duk suka shige bayan motar, ita kuma ta xauna gaba, ta
madubi yake kallon Nihal, tace "Barka da rana" xai amsa Sudais da Fadil suka
gaishesa su ma, amsa masu yayi gaba daya sannan ya maida hankalinsa kan driving din
da yake. Nihad na tsaye bakin parlon Abba tana jiran ya amsa sallamar da tayi, yana
amsawa ta shiga, ta karasa parlon ta xauna saman kujera tace "Abba ina yini" yace
"Nihad me yasa kika ki shiga ku gaisa da inna da mutanen gidan?" Ta langwabar da
kai bata ce komai ba, glasses dinsa ya saka yana maida dubansa kan laptop din
gabansa, tace "Abba i came to report this new driver to you" Sake kallonta yayi
yace "What about him?" Tace "Abba kawai don nace ya maida ni gida i am press shine
mutumin nan ya ki, infact yi yayi kamar bai ji abinda nake cewa ba ya bar ni a
tsaye" Abba yace "Is that so?" Tace "Wllh Abba, and it's not as if i was rude to
him, kawai cewa nayi don Allah ka maida ni gida ina son xan koma, kawai sai yayi
min banxa, wllh Sagir mai gadi ne shaidata" Abba dai yayi shiru yana kallonta, bude
kofar parlon Abba aka yi sai ga su Sudais da Fadil sun shigo gaida Abban nasu ganin
motarsa a gida, Nihal ce ta shigo bayansu, Abba yace "Welcome Nihal, tell the
driver to wait me at the balcony...." Juyawa tayi ta fita, ba a wani dau lkci ba
sai ga ta ta dawo tace "Abba na gaya masa" Abba ya ajiye laptop din kafarsa ya mike
ya nufi kofa, Nihad taji wani dadi har cikin ranta dama babu abinda xata ce ma
Abbanta tana so da baya yi, mikewa tayi da sauri ta bi bayansa Nihal ta bi ta da
kallo, Abba na kallon Khalil bayan ya zauna saman daya daga kujerun dake wajen yace
"Ibrahim me yasa tace ka maido ta gida ka ki?" Khalil ya durkusa kasa yace
"Yallabai ban ki ba, ce mata nayi kar ka fito ka tarar bana nan kace inyi jiranka,
amma daga karshe na daukota na dawo da ita gidan" Nihad dake jikin kofa ta hade rai
jin abinda yace, Abba ya juya ya kalleta yace "Is that so?" Tace "To Abba sae fa da
ya ja min rai, maimakon ina gaya masa kawai ya tashi ya kai ni gida" Abba ya kalli
khalil yace "Je ka" Mikewa Khalil yayi yana kallonta yace "Kiyi hakuri, ban san
haƙan xai bata maki rai ba" Wani shegen kallo tayi masa ta juya tayi wucewarta
ciki. Bangaren Umma Nihad ta koma, Kamar xata fashe da kuka tace "Umma kin ga Abba
bai dauki ko wani action ba dai ko?" Umma tace "Sai yace masa me?" Tace "Ba abinda
yace masa, ni wllh sai dai duk abinda xai faru ya faru, da kaina xan dinga driving
kaina, gashi gobe ina da lectures karfe goma a haka xai kai ni schl din? Nooo i
will prefer to drive my sef" Umma tace "To idan kika tafi da motar da wanne xa a
dauko kannenki daga makaranta?" Tace "Ba ga motar yaya Farooq ba ko yaya Usman"
Bata jira me umma xata ce ba ta fita daga parlon xuwa kitchen, Aminu mai gadi ta
gani a windown kitchen din ta baya, mai aikinsu Hafsah tana xuba wani abinci a
plate, kallonta tayi tace "Abincin waye wannan?" Kafin tayi magana Aminu yace "Na
sabon dreba ne" Buda baki tayi tace "Shi ma din sai an dinga basa abincin a nan?
Waye yace haka?" Daga mai aiki har mai gadin suka yi shiru, tace "Ohh kawai ku kuka
tsara hakan sbda ku ke siyan kayan abinci?? To Abba bai ce haka ba, ni ma kuma
bance ba, saboda haka ajiye abincin nan dake hannunki baxa a kai ba, kai kuma Aminu
ka kama gabanka, ba shi da portion din abinci a gidan nan" juyawa Aminu yayi ya bar
wajen a sanyaye, Hafsah ta nemi plate ta rufe abincin ita ma a sanyaye, tsaki Nihad
tayi ta dau plate ta debi abinda xata deba ta cika nama sannan ta fita, tana fita
Nihal ta shigo kitchen din ita ma xata xuba abinci, ganin wanda Hafsah ta rufe tace
"Hafsah wannan wa ya ci ya rage?" Hafsah dake wanke wanke tace "Aa ban dade da
xubawa ba, Aminu ne ya xo amsar ma sabon dreba abinci Aunty Nihad ta hana" Nihal
tayi shiru da mamaki, can tace "To saboda me?" Hafsah tace "Nima ban sani ba wllh"
Nihal ta buɗe abincin tana kallo, can ta rufe ta kalli Hafsah tace "Ki kai masa"
Hafsah ta xaro ido tace "Ta fa hana Aunty Nihal" Nihal bata kuma cewa komai ba ta
dau spoon ta daura saman abincin ta fita daga kitchen, xaune ta tadda Khalil bakin
gate da mai gadin, mai gadin ya dauko masa wani guntun bread dake ta ajiye dakinsa
da pure water ya basa, kallonta suke gaba daya, shi dai Khalil yana kokarin gane
wacece, don kamarsu ta ɓaci da Nihad, sai da ta karaso ya gane ba Nihad bace don
Nihad ta fi ta haske har ma da tsayin hanci, amma both suna da dimple, ta mika masa
abincin tace "Ga abincin" Amsa yayi ya d'an yi murmushi wanda iyakarsa Lips yace
"Nagode" Juyawa tayi ta koma ciki, Mai gadi yace "Kaga er albarka, muna ganin
abubuwan al'ajabi fa a gidan nan, halaye iri iri in gaya maka, kaga Nihal din nan
da kake gani, ko kadan bata yi halin uwarta Hajiya ba, yarinya ce nutsatssiya ga
sanin ya kamata, uwa uba ga girmama d'an adam ko da kuwa almajiri ne, ba dai ka
ganta da kawaye ba kuma, uwarta kuwa ban ta6a ganin mace mara kirki mara mutunci
irinta ba duk nan hakuri muke da ita, gashi bata da aiki sai shige ma matan manya
manyan kasar nan, sannan
ita kadai ce bata yarda Habibu ya ja ta a mota ba, duk sanda xata fita sai ta bari
Alhaji ya fita sannan ta ja mota ita ma, bata dawowa kuma sai dab da magariba motar
nan kaga duk yayi butu butu da laka malam, tana dawowa kuma xata sa Habibu ya wanke
motar, ita kuma wancan Ja'irar da ta hanaka abinci ban ta6a ganin me kirki irin
uwarta ba, wato matar Alhaji ta biyu kenan, ga dai ita ce ta fari gun uwarta,
tsakaninsu da Nihal kwana daya tak, shi sa xaka gansu kamar yan biyu, sai kuma
Allah ya basu kama daya, komai nasu iri daya ne, to wllh Hajiya Mumy uwar Nihad
mace ce me mutunta mutum babu ruwan baiwar Allahn nan da duniya, sai gashi Allah ya
hadata da shaidaniyar yarinya, bata da aiki sai na bitar kawaye da rashin daraja
ɗan adam, to haka Allah yayi ikonsa a gidan nan, kyansa ace Nihad uwarta Umma, ita
kuma Nihal uwarta Mumy kaga dai dai kenan, amma Allah bai tsara hakan ba, ni fa da
rana daya aka haifesu sai muce canja su aka yi a asibiti, amma Nihal aka fara haifa
er baka da ita washegari aka haifi Nihad ita kuma fara tass, kaga ko ai ba ayi
canje ba" Khalil dake kallonsa yana sauraronsa attentively yace "Ita Umman yaranta
nawa?" Mai gadi ya gyara xama irin abun nema ya samu din nan, yana kirga su da
yatsa yace "Kaga Farouq shine ɗan ta na fari, a Habuja yake aiki, ya kan yi wata
biyu ma bai leko gidan nan ba, ba laifi yana da kirki da faram faram da jama'a, shi
ma kuma bai yo halin uwarsa ba gaskiya, sai Usman shi kuma kadaran kadahan, shi ba
a ma gane alkibilarsa, yana da kirki oho, bashi da kirki oho, atoh a haka na san sa
gaskiya, sai Kamila warce tayi aure shekara biyu kenan, wani shegen mai kudi Umman
tasan yanda tayi ta hadata da ta aura, sai Nihal sannan autarsu Amina, amma fa ta
fi ji da Nihal din don ita ma auta take kiranta, ita wannan Aminar ma mara kunya ce
gaskiya amma fa akwai son karatun addini, tana ajin karshe na sakandari, Nihal kuma
ABU Zaria take, ita Nihad makarantarta ance yayi Miliyan biyu xuwa uku, haka naji
su Saminu ke cewa, Maryam Abatcha naji suka ce sunan makarantar" Khalil yace "Toh
ita me xuwa Maryam Abatcha din su nawa ne gun Mamarta" Mai gadi yace "Ai ita ce ta
fari, sai kanninta biyu duk maza, Sudess da Fadil" Khalil bai ce komai ba ya bude
abincin hannunsa ya dau spoon ya fara ci. Nihad na gama cin abinci ta tafi bangaren
Mum dinta, shiryawa ta sameta tana yi hankalinta a d'an tashe, Nihad tace "Mumy me
ya faru?" Mumy tace "Yanxu Jamila ta kirani wai kanwar mijinta ta rasu" Nihad ta
dafe kirji tace "Kaddai Aunty Salma?" Mumy tace "Ita" Salati Nihad ta saki tace
"Allah sarki, Allah ya ji kanta, Mumy in sa Hijab mu je" Mumy tace "Ki sameni a
waje, drivern bai fita ba dai ko?" Nihad tace "Mumy kiyi driving din mana ko kuma
ni inyi" ko tanka ta Mumy bata yi ba ta dau handbag dinta ta fita, bangaren Umma ta
fara shiga ta sanar mata rasuwan, Umma tace "Allah Ubangiji ya ji kanta, in sha
Allah idan xaki koma gobe sai mu je muyi gaisuwa mu ma, Allah ya ji kan musulmi"
Mumy tace "Ameen, Allah ya kai mu goben" Part din Abba ta nufa, shi ma ta sanar
masa rasuwan daga haka ta fita compound, Mai gadi yayi kasa da murya yana ma Khalil
magana yace "Yauwa kaga Hajiya Mumyn ita ce uwar Nihad, ina ga fita xata yi" Muryar
Mumy suka ji tana cewa "Aminu Drivern ya fita ne?" Mai gadi ya mike da sauri yace
"Aa gashi nan Hajiya a kusa da ni" Khalil ya mike ya gaisheta da ladabi, Mumy ta
amsa cikin mutuntawa tana kallonsa daga sama har kasa, sai kuma tace "Shi ne
Drivern?" Khalil yace "Ni ne Hajiya" Mumy tace "Don Allah xaka ajiye ni nan Hotoro
ne idan ba damuwa" yace "Toh Hajiya" Makullin motarta ta mika masa, ya amsa da
ladabi Aminu ya nuna masa motar Mumy, gun motar ya nufa, Mumy ta daga wayarta dake
ringing ta kai kunne, Nihad ce ta fito ita ma sanye da Hijab har kasa, tana ganinsa
cikin motar Mumy ta wani daure fuska, bayan yayi warming motar ya karaso da motar
har inda Mumy take ya tsaya, Mumy ta bude bayan motar ta shiga, Nihad ma ta bude
baya xata shiga mumy tace "Baxa ki xauna a gaba ba" Without looking at her mum tace
"No, i will be more comfortable at the back" Kulle motar tayi ta bude handbag dinta
ta ciro tsadadden shade dinta ta saka, Khalil ya ja motar Mai gadi na daga masu
hannu har suka fita compound din ya kulle gate, cike da nutsuwa Khalil ke driving
din xuwa hotoro da Mumy tace daga Nasarawa GRA. Suna isa dai dai family house din
mijin kanwarta Jamila ta sa yayi parking, Mumy ta fara sauka daga motar tana
kallonsa tace "Ko xaka je ka dawo xuwa bayan magrib ka daukemu, kar a bar ka kayi
ta jira a nan" Yace "Aa babu komai xan jira daga can tsallaken in sha Allah" Jin
haka Mumy tace "Toh shkkn" Daga haka ta juya ta shiga gidan rasuwar Nihad na biye
da ita a baya. Nihad bata yarda ta xauna cikin jama'a da suka fara taruwa gidan ba
ana koke koke, ta nemi waje at the far end of the compound ta inda generator din
gidan yake ta xauna ita daya a wajen, Iphone dinta ta ciro a jakarta, taga missed
calls din Husnah da Naf, da sauri tayi dialing Number Husnah, yana fara ring Husnah
ta daga tace "Ina kika shiga ne babe" Nihad tace "Wllh mun fita tare da Abba ne,
and i left my phone at home, what's up kun fitan ne?" Husnah tace "Tun yaushe, ke
in gaya maki akwai labari wllh" Nihad tace "Yanxu dai kuna ina?" Husnah tace "Tahir
guest palace, kiyi kokari ki taho yanxu kar ayi ba ke" Nihad tace "Husnah Hijab fa
ne a jikina, mun xo wani gaisuwa da Mumy a hotoro" Naf ta amshe wayar don a
handsfree Husnah ta sa, tace "Haba dai minti nawa kin shiga boutique Nihad" Nihad
tace "Toh shkkn bari in amshi makullin motar Mumy a hannun driver in taho kawai,
nasan before magrib xata koma gida kafin nan na dawo" Naf tace "Shkkn xa mu jira ki
a Tahir din be fast pls" Katse wayar Nihad tayi tana bin compound din da ido trying
to figure out where her mum is, har ta kare xaga tsakar gidan da idanuwanta bata ga
mumy ba alamar dai ta shiga cikin gidan, tashi tayi da sauri ta nufi gate ta bude
ta fita, nan ma ta dinga waige waigen inda xata hango drivern, tun da ta fito ya
ganta, don yana xaune daga tsallaken bakin titi wajen mai siyar da Fruits, hada ido
suka yi ta tsallaka da sauri ta nufesa babu yabo babu fallasa tace "Hey ka bani
makullin mota xan mika sako in dawo yanxu" Kallon me siyar da fruits din yayi kamar
dai da shi take, nan da nan Nihad ta harxuka cikin tsawa tace "Malam da kai nake fa
kake kallon wani" Ya kalleta sai kuma ya kara kunnensa gaba yace "Na'am?" Nihad was
soo mad at him, xuciyarta ya dinga tafarfasa ta rasa abun ce masa, shi ma kuma bai
kuma cewa komai ba sae ma dauke kansa da yayi, ruwan da ta gani cikin roba gun me
siyar da fruits din ta fixgo a fusace ta juye masa gaba daya tun daga saman kansa,
duk mutanen dake wajen suka kame a inda suke baki bude suna kallonta da mamaki,
Tana huci cikin bacin rai tace "Kai din banzaaa kana driver din gidanmu har xan
dinga maka magana kana mayar ni mahaukaciya, who do u think u are?? Waye kai??"

To gain access to the book, contact me directly via👇🏻

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD* 💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

~~~~~

Tun da Nihad ta kwara masa ruwan bai dago kansa da ya sunkuyar ba, lkci daya
kamanninsa suka sauya, sae kuma dai ya daga kai ya kalleta, Tana hararansa tace "To
wllh kaji ka sani, ka rasa aikinka a karkashin mu daga wannan moment din, yau ba
sai gobe ba xan sa Abbana ya dau wani sabon driver din ya sallameka, baka yi
deserving aiki a gidanmu ba..." Mai fruit din na girgiza kai rai bace yace "Amma
baki da mutunci, baki da kirki, baki san darajan da Allah yayi ma d'an Adam ba,
kuma uwa uba baki da tarbiya wllh..." Tayi masa wani matsiyacin kallo tace "Kai
kuma wa ya sako da kai Malam? Kai a wa xaka sako min bakinka cikin lamarina? Ina
ruwanka? Ko xaka tilasta ni in san darajan d'an Adam din ne??" Wani tsaki ta ja
tana harararsa, Wani mutumi a wajen ya karbe a fusace yace "Xa ki samu dai dai dake
a duniya wllh, ke yanxu irin tarbiyar da aka maki a gidanku kenan? Tir kuwa da
tarbiyan gidan nan naku, tir da tarbiyan da iyayenki suka maki, idan haka arxikin
ke sa mutane a hanyar halaka Allah ya hanamu..." Nan kowa na wajen yayi mata caaa,
ko wanne na gasa mata magana son ransa har da masu xaginta, abun da tayi ya basu
mamaki sosai ya kuma ta6a su, barin yanda suka ga khalil yayi shiru yaki ce mata
komai, har da masu ce mata arxikin ma sai sun nemesa sun rasa, da surutunsu ya
isheta ta ja dogon tsaki tace "Duk ku ji da abinda ya dame ku malamai, bani da ikon
hukunta driver din gidanmu aka ce maku, ina ruwanku da abinda na masa banda sa ido
irin na mutane" Tana fadin haka ta juya, sai ta kara jin ranta ya wani baci, yanxu
ya xata yi da xuwa wajensu Husnah, kwata kwata bata son hawa adaidaita, duk k'uran
duniya ya kare ma mutum, kuma ma ai ba girmanta bane taje Tahir guest palace a
adaidaita Sahu, bata sake bi ta kan mutanen wajen ba ta tsallaka titi abun ta, bin
ta da kallo kawai Khalil ke yi, mutanen wajen sai hakuri suke basa, wani dattijo
dake tsaye shi ma wajen a kan idonsa aka yi komai ya dafa khalil cike da jimami
yace "Kayi hakuri yaro, rayuwa ce, amma bari in baka shawara wannan aiki ba shine
xai kai ka aljanna ba balle ka ji shakkun barinsa, ka ajiye masu makullinsu, da dai
wannan axababben walakancin gwara ko dako ne kayi ka ci abinci, balle siffarka bai
yi kama da ta rago ba, ga ka namiji har namiji, ka nemi wata sana'ar sai Allah ya
dubeka, ni ko duk arxikin duniyar nan xa a tattara min amma a hada min da walakanci
to wllh na hakura da arxikin gwara inyi ta xama da talauci na, balle irin wannan
walakanci da cin fuskar da yarinyar da aƙalla xaka bata shekaru sha uku ko sha hudu
tayi maka a kan titi a bainar nasi babu kunya babu tsoron Allah, sannan babu ladama
a tattare da ita, aa gaskiya ka sake duba lamarin nan dai, Allah Ubangiji ya saka
maka wannan cin xarafi da cin mutuncin da tayi maka" Wani matashi ne da gidansu ke
nan bakin titin ya fito da wata jallabiyarsa yana kallon khalil yace "Ga wannan mu
shiga wancan shagon sai ka canxa, Allah ya saka maka abinda tayi maka" Mikewa
Khalil yayi ya amshi rigar yana kallon mutumin yace "Nagode sosai" shagon da ya
gwada masa ya nufa, duk mutanen wajen suka bi sa da kallo cike da tausayi barin ma
da suka ga ya ki cewa komai, ya shiga shagon, me shagon ya basa waje ya canxa
kayansa, wayarsa dake aljihunsa ya fara cirowa ya dinga jujjuya wayar kafin ya
ajiye gently a saman bench, canxa kayan yayi, me shagon ya taho masa da babban leda
don ya linke tasa kayan ya sa a ciki, amsa yayi ya masa godiya sannan ya linke ya
saka a ledar yana rike da ledar ya fito shagon, mai shagon ya kalli wayarsa da ya
bari kan bench, ya d'an bude ido yana sake kallon wayar sannan ya kalli khalil da
har ya wuce, da sauri yace "Malam ka bar wayarka" Dawowa Khalil yayi da sauri ya
dau wayar, ya zira a aljihun jallabiyar, yana ɗan murmushi yace "Nagode kwarai"
daga haka ya fita me shagon ya bi sa da kallo kamar me naxari. Mumy ce tsaye bakin
gate ta dalilin kiranta da aka yi ganin Nihad can tsallake ga jama'a a tsattsaye
sun taru an sa ta a tsakiya, Mumy na kallon Nihad tace "Lafiya Nihad, me ke
faruwa?" Nihad ta rungume hannunta tace "Mumy ko ba wancan driver din bane, wllh
bashi da kunya ko kadan" Mumy tace "Me yayi maki?" Nihad tace "Wai fa Sajida ce
tace min tana anguwan nan, dama akwai wani textbook da nake son amsa a wajenta,
shine nace ya d'an ajiye ni, can gaba ne ba nisa, shine fa yake gaya min maganar
banxa, shi wai baxai je ba" Mumy tace "Sai aka yi yaya?" Nihad na yatsina fuska
tace "Shikenan, su kuma wa encan bansan me yasa suka taru haka ba" Mumy tace "Ina
drivern?" Nihad ta kalli tsallaken titin ta ga ya fito wani shigo da jallabiya,
Kafin ta ce komai Mumy tace "Mu je wajen nasa" Da sauri Nihad tace "Aa Mumy kyalesa
kawai, ni ai ban biyesa ba, haka yayi min daxu ma a gidan Baffa, aa kawai dai ki
bar sa" Mumy tace "Tsallaka mu je nace, bana son surutu" Nihad tayi shiru ganin
Mumy ta tsallaka ta bi bayanta, amma gaba daya she isn't comfortable, Mumy ta nufi
driver, yana ganinta yace "Hajiya har kin fito?" Tace "Aa ya sunanka?" Yace
"Ibrahim" Tace "Ohk, ya ku ka yi da Nihad?" Gaba daya mutanen wajen kallonsu suke,
Nihad dai na tsaye ta ki karasowa ta wani sha kunu, Mumy ta kalleta tace "To karaso
mana Nihad" tana tafiya a hankali ta karasa inda suke tsaye da Umma ce baxa ta ji
wani shakku ba xata biyo amma Mumy bata da tabbas, Mumy na kallon khalil tace "Ina
jin ka" Nihad ta amshe tace "Na fa gaya maki abinda ya faru Mumy, nan nan wajen
Sajida xai ajiye ni in amso textbook shine yake min maganar banxa har sa zagina, ni
ko biyesa ban yi ba" Mai fruit dake tsaye shi ma ya saki salati yace "Wllh karya
take Hajiya, ba haka aka yi ba, ai ina nan a xaune, bokiti guda na ruwa ta dauka ta
kwara masa kawai ba laifin tsaye balle na xaune, baki ga ya canxa kaya ba, duk a
kan idonmu aka yi komai" Mumy bata bari me fruit ya rufe baki ba ta tsinka ma Nihad
mari, Nihad bata gama recover ba ta kuma sauke mata wani, wanda hakan ya ba mutane
da yawa dake wajen mamaki, dama ashe ana hukunta 'ya yan masu kudi, hakan ya kuma
mugun burgesu, fuska daure Mumy tace "Wuce ki basa hakuri" Nihad da tunda aka
haifeta tana jin ba a ta6a marinta ba ta dinga ganin dishi dishi, ta dafe kuncinta,
wani tsawa da Mumy tayi mata sai da ya dada hargitsa ta, Mumy tace "Tafi ki basa
hakuri nace kar 6allaki a nan" Bata san sanda ta nufesa ba ta tsaya a gabansa
hawaye cike idonta cikin rawan murya tace "Kayi hakuri" Shi dai kallon Mumy yayi
yace "Hajiya kiyi hakuri duk bai kai haka ba" Mumy ta bude handbag dinta fuska a
murtuke ta fiddo dubu biyu ta jefa mata nan kasa tace "Ki tsayar da Tricycle ki
kama hanyar gida yanxun nan, kuma ina nan biyo ki a baya, dama don kiyi displaying
bad altitude dinki kika biyo ni kenan, xan yi maganinki" Kuka kawai Nihad take tana
jin kamar ta kwanta nan kasa tayi ta birgima ko xata ji sanyi, ko damuwa da mutanen
dake kallonta wajen bata yi ba, Mumy na kallon khalil tace "Kayi hakuri don Allah
Ibrahim, ita kuma xa mu hadu a gida" Daga haka Mumy ta tsallaka ta koma cikin gidan
rasuwa. Nihad ta bude jakarta tana kuka sosai ta ciro wayarta tayi dialing number
Abba, yana fara ringing Abba ya daga ta kara rushewa da kuka me karfi tace "Abbaa"
Sai ta xama abar kallo a wajen, Abba yace "Subhanallah what happen Nihad?" Kin cewa
komai tayi banda kuka babu abinda take rera masa, Abba ya katse wayar ya kira Mumy,
tana dagawa yace "Where is Nihad?" Mumy tace "What about her?" Abba yace "Ta kirani
yanxu tana kuka, and she is not responding to my questions" Mumy tace "Ka rabu da
ita, ai muna tare, sai anjima" Daga haka Mumy ta katse wayar. Sai bayan magrib Mumy
ta dawo gida, Khalil yayi parking ya sauka daga motar, Mumy ma ta sauka, da ladabi
ya mika mata makullinta, ta amsa tace "Nagode, kuma kayi hakuri da abinda yarinyar
nan tayi maka ka ji" Ya d'an yi murmushi yace "Ba komai Hajiya, nagode" Juyawa tayi
ta shiga cikin gidan, shi kuma ya nufa gun mai gadi. Umma na jin shigowar motar
Mumy ta shigo main parlor, Tana tsaye tana jiranta har ta shigo, Umma tace "Kin
bani mamaki Maryam, yanxu a kan wani shegen driver xaki kama yarinya a titi cikin
mutane ki doka sbda rashin sanin ciwon kai?" Bata ba Mumy space din magana ba ta ci
gaba rai a bace, "Wallahi kin ban mamaki da gaske, ke a dole sai kin xama me kirki
me mutunci a idon duniya? yanxu menene amfanin abinda kika ma Nihad a bakin titi a
kan wani matsiyacin talaka ɗan iska can? To wllh in dai ba Ibrahim ne ubansa ba sai
ya bar gidan nan yau, aikinsa ya kare a gidan nan, idan yayi ma Nihad ya ci bulus
har kuma da tsaraban mari da duka da ya ja mata to wllh babu er da xai ma hakan a
gidan nan ya kwana kalau, ba a haifi Ubansa yace xai ma Nihal ko Amina haka ba, don
haka yau ba sai gobe ba xai kama gabansa, mu bama hulda da yan iska, sau biyu kenan
duk a yau ta kawo min kararsa, ashe d'an iska Habibu ya turo ma Alhaji ba a sani
ba, to kuwa xai kama gabansa yanxu yanxun nan, kwanansa daya dubi isa da mulki da
yake gwadawa ya yanmu?, nan gaba ai har Alhajin ma cewa xai yi baxai tuka a mota
ba" Mumy bata kuma tsayawa ta saurareta ba ta wuce part dinta. Mai gadi na kallon
Khalil bayan ya gama shanya kayan da Nihad ta xuba masa ruwa yace "Hakuri kawai
xaka yi, amma lallai yarinyar nan shaidaniya ce a siffar mutum..." shi dai khalil
bai ce komai ba, mai gadi yace "Ga can abinci da aka kawo mana, na debar maka naka
na ajiye" Khalil yace "Aa na koshi, yanxu wanka nake so xan yi" Mai gadi yace "To
mu je in raka ka bangarenku" A tare suka nufi boys quarters din bayan mai gadi ya
dauko wata er jakar kayan Khalil da ya bari a dakinsa tun xuwansa da safe, suna
shiga parlon banda warin kartin maza babu abinda yake, ko ina soo dirty and unkept,
ga saminu yayi bake bake kan 3 seater yana kallo ga plate din abinci da ya ajiye
saman kujeran, Isiya na one sitter yana shan rake da yake tarawa nan kasa gefensa,
Shafi'u kuma na 2 seater ga tasa plate din abincin ya gama ci ya bari saman kujera,
Mai gadi ya nufi Saminu yayi kasa da murya yace "Saminu ko xaka ɗan sam masa waje
ya dinga
kwana a dakinka, ka gansa bashi da matsala wllh..." Ko rufe baki Mai gadi bai yi
ba Saminu yayi saurin cewa "Aa nima dakin yayi min kadan" Mai gadi ya kalli Isiya
dake jin abinda ya ke cewa, kafin mai gadin yace masa komai yace "Toh wai ba falo
kace xai dinga kwana ba" Shafi'u yace "Shi dai na gani, Duka dakunan kaga ai babu
waje, wa ke son takura" Khalil ya amshi jakarsa dake hannun mai gadi, mai gadi yace
"Ko xa mu je can dakin nawa ka dinga kwana" Khalil yace "Aa kar ka damu, kayi
komawar ka bakin gate" Yana fadin haka ya nufi space da aka tanadar domin dinning
area a parlon, Kofar da ya gani ya bude ya ga kitchen ne, ya dinga kallon yanda
suka mayar da kitchen din kamar na mahaukata duk da ba girki suke ba, tsintsiyar da
ya gani wanda bai ga alamar ana amfani da shi ba ya dauka, ya hau share dinning
area din, mai gadi ya juya ya fita daga parlon da sauri jin kamar ana horn. Cikin
yan mintuna khalil ya gama gyara area din har da mopping, yana gamawa sai ga mai
gadi ya kawo masa wani yakunannen zanin gado, amsa yayi ya shimfida a saman tiles
din wajen, sannan ya bude window, ya shiga bandakin dake parlon, still yayi yana
bin bathroom din da kallo, ko public toilet is far far better and neater than this,
fita yayi ya koma gun mai gadi don ya amshi omo. Abba yayi shiru yana sauraron
Mumy, Mumy ta ci gaba tace "Kawai ita Hajiya duk wani abu na cin mutunci da cin
fuska shine dai dai a wajenta, ai wannan ba rayuwa me kyau bane, har take cewa ka
sallamesa, da yayi me? Ruwa fa ta dauka gun me kayan marmari ta watsa masa a jiki,
kawai dai ka haifi yaro baka haifi halinsa ba, haka ta sa Habibu a gaba daga baya
ta gaji ta saukar da kanta, mai aikin gidan nan ba dadin Nihad take ji ba, Nihal
kuma ba haka take ba, na rasa wannan baƙin hali irin na Nihad ni kam, ni dai ba
haka taga nake mu'amala da jama'a ba balle tace, kai kanka ba haka mu'amalar ka da
jama'a yake ba, to halin wa ta yo haka, idan ba shiga hakki ba wllh kar ka fara ce
ma bawan Allahn nan komai, a kan me xata ce sai ya bata makullin motata ta tafi
gantalinta da yamma sbda rashin kunya ma bata yi shakkar cewar motar tawa bace,
kuma naga ai ba ita ta basa makullin ba ni na basa, to a kan me xai bata..." Abba
dai yayi shiru bai ce komai ba, ganin ta gama fadin abinda xata fada yace "But that
doesn't warrant u to slap her publicly Maryam, why not ki bari idan kuka dawo gida
ki hukunta ta?" Mumy tace "Wato na goyi bayanta kenan Yallabai, ai yanda tayi
rashin kirkinta a bainar jama'a gwara nima na hukuntata a cikin jama'ar dai dai
kenan, ni fa i am not in support of walakanta d'an Adam Yallabai, kuma babu wani da
ya fi wani a wajen Allah sai wanda yafi tsoronsa, idan ma xaka share xancen nan ka
je ka huta to gwara ka share" Abba bai kuma cewa komai ba, Mumy tace "Can i excuse
my self?" Yace "Alright" ta mike tayi masa sai da safe sannan ta fita, Umma ta fito
daga bedroom din Abba don duk ta ji yanda suka yi da Mumy, tana ta6e baki tace "Yau
ni naga neman suna kiri kiri gun talakawa, ita a neman sunan ma ta rasa inda xata
dinga yi sai wajen talaka? Ai kamata yayi ta dinga kutsa kanta cikin manyan mutane
ana yi da ita, ta nan ne neman suna xai mata rana, amma ke kice duk abinda talaka
yayi dai dai ne, a dole sai kin burge?" Abba ya mike ya fita daga parlon, compound
ya fito, dai dai nan khalil ya fito daga dakin mai gadi ya amshi omo, ganin Abba ya
nufesa ya gaida shi da ladabi, Abba ya amsa yana kallonsa yace "Ibrahim, a dinga
hakuri da yaran nan don Allah, sannan duk sanda Nihad ta sameka da batun amsan
makullin mota kana da number ta ka kirani, idan wanda xaka bata ne sai ince ka
bata, don ba wai bata iya driving ba, tana driving to where ever she wants to, just
sbda security purpose ne bana barin suyi driving din da kansu, so kar kayi zaton
bata iya driving din bane, and u gat respect them all kamar yanda xaka yi
respecting dina ka ji" Khalil da kansa ke kasa a hankali yace "Toh in sha Allah
Alhaji" Abba yace "Sun baka daki a can boys quarters din ko? Don nasan akwai empty
room da Habibu ya bari" Khalil yace "Ehh an bani" Abba na kallon omon hannunsa yace
"Wanki xaka yi da omo?" Yace "Eh xan wanke bandaki ne" Abba yace "Ohk good, wannan
ai yayi kadan, no problem xa a kawo maka daga cikin gida yanxu" Yace "To nagode
Alhaji" daga haka Abba ya juya ya koma cikin gida, khalil ya koma can boys quarters
din. Abba na komawa part dinsa ya kalli Umma yace "Ki ba ko Sudais ne blanket with
some detergents ya kai boys quarters" Umma tace "A kai ma wa a can?" Abba yace
"Driver" Umma tace "Aa da dai kaje gun uwar dakinsa ta bada a kai masa, ni kam bani
da old blanket, kaji Alhaji da wani xance, shine yace ka basa blanket din?" mikewa
Abba yayi ya fita, ya tafi bangaren Mumy, tana daki ya sameta yace "Maryam blanket
xaki ba Sudais with some detergents ya kai ma driver din can" Mumy tace "Sudais ai
yayi bacci yallabai" Abba yace "To bani" Wani blanket dinta ta dauko, sannan ta dau
pack din omo da sabulu with toothpaste ta hada ta ba Abba, Abba ya amsa ya fita
dakin, a stairs ya hadu da Nihal xata dakinsu, tace "Abba where are u going with
the blanket" Yace "Boys quarters xa a kai ma drivern can" Nihal tace "Ohk, bari in
kai Abba" Abba yace "Good" Amsa tayi daga hannunsa don dama da Hijab a jikinta ta
juya ta koma downstairs ta nufi kofar fita main parlor, boys quarters din ta nufa,
tayi Knocking duk da kofar a bude take, isiya ne ya karaso ganinta ya gaisheta da
ladabi xai amshi blanket din yace "Wanki ne Hajiya?" Tace "Aa, ina sabon driver
yake?" Jin haka Khalil dake bandaki xai fara wankewa ya fito ya nufi kofar,
kallonta ya dinga yi don da farko ya xata Nihad ce, amma sai yaga ba itan bace don
wannan fuskarta bai rabo da murmushi, ya amshi abinda take mika masa, yace "Nagode
sosai" Juyawa tayi ta sauka chalet din, ya koma cikin parlon yana kallonsu Isiya
yace "Ku yi kokari ku bar barin kofar nan a bude sbda sauro" Da ido duk suka bi sa,
lkci daya suka kya6e baki, ya ajiye blanket din ganin omo, sabulun wanki da na
wanka sannan ga Toothpaste ya kwashe su gaba daya ya wuce bandakin, ya bata fiye da
minti talatin yana wankin bandakin don sae da omon yayi rabi, lkci daya bandakin ya
dawo hayyacinsa, wanka yyi ya fito, ya kulle bandakin da makulli sannan ya cire
makullin ya koma dinning area, ya shimfida babban bargon wanda laushinsa ba a cewa
komai, ya bude window dake wajen sannan ya kwanta ya rufe ido, bayan minti sha
biyar yaji ana magana, ya bude ido ya ga Saminu tsaye a kansa, shiru yayi yana
kallonsa, Saminu yace "Makullin bandaki da ka kulle xaka bada" Khalil yace "Ohk,
dama kuna amfani da bandakin kenan?" Saminu yace "Yo me xai hana" Khalil yace "Ohk,
shine ku ka bar shi yanda na samesa?" Bai jira Saminu yace komai ba, yace "Amma dai
kamar babu bandaki a dakunan naku iya wannan kadai ne ko?" Saminu yace "Akwai mana,
amma wannan din muke shiga gaba daya ai" Khalil ya ciro makullin da ya ajiye a
aljihun gaban rigarsa ya mayar aljihun wando sannan ya gyara kwanciyarsa ya rufe
ido, xuwa yanxu daga Isiya har Shafi'u na tsaye parlon suna kallonsa gaba daya,
Saminu yace "Toh wai kai gayen nan me kake nufi tukunna ma dai" Mikewa Khalil yayi
ya tsaya sai ga Saminu ɗan tsut a gabansa, Khalil na kallonsa da kyau ya tsaya dab
da shi yace "Baxan bada ba nake nufi" Shafi'u ya koma ya xauna haka ma Isiya suna
kikkifta ido, sui sui Saminu ya bar dinning area din shi ma yana gwaggwale ido.

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD* 💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

~~~~~~

Washegari Monday har karfe tara Nihad na ta kwance a dakinta, karfe tara da rabi
aka bude kofar dakin, ta juya ganin Umma ce ta shigo ta mike xaune a hankali, Umma
tace "Baxa ki makarantar bane Nihad, naga yau Monday" Nihad tace "Lectures din
karfe goma ne, Nihal ta tafi islamiyya?" Umma tace "Tun yaushe, ke dai kam na san
ba xa ki ba" Nihad bata ce komai ba, Umma ta juya ta fita, sauka tayi daga saman
gadon ta shiga bandaki, nan ma sai da ta bata kusan minti arba'in sannan ta fito,
shiryawa tayi cikin tsadadden bakar Abaya, wurin shirin ma ta 6ata kusan minti
talatin, banda kamshi babu abinda ke tashi a ko ina na jikinta, sosai Abayar ta
amshi farin fatarta kai kace balarabiya ce, ta dau karamin handbag ta sa flat shoe
sannan ta fito daga dakin bata kulle ba don Hafsah xata shiga tayi mata gyaran
dakin sannan ta wanke mata bandaki, tana tafiya kamar bata son tafiyar ta tafi part
din Mumy ta bude kofar parlon, xaune ta ganta parlon tana waya, ta cire takalminta
nan bakin kofa ta karasa ciki a hankali, ta xauna saman kujera fuskar nan nata babu
yabo babu fallasa, har Mumy ta gama wayar sannan ta gaisheta, Mumy ta amsa mata ita
ma a dakile without looking at her, mikewa tayi tace "Xan tafi makaranta" Mumy tace
"Allah ya tsare" fita tayi daga parlon ta wuce part din Umma, Umma tace "Ashe dai
za ki, toh Breakfast din fa?" Tace "Xan yi a makaranta" Umma tace "Toh Allah ya
tsare" Kamar xata yi kuka tace "Umma ni gaskiya baxan iya shiga mota daya da wannan
yaron ba" Umma tace "Toh yanxu ya xa ayi, idan na tafi na amsar maki makullin kin
san anjima xa a dauko yara a makaranta" A hankali Nihad tace "Toh pls Umma zaki
bani makullin motar ya Farooq" Umma ta rike ha6a tace "Farooq, to bari dai in dauko
maki" cike da farin ciki Nihad tace "Yauwa Umma, karfe hudu xan dawo in sha Allah
baxan wuce haka ba" Mikewa Umma tayi ta fita daga parlonta ta wuce dakin First son
dinta, makullin dake jikin kofar ta murda sannan ta bude ta shiga ciki ta dauko
makullin motarsa ta fito, farin ciki sosai Nihad tayi ta mashi makullin tana
murmushi tace "Umma nagode" Umma tace "Toh ki tafi a hankali dai, kar ki kwarzane
masa mota mu shiga uku" Nihad tace "A hankali xan tafi Umma" Daga haka tayi ma Umma
sallama ta fita daga parlon cike da murna, ta fitowa compound taga mai gadi xaune
tare da Khalil, lokaci daya ta wani murtuke fuska, ta nufi mai gadi tana juya
makullin hannunta tace "Hey Bude min gate xan fita" Tashi yayi da sauri ya tafi xai
bude gate din, ta nufi motar yayanta, ta gefen ido khalil ya bi ta da kallo, har ta
shiga motar, bayan ta gama warming tayi zoom off out of the compound duk don ta
tada k'uran interlock, Mai gadi ya daga mata hannu yace "Allah ya tsare Hajiya" ko
kallonsa bata yi ba balle ta tanka, ta ja motar tayi gaba, kulle gate din yayi ya
dawo yana kallon khalil yace "Hajiya ce xata bata motar Farooq da yake baya gari,
kuma ina tabbatar maka uwarta bata sani ba, dama Umman ke daure mata tayi ta abinda
ta ga dama a gidan nan ai, kai kam huta roro" Khalil yayi murmushi yace "Yanxu ina
xata haka?" Mai gadi ya xauna yace "Wai Makaranta mana, kasan jami'arta shegen
tsada ke garai" Khalil yace "Ita er uwarta fa?" Mai gadi yace "Baiwar Allah, ba
daxu ka ajiyeta a islamiyya ba, hutun makaranta ta dawo, amma kaga kullum sai taje
islamiyya abunta..." Khalil yace "Wacce makarantar take ita?" Mai gadi yace "Ba
nace maka a Zaria take, Ahmadu Bello" Khalil bai kuma cewa komai ba. Nihad na
driving tayi dialing number Husnah, Yana fara ringing Husnah ta daga, Nihad tace
"Kin shiga school ne?" Husnah tace "Me yasa kika kashe wayarki jiya bayan munyi
dake kina tahowa?" Nihad ta sauke ajiyar xuciya tace "It's a long story, but ya na
ji muryarki haka, are you okay?" Husnah tace "Partially" Nihad tace "Where are u at
now?" Husnah tace "Ni'ima guest palace" Nihad tace "Really? To bari in taho nan
kawai, nima I'm not even in the mood of attending lectures today" Husnah tace "Sai
kin xo" Katse wayar Nihad tayi ta dau hanyar Ni'ima guest palace din. Nihad na isa
tayi parking ta kirata, nan Husnah ta sanar mata room number dinta, Nihad ta sauka
motar ta shiga ciki, Knocking tayi kofar dakin, Naf ta bude, Nihad ta d'an buda ido
ganin Husnah a kwance ta lulluba, ta kalli Naf tace "Is she okay?" Naf tace "Shigo
in kulle kofa" Nihad ta shiga ta karasa gun Husnah, ta xauna gefen gadon tana kai
hannu jikinta tace "Ya dai Husnah?" Husnah ta mike xaune tana ta6e baki tace "Ashe
Yaks d'an iska ne duk bamu sani ba" Nihad ta ɗan bude ido tace "Me ya faru?" Husnah
tace "Kawai yaje ya sha kwayoyinsa jiya in gaya maki yayi assaulting dina" Nihad ta
xaro ido tace "Really?" Husnah tace "Wllh ke dai in gaya maki, ban da abunsa ai i
wouldn't have denied him" Nihad tace "Where was Nafee then?" Husnah tace "Ita suna
tare da saurayinta, kin san shi ma ya zo" Da mamaki Nihad tace "Yaks??" Husnah tace
"Ai kuwa baki ga yanda ya dinga tambayarki ba, nace kina hanya duk ya damu baki iso
ba, ke gwara ma da baki xo ba din, kilan rashin xuwanki ya sa haka ya faru," Nihad
tayi shiru, can tace "Tabdi, kuma a Tahir guest palace din?" Husnah tace "Wane
Tahir, ai ba a can muka yi birthday din ba, ke kinga haduwar birthday din nan kuwa
Nihad?? Gaskiya na jima ban ga birthday da yayi haduwar na Maska ba, it was light"
Nihad tace "Ni xancen yaks ne ya tsaya min a rai, Shi yasa fa kike ganin bana kula
clique dinsu, bana harka da maza marasu aji" Husnah tayi dariya tace "Ni kawai way
of approach dinsa ne ya kona min rai, amma what's there? norms ne ai, someone that
i have been crushing on from day one" Nihad tace "To karfe nawa ku ka bar wajen?"
Husnah tace "Kai dare yayi fa sosai, ke ni fa wllh gwara ma da Allah ya hanaki xuwa
nace maki, don da ban san ya xan yi da ke ba a wajen ga uban daren da muka yi, cabb
to wa ma xai saurareki, gaskiya birthday din nan yayi armashi, ai da naga daren
yayi sosai shine na fasa komawa hostel kawai muka kama daki a nan ni da Surayya,
ita Naf fa sai yau da safe ta xo nan ta same mu" Nihad ta kyabe baki ta ajiye
handbag dinta tace "I am jet hungry banyi breakfast ba, me suke siyarwa a nan?"
Husnah tace "Ke bamu dade da waya da Ayman ba xai taho mana da abinci yanxu, bari
in kirasa ince plate uku xai kawo, shi ma jiya ya dawo daga Egypt" Daga haka Husnah
ta kirasa ta sanar masa ya dado wani plate din, bayan ta ajiye wayar tana kallon
Nihad tace "Amma jiyan me ya hanaki xuwa don Allah?" Nihad ta sauke wani ajiyar
xuciya irin na takaici tace "Husnah in gaya maki wani sabon driver Abba ya dauka,
kin san ai ya bude ma Habibu Shago" Husnah ta gwalo ido tace "Don Allah, kina nufin
yanxu babu Habibu? Allah sarki, kai amma xaki yi kewan Habibu, sau da yawa fa da
shi kike hada baki, gashi duk inda kika ce ya kai ki kai tsaye yake kai ki, har ma
ya jira ki" Nihad ta marairaice tace "Ke dai bari, ai ni aka yi ma da Habibu ya bar
driving, sau nawa yake kai ni Tahir ko Bristol or prince hotel, kuma ya jirani
komin dadewar da xa mu yi, sau nawa xa mu fita in amshi mota a hannunsa shi ya tafi
harkar gabansa nima inyi tafiyata, sai na gama xan kirasa mu hadu a busstop mu koma
gida, Yawanci ba shi nake aika ya siyo min duk abinda nake bukata ba, ai har kuka
sai da nayi da naji Abba ya bude masa shago, Habibu ai mutum ne" Husnah tace "Amma
fa ya ci kudinki ba karya" Nihad tace "I wish Allah xai ta6a xuciyar Abba ya dawo
mana da Habibu kawai" Husnah tace "Toh shi sabon da aka dauka fa?" Nihad ta gyara
xama tace "Ai shi xan baki labari yanxu, wato wani tatattcen d'an iska, mara kunya
Abba ya dauko mana as driver Husnah, kinsan jiya a kansa sai da Mumy ta mareni har
sau biyu a titi cikin jama'a? Husnah as i am talking to u now i am boiling inside,
tun shekaranjiya nake cikin ɓacin rai da bakin cikin mutumin nan, daga fara aiki
shekaranjiya har ya raina ni baya girmama ni, ina masa magana sai yayi min banxa ko
kuma ya kalle wanda ke kusa da shi irin dai kamar ba da shi nake ba da na kusa da
shi nake, ko kuma ya kara min sheggun kunnuwansa gaba, irin dai na raini da
tantiranci, Husnah yayi mugun raina ni wllh, yanxu maganar da nake maki motar ya
Farooq Umma ta bani makulli na fito da shi, baxan juri xama a mota ni da shi yana
driving dina ba...." Tuni har hawaye ya cika idonta, Husnah dake ta sauraronta da
mugun mamaki ta gyara xama tace "What?? Shi ordinary driver din yake duk wannan
abinda kika lissafo min kuma kika kyalesa? Ta yaya kika basa wannan fuskar ya
rainaki daga fara aikinsa Nihad? Waye shi haka, kuma a ina Abba ya samo sa?? Wai ma
garin yaya kika yi creating room for this bullshit" Nihad na shessheka tace "Baxa
ki gane ba, wllh irin yan iskan nan ne yaron, cikin ruwan sanyi yake raininsa da
rashin mutunci, idan kin gansa ma xa kiyi xaton baya magana nan ko katon ɗan iska
ne, yanda fa kika san motarsa haka yake jin kansa daga fara aiki" Husnah ta rike
ha6a tace "Tabdi... to kuwa xa mu yi maganinsa, but what did Abba say about it? Ko
baki kai kararsa ba har yanxu?" Nihad tace "Babu wani action da Abba ya dauka tunda
Mumy ta zuzzuga sa, har Umma ma ta saka baki amma Abba yaki daukan kwakkwaran
action, the painful part of it is that Mumy supporting dinsa take kamar ta ta6a
saninsa, kinsan yanda take abubuwanta dai, to wllh a kansa ta gaggaura min mari
jiya a tsakiyar Hotoro dalilin da yasa na fasa xuwa Tahir palace kenan, to wannan
ne har xan dinga basa kudi yana kai ni duk inda nake so ba tare da yayi casting
dina ba wataran? Ina ai baxai yiwu ba, bana harka da fitsararrun yara ni...."
Husnah tace "Calm down besty, shi karamin kwaro ne wllh, kuma xa mu yi maganinsa,
Clique dinmu kadai mun ishesa" Naf dake ta sauraronsu ta kyabe baki tace "Lallai
wnn ɗan iska ne number 1, daga wani kauyen aka samo maku shi halan? Shi a yan
kauyen ma shege ne fa" Nihad tace "How will i even know, wlh d'an rainin wayo ne na
karshe, gashi baya wani magana nake gaya maku, yanda kuka san kurma, cikin ruwan
sanyi yake rashin mutunci da raini, ga wani ji da kai, to kana aiki karkashin
mutane
kana driving ina wani ji da kai??" Kwankwasa kofar aka yi, Husnah tace "Ayman is
here..." Naf ta nufi kofar ta bude, wani matashi ya shigo dakin rike da takeaway
uku with many drinks da bottle water, Ya ajiye ledan yana kallon Nihad yace "Manyan
mata, ashe dai kina kasar nan Nihad?" Nihad tace "To an zuga Abbana ya ki kai ni UK
karatu ba dole a gan ni a kasar ba" Dariya yayi yace "Gaskiya ne, to ya kwana da
yawa, kinsan ku manya ne ba kowa ku ke replying ma chat ba both WhatsApp and IG"
Nihad tace "Not at all" Husnah ta mike ta dauko takeaway daya ta ajiye ma Nihad,
Ayman na kallon Husnah yace "I think bari in kama wani dakin kawai" Husnah tace
"Ohk then" Daga haka ya fita daga dakin, Naf ta ja tsaki tace "Sai shegen girman
kai, wato jira yake in fara masa magana ko" Husnah tace "Ke dai kowa sai kice yana
da girman kai bayan kema kina fama da naki, duk fa Salman ne ya hura maki kunne ki
daina kula kowa sai ki dinga fakewa da ana maki girman kai" Naf tace "Ni fita ma
xan xo in yi yanxu, amma xan dawo later" Husnah tace "Ina xa ki? Baxa ki ci abincin
ba?" Tace "Idan na dawo xan ci" Husnah tace "Kar fa ki ki dawowa Naf, saboda ke
naki gayyato Zully nan fa" Naf tace "Ke wllh xan dawo, wani Alhaji ne ke ta damuna
da kira ya shigo kano, to yayi min alkawarin waya dama, shine xan je" Husnah tace
"Ahh, to maza ki je, Allah ya sa mu ga latest iphone" Naf ta dau figigin gyalenta
tace "Toh Allah ya sa bari in je, Nihad idan na dawo xa mu tsara yanda xa ayi da
ɗan kauyen can shi kuma" Nihad tace "Toh sai kin dawo" Daga haka Naf ta fita daga
dakin, Husnah tace "Tabdi, yau ni naga karfin hali wai barawo da sallama, wannan
idan yayi wata daya a gidan ai sai dai kuma ya koma rayuwa cikin main building ya
bar boys quarters kawai" Nihad tace "Sai yanzu rashin barina in xauna a hostel da
Mumy tayi ke kara damuna sosai, kinsan da na hakura amma tun da aka kawo wannan
drivern damuwan ya dawo sabo" Husnah tace "To ko xaki kara gwada yi ma Abba
magana?" Nihad tace "Babu yanda Umma bata yi da shi ba, amma da yake Mumy da ya
farooq sun hure masa kunne ya ki amincewa, sae dae kawai yayi ta bani hakuri wai
there is time for everything" Husnah tace "Gaskiya in har ba sallaman driver din
nan aka yi ba xaki takura sosai, gashi Abba baxai baki mota ba ko" Nihad tace "Ba
fa ruwan Abba, Mumy ce matsalar gidan nan sae yaya Farooq, amma ae Umma tayi
kokarin ganin an bani motar kwanaki hakan bai yiwu ba" Husnah xata yi magana
wayarta ya fara ring, tana dubawa taga Ayman ne, dagawa tayi tace "Ya? Wani room
number kake?" Yace "102... Pls Nihad ta bani minti goma mu yi magana mana" Husnah
tace "Ohk over there?" Yace "Yeah" katse wayar tayi tana kallon Nihad tace "Ayman
wants to speak to you" Nihad tace "Ohk kin katse wayar kuma" Husnah tace "No, yana
room 102" Nihad tace "Ina ga ya sha kwaya, nice xan bi sa dakin??" Husnah tace
"C'mon, minti nawa xa kiyi ki fito, he said just 10 mins, behave like the big girl
u are mana" Nihad tace "Look, ya bar ni ma inji da damuwata i don't have that
strength to talk" Husnah tace "Don Allah kiyi hakuri ki je Nihad, minti goman nayi
ko bai gama magana ba ki fito kawai, ko albarkacina ya ci mana, yana ganin idan na
gaya maki xaki ji shi yasa ya biyo ta wajena, ki je ki dawo ki ji yanda xa mu yi da
wancan ɗan kauyen shi kuma" Nihad ta d'an kyabe baki, sai kuma ta mike tana gyara
veil din abayanta tace "Wani room ma kika ce?" Husnah ta gaya mata, daga nan ta
fita xuwa dakin. Kwankwasa kofar dakin tayi, sai gashi ya bude yana kallonta da
murmushi fuskarsa yace "Welcome Nihad" gefensa ta bi ta shiga dakin ta xauna saman
one seater dake dakin tana kallonsa har ya dawo ya xauna gefen gado sannan tace "I
am all ears" shiru yayi yana kallonta, ta langwabar da kai tace "Kayi shiru" Ɗan
murmushi yayi yace "Donno where to start from, kinsan kina da wani kwarjini na
daban Nihad" Ta kalli agogon dake wrist dinta, sannan tace "Then just start from d
end" Dariya yayi sannan yace "Ohk, a takaice kawai ina son ki bani dama let date"
Tace "Sorry but i don't double date Ayman" Yace "What's d big deal about double
dating Nihad?" Ta girgiza kai tace "Tsari na kenan, i have my boyfriend, and yana
sona kamar yanda nima nake son sa, so what's d need of dating else where?" Shiru
Ayman yayi, can ya mike ya koma kan kujerar da take ya xauna a hannun kujeran xai
kama hannunta ta fixge ta matsa gefe sannan tace "I am sorry Ayman, ina da
saurayina kuma duk kun sani" Yayi kasa da murya yace "Yeah i know, but pls Nihad...
even if it's once a while, i will always provide u with all ur needs, i am not
talking about petty needs" Da mamaki tace "What's that u are talking about?" The
way he was looking at her directly in the eyes yasa ta mike tana kallonsa da kyau
tace "Seems Husnah bata ta6a baka labarina ba ko?? Kawai kana ganin mu tare, duk
inda take xaka gan ni, Ohk get this Ayman, my obstinacy have limit, it hasn't
attain to this extent, sorry" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice
daga dakin ta kullo masa kofar. Tana komawa wajen Husnah, Husnah ta katse wayar da
take ta ajiye, Nihad tace "Baki ta6a gaya ma Ayman wacece ni ba ko?" Husnah bata ce
mata komai ba, Nihad ta nemi waje ta xauna, Husnah tace "Toh wai meye a ciki, kawai
kin bi kin makale ma Aliyu da definitely kinsan yana da yan mata iri iri shi ma, ni
wllh Aliyun nan haushi yake bani, ga shegen ji da kai kamar ɗan jinin sarauta, duk
abinda ya daura ki a kai shi kike yi, ga samari iri iri ko wanne na sonki amma
kince ke sai Aliyu, to Aliyun me" Nan da nan Nihad ta hade rai tana kallon Husnah,
can ta ja tsaki ta dau jakarta ta mike ta nufi kofa, Husnah tace "Tun da an ta6a
numfashin ki ba dole ki nufi kofa ba, to baxa ki tsaya ki ji yanda xa mu yi da
sabon drivern naku ba" Ko sauraronta Nihad bata yi ba har ta fice daga dakin,
Husnah ta ta6e baki tace "Kawai ki makale ma mutumin da yan mata ke rububi a kansa,
ki dauki son duniya ki dora masa, shi kuma yayi ta yin kamar bai san kina yi ba, da
ma yana baki lokacinsa yanda ya kamata ne abun baxai dameni ba" Husnah ta ja tsaki
ta jawo abincin gabanta ta bude.....

Contact me directly via👇🏻

07087865788 WhatsApp only.💖💖 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

~~~~~~~
Sai bayan la'asar Nihad ta iso gida, bayan ta fito daga wajen Husnah school kawai
ta wuce tayi attending lectures daya, mai gadi na bude gate ta shiga gidan ba tare
da ta saurari gaisheta da yake ba, tayi parking dai dai inda motar take ta kashe,
sauka tayi ta kulle motar tana kallon inda mai gadin ke xama ko xata ga Khalil, ai
ko yana xaune, ko da wasa bai kalli inda take ba, sai ma danna torchlight phone
dake hannunsa da yake with full concentration, nan da nan taji har ranta ya fara
baci, wai wa yayi ma wannan mutumin hanyar xuwa neman aiki a gidansu? har ta juya
xata wuce ciki sai kuma ta dawo, fuskarta daure ta nufesu, Mai gadi na ganin ta
doso inda suke ya mike daga xaunen da yake yana gaisheta, Babu yabo babu fallasa ta
amsa sannan tace "Aminu kuna canza ma tsuntsaye na abinci da ruwa kuwa??" Yace "Ehh
Hajiya ko daxu da kaina naje wajen na basu abinci da ruwan" Mai gadi ne ke mata
magana amma banda hararan khalil babu abinda take with hatred, how dare him baxai
gaisheta ba ma, wani dogon tsaki ta ja tace "Aminu ka sameni wajen tsuntsayen" Daga
haka ta wuce fuuu xuwa bayan gidan inda cage din birds din nata suke, Aminu ya
kalli khalil sannan ya bi bayanta da sauri, sai a snn Khalil ya daga kai ya bi su
da kallo, suna isa wajen tsuntsayen tace "Aminu in tambayeka mana" Yayi kasa da kai
yace "Toh Hajiya" Tace "Wai waye ya kawo wancan yaron gidan nan da sunan ya nemi
aikin driving?" Aminu yace "Hajiya Habibu ne ya kawosa ae" Da mamaki tace
"Habibu??? Habibu dai?" Aminu yace "Kwarai Hajiya" Juyawa tayi ta wuce ta bar sa
tsaye a wajen, gida ta shige, Aminu ya dawo bakin gate ya xauna yana kallon khalil
dake kallonsa shi ma, yayi kasa da murya yace "Wai tambaya take wa ya kawoka, to
ban san ko na kwabsa ba da nace Habibu, kasan fa Habibu mutuminta ne, har makudan
kudi tana basa, to duk inda xata kai tsaye yake kai ta har ya jirata, ya sha gaya
min maganganu amma yace kar in gaya ma kowa" Khalil yace "Wani magana?" Aminu ya
gyara xama yace "Ae otal daddaya ne a garin nan da wajen shakatawa irin ta manya
bai ta6a ajiyeta ba... Kai duk dai wani otal dake kano da ya amsa sunansa otal xuwa
take, wani lkcn tun safe sae dare xae je ya daukota, Khalil dake ta kallonsa da
mamaki yace "Hotel?? Me ke kai ta can?" Aminu yace "Ahaf ka ji ka da wani xance, me
ake zuwa yi otal, kuma kaf babu wanda ya sani a gidan nan sae Habibu sae kuma ni da
yake gaya ma, kai wani lkcn har Habuja tana xuwa kuma ta dawo a ranan, kasan
sha'anin jirgi, peee ta tafi peee ta dawo ita da kawayenta, babu wanda xae sani,
duk kowa tunaninsa tana makaranta, ita ce Kaduna, Ita ce legas, patacot.....kai
manyan garuruwan kasar nan dai da ka sani babu inda yarinyar nan bata xuwa, babu
abinda Habibu bai sani ba game da ita ai, ina ga shi yasa taji haushin barin dreba
da yayi" Khalil dai yayi shiru, Mai gadi yace "Atoh ni kallonta kawai nake kyar"
Khalil yace "Allah ya kiyaye" Mai gadi yace "Ameen dae" Nihad na shiga bedroom
dinta ta ajiye jakarta da mayafi ta dau wayarta tayi dialing number Habibu, yana
fara ringing ta nemi gefen gado ta xauna babu bata lkci ya daga hade da sallama
yace "Hajjaju Hajjaju ina yini" Tace "Lafiya lau Habibu" Yace "Ya kwana biyu kuma?"
Tace "Lafiya lau, Kana ji na?" Yace "Ina ji Hajiya" Tace "Wannan drivern da ka kawo
ma Abba, a ina ka san sa?" Habibu yace "Wani abu ya faru ne Hajiya?" Tace
"Tambayarka nake kana tambayata" Yace "Ehh Hajiya na san sa, d'an uwa na ne,
garinmu daya" Nihad tace "Bana son karya ta ina ya xama ɗan uwanka kana baƙi yana
fari??" Habibu yace "Ayya Hajiya ai in dai ka fito kauye daya da mutum ku ka shigo
maraya dan uwanka xaka kirasa, haka abun yake ki tambayi kowa ma" Ta kyabe baki
tace "Toh abu daya nake so da kai yanxu" Yace "Toh ina ji Hajiya" Tace "Ko nawa
kake so xan baka Habibu, in dai kudi ne kar ka ji komai" Shi dai yayi shiru, tace
"Kana ji na?" Yace "Ehh ina ji Hajiya" Tace "So nake ka kira Abba ka 6ata sa a
wajensa, ka kirkiro wani babban laifi kace yayi a garin naku ashe dalilin da ya sa
ya bar garin kenan, kai baka sani ba sai yanxu wani ɗan garin naku ke sanar maka"
Jin shirun da Habibu yayi tace "Kayi min shiru?" Da sauri yace "Ehh ina jin ki
Hajiya, ina sauraronki" Nihad tace "Good, yaushe xan saurareka?" Yace "Xuwa gobe in
sha Allah" Tace "Ohkk" daga haka ta katse wayar ta mike ta nufi window tana jin
wani relieve a ranta. Khalil na shigowa parlon chalet din da suke ciki dab da
magrib ya dinga bin parlon da kallo, tun safe da ya fito bai sake shigowa ba sai
yanxu, kuma kafin ya fita tass ya share ko ina, amma yanxu parlon wani sai yace
yara kanana sun shiga sun yi wasa da rana, beside that every where is so untidy,
nan kayan wanki, can kayan guga da Isiya ke yi, ga plate din abinci da cups a
tsakar parlon, kofar ma a wangale ake barinsa sauro su shiga yanda suka ga dama, Ya
dinga kallon Saminu, Isiya da Shafi'u da ke parlon, Kafin ya ce komai Shafi'u yace
"Ana ta kiran wayarka tun daxu fa" Kallon direction din da jakarsa yake yayi, sai
kuma ya kallesu yace "Amma nace ku yi hakuri ku bar barin kofa a bude sbda sauro,
tunda a parlor nake kwanciya ko" Isiya yace "Baka ga fankar ya lalace jiya ba, AC
dama tun da ka xo ai baya yi, shhkn sbda sauro sai mu ki bude kofa iska ya shigo"
Khalil ya dinga kallonsa, Saminu yace "Haba kai tun da ka zo sai kayi ta abu isa
isa da gadara don kaga muna maka shiru, mu kafin ka zo haka muka saba barin kofa
gaskiya" Khalil bai kuma ce masu komai ba ya nufi gun kayansa, ya dau jakarsa da
blanket, sai tsintsiya da parker da yake shara, hanyar dakuna uku dake chalet din
ya nufa, duk suka bi sa da ido har da waigawa, sai da ya bude ko wani daki sannan
daga karshe ya shiga na dama, ajiye jakarsa da blanket yayi, duk wani ghana must go
da jaka da ya gani a dakin sai da ya cilla sa waje, sannan ya cire dukunannen zanin
gadon dake kan gadon shi ma ya cilla masu waje, tas ya share dakin, sannan ya shiga
bandaki nan ma ya wanke, ya fito ya bude jakarsa da makulli ya dauko Harpic da hypo
ya koma bandakin, bayan ko ina ya dawo yanda yake son ganinsa, yayi wanka ya dauro
alwala ya fito, har xai kulle jakarsa sai ya tuna wayarsa ya dauko ya ga miss calls
din Habibu kusan 7, ya gama kare ma number kallo sannan ya ajiye wayar ya mike ya
fita daga dakin ya sa makulli, ya zira makullin a aljihun jallabiyan jikinsa, babu
yabo babu fallasa ya fito parlon ya nufi kofa duk suka bi sa da kallo babu wanda ya
iya cewa komai har ya fita. Bayan khalil yayi sallah yana xaune gefen mai gadi sai
ga Hafsah ta kawo ma mai gadin abinci, Mai gadi na kallonta yace "Shi ma ki kawo
masa tasa abincin nan kawai" Tace "Toh" sannan ta juya ta koma ciki, Khalil ya mike
yace "Xan dau wayata da ka sa a caji" Daga haka ya shiga dakin mai gadin ya dauko
wayar ya dawo ya xauna, yayi dialing number Habibu ya kai kunne, ba a dauki lokaci
ba Habibu ya daga yace "Ranka shi dade" Khalil ya gyara xama yace "Ya kake" Habibu
yace "Lafiya qlau wllh, ya aikin?" Khalil yace "Alhamdulillah" Habibu yace "To
madallah, kana ji na" Khalil yace "Ina ji" Habibu yace "Wani abun ya hadaku da
wannan yarinyar Nihad ne?" Khalil yace "Wani abu kamar me?" Habibu yace "Aa wai ko
sa'insa, ko dai makamancin hakan" Khalil yace "Ko daya" Habibu yace "Tohh, akwai fa
matsala" Khalil yace "Ta me kenan" nan Habibu ya sanar masa yanda suka yi da Nihad
daxu, Khalil yace "xan kiraka anjima" Daga haka ya katse wayar ya amshi abincin da
Hafsah ta kawo masa yace "Nagode" Nihad ta fito daga wanka kenan da daddare Mumy ta
shigo dakinta, sunkuyar da kai tayi tana goge jikinta tace "Ina yini" Mumy tace "Wa
ya baki makullin motar Farooq daxu?" Nihad ta kalleta da sauri, sai kuma ta
marairaice tace "Umma ce ta bani" Mumy tace "Ke yanxu Nihad duk wata hanyar da xaki
bi ki sani magana shi kike nema a rayuwarki ko?? Kwata kwata baki daukeni bakin
komai ba, duk abinda xai 6ata min rai shi kike rawan jiki kiyi, ki kama ki dau mota
ki kama hanyar makaranta without i and ur dad knowing ko Nihad" Nihad ta fara
shessheka tace "Mumy u don't want to be considering me, ni baxan iya shiga mota
daya da wancan sabon driver din ba shi yasa na amshi makullin motar ya Farooq gun
Umma" Mumy tace "A saboda meye baxa ki shiga mota daya da shi ba? Saboda shi ba
mutum bane? Kawai don bai baki makullin mota kin tafi gantali ba shine kika dau
karan tsana kika daura ma mutumi? He is only trying to protect his job don ai ba a
basa umarnin ya baki makulli ba ko" Kuka Nihad take sosai tace "Ko me nace Mumy
baki supporting dina, wllh yaron ba shi da kunya, ya raina ni kawai" Mumy tace
"Wato yaro ne ma?? Me yasa ita Nihal bata complain a kansa, ina ce shi ke dropping
dinta a islamiyya kullum, i even ask her ko taga yana da matsala tace min he is so
friendly, me yasa ke baxa ki sauke kanki yanda er uwarki ke yi ba" Nihad ta hade
rai tace "Wannan wawiyar me ta sani, ko bai mata magana ba ma ai washe masa hakora
xata yi ita tayi masa, baxa ma ta jira ya gaisheta ba ita xata fara gaishesa sbda
bata da hankali, pls mumy ki daina sa Nihal a cikin mutane" Mumy tace "Ki bi duniya
a sannu Nihad, babban matashi irin wannan sbda yana aiki karkashin Abbanki kice
baxa ki gaishesa ba sai dai ke ya gaisheki, me yasa baxa kiyi koyi da Nihal ba, me
yasa kika dau duniya da xafi haka" Nihad tace "Ni dai Mumy kiyi hakuri ki bani
makullin motar ki yau wllh ina da lectures karfe goma, Ni kuma baxan juri shiga
mota daya da shi ba" Mumy tace "Toh xa mu gani kuwa, kuma wllh kika sake xuwa gun
Hajiya kika amshi makulli sai na 6abbalaki a gidan nan" Nihad tace "Shikenan ni
baxan je makarantar ba kawai" Mumy tace "Ohk ni kike gaya ma wannan ko" Ta fashe da
kuka sosai tace "Toh Mumy ya kike son inyi, ni naga kamar ma kin fi son driver din
nan a kaina kawai" Mumy tace "Ehh na fi sonsa a kanki, kuma wllh kar ki kuskura ki
bari karfe goma yayi maki a gidan nan, sannan shi din xai kai ki, idan kuwa ba haka
ba xaki sha mamakin abinda xan maki, tunda ke kin dau girman kan duniya kin daura
ma kanki" Daga haka Mumy
ta fice daga dakin, Nihad tayi kukanta ma'ishi, taji ta tsani wannan bawan Allah,
ta tsanesa... Babu yanda ta iya haka ta tashi ta shirya, karfe goma saura minti
biyar ta fito compound, atamfa ce jikinta da wata mitsitsiyar mayafi da ta rataya a
wuya, hannunta rike da laptop dinta da jaka, fuskarta a daura ta nufi can inda ta
hango Driver din a xaune da Aminu, tana masa wani matsiyacin kallo, cike da isa da
gadara tace "Tasowa xaka yi kayi dropping dina a school idan ka ga dama, kai kuma
Aminu sai ka gaya masa makarantar tamu" Daga haka ta juya ta bar wajen ta tafi can
gun motar, murya can kasa kasa Aminu yace "Iko sai Allah" Mikewa Khalil yayi ya
nufi motar, Har xata bude back seat sae kuma ta fasa ta xaga ta bude seat din gaba
ta shiga, yanda ta hade rai sai kayi xaton ko dariya bata ta6a ba, shi ma ya shiga
motar, suna fita compound Aminu ya daga masu hannu, AC din motar Nihad ta kunna,
shi dai bai nuna yasan abinda tayi ba, suna hawa saman titi tayi connecting phone
dinta ta kure waka a motar, shi dai driving dinsa kawai yake, bayan kusan minti
talatin suna tafiya, ganin tafiyar tasa babu direction, ta wani juya ta kallesa
tace "Wai malam baka san inda xaka kai ni bane, ko Aminun bai gaya maka ba?"
Tafiyarsa kawai yake pretending he didn't know she is talking duk da yana jinta,
rage volume din wakan tayi can kasa, a fusace tace "Malam da kai nake" Ya kalleta
yace "Ohk magana kike, wakar ki ce ta hana inji" Ta yi masa wani kallo tace "Da
yake kai kurma ne ba dole waka ya hanaka ji, Aminu wai bai gaya maka inda xaka kai
ni ba?" Yayi slow down sannan yayi parking yace "Ina ta sauraren kice ga inda xaki
ne ai" Buda baki tayi tana kallonsa, Cikin daga murya tace "Aminu bai gaya maka
bane?" Yace "Toh ai ban ga Aminu cikin motar ba" She couldn't stop looking at him,
ita ba abin ta sauka ba, dakewa tayi tace "Saboda ba kai ke xuba fetur a motar ba
shi yasa kake ta yawo da ni a cikin garin kano ba tare da kasan inda xan je ba ko?"
Bai bata amsa ba, bata kuma ga alamar xai ce komai ba, wani dogon tsaki ta ja, ta
gyara xama tace "Dama harka da ɗan kauye ya gaji haka, idan kaga dama Maryam
Abatcha American University of Nigeria xaka kai ni" Without looking at her yace
"Ohk sai kin dinga min kwatance" Tace "Ban gane sai an maka kwatance ba, kai dama
babu inda ka sani a kanon ka xo ka nemi driving a gidanmu?" Yace "Ehh idan aka ci
gaba da nuna min wajajen xan sani ai" Tace "Amma wllh baka da amfani" Tsaki ta ja
tace "Ai sai ka juya kan motar idan dai ba garinku xa mu je ba" yace "In kince aje
can din ma ai sai aje" Bude baki tayi, sai kuma tace "Wallahi yaron nan ka raina
ni" Sai a sannan ya juya ya kalleta jin abinda tace, ta galla masa wani harara tace
"Malam kana bata min lkci xan je makaranta" Yace "Na xata garin namu xa mu" Daga
haka ya juya, rai a bace ta dinga gwada masa inda xai bi har suka iso makarantar,
ganin yayi parking a waje tace "Malam tada motar nan ka shigar dani ciki, ko duk
nan akwai wanda kaga anyi dropping a titi?" ya ci gaba da driving din slowly, dai
dai gate din makarantar ya tsaya ya sauke glass din motar, gaishesa security din
suka yi, ya amsa ya amshi pass ya shiga cikin makarantar yace "Ina?" Rudely tace
"Duk inda ka ga wancan jan motar ta bi kai ma ka bi, bani da lkcn yi maka wani
kwatancen" Bai ce mata komai ba, ya ci gaba da driving dinsa, Dai dai wajen da
motar ta tsaya ya samu waje yayi parking shi ma, ta ciro wayarta ta kira Husnah,
Husnah na dagawa tace "Kin shigo school?" Husnah tace "Ehh, ke kina ina?" Nihad
tace "Ku fito parking space ke da su Naf ku sameni yanzu yanzu, ki tabbatar har da
Zully xa ku taho" Husnah tace "Ke kika yi driving din yau ma?" Nihad tace "Ke dai
nace ku zo sharp sharp" daga haka ta katse wayar, ta zuge zip din jakarta ta fiddo
chewing gum ta jefa cikin bakinta tana tauna a hankali, Shi dae gabansa kawai yake
kallo, Bayan few seconds ya kashe motar ya zare makullin ya ajiye nan kusa da ita
without looking at her, ya bude motar xae sauka, da mamaki tana kallonsa tace
"Heyy, meye hakan kake yi? Waye xaka bar ma motar?" Still bai kalleta ba yace "Masu
shi" Daga haka ya kulle motar ya juya ya bar wajen, kasa cewa komai tayi sbda
mamaki, can ta sauka motar tana bin sa da ido baki bude, sae ga Husnah da Naf with
Zully da wata kawar Zully, Husnah ta karasa kusa da ita da sauri tace "Nihad what
happened, ya da bude baki haka" Nihad ta kalleta tace "I don't think this guy is
okay, ji tafiya yayi ya bar min motar fa Husnah" Husnah tace "Wa??" Nihad tace "New
driver din, kiranku fa nayi wai ku gansa, mu yi masa tijara..." Husnah tace "Wai
wancan me bakar rigar dake tafiya?" Kasa bata amsa Nihad tayi don da gaske mamaki
ne kawai ya cikata, Naf tace "Kawai haka nan ya kama ya tafi babu magana?" Nihad
tace "Not at all, ajiye min makulli yayi kusa da ni, nace wa xai bar ma motar, wai
masu shi.... kawai ya saka kai yayi tafiyarsa" Lkci daya Husnah da su Naf suka
kwashe da dariya har da kyakyatawa, Nihad ta hade rai, Husnah tayi dariya me isarta
sannan tace "Gaskiya wannan drivern dan duniya ne, ni ko na so in gansa wllh, ya
iya bada amsa dai dai da tambaya" Nihad ta hade rai tayi locking motar ta bar su
wajen a tsaye ta wuce aji, bin ta suka yi har sannan suna dariya, a lecture room
suka sameta, Husnah ta xauna kusa da ita tace "Anya ba ajiye aikin yayi gaba daya
ba" Nihad tace "Toh ni ya kamata ya ba makulli? Ko dama ni na basa makullin?"
Husnah ta fashe da dariya har da kife kai.

*Know the frnds of ur kids*

To gain Access to the book Nihad Contact me directly via👇🏻

07087865788

_Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices,
siyan daya ko sari_

Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake.....
*tested and trusted*

If interested contact
👇🏻
08052466875 via WhatsApp💖💖 *NIHAAD* 💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

8......

Throughout the day's lecture mood din Nihad was so dull, gaba daya she wasn't her
self, Husnah tace "Nihad mu je mu ci abinci ni dai na fara jin yunwa" A takaice
tace "I am not hungry" Husnah tace "C'mon babe, wai me ke faruwa ne? Gaba daya you
look dull today, don Allah ki gaya min me ke faruwa" Nihad ta sauke ajiyar xuciya
tace "Wai har ni mutumin nan xai ma walakanci ya ajiye ma makulli ya wuce Husnah?"
Husnah ta ja wani dogon tsaki tace "Ohh this? Wai wannan ne ya canxa maki mood
throughout? Lallai ma, To wai meye abun damuwa, kika sani ko barin aikin ma yayi?
Ni na fi tunani ya ajiye aikin ne, ba gashi da kika tambayesa wa ya bar ma motar
yace maki masu shi ba, probably yayi quitting ne" Nihad dake ta kallonta tace "Sai
ya rasa wanda xai ajiye ma aiki sai ni, me yasa bai kai ma Abba makullin ba, salon
ayi xaton ni ce na koresa? dama babu wanda ke considering dina a gidan banda Umma,
kawai so yake ya kara ja min bakin jini wajen Mumy" Husnah ta ja tsaki tace "Soo
what? Idan ma ajiye aikin yayi ai hakan ke kika fi so, abinda kike ta so ne ya faru
fa, karkari su gama surutunsu na kwana biyu su yi shiru, sannan a samo wani driver
din wanda xa ki juya yanda kike so, ba shikenan ba?" Nihad ta taɓe baki ta mike
tana harhada material din karatunta tace "Xan tafi gida" Husnah tace "Gida kuma? Da
wuri haka? Ke da nace maki xa mu je guest inn din su Bill yanxu, Kai Nihad yau da
kike da full control din mota an bar maki kiyi yanda kika ga dama shine xa ki wuce
gida da wuri, haba yan mata, ki bari wajajen six ki koma gidan mana" Nihad tace "Ni
kawai gida xan tafi duk raina a bace yake" Husnah ta juya ido tace "Toh ai shkkn,
bari in raka ki gun motar" Tare suka isa inda motar yake, Nihad ta ajiye jakanta da
kayan karatunta a bayan motar, sannan ta zaga ta shiga driver seat, Husnah na tsaye
har ta tada motar ta fara tafiya..... Nihad na isa gate din gidansu tayi horn, mai
gadi ya fito da sauri ya bude gate din, ta shiga gidan tayi parking, sannan ta
kashe motar ta sauka, kallon inda mai gadin yake tayi, ta ga shi kadai ne a wajen,
ta nufi cikin gida ba tare da ta dau material din makarantar ta dake bayan mota ba,
Mumy na xaune parlor da Nihal, sai Umma dake parlon ita ma duk suna kallo, ta gaida
su xata wuce, Mumy tace "Bani makullin da kika amsa wajen driver daxu" Tsayawa tayi
cike da mamaki tana kallon Mumy tace "Mumy wa yace ni na amsa makullin?" Umma tace
"Atoh, nima dai nace baxa kiyi haka ba, amma shi algungumin yace kin amshi makulli,
kuma sun yarda" Nihad tayi narai narai da ido tace "A yaushe na amshi makulli
wajensa? Wllh Umma sharri yayi min" Mumy tace "Ban tambayeki ba'asi ba, makulli
nace kawai ki bani, xa kuma mu hade a daki" Nihad ta fashe da kuka tace "Ni wllh
Allah ya isa wannan sharrin da yayi min, Allah ya isa tsakanina da shi munafuki
kawai, ajiye min makullin fa kawai...." Throw pillow Mumy ta dauke ta jefa mata
tace "Tafi ki bani waje, ga ki nan munafuka, wllh tunda haka kika xaba xa mu sa
kafar wando daya dake a gidan nan, kuma daga yau kika sake driving da kanki sai dai
ki canza wata uwar bani ba" Umma tace "Wai ya kike haka ne Maryam? Shikenan kai da
ɗan ka baxa ka ja sa jiki ba komai ya fada maka sai ka karyatasa baxa ka goyi
bayansa ba, me yasa kike fiffita bare akan naki? Wannan wace irin rayuwa ce? Ki bar
ta tayi bayani ma kin ki sbda rashin adalci" A fusace Mumy tace "Bana son
bayaninta, wani bayani xata min sai kace bani na haifeta ba, ko kuma ban san
halinta ba, wllh daga ni har ubanki babu me irin wannan mugun hali naki don ma
kiji, in har kince ke sai dai ki tuka kanki to wllh ki nemi wata uwar, kuma ai kin
saba cewa a baki makullin ba wnn ne karo na farko ba, don haka babu abinda xa ki
gaya min in yarda" Kuka kawai Nihad take xuciyarta na suya, ta ajiye makullin motar
nan saman kujera tace "Allah ya isa karyan da ya laka min, Allah ya isa tsakanina
da shi..." Tashi Mumy tayi, Nihad na ganin haka ta wuce sama da gudu, Mumy tace
"Tsaya dai ki min rashin kunya" Mikewa Umma tayi ta fita daga parlon, tana fita
compound ta kwalo ma Aminu kira ya taho da sauri, tace "Ina dreban nan yake?" Mai
gadi yace "Ya fita ya ɗan amso abu" Tace "Toh xai dawo ya sameni" Daga haka ta juya
fuu ta koma ciki. Nihad na shiga dakinta ta sa makulli ta dinga rusa kuka ta dau
wayarta tayi dialing number Abba, yana fara ringing ya daga yace "Hello Dear, ina
meeting i will get back to you" Ta fashe da kuka tace "Abba ni dai kawai a canza
driver din nan, bana son ganinsa kuma, i can't withstand the sight of him any
longer, kawai ni dai Abba ka sallamesa" Abba ya ɗan yi shiru sai kuma yace "Why did
u ask him to hand over the key to you da ya kai ki makaranta?" Nihad ta xaro ido
tace "Abba wllh sharri ya min, ta yaya xan ce ya bani makulli, wllh karya yake min
ni ban ce masa haka ba" Abba yace "Idan na dawo gida xa mu yi magana yanxu muna
meeting ne" Daga haka ya katse wayar, kuka ta dinga yi, nobody is getting her banda
Umma, wato dawowa gida yayi ya laka mata wannan uban sharrin gashi kowa ya yarda,
number Farooq tayi dialing, yana dagawa shi ma ta rushe masa da kuka yace
"Lafiya??" Cikin kuka tace "Yaya dama Abba ne ya dau wani sabon driver, yaya tun da
ya fara aiki yake laka min sharri iri iri, yana sa Mumy na kara tsanata, wai daxu
ya kai ni schl shine ya ajiye min makulli yayi wucewarsa, da ya dawo gida shine ya
je yace ma su Abba da Mumy ni nace ya ajiye min makullin" Farooq yace "To ai
halinki ne wannan, amsan makulli a wajen drivers kiyi driving da kanki, ke ko wani
driver sai kin samu matsala da shi, haka Habibu farkon da ya fara aiki a gidan nan,
why are u always having issues with everybody? Me yasa ita Nihal bata ce an mata
ba" Lkci daya ta hade rai, yace "Shi wannan din yaushe ya fara aiki har kika fara
samun matsala da shi Nihad?" Kin cewa komai tayi, yace "Ki min magana ko in kashe
wayata" Murya can ciki ciki tace "Sallah xan yi" Katse wayar yayi, ta jefar da nata
wayar, wato nobody is even supporting her, then xata dau action da kanta. Tana
kwance bayan tayi wanka tayi sallah wayarta ya fara ring, ta jawo wayar ganin
number da ke kiranta ta mike zaune ta daga tana wara ido tace "Shine baka ce min
xaka dawo ba bayan ko jiya mun yi magana" Yace "How are you?" Ta lumshe ido tace "I
am fine, ya hanya?" Yace "Alhamdulillah, yaushe za mu hadu? I will be leaving for
Abuja next tomorrow" Tace "Wai yau kake nufi xa mu hadu?" Yace "Toh shikenan tunda
ba yau ba" Da sauri tace "Noo ba haka nake nufi ba, i only asked, okay yanxu xan
shirya in fito in sha Allah" Yace "Where are we meeting?" Tace "U suggest" Yace
"How about Royal park..." A hankali tace "Kasan fa an canza mana driver" Yace "Ohh
really, when?" Tace "Kwanan nan" Yace "So u are not use to the new one ko?" Ta taɓe
baki tace "Aa wannan dan rainin hankali ne, i don't think we can eva get use to
each other" Yace "To yanxu ya za mu yi? Sbda ke na sauka kano fa" Tace "For now pls
mu hadu ko a wellcare ne, dama xan ɗan yi shopping..." Yace "Nahh, baxan iya fita
don kawai in je wellcare ba, kina nufin a tsaye xan ganki sannan mu rabu?" Tace "No
pls, after today i will plan where we will be meeting, ba kace next tomorrow xaka
koma ba" Yace "Karfe nawa xa ki wellcare din?" Tace "Kawai shiryawa xan yi yanxu"
Yace "Drivern ne zai kawo ki?" Tace "To ya xan yi shi din xai kawo ni, dama kuma
Abba ya bani kudin shopping kawai dai ban je nayi ba ne har ynxu" Yace "Okay idan
xa ki fito ki kirani" Tace "Tohm, i will call you" Daga haka ya katse wayar. Sosai
taji xuciyarta yayi sanyi duk wani bacin rai dake tare da ita ta nema ta rasa kawai
muryarsa da ta ji. Bayan ta shirya ta fito ta tafi bangaren Mumy, Tana tsaye a
parlon tace "Abba ya turo min kudin shopping, cream dina da sabulu sun kare, ina
son xan je in siya yanxu, sai driver yayi dropping dina a can" Mumy tace "Gobe
Nihal xata je shopping xata koma makaranta, sai ki bari ku tafi tare" Nihad da
gabanta ya fadi tace "Mumy bani da cream din da xan shafa ne fa, let me get even if
it's just the cream today idan ya so goben sai mu je tare, ina gama siyan cream din
xa mu dawo gida" Mumy tace "Allah ya tsare, sannan kuma ki yi masa abinda kika
saba, ki tabbatar tare xa ku dawo gidan nan da shi" Nihad dai bata ce komai ba ta
juya ta bude kofar dakin sannan ta fita. Tana fita compound taga bata ga drivern
ba, ta tambayi mai gadi yace "Yanxun nan ya bar nan, ya shiga can bangarensu.... "
Chalet din ta nufa, ta hangosa zaune saman matakalan dake wajen waya kare a
kunnensa, yana hangota ya katse wayar kuma ya ki kallonta, ta karaso babu yabo bbu
fallasa tace "Hey idan ka ga dama zaka ajiyeni a well care yanxu yanxu" tana fadin
haka ta juya ta bar wajen. Da ido ya bi ta, sai kuma ya mike ya ciro makullin a
aljihunsa ya bi bayanta, tana tsaye compound din ta kira Aliyu, ta sanar masa gata
nan xata fito, bayan ta gama wayar ta karasa ta shiga bayan motar, sai da suka hau
saman titi sannan yace "Kwatance xa ki yi" Ta hade rai tace "Kai ko ina sai kace
baka sani ba sai an maka kwatance, baka da Google map ne??" Yace "Ban da" Tsaki ta
ja, haka ta dinga gwada masa inda xa su bi har suka iso well care, parking yayi a
space da ake parking din, tayi dialing number Aliyu, yana dagawa tace "Are u
inside?" Waige waige ta fara yi jin abinda yace, tace "I am also outside, where did
u park?" Sauke glass tayi, lkci daya ta hangosa, murmushinsa me kyau ya sakar mata
yana kallonta, xata katse wayar yayi saurin cewa "Waitt" sai ta fasa kashewa tana
sauraronsa, yace "What if idan an ɗan basa wani abu mu ce ya jira mu a nan, mu je
eatry... i am jet hungry" Rasa abinda xata ce masa tayi, don ta ce ma Mumy baxata
dade ba, can ta saci kallon Khalil ta ga idonsa a kan Aliyu yake ko kiftawa bai yi,
duk da glass din a dage yake, kuma tinted ne ba me duhu can ba, a ranta tace wannan
ma yayi kama da wanda xai amshi abu idan an basa, bude motar tayi ta sauka ta nufi
inda Aliyu yake, shi dai Khalil bai daina kallon Aliyu ba kamar ya ga wani halitta
na daban, tana
karasawa gun motar Aliyu dake ta kallonta underneath his breathe yace "Waow, baby
kin kara kyau fa, tell me what is d secret" Tayi masa murmushi wanda har dimple
dinta sai da ya lotsa, sauke idonsa yayi kasa, can ya zaro dollar 100 a aljihunsa
yace "In bashi wannan ya jira mu a nan?" Tana kallon kudin tace "Toh kasan dai ba
wai mun saba da shi bane, snn bashi da kirki fa wllh" Aliyu yace "Kudi ne baki fara
basa ba shi yasa baku saba ba, yana ganin wannan yanxu xaki ga kun dawo kun dai
daita kun saba" Bude motar yayi ya fito, walking majestically ya nufi motar, Nihad
ta bi sa da kallo, Waige waige khalil ya fara yi da sauri, as if looking for an
alternative kafin Aliyu ya karaso gun motar, lokaci daya kawai yayi locking motar
kafin ya iso, Aliyu na karasowa ya bude motar yaji a kulle, kwankwasa glass din
motar yayi, Khalil ya kauda kai duk da Aliyun ba ganinsa yake ba, Sau biyu Aliyu na
kwankwasawa kafin ya daga kai ya kalli Nihad, ta buda masa hannu alamar i told u
dama, mamaki ne ya cika Aliyu ya dinga kallon motar, can ya sake Kwankwasa glass
din, tace "Dear just leave him ka bar wajen kawai, ba nace maka ɗan iskan yaro
bane" Aliyu da ransa ya gama baci yace "Who did he think he is, da driving din da
yake yi ake biyansa yake takama ko me? Waye shi yana matsayin just driver xai kulle
mota yana jin ana kwankwasawa ya ki budewa, kuma ba wai bai gan ni bane" Nihad tace
"Ai ban ta6a ganin mutum me karfin hali irin yaron nan ba" Aliyu yace "Look Nihad
idan kika shiga school gobe xa mu hadu, i can't stand here any longer, mood dina ya
baci seriously, ba a ta6a ci min fuska irin yau ba" Nihad tayi shiru tana kallonsa
duk jikinta yayi sanyi, don kana ganinsa kasan ransa yayi mugun baci da gaske,
tafiya ya fara yi kawai ya koma gun motarsa ya shiga ya tada yayi zoom off, da ido
khalil ya bi sa har ya hau saman titi, Nihad ta dinga kallon motar tana jin kamar
ta rushe da kuka ko xata ji sauki a ranta, mutumin da tayi wata da watanni bata
gani ba, shine wannan drivern xai 6ata ma rai har ya tafi?? Ta fi minti biyu tsaye
kawai kallon motar take with different thought running her mind ga wani kullutu da
ya tokareta a makogwaro sbda bakin ciki da takaici, a duk abubuwan da yake mata
bata jin akwai wanda ya mata ciwo ya ta6a har karshen xuciyarta irin wannan, she is
trying her best not to cry, don har idonta ya cicciko, kiris ya rage ta fashe da
kuka a wajen, Khalil dake ta kallon duk expression da reaction dinta ya shafa
kansa, sai kuma ya sauke both glasses yace "Naga kamar kin fasa siyayyan, kuma ga
hadari, ni kuma bana tuki cikin ruwa ko in baki makullin in yi tafiyata??" Wani
matsiyacin shegen kallo tayi masa, ta bude back seat ta shige motar ta kulle da
karfi tana kara danne kukan dake cin ta, tada motar yayi, yayi reverse ya dau
hanyar gida, har suka isa gida Nihad danna kukanta take, bayan yayi parking ta bude
motar ta sauka ta tafi gun driver seat ta tsaya tana nunasa da yatsa tana huci tace
"Sai kayi da ka sanin abinda kayi min yau wllh, kuma ni ce sanadin barin ka gidan
nan, banza mahaukaci kawai talaka" Kashe motar yayi ya sauka yana kallonta ya kara
mata kunne gaba yace "Kamar kina magana?" Da wani bakin ciki ya mamayeta bata san
sanda ta cakumo kwalarsa ba duk da uban tsayinsa tsaurin idonta bai sa taga hakan
ba, tana jijjigasa da duk karfinta hade da kunduma masa wani mummunan zagi, mai
gadi dake ganin komai ya karaso da gudu jikinsa na bari yana cewa "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un, Subhanallahi... " Khalil dai kallonta kawai yake baya ko
kiftawa, cikin nutsuwa yace "Cika ni" Ta buga wani uban tsawa tana dungure masa
goshi tace "An ki a cika ka din, kayi uban da xaka yi in ga, kai har ka isa kana
aiki ƙarƙashinmu kana matsayin Drivern gidanmu ka dinga kawo min raini? Ni ce ma
zaka raina? Kasan wa ka walakanta daxu?? To wllh ko kaff zuri'arka xa a siyar idan
har Aliyu ya daureka kudin da aka siyesu bai isa yayi bailing dinka ba" Nihal ta
fito cikin gida da kawarta xata mata rakiya ganin abinda ke faruwa ta karaso da
sauri xata ta janye Nihad tace "Nihad what's this u are doing, don't u have
manners? Meye wannan kike yi?" Nihad na huci ta bangajeta a fusace tace "Eh ban da
shi, sai ki ara min naki ke me shi, a kan matsiyacin nan xaki ce min bani da
manner, kin san abinda yayi min ne?" Nihal na kallon Khalil cike da damuwa tace
"Don Allah kayi hakuri" Yana warware rigarsa da Nihad ta cakuikuye yace "Ba
komai... fita xa ki yi ne?" Nihal dai duk jikinta yayi sanyi ta kasa cewa komai,
yace "Ko ba fita xa ki yi ba?" tace "Aa Kawata xan raka bakin titi" ya kalli
kawartata dake tsaye ita ma tana kallon abun mamaki, yace "Ohk to, ta hau sai na
ajiyeta a gida, xan jira ta a waje...." Yana fadin haka ya koma motar ya tada ya
bar wajen, mai gadi ya tafi da sauri ya bude gate, Nihad bata san sanda ta fashe
da kuka ba, da hanzari ta shige cikin gida tana kuka sosai. Bayan ta ci kukanta me
isarta ta dau wayarta ta kira Aliyu, har ya katse bai daga ba, ta kuma kiransa nan
ma no response, hawaye ne ya dinga sauka idonta, bayan kusan awa daya ta mike ta
gyara idonta ta fita, bangaren Mumy ta tafi sai taga kamar tana da bakuwa, hakan ya
sa ta bar wajen ta tafi gun Umma, Umma tace "Lafiya me ya sami idonki Nihad?" Cikin
rawan murya tace "Umma Aliyu ne ya dawo shine muka yi da shi xa mu hadu a wellcare,
bayan mun hadu sai ya sauko daga motarsa yace bari su gaisa da driver ai ko in gaya
maki mutumin nan yayi masa walakanci mafi muni, ya kulle motar ya kuma ki ya sauke
glass, banda Abba da ya ja mana ina Driver xai ma tsaya same place inda nake balle
Aliyu? Yasan waye uban Aliyu a kasar nan, kaskantar da kansa fa yayi ya tafi su
gaisa maimakon shi drivern ya sauko ya taho har inda yake ya gaishesa amma ya masa
wannan mugun walakancin" Umma dai sakin baki tayi tana kallon Nihad, can tayi kasa
da murya tace "Wai har yanzu kuna tare da Aliyun nan ne dama?" Nihad ta gyada mata
kai tana matsar kwalla, Umma tace "Ba kince min kun rabu ba kwanaki?" Nihad tace
"We came back together 1 month ago" Umma tace "Ke dai bakya ji Nihad nace ki fita
harkan yaron nan, ba mutunci ne da familynsu ba kin ki, nace ki rabu da shi in kina
son sama ma kanki mutunci kina son ki tsira da mutuncin ki, ina ke ina Aliyu banda
dai yaudaran kai Nihad? Kika san wasu irin yan mata yake hulda da? 'ya yan shugaban
kasa yake hulda da fa" Nihad taki cewa, Umma tace "Gaskiya kar ki sake kulasa ni
dai na gaya maki, yana son ki ne ko sau daya bai ta6a takowa ya xo gidanku ba? Sai
dai soyayya a titi da makaranta, kema kinsan yaudaran kanki kike don Aliyu ya fi
karfin ki, me ma xai kawosa gidan nan? waye ubanki a inda ubansa yake, inaa ai
nisan ma yayi yawa, balle ma duk yan iska ne yaran masu kudin nan wa enda idonsu ya
yage har kunne, banda lalata yara da bata masu rayuwa babu abinda suke" Nihad still
ta ki cewa komai, Umma tace "Kin min alkawarin xa ki rabu da shi kiyi blocking
dinsa kamar yanda kika yi blocking din Ahmad yanxu?" Nihad ta turo baki tace "Ni
dai ina sonsa Umma, shi ma kuma yana so na ai, da baya so na baxai dinga kirana ba
har yace mu hadu a wani waje, dama ce maki xanyi xan je gidansu Baffa ko da Mumy ta
tambayeni" Daga haka tayi ficewarta daga parlon Umma ta bi ta da ido ko kiftawa
babu, Nihad na sauka downstairs ta fito compound, fuskar nan nata a murtuke ta nufi
gate, mai gadi dai ya kauda kai da sauri don tare suke da Khalil, shi dai ya rasa
kan wannan abinda ke faruwa tsakaninta da Khalil, yana mugun ganin karfin halin
Khalil da baya nuna shakkarta kamar su, har ta fita gate ta dawo tana kallon mai
gadi fuskar nan nata babu rahama tace "Kai in ji dai kuna kula min da tsuntsaye na?
Don idan har wani abu ya samesu wllh kaf gidan nan duk sai kun raina kanku ban cire
kowa ba kuma" Da ladabi yace "Ko daxu sai da naje can da kaina Hajiya" Ficewa tayi
daga gate din bayan ta maka ma khalil da bai ma san tana yi ba harara, Mai gadi ya
kalli khalil yace "Sai fargaba nake kar tace xaka kai ta wani waje" Khalil yayi
murmushi yace "Meye a ciki, sai a kai ta ai..." Da yake babu wani nisa da kafa
Nihad ta bi ta cikin anguwanni har ta isa gidan yayan Abbanta, Hamid na xaune
compound tare da wani abokinsa, kallo daya tayi masu ta kara gaba abunta, Abokin
nasa yace "Wannan ba cousin din nan taka bace, naga ta wuce bata ce maka komai ba,
and kamar kuna good time da ita ai" Hamid yace "Noo, step sisters dinta ne muke
good time, wannan ai yar iska ce" Abokin yace "Shit but sun yi kama sosai, kamar
har ya wuce misali" Hamid yace "Toh wannan da kake gani ji take da girman kai da
rainin wayo, sannan runz girl ce..." Abokin ya wara ido yace "Waow dai dai mu
kenan, ka hadu mu to" Hamid ya masa wani shegen kallo yace "Ai da manyan mata ake
runz ba kwailaye ba, kwailar ma fitsararriya irin wannan" Tuni Nihad ta shige
gidan, direct part din Kakarta ta nufa, tana bude kofar dakin ta shiga, inna tace
"Aa, daga ina haka, Ibrahim din ya shigo ne" Nihad tace "Ni kadai ce" Inna tace "Aa
naga sai ya taso keyarki kike xuwa shi sa abun ya daure min kai, ina ce tare ku ke"
Nihad ta nemi waje ta xauna, Inna tace "Baki da lafiya ne?" Nihad ta fashe da kuka
kamar jira take tace "Inna wani sabon driver Abba ya dauka, yaron ba shi da kunya
ya raina ni inna, ba irin rashin mutuncin da baya min" Inna da ta saki baki tace
"Shi Dreban?" Nihad ta gyada mata kai tana goge hawayen idonta, Inna tace "Ko ba
wani gansameme ba yana tafiya gansan gansan?" Nihad tace "Shi" Inna tace "Toh ai
Ibrahim din ya kawo sa har nan ya gaisheni, amma ni na xata ɗan arxiki ne, don har
kasa ya duka ya gaida ni" Nihad tace "Wllh na munafurci ne...." Nan ta labarta ma
inna abinda ya faru kamar yanda ta gaya ma Umma, Inna tace "Ba lafiya, shi
dreban??"

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖
✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

9.....

Nihad na shesshekan kuka tace "Wllh shi inna, kawai an bar sa yana ta abinda ya ga
dama a gidan kamar gidan ubansa, duk ya gama rena ni, ko gaisuwa bata hadani da
shi" Inna tace "Duk ba wannan ba, yanxu kin kira Aliyun??" Nihad ta daura kanta
gefen gadon inna hawaye na sauka idonta tace "Bayan ya ki dagawa" Inna ta dauko
wayarta ta mika mata tace "Kirasa da nawa" Nihad tace "Ae idan ba shi da numberka
baxa ka iya samunsa ba, ya sa layinsa a Private" Inna tace "Wai ko ba dai Aliyu
ɗ'an wajen janaral Habubakar jikamshi ba?" A hankali Nihad tace "Shi..." Inna tace
"To wannan dreba duk yanda aka yi tsinanne ne, ko don nace masa ya saki jikinsa
yasa ya sake kamar gidan ubansa? to ai ni na xata yaron arxiki ne" Salati inna ta
saki tayi tagumi tace "Yau naga dreban jaraba, ashe duk ni na ja komai da nace ya
saki jikinsa, to a kira min Ibrahim din tun yamma bai yi ba ya sallamesa" Nihad ta
dau wayar inna da sauri ta fara neman number Abba tayi dialing, Inna ta bude baki
ta rike ha6a tace "To shi kuma Aliyun banda abunsa garin yaya xai ce sai yayi ma
dreba magana mutumin da ba ajinsa ba, ai abinda bai sani ba talakawan nan haka suke
da dacin rai kamar mutum ne ya doro masu talaucin, ina shi ina wani basamuden buzun
dreba can? To ko a almajiri dai baxa su yarda su ajiye wannan mutumi a gidansu ba
balle dreba, su da tun daga titin da ya yanka unguwarsu xaka fara ganin dirka
dirkan sojoji har da motocinsu...." Nihad ta turo baki tace "Abba bai daga ba" Inna
tace "Ina xai daga, ya tashi ya kawo wani kato gansameme kamar mutanen farko ya dau
mota ya basa, ni wllh ranan da na fara ganinsa sai da na tsure, sai fa ya daga
mutum ya nanasa da kasa sau biyar bai gaji ba, irinsu ai gadin dogon banki ya
kamata a basu ba wai motar mutane ba" Nihad dai tayi tagumi don abinda ya dameta
daban, ita yanxu ta ya xata fara shawo kan Aliyu, da yaya ma suka dawo soyayyar,
Inna tace "To ko kin san inda ya sauka ki rakani mu je in basa hakuri" Nihad ta
kalleta tace "Ji ki kuma, kawai don ki ja min raini?" Inna tace "Wani raini mutumi
na nema ya kubuce, wa ke ta wani raini Nihad, idan ma baxa ki shiga ba ni ki rakani
ki nuna min hanya in je in samesa" Nihad tace "Aa ke dai kawai duk yanda xa kiyi
kiyi Abba ya kori driver din nan kawai" Inna tace "Yo sai ma kin fada, abu har ya
kai yana korar ma jikokina samari" Hamid ne ya bude kofar dakin ya shiga yana
kallon Nihad yace "Ke don uwarki ni sa'anki ne xaki wuce ni da abokina baki
gaishemu ba" Nihad ta turo baki ta koma gefen Inna, Inna dai bata ce komai ba, Yace
"Mahaukaciya kawai, uban wa xaki dinga daga ma kai?" A fusace Nihad tace "Kina dai
gani babu abinda na masa ya xo ya fara xagina ko inna, ni fa shi yasa bana son xuwa
gidan nan wllh, kowa yaje yaji da mugun halinsa" Cikin xafin nama ya nufeta, Inna
ta mike ta wangale hannu tana tare Nihad tace "Dokeni to, Hamidu nace ka dokeni"
Huci yake yana kallonta, Inna tace "Ai dama ka saba dukan nawa yanxun ma ka duka,
ranan da ka biyo Bilkisu ai ni ka jibga ba ita ba" Nihad ko kallonsa bata yarda ta
sake yi ba, Yayi wani kwafa ya fice daga dakin, Inna ta kulle dakinta tace "Kinsan
korosa aka yi daga can kasar wajen wai wa'adinsa ya kare a can, to kuma sai kayi ta
hucewa kan ya yan mutane" Nihad bata san lkcn da ta kyalkyale da dariya ba, Inna
tace "Allah haka uban yace min, duk a booth din jirgi aka kwaso su aka dawo" Nihad
dai bata ce komai ba, Inna tace "Yanxu ko kin boye number ki baxai daga wayar ba?"
Nihad ta mike tace "Ni dai xan tafi inna dama anjima da daddare kice Hamid din ya
kawoki nan gidanmu ki samu Abba da kanki" Inna tace "Toh shkkn ma, kawai bari inje
in riskesa a gidan ba sai mun yi waya ba, idan ma ya kama ko shi sai ya kira Aliyun
ya basa hakuri" Bude baki Nihad tayi, can ta kyabe bakin tace "Ni dai sai kin zo"
Daga haka ta fita daga dakin, A bakin gate abokin Hamid ya tare ta da ya faki idon
Hamid ya biyota, yana fara magana ta dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu tana
yatsine fuska tace "Ina wasa da kai ne malam?" Daga haka ta ja tsaki tayi ficewarta
daga gate din, ya bi ta da kallo baki bude, dama Hamid ya gaya masa ya ki ji. Nihad
na komawa anguwansu ta yi ido hudu da Khalil dake xaune kan dakali a kofar gida
wayarsa na kare kunnensa, yana ganinta bai sake cewa komai ba a wayar da yake kuma
bai cire wayar a kunnensa ba, har ta isa dai dai inda yake, tayi masa wani harara
ta ja tsaki ta shige cikin gida tayi banging gate din. Abba na tsaye balcony bayan
magrib Khalil ya karaso da ladabi yana kallonsa yace "Gani Alhaji" Abba yace "Yauwa
pharmacy xan aikeka ka siyo min magani yanxu" Khalil yace "Toh, ya sunan maganin?"
Abba na duba wayarsa yace "Yanxu likitana ya turo min ta message bari dai in duba"
Abba na shiga message din har ya fara pronouncing sunan maganin kawai ya fasa kar
khalil yaje ya masa shirme, yace "Bari kawai xan rubuta maka a takarda kaje ka
siyo, idan ka siyo sai...." Abba ya dakata ganin mai gadi na bude gate, sai ga
motar Hamid ya shigo compound din, Abba yace "Je ka xan rubuta sunan maganin a kawo
maka yanxu" Yace "Toh Alhaji" daga haka ya nufi boys quarters, Inna ce ta sauka
daga motar ta nufo balcony, Abba dai na tsaye yana ta tunanin ko lafiya, Tana isowa
ganin yanayinta yace "Lafiya inna?" Tace "Ina fa lafiya, mu je parlor baxan iya
tsayuwa ba" Sai da ta fara shiga parlon Abba ya bi ta, kanta tsaye ta tafi parlonsa
duk yana biye da ita, ta nemi waje ta xauna shi ma ya xauna yace "Ina yini Inna?"
Tace "Ibrahim a ina ka samo wannan gansamemen dreban naka?" Abba yace "Wani abu ya
faru ne?" Tace "Meye baxai faru ba, ya kora ma Nihad saurayi, d'an wajen Janaral
Jikamshi, har yaron ya goge numberta yanxu haka da nake maka magana" Abba yayi
shirui yana kallonta as if confused don ya kasa fahimtar xancen nata, Inna tace "A
kara min Ac, xafi ya isheni" Abba ya dau remote ya kunna Ac din, yace "Ban fahimta
ba Inna" Nan inna ta xauna tayi ma Abba tsari da abinda Nihad ta fada mata da ma
wanda bata fada mata ba duk ta dire ma Abba, Abba yace "Ikon Allah, ke yanxu wa ya
sanar maki wannan?" Inna tace "Har gida ta sameni tana kuka kamar ranta xai fita,
hankalina yayi mugun tashi shine nace da kaina xan taho da daddaren nan, sannan a
kira min dreban in ji uban da ya aikosa wajenmu, ni dama ina ganinsa na sha jinin
jikina ban yarda da shi ba kawai nayi shiru ne, wa yasan adadin binne binnen da
yayi maka a gidan nan yanxu? Huhuhu kana wasa da buzun mutum, Ai irinsu xuwa suke
su tarwatse gida kai har ma su talauce mai gidan su saci abinda xa su sata su gudu
su koma Nijar, to Ibrahim ko motar nan ma ya gudu maka da shi ai ya cuceka, to
yanxu ni dai a kira min shi ko in tafi in samesa da kaina" Abba yace "Aa ba sai kin
samesa ba, ai sallamarsa kawai xanyi ya tafi ba sai anyi wani tashin tashina ba"
Inna tace "Aa ko xagi ne a bari in masa kafin ya tafi ai" Abba yace "Ke dai nace ki
bar komai a hannuna, bari Hamid ya xo ya maida ki gida dare yayi" Tace "Ai
Habubakar ne ya sa ya kawoni banda haka waye ubana Hamid xai kawoni, tun fa da aka
korosa daga kasar wajen yake jin haushin kowa, to ni nasan sanda ya koma can da
xama balle sanda aka korosa, kawai gani nayi ya dawo da manyan jakunkuna, ji yake
kamar duk ya kashe mu yanxu haka" Abba yace "Ke wa yace maki an korosa, don Allah
ki bar fadin wnn magana a xata da gaske ne" Mikewa yayi ya fita daga parlon ya kira
Hamid dake main parlor yace "Zo ka maida Hajiya gida" Yace "Toh Abba" Har mota ya
rakata, bata ce xata shiga wajen matansa ba shi ma bai ce ta shiga ba, don da suka
fito parlor ma yace Nihal ta kirasu su gaisheta ta hana, yana tsaye compound din
har motar ta fita, yana kallon mai gadi dake kulle gate yace "Kai ina Ibrahim?"
Aminu bai kai ga bada amsa ba sai ga khalil da mota, Aminu ya kara bude gate din
Khalil ya shiga compound din da motar sannan yayi parking a parking space Abba dai
ya bisa da kallo, yana sauka daga motar ganin Abba a tsaye, ya nufesa da ledan
pharmacy a hannunsa ya ɗan risina yace "Ga maganin Alhaji" Abba yace "Wani Magani?"
Khalil ya kallesa yace "Da kace a siyo" Abba yace "Na gaya maka maganin da zaka
siyo min ne?" Khalil ya kalli ledan hannunsa da sauri, kawai sai ya rasa abinda xai
ce, Abba ya amshi ledan ya bude maganin sannan ya bude wayarsa ya shiga message din
da Dr dinsa ya turo masa yaga maganin ne Khalil ya siyo, Abba ya daga kai yana
kallonsa daga sama har kasa, kafin yace komai khalil yayi saurin cewa "Ai ka fada
min sunan maganin, rikewa nayi a kai" Abba dai bai ce komai ba sai kallonsa yake,
Khalil kam ya kasa barin su hada ido, Can Abba yace "Ban gaya maka sunan maganin
fully ba" Da sauri khalil yace "Ka tambayi Habibu a can garinmu akwai wani likita
da ya bude Kemist na siyar da magunguna, na fi shekara takwas ina jire masa shago
yana bani wani abu duk wata, Allah ya bunkasa masa shagon sosai, rasuwa Allah yayi
masa shine yaransa suka rufe shagon bayan sun bada sarin duk magungunan da ya bari,
wannan dalilin ne ma har yasa da Habibu yayi min tayin wannan aikin na taho kano
don ina xaune babu abinda nake, don haka babu wani magani da ban sani ba yanxu haka
sai abinda ba a rasa ba..." Abba yace "Allah ya rufa asiri.... Yau kuma me ya
hadaka da Nihad?" Khalil ya sunkuyar da kai yace "Bani da masaniyar na mata wani
laifin yau, kawai dai abinda na sani saurayinta ya zo zai bani kudi yau da na kai
ta babban shago xata yi siyayya, sai na nuna baxan amsa ba, shkkn abinda na sani
kenan Alhaji" Abba yace "Kaje xa mu yi magana gobe" Daga haka Abba ya nufi cikin
gida, Khalil ya koma gun mai gadi ya zauna letting out a deep breath. Washegari da
safe Nihad ta leka window ya fi sau goma wai taga ko driver ya fara harhada kayansa
xai bar gidan, amma sai taga ya kai su Sudais da Amina school, kuma da ya dawo taga
ya ci gaba da zama bakin gate, kasa samun sunkuni tayi, ta dau wayarta tayi dialing
number Inna, yana fara ringing ta daga, tace "Ina kwana inna" Inna tace "An tashi
lafiya" Nihad tace "Inna wai jiya ya ku ka yi da Abba da kika xo ne?" Inna
tace "Yace xai yi masa koren kare, ai shi bai san haka yake ba, da kyar ma in ya
kwana a gidan ki bincika ki ga" Nihad tace "Wani bincike bayan ga mutum can a zaune
ina kallonsa" Inna tace "Atoh, Kilan sai yau xai tafi, ai na gaya ma Ibrahim
maganganu masu ta6a xuciya jiya, yace min in sha Allahu xai sallamesa, ina jin sai
yau din xai koresa don jiya kinga ai dare yayi kar ace mutum bai da imani yayi kora
cikin dare" Nihad tace "Sai anjima" Katse wayar tayi ta bude kofar daki ta fito, a
parlor ta hadu da Nihal, Nihal tace "Kinsan in two days time xan koma school" Nihad
ta tsaya ta kalleta tace "Toh ai baki gaya min ba" Nihal tace "Toh yanxu na gaya
maki" Nihad tace "Toh yanxu da Habibu baya nan waye xai kai ki Zaria?" Nihal tace
"Ni ma ban sani ba, sai Abba yayi magana" Nihad tace "Don kinga wannan drivern
sallamarsa xa ayi yau" Nihal dake ta kallonta tace "Okay" Nihad tace "Ko dai har
kinyi shopping din ki?" Nihal tace "Aa probably today or tomorrow, sai yanda Abba
yace" Nihad tace "Okay ki min magana sai mu je har da ni" Nihal tace "Okay, baki da
lectures yau?" Nihad tace "Toh ko ina da lectures ai babu driver da xai kai ni, but
karfe tara nake da lectures" Bata jira cewar Nihal ba ta nufi kofar fita parlon ta
fito compound, Backyard din gidan ta nufa kai tsaye gun tsuntsayenta su Saminu na
gaisheta duk tayi kamar bata ji su ba, tsaye tayi bata motsin kirki tana kallon
cages din birds din da duk suke a bude kuma babu birds din a ciki sai roban
abincinsu da ruwa, duk cages din guda hudu a bude suke har na parrot dinta, Dawowa
tayi da gudu cikin gida tana kallon Saminu dake shara Shafi'u na watering flowers
din gidan cikin tashin hankali tace "Saminu ina tsuntsaye na aka kai min?" Saminu
ya mike da sauri haka Shafi'u da yayi dropping watering can din hannunsa, Saminu
yace "Suna can cikin kejinsu Hajiya" Ta gwalo ido tace "Wani cage din??" Duk suka
nufi inda birds din suke, sai ga su sun dawo suna wuri wuri da ido, Saminu na in
ina yace "Wllh Hajiya ko jiya sai da muka xuba masu abinci da ruwa...." Da sauri ta
juya ta bar wajen ta nufi gun mai gadi cikin rawan murya tace "Aminu ina aka kai
min tsuntsaye na?" Aminu yace "Suna can keji Hajiya" Cikin daga murya tace "Wani
Cage din, abinda naje na tarar a bude babu komai ciki" Mai gadi ya mike da sauri
yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, babu komai ciki?" Shi dai Khalil na xaune
yana danne danne da torchlight phone, Aminu ya nufi inda birds din suke da sauri,
Nihad da har kanta ya sara mata ta bi bayansa gabanta na faduwa, can ba a dau lkci
ba sai ga ta ta dawo tsakar compound ta rusa wani uban ihu ta daura hannu a ka uwa
warce aka yi ma mutuwa, Nihal ce ta fara fitowa a guje ta nufota tace "Nihad what
happened?" Nihad ta fashe da matsanancin kuka tace "Wani yaje ya bude min cage din
birds dina duk sun gudu, wayyo Allah na na shiga uku, wllh har sun saba dani Nihal,
Parrot din har kiran sunana yake yace good morning" Su Aminu da Saminu dai na can
gefe a tsaye sai wuwwurga idanuwa suke, Umma ce ta fito compound din Mumy na biye
da ita a baya, Hankali tashe Umma tace "Lafiya Nihad, me ya faru?" Nihad ta nufeta
tana kuka sosai ta kamo hannunta tace "Umma wani yayi releasing din min birds dina
duk sun gudu babu ko daya" Umma ta saki salati tace "Waye da wannan danyen aikin,
yanxu babu ko daya wa ennan tsadaddun tsuntsayen da Abbanki ya siya maki" Nihad na
gyada kai cikin kuka tace "Wllh duk sun gudu, bude masu cage din aka yi don su
gudu" Mumy dake kallonta tace "Shine xa ki 6ara baki haka ki daga mana hankali
Nihad?" Umma ta kalli Mumy tace "Haba Maryam, ko don ba ke kika bada kudin siyan
tsuntsun ba, kinsan yanda dabba ke da shiga rai kuwa" Mumy tace "Toh waye ya budesu
har suka gudu? Sannan ita me yasa bata xuwa dubasu a kai kai yaushe rabon da taje
inda suke" Cikin kuka Nihad tace "Wllh ina xuwa dubasu ki tambayi Aminu, kullum sai
naje dubasu" Nihal tace "Toh ko da aka basu abinci ne aka mance ba a kulle cage din
ba" Nihad ta durkushe wajen tana kuka kamar ranta xai fita tace "Ni wllh ko ma wa
yayi min haka Allah ya isa ban yafe ba, Allah ya tsine ma koma waye, Allah ya isa,
shi ma sai an nemasa an rasa wataran yanda na rasa tsuntsaye nahhh" Juyawa Mumy
tayi ta wuce cikin gida, Umma ta dagota tace "Ai ba Allah ya isa xa kiyi ba, koma
uban wa yayi wannan aika aikan dole a ganosa a hukuntasa, ki bar komai a hannuna
kawai" Nihad na shessheka tace "Umma wanda yayi mun haka ya tsaneni ne shi sa yayi
haka kuma sai Allah ya tsine masa albarka ya daidaice, Allah ya isana" Nihal tace
"Ki daina cewa haka baki san ko..." A fusace Nihad ta mike ta hankadeta har sai da
ta kusa faduwa, tace "Shut up plss if have nothing good to say" Bude baki Umma
tayi, sae kuma ta kalli Nihal tace "To wuce ciki" Nihal ta ta6e baki ta juya ta
koma ciki, Umma ta juya ita ma ta bar wajen, Nihad ta hade rai ganin yanda
ma'aikatan gidan ke kallonta, cikin tsawa tace "Uban meye kuke wani kallona
munafukai yan iska, ai har da hadin bakin ku aka sakar min tsuntsaye suka bi
duniya, to ku sani wllh daga yau sbda ku ni xan dinga shiga kitchen sai in ga d'an
iskan da xai xubo maku abinci ya kawo maku, for one week ba ku da abinci wllh a
gidan nan tunda har aka sakar min tsuntsu suka gudu" Tana fadin haka ta juya fuuuu
ta wuce ciki. Da yammacin ranan Farooq ya shigo gidan daga Abuja, Nihad da abun
duniya ya isheta don har sannan Aliyu isn't picking her calls, ga kuma har yanxu
bata ga Driver ya bar gidan ba, kuma babu ma wata alamar da ta nuna xai bari, yana
nan a xaune tare da mai gadi, ko makaranta bata je ba sbda damuwa gashi har test
Husnah tace mata anyi, ta mike daga xaman da take ta yi a parlor ta fito compound
jin motar Farooq, tamke fuska tayi ganin Khalil da Aminu sun nufi Farooq, Khalil ya
fara basa hannu da ladabi, suka gaisa, farooq dai sai kallonsa yake, Aminu dake ta
rawar kafa yana washe baki yace "Ae shine sabon dreban gidan tun bayan tafiyar
Habibu, yau kwanansa biyar ina jin a gidan nan" Farooq ya kara kallon Khalil daga
sama har kasa, sai kuma yace "Driver??" Sai kuma yayi saurin cewa "Ohk maa sha
Allah, ya sunanka?" Khalil yace "Ibrahim" Farooq ya gyada kai yace "Maa sha
Allah...." Tuni Mai gadi ya dau jakar Farooq ya nufi cikin gida da shi, Nihad dake
tsaye balcony ta hade rai tace "Toh ajiye kayi tafiyarka ko ka aikesa ne??" Aminu
ya ajiye jakar ya juya sui sui ya bar wajen, Farooq ya amsa gaisuwan da Nihal ke yi
masa ya nufi Nihad yace "What happened Nihad?" Kamar jira take ta fashe da
matsanancin kuka, yace "Meye haka?" Cikin kuka tace "Ya Farooq wani axxalumin da
baya tsoron Allah ya bude ma tsuntsaye na cage duk sun gudu har parrot din" Bude
baki Farooq yayi yace "Garin yaya?" Ta karasa ta rungumesa tana kuka sosai, ta
gefen ido khalil ya kalleta kafin ya juya ya bar wajen, Farooq ya dago kanta yace
"But how did it happen" Tace "Kawai yau da safe naje basu abinci naga ba komai
cikin cage din" Yace "Ow that's bad, bari anjima sai mu je ki siyo wasu" Ta
marairaice tace "But how will d parrot get to know me just as the old one?" Yace
"Yanda wancan din ya sanki sabon ma haka xai san ki" Daga haka ya kama hannunta
suka shiga gidan tana share idonta. Bayan ta amshi nata tsaraban da farooq ya kawo
mata ta wuce sama xuwa dakinta, wayarta ta dauka ta sake kiran Inna, yana fara ring
Inna ta daga, Nihad tace "Inna har yanxu fa driver din na nan babu inda ya tafi don
ma in gaya maki" A fusace inna tace "Ke raba ni da wani shegen dreba an shigo an
kwashe min yan canjina wai barin gidan da nayi jiya da magariba, kowa sai ce min
yake ba shi bane, to ni na saci abina koko?" Nihad ta tabe baki ta katse wayarta,
sai kuma ta ja tsaki tace "Dama ba a abun arxiki dake..." Da daddare tana dakin
farooq dake kallonta yace "Toh sai in ce masa me idan na kirasa?" A hankali tace
"Kawai hakuri xaka basa a kan abinda driver din yayi masa" Farooq yace "Ba kince
layinsa a kulle yake ba?" Tace "Aa ya ta6a saving numberka a gabana ai, ka tuna
sanda ya kiraka da baka da lafiya?" Yace "Oh, ohk" Daukar wayarsa yayi ta kira masa
number Aliyu yayi dialing, a kashe suka ji wayar, yace "It's switch off" Shiru tayi
bata ce komai ba, yace "Ki je kawai, gobe sai in kirasa" Mikewa tayi tace "To sai
da safe yaya....."

Saura how many page free pages ya kare???


07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

By _Khaleesat Haiydar_✍🏻

10......

Khalil na xaune yana waya a bakin gate mai gadi ya karaso wajen daga boys quarters,
Khalil ya saka wayar a aljihunsa bayan ya gama, Aminu da har ya xauna ya mike yace
"Aa bari in baka waje ka ci gaba da wayarka...." Khalil yace "Na gama" Aminu ya
dawo ya xauna yana kallonsa yace "Na lura baka son kayi waya a gaban mutane saboda
hayaniya ko?" khalil yace "Haka ne" Aminu yace "Ina can tare da su Saminu muna ta
jajanta lamarin tsuntsayen nan da suka gudu, abun da mamaki da al'ajabi, sun kusa
shekara daya da rabi fa a wajen ba a ta6a nemansu an rasa ba sai yau" Khalil yace
"Ai gwara da suka gudu kar xunubanta ya dinga shafarsu su ma" Aminu ya kyalkyale da
dariya yace "Wllh baka da dama, ni tashin hankalina abincin da tace xa a hanamu, in
an hanamu abinci ya xa mu yi? Ba fa kanta kenan, duk da nasan uwarta baxata yarda
da hakan ba, amma makira ce tana iya biyomu ta kwace idan an kawo mana" Khalil yayi
murmushi kawai, Aminu yace "Amma fa kana bani tsoro da mamaki yanda kake nuna mata
baka shakkarta, akwai wani littafi da na ta6a saurara a shafa labari, kaga yanda ta
sa ka gaba haka? To haka ita ma yarinyar littafin ta sa mutumin gaba yana aiki a
kampanin babanta ita kuma ita ce manaja a kampanin, tayi ta masa walakanci da
rashin mutunci daga baya ta xurma sonsa in gaya maka, To sai...." Dakatar da shi
khalil yayi yace "Me kake nufi?" Aminu ya gyara xama yana washe baki yace "Toh wa
ya sani ko hakan xai iya faruwa wataran, barin taga sambalele me dogon hanci, ka fa
san matan nan ba alkibla garesu ba...." Khalil yace "Ta wahala.... banda abun ka
ina ita ina talaka? Sai dai kuma bata san wani talakan ma ko da kudi aka hadasa
bazai saurareta ba, in dai kamar ni talakan yake wllh ko kallonta baxai yi ba"
Aminu ya gwale ido, sai kuma ya tuntsire da dariya yace "Yanxu kana nufi misali yau
ace maka gata nan ka aura baxa ka aura ba?" Khalil yace "Misalinka ba me yiwuwa
bane har duniya ta nade, don kuwa da in aureta gwara na aura Krista, ko kuma in
dauwama ba auren, kai kasan darajan da Allah yayi ma ɗan Adam kuwa? To bari kaji ko
da kudi wannan yarinyar baxata tsaya inda budurwata take ba, ga ta dai yar talakawa
kamar ni amma ita wannan fitsararriyar baxata tsaya inda xata tsaya ba wllh...."
Aminu yace "Aa dole xaka ji haushinta wllh, nima kuma ina taya ka jin haushinta
kullum, ji tijaran fa da tayi maka daxu, banda yanayin rayuwa a ina xata ganka har
ta cakume kwalar rigarka tana dungure kanka tana maka munanan xagi, a ƙalla ai xaka
bata kusan shekara goma na sani, amma ta maka wnn cin mutunci da tijara gaban Nihal
da kawarta, ba ma wannan ba ji yanda ta dau bahon ruwa gaba daya ta juye maka a
cikin jama'a" Khalil yayi wani Murmushi bai dai ce komai ba, Aminu yace "Ni dai yau
ace min ga ta in aura xan yarda in aureta ko don kudin babanta da kuma halaccinsa,
sai kuma in saita mata xama...." Daga sama har kasa khalil ya kalli Aminu, bai san
sanda yayi dariya ba yace "Kai ta kudin kake kenan" Aminu ya washe hakora, Khalil
ya girgiza kai yana Murmushi, Aminu yace "Wllh ni fa naji dadin bude kejin nan da
aka yi tsuntsayen suka gudu, Allah ne ya bi min hakki na abinda ta min jiya a kan
su" Khalil yace "Ku kuka bar mata tsuntsayen suka kai har warhaka a gidan ai" Daga
haka ya mike ya bar Aminu a wajen xai je yayi alwala kafin a kira isha'i. Nihad na
komawa dakinta taga missed calls din Husnah da yawa, ta xauna gefen gado ta kirata,
yana fara ringing Husnah ta daga, Nihad ta dinga jin hayaniya tace "Kina ina haka?"
Husnah tace "Mozida suite" Nihad tace "Me ake yi a nan?" Husnah tace "Wllh na manta
ban gaya maki ba shekaranjiya a schl, Abokin saurayin Naf ne ke birthday, nayi ta
kiranki tun daxu baki daga ba dama wai in gaya maki" Nihad tace "Toh ai tun jiya ya
kamata ku gaya min, kuma yanxu kinga dare yayi" Husnah tace "Kashhh, kinga ke
matsalarki kenan Nihad, karfe takwas din ne dare?" Nihad tace "Toh ta yaya ma xa
ayi in taho babu me kai ni, kinsan wawan nan har yanzu Abbanmu bai koresa ba wa
yasani ma ko asiri yayi ma yan gidan duk suke supporting dinsa, Umma ce kadai ke
bayana a ko da yaushe, throughout na xuba ido yau in ga ko xai tafi ban ga ya tafi
ba" Husnah tace "Kinsan abinda zai faru?" Nihad tace "Aa" Husnah tace "Yanxu xa mu
fita mu karo wasu wine, kawai ki san duk yanda xa ayi ki fito mu hadu a wannan
katon supermarket din na anguwarku" Nihad tace "Kar fa ku bar ni inyi ta jira
Husnah" Husnah tace "Haba wani jira, bayan gashi nan yanxu ni da Naff da Sumy za mu
fito" Nihad tace "Okay, bari a shiga masallaci sbda yan sa ido, sai in fito" Husnah
tace "Sai mun hade, kar kuma kice ban gaya maki ba, A abokan celebrant din har da
'ya yan gwamnoni, shiga ce ta kece raini xa ki yi, duk da nasan ki ba wasa" daga
haka Husnah ta katse wayar. Nihad ta mike ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje jin
ana kiran isha'i, ta dauro alwala ta fito da sauri, tada sallah tayi bayan ta idar
ta fito da wani ubansun gown dinta ja wanda Aliyu ne ya siyo mata daga kasar waje
ta saka, ko make up bata yi ba duk ta harhada kayan make up din da turarruka a wani
babban jakarta da xae iya daukan hijab da takalmi da tarkace da yawa, tana jin an
tada sllh sae da ta jira aka yi raka'a daya snn ta fita da sauri bayan ta sa ma
dakinta makulli, tayi surveying parlor don tabbatar da babu kowa a ciki, ko wa na
dakinsa, dama kuma gidan ana magrib kowa ke shigewa daki babu me shiga privacy din
wani, sai kuma washegari idan an hadu wajen breakfast, yawanci da yake a bangaren
Umma dakinta yake, Umma kan shigo taga ko tana waya kuma da wa take wayar, to dai
ta sa ma dakin makulli ko taje xata shiga xata ji sa a kulle, da sauri da sauri ta
fito compound nan ma ta ci sa'a babu kowa, duk suna masallaci, kan kace me ta bar
compound din ta kama hanyar inda supermarket din da Husnah tace ta jirasu yake,
tana isa wajen ko minti biyar ba ayi ba sai ga motarsu Husnah suka dauketa suka
wuce, Husnah tace "Yanxu da Habibu na nan nasan da kansa zai xo ya daukeki idan aka
gama partyn ko karfe sha biyun dare ne, yanxu dole kinga sai mun ajiye ki a nan
after the party in ba dai saurayi kika yi a can ba" Nihad dai ta xuge jakarta ta
fara gyara fuskarta xata yi light make up. Wajen partyn ya hadu iya haduwa kamar
yanda Husnah ta fada ai kam ya yan manya ne suka cika wajen, very dim light ne
kunne a inda suke birthday din, babu abincin da babu da abun sha tun daga ruwa,
lemo, wine, alcoholic drinks, kai komai da akwai a wajen, gasassun rago biyu aka
bankare wajen, ga manya manyan pepper chicken... cake din da budurwarsa tayi masa
ma kadai abun kallo ne... duk hayakin cigarette ya turnike wajen, an sha shagali
iya shagali a birthday din nan, abinda Nihad bata yarda da shi ba shine ta sake ma
maza fuska a wajen, xata dai shige cikin kawayenta mata amma bata xama cikin maza,
ko da kana ta shisshige mata ma banxa xata yi da kai tayi ta danna waya, Husnah ta
kwankwade glass din wani alcoholic wine, glass na biyu kenan ta sha, su Naf da
sauran yan matan wajen su ma duk wine din suke sha, Husnah na kallon Nihad dake
rike da cinyar kaza da wani can drink a gabanta tace "Wllh ki ɗan dana wine din nan
ya fi na wancan ranan dadi sannan shi wannan babu abinda xa ki ji idan kika sha,
wllh soo cool" Nihad tace "Aa baxan sha ba drink din nan ya isheni" Zully tace "Ke
dadina dake kwabsin ki yayi yawa, don Allah ki ɗan kurba idan bai maki ba sai ki
bari kar ki sha, nima kinsan ai ban fiye son wines haka ba, amma tunda kika ga ina
shan wannan ya kamata kisan ba karya" Nan duk suka mata caaa akan cewa ta ɗandana
idan bata ji dadinsa ba sai ta bari, Husnah ta cika mata glass din gabanta tace
"Kiyi sipping first ki ji" Nihad ta dauka ta kai baki ta kurbi kadan, bayan few
seconds ta wara ido tana kallonsu tace "Waow its really nyc, it tastes good" Husnah
ta kyalkyale da dariya tace "Ba na gaya maki ba da kin tsaya kin kwabsawa" Nan
Nihad ta kwankwade wine din, Husnah ta kara cika mata glass nan ma ta shanye, Naff
sai dariya take tana cewa "Wllh ki bar ta haka Husnah tam ni dai na gaya maki"
Husnah tace "Toh meye a ciki ai baya wani bugarwa" Haka dai Nihad ta sha wine tayi
nak, party din da ba a karasa da ita ba kenan tayi ta masu layi a wajen, banda
dariya babu abinda suke mata, Husnah tace "Kaii amma jininta ma bai da karfi wllh,
ɗan wannan wine din shine xai bugar da ita" Nan suka ci gaba da shagulgulansu,
Nihad kuwa ta kife kai a wajen sai bacci, ba a tashi birthday din nan ba sai karfe
dayan dare, Husnah ba irin tashin da bata yi ma Nihad ba amma ta ki tashi, da ta
dagota xata koma ta kife kai, wani abokin celebrant din yace "Na kama daki a nan
why not kawai ku barta ta kwanta ta huta" Husnah tace "Aa nasan halinta tana
farkawa xa mu samu matsala da ita, kawai dai kamata yayi mu ma a kama mana dakin
dama dare yayi ba lallai a bari mu shiga schl ba yanxu, idan ya so duk sai mu kwana
a nan" Ba don ransa ya so ba haka nan ya kama masu dakin, suka ciccibi Nihad sai
dakin suka kwantar da ita saman gado, Husnah dai na ta kaffa kaffa da Iphone din
Nihad a wajen tunda ta san halin wasu daga yan matan dake wajen. Sai kusan biyu
suka kwanta a dakin bayan duk sun yi wanka.
Karfe hudu da rabi Nihad ta farka da wani axababben ciwon kai, da kyar ta mike
xaune tana bin dakin da kallo, sai kuma ta sauka tana layi ta nufi kofar dake dakin
wanda bandaki ne, ta kuma sani tunda sun saba lodging a wajen ita da su Husnah,
tana shiga bayin bayan tayi fitsari taji wani amai ya taho mata, nan ta dinga
kwarara aman tana rike da cikinta dake juya mata, da kyar ta wanke bakinta bayan ya
lafa mata ta fito, bata sake komawa baccin ba sbda ciwon kai me tsanani da ya
takurata, ganin biyar ya kusa ta ta6a Husnah da kyar, ta fi minti goma tana tada
Husnah dake xuba minshari kamar wani kato, kafin ta bude ido cikin magagin bacci
tace "Wai ya aka yi Nihad?" Da kyar Nihad tace "Don Allah wa xai yi dropping dina
gida kafin yan gidanmu suyi noticing bana nan, asuba ya riga yayi" Husnah ta ja
tsaki tace "Tsakar daren nan wa xai wani kai ki gida kowa na bacci, ki bari gobe
kawai" Nihad tace "Ke asuba fa yayi ki duba agogo ki ga, wllh na manta yayanmu na
gida zai iya xuwa bedroom dina yace xai tasheni inyi sallah, idan yana gari duk
yana tashin mu...." Husnah tace "Ohh God Nihad ki barni inyi bacci mana, haba" Daga
haka ta juya ta ci gaba da baccinta, tashi Nihad tayi da kyar ta bude jakarta ta
dau Hijab dinta ta saka sannan ta bude kofar dakin ta fita, babu kowa reception din
hotel din sai tv dake aiki, ta fita haraban wajen, wani mutumi ta gani xaune yana
ta xukar ta6a a waje, ganinta ya kashe ta6ar, ta nufesa tana kallonsa ganin
bahaushe ne tace "Bawan Allah idan babu damuwa ina son taimako wajenka don Allah"
Daga sama har kasa yake kallonta yace "Taimakon me?" Tace "Nasarawa GRA nake son ka
ajiyeni pls, kawayena da muke tare da su bacci suke ni kuma ban xo da motata ba"
Yace "Ohk babu damuwa, bari in dauko makullin motata" Tace "Toh Nagode, nima xan
dauko jakata" Daga haka duk suka koma ciki, ta shiga dakinsu, shi ma ya shiga nasa,
ta tattara komai nata a jakarta, wayarta ne kawai bata gani ba, zaro ido tayi lkci
daya hankalinta ya tashi ta fara tashin Husnah a rikice tace "Husnah ina wayata??"
Da kyar Husnah dake ta snore kamar doki ta bude ido, a fusace tace "Ohh my God
Nihad ki kyaleni mana inyi bacci, me yasa kin fiye takura ne wai" hankali tashe
Nihad tace "Dalla can ina wayata??" Husnah ta ja wani dogon tsaki ta daga pillow
dinta ta zaro wayar ta ajiye mata a gefe sannan ta ci gaba da baccinta, Nihad ta
sauke ajiyar xuciya sannan ta dau jakarta da wayar da sauri ta fita, Tsaye ta gansa
a haraban hotel din yana jiranta jikin motarsa, bayan ta shiga motar shi ma ya
shiga, suna fita daga suite din yace "Ku ne ku ka yi birthday jiya?" Gyada masa kai
tayi kawai, yace "Gaskiya ne, birthday din na manya ne" Duk surutun da yake Nihad
ba tankasa take ba, banda tashi babu abinda xuciyarta yake, she was so
uncomfortable, a haka ta dinga daurewa tana masa kwatance har suka isa dai dai inda
su Husnah suka dauketa daren jiya, yace "Ina gidan naku?" Ta nuna masa wani layi
dake a rufe tace "xan karasa da kafa, kaga gate din a kulle yake" yace "Ohk amma ya
sunanki?" Cike da karfin hali tace "Aysha" yace "Maa sha Allah, Aysha ki bani digit
dinki mana" ta gyada masa kai kawai, ya mika mata wayarsa ta amsa tayi dialing wani
old line dinta dake a kashe tace "Wayar a kashe yake sai na shiga gida na kunna"
yace "Toh shkkn nagode Aysha ni sunana Mustapha" tace "Nagode, sae anjima" daga
haka ta bude motar ta sauka, cike da karfin hali take tafiya don jiri ke dibanta,
ta shiga layin da ta nuna masa, sae da ya ga tayi nisa sosai a layin sannan yayi
reverse ya bar wajen, tana waigowa taga ya wuce, ta juya da sauri ta dawo ta fita
daga layin sannan ta dau hanyar nasu layin, gani tayi kamar an idar da sallah bayan
ta iso kusa da gate din gidansu, da sauri ta bude karfen inda aka xagaye da flowers
a kofar gidan nasu ta shige bayan flowers din ta buya tana maida numfashi, don har
an fara fitowa daga masallaci, tana jin aka shiga cikin gida aka kulle gate, Sai
kuma ta sake jin an bude gate din, Muryar Abbanta taji yana amsa gaisuwa nan bakin
kofar gate din, sai da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta, ta kara yin lamo a cikin
flowers din duk da ant da taji suna cizonta bata damu ba, ta fi minti bakwai a haka
bata sake jin motsin kowa ba bakin gate din, hautsinewa cikinta ke yi taji amai na
taho mata, kokarin fitowa take yi daga flower din don ta samu ta shige cikin gida,
kawai taga mutum xaune a dakalin dake kusa da inda take labe, sai da zuciyarta ya
kusa shigewa cikinta don duk xatonta ya Farooq ne don shi ma ya kan xauna a waje
idan aka idar da sallah, ya daga kai jin motsi, sai kuma ya mike tsaye da sauri,
komawa baya yayi yana kallonta with surprise, ita kuwa tsabar tsorata aman da take
rikewa ya taho mata, ta durkusa ta dinga kwarara aman a wajen, kauda kansa yayi
bayan yayi perceiving din aman da take yi, ya sake kallonta this time around da
wani expression a fuskarsa, duk sae da ta amaye sauran liquor din cikinta sannan ta
mike da kyar, ko kallonsa bata yarda tayi ba ta shige gate din gidan, ya bi ta da
kallo babu ko kiftawa, ko second ashirin ba ayi da shigarta ba sae ga mai gadi da
gudu ya fito waje yana kallon Khalil yana zare ido yace "Ina me tabbatar maka bata
kwana gida ba, dawowarta kenan daga duk inda ma taje wllh" Khalil dai bai ce komai
ba, mai gadi ya yamutse fuska yace "Ni warin giya ma nake ji, ko kai baka ji ba don
Allah?" Khalil ya juya ya shiga gate din gidan ya xauna nan saman bench dake gefen
dakin mai gadi with numerous thought running his mind, mai gadin ma ya shigo ya
zauna yace "Ni fa sai nake ganin ma kamar warin giya take ko kai baka ji ba?"
Khalil ya kallesa yace "Amma baka wanke bakin ka ba ko?" Mai gadi ya ɗan zaro ido,
sai kuma yayi yake yace "Ai shi xan wanke ma na fito yanxu..." Tashi yayi da sauri
ya shige dakinsa, Khalil ya kalli hanyar gate din, sai kuma ya mike ya fita,
jakanta da ya hango cikin flowers da ta bari ya dauko ya shige cikin gidan sannan
ya nufi chalet dinsu, A parlor ya tadda Su Saminu sun yi dai dai duk suna bacci, ya
ciro makullin daki a aljihu, ya bude dakin sannan ya shiga ya kulle kofar, xaunawa
yayi gefen gado ya bude jakar, takalma heels ya fara cirowa da kayan kwalliya da
turarruka, sai iphone dinta da ya gani, ya dinga jujjuya wayar don a lock yake, sai
kuma ya ajiye ya ci gaba da ciro sauran kayan jakan, bai san sanda ya bude baki ba
ganin kwalban Codeine, can ya ajiye a gefe, ya bude wani zip dake cikin jakar,
still yayi ya dinga kallon abinda ke wajen babu ko kiftawa, ya kai hannu a hankali
ya cirosu gaba daya yana jujjuyawa, prophylactics ne na maza da na mata, ya ajiye
su a gefen gado ya mike ya nufi window din dakin yana kallon waje babu ko kiftawa.
Nihad na fitowa daga wanka aka bude kofar dakin, sae da zuciyarta ya kusa shigewa
cikinta don tsoro, Umma ce ta shigo dakin ta rufe kofar murya can kasa tace "Daga
ina kike Nihad?" Nihad ta daburce tace "Ni Umma?" Umma tace "Aa ban son karya ba
yanxun nan naga giftawarki ba na fito daga parlon Abbanku?" Nihad tayi narai narai
da ido tayi shiru, Umma tace "Gaya min gaskiyan inda kika je" A hankali tace "Wata
kawarmu ce ke birthday Umma" Umma tace "Ki dai nutsu, in ma xaki birthday ae sai ji
gaya min ni baxan hanaki ba, amma baxa je makarantar yau ba bacci xa kiyi ko?" Tace
"Aa xan je" Umma tace "Toh sai kiyi ki shirya karki makara" Daga haka Umma ta juya
ta fita, Nihad ta sauke ajiyar xuciya, sai yanxu da ta sake wani aman da xata yi
wanka taji ta ɗan fara dawowa dai dai, kanta ya daina juya mata, tana gaban madubi
tana shafa mai ta tuna da jakarta, xaro ido tayi ta mike da sauri ta dau hijab
dinta gogagge ta saka sannan ta fito daga dakinta, downstairs ta sauka ganin Farooq
a xaune dining area tace "Yaya ina kwana?" Yace "Kina jin ina Knocking ki ka ki
bude kofa daxu?" Tace "Aa yaya ina bandaki ne, ai na tashi sannan ma" Bai ce komai
ba, ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ta bude kofa, yace "Ina xa ki?" Ta
marairaice tace "Xan je in duba ko Allah xai sa tsuntsayen sun dawo" Murmushi kawai
yayi ta juya ta fita, da sauri ta nufi gate, taji dadin ganin mai gadi baya bakin
gate din, sannan khalil ma baya wajen, tana bude gate ta samesu su biyu xaune kofar
gidan, suna hada ido da khalil ta daburce, sai ta hau kame kame, bata amsa gaisuwar
da mai gadi ke mata ba tace "Aminu a layin nan babu inda zan samu katin waya?"
Aminu yace "Inaa, Hajiya ai sai an fita can supermarket" Tace "Ohk" Da gefen ido ta
dinga lekan cikin flowers din dai dai inda ta buya amma bata ga alamar jaka ba, nan
hankalinta ya tashi sbda wayarta na ciki, bata san lkcn da ta karasa wajen ba tana
kara dubawa da kyau, Aminu yace "Wani abu kike nema ne Hajiya?" Wani shegen kallo
tayi masa tace "Toh ina ruwanka?" Khalil dai na ta danna er karamar wayar hannunsa,
ta saci kallonsa.
07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

11

Juyawa Nihad tayi daga karshe ta koma cikin gidan don ko kallon inda take Khalil
bai yi ba, to wai wa ya dau jakarta? lkci daya jikinta yayi sanyi hankalinta ya
tashi fiye da da, haka nan ta shiga gida jiki ba kwari ta koma dakinta ta shirya,
Hijab har kasa ta saka ko powder bata shafa a fuskar ba, ta fito ta tafi bangaren
Mumy, xaunawa tayi saman kujera ta gaisheta sannan tace "Mumy xan tafi makaranta
ina da lectures karfe takwas" Mumy ta kalli agogo ganin bakwai da rabi tace "Kinyi
breakfast ne?" Tace "Xan yi idan na sauka" Mumy tace "To ko ke fa da kika sa Hijab
yau, kinga yanda yayi maki kyau, amma kullum in ta maki magana daya a kan shegun
mayafan nan da kike sawa ba kya ji" Nihad ta ɗan kirkiri murmushi ta mike tace "Sae
na dawo" Mumy tace "Toh Allah ya tsare, kiyi addu'a kafin ki fita" Nihad ta amsa da
"Toh" sannan ta fita. Gaba daya Nihad neman appetite dinta tayi ta rasa, daga
karshe nan ta bar abincin tayi ma Umma dake parlor sallama ta fita gidan, mai gadi
kadai ta samu xaune bakin gate, ta nufesa tana tsaye dab da shi tace "Aminu don
Allah baka ga min jaka a bakin gate ba? Kamar a nan na yar jiya da daddare, ko da
safe nan don Allah baka gani ba??" Yace "Subhanallahi jaka Hajiya? ae ko wllh tllh
ban gani ba, kema kin san da na gani ae xan adana maki" Nihad ta rasa abun cewa
tayi shiru, iphone dinta fa na jakar yanxu ta ina xata fara? Wani xufa ta ji na
keto mata, can ta dake tace "Ina driver din?" Aminu yace "Ya tafi yayi wanka" Tace
"Sae kaje kace masa ya fito ya kai ni makaranta ni dai" Aminu ya mike da sauri yace
"Toh Hajiya" daga nan ya nufi chalet din. Bayan Aminu ya shiga har dakin da khalil
ke ciki ya sanar masa abinda Nihad tace, khalil dake zaune gefen gado yana combing
kansa yace "Ta saba xuwa makaranta karfe bakwai da rabi dama?" Aminu yace "Atoh
dae, nima ban ta6a ganin ta fita da safe xuwa makaranta ba wai kuma ran asabar,
amma kai dai kawai ka fito kaje ka kai ta kar ta kara maka wani fitsarar" Khalil ya
kallesa bai dae ce komai ba yana ci gaba da combing din kansa, Aminu ya bi dakin da
kallo yace "Wai!!! amma kana kokarin gyara dakin nan, dubi fa dakin kamar a can
daya bangaren, ba dauda ba wari ba tarkace, wannan ai idan na kwanta a nan sai in
makara al-qur'an...." Khalil ya mike yace "Mu je..." Aminu ya kasa kunne yace "Ba
waya bace ke wannan rurin?" Khalil yace "Mu dai je" Aminu ya mike ya fita dakin,
Khalil ya bi sa da kallo kafin ya dage duvet din da ya lullube jakar Nihad da shi a
saman gado sannan ya bude jakar ya ciro wayarta dake ta vibrate alamar kira, Husnah
ya kara gani for the fourth time a jikin screen din wayar, tun daxu take kira,
nannade wayar yayi da duvet don baxae iya silencing dinsa ba sbda security dake
jiki, ya dau makullin mota ya fita daga dakin ya kulle sannan ya fita compound.
Yanda xaka san abun duniya ya taran ma Nihad xama tayi a kan bench da mai gadi da
Khalil ke xama, ita dai tana da yakinin dole Khalil xai hango jakar a bayan flowers
kuma ai a bude ma ta bar karfen wajen, wai to don bashi da kunya sai kawai ya kama
ya dau mata jaka, yaushe ta sake masa har xai kai hannunsa kan jakarta, wato yanxu
jira yake sai ta tambayesa kenan? Cabdi... tana hangosu tayi maza ta mike ta sha
kunu, Khalil dai ko kallon direction dinta bai yi ba ya tafi gun motar ya bude ya
shiga, bayan yayi warming mai gadi ya bude masa gate, Sai da ya fita compound
sannan Nihad ta fita ita ma tana tafiya a hankali ta bude back seat ta shiga ta
xauna, Aminu ya dinga daga mata hannu alamar a dawo lafiya, ko kallonsa bata yi ba,
Khalil ya ja motar suka bar layin, tunani take to yanxu dai tambayarsa jakarta xata
yi? Cab gaskiya baxata yi hakan ba, m ta saci kallonsa ta madubi suka yi ido hudu,
da sauri ta dauke kanta ta wani daure fuska ta zuge zip din wani jakar da ta dauko
ta fiddo chewing gum ta bude ta jefa baki, shi dai driving kawai yake, sai da suka
kusa makarantar tayi gyaran murya tace "Malam ka bude min Ac xafi ya dameni...." A
takaice yace "Ke kika san meye shi" Tayi masa wani kallo tace "kace me??" Bai tanka
ta ba, ta masa wani shegen harara ta ja tsaki kasa kasa ta ci gaba da taunar
chewing gum dinta, suna isa makarantar dai dai department din nasu yayi parking,
tana ta sauraron ta ji ko xai yi maganar jakar amma shiru, gabansa kawai yake
kallo, ganin bata sauka ba, kuma kamar bata da niyyar saukan yace "Ko yau ma xa a
bar maki makullin ne?" Ta galla masa wani harara tace "Ai ba ni na kawo motar ba
balle ka bar min makullin" tana gama fadin haka ta bude motar ta sauka ta ki kulle
door din tayi tafiyarta, ya bi ta da wani kallo, sai kuma ya sauka ya kulle sannan
ya hau motar ya tafi.... Husnah na ganin Nihad tace "Shine nake ta kiranki kike
danna min busy Nihad?" Nihad ta sauke ajiyar xuciya amma ta ki bata amsa, ta nemi
seat ta xauna, wato dai a takaice drivern nan ne ya dau jakar tunda gashi har
Husnah ta kira ana ta danna mata busy, lallai mutumin nan raini me karfi ya shiga
tsakaninsu, bayan dauke mata jaka sbda guts har bude jakar ma yayi kenan, muryar
Husnah ya dawo da ita daga tunanin da take, tace "Ina magana kin min shiru, dama ba
komai bane ce maki xanyi ki taho da jakar da kika je birthday jiya da shi, don
akwai abubuwana a ciki" Nihad ta kalleta tace "Abubuwanki kamar me?" Husnah tace
"Kwalban Codeine dina da Naff na ciki, sai prophylactics, ni ina jin kamar ma har
da lingerie dina a jakar, don na duba ban gani ba...." Nihad ta zaro manyan idonta
tace "Duk a cikin ina???" Husnah tace "Jakarki mana, kinsan yana da girma" Nihad
bata san sanda ta mike ta dafe kirjinta ba tace "Na shiga uku...." Da mamaki Husnah
tace "Kin shiga uku kuma? Me ya faru?" Nihad tayi narai narai da tace "Wayyo Allah
na, Me yasa xa ki min haka ki ajiye abubuwan nan a cikin jakata Husnah? Me yasa xa
ki min haka? Gashi yanxu jakar ta fadi a bakin gate ban san wanda ya dauke min ba"
Husnah ta gwalo ido tace "Kaiii, garin yaya kika yarda jaka a bakin gate Nihad?"
Nihad da abun duniya ya isheta ta koma ta xauna ta cije yatsa tace "Na shiga uku"
Husnah ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh kinsan wa ya dau jakar ne?" Ta kalli Husnah
tace "Wallahi wannan driver din nake zargi don shi kadai ya gan ni sanda na dawo da
asuba don a bayan flowers dake kofar gida na fara buya as a result of people coming
out from the mosque after subhi prayer" Husnah ta rike ha6a tace "Ji tsiya, Driver
kuma?" Nihad ta kasa cewa komai tayi tagumi, Husnah tace "Tabb shine kika yi shiru,
to me kike jira da har yanxu baki tambayesa ba?" Nihad tace "Toh me xan ce masa?
Bayan ban ga sanda ya dauka ba, Har wayata fa na cikin jakar, idan ba sata yake son
yi ba ai xai ba Aminu ya ajiye min" Husnah tace "Ehh lallai wannan mutumin ya rika,
shi ke ta ja min busy kenan? Wato dai har ya bude jakar" Nihad ta xaro ido tace "Na
shiga uku, gashi kin xuba abubuwa kika ce cikin jakar" Husnah ta mata wani kallo
tace "Ke dalla to meye, koma me ya gani cikin jakar ba shi ya ga duhu ba, kuma ma
bansan uban me kike jira da har yanxu baki tambayesa jakarki ba, ko tsoronsa kika
fara ji? ai ba ma tambayarsa xa ki yi ba wai ko ya ga jaka ko bai gani ba, kawai ce
masa xa ki yi ya baki jakar ki da ya dauka kar kiyi masa rashin mutunci, kuma kada
ya sake ta6a maki kayanki ko da kuwa a titi kika yar don baki aikesa ba" Nihad dai
ta rasa abun cewa tunani iri iri ke yawo a ranta, Husnah ta kyabe baki tace "Ni dai
ki adana min prophylactics din nan foreign ne ba na kasar nan bane kuma tsada ke
garesu, Codeine din kuma shi ma nasan ba kya sha, kar ki je ki xubar ki adana mana
gaskiya" Tashi Nihad tayi ta bar mata wajen ta koma seat din baya abun duniya ya
isheta, yanxu mutumin nan duk ya ga abinda Husnah ta saka mata a jaka? To amma ya
ma yi mugun rainata gaskiya, waye shi da har xai bincika mata jakarta?? A daddafe
Nihad ta yi lectures daya tace xata tafi gida, Husnah tace "Ke don Allah ki saki
ranki, ko Abba ne ya ga jakar nan ya dauka ya bincika ai sai haka, me xai dameki
akan wani shegen driver dinku ya bude jakar ki? Ae rashin mutunci mafi muni xaki
masa idan kin koma gida anjima, ni abinda ya fi damu na ma wayarki ne wllh, don
matsiyacin sai ya iya dauka yace xai je ya siyar bai san wayar nan sai ta siye duk
yan kauyensu ba, yanxu kawai ki xo mu je police station, cikin lokaci kalilan xa
ayi tracking" Nihad ta zaro ido tace "In tona ma kaina asiri kenan, kin zata na
gaya ma kowa cewar na yarda jaka da waya a ciki? To har Nihal bata sani ba" Husnah
tace "In kince ayi cikin sirri babu tonon asiri ai sai ayi hakan, duk fa mutanena
ne, amma wllh so nake a walakanta sa idan aka ga wayar a wajensa, a nakada masa
shegen duka" Nihad tace "Husnah bari in je gida ko xan ji saukin abinda ke damuna,
i can't endure anymore" Husnah ta ta6e baki tace "Wllh kina da sa ma kai damuwa,
duk ki bada space din da lamarin driver xai dinga damunki haka, to wai shi wannan
driver din daga ina ya xo yake abu isa isa da gadara haka?" Mikewa Nihad tayi tace
"Duk yanda ake ciki xan kiraki da wayar Nihal ai tana da number ki" Daga haka ta
fice daga hall din, tun da ta fara school din bata ta6a trekking da kafafuwanta har
bakin titi ba sai yau, haka nan ta tsayar da adaidaita shi ma xata iya kirga iya
sau nawa ta hau sa a rayuwarta, suna isa gida ta sauka ta bude jakarta ta basa kudi
sannan ta shiga gidan, Aminu ne kawai bakin gate, ta ɗan bi compound din da kallo
sai kuma tayi kasa da murya tace "Aminu baka tambayar min driver din can ko ya ga
jakata ba kuma?" Aminu yace "Anya, don ina da yakini da ya gani xai nuna min, ai
shi mutum ne me gaskiya da amana" Ta wani galla masa harara tace "Dallah Malam rufe
min baki, duka duka kwananku nawa tare xaka san yana da gaskiya da amana, ashe kai
dolo ne ma ban sani ba? To bari ka ji wayata ce ta kusan miliyan daya da rabi a
jakar nan" Driver ya gwalo ido yace "Subhanallahi, subhanallahi...." Nihad ta saci
kallon wanda ke tahowa ganin driver din ne ta daure fuska ta juya ta nufi cikin
gida da sauri, xaunawa Khalil yayi gefen Aminu ganin yanda yake
zaro ido kamar mara gaskiya yace "Me ya faru kake buda ido haka" Aminu yace "Ba
nace maka ta yarda jakarta ba daxu har tana tambayata ko na gani, to wllh wai har
da wayarta na miliyan biyu da rabi a cikin jakar" Khalil ya ciro karamar wayarsa
yace "To ta huta..." Aminu yace "Atoh dai, Ta kuwa huta wllh, don yau tana sa uban
a gaba ya siya mata sabo wallahi sai ya siya, sai dai uwarta ta hana amma tsaf in
dai ita ce xai siya mata, kai kaji waya har miliyan uku, ni yanxu na samu irin
kudin nan ai kauye xan koma in tada gini malam, inci me kyau in sha me kyau, sannan
in kara mata biyu...." Khalil na kallonsa yace "Haba?" Aminu yace "Wllh tllh,
albashin namu fa Hajiya ke amsowa a wajensa ta bamu, Ni dai ban san ko nawa yake
bata ba amma dubu 50 50 take bamu, kuma da farkon xuwana akwai wani lkcn da ya ta6a
bani da kansa wllh dubu 70 ya bani, to kilan dai har da kyautatawa ce irin tasa ban
dae sani ba" Khalil dae bai ce masa komai ba. Nihad na shiga cikin parlor ta tafi
dakinta direct, xaunawa tayi gefen gado ta rafka tagumi abun duniya ya isheta, tun
da shegen mutumin nan ya xo gidan nan bata da kwanciyar hankali, bude kofar dakin
aka yi Nihal ta shigo da sallama, Nihad ta daga kai tana kallonta, Nihal ta karaso
ta xauna gefenta tace "Amma ba ki jira ku gama lectures din yau ba kika taho ko"
Nihad ta yatsine fuska tace "I am tired, kawai shine na dawo" Nihal tace "Toh ki
kwanta ki huta, xuwa yamma sai ki rakani shopping din, kinsan gobe sunday xan tafi
fa" Nihad tace "Wa xai kai ki shopping din??" Nihal tace "Khalil" Nihad ta juya ido
tace "Waye haka?" Nihal tace "Driver..." Nihad ta bude baki ta rike ha6a tace "Wai
khalil? Shi uban wa ya basa wannan suna yana driver? Ni fa na xata kinyi wani
saurayi ne Khalil ban sani ba, shi driver din ne yace maki sunansa khalil?" Nihal
dai kallonta kawai take, Nihad ta gyada kai tace "Tabdi, ana iskanci a duniya, shi
yasan ma'anar Khalil din ma kuwa?? Yau naga mutumi da karfin hali, ke kuma wawuya
shine kika yarda sunansa Khalil, to wllh karya yake ba abinda ya hadasa da wannan
sunan" Nihal tace "To ko ma dai meye sunan Abbanmu garesa, ko so kike in kira sunan
Abba gatsau?" Nihad tace "Toh meye don kin kira tunda ba sunan Abban kika kira ba?
Meye don kin ce masa Ibrahim ba shine sunan nasa ba? Wato dai ke kika makala masa
khalil din kenan?" Nihal tace "Aa, yace haka ake kiransa dama, ni bani na sa masa
ba" Nihad ta bude baki tace "Ji shegen karya, to karya yake munafuki, uban wa ke ce
masa haka? Amma fa mutumin nan yayi mugun raina maki wayo ma dai, a kauye wa yasan
wani khalil, dama Halilu yace shine xan yarda, to wai tsaya ma tukun, fira ku ke
har yake gaya maki sunansa khalil??" Mikewa Nihal tayi tace "Woo na gaji da
question and answer din nan, Ko ma meye sunansa ba abu bane da za mu tsaya muna
bata lkci akai, ni dai anjima ki shirya mu je Sahad store din" Nihad tace "Allah ya
kiyaye in dai can xaki wllh baxan je ba, ga wajaje irinsu wellcare kice min Sahad,
ai kowa da kowa ke xuwa Sahad" Nihal ta juya ta kalleta, sai kuma ta girgiza kai
kawai ta fita daga dakin. Nihad ta rike ha6a tace "Ji maye wai khalil, shi a lallai
ya xo gidan masu kudi bari ya maida sunansa irin na yan gayu wai khalil, aa Khalo
ba khalil ba" Ta ja tsaki ta mike ta shige bandaki. Ta a fitowa ta koma gefen gado
da take xaune ta xauna, tunani ta shiga yi a ranta, to ko dai taje can chalet din
da kanta ta duba jakarta ne? Ta kalli agogo lkci daya ta mike ta fito main parlor
Umma tace "Aa har kin dawo er baba" Nihad ta gaisheta sannan ta fita balcony har
sannan taga yana xaune tare da Aminu a bakin gate, komawa ciki tayi ta shiga
kitchen sannan ta bude kofar kitchen din da xai sada ka da back yard din gidan
wanda ta nan ma xaka iya xagawa har xuwa Chalet, ganin yanda Hafsah ke kallonta ta
sha kunu tace "Ya dai da kallo haka ke kuma?" Hafsah ta kauda kanta, Nihad ta fita
da sauri ta xaga ta baya sai Chalet, bata ga takalmin kowa a bakin kofar ba alamar
su Isiyan ma duk basa nan kenan, a hankali ta bude kofar tana leka parlon sannan ta
shiga, da sauri sauri ta fara dudduba parlon, har xuwa dining area bata ga alamar
jakarta ba, har bandakin dake parlon sai da ta bude, wanda sai da ta kusa amai, ta
kullo da sauri tana yatsina fuska ta yi hanyar dakunan chalet din, duk dakuna biyun
dake a bude sai da shiga tana tottoshe hancinta tsabar tsami da doyi, na ta bincika
kaf Ghana must go da ta gani a dakunan amma bata ga jakarta ba, dakin da khalil ke
ciki ta murda ta ji a kulle, to ko dai nan dakin aka ajiye jakar nata shine har da
kullewa da makulli, tunanin inda xata fara nemo spare key ta shiga yi, can ta zare
key din dake jikin kofar su Isiya ta juya ta fita da sauri ta xaga ta koma kitchen,
sai da ta wanke hannunta da morning fresh ta hada har key din tana yatsina fuska
sannan ta shigo parlor, har wani tashi taji xuciyarta ke yi sbda warin da ta dinga
inhaling, kazami irin wannan har shi xai takura mata a gidan nan ya dinga shiga
gonarta, dubi wajen da suke kwana wanda ita ko pig take rearing baxata bari yayi
rayuwa a irin wannan kazantaccen wajen ba, tana wannan tunanin ta faki idon Umma
dake waya ta shige bangaren Abbanta, direct dakinsa ta wuce bayan ta shiga parlor,
nan ta hau bude duk wani drawer da ke dakin, a bedside drawer ne ta ga bunches of
spare keys na gidan, tayi murmushi ta kalli na hannunta sannan ta hau duba irinsa,
kaf irinsu guda uku dake wajen duk sai da ta dauka incase of necessity sannan ta
mayar da drawer din ta kulle ta mike ta fice daga dakin, kitchen ta sake bi ta xaga
xuwa Chalet din, da sauri ta shiga ciki ta nufi hanyar rooms din, dakin dake kulle
tayi facing, ta hau gwada makullen hannunta da sauri da sauri, lkci daya ta bude
dakin, wani farin ciki ne ya lullubeta, ta shige ciki ta kulle tana bin ko ina da
kallo gabanta na faduwa? Banda kamshi babu abinda ke tashi a dakin, rigarsa da ta
gani saman gado ya sa ta gane shine a dakin, rike ha6a tayi.... to gidan uban wa ya
samo wannan turaren da ya xuba a dakin haka, bata daina bin dakin da kallo ba ta
karasa middle of the room, the room look so different kamar ba a chalet din ba,
babu tarkace da kaya kamar irin na su isiya sannan everywhere looks so neat and
tidy, ta kyabe baki without bothering ta hau yin abinda ya kai ta dakin, Duvet ta
gani kamar an rufe abu da shi ta tafi da sauri ta daga sai ga jakarta a ajiye saman
gadon, xaro ido tayi wani farin ciki ya lullubeta, ta bude jakar tana bincikawa da
sauri, banda abubuwan da Husnah ta xuba mata a jakan sai nata tarkacen bata ga
alamar wayarta a ciki ba, nan kuma ta marairaice tana bin dakin da kallo, a ina to
ya ajiye mata wayar?? Sake jakar tayi ta nufi tasa jakar kayan dake dakin, sai bin
jakan take da kallo kafin ta durkusa ta xuge zip din, ko karasa bude zip din bata
yi ba tayi ido hudu da wayarta, babu bata lkci ta dauka, dai dai nan kuma aka bude
kofar dakin, tsabar rudewa da tsorata da tayi bata san sanda ta mike ta saki wayar
jikinta na rawa tace "Wayyoo... Innalillahi wa inna ilaihi raji'un"

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

By _Khaleesat Haiydar_✍🏻

12.....
Tsaye Khalil yayi bakin kofa yana kallonta with a weird facial expression, bata
sake yarda sun hada ido ba banda faduwa babu abinda gabanta yake, sai kuma ta hade
rai xata durkusa ta dau wayarta da ya fada saman jakar, yayi hanzarin shiga cikin
dakin ya sa kafa yayi changing position din jakar yana kallonta, tana ganin haka ta
bi jakar cike da tsiwa tace "Wai kai yaushe na fara wasa da kai a gidan nan ne da
xaka dinga raina ni haka? ina ruwanka da kayana ko a saman titi na jefar da xaka
ta6a min, how dare you?" Tana fadin haka ta ja tsaki ta kara dukawa zata dau wayar,
ya dauke jakar a wajen, buda baki tayi tana kallonsa da mamaki, sai kuma ta nufesa
da nufin cakumosa yanda ta saba amma ganin kallon da yake mata sai kawai ta tsaya
tana harararsa, cike da rashin kunya tace "Wallahi idan baka mika min wayata a
dakin nan ba xan maka sharrin da har abada baxa ka mance ba, ka bani wayata
nace..." cikin kakkausar murya yace "Idan kin fasa..." Ta kankance ido tana
kallonsa da mamaki jin abinda yace, ji take kamar ta kifa masa mari, da a waje ne
wllh ba abinda xai hanata marin sa, Yana mata wani kallo ya ajiye jakar a gabanta
yace "Idan kin isa ki ta6a" A fusace tace "Toh wai kai idan kana sata sai ka rasa
wayar warce xaka sata sai tawa a gidan nan? A kaina satarka xai kare? Idan na ta6a
uban me ka isa ka min? Wllh sai na ma sharrin da baxaka ta6a mantawa da ni ba" Duk
wannan babatun da take bata yarda ta ta6a jakar ba, banda faduwa kuma babu abinda
gabanta yake barin da ta ga irin kallon da yake mata, jakarta dake gefen gado ya
nufa ya dauka ya dawo inda take ya jefa mata a gabanta yace "Dauki ki fita...
Abubuwanki dake ciki xa su fi wayar muhimmanci gare ki" Kamar xata yi kuka tace "Ni
wllh ka bani wayata kar in hadaka da Abbana da yayana" Da Husky voice yace "Dauka
jakar ki nace ki fita" Bata ce masa komai ba ta tafi ta dau jakarta tana jin kamar
ta fashe da kuka, ta nufi kofar tana tafiya a hankali, ta gefen ido ta saci
kallonsa sae kuma ta dawo da gudu ta fixgo jakarsa ta nufi kofa a guje kamar an
aikota, tana shiga parlorn plate din da su Isiya suka ci abinci suka bari a wajen
ta take sai da ta tafi tsuuu kamar xata tashi sama sae ga ta a kasa timm, jakarsa
kuma yayi can hanyar kofar fita, nata kuma yayi wajen Tv, gwalo ido tayi tana
numfashin wahala da kyar tace "Wayyoo Abbana, wayyo bayana ya karye" tsaye yayi
bakin corridor din dakunan ya rungume hannunsa ya jingina da pillar din wajen yana
kallonta irin dai dai kenan, ta fashe da matsanancin kuka tana jujjuya kanta tace
"Wayyo Allah na a zo a taimakeni bayana ya karye, baxan iya tashi ba" karasowa
cikin parlon yayi zai tafi ya dau jakarsa, tana ganin haka ta yunkura ta tashi ta
nufi kofar da gudu ta figi jakar tasa, a dari da sittin ta fice ko bin ta kan nata
jakar bata yi ba a parlon, bai san sanda ya bi ta ba, tuni har ta dau hanyar
kitchen yace "Keeeee dau wayarki ki ajiye min jakata" haba da ya kara tuna valuable
dinsa dake jakar kawai ya bi ta, tana isa kofar kitchen ta murda ta ji sa a kulle,
ta gwalo ido tace "Na shiga uku, Hafsahhhh uban wa yace ki kulle" tana ganin ya
nufota kawai ta ajiye jakar a kasa tana kallonsa xuciyarta na bugawa, yana isa
gabanta ya duka ya dau jakarsa sannan ya bar wajen. Nihad bata san sanda ta fashe
da kuka ta sulale wajen ba tana cewa "Wallahi sai na maka rashin mutunci a gidan
nan, kawai mutum kamar maye ya sa min ido a gidan ubana duk ya bi ya takura ni" Sai
kuma ta mike ta xaga ta shiga cikin gidan, Umma dake parlor ta kalleta daga sama
har kasa tace "Lafiya?" Nihad tace "Ina Hafsah?" Sai ga Hafsah ta fito daga
bangaren Mumy, Nihad ta nufeta tana huci tace "Ke mahaukaciyar wace gari ce da xaki
rufe min kofa bayan kinsan na fita?" Hafsah tace "Ayya kiyi hakuri wllh ban san
baki shigo ba, na xata kin bi ta gaba kin shigo" Nihad ta mata tsawa tace "Aa ta
hancinki na bi na shigo" Tsaki ta ja ta juya ta bar wajen kamar xata tashi sama.
Umma dai ta bi ta da ido, direct dakin Nihal ta tafi, Nihal har ta gama shiryawa
tana kallon Nihad tace "Ohk baxa ki rakani din ba" Nihad tace "Nihal idan na fara
yi ma wancan driver din rashin mutunci ke ce ta farko da ke fara jin haushi, wllh
duk abinda na masa kar ki ga laifi na, don haka tun wuri ki je ki samesa ki amso
min wayata da jakata dake wajensa" Nihal dake kallonta with confusion tace "Me ya
kai jakarki da waya wajensa kuma?" Nihad tace "How will i even know?? I mistakenly
dropped my bag at the gate jiya, ko sani ma ban yi ba...." Nihal ta katseta tace
"How will u mistakenly drop a whole bag not even purse Nihad?" Nihad ta hade rai
tace "And that is none of ur concern, kawai abinda nace maki shine ki amsar min
kayana a wajensa kar in fara rashin mutunci na, don wllh idan bai yi hankali ba sai
na gaura masa mari kuma ba abinda xai faru" Dariya ta ba Nihal, sai dai bata yi ba,
tace "Ke yanxu wa yace maki shi ya dau maki jaka?" Nihad tayi saurin cewa "Aminu ne
ya gaya min, kuma don't forget wayana na ciki" Nihal tace "Amma ai ba yaki bane, xa
ki iya samunsa politely ki tambayesa jakar, na tabbata xai baki" Nihad ta yi wani
dariyar rainin hankali tace "Koh? To sannu, shi drivern xan je in sama politely
sbda ina tsoronsa ko? To abinda baki sani ba, Aminu ce min yayi satar jakar yayi
niyyarsa yayi shiru, bai kuma san Aminun ya gansa ba, to idan yana sata sai ya fara
ta kan kayana a gidan nan? Kaii amma mutumin nan ya kara bani tsoro wllh" Nihal ta
dau karamin handbag dinta tace "Yamma na yi, xan tafi shopping" Nihad ta hade rai
tace "Ohk baxan raka ki ba kenan?" Nihal tace "Oh na xata kince ai baxa ki ba"
Nihad ta harareta tace "Yaushe nace maki haka?" Nihal tace "Toh dauko hijab dinki
mu tafi" Nihad bata ce komai ba ta juya ta fita, Nihal ta bi bayanta, babban
dalilin da yasa Nihad xata shopping din nan kawai don Nihal ta amsar mata jakarta
da wayanta gun khalil, Nihal na fitowa parlor Umma tace "Har kin shirya auta?"
Nihal tace "Eh na shirya" Umma tace "To kar dai ki manta turarena" Nihal tace "Toh
baxan manta ba" Umma tace "To ya kika tsaya, ga yamma na yi" Nihal tace "Ina jiran
Nihad" Umma ta kalleta tace "Nihad? ita tace maki xata?" Nihal tace "Eh" Umma tace
"Ke da xaki yi maza kije kiyi abinda xai kai ki ki dawo, meye kuma sai kun yi zuga
kamar yan matan amare Nihal" Nihal tace "Aa nafi son mu je tare" Umma tayi shiru
bata kuma cewa komai ba, Nihad ta fito sanye da Hijab ita ma, Tana kallon Nihal
tace "Mu je" Nihal ta kalli Umma tace "Sai mun dawo" Umma tace "Allah ya tsare"
Nihad tace "Umma xa a taho maki da wani abu ne?" Umma tace "Aa babu komai, Allahj
ya tsare" Fita suka yi daga parlon, Nihad ta hade rai ganin khalil da Aminu, Nihal
ta nufesu tana kallon khalil tace "Idan baka yin komai xa mu iya tafiya yanxu?" Ya
mike yace "Ohk" Motar ya nufa, Nihad ta bi sa da wani shegen kallon tsana, duk
Aminu na lura da ita, Nihal ta bude front seat xata shiga Nihad tayi saurin cewa
"Me xa ki yi a gaba ke kuma?" Nihal tace "I prefer seating here" Nihad ta ja tsaki
ta bude back seat ta xauna, Tuni mai gadi ya bude gate din suka fita compound din,
Khalil yace "Wani supermarket din xa mu Hajiya?" Nihal tace "Ko wanda ya fi kusa"
Nihad tace "Kai Malam mu tafi Sufi Mart" Khalil dai driving dinsa kawai yake, next
thing kawai Nihad taga ya dau hanyar wani store din daban, ta kankance ido tace
"Wai kai kurma ne baka ji inda nace ka kai mu bane?" Driving dinsa kawai yake kamar
bai san da shi take ba, Nihal ta juya ta kalleta tace "But ai duk daya ne Nihad"
Nihad ta galla mata harara tace "To da ke nake ke kuma?" Nihal ta dauke kai bata ce
mata komai ba, A Danja Khalil ya sauke glass din motar ya amshi facemask hannun
wani yaro sannan ya basa kudi ya kulle glass din, Nihad ta kyabe baki, sai kuma ta
ja tsaki ba dai wanda yace mata komai a motar. Parking Khalil yayi a inda aka
tanadar don parking a harabar Supermarket din, ya kashe motar yana kallon Nihal,
tace "Baxa mu dade ba in sha Allah" Nihad tace "Toh da kike cewa haka wa xai dauko
kayan idan mun gama siyayyan? Ai sauka shi ma xae yi daga motar ya kwaso kaya ba
wai zama xae yi a driver seat ba" Nihal ta kalleta tace "But the staff in there
will do that, it's not necessary" Nihad tace "Wallahi u have a very big problem,
what is then the use of him? Why then did he have to drive us here if he can't come
out and help? Sannu good Samaritan" Nihal ta kalli khalil tace "Sae mun fito" Yace
"Toh a fito lafiya" Ta bude motar xata sauka yace "Amma bari in sa maki number ta
idan kin gama sae ki kirani in dau maki kayan" Tace "Akwai masu daukan kayan a ciki
kar ka damu" yace "Toh idan da wani abun sae ki kirani" Tace "Toh" wayarta ta mika
masa yayi dialing number din sa sannan ya mika mata, amsa tayi ta kira number,
karamar wayar dake aljihunsa ya fara ring, tace "Nagode" daga haka ta bude motar ta
sauka, Nihad dake ta kallon ikon Allah ta ja tsaki me tsayi sannan ta sauka, ko
barin wajen motar basu yi ba tace "Me ye na wani exchanging digit da driver idan ba
kaskantar da kai ba Nihal? Me yasa ke kin fiye over sabi a rayuwarki? Ni ban san me
yasa ke da Mumy ku ke yin haka ba wllh" Nihal taki tanka mata, Nihad tace "Though
wannan ba damuwata bace, my problem is ban ji kin masa maganar jakata da wayana
ba?" Nihal tace "Xan yi" Suna shiga mall din, Nihal ta fara daukan abubuwan da ta
xo siya tana xubawa a cart Nihad na tura mata cart din, duk inda suka gifta sae an
kallesu don babu wanda bazai ce su ba yan biyu bane, they look so cute, beautiful
and adorable, kawai dai Nihad ta fi Nihal haske da tsayin hanci with more cute
lips, ita kuma Nihal ta fi Nihad cika, though she isn't chubby but ta fi Nihad
warce iska me karfi idan aka yi xae iya tafiya da ita... Lol, tsayinsu daya haka ma
shape din large eyes dinsu, sae dai kana kallonsu kasan Nihad tafi Nihal wayewa
nesa ba kusa ba, ganin Nihad isn't taking anything Nihal tace "But kince kema xa
kiyi shopping kin fasa ne?" Nihad ta yatsina fuska tace "I won't shop here" Nihal
bata kuma ce mata komai ba, har ta gama
daukan duk abinda xata bukata a makaranta, sannan ta dau ma Umma turarurrukan da
tace, wani tsadadden turare da ta san Nihad na so ta daukar mata, Nihad ta amsa
tace "Thank you" Daga haka ta saka shi cikin cart din, Nihal ta dau wayarta tayi
dialing number da Khalil ya sa mata with the intention of asking him a question,
can kuma dae kawai ta katse ta fasa kiran nasa sbda Nihad dake ta kallonta, wasu
turarurrukan biyu ta deba ta sa a cart sannan tace "Shikenan na gama" Nihad ta tura
cart din suka nufi counter. Suna tsaye counter din Nihad tace "Na manta xan dau
Sanitary Napkin" Daga haka ta juya zuwa in da zata dauka, khalil ya shigo cikin
mall din with facemask, yana hango Nihal a counter ya nufi wajen yana kallonta yace
"Naga kiran ki..." Nihal tace "Oh bansan ya shiga ba" Yace "Ohk, sun gama in dau
kayan?" Xata yi magana kawai wata yarinya kamar balarabiya ta nufosu tana kallon
Khalil closely tace "KJay?" Juyawa yayi da sauri, Ta wara ido kafin ta ce komai
yace "Ohh Nadiya, daga ina haka?" Ta kyalkyale da dariya tace "How wonderful i
recognized u upon the nose mask KJay..." Ya kalli Nihal da sauri yace "erm, yi
hakuri don Allah minti daya..." kawai yace "Mu yi magana a waje Nadiya" yana fadin
haka ya bar wajen da sauri, Sai a sannan Nadiyar ta kalli Nihal dake ta kallonta
daga sama har kasa, Nadiya ta daga mata hannu tace "Hi" Nihal tayi murmushi ta daga
mata hannu ita ma, juyawa tayi ta bi bayan khalil da har ya fita mall din, Nihal ta
bi ta da kallo, har gadon baya ta saki dogon baƙin gashin kanta, daga ganinta kasan
half cast ce, sae ga Nihad ta ajiye Sanitary Napkin din a kan counter, tana kallon
Nihal sai kuma ta kalli inda take ta kallo amma tuni Nadiya ta fita daga mall din,
Nihad tace "What are u staring at?" Nihal ta dauke kanta da sauri tace "Nothing"
ma'aikatan wajen ne suka kwasar masu kayan xuwa mota bayan an biya kudin kayan,
Khalil na jingine jikin mota ya rungume hannunsa, ganin sun fito ya xaga ya bude
booth din motar, wanda ya tayasu fito da kayan ya shigar cikin booth, Nihal ta bude
handbag dinta ta dau dari biyar ta basa, yayi mata godiya sannan ya wuce, tuni
Nihad ta shige bayan mota, Nihal ta xauna gaban motar, ya tada motar suka bar
shopping mall din. Tunani iri iri ke yawo a xuciyar Nihal, she can't even think
straight, Nihad kuma ta kasa kunne taji Nihal tayi ma Khalil maganar wayarta amma
shiru, har ta shirya rashin mutuncin da xa tayi mata suna shiga gida don dab suke
da isa gidan kawai ta ga Nihal ta kallesa tace "Ina son xan maka magana don Allah"
Bai kalleta ba idonsa na kan titi yace "Toh ina jin ki Hajiya" Ina a polite state
tace "Jakar Nihad yana wajenka ko?" Yayi ɗan yi shiru kamar baxai ce komai ba,
Nihal dai kallonsa kawai take, sai kuma yace "Eh yana wajena" Tace "Toh xaka bani
don Allah idan mun isa gida" Yace "Toh ba damuwa, in sha Allah" Nihad ta galla masa
wani tsinannen harara ta kauda kai, da yace baxai bada ba ya gani mana, suna isa
gida yayi parking Nihad ta bude motar ta sauka ta tsaya nan parking space babu yabo
babu fallasa tana jiran jakarta. Nihal ta sauka ya bude mata booth ya saukar da
kayan kasa, xagawa tayi xuwa gun Nihad tace "Ki tafi ciki, ai xan amsar maki" Nihad
tace "Nooo, Baxan tafi ba, ina nan ina jira" Khalil dake jin abinda tace, ya dai
kwashi kayan Nihal gaba daya ya kai mata can bakin kofar shiga main building din
gidan ya ajiye, Nihal na tsaye har ya dawo yana kallonta yace "Anjima da daddare
xan baki jakar idan na shiga can bangaren kenan" Nihad tace "Ban gane anjima da
daddare ba, kai ko kunyan sata baka ji ba a ranka, to tun wuri ka shiga yanxun nan
ka fito min da jakata kar in tara maka mutanen gidan nan, wallahi rashin mutunci
xan maka don ma kaji in gaya maka" Khalil ya kalleta yace "Toh" Daga haka ya tafi
wajen mai gadi yayi xamansa, a fusace Nihad ta kalli Nihal tace "Kina dai gani ko,
wllh sai na nuna masa wacece ni yau kar ya fito min da jakata" Nihal tace "Ba sai
da nace ki shiga ciki xan taho maki da shi ba, toh ai gashi nan kin ji" Nihad tace
"Na ji me? Ai jakata baxata kara minti biyar a hannunsa ba, bari ya gani" Tana
fadin haka ta juya fuuu ta wuce cikin gida, ita damuwarta kar ya ba Nihal jakar ta
bude taga kayan Husnah dake ciki, Nihal ta nufe Khalil dake kusa da mai gadi ta
mika masa ledan hannunta tace "Gashi nan na daukar maka kai ma, amma don Allah kayi
hakuri ka bamu jakar yanxu" Yana kallon ledan yace "Nagode sosai Hajiya, Allah ya
saka da alkhairi.... Bari in dauko maki jakar" Daga haka ya mike ya nufi chalet, ta
bi sa da kallo sannan ta bi bayansa, da ya lura tana biye da shi, sai yayi slowing
pace dinsa, tana isa kusa da shi tace "Ina son xan maka tambaya" suna ci gaba da
tafiya ba tare da ya kalleta ba yace "Ohk ina sauraronki?" Tace "Tell me... who are
you?" Ya ɗan yi jim sai kuma yayi saurin cewa "Ban gane abinda kike nufi ba" Tace
"Nasan ka gane" Yace "Da gaske ban gane ba" suna isa Chalet din kafin tace komai,
yayi maza yace "Ina xuwa in dauko jajad yanxu" daga haka ya shiga ciki ta bi sa da
kallo, ba a dau lkci ba ya dawo rike da jakar Nihad, a bude zip din jakar yake, ya
mika ma Nihal ta amsa, babu abinda idonta ya fara cin karo da sai kwalban Codeine
da prophylactics da ke saman jakar, lkci daya ta rude apart from being shock, bata
san sanda ta rungume jakar ta juya da sauri xata bar wajen ba, yace "Ga wayarta"
Nihal ta juyo da kyar amma ta kasa barin su hada ido, ta dai amshi wayar da yake
mika mata ta juya ta bar wajen tana tafiya da sauri, tana shiga gida direct dakin
Nihad ta wuce, Nihad xata fito daga dakin kenan suka kusa cin karo, Nihad ta koma
baya, Nihal ta shiga dakin ta jefa mata jakar a kasa tana girgiza kai sadly tace
"Nihad meye wannan a cikin jakar ki??" Nihad ta kalli jakar lkci daya gabanta ya
fadi, Nihal ta karasa cikin dakin ta xauna gefen gado ta dafe kanta, Nihad dai sai
kallon jakarta take tana tunanin abinda xata ma khalil taji sanyi a ranta, ko daxu
da ta bude jakar bata ga abubuwan nan a saman jakar ba, wato shi ya daura su saman
jakar ya bar zip a bude don Nihal ta gani, Bayan kusan minti daya Nihad ta kalli
Nihal, hawaye ta gani idonta, Nihad tace "Look Nihal wllh wllh ba kayana bane na
Husnah ne, haba don't u trust me?? kema kinsan i can neva posses such stuffs, i
swear to God na Husnah ne, shi kuma munafuki algungumin da ya daura a saman jakar
ya jira ya ga abinda xai faru da shi a gidan nan" Tana fadin haka ta durkusa ta hau
tattara abubuwan dake cikin jakar ta kulle, Nihal dai bata ce komai ba ta mike a
sanyaye ta ajiye mata wayarta a gefen gado sannan ta fice daga dakin.

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

13.....

Zaunawa Nihad tayi ta dau wayarta ta bude, nan ta ga miss calls da ya wuce misali,
ta shiga call logs ta ga kiran Aliyu guda daya wanda yayi mata tun da safe, bata
san sanda ta sauke wani ajiyar xuciya ba, so he did call her, wani Murmushi tayi,
tayi dialing number sae da ya kusa katsewa ya daga, tayi kasa da murya tayi masa
sallama ya amsa, jin yayi shiru a hankali tace "Can you hear me?" Yace "Yea ina ji"
tace "You called da safe, bani da lafiya shi yasa ban samu dagawa ba" Yace "Baki da
lafiya? Me ya sameki?" Ta langwabar da murya tace "Na tashi da xaxxabi ne" Yace
"Subhanallah, how are u feeling now?" Tace "Da sauki shi yasa har na samu na
kiraka" Yace "Since when were u sick?" Tace "2 days ago" Ya dan yi shiru, sai kuma
yace "I am sorry, Allah Ubangiji ya baki lafiya" Ta lumshe ido tace "Ameen" Yace
"Hope kina iya cin abinci?" Tace "Ehh daxu na samu na ci" Yace "Get well soon dear"
Ta dan yi shiru sai kuma tace "Kayi hakuri da abinda ya faru few days back" Yace
"Nihad" Tace "Na'am" yace "Daga ina akayi employing driver din nan?" Tace "Wllh ban
sani ba i just saw him over night a gidan" Yace "Ya sunansa?" Ta gyara xama tace
"Halilu" Yace "Good, yana gidan har yanxu ko?" Tace "Yana nan wllh, rashin mutunci
kuwa sae abinda yayi gaba, i have just decided in dinga hawa adaidaita from
henceforth idan xan je makaranta" yace "You don't worry, i will bring an end to
everything" tayi wani Murmushi tace "Trust u dear" Yace "A gidan yake permanently
ko yana xuwa ya tafi ne?" Tace "Aa a nan yake permanently ba inda yake xuwa" Yace
"Ohk, gobe xan shigo kano in sha Allah" tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen, i
will call u back later" Tana Murmushi tace "Alright dear" daga haka ya katse wayar
ta lumshe ido ta bude cike da farin ciki, at last they will bring an end to this
forsaken driver, tasan tun da har ya shiga trap din Aliyu kuma ya shiga uku. Nihal
na ta xaune parlor a dining area har kusan karfe tara na dare, she her self don't
even know what exactly she is sitting down there for, har Umma sai da tayi mata
magana ta tafi ta kwanta ita da xata yi tafiya gobe, amma bata bar wajen ba, Farooq
ya shigo parlon ganin ita kadai yace "Me kike yi a nan?" Ta kirkiri murmushi tace
"Ba komai kawai ina duba waya ne" Yace "Ohk, xo ki amshi sako ki ba Aminu" Tace
"Toh" Mikewa tayi ta bi bayansa har xuwa bedroom dinsa ya dauko wani takalminsa ya
mika mata yace "ki kai masa" Ta amsa tace "Toh" Yace "Gobe da yaushe xa ki tafi?"
Tace "Da safe in sha Allah" Yace "Ohk" Juyawa tayi ta bar wajen, tana fitowa
compound ta tafi bakin gate inda Aminu yake, Bata ga Aminu a wajen ba sai khalil,
yana ganinta yace "Barka da yamma Hajiya" Ta gyada kai kawai tace "Ina Aminu?" Yace
"Ya ɗan fita xai dawo yanxu" Tace "Ohk, ba nisa yayi ba?" Yace "Ehh ban san ko yyi
nisa ba" Ta koma gefe ta tsaya tace "Ok i will wait" shi dai Khalil bai ce komai
ba, but from all indication he was uncomfortable with her by his side, bayan kusan
minti daya tayi breaking silent din tace "Daxu na maka tambaya baka ce min komai
ba" ya ki kallonta yace "Ohh, yi hakuri Hajiya wani tambaya kenan?" Tace "Kawai
cewa nayi, xan iya sanin ko kai waye?" Yayi shiru na few seconds, sai kuma yace
"Ohk amma ina son ya kasance tsakanina da ke, don ba kowa nake ba labarina ba"
Nihal tace "In sha Allah nayi alkawarin rike maka sirrin ka" Murmushi yayi ya gyara
xama yace "Kinyi alkawari har yar uwarki baxa ki gaya ma" Nihal tace "Nayi
alkawari" Yayi kasa da murya yace "Kamar yanda na sanar maki a baya, ni sunana
Ibrahim, amma a kan kirani da Khalil, ni haifaffen garin getso ne...." Ta katse sa
tace "Garinsu Malam Habibu?" Yace "Ehh, garinmu daya, har kuma yanxu iyayena na
garin duk da baabata yar Nijar ce, don ta kan daukeni da kannena mu je Nijar a
shekarun baya" Nihal dai tayi shiru bata ce komai ba tana ta kallonsa, ya sosa
kansa yace "Nayi karatun primary, daga bisanni na daura da na sakandari inda na
dakata a aji na uku ban ci gaba ba har yau, Baabata ta saka ni gareji a wancan
lkcn, amma Allah bai yi xan maida hankali in koyi gyaran motar ba, kawai na koma
aikin plumbing tare da wani d'an kanin babana a garin, sai dai ban dau lkci ina
aikin plumber ba kasancewar na iya karatu da rubutu dai dai gwargwado ya sa wani a
garin namu me suna Alhaji Mu'azu ya ajiyeni shagon chemist dinsa ina jire masa
shagon, na kuma fi shekara takwas ina xama a shagon har daga bisanni Allah yayi
masa rasuwa, da farko na samu wani aikin wanki da guga a gidan wani commissioner
nan cikin garin kano, wani yaron me chemist din yayi min hanyar aiki a gidan, to
yarinyar gidan ta kan xauna tare da ni mu yi hira, idan xata yi fita ba me nisa ba
ni take sa in rakata, duk wani aike nata ni ke xuwa, kuma duk abinda aka girka a
gidan da kanta take debo min ta kawo min, tana da kirki ainun, kuma baxan ta6a
mance alkhairinta gareni ba, ita ta karfafa min gwiwa muke turanci tare, wanda
banyi dai dai ba ta gyara min, bata kiran sunana kai tsaye sae dai ta ce min Kay...
Wannan kusancin namu ya sa mahaifiyarta warce 'yar daya daga kasashen larabawa ce
ta tilasta mai gidan sai da ya sallameni, a nata tunanin soyayya muke da
yarinyarta, wanda kuma ba haka bane, sunan yarinyar Nadeeyah... da ita muka hadu a
Supermarket daxu..." Nihal dae kallonsa take ko kiftawa babu, ya shafa kansa yace
"Yauwa abinda na mance ban gaya maki ba shine ina da iyali da yaro daya wanda Allah
yayi ma rasuwa ko wata biyu ba ayi ba yanxu, kuma shekarunsa biyar a duniya ya
rasu" Nihal ta buda ido sosai tana kallonsa with shock, ya sauke kansa daga
kallonta, he was looking sad, a hankali tace "Hasbunallah, Allah ya gafarta masa"
Yace "Ameen, sunan matata Jiddah, wannan dalilin ya sa Nadeeyah kan kirani da
Kay... Wani lkcn kuma ta kirani da KJay, har garinmu na kai ta wajen matata Jiddah"
Nihal dai bata ce komai ba, Khalil yace "Bayan kusan sati uku da sallamata da aka
yi daga gidansu Nadeeyah, shine Habibu yayi min hanyar wannan aikin a nan gidan,
kin ji takaitaccen tarihi na...." Ta daga kai ta kallesa, kallonta yyi jin bata ce
komai ba, a hankali tace "Allah ya taimake mu baki daya" Yace "Ameen" Aminu ne ya
shigo compound din rike da leda, yana ganinta da farko sae da gabansa ya fadi don a
xatonsa Nihad ce, sae ya ga ba ita bace, Aminu ya washe baki yace "Barka da dare
Hajjaju" yana fadin hakan ya shige dakinsa da ledan hannunsa, Khalil yace "Karfe
nawa xa kiyi tafiyar gobe?" Tace "Da safe in sha Allah" Yace "Ohk, ke kadai ce ai
ko?" Ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Aa yawanci tare da Nihad muke tafiya, idan sun
ajiyeni sai su juya" Yace "Ohk" ajiye takalmin hannunta tayi tace "Idan Aminu ya
fito ka basa inji ya Farooq" Yace "To" Tace "Sai da safe" Yace "Allah ya tashe mu
lfya" Juyawa tayi ta nufi cikin gidan ya bi ta da ido letting out a Sigh. Washegari
da safe Khalil ya fito ta dalilin aika Aminu da Abba yayi ya kirasa, A balcony ya
tadda Abba ya gaishesa da ladabi Abba yace "Xaka ajiye Nihal a Zaria, tare xa su
tafi da yar uwarta sai ku dawo tare" Khalil ya sunkuyar da kai yace "Na gane...
Amma sai dai na tashi yau bana jin dadi ranka shi dade" Abba yace "Me ke damunka?"
Khalil yace "Ina jin ko malaria" Abba yace "Ya salam, Allah ya sauwake, baka da net
ne?" Khalil ya girgiza kai yace "Aa bani da" Abba yace "Toh anjima xan baka kudi
kaje ka siya" Khalil yace "Toh nagode Abba" Abba yace "Madallah, Amma ko kai da
Saminu ne ku je asibiti a duba ka yanxu" Khalil yace "Toh in sha Allah" Abba yace
"Kafin ku tafi ka sanar da ni" Yace "Toh nagode" Abba yace "Ba damuwa tunda farooq
na nan sai yaje ya ajiyeta, kaje kawai" Khalil ya sakema Abba godiya sannan ya bar
wajen, da Nihal kadai ce xai kai ta, but kasancewa tare da Nihad ne shi yasa ya
gwammace yace bashi da lafiya, dalilin da yasa ma ya tambayu Nihal jiya kenan ta
sanar masa tare da Nihad ne, tun jiyan kuma yayi deciding he won't be going shi
yasa ya tashi da wannan plan din, he just can't withstand driving that far with
Nihad in the car... Abba na shiga parlor ya ga Nihal har ta fito da jakunkunan
kayanta, yace "Nihal ki jira in yi magana da Farooq ya kai ki, driver yace baya jin
dadi" Shiru Nihal tayi tana kallon Abba, sai kuma ta nemi kujera ta xauna, Abba
kuma ya tafi dakin Farooq, sai ga Nihad ta fito rike da handbag dinta tana kallon
Nihal tace "Ke wai wannan yaron ne xai kai mu har Zaria? Ni gaskiya i can't
withstand seating that long in the car with him, in har da shi ne gwara in fasa
kawai, kar ma yaje da gangan ya kasheni a hanya idan muna dawowa" ko kallonta Nihal
bata yi ba balle ta tanka ta, sai ga Abba ya fito yana kallonsu yace "Ku fita da
kayan Farooq xai kai ku yanxu" Nihad ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Better"
Trolly din Nihal daya ta dauka ta fita waje, tana ta tsaye a bakin motar har Nihal
ta fito tare da Amina dake rike da wani Trolly din, Bayan farooq ya fito duk suka
shiga motar, Mumy na tsaye balcony bayan tayi ma Nihal addu'ar Allah ya kai ta
lafiya Allah ya tsare, Ummu ma na balcony din a tsaye, a duk sanda Nihal xata koma
makaranta sai ta ji kamar xata yi xaxxabi, duk cikin yaranta babu wanda take ji har
ranta kamar Nihal, a haka har farooq ya gama warming motar ya fita, Aminu ya daga
masu hannu yana cewa "Allah ya bada sa'ar karatu, ku kuma Allah ya maido ku gida
lafiya" Nihad da ke xaune back seat ita da Nihal ko kallonsa bata yi ba, Farooq da
Nihal kadai suka amsa da Ameen.... Bayan sun dau hanya wayar Nihal dake jakarta ya
fara ring, Nihad ta juya tana kallonta, bude jakar tayi ta fiddo wayar tana kallon
screen din ta ga Khalil, Nihad ta kikkifta ido don ta kara tabbatar da sunan da ta
gani a jiki, bata san sanda ta bude baki ba don mamaki, Nihal ta daga kiran ta kai
kunne, Dubara Nihad tayi ta matsa dab da ita ko xata ji abinda xai ce, daga daya
bangaren Khalil yace "Kin tashi lafiya Hajiya?" Nihal tace "Alhmdlh, ina kwana?"
Yace "Lafiya, ban samu damar kai ki ba, kuma kin tafi ba mu yi sallama ba, Allah
Ubangiji ya tsare hanya, ya kai ku lafiya, ya baki sa'ar abinda aka
je nema" Ta sauke idonta kasa tace "Ameen nagode" Yace "Sai anjima" Tace "Nagode"
Katse wayar yayi, Nihad ta matsa tana kallonta da kyau tace "Nihal ba driver din
nan bane ya kira ki?" Nihal ta ki cewa komai, Nihad ta saki baki tana kallonta,
Farooq dake jin su yace "Wani Driver?" Da sauri Nihad tace "Ji fa yaya, driver din
gida fa, meye hadinta da shi har ma zai kirata yanxu??" Farooq dai sai kallon Nihal
yake ta madubi, Nihal ta hade rai tace "You have problem Nihad, komai ke sai kin
san yanda kika yi kika canxa masa ma'ana, what's wrong with me having the drivers
number, naga har number Saminu ina da shi me yasa be xama laifi ba? Ke lkcn da
Habibu yake nan baki da numbersa? Waye yafi communicate da Habibu a gidan banda
ke?" Nihad tace "Noo, ae Habibu daban wannan daban, kuma Habibu sai ta kama muke
magana da shi a waya...." A fusace Nihal tace "Toh wannan din ma kamawa yayi muka
yi maganar a waya" Farooq yace "Toh wai ke Nihad ina ruwanki??" Kallonsa Nihad
tayi, lkci daya ta hade rai bata ce komai ba, yace "Ke ce ai kika dau girman kai
kika daura ma kanki but there is nothing wrong to have people that are under you
phone number" All through the journey Nihad bata sake cewa komai ba amma fuskarta a
daure yake. Satan kallon Nihal take taga tana bacci, a hankali ta dauke wayarta
dake kafarta ta bude don ita bata sa password, ta shiga call logs tayi blocking
number Khalil sannan tayi deleting ta mayar mata da wayar ta ajiye. Har Nihad suka
kai Nihal Zaria bata ce ma kowa komai a motar ba, Farooq ya kalleta yace "Sauka ki
kama mata kaya ku shiga hostel" Ta ɗan daure fuska ta bude motar ta sauka, nan ta
taya Nihal suka kwashe kayanta xuwa hostel din, bayan Nihad ta ajiye jakar karshe
ta juya xata wuce Nihal tace "Are u still angry? Toh kiyi hakuri" Nihad ta kalleta
tace "Baxan yi ba, ba dai driver ya fi ni ba" Nihal tayi Murmushi tace "Ya xa ayi
driver ya fi ki, kema kinsan babu wanda ya fi ki a wajena, kiyi hakuri i didn't
mean to make u angry" Nihad ta harareta tace "Kamar da gaske" Rungumeta Nihal tayi
tace "Wllh kema kinsan da gaske nake blood" Nihad tace "Toh shkkn na hkura" Nihal
tace "Toh nagode" a tare suka koma gun mota inda Farooq ke jiran Nihad, Nihad ta
bude jakarta jin wayarta na vibrate, ganin Aliyu ke kiranta ta daga, bayan sun
gaisa yace "Xan shigo kano in the evening, ki turo min address din gidanku" Nihad
ta wara ido tace "Are u coming to our house" Yace "Ki turo ina jira" daga haka ya
katse wayar, Farin ciki ne ya lullubeta, bai ta6a cewa xai je gidansu ba sai yau, a
baya babu yanda bata yi da shi a kan ya xo gidan nasu ba amma sai ya ki, har ta
kagu ta gansu a gida ta tambayi Umma abubuwan da xata dafa masa, nazari ta shiga
yi... or is he coming because of that useless driver?? Ohh God that will be very
great.

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

14.....

Karfe biyu saura Nihad suka iso gida tare da farooq, yana kashe motar ta bude ta
sauka, kallon direction din Mai gadi dake kulle gate tayi bata ga khalil ba, ta
juya ta wuce cikin gida, direct part din Umma ta tafi, Umma dake parlonta tace
"Oyoyo, har kun dawo?" Nihad tace "Ehh Umma, yau dai in gaya maki bata yi kuka ba
da xa ku tafi" Umma tace "Toh ai gwara haka, kukan ba shi da amfani" Nihad ta xauna
gefen Umma tace "Umma guess what?" Umma tace "Aa... ni kinsan i am not a good
guesser, gaya min abinda ya faru daughter" Nihad na Murmushi tace "Umma Aliyu xai
xo gidan nan yau" Shiru Umma tayi tana kallonta babu ko kiftawa, can tace "Wani
Aliyu?" Nihad ta wara ido tace "Aliyu dai Umma" Umma tace "Amma ba kince min ya
daina daga kiranki ba?" Nihad tace "Ehh wllh, kawai sai na ga kiransa jiya Umma, he
called me him self" Umma ta girgiza kai tace "Nihad.... Nihad, bakya ji Nihad, baki
jin magana wllh, na gaya maki ki raba kanki da Aliyun nan kin ki ji, ban san yanda
xan yi da ke ba kuma, Aliyu ba komai xai yi ba illa ya yaudareki ya kama gabansa,
nace ki daina hada kanki da ya yan masu kasar nan, Aliyu ya fi karfinki, ki kula
dai dai ke amma kin ki ji, yaudarar ki kawai yake idan kin bibiya ma an sa masa
rana, su da junansu suke aure basa auren kasa da su" Nihad tayi narai narai da ido
tace "Umma wllh ba yaudarata yake ba, Aliyu yana so na, kuma yace min ina shiga
level 3 xai turo iyayensa wajensu Abba, wllh haka yace min ranan nan Umma" Umma ta
bude baki tace "Ehh Lallai ke shashasha ce mahaukaciya, shi Aliyun ne xai turo
iyayensa gun Abbanku? Nihad nace ki daina kai kanki inda Allah ba kai ki ba, shi
uban Aliyun ne xai bari ya aureki ko uwarsa?" Nihad ta hade rai tace "Ni dai kawai
Umma ki gaya min abinda xan girka masa..." Umma tace "Girki? Shi yace ki yi masa
girki?" Nihad tace "Aa, amma daga Abuja fa xai biyo flight ya xo, kin ga ai ya
kamata in ajiye masa abinci" Umma tace "Aa babu wani abinci, a xuwan farkon ne xaki
yi masa wani girki? Ai ba a girki sai in mutum ya xo ya fi sau biyar, kawai ruwa
xaki ajiye masa da lemo..." Nihad tace "To snacks fa?" Umma tace "Toh shkkn xan
maki small chops ki ajiye masa" Nihad tace "Toh Umma nagode, sai in taya ki?" Umma
tace "Aa ba sai kin taya ni ba, kawai ke dai kije ki shirya" Nihad tace "Toh Umma,
amma parlon visitors din Abba xan shigo da shi ko?" Umma tace "A wani dalili
mutumin da babu wanda ya san sa a gidan xaki shigo da shi parlon baƙin Abbanku? Ai
daga waje xaki ajiye masa kujera fari ya xauna" Nihad tace "Umma fa har na gaya ma
Ya farooq shi yace in ajiyesa parlon baƙin Abba" Umma tace "Toh shi wannan wawan me
ya sani? A xuwa na biyu ko uku shine xa a shigo da shi cikin gida" Nihad dai tayi
shiru, Umma tace "Yanxu dai tashi ki je ki shirya, nima xan tashi inje kitchen in
yi abinda xan yi" Nihad tace "Toh" Daga haka ta mike ta fice daga parlon Umma ta bi
ta da kallo, Nihad na komawa dakinta wanka tayi ta dauro alwala ta fito, tana xaune
kan darduma bayan ta idar da sallah tana danna wayarta Mumy ta shigo dakin, Nihad
ta ajiye wayar tana kallonta tace "Umma ina yini..." Sai kuma tayi saurin cewa "Au
Mumy ina yini?" Mumy tace "Ban yini ba, dama jira kike in shigo in gaisheki da ku
ka dawo?" Nihad ta xaro ido tace "Aa wllh Mumy, dama yanxu nake son idan na gama
addu'a in je in gaisheki" Mumy tace "Toh yayi kyau, ai naha addu'ar kike yanxu"
Nihad tayi Murmushi tace "Ya jikin su Sudais Mumy?" Mumy tace "Ban sani ba, kin
shiga duba su ne da kike tambayata" Nihad ta marairaice tace "Umma wllh yanxu nake
son in je" Mumy tace "Kika sake ce min Umma xan bata maki rai wllh Nihad" Rufe baki
Nihad tayi, Mumy ta juya ta fita daga dakin, tashi Nihad tayi ta bi bayanta, suna
komawa bangaren Mumy tace "Ina suke Mumy?" Mumy tace "Suna tsakar gida, hope Nihal
bata yi kuka ba yau, na dai kirata daxu tace tun 11 ku ka ajiyeta" Nihad tace "Ehh
Mumy bata yi kuka ba ta fara xama big girl, Mumy Kinsan me?" Mumy tace "Ina jin ki"
Nihad tace "Mumy Aliyu xai zo yau" Mumy tace "Wani Aliyu?" Nihad tace "Lahh, Aliyu
da nake baki labari mana" Mumy tace "Ohk, toh Allah ya kawosa lafiya" Nihad tace
"Ameen" Mumy tace "Me xaki tanadar masa?" Nihad tace "Mun gama maganan wannan da
Umma" Shiru Mumy tayi tana kallonta, Nihad tace "Bari in dubo su Fadil" Daga haka
ta fita daga parlon, ganin basa main parlor din gidan kawai ta fita compound, nan
ma ta bi compound din da kallo bata ga kowa ba sai Aminu a bakin gate, ta karasa
tace "Kai Aminu ina su Fadil?" Aminu yace "Barka da dawowa Hajiya" Nihad tace "Su
sudais nake tambayarka" Aminu yace "Ayyo suna can tare da khalil, da a nan ma suke"
Ta wani yamutse fuska tace "Waye kuma haka?" Aminu dai yayi shiru yana sosa kansa,
tace "Wai wannan driver din?" Aminu yace "Ehh Hajiya" Tace "Kan bala'i, me suka je
yi wajensa" sai kuma ta juya da sauri ta bar wajen ta nufi chalet ai ko ta ga
takalmansu a bakin kofa, nan da nan taji ranta ya baci, yanxu cikin kazantaccen
wajen nan ya shiga da su salon su ki warkewa, k'in shiga parlon tayi ta xaga ta
bayan windown dakin da tasan yake ciki, ai ko a bude ta tadda window din an dage
labule, can ta hangosa xaune far end of the bed da waya karama kare a kunnensa, su
kuma kannen nata suna kwance kan gadon ta jikin bango suna game, ƙafafuwan su kadai
take hangowa, a fusace tace "Uban meye ku ke a nan Sudais?" Da sauri Khalil ya juya
yayi stretching hannunsa ya amshi wayar hannun Fadil keeping the phone under the
bedsheet, duk kannin nata suka taso suna kallonta, Sudais yace "Aunty Mumy ce tace
muje mu yi ball a waje" Tace "In fasa maka kai a wajen, ball din kenan? Kun shigo
nan salon wari ya kashe ku ko? To wllh idan baku taso ba ku ka bari na shigo duk
sai na xane ku a wajen nan, meye hadinku da shi?" Duk suka nufi kofa, ita ko ta
dinga hararan khalil da ko kallon inda take bai sake yi ba, ta ja wani dogon tsaki
ta juya ta bar wajen. A bakin kofar chalet din ta tarar da su suna sa takalmansu,
ta ce "Uban meye ma ku ke yi a ciki? Waye yace ku shiga ciki?" Fadil yace "Game mu
ke yi da wayarsa ya ba mu" Ta tafe hannu tace "Shi game din nokia phone din ne ya
burge ku? Toh daga yau na sake ganin ƙafafuwan ku a hanyar wajen nan sai na xane ku
da dorina" Tana gama fadin haka ta fixgo hannunsu suka bar wajen, Sudais yace
"Aunty irin phone dinki yake da shi" Nihad ta kallesa tace "Wa xai basa irin phone
dina?? Ai har ya mutu" Fadil yace "Irin naki da na Aunty Nihal ne, exactly the type
of ur own..." Nihad tayi dariya tana jinjina shashancin kannen nata tace "He can
neva have the type of my phone till he die Fadil, my phone is over a million, kasan
kuma meye million?" Sudais yace "Har da Diary Milk chocolate ya ba mu each, Kuma
Aunty yana da su da yawa a jaka, ni dai i want him to be my frnd..." Muryar Umma ta
ji tana kiranta ta sake kannin nata ta shiga parlor da sauri tace "Na'am Umma?"
Umma tace "Yauwa nayi kokarin in ma Hafsah transfer taje kasuwa tayi min chefane
babu network, ke idan kina da network ki mata ta je da sauri ta dawo yanxu" Nihad
tace "Umma ba akwai abubuwan a freezer ba? Meye babu?" Umma tace "Aa ba komai bane
akwai Nihad, ki mata transfer din in gaya mata abubuwan da xata siyo min" Nihad
tace "Toh bari in dauko wayata" Daga haka ta wuce sama xuwa dakinta, tana dauko
wayar ta tura ma Hafsah dubu sha biyar, tace "Umma na tura mata 15k" Umma tace "Toh
shkkn, je ki ki shirya" Nihad ta koma sama. Tana fito da kayan da xata saka wayarta
ya fara ring tana dubawa ta ga Aliyu ne, ta daga yace "Flight dinmu xai taso yanxu
in sha Allah" Nihad ta wara ido tace "Toh sai ka iso, Allah ya tsare" Yace "Ameen"
katse wayar yayi, nan ta hau shiryawa da sauri, kaya kawai ta saka bata shafa komai
a fuskarta ba ta fito, tana sauka downstairs fridge ta fara dubawa taga wani drinks
ne a ciki, duk yawancin drinks din Aliyu bai damu da su ba, his favourite drink is
Can coke, sai kuma Hollandia milk, rufe fridge din tayi ta koma dakinta ta dauko
Atm card dinta ta fito, ta gyara dankwalin dake kanta ta fita compound, gun Aminu
ta nufa, yana xaune da Khalil a gefensa, ko kallon khalil bata yi ba tace "Aminu
xan ɗan aikeka supermarket yanxu" Yace "Toh Hajiya" Ta mika masa Atm card dinta
tace "Pack din coke na gwangwani xaka siyo min ka bude kunnenka da kyau na
gwangwani na aikeka ba na gora ba, sannan ka siyo pack din Hollandia milk, amma
farin ba jan ba..... farin ba jan ba, tamm don kana min shirme sai ka shanyesu tass
ka biyani kudina" Ya amshi Atm card din yace "Toh Hajiya, in sha Allahu" Tace "Ka
tuna password din?" Yace "Aa ya kwanta min wllh" ta saci kallon khalil da ko inda
take bai kalla ba, ta yatsine fuska tace "Mu je kofar gida in gaya maka" Yace "Toh"
Da sauri ya fita gate din, ta wuce ta gaban khalil xata fita kofar gida ba tare da
ta damu da cewa babu gyale a jikinta ba, sai a sannan Khalil ya bi ta da kallo,
tana fita waje ta kulle gate din ruf, tana kallon Aminu ta gaya masa pin din tace
"Saura kuma kaje ka min wasa da Atm a titi, dama kana dawowa ko tsayawa kar kayi a
bakin gate ka kawo min Atm card dina kada aje a min sata" Yace "Toh Hajiya" Daga
haka ta bude gate ta shigo gidan, tana tafiya kamar baxata taka kasa ba tana yi
tana yatsine fuska ta wuce khalil, juyawa tayi xata kallesa suka hada ido ta galla
masa wani shegen harara ta rike kugu tace "Da bashi ne?" Yace "Ke xan tambayi
wannan" Buda baki tayi tana kallonsa da mamaki, can ta dawo fuska daure tace "Kace
me???" Shiru yayi yaki cewa komai yana kallon sky, tace "Aa in ka isa da ka
maimaita ai tunda kai baka da kunya fitsararre kawai" Ya kalleta yace "Me kike son
in maimaita wai" Tace "Ban sani ba" Yace "Ohk, amma tunda har kika ga ban saci
abubuwan ki masu muhimmanci dake jakarki shekaranjiya ba, ba kuma wani satan da zan
maki, ko duk cikin muhimman kayanki akwai abinda kika nema kika rasa, har kwalban
nan ban ta6a ba ai" Tayi masa wani kallo tace "Wani kwalba??" Tashi yayi, yayi mika
ya nufi gate ya fita ya bar ta nan a tsaye, ta bi sa da wani irin kallo, sai kuma
ta
juya ta bar wajen. Xama tayi parlor ta jira har Aminu ya kawo mata sakonta da Atm
card sannan ta xuba su a fridge ta wuce sama. Har bayan kusan minti talatin Hafsah
bata dawo ba, Nihad da har ta gama kwalliya ta kashe dauri ta fito parlor ganin
Umma a xaune tana kallon wani film tace "Umma ya fa kirani 30 mins ago yace xa su
taso" Umma ta kalleta daga sama har kasa don ba karamin kyau tayi ba, kamar wata
balarabiya, atamfar yayi mugun amsar jikinta, ga make up din tayi sa very light,
she look so beautiful, Umma ta tabe baki tace "Toh gantalaliyar bata dawo daga
kasuwan ba har yanzu, ni ma har na gaji da jira abinda ya sa na xauna parlon kenan
ina jiran dawowarta, don ma ai ba wahala cikin lkci kankani xa a gama..." Nihad ta
kalli agogo tace "Toh Umma bata tafi da waya ba in kirata?" Umma ta nuna mata wayar
a kan kujera tace "Kin ga inda nace ta ajiye wayar don ma kar taje wani yace mata
su hadu a wani waje, kinsan gantalaliya ce, opportunity din fita kawai take jira"
Nihad ta nemi waje ta xauna ranta a bace, sai kuma ta tashi ta tafi parlon baƙi ta
kunna turaren wuta ta fito ta xauna, har bayan wani minti sha biyar din babu Hafsah
babu alamarta, Nihad taji kamar ta fashe da kuka, Umma dai is so engrossed a kallon
da take a parlon, wayar Nihad ya fara ring ta xaro ido ganin Aliyu ne, ta daga ta
kai kunne, yace "Na kusa shigowa layin ku fa... In 2 mins time" Nihad ta mike tace
"Ohk toh" Katse wayar yayi, Umma ta kalleta tace "Ya aka yi?" Nihad kamar ta fashe
da kuka tace "Wllh Umma babu abinda xai hadani lakada ma Hafsah shegen duka yau,
kin dai ga har gashi ya iso bata dawo ba ko, ni yanxu don Allah me xan basa??" Umma
ta xaro ido ta mike tace "Haba dai har ya iso?" Nihad ta wuce sama a fusace, make
up din fuskarta ne kawai yasa take danne hawayen da yake son ya taru a idonta, Umma
ta rike ha6a tace "Amma Hafsar nan anyi yar iska yarinya, shegiya kawai, nan nan
kasuwa taje ta dawo amma kamar an aiki bawa garinsu? To ai da na sani na bari ta
tafi da wayar, kuma ni ma banyi dubara ba da naji shiru ko kaji ne sai in dafa ayi
masa pepper chicken" Khalil na xaune kofar gida da Aminu tare da mai gadin gidan
dake kusa da su, Kallon motar da ya shigo layin tun daga nisa yake with full
interest, lkci daya ya gane motar from the other day, ya mike ya juya xai shiga
cikin gidan, Aminu na tambayarsa inda xa shi yace "Ina xuwa" karo suka kusa ci da
Nihad da xata fito gate din ita ma, ya koma baya da sauri, ta hade rai still
inhaling his strong enchanted perfume, k'in basa hanya ya wuce tayi.....

✍🏻
07087865788 ....

*Shin kina buqatar kayan gyara Wanda zai yi amfani dasu Dan samu nutsuwar ki ke da
oga??*

*To maza Garzaya wurin @Kayanmatan_zuru domin samun mini package me kunshe da
maganin sanyi, maganin niima, maganin Karin dandano, maganin matsi, maganin Kara
kuzari Akan farashi kalilan.....*

_Bugu da Kari akwai kyauta a cikin ko wani package..... Ku tuntube ta a Instagram_


@Kayanmatan_zuru
Ko whatsapp👇🏻

Wa.me/+2348033308307💖💖 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

Khalil ya koma baya yana kallonta, still taki barin wajen sai ma wayarta da ta hau
dannawa xata kira Aliyu taji ko ya karaso layin, kawai ya bangajeta ya wuce ciki,
xaro ido tayi lkci daya ta riko rigarsa a fusace ta cakumo kwalarsa tace "Are you
mad?? ni xaka bangaje ka wuce? baka da hankali ne ko ka fara shaye shaye?" Yana
kallonta straight in the eyes yace "Irin wanda kike sha?" Bai bari ta gama
digesting abinda ya fada ba ya fixge hannunta daga rigarsa ya juya ya bar wajen
yana tafiya majestically, baki bude ta bi sa da kallo, irin wanda take sha?? Me
yake nufi kenan?? Kallon wayarta da ya fara ring a hannunta tayi ganin Aliyu ne, ta
daga a hankali tace "Ina ji" yace "Gani kofar gida...." Leka gate tayi taga yayi
parking a kusa da gidan dake kallon nasu, ta fita gate din, duk yanda ta so ta sake
fuskarta kasa yin hakan tayi don abinda khalil ya fada mata yayi mugun tsaya mata a
rai, ta nufi motar, su Aminu suka bi ta da kallo, Aliyu ya sauke glass dinsa yana
kallonta, ta kirkiri murmushi tace "Sannu da xuwa" Sai a sannan ta lura ba shi
kadai bane a motar tare yake da abokinsa Mujahid, Mujahid yace "Madam ya gari" Tana
murmushi tace "MB, ya kwana biyu?" Yace "Alhmdlh Nihad, ya karatu" Tace "Alhmdlh,
sannun ku da xuwa" Ta kalli Aliyu dake kallonta tace "Bismillah mu shiga ciki" Yana
kallon masu gadi yace "driver din ne can a xaune?" Ta girgiza kai tace "Ya shiga
ciki" Bude motar Aliyu yayi ya sauko, Mujahid ma ya sauko, tayi leading dinsu xuwa
cikin gidan, Aminu ya dinga kallonsu ta side eye, tun daga takalman kafarsu, kayan
jikinsu, agogon wrist dinsu, da hula xaka san rich kids ne, su ne elite... tuni
kamshin turarensu ya baxa tun daga bakin gate har cikin compound din, in dai kyau
ne kam a wajen Aliyu ba a cewa komai sai dai kawai he is black! Fine black. Nihad
dai na gaba suna baya, ta kai su har parlon baƙin Abbanta, the parlor was cool and
smelling so nyc sbda AC da ta bari a kunne tun daxu, bayan sun xauna, ita ma ta
xauna saman kujera ta gaishesu gaba daya, suka amsa tana Murmushi tace "Bari in
kawo maku ruwa" Aliyu ya shafa kansa yace "With food, Kinsan ko lunch ba mu yi daga
Abuja ba" Lkci daya jikinta yayi sanyi ta dai saki murmushi tace "Ohk, let me get
the water first" Fita tayi daga parlon, she was so confused, bata san me xata yi
ba, to ko order din abinci xata yi kawai ta juye masu a plate ta kai masu, but that
might take a long time kafin ma abincin ya iso, tana shiga main parlor bata ga kowa
ba, ta nufi kitchen jiki ba kwari, Umma ta gani tsaye a bakin kofa tana cewa "Ni
dama idan da an bi ta nawa a gidan nan tuntuni da an sallameta, babu dama ka aiketa
yanda kasan ta tafi da pillow da katifa, idan kayi magana ace ka fiye takura ka
fiye tsanani, haka Farooq ke ce min, ko kema nasan haka kike gani, amma ba haka
bane dole sai mutum yana yi yana jan ido, to ai gwara da ta guma ma kowa yau..."
Umma ta juya ganin Nihad tace "Kin shigo da su Daughter?" Nihad kamar xata yi kuka
tace "Umma abinci fa xa su ci wai, ni yanxu ya xan yi don girman Allah?" Umma tace
"Atoh ai dama baxa mu bar su haka ba, dole xa a samu alternative...." Nihad ta leka
kitchen din ta ga Mumy tsaye bakin gas tana hada ingredients din Chinese fried rice
da yake akwai left over cooked rice a kitchen din, sannan ga kaza a gefe tana
sarrafa shi, farin ciki ne ya rufe Nihad, Umma tace "Ai ban ta6a ganin tsinanniyar
yarinya irin Hafsah ba, ko kare ya shafa mata lafiya a yawo, babu dama ka aiketa ko
nan da nan ne sai ta bata maka rai" Mumy dai aikinta kawai take, Nihad ta karasa
kitchen din ta dau abinda xata daura masu drinks, ta dau glass cups tana kallon
Mumy, a hankali tace "Mumy nagode" Ko kallonta Mumy bata yi ba, sum sum ta juya ta
bude fridge ta debi drinks din ta daura a tray ta fita kitchen din, tana ajiye masu
a parlor Aliyu yace "Xa mu gaisa da su Mumy yanxu ko?" Tace "Toh bari in sanar
masu" Mikewa tayi ta fita, suka dau lemo da cup, tana komawa kitchen ta kalli Umma
tace "Umma wai xa ku gaisa" Umma tace "Toh su shigo nan parlon, ai a shirye muke"
Juyawa Nihad tayi ta koma, Umma tace "Ai ba sai mun wani yafa mayafi kamar wasu
tsofaffi Maryam, suna shigowa parlon sai mu fita kawai" Mumy dai tayi Murmushi tace
"Gaskiya ne" Umma ta karasa bakin gas din tace "Ko da yake ke nasan sai kice baxa
ki fita haka ba sai da Hijab, bari in dinga duba girkin ki dauko Hijab din naki a
sama" Mumy tace "Xai iya yiwuwa sun shigo parlon yanxu ai ko" tana fadin haka ta
tafi inda ta ajiye wayarta a kitchen din ta dauka tayi dialing number kanwarta
Jamila, tana dagawa tace "Jamila sauko min da Hijab dina sai ki taho da snacks din"
Tana fadin haka ta katse wayar, taje ta ci gaba da abinda take, sai ga Nihad ta
dawo tace "Umma suna parlon" Umma tace "Toh bari mu je a gaisa" Umma na fita
kitchen din jamila ta shigo da hijab din Mumy, Mumy ta amsa ta saka, Umma na shiga
parlon ta samesu xaune su biyu saman lallausan Carpet dake tsakar parlon, Umma ta
xauna saman kujera tana masu sannu da xuwa, suka gaisheta da ladabi ta amsa tace
"Fatan kun xo lafiya ya tsofaffin?" Suka amsa mata da "Alhamdulillah" Umma tace
"Toh madallah, sannunku da xuwa... Tana ta cewa xaka zo yau dai gashi Allah yayi"
Mumy ta fito suka gaisa a tsattsaye ta juya ta koma kitchen din, Umma na Murmushi
tace "Toh wanene surukin namu cikin ku" Mujahid ya nuna Aliyu yace "Shine Aliyu"
Umma na kare masa kallo tace "Madallah, maa sha Allah, Allah Ubangiji ya sanya
alkhairi Aliyu, Allah yasa ayi da mu, ya nuna mana wannan lokaci lafiya" Suka amsa
da "Ameen" Umma tace "Kai ne ɗan Janar na fari kenan ko?" Yayi Murmushi yace "Ehh
haka ne" Umma tace "Allah sarki, Baabarka ce uwargida amma?" Jamila dake can bakin
kofar kitchen tana juyo conversation din da Umma ke yi da su ta saki baki da mamaki
tana saurara, Aliyu yace "Aa ba ita bace" Umma tace "Ikon Allah, ta biyu ce kenan,
dama kam ance matansa biyu ashe da gaske ne, Allah sarki, amma kai ne dan sa namiji
babba ko kana da yayyi maza?" Ya girgiza kai yace "Kanana ne kannena maza" Umma
tace "Maa sha Allah, abu yayi kyau wllh, amma ai duk ku kan zo hutu kano" Yace "Ehh
muna xuwa lokaci lokaci" Tace "Madallah, ita uwar gidan bata da namiji ko daya
kenan?" Ya girgiza kai yace "Mata ne" Umma tace "Ikon Allah, matan har nawa?" Aliyu
ya daga kai ya kalleta for the first time, haka Mujahid ma kallonta yake ta yi,
Aliyu yace "Su uku" Umma tace "Wayyo, wato dai Ummarka ita ce me 'ya ya da yawa a
gidan, toh ai hakan da kyau" Farooq na tsaye can bakin stairs ya kasa karasowa jin
interrogation din da Mum dinsa ke masu, Jamila ta shiga kitchen a fusace tana kallo
Nihad dake hada inda xa a sa masu abinci tace "Ke, maza tafi kice masu ga abinci
can xa a kai su tashi daga parlon nan haka" Nihad tace "Toh" Daga haka ta fita daga
kitchen din xuwa main parlor, Umma tace "Amma ai kai ba kasar nan kayi karatu ba
ko?" Yace "Eh" Umma tace "Yauwa ko da na ji, ka kama aiki dai" Ya sauke kansa yace
"Eh" Tace "Aa abu yayi kyau, wani aikin kake yi?" A takaice Aliyu yace "Business"
Umma yace "Toh Allah ya sa albarka, yaushe xa ka turo magabatan naka kenan, in ji
dai ba yanxu ba ko?" Aliyu yace "Yanda Allah ya tsara" Umma tace "Gaskiya ne, batun
aure a hankali ake bin sa ba abu bane na gaggawa, ku kara fahimtar kanku sosai kar
ayi gaggawa a lamarin nan, Nihad dai 'ya ta ce, bata da wata matsala wllh baxan
cuceka ba, kuma ina fatan Mahaifiyarka tasan kana nemanta dai ko?" Yace "Eh" Nihad
ce ta shigo parlon tana kallonsu tace "Xa a kai abinci can" Umma tace "Eh kwarai
kuwa, ga abinci can ku je a kai maku, sannunku da xuwa, Allah yayi maku albarka"
Mikewa Aliyu yayi Mujahid ma ya tashi suka koma can daya parlon, Umma na kallon
Nihad tayi kasa da murya tace "Ke bandir din daloli ne a aljihunsa wllh na hango"
Dariya Nihad tayi, Umma tace "Allah kuwa, kawai ki ce masa wayarki ta samu matsala,
su ai kudi abar banxa ce a wajensu...." Aunty Jamila ta kwalo ma Nihad kira ta tafi
da sauri, Farooq ya karaso parlon rai a bace yace "Haba Umma, Haba Umma yanxu duk
wannan tambayoyin kina matsayin surkarsu kinga ya dace kiyi masu? Me ya kai ki
wannan tambayoyin fisabilillah?" Umma ta buda baki da mamaki tace "Wani tambaya
nayi da bai dace ba farooq?" Yace "Umma ina ruwanki da ko matan babansa nawa ne,
meye na tambayar baabarsa ce ta farko ko ta biyu, meye fa'idar tambayarsa ko a
kasar nan yayi karatu kuma wani aiki yake? Ina ruwanki da tambayar 'ya yan kishiyar
baabarsa nawa" Umma ta hade rai ta kunduma masa zagi tace "Ka fita idona in rufe a
gidan nan farooq, haka lkcn Kamila komai nayi kace ban iya ba ko bai dace ba, wai
shin kai ka haifeni ko ni na haifeka? Laifi ne don nayi bincike insan inda xa mu
tura er mu? Meye aibun tambayoyina? Ba neman aure ya xo ba? To kuwa ai dole ayi
masa tambayoyi, Ko dama ance maza ne kadai xa su yi bincike banda mata? To wllh ka
shiga hankalinka, ba ruwanka da harkana ko lamarina a gidan nan ina sake ja maka
kunne" Farooq dai sai kallonta yake, can ya juya a fusace ya bar wajen, Umma ta bi
sa da harara, Hafsah ce ta shigo parlon da leda a hannunta, Umma tace "Makira sai
yanxu kika ga dama kenan, to kin kyauta kin ji ko? Ki tafi can parlona a sama ki
jirani in xo in sameki ki gaya min gidan uban da kika je" Hafsah tace "Zan kai
ledar kitchen" Umma tace "Aa wuce da shi sama, xa mu hade da ke a can" Hafsah bata
ce komai ba ta wuce sama xuwa bangaren Umma, Nihad ta kai masu abincin da Mumy ta
gama hadawa, wani tray kuma ga meat pie, samosa, spring rolls da doughnuts da Aunty
Jamila ta kawo bayan Mumy tayi mata waya ta gaya mata tayi ta kawo, da yake tana da
ma'aikata cikin kankanin lokaci suka yi suka gama, wani bowl me dauke da apples
kusan goma ta kai masu a karshe ta ajiye, sannan tayi serving dinsu abincin. Bayan
sun gama cin abincin, Nihad ta shigo parlon tare da Ya farooq, bayan ya gaisa da su
ya fita, Mujahid ya mike yana kallon Aliyu yace "Bani makulli in dauko wayata a
mota, they might be plenty of calls i missed" Aliyu ya mika masa makullin ya amsa
ya fita, Nihad dai kallonsa kawai take, wayarsa ya ciro a aljihu ya shiga gallery
bayan few seconds ya mika mata, ta amsa tana kallon screen din wayar, sosai gabanta
ya fadi, ta dai yi shiru bata ce komai ba, yace "You promised kin daina dukka ire
iren outing din nan, so where did this come from?" Nihad ta marairaice tana kara
kallon hoton, 4 weeks ago ne suka je wani babban restaurant da su Naf da Husnah da
samarin su, shine aka yi hoton a can, wando ne a jikinta sai crop top me shegen
kyau da tsadadden sneakers a kafarta, sannan ta daura baƙin dankwali a kai ta xubo
dogon gashinta, su Husnah ma duk ire iren shigar suka yi a hoton... jin tayi shiru
Aliyu yace "Why are u quiet?" Ta daga kai ta kallesa a hankali tace "Hoton nan ai
ya dade" Yace "Karya kike, this is a recent pix, jiya da daddare Naf ta daura a
status na gani nayi saving" Nihad tace "Am serious ba kwanan nan muka yi ba, kuma
ai kafin in maka alkawarin daina fita tare da su ne muka yi hoton nan, ka tambayi
Naf din ma" Yace "Nihad!!" Shiru tayi tana kallonsa gabanta na faduwa, yace "Saboda
ina sonki da aure ya sa ki ka ga har nake hanaki abubuwan nan da kike, banda haka i
have no business with ur life style, quite alright kinsan i have other babes wa
enda muke tare da su har yanxu, but ban ta6a daga kai na hana yarinya yin abinda
tayi niyya ma rayuwarta ba, ban ta6a hanasu holewarsu yanda suke so ba, but ke
saboda intention dina a kanki daban shi yasa nake hanaki duk wannan shiriritar da
kike, Upon how wealthy my parents are, baxa su ta6a yarda in kawo masu mace mara
kamun kai ince xan aura ba, baxa su ta6a amincewa, kuma ya kamata ki kara yarda
yanxu tunda har na tako tun daga Abuja na xo gidanku to da gaske aurenki nake son
yi, i will neva do that for any lady, sai sai idan dama ina da wata sabgar da xanyi
a kano.... Nihad this should be ur last warning!!!" A hankali tace "Toh kayi
hakuri, in sha Allah hakan baxai kara faruwa ba, i am promising u this" Yayi shiru
yana kallonta, tace "Wllh da gaske nake baxan kara ba" Yace "Toh Allah ya sa..." A
hankali tace "Ameen" Yace "Kince min driver din a nan yake zama" Nihad ta gyara
xama tace "Ehh wllh, yanxu haka ma yana nan, ai yana kofar gida sanda ku ka shigo
layin shi ne ya shiga cikin gidan" Aliyu dake ta kallonta yace "Da muka shigo layin
ne ya shiga ciki?" Tace "Aa ai sannan baku karaso ba" Yace "Ohk where is he now?"
Nihad tace "What will happen now, kawai mu fita sai ka xauna a compound ni kuma xan
je in samesa a can boys quarters da yake zama, ince xan je karbo sako ya xo ya kai
ni, daga nan idan ya fito compound xaka gan shi" Aliyu yace "Kamar wasan yara...
But i urgently wants to see him" Nihad tace "Noo, ta haka kadai xai fito compound
har ka gansa, so now let's go outside" Tashi tayi ta dau bowl din apples tace "Bari
in kai maka wannan ka dinga ci" Daga haka ta fita, ya mike ya bi bayanta suka fito
compound din, can karkashin thatch dake dauke da kujeru ta kai masa apples din ta
ajiye saman table, ya xauna yana kallonta yace "Kin yi kyau" Tayi wani blush tace
"Thank you, bari in je in samesa yanxu" Yace "Ohk" Hanyar Chalet ta nufa ya bi ta
da ido har ta bace, ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna hudu saura, Nihad na isa
chalet din ta hade rai tana lekan parlor, isiya ta hango yayi dai dai kan kujera
yana ganinta ya mike da sauri ya fito yace "Kaya xa a amsa Hajiya?" Tace "Ina
wannan yaron?" Yace "Wani yaro?" Tace "Halilu" Isiya ya ɗan gwale ido a ransa yana
kara nanata yaro da tace, can yayi saurin cewa "Yana can daki" Tace "Toh kaje ka
kirasa Mumy ta bada sako a basa" Juyawa yayi yace "Toh Hajiya" Ya fi minti daya
yana kwankwasa kofar dakin da Khalil yake ciki amma bai bude ba, shi dai yasan baya
baccin rana balle yace, to ko kila yana bandaki, bai yi gigin bude kofar ba tun
ranan da Saminu yayi masa haka yayi cutting din masa warning me lafiya, Bude kofar
aka yi khalil na kallonsa yace "Ya aka yi?" Isiya yace "Aa dama mamarsu Sudais ce
ta bada sako wai xa a gaya maka a waje" Khalil yace "Ohk" Fita yayi tun daga cikin
parlor ya hangota, yana fitowa ya tsaya bakin kofa yana kallonta, Tana yatsine
yatsine tace "Yauwa xaka yi dropping dina in amso sako yanxu, kaje ka dauko makulli
ina jira" Juyawa yayi ya koma ciki ba a dau lkci ba ya fito rike da makullin motar,
yana kallonta ya mika mata, ta hade rai tace "Meye kake mika min makulli cewa nayi
ajiye ni xaka je kayi in amso sako ko kai kurma ne" Ya ajiye makullin saman
matakalan chalet din yace "Toh baxan je ba, wanda ya daukeni aikin ma ya daga min
kafan aiki yau...." Ya juya xai koma cikin parlon yace "Shi saurayin naki ya kai ki
ki amso sakon...." Kasa cewa komai Nihad tayi ta bi sa da kallo, ta fi minti daya
tsaye a wajen kafin ta juya ta koma gun Aliyu rai a bace.... Murmushi Aliyu yayi
bayan ta sanar masa yanda suka yi da Drivern yace "Ohk, there is next time, xan
kuma sauke masa girman kan da ke yaudaransa" Nihad tace "Toh wai dama talaka na
irin wannan girman kan? Wllh sai ka xata fa gidan Ubansa ne nan din yanda yake
abubuwansa" Aliyu dai bai ce komai ba, but all his thought is with the driver, he
seriously want them to meet. Sai kusan karfe biyar Aliyu ya bar gidan tare da
Mujahid bayan sun shiga sun ma Mumy da Umma sallama, Dollar dari biyu ya ba Nihad,
yana tafiya dakin Umma ta fara shiga ta nuna mata kudin, Umma ta ja tsaki tace
"Meye haka, ko dubu dari da hamsin bai kai ba, amma ya bani kunya duk wannan girke
girken da ya kwasa?" Nihad tace "Umma fa a ko da yaushe cikin yi min kyauta yake,
wannan ma cewa yayi inje saloon inyi gyaran gashi da shi fa" Umma tace "Toh Allah
na tuba ina laifin ya baki dubu dari biyu da hamsin ma, duk kudin ubansa sannan
kuma shi ma yace min yana business nasan baxai wuce exportation and Importation
yake ba" Nihad bata kuma cewa komai ba, ta bude karamin jakarta dake hannunta ta
saka kudin. Bayan magrib Khalil da Aminu na xaune kofar gida Aminu sai basa labarin
samarin Nihad yake da irin shigar da suka yi, Khalil dai yana ta sauraronsa amma ba
kallonsa yake ba, Aminu yace "Ina gaya maka wllh turarensu har bakin titi, kai kaga
wani rantsattsen takalman da suka saka kuwa, kana ganin yanda suke tafiya kasan 'ya
yan wasu shegu ne a kasar nan, wato barayin kasar nan" sai a nan Khalil ya daga kai
da sauri yana kallonsa, Aminu ya kwashe da dariya yace "Allah kuwa, barayin
gwamnati kenan" Motar da ke tahowa yasa Aminu yayi shiru suna kallon motar gaba
daya don ta hasko su, Khalil ya mike kamar xai shiga gate, sai kuma aka yi kasa da
fitilar motar....

✍🏻
07087865788

Mu hadu after EID in sha Allah, sannan duk ku bi gidan yan uwa da abokan arziki aje
yawon sallah a samo kudin littafin Nihad, don kuwa bayan EID sae dai in baku last
free page inyi mursisi in koma gefe inyi shiru abu na, idan kuma an tattala kudin
yawon sallah an xo an biya littafin Nihad ba wani xancen yin shiru daurawa kawai xa
mu yi abun mu, idan Allah ya ta6a xuciyata ma har page biyu sae mu dinga yi......
😁😜 Amma fa sai na ga kudi kaca kaca🙄

Allah Allah nake in gano wanda Abba ya aura ma Nihad da ja'irar ta suma amma abun
ya ci tura jama'a, to ko dai Aminu ne don shi dama yace zai iya maneji da ita idan
aka hadasa da kudi😯

*Shin kina buqatar kayan gyara Wanda zai yi amfani dasu Dan samu nutsuwar ki ke da
oga??*

*To maza Garzaya wurin @Kayanmatan_zuru domin samun mini package me kunshe da
maganin sanyi, maganin niima, maganin Karin dandano, maganin matsi, maganin Kara
kuzari Akan farashi kalilan.....*

_Bugu da Kari akwai kyauta a cikin ko wani package..... Ku tuntube ta a Instagram_


@Kayanmatan_zuru
Ko whatsapp👇🏻

Wa.me/+2348033308307💖💖 *NIHAAD* 💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

Aminu ya kalli Khalil yace "Ni wallahi ca nake saurayin nata ne ya dawo da daddaren
nan kuma, kasan fa sai ya iya xuwa ya dauketa su tafi babu wanda xai sani banda ni
da nake bakin gate din nan" Khalil yace "Saurayin wa?" Aminu bai kai ga basa amsa
ba aka bude Driver seat, Hamid ne ya sauko tare da abokinsa Mujahid, a tare suka
nufo gate din, tuni Aminu ya dinga jera ma Hamid gaisuwa uwa maroki, Hamid ya amsa
yana kallon Khalil, sai kuma ya mika masa hannu, Khalil ya kai nasa hannun suka
gaisa, Mujahid dai sai kallon Khalil yake, kauda kai khalil yayi ya fara tafiya
xuwa gun mai gadin daya gidan dake kusa da su, Bayan sun shiga gate Mujahid na
kallon Hamid yace "Waye wannan gayen?" Hamid yace "I don't know, ni ma yau na fara
ganinsa, probably gidansu na nan layin" Mujahid yace "No, he looks a bit familiar,
amma gaba daya na mance inda na san shi..." Hamid yace "Wait" Juyawa yayi ya koma
bakin gate, Mujahid ya bi bayansa, Hamid na kallon Aminu yace "Aminu" Da sauri
Aminu ya nufi gate din yace "Na'am ranka shi dade" Hamid yace "Wanene mutumin nan
da ku ke tsaye da shi?" Aminu yace "Au.. ai sabon dreba ne, kasan Habibu ya bar
gidan nan, Alhaji ya bude masa tafkeken shago ya koma can, shine ya kawo wannan, ai
ya kwana biyu da fara aikin ma" Hamid dai sai kallon Aminu yake, Mujahid yace
"Driver????" Aminu yace "Ehh dreban gidan ne" Mujahid ya kalli Hamid, Hamid ya juya
ya koma cikin gidan, Mujahid ya bi bayansa yace "Seriously kamar na san shi a UK"
Hamid yayi dariya yace "Kai dai kasan me kama da shi a UK" Mujahid yace "Toh amma
kaman is very obvious, kawai dai i can't recall..." Parlon gidan suka shiga, Nihad
na kwance parlor tana danna wayarta, tana ganinsu ta mike tayi wucewarta sama,
Hamid ya bi ta da wani irin kallo, Mujahid ya saki baki shi ma yana kallonta, can
yace "Yarinyar nan fa na feeling kanta da yawa" Hamid yace "A very spoilt Brat,
right from when she is little bata da manners dama, unlike her half-sister
Nihal..." Hamid ya xauna ya dau wayarsa ya hau kiran Farooq don dama wajensa suka
zo. Washegari Monday Nihad ta gama shiryawa misalin karfe tara da rabi ta fito
parlor, gaida Farooq da ya bi ta da kallo tayi, yace "Amma ba da wannan ɗan iskan
mayafin xa ki fita ba Nihad?" Ta juyo tana kallonsa ta marairaice tace "Yanxu yaya
me ya samu wannan mayafin? Dubi fa ya sauka har bayana fa" Yace "Wuce ki canxa"
Muryar Umma suka ji tace "Ta canxa a saboda kai ke siya mata mayafan? Ko kuma
sabida a jikinka ta yafa?" Ya juya ya kalli Umma, Umma tace "Sharesa kije kiyi
breakfast din ki, ki kama gabanki" Dinning area ta nufa, Umma ta shigo parlon ta
zauna, Farooq bai sake cewa komai ba, Nihad ta gama shan shayin da ta hada sannan
ta mike, ta gefen ido farooq ke hararanta taki yarda ta kallesa ta nufi bangaren
Mumy, a handle din kofar parlonta ta rataye mayafin sannan ta shiga parlon, zaunawa
tayi saman kujera tana kallon Mumy tace "Ina kwana Mumy" Mumy tace "Wato sai kin
gama duk abinda kike sannan xaki shigo ki gaisheni ko Nihad? Nihal bata ta6a kai wa
karfe bakwai bata shigo nan ta gaisheni ba, amma ke sai sanda kika ga dama" Nihad
tace "Toh Mumy ai saboda Nihal a nan bangaren take kwana shi yasa, ni kuma ai ba
nan nake ba" Mumy tace "Toh yayi kyau ki ci gaba, nan gaba ma ki daina shigowa
gaisheni kawai xai fi maki alkhairi" Nihad tayi shiru sai kuma tace "Kiyi hakuri"
Mumy na kallon kayan jikinta tace "Wannan ɗan iskan dinkin kika yi da tsadadden
atamfar nan kenan?" Nihad tace "Mumy gown ne fa" Sai kuma ta mike tace "Mumy na
makara, yau muna da test" Mumy tace "Ki tabbatar Hijab xa ki sa Nihad" Tace "Toh,
sai na dawo" Daga haka ta fita daga parlon, zare mayafinta tayi ta bar wajen da
sauri sai da ta tafi dakinta ta dau jakarta sannan ta dawo parlor, lekan parlon ta
dinga yi ta ga har lokacin Farooq na xaune, Umma ma na parlon, tana kallon Umma
tace "Umma sai na dawo" Umma na Murmushi tace "Toh Allah ya tsare daughter" Ta saci
kallon farooq tace "Yaya sai na dawo" Banza yayi da ita, bata ko kallesa ba ta
fita, tana isa gate ko kallon Mai gadi da Khalil dake wajen bata yi ba tayi
ficewarta daga gate din tana tafiya cike da isa, ta riga ta dau vow daga yanxu, da
dai Khalil ya sake jan ta a mota gwara taje ta hau adaidaita, tayi canceling ta hau
mota yayi driving dinta. Mai gadi na mata Allah ya tsare ko kallonsa bata yi ba
balle ta amsa masa, kamar yanda bata kalli Khalil ba shi ma haka ba kalli inda ta
bi ba, Mai gadi yace "Ikon Allah, yau kuma da kafa xa a makarantar" Khalil yayi
murmushi kawai bai ce komai ba. Nihad na isa makaranta har wajen karfe sha daya
basu da niyyar shiga lectures da su Husnah suna xauna Cafeteria suna ta hira
abunsu, kaf Clique din sun canxa xuwa latest iphone da ya fito ko wata daya ba ayi
ba amma banda Nihad, kuma kaf dinsu babu warce iyayenta suka siya ma, sun dai yi
kame kamensu sun samu waya, Naf tace "Amma nayi mamaki kice ke baki da just 250k da
xaki cika ki canxa waya, to shi wannan saurayin naki Aliyu meye amfaninsa?" Nihad
tace "Aa ni dai baxan tambayesa ba, kuma dama ni bana tambayarsa komai" Sai kuma ta
dau wayarta tayi dialing number Abba ta saka handsfree tayi masu alama su yi shiru,
yana fara ring Abba ya daga yace "Hello dear" Shessheka ta fara yi tace "Abbaa"
Daga daya bangaren Abba yace "What happened?? Me ya sameki?" A hankali tace "Abba
ina shigowa makaranta xan sauka daga mota wayata ta fadi screen din ya fashe gaba
daya" Abba yace "Subhanallah" Nihad tace "Yanxu ga shi wayar ya dauke" Abba yace
"Hasbunallah, baya yi yanxu wayar kenan?" Tace "Ehh baya yi" Abba yace "Toh abinda
xai faru idan kin koma gida ki ba wannan driver din ya je inda ake gyaran waya a
gyara ko nawa ne ma sai ya kirani ya sanar min" A hankali Nihad tace "Toh" Abba
yace "Shikenan, Allah ya tsare gaba" Nihad tace "Ameen, Nagode Abba, sai anjima"
Daga haka ta katse wayar tana kallonsu Naf dake sauraron Abba gaba dayansu, suka
kyalkyale da dariya suka ce "Gaskiya ne er daddy" Nihad tace "Toh amma me yasa xai
hadani da wannan fitsararren yaron, this plan isn't going to work idan da shi fa"
Husnah ta cije yatsa tace "Kashh, yau ga ranan Habibu, to wai shi wannan din dama
har yanxu ba a koresa bane?" Nihad ta tabe baki tace "Toh mayen xai tafi ne?
Wallahi duk abubuwan da nake masa ya ki tafiya sai ma gyara xama da yake yi a gidan
yanda ku ka san gidan ubansa, yau ma fa wani gaye ne ya kawo ni schl don nace baxan
sake shiga mota daya da drivern nan ba, ina tsaye busstop din anguwanmu sai ga benz
din gayen, shine ya rage min hanya har cikin makarantar nan, amma da da adaidaita
Sahu xa ku gan ni ae" Zully tace "Aa to baki yi masa yanda xai bar gidan bane, da
nice tuni xan masa check out wllh, wannan ai karamin kwari ne" Nihad tace "Kai
Zully wasu fa mayu ne, shi wannan a maitan ma yayi nisa, gaba daya na lura bai son
barin gidan ne, tunda yana cin me kyau ya sha me kyau" Husnah tace "Kawai shiryawa
xa mu yi mu je har gidan mu ci maki ubansa mu masa tijara" Nihad ta kyalkyale da
dariya tace "Yauwa don Allah ku shirya ku zo dama 24/7 yana xaune bakin gate da mai
gadi, amma fa you girls should dress decently kun san halin Mumy" Husnah tace
"Wannan ba matsala bane duk xa mu sa Hijab a jaka, xuwa Thursday xa mu zo don ranan
ne muke da time, gobe akwai club da xa mu je, Wednesday kuma xa mu je wani picnic,
yauwa ki shirya mu je na ranan Wednesday din nan ba da daddare bane da yamma za
ayi" Nihad tace "Ohk drop location" Throughout ranan babu wanda ya je kusa da dept
balle ya shiga lectures, daga karshe ma fita suka yi xuwa wani babban eatry
saurayin Zully xae siya masu abinci. Da yamma bayan la'asar Khalil na tsaye bakin
gate yana sauraron Aminu dake basa labarin wani abokinsa da suka taso tare, lkci
daya yayi mahaukacin kudi ya guji kowa daga karshe aka gano ashe kidnapping yake,
Aminu dake ta kumfar baki yace "Har yau xancen da nake maka Inusa na dogon gida,
yau kuma shekara uku kenan...." Bude gate aka yi duk suka juya, Inna ce ta shigo
gidan da sallama tana rike da jakarta me kyau, Aminu ya mike da sauri yana washe
hakora yace "Barka da zuwa Hajjaju" Inna ta ɗan kalli Khalil ta tsaya daga bakin
gate din tace "Yauwa Aminu, yan gidan basa nan ne, naji ko ina shiru?" Khalil ya
karasa ya gaisheta da ladabi ta kallesa tace "Auu, ni ai ban ganka ba Aminu kadai
na hango, sannu ya kake" Khalil yace "Lafiya lau, Ya gida Hajiya?" Tace "Toh
Alhamdulillah, yanxu Hamid ya ajiye ni a mota ko gama sauka ban yi ba ya juya yayi
wucewarsa, gashi a can bakin titi in gaya maka naga wani apple me kyau ana siyarwa
amma ya ki tsayawa in taya balle in siya, mun baro wajen can farkon shigowa anguwar
nan wallahi" Khalil yace "Toh bari a dubo maki" Inna tace "Yauwa maza kaje kaji
nawa nawa ne ka dawo ka gaya min" Fita gate din yayi, Inna ta bi sa da kallo, sai
kuma tayi kasa da murya tace "Wai dama har yanzu basamuden nan na gidan nan Aminu?"
Aminu na danne dariyarsa yace "Yana nan Hajiya" Inna tace "Toh saboda me? Shi
Ibrahim din ne ya bar sa ya ci gaba da zama a gidan ko ko? Yau naga fitina" Aminu
yace "Ae ba shi da matsala fa Hajiya, kowa a gidan ya shaida, kullum nan muke yini
tare da shi" Inna tace "Aa rufe min baki Aminu, wllh in nice a gidan nan da ido
daya zan dinga bacci" Tayi kasa da murya tace "Irinsu ne fa ke aikata mugayen
abubuwa a duniya yanxu Aminu, ko kai baka ga siffarsa ba, wannan idan cacan baki ya
hadaka da shi sai dai ya daga ka ya nana shege da kasa, to bai cuceka ba? Da nayi
niyyar kwana amma gaskiya baxan iya ba da wannan mutumi a gidan nan, ina dalili"
Dariya kawai Aminu yake, Inna tace "Bari in shiga mu gaisa da su kawai inyi
fitowata in wuce" Daga haka ta wuce cikin gidan, tana zaune parlor da Mumy dake ta
sauraronta Khalil yayi sallama bakin kofar, Inna tayi kasa da murya tace "Kaddai
shi ne? Har nan ku ke bari ya xo maku??" Mikewa Mumy tayi ta nufi kofa, Khalil ya
gaisheta da ladabi ta amsa tana tambayarsa ya aiki, yace "Alhamdulillah" ledan
hannunsa ya mika mata yace "Sakon Hajiya ne" Mumy ta amsa ta juya
ta koma cikin parlon, inna ta hangame baki ganin leda shake da manyan apples tace
"Meye wanan din? a ina naga kudin biyan wannan apple cike a leda, amma dai wawa ne
wannan yaron, maza ciro kwara biyu ga dari biyu ki basa, sauran kuma ya mayar yace
ance baxa a siya ba" Mumy na kallon Inna tace "Wai da na nawa kika ce ya siyo
inna?" Inna tace "Aa ni ban aikesa ya siyo ba, kawai cewa nayi yaje ya tambayo nawa
nawa ne, ni ban aikesa ya kwaso min ba wallahi" Mumy tace "Atoh ina amfanin mayar
da abinda aka riga aka karbo Inna" ko rufe baki Inna bata jira Mumy tayi ba ta mike
ta fixge ledan tace "Ai ba sata nake yi ba da xan siye duk apple din nan, kuma 'ya
yana ba kudin banxa suke samu ba" Tana gama fadin haka ta fita waje da sauri, can
bakin gate ta hango khalil a zaune tace "Yau naga gantalallen mutumi, wa ya bamu
kudin siyan wannan uban apple din, ko don ya ga makeken gida ya zata sata ake yi"
Tana isa kusa da su tayi kasa da murya tace "Ɗan nan cewa nayi ka tambayo nawa nawa
ne, bar ganina haka, wllh rufin asirin Allah kawai nake takama da shi, bani da
komai, maza ka maida masu kace biyu aka aiko ka kaji" Khalil yace "Aa Hajiya na
siya maki ne kawai ki ci" Inna tace "Ka siya min? Ko dai lemo ka kwaso min?" Tana
fadin haka ta kara bude ledan da sauri tana lekan ciki, ai ko taga apple ne ya fi
goma, Inna ta gwalo ido tace "Albashin naka ka kwashe ka siyo min apple din?"
Khalil yayi murmushi kawai, Inna ta rike ha6a tace "Kaii amma wallahi nagode, Allah
yayi maka albarka, ko jikokina babu wanda ya ta6a min haka cikinsu, dari uku uku fa
ake siyar da duk guda daya" Shi dai khalil murmushi kawai yake, Tace "Amshi ledan
mu shiga Maryam ta maka godiya" Da sauri yace "Aa Hajiya" Inna tace "Amsa kawai mu
tafi nace" Amsan ledan yayi tana gaba ya bi bayanta har main parlor, tana ganin ya
tsaya bakin kofa tace "Aa shigo kanka tsaye" Still yaki shiga, Inna tace "Wai ba ni
nace ka shigo ba, ni fa na haifi me gidan" Mumy dake kallonsu tace "Ka karaso"
Shiga parlon yayi da sallama, Inna ta kulle kofa tana nuna ma Mumy ledan tace "Wllh
Maryam ashe siya min yayi da albashin sa, kin dai ga bare ne fa amma yasan kyautata
ma tsohuwa" Mumy tace "Toh Allah ya saka da Alkhairi, maa sha Allah" Inna tace
"Allah sai naji ya fiye min Hamid da su Farooq sau dubu" Mumy dai bata ce komai ba,
Inna ta rike ha6a tace "Allah yayi maka albarka ka ji" Yace "Ameen Nagode" Bude
kofar parlon aka yi Nihad ta shigo, still tayi bakin kofar tana kallon Khalil da
mamaki, sai kuma ta kalli Inna da Mumy tace "Me wannan kuma yake yi har cikin
parlor?" Mumy tace "Uwarki yake yi" Nihad ta hade rai tace "Mumy parlon mu fa,
privacy dinmu, this is uncalled for gaskiya, ko su Aminu da suka yi shekara da
shekaru a gidan nan xa a bari su shigo nan balle wannan driver din..." Mikewa Mumy
tayi tana ganin haka tayi hanyar stairs da sauri, Mumy bata fasa bin ta ba, Inna
tayi kasa da murya tana kallon Khalil tace "Wallahi duk hakuri muke da ita, duk ta
fi karfin kowa in gaya maka, shi yasa kwanaki da ta je ta kai karar ka gu na wai in
sa a kore ka nace waa? Me ka min xan maka sanadin aikin ka, wllh naki biye mata
shine ta kullace ni har yau, dama dai bansan mugun halinta bane shine xan biye mata
amma ai kaga ban biye mata ba gashi har yanxu kana aikinka cikin rufin asiri har da
siyo min apple, ni duk inda harkar rashin gaskiya take ba ni a ciki, Nihad kam bata
da gaskiya wllh" Khalil dai kansa na kasa, Inna tace "In ji suna baka abinci
isasshe dai?" Yana murmushi yace "Ehh ana bamu" Inna tace "Toh shkkn, can gidan
Habubakar din ma ka iya dinga xuwa kullum, ai yanxu kam ka zama ɗan gida" Murmushi
yayi yace "Nagode Hajiya" Tace "Yauwa je ka" Juyawa yayi ya fita daga parlon. Da
daddare Nihad na kitchen tana pancake da xata ci kafin ta kwanta Sudais ya shigo
kitchen din, cup din hannunsa ya ajiye a sink yana kallonta yace "Lahh Aunty Nihal
ma tace mana tayi pancake ta ci yau a makaranta" Nihad na juya pancake dinta ba
tare da ta kallesa ba tace "Did u spoke with her today?" Yace "Yess, Uncle driver
ne ya kira mana ita, muna ta magana da ita for long" Juyawa Nihad tayi ta ajiye
spatula din hannunta tace "Who is uncle driver?" Yace "Wannan da yake kai mu
school" Ta bude baki, sai kuma tace "Yaushe ya kira maku ita?" Sudais yace "After
magrib prayer" Sake baki Nihad tayi tana kallonsa, jin kaurin pancake dinta ta
kashe gas din da sauri ta fita daga kitchen din, sama ta tafi bangaren Umma, har
bedroom ta shiga ta sameta tace "Umma kinsan da wa Nihal ke waya yanxu?" Umma tace
"Wa?" Nihad tace "Wai driver, yanxu su Sudais suke ce min ai ya kira masu ita,
ranan da xa mu je shopping ne fa ya amshi numberta, toh a ranan da xa mu kai ta
school ma ya kirata ya fi a kirga, sai ga yanxu su sudais suka xo suna gaya min ai
driver ya kira masu ita" Da wani expression Umma tace "Driver? Wani drivern ni
Sumayya?" Nihad tace "Driver dae da kika sani" Umma tace "Ko dai Nihal ta fara
hauka ne?" Nihad ta kyabe baki ta zauna gefen gado, Umma ta dau wayarta ta hau
kiran Nihal, yana fara ring Nihal ta daga, Umma tace "Nihal kiran me ku ke yi ke da
drivern gidan nan?" Nihal tace "Driver kuma?" Umma tace "Ban sani ba" Nihal tace
"Wallahi ba komai Umma kawai wani lkcn yana ba su Sudais ne mu yi magana da su"
Umma ta kunduma mata zagi tace "Kanin uwarki ko na ubanki? Banda xubar da aji meye
na wani waya da drivern gidanku? Sa'anninki na waya da mutanen arxiki ke kina waya
da driver, ke wace irin yarinya ce? to wllh xan ci kaza kazanki idan baki kama
kanki kin goge number tasa ba, kaji min gantalalliya dai" Nihal dai tayi shiru,
Umma tace "Na dai gaya maki tun wuri ki goge number nan ko in ci maku ke da shi"
Umma na kai wa nan ta katse wayar, sosai ranta ya baci, ita kam wace irin yarinya
ce Allah ya bata, duk abun kaskantar da kai ta iya shi, banda haka meye ya kai ta
dinga waya da driver, Nihad tace "Wllh Nihal is so annoying, how comfortable is she
making call with that wretched man" Umma tace "Ki kyale mahaukaciya mana" Nihad ta
mike ta tabe baki ta fita daga dakin, Zaga dakin Umma ta dinga yi. Nihad na gama
pancake din ta shiga bangaren Abbanta, bayan ta gaishesa tayi shiru saboda Mumy
dake zaune a parlon, Abba ya kalli Mumy, murmushi kawai tayi ta mike ta bar masu
parlon, Abba na kallonta yace "Ya aka yi daughter?" A hankali tace "Abba na tambayi
wata kawata gyaran screen din wai 150k ne" Abba yace "Har 150k?" Ta marairaice tace
"Eh Abba" Shiru yayi, can yace "Ohk gobe zan tura maki, amma baxa ki wajen gyaran
ke kadai ba, ko ku je da farooq?" Da sauri tace "Aa Abba ba kace driver ba?" Abba
yace "Ohk, no problem sae ku je tare, kin gyara account din naki ne?" Tace "Aa sae
next week, I'm busy with lectures throughout this week" Abba yace "Ohk xan sa kudin
a account din Farooq sae ya baki" Ta hadiye abu da kyar sai kuma tace "Abba driver
din bashi da account?" Abba yace "No I don't know" Tace "Abba idan yana da shi
kawai ka sa mashi tunda tare xa mu, ba sae ka tura ma ya Farooq ba" Yace "Ohk,
Allah ya kai mu goben" tace "Ameen" mikewa tayi bayan ta ma Abba sae da safe ta
fita tana Murmushi, tana da kusan 70k a account dinta, ga kuma dala dari biyu da
Aliyu ya bata, now with additional 150k from her father, latest iphone is sure
gobe. Washegari Nihad na ta kallo ta window har Khalil ya tafi ajiye su Amina a
makaranta, Hijab ta saka har kasa ta sauko, gun Aminu ta nufa yace "Barka da Safiya
Hajiya" Tace "Aminu ina son tambayarka ne don Allah" Aminu yace "Toh Allah ya sa na
sani Hajiya" Tace "Yaron nan Driver yana da account number ne?" Aminu yace "Anyaa,
gaskiya ban ta6a jin yace xai cire kudi ba" Ta ta6e baki tace "Okay" Juyawa tayi ta
koma ciki, tun jiya take avoiding ya farooq wannan ne ma yasa ta ki zama a parlor,
ta koma dakinta tana jin dawowar Khalil ta sauko kasa da sauri, hade rai tayi ganin
Ya Farooq a parlor ta gaishesa tayi ficewarta ba tare da ta jira ya amsa ba, Direct
wajen khalil ta nufa babu yabo babu fallasa tace "Ehm ya ma ake kiranka? Abbana
yace ka bada account number" Khalil ya kalli Aminu kamar dai yana jiran Aminu ya
bata amsa, a fusace tace "Malam ai ba Aminu xaka kalla ba, da kai nake ni xaka
kalla" Ya kalleta yace "Ohk, bani da account" Ta masa wani kallo tace "I thought as
much" sai kuma ta ja tsaki ta juya ta koma ciki, Aminu yayi kasa da murya yace
"Alhaji fa ya tambayi account din naka kasan ko ihisani xai maka" Khalil ya girgiza
kai yace "To ai bani da account din ne" Aminu yace "Kashh" Nihad ta daidaici lkcn
fitan Abbanta ta fito parlor da sauri yana ganinta yace "Yauwa kin amso account
din" Tace "Abba bashi da shi, kawai ka sa a na kawata Husnah ita ta ma san wajen
gyaran don nata ma ya ta6a lalacewa kamar nawa, don haka ita xata raka mu" Yace
"Okay, forward the account to me via Sms" Tace "Toh Abba nagode, Allah ya kara
budi" Yace "Ameen" Daga haka ya fita parlon Mumy tayi masa Allah ya tsare, Umma na
tsaye bakin kofar kitchen tana kallonsu, Bayan fitan Abba Nihad ta juya da sauri
xata bar wajen Mumy tace "Zo nan me xa a gyara?" Tace "Mumy laptop dina ne yake
bani matsala shine xai tura min kudin gyara" Mumy tace "Toh amma lallai sai an sa
kudi account din Husnah? Me yasa baxa ki je ki gyara account dinki ba, kuma nace
maki bana son alakar ku da yarinyar nan kin ki ji, wai sai na fara nakada maki duka
a gidan nan xaki nutsu Nihad?" Nihad ta marairaice tace "Mumy Coursemate dita ce
fa, dole muna haduwa a class ko ban kulata ba ita tana kulani kuma ita kadai tasan
inda ake gyara laptop din nan tunda nata ma ya ta6a lalacewa" Farooq yace "Dauko
laptop din naki da ya lalace ki kawo min" Juyawa tayi ta kallesa, Umma ta karaso
parlon tace "A saboda ka fara gyaran laptop??" Mumy tace "Ta dai je ta dauko masa
laptop din da ya lalace" Umma tace "Toh naga ai ba shi ya bada kudin gyaran ba da
xai hau tuhumarta" sum sum Nihad ta wuce sama, cikin lkci kankani ta shirya ta dau
jakar laptop dinta ta fito, Umma kadae taje tayi ma sallama Umma tace "Toh Allah ya
tsare daughter" Aminu ya
kalli Khalil bayan ta fita yace "Kai fa yanxu huta roro, adaidaita take hawa xuwa
duk inda xa ta." Nihad bata dawo gida ranan ba sai da sabon Iphone dinta dal a
kwali, babu wanda ta sanar ma ta canza waya banda Nihal da Umma, Umma na jujjuya
wayar tace "Gaskiya ne er daddy, yanxu duk kawayen naki su ma irin wannan ke
hannunsu kenan?" Nihad ta washe fararen hakoranta tace "Ehh wllh Umma, shi yasa
nima na dage sai da na canza, ai abun kunya ce ace ni kadai ce ban canxa waya ba a
cikinsu" Umma tace "Ai ko kina da gaskiya abun ki" Nihad tace "Umma kinsan me?"
Umma tace "Aa sai kin fada" Nihad tace "Umma xa mu fara exams nan da kamar sati uku
kuma wllh ina son in koma hostel don in dinga karatu sosai, nasan Mumy da Ya farooq
xa su xuga Abba kuma baxai bari in koma ba, pls ko xaki taya ni convincing Abbana?"
Umma tace "Gaskiya ya kamata ki koma hostel din don ki maida hankali kiyi karatu
sosai, amma kinsan me xai faru?" Nihad tace "Aa" Umma tace "Zan ce ma Abbanku Mijin
Kamila xai yi tafiya kasar waje kuma xai yi kusan wata biyu a can, tace ki je ki
dinga tayata kwana idan ya so daga can sai ki dinga xuwa makaranta, ita ma Kamilan
xan sa ta kira Abban naku" Nihad ta wara ido cike da farin ciki tace "Yauwa Ummana,
wannan shawarar taki tayi wllh" Umma tace "Kinga kawai daga nan sai kiyi komawarki
hostel har sanda xa ku gama jarabawan, babu wanda xai san baki gidan Kamila" Nihad
tace "Ai kuwa Umma, don Allah gobe da safe kiyi ma Abba maganar da wuri, on
Thursday ma nake son in koma ni dai" Umma tace "Toh shikenan, Allah ya kai mu
goben, ai gobe Wednesday" Nihad ta fita dakin cike da farin ciki, shi yasa take son
Umma, haba she will be free for a while, babu me takurata. Da safe babu wani bata
lkci Umma tayi convincing Abba, yace "Toh Allah ya kai mu alhamis din" Umma tayi
murmushi tace "Ameen Yallabai, sai kayi ma Maryam magana da kanka ko?" Yace "Aa
kema xa ki iya yi mata ai, menene a ciki" Umma tace "Aa gwara dai kai kayi mata,
kace mata Kamila ce ta roki alfarman Nihad ta koma wajenta na kwana biyu mijinta
xai yi tafiya" Abba yace "Ohk, amma suna da driver ne a can da xai dinga dropping
dinta school?" Umma tace "Anya, da yake kasan shi yake ajiye kamilan duk inda xata
je" Abba yace "Toh duk safiya sai Ibrahim ya dinga xuwa can yana daukarta ya ajiye
ta makaranta, when ever her lectures is terminating sai ta gaya masa yaje ya
dauketa ya maida ta gida" Umma tace "Hakan ma yayi kam" kafin Abba ya fita aiki ya
shiga bangaren Mumy, nan ya sanar mata abinda Umma tace masa, Mumy tayi shiru
alamar ta ma rasa abinda xata ce, Abba yace "Sai ki gaya ma Nihad din ta fara
shiri" Mumy ta sauke boyayyen ajiyar xuciya tace "Alhaji idan Nihad taje gidan
Kamila babu me kwaba mata, kasan ta da rawan kai fa, tana nan gida ma ya aka karke
balle bata gida" Abba yace "So what are u insinuating?" Mumy ta girgiza masa kai
kawai, Abba yace "Kar taje ta taya er uwartata xama kenan?" Mumy tace "Ko daya ba
haka nake nufi ba" Abba yace "Toh Maa sha Allah, gobe alhamis ta shirya ta koma can
gidan" Daga haka ya fice daga parlon, har ran Mumy bata son xuwan Nihad gidan
Kamila amma to ya xata yi? Hakan ya sa ta tunani iri iri.

Barka da sallah fams, Allah Ubangiji ya maimaita mana

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD*💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

Har daki Umma ta tadda Nihad tace "Toh Abbanki ya amince sai ki fara hada kayanki"
Cike da farin ciki Nihad ta mike ta rungumeta tace "Nagode sosai Umma" Umma tace
"Sai dai fa Abbanki yace driver xai dinga xuwa duk safiya yana daukarki ya kai ki
makarantar sannan idan kun gama lectures ya maida ki gida" Nihad ta zaro ido tace
"Toh Umma ya xan yi?" Umma tace "To na dai amsa ma Abbanki, amma ke yanxu sai ki
samu Drivern kice masa ba sai ya je ba, xaki dinga tafiya da motar Kamila, should
Incase Abbanki xai masa magana...." Nihad tace "Toh shkkn Umma" Umma tace "Xaki
makarantar yau?" Nihad tace "Ehh ina da lectures karfe sha biyu" Umma tace "Da
sauran lokaci ai, sai ki fara harhada kayanki against tomorrow..." Daga haka Umma
ta juya ta fita dakin, Murna a wajen Nihad ba a cewa komai, she is going to have
enough freedom yanxu, wanka ta shiga bandaki tayi sannan ta fito ta shirya, bayan
ta shirya ta fita xuwa bangaren Mumy, Mumy na gyaran bedroom dinta Nihad ta jingina
da kofar dakin da damuwa tace "Mumy kin ji abinda Abba yace?" Mumy ta kalleta tace
"Na me kenan?" Nihad ta marairaice tace "Mumy ni ba son zaman gidan Aunty Kamila
nake ba, it's so boring there, ni kuma ban san ya xan yi ba" Mumy tace "Then u
speak for ur self Nihad, ni me kike son ince a nan?" Nihad tace "I don't Know what
to tell Abba" Mumy tace "Ki nemi abinda xaki ce masa ai baxai maki tilas sai kin ji
ba" A hankali Nihad tace "Toh" Daga haka ta fita daga dakin ta koma dakinta, hada
kayanta ta shiga yi a akwatunan ta cike da farin ciki, bayan ta gama ta sauka
downstairs tayi breakfast, sae wajen karfe sha daya da rabi ta fita gidan zuwa
makaranta ranta fari sol, yau ma dai adaidaita Sahu ta tafi ta hau bata bi ta kan
Khalil ba, su Husnah da Naf har sun fi ta murna da ta sanar masu xata dawo hostel
ta kuma gaya masu irin plan din da Umma tayi ma Abbanta, Husnah tayi shewa tace
"Kai amma Allah ya shi ma wannan Umman albarka, Allah tana sonki sosai, ta san kan
komai..." Nihad tace "Ke dai bari, ba don ita ba i will keep on being miserable in
that house ga Yaya Farooq ga Mumy, the house is already a living hell for me, yanxu
gobe xan taho da kayana hostel, har na gama hadawa kafin in fito" Husnah tace "Kuma
albishirin ki, kin san saurayina ya kama mana tsadadden hostel a off K, xuwa next
week xa mu koma wllh..." Nihad tace "Haba dai" Husnah tace "Wallahi, dama ina ta
son xan gaya maki sai in manta, yanxu kinga Da ni, ke, Naf, Zully, da Ummi xa mu
xauna dakin, ita Ummi part time xata dinga xama kinsan tafi zama wajen saurayinta
sai in baya gari ne take xuwa hostel" Nihad tace "But bamu yi yawa ba Husnah?
Kinsan fa bana wani son takura a rayuwata" Naf dake danna wayarta tace "Kin ji ki,
2 bedroom ne fa sannan har da parlor with two toilet, ai baki kai ni rashin son
takura ba" Nihad tace "Ohk that's enough...." Kamar shekaranjiya da jiya yau ma dai
haka suka shiririce a Cafeteria babu wanda ya shiga lectures cikinsu, daga karshe
ma suka fita xuwa cin pizza a cikin gari, suna wajen cin pizza Nihad tace "Lah
gashi har xan dawo hostel ba ku je gidan mu kun ga wawan yaron can ba" Husnah tace
"Ai ko yau ya kamata kawai mu je" Nihad tace "Toh ae ke wannan gashin dake kanki ne
matsalar kuma ya Farooq na gari wallahi" Husnah tace "A jakarki ba kina yawo da
Hijab din sallah ba" Nihad tace "Eh" Husnah tace "To ara min kawai in sa don baxan
iya wani komawa hostel ba" Nihad tace "Ohk" Zully tace "Kawai ku tashi mu tafi
yanxu tunda biyu ya wuce" Naf tace "Amma yana gidan idan mun je yanxu?" Nihad tace
"Nace maku 24/7 babu inda yake xuwa, da ma talla ya kasa a bakin gate din da ya
dinga ciniki" duk suka kwashe da dariya, tashi suka yi gaba daya suka nufi motar
Naf Husnah ta shige gaba, Nihad da Zully suka zauna baya, gaba dayansu tsadadden
abaya suka saka, Nihad ce kadai ta sa atamfa da gyale. Karfe uku da yan mintuna Naf
tayi parking dai dai gate din gidansu Nihad tace "Ashe dai xan iya gane gidan"
Husnah tace "Ka ji ta bayan na gama baki direction kenan" Nihad ta sauka daga motar
praying and hoping that khalil na bakin gate, sauran yan matan ma duk suka sauka
daga motar, ta shiga gaba suna biye da ita har suka shiga gate din gidan, Aminu ya
mike yana masu barka da xuwa, Nihad na kallonsa daga sama har kasa tace "Ina
Drivern?" Aminu yace "Ai ko minti biyar bai yi da barin nan ba, yaje can ciki ya
watsa ruwa yace min" Nihad tace shit a xuciyarta, why today of all days xai bar
bakin gate din, kallon su Husnah tayi sai kuma da turanci tace masu su shiga ciki
kawai kafin su fito xai dawo bakin gate din, a haka duk suka bi ta har xuwa main
parlor din gidan, Aminu ya bi su da kallo, direct parlon Umma ta tafi da su, Umma
ta fito daga dakinta jin sallama tana kallonsu tace "Sannunku da xuwa" Duk suka
gaisheta suka xauna saman kujera, Nihad tace "Umma frnds dina ne da nake yawan baki
labarinsu, Zully da Naf, Husnah kuma tana xuwa gidan nan ai kin ganeta ko?" Umma
tace "Kwarai kuwa na gane Husnah, sauran ne dai sai yau na san su, Allah sarki,
sannunku da zuwa yan mata, ya karatu?" Duk suka amsa da Alhamdulillah, Umma tace
"Madallah, kun kwaso rana kuwa" Daga haka tace "Ina zuwa" fita tayi daga parlon,
Naf tayi kasa da murya tana kallon Nihad tace "Is she ur step mom that u are
talking about" Nihad tace "Yeah she is" Naf tace "Waow she is really nyc wllh, very
nyc woman" Nihad tayi Murmushi tace "Sure she is" Ba a dau lkci ba sai ga Hafsah da
tray din lemo da ruwa ta ajiye masu bayan ta gaishe su ta fita, sai gata ta dawo da
warmer din abinci da plates da spoon, ta ajiye ta fita, duk suka sauko suka yi
serving kansu, Nihad ma ta dau plate ta debi abincin. Aminu na ganin shigarsu Nihad
gida dama ya tafi da sauri ya kai ma Khalil tsegumin Nihad ta xo da kawayenta su
biyar suna ta tambayarsa da harshen turanci, ko minti daya bai kara a chalet din ba
ya koma bakin gate da sauri ya zauna, sai bayan la'asar su Naf suka shirya xa su
bar gidan bayan sun ci sun yi nak, har da coslow Umma ta hada masu, Umma tace "Toh
kin kai su sun gaida Maryam kuwa Nihad?" Nihad tace "Tana nan ko?" Umma tace "Aa
tana ciki, su je su gaisheta" Ta fita da kawayen nata xuwa ɓangaren Mumy, duk basu
xauna ba suka gaida Mumy da bata wani sake masu fuska ba, kai kana ganinsu kaga
yara marasu tarbiya marasu kamun kai, Nails Naf tayi fixing a farcenta, Zully kuwa
kana iya hango tatoo dake bayan wuyanta duk da mayafin abaya dake jikinta, Husnah
kuma boobs dinta da bayanta ba a cewa komai kuma farko da Mumy ta santa lkcn
farawansu makaranta ba haka take ba, yar siririya ce ita ma, amma lkci daya ta dawo
uwar mata, Duk gaba daya sun tsargu da kallon da Mumy ke masu, Nihad tace "Za su
wuce ne Mumy shine suka shigo su gaisheki" Mumy tace "Toh maa sha Allah, Allah yayi
albarka" suka amsa da Ameen suka fita daga parlon, Mumy ta kira Nihad ta dawo, Mumy
na kallonta tace "Kar ki kuskura ki wuce bakin gate din gidan nan" A hankali Nihad
tace "Toh" Daga haka ta juya ta fita tana turo baki. Downstairs ta tarda su, Zully
tace "Ur mother is too serious oo" Nihad ta kyabe baki ta fita suka bi bayanta, Naf
tace "The real African Mothers they are talking about" Duk suka kwashe da dariya,
tsaye Nihad tayi balcony ganin har sannan Khalil bai fito ba banda Aminu kawai da
take hangowa a bakin gate, Naf tace "Toh ina ɗan iskan drivern ne?" Nihad tayi
shiru, sai kuma tace "Ina xuwa, ku jira ni" Gun Aminu ta tafi tana kallonsa tace
"Kai Aminu har yanxu bai fito bane, zai ɗan rage ma kawayena biyu hanya ne" Aminu
yace "Ni ma kin ga shi nake ta jira a nan Hajiya" Juyawa tayi ta koma balcony tace
"Idan na tafi chalet da few minutes ku biyo ni can din" Tana fadin haka ta dau
hanyar chalet din, bata ga takalmin kowa a bakin kofa ba, dama isiya da Saminu
gantalallu ne wani lkcn idan suka gama duk abinda suke da safe sai su fita, su da
dawowa kuma sai biyar xuwa shidda, a hankali ta bude kofar parlon duk da haka sai
da yayi kara, ta shiga da takalminta tana yamutse fuska tana bin ko ina da kallo,
ba laifi yau parlon bai yi kaca kaca ba, kuma babu wari, cikin sanda ta nufi
corridor din dakuna, ta kai hannu handle din kofar dakin da Khalil yake ta murda a
hankali ta tura kofar dakin, mikewa zaune yayi da sauri daga kwancen da yake saman
gado, lkci daya ya hade rai kamar yanda ita ma ta hade rai, Tana masa wani kallo
tace "Samun waje, kana bakin aikin ne xaka shanya baki da yamman nan kana bacci?"
Khalil ya dau pillow ya daura kan wayarsa dake gefensa sannan ya saukar da kafarsa
daga saman gadon, kallon fararen ƙafafuwan nasa take wa enda kamar bai ta6a taka
kasa ba har ya mike tsaye calmly yace "Don ina aiki gidanku ba shi ne ya baki daman
ki fado min daki kanki tsaye kamar ba musulma ba Hajiya" Wani dariyar rainin
hankali tayi tace "Toh ai naga ba da dakin ka zo gidan ba, ko da shi ka zo?? kuma
ashe kasan aiki kake gidanmu amma kake min rashin kunya iri iri saboda kai
fitsararre ne, banda rainin hankali ma yanxu lokacin shigowa daki a kwanta ne? Shi
kansa mai gidan naga yana wajen aiki yanxu haka, to idan ka ga dama ka fito Mumy
tana kiranka, sako ne dama aka bani in isar maka kuma na isar, idan kuma baka ga
dama ba sai ka shanya bakin ka ci gaba da baccin..." Jin motsi a parlor ta juya ta
ga su Husnah bakin kofar duk sun shigo, alama tayi masu da su karaso, Khalil dake
ta lura da ita ya karasa bakin kofar dakin bata ankara ba kawai gani tayi yayi
banging kofar dakin almost on her face sannan ya sa makulli ya kulle, buda baki
tayi da shock tana kallon kofar su Husnah suka karaso da sauri, tana zaro ido tace
"Kun ga abinda yayi min yanxun nan" Naf ta kwankwasa kofar da karfi tace "Ashe dai
kai karamin ɗan iska ne mahaukaci tunda har ka kulle kofar, da ka jira mu karaso
kaga ikon Allah mana, wallahi da sai mun ji uban da ya tsaya maka yau kafin mu bar
nan, kuma wallahi kaji kunya tunda har mata suka tsorata ka ka kulle kofa da sauri"
Nan duk suka hau gaggayan bakaken maganganu marasu dadi a bakin kofar dakin, ita
dai Nihad mamakin abinda yayi mata
ya sa ta kasa cewa komai sai kallon kofar take, suka kare masa zagi na cin mutunci
tass sannan Husnah na huci tace "Mu je, ai akwai wani lokacin, ni ban san shegen
matsoraci bane ba ma ai...." Duk Khalil na jin su, and he was calming himself and
controlling his mood at the same time, duk da it's too much and too heavy for him,
lokaci daya launin idonsa ya canza, daga karshe ya daina juyo muryarsu gaba daya,
Mikewa yayi walking slowly ya tafi bakin window ya tsaya yana kallon waje ko
kiftawa baya yi, tunda ya xo gidan sai ranan ya ji da gaske he truly hate the sight
of Nihad, at first he was trying his best not to hate her sbda bai iya tsanar
mutum, shi yasa yake kokarin ganin bai tsane mutum ba no matter what, but he now
realized he hate everything about her, da ya san xai zo gidan nan har ya hadu da
ita da ya hakura da zuwan nasa no matter what and he is going to loose nothing,
juyawa yayi ya tafi jakarsa ya bincika har kasa ya fiddo wani abu me kamar diary da
pen dinsa, ya bude plane page yayi rubutu da bai wuce layi uku ba ya ajiye pen din
yana kallon takardan, rufewa yayi ya mayar karkashin jakar ya kulle sannan ya mike
ya koma gun window din ya tsaya, he is so hurt, it's been long he felt this way,
but they can't just come and insult him then go scot free, wayarsa dake vibrate
saman gado ya karasa kamar bai son tafiyar ya daga pillown ya dau wayar, Nihal ce
ke kiransa, ya ajiye wayar ya zauna gefen gado har ya katse, sake kira tayi hakan
yasa ya dauka ya daga ya kai kunne cikin low voice yace "Barka da yamma Hajiya"
Nihal ta gaishesa tace "Friend dita fatima tace min ka amsar min sakon nagode
sosai, Allah ya saka da alkhairi" Gently yace "Ameen, ya karatu?" Tace
"Alhamdulillah" Yace "Allah ya bada sa'a" Tace "Ameen nagode" Yace "Ki turo number
Tailor din naki" Tace "Toh xan tura maka, nagode" Yace "Yauwa sai anjima" Daga haka
ya katse wayar ya ajiye gefensa. Da daddare Nihad ta shiga bangaren Umma da
sleeping dress dinta, zama tayi a bedroom dinta har ta fito daga bandaki tace "Ya
aka yi Nihad?" Nihad tace "Umma dama wancan drivern xaki taya ni yi ma magana gobe
da safe xai kai ni can gidan Aunty Kamila da kayana idan ya so daga can sai Naf ta
zo da mota ta kwasar min kayan mu tafi hostel" Umma tace "Toh ke me yasa baxa kiyi
masa maganar ba, tsoronsa kike ko me?" Nihad ta wani zaro ido tace "Cabdi, inji
tsoron wa? Ko Abbana bana tsoronsa sai wani mere Drivern gidanmu, kawai bana son ko
wani magana ya sake hadani da shi har abada a gidan nan, don naga ba shi da manner
sannan ya gama rainani, tunda Mumy ta mareni a gabansa shkkn ya daina respecting
dina yana ganin dai dai muke, duk Mumy ce ta janyo min komai, to wannan yasa na yi
vow har motar ma baxan dinga shiga tare da shi ba, wannan ma kawai dole ne ya sa
don babu yanda xa ayi kayana ya dau adaidaita sahu" Umma tace "Balle ma shiga
adaidaita Sahu ba girmanki bane, ita kuma Maryam in taga disgaki gaban ma'aikatan
gidan shine dai dai sai ta ci gaba, shi yasa a rayuwa kar ki kuskura ki raga ma
talaka ina maki wannan hudubar, don da ya ga fuska shikenan raini sai wanda ya
manta, barin yan kauyen nan shi yasa ko kallon arziki kar ki yarda ya hadaku ma"
Nihad tace "Ai ni dama bana masu kallon arxiki Umma" Umma tace "Ya dai fi miki,
ajin ki daban da nasu, shkkn ki je ki kwanta goben xan masa magana idan Allah ya
kai mu" Nihad tace "Nagode Umma" Zata fita dakin Umma tace "Kuna dai waya da Aliyun
ko?" Nihad ta juyo tace "Ehh muna yi, yanxu ma da shi muka gama magana na fito"
Umma tace "To madallah, yaushe xai kara zuwa?" Nihad tace "Umma kinsan akwai wani
business din Abbansu a can kasar waje shi ne manager so he is not always in
Nigeria, though sauran business din Abban nasu na nan kasar ma duk shi ke running
dinsu, haka ne ma yasa bayan watanni kadan yake shigowa Nigeria, amma yace min in a
month time xai shigo in sha Allah" Umma tayi shiru, Nihad tace "His father owns a
big company shi da wani White Man, so Aliyu is managing it for him in there" Umma
ta ɗan yi murmushi tace "Ba shakka, Allah ya sanya Alkhairi, kice koman baban nasa
a hannunsa yake" Nihad tace "Ehh, he is his dad favorite also" Umma tayi murmushi
tace "Kamar ke kenan ko" dariya kawai Nihad tayi ta nufi kofa Umma ta bi ta da
kallo har ta fita daga dakin sai kuma ta sauke ajiyar xuciya. Washegari Umma ta
samu Khalil bayan ya dawo daga kai su Amina makaranta, da ladabi ya gaisheta
fuskarta kamar bata ta6a dariya ba tace "Kai nan da karfe tara xaka kai Nihad gidan
yayarta" Khalil da kansa ke kasa yace "Toh Hajiya" Juyawa tayi ta bar sa wajen a
tsaye, ya daga kai ya bi ta da kallo. Kamar yanda Umma tace karfe tara saura Nihad
ta fara fitowa daga akwatunan ta nan balcony ta ajiyesu ta tafi bakin gate tana
kallon Khalil dake zaune, Ta ɗan tabe baki tace "Ga akwatunan da xa a sa a booth a
can balcony" Ko kallon direction din da take tsaye bai yi ba, sai ma kara hade rai
da yayi, tace "Malam magana fa nake maka fa" Still khalil yaki kallon inda take
balle ta sa ran yace wani abu, Aminu ya mike da sauri ya tafi balcony din Nihad ta
bi sa da kallo, sai kuma ta kalli khalil cike da takaici amma ta kasa ce masa
komai, har Aminu ya gama kwaso kayan ya ajiye a garage, ya taho gun khalil yace
"Ɗan bude booth din a xuba su" Mikewa Khalil yayi ya tafi gun motar bayan ya bude
booth ta makullin ya shiga driver seat, Nihad ta bi sa da wani shegen kallo, tana
mamakin irin wannan feeling din da yake, sai kuma ta ji haushin kanta da bata sa
Aminu ya kwaso akwatunan ba tayi ma wannan banzan magana ya kyaleta, bayan ya tada
motar ta tuna bata ma Mumy sallama ba, komawa cikin gidan tayi ta tafi bangaren
Mumy, khalil ya fi minti sha biyar a kofar gida yana jiranta cikin mota, tana sane
tayi xamanta cikin gida don yayi ta jiranta a mota, sai da taga ta 6ata minti
ashirin sannan ta mike ta fita tana rike da handbag dinta, back seat ta zauna ta
kulle motar tana kallonsa, ya ɗan kwantar da driver seat ya rufe idonsa kamar mai
bacci, da har xata masa magana ta tuna sabon vow din da ta dauka na cewar ba
maganar da xai sake hadata da shi, yau ne last. Har bayan minti biyar bata ga ya
bude ido ba balle ya tada motar su bar wajen, ta wani hade rai tana kallonsa, wasa
wasa har sai da aka yi minti goma suna nan a haka, tana ta control din kanta kar
tayi masa magana, Aminu dai sai lekosu yake yana dariya kasa kasa, wato sai ya rama
shanyasa da tayi cikin mota, tana ta xaune motar ta cika tayi fam amma taki cewa
komai kuma bata sauka ba har sai da aka yi minti ashirin da biyar sannan ya bude
ido ya gyara zamansa ya kunna motar suka bar wajen, da yake ya ta6a kai Nihal gidan
yayarsu kamar yanda ta ce masa, saboda shi ma baya son wata magana ta hadasa da
Nihad direct gidan ya nufa ba tare da ya damu can din ne ko ba can ba, the ride was
so silent, ko wannensu fuska a tamke, lkci lkci take satan kallonsa sai kuma ta
kyabe baki ko ta ja tsaki can kasa kasa, har yayi parking dai dai gate din gidan
kamila ya kashe motar, Nihad ta bude ta sauka ta tafi ta kira mai gadin gidan tace
"Don Allah ka zo ka sauke min kayana a mota" Ya fito daga gate din ya bude booth
don khalil ya riga ya bude, nan ya ciro mata akwatunan ya kai su bakin gate, kafin
ya ciro na karshen tana kallonsa tace "Don Allah ka je kace ma wancan drivern nace
ba sai ya wani zo yana kai ni makaranta ba don bana bukatarsa kwata kwata" Mai
gadin ya tafi yana kallon Khalil bayan sun gaisa yace "Wai Hajiya tace ba sai ka zo
kai ta makaranta ba" Khalil yace "Ok" Juyawa yayi ya tafi ya cire akwatin karshe ya
kulle booth din, khalil ya ja motar yayi zoom off, Nihad ta bi sa da harara tace
"Uwa motar ubansa, wllh ni ce sanadin aikinka a gidan nan mu dai je zuwa, sai kayi
da ka sanin sanina a rayuwarka" Shi da mai gadin kallonta yake yana kokarin kai
akwatunan cikin gidan, ko karamin bata dauka ba haka ta bar masa su dukka ta wuce
ciki, Kamila dake parlor tace "Mutanen Maryam Abatcha American University" Murmushi
Nihad tayi tace "Aunty ina kwana?" kamila tace "Lafiya lau, amma fa ki kira warce
xata xo ta dau kayan naki xuwa hostel don karfe sha biyu xan fita nima" Nihad tace
"Ehh tace min karfe sha daya xata zo" Kamila tace "Toh ya dai fi, daxu ma Mumy ta
kirani wai in sa maki ido nace toh" Nihad tayi dariya tace "Aunty kamila mumy sai
tayi ta treating dina kamar wata er yarinya" Kamila tace "Gaskiya kam, ga ki ke ba
yarinya ba, makarantar ki ma ba ta yara ba" Dariya kawai Nihad take, Kamila tace
"Atoh dai" Karfe sha daya Naf da Husnah suka iso kofar gidan Kamila na tsaye
compound duk suka saka akwatunan a motar Naf, Bayan sun gama tace "Toh Allah ya
tsare" Nihad tace "Ameen Aunty" su Naf suka mata sallama, tana kallonsu har suka
bar compound din ta juya tayi komawarta ciki, murna a cikin Nihad ba a cewa komai,
a haka ta koma rayuwarta a hostel babu me sa ta babu me hanata, duk sanda Mumy ta
kirata sai ta shige bandaki ta kulle su yi waya don kar ma taji hayaniyar su Naf da
Husnah, night party kuwa sai wanda suka mance ne baxa su ba, duk yanda suka so
rinjayar Nihad ta dinga shan kwayoyin da suke sha bata ta6a sha ko da wasa ba, sau
daya Husnah ta shammace ta ta xuba mata a lemo shi ma sai da ta kwana ta yini tana
baccin wahala, hakan ya sa suka rabu da ita da batun drugs, sai kuma suka fara jan
ra'ayinta zuwa kwanan hotels da suke da boyfriend dinsu, nan ma dai ta ki, ko min
daren da suka yi a waje ita dai sai ta dawo hostel, duk sanda suka yi waya da Umma
sai ta ja mata kunne kan cewar kar fa ta dinga bin duk wani wuri da xata iya haduwa
da Abbanta ko Farooq, ita kanta Nihad is so careful about that, a haka har suka
fara exams, duk cikinsu Nihad ce ke maida hankalin karatu, sauran ko bude takarda,
duk sanda Mumy ta bukaci Nihad ta zo gida sai tayi karyan karatun exams yayi mata
yawa, bayan an gama exams din ma don kar Mumy tace Nihad ta zo gida Umma ta sa
kamila ta kirata tace xa su garin mijinta, haka nan aka kare hutu Nihad na hostel
abun ta suna baza life, su ne har Kaduna da hutun,
sau biyu ta je gidan Kamila shi ma ɗon Aliyu ya shigo kasar ne xa su hadu sai taje
gidan kamila shi ma ta ce masa mijinta ne yayi tafiya take taya ta zama......

One more free page.

07087865788 ✍🏻 *NIHAAD* 💖💖

✍🏻
By _Khaleesat Haiydar_

End of free pages...

Har aka kare hutun wata biyu Nihad bata nufi hanyar gidan Kamila ba balle nasu
gidan, kamar yanda Mumy ke kiranta kullum haka ma Abbanta, a ko da yaushe cikin
demanding kudi take daga wajensa kuma ko sau daya bai ta6a hanata ba, da tayi
magana xai tura mata fiye da yanda ta tambaya, Umma ma kusan kullum sai ta kirata,
duk kuma wannan abun Abba da Mumy na xaton Nihad na Kebbi tare da Kamila, Umma ce
kadai ta san Nihad na kano sai kamilar, gaba daya Kamila ta daina xuwa gida a zuwan
tana can kebbi, idan da wani abu sai dai Umma ta shirya ita taje gidanta, A kullum
Mumy bin Nihad take da addu'a, ta rasa dalilin da hankalinta ya ki kwanciya tun
barin Nihad gidan, bata da rest of mind kwata kwata, gashi babu abinda xata iya yi
game da hakan, ko me xata ce ma Abba baxai ta6a fahimtar ta ba sai dai ma ya juya
xancen, a ko da yaushe ta kira Nihad sai ta mata nasiha a kan ta dai kula kuma
banda rawan kai da yin kawaye, sai Nihad tace "Mumy ni da ba kowa na sani ba a
garin sannan babu inda muke zuwa, kawai karatu nake ta yi against next semester" A
haka dai kullum take gaya ma Mumy. Ranan wata juma'ah Nihad da kawayenta duk suka
shirya xa su je duba wata kawar Zully da tayi rashin lafiya, Naf ke driving din,
Husnah tace "Amma fa ku kirata ko an sallameta asibiti kar mu je mu yi wahalar
banza" Zully tace "Ai ko dai" wayarta ta dauka ta kira kawartata Yusra ta sa
handsfree, tana dagawa Zully tace "Ya kuna asibitin har yanzu?" Yusrah tace "Wani
asibiti da aka sallame mu tun jiya, ni kin gan ni a Bristol ina shan Ac, Saurayina
Alhaji Muktar ne ya biya kudin kwana hudu sai gashi tafiyar gaggawa ya kamasa yau
da safe kuma yace min xai kwana uku a Abuja, sai jibi kudin xai kare shine nace
gwara in yi zamana a nan" Zully ta kyalkyale da dariya tace "Me ya fi ranki, to
bari mu taho can din kawai" Yusrah tace "Ai ko ku zo, ga abinci ga enough drinks,
sannan ga Ac 24/7" Zully tace "To sai mun iso" Tana katse wayar, Naf ta dau hanyar
Bristol, Husnah tace "Mu ma muje mu sha Ac kawai" Dariya duk suka yi, Nihad tace
"Amma yaushe xa mu fito, kunsan ni bana son xuwa irin wajajen nan in broad
daylight" Husnah tace "Mu da xa mu shiga daki mu yi xaman mu meye na wani damuwa"
Nihad bata ce komai ba ta ci gaba da danna wayarta, suna isa makeken hotel din Naf
ta samu wajen parking, Dai dai nan wayar Nihad ya fara ringing, ganin Abba ne ta
ɗan wara ido, Husnah ta kalleta tace "Waye?" Nihad ta nuna mata screen din wayar,
Husnah tace "Ohk, bari kawai mu sauka mu tafi ciki, sai ki tsaya motar ku yi waya,
idan kun gama ki fito ki kulle sannan ki kirani mu gaya maki room number" Nihad
tace "Ohk" Duk suka sauka daga motar, Naf ta mika mata makulli suka wuce ciki, tuni
wayar Nihad ya katse sai ga Abba ya kara kiranta, dagawa tayi hade da sallama tace
"Abba ina yini?" Yace "Lafiya lau dear, how are you?" Tace "Alhamdulillah Abba ya
aiki?" Abba yace "Mun gode Allah, yaushe xa ku yi resuming ne?" Nihad tace "In two
weeks time Abba" Abba yace "Ohk, yaushe kamilar tace maki xa ku dawo?" Nihad tace
"Ana saura 2 days mu koma school, tare da mijin xa mu dawo gaba daya" Abba yace
"Ohk that's good, take care dear" Nihad tace "Alright Abba, bye" Katse wayar Abba
yayi, ta bude motar ta sauka sannan ta kulle, tana rike da jakarta bayan ta kulle
motar ta nufi entrance din hotel din tana kokarin dialing number Husnah, sunanta ta
ji an kira, ta juya da sauri, wani tsohon saurayin Husnah ne, ya nufota da sauri
yace "Hi Nihad" Ta ɗan yi murmushi tace "How are you Kabir" Yace "Alhamdulillah, ya
kwana biyu?" Tace "Cool" Yayi er dariya yace "Kina da appointment yau a nan kenan?"
Ta ɗan kallesa sai kuma tace "Tare da kawayena nake, suna ciki" Yace "Ohk maa sha
Allah, ya school" tace "Fine" A tare suka jera xuwa cikin reception din hotel din
yana jan ta da hira, zaune yake a haraban hotel din karkashin inuwa tare da wani da
baxai wuce sa'ansa ba yana sauraron duk abinda yake ce masa, da ido ya bi ta da
Kabir, at first he quickly imagined ba ita bace kamace kawai, but yanayin tafiyarta
da kuma jakar hannunta wanda duk ya sani ya sa shi ajiye goran ruwan dake hannunsa
ya bi ta da kallo babu ko kiftawa, Buga table din abokinsa yayi da mamaki yace
"Heyy!!" Da sauri ya dauke idonsa daga kallonta ya kalli abokin nasa, abokin yace
"Why are u staring at her that way, burge ka tayi ko me? Kaga yarinya da saurayinta
sun zo holewarsu kayi ta kallonta?" Still bai ce komai ba sai kallon abokin nasa
yake babu ko kiftawa, Abokin yace "Khalil" Sauke idonsa yayi daga kallonsa sai kuma
ya sauke ajiyar xuciya yace "Yea mamaki abun ya bani shi yasa na bi su da kallo"
Dariya Sultan yayi yace "Haba kai ma ai kasan wannan ba sabon abu bane, yan matan
yanxu kam ai sun xama abinda suka zama sai addu'a, basa ma jin kunyan iskanci
yanxu, ko wani hotels ka bi su ne, baka lura bane ko 10 mins ba ayi ba set of 3
girls suka wuce mu a nan, su ma kuma duk gun samarin suka zo na sani" Shi dai
khalil bai ce komai ba, he was really shock, yarinyar da aka ce tana Kebbi ce ya
gani a Bristol, Sultan yace "Kai dai tunda kana da Nadeeyah and upon her parents
wealth she is decent sai ka gode ma Allah" Murmushi kawai khalil yayi, Sultan yace
"Kuma kuna magana da ita all this while?" Khalil yace "Muna yi" Sultan yace "Tasan
kana kano?" Girgiza masa kai kawai khalil yayi, Sultan yace "Ya batun turawa
gidansu?" Khalil yace "Yana nan" Sultan yace "Toh Allah ya nuna mana, but ya kamata
kayi nazarin duk abinda nace maka Khalil, pls do so Frnd" Khalil ya sauke ajiyar
xuciya yace "In sha Allah, and i appreciate u Sultan" Sultan yace "Nima nagode da
ka bani lokacinka har ka saurareni" Murmushi kawai khalil yayi, Sultan ya mike yace
"Toh ka koma can inda ka samar ma kanka aiki kar a fara nemanka ko" Khalil yace
"Ina jiran wani ne still" Sultan yace "Wa kenan?" Khalil yayi kasa da murya yace
"Another caring frnd like you" Sultan ya sauke ajiyar xuciya yace "All this shall
come to pass in sha Allah Khalil" khalil ya ɗan yi murmushi ya mike tsaye ya mika
masa hannu sannan yace "I truly appreciate ur care Sultan, nagode kwarai" Sultan
yace "Mention not abokina" Har mota Khalil ya rakasa sannan ya dawo ya zauna inda
yake zaune har sannan yana cike da mamaki, har karfe shidda na yamma yana xaune
wajen bai ga fitowar Nihad ba balle shi mutumin da ta shiga ciki da, kiran Aminu ne
ya shigo wayarsa ya ciro ya daga ya kai kunne, Aminu yace "Toh na ji ka shiru daga
cewa xaka bakin titi ka dawo" Khalil yace "Ina nan dawowa yanxu" Aminu yace "Toh ga
manyan mangwaro ma Hajiya Inna ta zo ta bada a ajiye maka" Khalil yayi murmushi
yace "Toh nagode, sai na dawo" daga haka ya katse wayar. Har aka yi magrib Khalil
bai ga fitowar Nihad ba, babu warce ta fado masa a rai sai Mahaifiyarta, ya ji
tausayinta sosai, mata me kirki da mutunta ɗan Adam, and such a nyc woman didn't
deserve Nihad as a child... Wayarsa ya dauka yayi dialing number Nihal ya kai
kunne, tana dagawa tayi masa sallama, ya amsa yace "Ya kike?" Tace "Alhmdlh, ina
yini?" Yace "Lafiya lau, ya lectures?" Tace "Ya shirin jarabawa dai" Yace "Ohh haka
ne, ya shirin jarabawa?" Tace "Alhmdlh" yace "Tare xa ku dawo da er uwarki kenan?"
Nihal tace "Noo, ai ita tana kebbi" Yace "Ko?" Tace "Eh" Yace "Ita da wa suka tafi
kebbi?" Nihal tace "Wannan yayar tawa da ka kai ni gidanta kwanaki" yace "Ohk,
yaushe xa su dawo?" Tace "Jiya da na tambayi Umma tace min nan da sati biyu" Khalil
ya ma rasa abinda xai ce, jin shiru tace "Hello" Yace "Eh ina jin ki, to shkkn,
dama tambayarki xan yi ya jarabawa" Tace "Toh Nagode" Yace "Sai anjima" Daga haka
ya katse wayar, kallon cikin hotel din yayi, yana ta xaune har kusan Isha'i ganin
Nihad ba fitowa xata yi ba ya mike ya tafi can inda yayi parking motar gidansu
Nihad ya shiga ya bar hotel din, direct gidan Kamila ya nufa, bayan sun gaisa da
mai gadin yace "Matar gidan na nan?" Mai gadin yace "Ehh tana ciki" Khalil yayi
shiru, sai kuma yace "Ohk an aiko ni wajenta ne" Mai gadin yace "Toh bari ayi mata
magana" Yana shiga gate khalil ya juya ya shiga motar ya bar layin. Direct gida
khalil ya nufa erasing everything off his mind kamar ba ayi ba, after all it's none
of his business and will neva be any of his business. Bayan sati biyun da Umma tace
ma Abba su Nihad xa su dawo kano, sai ga Nihad tare da kamila a gidan da yamma,
babu irin rokon da Umma bata yi ma Kamila akan su xo gida tare da kyar dai daga
karshe ta yarda suka taho gidan da Nihad, akwatin kayanta daya kawai ta dawo gida
da, tun da suka shigo gate Khalil ke kallon Nihad, ita kuwa shaff ta mance da wani
batunsa a gidan sai yanxu da ta gansa, tana ganinsa kuwa mood dinta ya canxa, shkkn
kuma ta dawo miserable house din nan da driver din nan a ciki, noo gaskiya ita dai
baxata iya ba, xata roki Umma ta yi come up with another plan da xai sa ta sake
barin gidan, Kamila ce kawai ta amsa gaisuwan mai gadi da khalil da ke gaisheta,
Nihad kuwa tafiya take cike da isa ta nufi entrance din parlor, tayi wani kyau ta
kara haske, kana ganinta kasan bata da damuwar komai, ba komai ya haddasa mata kara
haske ba sai cream me shegen tsada irin nasu Husnah da take shafawa yanxu, ga
sabulu ga shower gel, Khalil ya bi ta da kallo, suna shiga parlor Aminu yayi kasa
da murya yace "Kaga yanda tayi wani haske tayi kyau uwa warce ta tafi duniyanci?"
Khalil bai ce komai ba, but he really felt sorry for Abba and Mumy, ya jima bai
hadu da mutane masu kirki da karamci irin tasu ba, a watanninsa kusan shidda a
gidan Abba ya ja sa jiki kamar nasa, ya kai ya kawo yanxu hatta Atm card Abba na
basa ya ciro masa kudi wanda ko Habibu baya ba Atm card dinsa, shi ko Abba ya ya6a
da hankali nutsuwa da girmamawa irin ta Khalil, ya sha gwadasa ya aikesa ya siyo
masa abu sai ya linka kudin sau uku ya basa yace haka ake siyarwa amma in sha Allah
sai Khalil ya kawo masa canjinsa, ya gwadasa ta fanni daban daban wanda shi khalil
bai ma san yana yi ba, duk gidan babu wanda yake da matsala da warce ta zama second
Nihad sai Umma, gaba daya ta dau
karan tsana ta daura masa tun da Nihad ta fesa mata yana waya da Nihal, to uban me
Nihal dinta xata yi da shi, duk abinda take yi kuma baya damun khalil, Usman ma dai
in ya zo basa wani gaisawa, amma Farooq idan yana gari mayar da bakin gate wajen
zamansa yake yi sbda Khalil, xaka yi tunanin ya ta6a saninsa, kawai he enjoys
gisting with him sbda yana magana kamar wanda yayi ilimi me zurfi, gashi he knows
almost everything that's happening in the world wato he is current, suna dadewa
sosai suna hira.... Sai kuma Hajiya Inna da takanas sai ta aiki dreban gidansu
Hamid ya zo ya kira mata khalil xata aikesa don hankalinta yafi kwanciya ta basa
dukiyarta a kan yaran gidan, kuma aiken baya wuce na dari ko dari biyu. Tun da
Nihad ta shiga bangaren Mumy bayan ta fito daga bangaren Umma Mumy ke kallonta, ita
dai tana xaune tana ta danna waya, Mumy tace "Wani mai kike shafawa Nihad?" Nihad
ta daga kai tace "Mumy cream din Aunty Kamila ne tace in dinga shafawa" Mumy bata
ce komai ba, bayan few seconds tace "Ina sauran kayanki?" Nihad tace "Mumy Aunty
Kamila tace in bar su a can gidanta" Mumy tace "To tashi driver ya kai ki ki kwaso
yanxu" Nihad ta marairaice tace "Mumy ni fa ba abinda nake bukata a cikin kayan"
Tsawa Mumy tayi mata tace "Baxa ki tashi ba" Tashi Nihad tayi kamar xata yi kuka,
sai kuma tace "Toh Ai Aunty Kamilan na nan ki bari idan ta koma gida Mumy" Mumy
tace "Ba dai gobe za ku fara lectures ba?" Nihad ta gyada mata kai a hankali, Mumy
tace "Toh dama ki tabbatar baki dawo gidan nan ba tare da akwatunan ki ba" Mumy na
fadin haka ta wuce dakinta, Nihad ta turo baki ta mike ta fice daga parlon, ita har
ta mance yaushe rabon a harareta balle a mata fada sai yau... Washegari bayan ta
shirya xuwa makaranta sai da Mumy ta kara jaddada mata kwaso akwatunan ta, har da
guntun hawayenta, bayan ta fito compound ta ji ranta ya kara baci da ta tuna cewar
shegen mutumin nan ne har yanxu Driver din gidan, kuma ita wllh baxata wani je ta
hau adaidaita Sahu ba, tana isa gate suka hada ido da shi don kallon sama har kasa
yake mata, wani matsiyacin kallo tayi masa tace "Da bashi ne kake kallona haka?"
Aminu dai sai gwaggwale ido yake, Ta wani ja tsaki ta ma gwammace taje ta hau
adaidaitan sbda ganinsa kadai na kona mata rai, ficewarta tayi daga gate Aminu yace
"Ohh fitina ta dawo ni Aminu, wllh har na manta da ita a duniyar nan" Khalil dai
bai ce komai ba. Bayan kwana biyu da komowar Nihad gida tana kwance bedroom din
Umma tana bata labarin yanda suka yi da Aliyu jiya da daddare, Umma dake xaune
gefen gadon ita ma ta mike da sauri tace "Kice wllh" Nihad na Murmushi tace
"Wallahi Umma" Wani guda Umma ta saki tace "Alhamdulillah, Allah na gode maka...
Yaushe yace xa su xo?" Nihad tace "Nan da sati biyu" Umma tace "Alhamdulillah,
Alhamdulillah, amma in ji baki gaya ma kowa ba?" Nihad tace "Aa ke kadai da Husnah
na fada ma" Umma tace "Kin ji ki, wacece kuma Husnah, meye na gaya mata xa a kawo
kudin ki? Duniyar nan da ta lalace yanxu ai kowa boye kansa yake, kar ki sake gaya
ma kowa" Nihad tace "Har Mumy?" Nihad tace "Aa ba dai kin gaya min ba ai shkkn, ni
xan mata magana sannan inyi ma Abbanku magana, amma sai xuwa next week" Nihad tace
"Toh Umma" Wani gudar Umma ta kuma saki tace "Allah nagode maka diyata xata xama
surkar Janar jikamshi" Dariya kawai Nihad tayi, Umma tace "Toh sai ki kula ki kama
kanki kar ki sake kula kowa tunda dai kina da tsayayye yanxu" Nihad tace "Toh, amma
Umma yana wani ce min xai rabani da su Husnah" Umma tace "Ahhh!!! shi kuma ya
haka??" Nihad tace "Wallahi, kuma ni banga abinda xai sa ya rabani da su ba" Umma
tace "Toh ke dai kar ki musa masa ku samu matsala, kiyi ta bin sa duk abinda yace
kice to, su kuma ko a hankali ai xa a rabu, ke da kasar waje xa ku xauna? Ko ba
haka ba" Nihad tace "Haka yace min" Umma tace "Toh kinga, su Husnah da ba kasar
wajen xa su bi ki ba" Nihad tace "Ai shine" Umma tace "Kai amma nayi farin ciki da
wannan labarin Nihad, Allah Ubangiji ya nuna na yan baya haka" Nihad tace "Ameen,
Umma bari in dauko wayana" Umma tace "Toh je ki dauko" Daga haka ta fita daga
dakin. Ko da wasa Nihad bata sanar ma Mumy ba, tana ta sabgar gabanta throughout
the week, kuma har tambayarta Aliyun yayi ko ta gaya ma Mumy tace masa eh. Duk da
warning din da Umma tayi ma Nihad na kan cewa kar ta sake gaya ma kowa Aliyu xai
turo sai da ta gaya ma Farooq, kamar yanda take favourite din Abbanta haka take
favourite din Farooq a gidan, a WhatsApp suke chatting ta gaya masa sai ga shi ya
sauka ya kirata, tana dagawa yace "Are you serious?" Tace "Ehh ya farooq" Yace
"Tohh maa sha Allah, Amma Abba bai sanar min ba" Nihad ta zaro ido tace "Yaya Umma
tace xata gaya masa" Farooq yace "Ohk, toh Allah ya kai mu next week din, though
xan shigo kano jibi" Tace "Toh Allah ya kai mu" Sallama yayi mata ya katse wayar,
Tana komawa saman chatting taga message din Nihal tana congratulating dinta, wato
har Umma ta gaya mata, murmushi Nihad tayi tace "Thanks twinny" Washegari da Nihad
ta fito xata school khalil ya bi ta da kallo disgustingly as usual, sarai jiya
Nihal ta gaya masa xa a kawo kudinta next week ta kuma gaya masa daga familyn da xa
a kawo kudin, and he really pity the well reputable family, da shi kansa wanda xai
aureta din, ganin irin kallon da yake mata ta tsaya tana kallonsa tace "Wai kai
Allah ya tsine maka ne da xaka dinga min wani irin kallo idan kaga na fito? Ko da
wani abu da muka hada ne ban sani ba? Toh wllh wllh wllh duk ranan da na sake
fitowa ka min kallon walakanci Allah sai na gaura maka mari, kaji har na rantse"
Khalil na kallonta yace "Ki mari wa?" Cike da rashin kunya tace "In mareka nace, ko
uban waye kai da kake tunanin baxan iya marinka ba? Ni fa wallahi bayan na bar
gidan nan na mance an halicce wani mutum me kama da kai a duniya? Toh akan me daga
dawowa ta xaka dinga bi na da kallon raini?" Khalil bai ce mata komai ba cause the
sight of her is making him feel feverish, ga wani tafarfasa da zuciyarsa yake, jin
bai ce mata komai ba ta ja wani tsaki tace "Banza kawai" Daga haka ta fice daga
gidan, Aminu dake lekosu ta dakinsa ya fito yace "kaii, Allah ya wadaran wannan
yarinya"

Ana saura kwana hudu su Aliyu xa su kawo kudi, Nihad na bacci da rana Kasancewar
ranan asabar ce babu lectures wayarta ya fara vibrate, bude ido tayi don Aliyu yace
xai kirata tana jawo wayar taga wata Coursemate dinta Sajida da ba wani shiri suke
ba ce ke kiranta, da kamar baxata daga ba sai kuma ta daga ta kai kunne, Sajidah
tace "Nihad what is this i am seeing on social media?" Nihad ta bude ido tace
"Kamar me?" Sajidah tace "Hau WhatsApp" Daga haka ta katse wayar, sai ga kiran wata
secondary school mate dinta Hafsah, tana ta kallon kiran sai kuma ta daga, daga
daya bangaren Hafsah tace "Nihad what's happening?" Nihad ta mike xaune tace "Ban
gane ba?" Hafsah tace "Ki hau WhatsApp" Nihad na kokarin shiga WhatsApp sai ga
kiran wata warce suka yi islamiyya tare, kawai haka nan taji gabanta ya fadi, ta
dai daga kiran, Badiyya tace "Nihad garin yaya haka don girman Allah??" Hankali
tashe Nihad tace "Wai me ke faruwa?" Badiyya tace "Ki kunna data" Nan Nihad taji
jikinta ya fara rawa, wani kiran ne ya shigo taki dagawa tayi rejecting ta bude
data ta hau WhatsApp din da sauri, messages ta gani rututu na shigo mata, kawai ta
bude wanda hannunta ya kai, Wata school mate dinta ce ta turo mata video tana
tambayar "what is this Nihad??" Hannun Nihad na rawa ta bude video din, kanta ta
gani with just skimpy undies a saman gado ba kuma bacci take ba, sai kuma taga ta
mike tsaye turning all over jefar da wayar tayi jikinta na rawa tana zaro ido tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" sai kuma ta saki wani kara ta sauka daga kan
gadon ta durkusa kasa, ringing kawai wayarta ke yi amma ta kasa motsawa daga inda
take, bude kofar dakinta aka yi ta daga kai da sauri, Umma ta shigo tana zaro ido
tace "Nihad me ke faruwa a social media yanxu Nihal ta kirani tana kuka, kuma wai
ta kiraki bakya dagawa" Nihad ta kasa cewa komai, bata ta6a zama soo weak all her
life ba kamar wannan moment din, ji take kamar komai na jikinta ma ya daina aiki,
wayar Umma ne ya fara ring ta daga da sauri, Nihal na shessheka tace "Umma ki hau
WhatsApp na tura maki" Umma tace "Tohh" Da sauri Umma ta hau WhatsApp ta shiga chat
dinta da Nihal ta bude video din, salati ta saki bayan ta gama kallon video din har
karshe ta jefar da wayarta kan gado tace "Nihaddd????" Dai dai da second daya wayar
Nihad bai samu breathing space ba, kiran su Husnah ne, Naf, Zully, infact calls
upon calls kawai amma ta kasa kwakkwaran motsi inda take a durkushe balle ta daga
wani waya, sai rufe ido take tana budewa kamar dai warce ke mafarki tana son ta
farka, Umma na tafe hannu ta fashe da kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un, na shiga uku na lalace ni Sumayya, Nihad wa ya maki haka? Garin yaya haka
Nihad?" Bude kofar dakin aka yi Mumy ta shigo da tashin hankali kwance fuskarta,
Umma ta fashe da matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah
mun gode maka ni Sumayya, me xa mu gani haka Nihad" muryan Mumy na rawa tace
"Nihad??" Kawai sai ga hawaye na xuba idonta tana girgiza kai, Wannan ne yasa Nihad
ta fashe da matsanancin kuka tace "Na shiga uku na lalace" Kwalban turare da Mumy
ta gani gaban mirror din dakin ta figa tayi kanta amma tuni Nihad ta shige bandaki
ta sa makulli, Umma kuma ta rirrike Mumy tana kuka tace "Aa Maryam ki kai zuciyarki
nesa kiyi ta furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un, nima shi nake yi" A haka ta
ja mumy dake kukan bakin ciki da takaici suka fita daga dakin.
kafin dare kai ka ce mutuwa aka yi a gidan, gaba daya iyalan gidan Alhaji Abubakar
sun iso gidan Abba, makusantan Mumy duk sun xo gidan, Umma ma yan uwanta da
kawayenta duk suna gidan, Aminu sai bin duk wanda ya shigo yake da kallo cike da
mamaki don ba ace masu kowa ya mutu a cikin gidan ba gashi khalil da yake ma gulma
baya nan tun rana ya fita, kowa kuma ya shigo babu walwala yake nufar entrance din
parlor, all the way from Abuja haka Farooq ya biyo flight ya dawo, Usman ma daga
kaduna haka ya taho... Tun faruwan abun nan Umma ke kuka non stop, handkici hudu
duk sun yi jagab a hannunta, Mumy kuwa in ka ganta sai ka tausaya mata she is so
heartbroken, banda kanninta mata biyu da Yaya farooq da suka jibgi Nihad son ransu
babu wanda yayi attempting ta6a ta ko ce mata komai a gidan...... Tashin hankalin
Nihad bai linku ba sai da taga alamar Aliyu yayi blocking dinta ta ko ina,
WhatsApp, IG, Phone call, Twitter, infact all, kawai sai take fatan Allah ya dau
ranta ta huta kawai, gashi har lkcn ta rasa a ina aka mata wannan video din idonta
biyu ba bacci take ba.....

*Ci gaban labari*

A hankali Nihad ta bude idonta tana bin inda take yashe da kallo, tsakiyar parlor
ne kuma a kasan Carpet, gashi babu kowa parlon, everywhere looks strange to her, da
sauri ta mike xaune as if trying to recall something, dai dai nan aka bude kofar
wani daki ta juya suka yi ido hudu da shi, sai da numfashinta ya dauke na few
seconds da kyar ta jawo numfashin, lkci daya komai ya dawo mata ta kurma wani uban
ihu jikinta na rawa tana kallonsa, sai kuma ta mike a guje tayi hanyar kitchen
kamar mahaukaciya....

Nan na kawo karshen free pages, sai mu hadu a payment group.


Domin samun ci gaban littafin *Nihaad* it is only 500 via 3276052019 fcmb Hauwa
Bello Jiddah

And u show ur evidence via👇🏻


07087865788
Thank you as u patronize and i am assuring u that Nihad will be counted among my
best In sha Allah💖

+234 7014979567[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: At first tsayawa yayi kamar
bazai bi ta ba amma ganin ta kulle kofar kitchen din yayi saurin bin bayanta, Tsaye
ya ganta ta dau table knife tana kuka sosai facing the knife towards her stomach,
ya kalleta daga sama har kasa, sae kuma ya shiga cikin kitchen din ya dau asalin
wuka ya karasa har gabanta ya mika mata yace "In da gaske kike" runtse ido tayi
tana kuka iya karfinta, ya kamo hannunta ya saka wukar a ciki sannan ya koma bakin
kofa ya jingina da wall din wajen ya rungume hannunsa yana kallonta da wani scorned
expression, ta bude ido a hankali ta jefar da wukar ta sulale kasa tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wayyo na shiga uku na lalace" sai kuma ta
daura hannu a ka ta kurma uban ihu tana kallonsa, juyawa yayi ya bata waje, Ko
sanda aka yi leaking Video dinta bata tunanin tashin hankalinta ya kai wanda take
ciki yanxu, she is still yet to believe who she is seeing, wani ihun tashin hankali
ta kuma kurmawa lkci daya kuma tayi shiru, to ko dai aiko sa aka yi gidan, tunanin
hakan ya sa ta hau share idonta gabanta na bugawa da sauri, lkci daya tayi assuring
kanta kawai aikosa aka yi gidan shine ya shigo masu har ciki, da kyar ta mike tsaye
kamar me tsoron taka kasa ta karasa kofar kitchen din ta leko parlon a hankali with
throbbing heart, zaune ta gansa saman kujera, suna hada ido ta wani hade rai har
sannan gabanta na faduwa tayi karfin halin cewa "Malam idan aikoka aka yi sai ka
shigo ma mutane har cikin nan? Wannan wani irin samun waje ne? Duk tsakar gida bai
isheka ba sai ka shigo har nan" Kallonta kawai yake da wani stern look a fuskarsa,
ta wani kara shan kunu tace "ko shi mai gidan ne ya baka damar shigo mana har cikin
nan?" Ba abinda yace mata still, kuma babu alamar xai ce mata komai sai ma dauke
idonsa da yayi, ta dake ta fito daga kitchen din gaba daya, tace "Wai baka jin ina
maka magana ne ko nan din ma rashin kunyan xaka min?" Yace "Ok" Yana fadin haka ya
mike ya juya yayi hanyar kofar fita daga parlon, wani irin kwanciya hankalinta
yayi, taji ta samu relieve da nutsuwa, sulalewa kan kujera tayi ta jinginar da
kanta da kujerar tare da sauke wani dogon ajiyar xuciya, haba ita dama ta san
aikosa gidan aka yi shine xai shigo ma mutane har parlor saboda samun waje, shi kam
yana fita ya kulle kofar parlon, Nihad ta share hawayen idonta a hankali tana
tunanin to ina wanda aka aura mata din, har yanxu fa bata gansa ba, mikewa tayi ta
nufi hanyar dakuna ta bude wani daki a hankali ta leka ciki taga babu komai dakin
banda katifa, ta kulle ta sake bude wani taga shi ma katifar ce kawai, toh where is
the so called husband, a hankali ta juya ta koma dakin da ta kwana ta xauna gefen
gado, she is just imagining ace abinda tayi tunani daxu a kitchen gaskiya ne ai da
kawai da gaske kashe kan nata xata yi kowa ma ya huta, but why will she even think
that way at the first place, it is something that is neva and neva going to happen,
agogon dake dakin ta kalla taga karfe goma sha daya saura, har lokacin bata ji tana
jin yunwa ba, ita ta ma mance rabonta da cin abinci a cikinta, tana ta xaune dakin
with different thought and imagination a ranta, can kuma ta mike duk jiki ba kwari
tana tafiya a hankali ta koma parlor, windown dake kusa da kofar parlon ta tafi
tana leka compound din, karamin compound ne da xai iya cin mota uku, ga mamakinta
sai ta gansa xaune kan wani dakali a tsakar gidan ya rike kansa, wani faduwar gaba
taji ya dirar mata, but seriously what is this man doing in this house for God
sake, me yake har yanxu bai tafi ba, to ko dai mai gidan ne yace ya jirasa, this
time around ta ma rasa wani takamaiman tunanin xata yi, duk sai ta birkice taji
jikinta na rawa.... amma taki barin ƙwaƙwalwarta ya fassara mata abinda xuciyarta
ke raya mata a lokacin, noooo it can't and will never be, tasan aikosa gidan kawai
aka yi wallahi...... _Har a lokacin da ya gama hada takalman idon Abba na kansa,
ganin xai fita parlon Abba yace "Ibrahim" Juyowa yayi yana kallon Abba, Abba ya
nuna masa waje alamar ya xauna, komawa yayi ya xauna a hankali yana kallon Abban,
Abba ya nisa yace "Kana da mata ne Ibrahim?" Khalil ya ɗan yi jim, amma ganin yanda
Abba ya kafe sa da ido yayi saurin girgiza kai yace "Aa" Abba yayi kasa da murya
yace "Ohk! Kana da wani dalilin da yasa baka yi auren ba har ynxu ko kawai
ra'ayinka ne?" Khalil ya sunkuyar da kai yace "Dama da kaka aka ce xan yi auren
idan Allah ya yarda" Abba yace "Kana da yarinyar da xaka aura ne Ibrahim?" Khalil
ya dago ya kalli Abba dake ta kallonsa, sai kuma ya sake sunkuyar da kai a hankali
yace "Aa ban samu ba dai tukun" Abba yayi shiru yana kallonsa as if thinking of
where to start from, kallonsa kawai Abba yake daga sama har kasa duk da a xaune
yake, kamar jikinsa ya basa Abban na kallonsa, sai duk ya tsargu, upside down ya
juya palm dinsa a hankali not wanting to disclose the ring he is putting on, muryar
Abba yaji yace "Ina son xan maka aure, xan kuma yi maka komai na auren sannan in
baka gida ku xauna don na ya6a da nutsuwa da hankalin ka, bana jin ina da fargaba a
kanka Ibrahim.... amma baxan yi hakan ba tare da yardar ka ba, da kuma yardar
iyayenka, ina rokan wannan alfarman a wajenka Ibrahim" Khalil ya ji komai ya tsaya
masa na kusan 10 seconds, lkci daya ya ji he is feeling heat all over, ya dai yi
karfin halin dago kai ya kalli Abba, ganin yanda Abba ke kallonsa wanda in dai ka
san Abba to xaka fahimci yana cikin damuwa wanda baya iya boyuwa ko min pretence
din mutum, Khalil ya kirkiri fara'a a fuskarsa yace "Amma nagode sosai Alhaji,
Allah ya kara girma, Allah ya saka da alkhairi, Nagode Alhaji" Abba yaji dadin
reaction dinsa sosai cause he neva expect that, ya xata xai ce Aa ko kuma ya kawo
wani excuse din, Abba ya sauke boyayyen ajiyar xuciya yace "Ameen Ibrahim, sai mu
je can gun iyayenka yau mu yi magana da su ko? Su ma kuma ina fatan Allah xai sa su
amince" Khalil ya hadiye abu da kyar yace "To ba damuwa Alhaji" Abba yace "Ka
shirya nan da awa biyu mu tafi" Yace "Toh Alhaji" Abba yace "Nagode, amma sai dai
baka tambayeni da warce xan hada ka ba" Khalil kallon Abba kawai yake, Abba yace
"Yar cikina ce ba wata ba, saboda na yaba da komai naka ya sa nake son hada zuri'a
da kai, ni kadai na yanke shawarar nan, kuma idan Allah ya yarda ban yi abun da xai
cutar da kai a gaba ba Ibrahim, xaka yi farin ciki da hadin nan wataran, kawai tun
yanxu ina neman alfarman ka koyi hakuri da ita don yarinya ce, kuma ita ma nasan
watarana xata yi alfahari da xabin da nayi mata, fatana kawai Allah ya dora ni kan
iyayenka" Khalil kam yayi nisa tunanin da yake don bai ma assimilating maganganun
Abba, thousands of thought ne suka yi crossing mind dinsa a moment din nan, why him
of all people, this means disappointing every of his relative, ko Abba bai fada
masa wacece cikin yaran nasa ba ya san wacece, no!!! they are not and will neva be
compatible, how will that even be? Muryar Abba ya tsinta a tsakiyar kansa ya a ce
masa "Xaka iya tafiya, Allah yayi maka albarka" Ko Ameen din khalil bai iya ya amsa
ba ya mike ya kwashi takalman Abba ya fita daga parlon, lkci daya yanayinsa ya
sauya, wasu xufa suka hau keto masa, Yana fita compound ya nufi mai gadi ya dire
masa takalman, Aminu ya mike da sauri yace "Lafiya na ganka a birkice haka? Me ya
faru?" Khalil bai basa amsa ba ya nufi chalet, har idanuwansa sun kada .... Muryar
Nihad ne ya dawo da Khalil duniyar tunanin da ya fada a tsakar gidan, ya daga kai
fuskarsa daure yana kallonta, a fusace tace "Wai baka ji abinda nake ce maka bane?
Ka gaya min uban me ya kawo ka gidan nan?" Mikewa yayi yace "Ki kira babanki ki
tambayesa, don shi ya kamata ya baki wannan amsan" Kasake tayi tana kallonsa
gabanta na faduwa, har ya juya ya fara tafiya sai kuma ya juyo, severely yace
"Sannan ina me baki shawaran kada ki sake daga min murya, ko kuma ki sake min wasu
tambayoyi a gidan nan" Daga haka ya bar ta wajen tsaye ya koma cikin gidan walking
fast, shikenan abinda take ta hana ƙwaƙwalwarta fassara mata ya tabbata, shikenan
tsoronta da fargabanta ya tabbata, ta fashe da wani matsanancin kuka me ban tausayi
ta sulale kasa ta daura hannu a ka ta kurma wani uban ihu tace "Na shiga uku na
lalace, na banu na lalace, Me nayi ma Abbana xai min haka, me yasa Abbana xai min
haka, me nayi ma yan gidanmu suka min haka, innalillahi wa inna ilaihi raji'un"
Kuka take sosai kamar ranta xai fita, ta fi minti ashirin xaune kasan interlock ta
kasa tashi, she is more than shock, why her?? Ganin abun ma take kamar a mafarki,
Nihad ta ci kuka ta gode Allah a zaune wajen, daga karshe ta kalli gate din gidan
sai kuma ta mike da sauri ta nufi gate din amma tana kokarin budewa taji key aka
sa, sulalewa wajen tayi tana ci gaba da kuka tana girgiza kanta, nan ma tafi min
sha biyar, bata ta66atar da gaske an tsaneta a gidansu ba sai yanxu, sosai kanta ya
fara mata ciwo, jin strength dinta ya fara karewa saboda kukan da take tayi karfin
halin tashi tana layi ta koma cikin gidan, kitchen ta shiga tana kallon wukar da ya
bata ta wurgar daxu, karasawa tayi ta dau wukar hawaye me xafi na sauka idonta,
jingina tayi da cabinet tana kuka a hankali, to ai in tayi hakan wuta kawai xata,
jefar da wukar tayi daga karshe ta fito parlon tana bin ko ina da kallo hawaye na
bin idonta, karamar wayarsa ta gani saman kujera ta karasa da sauri saman kujeran
ta dau wayar ta shige dakin da ta kwana, xaunawa tayi gefen gado hawaye wasu na bin
wani a idonta tayi dialing number Nihal, tana sa wa sunan Nihal ya fito baro baro,
ta kai kunne, yana fara ring ba a wani dau lkci ba Nihal ta daga, kasa cewa komai
Nihad tayi tana kuka a hankali ta runtse idonta, jin shiru ba ace komai ba cikin
sanyin murya Nihal tace "Hello" Nihad ta fashe da matsanancin kuka tace "Na shiga
uku Nihal, kinga abinda su Abba suka min ko, dama ashe har Abba baya so na, dama
haka aka tsaneni a gidan nan ban sani ba? wayyo Nihal wllh da Allah baxai jefani
wuta ba yau da na kashe
kaina kowa ma ya huta, zuciyata kamar xata fashe nake ji yanxu, i can't take this
any longer, me yasa su Abba xa su min haka, sun san ma meye aure kuwa?" Kuka take
kamar ranta xai fita, Nihal dai tayi shiru bata ce komai ba, Nihad na shessheka
tace "Pls ki turo min number Husnah yanxu ta nan, nasan kina da shi send it now
plss i need it...." Tana gama fadin haka ta katse wayar ta fada kan gado tana rera
sabon kuka, ko minti daya ba ayi ba Nihad taji shigowar message a wayar, ta mike
xaune da sauri taga number Husnah ne Nihal ta turo mata, da sauri ta hau kiran
number, yana fara ring Husnah ta daga tace "Hello" Nihad ta rushe mata da kuka tace
"Husnah tawa ta kare, Abba na ya tsaneni baya so na, Husnah kila ma ba su suka
haifeni ba wallahi" Da sauri Husnah ta rage volume din Mp da suka cika a daki tace
"Calm down Nihad, kar ki je ki sa ma kanki wani ciwon mu shiga uku, wllh tsoron
xuwa gidan nan naku nake saboda yayanki, babu ta inda kuma xan san halin da kike
ciki tunda bani da number kowa a gidan, Nihal da nake da number ta tana school da
na kirata tace min haka" Nihad tayi karfin halin cewa "Husnah kin san wa Abbana ya
aura min?" Husnah ta gyara xama tana gwale ido tace "Aa waye?" Nihad ta kwanta
gefen gado hawaye me xafi na sauka idonta tace "Husnah of all people wai drivern
gidanmu Abba ya aura min" Husnah dake xaune sai da ta mike tsaye tace "Whattt???"
Bude kofar dakin aka yi Nihad ta mike xaune da sauri lkci daya ta hade rai, yana
mata wani kallo ya karasa cikin dakin fuska daure yace "Kar ki sake ta6a min waya a
gidan nan" Wani matsiyacin kallo tayi masa ta wurgar da wayar tana ta6e baki tace
"Wannan gwangwanin kake kira waya?" Kallonta kawai khalil yake babu ko kiftawa
trying his possible best to calm himself, Nihad ta ja tsaki ta tashi ta koma can
karshen gado ta xauna fuska daure tace "Wai waya, kai baka ma ji kunyan kiran
wannan waya ba" Gyada kai yayi ya juya ya durkusa ya dau wayar da batur dinsa da
yayi gefe daya ya mayar sannan ya mike ya nufi kofa ya fice daga dakin, wani sabon
kukan ta saki tace "Wayyo Allah na." Wajen karfe sha biyu da rabi Nihad da har ta
gaji da kukan da take ta ji ana kwankwasa gate din gidan, kamar tana expecting
hakan ta mike da sauri tana share idonta ta fice daga dakin, dai dai fitowarsa shi
ma daga dakin da yake, ta wani hade rai, ko kallonta bai yi ba ya nufi kofa ya
fita, wani mugun tsanarsa da tafi ta ko yaushe take ji a ranta, even with joke
baxata ta6a kiran wannan mutumin wai mijinta ba, mijinta ta ina? Shi har ya isa ya
xama mijinta? This is even weird to imagine, bakin kofar parlon ta tafi ta tsaya
fuska daure, yana bude gate din Umma ta shigo, har kasa ya durkusa yace "Barka da
xuwa Hajiya, ina yini" Wani kallo Umma tayi masa sae kuma ta kyabe baki ta wuce ta
bar sa durkushe a wajen, Nihad na ganin Umma ta taho da gudu ta Rungumeta ta sakar
mata kuka da karfi tace "Umma na shiga uku, me yasa Abba xae min haka, me yasa Abba
xae lalata min rayuwa, Umma ashe duk ba sona ake a gidanmu ba ban sani ba" Umma ta
rungumeta cike da damuwa tace "Yi shiru mu shiga ciki Nihad, yi shiru" A haka Umma
ta ja xuwa parlor, khalil da ya bi su da ido ya tafi kan dakalin da ya xauna daxu
ya xauna, Umma na rungume da Nihad bayan ta zauna kan kujera tace "Wai ba nace kiyi
shiru ba ko in tashe in tafi ne?" Nihad ta girgiza kai tana shessheka a hankali
tana goge idonta, Umma tace "Ke yanxu kin yarda an aurar da ke kenan?" Nihad ta
daga kai tana kallon Umma da kumburarran idonta, ba idonta ba har fuskarta ya koma
ja, Umma tace "Ohh kin yarda kenan an daura maki aure da Driver?" Nihad ta girgiza
kai disgustingly tace "Allah ya kiyaye wllh" Umma tace "Toh Alhamdulillah, yanda ko
wace budurwa take rayuwarta haka xaki ci gaba babu batun auren kowa a kanki, kar ki
kuskura ki amince wai kina da wani wai shi miji, a nan din ma bai wuce ɗan aiken ki
ba kuma drivern ki, ki sa a ranki kema budurwa ce da xata iya shiga duk inda take
so ta fito, ki ci gaba da rayuwarki yanda kika saba, sannan kar ki kuskura ki raga
masa balle ya ga fuskar kawo maki raini, ba kowa bane shi facce drivern gidanku
kuma har a yanxu dreban ne, kuma ɗan aike" Nihad tace "Toh Umma yanxu a gida daya
xa mu xauna da shi kenan? Wallahi i just can't imagine that, ta yaya xa ace muna
gida daya da shi?" Umma tace "Ka ji ki, Toh ina ruwanki da shi? Meye hadin ki da
shi? Rayuwarki kawai xaki dinga yi kamar kina gidan ubanki, kar ki yarda ko kallon
kirki ya hada ku da shi, har yau shi din ma'aikacin gidanku ne don haka a karkashin
ki yake" A hankali Nihad tace "Toh, amma Umma shikenan baxan ci gaba da karatuna ba
kenan" Umma tace "A saboda me? Ai kwantar da hankalin ki, yanxu daga nan gidan
Alhaji Abubakar xan nufa tunda dai sun aurar da ke sai su bari kuma ki ci gaba da
karatun ki" Nihad ta sauke ajiyar xuciya tace "Nagode Umma" Umma tace "Kar ki yarda
ki kara xubar da hawayenki a banza a hofi, ke da ma kika samu freedom din kanki
yanxu, da kin tashi fita kawai fitar ki xa ki yi kanki tsaye babu neman izinin ko
wani shege, sanda kika ga dama kuma xa ki dawo babu me tuhumarki" Nihad da ta ji
hankalinta ya kwanta sosai tace "Haka ne Ummana" Umma tace "Toh ko ke fa, sannan
duk kawayenki xa su iya xuwa nan su dinga kwana kuna yini tare, kuyi duk wani
sabgarku a nan babu me cewa don me" Nihad tace "Gaskiya ne Umma, amma ni damuwata
kawai ganinsa da xan dinga yi a gidan, baxai yiwu ya koma can gidan ba kawai gaba
daya ni kadai in zauna a nan, wllh i hate the sight of him, na tsani ganinsa, na
tsanesa" Umma tace "Aa ke kuma, ai xai ci gaba da aikinsa na tuki, kinga duk safiya
xai dinga xuwa can gidan kilan kuma sai ya dawo da Abbanku daga office sannan ace
xai dawo nan gidan" Nihad ta yatsina fuska, Umma tace "Ke ma abinda idan kika fita
kilan sai daren xa ki dinga dawowa gida" Nihad tace "Dama mana, yanxu kawai xance
su Husnah da Naf su kwaso kayansu su dawo nan mu zauna" Umma tace "Shikenan kuwa"
Nihad ta sauke ajiyar xuciyar relieve, Umma tace "Kin ci abinci kuwa?" Girgiza kai
Nihad tayi, Umma tace "Me yasa? To tashi ki tafi kitchen ko indomie ne ki dafa"
Nihad tace "Toh" Mikewa tayi cike da energy ta wuce kitchen, sosai ta samu nutsuwa
bayan abubuwan da Umma ta gaya mata, ta dafa indomie sannan ta fito, Umma tace
"Bari in xo in tafi don in samu Alhaji Abubakar a gida" Nihad tace "Umma bani da
waya wllh" Umma tace "Akwai nokia din yayanku bari ko Amina xan ba ta kawo maki
anjima" Nihad tayi Murmushi tace "To Umma Nagode" sai da ta gama cin indomie sannan
Umma tace ta taso ta rakata, Nihad ta mike suka fito compound da Umma, har sannan
khalil na xaune inda yake, Ya mike yana kallon Umma yace "Sai anjima Hajiya" Umma
ta wani kallesa, sai kuma ta kyabe baki ta ci gaba da tafiyarta Nihad ta hade rai
tana biye da ita a gefenta, Komawa yayi ya zauna ya bi su da kallo, suna isa gate
Umma tace "Toh sai kin ji ni, idan Amina ta kawo maki wayar sai ki kirani don xan
sa a siyo maki sim ayi register sai ta taho maki da shi" Nihad tace "Toh Umma" Umma
tace "Maza tafi kiyi sallah ga azahar yayi, sai ki kwanta ki huta" daga haka tayi
mata sallama ta wuce, Nihad ta kulle gate din, fuska daure ta nufi cikin gidan. Har
bayan magrib Nihad na ta jiran Amina ta kawo mata waya amma shiru, gashi babu yanda
xata yi ta kira Umma duk da tana da numberta a kai, wannan ne yasa ta kara shiga
wani damuwa, karfe takwas da rabi ta mike a hankali ta fito daga dakinta, dai dai
nan Khalil ma ya fito... sosai gabanta ya fadi ta ɗan koma baya, sai kuma ta daure
fuska, ko kallonta bai yi ba ya shiga parlor, ta bi sa da kallo taga kamar fita zai
yi, tuni turarensa ya gauraye duk parlon, ko burgeta kamshin nan nasa baya yi, ta
kasa kunne taji ko fita gate xai yi, ai ko taji ya bude gate, da sauri ta shige
dakinsa ta kulle kofar, banda kamshi babu abinda dakin ma yake, ta tafi gefen gado
ta dau karamar wayarsa da ta gani ta hau dialing din number Umma sharp sharp, yana
fara ringing Umma ta daga hade da sallama, Nihad ta marairaice tace "Umma ni ce"
Umma tace "Aa Nihad, Number waye haka duk zero zalla" Nihad tace "Wayar yaron nan
ne Umma, ya fita yanxu shine na dauka da sauri na kiraki kafin ya dawo" Umma tace
"Kin ji shiru ko, wllh ba a samu anyi rijistan layin yau ba sai gobe wai, don haka
gobe da kaina xanje ayi, ita kuma Amina tana dawowa islamiyya xan bata ta kawo maki
kin ji" Nihad tace "Toh shkkn Umma, Allah ya kai mu goben" Umma tace "Toh Ameen,
sai da safe daughter" Daga haka ta katse wayar, Nihad na duba call logs don ta kira
Husnah tunda daxu ta saka numberta a wayar amma bata gani ba alamar ya goge number,
instead sai number Nihal ta gani wanda ko awa daya ba ayi ba da suka yi wayan da
ita, ta dinga kallon number babu kiftawa, bude kofar dakin aka yi, Nihad ta zaro
ido hade da kurma ihu a tsorace ta saki wayar hannunta jikinta na rawa, tsaye yayi
bakin kofa yana kallonta da wani Strict expression, lkci daya ta wani sha kunu ita
ma, can dai ta tafi can jikin bango har sannan gabanta na faduwa amma bata nuna
hakan a fuskarta ba, ya karaso cikin dakin ta hadiye wani abu da ya tokareta a
makogwaro da kyar xuciyarta sai bugawa yake tana kara shigewa jikin bango, yana
dukawa zai dau wayar ta yi hanyar kofa a mugun guje, da hannu daya yayi hanzarin
fixgota ta fasa ihu tana kokarin kwace kanta tace "Wallahi xan cijeka idan baka
sakeni ba, ni me xanyi da gwangwanin wayarka"

*Da kun kai hannunku xa ku danna wajen fowarding littafin nan xuwa groups ku dubi
girman Allah, ku dubi darajan annabi S.A.W, da kuma son da ku ke ma iyayenku ku
tuna da cewar nace don girman Allah ayi hakuri kar a min sharing to groups with
over thousand members, plss i am begging sincerely ba da fada ba ko gadara, ayi
hakuri a min wannan alfarman, masu siya kawai don su tura groups su yi hakuri domin
Allah kar su yi haka, And if u should come across this book roaming in any group
kayi kokari kayi subscribing before reading saboda ba free book bane, ur conscience
shouldn't allow u to read my dear, ko yaya ne try and give something, ina kuma
alfahari da duk wa enda suka yi patronizing dina, ina kuma maku fatan alkhairi...*

Nihad is just....

500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

And u show ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: Hadeta Khalil yayi da bango fuskarsa a daure
yana kallonta cikin kakkausar murya yace "Zan maki gargadi na karshe, kar ki sake
ta6a min wayata a gidan nan, kar kuma ki sake shigo min nan, ina me baki wannan
shawarar" Nihad dai gabanta sai faduwa yake ganin how huge he is a gabanta, ita
bata ta6a sanin ma haka yake da tsayi ba, gashi ya murtuke fuska uwa ba drivern
gidansu ba, amma duk hakan bai sa ta fasa daure masa nata fuskar ba ita ma, sai dai
bata ce komai ba, komawa baya yayi yana kallonta, irin kallon kyama sannan ya nuna
mata kofa calmly yace "Fita" Ba musu ta nufi kofa, tana isa dai dai kofar ta juyo
ta kallesa tana wani yatsine fuska har da harararsa tace "Sai ka gaya min nawa ka
siya shegen wayar taka in baka kudin wanda ya fi shi yanxun nan, ban ta6a ganin
wanda ke takama da rakani kashi ba sai kai" Still yayi yana kallonta babu ko
kiftawa, tana gama fadin abinda xata fada ta bar wajen da sauri tayi hanyar dakinta
ta shige ciki ta kulle kofar tana sauke ajiyar xuciya, jingina tayi da kofar wani
bakin ciki da takaici ya turnuketa wai yau ita da drivern gidansu ne kadai a gida
daya har yana gaya mata maganar banza, ta ji xuciyarta na tafarfasa, she is still
yet to believe this, ta kasa yarda wai da gaske wannan mutumin Abba ya sa su gida
daya su dinga xama, how will that even be, fadawa tayi saman gado ta fashe da kuka
tace "Wayyo Abba me yasa xaka min haka" Ita da dai drivern nan ai gwara ko almajiri
ne Abba ya nemo mata su xauna gida daya, ta ci kukanta me isarta bacci ya dauketa a
haka. Washegari har kusan karfe goma bata fito ba ga wani mugun yunwa da take ji,
tashi tayi da kyar daga karshe ta shiga bandaki tayi wanka ta fito, daya daga
akwatunanta dake dakin ta bude ta fiddo wata doguwar rigarta ta saka, xaunawa gefen
gado tayi feeling so sad and dejected, daga karshe ta mike ta nufi kofa tana tafiya
a hankali ta bude kofar ta fito parlor, babu kowa parlon sai take away din abinci
da ta gani a tsakar parlon, ta saci kallon ko ina na parlon sannan ta karasa inda
abincin yake tana ta6e baki ta bude take away din tana kallon abincin ciki, jollof
rice ne sai sheki yake da katon kaza, ko rabi kuma bai ci ba, kazar ma bai wani ci
ba ya bari, ta bude ledan dake wajen taga drinks ne sai chocolates me yawa,
vibration din waya taji saman kujera ta kalla da sauri amma bata ga wayar ba, wanda
hakan yasa ta gane wayar na karkashen throw pillow dake saman kujeran, har xata kai
hannu ta daga pillow din ta ji an kulle kofar kitchen, sosai gabanta ya fadi ta
juyo da sauri suka yi ido hudu da shi ya fito daga kitchen din rike da cup din
shayi, sai a sannan ya ji vibration din wayarsa ya karaso da sauri, wanda tun kan
ma ya karaso Nihad tayi hanyar dakinta tana harararsa, ya ajiye cup din hannunsa ya
bi ta da kallo har ta shige dakin, xaunawa yayi saman kujera yana kallon throw
pillow din kamar me son gano ko ta ta6a ko bata ta6a ba, da sauri ya dau wayar
kafin ya katse ya daga ganin Abba ne, gaishesa yayi da ladabi Abba ya amsa yace
"Anjima da yamma ka daukota ku zo gida ina son magana da ku" Khalil yace "Toh in
sha Allah" Abba yace "Ai motar na can gidan ko?" Khalil yace "Ehh yana nan" Abba
yace "Ina sauraronku xuwa nan da bayan la'asar" Khalil yace "In sha Allah" Daga
haka Abba ya katse wayar, ajiye wayarsa yayi ya jinginar da kansa da kujera, this
spoilt his mood the more, Allah ya sani he can't endure staying under the same roof
with this Brat, he wish this never happened, he detest the sight of her, da yasan
this is how things will end babu abinda xai kawosa gidansu, da baxai fara ba, yanxu
ta yanda ma xai ce ta shirya su je gida shine babban aiki a wajensa, ko magana baya
son yana hadasa da ita, mikewa yayi ya dau wayarsa ya zura a aljihu ya fice daga
parlon xuwa compound don ya fi zama comfortable xama a nan, abinda Nihad bata sani
ba shine shi ya ma fita shiga damuwa kawai dakewa yake yi, kuma bata ki jininsa ba
yanda shi ya ki jininta. Ganin yunwa na neman mata illa ta kara fitowa parlor, this
time around hanyar kitchen ta nufa tana bin ko ina da kallo, ga kayan abinci amma
babu kayan miya, gashi ita ba gwanar cin indomie ba ce, babu yanda ta iya haka ta
dafa indomien ta fito ta wuce dakinta, tana ajiye indomien ta fashe da kuka sosai
cike da tausayin rayuwarta, why did this happen to her, waye yayi mata haka yayi
ruining happiness dinta all of a sudden, tasan duk rashin jin ta ko da singlet bata
xama comfortable zama a inda ba gidansu bane, ko su Husnah da take bi she is very
cautious of her self and her body, kuka take yi sosai wishing duk wannan abun bai
faru da ita ba, indomien da bata ci ba kenan daga karshe, kawai ta tashi tayi
alwala tayi sallahn azahar ta kwanta gefen gado hawaye na sauka idonta. Ana la'asar
Khalil ya shigo parlor ya zauna yayi dialing number Abba, Abba na dagawa ya
gaishesa sannan yayi kasa da murya yace "Abba tace ita baxata ba" Abba yace "Ohk,
ba ta waya" Khalil yace "Toh" Mikewa yayi ya nufi hanyar dakin da take ciki, yanda
kasan yana kallonta jikin kofar haka ya hade rai yana kallon kofar, sai kuma yayi
Knocking kofar, Nihad da ke kwance har sannan ta mike zaune tana kallon kofar, sai
da ya sake Kwankwasawa ta mike xaune ta wani hade rai, sai kuma ta tashi ta tafi
gun kofar ta bude cike da tsiwa tana harararsa tace "Lafiya kake kwankwasa min kofa
Malam? Ko da bashi ne?" Mika mata wayar hannunsa yayi ba tare da ya kalli fuskarta
ba, ta kalli wayar da kamar baxata amsa ba sai kuma tayi tunanin kila Umma ce,
fixge wayar tayi daga hannunsa tana kallon Number sai taga number Abbanta ne, sosai
gabanta ya fadi, tayi karfin halin kai wayar kunne, cikin sanyin murya tayi
sallama, Zaro ido tayi tana sauraron abinda Abba ke ce mata with strictness, can ta
kalli Khalil da ya koma can gefe ya jingina da bango ya rungume hannunsa, Abba bai
bar ma Nihad space din cewa komai ba ya katse wayarsa daga karshe, ta fashe da wani
matsanancin kuka tana kallo Khalil tace "Allah ya isa, ban yafe maka ba wllh,
yaushe kace min mu je can gida nace Aa?? Wallahi ni baxan ta6a yafe maka ba" Sai
kuma ta durkushe wajen tana kuka sosai ta kalli wayarsa dake hannunta tayi wurgi da
shi ta mike ta shige cikin daki ta fada kan gado tana rera kuka, ya dau wayar tasa
ya bar wajen. Bayan Nihad ta ci kukanta ta koshi ta mike ta dau hijab din da tayi
sallah ta saka sannan ta fito daga dakin, compound ta fito ta gansa xaune driver
seat ya bar motar a bude alamar dai ita yake jira, fuskarta a murtuke ta bude back
seat ta shiga ta xauna, ya sauka daga motar ya tafi ya bude gate..... Har suka kusa
gida Nihad bata daina hawayen da take ba a motar, Horn khalil yayi mai gadi ya leko
ganinsa ya daga masa hannu yana washe hakora ya bude gate din, Khalil na parking ya
kashe motar ya sauka ya tafi gun Aminu, tuni Nihad ta shige cikin gida, Aminu yayi
kasa da murya yana zazzare ido yace "Wani labari muke ji haka mutumina??" Khalil
yace "Na me fa?" Kafin Aminu yace komai, Khalil yace "Bari in shiga in fito yanxu"
Aminu yace "Toh ina nan ina jiranka" Juyawa khalil yayi ya nufi entrance din gidan,
Khalil na tsaye balcony yayi dialing number Abba ya sanar masa sun iso, Abba ya
masa izinin shigowa har parlonsa, babu kowa main parlor, Khalil yayi sallama
bangaren Abba, Abba ya amsa sannan ya shiga ciki, kansa a kasa ya zauna nan saman
Carpet ya kara gaida Abba, Abba ya amsa ganin Nihad bata shigo ba yace "Tana ina?"
Khalil yace "Ta riga ni shigowa" Nihad kuwa tana shiga gidan dama direct bangaren
Umma ta tafi, Abba ya mike ya fita, a side din Umma ya ga Amina yace "Ina Nihad?"
Amina tace "Tana dakin Umma" Yace "Ki shiga ki kira min ita" Amina ta juya ta koma
ciki, Abba ya koma parlonsa, bayan wasu yan mintuna sai ga Nihad ta shigo parlon
Abbanta kanta a kasa, sallama tayi da muryarta da har ya fara dashewa saboda kuka,
bata yarda ta daga kai ba balle ta kalli Abbanta, ta nemi waje daga opposite din
inda khalil ya zauna ta zauna, Cikin rawar murya tace "Abba ina yini" Abba bai amsa
ba, bai kuma kalleta ba, dai dai nan Umma ta shigo parlon da sallama, kallonta
kawai Abba yake, Khalil ya gaisheta ta amsa ta zauna fuskarta dauke da damuwa tana
kallon Abba, Abba dai ya kalli Khalil yace "Nagode da wannan alfarma da ka min na
auren yarinyar nan Ibrahim, Allah Ubangiji ya baka aljanna" Khalil yayi kasa da kai
a hankali yace "Ameen" Abba yace "Ina kuma fatan Allah Ubangiji ya baka hakuri da
juriyar zama da ita.... In dai da akwai wani abu kar kayi kasa a gwiwan kirana ka
sanar min koma menene shi" Nihad ta fashe da matsanancin kuka tana kallon Abba tace
"Abba wallahi bana sonsa kuma baxan ta6a sonsa ba, na tsanesa na tsanesa, ni baxan
ta6a xama da shi a gida daya ba, wallahi i hate him...." Mikewa Abba yayi lokaci
daya ya sauke mata mari me lafiya a fuskarta, ihu ta fasa ta dafe kuncinta, Umma ta
bude baki tana kallon Abba, sai kuma tace "Haba Alhaji, Haba Alhaji...." Dakatar da
ita Abba yayi a fusace yace "Bana son jin komai daga gareki, ki tashi ma ki fita"
Umma ta ja bakinta tayi shiru, cike da bacin rai Abba na kallon Nihad yace "U think
i brought u here to ask for ur opinion? Is that what u think?" Abba ya girgiza kai
cike da takaici yace "You are nothing but a disappointment to me Nihad, i regret
having u as a child...." Kuka kawai Nihad take tana jin kamar a mafarki wai ita
Abba ya mara kuma yake gaya mata wannan maganganun, wanda ko fada bai ta6a mata ba
tunda aka haifeta, Strictly Abba ya ci gaba yace "Kuma in har ba so kike inyi
disowning dinki ba baki da miji da ya wuce Ibrahim, kuma dolenki kiyi masa biyayya
ki bisa, idan ko ba haka ba ki nemi wani uban ba ni ba, sannan idan ba shi ya dauko
ki ya kawo ki gidan nan ba bana son in ga kafarki a nan ko da kuwa xa ayi shekara
ne bai kawo ki ba, ki sa a ranki baki da wani a yanxu banda shi, shine gatanki,
shine komai naki, samun kwanciyar hankalin ki a rayuwa ki bi sa, ko mu da muka
haifeki yanxu bamu da iko da ke sama da shi" Kuka kawai Nihad take xuciyarta
na mata xafi, ita fa she still can't believe Abbanta ne ke gaya mata wa ennan
maganganun, Abba na kallon Khalil da ya sunkuyar da kansa yace "Kai kuma Ibrahim
ina me baka umarni in har Nihad xata kawo maka iskanci ko raini ka zaneta, ni na
baka wannan umarnin ba wani ba" Khalil dai bai dago kansa ba, Abba yace "Shikenan
kiran dama, xa ku iya tafiya" Da kyar khalil ya iya dago kai yace "Nagode Abba,
Allah ya kara girma" Abba yace "Ameen" mikewa yayi yana kallon Umma yace "Sai
anjima" Umma ta dinga harararsa, shi dai ya nufi kofa, ganin Nihad ta ki tashi sai
kuka take kamar ranta xai fita Abba ya daka mata tsawa yace "Tashi ki bar min
gidana, useless girl" Tashi tayi da sauri tana kuka sosai ta nufi kofar ita ma, sai
kuma ta juyo cikin rawar murya tace "Abba makaranta na fa?" Abba yace "Sai abinda
mijin ki yace, don shi ke da iko dake yanxu, don in xai dau shawarata ma babu ke
babu makaranta har abada, maza bi sa ku bar min gidana" Khalil dake jin Abba ya
fita daga parlon ta bi bayansa tana kuka sosai, shi dai ko kallonta bai yi ba ya
fita xuwa gun mota, Aminu sai wage ido yake yana jiran fitowar Khalil, yana ganinsa
ya fito kuma ya shige mota, Nihad ta bude bayan motar ta shiga ta hade kanta da
gwiwa tana shessheka tana jin kamar numfashinta zai dauke, Khalil na isa gate Aminu
yace "Ina ta jiranka" Khalil yace "Xan zo da daddare" Aminu ya washe hakora yace
"Toh toh sai ka zo" Da gefen ido ya dinga lekan Nihad dake bayan mota, khalil ya ja
motar suka bar gidan. Sai kusan karfe shidda suka isa gida, Khalil na parking ya
sauka ya tafi ya kulle gate sannan ya dawo ya kashe motar, har sannan Nihad bata
dago kanta da ta kife a bayan motar tana kuka ba, tana jin ya kashe motar ta bude
side dinta ta sauka, gaba daya ta jike hijab dinta da hawaye har a sannan kuma ba
daina kukan tayi ba, ta fara tafiya towards the building of the house, ji tayi ko
ina na juya mata a ido, Rufe motar khalil yayi da sauri ya nufeta ganin abinda
take, amma kafin ya isa inda take tuni ta kai kasa, ba karamin faduwa tayi a wajen
ba, ya zura makullin hannunsa cikin aljihu da sauri ya durkusa gabanta ya dagota
amma tuni tayi pass out, daukarta yayi ya nufi cikin gidan da ita.

_kiyi subscription ki karanta hankalinki kwance. Nima kuma sai in samu kwarin
gwiwan dinga yi maku double update_

I am soo grateful for the patronage, Allah ya saka maku da Alkhairi ya biya maku
duk wata buƙatar ku ta Alkhairi, Allah ya kara ma iyayenku lafiya.

*Nihaad* is 500 via Fcmb Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence via👇🏻


07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: A hankali Nihad ta bude idonta tana bin inda
take kwance da kallo, a daki take saman gado, ta mike xaune da kyar tana jin ko ina
na jikinta na mata ciwo ga wani sanyi da ke shigarta duk da fankan dakin a kashe
yake, ta kalli agogon dakin taga karfe biyu dai dai, window ta kalla ganin duhu
yasa ta fahimci biyu na dare ne, hade kai tayi da gwiwa bayan tayi recalling duk
abubuwan da suka faru, she couldn't stop tears from rolling down her eyes, ta dinga
shessheka a hankali, tunawa da tayi bata yi sallan magrib ba balle Isha'i ya sa ta
dago kanta tana goge idonta da ya kumbura, tayi kokarin sauka daga saman gadon amma
taji baxata iya ba, ko ina ciwo take ji yake mata a jikinta, hakan ya sa ta koma ta
kwanta a hankali, Hijab dinta dake gefenta ta jawo ta lullube da shi ta takure waje
daya sbda sanyin da take ji sosai, amma bai taimaka mata da komai ba sai rawan dari
take, bayan kusan minti talatin ta ji an bude kofar dakin, ita dai tana takure inda
take ta rufe har kanta da Hijab, tsaye yayi bakin kofar dakin yana kallonta, dama
ya zo dubawa ne ya ga ko ta tashi or she is still unconscious cause he isn't as bad
as she is, he have human conscience in him unlike her, har xai juya ya fita sae
kuma ya karasa cikin dakin ganin kamar she is shivering, ya isa kusa da gadon yana
kallonta xai cire Hijab din da ta rufe fuskarta da shi, ta riko hijab din a fusace
cike da tsiwa tace "Baka da hankali ne?? Uban meye xaka shigo min daki cikin daren
nan?" Sake Hijab din yayi ya juya ya fice daga dakin ta bi sa da harara sai kuma ta
ja tsaki ta koma ta kwanta jikinta na rawan sanyi sosai. Har aka yi asuba Nihad ta
kasa motsawa daga exact spot din da take a kan gadon tun cikin dare, she is so sick
and weak, tayi yunkurin tashi ya fi a kirga amma kamar an danneta saman gadon take
ji, duk da babu wani abun da ta ci tun jiya amma haka ta dinga jin amai yana
damunta kamar xai taho mata, ga ciwon kai me tsanani da ya addabeta, wajen karfe
takwas taji aman ya taho mata, bata san sanda wani strength ya xo mata ba ta sauka
daga kan gadon tana layi ta bude kofar bandaki, nan ta durkusa ta dinga kakarin
amai amma ba abinda ya fito, Khalil na kwance parlor yana jin ta amma ko motsawa
bai yi ba daga saman kujeran da yake, a nan tsakar dakin Nihad ta kwanta tana maida
numfashi hawaye me xafi na sauka idonta, tana nan a haka har kusan karfe sha daya
na safe, zuwa lkcn kuma xaxxabin ya ci karfinta, Duk yanda ya so fita harkarta a
gidan kasawa yayi, cause he wasn't raised to be mean, ya kuma san bata ci abinci ba
throughout jiya don shi ya fito da indomie da ta bari a daki bata ta6a ba, karfe
sha biyu saura ya mike yayi hanyar dakin after soothing himself to do so, kwata
kwata ba don ranshi ya so ba ko don tayi deserving ba yayi hakan kawai dai shi din
me tausayi ne, yana bude kofar dakin ya ganta nan tsakiyar dakin a kwance, ya fi
minti daya tsaye bakin kofar yana kallonta kafin ya karasa cikin bedroom din, ya
duka a gabanta ya cire hijab din da ta rufe fuskarta da shi, ta bude idonta da yayi
jajir amma babu strength din rashin kunya ko tsiwa, bai kai hannu jikinta ba but
yana jin hucin zafi a jikinta, ya mike ya fita daga dakin ya dau wayarsa, bayan ya
gama kiran da xai yi ya shiga kitchen, ruwan gora ya juye a kettle ya daura saman
gas, bayan ruwan yayi xafi ya hada shayi a cup ya fito, dakin ya koma ya ajiye mata
shayin, amma ya kasa ce mata ta tashi ta sha, har cikin ransa bai son ko magana ya
hada shi da wannan yarinyar, kawai daga karshe ya fice daga dakin ba tare da ya ce
mata komai ba, bayan kusan awa daya ya fita kofar gida ya shigo da wani likita,
wani asibiti dake home service ya kira suka turo masa likitan, bayan sun gaisa ya
kai sa har dakinta, likitan ya ajiye abubuwan da ya taho da su yana kallon Nihad,
Khalil ya juya ya basu waje yayi zamansa a parlor, bayan likitan ya dubata ya
tilastata ta dan sha shayi, sai da yayi yakin kusan minti sha biyar kafin ya samu
da kyar yayi mata allurai, ya kuma bata magunguna ta sha, da tace masa sanyi take
ji ya dauko wani zanin gado da ya gani a leda ya bude sannan ya bata ta rufa da
shi, yace "Allah ya sauwake, Anjima da daddare xa a dawo yi maki allura" Ita dai
bata ce komai ba don bacci taji yana hauro mata har ya fita daga dakin, yayi ma
khalil sallama sannan ya bar gidan..... Tashi khalil yayi wajajen karfe uku ta
dalilin gate da ake kwankwasawa ya fita zuwa gate din ya bude, Aunty Jamila ya gani
bakin kofar, sosai take kama da Mummy, ya mata sannu da xuwa sannan ya bata hanya
ta shigo gidan, sai da suka shiga parlor ya xauna kasa ya gaisheta ta amsa da
fara'a tace "Ya sabon waje" Yace "Alhmdlh" Tace "Toh madallah, Allah Ubangiji ya
baku zaman lafiya" Bayan few seconds ta sake kallonsa tace "Ina Nihad din?" Ya dan
kalli hanyar daki yace "Tana ciki" Aunty Jamila tace "Toh sanar mata na zo" Mikewa
yayi ya nufi hanyar dakin sai kuma ya dawo yace "Aunty bata jin dadi ne tun jiya
daxu likita ya zo dubata, ki karasa cikin dakin" Aunty Jamila ta mike ta bi bayansa
zuwa dakin, kofar kawai ya bude mata ya koma gefe, ta shiga dakin da sallama ya
juya yayi komawarsa parlor, don tunda likitan ma ya bar gidan shi bai shiga dakin
ba. A hankali Nihad ta mike xaune tana kallon Aunt dinta, Aunty Jamila ma kallonta
kawai take don ba karamin rama tayi ba, Aunty Jamila ta sauke boyayyen ajiyar
xuciya tace "Ya jikin" kamar jira Nihad take ta fashe mata da kuka tace "Aunty don
Allah ku yafe min, wallahi ban san daga inda video din nan yake ba, ni ban ta6a
video haka ba, kuma ban ta6a bari a min video haka ba, i don't know how everything
happened" Aunty Jamila ta ma rasa abinda xata ce mata, Kuka kawai Nihad take ta
hade kanta da gado, Aunty Jamila ta dagota tace "Ya isa haka, ba kuka na zo ki min
ba, abinda ya faru kuma ya riga ya faru babu me ja da Ubangiji" Nihad dai goge
hawayen da ya ki tsaya mata kawai take, Aunty Jamila ta girgiza kai tace "Da kina
jin maganar uwarki duk haka da bai faru dake ba Nihad, ke ce tara kawaye, ke ce
gantali, ke ce shiga kamar ba yar musulmai ba, kina ganin yanda yar uwarki ke
rayuwarta gwanin sha'awa ita da ma ba gaban iyayenku take karatu ba, kin bata
wayonki Nihad, kin kuma yi ma kanki damage din da baxai ta6a goguwa ba a doron kasa
ba, ina ne wannan Video din naki bai je ba a internet?" Nihad dai kuka take kamar
ranta xai fita, Aunty Jamila tace "Da kika je can kebbi din kinyi kawaye ne?" Nihad
ta girgiza mata kai kawai, Aunty Jamila tace "Ta yaya ma xa ki ce ke baki san daga
inda video din nan ya fito ba? Ba fa daura fuskarki aka yi ba ko wani abu, ke din
ce a video din, ko Inner wear din ma ai ni na siyo maki su a Lagos ba a dade ba"
Nihad ta ma rasa abun cewa, Aunty Jamila tace "Idan kin je makarantar baki zama a
hostel ne?" Nihad ta sunkuyar da kanta, Aunty Jamila tace "Buda baki xa kiyi ki min
magana" Cikin rawar murya tace "Aa" Wani shegen kallo Aunty jamila ta mata tace "Ba
kin ce min kawayenki a hostel su ke ba?" Nihad ta gyada kai tace "Ehh amma a aji
muke haduwa da su" Aunty Jamila tace "Baxa ki daina min karya ba?" Nihad ta hadiye
abu da kyar tace "Da gaske Aunty" Aunty Jamila tace "Toh ke kika sani, ki rike
gaskiyarki a ciki, xan ga ta yanda xa ayi a gano ta ina video din ya fito idan kin
ma mutane karya" Nihad dai tayi shiru gabanta sai faduwa yake, ta yaya ma xata fara
ce ma Aunty Jamila babu wani kebbi da suka je da Aunty Kamila hostel ta koma da
zama, cab ai rufeta kawai xata yi da duka a nan, sannan ko jiya da suka je gida sai
da Umma ta bata shawaran ko da wasa kar ta ce ma wani ai bata je kebbi ba hostel ta
koma, ko da xa a cika ta da tambayoyi, balle ita tasan Husnah da Naf da Zully,
enemies dinsu ma basu ma video ba balle ita, idan ma Zully na video suna daki tunda
ita mayyar video ce Husnah tayi ta masifa kenan tunda su dama sun saba xama daga su
sai lingerie, Aunty Jamila ta katse mata tunaninta tace "Don uwarki wataran da
kanki xaki bude baki ki fadi ta inda video ya fito, dena wani tunane tunane, yanxu
dai ki gama nuku nukunki da karyarki aikin gama ya riga ya gama tunda ga ki a gidan
mijin ki" Nihad ta fashe da matsanancin kuka tace "Wallahi ni ba mijina bane shi
Aunty, kuma baxai ta6a xama mijina ba, shi drivern ne zai zama mijina? Wllh baxan
ta6a yarda ba" Aunty Jamila tace "Gaskiya kam, tunda xa ki iya daukan takarda ki
rubuta masa saki ki sake sa... Kinga karshen rashin yarda kenan" Nihad ta kara
rushewa da kukan takaici, ita fa da taji ance khalil mijinta sai taji kamar an dau
duniyar gaba daya an aza mata a kai, da dai a dinga furta mata wannan kalmar gwara
a nuna mata bindiga kawai a harbeta, Aunty Jamila bata damu da kukanta ba ta bude
cup din da ta gani a rufe ta ga shayi ne a ciki, tace "Me kika ci yau?" Ta girgiza
mata kai hawaye caba caba a fuskarta tace "Ban ci komai ba" Aunty Jamila ta mike ta
fita daga dakin, Nihad ta fada kan gado tana rera kuka, Khalil na ganin Aunty
Jamila ya mike yace "Za a dauko maki wani abun ne Aunty?" Aunty Jamila tace "Aa, so
nake ko shinkafa da miya ne a samu a dafa, inji akwai kayan miya a gidan?" Yace "Aa
xan fita in siyo yanxu" Aunty jamila tace "Toh shkkn" Daga haka ta shiga kitchen
don daura ruwan shinkafa, Nihad ta hadiye kukan da take ta jawo jakar Aunty Jamila
ta zuge zip din, Wayarta ta ciro tayi dialing number din Nihal, sai ga number ya
fito da suna, aika kiran tayi ta kai kunne, Nihal na dagawa tayi sallama hade da
cewa "Ina yini Aunty?" Nihad ta wani kyabe baki tace "To ni ce nan ba ita ba" bata
jira Nihal ta saurari Nihal ba tace "Kin ga Number Husnah xa ki turo min ta nan
yanxun nan ba wani magana na kira ki min ba" Nihal tace "Ke me xa ki yi da number
Husnar nan ne?" Nihad tace "Wannan bai shafe ki ba, kawai ki turo min abinda na
tambaye ki" Magana Nihal take amma Nihad ta katse wayar kawai, ba a wani dau lkci
ba sai ga number Husnah ya shigo wayar Aunty Jamila, Nihad ta mike da sauri ta tafi
gun jakarta ta bude ta dauko biro da jotter, A hankali ta dawo ta zauna
sbda har sannan bata gama dawowa dai dai ba tana dan jin jiri, bayan ta kwashe
number ta tura takardan cikin pillow case dinta, sannan tayi dialing number Husnah,
yana fara ring Husnah ta daga, Nihad tace "Ni ce Husnah" Husnah dake cikin kasuwa
ta nemi wani shago ta shiga da sauri ta zauna tace "Nihad ina ta kiran wancan layin
da kika kirani da shi jiya naji kamar anyi blocking, line busy kawai yake sa min,
har dare ina trying wllh, to ni kuma na rasa ta inda xan sameki" Nihad tace "Ai
wayar wancan wawan yaron ne, wato blocking din ki yayi ko?" Husnah tace "Wallahi
kuwa, wai yanxu kina nufin daga ke sai shi a gida daya?" Nihad ta fashe da kuka
tace "Wallahi the thought of this na sa inji kamar in kashe kaina Husnah" Husnah
tace "Ki kashe kanki a kan wa?? Aa wallahi turo min address din gidan yanxu" Nihad
tace "Toh ai ban san ko ina ne nan din ba, amma bari in kira Umma in tambayeta"
Husnah tace "Toh maza kirata ko ki turo min numberta ni in kira" Nihad tace "Toh"
Katse wayar tayi ta hau kiran Umma, yana fara ring Umma ta daga, Nihad tace "Umma
ni ce" Umma tace "Aa Jamilan na can kenan yau?" Nihad tace "Ehh" Umma tace "Toh
anjima Amina na nan xuwa maki da wayar anyi rijistan layin" Nihad tace "Toh, Umma
su Husnah ne ke son xuwa kuma ni ban san address din nan ba" Umma tace "Gaskiya
baxa ki sani ba, kinsan me xai faru?" Nihad tace "Aa" Umma tace "Kice kawai su taho
nan gida sai su biyo Amina tunda ita ta san gidan" Nihad tace "Toh Umma" daga haka
Nihad tayi mata sallama ta katse wayar, ta kira Husnah ta sanar mata yanda suka yi
da Umma, Husnah tace "Hakan ma yafi sauki wllh, turo min number Aminar" Nihad tace
"Toh, amma kar ki kira layin nan na kanwar Mumy ce" Husnah tace "Toh shkkn, kawai
sai mun zo anjiman" Nihad tace "Toh" Daga haka ta katse wayar, tayi deleting duk
calls din da tayi ta goge message da tayi ma Husnah na number Amina, sannan ta
mayar da wayar cikin jakar. Bayan la'asar Aunty Jamila ta gama girka shinkafa da
miyan, A plate ta xubo ma Nihad ta fito parlor tana kallon khalil tace "Ga can
abincin an gama" Yace "Toh sannu da aiki Aunty, Mun gode" Dakin Nihad ta wuce ta
ajiye abincin a kasa, Nihad ta fito daga bandaki daure da towel, ta xauna gefen
gado tana kallon Aunty Jamila tace "Sannu da aiki Aunty" Aunty Jamila tace "Yauwa
sannu, kiyi maza ki ci abincin" Nihad tace "Toh nagode" nan ko ta rasa ta yanda
xata tambayeta yaushe xata tafi don bata son su Husnah su zo tana gidan nan, ganin
bata da niyyar tashi Aunty Jamila tace "Toh tashi ki fiddo kayan da xa ki sa mana"
Nihad ta mike ta bude jakar ta dauko riga da skirt, bayan ta shafa mai ta sa turare
sannan ta sa kayan, Aunty Jamila ta dauko abincin ta mika mata, amsa tayi ta fara
ci, gaba daya taji bakinta babu dadi tura abincin kawai take, Aunty Jamila ta mike
ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito tayi sallah, tana idar da sallah tace
"Aunty ke baxa ki ci abincin ba?" Aunty Jamila tace "Aa na ci abinci kan in fito
gida" Nihad bata kuma cewa komai ba, Aunty Jamila tace "Toh ni xan tafi Nihad"
Nihad ta sauke ajiyar xuciyar relieve don abinda take ta jiran ji kenan ganin hudu
da rabi yayi tasan kilan ma su Husnah na hanya yanxu, Aunty jamila tace "Ki bude
kunnenki ki saurare abubuwan da xan gaya maki da kyau" Nihad ta sauke idonta a
hankali tace "Ina ji Aunty" Aunty Jamila tace "Ki nutsu ki dawo hankalinki, kinga
wancan mutumin dake parlor??" Nihad ta daga kai ta kalleta, lkci daya har hawaye ya
cika idonta tun bata ji abinda xata ce ba, Aunty Jamila tace "Toh mijinki ne shi
yanzu...." Nihad ta rushe da kuka tace "Don Allah Aunty ki daina cewa haka, wayyo
ni a daina ce min haka gaskiya" Aunty jamila tace "Ba shakka, to rufeni da duka sai
in daina ce maki haka, ke ba taimakonki yayi ba da ya rufa maki asiri ya aureki?"
Kuka kawai Nihad take, Aunty Jamila tace "Toh wllh idan ba fushin Ubangiji kike son
ja ma kanki ba ki bi mijinki kiyi masa biyayya ki zauna lafiya a duniya, naga kamar
baki saduda ba har yanzu baki dau darasi daga abinda ya sameki ba, ni iyakar abinda
xan gaya maki kenan idan kin ji yayi maki amfani idan kika yi watsi da shi kuwa
kuka bai kare maki ba a duniya" Daga haka Aunty Jamila ta mike ta dau mayafinta ta
yafa, ta dau handbag dinta, kuka kawai Nihad take ganin ta nufi kofa sai kuma ta
mike ta bi bayanta cikin rawar murya tace "Toh Aunty karatuna fa?" Aunty Jamila ta
juyo ta kalleta tace "Wannan kuma sai ki tuntubi mijinki ki ji, mu kam ai bamu da
iko da wannan, in ya amince sai ki ci gaba" Nihad na girgiza kai tace "Aunty don
Allah kice masa ran monda xan tafi makaranta ni dai" Aunty Jamila tace "Ohk ni ce
ma xan gaya masa, ashe shkkn iyakar karatunki kenan a duniya in har ni xan gaya
masa" Fita Aunty Jamila tayi daga dakin tayi ma Khalil sallama a parlor, ya mike
yace "Aunty har za ki koma" Tace "Ehh wllh na bar yara a gida" Yace "Toh bari in
ajiye ki" Tace "Aa da kayi zamanka kawai Nagode, ina fita xan samu adaidaita sahu"
Yace "Aa bakomai, xan ajiye ki yanxu" daga haka ya dau makullin mota ya fita, sai
taji dadin yanda ya karramata sosai, kuma ko ba komai xata samu enough chance tayi
masa magana a mota a kan Nihad, Nihad ta bi sa da wani harara, Aunty Jamila ta
kalleta bayan ya fita tace "Wa kike harara Nihad?" Kin cewa komai Nihad tayi, Aunty
jamila tace "To ki sani yau shine ganina na karshe da xaki yi a gidanki, indai baxa
ki kwantar da kai ki zauna lafiya da mijinki ba" Nihad ta fashe da kuka har da
bubbuga kafa tace "Ni Aunty ki daina ce masa mijina don Allah, wayyo Allahna na
shiga uku" Kofa Aunty jamila ta nufa ta fice daga parlon, sai da suka fita daga
gidan Nihad ta koma dakinta tana share idonta, Allah ya kiyaye wannan ya zama
personal driver dinta balle kuma wai miji, suna fita ko minti goma ba ayi ba taji
ana kwankwasa gate, da sauri ta mike ta fice daga dakin ta tafi compound don ta san
su Husnah ne suka iso, tana isa gate din taji muryarsu kuwa, sosai wani farin ciki
ya lullubeta amma kuma lkci daya fara'ar fuskarta ya bace da ta ji ta kasa bude
gate din, kuma kamar ta waje aka kulle, Naf tace "Gate din ya ki buduwa ne kin bar
mu tsaye cikin rana?" Nihad tayi narai narai da ido tace "Wllh kamar ta waje ya
kulle" Husnah ta bude baki haka Zully, Naf tace "Amma dai wannan a yan iskan ma A
ne shi, ta waje ya kulle gate? To a saboda me? Akuyarsa ya ajiye a gidan yake
tsoron kar ta gudu da xai kulle ki cikin gida?" Nihad bata san sanda ta fashe da
kukan takaici ba shkkn da gaske kulleta yayi, Husnah tace "Ke kuma matsalarki
kenan, to meye na wani kuka" Amina dai na tsaye rike da ledan waya a hannu, Naf
tace "Toh wai ina yaje?" Nihad tace "Wai fa Auntyna ya kai gida shine sabida bashi
da hankali ya kulle min gate ta waje kamar gidan ubansa" Husnah tace "Kuma wllh
makulli ya sa, ni ko har na kagu in ga wannan me ido da kwallin" Nihad ta goge
idonta tace "Kawai ku ɗan jira a nan yanxu xa ku ga ya dawo" Haka suka yi ta jira a
bakin gate din, ita kuma ta zauna kan dakalin dakin da aka tanadar don mai gadi a
compound din, tun daga nesa khalil ke kallonsu a bakin gate din, yayi parking ɗan
nesa da gidan, Amina tace "Yauwa gashi can, motar gidanmu ce wannan" Su Naf duk
suka kafe motar da ido ana jiran aga fitowarsa amma bai fito ba, Husnah tace "Ji
gantalalle ya ki saukowa a motar" Zully tace "Shi ne ai nake kallon ikon Allah" Naf
ta kalli Amina tace "Ke tafi ki karbo mana makulli wajensa tunda ba shi da hankali,
uban wa zai bari tsaye cikin rana" Amina ta tafi a gun motar yana ganinta ya sauke
glass din can side din don duk sun gwala ido su ga ya sauke glass din side dinsa ko
xa su samu a little glimpse of him, Amina na ganin haka ta zaga tana kallonsa ta
cikin motar tace "Ka bamu makullin gidan" Yace "Su waye bakin gate din?" Amina tace
"Kawayen Aunty Nihad" Yace "Ohk, ke kika kawo su kenan?" Tace "Ehh Umma ta bani
sako in kawo mata ne shine muka taho tare da su don basu san gidan ba" Ya mika
hannu yace "Toh kawo a ajiye mata sakon, yanxu kasuwa xanje in yanko wani makullin
wancan ya fadi" Amina tayi kasake tana kallonsa, mika hannu yayi ya amshe ledan
hannunta yace "Ko xaki shigo in ajiye ki gida daga nan in wuce kasuwar?" Amina ta
daure fuska tace "Ni ai a motarsu muka zo" Yace "Toh koma motar tasu" Daga haka ya
ja glass ya tada motar yayi reverse ya bar layin.....

*Kiyi subscription ki karanta hankalinki kwance yar uwa*

*Nihaad* is 500 via Fcmb Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence via👇🏻


07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: Husnah ta kalli su Naf jin abinda Umma tace,
Naf tace "Aa Umma bamu zo da kaya ba, mu ma kawai yanzu xa mu wuce, idan ya so ko
gobe ne ma dawo" Umma tace "Toh shkkn, hakan ma yayi, Allah yayi maku albarka,
tunda ba da mota na zo ba mu je kawai ku ajiye ni" Duk jikin Nihad yayi sanyi ganin
xa su tafi su bar ta, babu yanda ta iya haka ta rakasu har bakin gate suka wuce
sannan ta dawo cikin gidan tana ta kumbure kumbure. Sai da su Naf suka kai Umma har
kofar gida tayi masu godiya tana sa masu albarka, sannan suka juya ita kuma ta
shiga gate, Aminu na gaisheta ko bin ta kansa bata yi ba ganin Abba a tsaye
balcony, karasawa balcony din tayi da sauri tace "Har ka dawo daga gidan Baffan?"
Abba na kallonta daga sama har kasa yace "Daga ina kike?" Ta sauke ajiyar xuciya
tace "Kayi hakuri ban ce maka xan fita ba, na fita babu izinu, wallahi Yallabai
Nihad ce kira ba dare ba rana ko da yaushe cikin kuka, to shine yau da abun ya
isheni nace bari dai in je in ga wani hali take ciki a gidan, kasan tun da muka kai
ta ai ban koma ba" Abba dake ta sauraronta har ta kai aya yace "Toh daga yau kada
ki sake xuwa gidan...." Da mamaki Umma tace "Kamar yaya fa Alhaji? Shikenan saboda
iftilai ya fada ma yarinya sai ka sallama ma duniya ita, mu ma kuma ka nemi mu
sallama ma duniya ita? duka duka nawa Nihad din take fisabilillahi Yallabai?
Yarinyar da ko shekara ashirin bata yi ba a duniya, me ta sani akan rayuwa at this
her early stage? so kake wani cutar yaje ya kamata a banza mu shiga uku? Kai kanka
kasan wannan yaron tun zuwansa gidan nan ba shiri suke ba, jininsu bai ta6a haduwa
ba amma ka rasa wanda zaka hadata aure da sai shi? Me yasa ma idan hadin ne baxa ka
hadata da wanda bata sani ba bai santa ba, sai Dreban gidansu? Haba wannan ai babu
adalaci yallabai, baka kyauta mata, wannan fa kaddararta ce, sannan ace duk
soyayyar da kake mata amma ka rufe ido ka saka rayuwarta a garari kawai don an samu
wasu shegu sun hada mata makirci?" Abba yayi shiru yana kallonta, can yace "Yanzu
shawara kike bani a warware auren kenan?" Umma ta kalli Abba, ganin how sincerely
he spoke, tayi kasa da kai tace "Ni ba haka nake nufi ba, kuma ai kai ba karamin
mutum bane aji an daura aure kuma an warware sa, mutuncin da kimarka ya wuce haka,
kawai dai ina jimamin abun ne, amma don Allah kar ka hanani zuwa wajenta ko ba
komai zan dinga kwantar mata da hankali har ta hakura da wannan auren" Abba yace
"Sumayya" Ta yi shiru tana sauraronsa, on a serious note yace "In har kina son
zaman lafiya da ni toh na haneki da kara taka kafarki zuwa gidan nan, idan da wani
abu xai kawota gida ba sai kin je, ina kara ja maki kunne babu ke babu gidansu,
sannan ko mutuwa take ke kina tunanin zan sa a warware auren? Ai sai dai ta mutu a
dakinta" Umma tace "Tabdi, to yallabai kamar yanda baxan yi shiru ba idan Nihal ce
aka ma haka to Nihad ma baxan yi shiru ba don duk daya suke a wajena babu banbanci,
don haka hanani zuwa gidan 'ya ta bai taso ba...." Abba yace "Good! Don Allah gobe
ma ki shirya ki kara komawa gidan, ina me tabbatar maki a nan xaki ga the other
side of me" Yana kai wa nan ya juya ya shige cikin gida, Umma ta bi sa da kallo sai
kuma ta kyabe baki ta bi bayansa. Su Husnah na komawa hostel duk suka shantake a
saman gado babu zancen sallah balle salati, Naf ta sauke wani ajiyar xuciya tayi
kasa da murya tace "Amma don Allah ku ya ku ka ga wannan drivern? Isn't this
strange?" Zully ta riƙe ha6a tace "Not as i expected, anya kuwa da gaske shine
drivern? Ni fa har muka dawo ina kokwanto a raina gaskiya" Husnah tace "Kun ji ku,
idan fa an bibiya irin shuwan nan ne fa wanda ba shi da galihu, farin fatarsa ce
tasa ku ke kokwanto ko driver ne shi ko ba driver ba?" Zully ta kalleta tace "Aa
maganar gaskiya duk da Umma ta tabbatar mana da shi din ne har xuciyata na kasa
yarda, ta yaya wannan cikakken mutumin xa ace driver ne? His skin... Ko ku baku
lura da shi ba, no plss he is so fresh abeg" Naf tace "Ohhhhoo ashe dai bani kadai
ma lura da skin dinsa ba, ni wallahi da ba don kar inyi karya ba ma sai nake ganin
kamar na ta6a ganinsa, ko me kama da shine oho" Husnah ta kyabe baki tace "Kanku
ake ji" Zully tace "Kai amma gayen nan Allah ya xuba masa kyau frankly speaking,
kawai mu fadi gaskiya, duk inda me kyau xai shiga shi ma xai shiga, kuma ina
tabbatar maku Nihad haukan ta bai taba barin ta nutsu ta kare masa kallo ba" Husnah
tayi wani dariya tace "Kai kuma da da wani zance, Ina amfanin kyau ba nera? kina
jin mutum na tukin mota for a living, kun ishe ni da wani yana da kyau? kawai Nihad
din ma kadai ya raina dan ya ganta er karamar yarinya ne, mu kuwa da muka kusa
talatin a duniya baki ga da muka masa wankin soso da sabulu bai iya yace mana komai
ba sai sissine kai da yake, ni fa baxan yi mamaki ba idan aka ce shege ne mutumin
nan, kilan uwarsa a titi ta haifesa ta yarda shi shine yake ta garari har ya samu
driving gidansu Nihad" Zully ta kwashe da dariya ita dai Naf bata ce komai ba,
Husnah ta kalleta tace "Ya dai... Kin yi shiru" Naf ta ɗan tabe baki tace "No kawai
ni dai i am not comfortable cewar shi din mere driver ne, he might definitely have
a mission, haba u girls should think deep mana, sai kace ba big babes ba, ko kayan
jikinsa idan kuka lura ai ba na banza bane, ni fa har takalminsa sai da na kalla,
wallahi da kyar idan mutumin nan ba wani mission garesa ba" Husnah da Zully suka
kwashe da dariya har da kyakyatawa, Husnah tace "Wllh shi ba kowa bane don ma ki ji
in gaya maki, a wannan zamanin babu wanda xai bata lkcnsa ya zo gidan mutane for
almost a year now wai da sunan mission, sai kace wani film ko novel, mission for
almost one year ace ba ayi accomplishing dinsa ba har yanxu? Ke dai ki yarda ɗan
talakawa ne mukus me shegen girman kai, don yaga fatarsa ja ce sannan gashinsa irin
na halfcast shine yake wani feeling, ba ga ire irensa ba a can Ibadan da Lagos suna
bara bakin titi, kilan shi ma daga can ya gudo arewa bayan ya girma" Zully tace
"Kuma haka ne wallahi, gasu can a karkashin gadan lagos har Ibadan" Zully ta kyabe
baki ta mike tace "Ni dai bari in je in yi wanka in zo in kira babyna, ba ruwana da
wani batun shegen dreba can" Naf tace "Yanxu yaushe za mu je mata can din, kun san
fa mun sa mata rai" Husnah tace "Mu bari kawai jibi don gobe kinga xa mu je
minjibir park" Naf tace "Ehh haka ne kuma, Allah ya kai mu" Washegari tuesday da
safe Nihad ta shirya tsaf xata makaranta abunta tunda ga makulli a hannunta,
mayafinta ta yafa ta dau jakarta bayan ta feshe turare kusan kala biyar a jikinta
ta fito daga dakin, yana jin fitowarta yayi saurain mayar da wayarsa dake hannunsa
xuwa bayan kujeran da yake zaune, bata ko kallesa ba ta nufi kofa ta fita abun ta,
da ido ya bi ta imagining if tsallake gate din xata yi, rabonsa da ita tun jiya
bayan ya bude ma Umma gate da suka zo, can dai ya mike ya fita parlon ya tsaya
bakin kofa yana kallon ikon Allah, tana isa gate ta bude jakarta ta ciro makullin
tana kokarin bude gate din taji yace "Keee" bata fasa bude gate din ba ta juya ta
kallesa bayan ta bude tace "Saboda baka yi karatu ba baka san muhimmancin karatu ba
kana tunanin ka isa ka hana ni zuwa makaranta ko, to baka isa ba, ba a kuma haifeka
ba" Tana gama fadin haka ta fice daga gate din, mamaki ne ya cika sa yayi saurin
ciro makullin aljihunsa yana kallo yaga it's intact, then where did she get a space
key?? bai yi attempting bin ta ba balle har tayi showcasing altitude dinta a bakin
titi, ya juya ya koma parlor filled with surprise. Ba karamin mamaki su Husnah suka
yi ba ganin Nihad a school, Nihad ta zauna aji jikinta duk a sanyaye don tun da ta
shigo schl ake nunata, wai ga warce ke cikin video din nan, har ta iso ajin da suke
lectures idon jama'a na kanta, bata kara jin damuwan video dinta da ya bazu duniya
ba sai a yanzu, dama haka abun ya tafi viral, a ajin ma sai satan kallonta ake ana
kuskus, kai har ma da masu shigowa duk da ba department dinsu ba don kawai a zo a
ganta, sai a sannan tayi da ta sanin fitowa, kuma fitowar ma da ɗan karamin mayafi,
daga karshe dole su Naf suka dauketa suka fita makarantar xuwa hostel dinsu, Nihad
ta zauna gefen gado lkci daya hawaye ya kawo idonta, Husnah tace "Kin ji ki, meye
abun damuwa, abinda ba kanki farau ba kuma ba kanki za a kare ba, duk dan iskan da
ya isa ya tinkare mu yace ai kece a video yaga yanda xa mu ci ubansa, ni ai baki ce
min xaki taho makaranta yau ba da na hanaki don su yanxu ma suke tashen labarin,
kuma ana ta jira aga kin shigo makaranta sai ga ki yau, ni ban ta6a ganin munafukai
yan sa ido marasa aikin yi kamar yan makarantar nan namu ba, abu kusan sati daya
amma kullum maimaita zancen ake kamar yau ya faru" Nihad ta hade kanta da gwiwa
tana shessheka tace "Da na sani ban fito ba" Naf tace "Surutun mutane zai sa ki
fasa rayuwarki yanda kike so? Ai ba a biye ma mutane, gwara su yi ta ganinki din
har su gaji su yi shiru zancen ya mutu, yanzu dai ina kika baro ɗan rainin wayon
Drivern can?" Nihad na goge idonta cikin sanyin murya tace "Toh meye hadina da
wannan kuma kike tambayata" Naf tace "Aa babu hadinki da shi kam, ni ai na ga
kokarinki ma da kike iya kwana gida daya da shi, da ni ce kwasan kayana xan yi in
bar gidan iyaka Abba yayi bambami a wuce wajen" Nihad ta kalleta tace "Abbanmu yace
xai yi disowning dina if i try anything of such" sai kuma ta fashe da kuka sosai,
Naf tace "Aa ba kuka xa kiyi ba, nema ma kanki mafita xa ki yi" Nihad tace "Don
Allah ku dawo gidan mu zauna gaba daya a can" Naf tace "Dama gobe muka yi ai za mu
je can din" Nihad tace "Tunda na fito yau don Allah ku dau kayanku kawai mu koma
can gaba-daya, the house is nothing but a living hell for me" Naf ta kalli Husnah
dake ta danna wayarta bata ce komai ba tace "Husnah ya kika ga" Husnah tace "Duk
yanda ku ka yi" Naf tace "Toh kawai duk mu dau kaya ko kala biyar biyar ne mu tafi
can din gaba daya" Nihad tayi murmushin jin dadi tace "Amma naji dadi Nagode wllh"
Zully tace "What are friends
for, ai amfaninmu kenan" Nihad tayi kasa da murya tana kallon Naf tace "How about
Aliyu?" Naf tace "Hmm, kinsan he is off social media tun da abun nan ya faru, to in
gaya maki 3 days ago mun yi chatting da wani frnd dinsa yake ce min ai ba shi da
lafiya ma" Nihad tayi narai narai da ido tace "Da gaske?" Naf tace "Wllh kuwa bari
ma in nuna maki chatting din" Jawo wayarta tayi ta bude ta shiga chatting dinta da
wani abokin Aliyu ta mika ma Nihad wayar, Nihad ta amshi wayar jiki a sanyaye ta
dinga bin chat din, abokin gaya ma Naf halin da Aliyun ya shiga bayan faruwan
lamarin yake, ya kuma ce mata har su abokanansa yayi isolating din kansa daga
cikinsu ba ma social media ba kadai, abokin ya dinga nuna yanda Nihad ta kwafsa ga
shi Aliyu yayi trusting dinta sosai kuma ya sa ran zai aureta duk da tulin manya
manyan babes dinsa, Nihad ta hade kai da gwiwa tana shesshekar kuka tace "I don't
know who did this to me, i don't know who is this that ruined my happiness" Husnah
ta sauke ajiyar xuciya tace "Na fi ki son mu gano wanda yayi maki haka Nihad, amma
abun akwai rikitarwa ni wallahi kawai zuciyata ta kasa yarda cewar ke ce a video
din, ke baki zama da undies haka kamar yanda mu muke yi, sannan duk party tare muke
zuwa balle ace wani partyn kika je aka maki haka, abun dai akwai confusion sosai
wallahi, wanda ya sanki sosai sosai ne yayi maki wannan abun, i wish Abba xai ajiye
duk wani fushi ya tsananta binciken ta ina wannan video din ya fito" Zully ta sauke
ajiyar xuciya tace "Ai na dau darasi ni kam, ko daga ni sai singlet da skin tide
baxan sake xama a waje ba balle undies, na saka kaina a shoes din Nihad ya fi a
kirga but luckily the shoe did not even size me, waiii ai ni kashe ni kawai xa ayi
a gida wallahi" Naf ta tabe baki tace "Koma waye da kansa zai tona ma kansa asiri
nan ba da dadewa ba" Nihad ta share hawayen da ya ki tsaya mata tace "Pls Naf try
calling Aliyu ki ga ko zai daga" Naf tace "Toh Allah ya sa ya daga, ko kuma ma dai
Allah ya sa ya shiga" Contacts dinta ta shiga tayi dialing number Aliyu, ai ko ya
fara ringing, gaban Nihad ya dinga faduwa tana kallon wayar, su kansu gaba daya
kallon wayar suke, sai gashi kuwa ya daga, sai da Nihad taji xuciyarta ya kusa
shigewa cikinta, Naf tace "Hello Aliyu what's up?" Daga daya bangaren cikin cool
voice yace "Fine Nafisah, how are you doing" Tace "Cool, ya garin" Yayi shiru, tace
"Are u there?" Yayi kasa da murya yace "U saw how ur frnd played with my heart
right?" Nihad ta kauda kanta hawaye sai zarya yake a fuskarta, Naf tace "Calm down
Aliyu, duk wannan abun set up ne ba wani abu ba, ka fi kowa sanin halin Nihad,
sannan mu da muke tare da ita always xa mu shaideta, wllh wllh Nihad bata tsayawa a
cikinmu daga ita singlet balle undies, wannan lamarin da rikitarwa yake, wa ya sani
ko anyi hakan ne don a raba ku tunda anji xaka turo gidansu" Aliyu yace "But i have
warned her severally Nafisah, na sha ja mata kunne duk yawace yawacen zuwa party ta
daina, but unfortunately bata daina ba, and ga abinda ya faru daga karshe" Naf tace
"Kai wai wa yace maka a wajen party aka yi mata haka? Ko a gida baxa ayi iya yi ma
mutum haka ba sai wajen party kawai? Kai dai kawai ka kyale makiyi Ali" Aliyu yace
"I am so heartbroken Nafisah" Naf tace "So is she also" Yace "Tana ina yanxu?" Naf
ta kalli Nihad sai kuma ta ɗan yi murmushi tace "Mun zo gidansu ne daxu ganin halin
da take ciki shine nace bari dai kawai in kiraka" Yayi shiru, tace "In kai mata
wayar pls?" Nan ma dai shirun yayi, tace "Don Allah kar kace A'a, ko sai kaji ta
mutu xaka fara da ka sani an kai mata wayar? Wallahi she is seriously sick" Yace
"Kai mata" tace "Yauwa my guy" kallon Nihad tayi tana Murmushi, ita dai Nihad ta
sunkuyar da kanta kawai, Naf ta kamo hannunta ta saka mata wayar a ciki, a hankali
ta kai kunne tayi sallama. Aliyu yace "Now u get the reason why nake rabaki xuwa
party?" Bata iya ta ce masa komai ba ta a goge idonta, yayi kasa da murya yace "Why
Nihad, why?" Cikin rawan murya tace "I don't know how everything happened, kayi
hakuri don girman Allah" yace "In yi hakuri Nihad? Ta yaya iyayena xa su amince da
aurenmu bayan duk sisters dina babu warce bata ga wannan video din naki ba, hatta
mum dita ta gani, innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Nihad dai bata ce komai ba,
Yace "How will we mend this damage?" Nihad tace "Abbana yace min wai ya min aure"
Aliyu yace "Ban gane yayi maki aure ba, kina nufin aure Abba xai maki?" Cikin kuka
tace "Ehh har ya min" Aliyu yace "Stop it Nihad, yaushe yace maki haka" A raunane
Nihad ta sanar masa yanzu ita da khalil suke zama gida daya, kuma Abba ya sanar
mata wai yayi mata aure da shi, lkci daya ya birkice mata yace "Baby yanxu kina
nufin aure aka maki, aure da drivern nan na gidanku?" Nihad ta girgiza kai da sauri
tace "Ni ba a min aure da shi ba, kawai Abba ne ke fadan hakan, ni ban yarda an min
aure da shi ba" Aliyu yace "Nooo, it can never be, not when i am alive, hakan baxai
ta6a yiwuwa ba, na yi isolating kaina from everything na kwana biyu ne but nasan
baxan ta6a iya rabuwa dake ko da nayi attempting din yin hakan ba, i know i will
come back to you, kuma ko iyayena bana jin xa su hanani in aureki don sun san ina
son ki, ko da nude video dinki ne yayi yawo i stil love u Nihad, and i will still
marry u" Nihad dai ta yi kasa da kanta ta kasa cewa komai yace "Ki kulan min da
kanki Nihad, do not break my heart for the second time pls, sannan ta ina xan dinga
samunki ko 2 days ago i tried ur number naji switch off" a hankali tace "Xan kiraka
da sabon line dina idan na koma gida" Yace "I will be expecting pls" Sallama suka
yi, Naf ta amshi Wayarta tace "Alhamdulillah" Nihad ta ɗan yi murmushi, Husnah tace
"Gaskiya Aliyu ya san kaddara, yanxu ke kuma sai ki san duk yanda xa kiyi ku raba
jaha da wancan driver din, koma yaya xa ayi kawai ya sake ki tunda Aliyu is still
willing to marry u" Nihad ta kalleta tace "Ya sakeni?? To da aurena yayi da xai
sakeni? Ai kawai xama muke gida daya bisa umarnin Abba, but i am for Aliyu alone"
Zully tace "Atoh, kunsan akwai wani aure da xaka ji sa kamar wasan yara, to irin
auren nan naku da drivern kenan, ko ni bana kallonsa a matsayin mijin Nihad
wallahi, kilan kawai Abba is playing u, amma ta yaya ma xai ce ya maki aure da
dreba" Nihad tace "Toh kun ga lkci na wucewa mu tafi pls" Naf tace "Bari in kara
watsa ruwa" Zully ta mike tace "Ina zuwa in kwaso kayana" daga haka ta fita daga
parlon, Husnah ta kalli Nihad tayi kasa da murya tace "In baki shawara? Toh wallahi
kar ki yarda su wani bi ki, gwara kiyi tafiyarki ke kadai daga baya ni kadai sai in
biyoki gidan, idan ba haka ba akwai matsala" Nihad tace "Matsalar me fa?" Husnah
tace "Toh shkkn ki tsaya tambayar ta me, naga dai ni kika fara sani kafin su, kuma
ta dalilina kika san su, don haka kawai yanxu kice masu gidanku xa ki daga can ne
xaki wuce gida kina komawa gida kuma xaki kira kice mu taho gaba daya" Nihad tace
"Toh shkkn" Mikewa Husnah tayi ta fita daga dakin. Khalil ya fito compound jin ana
Knocking gate, yana bude gate din ya ga Farooq a tsaye, welcoming dinsa Khalil yayi
with smile all over his face, Khalil ya rufe gidan suka koma can parlor tare,
Farooq na cewa "Gobe xan koma aiki shine nace bari in shigo yau dai" khalil yace
"Allah sarki" Suna shiga parlon Farooq na bin ko ina da kallo yace "Ina take?"
Khalil bai basa amsa ba kawai ya tafi kitchen don ya dauko masa ruwa, Farooq ya dau
throw pillow da ke kan kujeran da yake kokarin zama sai ya ga Iphone, duk tunaninsa
na Nihad ne duk da a gabansa Abba ya kwace Iphone din nata, Farooq ya zauna yana
jujjuya wayar amma sai ya ga ba na Nihad bane, dai dai nan khalil ya fito daga
kitchen with bottle water and glass cup, still yayi yana kallon Farooq.....

Nihaad is 500 via 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah

And u show ur evidence of payment via 👇🏻

07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: Husnah suka kalli junansu da sauri ganin Khalil
ya juya motar xai bar layin, Amina ta dawo fuska a daure tace "Wai wani zai je ya
yanko wani makullin" Husnah ta rike kugu tace "Tashin hankali, lallai wannan
mutumin dan iska ne, karya fa yake yi wllh, mu din dai ne baxai bude ma gidan mu
shiga ba" Nihad ta taso da sauri ta tsaya jikin gate din tace "Me ya faru?" Naf dai
ta kasa cewa komai tun da ta bi motar da ido baki bude, Zully tayi wani dariya ta
rike ha6a tace "Kan uban can... Amma gayen nan daga ɗan iska sai shi, but don Allah
ku baku ji kun kagu kuna son ganinsa ba? It's the gut for me" Nihad dake ta zaro
ido ta kasa fahimtar abinda suke cewa tace "Don Allah ku min magana mana, ya dawo
ne?" Husnah ta sauke wani uban ajiyar zuciya ta koma bakin flower ta zauna tana
girgiza kafa, Naf da wani bakin ciki ya isheta tace "Amma idan ban tara yan sara
suka da yan da6a sun ma drivern nan mugun bugu ba ku ce bani bace, don kaza kazansa
da uwar me yake takama xae walakanta mu haka da girman mu, wa ye shi xai dinga
feeling kansa haka yana fama da talauci..." Tuni Nihad ta fara fahimtar abinda ya
faru hawaye ya cika idonta, ita dai ta shiga uku da abinda wannan yaron ke yi mata,
Husnah ta kara sauke wani axababben ajiyar xuciya ta mike tace "Nihad mu xa mu
tafi, ashe da gasken gaske tsinanne ne mutumin nan sai yau na sake tabbatarwa, wato
tantirin ɗan iska ne na bugawa a jarida, har mu zai walakanta ya juya kan mota ya
bar mu uwa yan iska a tsaye bakin gate? Who the hell did he think he is" Nihad ta
sakar masu kuka tace "Ba ina gaya maku ba kun zata exaggerating nake, ai wallahi
zai iya yin abinda ya fi haka, ina Amina?" Amina tace "Ga ni" Nihad tace "Ki kira
Umma da wayarki ki gaya mata abinda dan iskan yayi maku" Amina ta fiddo wayarta a
jaka ta hau kiran Umma, Umma na dagawa ta larabta mata abinda khalil yayi masu a
bakin gate, Umma ta rike ha6a bayan ta gama sauraron Amina tace "Yau ga shegen
mutumi, kuna nan har yanzu bakin gate din kenan a tsaye?" Amina tace "Wallahi" Umma
tace "Ina wayar Nihad din?" Amina tace "Ya karɓe wai xai ajiye mata" Umma ta wani
mulmulo zagi ta lafta mata tace "Uban wa yace ki basa? Wajensa na aiko ki xaki basa
waya? To wallahi duk inda xaki nemosa ki nemosa ki amsar min wayata, kaji min
doluwar yarinya kawai" Amina ta turo baki tace "To wai ba karbewa yayi a hannu na
ba, ni me xan ce masa" Umma ta kara kunduma mata zagi tace "Ubanki ne ya siya min
wayar da xa ki ba wani ɗan iska can? Na dai gaya maki kar ki kuskura ki dawo min
gida babu wannan ledar wayar, shashashar banza kawai doluwa" Daga haka umma ta
katse wayar tana huci, Nihad tace "Ban gane ba, wayar kika basa Amina?" Amina tace
"Toh wai ba amshewa yayi a hannuna ba yace xai ajiye maki" Nihad ta kunduma mata
zagi ita ma tace "Wallahi maza ki bi sa ki amso min wayata, meye hadina da shi da
har xai amsar min waya yace xai ajiye? Munafuki kawai" Amina tace "Ni dai wallahi
ku daina min masifa tunda ba ni na mika masa ba" Husnah tace "Toh wannan takadirin
ai ko bata basa ba xai iya fizgewa a hannunta, don naga kamar ya ta6a dabanci, ni
dai wllh bai walakanta banza yau din nan ba, xai san ya ta6a Clique dinmu..." Naf
duk ta fi su shiga takaici a wajen, she really wants to meet with Khalil ya ga
karshen rashin mutunci da tijara, Zully tace "Ni anya ma ba shi yaje ya samu Abban
yace a basa auren Nihad din ba kawai don ya samu hanyar dinga walakantata?" Nihad
na tafe hannu tace "Ai ko da kansa xai tafi ya samu Abban yace masa yayi hakuri ya
fasa auren, i am going to make life miserable for him, xai san cewar ni ba sa'ar
zama waje daya da shi bace balle uwa uba aure, shi har ya isa ya aureni? Wallahi da
wuri wuri zai koma gun Abba yace ya fasa" Husnah tace "Atoh, duk wannan koke koken
da kike yau kwana da kwanaki babu abinda xai tsinana maki sai ma 6ata lokacin ki da
kike ki ji in gaya maki, yanzu kamata yayi ace kin zauna kin nutsu kin fara nazarin
ta yanda zaki fara musguna ma shege, kar ki kuskura ki raga masa daga cikin tijara
da iskanci da muka iya a Clique dinmu, In his next life ko million daya xa a dinga
basa ya zo gidan masu kudi yayi driving wallahi baxai zo ba, shi din banza shi din
hofi" Sosai hudubar Husnah ke shigar Nihad da taji daga wannan moment din ta daina
kuka, baxata kara asaran hawayenta ba akan Halilu, sai dai ta fara daukan action a
kansa, kuma da ƙafafuwansa xai gudu ya bar mata gidan ya koma kauyensu na har
abada, Husnah tace "Kuma gidan nan ko da uban wa yake yawo sai mun shiga gobe,
balle daga shi sai talauci yake yawon ma, wallahi kamar mun shiga gobe, Allah ya
kai mu goben, kuma ina fatan Allah Ubangiji ya hada mu da shi face to face goben"
Nihad ta sauke ajiyar xuciya saboda sosai ta samu kwarin gwiwa, tace "Amina ki ɗan
ara min wayarki mana zuwa gobe" Amina tace "Toh ni sai in yi amfani da wanne?" A
fusace Nihad tace "In za ki ara min ki ara min malama, banza kawai ba ke kika je
kika mika ma wawan can wanda Umma ta baki ki kawo min ba? Dallah bani wayarki ai ba
cinyewa xan yi ba" Amina tace "Ban ga xan iya ba, ni islamiyya ma xan yi tafiyata
daga nan, duk an bata ma mutum lokaci ansa na makara kawai a banxa, sai da nace ma
Umma ni islamiyya xan tafi amma ta ki" daga haka ta juya fuuu ta bar su wajen a
tsaye, Husnah tace "Ke rabu da wani aran waya, gobe ni da kaina xan kawo maki waya,
screen touch kuwa" Nihad tace "Toh ta yaya, bayan kina ganin abinda yake yi da
gidan kamar na ubansa" Husnah tace "Baki yi trusting dinmu ba kenan?" Naf tayi wani
Murmushi tace "Ai kamar mun shiga gidan nan gobe idan Allah ya kai mu, ki saurare
mu idan mun tashi test" A hankali Nihad tace "Toh shikenan, Allah ya kai mu" Zully
tace "Toh wai ya sunan wannan tatattcen mutumin ne?" Nihad tace "Halilu naji ana
kiransa" Duk suka kwashe da dariya Husnah tace "Za mu haliro masa gobe kuwa" Daga
haka suka yi mata sallama, tana jin suka shiga motarsu suka bar layin, ta sauke
wani ajiyar xuciya ta juya ta koma cikin gidan. Sai bayan magrib Nihad ta ji
shigowar Khalil gidan, nan da nan taji bacin ranta ya ninku a kan na da, tana jin
sa ya shigo parlor ta mike ta fito parlon, bai ko kalleta ba ya ajiye ledan
hannunsa ya zauna saman kujera ya dau remote yayi powering tv, a fusace ta karaso
cikin parlon ta fixgo ledan da ya ajiye don a tunaninta wayarta ce, da ido ya bi ta
har ta gama bincika ledan ganin fruits ne ta cillar a gefe, tana tafe hannu cike da
tsiwa tace "Ka buda kunnenka da kyau ka saurareni, yau ya zama first and last day
da xaka sake kulleni a gida idan xaka fita don ni ba akuyarka ko tinkiyarka bace,
kuma ka bani wayar da Ummata ta aiko min" Kallon Tv kawai khalil yake, tayi masa
wani tsawa tace "Baka ji na ne ina maka magana?" Still bai kalleta ba balle ta sa
ran xai amsa, a mugun fusace ta tafi ta kashe socket din gun Tv din gaba daya tana
kallonsa tana huci, Khalil ya kalli karamar wayarsa dake ring, dagawa yayi ya kai
kunne yace "Idan na gama abinda nake xan kira ki Hajiya" Huci kawai Nihad take tana
kallonsa, yana katse wayar ya mike ya nufi bedroom, wani bakin ciki ya kara rufeta
ta bi sa da sauri ta shige gabansa tana cewa "Ni ce ma zan dinga maka magana zaka
tashi ka bar wajen, to wallahi baka isa ba...." zata cakumosa kamar yanda ta saba
ganin kallon da yake mata sai ta fasa kai hannun nata kwalarsa, Cikin kakkausar
murya yace "Matsa ki bani waje" Duk da yanda gabanta ke faduwa tace "Baxan matsa
ba, ka bani wayata tunda ba kai ka siya ba...." Irin kallon da taga yake mata yasa
ta fashe da matsanancin kuka ta durkushe wajen don can kasan xuciyarta a tsorace
take da shi, ya bi gefenta ya shige daki abunsa ya kulle kofar. Mikewa tayi tana
kuka tana bubbuga masa kofa tace "Ni wallahi ka bani wayata tunda ba da kudinka aka
siya ba, ina ruwanka da sakon da aka kawo min da xaka sa hannunka ka amsa" Banza
yayi mata, ita kuma bata fasa bubbuga kofar ba, bayan kusan minti biyar taji ya
bude kofar sosai gabanta ya fadi ta koma gefe da sauri amma kuma bata fasa fadan
abinda take fada ba, taga ya sa ma dakin makulli ya cire sannan yayi hanyar kitchen
ya shiga, bin sa tayi har bakin kofar kitchen din ta tsaya tana kuka tace "Wallahi
idan na maka Allah ya isa sai ya bi ka har generation dinka, ka bani wayana nace"
Gas ya kunna ya dau karamin tukunya sabo ya dauraye ya sa ruwa a ciki ya daura
saman gas din, bata fasa masa fitsaran da take ba a bakin kofa, ya juya ya ɗan
kalleta, ta wani maka masa harara tace "In kuma siyarwa kaje kayi sai ka gaya min
in cire rai" Shi dai bai ce mata komai ba ya rungume hannunsa yana jiran ruwan ya
tafasa, ta rushe da kuka ta hade kanta da kofa tace "Wayyo Allahna na shiga uku" Ya
daga kai ya ɗan kalleta, juyawa yayi yana kallon ruwansa dake saman gas, ta dago
kai cikin kuka tace "Koma me kayi da wayar ban yafe ba...." Ko rufe baki bata yi ba
taga ya cire hannunsa da sauri daga handle din tukunyar alamar ya kona sa, ya koma
baya yana kallon tukunyar, wani shegen dariya ta saki har da kyakyatawa ta durkusa
a wajen, yanda take dariyar kai kace bata da sauran damuwa a duniya, ya ɗan kalleta
sai kuma ya shafa kansa ya juya yana murmushi ya kalli inda ya tukunyar ta kona sa,
ruwan da bai juye ba kenan ya bi gefenta ya fice daga kitchen din ya bar ta a ciki,
bayan ta ci dariyarta ya isheta sai kuma ta mike ta hade rai, a hankali ta dauke
tukunyar shinkafar da Aunty Jamila ta girka, ta dau na miyan ma duk ta kai dakinta
da plate da spoon sannan ta koma ta jawo kofar kitchen din ta saka makulli ta zare,
sai ta ga ta yanda xai sha shayin yau, infact forever and ever, don ta kulle
kitchen din kenan har abada, Dakinta ta wuce ta bude akwatunta ta binciko duk kayan
ta ajiye makullin karkashin akwatin sannan ta mayar da kayan ta kulle akwatin ta
koma gefen gado ta zauna. Tun kafin tayi sallan magrib tayi wanka, don haka ta zuba
abinci ta ci, ta tashi ta shiga bandaki ta wanke bakinta ta dauro alwala, tana yin
sallan isha'i ta sa ma dakinta makulli ta ta dawo ta kwanta. Washegari bayan
Nihad tayi wanka ta wanke bandakinta, she can be lazy in all aspects but not when
it comes to her bathroom and Bedroom, bayan ta fito sai da ta fara gyara dakinta
sannan ta saka kaya, sbda mugunta haka ta zuba sauran shinkafar da sanyi ta ci, ta
koma bandaki ta kuskure bakinta da mouth wash ta fito, Hijab har kasa ta daura
saman kayanta, sannan ta dau jakar da take xuwa makaranta da shi ta bude kofa a
hankali ta fito parlor, yana kwance saman doguwar kujera, ta galla masa wani harara
ta karasa cikin parlon, ta tsaya bayan 2 seater, ta dake tace "Makaranta xaka
ajiyeni malam" Khalil ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya mike zaune yace "Ohk,
wace makarantar?" Babu yabo babu fallasa tana juya ido tace "Wanda ka saba kai ni"
ya gyada kai yace "Ohk" Sai kuma ya koma ya kwanta, a mugun fusace tace "Kana bata
min lokaci lectures din safe gareni, ko kuma ka bani makullin motarmu inyi
tafiyata" Khalil yace "Ki jira duk sanda Allah ya nufa kin koma can gidan naku da
xama sai ki ci gaba da xuwa makarantar, amma a nan gidan kam ke da fita ko nan da
gate sai wani ikon Allah, na soke xuwa wannan makarantar har abada" Da mamaki take
kallonsa baki bude, sai kuma ta hadiye abu da kyar tace "Kai kuma a uban wa xaka
gaya min haka? Kai a wa xaka soke min xuwa makarantata?" Ya kalleta yace "Kira
Abbanki ki tambayesa" Bata san sanda ta fashe da kukan takaici ba tana kallonsa,
yace "Allah ya amfana ɗan wanda kika samu" Yana kai wa nan ya mike ya shige daki ya
bar ta wajen, sulalewa kasa tayi tana kuka sosai, wai yau common driver ne yake ce
mata baxata je makaranta ba wai ya soke, whatttt??? Nihad ta ci kuka ta gode Allah
a wajen kafin ta shiga daki, komai na duniyar ta ji ya isheta.... Throughout ranan
haka ta yini a kwance tana hawaye, tana mugun son tayi magana da Umma amma babu
dama, don babu wayar da xata yi kiran, she needs to tell Umma this, bayan Umma bata
da wani wanda xata gaya ma, tana jin an kira la'asar ta mike zaune, sosai kanta
yayi mata nauyi, ga magungunanta rabon da ta sha tun jiya, kuma bata jin xata sha,
shiru shiru bata ji alamar ya fita gate ba gashi har an tada sallah, mikewa tayi a
hankali ta fita parlor, ta dinga bin parlon da kallo ta kalli bakin kofa taga ba
takalminsa, to har ya fita kenan bata ji ba, komawa corridor din dakunan tayi ta
kai hannunta handle din kofar dakinsa ta murda a hankali kofar ya bude, ta leka
cikin dakin ta ga ba kowa, kallon karamar wayarsa dake saman gado ta dinga yi, dai
dai nan ya bude kofar bandaki ya fito, tayi masa wani tsinannen harara ta juya ta
koma dakinta. Bayan ya dawo masallaci yana zaune compound bai shigo parlon ba yaji
an kwankwasa gate, ya dinga kallon gate din kafin ya mike ya tafi bakin gate din,
har sannan ba a fasa kwankwasawa ba, yace "Waye?" a fusace Umma tace "Malam xaka
bude min kofa ko kuwa? Ji wani tambayar walakanci wai waye, shi dama talaka ai bai
iya samun waje ba, ka tashi ka garkame gida kamar na ubanka, da an kwankwasa kuma
kace waye, to masu shi ne sai ka bude ko?" Khalil na tsaye yana sauraronta, sai da
ya dau kusan 40 seconds kafin ya bude gate din, Umma ce tsaye da su Husnah a bakin
gate din, Yayi kasa da kansa yace "Ina yini" Umma tayi mitsi mitsi da ido tace
"Ban yini ba, nace ban yini ba, ɗan marasu mutunci" Ya so juyawa ya bar wajen amma
ya kasa sbda girma da mutuncin da Abba ke da shi a idonsa, Husnah, Naf da Zully
suka dinga kallonsa babu kwakkwaran kiftawa, duk tambaya daya ce ke yawo a
xuciyarsu, wannan shi ne dreban, is he the driver? Husnah tace "Umma wai shine
driver din??" Umma tace "Gashi kuwa kin gansa" Duk suka kalli junansu, Husnah ta
tafe hannu tana kallon khalil tace "Wato kai ne ɗan rainin wayon da ya barmu bakin
gate jiya? Kai ga ka shafaffe da mai ko?" Naf na nuna sa da yatsa tace "Kai kana
buzu har xaka zo kasar mutane kana bubbusa hanci kamar algaita? Waye kai? Kuma uban
me kake takama da shi? Kasan mu su waye da kake tunanin zaka mana walakanci ka
kwana lafiya?" Zully tace "Ai ni na ma rasa ta cewa, wato wannan dai shine driver
me ba kawar mu though time, toh hasken naka kake takama da shi kake tijara ko me?"
Nihad ce ta taho da gudu ganin Umma ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Sai
kuma ta sake Umma ta rungume su Husnah gaba daya har da hawayenta sbda tsabar farin
ciki, juyawa khalil yayi ya bar wajen kamar zai tashi sama, Husnah tace "Sai ga mu
ga ɗan rainin wayon nan yau" Nihad ta sauke wani ajiyar xuciyar takaici, Umma tace
"Wato bai baki wayar ba dai" Nihad tace "Wallahi kuwa, ya ki bani" Umma tace "Mu je
ciki, sai na ci kaxa kazansa, wato yanxu baya ganin kowa da gashi sbda Alhaji ya
gama bada mu gabansa yayi mugun raina mu, yo ya bada mu mana tunda har xai dau yar
sa ya basa, idan ma hadin yake son yi ina 'ya yan abokanansa?" Duk suka dukufa xuwa
cikin parlon Umma na ƙare ma Khalil zagi su Husnah na tayata, shi kam tuni ya shige
daki ya sa makulli, sabuwar waya dal Husnah ta siya ma Nihad har da sim card a
ciki, murna wajen Nihad ba a cewa komai, gaba daya ta mance damuwar da take ciki,
Umma tace "Kinga shikenan sai ki kwantar da hankalinki yanxu, tunda sun ga gida
kullum kya gansu, kafin dai su dawo nan din gaba daya" Nihad ta marairaice tace
"Umma fa kulle gate din yake yi kuma makullin na jikinsa" Naf tace "Amma fa kamar a
jikin gate din ya bar makullin yanxu da ya bude mana fa" Husnah tace "Idan ko haka
ne kawai cirewa xa mu yi mu je a yanko mana spare" Zully tace "Bari in duba" Mikewa
tayi ta fita, sai ga ta ta dawo rike da makullin tace "Ai ko dai gashi" Umma tace
"Toh Alhamdulillah, tunda dare bai yi ba yanzu me xai hana ku je inda ake yankan
spare din a yanka maku?" Naf ta mike tace "Yanzu kuwa, kawai kudi za mu cika masu
yau yau din nan xa a yanka a bamu" Naf da Zully ne suka tafi da makullin wajen
yankar makulli, Nihad ta dauko ma Husnah makullin kitchen xata dafa masu taliya
wai, Nihad na kallon Umma ta marairaice tace "Umma yau na shirya xan je makaranta
ya hanani wai ya soke" Buda baki Umma tayi tana kallon Nihad, sai kuma tace "Toh ba
a haifi ubansa ba balle shi, shi har ya isa ya soke maki karatu? Bari dai su yanko
makullin kawai, ki kwantar da hankalin ki, ai indai da raina babu me cutarki a
duniya Nihad, sannan nace maki ki wani manta da batun dreba kiyi rayuwarki yanda
kike so, ga makulli nan xa a kawo ai, rayuwarki kawai za ki dinga yi yanda kike so
kanki tsaye" Nihad ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh Umma" Umma ta sauke wani ajiyar
xuciya tace "Yanxu shkkn har yau Aliyu ba neme ki ba ko?" Lkci daya hawaye ya kawo
idon Nihad ta girgiza kai hawayen na sauka fuskarta tace "Ai blocking dina yayi
Umma, kuma sim din ma na karya ai... Umma ban san waye yayi min haka ba kilan don a
rabani da Aliyu ne." Kuka take yi sosai kamar ranta xai fita, cikin rawar murya
tace "Wallahi ina sonsa Umma, gashi yanxu an rabani da shi" Umma tace "Aa ki daina
cewa an raba ku, kina fara xuwa makaranta duk yanda xa ayi ki nemi numbersa ki
nema, ba kince min a kawayenki akwai me numbersa ba?" Nihad ta gyada kai hawaye na
gangarowa fuskarta tace "Naf tana da numbersa, dama can sun san juna a Uk" Umma
tace "Toh ko wajenta ki amsa, kar ma ko da wasa ki wani ce ai Abbanki ya maki aure
ko da xa ku fara magana da shi" Nihad dai tayi shiru bata ce komai ba, har kusan
magrib Umma na parlor da Nihad, Husnah ta kawo taliyar duk suka ci, all this while
kuma khalil na kwance daki ko masallaci bai fita ba, Karfe bakwai su Naf suka dawo
da makulli, Umma tace "Yauwa yan albarka, gasu nan kuwa har uku, toh sannunku,
Allah ya maku albarka" ta mika ma Nihad daya, ta saka daya a jakarta sannan ta basu
su ma daya, tace "Toh kun ga dare yayi ni xan koma gida, ku sai anjima ko? Ko dai a
nan xa ku kwana kawai?"

Nihaad* is 500 via Fcmb Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence via👇🏻


07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

25

Khalil na ganin number dake saman screen dinsa ya kalleta da sauri, bai san lkcn da
ya saketa ba ya shiga call logs dinsa hurriedly to check if tayi sending kiran,
Nihad tayi using opportunity din saketan da yayi ta fice daga dakin a guje ta shige
nata ta kulle, jingina tayi da kofar tana maida numfashi with surprise written all
over her face, why did Aliyu's number appeared on his phone daga fara dialing, how
will that be? lokaci daya tayi assuring kanta cewa ai jiya ne ya kwashe number a
wayarta bayan ya dauke mata wayar, karasawa tayi ta zauna gefen gado da tunani iri
iri a ranta, does it mean bayan ya jefa wayar cikin ruwan cirowa yayi ya busar
kenan ya shiga call logs dinta ya dau number Aliyun? Dama kuma da Aliyu da Umma sai
su Husnah kadai tayi magana da a sabon wayar, numbobinsu kadai ne a wayar, tsaki ta
ja ta mike ta tafi kusa da window ta tsaya, why will she even be stressing her
self, takaicinta guda yanxu da bata tsoma wayar tasa cikin ruwa ta fito da sauri
ba, yunwan da ya addabeta wajen karfe sha biyu ya sa ta bude kofar dakinta a
hankali ta fito parlor, bata gansa a parlon ba ta saci kallon kofar dakinsa sai
kuma ta shige kitchen da sauri, ta bayan windown kitchen din ta hangosa xaune saman
farin kujera yana waya, kasa kunne tayi amma babu abinda take ji saboda window din
kitchen din dake a kulle, idan kuma tace xata bude xata yi drawing attention dinsa,
juyawa tayi ta fice daga kitchen din ta nufi kofar fita parlor, cikin sanda ta isa
har ta wajen da yake ta tsaya inda baxai hangota ba don backing wajen yayi, kawai
tana son tabbatar da cewa da Nihal yake waya kafin ta san irin rashin mutuncin da
xata mata sannan kuma ta hadata da Umma, ji tayi yayi kasa da murya yana cewa "Amma
Baby me yasa kike tunanin ina Nigeria?? Wani yace maki ya gan ni a Naija ne?" Gwalo
ido Nihad tayi ta bude baki tana kallonsa, murmushi taga yayi yace "Ranan da na
dawo ai bayan wajen Mamina wajen ki xan taho har sai kince min in tafi, kinga ko
abinci ma kadan xan ci na Mami.... Naki ne xan ci in koshi" Nihad dai ta kasa rufe
baki sai kallonsa take da mugun mamaki, cikin cool voice dinsa yace "Nasani
Nadeeyah.... In sha Allah ina dawowa babu bata lokaci kuma kamar yanda na maki
alƙawari xa mu yi aure...." Sai a sannan Nihad tayi wani dariya tana tafe hannu
tace "Yau naga ikon Allah, babba da shirga karya" juyawa yayi da sauri yana
kallonta, ta wani hade rai tace "Katon mutumi da kai baka ji kunyar irin wannan
karyar da ka zauna kake laftawa ba? Wato ba a Nigeria kake ba, na shiga uku ku ji
wai baya Nigeria, to a wani kasar kake? ko da yake ita ce babban mahaukaciyar da ta
tsaya take sauraronka har kake fesa mata wannan mugun karya haka..." Tuni khalil ya
katse wayar ya mike yana mata wani kallo yace "Kar ki sake kiranta da mahaukaciya"
A fusace Nihad tace "Ance mata mahaukaciyar me xaka yi? idan waya xaka yi da ita ka
fita titi kayi mana ai dai naga nan gidan Ubana ne ko? Ko Abbana ce maka yayi ka zo
ka dinga masa waya da mata a gidansa?" Khalil yace "Zaki gane ke ce mahaukaciya ba
ita ba" Cike da tsiwa tace "Sai dai ku ne mahaukata ba ni ba wallahi, kuma kar ka
sake kiran wata banzan mace a gidan Abbana" Bai kuma ce mata komai ba ya gyada kai
kawai ya bar wajen, ta bi sa da wani harara, sai kuma ta ja tsaki tace "Wai baya
Nigeria, kai har kana da kudin fita nan nan Niger ma balle wata kasar?? Ai har ka
mutu ko kamshin airport baxa ka ta6a ji ba don ma kaji in gaya maka" Shi dai tuni
ya bar wajen don Nadeeyah na ta kiransa a waya, Bin bayansa Nihad tayi tace "Dama
idan waya xaka yi ka fita can titi kaje kayi ba dai a gidan Abbana ba na gaya maka"
kafin ma ta shigo parlorn har ya shiga dakinsa ya kulle da makulli, ta ja tsaki
tace "Aikin banza" kitchen ta tafi ta dafa indomie, tana kitchen din taji ana
kwankwasa gate, ta ɗan leka parlor sai gashi ya fito daga dakinsa ya fita compound,
kashe gas din tayi da sauri ta fito daga kitchen din ta shige dakinsa, gun wayarsa
dake saman gado ta nufa, sbda tsoro har wani rawa hannnunta yake ta dau wayar ta
shiga call log don taga da warce yake waya har yake karyan ba a Nigeria yake ba,
Nadeeyah ta gani, mamaki ne ya cika ta don ai tayi blocking number jiya, ai ko yau
sai ta tona masa asiri ba dai baya Nigeria ba, xai ga aiki da cikawa yanxun nan,
dialing number tayi har ya gama ring ba a daga ba, ta sake kira nan ma yana ta
ringing no response... Khalil na isa gate din ya bude, Husnah ce tsaye bakin gate
din tana sanye da Hijab har kasa, ta ɗan yi murmushi tana kallonsa tace "Ina yini?"
Babu yabo babu fallasa yace "Daga ina kuma wa kike nema?" Tana Murmushi still tace
"Ba lallai dama ka nuna ka gane ni ba duk da nasan ka gane ni, dama ba wani abu ya
kawo ni nan ba illa in baka hakuri akan abinda muka maka shekaranjiya ni da
kawayena, tun ranan wallahi ban samu nutsuwa ba sabda walakanta d'an Adam ba shi
daga cikin halina, ba tarbiyar gidanmu bane, ni ban ta6a ba sai ranan, kuma mun yi
hakan ne kawai don mu faranta ma kawar mu kamar yanda ta bukaci mu yi, daga baya na
gane bamu kyauta ba biye mata da muka yi muka ci maka mutunci.... Nayi magana da
sauran kawayena mu zo mu baka hakuri ko ba tare da sanin Nihad din ba amma sun nuna
baxa su iya xuwa ba shine ni na taso da kaina in zo har nan in baka hakuri, don
girman Allah kayi hakuri ka yafe mana gaba daya, ko a jiya ma da ta fito xuwa
makaranta idan ka lura ai da wuri ta dawo, to mu muka sa ta gaba muna nuna mata
illan kin yi ma miji biyayya ko da kuwa baka son shi, dalilin barin ta makaranta
kenan da wuri ta dawo gida, yanxu haka bata san xan xo nan ba, kawai kaina tsaye na
taho...." Khalil yace "A takaice dai me ya kawo ki nan Malama?" Ta sauke idonta a
hankali tace "In baka hakurin abinda muka yi maka ni da kawayena, kuma mu nemi
gafararka" Yace "Toh rike hakurin ki, su ma ki mayar masu da nasu, don ba ku kai ku
min abinda xai bata min rai har ki xo bani hakuri ba" Ta daga kai ta kallesa tace
"Baka dai hakuran ba kenan?" Da wani expression yace "Shine nace kun min wani abu
ne da ya bata min rai har xa ki zo bani hakuri tukunna?" Ta langwabar da kai tace
"By the way, sunana Asma'u, amma kawayena na kirana da Husnah...." Ko rufe baki
bata yi ba ya kulle gate din almost on her face ya juya ya koma cikin gida. Yana
shiga daki ya dau wayarsa dake ring ganin Nadeeyah ce ke kiransa ya daga ya kai
kunne, daga daya bangaren tace "I saw ur calls" Ya d'an yi shiru, da mamaki yace
"My calls?" Tace "Yea, minutes ago" Yace "Ohh, sorry mistake ne" Tace "Ohk, sai
anjima kenan?" Yace "Sure" Katse wayar tayi, ya hau duba call logs dinsa da sauri,
Nadeeyah kawai ya ga ta kira, ya kalli kofar dakin ko kiftawa baya yi. Da yamma
Khalil ya shirya xai tafi can gida saboda kiransa da Abba yayi, Nihad dai na daki
abun duniya duk ya bi ya isheta, da ta gaji da wannan bangaren gadon ta koma daya
bangaren, ko kuma ta sauka kasa ta zauna, ita bata saba xama waje daya kamar
jaririya ba, all through the week ko bata da lectures sai ta shiga school, daga
school kuma su tafi yawonsu da su Husnah, tun goma na safe idan ta fita gida dama
sai magariba take dawowa, sai gashi yanxu wai ita ce daga daki sai bandaki, sannan
babu waya ba komai, ita da 24/7 wayarta na hannunta, tunanin hakan yasa ta rushe da
kuka tana jin kamar ta samu wanda xai harbe mata khalil ta huta, gaba daya ta rasa
me ke mata dadi a duniyar, why is this happening to her, kuka ta dinga rerawa tana
bubbuga kafa. Khalil na isa gida a waje yayi parking Aminu na hangosa ya taso da
sauri yana daddaga hannu sama yana washe hakora yace "Sai kayi oga...." Khalil ya
kashe motar ya sauko, Aminu ya kyalkyale da dariya yace "Shekaranjiya Saminu ya
jiyo mana wannan lamari me ban mamaki daga bakin Hafsah me aiki, yanzu haka aka yi
dama?" Khalil yace "Wani lamari kenan?" Aminu ya washe baki yace "Ahh haba ni ne fa
Aminu, meye kuma xaka boye min banda abun ka" murmushi khalil yayi yace "Ba abinda
xa a boye maka" Aminu ya ja sa har xuwa kan bencinsa yace "Shi kansa bencin nan
yasan ba ka a gidan nan mutumina" Khalil ya shafa kai yace "Toh ya ake ciki?" Aminu
yace "Ana nan dai yanda ka tafi ka bari in gaya maka, har yanzu kasan Alhaji bai
fara fita aiki ba, yanxu haka yana da baki yan zuwa jaje a parlonsa, Ita kuwa uwar
Nihad din na can kwance ba lafiya har da karin ruwa don har gida likitan ke xuwa
dubata, kanwarta me shegen kama da ita din nan ce ke wajenta yanxu haka, Umma kuma
jiya da sassafe ta fita a mota bata dubi halin da abokiyar xamanta ke ciki ba sai
ga ta ta dawo mota duk ya lotse wai tayi dan karamin hatsari a hanya amma babu
abinda ya sameta, ko kwarzane bata yi ba, xancen da nake maka har yanxu Alhaji bai
sani ba, ko mu tace kar mu yi magana, baka ga inda taje tayi parking motar ba don
kar ya gani" Khalil dai bai ce komai ba, amma Mumy da aka ce bata da lafiya ce ta
tsaya masa a rai, Aminu ya tuntsire da dariya yace "Yanxu don Allah yaya zaman naku
da yarinyar nan, ni fa na dauka xa ace ta kashe kanta da taga Alhaji ya aura maka
ita, kiyayya ce fa ta gaske take maka" Khalil yace "Ni ban kashe kaina ba sai ita
xata kashe kanta?" Dariya sosai Aminu yake yace "Gaskiya kam kai aka cuta, anyi
mugun kwararka mutumina, yanxu fa har yara da jikoki sai sun ga wannan videon nata
da yayi yawo a yanar gizo, tabo ne da baxai ta6a goguwa ba har karshen rayuwarta,
kai don ma dai iyayenka ba yan boko bane basa hawa yanar gizo, ai da wallahi baxa
su amince ka auri yarinyar nan ba, ko kai baka kare ma videon kallo bane? Saminu fa
har jawo mana shi yayi kusa kusa yanda xa mu gani da kyau, ita wannan ba ma wani
amfani ta sake yawo da kaya a jikinta bayan duk duniya sun san surarta" Lkci daya
mood din khalil ya sauya, Aminu ya girgiza kai yace "Tirr, amma a gaskiya hada
zuri'a da wannan yarinyar ma bala'i ne, banda kana jin nauyin ubanta me xai kai ka?
Kai da kake da mutunci haka, Sauran titi ce fa, duk ta yasar da darajan nata ta
rarrabar a titi, nan nan nan ranan ni da kai muka ganta da asuba ta dawo daga sheka
ayarta tana
ta rabe rabe bakin gate, kuma ta sha yin hakan tun ma baka xo gidan nan ba ya fi a
kirga, labarinta ma ai sai a bakin Habibu, nasan bai san da wannan hadin ba da ya
zuga ka yace kar ka yarda komin me ubanta xai ce maka, shi ma dai Alhajin ya so
kansa da yawa, bai kuma yi maka adalci ba, ya rasa warce xai aura mata sai Nihad
bayan ga salihar er uwarta Nihal, lalatacciya ce fa babu wanda bai sani ba, ni
wallahi da kudi ma baxan amince in aureta ba balle kyauta...." Mikewa Khalil yyi ya
nufi cikin gidan, Aminu yace "Auu har mun gama hirar? Ko xaka shiga ka fito?"
Khalil na isa balcony ya kira Abba ya sanar masa yana gidan, Abba yace ya basa few
minutes yana da baki, Khalil ya amsa masa da to sannan ya xauna saman kujeran dake
wajen, har wani sarawa yaji kansa ke yi da maganganun Aminu, yana ta xaune balcony
din sai ga Aunty Jamila ta fito xata kwaso kayan shanya da tayi a baya, mikewa yayi
, ganinsa tace "Aa kai ne a nan..." Gaisheta yayi, ta amsa tace "Ya gida?" Yace
"Alhamdulillah" Tace "Toh ka shiga ciki mana" kawai murmushi yayi bai ce komai ba,
tace "Ka karasa Sudais ya kai ka ka duba Mumy kasan bata ji dadi ba" yace
"Subhanallah, amma da sauki ko?" Tace "Alhmdlh" yace "Toh Allah ya bata lafiya"
Tace "Ameen" tana barin wajen ya shiga parlon kansa a kasa, Sudais na ganinsa ya
taho da gudu ya rungumesa yace "Uncle mun daina ganinka" Ya shafa kansa yace "Gani
na zo ai, ina fadil?" Yace "Yana wajen Mumynmu bata da lafiya" Khalil yace "Toh kai
ni in gaisheta" Har part din Mumy Sudais ya kai sa, yayi sallama bakin kofar
parlon, Wata frnd din Mumy ta amsa, shiga parlon yayi kansa a kasa ya nemi saman
carpet ya xauna ya gaishesu, duk suka amsa, Mumy dake xaune parlon an cire mata
last drip dai kallonsa kawai take, Bayan few seconds ya daga kai ya kalleta yace
"Ya jikin Mumy?" Cikin sanyin murya tace "Alhamdulillah Ibrahim, ya gida?" Ya sauke
kansa yace "Lafiya lau, Allah Ubangiji ya kara Lafiya" Tace "Ameen Nagode" Bai kuma
cewa komai ba, Hajiya Zara ta mike ta fita daga parlon, bayan few minutes Mumy tace
"Kayi hakuri Ibrahim, an cuceka an hadaka aure da warce bata cacanceka ba, nasan
baka da yanda xaka yi ne kuma baxa ka iya k'in amsan tayinta da mahaifinta yayi
maka ba...." Da sauri yace "Aa Mumy, Allah ne ya tsara haka, kuma muna fatan Allahn
yasa hakan shine mafi alkhairi" Hawaye na sauka idon Mumy tace "Ni kam bani da
abinda xan ce maka sai dai in baka hakuri akan abinda Alhaji ya maka, sannan ni
baxan ce kayi hakuri da Nihad ba, idan kaga baxa ka iya ba ko xaka cutu ina me goya
maka bayan ka saketa kawai ta dawo gida...." Cike da karfin hali Khalil yace "In
sha Allah baxa ayi haka ba Mumy" Mumy ta share idonta bata kuma cewa komai ba, Wani
duniyar tunani khalil ya fada gaba daya jikinsa yayi sanyi, he couldn't even think
straight, kiran sallahn magrib da ake ne yasa ya dago kai ya kalli Mumy ya ga
kallonsa take, a hankali yace "Xan je masallaci Mumy, Allah ya kara lafiya" Tace
"Ameen Ibrahim nagode" Tashi yayi a hankali ya fita daga parlon, Umma ya tarar a
main parlor ta masa wani kallo sai kuma ta ja tsaki tayi hanyar kitchen, ya bi ta
da ido kawai. Bayan an idar da sallan magrib tare suka shigo gidan da Abba har xuwa
parlonsa, Khalil ya xauna ya gaida Abba da ladabi, Abba ya amsa yace "Ya gidan?"
Yace "Alhamdulillah" Abba yace "Ya kamata xuwa gobe ku shirya ka tafi da ita can
garinku ta gaida iyayenka, bayan kwana biyu sai ku dawo" Khalil ya ɗan yi jim, sai
kuma ya dago ya kalli Abba yace "Toh in sha Allah Alhaji, Allah ya kai mu goben"
Abba yace "Ameen, farooq ya zo min da wani batu jiya amma sai kun dawo dai" Khalil
yace "Toh Alhaji, nagode" Abba ya ciro dubu dari ya mika masa yace "Ka yi full
tank, sannan kayi ma iyayenka tsaraba da sauran" Khalil ya sa hannu biyu ya amsa
yace "Toh Allah ya saka da alkhairi Alhaji" Abba yace "Ameen, Allah ya maka
albarka" Khalil ya amsa da "Ameen" a tare suka fito main parlor da Abba, Umma ta
fito daga kitchen kenan ganinsa da Abba tace "Aa Ibrahim har xa ka tafi, bari to ga
abinci ka kai ma Nihad tunda an gama" Ya kalleta yace "Toh" Komawa kitchen tayi da
sauri, Abba dai ya zauna parlon har sannan kana ganinsa xaka san yana cikin damuwa,
dake xuciyarsa kawai yake yana ma Nihad wasu abubuwan as form of punishment amma
shi yasan sonta a jininsa yake, but he can't help it, tayi disappointing dinsa
sannan ta xubar masa da mutunci a idon duniya, Umma ta cika warmer da abinci,
sannan ga wani warmer din daban na kaza ta fito parlor, sai da ta bubbude warmer
din tana kallon khalil cike da damuwa tace "Don Allah idan ka je ka lallabata ta ci
abincin nan, duk ta rame ta lalace wallahi, Shekaranjiya da naje ma da ya na samu
ta ci abincin, yanxu kam ban san halin da take ciki ba baiwar Allah, wa yasani ma
ko bata cin komai" Shi dai Abba bai ce komai ba, khalil kuwa banda kallonta babu
abinda yake, Abba ya mike yace "Ka jirani Ibrahim" Khalil yace "Toh Abba" Ba a dau
lkci ba sai ga shi ya dawo da dubu talatin ya mika ma Khalil yace "Ka siya mata
carton din maltina da na madaran gwangwani" Ta gefen ido Umma ke ta kallon Abba,
Khalil ya amsa yace "Toh In sha Allah Abba" Abba yace "Sai da safe, Allah ya tsare"
Juyawa Umma tayi ta shige kitchen ta tsaya jikin cabinet kamar me nazari. Khalil na
isa gida sai da yayi isha a masallacin dake layin sannan ya shiga gida da motar
yayi parking, bayan ya kulle gate din ya dawo ya fiddo abincin daga cikin mota ya
kai parlor ya sake fitowa ya kai maltina da madara parlon ya ajiye sannan ya kulle
gidan, xaunawa yayi saman kujera ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, da
yasan haka abubuwa xa su kasance masa da bai yarda ya fara shigowa garin kano ba,
where will he even start this amendment from?? Babu warce ta tsaya masa a rai sai
Mahaifiyarsa, this seriously isn't going to be easy, Mikewa yayi daga karshe ya
nufi dakinsa yana tafiya a hankali, har ya bude kofar sai kuma ya fasa shiga, ya
dawo ya bude dakinta, zaune ya ganta a kasa idonta yayi bulu bulu alamar tayi kukan
gaske yau, ya tabe baki ya kulle kofar ya koma parlor kawai yayi xamansa, tashi
Nihad tayi ta bi bayansa, ta tsaya bayan kujera tana shesshekar kuka..., ya ɗan
daga kai ya kalleta kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Da bashi ne?" Wani bakin
ciki ya rufeta a fusace tace "Ban sani ba, ka zata kai ka isa ka dinga punishing
dina? Waya biyu aka kawo min gidan nan ka salwantar min da su, toh wallahi zaka sha
mamakin abinda xai faru idan baka bani wayata ba" Mikewa yayi ya bar mata parlon ya
shige dakinsa ya kulle, kuka kawai take kamar ranta xai fita, babban tashin
hankalinta shine Aliyu da xai yi ta kiranta ya ji a kashe, yanxu babu ta inda xata
yi ta iya kiransa, da ma baya kulle gate ne ko makota ita sai ta shiga don ta kira
Aliyu, amma ko daxu da xai fita kulleta yayi ta ciki, ko bin ta kan warmers din
abincin dake parlon bata yi ba ta koma daki ta dinga kuka kamar ranta zai fita, har
kusan karfe biyun dare Nihad bata yi bacci ba, abun duniya ya taru yayi mata yawa,
last week fa warhaka tana baccinta peacefully a saman gadonta, tashi tayi a hankali
ta goge idonta ta nufi kofa, a hankali ta bude kofar dakin nata ta fito, taga ya
kashe duk wutan gidan, ko ina yayi duhu, tana lalubawa ta tafi hanyar dakinsa ta
kai hannu handle din kofar ta murda a hankali ta bude ta shiga dakin, nan ma dai ya
kashe fitilar, sai da ta fara tattaba socket din dakin cikin duhun ko xata ga
karamar wayarsa a jiki taga babu, cikin sanda ta nufi gadon dakin ta durkusa, hannu
ta kai xata laluba kan gadon taji hannunta saman broad haired chest dinsa, zaro ido
tayi a mugun tsorace xata mike ta gudu ya fixgota ta fado saman gadon daga gefensa,
yayi kneeling dai dai inda take har tana jiyo respiration dinsa, yana kallonta
cikin duhun kafin yace komai jikinta na rawa tace "Wayyo na shiga uku, wallahi
torchlight nake nema xan je in sha ruwa a kitchen...."

*Littafin Nihad dari biyar ne, ki fita hakkina kafin ki karanta min littafi
hankalinki kwance*

3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence via👇🏻

07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

24

Farooq ya daga kai ya kallesa har sannan kuma wayar na hannunsa yana jujjuyawa,
karasowa parlon Khalil yayi ya ajiye ruwa da glass din hannunsa, ya ki yarda su
hada ido da Farooq yace "Oh kamar fa na makotanmu ne da suka shigo daxu, babu
tantama wayar daya daga cikinsu ne, ban ma kula ba sai yanxu...." Farooq dake ta
kallonsa ko kiftawa babu kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Now tell me who you
are Khalil!!!" Khalil ya ɗan yi jim, can yace "Ban fahimce ka ba" duk wannan abun
ya ki yarda su hada ido da Farooq, mikewa Farooq yayi ya dafa sa yace "Tell me what
ur mission is, what is ur intention of coming to stay with us? ka gaya min kai
wanene, menene manufar xuwanka gidanmu" Sai a sannan khalil ya daga kai ya kallesa
amma bai ce komai ba, Farooq yace "From day one, i know u are not who u claim u
are, u lied about ur personality to us, you have a mission definitely, be it
revenge, spy, Dss.... And what have u!" Khalil ya girgiza kai a hankali yace "I
have no mission Farooq, and my intentions of staying with u people is pure, aiki
kawai ya kai ni gidanku, baya ga shi kuma babu wani abinda ya kai ni gidanku...."
Farooq na kallonsa keenly yace "I will like to know u more" Khalil ya koma ya
zauna, kamar baxai ce komai ba sai kuma ya sauke ajiyar xuciya yace "Duk abinda na
gaya maka a kaina a baya hakan yake, i am a nobody like i said earlier, i was just
opportune to go to school, i was opportune to be a literate, nayi diploma a fce nan
kano wanda har yau ban samu aiki ba, bayan wannan komai game da ni na gaya maka a
baya, u can even call Habib and confirm" Farooq yace "But meyasa kace iyakarka
secondary?" Khalil yace "Ina tsoron kar a ki bani aiki a gidan ne" Farooq dai
kallonsa kawai yake as if forcing himself to believe him, Can yace "Wani course din
kayi?" Ba tare da Khalil ya kallesa ba yace "Business Admin" Farooq ya koma ya
zauna kamar me naxari, ta gefen ido Khalil ke kallonsa hoping he is fully
convinced, Farooq na daga kai Khalil yayi saurin dauke idonsa daga kansa, Farooq ya
sauke wani ajiyar xuciya yace "Ohk then, in sha Allah xa mu yi magana da Abba,
nasan xai yi iya kokarin ganin ya samar maka aiki dai dai da qualifications dinka"
Khalil yace "Toh nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Farooq yace "Ameen" Bayan
few minutes Farooq yace "Ina Nihad din?" A hankali Khalil yace "Ban san inda ta
tafi ba" Da wani expression Farooq yace "Ban gane baka san inda ta tafi ba, isn't
she under ur control now?" Khalil yace "Nayi kokarin hanata fita amma ta ki" Farooq
yace "What? Sai kai kuma ka saka mata ido har ta fita?" Khalil dai yayi shiru.
Nihad ce ta sauka bakin gate ita da Husnah da tayi ma kawayensu karyan xata je park
ta amso sako, nan kuma ta gaya ma Nihad inda xata jira ta su hadu sannan su taho
gidan gaba daya, Sosai gaban Nihad ya fadi ganin motar ya Farooq a waje, Husnah ta
zaro ido tace "Toh yanxu ya xa mu yi kenan?" Nihad ta hade rai tace "Toh ba daga
makaranta nake ba, shiga kawai za mu yi, ai ba yawo na tafi ba" Husnah tace "Aa,
kinsan yayan nan naki ba saiti garesa ba haka kawai inje ya ritsa da ni" Nihad tace
"To me xai min? Kawai mu shiga idan ya so sai ki zaga bayan gidan ki nemi waje ki
zauna, idan ya tafi xan fito in gaya maki sai ki shigo" Husnah tace "Toh gwara haka
dai" A tare suka shiga gidan Nihad ta kulle gate, duk da yanda gabanta ke faduwa
hakan bai hanata dakewa ba ta nufi cikin gidan kamar wata boss, Husnah ma dai duk a
tsorace take, tayi sauri ta zaga bayan gidan ta nemi waje ta zauna, a hankali Nihad
ta murda kofar parlon ta shiga ciki da sallama, ta kara kicin kicin da fuska ta
karasa cikin parlon tana kallon yaya Farooq da ya bi ta da ido, ta ɗan durkusa tace
"Yaya ina yini" Mikewa yayi, yayi ball da ita cikin xafin nama, yace "Daga gidan
uban wa kike?" Ta fashe da kuka ta mike xata gudu ya fincikota, jikinta na rawa
tace "Yaya wallahi makaranta na tafi ba ko ina ba, ka kira makarantar ma ka
tambaya" Duk a gigice take don a wajen duka xa a iya ba Farooq A1, Ya kai mata wani
wawan mari yace "Uban wa ya baki izinin tafiya makaranta?" Ta rushe da kuka jiki na
rawa tace "Wallahi na gaya ma Umma kafin in fita, ita tace in tafi, ka kirata ka
tambayeta" Hauri ya kai mata yace "Ke da Umma ce a gidan nan? Ko Umma ke da iko
dake yanxu?" hankali tashe tace "Don Allah kayi hakuri yaya baxan kara ba wallahi,
kaji har na rantse maka" Shi dai khalil na xaune bai ce komai ba sai kallonsu yake,
Har baya Husnah ke jiyo muryar Nihad tana ihun neman agaji, ba shiri ta mike ta
nufi gate da gudu tun kan Nihad tace tare su ke, da hannu farooq ya dinga makan
Nihad, mari kuwa yayi mata har sau uku, kuka take iya karfinta tana basa hakuri
tana cewa baxata kara fita ba, daga karshe yayi ball da ita ta mike tsaye da gudu
ta shige dakinta ta sa makulli tana rusa kuka, Farooq yace "Gobe ko nan da gate ki
fita in samu labari ki ga yanda xan faffasa maki jiki da belt, munafuka kawai" Ko
minti uku bai kara a gidan ba yayi ma Khalil sallama, khalil ya rakasa har mota,
farooq na kallonsa da kyau yace "Kar ka kuskura ka raga mata ko na second daya idan
tace xata dinga kawo maka raini" Khalil ya ɗan yi murmushi kawai, Farooq yayi masa
sallama ya ja motarsa ya bar layin, juyawa khalil yayi ya koma cikin gidan, ya
zauna saman kujera ya dau Iphone dinsa hade da sauke ajiyar zuciya, tashi yayi ya
tafi daki ya ajiye wayar, Nihad na jin ya bude kofar dakinsa ta fito da sauri,
parlor ta tafi ta tabbatar da gaske yaya farooq ya tafi, sai da ta kara duba
takalmansa nan ma taga babu alamar dai ya tafi, share hawayenta tayi ta nufi dakin
nasa ta bude hade da turawa da karfi, tana kallonsa cike da rashin mutunci da tsiwa
tace "Toh da ka kirasa ka gaya masa sai aka yi yaya? Nace sai me da ka kirasa?
Mutuwa ka ga nayi bayan muguntan da yayi min? Kuma ka zata xan fasa fita in tafi
makarantana ne ko in tafi duk inda nake so? To wallahi karya kake yaro don ko gobe
ma ba a haifi wanda xai hanani xuwa makaranta ba kaji in gaya maka, Kuma da kai da
ka kirasa da shi da dokeni Allah ya isa ban yafe maku ba...." Wani tsaki ta ja tana
hararansa cike da tsana, ya girgiza kai yace "Akwai lkcn da matsayin tsayawa bakin
kofar dakina ma baxa ki samu ba balle ki gwada min halinki na rashin tarbiya...
bari kiji ba bakin kofar dakina ba har bangarena ma sai ya haramta gare ki wataran
wallahi...." Sai kuma ya mike ya nufeta, sosai gabanta ke faduwa ganin yanda ya
daure fuska amma ta dake ta tsaya bakin kofar, ya tsaya dab da ita yace "Kinsan me
yasa baxan ke kulaki ba idan kina nuna rashin tarbiyar ki? Saboda ke din ban dauke
ki a bakin komai ba, ban dauke ki mace ba, ba kuma kallon mace nake maki ba, kallon
yar titi kuma er bariki nake maki, na dai girmama mahaifinki na amshi tayinki da
yayi min don shi din mutum ne me daraja da kima a idona, banda haka ko da duk
arxikin duniya aka hadani da ke wallahi wallahi baxan aureki ba don ni ba ajinki
bane ta ko ina na fi karfin ki...." Nihad ta zaro ido hade da bude baki tana
kallonsa, sai kuma ta cakumo kwalarsa cike da tsiwa tace "Ni kake ce ma yar titi
kuma er bariki??" Shaketa yayi ya hadeta da kofa ba shiri ta sakesa gabanta na
mugun faduwa, ya dinga kallonta fiercely yace "ina me baki shawara da kakkausar
murya, Kar ki sake gigin kai hannunki jikina, idan ko kika sake yin wannan kuskuren
to xaki sha mamakin abinda xan maki a gidan nan" Yana gama fadin haka ya turata
waje ya kulle kofarsa, kiris ya rage ta fadi, tana huci bayan tayi regaining
balance dinta tace "Kai din banza zaka bani shawara da kakkausar murya, aa sai dai
karyayyen murya, waye kai kuma me kake takama da shi, kuma wallahi ni ba er titi
bace don ina da gatana kuma da arxikin iyayena, kai kuma fa? Naga sai kayi tuki
kake samun na xubawa a aljihu?" Sai kawai ta fashe da kuka ta shige dakinta ta fada
kan gado tana rera kuka, duk Abba ne ya ja mata yau wai driver din gidansu ke
kiranta yar titi kuma yar bariki, kuka take kamar ranta xai fita, gaba daya ta
mance da wata Husnah, sai da taji ana kiran magrib sannan ta tashi ta goge idonta
ta xauna saman gadon, tana jinsa ya fita masallaci, banda muguwar tsanarsa babu
abinda ya cika xuciyarta, wallahi ta tsanesa, she hate him with passion, tana jin
ya fita masallaci ta mike ta dau mayafinta ta fita xuwa baya wajen Husnah, wayam ta
ga wajen, ta juya ta koma ciki, wayarta ta fiddo can kasan jakarta ta hau dialing
number Umma, Sai da ya kusa katsewa Umma ta daga, bayan sun gaisa ta fashe da kuka
tace "Umma ya farooq ya zo har gida ya zane ni saboda na tafi makaranta wai" Umma
ta bude baki tace "Shi farooq din?" Cikin kuka tace "Ehh Umma" Umma tace "Yi shiru
xan yi maganinsa don ubansa" Nihad na shessheka tace "Toh Umma yace kada in sake
fita makarantar kuma" Umma tace "Ai ba shi ya haifeki ba da xai hanaki xuwa
makaranta, kanki tsaye gobe ma ki shirya kiyi tafiyarki duk inda xa ki ba ma
makaranta kadai ba, ki kyaleni da shi kawai xan yi maganinsa" Nihad tace "Toh" Umma
tace "Kar ki sake asaran hawayenki a banza, kinji abinda nace maki" A hankali Nihad
tace "Na ji" Umma tace "To sai da safe" Daga haka ta katse wayar, mikewa tayi
direct ta tafi dakin farooq, luckily ta samesa xai fita Masallaci, strictly tace
"Farooq daga yau sai yau in har ba baki kake son in maka ba bana son in sake kara
ganin ƙafafuwanka a hanyar gidan Nihad, kuma babu ruwanka da harkarta da abinda
take yi, in dai ba so kake in ce maka je ka ka gani, kai ko a waya na haneka da
kiranta" Da mamaki Farooq ke kallonta, tace "Ni dai na gaya maka, kana kiranta ko
da a waya ne Allah ya isa, balle har ya kai ka taka har gidanta, daga yau bana son
magana ya sake hadaka da ita ko a ina kuwa" Tana gama fadin haka ta juya fuuu ta
fice ya bi ta da kallo, a parlor ta tadda Amina xata fita, tace "Ke kuma ina xa
ki?" Amina tace "Umma kati xan amso" Umma tace "Ban hanaki fesa turare haka ba idan
xa ki fita? Kuma ba nace maki wannan hijabin bana son kina sa shi ba? Meye amfanin
hijabi da xai dinga nuna surarka? Maza koma ki dau wani hijabin"
Amina ta juya tace "Dama kyautar da hijab din xan yi Umma, kawai bana son daukan
gogagge ne shi sa na sa shi yanxu" Umma tace "Maxa ki bayar idan ba haka ba in
kona, bana son sake ganin ɗan iskan hijabin nan a gidan nan" Amina ta juya ta koma
daki, Umma ta wuce ɓangarenta. Karfe tara da wani abu Nihad ta gama shirinta xata
kwanta, har sannan taki daina kukan maganganun da Khalil ya gaya mata, wai er titi,
sannan har da cewa tayinta Abba ya basa, takaici kamar ta hadiye xuciya, can ta
mike ta fita daga dakin nata, a parlor ta gansa xaune yana kallo, tana harararsa
tana huci tace "Ba dole ka sa tv a gaba ba tunda babu a house" Shi dai bai ko
kalleta ba, tace "Kuma da kake cewa Abbana tayina yayi maka, in ka cika ɗan halas
ka sakeni yanxu yanxu mana..." Sai a sannan ya daga kai ya kalleta, ta maka masa
wani harara tace "Idan kuma baka da takarda da biro ni ina da su" Bayan few seconds
yace "Ohk ashe dai kinsan da aurena a kanki?" Ta wani kyabe baki tace "Oho dai" Ya
gyada kai yace "Kar ki damu akwai lokaci, kawai mu jira lokacin, ina son sai sanda
kika fahimci ni ba sa'an aurenki bane sannan xan sake ki...." Tace "Aikin banza
kenan, yanxu ya kamata ai, don tun yanxu nasan ni ba class dinka bace, kuma baxan
ta6a xama class dinka ba" Khalil bai sake tanka ta ba, ta juya fuuu ta koma ciki,
wayarta ta dauka a karkashin pillow tayi dialing number Aliyu, amma ta kasa samunsa
sbda ba shi da number, Naf ta kira tace "Naf don Allah ki kira Aliyu kiyi mashi
sending wannan number nawa yayi saving i want to talk to him" Naf tace "Ohk" Daga
haka ta katse wayar, bayan wani lkci Naf ta sake kiran Nihad tace "Nihad na tura
masa number taki yace xai kiraki" Nihad tace "Toh nagode sosai" Nihad na kwance
tayi lamo kan pillow tana ta jiran kiran Aliyu, sai ga kiran nasa, farin ciki ne ya
cikata ta mike xaune da sauri ta daga kiran, a hankali tayi masa sallama, ya amsa
yace "How are you?" cikin sanyin murya tace "Alhmdlh" Yace "Are okay?" Lokaci daya
hawaye ya kawo idonta tace "No" Da damuwa yace "Me kuma ya faru?" Tana girgiza kai
hawaye na sauka idonta tace "Baxan iya jure xama waje daya da wannan drivern din
ba, Har xagina sai da yayi daxu fa" Aliyu yace "Ya zage ki?" Cikin kuka tace "Ehh,
wai ni ya ce ma er titi, er tasha, har da cewa Abbana tayina ya basa" Aliyu yace
"Shi Drivern?" Tace "Ehh" kasa cewa komai Aliyu yayi, can yace "Wait u mean driver
ne ya gaya maki wa ennan maganganun?" Nihad tace "Wallahi" Rai bace yace "Har ya
kira ki da er titi?" Cikin rawan murya tace "Haka yace" Aliyu ya fuzar da iska yace
"Kar ki damu, ki kwantar da hankalin ki, xan dawo Nigeria soon, and everything will
soon come to an end in sha Allah" Tana share idonta tace "Nagode" Yace "Kar ki sake
xubar da hawayenki, sai yayi da ya sanin zagin nan da yayi maki wallahi" Nihad tace
"Sannan nace ya sakeni ya ki" Aliyu yace "He just have to, cause u are not meant
for him...." Ɗan murmushin jin dadi tayi, yace "Are u on WhatsApp?" Tace "Aa xan
bude yanxu" Yace "Idan kin bude, ki kirani" Tace "Ohk" Daga haka ya katse wayar,
sosai hankalinta ya kwanta da abubuwan da Aliyu ya gaya mata, bayan ta bude
WhatsApp din Video call suka yi da Aliyu har kusan karfe dayan dare, tun bayan da
Video dinta ya tafi viral sai ranan tayi bacci cikin dadin rai. Cikin dare taji
kamar ana daga pillow din da ta daura kanta, ta bude ido da sauri, bata ga kowa ba
banda duhu dake dakin, gabanta ya dinga faduwa don da gaske taji kamar ana daga
pillow dinta, ta mike xaune tana bin ko ina da kallo duk da duhun dake dakin,
hannunta ta kai xata yi switching wutan dakin taji ta daura a kan hannun mutum,
wani ihu ta fasa a mugun tsorace xata sauko daga kan gadon taga an kunna wutan
dakin haske ya gauraye ko ina, yana jingine jikin bango kusa da bed side drawer,
tsaye tayi bakin kofa tana kallonsa a mugun tsorace kuma da mamaki, ya daga
pillownta ya dau wayar dake ƙarƙashi, xaro ido tayi ta taho da sauri tace "Wallahi
kar ka kuskura ka ta6a min...." Wani mugun kallo yake mata yace "Kar ki matso kusa
da ni" Ta fashe da kuka sosai tace "Wallahi ka bani wayata, kaga ba kai ka siya min
ba, ba kuma da sisin ka aka siya ba" Kofa ya nufa ta koma gefe tana kuka tana
kallonsa har ya fice daga dakin, da sauri ta bi sa dakinsa tana cewa "Wallahi ka
bani wayata" Bude kofar bandaki taga yayi tana kallo ya tara ruwa a bucket sannan
ya cilla wayar a ciki ya fito ya sa ma bandakin makulli, saboda shock kasa ce masa
komai tayi ta tsaya tana kallonsa ko kiftawa babu, bai ko kalleta ba ya kashe wutan
dakin yayi kwanciyarsa saman gado.... Har gari ya waye Nihad bata yi wani bacci ba,
ta ci kuka har ta gode Allah, ta sake tabbatar da cewa bata ta6a tsanar mutum a
duniya irin khalil ba, karfe takwas saura taji kamar ana welding a bakin gate, ta
mike da kyar ta fito parlor ta tafi kofar fita parlorn, tsaye ta gansa a compound,
ga kuma me welder da me canza lock din gate suna ta aiki a bakin gate, juyawa tayi
da sauri hawaye cike idonta ta koma dakinta, ta xauna gefen gado tana shessheka, ta
shi tayi ta tafi dakinsa ta bude kofar bandakin ta duba bucket din da ya jefa
wayarta taga babu wayar a ciki, ta fito ta ga karamar wayarsa a gefen gado, da
sauri ta dauka ta fito ta shige dakinta, Call logs ta shiga taga number anyi Saving
da Nadeeyah with love Emoji, kallon Number ta dinga yi sai kuma tayi scrolling xuwa
kasa taga number Nihal wanda ko jiya ma sun yi waya, shiga tayi taga maganar minti
nawa suka yi taga kusan minti goma, dialing number tayi yana fara ring Nihal ta
daga, Rai bace Nihad tace "Ban san ke munafuka bace kuma algunguma sai yanxu Nihal,
kuma in sha Allahu ke abinda xai sameki sai ya fi wanda ya sameni ki rubuta ki
ajiye, don naga kamar farin ciki kike da condition din da nake ciki, banda kina
farin ciki da abinda ya sameni wayar me xaki dinga yi da enemy din nan nawa? Me
yake gaya maki, me kike gaya masa?" Nihal tace "Haba Nihad, what is this u are
saying? Da kinsan wayar da nakeyi da shi da baki kirani kina gaggaya min wa ennan
maganganun ba, kema kinsan baxan ta6a farin ciki da bakin cikin ki ba..." A fusace
Nihad tace "Babu abinda xa ki gaya min da xai gamshe ni, kuma xan ga ta inda xaki
sake waya da shi" Nihal tace "Toh shikenan, amma ki sani ko na kirasa ke nake cewa
ya ba waya sai baxai baki ba" Nihad tace "Oho wannan ke da shi ya shafa" Nihal tace
"Jibi xa mu yi hutu, and we need to talk idan na dawo Nihad" Nihad bata kuma
sauraronta ba tayi ending call din, Yanxu tasan xamanta da kowa a duniya, Abba ne
oo, Mumy, Ya farooq, Nihal, duk ashe ba sonta suke ba, kuka sosai ta saki, sai kuma
tayi blocking number Nihal a wayar sannan ta bi duk calls din ta goge, Kallon
Number Nadeeyah ta dinga yi ganin how special the line is with multiple 2's, can ta
ja wani tsaki ta danna masa block sannan tayi deleting shi ma gaba daya a call
logs, sai kuma ta tuna cewar she needs to tell Aliyu cewar ya amshe mata waya
incase zai yi ta nemanta, dialing number Aliyu ta fara yi, ko digit hudu bata sa ba
sai taga number ya fito barau barau amma ba tare da suna ba, still tayi tana ta
kallon screen din karamar wayar baki bude da mugun mamaki, to ko dai jiya da ya dau
wayarta ne ya kwashe number??? lkci daya ta juya da sauri jin taku, wani irin
faduwa gabanta yayi ganinsa a bakin kofar dakin yana kallonta, cikin rikicewa ta
ajiye wayar hannunta gefen gadon gabanta na faduwa, shigowa dakin taga zai yi, ta
marairaice ta koma can karshen bangon dakin xuciyarta na bugawa tana kallonsa amma
hakan bai hanata hade rai ba, ya kalli wayarsa sannan ya kalleta, daukar wayar taga
xai yi ta nufi kofa a guje yayi saurin fixgota, kuka ta saki ta rirrike hannunsa
tace "Ni wallahi ka sakeni, me kaga nayi kuma again, ba yar uwata na zo inyi magana
da ba na dade ban ji muryarta ba...."

Nihaad is 500 via 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah


And u show ur evidence via👇🏻

07087865788✍🏻
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD💖💖

27

Kunna wutan dakin Khalil yayi ya koma gefen gadon ya zauna fuskarsa daure yace
"Ohk, dauki torchlight din ki fita" Har sannan gabanta bai daina faduwa ba, a
hankali ta dawo edge din gadon tana satan kallonsa, ba tare da ya kalleta ba yace
"Dauki ki fita nace" Ta sauke ƙafafuwanta kasa a hankali tana kallon karamar
wayarsa da ta hango gefen pillow, Ya jefa mata wani mugun kallo yace "Ko bayan shi
da wani abun da kike so ne?" Ta ɗan turo baki tace "Ga can torchlight din da xan
ara" Ya kalli inda take nuna masa, sai kuma yace "Ohk" dauko wayar tasa yayi ya
mika mata yana kallonta, a hankali ta kai hannu xata amsa, da karfi ya buge mata
hannu da wayar, da sauri ta janye hannunta ta bude baki tana kallonsa tana yarfe
hannun, ya mike ya dau shirt dinsa ya saka sannan ya nufi kofa ya bude mata da
kyau, fuska daure yace "Zo ki fita" Ta fashe da kuka tace "Shine har sai ka kwala
min waya a hannuna? Sai kace kai baka shigo min daki idan ina bacci" Cikin
kakkausar murya yace "Zo ki fita nace" ganin babu alamar wasa tattare da shi ta
mike ta nufi kofar hawaye cike idonta, tana fita ta juyo ta kallesa tace "Ban yafe
buge min hannu da kayi da shegen wayarka ba, don ma ka samu xa a ari torchlight din
shegen wayar" Yi yayi kamar xai bi ta, ta ruga ta shige dakinta ta kulle kofar da
sauri tana maida numfashi. Washegari da yamma bayan Khalil ya gama shiryawa yanda
xai je ya sanar ma Nihad ta shirya xa su yi tafiya ne babban aiki a wajensa, tun
safe ya fice gidan don kawai ya daina ganinta, ko awa daya bai yi da dawowa ba kuma
bai ji motsinta ba bai kuma duba dakin nata ba, daga karshe kawai yayi dialing
number Nihal tana dagawa ta gaishesa ya amsa yace "Ya makaranta?" Tace
"Alhamdulillah" Yace "Kin dawo ne?" Tace "Aa ya farooq yace min yana hanya" Khalil
yace "Toh Allah ya kawo ku lafiya" Tace "Ameen" Shafa kansa yayi yace "Dama so nake
ki sanar ma er uwarki ta shirya kayanta kala uku xa mu je can gida, kawai haka xa
ki ce mata" A hankali Nihal tace "Baxa ka iya gaya mata ba kai kenan?" A takaice
yace "Ehh" Tace "Toh Shkkn, ka bata wayar" yace "Zan kai mata yanzu" Nihal tace
"Ohk" mikewa yayi ya tafi dakin Nihad ya bude kofar dakin, tana tsaye jikin window
abun duniya ya tarar mata, har ta gaji da kuka, tun da garin Allah ya waye ruwa
kawai take ta sha don ta gaji da cin indomie gashi babu kayan miya a gidan, yunwa
take ji sosai, jin ya bude mata kofa ta juya a fusace tace "Malam ka daina shigo
min daki kanka tsaye kamar wata matarka, idan ma wani abun ne baxa ka kwankwasa ka
jira in fito ba?? Balle ma ni bana son kana min magana a gidan nan har abada"
Kallonta kawai yake, ta murguda baki ta ci gaba da kallon tsuntsayen da take kallo
ta window, khalil ya sa handsfree a wayar hannunsa yana daga inda yake tsaye yace
"Gashi ki gaya mata" Nihal tace "Hello Nihad" Nihad ta wani tamke fuska tace
"Menene??" Nihal tace "Abba yace ki shirya kayanki xa ku je can gidan" Nihad ta
buda ido sosai tace "Don Allah da gaske?" Nihal tace "Ehh" Wani farin ciki ne ya
rufeta, cike da murna tace "Ai kayana a hade suke ban ciro su a akwatin ba" Khalil
bai bari Nihal tace komai ba ya katse wayar ya juya ya fita, kan kace me Nihad ta
gama rurrufe akwatunanta ta ja su ta kai parlor gaba daya, ji take kamar mafarki
wai xata koma gida, she sooo happy, da ido Khalil ya dinga bin ta, haka ta ja
akwatunan duk da nauyinsu har gun mota sannan ta koma ta dauko handbag dinta, xata
fita khalil dake ta bin ta da kallo yace "Duk wa enan kayan ina xa ki kai su?" Tayi
masa wani shegen kallo tace "Ohk da so kayi in bar maka wasu ka dauka kaje ka siyar
ka samu na xubawa a aljihu? To baxa a bari ba" tana gama fadin haka ta fice ta tafi
jikin mota tana jiransa, bayan few minutes sai ga shi ya fito, cike da gadara tace
"Bude min booth Malam" Ba musu ya bude mata booth din, ta daddage ta shigar da
akwatunanta booth da duk karfin da Allah ya bata, back seat ta bude ta shiga ta
zauna farin ciki fal ranta, ta lumshe ido tare da sauke wani ajiyar xuciya, at
last.... Ganin ya ki tada motar ta ki ce masa komai, don ita kam baxata biyesa ba
tunda dai ta samu xata koma gida, bayan few minutes ya sauka motar yaje ya bude
gate, lumshe ido Nihad tayi bayan ya ja motar sun bar compound din, ya sauka ya
kulle gidan sannan ya dawo cikin motar, Ta madubi yake ta kallonta kai kana ganinta
kasan she is over happy, tun Nihad na tunanin traffic yake kaucewa ganin hanyar da
suke ta bi har dai taga sun dau hanyar da baxae ta6a kai ka gidansu ba, ta dake
tace "Malam mance hanyar gidan namu kayi ne ko kuma Shaye shaye ka fara? Ba ga can
hanyar da xaka bi ba" Banza yayi mata, a mugun fusace tace "Tunda kai ba kurma bane
nasan kana ji na, ka gaya min ta ina hanyar nan da muke bi xai kai mu gida??" Nan
ma yaki tanka ta, mamaki ne ya cika Nihad ta dinga bin hanyar da kallo, to ina xai
kai ta, bata kuma ce masa komai ba tana ta kallon ikon Allah, bayan tafiyar kusan
minti arba'in taga sun shigo wani karamin gari da xa a iya kiransa da kauye, she
was more than shock, wanda hakan yasa ta kasa ce masa komai, sae kallonsa take baki
bude, a wani gida da aka xagaye da katangar kasa yayi parking bayan sun lula can
cikin garin, ya kashe motar, sannan ya bude ya sauka, duk motar tayi butu butu da
jan kasa, ga yara da ke ta bin motar tun shigowarsu karamin garin, har Khalil yayi
parking, yaran duk suka kewaye motar suna murnan ganin mota, Haka Nihad ta dinga
kallon inda suke with shock, khalil ya bude side dinta yana mata kallon cikin ido
yace "Sauko" Ta fashe da wani matsanancin kuka tace "In sauko in yi me?? Wallahi
baxan sauko ba" Duk da dariyar da ta basa haka ya dake ya hade rai yace "Baxa ki
sauko ba??" Cikin kuka tace "Ehh, ina ne nan din da ka kawo ni da kake cewa in
sauko?" A takaice yace "Garin mu!!! don ki tabbatar mu ma muna da gida, dolenki
kuma ki sauko ki gaida iyayena, sannan adadin kayan da kika kwaso adadin kwanakin
da xa mu yi a garin nan kenan" Ta fashe da kuka hankali tashe tace "Na shiga uku na
lalace...." Ko sauraronta bai kuma yi ba ya xaga bayan booth ya hau sauke
akwatunanta, ta gwale ido ganin yayi hanyar shiga cikin gidan da shi, kuka take
kamar ranta xai fita tana cewa ta shiga uku ta lalace, tun da aka haifeta ita kam
sai dai taga irin wajajen nan a Tv, dama da gaske akwai irin garin nan a reality??
Ba a dau lokaci ba sai gashi ya fito da wata dattijuwa tana washe baki ta taho ba
ko takalmi a kafarta tana cewa "Lale lale" Sake baki Nihad tayi tana kallonta a
tsorace, matar ta karaso kusa da mota tace "Sannu da xuwa, lale lale" Nihad ta
hadiye wani abu da kyar tace "Ina yini?" Khalil dake tsaye gefen matan yace "Sauko"
Da kyar tayi karfin halin saukowa daga motar, kana ganinta kasan a tsorace take,
matar tace "Bismillah mu shiga ciki, lale" Tana jan kafa ta bi matar xuwa cikin
gidan, Khalil ya bi ta da kallo yana wani side smile, sai da Nihad ta duka kafin ta
iya shiga cikin gidan, nan taga hut a jere kusan hudu a karamin tsakar gidan, lkci
daya tsikar jikinta ya dinga tashi taji ta fara jin sanyi kamar xaxxabi xae rufeta,
Matar ta shiga wani hut din tace "Bismillah shigo ciki...." Nan ma sai da Nihad ta
duka sosai kafin ta iya shiga hut din, banda karnin nono babu abinda hut din yake,
sae da ta kara gwalo ido don ta tabbatar kasa ne kwance a dakin kamar waje, sai
gadon kara an shimfida wani yamutsatsen zanin gado a kai, daga can gefe kuma kwarya
ne sun kusa goma an jera, Matar ta dinga nuna ma Nihad gefen gadon karan wai ta
xauna, cike da karfin hali Nihad ta xauna tana kokarin ganin bata fashe da kukan
dake cin ta ba, dattijuwar ta fita daga dakin tana cewa "Bari a kawo maki ruwa"
Wani hawaye ya xubo idon Nihad a hankali tace "Na shiga uku na lalace" da sauri ta
goge idonta ganin wasu mata sanye da kaya irin na fulani sun tsaya bakin kofa suna
gaisheta da fara'a, Da kyar tayi karfin halin gyada tana kirkiran murmushi tace
"Nagode" Ai kuwa da wannan set din matan sun tafi sai wasu set din sun taho duk ana
zuwa yi mata lale, sai ga dattijuwar da kwanon sha dauke da ruwa ta ajiye ma Nihad
a kasa, Nihad ta dinga kallon ruwan ganin particles na ta swimming a ruwan, tun da
aka haifeta bata ta6a ganin irin kwanon shan da aka xubo mata ruwan ba a ciki gashi
duk yayi tsatsa, wata mata ce ta shigo rike da kwarya da nono a ciki, ta ajiye mata
da wani karamin kwaryar me dauke da fura, tace "Sai ki dama hurar iya yanda kike
so, idan kuma kina son suga sai a amso maki" Nihad dai ba bakin magana sai gyada
kai, suka fita suka barta ita kadai da kudaje dake ta zaryarsu a dakin, a hankali
ta fashe da kuka tana bin bukkar da kallo, who have she offend to deserve this in
her life? Why is all this happening to her?? Khalil ya shigo ciki yana kallonta
kasa kasa, cikin kuka tace "Don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ka maida
ni gida, wallahi baxan sake maka duk abinda nake yi ba...." Ko rufe baki bata yi ba
sai ga akwatunanta ana shigo mata da su dakin, da sauri ta share idonta tana bin
yaran da suka shigo da akwatunan da kallo kamar idanuwanta xa su fito, Khalil ya
jira har suka gama shigowa da su yace "Yauwa sannunku" Tana kallonsa ya tafi ya hau
jera mata akwatunan step by step, ta rushe da matsanancin kuka tace "Na shiga uku
na lalace, me nayi maka kake min haka don Allah???" Ko tanka ta bai yi ba, ya dawo
yana kallon fura da nonon yace "Ba lallai kin iya damawa ba, bari a dama maki" wata
karamar tabarma da ya gani a dakin ya shimfida kasa sannan ya xauna ya tankwashe
fararen kafarsa ya hau dama mata furan hade da nono a kwarya, kallonsa kawai take
hawaye na sauka idonta tace "Don girman Allah kayi hakuri ka maida ni gida" Ba tare
da ya kalleta ba yace "Sai kin gama sanye duk kayan dake akwatinki... Sannan nan
din gidanmu ne, gidan iyayena ne dolenki ki xauna, adadin kayan akwatunanki adadin
kwanakin da xa mu yi....." Hade kanta tayi da gadon karan da take zaune kai tana
shessheka a hankali. Bayan ya gama dama furar ya dauka yana kallonta ya mika mata
yace "Gashi" Dago kanta tayi tana kallonsa
cikin rawan murya tace "Wallahi baxan iya xama a nan ba kaji na rantse maka" Yace
"Xa ki iya idan kika kwana biyu, har ma xaki saba da kowa na garin" Ta fashe da
sabon kuka tace "Na shiga uku wayyo Abbana" mikewa yayi ya ajiye mata furan a
gefenta sannan ya fita daga bukkar, Nihad ta ci kukanta ta gode Allah, da ta ji
alamar xa a shigo sae tayi maza ta goge idonta tayi feigning smile kamar ba komai,
ga mutanen are so hospitable, sun ma rasa inda xa su sa ta, they are trying all
they can to make her comfortable, hankalinta bai kara tashi ba sai da taga yamma
yayi likis alamar dabb ake da magariba, gashi har sannan bata sake ganin Khalil ya
shigo ba, Dattijuwar ta shigo tace "Fito kiyi alwala kin ji" Da kyar ta mike ta
fito daga bukkar ta tafi inda aka nuna mata buta kusa da tulunaye uku, tana xuwa
wajen Dattijuwar ta bi ta tace "Ko xa ki kama ruwa?" Ta girgixa kai da sauri, haka
dai tayi alwala ta dawo bukkar matar ta nuna mata inda xata kalla tayi sallah,
Nihad na ta xaune saman abinda tayi sallah, ita kam yau xata ga yanda ake kwana a
wannan hut din, Wata budurwa ta shigo ta kunna mata wani fitila wanda da shi gwara
babu, yarinyar na fita Nihad ta fara sabon kuka, wata mata ce ta shigo mata da
tuwon dawa da wata shegiyar miyar kuka wanda warinsa kadai ma ya isa yasa mutum
yayi throw up, Nihad ta jinginar da kanta jikin gadon karan wasu hawayen na taruwa
idonta, ita kam yau taga ta kanta, miyar kuka da ake yi me dadi da yaji naman kaza
ma ba ci take a gida ba balle wannan me offensive smell, ga wani mugun yunwa da
take ji, ko furan bata sha ba balle tuwon dawa, khalil kam babu shi babu alamarsa,
har kusan Isha'i bata gansa ba wanda wannan ne ya kara daga mata hankali, ko ba
komai ta ma dinga ganinsa kawai kilan hankalinta xai kwanta, hakurinta na rashin
ganinsa ya kare, tana ganin giftawar tsohuwar ta mike da sauri ta tsaya bakin
bukkar cikin sanyin murya tace "Mama ya fita ne? Naga bai dawo ba" Ko rufe baki
Nihad bata yi ba sai gashi ya shigo gidan, dattijuwar tace "Toh gashi ma ya dawo"
Khalil yace "Sannu Gwaggwo" Gwaggo tace "Yanxu matarka ke Tambayarka" Ya ɗan kalli
cikin dakin, Nihad ta hade rai ta koma ta zauna, ya karasa ya shiga ciki ya fito da
karamar wayarsa ya haska tuwon dake gabanta yace "Har kin ci tuwon" Cikin rawan
murya tace "Ta yaya xan iya cin wannan abun fisabilillah?" Yace "Ta yanda kike cin
abinci a gidanku mana, kawai wanke hannu xa ki yi ki fara kai loma" Ta fashe da
kuka tace "Wallahi baxan ta6a iya cin wannan abun ba" yace "Ohk, ashe ba yunwa kike
ji ba" Ya haska furan nan ma yaga bata sha ba, gyada kai yayi ya juya xai fita, da
sauri tace "Don girman Allah ka daina barina ni kadai" Hankalinta a tashe tayi
maganar, yace "Me xan maki in na zauna? Yau kuma nine baki son in bar ki ke kadai?"
Shiru tayi ta sunkuyar da kanta, ficewarsa yayi daga dakin ta bi sa da kallo
hawaye cike idonta, har kusan karfe goma Nihad na xaune inda take sauro duk ya gama
yagalgala ta, wata mata ta shigo bukkar da gidan sauro da wani yakunannen zanin
gado tace "Can cikin dare xa ku ji sanyi sosai, sai ki rufa da wannan, bari a daura
maki gidan sauro don akwai sauro" a hankali Nihad tace "Toh" can gefe matar ta
matsar da tuwo da miya da kwaryan fura dake a kulle, ta gama daura net din a saman
gadon karan ta fita, Har Nihad ta fara bacci a zaunen da take ba tare da ta damu da
sauro ba Khalil ya shigo bukkar, kulle karamin kofar bukkar da yayi ne ya farkar da
ita, ya haska ta da torchlight sannan ya haska saman gadon karan yace "Baxa ki
shiga ki kwanta ba malama" Cikin rawan murya tace "Wallahi yunwa nake ji" Ya karasa
ya dauko kwaryan fura da nonon da ya dama daxu ya ajiye mata, bata da wani option
don mugun yunwa take ji, haka ta dau ludayin tana deban furan a hankali tana kaiwa
baki, da kyar take hadiyewa saboda kyankyami, tana yin ludayi uku ta matsar daga
gabanta ta rufe tana yamutse fuska, shi dai kallonta kawai yake, yace "Shiga net
Hajiya" Ta daga kai ta kallesa ta marairaice tace "Kai a ina xaka kwanta?" Ya hade
rai yace "Ina ruwanki?" Bata kuma cewa komai ba ta mike ta shiga net din, abinda
bata ta6a shiga ba tunda aka haifeta, ji tayi kamar a saman siminti ta kwanta, ta
kai hannu ta tattaba wajen, danne dariyarsa kawai yake, can dai ta hakura ta koma
ta kwanta a hankali amma sai taji kamar she is going to suffocate inside the
mosquito net, xaunawa yayi saman tabarma yana jin babban wayarsa dake aljihunsa na
vibrate amma bai ciro ba, wajajen karfe sha biyu ya mike yana haska fuskarta yaga
tayi baccin wahala, ya fi minti biyu tsaye kamar me contemplating, can kawai ya
dage net din ya shiga ya kwanta ya juya mata baya sannan ya sake net din. Yana jin
ta wajajen karfe daya da rabi tana juye juye, don bai yi bacci ba, can ta mike
xaune tana lalubasa, hade rai yayi sae dai bai ce mata komai ba, bayan ta tabbatar
shi din ne, ta hau tashinsa tace "Don Allah ni ban san inda xan je in yi fitsari
ba" A takaice yace "Sai ki fita ki duba ai" Ya dage net din ya sauka don ya bata
waje ta fita, ta sauko kasa tana kallonsa cikin duhun tace "Wayyo wallahi ya
matseni" Ya kunna fitilar karamar wayarsa ya mike ya bude kofar bukkar ya fita ta
bi bayansa da sauri ta dau butar da tagani tsakar gida, yana nuna mata bandakin
dake xagaye da kara ta gwalo ido tana lekan ciki tace "A nan din xan yi fitsari?"
Banxa yayi mata ya koma gefe ya tsaya, babu yanda ta iya haka ta shige ciki tana
toshe hanci, tana fitowa ya koma bukka ta bi bayansa da sauri, ta xauna kasan
tabarman dakin hawaye har ya cika idonta tace "Wallahi yunwa nake ji baxan iya
bacci hka ba" ledan da ya shigo da shi daxu ya dauka ya ciro bread ya mika mata, ta
dinga kallon bread din sai kuma ta amsa ta bude ta jinginar da kanta jikin gadon
karan ta fara cin bread din a hankali, bata wani ci da yawa ba haka ta dau ruwan da
take kyankyami ta sha kadan, shi dai yana zaune bai ko kallon direction dinta, a
sanyaye ta mike ta shiga cikin net din ta koma can karshe ta kwanta, bayan wasu
mintuna da shigarta shi ma ya shiga ya saki net din, nan da nan bacci ya kara
dauketa, sae kusan karfe biyu da rabi yayi bacci shi ma, kusa da asuba garin yayi
sanyi sosai, kamshin da ya ishesa ya sa ya bude ido a hankali, dab da shi ya ganta
ta takure waje daya alamar tana jin sanyi, ya kalli gashinta wanda shi ne ya damesa
da kamshi, hade rai yayi a hankali ya juya mata baya, ganin tana matsowa ya ɗan
juya ya kalleta, bayan few minutes ya daga net din a hankali fuska daure ya sauka
kasa, zanin gadon da mata ta kawo mata ya shimfida saman tabarma ya kwanta, bai
sake komawa bacci ba har asuba tayi. Zaro ido Nihad da ta farka da safe tayi ganin
gari yayi shar, ta kalli gefenta taga baya nan, da sauri ta sauka ta fita tsakar
gida, bayan ta dauro alwala ta shigo bukkar ta dau hijab dinta tayi sallah, bayan
ta idar ta mike ta koma gefen gadon karan ta zauna abun duniya duk ya dameta, ta
kalli uban kayanta bayan ta tuna abinda ya ce mata wai sai ta gama sa su sannan xa
su bar kauyen nan, da daddaya da daddaya aka dinga shigowa gaisheta, mata ta farko
da ta fara shigowa gaisheta haka ta bude akwati ta bata atamfa riga da skirt, a
haka ta dinga rarrabar da kayan nata, ai ko har da makota a shigowa gaisheta, har
kayan kwalliya da shafe shafenta bata bari ba, daga karshe ta ba dattijuwar akwati
daya, mata biyun dake gidan su ma duk ta basu kyautar akwatuna daddaya, da atamfa
kala daya da Hijab ta tsira sai turare shi ma daya da handbag dinta da takalmi
sauran duk ta yi sadakansu, ai ko ta sha godiya sannan albarka ta sha shi kwando
kwando, wani kunu me ruwa ruwa aka dire mata as breakfast da dumamen tuwon da bata
ci jiya ba, Nihad tayi tagumi tana kokarin ganin bata bar hawayen idonta ya xubo
ba, wajen karfe takwas aka kai mata ruwa tayi wanka bayan ta dawo bukkar ta shirya
sai ga khalil ya shigo gidan tun daga bakin kofa Dattijuwar ke basa labarin
alkhairin da Nihad tayi masu da makota, har da fito da akwatin da Nihad ta bata ta
nuna masa, yana shiga bukkar da Nihad take yaga babu kaya ko daya ya kalleta, ita
dai kanta na kasa, can yace "Ina kayanki suke?" A takaice tace "Na rabar, ko kai
baka ga kayan da suke sa wa bane" Yace "Ohk, ashe xaki yi ta maimaita kaya
kenan...." Ta fashe da matsanancin kuka tace "Toh meye don na masu sadakan kaya,
idan haka ne mu koma gida in kwaso wasu kayan sannan mu dawo mana" Yace "Koh?" Tace
"Ehh mana" yace "Okay, xamu koma ki debo duk kayan naki sai mu dawo" tana share
idonta tace "Na yarda, daga nan ma sai mu taho da ruwan gora da biscuits" Yace
"Toh" Daga haka ya fita daga bukkar. Har rana ya fara yi Nihad na ta baza ido bata
ga Khalil ba balle su bar garin, da rana aka kawo mata ordinary wake da aka dafa
aka xuba masa man gyada ita da bata cin wake, ga shi wani axababben yunwa take ji,
haka ta bar masu tsiyarsu, wasa wasa har kusan la'asar ba khalil ba labarinsa, da
taga yunwa xai mata illa haka ta daure ta dinga danna fura da nonon da aka dama
mata, shiru shiru har magrib, bayan ta idar da sllh ta ci kukanta ta gode Allah,
har aka yi isha bata ga Khalil ba har ta daina tambayar dattijuwar dake assuring
dinta yanxu xai shigo, bayan tayi sallan isha kawai ta dage net ta shige tana
shesshekar kuka ba tare da ta bi ta kan tuwon dawar su ba, can wajajen karfe goma
sha daya saura ta dinga jin kamshin turarensa, sai kuma ta ji suna gaisawa da
mutanen dake tsakar gida kafin ta shigo, xa a kawo masa abinci yace masu ya koshi,
bayan like 10 mins ya dage net ya hau saman gadon ya haskata da karamar wayarsa,
duk da tana jin sa bata yarda ta bude idonta ba, kashe fitilan yayi ya kwanta, ta
bude ido ta dawo kusa da shi ta fashe da kuka tana shessheka tace "Kai fa kace idan
na gama sanye kayan da na kawo za mu tafi gida, toh gashi yanxu ko kayan da xan
canza gobe bani da shi" Yace "Sae ki maimaita na yau" kuka take sosai, ya juya mata
baya, ta ci kukanta ta gode Allah sannan ta koma ta kwanta a hankali, bayan kusan
awa daya ya kunna torch dinsa ya haska fuskarta ya ga bacci take.
Can kusan asuba xafin jikinta ya farkar da shi, kamar jiya tana kusa da shi ta
takure waje daya, ya kai hannu jikinta ya ji da xafi....

*Ki biya dari biyar ki karanta hankalinki kwance er uwa*

NIHAAD is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence of
payment via👇🏻

07087865788....
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

26

Khalil na ganin number dake saman screen dinsa ya kalleta da sauri, bai san lkcn da
ya saketa ba ya shiga call logs dinsa hurriedly to check if tayi sending kiran,
Nihad tayi using opportunity din saketan da yayi ta fice daga dakin a guje ta shige
nata ta kulle, jingina tayi da kofar tana maida numfashi with surprise written all
over her face, why did Aliyu's number appeared on his phone daga fara dialing, how
will that be? lokaci daya tayi assuring kanta cewa ai jiya ne ya kwashe number a
wayarta bayan ya dauke mata wayar, karasawa tayi ta zauna gefen gado da tunani iri
iri a ranta, does it mean bayan ya jefa wayar cikin ruwan cirowa yayi ya busar
kenan ya shiga call logs dinta ya dau number Aliyun? Dama kuma da Aliyu da Umma sai
su Husnah kadai tayi magana da a sabon wayar, numbobinsu kadai ne a wayar, tsaki ta
ja ta mike ta tafi kusa da window ta tsaya, why will she even be stressing her
self, takaicinta guda yanxu da bata tsoma wayar tasa cikin ruwa ta fito da sauri
ba, yunwan da ya addabeta wajen karfe sha biyu ya sa ta bude kofar dakinta a
hankali ta fito parlor, bata gansa a parlon ba ta saci kallon kofar dakinsa sai
kuma ta shige kitchen da sauri, ta bayan windown kitchen din ta hangosa xaune saman
farin kujera yana waya, kasa kunne tayi amma babu abinda take ji saboda window din
kitchen din dake a kulle, idan kuma tace xata bude xata yi drawing attention dinsa,
juyawa tayi ta fice daga kitchen din ta nufi kofar fita parlor, cikin sanda ta isa
har ta wajen da yake ta tsaya inda baxai hangota ba don backing wajen yayi, kawai
tana son tabbatar da cewa da Nihal yake waya kafin ta san irin rashin mutuncin da
xata mata sannan kuma ta hadata da Umma, ji tayi yayi kasa da murya yana cewa "Amma
Baby me yasa kike tunanin ina Nigeria?? Wani yace maki ya gan ni a Naija ne?" Gwalo
ido Nihad tayi ta bude baki tana kallonsa, murmushi taga yayi yace "Ranan da na
dawo ai bayan wajen Mamina wajen ki xan taho har sai kince min in tafi, kinga ko
abinci ma kadan xan ci na Mami.... Naki ne xan ci in koshi" Nihad dai ta kasa rufe
baki sai kallonsa take da mugun mamaki, cikin cool voice dinsa yace "Nasani
Nadeeyah.... In sha Allah ina dawowa babu bata lokaci kuma kamar yanda na maki
alƙawari xa mu yi aure...." Sai a sannan Nihad tayi wani dariya tana tafe hannu
tace "Yau naga ikon Allah, babba da shirga karya" juyawa yayi da sauri yana
kallonta, ta wani hade rai tace "Katon mutumi da kai baka ji kunyar irin wannan
karyar da ka zauna kake laftawa ba? Wato ba a Nigeria kake ba, na shiga uku ku ji
wai baya Nigeria, to a wani kasar kake? ko da yake ita ce babban mahaukaciyar da ta
tsaya take sauraronka har kake fesa mata wannan mugun karya haka..." Tuni khalil ya
katse wayar ya mike yana mata wani kallo yace "Kar ki sake kiranta da mahaukaciya"
A fusace Nihad tace "Ance mata mahaukaciyar me xaka yi? idan waya xaka yi da ita ka
fita titi kayi mana ai dai naga nan gidan Ubana ne ko? Ko Abbana ce maka yayi ka zo
ka dinga masa waya da mata a gidansa?" Khalil yace "Zaki gane ke ce mahaukaciya ba
ita ba" Cike da tsiwa tace "Sai dai ku ne mahaukata ba ni ba wallahi, kuma kar ka
sake kiran wata banzan mace a gidan Abbana" Bai kuma ce mata komai ba ya gyada kai
kawai ya bar wajen, ta bi sa da wani harara, sai kuma ta ja tsaki tace "Wai baya
Nigeria, kai har kana da kudin fita nan nan Niger ma balle wata kasar?? Ai har ka
mutu ko kamshin airport baxa ka ta6a ji ba don ma kaji in gaya maka" Shi dai tuni
ya bar wajen don Nadeeyah na ta kiransa a waya, Bin bayansa Nihad tayi tace "Dama
idan waya xaka yi ka fita can titi kaje kayi ba dai a gidan Abbana ba na gaya maka"
kafin ma ta shigo parlorn har ya shiga dakinsa ya kulle da makulli, ta ja tsaki
tace "Aikin banza" kitchen ta tafi ta dafa indomie, tana kitchen din taji ana
kwankwasa gate, ta ɗan leka parlor sai gashi ya fito daga dakinsa ya fita compound,
kashe gas din tayi da sauri ta fito daga kitchen din ta shige dakinsa, gun wayarsa
dake saman gado ta nufa, sbda tsoro har wani rawa hannnunta yake ta dau wayar ta
shiga call log don taga da warce yake waya har yake karyan ba a Nigeria yake ba,
Nadeeyah ta gani, mamaki ne ya cika ta don ai tayi blocking number jiya, ai ko yau
sai ta tona masa asiri ba dai baya Nigeria ba, xai ga aiki da cikawa yanxun nan,
dialing number tayi har ya gama ring ba a daga ba, ta sake kira nan ma yana ta
ringing no response... Khalil na isa gate din ya bude, Husnah ce tsaye bakin gate
din tana sanye da Hijab har kasa, ta ɗan yi murmushi tana kallonsa tace "Ina yini?"
Babu yabo babu fallasa yace "Daga ina kuma wa kike nema?" Tana Murmushi still tace
"Ba lallai dama ka nuna ka gane ni ba duk da nasan ka gane ni, dama ba wani abu ya
kawo ni nan ba illa in baka hakuri akan abinda muka maka shekaranjiya ni da
kawayena, tun ranan wallahi ban samu nutsuwa ba sabda walakanta d'an Adam ba shi
daga cikin halina, ba tarbiyar gidanmu bane, ni ban ta6a ba sai ranan, kuma mun yi
hakan ne kawai don mu faranta ma kawar mu kamar yanda ta bukaci mu yi, daga baya na
gane bamu kyauta ba biye mata da muka yi muka ci maka mutunci.... Nayi magana da
sauran kawayena mu zo mu baka hakuri ko ba tare da sanin Nihad din ba amma sun nuna
baxa su iya xuwa ba shine ni na taso da kaina in zo har nan in baka hakuri, don
girman Allah kayi hakuri ka yafe mana gaba daya, ko a jiya ma da ta fito xuwa
makaranta idan ka lura ai da wuri ta dawo, to mu muka sa ta gaba muna nuna mata
illan kin yi ma miji biyayya ko da kuwa baka son shi, dalilin barin ta makaranta
kenan da wuri ta dawo gida, yanxu haka bata san xan xo nan ba, kawai kaina tsaye na
taho...." Khalil yace "A takaice dai me ya kawo ki nan Malama?" Ta sauke idonta a
hankali tace "In baka hakurin abinda muka yi maka ni da kawayena, kuma mu nemi
gafararka" Yace "Toh rike hakurin ki, su ma ki mayar masu da nasu, don ba ku kai ku
min abinda xai bata min rai har ki xo bani hakuri ba" Ta daga kai ta kallesa tace
"Baka dai hakuran ba kenan?" Da wani expression yace "Shine nace kun min wani abu
ne da ya bata min rai har xa ki zo bani hakuri tukunna?" Ta langwabar da kai tace
"By the way, sunana Asma'u, amma kawayena na kirana da Husnah...." Ko rufe baki
bata yi ba ya kulle gate din almost on her face ya juya ya koma cikin gida. Yana
shiga daki ya dau wayarsa dake ring ganin Nadeeyah ce ke kiransa ya daga ya kai
kunne, daga daya bangaren tace "I saw ur calls" Ya d'an yi shiru, da mamaki yace
"My calls?" Tace "Yea, minutes ago" Yace "Ohh, sorry mistake ne" Tace "Ohk, sai
anjima kenan?" Yace "Sure" Katse wayar tayi, ya hau duba call logs dinsa da sauri,
Nadeeyah kawai ya ga ta kira, ya kalli kofar dakin ko kiftawa baya yi. Da yamma
Khalil ya shirya xai tafi can gida saboda kiransa da Abba yayi, Nihad dai na daki
abun duniya duk ya bi ya isheta, da ta gaji da wannan bangaren gadon ta koma daya
bangaren, ko kuma ta sauka kasa ta zauna, ita bata saba xama waje daya kamar
jaririya ba, all through the week ko bata da lectures sai ta shiga school, daga
school kuma su tafi yawonsu da su Husnah, tun goma na safe idan ta fita gida dama
sai magariba take dawowa, sai gashi yanxu wai ita ce daga daki sai bandaki, sannan
babu waya ba komai, ita da 24/7 wayarta na hannunta, tunanin hakan yasa ta rushe da
kuka tana jin kamar ta samu wanda xai harbe mata khalil ta huta, gaba daya ta rasa
me ke mata dadi a duniyar, why is this happening to her, kuka ta dinga rerawa tana
bubbuga kafa. Khalil na isa gida a waje yayi parking Aminu na hangosa ya taso da
sauri yana daddaga hannu sama yana washe hakora yace "Sai kayi oga...." Khalil ya
kashe motar ya sauko, Aminu ya kyalkyale da dariya yace "Shekaranjiya Saminu ya
jiyo mana wannan lamari me ban mamaki daga bakin Hafsah me aiki, yanzu haka aka yi
dama?" Khalil yace "Wani lamari kenan?" Aminu ya washe baki yace "Ahh haba ni ne fa
Aminu, meye kuma xaka boye min banda abun ka" murmushi khalil yayi yace "Ba abinda
xa a boye maka" Aminu ya ja sa har xuwa kan bencinsa yace "Shi kansa bencin nan
yasan ba ka a gidan nan mutumina" Khalil ya shafa kai yace "Toh ya ake ciki?" Aminu
yace "Ana nan dai yanda ka tafi ka bari in gaya maka, har yanzu kasan Alhaji bai
fara fita aiki ba, yanxu haka yana da baki yan zuwa jaje a parlonsa, Ita kuwa uwar
Nihad din na can kwance ba lafiya har da karin ruwa don har gida likitan ke xuwa
dubata, kanwarta me shegen kama da ita din nan ce ke wajenta yanxu haka, Umma kuma
jiya da sassafe ta fita a mota bata dubi halin da abokiyar xamanta ke ciki ba sai
ga ta ta dawo mota duk ya lotse wai tayi dan karamin hatsari a hanya amma babu
abinda ya sameta, ko kwarzane bata yi ba, xancen da nake maka har yanxu Alhaji bai
sani ba, ko mu tace kar mu yi magana, baka ga inda taje tayi parking motar ba don
kar ya gani" Khalil dai bai ce komai ba, amma Mumy da aka ce bata da lafiya ce ta
tsaya masa a rai, Aminu ya tuntsire da dariya yace "Yanxu don Allah yaya zaman naku
da yarinyar nan, ni fa na dauka xa ace ta kashe kanta da taga Alhaji ya aura maka
ita, kiyayya ce fa ta gaske take maka" Khalil yace "Ni ban kashe kaina ba sai ita
xata kashe kanta?" Dariya sosai Aminu yake yace "Gaskiya kam kai aka cuta, anyi
mugun kwararka mutumina, yanxu fa har yara da jikoki sai sun ga wannan videon nata
da yayi yawo a yanar gizo, tabo ne da baxai ta6a goguwa ba har karshen rayuwarta,
kai don ma dai iyayenka ba yan boko bane basa hawa yanar gizo, ai da wallahi baxa
su amince ka auri yarinyar nan ba, ko kai baka kare ma videon kallo bane? Saminu fa
har jawo mana shi yayi kusa kusa yanda xa mu gani da kyau, ita wannan ba ma wani
amfani ta sake yawo da kaya a jikinta bayan duk duniya sun san surarta" Lkci daya
mood din khalil ya sauya, Aminu ya girgiza kai yace "Tirr, amma a gaskiya hada
zuri'a da wannan yarinyar ma bala'i ne, banda kana jin nauyin ubanta me xai kai ka?
Kai da kake da mutunci haka, Sauran titi ce fa, duk ta yasar da darajan nata ta
rarrabar a titi, nan nan nan ranan ni da kai muka ganta da asuba ta dawo daga sheka
ayarta tana
ta rabe rabe bakin gate, kuma ta sha yin hakan tun ma baka xo gidan nan ba ya fi a
kirga, labarinta ma ai sai a bakin Habibu, nasan bai san da wannan hadin ba da ya
zuga ka yace kar ka yarda komin me ubanta xai ce maka, shi ma dai Alhajin ya so
kansa da yawa, bai kuma yi maka adalci ba, ya rasa warce xai aura mata sai Nihad
bayan ga salihar er uwarta Nihal, lalatacciya ce fa babu wanda bai sani ba, ni
wallahi da kudi ma baxan amince in aureta ba balle kyauta...." Mikewa Khalil yyi ya
nufi cikin gidan, Aminu yace "Auu har mun gama hirar? Ko xaka shiga ka fito?"
Khalil na isa balcony ya kira Abba ya sanar masa yana gidan, Abba yace ya basa few
minutes yana da baki, Khalil ya amsa masa da to sannan ya xauna saman kujeran dake
wajen, har wani sarawa yaji kansa ke yi da maganganun Aminu, yana ta xaune balcony
din sai ga Aunty Jamila ta fito xata kwaso kayan shanya da tayi a baya, mikewa yayi
, ganinsa tace "Aa kai ne a nan..." Gaisheta yayi, ta amsa tace "Ya gida?" Yace
"Alhamdulillah" Tace "Toh ka shiga ciki mana" kawai murmushi yayi bai ce komai ba,
tace "Ka karasa Sudais ya kai ka ka duba Mumy kasan bata ji dadi ba" yace
"Subhanallah, amma da sauki ko?" Tace "Alhmdlh" yace "Toh Allah ya bata lafiya"
Tace "Ameen" tana barin wajen ya shiga parlon kansa a kasa, Sudais na ganinsa ya
taho da gudu ya rungumesa yace "Uncle mun daina ganinka" Ya shafa kansa yace "Gani
na zo ai, ina fadil?" Yace "Yana wajen Mumynmu bata da lafiya" Khalil yace "Toh kai
ni in gaisheta" Har part din Mumy Sudais ya kai sa, yayi sallama bakin kofar
parlon, Wata frnd din Mumy ta amsa, shiga parlon yayi kansa a kasa ya nemi saman
carpet ya xauna ya gaishesu, duk suka amsa, Mumy dake xaune parlon an cire mata
last drip dai kallonsa kawai take, Bayan few seconds ya daga kai ya kalleta yace
"Ya jikin Mumy?" Cikin sanyin murya tace "Alhamdulillah Ibrahim, ya gida?" Ya sauke
kansa yace "Lafiya lau, Allah Ubangiji ya kara Lafiya" Tace "Ameen Nagode" Bai kuma
cewa komai ba, Hajiya Zara ta mike ta fita daga parlon, bayan few minutes Mumy tace
"Kayi hakuri Ibrahim, an cuceka an hadaka aure da warce bata cacanceka ba, nasan
baka da yanda xaka yi ne kuma baxa ka iya k'in amsan tayinta da mahaifinta yayi
maka ba...." Da sauri yace "Aa Mumy, Allah ne ya tsara haka, kuma muna fatan Allahn
yasa hakan shine mafi alkhairi" Hawaye na sauka idon Mumy tace "Ni kam bani da
abinda xan ce maka sai dai in baka hakuri akan abinda Alhaji ya maka, sannan ni
baxan ce kayi hakuri da Nihad ba, idan kaga baxa ka iya ba ko xaka cutu ina me goya
maka bayan ka saketa kawai ta dawo gida...." Cike da karfin hali Khalil yace "In
sha Allah baxa ayi haka ba Mumy" Mumy ta share idonta bata kuma cewa komai ba, Wani
duniyar tunani khalil ya fada gaba daya jikinsa yayi sanyi, he couldn't even think
straight, kiran sallahn magrib da ake ne yasa ya dago kai ya kalli Mumy ya ga
kallonsa take, a hankali yace "Xan je masallaci Mumy, Allah ya kara lafiya" Tace
"Ameen Ibrahim nagode" Tashi yayi a hankali ya fita daga parlon, Umma ya tarar a
main parlor ta masa wani kallo sai kuma ta ja tsaki tayi hanyar kitchen, ya bi ta
da ido kawai. Bayan an idar da sallan magrib tare suka shigo gidan da Abba har xuwa
parlonsa, Khalil ya xauna ya gaida Abba da ladabi, Abba ya amsa yace "Ya gidan?"
Yace "Alhamdulillah" Abba yace "Ya kamata xuwa gobe ku shirya ka tafi da ita can
garinku ta gaida iyayenka, bayan kwana biyu sai ku dawo" Khalil ya ɗan yi jim, sai
kuma ya dago ya kalli Abba yace "Toh in sha Allah Alhaji, Allah ya kai mu goben"
Abba yace "Ameen, farooq ya zo min da wani batu jiya amma sai kun dawo dai" Khalil
yace "Toh Alhaji, nagode" Abba ya ciro dubu dari ya mika masa yace "Ka yi full
tank, sannan kayi ma iyayenka tsaraba da sauran" Khalil ya sa hannu biyu ya amsa
yace "Toh Allah ya saka da alkhairi Alhaji" Abba yace "Ameen, Allah ya maka
albarka" Khalil ya amsa da "Ameen" a tare suka fito main parlor da Abba, Umma ta
fito daga kitchen kenan ganinsa da Abba tace "Aa Ibrahim har xa ka tafi, bari to ga
abinci ka kai ma Nihad tunda an gama" Ya kalleta yace "Toh" Komawa kitchen tayi da
sauri, Abba dai ya zauna parlon har sannan kana ganinsa xaka san yana cikin damuwa,
dake xuciyarsa kawai yake yana ma Nihad wasu abubuwan as form of punishment amma
shi yasan sonta a jininsa yake, but he can't help it, tayi disappointing dinsa
sannan ta xubar masa da mutunci a idon duniya, Umma ta cika warmer da abinci,
sannan ga wani warmer din daban na kaza ta fito parlor, sai da ta bubbude warmer
din tana kallon khalil cike da damuwa tace "Don Allah idan ka je ka lallabata ta ci
abincin nan, duk ta rame ta lalace wallahi, Shekaranjiya da naje ma da ya na samu
ta ci abincin, yanxu kam ban san halin da take ciki ba baiwar Allah, wa yasani ma
ko bata cin komai" Shi dai Abba bai ce komai ba, khalil kuwa banda kallonta babu
abinda yake, Abba ya mike yace "Ka jirani Ibrahim" Khalil yace "Toh Abba" Ba a dau
lkci ba sai ga shi ya dawo da dubu talatin ya mika ma Khalil yace "Ka siya mata
carton din maltina da na madaran gwangwani" Ta gefen ido Umma ke ta kallon Abba,
Khalil ya amsa yace "Toh In sha Allah Abba" Abba yace "Sai da safe, Allah ya tsare"
Juyawa Umma tayi ta shige kitchen ta tsaya jikin cabinet kamar me nazari. Khalil na
isa gida sai da yayi isha a masallacin dake layin sannan ya shiga gida da motar
yayi parking, bayan ya kulle gate din ya dawo ya fiddo abincin daga cikin mota ya
kai parlor ya sake fitowa ya kai maltina da madara parlon ya ajiye sannan ya kulle
gidan, xaunawa yayi saman kujera ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, da
yasan haka abubuwa xa su kasance masa da bai yarda ya fara shigowa garin kano ba,
where will he even start this amendment from?? Babu warce ta tsaya masa a rai sai
Mahaifiyarsa, this seriously isn't going to be easy, Mikewa yayi daga karshe ya
nufi dakinsa yana tafiya a hankali, har ya bude kofar sai kuma ya fasa shiga, ya
dawo ya bude dakinta, zaune ya ganta a kasa idonta yayi bulu bulu alamar tayi kukan
gaske yau, ya tabe baki ya kulle kofar ya koma parlor kawai yayi xamansa, tashi
Nihad tayi ta bi bayansa, ta tsaya bayan kujera tana shesshekar kuka..., ya ɗan
daga kai ya kalleta kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Da bashi ne?" Wani bakin
ciki ya rufeta a fusace tace "Ban sani ba, ka zata kai ka isa ka dinga punishing
dina? Waya biyu aka kawo min gidan nan ka salwantar min da su, toh wallahi zaka sha
mamakin abinda xai faru idan baka bani wayata ba" Mikewa yayi ya bar mata parlon ya
shige dakinsa ya kulle, kuka kawai take kamar ranta xai fita, babban tashin
hankalinta shine Aliyu da xai yi ta kiranta ya ji a kashe, yanxu babu ta inda xata
yi ta iya kiransa, da ma baya kulle gate ne ko makota ita sai ta shiga don ta kira
Aliyu, amma ko daxu da xai fita kulleta yayi ta ciki, ko bin ta kan warmers din
abincin dake parlon bata yi ba ta koma daki ta dinga kuka kamar ranta zai fita, har
kusan karfe biyun dare Nihad bata yi bacci ba, abun duniya ya taru yayi mata yawa,
last week fa warhaka tana baccinta peacefully a saman gadonta, tashi tayi a hankali
ta goge idonta ta nufi kofa, a hankali ta bude kofar dakin nata ta fito, taga ya
kashe duk wutan gidan, ko ina yayi duhu, tana lalubawa ta tafi hanyar dakinsa ta
kai hannu handle din kofar ta murda a hankali ta bude ta shiga dakin, nan ma dai ya
kashe fitilar, sai da ta fara tattaba socket din dakin cikin duhun ko xata ga
karamar wayarsa a jiki taga babu, cikin sanda ta nufi gadon dakin ta durkusa, hannu
ta kai xata laluba kan gadon taji hannunta saman broad haired chest dinsa, zaro ido
tayi a mugun tsorace xata mike ta gudu ya fixgota ta fado saman gadon daga gefensa,
yayi kneeling dai dai inda take har tana jiyo respiration dinsa, yana kallonta
cikin duhun kafin yace komai jikinta na rawa tace "Wayyo na shiga uku, wallahi
torchlight nake nema xan je in sha ruwa a kitchen...."

*Littafin Nihad dari biyar ne, ki fita hakkina kafin ki karanta min littafi
hankalinki kwance*

3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence via👇🏻

07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

29
A hankali Nihad ta bude idonta ta dalilin sanyin da take ji, at first sai da tayi
imagining cewar ai fa kauyen nan take, a firgice ta tashi xaune tana tattaba daya
side din gadon don wutan dakin a kashe yake, amma taji ba kowa wajen, jin laushin
duvet yasa ta tuna ashe a hotel suke, wani boyayyen ajiyar xuciya ta sauke, ta
sauka daga kan gadon tunda hotel din ba bakonta bane ta san inda switch yake, tana
tafiya a hankali ta xagoya xata kunna wutan taci tuntube da mutum ta fada kansa duk
da a zaune yake, da farko tayi mugun tsorata amma tana jin kamshin turarensa ta
gane shi ne, tashi tayi ta dafa bango ta kunna wutan, zaune ta gansa saman darduma
alamar sallah yake, ta zaga daya side din ta kalli agogon dakin ta ga karfe biyu da
minti goma, komawa tayi gefen gado ta zauna tayi tagumi, sai kuma ta tuna bata yi
isha'i ba ta tashi da sauri ta shiga bandaki. Har ta idar da isha'i sallah yake
shima, ta ɗan yi jim kamar xata tashi ta koma ta kwanta can dai kuma kawai ta mike
ta hau sallan nafila, har ta mance rabon da tayi qiyamul lail, sai dai in
mistakenly ta kwana dakin Nihal shine Mumy ke tashinsu su yi sallan dare, don dare
daddaye ne Mumy bata sallan dare, a wannan daren kuma tayi addu'a sosai a kan Allah
ya toni asirin duk wanda yayi ruining happiness dinta cikin gaggawa, abinda bata
ta6a yi ba tun da abun ya faru, daga karshe tayi addu'ar Allah ya sa khalil ya rabu
da ita na har abada don ita ba class dinsa bace, sannan baxata ta6a zama da shi a
matsayin mijinta ba, ta kuma yi addu'an bayan Khalil ya rabu da ita Allah ya
mallaka mata Aliyu, wajajen karfe Uku da rabi ta fara jin bacci, ta ɗan saci kallon
side dinsa, yana zaune saman darduma shi ma da alamar ya idar, amma kana kallonsa
xaka san yayi nisa tunanin da yake, and he look so distressing, dauke idonta tayi
daga kansa tayi kwanciyarta saman inda tayi sallan, har dai bacci ya dauke wajen
karfe hudu bata ga alamar Khalil xai kwanta ba. Da asuba loudspeaker din masallacin
dake hotel ne ya tasheta, bata gansa a dakin ba alamar ya tafi masallaci, bayan ta
idar tana zaune saman darduma tana azkar ya shigo dakin, ba tare da ya kalleta ba
ya shiga bandaki, tana ta zaune kan darduma taji ring din wayarsa kallon gaban
madubin tayi da sauri don bata san wayar na nan ba, kuma bata ta6a jin wayarsa na
ring ba sai da vibrate, ta mike tana tafiya a hankali ta tafi gaban madubin, Mami
ta gani gaban screen din karamar wayar, ta dauka kenan kawai ya bude bandakin ya
fito da sauri ya nufota yace "Keee" Ba karamin rikicewa tayi ba ta juyo wayar na
hannunta, zaro ido tayi ta saki wata er kara ganinsa daure da towel ta durkushe
kasa ta rufe fuskarta da gwiwanta a tsorace, yana isa inda ta durkusa ya warce
wayarsa a hannunta ya koma bandakin, duk da taji rufewar kofar bandakin taki dago
kanta, bayan kusan minti daya ta dago a hankali tana kallon kumfan da ya sa mata a
hannu wajen warce wayarsa, turo baki tayi ta mike jiki a sanyaye ta koma can daya
side din gadon ta kwanta tare da juya ma kofar bandakin baya. Tana ji ya fito daga
bandaki bayan kusan minti sha biyar sai kuma ta ji ya fita daga dakin gaba daya.
Wajen karfe takwas ta gaji da kwanciya ta tashi ta zaga ta shiga bandakin, wanka
tayi ta fito bayan ta goge jikinta ta maida kayan da ta cire, tana zaune gefen gado
ta jinginar da kanta da gadon tana kallon Tv duk da hankalinta baya kan kallon ya
bude kofa ya shigo dakin, tunda ta kallesa sau daya bata yarda ta sake kallonsa ba,
ta dai ga ya canxa kaya, shi kam bai kalli inda take ba ya dau towel din da ta
yasar saman gado ya shigar da shi bandaki ya fito, ya dauko magungunan da ya siyo
mata jiya dake yashe kasan dakin ya jefa mata gefenta ya hade rai yace "Wato dama
lafiyarki qlau kika sa naje chemist nayi asaran kudina ko?" Ba tare da ta kallesa
ba tace "Kudin babana dai" kallonta kawai yake ba ko kiftawa, can yace "Gaskiya ne,
kudin babanki ne, sai ki taso mu koma can garin kiyi kumallo a can gidanmu, kinga
can ai kudin babana ne ba na baban wani ba" Kallonsa tayi da sauri, ganin hada
abubuwansa dake dakin kawai yake, tayi karfin halin cewa "Wani garin xan je in yi
kumallo?" Ba tare da ya kalleta ba ya nufi kofa yace "Ina jiranki a waje" Ta fashe
da matsanancin kuka tace "Ni wallahi baxa ka maida ni wannan garin ba, wai kai baka
tsoron Allah ne?" Juyowa yayi ya rungume hannu ya jingina da kofa yace "Sai ke"
Cikin kuka tace "Allah baxan je ba, kaji har na rantse, dama ba kwana biyu kawai xa
mu yi ba? To wllh baka isa ka maida ni ba" Yace "Ohk, xan nuna maki kuwa na isa,
sannan in mun koma sai mun yi wata daya kafin mu bar garin, kinga baxa ki kara min
gorin kudin babanki nake ci ba" Cikin tashin hankali tace "Kaga don girman Allah
kayi hakuri ka daina ce min haka, wallahi in ka sake maida ni kauyen nan xan iya
mutuwa kawai" Khalil yace "Toh mu je a ga adadin kwanakin da xaki iya a can din
kafin ki mutu" Cikin kuka tace "Don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri"
Shiru yayi na few seconds, sai kuma yace "Ohk, baxan maida ki garin ba amma da
sharadi" Tana goge idonta tace "Ina ji" Ya fi second talatin yana kallonta kafin
yace "Nasan komin daren dadewa xa mu rabu... Don haka idan Allah ya kai mu lokacin
ina son ko me xai faru baxa ki fasa nuna ma iyayenki cewar ke kika bukaci mu rabu
ba ni ba....." Nihad dake ta kallonsa da mamaki tace "Toh me yasa yanxun baxa mu
rabu ba kawai, kuma wallahi babu wanda xan gaya ma, kaga babu wanda xai sani sae mu
biyu" Yana kallonta yace "Ohk ta yaya kike tunanin xa mu rabun yanxu?" Ta gyara
xama tace "Kawai kace ka sakeni, babu me sani sai ni da kai" Yace "Toh idan aka yi
hakan sai me xai faru?" Ta daga kafada tace "Ba komai, kawai kayi rayuwarka inyi ta
wa, ni xan ma iya bar maka gidan gaba daya kawai sai dai in dinga xuwa diban
kayana, idan kana so ma sai ka saka yan haya ka dinga karban kudin kana xubawa a
aljihu" Khalil ya ɗan yi murmushi ya gyara tsayuwarsa yace "Ohk, sai ki ci gaba da
iskancinki daga inda kika tsaya kenan ko?" Tayi masa wani kallo tace "Me kake nufi?
Ni nake yin iskanci? Kana nufin ni yar iska ce?" Yayi wani murmushin takaici yace
"Toh baxan yi abinda kike so yanxu ba, kawai dai ki sa a ranki lokacin hakan na
zuwa, nan ba da dadewa ba" Ta kyabe baki tace "Ni fa lokacin da kake nufi da yanxu
duk daya ne ni a wajena" Ya daga kafada yace "Gwara dai a jira lokacin" Ita dai
bata kuma cewa komai ba amma a ranta tunani take ashe ma ba wani babban sharadi
bane, dama ita ai babban burinta su rabu na har abada, Ta kallesa tace "Ka dai yi
alkawarin rabuwa da ni??" Yace "In sha Allah" Wani farin ciki taji ya rufeta tace
"Toh nima in sha Allah ko ma me xai faru xan ce nice nace mu rabu babu ruwanka"
Yace "Toh" Tace "Toh nima ina da deal dina in har kana son inyi abinda kace nima
sae kayi abinda nake so" Yace "Ina sauraronki" tana gyara zama tace "Na farko ina
son ka bar ni in ci gaba da xuwa makaranta na, na biyu baxa ka hana duk wanda xai
zo wajena xuwa ba, like kawayena infact everybody, na uku xaka bani spare key na
gida nima, sannan na karshe ina son ka bar ni da wayata..." Kallonta kawai khalil
yake, ta langwabar da kai ta wara ido tace "Ehh, ni gwara nawa minor request ne,
babu abinda xai ragu a jikinka idan kayi accepting, naka request din kuwa kilan har
tsine min xa a iya yi a gida amma kuma ban damu da hakan ba na amince xanyi yanda
kace" Khalil yace "Abu biyu kadai xan iya maki a abubuwan da kika ce, idan kuma
kinga hakan bai maki ba kawai a bari, mu ci gaba da zaman mu yanda muke, kuma dole
a titi ace maki matar drivern gidanku" Ta marairaice sai kuma tace "Toh ina ji, ka
gaya min abu biyun" Yace "Babu xancen xuwa makaranta sannan baxa ki rike waya
ba!!!" Shiru Nihad tayi tana nazari, wato kawayenta xa su iya xuwa gidan sannan xai
bata makullin gida, daga kai tayi ta kallesa taga kallonta yake yana jiran jin me
xata ce, tace "Toh ai shikenan, na amince" Yace "Sannan abu na karshe wanda
muhimmancinsa kusan daya da sharadin farko...." Tace "Ina jin sa" Yace "Babu ke
babu kallon inda wayata take balle ki ta6a, a takaice babu ruwanki da wayana har
xuwa lokacin da xa mu rabu" Nihad ta kyabe baki tace "Toh dama ni meye ruwana da
torchlight phone dinka bawan Allah??" Ya gyada kai yace "Toh" Juyawa yayi ya fita
daga dakin, ta mike ta dau ledan magungunanta ta saka Hijab sannan ta bi bayansa. A
reception ta tarar da shi ya bada makullin dakin ya fita compound din hotel din ta
bi bayansa, wani ma'aikacin hotel din ne irin masu share share ya ganta yace "Ahh
Hajiya kwana biyu kin buya, ya kawayenki" Nihad ta juya ta kallesa, murmushi tayi
tace "Lafiya lau ya aiki?" Yace "Alhamdulillah, yau baku zo da kawayen naki ba
kenan? Naga kullum tare ku ke" Sai kuma ya kalli Khalil dake tafiya yace "Au ashe
da oga ku ke...." Katse sa Nihad tayi da sauri tace "Aa, drivern gidanmu ne, ya
kawo ni in amshi sako wajen wani" Murmushi kawai Khalil dake tafiya xuwa inda ya
ajiye mota yayi ba tare da ya juyo ya kallesu ba, Ma'aikacin ya fasa gaida Khalil
da yayi niyyar gaidawa, sai kuma yace "Allah sarki ni na zata oga ne ae nagansa
kalarki, to na gaisheki Hajiya" Bude jakarta tayi taga dari biyar ta zaro ta mika
masa, ya amsa da ladabi yana mata godiya, tuni Khalil har ya kai gun mota ya bude
driver seat ya shiga, Nihad ta karasa ta bude back seat ta shiga ta kulle, har suka
isa gida bai ce mata ba bata ce masa ba, bayan yayi parking ya sauka ya tafi ya
kulle gate, sannan ya nufi entrance din gidan ya bude kofar main parlor, Nihad dake
ta tsaye tana jiran ya xo ya bude ta kyabe baki ta bi bayansa suka shiga parlon,
wani ajiyar xuciya ta sauke direct ta nufi dakinta. Bacci sosai Nihad tayi bayan ta
shiga dakinta, wajen karfe sha daya da rabi ta farka ta dalilin yunwan da take ji,
a hankali ta mike ta shiga banɗaki tayi wanka ta wanke baki sannan ta fito, bata
gansa a parlor ba har ta nufi dakinsa sai kuma ta fasa bude kofar ta dawo parlor ta
zauna tana jiran ganin fitowarsa bude kofar parlor aka yi ta juya da sauri, taga ya
shigo parlon rike
da leda kallo daya yayi mata ya dauke kai ya karaso cikin parlon, a takaice tace
"Makulli xaka bani xan fita in siyo kayan miya, sannan anjima xan je kasuwa siyo
atamfofi don na kyautar da duk kayana a can garinku" Ya girgiza kai yace "Baya daga
cikin sharadinmu, duk me kike bukata xa a siyo a ajiye maki" Ta kyabe baki tace
"Toh a fita a siyo min kayan miya" Cike da isa tayi maganan, yace "Sai sanda nayi
niyya" Yana gama fadin haka ya ajiye ledan hannunsa ya nufi kitchen don dauko
plate, bin sa tayi da kallo yana shiga tayi saurin dauke ledan abincin nasa ta
shige daki da sauri ta sa makulli, shinkafa ne da miyya da yaji uban nama sannan ga
coslow a wani karamin takeaway din, ga ruwan roba me sanyi da drink, tayi er dariya
ta gyara zamanta ta dau cokali ta fara cin abincin. Wajajen karfe uku Nihal ta kira
Khalil, bayan sun gaisa yace "Kin dawo lafiya?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Maa sha
daya, yaushe xa ki zo ganin er uwar taki?" Nihal tace "Shine dama nake son in ce
mata xan zo yau, ka kai mata wayar pls" Yace "Xan gaya mata, Allah ya kawo ki
lafiya" Tace "Ameen" daga haka ya katse wayar, tun da Nihad ta shige masa da abinci
daki bata sake fitowa ba, don bayan ta ci ta koshi ma ramuwan baccin da bata yi a
kauye ba ta ci gaba da yi. Wajen karfe biyar Nihal ta iso gidan, Khalil ne ya bude
mata gate bayan ta kirasa a waya ta sanar masa tana bakin gate, ta sunkuyar da kai
ta gaishesa ya amsa da murmushi yace "How are you Nihal?" Ta daga kai ta kallesa
tace "Alhamdulillah" Yace "Maa sha Allah" Tana biye da shi suka shiga parlon gidan,
ganin ta zauna a parlon ya daga kafada yace "Tana can daki, ki shiga" Nihal tace
"Ko zaka dan mata magana ta fito" Yace "Aa, just go in" Mikewa tayi ta nufi kofar
dakin da ya nuna mata, a hankali ta kwankwasa kofar, Nihad ta juya tana kallon
kofar, to me xai ce mata yake mata Knocking, can dai ta mike ta nufi kofar ta bude
a hankali, ido hudu suka yi da Nihal, wara ido tayi ta rungumeta tace "Yaushe kika
dawo Nihal?" Nihal na Murmushi tace "3 days ago" Sai kuma Nihad ta hade rai ta koma
cikin dakin, Nihal ta bi ta da kallo sai kuma ta bi ta cikin dakin ta kulle kofar,
Nihad tace "Wato ke har xa a iya hada baki dake a cuceni ko Nihal? Ni nasan babu
yanda xa ayi kice baki san komai a kan abin nan da Abba yayi min ba" Innocently
Nihal tace "Wallahi ban san komai ba Nihad, kiji har na rantse" Nihad tace "Toh sai
aka ce maki yarda xan yi da ke? Bayan nasan har tadi ku ke yi da drivern nan a waya
amma kice baki sani ba?" A hankali Nihal tace "Allah ne shaida na, amma meye ribata
idan nayi maki karya?" Nihad ta tabe baki tace "We have already sort out things da
shi daxu da safe, and we are okay with our plan" Nihal tace "What plan?" Nihad tace
"Ba sai kin ji ba, ina umma?" Nihal ta mika mata wayarta tace "Tace in na xo ki
kirata" Murmushi Nihad tayi ta amshi wayar ta tafi can karshen gado ta hau kiran
Umma, Umma na dagawa tace "Auta har kin je gidan ne?" Nihad tace "Umma ni ce" Umma
tace "Aa Nihad, wato dai wannan matsiyacin duk wayar da aka baki sai ya karbe ga
shi tatattce ko?" Nihad ta tabe baki tace "Wallahi Umma" Umma tace "Toh xa mu xuba
da shi kuwa, xan kawo maki waya sannan in mika masa a gabana ya damka maki wayar da
hannunsa" Nihad tace "Kin ma san abinda yayi min Umma?" Umma ta zaro ido tace "Me
yayi maki?" Nan Nihad ta labarta ma Umma garinsu da ya kai ta ta kusa mutuwa, Umma
tace "Ikon Allah, amma shine matsiyacin nan ya samu waje yake nuna ma mutane isa
daga an aura maki shi? Asha ɗan kauyen kayau ne" Nihad tace "Wllh Umma ban gama
rainasa ba sai da naje garinsu, yanxu 100% na rainasa wallah, Umma ko wuta fa babu
a garin, sannan rafi suke xuwa debo ruwa, kai ni baxan ma iya baki labarin garin
nan da baki ba, sai da nayi rashin lafiya kamar xan mutu sannan ya dawo da ni cikin
gari" Umma da ke ta sauraronta tace "Ikon Allah, dama ance talaka da matsiyaci basu
iya samun waje ba, ki ga yanda ya dawo birni ya kile yake daddaga ma mutane kai
alhalin ko mage me gata baxata iya rayuwa a kauyen ba" Nihad ta sauke ajiyar xuciya
tace "Na sha mamaki Umma, ɗan kauyen kayau ne wllh, kuma yanda kika gansa fari haka
family dinsa suke da haske a kauyen" Umma tace "Toh Allah ya kyauta, in sha Allah
gobe ko jibi ina nan shigowa daughter" Nihad tace "Toh Umma kar ki manta wayar,
idan ya so kamar yanda kika ce sai ki basa ya bani a gabanki sannan ki ja masa
kunne sosai kar yace xai amshe" Umma tace "Kar ki damu sai dai na zo" Daga haka
suka yi sallama, Nihal na kallon Nihad tace "kinsan Mumy bata da lafiya kuwa
Nihad?" Nihad ta kalleta tace "Haba? To ai ni ba a gaya min ba" Nihal tace "Ai kam
bata da lafiya, in kirata ku gaisa?" Nihad ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Ki bari
anjima da daddare xan kirata" Nihal tace "Toh shkkn" Nihad tace "Idan xa ki ci
abinci ga indomie can kitchen ki dafa fa" Nihal ta mike ta fita daga dakin, tana
shiga kitchen taga kayan miya kawai tayi deciding ta dafa jollof rice, tana cikin
grating kayan miyan taji muryar khalil yace "Sannu da aiki" Ta kalli kofar da sauri
sai kuma tayi murmushi tace "Nagode" Yace "Yaushe xa ku kare hutun?" Tace "Nan da
sati biyu" Yace "Ohk nan xaki gama hutun ko?" Tace "Aa ni da gobe xan tafi, i don't
want to over stay my welcome" Murmushi yayi yace "Aa kiyi hutunki kawai a nan" Ita
dai bata ce komai ba tana ci gaba da aikinta, juyawa yayi daga karshe ya bar
kitchen din. Bayan Magriba yana xaune a parlor Nihal ta fito daga daki xata je
kitchen ta xuba ma ita da Nihad abinci, ganin khalil zaune parlon ta koma daki
wajen Nihad tace "Ki fito ki zuba masa abinci, ban fa xuba masa ba tun daxu" Da
mamaki Nihad ke kallonta, sai kuma tace "A saboda me xan xo in xuba masa abinci?
Dama da shi kika dafa abincin ne?" Nihal dai bata ce mata komai ba ta juya ta fita,
Nihad ta rike ha6a tace "Ji wani iyayi wai in xuba masa abinci kamar wani mijina,
ashe xai tsufa bai ci abincin ba" Tsaki ta ja ta jawo wayar Nihal for the 10th time
ta sake kiran layin Aliyu amma a kashe, kwantar da kanta tayi saman pillow kamar
xata yi kuka don har ta gaji da trying layin nasa, tun xuwan Nihal take abu daya,
Nihal na komawa kitchen ta fara xuba masa abincin a plate sannan ta dauka ta fito
parlor ta nufesa ta durkusa tace "Ga abinci" Yana kallonta yace "Thank you Nihal"
Ta mike ta koma kitchen din ta xuba ma ita da Nihad a tare, kadan Nihad ta ci
abinci duk hankalinta a tashe yake bata samu Aliyu ba, Nihal ta ci abinda xata ci
ta bar mata ta koma saman gado ta dau wayarta tana dannawa, Daga karshe wajen karfe
goma da taga Nihad ba ci xata yi ba ta dau plate din ta fita, Bayan ta kai kitchen
ta fito khalil na kallonta yace "Wani level kike a makaranta?" Ta tsaya tace "Level
daya muke da Nihad" Yace "But in tambayeki" Ta ɗan tsaya sai kuma ta dawo parlon ta
xauna tana kallonsa yace "Ke kika ce ma Abba Ahmadu Bello University kike so?"
Nihal tayi murmushi tace "Aa, kawai cewa yayi can xan je ni" Yace "Ita kuma er
uwarki fa?" Ta sunkuyar da kanta tace "He gave her option" Khalil dake ta kallonta
yace "Ohk ke daga baya baki ce masa makaranta daya kike son xuwa da er uwar taki
ba?" Nihal tace "Ya Usman da Mumy sun masa magana a lkcn, Mumy tace masa tunda har
Nihad ta zaba Maryam Abatcha nima ya biya mun Maryam Abatcha din mu tafi tare ko
kuma duk mu tafi ABU, amma sai yace Nihad kawai xata je ni in tafi ABU, he can't
afford the fee of Maryam Abatcha for the two of us" Shiru Khalil yayi yana
kallonta, can yace "Kuma Ummanku bata ce komai ba?" Nihal ta girgiza kai tace
"Kawai ce min tayi inyi hakuri in tafi ABU din" Khalil ya gyada kai yace "Amma
secondary daya ku ka yi ko?" Nihal ta girgiza kai tace "Shi ma ba daya muka yi ba,
ita Nigerian Turkish tayi, ni kuma Yan dutse nayi" Khalil ya gyada kai yace "Ohk,
yan dutsen kamar su Amina da Sudais nan suke xuwa ko?" Nihal tace "Har Aunty
Kamila da Ya Usman da ya farooq ma can suka yi, Nihad kadai ce tayi Nigerian
turkish" Khalil yace "Amma kamar er uwartaki tafi sabawa da Ummanki akan mamanta
ko" Nihal tace "To ai a bangaren Umma take, ni kuma ina side din Mum dinta, though
I don't know for her" Shiru Khalil yayi yana kallonta, can yace "Maa sha Allah,
hakan yayi.... amma wani saurayinta da ya zo can gida ranan, sun dade tare ne?"
Nihal tace "Wai Aliyu? Yea definitely shi, don ita bata kula wani saurayi idan ba
shi ba, shekaran da ta shiga Maryam Abatcha suka hadu, shekara uku kenan" Yace
"Ohk, kinsan saurayin sosai kenan?" Nihal ta bude ido tace "Nasan shi mana, he is
the son of General Jikamshi..." Muryan Nihad dake labe jikin pillar din corridor
tum daxu ya katse Nihal, cike da bacin rai Nihad tace "A gidan uwar wa kika san
shi? Shi Aliyun kike tunani kinsani? Har da wani gaya masa sunan babansa salon yayi
masa mugun abu irin nasu na kauye? To wallahi baki san shi ba kuma baxa ki ta6a
saninsa ba, dama don ki zo ki hadu da wannan mutumin ku kafa munafurcina ya sa kika
zo gidan nan ashe ban sani ba? To wallahi ni dai ki tashi ki tafi baxa ki kwanan
min a gida ba, ai dai mun ga juna, har da wani ce masa ni kadai nayi Nigerian
turkish, to wani yace kar kema kice ma Abba can kike so? Naga dai choice dina ne
kuma Abba yayi accepting, sannan Maryam Abatcha ma wani yace kar ki sakar ma Abba
kuka kice ke baxa ki je ABU ba sai dai Maryam Abatcha? Wallahi kin ban mamaki har
xaki zauna da bare kuna cakalkalar namana ko tausayina baki ji ba, to Allah ya isa
wannan gulman nawa da kika yi" Nihal dai bata ce mata komai ba, Banda kallon Nihad
babu abinda khalil ke yi, tana huci tace "Shi kuma saboda gulma har da wani cewa
nafi son Umma, dama ashe maza na gulma ban sani ba? Kuma ai Umma da Mumy duk daya
suke a wajena babu wani bambanci, to tunda dai mun ga juna zo ki dau handbag dinki
kiyi tafiyarki" Mikewa Nihal tayi ta nufi daki, Nihad ta bi ta da harara, sai ga ta
ta fito sanye da hijab tana rike da handbag dinta ganin xata nufi kofa Nihad ta
rikota tace "Ina xa ki tafi da daddaren nan" Nihal ta fizge Hijab dinta hawaye cike
idonta ta nufi kofa, Nihad
ta bi bayanta da sauri tace "Ke ni fa wasa nake maki ina zaki da daddaren nan"
Tuni Nihal ta fice daga parlon, Nihad ta marairaice tana kallon Khalil tace "Don
Allah kayi mata magana, ni wallahi ba haka nake nufi ba" Ko kallonta Khalil bai yi
ba, hakan yasa ta fita da sauri, can ta tarar da Nihal zaune bakin gate dake kulle
tana rera kuka, kukan ta ita ma ta fara ta durkusa gabanta tace "Don Allah kiyi
hakuri wallahi i didn't mean it, ni ba da ke nake ba, da shi nake"

*Nihad* dari biyar ne, ki fita hakkina ki karanta hankalinki kwance yar uwa

3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah ur evidence via👇🏻

07087865788

*Assalamu alaikum er uwa, kina neman organic Supplement irin masu gyaran jiki ciki
da waje? Ko kuma mai fitar Maki da duk wani infection komai nacinsa? Sannan mai
maido Maki martabar fatarki? Ko kina fama da dry HQ? Ko hips ne matsalarki da
boobs? To kwantar da hankalinki *GHT Organic supplement care gat ur back*

Domin karin bayani ki tuntubi wannan number 👇🏻

✍🏻
+2347057607751

https://chat.whatsapp.com/G91KmKaihzAL76lSmkXqG9
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

28

Yau ma kamar jiya hasken rana ne ya sa Nihad ta farka, da kyar ta mike xaune tana
jin duk jikinta na mata ciwo barin kanta da yayi mata nauyi, sosai hankalinta ya
tashi ganin khalil baya dakin, ta hade kai da gadon karan da take kai tana kuka a
hankali, can dae tayi karfin halin mikewa ganin lokaci na tafiya bata yi sallah ba,
ta nufi yar jakar da ta sa brush dinta da Toothpaste ta dauka ta fita daga bukkar.
Bayan ta idar da sallah tana xaune saman abun da tayi sallan lkci lkci tana share
hawayen dake gangaro mata, rashin ganinsa na kara saka mata damuwa a kan wanda take
ciki, shadow da ta gani bakin kofa ya sa ta daga kai da sauri hoping shi ne ya
dawo, amma sai ta ga ba shi bane, wata budurwa ce warce xa su yi sa'anni da Nihad
din ta shigo dakin, fara ce kal kal don duk hasken Nihad yarinyar ta fi ta, ga ta
kyakkyawa ajin karshe, dogon gashinta da aka kitsa gida biyu manya manya har
ƙafadunta suke tabowa, ga uban wushiryarta a baki, Nihad ta ganeta don jiya kaya
kala biyu ta bata da turare, budurwar na murmushi ta duka gaban Nihad ta ajiye mata
kwanon sha dake hannunta tace "Hannu, yau kamar kin makara ko" Nihad ta kirkiri
murmushin ita ma tace "An tashi lafiya" Yarinyar tace "Lafiya lau, ga farau farau
nan na kawo maki, yanxu xa a dunduma tuwon sae a kawo maki" Sosai gaban Nihad ya
fadi jin kalmar tuwo, ita fa bata ta6a sanin akwai wani kalan tuwo bayan fari ba,
gwara gwara amala ta san baki ne, to da wannan abun da suke kira tuwo ba gwara a
bata amalan ba, ta dai sakar mata wani murmushin karfin halin tace "Toh, nagode"
Yarinyar na wasa da gashinta tace "Ni sunana Furera amma ana kirana Fure ke kuma
fa?" Nihad ta sauke idonta tace "Sunana Nihad" Yarinyar ta zaro ido tace "Sunan yan
birni, ae baxan ma iya kiran sunan ba" Nihad tace "Toh ki kirani Ummi" Fure tace
"Yauwa gwara wannan, amma ae xa ku yi sati a nan ko?" Nihad ta kalleta da sauri ta
girgiza kai tace "Aa yau xa mu tafi" Yarinyar tace "Gwaggo fa tace min xa ku yi
sati" Nihad xata yi magana sai ga Khalil ya shigo bukkar da sallama, lkci daya
kamshinsa ya cika Bukkar, Fure ta koma gefe tana d'an Murmushi, tace "Hamma wai
ashe yau xa ku tafi?" Yanda take maganar kasan a kunyace take da Khalil, Khalil ya
kalleta yace "In ji wa?" Fure ta nuna masa Nihad, yace "Aa xa mu yi sati" Gaban
Nihad yayi mugun faduwa ta gwalo ido tana kallon khalil a ranta ta dinga nanata
satin da yace, meye kuma sati, ba dai sati daya yake nufi ba, cike da murna fure
tace "Yauwa dama haka Gwaggo ta sanar min, ai ko naji dadi sosai, duk xan bi in
xaga da Ummi kauyen mu da wanda ke gaba da namu, a kawo maka farau farau din ne ko
fura da nono xaka sha, nonon ma sabuwa ce jiya aka tatso" Yace "Toh kawo min fura
da nonon" Tace "Toh" daga haka ta fita, Nihad ta marairaice tana kallonsa tace
"Amma dai xaka maida ni gida sae kai ka dawo kayi satin a nan?" Ya dauko tabarma ya
xauna kai ba tare da ya kalleta ba yace "Ko kuma ni in tafi bayan sati daya in xo
in dauke ki ba" Bata san sanda ta fashe da wani matsanancin kuka ba tace "Don
girman Allah kar ka min haka ka rufa min asiri..." sai a sannan ya daga kai ya
kalleta, ta hade tafin hannunta tana kuka a hankali tace "Don Allah kayi hakuri,
wallahi baxan iya ba, kaji har na rantse" Gyara xama yayi yace "Bukka guda Gwaggo
xa ta bar maki kiyi rayuwarki ke kadai har bayan sati dayan babu me takura ki"
Nihad ta mike da sauri ta nufesa ta durkusa gabansa tana kuka tace "Wallahi xan iya
mutuwa idan ka tafi ka bar ni a nan, kar ka tafi ka bar ni" Kallonta kawai khalil
yake, dai dai nan Fure ta turo kai cikin Bukkar rike da kwaryan nono da fura, Nihad
ta koma gefensa da sauri ta zauna, Fure ta durkusa gabansa ta ajiye fura da nonon
tana kallonsa tace "Kana son sukari?" Khalil yace "Kadan" Mikewa tayi ta nufi kofa
xata fita, khalil ya bi ta da kallo, Nihad ta kallesa, sannan ta kalli yarinyar har
ta fita, Khalil tankwashe kafarsa yana kallon fura da nonon dake cikin kwarya a
gabansa, muryar Nihad ya ji kamar daga sama tace "Kanwarka ce?" Ya ɗan kalleta, sai
kuma yace "Aa, er makotanmu ce, Baabarta ai ta shigo kun gaisa jiya" Sai ga fure ta
shigo rike da sugar a hannunta, durkusawa tayi gaban Khalil tana murmushi ta juye
sugar din a kwaryan nonon, ta ɗan kallesa tace "In dama maka?" Ya gyada mata kai
yace "Ehh" Nihad dake kallonta ta mike tace "Bar shi xan yi" Fure ta kalleta sai
kuma ta mike tace "Toh" Kallonta kawai khalil yake babu yabo babu fallasa ta dawo
gabansa ta durkusa ta dau ludayi ta saka cikin kwaryan, Fure ta mike ta fita, Nihad
na kiciniyar dama fura da nonon kwaryan ya kife duk suka malale a kasa, da mamaki
Khalil da ya koma baya yake kallonta, kana ganinta kasan bata ta6a dama fura da
nono ba, ta turo baki ta mike ta bar wajen ta koma can karshen gadon kara ta zauna
tana kallon mess din da tayi a kasa, khalil yace "Na kara sati daya a kan satin da
nace xa ki yi a nan" da sauri ta mike ta nufosa ta fashe da kuka tace "Wallahi ba
da gangan nayi ba, kwa6ewa yayi a hannuna" Ya hade rai yace "Da baki iya ba me yasa
baki bar warce ta iya ba tayi" Tana goge hawayen idonta tace "Toh meye xata wani zo
tana ma mutane yauki kamar kubewa a nan?" Mikewa khalil yayi yace "Ni dai na gaya
maki, ki shirya kwana sha biyu nan gaba a nan" Nihad na kuka ta riko rigarsa da
sauri ganin xae fita cikin rawan murya tace "Don Allah kayi hakuri, idan na kara ko
kwana daya a kauyen nan yunwa xae iya kashe ni" Ya janye rigarsa daga hannunsa ya
fice daga bukkar, Nihad ta sulale kan inda ya tashi tana kuka a hankali. Goge
idonta tayi da sauri jin ana sallama, ta kalli matan da suka fara tururuwan xuwa
kofar Bukkar da take don gaisheta, da murmushi take amsa masu gaisuwar tasu cike da
karfin hali don yunwa ba na wasa ba take ji, tunda take bata ta6a jin irin wannan
kalan yunwan da take ji ba, wata mata ta shigo ta kwashe kasar dai dai inda fura da
nono ya xuba ta fita da shi, Nihad ta bi ta da kallo, to ko kiwon dabba ake yi ai a
tunaninta ba a kiwonsa a ordinary sand balle mutum, ko kaji ma ana shimfida masu
kwali.... Nan ko ga kasa kiri kiri a daki kamar a kofar gida, Gwaggo ce ta shigo
daga karshe rike da kwanon dumamen tuwo ta ajiye mata tace "Hannu Ummi, an tashi
qlau dai ko?" Nihad na Murmushin karfin hali tace "Ina kwana Mama" Gwaggo tace
"Lafiya lau, ga tuwo ki ci kafin kiyi wanka, ko dai kina son yajin daddawa a kawo
maki da man shanu" Da sauri Nihad tace "Aa nagode xan ci haka" Gwaggo tace "Toh,
Don naga jiya ma kamar baki wani ci tuwon ba, wannan na barbada maki me tauraro a
kai, xaki ji dadinsa, kinsan ku yan birni baku amfani da manda a girki" Nihad dai
sai ka rantse tallan close up take yanda take murmushin karfin hali tana kallon
tsohuwar, Gwaggo tace "Ko a damo maki hurar ki hada da tuwon naga faro faron ma
baki sha ba" Nihad ta girgiza kai tace "Aa wannan ya isa mama, nagode" Gwaggwo tace
"Idan kin gama ci sai ki fito an kai maki ruwan wanka" Nihad tace "Toh" Bayan
fitarta da kamar minti sha biyar Nihad ta mike ta fita tsakar gida, haka duk matan
gidan dake shirin surfe suka bi ta da kallo, Gwaggwo ta taso tace "Har kin cinye"
Nihad tace "Ina son xan yi wanka" Gwaggo ta rakata xuwa bandakin ta bude mata kofar
karan tace "Ga ruwan a ciki" Nihad ta saka kai ta shiga ciki, bayan matar ta bar
wajen kawai ta fashe da kuka, yau ita ke ganin rayuwa haka, yanzu a haka xata yi
wankan?? A daddafe ta watsa ruwa tana rike numfashi sbda uban zarnin da wajen ke yi
ta fito da sauri, har ta shiga bukka kallonta matan tsakar gidan suke, ko mai Nihad
bata shafa ba ta saka kayanta ta xauna gefen gadon kara jiki a sanyaye tana bin
kudajen dake ta shawagi a dakin da kallo, Sai kuma ta hade kai da gwiwa ta fara
shesshekar kuka tana jin kamar Ulcer xai iya kamata at anytime. Har rana bata ga
Khalil ba, aka kawo mata gwaza da mai da gishiri, da farko tayi xaton doya ce amma
bayan warce ta kawo mata ta fita, ta dauka tana kare masa kallo kafin ta 6are ta
kai baki a hankali, da sauri ta fito da shi tana yamutse fuska, a haka ta matsar da
kwanon a inda kwanon tuwo da faro faro suke tayi tagumi, cike da tausayin kanta.
Kusan karfe hudu saura Gwaggo ta leko bukkar tace "Ke baki fitowa shan iska Ummi,
ai da xafi dakin..." Nihad ta girgiza kai a hankali tana mata murmushin karfin
hali, alamar bata son ta fitowa, Gwaggo ta kyaleta ta tafi ta ci gaba da abinda
take, duk motsin da xata ji sai ta leka ko Khalil ne amma sai taga ba shi bane, a
haka har ta fita taje tayi alwala ta dawo tayi la'asar, xuwa lkcn jikinta rawa yake
saboda yunwa, she is very very hungry, amma babu abinda xata iya ci cikin abubuwan
da aka kawo mata, kukan ma ta gaji da yin sa yanxu ta daina, tana idar da sallah ta
kwanta saman gadon karan tana juye juye, daga karshe ta mike ta sauko kasa jikinta
na rawa ta bude farau faron dake kulle ta dauka, runtse ido tayi cike da karfin
hali ta kai bakinta kan kwanon ta rike breathing dinta sannan ta hau kwankwada,
ajiye kwanon tayi da sauri bayan ta kwankwadi kusan rabi, saboda wani amai da taji
ya taho mata, ta mike da gudu ta fita daga dakin, gwaggo da matan tsakar gidan dake
surfe suka taso da sauri suna tambayarta lafiya, nan ta dinga kwararar masu aman
abinda ta sha kamar xata shide, Gwaggo da duk ta rude tace "Subhanallahi, me ya
sameki, gashi baya nan" Wata mata ta kawo ruwa da sauri suka ba Nihad dake maida
numfashi, amsan ruwan tayi da kyar ta wanke bakinta duk jikinta na rawa, Gwaggo da
hankalinta yayi mugun tashi ta kawo mata kujerar tsugunno tace "Hannu, zauna nan,
zauna" Nihad ta xauna a hankali kan kujeran tana maida numfashi, Gwaggwo tace "Me
ya sameki kike hararwa haka?" Da kyar tace "Bani da lafiya ne dama" Matan gidan
suka dinga yi mata sannu, ganin yanda jikinta ke rawa Gwaggo ta maida ta cikin
Bukkar tana mata sannu ba adadi, wata yarinya da ta aika ta dubo mata Khalil a waje
ta dawo ta shigo Bukkar tace "Gwaggo bamu gansa ba" Gwaggo tace "Toh bari a mata
jike jike tasha ko xaxxabin xai sauka" Daga haka Gwaggo ta fita, kuka Nihad take a
hankali tana juye
juye tana jin kamar kanta xai fashe don ciwo, bayan wani lokaci sai ga gwaggwo da
kwano ta ajiye kasa ta dago Nihad tace "Ga nan jike jiken sassaken itatuwa na maki,
tashi ki sha, ba daci ba bauri, ba hamami" Nihad ta mike tana rawan sanyi Gwaggwo
ta dauko kwanon ta kai mata baki tace "Ungo sha" Cike da karfin hali Nihad dake ta
kallon cikin kwanon ta kurbi ruwan ciki, Gwaggo tace "Kara sha" Nihad ta runtse ido
ta kara kurba ta hadiye tsikar jikinta na tashi, dacin ruwan kuwa ba a cewa komai,
Gwaggo tace "Yauwa, to koma ki kwanta yanxun nan xaki fara xufa, su ararrabi ne da
sabara da tazargade, ga su nan dai" Nihad ta koma ta kwanta Gwaggwo na kokarin
lullubeta Khalil ya shigo Bukkar ya nufo Nihad yana kallonta, Gwaggwo tace "Wallahi
mugun zazzaɓi ne ya rufeta yanxun nan sai hararwa take" Khalil ya duka yana
kallonta ya kai hannu jikinta wanda yayi zafi kamar wuta, cike da damuwa Gwaggwo
tace "Akwai wani karamin asibiti a gidan Darho, kauyen da xaka wuto kafin ka zo
wannan, ko xaka kai ta a dubata a bata magani ɗan nan?" Khalil yace "Toh xa mu je
can" juyawa tayi ta fita daga Bukkar, Hannu ya kai goshinta duk da idonta a kulle
yake yace "Ina ke maki ciwo" Ta fashe da kuka ta tura hannunsa daga goshinta tace
"Ni ka maida ni gidanmu, idan ba haka ba sai Allah ya kama ka" kallonta ya tsaya
yi, can ya gyada kai ya koma gefe yace "Ohkk" tayi karfin halin mikewa cikin kuka
ta kamo hannunsa tace "Don Allah kayi hakuri ba don halina ba ka maida ni gida"
Yace "Toh ina ke maki ciwo?" Tana shessheka tace "Kai na, kuma ina jin yunwa" Ya
mike yace "Sakko" Da sauri ta mike xaune amma ta kasa tashi daga saman gadon duk
yana kallonta, ya mika mata hannunsa ta rike sannan ta mike tsaye a hankali, dukawa
tayi yana rike da hannunta ta dau Hijab jikinta na rawa ta saka, sannan ta dau
handbag dinta, ko bin ta kan atamfarta na karshe da kayan shafe shafenta bata yi
ba, a haka suka fita daga Bukkar, Gwaggwo da matan gidan suka taso, ana mata sannu
in chorus, Gwaggwo tace "Can asibitin ku ka nufa ko?" Yace "Ehh" Nan dai aka dinga
mata Allah ya sauwake, Fure dake tsaye kusa da wani ɗan mariki da aka daure tace
"Gwaggwo in rakasu asibitin" Da sauri Nihad ta kalleta, murya can kasa Nihad ke
girgiza ma Khalil kai tana cewa "Aa baxa mu je da ita ba" Ya ɗan kalleta ta gefen
ido, Gwaggwo tace "Toh ko kama maka ita ai sai fure ta dinga yi a asibitin ko" Da
sauri Nihad na Murmushi tace "Aa mama xan iya ai" Gwaggwo tace "Toh shkkn, Allah ya
baki lafiya sai kun dawo" Nihad dai bata ce komai ba a ranta kuwa tunani take ina
din xa su dawo da take ce masu sai sun dawo? Dalilin ma da yasa bata son Fure ta bi
su kenan don in sun tafi da ita ai dole su dawo da ita kauyen, ita kuwa bata fatan
abinda xai sake dawowa da ita kauyen nan, suna isa inda Khalil ya ajiye mota ya
saketa ya zaga daya side din, a hankali ta bude front seat din ta shiga, bayan yayi
warming motar ya ja motar, matan gidan da suka taru bakin kofar shiga gidan har da
masu daurin kirji, ga yaransu duk ba wando a tsattsaye su ma, sai daga masu hannu
suke kana ganinsu dai kaga yan kauyen kayau, haka ma sauran makota da suka fiffito
jin karar mota, Nihad ta sauke wani ajiyar xuciya, at long last!!! har taji
xaxxabin ya tafi sai kuma bakar yunwan da take ji, tafiyar minti talatin suka yi ta
ga alamar sun fara shigowa gari, farin ciki gunta ba a cewa komai, bata ta6a
tunanin xata fito daga kauyen can da ranta ba, ta zata sai buzunta, so truly akwai
mutane irin haka a rayuwar nan, akwai mutane dake rayuwarsu cikin kauye haka? lkci
daya jikinta yayi sanyi, and they are leaving happily abunsu babu wani damuwa, ko
pole din wuta ita bata gani a garin ba balle a je ga an ja masu wuta, parking ta ga
khalil yayi dai dai wani pharmacy, duk da bata san inda suke ba amma tasan sun
shigo cikin gari gaba daya, ya kashe motar ya sauka yana kallonta yace "Sauko
malama" A hankali ta bude motar ta sauko ta bi bayansa tana jan kafa saboda jiri da
take gani, suka shiga pharmacy din, bayan sun gaisa da me Pharmacy din ya koma gefe
ya tsaya yana kallon Nihad da ta jingina da kofar pharmacy din bata shigo ba, har
ta rame tayi wani uban duhu kamar ba Nihad ba, Ya kalli me Pharmacy din yace "Ita
ce bata da lafiya" Me Pharmacy din yace "Sannu Hajiya karaso" Tana jan kafa ta tafi
gaban table dinsa ta xauna, Tunda aka haifeta ba a taba kawo su pharmacy idan basu
da lafiya ba, sai dai asibiti, amma wai yau ita ce a pharmacy xa a mata treatment
bata da lafiya instead of hospital, muryar Pharmacist din ne ya dawo da ita duniyar
tunanin da ta tafi, ta sauke idonta kasa a hankali tace "Zazzaɓi nake ji da ciwon
kai" Yace "Kina amai ne?" Ta gyada masa kai tace "Ehh nayi daxu" Yace "Ohk" Kallon
khalil yayi yace "Xa a maganunguna da allurai...." Khalil ya rungume hannunsa yace
"Sai dai magungunan kadai, don kauyen da muke akwai nisa, baxai yiwu mu dinga xuwa
muna komawa ba kullum" Da mugun shock Nihad ta kallesa, bata san sanda ta fashe da
matsanancin kuka tace "Don girman Allah ka rufa min asiri kar ka maida ni garin
nan" Khalil ya danne dariyarsa ya hade rai, Me Pharmacy ya tuntsire da dariya yana
kallon Nihad da duk ta gama rikicewa, Khalil yace "Shi garin namu kike ce ma garin
nan" Ta hade hannunta cikin kuka tace "Ka rufa min asiri mu wuce gida don Allah"
Khalil ya kalli me pharmacy yace "Malam ba mu maganin kawai, hanyar kauyen ba shi
da dadin tafiya da daddare, kaga magariba ya kusa" Kuka kawai Nihad take hankali
tashe tana kallon khalil, me pharmacy dai ya basu magunguna ya sa a leda ya mika ma
khalil yace "Duk prescriptions din na jiki" Khalil ya amsa yace "Nawa ne?" Me
pharmacy din ya gaya masa ya zaro kudin a aljihu ya mika masa, Yana kallon Nihad ya
daure fuska yace "Tashi mu je" Ta mike tana kuka tace "Kayi min rai kar ka sake
maida ni garin nan wallahi baxan iya xama ba kilan ma in mutu" Khalil yace "Fita mu
je" Fita tayi daga pharmacy din ya bi bayanta, tayi mugun ba me pharmacy din dariya
don sai kallonta yake, ta tafi gun mota tana kuka kamar an aikota ba tare da ta
damu da mutanen dake kallonta a wajen ba, bude mata back seat yayi yace "Shiga inda
kika fi jin dadin zama ki xage mutane kiyi masu rashin kunya...." Ta shiga bayan
motar tana kuka kamar ranta xai fita, ya ajiye mata ledan maganinta ya koma driver
seat ya ja motar suka bar wajen..... Wani eatry Khalil yayi parking ya kashe motar
bayan ya ɗan sauke glass ya sauka sannan yayi locking motar, ita dai kuka kawai
take don har ta saka a ranta cewar in har taga sun nufi hanyar kauyen nan to suma
kawai xata yi a cikin motar kuma duk abinda xa ayi mata baxata farfado ba, ba a dau
lkci sosai ba ya dawo rike da ledan take away, ya ajiye a back seat sannan ya shiga
mazaunin driver yana kallonta ta madubi yace "Bari a kai ki inda xa ki yi wanka
kafin mu koma, don naga babu wajen wanka a garin" daga haka yayi reverse suka bar
haraban eatry din, Rokonsa Nihad ta dinga yi hankali tashe tana cewa ya rufa mata
asiri su koma gida amma bai tanka ta ba, a wani hotel taga ya shiga yayi parking,
tsaf ta gane hotel din don sun ta6a xuwa da su Husnah, yanxu da gaske wankan xata
yi su koma wannan kauyen?? yana parking ya sauka ya kulle motar ya bude side dinta
fuska daure yace "Sauko malama" A hankali ta sauko daga motar, ya dau ledan
maganinta da abinci, yana gaba tana biye da shi suka shiga reception din hotel din,
ya gaisa da masu aiki a nan, makulli kawai ya amsa alamar dai ya kama dakin
tuntuni, ganin yayi hanyar stairs ta bi bayansa tana ji kamar iska xai kadata ta
fadi, ya bude dakin ya shiga ita ma ta shiga sannan ya kulle kofar, bin dakin take
yi da kallo, taga tray me dauke da kayan shayi da cup din shayi alamar an sha
shayi, ya kunna wutan dakin ya sauke curtains sannan ya shiga bandaki, tana jin
alamar wanka yake yi ta zamo kasa a hankali ta zauna ta jawo ledan abincin da ya
ajiye ta bude, fried rice da yaji liver hade da spicy jollof rice a gefe ta gani,
sai peppered chicken, tayi unwrapping cokalin daga tissue dake jiki, har wani rawa
jikinta yake ta fara cin abincin, Nihad da bata wani cin abinci sai gata ta cinye
abincin nan tasss naman kawai ta ci kadan ta bari don ita cin nama aiki ne a
wajenta, kai ta yage yage kana bata baki da maiko, ta bude chilled chivita dake
leda shi ma kadan ta sha sannan ta ajiye, Sai a sannan ta fara gani dai dai ta
daina jin jirin da take ji, fitowa khalil yayi daga bandaki ya dinga kallonta da
mamaki, can yace "Amma wa yace maki naki ne da kika dauka kika ci?" Ko kallonsa
bata yi ba balle ya sa ran amsa, sai kuma ta mike ta wuce ta gabansa ta tafi jikin
window tana kallon waje da motocin dake ta tafiya saman titi, waii lallai ta
jinjina ma yan kauye, Allah Ubangiji ya kawo masu mafita. Tana jin ya fita daga
dakin ta juyo a hankali ta dawo gefen gado ta zauna tana tunanin irin rayuwar da
tayi na kwana biyu kacal, ita kanta tasan ta rame kuma ta yi baki, tashi tayi daga
karshe ta shiga bandaki tayi wanka ta dauro alwala ta fito, tana sallan Magrib,
banda Aliyu babu wanda ke ranta, ta mike a hankali ta tafi kofar dakin ta murda
taji a kulle, dawowa tayi ta fada saman gado ta lumshe ido, nan da nan bacci ya
dauketa......

*Nihad* is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via👇🏻

✍🏻
07087865788
Assalamu alaikum er uwa, kina neman organic Supplement irin masu gyaran jiki ciki
da waje? Ko kuma mai fitar Maki da duk wani infection komai nacinsa? Sannan mai
maido Maki martabar fatarki? Ko kina fama da dry HQ? Ko hips ne matsalarki da
boobs? To kwantar da hankalinki *GHT Organic supplement care gat ur back*

Domin karin bayani ki tuntubi wannan number 👇🏻

✍🏻
+2347057607751
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

30

Ganin Nihal taki tanka ta sai kuka take, Nihad ta mike da sauri ta koma cikin gidan
zata kira Khalil, a bakin kofa ta kusa buge sa ya turata tayi baya xata fadi ganin
hakan yayi saurin jawota ta fado chest dinsa, ta zaro ido ta daga kai tana
kallonsa, ba tare da ya kalleta ba ya turata gefe ya sauka xuwa wajen Nihal, bin sa
tayi da kallo, yana isa wajen ya durkusa gabanta a hankali yace "Ki yi hakuri
Nihal, don't take all what she said personal" tana goge hawayen da ya ki tsaya mata
tace "Ka bude min gate in tafi gida" Yace "Ba amfani hakurin da nake baki kenan?"
ta girgiza masa kai kawai, yace "Now, Behave like the good girl u always are, tashi
mu koma ciki" Daga haka ya mike, ita ma ta tashi tana ci gaba da goge idonta, yana
gaba tana bin sa har xuwa parlon, Nihad ta riga su shiga parlon kafin su karaso,
bayan sun shigo tana kallon Nihal a hankali tace "Kiyi hakuri plss, i didn't mean
it" Nihal dai bata ce mata komai ba ta yi wucewarta daki, Nihad ta jefa ma Khalil
wani kallo tace "Ai dai kaga abinda ka jawo, kawai ka sa yarinya a gaba kana koya
mata gulma da munafurci alhalin ba halinta bane" Daga kai yayi ya kalleta, speaking
calmly yace "Idan kina ci gaba da min rashin tarbiya, Billah xan tattara ki in
mayar da ke kauyen can" Shiru tayi tana kallonsa, sai kuma ta 6ata fuska tace "Toh
ni nace wani abu ne?" Bai sake kallonta ba, ta turo baki ta juya ta koma dakinta.
Har Nihad ta gama shirin bacci Nihal bata ce mata komai ba, Nihad ta gama saka
kayan baccinta wanda shi kadai ta tsira da shi a gidan ta dawo gefen Nihal da
damuwa tace "Shine ina ta maki magana kin ki cewa komai ko?" Nihal ta daga ido ta
kalleta tace "Me kike son in ce maki?" Nihad tace "Wallahi kema kinsan i didn't
mean it, you know i love u to the extent that i will never hurt you" Nihal ta ɗan
yi murmushi tace "Amma duk kwanan nan jaraba kike min a waya ai" Nihad ta
marairaice tace "Toh me yasa xaki dinga magana da worst enemy dina a waya? Yanxu da
Amina ce ke waya da shi ko wasu can daban ai ni baxan damu ba, amma ke fa kinsan i
Cherish u so much, why will u be communicating with my worst enemy?" Nihal tace
"Toh shikenan, na maki alƙawarin baxan sake waya da shi ba, dama yawanci ina ce
masa ya kai maki waya ne...." Nihad tace "No, just block him kawai" Nihal tace "If
that will please u" Tana fadin haka ta dauko wayarta tayi blocking number Khalil
sanan tayi deleting number daga wayar tana kallon Nihad tace "Done!!" Nihad tayi
Murmushi tace "Kin hakura yanxu?" Nihal tace "On one condition" Nihad na kallonta
tace "Ina jin ki" Nihal tace "Ki tashi ki tafi dakinsa" da mamaki Nihad ke
kallonta, can tace "Amma ina ga baki da hankali, inje dakinsa inyi masa me? So now
u are keeping it in mind cewar mijina ne shi da har xa ki ce in je dakinsa? Why
will u leave such thought a xuciyarki idan har ke masoyiyata ce?" Nihal bata ce
mata komai ba ta ja bargo ta lumshe ido, Nihad ta ja tsaki ta mike ta koma can edge
din gadon, ta fi minti sha biyar zaune kafin daga karshe ta mike fuskarta daure
tana kallon Nihal tace "If that will please you shikenan" Daga haka ta dau Hijab
dinta ta fice daga dakin kamar xata tashi sama, bayan ta saka hijab dinta ta kunna
wutan corridor din tana kallon kofar dakinsa, can ta kyabe baki a ranta tace ba
gwara taje parlor ta kwanta abunta kawai, kashe wutan tayi ta karasa cikin parlon
tana tafiya a hankali sbda duhu, laluban dogon kujeran da xata kwanta ta shiga yi
bayan ta shigo tsakiyar parlon, a tsorace ta koma baya rana zaro ido bayan
lalubenta ya kai ta har jikinsa, ya mike zaune yana haskata da karamar wayarsa,
kunya taji ya kamata ta juya tana sosa kai xata bar wajen, yace "Da wani abun da
kike so ne???" Ta juyo duk da bata ganin fuskarsa sbda haskata da yayi ta daure
fuska tace "Wani abu kamar me?" Yace "Kin fi ni sani ai tunda kika biyo ni nan kina
tattaba ni" Tsayawa tayi tana kallonsa kamar me son fahimtar abinda yake nufi, can
tace "Kai kasan abinda kake nufi ni ban sani ba" yace "Aa ki dai fada abinda kike
so" a takaice tace "Abinda ke ranka shi nake so" daga haka ta xabga masa harara
xata bar wajen ya fixgota ta fado gefensa, a tsorace tace "Don Allah kayi hakuri
wallahi kwanciya na zo in yi, ni ba wajen ka na zo ba" Cikin husky voice dinsa yace
"Duk dakinki babu wajen kwanciya sai kin fito parlor?" Ta boye fuskarta a huge
muscles dinsa tace "Nihal ce tace idan ina son ta hakura sai na je dakinka, to ni
kuma ina son ta hakura" kallonta kawai yake yana kara tabbatar da ainahin
childishness dinta, Wani sanyayyen kamshi ke tashi a jikinta har gashin kanta, lkci
daya kuma ya hade rai ya saketa, ta dago kai a hankali tana kallonsa, matsawa yayi
daga kusa da ita ya koma daya side din kujeran, With full audacity tace "Xan shiga
dakinka in kwanta kuma kar ka sake ka shigo har sai na fito" Bai tanka ta ba, ita
ma bata jira yace komai ba ta mike ta nufi dakinsa, murda kofar dakin tayi ta shiga
tana bin ko ina da kallo, wani kamshi ke tashi a dakin, ta kalli jakarsa dake dakin
ta juya ta kalli kofa, tana ta tsaye tana kallon kofar sai kuma ta nufi jakar ta
tsugunna ta bude zip din, Chargern Iphone ta fara cin karo da, ta dinga kallon
chargern tana jujjuyawa, wannan kuma na waye? Ko dai na Nihal ne? Tabe baki tayi ta
ajiye, ta maida idonta kan Diary Milk chocolate masu uban yawa a jakar, kai....a
ina ya samu kudin siyan wannan uban chocolate din, ko da yake kudin babanta ne,
wato saboda samun waje har da su siyan chocolate, wani hoto ta gani ta dauka tana
kallon matar da ke jikin hoton warce baxata wuce shekaru 54 ba, kana ganinta kaga
halfcast, keenly Nihad ke kallon hoton tana ji a jikinta kamar ta ta6a ganin wannan
matar, amma a ina?? Duk yanda ta so tunawa ta kasa, as in, she k6s sure ta ta6a
ganin hotonta but where?? Bude kofar dakin aka yi ta mike a rikice, da sauri ya
nufota ya warce hoton daga hannunta ya hadeta da bango yana mata wani mugun kallo
lkci daya kamanninsa suka sauya, Sosai ta tsorata jikinta na rawa tace "A bude fa
naga jakar xan...." Turata yayi har sai da ta fadi kasa rigijib, ya dau jakar gaba
daya ya fice daga dakin. Da safe karfe tara saura khalil na zaune parlor Nihal ta
fito, ta tsaya jikin kujera ta gaishesa ya amsa yace "How was ur night?" Tace
"Alhamdulillah, Nihad bata tashi ba har yanxu?" Duk da tun jiya da daddare rabonsa
da dakin bayan ya fita amma haka yace "Probably" Tace "Ohk, ni xan tafi" Yace "Ina
za ki tafi?" Ta sunkuyar da kanta tace "Umma ta aikeni gidan wata frnd dinta in
amsar mata sako, so karfe tara matar ke fita aiki, shine tace in je kafin tara"
Khalil yace "But baki yi breakfast ba ai" Tace "Na tashi da azumi yau" Shiru yayi
yana kallonta tace "Idan ta tashi kace mata naje amsar ma Umma sako" Yace "Toh mu
je in ajiye ki" Da sauri tace "Aa ba fa nisa, kuma in sha Allah xan dawo anjima"
Yace "Are you sure?" Tace "Sure" Yace "Toh Allah ya tsare" Tace "Ameen" Daga haka
ta nufi kofa ta fita. Goma saura Khalil ya tashi ya shiga dakinsa don wanka yake
son yi kuma yaga bata da niyyar fitowa, kwance ya sameta a kasa, ya tsaya bakin
kofa yana kallonta, ta mike xaune cikin rawar tace "Ba shkkn ba hankalinka ya
kwanta kafana na min ciwo yanzu" Kallon kafar yayi, kafin ya karasa kusa da ita ya
durkusa ya daga kafar, ta sakar masa kuka ta janye, hade rai yayi yana kallonta sai
kuma ya sake jawo kafar, ihu ta kwala tace "Wallahi ciwo yake min" Targade ya ga
tayi a kafar, ya mike ya fita daga dakin ta bi sa da kallo, da kyar ta iya daurewa
ta shiga bandaki da asuba ta wanke bakinta da mouth wash ta dauro alwala ta fito
tayi sallah, kamar kar ta ɗan motsa xuwa bandakin shine kafar yayi mata tsami kafin
gari ya waye, dawowa dakin yayi ta daga kai tana kallonsa, ya karaso gabanta ya
durkusa ya bude man zafin hannunsa, ita dai kallonsa kawai take, bayan ya debi man
zafin ya kamo kafarta, zaro ido tayi tana kokarin janye hannunsa a kafarta ya daure
fuska yace "Kar ki sake ta6a ni Malama" yana gama fadin haka ya fara ja mata kafar
yana kokarin gyara mata targaden, ai bata san sanda ta yunkuro ta rirrikesa ba tana
kukan azaba tace "Nashiga uku Abba" Bai sarara mata ba har sai da ya tabbatar kafar
ta dawo dai dai, kuka kawai take ta kankamesa duk ta hada zufar wahala, bayan ya
sakar mata kafa shi ma ta sakesa tana komawa baya, kallonta kawai yake, ta turo
baki tana share idonta, yace "Sallan asuban ma yafe maki aka yi sbda kinyi targade
ko" Ta hade rai tana kallonsa tace "Ai ni ba kafura bace" Bai ce mata komai ba ya
mike ya nufi kofa, da sauri tace "Ka kira min Nihal plss" yace "Warce kika kora ko
wacce?" daga haka ya fita dakin, a hankali ta lallaba ta mike ta hau saman gadon ta
kwanta tayi lamo a saman pillow, wato tafiya Nihal tayi upon all her pleas. Kafin
azahar Nihad taji tana iya taka kafar, a hankali take dingishin ta fito daga dakin,
ta shiga nata dakin, kallon katon ledan dake saman gado ta dinga yi, kafin ta
karasa ta bude ledan, abaya ta gani masu ɗan karan tsada sun kusa kala goma, da
mamaki ta dinga kallonsu tana warwaresu, sannan ga undies da cream din shafawa da
turarurruka duk a cikin katon ledan, da sauri ta fito parlor tana kallonsa tace "A
ina ka samu kudi ka siya min abayan nan?" Ya kalleta a takaice yace "Kudin babanki
mana" Nihad tace "To amma wa ya zabo abayan?" Yace "Ni ɗan aike ne, kasuwa kawai
aka aike ni naje na amso" Ta kyabe baki tace "I thought as much" Daga haka ta juya
ya bi ta da kallo har ta shiga daki, wani Murmushi yayi ya maida idonsa kan tv da
yake kallo. Bayan ta yi wanka ta shirya cikin daya daga abayan, sosai yayi mata
kyau ya amshi fatarta, ba laifi haskenta ya fara dawowa amma ramar na nan, ta fito
parlor, kallo daya yayi mata ya dauke idonsa, ta wuce kitchen sauran abincin da
Nihal ta dafa daren jiya ta kara dumamawa ta xuba ta koma daki ta ci, har kusan
la'asar Nihad na ta xuba ido taga ko Umma xata zo yau din ko sai gobe, amma bata zo
ba, wajen karfe biyar ya bude kofar dakinta yace "Ki sameni a mota" Da ido ta bi sa
har ya bar wajen, sai kuma ta mike
ta dau mayafinta ta bi bayansa, duk da yana cikin motar ta ki shiga, she can't
take that risk anymore, tana kallonsa da kyau tace "Ina za mu je?" Yace "Gidanku"
Ta ɗan yi jim, sai kuma dai ta shiga bayan motar ta kulle, suna barin gida taga sun
dau hanyar gida, ta ma rasa ko farin ciki xata yi ko akasin hka, the only good
thing of going to that house is that xata ga Umma bayan nan ita bata marmarin ma
zuwa gidan.... Sai da suka kusa yace "Ki bude kunnuwanki ki saurareni da kyau, zan
kai ki gida ba don komai ba sai don ki gaida mahaifiyarki da bata da lafiya, idan
Abba na nan shi ma ki gaishesa, bayan haka xa mu fito daga gidan..." Da mamaki
Nihad tace "Kana nufin sai in shiga har gidanmu in fito ban je bangaren Umma na
gaidata ba??" Dai dai nan suka shigo layin, yana kallonta da kyau ta madubi yace
"Ba don ki je bangarenta ki gaidata na kawoki gidan ba, a duk inda kika hadu da ita
a nan xaki gaisheta babu xancen xuwa ɓangarenta, idan kuwa kika ce baxa ki bi
umarnina ba, Billah na maki alƙawarin muna fitowa daga gidan xan maida ke garinmu
da zama na har abada" Shiru Nihad tayi bata ce komai ba, bayan yayi parking yace
"Kin ji ko baki ji ba?" Ta hade rai tace "Na ji" Bude motar yayi ya sauka ita ma ta
sauka fuska daure, har sannan dingishi take, Aminu kamar xai goya Khalil tsabar
farin cikin ganinsa, Nihad ta kara tsuke fuska ko kallonsa bata yi ba ta shige
cikin gidan, Aminu yayi kasa da murya yace "Ciwo ta ji a kafar take dingishi?"
Khalil yace "Zan fito yanxun nan" Daga haka ya bi bayan Nihad, Umma ta fito daga
bangarenta kenan ganin Nihad ta hau tafa hannu tana cewa "Oyoyo oyoyo" Nihad ta ɗan
saci kallon Khalil dake bayanta yana kallonta, ta sunkuyar da kai a hankali tace
"Umma ina yini" Umma tace "Karaso mu shiga ciki daughter" Nihad tayi karfin halin
cewa "Xan shiga wajen Mumy ne tukunna" Umma ta saki baki tana kallonta, tuni khalil
yayi part din Mumy, Nihad ta bi bayansa kamar xata yi kuka, haka Umma ta bi su da
kallon mamaki, kai ko makaranta Nihad ta dawo ba wani lallai taje bangaren Mumy ta
gaidata ba, Umma kuwa dama kafin ta fita sai ta shiga ta gaya mata ga inda xata,
haka kuma idan ta dawo, abinda Nihad tayi yanxu sai yayi mugun daure ma Umma kai.
Nihad ta kasa hada ido da Mahaifiyarta bayan sun shiga parlon, Mumy ta amsa
gaisuwar khalil da fara'a, Yace "Ya karfin jikin?" Tace "Alhamdulillah jiki da
sauki" Nihad na wasa da veil dinta tace "Mumy ya jikin?" Mumy dake kallonta tace
"Alhmdlh" cousin din Mumy ce ta fito daga bedroom suka gaisa da khalil cikin
mutuntawa, Nihad dai sae kallonta take, ganin ta juya ta koma daki ba tare da ta bi
ta kanta ba, Nihad ta mike a sanyaye ta bi bayanta, gaisheta tayi, maimakon ta
amsa sai ta hau ta da fada, tace "Ban kara tabbatar da cewa ke mahaukaciya bace
shashasha sai yanxu, ace uwarki ba lafiya tun da kika bar gidan nan amma kika rasa
inda xaki samu wayar kiranta? nan kuwa a duk sanda matar nan Umma ta shigo sai tace
ai kunyi waya, anya kina son gamawa da duniya lafiya kuwa Nihad? Kullum bawan
Allahn nan sae ya shigo gidan nan gaida uwarki amma sbda ke ba yar halaq bace baki
ta6a cewa xaki biyosa ki duba jikinta ba, to duniya ce dai wanda bai zo ba ma
jiransa take, idan kuma Umma ce tayi nakudarki ta haifeki xa mu ji" Nihad ta zauna
hawaye na sauka idonta tace "Aunty ni tsoro nake ji shi yasa ban kirata ba, kuma
wallahi bai ta6a ce min xai zo nan ba ban biyosa ba" a fusace Aunty Zulai tace "Sai
yace maki xai zo?? Shashasha kawai kin bi kin ja mana abun kunya a duniya wanda har
yanzu kukan wannan mugun abun naki muke, wallahi sai nan gaba xaki yi kukan gaske
da hawayenki a kan wannan video din Nihad, nan gaba xaki san illar da kika ma kanki
a duniya a kan video din nan, kuma yau da ace wannan mijin naki iyayensa da
danginsa yan boko ne ko a cikin gari suke wllh baxa su ta6a bari ya aureki ba ko da
kuwa shi ya ganki yace yana so balle wannan manna masa ke kawai aka yi sbda babanki
ya yaba da hankalinsa, amma da ace ɗan birni ne wllh gori wajen danginsa da yan uwa
ma kawai ya isheki ki hadiye xuciya ki mutu wataran, kina ganin kamar abu ya lafa
ai shkkn an manta, yarinya sai nan gaba xaki gane abinda nake gaya maki ba yanzu
ba, don haka in zaki rungumi mijinki ki bisa ki masa biyayya ki lallaba aurenki, to
gatanki, idan kuwa kin ce ba haka ba kika kuskura kika bari aurenki da bawan Allahn
nan ya samu matsala to idan ba kauyen ubanki xai sake komawa ya samo maki wani
mijin ba ina me tabbatar maki babu wanda xai aureki don ma in gaya maki ki ji da
kyau" kuka kawai Nihad take tana kallonta, Aunty Zulai tace "Shikenan ni abinda xan
gaya maki kenan, tashi ki bani waje" Nihad ta mike tana goge hawayen da ya ki tsaya
mata ta fito parlor kanta a kasa, zaunawa tayi saman Carpet ta dago kai a hankali
ta kalli Mumy taga kallonta take, cikin sanyin murya tace "Mumy ina su Sudais" Mumy
tace "Sun tafi makaranta" Nihad bata kuma cewa komai ba, bayan few minutes Mumy
tace "Kin ga wancan bawan Allahn dake zaune?" Nihad ta daga kai ta kalli Khalil da
Mumy ke nuna mata bata dai ce komai ba, Mumy tace "In har kina son gamawa da ni
lafiya to ki zauna lafiya tare da shi, idan kuwa kince ba haka ba, ba baki na maki
ba amma baxa ki ta6a ganin daidaituwar lamarinka ba, don haka kika kuskura kika
kashe auren nan naki sae dai ki nemi warce ta haifeki ba ni ba" Nihad ta fashe da
kuka sosai tana kallon Mumy, shi dai Khalil bai iya ya daga kai ya kallesu ba, Mumy
ta kallesa tace "Ku gaida gida Ibrahim.... nagode sosai, xan shiga ciki" Yana
kallonta cikin sanyin murya yace "Allah ya kara lafiya" Ta amsa da Ameen ta mike ta
shiga dakinta, kuka kawai Nihad take kamar ranta xai fita a parlon, bayan few
seconds Khalil ya mike ya fita daga parlon, mikewa ita ma tayi tana kuka ta bi
bayansa.

*Nihad* is 500 via 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah

And u show ur evidence via👇🏻

07087865788

Assalamu alaikum er uwa, kina neman organic Supplement irin masu gyaran jiki ciki
da waje? Ko kuma mai fitar Maki da duk wani infection komai nacinsa? Sannan mai
maido Maki martabar fatarki? Ko kina fama da dry HQ? Ko hips ne matsalarki da
boobs? To kwantar da hankalinki *GHT Organic supplement care gat ur back*

Domin karin bayani ki tuntubi wannan number 👇🏻


✍🏻
+2347057607751
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

31

*Masu forwarding min novels daga nayi posting to other groups su sani hakkina bazai
ta6a barinsu ba don good 4 hours nake using wajen ganin na hada just 1 page, babu
ruwana da wai mutum daya ya siya a group sai ya tura ma saura tunda ni ba er iska
bace ban yarda da wnn iskancin ba, duk me yin hakan taje ita da Allah, kuma Allah
zai saka min, dama ɗ'an abinda mutum ke rainawa yake maida shi ba komai ba bai san
shine doom dinsa ba a rayuwa, wani ba wai bai da 500 din biya ba, kawai kyashi ne
baxai barsa ba amma ya iya karatu ya ji dadi, sannan masu min posting a facebook
suma su da ALLAH!!!* Na gaji da zuba maku ido kuma haka.

Suna fitowa parlor Nihad na kallon khalil cikin kuka tace "Don Allah ni ka barni in
je in gaida Umma" Juyowa yayi yana kallonta yace "Akwai wata Umma bayan warce kike
gaida da muka shigo daxu?" Muryarta na rawa tace "Toh kawai a parlor xan gaisheta?"
Yace "Eh" Kuka kawai take tana kallonsa ta wuce sa kamar xata tashi sama ta nufi
kofar fita parlon, bin bayanta yayi ya sameta jikin mota tana kuka kamar ranta xai
fita, ya zaga driver seat ya bude ya shiga, bude bayan motar tayi ta shiga don ita
har yanzu Drivern gidansu ne shi, Aminu ya marairaice bayan Khalil ya fito da mota
waje yace "Ina ta rokon Saminu ya jira min gate in kawo maka ziyara amma ya ki..."
Khalil na kallonsa yace "Wataran ma baxa kayi gadin ba gaba daya, sannan matsayinka
xai dawo dai dai da na kowa a duniya" Aminu ya daga hannu biyu sama yace "Allah
Ubangiji ya amsa bakinka, Allah ya dubemu yanda ya dubeka lkci daya, wannan
gagarumin ci gaban da ka samu Allah ya sa mu a danshinka, wayyo wa yaga Aminu ya
daina gadi, duk basur ya cinye ni sbda zama kan benchi daga safe har dare, na ma ji
Alhaji yace xa a dubo sabon driver tunda kai yanxu ai ba batun tuki kuma" Murmushi
kawai khalil yayi ya sa hannu a aljihu ya ciro dubu daya ya mika masa yace "Ga
wannan ka sha kankana" Aminu ya karba hannu bibbiyu yana cewa "Allah ya taimakeka
oga" Wani shegen kallo Nihad ke ma daga Khalil din har Aminu tana jin kamar ta
hadiye zuciya don takaici, nan ta kara jin wani sabon tsanar Khalil ya dirar mata,
wato fafa yake yi sbda Abba ya aura masa ita, ji yake babu ya shi a duniya, Bayan
sun bar layin tana kallonsa ta madubi tace "Kai yanzu kawai jin kanka kake saboda
Abbana ya daukeni ya aura maka ko? Gani kake ka fi kowa sa'a a duniya tunda yanxu
kudin da Abbana ke baka ya ninku linkin ba linkin har da su kyautar dubu daya,
shkkn xaka dinga amfani da ni kana cin kudin Abbana" Khalil yayi wani murmushi bai
tanka ta ba, ta murguda baki tace "Ai shi dama talaka bai iya samun waje ba, nasan
yanxu alfahari kake yau gani matarka ko?" Yace "Ohk" Ta kara murguda baki bata kuma
ce masa komai ba har suka isa gida, sauka tayi daga motar bayan ya bude gate tayi
shigewarta ciki kamar xata tashi ciki, yayi wani murmushi kawai ya motar ya shigar
da shi compound din. Bayan Nihad ta idar da magrib ta fito parlor ta samesa kwance
saman dogon kujera yana waya, ganin bai lura da fitowarta ba duka a hankali ta
rarrafa har bayan kujeran ta kasa kunne tana sauraron wayar da yake yi, A hankali
taji yace "Nan da wata daya in sha Allah xan dawo, idan kuma na dawo baxan sake
fita ba sai bayan aurenmu" Yana fadin haka babu sunan da ya fado ran Nihad sai
Nadeeyah don har ta haddace sunan nata a xuciyarta, ta ɗan kyabe baki tana tsugunne
bayan kujeran tana kara kasa kunne, Taji yace "Aa, akwai dalilin da ya sa na dade
wannan karan Nadeeyah, ba wai da son raina bane, amma in sha Allah na kusa gama
abinda nake yi, ni kaina na gaji da USA haka" Buda baki Nihad tayi hangangan jin
sunan kasar da ya kira, Tunda aka haifeta bata ta6a ganin me lafta karya kamar
wannan mutumin ba, wato USA?? Mutumin da ko ruwa ta kasa sha a garinsu balle ta ci
abinci shine yake karyan yana USA, ya ma san full meaning din USA din kuwa?? Taji
yayi dariya ya mike zaune yace "Wai da gaske??" Magana yake amma bin parlon kawai
yake da idanuwansa don banda kamshin Nihad babu abinda yake ji a parlon, amma kuma
bai ga alamarta ba, don haka ya koma ya kwanta a hankali yace "Ke ce farko kece
karshe Nadeeyah, in sha Allah baxan hada ki da kowace mace ba, don kin min hallacin
da baxan manta ba, in dai kuma ba baturiya kike son in auro mu dawo Naija tare in
hada ku gida daya ku zauna ba, kinga ai nasan baxa kiyi kishiya da ita ba" bayan
few seconds yayi murmushi yace "Ya na ji kin yi shiru?" Mikewa Nihad tayi tana tafe
hannu tace "Ni wallahi ban ta6a ganin inda babba yake karya ba sai kai..." tuni
Khalil ya katse wayar, ya mike tsaye yana kallonta, da mamaki Nihad tace "Kasan
ma'anar USA kuwa? Kasan ina ne Usa? Me yasa baka tsoron yin karya a rayuwarka?"
Yace "Kin karya daya daga sharadinmu don haka nima dole xan karya daya...." Yana
gama fadin haka ya bar parlon ta marairaice ta bi sa da kallo har ya shige dakinsa,
ta fi minti biyar tsaye parlon can dai ta bi bayansa, a hankali ta murda kofar
dakinsa, tsaye ta gansa yana unbuttoning shirt dinsa, ta turo baki tace "Toh kayi
hakuri" Ya juyo ya jefa mata wani kallo yace "Baxan yi" Ta marairaice tace "Don
Allah mana" Bai sake kulata ba ya shige bandaki, ta ɗan kyabe baki, sai kuma ta
dinga kallon wayar tasa dake gefen gado, tana tafiya a hankali kamar munafuka ta
karasa gadon ta dau wayar, number Nadeeyah ta shiga tana kallon number tana ta6e
baki, wai ba ma tayi blocking din number nan ba, wato unblocking yayi, tana dai ta
kallon number, can ta ja tsaki kasa kasa ta kara blocking number tayi deleting ta
ajiye wayar ta fita da sauri. Fitowa Nihad tayi dai dai sanda Khalil ma ya fito
daga dakinsa, ta 6ata fuska tace "To ai cikin deal dinmu baka ce idan ana kwankwasa
gate kai kadai ne xaka dinga xuwa budewa ba, nima xan iya fita in bude tunda ba kai
kadai bane cikin gidan" Ba abinda yace mata ya nufi kofar parlor xai je bude gate
din da ake ta bubbugawa kamar xa a cire, Nihad ta tafi jikin window dake parlon
tana kallonsa har ya isa gate din, Yana tsaye bakin gate din yace "Waye?" A mugun
fusace Umma tace "Uban me tambaya, nace uban me tambaya, halan gidan na ubanka ne
idan ka ji an kwankwasa gate sai ka tambayi waye sannan ka bude?" Kawar Umma dake
gefenta tace "Wai kaddai Dreban ne ke maki wannan tambayar?" Umma tace "Atoh ba
matsiyaci bane? Kuma kin mance matsiyata basu iya samun waje ba?" Hajiya Turai tace
"Aa ga alama" Umma tace "Ai kinsan gidan Ardo ko Nenne dake kauye ne shi yasa yake
tambayar waye" Hajiya Turai ta kwashe da dariya tace "Sai dai haka kam" A mugun
fusace Umma tace "Au, baxa ka bude min gate din ba??" Khalil yace "Me gyara yana
hanya don tun jiya gate din ya samu matsala, mu ma bamu samu fita ba duk yau, don
haka sai ku jira" Buda baki Umma da kawarta suka yi jin abinda yace, shi kam yana
gama fadin haka ya juya ya bar bakin gate din ya koma ciki, Nihad na masa wani
kallo tace "Waye a gate din da kaki budewa?" Yana kallonta da kyau yace "Warce kika
yaudari kanki kika bai ma matsayin mahaifiyarki" Nihad ta zaro ido tace "Umma??
Shine kaki bude mata gate din?" Bata tsaya jin abinda xai ce ba a fusace ta taho
xata fita daga parlon ta je ta bude ya fixgota, tana tsaye dab da shi yana kallonta
da kyau yace "In har kina son mu rabu cikin salama ba tare da iyayenki sun yi fushi
da ke ba ko an ga laifinki to kar ki tsallake umarnina ko daya, datse alqarki da
warce kike kira da Umma yana daga cikin umarnina gare ki, bayan mun rabu xaki iya
ci gaba da mu'amala da ita wannan ba matsalata bace, amma muddin muna tare babu ke
babu ita" Nihad was shocked and lost of words at first, can dai tana girgiza tace
"Amma kasan abinda kake cewa kuwa? Kasan warce kake cewa xaka datse alaqata da
ita?? Kasan wacece Umma kuwa ko dai duk zamanka gidanmu baka san matsayinta ba?
Matar Abbana ce fa? First wife din Abbana ce, She is my step mother, kuma duk
duniya babu wanda ke sona baya ga ita, ban san dai ko Mumy da ta haifeni ba ba
tunda ita bata ta6a nuna min son da take min a fili ba na Umma kawai na sani, Umma
tun tasowata ban ta6a cewa ga abinda nake so a duniya an hanani a gidanmu ba, kome
nake so shi nake samu, yanda Umma taga Abbana ke ji da ni haka ita ma tafi sa ji da
ni, kuma bata ta6a hanani yin duk abinda nake so in yi ba tunda a ɓangarenta ma na
taso, she is 100% in support of me always, ta daukeni kamar er da ta haifa a
cikinta, dai dai da second daya bata ta6a banbanta ni da Nihal ba, don sai taki
goyon bayan Nihal amma ni ta goyi bayana, ba kuma ta son bacin rai na ko na second
daya, yanda na shaku da Umma ko Mahaifiyata ban shaku da ita haka ba wllh, don dama
tun ina karama ta maidoni dakinta, ita ce komai na, amma shine yau xaka bude baki
kace min xaka datse alakata da Umma?? Kana da hankali ma kuwa?" Kallon cikin ido
kawai khalil ke mata, bai kuma ta6a jin tausayin rayuwarta ba sai a wannan lokacin,
Ta fashe da kuka tace "In har a sharadin rabuwar mu har da datse alakata da Umma to
kar mu rabu din, kai xaka wahala ba ni ba" Tana gama fadin haka ta kwace hannunta
daga rikon da yayi mata ta shige dakinta, zaunawa khalil yayi saman kujera deep in
his thought yana sake digesting duk abubuwan da Nihad ta gama fada masa..... Ana
magrib Nihad taji fitar Khalil, tun da rana take kuka duk idanuwanta sun kumbura
saboda ya hana Umma shigowa gidan, tana jin fitarsa ta fito bakin gate din sai taji
ya sa makulli, ji tayi kamar ta kwanta wajen tayi ta birgima, ta dinga rera kuka
kamar ranta xai fita a wajen. Khalil na zaune parlon Abba, ya gaishesa kansa a
kasa, kallonsa kawai Abba yake yana son jin me ke tafe da shi, hoping ba wani abun
Nihad tayi masa ba, Khalil yayi kasa da murya yace "Alhaji dama na zo neman alfarma
ne gun ka" Abba na kallonsa yace "Ina jin ka Ibrahim, fadi koma meye kanka tsaye"
Khalil yace "Ina son xan koma garin mahaifiyata can Zaria tare da ita... Saboda xan
ɗan yi noma a can tunda damuna ya fadi" Abba yace "Yanzu ai karkashin ikon ka take
Ibrahim, ba sai ka tambayeni izini ba don xaka canza wajen zama da ita, iyaka ka
sanar min don in maku fatan alkhairi sannan idan da tallafawan da xan maku sai a
maku" Khalil dai ya sunkuyar da kansa, Abba yace "Maa sha Allah naji dadin noma da
kace zaka yi, don noma ai shine tushen arziki dama, Allah Ubangiji ya baka nasara
Ibrahim" Khalil yace "Ameen Alhaji, nagode" Abba yace "Yanzu dai ka sa a bincika
maka nawa ake bada hayan gida a garin" Khalil yace "Ina da wani aboki a can na
tambayesa jiya" Abba yace "Nawa yace maka?" Khalil yace "Dubu dari yace min"
Kallonsa Abba yake ba ko kiftawa, can yace "Aa da dai a samo na sama da hakan
Ibrahim, ni ko nawa ne ba matsala bane xan bada" Khalil na kallon Abba yace "Gidan
a kusa da kauyen da
xan yi noman yake, shi sa nace xan amsa" Abba yace "Dubu dari nawa kace?" Khalil
yace "Dubu dari daya" Abba ya kasa cewa komai yana kallonsa, Gaba daya tunaninsa na
kan Nihad duk da haushinta da yake kwana yake tashi da shi a ransa yasan baxai ta6a
son ta zama uncomfortable a rayuwarta ba, deep down him yasan he still love his
daughter" Abba ya sauke boyayyen ajiyar xuciya yace "Shikenan zan sa maka kudin"
Khalil yayi noticing change a muryar Abba hakan ya sa bai dago kansa ba, Abba yayi
breaking few second silence da ya biyo baya yace "Yaushe xa ku tafi?" Khalil yace
"Ko zuwa satin da xa mu shiga in sha Allah" Abba yace "Ohk to amma ka sa abokin
naka ya ɗan bincika min ko za a samu filaye a nan arean" Khalil ya daga kai ya
kalli Abba yace "Toh Alhaji" Abba yace "Ina sauraronka zuwa gobe da safe" Khalil
yace "Toh in sha Allah" Daga haka yayi ma Abba sallama ya mike ya fita, ɗan
murmushi yayi kawai ya fice daga main parlor. Yana fita parlon Umma ta shigo da
sallama, bayan ta zauna tace "Bako kayi ne halan" Abba ya girgiza kai yace "Ibrahim
ne" Umma tace "Allah sarki, haka dai kawai ka hanani zuwa gun 'ya ta in dinga duba
halin da take ciki, yau kusan sati biyu kenan rabona da ita, wallahi kullum da ita
nake kwana nake tashi a raina, in ji dai suna lafiya?" Abba yace "Lafiya lau, zuwa
yayi min da wani batu" Umma ta gyara zama tace "Wani batu kuma, to Allah ya sa dai
lafiya" Abba yace "Lafiya lau, wai zai je noma garinsu xai tafi da ita" Umma ta
zaro ido tace "Ya tafi da ita ina?? Yaushe Nihad xata wani iya zama a garinsu? To
sai kace masa me Alhaji?" Abba yace "Toh ai a yanzu dai ya fi mu iko da ita, babu
ta yanda xan iya hanasa tafiya da matarsa Sumayya" Umma na girgiza kai tace "Aa
Yallabai wannan ba magana bace, to ko dai ka sallama ma duniya er nan ne bamu da
masaniya? Duk wannan punishment din da kayi mata na aura mata dreba bai isheka ba
sai ka ba dreba goyon bayan tafiya da ita kauyensu da sunan noma? Haba Alhaji ko ba
kai ka haifi er nan ba kaddarar nan ya fada mata ai ka ji tausayinta ka raga mata
balle er cikinka ce kuma masoyiyarka, ina laifin kace ya kawota nan gida ta zauna
har sanda xai gama nomar tasa ya dawo daga kauyen nasu?" Abba yace "Aa, ai mu ba
kananun mutane bane da zance ya bar ta gida Sumayya, tunda har ya girmama ni ya zo
neman izinin tafiya da ita ni kuma baxan yi karanta ba a matsayina na mutum me
kamala a gunsa, yanxu dai nace ya sa a bincika min fili a inda xa su zauna din, ko
nawa ne xan siya, idan ya so ko 3 bedroom flat ne in sa a gina babu bata lkci, don
yana min maganan sun samu gidan dubu dari, dama akwai gidan dubu dari a zamanin
nan?" Shiru Umma tayi tana kallonsa babu ko kiftawa, Abba ya daga kai ya kalleta
jin tayi shiru, tayi murmushi tace "Maa sha Allah, gida xaka gina ma Nihad din a
can kenan?" Abba yace "Hakan xai fi gaskiya, idan ma babu wuta garin a saka masu
solar 24/7, sannan ayi borehole a gidan, ayi furnishing yanda ya kamata" Umma ta
gyara zama tana Murmushi tace "Hakan yayi kyau kam gaskiya, Allah ya saka maka da
alkhairi ya kara budi, kaga zata zauna comfortably baxata takura ba, har ma ta sake
a gidan ta ji kamar a cikin gari take" Abba yace "Yeah!! So i think duka duka da
filin da ginin ai baxai ci miliyan goma ko sha biyu ba ko?" Umma tace "Ehh to, xai
iya zama hakan tunda ai ba cikin gari bane kila, balle ace filin xai yi tsada
sosai" Abba yace "In sha Allah, ko zuwa gobe aka samu filin xa a daura gini kawai"
Umma na Murmushi tace "Madallah, Allah ya kai mu goben, bari in je in gama abinda
nake a sama" Abba yace "Alright" mikewa tayi ta fita daga parlon. Yau ma kamar jiya
ana kwankwasa gate Nihad da Khalil suka fito a tare, bai ko kalleta ba har ya fita,
ta bi bayansa don wannan karan sai dai duk abinda xa ayi ayi a bakin gate din in
dai Umma ce sai ta bude mata, Ya hade rai ya juya yana kallonta yace "Meye kike bi
na?" Ita ma ta hade rai tace "Kayi tafiyarka inyi tawa mana" ya ci gaba da tafiya
tana bin sa har suka iso gate din, yace "Wanene?" Husnah tace "Assalamu alaikum" Ya
wani hade rai yace "Nace waye?" A hankali tace "Husnah ce" Nihad ta hade tafin
hannunta kamar xata yi kuka tace "Don girman Allah kayi hakuri ka bude mata, ni
kenan sai inyi ta zama babu wanda ke xuwa wajena kamar mayya,x kuma ai a sharadinmu
nace baxa ka ki barin kawayena su zo wajena ba kuma ka yarda" Kallonta kawai yake,
nan da nan hawaye ya cika idonta tace "Don Allah fa nace maka" Duk Husnah na jin su
ita kanta addu'a take Allah ya ta6a zuciyar Khalil ya bude mata gate din, Juyawa
khalil yayi ya bar wajen, Nihad ta wara ido cike da farin ciki ta bude gate din,
tayi tsalle ta rungume Husnah tace "Wallahi nayi missing dinki kawata, ina su Naf
da zully?" Husnah tace "Ba su ma san xan zo nan ba wallahi, tun shekaranjiya kike
raina in gaya maki, shine kawai nayi tahowata ban gaya masu ba" Nihad ta kulle gate
din tana Murmushin jin dadi ta kama hannun Husnah da ta bi khalil da kallo har ya
shige parlor, suna isa balcony Husnah tayi kasa da murya tace "Amma dai kawai in
gaida mutumin nan don gobe ma ya barni in shigo, kinsan abun sai da siyasa kawata,
barin ma shi da yake ɗan kauye gaishesan da xanyi yanxu xa ki ga farin cikin da zai
yi kansa yayi kato, kinsan bakauye akwai son girma" Nihad ta kyabe baki tace "Kar
ki wani gaishesa, meye hadinki da shi ko ina ruwanki da shi bayan ba wajensa kika
zo ba, ni kaina da nake gidan ban ta6a gaishesa ba saboda bai isa ba balle ke"
Nihad na gama fadin haka ta ja hannun Husnah suka shiga parlon, Husnah na hada ido
da shi ta janye hannunta daga na Nihad dake jan ta zuwa daki, ta dan yi murmushin
yake tace "Ina wuninmu?" A fusace Nihad ta ja Husnah fuuu suka wuce daki ta kulle
kofar tace "Amma ba nace kar ki gaishesa ba? Meye amfanin gaishesa yanzu?" Husnah
ta yatsine fuska tace "Ni kaina wllh sai bayan da na gaishesa naga rashin dacewan
hakan, baki ga ma wani shan kamshi da yake shi a dole ya aureki ba, yanzu fa ji
yake shi wani shege ne ya auri er mai kudi" Nihad tace "Ke mu fa mun riga mun ajiye
deal kan cewa xai sakeni, na amince shi ma kuma ya amince ya kuma yarda ni ba class
dinsa bace" Husnah ta zaro ido tace "Haba??" Nihad tace "Wallahi in gaya maki, ai
yaga tsanar da nake masa tayi yawa baxan kuma ta6a raga masa ba shi yasa yaga gwara
mu rabu..." Husnah tace "Yanzu yaushe yace xai sake kin?" Nihad tace "Ku dai kawai
ku zuba ido ku ga ikon Allah" Husnah tace "Kai amma na tayaki murna wallahi, ashe
shegen ya san abinda yake yasan ke ba class dinsa bace cikin ruwan sanyi xai rabu
da ke" Nihad ta tuntsire da dariya tace "Wallahi fa in gaya maki" Husnah ta cire
Hijab din jikinta ta jefar kan gado, Nihad tace "Yaushe kika dinka hijab ke da baki
da ko guda daya" Husnah tace "Wannan ma a hostel na aro shi, ke akwai abinci yunwa
nake ji" Nihad tace "Ehh daxu nayi stew, kawai spaghetti xan yi boiling" Husnah
tace "Toh bari in yi boiling dinsa, akwai a kitchen ai?" Nihad tace "Ehh akwai"
Mikewa Husnah tayi ta bude handbag dinta ta fiddo after dress ta daura a kan riga
da wandon jikinta ta fita, Nihad ta jawo jakarta bayan ta fita ta bude, as usual
kayan maye iri iri ta ga a jakar da Prophylactics dinta, Nihad ta mayar mata da
kayanta ta dau wayarta da ta gani ta bude password don tasan password din nata, har
tayi dialing number Aliyu sai ta tuna ba shi da number Husnah don haka baxata
samesa ba, lkci daya jikinta yayi sanyi, sai dai kawai tayi dialing number Umma,
Umma na jin muryata tace "Daughter, ina ta tunanin ta yanda xanyi waya dake tun
jiya wllh, har cewa Nihal ta kai maki waya gida nayi amma er nan taki, Amina kuma
kinga tunda ana hutu islamiyya take safe da yamma ita ma baxata yarda tayi fashi ba
don in aikota wajenki" Nihad ta marairaice tace "Nima babu ta inda xan kira ki
Umma" Umma tace "Kina ji na?" Nihad tace "Ina ji Umma" Umma tace "Kullum nayi
sallah ina saka wannan tsinannen dreban a addu'a kan cewa Allah Ubangiji ya rabaki
da shi cikin aminci, to sunansa kawai na sani ban san sunan mahaifinsa ba ko
uwarsa" Nihad tayi shiru, sai kuma tace "Nima wallahi ban sani ba Umma" Umma tace
"Yo ai nasan baki sani ba, ke baxa ki iya dubara irin na mace ba ki tambayesa sunan
ya gaya maki, sai kace ba wayayyar Nihad dita ba, ai cikin salo irin na wayayyun
mata zaki bi masa har ya gaya maki" Nihad tayi Murmushi tace "Toh shikenan Umma"
Umma tace "Yauwa zuwa yaushe xan saurareki?" Nihad tace "Gobe" Umma tace "Amma
number waye wannan?" Nihad tace "Na Husnah ne" Umma tace "Au tana can shegen ya bar
ta ta shiga kenan" Nihad tace "Wallahi kuwa Umma" Umma tace "To yaushe xata tafi?"
Nihad tace "Kamar fa kwana xata yi naga kaya kala biyu a jakarta" Umma tace
"Madallah dai dai kenan, kinga gobe sai ki kirani kawai ta wayar nata" Nihad tace
"Toh Umma" Daga haka Umma tayi mata sallama Nihad ta katse wayar, dai dai nan taji
Husnah tayi wani kara, ta mike da sauri ta fice daga dakinta, Tana fita parlor
Khalil na shiga kitchen din, ita ma ta nufi kitchen din da sauri.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah,

ki fita hakkina ki karanta cikin salama er uwa

Ur evidence via👇🏻
07087865788

Assalamu alaikum er uwa, kina neman organic Supplement irin masu gyaran jiki ciki
da waje? Ko kuma mai fitar Maki da duk wani infection komai nacinsa? Sannan mai
maido Maki martabar fatarki? Ko kina fama da dry HQ? Ko hips ne matsalarki da
boobs? To kwantar da hankalinki *GHT Organic supplement care gat ur back*

Domin karin bayani ki tuntubi wannan number 👇🏻

✍🏻
+2347057607751
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

32

Husnah ce tayi zaman dirshan a kitchen din dake malale da ruwa, gaba daya ta jike
jagab daga saman cikinta har xuwa ƙafafuwanta, ta wawwara hannu ta runtse ido cikin
daga murya tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Wayyoo na shiga uku na
lalace, gaba daya na kone a jiki... Don Allah a kawo min agajin gaggawa" daga
gefenta tukunya ce dauke da ruwan zafi a ajiye, Khalil ya shiga kitchen din da
sauri yace "Me ya faru haka?" Ta bude ido ta fashe da matsanancin kuka tana
kallonsa tace "Don Allah ka taimakeni wallahi, ruwa me uban zafi ne ya kwaro min
gaba daya tun daga cikina har kafa, taliya naje zan zuba ruwan ya kifo min, don
Allah ka kawo min agaji kar jikina ya toye" Da mamaki Khalil ke kallonta, kuka
kawai take tana jijjige kafarta da hannu tana cewa "Wayyo Allah na, wllh ruwan ya
tafasa sosai, don Allah a taimakeni duk radadi jikina yake min" Khalil yayi ma
kofar kitchen din kallon kasa kasa jin kamshin Nihad, ya ganta tsaye bakin kofar,
bai yarda ya kalli fuskarta ba, ya kashe gas din ya karasa kusa da Husnah ya mika
mata hannu yace "Taso" Karaf ta cafke hannunsa ya dagota ta mike tana kara sautin
ihunta tana cewa "Wayyoo mamata, Wayyoo zafi, na shiga uku me za a shafa min ya
daina min wannan radadin da nake ji..m" Hanyar kofar kitchen din ya nufa da ita
still ya ki kallon Nihad, ita kanta Husnah bata kalli Nihad ba sai gunjin kuka take
tana jijjiga kai tana yi tana runtse ido, ganin Nihad ta ki matsawa daga kofar
kitchen din Khalil ya daga kai a karo na farko ya kalleta, rungume hannu tayi tana
kallon su, yace "Matsa a hanya" Ta zabga masa wani ta juya da sauri ta bar wajen ta
wuce dakinta, Husnah ta bi Nihad da kallon gefen ido tana cewa "Don Allah a
taimakeni kar jikina ya kwaile in ma asibiti ne mu je" sai kuma ta zame hannunta
daga nasa tayi dai dai a kasa ta kwanta tana birgima tana kuka, dakinsa ya nufa ta
bi sa da kallo, sai ga shi ya fito da makullin mota yana kallonta yace "Mu tafi
asibitin" tana girgiza kai cikin kuka tace "Wallahi baxan iya tashi ba" Yace "Toh
kira kawarki" Daga haka ya fita ya je parking space ya tada mota, Mikewa Husnah
tayi tana gunjin kuka ta tattale hannu ta bi bayansa, tuni ta isa gun motar tana
cewa "Don girman Allah mu yi mu tafi asibitin kar na mutu, ko ina zugi yake min" Ya
bude mata back seat ta shige ciki, Tun da ya tada motar Nihad ta fito parlor ta
tsaya jikin window tana kallon su, sai da ya bude gate ta ga ya dawo zai shiga
motar kawai ta fito ta nufi front seat ta shiga ta kulle, ya bude gefen mazaunin
driver yana kallonta da kyau yace "Ina za ki?" Ba tare da ta kallesa ba tace
"Asibitin da za ku" Ya kalleta daga sama har kasa yace "Ohk, haka za ki je asibitin
kenan" Fuska daure tace "Sai ka jira ni in dauko mayafina" Daga haka ta fice daga
motar da Husnah ta cika da ihu kamar warce ake gunduwa gunduwa da namanta, tana
ganin Nihad ta sauka tace "Don ya Rasulullahi ka ja motar mu tafi kar a rasa fatar
jikina, wllh jin jikin nake kamar ba nawa ba, kar fatana ya karasa zagwanyewa" Bai
ce mata komai ba ya shiga motar, amma bai ja motar ba, sai ga Nihad sanye da Hijab
ta shige gaban motar, ya ja motar suka fita gidan ya sauka ya kulle gate. Wani
asibiti da babu nisa daga anguwansu ya kai ta, duk nurses suka tattaso da sauri
saboda tun daga Gate ihun Husnah ya cika asibitin, Nurse daya na kallon Khalil tace
"Me ya sameta?" Khalil da ya koma gefe ya tsaya yace "Wai konewa tayi" Nan aka
shiga da ita emergency aka dau scissors za a fara barke riga da wandon jikinta,
Nihad dai na reception din hospital din ta zauna, babu wanda zai ce tare suke,
Khalil kuma na kofar shiga reception din ya jingina da bango ya rungume hannunsa,
wani ihu Husnah ta sakar ma nurses da Dr din tace "Don Allah a kira min yayana ya
zo kila mutuwa zan yi, a kirasa ya zo kusa da ni" Wata Nurse ta fita ta kira
Khalil, yana kallonta yace "Me xan yi a can din?" Rai bace Nurse din tace "Haba
bawan Allah ko da baka santa ba ta bukaci ka je ai ko don saboda condition da take
ciki zaka je, wai ko ba matarka bace?" Daga haka ta juya ta koma emergency ward
din, Khalil ya bi ta da kallo kafin ya shiga asibitin ya bi bayanta, Nihad ta bi sa
da wani kallo, bai ma san tana yi ba, yana tsaye bakin kofar ward din Husnah ta
hangosa ta dinga miko masa hannu wai ya zo ya ceceta kar ta mutu, likitan da Nurse
dai sun gama 6arke kayanta da scissors suna neman inda ta kone, Can likitan ya
kalli Khalil da ya ki karasawa ciki yace "Wani irin ruwa ne ya zubar mata?" Khalil
ya buda ido yace "Ban sani ba fa, ko kafin na fito ruwan ya gama kwararewa a
jikinta" Nurse din na kallonta tace "Ruwan zafi ne ko dai ruwan dumi" Husnah ta
hade rai tace "Ban gane ruwan dumi ba, sharrin zan ma kaina ince ruwa zafi ya zubar
min a jiki bai zuba ba, kawai dai dama fata iri iri ce, amma Allah kadai yasan zugi
da radadi da nake ji yanxu haka, har cikin raina nake jin wannan axaban wallahi"
Tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka, likitan ya cire safan hannunsa yace
"Nurse ki basu magunguna" Yana kai wa nan ya fice daga ward din, nan nurse ta fito
reception ta harhada magungunan ta dawo ta mika ma Khalil Bill din dubu sha biyar,
amsa yayi ya fiddo Atm card dinsa ya mika ma nurse din, daga baya ta sake dawowa ta
bukaci pin dinsa sannan ta juya, Husnah dai sai gunjin kuka take tana kallon wata
nurse dake mayar da kayan aikinsu mazaunin su tace "Aunty Nurses babu wani abu da
za a shafa min?" Nurse din tace "An rubuta maki magani da za ki sha, Allah ya
sauwake" Daga haka ta fita, Nurse din ta kawo ma Khalil magungunan tana kallon
Husnah tace "Allah ya kiyaye gaba, za ku iya tafiya yanxu ga magunguna da
prescriptions a jiki" Daga haka ta juya ta bar wajen, Khalil ya daga kai ya kalli
Husnah, share hawayenta tayi ta sauko daga kan gadon da take a hankali kamar me
gudun kar ta fama wani ciwo a jikinta, duk sun yayyaga mata kayanta wandon ne kawai
basu karasa ba, amma daga saman cikinta duk a bude yake, Khalil zai juya ya bar
wajen cikin kuka tace "Wallahi baxan iya tafiya ba ko Nihad ce ka turo ta kama min
hannu" Har ya fara tafiya sai kuma ya dawo, da sauri ta karaso kusa da shi ta kama
hannunsa, ya dake ya fara tafiya tana dingishi tana bin sa har suka fito reception
din, har suka isa mota Husnah ta shiga baya ta zauna Nihad bata fito ba, Khalil na
tsaye jikin motar for almost 5 mins ganin bata fito ba still ya koma reception din,
hade rai yayi yace "Malama ke muke jira" Ko Kallonsa bata yi ba ta tsura ma Tvn
dake aiki a reception din ido, yace "Ohk ga kudin mota duk sanda kika zaman sai ki
dawo gida" Ya ciro dari biyar ya mika mata, zuwa lkcn nurses din sun fara kuskus ko
kishiya da kishiya ne, can ta mike ta fice daga reception din fuskarta a daure,
juyawa yayi ya bi bayanta sai yaga ta bude front seat ta shiga, ya shiga motar shi
ma suka bar asibitin, suna hawa saman titi Nihad tace "Hostel za a kai ki ko ina?"
Husnah tace "Wallahi kin bani mamaki Nihad har in kone a gidanki amma ki kasa budan
baki ki min sannu? Sai yanxu ki wani bude baki kice hostel xa a kai ni ko ina?"
Nihad tace "Saboda ai sai da nace ki bari in dafa kika ki, Yanzu idan wani abu da
yafi wannan ya sameki su Mumy da Abba suka ji bayan sun hana in kawo kowa gidan fa?
What did u want me to tell my parent? Ni yanzu dai hostel za a kai ki ko ina, kin
dai ga dare yayi" Khalil yace "Kinsan dare yayi kike kira mata hostel yanzu? Ba
kwana ta zo maki ba dama?" Nihad ta wani jefa masa kallo tace "Ni bata ce min zata
kwana ba, salon mu koma gida wani abu da yafi wannan ya sameta in shiga uku? Kawai
ta koma hostel ko gobe sai in kai mata jakarta can din" Kallon Nihad kawai Khalil
ke yi, Husnah tace "To baxan wani je hostel ba jakana na gidanki kuma ID card dina
na ciki, kuma ai soyayya ce tasa na zo gidanki ba wani abu ba, me yasa su Naf da
Zully basu zo ba, amma ba komai Nagode da walakancin da kika min Nihad" Khalil dai
ya nufi hanyar gida, bayan ya shiga ciki yayi parking Nihad ta bude motar ta sauka
ta wuce ciki, Husnah ta sauka ita ma ta shiga gidan Khalil ya bi su da kallo,
jingina yayi da motar ta ta6e baki. Husnah na shiga dakin Nihad ta fashe da kuka
sosai tace "I never expect this from you, in wani yace min zaki min haka wallahi
baxan yarda ba, saboda wannan mere Drivern ya taimakeni ya kai ni hospital kike jin
haushi Nihad?" Nihad tace "Ya baxan ji haushi ba mutumin da ko magana bana yi masa
za ki ja min raini a wajensa ya zata ya mana alfarma, ko kadan i am not happy with
what happened da kawai kirawoni kika yi na fita waje na nemo mana taimako akan
wannan yaron da kika kula, yaron da ya tsaneni nima na tsanesa shine har zaki yarda
ya wani kai ki asibiti?" Husnah tace "Tohh idan mutum na cikin azaba ai baya ma
tunanin komai, kawai burinsa a fitar da shi daga axaban da yake ciki, to situation
din da na tsinci kaina kenan, amma ni kaina ina ni ina wani driver can" Nihad bata
sake cewa komai ba, Husnah tace "Shikenan, tunda har kika koreni bari in yi
tafiyata ko hotel ne in kwana don a hostel na riga nace masu baxan dawo yau ba"
Nihad tace "Ni fa bance kar ki kwana ba, kawai haushin yaron can ne yasa nace mu
kai ki hostel" Tana kai wa nan ta mike ta cire Hijab din jikinta tace "Bari in mana
boiling din spaghetti din yanzu, daga can xan gyara kitchen din" Tana fadin haka ta
fita parlor ta wuce kitchen tsaye taga Khalil yana kokarin mopping din kitchen din,
ta wani hade rai, yana ganinta ya ajiye mop din ya fice daga kitchen din ya shiga
dakinsa, bayan few minutes da fitar Nihad Husnah ta leko daga dakin tana lekan
parlor amma bata ga Khalil a ciki ba, komawa dakin tayi ta cire yagaggen wandon
jikinta da riga ya rage daga ita sai bra da skin tide ta dau after dress dinta ta
saka tayi buttoning dinsa sannan ta fito, ta fi second goma tana kallon kofar da
take tunanin dakinsa ne sai kuma ta murda, dago kai yayi suna hada ido ta sunkuyar
da kai ta shiga dakin ta tura kofar tana tsaye bakin kofar tace "Dama nace bari in
maka godiyan dawainiyar da kayi da ni, Allah ya saka da
Alkhairi.... kuma don Allah abinda ya faru kwanaki ina sake neman yafiyarka don
wancan ranan baka ce min komai ba da na baka hakuri" Kallonta kawai Khalil yake,
can ya ajiye lemon kwalin dake hannunsa yace "Ohk, kawarki ki ce ta aikoki ki bani
hakuri kenan?" Husnah ta zaro ido tace "Waaa?? Ai inda muka bambanta da ita kenan,
da ita ce baxa ta ta6a baka hakuri ba, kasanta da taurin kai da kafiya, yanzun ma
bata san na shigo nan ba da baxata bari ba, amma ka sani wllh tunda muka maka
wannan rashin kirkin bana samun nutsuwa saboda ba halina bane" Yace "Ohk ai na zata
duk ku ke sa ta a hanyar walakanta mu talakawa" Husnah ta dafe kirji ta karasa
cikin dakin tace "Waa?? Halin kishiyar mamarta ne ta dauko, kasan duk abinda ta
sata tayi shi take yi, amma basu san da talaka da mai kudi duk Allah ne yayi su ba,
ka gan ni nan babana yalo yake siyarwa a kawo kaduna, ni ba er kowa bace shi yasa
nasan mutuncin ɗan adam" Khalil yace "Ohk, ai ina ce er kano ce" Husnah tayi wani
dariya tana jujjuya ido tace "Wallah er kaduna ce ni gaba da baya, Zully da Naf ne
yan kano" Yace "Toh naga makarantar taki ta masu kudi ce" Husnah tace "Ehh wallahi
wani saurayina ne ya biyamin tun daga level one har karshe, wata kawar mu zully ma
saurayinta ke biya mata, Naf ce dai iyayenta ke biya mata don su ma masu kudi ne"
Khalil ya gyada kai yace "Allah sarki" Husnah ta zauna gefen gadon tace "Amma ina
jiye maka zama gida daya da Nihad, yanda bata kaunarka ta tsaneka kullum a
makaranta cikin tsine maka take wai kana matsayin driver kana nuna mata isa, bayan
anyi auren nan har ikirari tayi wai zata kasheka, nan kuwa kai jahadi kayi, halan
baka hawa social media? Ina nufin baka da babban waya?" Ya girgiza kai yace "Bani
da" Husnah ta gyada kai tace "Allah sarki, kawai dai ka saka ido sosai kada kiyayya
yaje ya kaita ga aikata abinda ba shi kenan ba, in sha Allah in xan sake dawowa
nayi maka alkawarin babban waya" Khalil yace "Toh Nagode, amma kawar taki bata da
saurayi ne?" Husnah ta rike ha6a tace "Ita kuwa take da saurayi wanda ita ta makale
masa ba shi ba, kana jin janaral jikamshi?" Khalil yace "Eh nasan shi, ko ba wani
babban soja ba?" Husnah ta dafa kafarsa cike da kissa tace "Yauwaaa, Toh shi fa....
ɗan sa kwaya daya take so kamar ta kashe kanta, tun yana basar da ita har dai ban
san sanda suka dinke ba, mu dai mun fi zargin bashi kanta tayi, don kawai lkci daya
muka ga ya fara kiranta ba kakkautawa a maimakon ita da ke yawan kiransa" Khalil ya
sauke idonsa kasa daga kallon da yake ma Husnah, Husnah tace "Kuma fa duk wannan
abun sau daya ya zo wajenta a nan kano suka hadu a wani waje, kamar dai kar su hadu
shkkn ya makale mata, kasan mu mata idan muna son abu babu abinda baxa mu yi kan
abun ba, to tun dai daga sannan ya fara kulata sosai, kuma kar kace fa yana zuwa
gidansu, aa sam... duk xuwan da yake yi wajenta nan kano sai dai su hadu a wani
waje su yini sannan yayi tafiyarsa, toh kwanaki can ban san ya aka yi ba yaje
gidansu wai xai tura iyayensa, mu dai ko gaya mana bata yi ba gaskiya sai daga
baya, ai ko muna ta murna xa mu hade da 'ya yan manya mu ma a dama damu tunda
abokanansa duk 'ya yan manyan kasar nan ne kawai wai sai ga videon tsaraicinta ya
bazu a duniya, ni takaicina daya da ba a bari sai da muka hadu da abokansa ba, har
yau mun rasa ta ina video din nan ya fita, muna dai tunanin garin yawace yawacenta
ne aka mata video din nan" Khalil bai kuma cewa komai ba, lkci daya kuma duk mood
dinsa ya canza, Husnah ta shafa kafarsa a hankali tana kallon kwayar idonsa tace
"Sai kaji babu dadi ace videon tsaraicin warce aka aura maka na ta yawo a duniya
ko? A ranka kana tunanin an cuceka ko?" Kallonta Khalil yayi, tana Murmushi ta
janye hannunta a hankali tace "Toh Nagode bari in je inyi wanka" Daga haka ta mike
tana juya manyan mazaunanta ta nufi kofa, tunda ya kalleta sau daya ya dauke kai
har ta fita dakin, karo ta kusa ci da Nihad, Nihad ta tsaya tana kallonta daga sama
har kasaasa, Husnah tace "Ke yace min maganin na wajenki kuma ni ban gansa a
dakinki ba" can kasa kasa Nihad tace "Ba ya wajena" Daga haka ta shige dakinta,
Husnah ta tafi parlor ta dau magungunan nata ta dawo dakin Nihad. Nihad dai na ta
zaune gefen gado, Husnah tace "Wai taliyar bata yi bane Nihad?" Sai a sannan Nihad
ta kalleta tace "Mu je mu duba" Husnah tace "Ohk" Daga haka ta mike ta fita Nihad
ta tashi ta bi bayanta, tana tsaye parlor har Husnah ta shiga kitchen, a hankali ta
bude kofar dakinsa ta leka taga baya ciki, ta kalli kofar bandaki sai kuma ta kulle
kofar dakin, entrance din fita ta kalla bata ga takalminsa ba, ta karasa jikin
window ta tsaya ta bude labulen a hankali tana lekan waje, yana tsaye balcony ya
rungume hannunsa, can ta ga ya nufi dakalin da yake son zama ya zauna kana ganinsa
kasan he is moody, Husnah ta fito daga kitchen tace "Me kike nema a waje" Nihad
tace "Ba komai, kin zubo taliyar?" Husnah tace "Ehh na zuba, ashe har kin sauke"
Nihad tace "Toh dauko mu je daki" Husnah ta koma ta dauko suka wuce dakin, bayan
sun gama cin abincin Nihad ta fitar da kwanukan ta sake leka waje taga har sannan
khalil na zaune inda yake staring into space, kafin Nihad ta dawo Husnah ta jawo
jakarta ta fito da kayan mayenta ta sha sannan ta mayar da jakar ta ajiye ta
kwanta, Nihad na dawowa dakin ta zauna gefen gado, tana son shiga bandaki tayi
wanka amma ta kasa tashi, Wajen karfe sha daya da rabi Husnah ta mike Nihad na
kallonta tace "Ina za ki?" Husnah tace "Ruwa zan dauko kitchen" Nihad ta dauko wani
bottle water dake daya side din gadon ta mika mata, Husnah ta amsa ta koma ta zauna
tana sauke numfashi a hankali, ita fa dama kwana biyu duk samarin nata basa Kano
gaba daya a takure take dama, daga karshe dai Husnah ta kwanta ta kulle ido duk da
ba bacci tayi ba, Wajen karfe sha biyu da rabi Nihad ta mike daga kwancen da take
ta nufi kofa ta sa makulli sannan ta ciro, Da mamaki Husnah ta mike zaune tana
kallonta tace "Me yasa zaki kulle mu har da cire makulli Nihad?" Nihad tace "Saboda
duk dare haka nake yi dama" Husnah bata kuma cewa komai ba ta kyabe baki ta koma ta
kwanta, Nihad ta saka makullin cikin pillow ta kwanta kai. Washegari da sassafe
bayan sun yi sallan asuba sun koma bacci kiran Umma ya tashe su, Bayan Husnah ta
daga jin muryar Umma tace "Auu Umma ce, ina kwana?" Umma tace "Lafiya lau Husnah
baki yi saving number na har yanzu ba ko?" Husnah tace "Yanzu xan yi Umma, ya
gida?" Umma tace "Alhamdulillah, ina Nihad din?" Husnah ta mika ma Nihad waya ta
koma ta kwanta, Bayan Nihad ta gaidata, Umma tace "Ya, kin gano sunan iyayen nasa
kuwa Nihad?" Nihad tace "Aa Umma, dama sai yau" Umma tace "Kin ji irin shiriritar
taki ko? Ke da tun jiya nace kisan yanda kika yi ya gaya maki amma sbda shashanci
baki yi ba? Ko dai kin fi son kiyi ta zama da dreban nan ne Nihad?" Da sauri Nihad
tace "A'a Umma, in sha Allahu yau xan gaya maki" Umma tace "Toh kar ki bari Husnah
ta bar gidan nan sai kin gano kin sanar min ta wayarta tukunna" Nihad tace "Toh
Umma" Umma tace "A handsfree wayar yake ne naji maganata na dawo min?" Nihad tace
"Aa" Umma tayi kasa da murya tace "To dai ki xama me rike sirrinki a ciki, ciki da
kike gani ba don tuwo kadai aka yi sa ba, ko da mun gana waya kawarki ta tambayeki
me muka ce kice mata ba komai kawai daddawa da kuka nace xan bada a kawo maki, don
ba komai ake sanar ma k'awa ba, wa ya sani ko da hadin bakinsu aka saki video dinki
a duniya" Nihad tace "Aa Umma ba haka bane gaskiya" Umma tace "Toh shikenan, ina
sauraronki zuwa anjima" Nihad tace "Toh" Daga haka ta katse wayar, Husnah na
kallonta tace "Wai me ya faru?" Nihad tace "Aa ba komai, abubuwan da zata kawo min
ne take tambayata" Husnah tace "Ohk" Komawa tayi ta kwanta, Nihad ta mike ta dau
Hijab dinta ta daura kan kayan baccinta ta nufi kofa Husnah ta bi ta da kallo har
ta fita, Nihad na murda kofar dakin Khalil taji an sa makulli, ta fi minti daya
tsaye bakin kofar, can ta juya ta tafi parlor ta zauna, tana fitowa da minti biyar
sai ga Husnah ma ta fito ta zauna parlon, jan Nihad ta dinga yi da hira, daga
karshe wajen karfe tara Khalil ya fito daga dakinsa, babu warce ya kalla a cikinsu
ya fita daga gidan, Husnah na ji ya fita da mota ta kalli Nihad tace "Lallai ke me
hakuri ce da har kika kai warhaka da mutumin nan a gidan nan, Dubi fa yanda ya wani
zo ya wuce mu ko gaisuwa babu, kai kana talaka da kai kayi ta yin abu isa isa?"
Nihad ta kyabe baki tace "Ke ma kika lura da mutum ya zo ya wuce ta nan, ai ni ban
ga kowa ba" Husnah ta kyalkyale da dariya tace "Ahh lallai kam" Nihad tace "Tashe
mu je ko irish ne mu soya da kwai, ni dai na fara jin yunwa" Husnah ta mike suka
wuce kitchen din, har kusan la'asar Khalil bai dawo gidan ba, kiran Umma uku duk
sai Nihad tace mata ai bai dawo ba, kiran karshe da Umma tayi mata da ta kara sanar
mata har sannan bai dawo ba, Umma tace "To kar ki yarda ki bari Husnah ta bar
gidan, don tana tafiya babu ta inda xa mu yi communicate" Nihad ta kalli Husnah da
ita dama bata ga alamar xata tafi ba tace "Toh Umma" Labari har da na kauyensu
Khalil sai da Nihad ta ba Husnah dake ta kyalkyalewa da dariya har da faduwa kasa,
tace "Kice ke kika ga asalin dreba ganin idonki?" Nihad tace "Hmm... I wish xaki ga
kauyen nan Husnah, wllh with millons baxa ki yarda kiyi minti sha biyar a garin nan
ba, it's hell on earth" Husnah dai sai dariya take, sai ga Naf ta kira Husnah,
Nihad da wayar ke kusa da ita tayi saurin dagawa ta kai kunne, Naf na jin muryar
Nihad tace "Amma Husnah munafuka ce shine bata gaya mana ba tayi tafiyarta ita
kadai" Nihad tace "Wallahi nima ban ji dadin da baku zo gaba daya ba, gashi
throughout today I wasn't lonely, muna ta hira da Husnah" Husnah ta fixge wayar
tace "Toh ai naga xaku fita ne shi yasa bance maku mu taho ba Naf, amma meye a ciki
next time idan xan zo ai sai mu taho gaba daya, ba wani tashin hankali bane" Naf
tace "No but like seriously kinsan indai kince mana wajen Nihad xa ki babu abinda
xai hanamu binki, kuma banji dadin abinda
kika mana ba, yanzu ma kawai xa mu iya tahowa da zully tunda babu abinda muke"
Husnah ta dinga cewa Hello hello, daga haka ta katse wayar tace "Ji shegen network
din ya dauke" Hirar da take ma Nihad ta ci gaba da yi mata, Nihad tace "Kinga
lokaci na wucewa me xa mu ci da daddare Husnah?" Husnah tace "Ni yanzu xan fita in
amso wani sako na, ko indomie ce ma ci da daddaren, Hijabi kawai xan sa in je in
dawo" Nihad na kallonta tace "Kar fa ki ki dawowa Husnah" Husnah ta zaro ido tace
"Me xai hanani dawowa kuwa, cabb ai kamar na dawo kinsan yanda nayi kewar ki kuwa,
to a nan ma xan bar wayata, amma kar ki cire min a flight mode har in dawo" Nihad
tace "Toh" daga haka Husnah ta sa hijab ta dau handbag dinta ta bar gidan, ko da ta
dawo bayan kusan awa daya Nihad ta dinga kallon hannunta ganin ba leda tace "Ina
sakon?" Husnah ta ja tsaki tace "Wai ashe sai gobe, shine suka bari naje nayi
asaran kudin motata na dawo" Daga haka ta shiga dakin Nihad. Sai after Magrib
Khalil ya dawo gidan, Husnah da fitowarta daga wanka kenan ta dauki mai zata shafa
ta rike ha6a tace "Dama haka yake yi ya fita tun safe sai dare kamar me siye da
siyarwa a kasuwa" Nihad ta kyabe baki tace "Ohk ya dawo ne" Dariya kawai Husnah
tayi bayan ta gama shafa cream dinta tace "Ke baxa ki yi wankan bane" Nihad ta mike
tace "Zan yi" Daga haka ta shiga bandaki, mikewa Husnah tayi da sauri ta bude kofar
dakin tana leka parlor, ba kowa parlon sai leda da ta gani a ajiye na eatry, ta
dawo daki ta dau handbag dinta sannan ta fice tana waige waige kamar munafuka ta
shiga kitchen ta bude handbag dinta ta dau allura me cike da wani liquid a ciki ta
bude murfin syringe din, ta dawo parlor har tana tuntube ta tafi gun ledan ta bude
ta ciro drink din kwali da ta gani ta tsira masa alluran ta sama ta juye duk
content din ciki sannan ta mayar da shi ledan hannunta na rawa, sbda rudewa
maimakon ta koma daki sai ta shige kitchen, ta fi second talatin a kitchen din
kafin ta leko parlon a hankali still taga ba kowa da sauri ta wuce dakin Nihad ta
kulle kofa ta zura doguwar rigarta ta dau wayarta ta kwanta saman gado tana danne
danne tana ɗan murmushi.....

*Few mutanen da suka sameni jiya for discount wai basu da halin dari biyar, bayan
message dina na jiya, sorry i didn't acknowledge u guys yesterday, after all ni din
ce dai zan yi loose still😏, don haka na amince nayi discount daga yanzu xuwa gobe
in sha Allah*

3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via👇🏻

07087865788

Assalamu alaikum manyan mata!!

For your Egyptian Abaya's, mad gowns, laces and handbags and all sort of
jewelries... Give me the privilege to be ur plug plss, and u will never regret it🥰

Ping me on WhatsApp to view our catalogue 👇🏻

https://wa.me/c/2349090591769
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

33

Nihad ta fito daga wanka bayan ta gama shafe shafenta ta zauna tana tunanin abinda
xata sa yau ta kwanta don dama kayan baccin biyu ne kawai ya rage mata kuma duk ta
sa su bata wanke ba, ita tunda take ma ta ta6a wanki a rayuwarta banda pant da bra,
Husnah tayi mika tana kallonta tace "Ke kuma tunanin me kike haka?" Nihad ta
kalleta a sanyaye tace "Toh kayan baccin nawa duka duka biyu ya rage fa a gidan nan
gashi nan kuma duk na sanyesu ba a wanke ba" Husnah ta mike zaune tace "Toh ke
garin yaya kika zo da kayan bacci kala biyu kawai?" Nihad tace "Ko ba can kauyensu
na rabar ba, da tsummokara fa mutanen kauyen ke yawo wallahi" Dariya Husnah tayi
tace "Toh kawai ki saka undies dinki sai ki saka hijabi ki kwanta" Nihad tace "Kin
ta6a ganin na kwanta haka?" Husnah tace "Yanzu ma dai ina kayan wanki naki yake?"
Nihad ta nuna mata inda ta ajiye su har da hijab kala biyu, Husnah ta mike tace
"Nasan ko tsutsa xa su yi a nan ba wanke su xa kiyi ba bari in wanke maki su in
samu ladanki" Daga haka ta kwashi kayan ta shige bandaki, Nihad ta mike ta dau
Hijab dinta kawai ta saka don dama akwai sanyi sanyi garin alamar hadari, tana ta
zaune tana game da wayar Husnah, sai ga Husnah ta fito rike da bucket tace "Can
waje zan je in shanyasu ko?" Nihad tace "Ehh ta baya xa ki ga wajen da xakiyi
shanyan" Daga sama har kasa Nihad ke kallonta don wani skimpy night wear ne a
jikinta, gashi ko bra bata saka ba, Mikewa Nihad tayi tace "Bari kawai in shanya"
Husnah tace "Ka ji ki, Aa wllh gwara in cike ladana, da me ya hanaki wankewa balle
ki shanya, kawai ni bari in je inyi shanyana" Daga haka ta nufi kofa, Nihad ta
kwashe gwangwanin maltina da suka sha da bottle wata ta bi bayanta, Yana zaune
parlor hannunsa rike da remote, ga ledan abincin nasa har sannan bai ta6a ba,
Husnah sai satan kallon ledan take har sai da ta buge da kujera ta kusa faduwa, da
ido ya bi ta, ta nufi kofa da sauri, Nihad dake kallonta har ta fita ita kuma tayi
hanyar kitchen taje tayi disposing thrash din hannunta a dustbin sannan ta fito
parlo, ta koma kamar xata shiga daki sai kuma ta tsaya bayan 2 seater dake side din
tana kallonsa, shi dai idonsa na kan tv, ta yanda xata fara masa tambayar da Umma
tace tayi masa kawai take tunani, Ganin bata da alamar barin wajen can dai ya daga
kansa ya kalleta yace "Lafiya?" ta jefa masa wani kallo tace "To banda ina son inyi
maka tambaya ance maka xan tsaya nan ne" Ya ɗan yi shiru sai kuma yace "Wa za ki yi
ma tambaya?" A takaice tace "Kai" Yace "Ohk, ni za ki yi ma tambaya kenan"
Hararansa ta dinga yi wato har wani feeling kanshi yake zata masa tambaya, ya
kafeta da ido yace "Yi tambayar ki" Babu yabo babu fallasa tace "Dama baka gaya min
sunan gwaggwonka ba a can garin, har da babanka ma duk baka gaya min sunansa ba"
Ita kanta tasan she sounds stupid, sai kuma ta fara sosa kai, kallonta kawai yake
ba ko kiftawa, can yace "Tun a garin baki tambayeni ba sai yanxu da daddare?" A
takaice tace "Ehh saboda sai yanxu na tuna" Yana gyada kai yace "Ohk!! To wa ya
aikoki ki tambayeni sunan su?" Ta wara ido kamar munafuka tace "Aa fa, ba wanda ya
aikoni yace in tambayeka nice kawai na tambayeka ina son sani" Yana kallon kwayar
idonta yace "NIHAD" ta kara buda ido a ɗan rikice tace "Na'am" Yace "Sunanta kenan"
Lokaci daya ta hade rai tace "Ban gane Nihad ba, sunanta ne sunana?" Yace "Ehh" Ta
dinga masa wani mugun kallo, can tace "Toh don baka da kunya sai ka wani kira
sunana gatsau wai Nihad, sunan nawa ka raina haka? waye ma ya gaya maka sunana?
Aminu me gadi ko???" Khalil bai kuma ce mata komai ba ya bude ledan dake ajiye
gabansa ya ciro drink din, dai dai nan Husnah ta shigo parlon ganin lemon a
hannunsa wani farin ciki ya mamayeta tana kallon Nihad tace "Ke an fara yayyafi fa,
kije ki rufe windows ko" Khalil ya ajiye kwalin lemun hannunsa ya mike ya shiga
kitchen xai dauko glass cup, wajen lemon Nihad ta nufa da gudu, Husnah da ke
kokarin shiga daki tana ta murmushi ita kadai kamar ance ta juya taga Nihad ta
kinkimo lemun ta taho da gudu xata shige daki, cike da zafin nama Husnah ta fixge
lemon daga hannunta tace "Meye haka sai kace mayunwaciya Nihad, bai siyo ya baki ba
sbda rashin hankali kin wani dauko masa abinda kika fi karfi, me xa ki yi da abin
hannunsa, bayan kudin ma kinsan na wanene ya ke ci, a'a wllh kin bani mamaki" Bata
jira cewar Nihad ba ta koma da sauri sauri ta ajiye masa lemon ta bar wajen sai
gashi ya fito kitchen, tuni Husnah ta figi hannun Nihad ta shige daki da ita ta
kulle kofar tace "Wallahi kin bani kunya, me xa kiyi da lemonsa ke da ko ni kika ce
in kawo maki carton din lemon can tsaf xan siyo in kawo maki, balle Umma ma kina
gaya mata xata bayar a kawo maki har gida? Me ya kai ki? Ke fa har yanxu yarinta na
damunki wllh, banda yarinta meye kike abu haka babu class, yanzu na gano dalilin da
yasa yayi mugun raina ki" Nihad dai bata ce komai ba, Husnah ta sauke wani boyayyen
ajiyar zuciya, dai dai nan aka fara ruwan sama kamar da bakin kwarya, Husnah ta
zaro ido tace "Lahh ga ruwan ya sauko, ki kulle windows din dakunan ni kuma bari
inje in kulle na parlor" Daga haka ta fice da sauri zuwa parlor, Nihad ta bi ta da
kallo sai kuma ta bi bayanta, farin ciki bai kara lullube Husnah ba sai da tagansa
rike da lemon a glass yana sha, ta kasa daina murmushi ta tafi ta kulle windown
parlon ta shiga ma kitchen ma ta kulle sannan ta fito tana kallonsa tace "Sai da
safe" Bata damu da ta ji ya amsa ba ta nufi daki tana jijjige inda ya kamata a
jikinta, Tana kallon Nihad dake bakin kofa tace "Wai duk kika ga na fito sai ki
biyoni" Nihad tace "Aa ni kitchen xan tafi ne" Husnah bata ce mata komai ba ta
shige daki, Nihad ta shiga kitchen ita kanta tasan babu abinda xata yi a kitchen
din bayan ta gama zagaye zagayenta ta fito ta nufi dakinta, da ido khalil ya bi ta
har ta shiga dakin, makulli ta saka ta zare makullin, Husnah dake kwance tana danna
waya tace "Kamar da wasa fa sai ga ruwa ko ba komai garin yayi sanyi naturally ayi
bacci me dadi" Nihad dai bata ce komai n a ta hau saman gado daga daya side din ta
jawo pillon ta jefa makulli a ciki Husnah dai na ta kallonta da gefen ido, Husnah
ta mike zaune tana kallonta tace "I want to take malt but gaskiya baxan iya shanye
daya ba, idan na rage maki xa ki sha ai ko?" Nihad ta girgiza kai tace "Aa na
koshi" a hankali Husnah tace "Toh shikenan, bari in bari kawai kar ayi asaran sa"
Nihad tace "Ki sha ki rage ki ajiye mana" Husnah tace "Aa ni kinsan bana son
almubazzaranci ke kuma dama kin iya walakanta abinci, da dai kuna da fridge ne sai
in je in ajiye sauran amma idan aka bar shi haka ai lalacewa xai yi, ba fa wai da
yawa xan rage ba ni nasan gejin cika na, kadan zan rage wllh" Nihad tace "Wa yace
maki malt na lalacewa??" Husnah tace "Ke dai tunda baxa ki sha sauran ba shikenan
sai in hakura in kwanta da craving dina" Nihad tace "Ni wallahi ban ta6a jin inda
malt ya lalace ba sai a bakin ki, ki sha kawai ki rage yayi ta lalacewan mana"
Husnah bata kuma cewa komai ba ta kwanta, bayan kusan 10 mins ta mike zaune tana
kallon agogo dake nuna karfe goma da rabi ta jawo malt daya kawai ta bude ta fara
sha, kallon Nihad tayi ganin kamar ta fara bacci ta tasheta, Nihad ta bude ido a
hankali Husnah tace "Wai kin daina alwala ne idan xaki kwanta?" Nihad na lullumshe
ido tace "Zan yi" Husnah tace "Aa tashi kije kiyi gaskiya kafin bacci me nauyi ya
dauke ki" Sai da ta tashi Nihad kusan sau uku sannan Nihad ta tashi da kyar duk da
tunda ta xo gidan nan bata ta6a alwala idan xata kwanta ba amma dabi'arta ce yin
hakan tun bayan da taje tayi wani hutu wajen Aunty Jamila na sati uku, Aunty Jamila
bata ta6a barin ta kwanta bata yi alwala ba, kuma bayan ta dawo gida kawai training
din ya zama jikinta, in dai xata kwanta sai tayi alwala wani lkcn Umma tayi ta mata
fada idan taga tayi tace so take sanyi ya shiga jikinta, Nihad na shiga bandakin
Husnah ta jawo jakarta da sauri ta bude wani abun maye ta zuba kusan quarter a
cikin ɗan malt din ta rage sannan tayi saurin mayar da shi cikin jaka ta ajiye
jakar, har ta dauko pillown Nihad xata cire makulli sai kuma ta fasa ta mayar da
sauri, Nihad ta fito daga bandakin bayan tayi alwalan ta nufi inda xata kwanta
Husnah tace "Don girman Allah ki shanye guntun malt din nan saura kadan, ta6a ki
ji" Nihad ta girgiza kai tace "Aa baxan sha ba kawai ki ajiye" Husnah ta dinga
kallonta sai kuma tace "Ohhh sai yanxu ma na gane, wai kyankyami yasa baki son ki
sha kamar warce ta zuba na bakinta a ciki?" Nihad ta kalleta tace "Ni nace maki
haka?" Husnah tace "Aa haka ne mana, banda haka meye don na sha malt na rage maki
ki ki shi Nihad?" Nihad tace "Ke dai kin san yanda xa ki bi ki juya magana, ni na
gaya maki haka? Ko daxu da kika dau ruwana kika sha gani kika yi na zubar?" Husnah
ta mika mata gwangwanin tace "Ni dai gashi babu yawa ki sha don bana son Allah ya
kamani da walakanci da abinci" Nihad tace "Wai ba daxu kika ga na dau malt na sha
ba salon inyi ta tashi cikin dare fitsari" Tsaki Nihad ta ja ta amshi gwangwanin
hannun Husnah ta kwankwade lokaci daya ta ajiye gwangwanin, Husnah sai kallonta
take tayi wani Murmushi, Nihad ta kalleta, da sauri Husnah ta dauke kai ta lulluba
da duvet tana cewa "Ki kashe mana wutan sai da safe" Nihad na yamutse fuska tace
"It has a different taste" Husnah tace "Aa hajiya sai dai bakinki ne" Nihad na
kallonta tace "Amma tsakaninki da Allah babu abinda kika zuba a malt din nan
Husnah, ni na sha gaya maki bana son irin abubuwan nan kuna forcing dina sai na
sha, dama shi yasa kika dage sai na sha?" Dariya kawai Husnah tayi tace "Oho dai,
ko ba komai yau xaki yi bacci me dadi brain dinki yayi relax, habaa" Daga haka
Husnah ta shige duvet, Nihad ta dinga mata wani irin kallo, can ta ja tsaki ta yi
kwanciyarta, she wish ta gano abinda Husnah xata mata kenan da baxata sha malt din
ba ko me xai faru, ko minti goma ba ayi ba Nihad ta bingire da wani nannauyan
bacci, Husnah ta juya tana kallonta tana Murmushi, har sannan kuma ruwa ake
kamar da bakin kwarya. Sha daya dai dai Husnah ta cire duvet din jikinta, ta sauka
daga kan gadon, ta zaga ta inda Nihad take bacci kamar warce tayi tseren awa biyu,
janye pillon kanta tayi ta ciro makullin ciki sannan ta ajiye pillown nan gefenta
ta bude jakarta tayi shafe shafen da xata yi sannan ta nufi kofa, bude kofar tayi a
hankali ta fita, taga duk an kashe wutan gidan, tana lalubawa ta nufi dakinsa,
murda kofar dakin tayi slowly ta bude, she saw him kneeling a kusa da gadonsa ya
daura kansa saman gadon wearing just his trousers, ta shigo dakin da sauri ta kulle
kofar da makulli tace "Subhanallahi, me ya faru? Lafiyarka kuwa?" Lkci daya ya dago
da fierce eyes yana kallonta, tayi kasa da murya ta karasa kusa da shi ta durkusa
gabansa tana kallon broad chest dinsa tace "Ko dai baka da lafiya ne?" Bata jira me
zai ce ba don she was more than Randy a moment din, ta kai hannu chest dinsa, lkci
daya cikin dubara tayi loosening din igiyar rigarta, rungumesa tayi gam murya can
kasa tace "Ka gaya min me ya sameka...." rufe idonsa yayi sai kuma ya bude da
sauri, da duk karfinsa yayi karfin halin hankadata gefe har sai da ta fadi, sai
kuma ya mike cikin husky voice dinsa yace "Me ya kawo ki dakin nan?" Daga sama har
kasa take kallonsa, dariya ma ya bata, a wannan yanayin da take kallonsa daga sama
har kasa har yake da karfin halin tambayarta me ya kawota dakinsa, wani er dariyar
bariki tayi, tasan yau TBD straight up, cike da kissa ta cire rigar jikinta ta
jefar nan gefensa tana masa wani shu'umin kallo da lumsassun idanuwa, kauda kai
yayi cikin zafin nama ya nufi belt dinsa dake saman jaka bata ankaraba sai jin
saukan belt tayi a jikinta, gigicewa tayi saboda azaba, ya dinga zabga mata belt
din iya karfinsa, ihu take tana jin kamar ranta ake zarewa sbda azaban belt, ta
dinga neman yanda xata kubuta daga hannunsa ta ihu a gigice, duk inda ta yi haka ya
dinga bin ta yana sauke mata belt din duk inda ya samu a jikinta, a wannan daren
Husnah ta ga jalala, kawai ta sa ma ranta karshen rayuwarta ne ya zo, tun tana
rokonsa da muryarta har muryar nata ya daina fitowa, dukanta yake iya karfinsa da
belt kamar an aikosa, ga shi ta garkame kofar dakin balle ta fita, har bandaki ta
shiga ya bi ta yana duka daga karshe ta fito da rarrafe, dukan da yake mata ya sa
shi jin saukin axaban da yake ji a lkcn, sai da ya gaji don kansa bayan yaga yayi
mata lilis sannan ya jefar da belt din after 30mins kenan, nan ya bude kofar dakin
yana sauke numfashi, tsabar yanda ta jibgu ga kofa a bude amma ta kasa motsawa daga
inda take balle ta fita, ya nufota ya kalla mata wani wawan mari har sau biyu a
fuska ya dau shegiyar rigar baccinta ya hada da ita yana janta ya fito da ita
parlor yayi wani hajijiya da ita sannan ya cillar da ita da rigar ya koma dakinsa,
gudun kar ya sake dawowa ya sa ta karfin halim rarrafawa da kyar ta nufi kitchen,
gaba daya jikinta shatin belt ne rudu rudu ga bakinta sai zuban jini yake, idonta
daya kuwa ya kulle, tana shiga kitchen din hannunta na rawa da strength dinta na
karshe ta saka makulli kafin ta fada kasa rigijib. Tun Khalil na daurewa yana
cijewa, daga nan ya koma can, daga can ya mirgina ya koma nan kamar me labor har
dai yaji he is going to harm himself, he couldn't bear it anymore, Mikewa yayi
kamar wanda aka tsikara ya fice daga dakin, tsaye yayi corridor ya hade kansa da
bango corridon, yana ta tsaye a haka for almost 5 mins sai kuma ya kalli kofar
dakin Nihad, murda kofar yayi amma bai bude ba, can ya runtse ido ya sa kafa ya
tura kofar staggering inside the room, ya manna hannunsa jikin switch din dakin
yana sauke numfashi, standing there for another 2 mins kafin ya kunna wutan dakin a
hankali, tana saman gado ta dukunkune can saman jikinta da hijab daga kasan waist
dinta har ƙafafuwanta kuma babu wani obstacle sai na lingerie dinta and she is
sleeping heavily, hade kai yayi da bango ya rufe ido yana sauke breathing dinsa a
hankali, can ya bude idanuwansa da suka yi jajir, ya kashe wutan dakin ya nufi kan
gadon, gefenta ya fada yayi rub da ciki, perceiving her scent all over, da yayi
attempting kai hannunsa jikinta sai wasu abubuwa suka dinga fado masa a xuciya, and
all of a sudden ya janye hannunsa ya zamo kasa a hankalii ya daura kansa gefen
gadon, yana ta durkushe a hakan har kusan karfe biyun dare, zuwa sannan yayyafi
kawai ake ruwan ya tsagaita... Da kyar Nihad ta bude idonta ta dalilin fitsari da
take ji, ana ta kiraye kirayen sallahn asuba ta sauko daga saman gadon tana layi
xata bandaki, gaba daya jikinta is so weak, tutunbe ta ji ta ci da mutum a kasa
lkci daya kuma ta fada kansa, wani ihu ta fasa a mugun tsorace tana tattabasa amma
lkci daya hankalinta ya ɗan kwanta jin kamshin turarensa, zamewa tayi ta sauka daga
jikinsa ta zauna gefe tana kallonsa cikin duhun don jikinsa taji xafi kamar me, nan
da nan mugun baccin da ke idonta ya washe gaba daya, da sauri ta mike ta tafi ta
kunna switch din dakin, kwance ta gansa nan kasan tiles ko riga babu a jikinsa, ya
bude jajayen idonsa, ta dawo ta duka gabansa tana kallonsa, bata san sanda tace
"Baka da lafiya ne?" Bai ce mata komai ba yayi karfin halin mikewa zaune, ta koma
baya bata kara ce masa komai ba, Mikewa tsaye yayi taga yana layi kamar wanda ya
sha ya bugu, ta tashi tsaye da sauri kafin tace komai yayi baya zai fadi, xaro ido
tayi ta jawosa ita a dole xata tarosa, amma ya rinjayeta sai ga su a kasa, ta zaro
ido cike da azaba tace "Wayyo bayana" Cike da karfin hali ya dagata ya fada gefenta
can underneath his breathe ba tare da yasan ya fada ba yace "Sorry" daga haka ya
kulle idonsa, ta mike zaune tana kallonsa sosai jikinsa yayi zafi, bubbuga gado ta
shiga yi da sauri tana cewa "Husnah, Husnah ki tashi" Amma jin shiru ta daga kai
taga wayam babu Husnah a dakin, mikewa tayi da sauri ta fita parlor nan ma ta
dudduba bata ga Husnah ba, kamar xata yi kuka tace "Toh ina ta tafi?" Sai kuma ta
marairaice tace "Toh ni ya zan yi yanzu?" Juyowa tayi da sauri ta dawo dakin ta
durkusa gabansa tana kallonsa, sai kuma tace "Toh Abba xan kira da wayarka?" Ya
bude jajayen idonsa da sauri yace "Aa" Tashi tayi ta kara fita parlor dai dai nan
taji kamar ana bude kofar kitchen, tsorata tayi tayi hanyar daki da sauri tana
lekan kofar kitchen din, sai ga Husnah baki ya kumbura suntummm lebbenta ya koma
kamar na rakumi, ga fuskarta yayi jajir kamar nama, jini kuma ya kwanta a idonta
daya, dayan idon kuwa ya manne, kayan baccinta ne a jikinta, Nihad ta dafe kirji a
tsorace tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Husnah what happened" Husnah na
dingishi da kyar tace "Aljanun dare" Nihad ta jingina da bango a mugun tsorace tana
zaro ido tace "Aljanun dare kuma?" Husnah ta gyada kai da kyar tace "Akwaisu a
gidan nan wllh, Dauko min jakata da hijabi na" Nihad da hankalinta yayi mugun tashi
tace "Ganinsu kika yi?" Husnah na sauke numfashi tace "Nace ki dauko min jakata da
hijabi" Nihad taki motsawa daga inda take saboda tsoro, Husnah tayi zaman dirshan a
kasa ta rasa inda xata sa ranta ta ji dadi, gaba daya shatin belt din jikinta yayi
jajir gasu rudu rudu, Nihad dake ta kallonta a mugun tsorace tace "Husnah kalli
jikinki fa" A fusace Husnah tace "Ki dauko min jakata da hijabi nace" Nihad ta juya
ta koma daki da sauri bata ga Khalil kwance inda ta bar sa ba, cikin second biyar
ta fixgo hijabi, jaka da wayar Husnah ta fito da gudu daga dakin, Husnah na ganinta
ta mike ko ina na jikinta na rawa ta amshe jakarta da hijab da waya, bayan ta saka
hijab din ta nufi kofa da sauri, Nihad ta fashe da kuka tace "Tafiya za kiyi ki
barni Husnah?" Ko tsayawa Husnah bata yi ba balle ta juyo ta saurari Nihad tuni ta
bude kofar parlon ta fice da sauri ta saka takalminta luckily taga lock kawai aka
sa ma gate din babu key ta bude ta fice daga gidan. Nihad ta koma dakin Khalil da
gudu ta kulle kofar, kan darduma ta gansa sallan ma ya kasa tashi tsaye, ta durkusa
nan kusa da gado tana kallonsa kana ganin idonta kasan ta tsorata sosai, har ya
idar taga ya fada kan darduman ya kwanta ya kulle ido, ita dai tana ta zaune
maganar Husnah na mata yawo a kai, can ta mike a hankali ta nufi bandakinsa, a bude
ta bar kofar, bayan ta kama ruwa ta dauro alwala ta fito da sauri... Tana idar da
sallah ta juya tana kallonsa, tashi tayi ta koma inda yake ta duka hucin zafi take
ji a jikinsa, ta dinga kallonsa, a hankali ya bude idanuwansa jin ta a gefensa, ta
6ata fuska tace "Toh kuma kace kar in kira Abba" Wayarsa da ta hango gefen gado ta
kai hannu ta dauka, yayi karfin halin kwace wayar a hannunta ya lumshe ido, tagumi
tayi tana kallonsa, a hankali tace "Toh ni ya zan yi?" Tana ta zaune gefensa har
gari ya waye gaba daya, tun da ya amshe wayarsa a hannunta bai sake bude idonsa ba,
duk da baccin da take ji amma bata yi ba tana gefensa a zaune, lkci daya taga ya
yunkura ya mike zaune, ta zaro ido ta koma baya tace "Amai zaka yi" Ya sunkuyar da
kansa bayan few minutes ya koma ya kwanta ya kulle ido, a hankali ta kai hannu
forehead dinsa taji har sannan da xafi, ya bude ido yana kallonta, tace "Toh safiya
yayi yanzu ka bani wayar in kira Abbana" murya can kasa taji yace "Dauko takarda da
biro" Tace "Takarda da biro kuma??" Jin bai ce komai ba ta mike har ta nufi kofa
sai ga ta ta dawo da gudu ta tsugunna kusa da shi kamar xata yi kuka tace "Wallahi
Husnah tace min akwai Aljanun dare a gidan nan, duk sun mata duka bakinta ya canxa
yayi wani iri"
Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, kiyi subscription ki karanta
cikin salama er uwa!!!!

Ur evidence via👇🏻

✍🏻
07087865788

Assalamu alaikum manyan mata!!

For your Egyptian Abaya's, mad gowns, laces and handbags and all sort of
jewelries... Give me the privilege to be ur plug plss, and u will never regret it🥰

Message via👇🏻
https://wa.me/c/2349090591769

To view our catalogue🥰


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

34

Nihad tayi shiru tana kallonsa jin bai ce komai ba, bayan few seconds cike da
karfin hali yace "Baxa ki dauko min ba?" Ta marairaice tace "To wai ba nace maka
tsoro nake ji ba, ni baxan iya fita ni kadai ba wallahi, bayan Husnah tace min
aljanun dare na gidan nan" Da kyar ya mike zaune ya nuna mata jakarsa murya can
kasa yace "Bani shi" Mikewa tayi ta tafi ta dauko jakar ta ajiye masa tana
kallonsa, ya jingina da gado, kana ganinsa kasan ba shi da strength, bayan few
seconds a hankali ya bude side din jakar ya ciro jotter da biro ya ciri jotter daya
ya daura kan main jotter din ya fara rubutu da biron, iya layi hudu yayi rubutun
sai kuma ya rubuta digit hudu sannan ya ajiye biron ya kwanta breathing slowly, ta
dau takardan tana ta kallon rubutun sai kuma ta kallesa tace "Wa ya koya ma rubutu
haka?" Ya nuna mata makullin mota yace "Ki je pharmacy ki basu, akwai Atm card dina
a nan, ga pin na rubuta, current account" Sake baki tayi ta kallesa ta sake kallon
takardan hannunta, can tace "lallai, kai ne xaka wani rubuta ma kanka magani, a ina
ka san magani da har zaka rubuta ma kanka? Ko mutuwa kake so kayi?" fizge takardan
hannunta yayi a fusace yace "Bar shi ma" Ta wani hararesa ta kwace takardan tace
"Toh a ina aka ce ka siya maganin nan ka sha tunda kai dai ba likita bane" Kamar
baxai bata amsa ba don shi kadai yasan me yake ji a jikinsa, sai kuma yayi karfin
halin cewa "Likita ya turo min jiya da daddare" Tace "Wannan da ya zo ya dubani
ranan?" Mika mata hannu yayi yace "Idan baxa ki je ba bani takardan" Tabe baki tayi
ta mike ta tafi inda makullin motar yake ta dauka tare da makullin gida da Atm card
dinsa, sai kuma ta kallesa tace "Savings account?" Ba tare da ya buda idonsa da ya
kulle ba yace "Current" Tsayawa tayi tana kallonsa, sai kuma tace "Kasan meye
current account kuwa?" ya bude ido a hankali yace "Bani, ba sai kinje ba kuma" Ta
turo baki tace "To ai ni dai ba ruwana idan naje aka sa current aka rufe maka
account dinka" Daga haka ta nufi kofar har ta bude sai kuma ta dawo ta marairaice
tace "Ni fa tsoro nake ji" Lumshe ido kawai yayi, tayi shiru tana kallonsa, can ta
bude kofar a hankali ta fita kafin kiftawar ido sai ga ta a compound tana maida
numfashi, gun motar ta nufa ta bude ta shiga ta kunna tana warming, sauka tayi ta
tafi gate amma ta kasa turawa har xata koma ta gaya masa sai kuma a hankali tace
"Toh ai shi ma ba iyawa xai yi ba tunda ba shi da lafiya" bude gate din tayi ta
fita kofar gida, ganin wani mutumi tace "Don Allah ka tayani bude gate din nan xan
fita da mota" yana shigowa zai bude mata ta tafi ta shiga motar, bayan ya bude ta
fita da motar waje, tana ganin ya kulle gate din ya fito tayi masa godiya sannan ta
sauka ta kulle gidan da makulli ta hau motar xuwa pharmacy, bayan magunguna har da
allurai taga an hada mata, ta basu Atm card dinsa da har xata ce masu Savings don
bata yarda da current da yace mata ba, sai dai kuma tace "Current" Suka cire
kudinsu suka mayar mata da atm card din ta amsa ta dinga jujjuyawa tana kallonsa,
daga karshe ta amshi ledan maganin ta fito ta tafi zuwa inda tayi parking. Nihad na
isa gida sai da ta kara neman wanda ya bude mata gate ta shiga da mota sannan ya
kulle, godiya tayi masa ta nufi kofar shiga ciki ta bude ta tsaya tana bin ko ina
na parlon da kallo, to ta ina Aljanun dare xa su shigo gidan bayan ko ina a kulle?
sai kuma tayi karfin halin shiga tana tafiya a hankali ta karasa dakinsa ta bude ta
shiga, kwance ta samesa yanda ta barsa ta ajiye ledan maganin hannunta ta durkusa
tana kallonsa tace "Ga maganin na siyo" Ya bude ido a hankali yana kallonta, ajiye
makulli da Atm card din hannunta tayi ta fita daga dakin zuwa kitchen, ba a dau
lkci ba ta dawo dakin rike da cup din shayi ta ajiye masa tace "Gashi" Tashi yayi
ya zauna ya bude ledan maganin da ta kawo ya fiddo su gaba daya, ta dau cup din
shayin ta mika masa tace "Gashi" Ya kalli cup din ya kalleta sai kuma ya amsa,
komawa gefe tayi ta zauna, lkci lkci take satan kallonsa kamar yanda shima yake
satan kallonta, da sun hada ido kuma sai kowa ya dauke kai, har ya kusa shanye
shayin sannan ya ajiye cup din taga ya fara hada allura, tana ta kallon ikon Allah,
taga ya sauke trousers dinsa, zaro ido tayi ta kauda kai da sauri ta rufe fuskarta
da tafin hannunta, bayan few seconds ta juyo a hankali, empy syringe ta gani, ta
mike da sauri tace "Me yasa zaka ma kanka allura?" Bai ko kalleta ba ya bude
maganin ya sha da sauran shayin da ya rage sannan ya koma ya kwanta ya lumshe ido
ta dinga kallonsa da mamaki, har bayan kusan minti goma bata ga ya bude idon ba sai
ma taga kamar bacci yake, juyawa tayi ta fita daga dakin ta koma parlor ta zauna,
ko minti sha biyar bata yi a parlon ba taji ana kwankwasa gate, ta tashi da sauri
ta koma daki, bacci taga yana yi heavily, ta dau makullin gidan ta fita zuwa gate
ta bude, Amina ta gani a tsaye sanye da uniform din islamiyya don ranan lahadi ce,
Amina na mika mata waya tace "Ina kwana, wai gashi Umma xata maki magana" Nihad ta
amshi wayar sai ga kiran Umma dagawa tayi ta kai kunne daga daya bangaren Umma tace
"Kin isa gidan Amina?" A hankali Nihad tace "Umma ina kwana?" Umma tace "Ya haka
Nihad, tun jiya ina ta jiranki shiru, Nayi ta kiran Husnah kuma bata daga wayar, ko
ta bar gidan ne?" Nihad tace "Ehh ta tafi Umma" Umma tace "Amma ba sai da nace maki
kar ki bari ta bar gidan ba sai mun gama magana da ke?" Nihad tace "Nima tashi nayi
naga bata gidan" Umma tace "Toh Allah ya kyauta, kin tambayesan kuwa?" Nihad tace
"Ehh Umma, yace min sunan Mamarsa Nihad" Umma tace "Amma dai ke shashasha ce
wawuya, sai kika yi shiru kika kyalesa da yace maki haka?" Nihad tace "Wallahi haka
yace min" Tsaki Umma tayi tace "Baki da wayo ko kadan wallahi, kuma banga alamar za
kiyi wayon nan ba, ai shkkn sai kiyi ta zama da dreban, ni sai anjima, haba sai
kace ba mace ba ki rasa yanda xa ki bi da shi har ya gaya maki sunan iyayensa, ni
gata nake maki, gatan da uwarki ko mutuwa xaki yi baxata ta6a maki ba" Cikin sanyin
murya Nihad tace "Toh xan kara tambayarsa Umma kiyi hakuri" Umma tace "Ni sai
anjima da Allah" daga haka ta katse wayar cike da bacin rai, Amina ta karba tace
"Kin gama?" Nihad bata ce mata komai ba, Amina tace "Sai anjima" Daga haka ta shiga
adaidaita da xai kai ta islamiyya don kudin drop Umma ta bata, a hankali Nihad ta
juya ta koma cikin gidan. Umma ce zaune gaban wani Rantamemen mutumi ita da Hajiya
Turai, Umma na girgiza kai tace "Wallahi Malam ba a samo sunan iyayen nasa ba,
kasan yarinyar shashasha ce ga ta kuma er fari, ba wayo" Mutumin dake kallonsu da
jajayen tulla tullan idonsa yace "To ai tun farko nace maki xa a iya aiki da sunan
nasa kadai kuma aiki zai ci kamar yankan wuka, kawai ku dai in ji dumuss" Umma ta
gyara zama tace "Toh madallah malam, kuma ai kai ma kasan kudi ba matsala bace"
Yana muxurai yace "Ya kika ce sunan nasa?" Umma tace "Ibrahim" Girgiza kafa ya
dinga yi, bayan kusan minti daya ya kalleta da gefen ido yana murmushi yace "Yana
nan wani me kyau, dogo sangameme sannan shi ba baki ba, yana kuma da faffadan
kirji" Umma tace "Haka yake wallahi malam, duk yanda ka fada wllh haka ne" ya
kyalkyale da wani dariya Yace "Toh ai jefaffe ne tun asali, Jifa kuwa ba na wasa ba
aka yi masa, ga shi nan naga jifa iri iri a kansa, a jefe yake..." Su Umma dai suka
yi shiru suna kallonsa, ya langwabar da kai kamar me nazari sae kuma ya gyada kai
yace "Gashi nan an nuna min, ashe ma ruwa biyu ne, ko ta ɓangaren uwa ko na uba"
Umma tace "Ba shakka, hakan take malam, ai buzu ne, uwarsa wai er Nijar ce" Yayi
wani dariya yana jijjiga kai, Umma tace "Toh amma daga ina aka masa asirin Malam?"
Mutumin yayi wani shu'umin murmushi yace "Ɗan wani kauye ne kika ce?" Umma ta
girgiza kai tace "Aa, shi dai maigidana ne yasan sunan kauyen nasu tunda har can
yaje aka daura auren amma ni ban sani ba gaskiya" Yace "Toh daga kauyen nasu aka
jefesa, wato ana masa bakin ciki da ɗan abun da yake samu" Yana gyada kai yace "Shi
din me kwazon nema ne tun da ya taso, yana kuma da farin jini, dalilin da yasa ake
jifansa kenan.... Sihiri me karfi aka yi masa gashi nan na gani" Umma tace "Ikon
Allah, kuma gashi an ga ya fito birni nema dole kuma ya dinga samu sosai" Mutumin
yace "Kwarai kuwa, sannan kamar yanda nace maki Allah yayi sa da farin jini da
cikar kamala, duk wanda ya ra6a sai ya so shi so na gaske, zai kuma iya damka masa
amanar dukiyarsa sbda yarda" Umma ta wani hade rai tace "Toh ni sai6 yanzu so nake
ayi masa yanda sisin me gidana baxai sake shiga hannunsa ba don Ubansa, kasa masa
mugun tsanarsa wanda xai ji baya son ganinsa baya son mu'amala da shi har abada"
Hajiya Turai dake kallonta tace "Idan aka yi haka ke kuma ai sai ya iya cewa sai ya
sakar masa er sa" Shiru Umma tayi tana nazari, can wayar Umma ya fara ring ta bude
jaka da sauri ta fiddo ganin me kiranta tace "Minti biyu Malam" Daga haka ta mike
ta fita can tsakar gida ta daga wayar ta kai kunne tace "Malam barkanmu da safiya"
Ta kara da cewa "Eh ba a dai samo sunan ba amma nan da awa daya za mu karaso in sha
Allah, don Allah ka jira mu Malam kaga dai daga waje me nisa za mu zo" Hajiya Turai
na kallon Mutumin dake gabanta tace "Kana ji malam? so muke shi Alhajin ya fita
tsabgar daga shi dreban har yar tasa, sannan maganan gini da yace zai ma yar a
Zaria a rushe zancen kwata kwata, malam gaba daya a sa yaji bai son su gaba daya,
bai kuma son ganinsu, ita yar dama kawai ya sallama ma duniya ita, sannan abu na
karshe ka saka ma shi dreban jin son zai koma inda ya fito wato kauyensu, ka sa
zaman birnin ya gagaresa, idan ya so su koma can inda ya fito su ci gaba da zama
shi da ita yarinyar" Umma ta shigo ta zauna, Hajiya Turai ta kalleta tace "Duk na
gama gaya masa abinda zai yi" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh shikenan"
Dariya mutumin yayi sosai yace "Kudi... Aikinku aiki ne babba, kuma aiki dole sai
da kudi, kinga kafin mu daura aiki a kansa dole za mu warware kadan daga abubuwan
da aka masa sannan aikin mu
xai samu shiga, ba a hada aiki da aiki ai, sai wancan aikin nasu ya lalata min
nawa, wato ya ki barin nawa yayi wani tasiri, ko kuma nawa ya rage tasirin nasu,
haka abun yake, yanzu dai nine xan rage tasirin na kansa sannan in dora nawa" Umma
tace "Tohh mu dai koma yaya za ayi kawai mu ga mun ci nasara malam, sannan ya dai
ci ace an saba yanzu Malam, abu dai shekara da shekaru ana tare ana harka, wannan
karan a dubemu karba tsula mana kudi" Hajiya Turai tace "Ai kuwa dai malam, ayi
mana sassauci gaskiya" Yana ta6e baki na wasu yan sakwanni sai kuma yace "Kawai ki
dire dubu dari da hamsin idan aikinki ya ci ki cika dubu hamsin" Umma ta bude
jakarta ta ciro zoben gwal ta ajiye masa tace "Gashi nan wannan dubu dari da
tamanin ce, ka rike ka fara min aiki" Ya amsa yace "An gama" tace "Toh malam zuwa
nan da yaushe za a fara aikin sannan za a fara ganin tasirin aikin?" Yace "Yanzu
zan afka jeji in fara aikinku babu bata lokaci, gaba daya a yau xan yi duk abinda
xan yi, zuwa gobe kuma aiki zai fara ci kamar yankan wuka" Umma na Murmushi tace
"Toh mun gode Malam, Allah ya saka maka da alkhairi, aikin ka ai mun san ba wasa,
mu yanzu za mu tafi sai na kira ka" Daga haka suka masa sallama suka kama hanyar
wani kauyen daban. Nihad na ta zaune parlor har kusan sha biyu, can ta mike ta nufi
dakin da yake kwance, a hankali ta murda kofar dakin tana kallonsa saman gado ta
gansa yana bacci, ta rufo dakin sannan ta shiga dayan dakin tayi wanka ta dauro
alwala ta shirya ta fito, sai da ta fara zagayawa ta kwaso kayan da Husnah ta wanke
mata ta kai su daki ta linke daga nan ta dawo parlor ta shiga kitchen, kallon
kitchen din kawai take, akwai kayan miya da komai a gidan kawai nama ne babu tunda
babu fridge, ta fito ta tafi dakinsa, ta bude kofar trying to make no sound, gun
Atm card dinsa ta tafi ta dauka da makullin mota da na gida sannan ta fito, cikin
mintin da bai wuce talatin ba ta fita taje ta siyo frozen chicken guda biyu da few
spices sannan ta dawo gida, ta sake daura alwala tayi sallah bayan ta idar ta koma
kitchen din, sai kusan karfe biyu ta fito daga kitchen bayan ta gama duk abinda
take, gaba daya ta gaji likis uwa wace tayi girkin mutane goma, ta fada kan kujera,
har ta mance rabon da tayi girki don ko da wasa Umma bata sa ta wai saboda hayaki
da warin gas, duk sanda taje gidan Aunty Jamila ne take girki don dama Aunty Jamila
chef ce, tana gwada mata abubuwa da yawa na girke girke, saving grace din Nihad
kenan da har Allah ya taimaketa ta iya girkin, tana ta zaune parlon sai kuma ta
mike ta tafi dakinsa ta bude tana kallonsa, bata ga alamar yayi sallah ba, ta
karasa ciki ta tsaya side din gadon ta bubbuga pillown da yake a kai tace "Baka yi
sallah ba" Ya bude ido da kyar ya kalleta yace "Ina ruwanki?" Kyabe baki tayi tace
"Toh don ma ka samu ina tashin ka?" Ta wani juya ido ta juya xata fita ya bi ta da
kallo, sai kuma yace "Ina son ruwan zafi" Ta jefa masa wani kallo tace "Toh meye
zaka gaya min? Ko house help dinka ce ni?" Daga haka ta fice daga dakin, lumshe ido
yayi yana son tashi amma ba shi da enough strength din yin hakan, bayan kusan minti
ashirin har wani baccin ya kara daukesa ta shigo dakin rike da kettle din ruwan
zafi, ya bude ido da sauri jin sound din bude kofar, bandaki ta shiga ta dauraye
bucket ta juye masa ruwan zafin a ciki tana fitowa kuma ta fita daga dakin ba tare
da ta kallesa ba, ya yunkura ya mike zaune sannan ya sauka daga saman gadon ya
shiga bandakin. Ko da ya fito yaga abinci ajiye a dakin, ya gama shiryawa yayi
sallahn zuhur, yana ta zaune saman darduma yana kallon warmers din abincin, can ya
jawo karamin warmer din ya bude aroma din miyan ya doki hancinsa, ya bude dayan ya
ga shinkafa ce, kawai zuciyarsa ya basa ai aiko mata da abincin aka yi ya kulle ya
matsar daga kusa da shi. Har aka yi la'asar Nihad bata sake shigowa dakin ba, zuwa
lkcn he is feeling much better, fitowa daga daki yayi ya ganta kwance kan 2 seater
tana bacci, ya karasa cikin parlon, a hankali ya kai hannu ya buga kujeran, ta bude
ido da sauri zata kwala ihu ta gansa, don duk tunaninta aljanin daren ne ita ma ya
zo mata, Ya dauke idonsa daga kallonta yace "Sallah" Tace "Ina ruwanka?" Bai ce
komai ba ya juya ya koma daki, karamar wayarsa ya dauka ya zauna gefen gado yaga
miss calls din Nadeeyah har hudu sai kuma miss calls din Abba biyu, sannan message
na debit din dubu ashirin da biyar bayan debit din drugs da ta siyo masa da safe,
yana ta kallon debit din sai kuma ya mike ya fita daga dakin tana zaune kan kujera
yana kallonta yace "Me kika min da dubu ashirin da biyar?" Ta kyabe baki tace "Toh
kaza naje na siya na dubu goma nayi girki don ni baxan dinga cin abinci lami ba,
bayan nasan Abbana na baka har da kuɗin nama, dubu biyar kuma na siyo spices, dubu
goma kuma na zuba mai a mota, idan ma kudin account din ne suka kare ai sai ka
kirasa kace sun kare" Kallonta ya dinga yi, ta ɗan kallesa ta gefen ido, sai kuma
ta turo baki ta mike ta wuce dakinta ya bi ta da kallo, komawa cikin dakin yayi ya
kara bude abincin da tace tayi yana kallo, har cikin ransa bai yarda ita tayi
girkin ba duk da bai ci ba, can dai ya dau spoon yayi tasting stew din, nan ya kara
tabbatar ma kansa ba ita tayi ba, duk da yunwan da yake ji bai ci abincin ba. Da
magrib bayan ya fito daga masallaci ya ga almajirai biyu ya tsayar da su sannan ya
shiga cikin gidan ya fito da abincin ya juye masu ya koma kitchen ya wanke warmers
din ya fito, daki ya shiga ya dauko makullin mota da atm card dinsa ya bar gidan,
tana jin ya fita ta fito balcony da sauri ko gama goge jikinta bata yi ba don wanka
take taji ya kunna mota ta kwara ruwa kawai ta daura tawul ta fito da gudu, Hijab
dinta da ta fizgo ta saka a kan tawul din, duk a tsorace take da gidan tun da taga
gari ya fara duhu dama hankalinta ya tashi, can saman dakalin da yake zama ta tafi
ta zauna hawaye cike idonta, ta fi awa daya wajen zaune ga uban sauro dake ta
cizonta har da guntun gyangyadinta, sai bayan isha ya shigo gidan, bayan yayi
parking ya tafi ya kulle gate ya dawo yana kallonta amma bai ce mata komai ba,
juyawa yayi ya shiga cikin gidan ta bi bayansa da sauri cikin kuka tace "Ni wallahi
kar ka sake fita ka barni ni kadai cikin gidan nan da daddare, don baka ga abinda
ya faru da Husnah bane har ta bar gidan shi yasa zaka wani tafi ka bar ni kadai
kuma ka tafi da makulli" Ya juya ya kalleta yace "Wacece Husnah?" Ta hade rai tace
"Kawata da ta zo gidan nan ta kwana mana" Yace "Ohhh ta tafi ne?" Nihad tace
"Aljanun dare ne fa suka zaneta fuskarta duk ya kumbura shine ta gudu" Yace "Au
haba?" Ta wani daure fuska tana kallonsa, yace "Toh Allah ya sa kar su dawo kanki
tunda ita ta gudu" Yana fadin haka yayi hanyar dakinsa ta bi sa da gudu ta fashe da
kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me yasa zaka ce min haka? Me nayi
masu ni za su dawo kaina?" Yana shiga dakinsa ita ma ta shige tana kallonsa tana
maida numfashi hawaye cike idonta, duk a mugun tsorace take, yace "Malama kwanciya
xan yi ki tafi dakinki sai da safe" Ta wani gwalo ido tana kallonsa, sai kuma kawai
ta nufi can karshen gadon dakin ta zauna, ya tsaya yana kallonta sai kuma yace
"Ohk, sai in bar maki dakin in koma wancan" Bata san sanda ta fashe da kuka ba tace
"Don girman Allah kar ka barni ni kadai wallahi tsoro nake ji kuma baxan iya kwana
a dakin ni kadai ba" Sai kuma ta hade kai da gwiwa tana rera kuka, bai kuma ce mata
komai ba ya kulle kofar ya karasa cikin dakin. A hankali ta mike ta shiga bandaki
ta dauro alwala ta fito ta tada sallan isha, yana kwance daya side din gadon waya
kare kunnensa, duk da can kasa kasa yake magana amma lkci daya ta gane da warce
yake wayar, ta ja tsaki ta mike ta dauke darduman ta linke ta ajiye ta nufi saman
gadon ta fizge duvet da ke kai ta dau pillow daya ta shimfida duvet din a kasa
sannan ta ajiye pillon ta kwanta, tana ta juye juye kan duvet din can ta kara jan
wani tsaki ta tashi ta tafi ta kashe wutan dakin ta dawo ta kwanta, shi dai bai
daina wayar da yake ba kuma duk maitarta baxata ce ta ji abinda yake cewa a wayar
ba, for almost one hour bai gama wayar ba, ya mike sabida iska da aka fara alamar
hadari, kunna wutan dakin yayi Nihad da tayi lamo a kasa tana jin iskan ita ma ta
mike zaune da sauri ta bi sa da kallo sai kuma ta tashi ta bisa parlon, ya juya ya
kalleta, sai kuma yace "Zan kwanta yanzu kinsan nace maki bani da lafiya, za mu yi
magana gobe" Daga haka ya katse wayar yace "Lafiya kike bi na?" Kin cewa komai tayi
tana kallonsa, haka kawai tayi masa rashin kunya ya ki yarda ta kwana a dakinsa,
shi sa ma taki ce masa komai juyawa yayi ya tafi ya kulle duk windows din gidan,
duk inda ya nufa sai ta bi sa har dakinta sai da ya shiga ya kulle windows sannan
ya fito tana biye da shi suka koma dakin nasa, kulle nasa windows din yayi ya kashe
wutan dakin ya kwanta daya side din, ba a wani dau lokaci ba aka fara yayyafi,
Nihad dai duk a tsorace take a kasa da take kwance, can ta mike zaune a hankali
tana kallon saman gadon, sai kuma ta turo baki ta mike ta dauke pillown da duvet ta
koma saman gadon ta kwanta, yana jin ta bai ce komai ba sai ma juya mata baya da
yayi ya rufe ido, Nihad na jin sauwkan ruwa ta mirgina a hankali ta koma bayansa
tayi lamo, ta dade a hka ta kasa bacci, kamar yanda shi ma ya kasa baccin, da taji
anyi tsawa sae ta kara matsawa gun sa, a haka har bacci ya dauketa daga karshe....
Can cikin bacci ta ji ana ta6a ta, ta bude ido a tsorace, xata bara ihu ya rufe
bakinta da Palm dinsa.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence of payment via 07087865788

Assalamu alaikum manyan mata!!

For your Egyptian Abaya's, mad gowns, laces and handbags and all sort of
jewelries... Give me the privilege to be ur plug plss, and u will never regret it🥰

Join my WhatsApp group for beautiful samples. https://wa.me/c/2349090591769[8/15,


8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

35

Bayan sun isa gida Khalil ya ba mai adaidaita sahun da ya kawosu kuɗinsa, Nihad dai
ta jingina da gate ta rufe fuskarta da Hijab din jikinta tana kuka kamar ranta zai
fita tana jin xuciyarta na mata zafi, har sannan she is finding it hard to believe
Abbanta ne yace baya son sake ganinta har abada, wai yau ita Abba ke ce ma haka,
where is all the love he showed her? she wish her life could end now let all this
be over, Khalil ya bude gate din ta shiga ciki da sauri tana kara sautin kukanta,
da ido ya bi ta bayan ya kulle gate din har ta shiga parlor, yana tafiya a hankali
ya tafi inda yake zama ya zauna ya jinginar da kansa da bango, har aka yi magrib
yana wajen a zaune yayi nisa tunanin da yake, at this point he knows he is confuse
because things have taken another turn, he neva saw all this coming, daga karshe ya
mike gwiwa a sanyaye yayi alwala a tap din dake compound din ya fita zuwa
masallaci, bai kuma fito daga masallacin ba har sai da aka yi sallan isha... Yana
dawowa ya shiga parlor, tana zaune a parlorn ta hade kanta da gwiwa har sannan bata
daina kukan da take ba, ya karasa ciki yana kallonta, zaunawa yayi saman kujera
still looking at her, he don't even know what to say to her, beside he don't even
have anything to say to her, he felt exactly what she is feeling right now some
years ago, and he knows the feeling, tuna hakan yasa zuciyarsa yayi rauni, tashi
kawai yayi daga karshe ya shige dakinsa ya kulle kofar. Khalil bai sake fitowa ba
sai kusan karfe sha biyun dare, kwance ya sameta inda ya bar ta bacci ya dauketa,
ya karasa ya durkusa gabanta yana kallonta, gently yayi tapping dinta, ta bude ido
da sauri, sai kuma ta mike xaune tana murza idanuwanta da suka kumbura, yace "Ki je
ki ci abinci ki yi sallah" Daga haka ya mike ya koma dakinsa ya kulle kofar, ta
jinginar da kanta da kujera wasu hawayen masu zafi na sauka idonta, gaba daya taji
duniyar yayi mata zafi, me yasa Abbanta zai ce mata baya son ganin har abada, me
yasa abbanta zai yi mata irin wannan koran kuma Umma na jinsa amma bata ce komai
ba, she saw everything that happen amma tayi shiru, sosai ta fashe da kuka kamar
ranta zai fita, bayan kusan minti talatim ta mike a hankali jiki ba kwari ta wuce
dakinta tana jin jiri, alwala kawai tayi, tayi magrib da Isha ta kwanta kan
darduman tana duk addu'an da ya zo bakinta hawaye na sintiri a gefen fuskarta,
daren nan Nihad bata yi baccin kirki ba, da baccin ya dauketa zata farka a firgice,
wajajen karfe tara na washegari Khalil ya bude kofar dakinta yana kallonta yace "Ki
dau duk abinda za ki dauka ki fito parlor, ina jiranki yanzu" Yana fadin haka ya
juya ya bar wajen, Nihad ta mike zaune just staring at the door, sosai kanta ke
mata ciwo kamar zai fashe, bayan few minutes ta mike ta canza hijab kawai ta fito
parlorn tana tafiya a hankali, yana zaune ya jinginar da kansa da kujera bayan ya
kashe duk wani abun wuta na gidan, ya kalleta yace "Ina kayan?" Ta girgiza kai
cikin karfin hali tace "Ba abinda xan dauka" Shiru yayi bai ce komai ba, can yace
"Ki je ki karya..." Nan ma ta girgiza masa kai alamar baxata yi breakfast din ba,
bai kuma cewa komai ba, ita dai tana ta tsaye parlon kanta a kasa, har zuwa lkcn
tana ganin scene din abinda ya faru jiya ya kasa bacewa a idonta, daga karshe
Khalil ya mike yace "Mu je" Bin bayansa tayi tana jin kamar zata fadi har suka fita
daga parlorn, ya kulle gidan, suna fita gate taga motar haya irin warce ke zuwa
kaduna, Abuja anyi parking a bakin gate din, tana dai tsaye har ya gama kulle gate
din gidan ba tare da ya kalleta ba yace "Shiga motar za ki yi" A hankali ta kai
hannu ta bude bayan motar ta shiga ta zauna ta kulle, ya zauna a gaba, tun da aka
haifeta bata ta6a shiga ire iren wannan motar ba sai yanzu, ta goge hawayen dake
makale idonta tana wasa da fingers dinta, sai da Khalil yasa suka fara zuwa can
gida ya mika ma Aminu makullin gida yace ya ba Abba, Aminu har da kwallarsa yace
"Toh yanxu sai yaushe kenan??" Khalil na kallonsa yayi murmushi cikin sanyi yace
"Khairan in sha Allah Aminu" Daga haka yayi patting shoulder dinsa ya shiga motar,
Aminu ya bi sa da kallo, dama tun da suka shigo layin Nihad ta hade kai da gwiwa
hawaye na sauka idonta don bata ma son taga gidan nasu, balle ace kallon karshe ta
ma gidan, har kuma suka bar layin bata dago ba sai shesshekar kuka take tana ganin
duk abinda ke faruwa kamar a mafarki, sai da taji sun yi nisa sannan ta dago kanta
tana goge hawayen da yaki tsaya mata.... Ba su yi awa daya ba suna tafiya taji
zuciyarta na tashi saboda warin fetur da take ji motar na yi, daga karshe ta toshe
hancinta da hijab din jikinta, tun dai tana daurewa har dai suna dab da isa garin
zaria ta tabo khalil dage gaba, ya juya da sauri, ganin yanda ta rufe bakinta da
hannu biyu yasa shi ce ma Drivern ya nemi waje ya tsaya, dreban na bakin a gefen
titi ta sauka da sauri ta dukurkusa gefen hanyan tana yunkurin amai, Khalil ya
sauko daga motar ya jingina da motar yana kallonta, kasancewar ba abinda ta ci yasa
bata yi aman ba, sai kokarin kakaro shi take amma babu abinda ya fito, shi dai yana
tsaye yana kallonta, bayan few minutes ta mike da kyar ta koma motar tana maida
numfashi, shi ma ya koma cikin motar, driver na mata sannu ta gyada masa kai kawai,
a haka suka ci gaba da tafiya, kafin su isa kaduna tayi hakan yayi sau hudu amma
duk bata iya tayi aman ba, Khalil ya sa drivern ya tsaya a wani restaurant cikin
garin kaduna ya sauka ya siyo mata abinci, yana fitowa daga restaurant din ya ganta
durkushe jikin motar ta sauko, duk tayi zuru zuru kamar ba ita na, tana ganinsa ta
mike da kyar, hawaye cike idonta cikin sanyin murya tace "Ni baxan iya ci gaba da
tafiya a motar nan ba, yana min warin fuel" Yace "Ohk, yanzu ya za ayi kenan?" Tayi
shiru bata ce komai ba tana share hawayen idonta, yace "Ko kina da kudi ki biya
mana jirgi" Ta daga kai da sauri ta kallesa, can kuma tace "Ina za mu je ne?" Yayi
shiru yana kallonta, sai kuma ya dauke kai yace "in kina da kudin jirgi sai ki siya
mana ticket kawai, babu ke babu jin warin fetur, in kuma baki da halin wannan za ki
iya siya mana ticket din jirgin kasa mu tafi mu hau yanzu" A hankali tace "To ai ni
bani da ko sisi a account dina" Yace "Shine kike korafin mota na maki warin fetur?"
Ita dai bata ce komai ba, yace "Kina bata mana lokaci" Juyawa tayi ta bude motar ta
shiga ya mika mata ledan hannunsa ta amsa ya kulle motar sannan ya shiga front seat
yana kallon dreban yace "Muje" Driver ya tada motar suka ci gaba da tafiya, iya
wahala Nihad ta wahala kafin su isa Abuja, abincin ma ta kasa ci, banda ruwa kawai
da ta sha, shi ma duk sai da ta amayar da shi, sai bayan la'asar suka shigo Abuja,
wani hotel kawai ya sa drivern ya sauke su, drivern ya sauko masa da kayansa daga
motar, Khalil yayi masa godiya sosai, sannan drivern ya ja motarsa ya bar wajen, A
reception din hotel din Nihad ta zauna ta kife kanta saman kujeran gefenta tana
maida numfashi, har khalil ya biya masu kudin daki bata sani ba, sai da ya kai
kayansa ciki sannan ya dawo yana kallonta, she looks sick and tired, yace "Nan din
ya fi maki ne?" Ta dago da sauri tana kallonsa, ya juya ya bar wajen, sai kuma ta
mike ta bi bayansa tana tafiya a hankali, bayan yayi leading dinta har zuwa dakin
ya sake fitowa yayi masu ordering abinci a hotel din, daga nan ya fita pharmacy ya
amso mata paracetamol sannan ya koma dakin, kwance ya sameta saman gadon tana
baccin wahala, ya tafi kan kujera dake dakin ya zauna, bayan few minutes aka
kwankwasa kofar dakin ya mike ya tafi ya bude ya amso abincin da yayi ordering
sannan ya kulle kofar ya dawo ciki ya ajiye abincin, dama abinda yake jira kenan,
ya shiga bandaki yayi wanka ya fito ya shirya sannan ya fita dakin don Bolt din da
yayi ordering na location dinsa, da har zai kulle kofar dakin da makulli sai kuma
ya fasa, yana fita hotel din ya shiga motar suka tafi. Tafiyar kusan minti talatin
da biyar suka yi bayan sun shigo wani anguwa wanda kai kana gani kasan ba kowa ke
shigowa area din ba, Drivern bolt din ya kalli khalil da turanci yake tambayarsa
ana shiga ciki dai ko? Khalil yace masa ya shiga kawai, drivern ya ja motar yana
driving din a hankali zuwa gate din dake gabansa, tasowa ma'aikatan dake wajen suka
yi, drivern ya kalli Khalil da ya sauke glass din motar ya gaisa da su sannan
drivern ya ci gaba da tafiya slowly, tafiyar minti sha biyar drivern yayi ya tsaya
dai dai wani gida wanda nan ne location da Khalil ya saka, ma'aikatan dake wajen
suka taso xuwa gun motar, Khalil ya bude motar ya sauka ya daga ma drivern bolt din
hannu sannan ya nufi gate din gidan, bai amsa gaisuwan da securities din ke masa ba
ya shiga ciki kawai, har ya isa main entrance din babban duplex din babu wanda ya
kalla a compound din balle ya amsa gaisuwan da suke masa, direct part din Maminsa
ya nufa ba tare da ya hadu da kowa a hanya ba, ya bude kofar parlonta na farko a
hankali, babu kowa ciki sai sanyin Ac da kamshi me dadi dake tashi a parlon, ya
karasa daya parlon ya shiga, nan ma ba kowa ciki..... Dai dai nan ta fito daga
bedroom dinta da Mai aikinta, tsaye tayi with shock tana kallonsa baki bude, ko
kwakkwaran motsi bata yi sbda shock, ya karasa a hankali ya rungumeta ya lumshe
idonsa, cike da karfin hali tace "Khalil??" Mai aikinta ma haka ta koma gefe ta
rufe baki da hannu tana kallonsa, kasa ce ma Maminsa komai yayi, ta dago kansa tana
kallonsa hawaye cike idonta tana girgiza kanta, yayi mata murmushi cike da karfin
hali yace "I have missed u soo much Mami" Ta kara rungumesa ta fashe da kuka sosai
tace "How did you get here? Who allowed you in? Ta ina ka shigo?" Ya kasa ce mata
komai lkci daya idanuwansa suka kada, Mai aikin ta nufi kofa ta fita ta kullo masa
kofar a hankali, Mami ta ja sa zuwa bedroom dinta tana kallonsa hawaye na sauka
idonta tace "How did you get here son?" Sauke idonsa kasa yayi ya tafi gefen
makeken gadonta ya zauna, tafiya tayi da sauri ta zauna gefensa ta kamo hannunsa
tana kare masa kallo,
ba ainahin haskensa ba kenan, sannan ba haka ya bar gidan nan ba, ta fashe da kuka
sosai ta dafe kanta ta kasa ce masa komai, yayi karfin halin cewa "Kiyi hakuri
Mami, surely everything that has beginning will definitely have an end" Ta dago kai
cikin kuka sosai tace "Amma ta yaya ka shigo gidan nan Khalil?" Kallonta kawai
yake, Bayan few seconds a hankali yace "Abba ne ya kirani" Mami ta zaro ido tana
kallonsa da kyau tace "You mean da kansa ya kiraka??" Khalil ya gyada mata kai yace
"Yea Mami, i don't know what he is seeing me for" Hankalin Maminsa ya kara tashi,
ta hadiye abu da kyar tace "When did he call you?" Khalil ya sauke idonsa yace
"Jiya...." Mami tayi tagumi with different thought running her mind, can ta tashi
tace "Ohk, but u are not moving an inch from here today, ka bari sai nan da jibi,
babu wanda xai san kana gidan nan, you just remain here for now, ok?" Kallonta
Khalil ya dinga yi ya kasa cewa komai, ta mike ta dau wayarta da sauri tayi dialing
number mai aikinta, tana dagawa tace "Bilkisu kada ki ce ma kowa khalil ya dawo
yana gidan nan, make sure babu wanda xa ki gaya ma har su Mimi" Bilkisu tace "Dama
babu wanda na gaya ma Mami" Mami tace "Good" Daga haka ta katse wayar, Khalil dake
ta kallonta yace "But i have to go out before Magrib Mami" Mami ta zaro ido tana
kallonsa tace "Out to where? u are going nowhere for now Khalil, ko nan da second
parlor dina baxa ka fita ba i am telling you, u will remain here for now" Kasa ce
mata komai yayi ya dinga kallonta, ta juya da sauri ta fita daga dakin, ba a dau
lokaci ba sai ga Mami da tray me dauke da different fruits ta ajiye masa, Mai
aikinta dake biye da ita ta ajiye nata tray din, before 5 minutes duk aka cika masa
gabansa da abinci iri iri da natural drinks, bayan mai aikin ta fita Mami ta kasa
daina kallon ɗan nata, tana yi tana share hawayen da ya ki tsaya mata, har sannan
gani take kamar a mafarki ne, gani take xata farka taga babu shi, dawowa tayi kusa
da shi cike da karfin hali tace "Tell me what u want to eat in zuba maka son, fried
rice? Jollof rice, tuwo da miyar taushe, sinasir? Cous cous? Is it the pepper
chicken u are taking first or the cow leg pepper soup?" Kallonta kawai yake ya kasa
cewa komai, lkci daya jikinsa yayi sanyi, he knows he missed all this, ta fashe da
kuka ta rungumesa tace "My prayers was always with you son, i know i have missed u
a lot, i just had nothing to do about it" Kuka take sosai, ya runtse ido yace "Pls
ki daina kukan nan Mami, i was fine and comfortable all through, kawai dai na kan
yi kewanki da kannena sosai hakan ne kadai ke samin damuwa" Mami ta sake sa ta
sauka ta fara zuba masa abincin iri iri a plate, shi dai kallonta kawai yake, bayan
ta gama zuba masa tace "Ka ci duk abinda kake son ci sai kayi wanka son, let me get
u what to change" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, fadawa yayi
saman gadon, gaba daya hankalinsa ya tafi kan Nihad da ya bari ita daya a dakin
hotel, from where will he start convincing his mami har ta hakura ta bar sa ya
fita?? Not even that, don kuwa wannan me sauki ne, now!! from where is he going to
start explaining to Mami cewar ai an masa aure? Ta yaya zai fara mata wannan
gagarumin bayanin and how will she even take it balle uwa uba Abbansa, tunanin
hakan scent cold all over his body, ya mike zaune a hankali yana jin wani sanyi na
shigarsa sosai, tun barinsu kano hankalinsa bai tashi haka ba sai yanzu, ta ina zai
fara wannan bayanin yace ai an masa aure wanda shi ma ba da son ransa ya amshi
auren ba, Yaya iyayensa da relatives dinsa da ma yan uwansa gaba daya za su dauki
wannan babban lamarin, aure without his parents consent, this now is his biggest
challenge so far, rike kansa yayi bayan yaji kansa ya wani tsara masa, After some
minutes Mami ta dawo dakin da kayansa da ta saka a leda don ma kada wani ya gani,
kannen Khalil kuwa duk ta hanasu zuwa ɓangarenta a sunan she is not okay and she
needs privacy, da sauri khalil ya dago bayan Maminsa ta shigo dakin, ganin bai ta6a
abincin ba da damuwa tace "C'mon pls ka sauko ka ci abinci Khalil kar ya huce, ko
dai akwai wani abun dake damunka har yanzu..." Khalil ya dinga kallonta yana
tunanin ta inda zai fara, can dai yayi karfin halin cewa "Mami na ji kince baxan
fita ba, kuma fitan da xanyi yanxu is very urgent" Mami ta zauna kusa da shi cikin
rawar murya tace "I am afraid baxan sake ganinka ba kuma Khalil, kilan idan ka fita
baxa a sake barin ka shigo gidan nan ba, i can't..." kawai sae ta fashe da kuka
tana girgiza kai cikin tashin hankali tace "Haka jikina ke bani, i can't endure
loosing u for the second time son, ban san me zai faru da ni ba idan hakan ta
kasance, me xaka fita kayi Plss?" Ya sauke idonsa da ya kada, bayan few seconds
cikin sanyin murya yace "Mami gidan da nake zama a garin kano da nace masu zan taho
Abuja yau sun hadani da er su muka taho tare da ita, zata karbi admission letter
dinta a wani makaranta da tayi applying a nan, she knows nobody in here Mami, kuma
har yanzu tana makarantar tana jirana" Mami tace "Oh my God, is that so?? Allah
sarki, bari in kira driver sai ka bani numberta in tura masa yaje ya daukota yanzu"
Khalil was shocked at what she just said, Mami ta mike da sauri xata dauko wayarta
ya bi ta da kallo, can sai gata ta dawo kafin ta kira Drivern yayi saurin cewa
"Mami she is just a young girl, bata da waya a hannu, dama sai xata fara karatun ne
za su bata waya, kawai ce mata nayi zan zo in dauketa a makarantar later" Mami dake
kallonsa tace "Toh ka fadi inda kace ta jira ka a makarantar mana in kira Drivern
in sanar masa yaje ya daukota, why are you making this a big deal son??" Khalil ya
kamo hannunta a hankali yace "Mami tsoronki kada in fita a hanani shigowa a bakin
gate ko? but trust me ya sanar masu zan zo ya kuma masu izinin barina in shigo shi
yasa har suka barni na shigo, idan da ba haka bane da baxan ta6a shigowa gidan nan
ba" Mami ta fashe da kuka tace "Bana son kowa yasan ka dawo Khalil" Khalil ya
girgiza kai a hankali yace "Mami, surely in dai yan gari xai tambayesu ko na zo
kuma za su sanar masa na zo ina gidan, kiyi hakuri in je in daukota yanzu in dawo
Mami, i promise you ko awa daya baxa ayi ba zan dawo" Mami dai tayi shiru tana goge
hawayen dake ta sauka idonta, sosai zuciyarsa ya karaya ganin yanda Maminsa ke
kuka, ya rungumeta ya runtse ido yace "Kiyi hakuri Mami, kowa a rayuwar nan da irin
tasa kaddarar, and Alhamdulillah so far" Mami ta gyada kai tace "Haka ne son" Yayi
kasa da murya yace "Ni kaina bana son ganin kowa na gidan nan a yanzu, don haka ki
kwantar da hankalin ki, i will follow the back door idan xan fita..." Cikin sanyin
murya tace "Toh mota fa?" Yace "I will order Bolt" Mami bata kuma cewa komai ba,
yace "In sha Allah idan na dawo zan ci abincin Mami" Yana fadin haka ya lumshe ido
yayi pecking dinta a forehead sannan ya mike, ta bi sa da kallo hawaye na zuba
idonta har ya fita daga dakin.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

And ur evidence via 07087865788

Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku
anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama
Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya
zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da
matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani
prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa
jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using
mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki
kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi
gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai
na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin
keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free
Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

37

Khalil na shiga parlon Abbansa bai bari suka hada ido ba, yana tafiya a hankali ya
zauna saman lallausan Carpet dake kasa, yayi gathering courage yace "Barka da dare
Abba" Shirun da Abban nasa yayi yasa a hankali ya daga kai ya kallesa yaga jaridar
hannunsa kawai yake dubawa, ya sunkuyar da kansa, bayan kusan minti biyu Abba ya
ajiye jaridar hannunsa yana kallonsa a takaice yace "Wani international joint
ventures na wata daya zaka min handling a Zanzibar, and the business isn't new to
you, you know everything about it, so u can chose to stay there in Zanzibar or come
back to Nigeria weekly, bayan kayi min sorting komai zaka iya komawa duk inda ka
fito ka ci gaba da rayuwarka since it's the best for you and you are okay with it,
i will neva beg you to come stay here!!" Yana gama fadin haka ya mike ya shiga
dakinsa Khalil ya bi sa da kallo, sai gashi ya fito da files ya jefa masa nan kasa
yace "Everything u will be needing is there, u can leave my sight now" Khalil ya
dau files din a hankali yace "In sha Allah, Nagode Abba" Daga haka ya mike ya nufi
kofa Abban nasa ya bi sa da kallo har ya fita, yana fita ya juya suna hada ido da
Abba, Abba yayi saurin juyawa ya shiga bedroom dinsa. Har Khalil ya shigo parlon
Mami na tsaye ta kasa zaune sai kai komo take a dakin, she is so disturbed and
worried, Allah ya sa kiran alkhairi yake masa, tana ganin Khalil ya shigo ta nufesa
da sauri tace "What did he say to you??" Khalil ya mika mata files din hannunsa ta
amsa tana dubawa da sauri, can ta kallesa tace "What about this?" Yace "He wants me
to be in charge" Mami ta dinga Kallonsa babu ko kiftawa can tace "He said so?"
Khalil yace "Yea" Murmushi tayi ta rungumesa tana hamdala a zuciyarta amma ta kasa
cewa komai hawaye ya cika idonta, ta sakesa tace "Yanzu yaushe zaka tafi?" Khalil
yace "I need to prepare" Tayi kasa da murya da damuwa tace "Zan so ka shirya first
thing in the morning ka bar gidan nan kafin wani yayi noticing dinka, har yanzu
basu san u are around ba, nasan shi ma bai sanar masu ba" Khalil bai iya yace mata
komai ba, ta goge idonta tace "Shigo ka ci abincin yanzu, i am so happy at this
good news" Ta kama hannunsa suka wuce can bedroom dinta, tsaye tayi bakin kofa da
mamaki tana kallon Nihad da ko motsi bata yi daga inda take ba balle ta ta6a abinda
Mami ta zuba mata a gabanta, Mami ta kalli khalil tayi kasa da murya tace "Are you
sure zata yarda ta kwana nan son? She hasn't taken anything yet, are sure baxaka
duba ko da akwai flight going to kano a yankar mata ticket ba?" Khalil dai sai
kallon Nihad yake, Mami tace "Do so before it's late plss, kasan wasu nature ne
hakan basu sakewa a wani waje ba gida ba, so kar a takurata" Juyawa tayi ta fita
daga dakin, khalil ya duka dab da ita yana kallonta, kin yarda su hada ido tayi,
lkci daya yaga hawaye ya ciko idonta, still looking at her yayi kasa da murya yace
"Where u offended in anyway?" Ta kallesa sai kawai ta fashe da kuka sosai, cikin
karfin hali tana magana da kyar tace "Don Allah... Kayi hakuri ko a motor park ne
ka kai ni ka sa ni a motar Jigawa in tafi wajen Aunty Jamila, don Allah kayi min
wannan last alfarman" Tana kuka me ban tausayi ta fadi hakan, sai kuma ta hade
kanta da gwiwa, yana ta kallonta kafin yace "An maki wani abu ne a nan din da za ki
tafi jigawa?" Ta daga idanuwanta da hawaye ke zuba tana girgiza kai tace "Ni bance
an min komai ba" ya dau duk abincin da Mami ta sa mata a plate ya kai parlor sannan
ya dawo yace "Fito ki ci" Tace "Ni na koshi" Yace "Fito nace" Mikewa tayi trying
hard not to burst into new cry ta fito daga dakin ta tafi ta zauna inda ya ajiye
abincin, ta hadiye wani abu da ya tokare mata throat da kyar, Yana kallonta yace
"Now eat" Bata san sanda kukan ya subuce mata ba tana girgiza masa kai, ya hade rai
yace "Kee" ta daga ido da sauri ta kallesa, ya durkusa yana kallonta, sai kuma ya
ciro handkerchief ya mika mata, Da sauri ta sunkuyar da kanta, ganin har sannan
mika mata handkerchief din yake ta kai hannu a hankali ta amsa, ta goge hawayen da
ke zuba idonta da shi shi dai kallonta kawai yake, bayan ta gama goge idon ta daga
kai a hankali tana kallonsa, ya sauke idonsa ya matsar da plate din abincin
gabanta, ta kalli cokalin dake cikin abincin ta dauka ta diba ta kai baki a hankali
ta fara ci, mikewa yayi ta bi sa da kallo har ya fita zuwa next parlor din, gaba
daya taji baxata iya cin abincin ba, she has clearly run out of appetite, this is
the third shock of her life so far, but this particular one is so strong and it's
about giving her heart attack, of all the shock, this made her felt bata da sauran
hope a duniya, this made her loose all hope, she now believe she is now all by her
self a duniyan, kwakkwaran wata daya ba ayi ba ta girgiza da lamari har kala uku,
yanda take ji a ranta ta kara tabbatar da bata da wani sauran gata kuma a duniya,
ganin komai take kamar mafarki amma ita dai tasan ba mafarki take ba, this is
nothing but reality, bata ta6a jin ta tsani kanta duk abubuwan dake faruwa ba sae
yau, she hate herself for everything so far, ta daure ta tashi da kyar ta mayar da
duk abincin cikin warmer dinsu ta fito don tasan baxata ta6a iya ci ba, ta zauna
kasa ta jingina da kujera, ko sanin hawaye na zuba idonta bata yi ba. Khalil na
zaune first parlor da Maminsa dake waya da sister dinta, she is happily telling her
that he is back, daga nan kuma ta kira aminiyarta warce kasar su daya and she is
always there for her at all time, shi dai khalil kallonta kawai yake har ta katse
wayar, Mami ta mike tace "An samu jirgin kuwa son?" Ya girgiza kai yace "Aa Mami"
Tace "Toh gobe first thing sai kayi mata booking ticket kafin ka tafi koh?" Khalil
bai ce komai ba, Mami ta koma can ciki, ba a dau lokaci ba sai gata da plate din
abinci ta zubo masu, tare suka ci abincin, ya ci peppered chicken din kawai a
maimakon pepper soup yace mata ya koshi, Mami ta kira Bilkisu ta kwashe duk
abubuwan ta fita da su daga part dinta. Karfe tara da rabi Mami ta shigo parlon da
Nihad take tana kallon Nihad tace "Toh ki tashi kiyi wanka don ki ji dadin jikinki
ko?" Nihad ta mike tsaye ba tare da ta bari sun hada ido ba, Mami dai sai kallonta
take, ganin ta nufi kofa tace "Ga bandaki nan a bedroom" Ta girgiza kai tace "Zanyi
a na parlor" Daga haka ta fita daga parlon zuwa daya parlon wanda bandakin ke ciki,
tayi hakan ne sbda la'akari da tayi da Mumynta, bata sharing bathroom din dakinta
da kowa, khalil dake danna waya ya daga kai ya kalleta, tun da ta kalli iphone din
hannunsa bata sake kallon direction din nasa ba, yaga ta shiga bandaki, Mami ta
shigo parlon ta kirasa ya mike ya bi bayanta, suna tsaye parlon farko tace "Toh
yanzu a haka da taki sakin jiki zan kai ta bangarensu Mimi?" Yace "Aa Mami ki yi
mata shimfida kawai a parlor nan ta kwanta" Mami tace "Aa haba dai, ya zata kwana a
parlor, abinda yasa kaga bance zata kwanta nawa bedroom din ba i am leaving it for
you kai ka kwanta, ni zan je in kwanta wani wajen" Yayi Murmushi yace "Aa Mami ba
sai kin bar min gadonki ba, kawai ki kwanta ni zan kwanta parlor, kema kinsan i
prefer sleeping on the couch" Tace "Toh shikenan sai mu kwanta da ita a daki, let
me get her sleeping dress wajensu Mimi...." Daga haka ta fita sai gashi ta dawo da
sabuwar rigar bacci na Noor ta kai dakinta ta ajiye ma Nihad a gefen gado da
tsadaddun spray biyu sannan ta fito, Nihad na fitowa daga wankan taki shiga dakin,
shi dai yana ta danna wayarsa, ta rakube jikin kujera, Mami ta fito parlon zata ma
Khalil shimfida, ganin Nihad a rakube tace "Baby shiga ciki ki shirya, za ki ga
sleeping dress da turare na ajiye maki saman gado" A hankali Nihad tace "Nagode"
Daga haka ta shiga dakin, Shimfida me lafiya Mami tayi ma Khalil a parlor na biyu,
shi dai bin ta kawai yake da kallo, yasan yayi kewar Maminsa fiye da zatonsa, he so
missed all this, har bedroom dinsa Mami kan shiga ta gyara masa back then, tana
gamawa ya mike ya nufeta yayi mata side Hug cikin sanyin murya yace "Thanks Mamina"
Tace "Ai kai ma zaka yi wankan ko?" Yace "Sure" Tace "Let me get u ur pajamas" Daga
haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo, sai kuma yayi murmushi ya shiga dakinta don
shiga banɗakinta yayi wankan, zaro ido Nihad tayi ta rufe jikinta da kayan baccin
da take kokarin sakawa ta durkusa kasa da sauri ta rufe fuskarta, ya sauke idonsa
ya juya ya fita daga dakin, bandakin da tayi wanka ya shiga kawai, Mami ta ajiye
masa pajamas din saman inda tayi masa shimfida bayan ta dawo ta tafi dakinta,
dariya Nihad ta bata ganin yanda ta rakube kasa jikin dressing mirror bayan ta saka
kayan baccin, Mami tace "To tashi ki hau gado ki kwanta" Nihad ta kalleta da sauri
cause she never expect it, can tace "Aa zan kwanta a kasa" Mami tace "Common hau
gado kiyi kwanciyar ki Baby" Shiru Nihad tayi sai kuma ta mike a hankali ta tafi ta
hau saman babban bed din wanda furnitures dinsa kadai ma abun kallo ne, Mami ta
dago mata duvet ta mika mata ta amsa ta rufe jikinta ɗon dakin yayi sanyi ta
dalilin Ac dake kunne. Har kusan karfe dayan dare Nihad bata ga bacci ba, tuni Mami
tayi bacci, da ta tuna wasu abubuwan sai taji hawaye me zafi ta gefen idonta na
zuba, she wish she could rewind everything from the scratch, she wish many things
didn't happen, daga karshe da taga she needs to cry out ko zata samu saukin abinda
take ji a ranta, cike da karfin hali ta mike zaune tana kallon Mami cikin duhu, a
hankali ta lallaba ta sauka daga kan gadon ta tafi bakin kofar, nan ma ta tsaya
tana tsoron kada kofar yayi kara idan ta bude har ya farkar da Mami, can dai ta
runtse ido ta kai hannu handle din kofar ta murda a hankali ta bude, bata ji yayi
kara ko kadan ba, ta fita ta kullo mata kofar, yana kwance parlon nan ma wutan a
kashe yake, a hankali tana tafiya making sure she isn't making any sound ta tafi ta
bude dayan kofar ta shiga daya parlon, can wani corner ta tafi ta zauna tana
shesshekan kuka cike da tausayin rayuwarta, hawaye kawai take wani na bin wani, tun
da ta fito daga
dakin Khalil da shi ma bai yi baccin ba ya bi ta da ido cikin duhun har ta tafi
daya parlon, he can't say why he is still awake may be over excitement ne na cewar
yau gashi a gida da Maminsa after some years, bayan kusan minti 7 ya mike a
hankali, shi ma bai kunna wutan ba ya nufi kofar ya bude gently ya fita, ta
direction da yake jin shesshekan kukanta ya nufa, kawai gani tayi wani abu da yayi
mata kama da statue tsaye a kanta, er kara tayi a mugun tsorace ta mike xata gudu
ya rikota, sai a sannan ta ji kamshin turarensa ta rufe fuskarta da sauri a jikinsa
tana kuka a hankali, bayan few seconds yace "Saboda kiyi kuka kika fito nan?" Ita
dai bata ce komai ba sai shesshekan kuka take tana Girgiza masa kai kawai, ya
janyeta jikinsa yace "Zauna nan" ta tattaba bayanta taji kujera, hakan ya sa ta
zauna a hankali, yana tsaye inda yake yace "Ki saurari duk abinda zan ce maki yanxu
cause it's for ur benefit" ita dae tayi shiru tana jin sa gabanta na faduwa, yayi
kasa da murya yace "On no condition xa ki gaya ma wani a gidan nan relationship
dinmu, that should be s secret between us har zuwa sanda xa mu cika ma juna
alkawarin da muka dauka a baya" Nihad dai kanta na kasa, yace "Nace ma yan gidan
admission letter kika zo amsa garin nan, so duk abinda zaki ji na gaya masu gobe ya
zama hakan kema a wajenki" Nihad ta share idonta ta gyada masa kai kawai, ya kunna
wutan parlon yana kallonta yace "Sai da safe" Bata yarda sun hada ido ba ta mike ta
nufi kofar shiga second parlon Mami ya jira har ta shiga sannan ya bi bayanta.
Washegari Nihad na tashi taga ita kadai ce dakin Mami, tana kokarin gyara gadon sai
ga Bilkisu ta shigo, Bilkisu na murmushi tace "Ina kwana" Nihad ta sauke idonta
tace "Mun tashi lafiya" Bilkisu tace "Ai da kin bar shi ma xan shigo in gyara,
aikina ne" Nihad dai bata ce mata komai ba ta shigo ta fara abinda zata yi, Nihad
ta fita parlor, tana bude kofar first parlor taga Mami da khalil a zaune parlon, Ta
gaida Mami da ladabi Mami ta amsa mata da fara'a, ta kalli Khalil suka hada ido, ta
kasa barin wajen bata gaishesa ba saboda Mami dake zaune, bata yarda ta kallesa ba
tace "Ina kwana?" Yace "Lafiya, ga breakfast din ki" Mami tace "Bari a kai mata can
parlon so that she will be comfortable" Yace "Aa za ta yi a nan" Nihad dai bata ce
komai ba, can ta karasa cikin parlon tana tafiya a hankali, ya nuna mata breakfast
din dake saman tray, ta dauka ya nuna mata inda xata zauna, Mami dai sai bin ta da
kallo take because she is so cute and meek, Mami ta kallesa tace "Amma 'yar mai
gidan da kake ce min kana zama wani lokacin a gidansa ce ko?" Khalil zai yi magana
aka bude kofar parlon, Mimi da Noor ne suka shigo, suka yi wani ihu a tare ganinsa,
daga inda yake zaune duk suka tafi da gudu suka rungumesa so happy seeing him, sai
ga wasu set din Yan matan biyu Hanan da Farhana, su ma duk suka rungumesa so so
happy seeing him, he couldn't help it but smile don shi ma yayi kewansu sosai, Mami
dai sai murmushi take, Mimi ta kalli Mami ta fashe da kuka tace "Mami mene ya sa
zaki boye mana yayanmu ya dawo, Abba yace he's been around since yesternight" Sai
kuma ta fashe da kuka, Khalil ya jawota gefensa yana kallonta yana murmushi yace
"Is there any diff between now and the yesternight" Tace "Yes of course, wallahi da
nasan kana nan nima a nan zan kwana jiya, i soo miss you yayanmu" Tana fadin haka
ta kara rungumesa tana hawaye, Nihad dai sai bin su take da kallo kana ganinsu
kasan su ne ainahin rich kids din, duk Mimi ta fi kama da shi, Noor ma fara ce
Farhana da Hanan ne kadai haskensu bai kai nasu Mimi ba, Farhana sai kallon Nihad
take keenly, can ta kalli Mami tace "Mami who is she?" Mami tace "Our visitor"
Tambayarta ne ya ja hankalin sauran yan matan suka kallo inda Nihad ke zaune, Noor
ta ɗan juya ido tace "Ohh She looks familiar" Hanan dai kallonta take babu ko
kiftawa kamar me son gano wani abu, can ta ja Noor suka fita daga parlon tana zare
ido tace "Kin tuna wata yarinya da video dinta ya tafi viral weeks ago?" Noor ta
zaro ido bayan tayi recalling video din tace "Ohh yess!! exactly, wallahi suna kama
sosai, i think baxan rasa video din a thrash bin dina ba" Tun da Khalil yaga
sisters din nasa duk sun yi concentrating kan Nihad, yace "Ohk, ohk now, i need
rest za mu hadu anjima a main parlor..." Mimi tace "Yayammu who is she, nima kamar
na santa" Mami tayi dariya tace "A ina kika santa, banda karya Mimi" Mimi ta juya
ta sake kallon Nihad da ta sunkuyar da kai gabanta na mugun faduwa don banda nude
video dinta babu abinda ya fado ranta, mikewa Khalil yayi yace "Mimi za mu hadu
anjima a main parlor, i said i need rest, ku fita" Sai ga Noor da Farhana sun shigo
da gudu parlon, Hanan ta biyosu da sauri, Noor ta nufi Mami har tana tuntube tana
mika mata wayarta tace "Mami u remember this???" Mami ta amshi wayar ganin video
din da take nuna mata tace "Wai ba nace ki goge video din nan ba Noor? What is it
still doing a wayarki?" Noor na zaro idanuwanta kamar za su fito tana nuna Nihad
tace "Ba ita bace warcan" Mami ta kalli Nihad da sauri, sai kuma ta amshi wayar
tana kallo, Kasa cewa komai Khalil yayi, Nihad da jikinta yayi sanyi kamar warce
aka kwara ma ruwan sanyi ta kasa kwakkwaran motsi inda take zaune ta dinga bin su
da kallo kamar warce tayi ma sarki karya, sai kuma ta sunkuyar da kanta with tears
in her eyes, Mami ta kalli Khalil da sauri, sai kuma ta kara kallon Nihad, tuni
Farhana ta tafi ta kirawo wasu set din yan mata biyu duk suka tsaya bakin kofa ko
warce da wayarta a hannu, da ta kalli videon sai ta leko ta kalli Nihad baki bude,
Mami da ita kanta jikinta yayi sanyi qlau ta kara kallon Khalil that is saying
nothing, can ta hadiye wani abu tace "No, no may be resemblance ne kawai, ai akwai
resemblance" Noor da Farhana suka wani gwalo ido har suna hada baki suka ce "Mami
wallahi ita ce, the video is so clear fa ba wai yayi dishi dishi bane, ki duba mana
ki ga, ita ce wllh" Da sauri Hanan ta tafi tana mika ma Mami waya wai don ta kara
gani da kyau, Mami ta ki amsar wayar bata kuma sake cewa komai ba, Sajida tace
"Ikon Allah, then who brought her to this house? Ance yar Maryam Abatcha American
University ce fa" Mimi dake tsaye gefen Khalil ta kallesa a hankali tace "Yayanmu
who is she?" Bai ce mata komai ba yana bin sisters din nasa da kallo ya nuna masu
kofa yace "Ku fita" Farhana ta kyabe baki haka ma Hanan duk suka juya, Noor ma tayi
ficewarta, Mimi ta dinga kallon Nihad dake ta hawaye, Ita ma ta fita daga parlon,
Mami dai mutuwar zaune tayi a inda take. Daga karshe ta mike ta shiga dakinta ta
zauna side din gado duk jikinta a sanyaye, a ina Khalil ya samo yarinyar nan har
zai shigo da ita gidan nan? Bilkisu ta fito daga bandaki tana kallon Mami ganin
yanayinta tace "Mami are you okay?" Mami tayi karfin halin cewa "Sure, ki tafi idan
ina bukatarki zan kira ki Bilkisu" Tace "Toh Mami" Daga haka ta fita daga dakin,
Har sannan Khalil na tsaye ya rasa abun yi, Nihad dai ta hade kai da gwiwa tana
shesshekar kuka, Bayan Bilkisu ta fita ya juya ya tafi dakin Maminsa, yana shigowa
dakin ya kulle Mami ta mike tana kallonsa cike da tuhuma tace "Khalil wacece warcan
yarinyar ka kawo mana gidan nan? Who is she? Menene alaqarku?" Yayi gathering
courage yace "Mami calm down pls, yarinyar mai gidan da nace maki nakan zauna
wajensa a kano ce, kuma ai na gaya maki dalilin da ya sa muka taho tare, Banda
wannan babu wani dalilin Mami" Mami tace "Toh zan tura maka kudin jirgi ka siya
mata ticket ta koma, ai ta gama abinda take ko?" Ya rasa abinda xai ce, Mami ta
hade rai tace "Ko baka ji abinda nace bane?" Yayi kasa da murya yace "Mami bata
gama ba, bata samu amsan admission letter din ba ma" Mami tace "Toh me kake nufi?
Ka gaya min me kake nufi Khalil?" Ya marairaice yace "Mami karki manta gidan
babanta fa nake all this while, bai san ni ba ya yarda da ni, yayi accomodating
dina na zauna cikinsu for almost 10 months now" Mami tace "Yanxu ya kake son ayi
khalil? Me kake son in fada a wannan issue din? Sai kace baka san mutanen gidan nan
ba ko mance halinsu ne? wait first... Wai ma ita ce a video din nan ko ba ita
bace?" Ya sauke idonsa kasa bai iya yace komai ba, Mami tayi masa tsawa tace "Baka
ji na ne?" Cike da karfin hali yace "Ita ce" Mami tace "Nawa ne kudin jirgin, zan
tura maka yanzu" Yana girgiza kai hankali tashe yace "Mami mun yi magana da
mahaifinta kan cewa ta zauna nan gunki har ta karbi admission letter din tunda bai
fito ba, Mami we can't repay him this way, he is one of the nicest person i have
met in life, kawai ka haifi yaro ne baka haifi halinsa ba, but her mother and
father are down to earth, sun min abinda baxan mance su a rayuwa ba, sannan Mami
duk yaran gidan mahaddatan qur'ani ne, kawai dai ita...." Sai kuma ya kasa ci gaba
don ya rasa me xai ce, Mami ta fashe da kuka tace "Magana kake son ja min yanzu
fisabilillah Khalil? A ina kake son in ajiyeta har ta zauna a gidan nan bayan kana
gani duk yan matan sun shaida ita ce a videon nan kuma sun je su idar, sannan har
shi Abbanku sae da ya tofa nasa a lokacin da ya ga video din nan kwanaki, he was so
disappointed yayi ta addu'an Allah ya shirya mana zuri'a, sai kawai yau a ganta a
gidan nan ba kuma kowa ya kawota ba kai?? Kai da kake da ta6o ta ko ina a gidan nan
shine zaka kara shafa ma kanka kashin kaji? Check this out khalil, yaushe har Abban
naka ya bukaci ka dawo da har zaka dawo tare da wannan issue din? Kayi min gata
kayi ma kanka gata ka fitar da ita daga gidan nan kafin wani ya kara noticing dinta
bayan kanninka, Plss take her out of this house Khalil"

Masu jira ina turawa su yi fowarding a dinga yi ana tunawa da hakki, ku kuma masu
karantawa a bati amma fa a duniya yake bati, duk na gaisheku kyauta ya damuna??
Masu posting on Facebook, Hassan Basiru majia, Aminu Arthur and the rest, Hmm an
dai ce prevention is better than cure, i warned first.

Nihaad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u show ur evidence via👇🏻

07087865788......

*Wato duk me son sanin wani turare Nihaad ke sakawa da ke sa Khalil jiyo kamshinta
da ta gifta waje upon the hatred ya biyoni pc don abun sirri ne, nima shi nake sa
wa Barrister ke jiyo kamshina tun daga gate, joke apart..., kuma saboda wannan
kamshin ya min alkawarin daga ni ba kari* 🤓🥰

_SCENTMANIA_💯
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

36

Khalil na isa hotel din ya nufi dakin direct ya bude kofar, sosai ya ji gabansa ya
fadi ganin babu kowa cikin dakin, da sauri ya karasa ciki yana kallon abincin da ya
ajiye mata yaga ko ta6awa bata yi ba, lkci daya yaji zufa na keto masa, kallon
kofar bandaki yayi nufi can da sauri ya bude kofar nan ma babu ita a ciki, nan yaji
hankalinsa ya kara tashi ya fice daga dakin ya sauka kasa yana kallon receptionist
din wajen yace "Don Allah yarinyar da muka shigo dazu..." Kafin ya karasa
receptionist din tace "Ta fita ai" kasa daina kallonta yayi, yayi karfin halin cewa
"Ta fita? When pls?" Matar tace "Some minutes ago" juyawa yayi da sauri ya nufi
kofar fita daga cikin hotel din, receptionist din ta bi sa da kallo, Khalil na fita
bakin titi yana waiga gefensa ya ganta can zaune daga jikin hotel din kamar
marainiya, lokaci daya ya hade rai ya nufeta, ita bata ma lura da shi ba tayi nisa
cikin tunanin da take, yana isa dai dai inda take yace "Baki da hankali ne zaki
fito nan bayan kinsan jakata na dakin?" Ta daga kai ta kallesa, sae kuma a hankali
tace "To ba kai nake nema ba" yace "Me yasa zaki nemeni? Saboda me?" Ita dai bata
ce komai ba, sai a sannan ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, ya juya ya bar ta
wajen, ordering wani bolt din ya mayar da wayarsa a aljihu ya juyo yana kallonta
yace "Ki jira ni a nan" Daga haka ya koma dakin don dauko jakarsa, yana fitowa sai
ga motar, bayan sun gaisa da drivern ya sa jakarsa a booth, ya juya ya kalli Nihad
dake kallonsa, ai bata ma jira yace ta taso ba ta taso ta nufosa, ya zaga ta daya
side din ya shiga motar, tana dai ta tsaye, jin bai ce mata komai ba ta bude
bangaren da take tsaye ta shiga ta jawo kofar motar a hankali. Kamar me Bolt din
dazu wannan ma sae da ya tambayi khalil ko zai iya shiga ciki ganin unguwan da suka
zo, Khalil ya sauke glass din side dinsa ya daga ma securities din wajen hannu
sannan suka wuce, Nihad dai tun da suka shigo anguwan nan take kalle kalle uwa
idanuwanta za su fito, she is wondering where he is taking her to, duk inda suka
wuce sai taga securities, very tight security, bata ta6a jin tsoron kasancewa da
Khalil ba sai wannan moment din, she looked at him looking very afraid, to ko dai
inda ake yankan kai ma zai kaita, sosai gabanta ya dinga faduwa hankalinta yayi
mugun tashi, ta dinga kallon Mad houses din da suke ta wucewa na masu kudi da suka
amsa sunan su kudi a kasar, hakurin Nihad ya soma karewa ta juya a hankali ta sake
kallon Khalil for the 5th time, gabansa kawai yake kallo fuskarsa babu yabo babu
fallasa, Ai bata san sanda ta marairaice masa ba cikin rawan tace "Don girman Allah
ina zaka kai ni? Don Allah kayi hakuri ka rufa min asiri, ina ne nan ka kawo ni?"
Sai ta sakar masa kuka a hankali jin ya ki ce mata komai, shi dai ko kallonta baya
yi, ko ma wanene yanda Khalil yayi keeping serious and straight face sai ya tsorata
balle Nihad da dama can matsoraciya ce, Shi kam drivern bolt din slowly yake tafiya
sbda Securities that are everywhere don zuwa lkcn gari yayi duhu, amma sai kayi
tunanin rana ce don ko ta ina haske ne tarr, har dai suka isa dai dai gidansu
Khalil, sai dai ba ta inda ya shigo dazu bane, wannan second gate din gidan ne dake
ta baya, drivern ya tsaya yana duban ma'aikatan da suka nufo motar gadan gadan,
Khalil ya bude motar ya sauka, suna ganinsa suka gaishesa suna komawa baya, Ganin
Nihad taki saukowa daga motar ya zaga ta inda take ya bude motar yana kallonta babu
yabo babu fallasa yace "Malama kina bata masa lokaci" Ta marairaice tana kallonsa
cikin rawan murya tace "Don girman Allah ina ne nan din ka kawoni, kayi hakuri ka
gaya min" Gaba daya tayi zuru zuru da ita kamar ba Nihad ba, shi dai kallonta kawai
yake, can yace "Neman taimako na zo yi nan din, tunda kin ga bamu da inda za mu je"
Ta gwalo ido sosai tana kallonsa da mamaki, can tayi karfin halin cewa "Taimako
kuma? Unguwar masu kudi ne sosai fa, ba kowa ne ke shigowa nan ba wallahi, kuma ko
kallonmu baxa su yi ba sai ma su kore mu ko su sakar mana karnuka, wllh ka shigo
idan ba haka ba securities din nan za su iya sa mu tsallan kwado yanzun nan" ya
dafa motar yana kallonta da kyau yace "Sa'armu za mu gwada, kuma ni nasan ina da
sa'a sai in ke ce baki da, Malama ki sakko kina bata ma me mota lokaci" Da sauri
Nihad ta kalli me tukin motar dake jiranta ta sauka patiently, can ta kalli khalil
pleadingly tace "Ni dai don Allah ka zo ka shiga mu koma, babu abinda za su mana a
nan" Yace "Idan muka koma kina da kudin da za mu ci abinci gobe? Ko kina da kudin
da zaki sake biya mana daki a hotel din?" Kallonsa ta dinga yi, lkci daya jikinta
yayi sanyi, hawaye ya kawo idonta, sai kuma ta sa hannu ta share idon nata a
hankali tace "Sai ka bani waya in kira ya Farooq nasan zai turo mana kudi" Yana
kallonta yace "Aa, wannan gidan dai nake son shiga in gwada sa'a ta" Ta kallesa
zata yi magana ya hade rai yace "Kina bata masa lokaci malama" a hankali ta sauko
daga motar tana kallon Khalil hawaye na bin kuncinta, ya daga ma mai bolt din hannu
ya ja motarsa ya bar wajen, cikin kuka tace "Toh ni dai da kace ya maida ni in
jiraka a can hotel din, in ya so kai kadai sai ka shiga gidan" Wani kallo yayi mata
ya nufi gate din gidan da tuni aka bude masa, Ta gefen ido take kallon securities
din gabanta na faduwa don wasu dirka dirkan bayin Allah ne, can dai tana ganin
Khalil ya shiga cikin gidan ta bi bayansa da sauri, ga mamakinta basu kulle ba suka
jira har ta shiga sannan suka rufe gate din, Nihad ta dinga bin makeken compound
din me dauke da wani ubansun mansion da kallo, kai kana ganin gidan nan kawai kasan
ba karya malam, Compound din kuwa yayi ukun nasu ga parking lot kaca kaca, ko wanne
da ride lafiyayye a parke, ita bata ma san ta bayan gidan suka shigo ba, don ta can
ne zata ga ainahin kyan gidan, chalet da aka yi can gefe da ta hango kuwa ya kusa
nasu main building din, tafiya kawai yake tana binsa zuciyarta na bugawa, but how
comes yana ta tafiya kansa tsaye and nobody is even stopping him, taga sun zaga ta
baya ya shiga wani stairs wanda aka shimfida ma carpet grass, shi kansa tsakar
gidan wajen duk malale yake da Carpet grass din, bude wani kofa yayi bayan sun
haura sama sun mike wani babban corridor, ya bude wata kofar duk tana biye da shi a
baya a tsorace, ko nisa bata son yayi mata, gaba daya she is really confused at how
he is just badging in babu shakka ba komai, ita tsoronta kada a kama su ayi masu
dukan tsiya, da ido ta dinga bin parlon da ya shiga tana makale bakin kofa ta kasa
shiga zuciyarta na bugawa, Can taga ya shiga wata kofar da sauri ta bi bayansa ko
kulle kofa bata yi ba, nan taga kofar da ya shiga wani parlon ne wanda ya fi wanda
suka baro haduwa, at this point, she is super confuse, bayan ya isa kofar dakin
Maminsa ya juyo yana kallonta, ya fi second goma yana kallonta wanda hakan ne ya
kara mugun tsoratata, can kuma babu yabo babu fallasa yace "Zauna nan" Ta kasa zama
har taga ya shiga wani kofar, Mami na nan zaune yanda khaleel ya bar ta don ta kasa
samun nutsuwa, gani kawai take shikenan kuma baxai sake dawowa ba, gaba daya
jikinta a sanyaye yake har zuwa yanzu da ya shigo dakin nata, da sauri ta mike
ganinsa with happiness written all over her face ta nufesa kace "U kept to ur
promise son, baka wuce awa dayan ba, i was so worried ina ga kamar tafiya ka kara
yi...." Yayi Murmushi ya kamo hannunta a hankali yace "Amma bana son ki saka rai da
yawa ki sakankance a kan cewar na dawo in zauna Mami, kar ki manta ban san kiran me
Abba ke min ba, he might still not be needing me in his house, kilan idan ya gama
fada min abinda zai fada xai iya cewa in bar masa gidansa and i don't have
choice...." Hawaye ya shiga sakkowa idon Mami tana girgiza kai tace "Baxan yarda da
hakan ba this time around son, sai dai duk abinda zai faru ya faru, shirun da nake
masu ya zo karshe, baxan sake shiru ba in har yace ka bar masa gidansa for the
second time" Shi dai khaleel bai ce komai ba sai kallon mahaifiyar tasa yake cike
da tausayinta, kamar yanda take ganin ya rame, shi ma haka yaga ta rame saboda
damuwa, Can Mami ta share idonta da sauri tace "Where is the young gal?" Ya kalli
kofa yace "She is at the parlor" Mami tace "Ohk" Daga haka ta nufi kofar ta fita ya
bi ta da kallo, zaunawa yayi gefen gado ya rike kansa, yasan ko me zai faru baxai
samu courage din sanar masu ai Nihad yarinya ce da babanta ya aura masa ba, shi
kuma ya amshi auren nata ba don ransa ya so ba sai don ganin girma da mutuncin
mahaifinta sannan baxai iya turning down din offer din mahaifinta ba, yasan baxai
ta6a fara masu wannan bayanin ba, fadawa saman gadon yayi ya kwanta ya lumshe ido
yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mami na fitowa parlor taga Nihad a tsaye
bakin kofa tana shesshekan kuka, tun bayan da taga khaleel ya mata wannan kallon
sannan ga shiga kofar ya kulle tayi saurin komawa bakin kofar fita parlon ta tsaya
zuciyarta na raya mata shikenan babu wani tantama ya kawota ne kawai a gille mata
kai ayi kudi da ita, dama masu kudin nan wasun su kowa yasan ai suna yankan kai, to
kila mai gidan ya ba khaleel contract din samo masa kan da za a gille shi yasa har
ya shigo gidan tare da ita babu wanda ya hanasa, sai ma bude masa kofa da
securities din suka yi har da masu gaishesa, irin dai ya saba shigowa gidan kenan,
sannan gashi taga kansa tsaye ya taho bangaren nan da ita, wato in da za a gille
mata kan kenan, uwa uba tun da suka shigo gidan bata ga ko wani mutumin ba sai
securities, Da mamaki Mami ke kallon Nihad ganin yanda take hawaye tace
"Subhanallah, Baby are you okay? why are you crying?" Kallon matar kawai Nihad take
hawaye na sauka idonta kuma taki ce mata komai, wannan ba ita ce ta gani a hoto
ranan a dakinsa ba? Mami tace "C'mon, come in dear...." Nihad taki karasowa sai
kallonta take, Mami na ganin haka ta juya ta koma dakinta ta shiga tana kallon
Khalil dake kwance saman gadonta da mamaki tace "Khaleel na ganta tsaye bakin kofa
tana kuka, is she okay? Nace ta shigo kuma
ta ki" Mikewa Khalil yayi ya fita parlon Mami ta bi bayansa, yana kallon Nihad, ya
dake yace "Shigo ciki" Mami ta karasa inda take tsaye ta kamo hannunta ta shigo da
ita parlon tana kallon Khalil murya can kasa tace "Doesn't she understands
English?" Bai ce komai ba ya juya ya koma dakin, Mami ta zauna gefen Nihad da ta
zaunar edge din kujera kamar me shirin fillawa da gudu, tace "Ya kike yan mata?"
Nihad ta goge idonta tana kallonta a hankali tace "Ina yini" Mami na Murmushi tace
"Alhamdulillah, ya su mamanki?" Nihad ta sauke idonta kasa cikin sanyi tace "Lafiya
lau" Haka kawai Nihad taji hankalinta ya ɗan kwanta ganin Mami, Mami ta kwantar da
murya tace "Ki saki jikinki kinji, nan ma duk gida ne" Nihad ta kasa ce mata komai,
Mami tace "Kin yi sallan magariba?" Nihad ta girgiza mata kai, Mami tace "To ga
banɗaki kije kiyi alwala, bari in kawo maki darduma a bedroom yanzu" Nihad ta mike
ta tafi kofar da Mami ta nuna mata a parlon ta bude a hankali tana kallon ciki,
bandakin ya kusa girman dakinta, ta karanto addu'ar shiga banɗaki a ranta sannan ta
shiga, Mami ta mike ta tafi daki ta ga Khalil ya dauro alwala ya fito, area din da
Mami tayi demarcating a dakin don yin sallah ya nufa, Mami ta dau ma Nihad darduma
daya ta kai parlor ta shimfida mata, sannan ta koma dakin ta shiga bandaki ita ma
ta dauro alwalan, Khalil na zaune saman darduma yana azkar bayan ya idar da sallah,
Mami ta mike bayan ita ma ta idar tana kallon side din da yake tace "Yanzu abincin
xan dauka in kai can parlon, ko ta shigo nan kawai ku ci?" Yace "Ki deba kawai ki
kai mata can parlon Mami" Mami tace "Ai ban san abinda tafi son ci ba, kawai bari
ta shigo ta yi serving kanta ko?" Mami na fadan haka ta fita zuwa parlor tana
kallon Nihad dake saman darduma tayi kuri da ido tace "Baby shigo ki ci abinci"
Nihad ta mike a hankali ta tafi kofar dakin ganin taki shigowa Mami tace "Shigo
mana" Cikin sanyin murya tayi sallama ta shiga dakin, ta dinga bin abincin dake
jibge a kasa da kallo kamar za ayi party, Mami tace "Ki duba duk abinda kike so ki
diba" Mami na fadan haka ta fita daga dakin, Nihad ta durkusa tana kallon Khalil,
murya can kasa tace "Don Allah ina ne nan ka kawo ni?" Sai a sannan Khalil ya
kalleta tun da ta shigo dakin yace "Inda za a mana alfarma ba tare da an walakanta
mu ko an ci zarafinmu ba, ba kuma tare da an damu da mu talaka ne ko masu arziki
ba" Shiru tayi tana kallonsa, ya mike ya zauna gefen gadon yace "Debi abinda zaki
deba ki fita" Ita dai ta kasa cewa komai kuma ta kasa bude ko warmer daya balle ta
zuba abincin, Mami ta dawo dakin rike da teapot da cups dinsa biyu a tray, da
mamaki ta ke kallon Nihad bayan ta ajiye tray din hannunta tace "Baki debi abincin
ba" Sai kuma ta kalli khalil kafin tace komai ya kirkiri murmushi yace "Haka take
Mami" Nihad ta daga kai ta kallesa, Mami tace "But why? pls tell her to feel free"
Khalil ya maida idonsa kan tv dake aiki silently bai ce komai ba, Mami ta dau plate
ta debar ma Nihad shinkafa da miya ta ajiye mata, ta debar mata duk wani abu da
xata dibar mata sannan ta mike, Nihad dai bata ta6a jin she is confuse kamar yanda
take ji yanzu ba, gaba daga kanta ya kulle ta kasa fahimtar komai, lkci lkci sai ta
kalli khalil sannan ta kalli Mami, Mami na kallon Khalil a hankali bayan ta gama
zuba ma Nihad abinci tace "When did you say he called you?" Khalil ya kalleta duk
da ya gane wanda take nufi yace "Ke baxa ki ci abincin ba Mami? Ki zuba mana tare
mu ci" Mami tace "Talk to me son, he is back now" Sai da gaban khalil ya fadi ya
mike yace "Really? But hope you didn't...." Sai kuma yayi shiru, ta gefen ido ya
kalli Nihad da ta kafesa da ido babu ko kiftawa, sai kuma ya fice daga dakin, Mami
na kallon Nihad da murmushi fuskarta tace "Ki ci abinci kin ji Baby" Daga haka ta
juya ta bi bayansa, Nihad ta bi su da kallo bata kwakkwaran numfashi, bayan kusan
minti sha biyar Khalil ya dawo dakin shi kadai, har sannan Nihad na zaune position
din da take kamar warce ruwa ya cinye, gaba daya jikinta yayi sanyi qlau kana mata
kallo daya zaka gane hakan, Ta bi sa da kallo har ya dau teapot da cup zai fita,
cikin sanyin murya tace "Ka gaya min, wanene kai?" Bai yarda ya kalleta ba yace
"Driver!!" Daga haka ya fice daga dakin, ta bi sa da ido babu ko kiftawa, abinda ya
fada dazu da turanci ne ke kai komo a ƙwaƙwalwarta, lokaci daya ta runtse ido ko
zata samu saukin sara mata da kanta ke yi. Khalil na zaune parlor sai ga Mami ta
shigo tana kallonsa, shi ma kallonta yake, a hankali tace "Kaje wajen Abbanka, yana
kiranka parlonsa" Khalil ya kalleta looking so worried yace "Mami da baki ce masa
na dawo yau ba" Mami ta girgiza kai tace "I never told him, tun daga gate ya
tambaya securities, su suka sanar masa kana gidan nan....." Yayi kasa da murya yace
"But bana son kowa ya san am around Mami" Mami tace "Zaka iya zagawa ta baya ai,
har yanzu babu wanda yasan kana gidan nan" Mikewa yayi ya nufi kofa yana tafiya a
hankali ta bi sa da kallo har ya fita.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and ur evidence via👇🏻

07087865788

Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku
anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama
Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya
zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da
matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani
prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa
jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using
mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki
kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi
gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai
na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin
keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD💖💖

39

Bayan Azahar Aunty Maryam ta sakko downstairs tana kallon mai aikinta dake parlor
tace "Kin kai ma bakuwar can abinci kuwa?" Mai aikin ta tashi da sauri tace
"Wallahi na manta Hajiya" Aunty Maryam ta saki baki tana kallonta tace "Amma ai
baki mance naki cikin ba" Da sauri mai aikin tayi hanyar kitchen, Aunty Maryam ta
nufi guess room, bude kofar dakin tayi taga Nihad zaune saman darduma, Aunty Maryam
ta shiga dakin, Nihad ta daga kai tana kallonta, Aunty Maryam tace "Kiyi hakuri
ashe wancan gantalalliyar bata kawo maki abinci ba ni ina can sama ban sani ba"
Nihad dai tayi murmushi kawai bata ce komai ba, Aunty Maryam tace "Me yasa kika ki
zama parlon kiyi kallo?" A hankali Nihad tace "Ba komai" Aunty Maryam bata kuma
cewa komai ba, Sai ga Murja ta shigo da abinci dakin ta ajiye ma Nihad, Aunty
Maryam na kallonta tace "Ki karo lemun" Da sauri Nihad tace "Aa ya isa Aunty" Aunty
Maryam tace "Toh zuba abincin ki ci" Daga haka ta juya ta fita daga dakin, All
through Khalil na compound wajen shan iska tare da Nadeeyah, kana ganinsu kasan
they really missed each other, abincin ma waje aka kai masu suka ci tare, bayan
Nadeeyah ta zuba masa drink din kwalin gabansa yana kallonta yace "Thank you" Tayi
murmushi tace "Continue... ina jin ka" Ya ɗan buda ido yace "Me xan ce kuma,?" Tace
"Ba labarin stay dinka a kano kake bani ba, ai baka gama ba" Yayi murmushi yana
shafa kansa yace "Shikenan, all the household are very nyc, i think that's the most
important of all" Tace "To ita wannan yarinyar da na ganku tare, yar gidan ce?"
Yayi shiru, sai kuma yace "Nihal!! Of course yarinyar mai gidan ce..." Nadeeyah
tace "Allah sarki, wani school take?" Yace "Ahmadu Bello" Nadeeyah tace "Ohk, but
kasan har yau yan gidanku basu san inda kake ba all those while, a lot of time
Farhana da Sajida suna yawan tambayata about u, irin dai suna son su san ko i know
about your whereabout" Yayi murmushi bai ce komai ba, tayi sipping drink din
gabanta tace "Kasan everything happens for a reason, may be don kaje ku hadu da yan
gidan ku kulla zumunci shi sa Allah ya kaddara zaka je kano har kuma ka je gidansu,
kaga ai baxa ka manta halaccinsu ba" Ya gyada kai yace "Haka ne" Tace "And you mean
har yanzu basu san kai waye ba har bayan da ka dawo Abuja?" Ya girgiza kai yace
"Basu sani ba" Tayi murmushi tace "Za su yi mamaki kuwa idan suka san kai wanene,
but menene ya ja ra'ayinka har ka je gidan nasu ka zauna bayan baka ta6a saninsu ba
sannan ba rasa wajen da zaka zauna a kano kayi ba, infact ko hayar nawa ne nasan
xaka iya affording, u can even decide to stay in the hotel don duk da ba salary
kake samu ba sannan babu wani source of income don duk Abba ya toshe hanyar but
still nasan u neva ran out of cash all that period, Mami na tura maka, Aunty
Maryam, Aunty Hamida even though bata kasar...." Murmushi yayi yana kallonta murya
can kasa yace "And even you yourself" Ta hararesa tace "A'a ni ka cireni a lissafi
don anything mine is urs" Ta tallabi chin dinta ta ci gaba tace "So how did u even
know about them? And me yasa kayi deciding zaman gidan?" Yayi shiru yana kallonta
kamar baxai ce komai, can kuma yace "I will tell u some other time Nadeeyah" Tace
"Why?" Yace "I don't want to talk about it now" Ta langwabar da kai a hankali tace
"Amma ka ta6a saninsu ne?" Ya girgiza kai yace "Nace xan baki labarin some other
time" Tace "Ohk, but ya kamata ko Mami ka hada da yan gidan su gaisa a waya, su ma
za su san kayi appreciating dinsu" Yace "I will do that dear" a hankali tace "But
why did u keep on telling me kana USA?" Yace "Saboda nasan xa ki iya cewa xaki zo
kano saboda ni, shi yasa ma ranan da muka hadu nace maki in few hours time flight
dina xai tashi, don kar ki saka ran za mu hadu" Murmushi kawai Nadeeyah tayi tana
kallonsa... sai kusan la'asar suka shiga cikin gida, Nadeeyah ta haura sama shi
kuma ya zauna parlor, ko minti biyar bai yi zaune parlon ba Nihad ta fito rike da
warmers na abinci da mai aikin Aunty Maryam ta kai mata, tun da suka hada ido sau
daya bata sake kallon direction dinsa ba, sai dai kuma bata san hanyar kitchen ba
don tayi zaton zata hadu da mai aikin ne a parlor, juyawa tayi ta koma inda ta
fito, sai ga Mami ta sauko downstairs tare da Mum din Nadeeyah da Aunty Maryam,
Mami tace "Khalil xaka ajiyesu gida daga can mu tafi gida, xata kira driver nace ba
sai ta kirasa ba mu ma yanzu za mu tafi gwara mu tafi gaba daya" Khalil ya mike
yace "Ohk" Mami ta nufi Aunty Maryam dake answering call tayi kasa da murya tace
"Kai ni mu yi sallama da ita, ina ga ai daga nan zata wuce in ta amshi abinda xata
amsa" Aunty Maryam ta nufi bangaren da Nihad take Mami na biye da ita a baya, Aunty
Maryam ta bude kofar, kwance suka ganta a kasa, Aunty Maryam ta katse wayar da take
tace "Me yasa xaki kwanta a kasa ga gado?" Nihad ta mike zaune bata ce komai ba,
Mami tace "Naga bata da sabo ne da wuri" Mami na Murmushi tace "Ya sunanki?" Nihad
bata iya ta dago kanta ba a hankali tace "Fatima amma ana kirana Nihad" Aunty
Maryam ta kalli Mami, Mami tace "To maa sha Allah Nihad, yaushe xa a baki admission
letter din?" Sai a sannan Nihad ta daga kai tana kallon Mami, Mami tace "Yaushe
suka ce?" Cikin sanyin murya tace "Nima ban sani ba" Mami tace "Toh jiya me suka ce
maki a makarantar" Ta sauke idonta kasa tace "Shi ne dai suka gaya ma ba ni ba"
Mami ta kalli Aunty Maryam, Sai kuma tace "Toh, ya dai ce kafin sati za ki samu,
idan na zo nan din kafin ki tafi to, idan kuma ban zo ba xan bada sako a kawo maki
kin ji? Sannan ki gaida su mamanki da kyau" Nihad ta gyada mata kai kawai, Mami
tace "Toh sai anjima" Cikin sanyin murya Nihad tace "Nagode" Tana fadin haka ta
fara cire dankunnen dake kunnenta tace "Ga dankunnen" Mami tace "Aa, na baki ne ki
dinga sa wa Nihad" Nihad ta mayar tace "Toh Nagode, Allah ya saka da Alkhairi" Mami
na Murmushi tace "Ameen" Daga haka tace "Mun tafi" Ta juya ta fita dakin, Aunty
Maryam ta bi bayanta ta kullo kofar dakin. Khalil kadai ke jiransu a parlon,
Nadeeyah da Mum dinta kuwa sun fita compound, Mami na kallon Khalil tace "Ina
suke?" Yace "They are outside" tace "Toh mu je" Ya kalli Aunty Maryam yace "Na sa
wayata caji idan na ajiyesu xan dawo in dauka anjima Aunty" Mami tace "Ji wani
wahalar da kai, ka dau wayar mana idan mun je gida ka sa a cajin" Aunty Maryam tayi
dariya tace "Baki ga yanda na saki baki ina kallonsa ba" Ya ɗan yi murmushi yana
sosa kai yace "Haka ne" Gun wayar ya nufa, Mami ta juya ta fita daga parlon, ya
juya ya kalli Aunty Maryam yace "Kawai bari in bar shi Aunty, ai bamu gama hiran ba
dama" Aunty Maryam tace "Toh je ka ajiyesu ka dawo, akwai abinda kake so ayi maka
kafin ka dawo" Yace "Aa coffee kawai xan sha idan na dawo" Tace "Toh sai ka dawo
son" Daga haka ya fita parlon da sauri zuwa parking space. Wajen karfe biyar da
wani abu Nihad ta fito parlor, Aunty Maryam dake zaune parlon tana rungume da
autanta Mus'ab ya dawo makaranta ta kalli Nihad tace "Kin fito" Nihad na wasa da
fingers dinta tace "Eh, akwai aikin da xa ayi Aunty?" Aunty Maryam tayi murmushi
tace "Aa Nihad, Murja ta ma kusa gama girkin ina ji yanzu, karaso ki zauna" Nihad
ta karaso cikin parlon ta zauna a kasa, Aunty Maryam tace "Hau saman kujera mana"
Nihad ta girgiza kai tace "Aa nan ya isa" Mus'ab dake kallonta yace "Ummi is she
our visitor?" Aunty Maryam tace "Yes dear, sauka kasa ka gaisheta" Ya sauka daga
jikin mamarsa yace "Good evening" Nihad na kallonsa tayi murmushi don mate din
Fadil dinsu ne tace "How are you?" Ya koma jikin mamarsa yace "Fine" Har Bayan
magrib Nihad na parlon tare da Aunty Maryam, aka bude kofa Khalil ya shigo da
sallama, Aunty Maryam ta amsa masa tana kallonsa tace "Sai yanzu?" Ya karaso cikin
parlon ya ajiye jakar hannunsa yace "Eh Aunty, good evening" Tace "Evening welcome,
wannan jakar fa? Ko na ta ne?" Ya nufi wayarsa yace "Eh nata ne" Ya dauko wayar ya
dawo ya zauna, Aunty Maryam na kallon Nihad tace "Dauka ki kai can dakin" Tashi
Nihad tayi ba tare da ta kalli inda yake ba ta dau jakar ta wuce ciki, Aunty Maryam
tana kallonsa tace "A kawo maka abincin ko coffeen dai" Yace "Na sha a gida Aunty"
Tace "Ohk, Mami tace xaka yi tafiya, yaushe ne tafiyar?" Ya ɗan yi shiru sai kuma
yace "Nan dai da kwana biyu idan na gama shirye shirye" Tace "Toh Allah ya kai mu"
Wayarsa yake dubawa ya ga missed calls din Farooq, ko jiya ya kirasa, Khalil yayi
dialing numbersa ya kai kunne, Farooq na dagawa suka gaisa, Farooq yace "Har yanzu
baka turo ba Khalil" Khalil ya shafa kansa yace "Nace kar ka damu Yallabai, da da
bukatar hakan xan tura maka" Farooq yace "Ehh naji, amma kawai ka turo min"
Murmushi Khalil yayi yace "Toh shkkn, Mun gode Allah ya saka da alkhairi" Farooq
yace "Fatan dai kuna lafiya?" Khalil yace "Alhmdlh" Farooq yace "Zariyan a wani
anguwa ku ke, ina ga in shigo ko jibi weekend" Khalil yace "Ohk zan tambaya" Khalil
yace "Ohk, tana kusa?" Khalil yace "Bari in bata" Mikewa yayi yana kallon Aunty
Maryam dake ta kallonsa ya mata alamar yana zuwa sannan ya tafi inda Nihad take,
saman gado ya sameta kwance, ya karasa ya mika mata wayar, ta mike zaune tana
kallon Iphone da yake mika mata, ta kai hannu ta amsa tana kallon screen din taga
number ya farooq don a haddace yake a kanta, ta kai kunne cikin sanyin murya tace
"Ya farooq" Daga daya bangaren yace "Na'am Lil sis ya kike" Lkci daya har hawaye ya
kawo idonta tana goge idonta cikin rawar murya tace "Lafiya lau" Yayi shiru, sai
kuma yayi kasa da murya yace "Yanzu kukan me kike? Ko akwai damuwa ne?" Ta kasa ce
masa komai, yace "Nihad" Tana goge idonta tace "Na'am" Shi dai khalil na tsaye yana
kallonta, Ya Farooq yace "Bana son wannan kukan naki Nihad, shi yasa ko na kirasa
bana cewa ya baki, kukan nan yana damuna idan kina yi" A hankali tace "Toh na daina
yaya" Yace "Good girl, kiyi hakuri in sha Allah komai xai wuce, komai yayi farko
xai yi karshe in sha Allah, don haka ke dai ki zama me biyayya ku zauna lafiya da
mijinki, sannan ki rike Ibada sosai, may Allah guide
and protect you for us" Cikin sanyin murya Nihad tace "Ameen yaya" Yace "Har yanzu
baki da atm card ko?" Ta gyada masa kai kamar yana ganinta, yace "Hello" Tace "Ehh
bani da shi" Yace "Toh shikenan, in sha Allah on Saturday xan zo, na gaya masa ma"
Nihad tace "Ina zaka zo yaya?" Yace "Wajenku idan Allah ya kai mu, be a good girl
always, Allah ya maki albarka" Tace "Ameen yaya" yace "Give him the phone" Mika
masa wayar tayi ba tare da ta bari sun hada ido ba, shi dai kallonta kawai yake,
bai kuma amshi wayar ba, ita kuma taki yarda ta kallesa, ganin still ya ki amsar
wayar ta ajiye masa nan gefen gado ta koma tayi kwanciyarta ta juya masa baya, ya
shafa beard dinsa, sai kuma ya dauki wayar ya juya ya fita ya kulle mata kofa.
Wajen karfe tara da rabi Aunty Maryam ta bude kofar dakin da Nihad ke ciki, zaune
ta sameta saman darduma ta jinginar da kanta da gado, Aunty Maryam tace "Sai yanzu
kika yi isha'in? Nihad ta girgiza kai tace "Aa tun daxu nayi" Aunty Maryam tace
"Toh baxa ki kara abinci ba ko?" Nihad ta gyada mata kai tace "Ehh Aunty nagode"
Aunty Maryam tace "Toh shkkn, tunda ga kayanki ya kawo ki yi wanka sai ki kwanta,
ga zani kiyi amfani da shi don towel din bandakin ba a wanke yake ba" Nihad ta
nufeta ta amshi zanin da take mika mata tace "Nagode" Aunty Maryam tace "Ni xan
tafi daki, Allah ya tashe mu lafiya" Nihad tace "Toh sai da safe" Juyawa Aunty
Maryam tayi ta rufo mata kofar ta bar wajen, Nihad ta koma gefen gadon ta ajiye
zanin, sannan ta cire Hijab din da tayi sallah ta linke ta ajiye don a dakin ta
gani. Ta kalli jakar da ta shigo da shi daxu dakin, can ta nufi gun jakar ta
durkusa ta bude zip din a hankali tana kallon ciki, Hijab da aka yi packaging a
leda ta ciro har guda hudu, sai kuma Abaya kala biyar da undies masu yawa, sai
kayan shafe shafe with perfumes kala biyar, da nighties su ma biyar, kulle jakar
tayi ta mike ta bar wajen. Duk da Nihad felt secured a gidan Aunty Maryam amma
wannan daren ma ta nemi bacci ta rasa, for almost 4 days now bata bacci da daddare
ko tayi a firgice zata farka bayan wasu mintuna, or is she been traumatic, bata
taɓa jin tana kewar Mahaifiyarta yanda take ji yanzu ba, maganganunta na karshe ya
kasa fita daga ranta da zuciyarta, she could vividly remember every single word shi
told her a rananta na karshe a gidansu, and she wish she could hear more of such
from her, Magana da tayi da Ya farooq daxu shi ma yayi contributing a rest of mind
dinta but she still couldn't sleep, gaba daya idanuwanta sun kekyashe daga jin
bacci, daga karshe ta tashi a hankali ta kumna switch din dakin ta ga karfe biyun
dare, cike da karfin hali ta nufi bandaki tana jan kafa, har kusan karfe uku da
rabi Nihad bata yi bacci ba tayi sallan har taji bata da sauran strength kawai ta
jinginar da kanta da gado tana daga zaune kan darduman, sai a sannan taji hawaye na
sauka idonta, cikin rawar murya tace "Ya Allah duk wanda yayi min wannan abun ka
tona asirinsa cikin gaggawa, come to my aid ya Allah, Allah ka kawo min mafita
alfarman ma'aiki" Kuka take sosai tana roƙon Allah, wanda tun faruwan abun yau ne
ta kwantar da hankali take kai kukanta wajen Allah cikin nutsuwa, ko jin sanda aka
bude kofar dakin bata yi, cause she is really hurt, sae yanxu take ganin she needs
to know who is this that betrayed her, she needs to know who did this to her da ya
tarwatse farin cikinta ya rabata da Abbanta ya bata mata suna yayi tarnishing image
dinta a idon duniya, Aunty Maryam dai sai kallonta take tana tsaye bakin kofa, dama
ka'idarta ce duk in Allah ya farkar da ita cikin dare ko dab da asuba ko da baxata
yi sallah ba sai ta fito ta dudduba condition din yaranta idan suna gidan, har
dakin mai aikinta takan bude ta dubata, in ma da wani bako gidan in dai ba babba
bane xata bude dakin ta duba, sai in Allah bai farkar da ita ba wanda hakan ma ya
zame mata jiki dole ko yaya sai ta tashi saboda ta maida shi daily routine dinta a
gidan.... (Yana da kyau iyaye mata su sa ido su yi kokarin dinga yin hakan ko da ba
kullum ba barin idan kana da yara yan mata teenagers, kai har ma da yara mazan, its
very very important, i have this aunty that kullum da daddare sai ta leko ku taga
halin da ku ke ciki a daki, ya ma riga ya zame mata jiki, da Mumyn Nihad na kokarin
yi ma Nihad haka ko da ba a bangarenta take ba da abubuwa da yawa basu faru ba
kamar zuwa night parties da take, wasu yan matan sai su kai har karfe daya ana
video call da saurayi kasa kasa, ko chatting din banza, wasu kuma a wannan lokacin
xa su samu daman shiga internet su yi kallace kallacen banxa, wasu masturbation da
dai sauransu, duk kina can kin shanya baki hangangan kina bacci, Allah Ubangiji ya
kare mana zuri'a ya raba mu da mugun ji da mugun gani) Duk abubuwan da Nihad ke
fada Aunty Maryam na jin ta don daga karshe ma kulle kofar dakin tayi a hankali,
wanda hakan ne yayi distracting Nihad ta juya da sauri, sai da gabanta ya fadi
ganinta tsaye bakin kofar, ta hau goge idonta da sauri, Aunty Maryam ta karaso
cikin dakin tana kallonta ta zauna gefen gado tayi kasa da murya tace "It's okay
dear, tunda ki ka kai kukanki wajen Allah kika hana kanki bacci a wannan lokacin,
to in sha Allah addu'arki baxata tashi a banza ba, ta yanda baki yi zato ba Allah
xai maki sakayya ya kuma tona asirin koma wanene yayi maki wannan abun" Hawaye ya
dinga sauka idon Nihad ta kasa ce ma Aunty Maryam komai, Aunty Maryam da taji
tausayinta ainun tace "Kiyi hakuri ki daina wannan kukan, tunda kika ambaci Allah
ai an wuce wajen kuma, amma me yasa kika yarda da kawaye har zaki zauna cikinsu
half naked?" Nihad ta girgiza kai cikin rawan murya tace "Wallahi Aunty ni ban taɓa
zama ko a gidanmu haka ba, sannan ni ba a hostel nake ba kawai zuwa nake, lokacin
da xa mu fara exams din first semester level 3 ne na koma hostel kuma ni ko da zani
bana zama cikinsu wallahi" Aunty Maryam na kallonta da mamaki tace "Toh a ina aka
dau video din?" Nihad ta buda hannu tace "Nima wallahi ban sani ba, yanda kowa ya
gansa haka na gansa" Aunty Maryam ta dinga kallonta dumbfounded, can tace "Ban gane
baki san a inda aka maki video din ba" Nihad ta fashe da kuka tace "Wallahi da
gaske Aunty, ni ban san ta yaya aka yi hakan ba, kuma ban ma san ko wani waje ne
ba" Aunty Maryam ta kasa cewa komai don mamaki, can dai tace "Toh kenan ba ke bace
a video din" Nihad na goge idonta tace "Ni ce Aunty, amma ban san ta yaya ba,
because under wears dina ne a jikina" Sosai wannan lamarin ya rikitar da Aunty
Maryam, can dai ta sake cewa "Kuma ba a hostel din bane?" Nihad tace "Ba nan bane
wllh" Aunty Maryam tace "Ba kuma gidanku bane?" Nihad ta girgiza kai tace "Ba
gidanmu bane" Aunty Maryam tace "Ikon Allah, kin tabbata bayan gida baki zuwa wani
wajen ko da kawaye haka?" Shiru Nihad tayi, Aunty Maryam tace "Kin yi shiru" Nihad
ta hadiye abu da kyar amma tana tsoron ce ma Aunty Maryam ai sun kan je hotel da
guess lodge da friends dinta, Aunty Maryam tace "Kina zuwa kenan?" Cikin sanyin
murya tace "Ina bin kawayena duk inda xa su wani lokacin" Aunty Maryam tace "Toh su
suka maki, ki gaya min tsakaninki da Allah baki shan komai?" Nihad ta dago da sauri
tana kallon Aunty Maryam tace "Aunty kamar me" Aunty Maryam tace "Kayan maye, gaya
min tsakaninki da Allah, kar ki min karya don kina min ma zan gwada ki kuma zan
gane, don ni Nurse ce" Nihad na girgiza kai hawaye na sauka idonta tace "Wallahi
Aunty bana shan komai kin ji har na rantse, idan ina shan wani abu Allah shine
shaidata, ki gwada ki ga Aunty" Aunty Maryam tace "Toh kawayen naki fa?" Nan Nihad
ta fara lissafo ma Aunty Maryam abubuwan da su Husnah suke sha Innocently, haka
Aunty Maryam ta saki baki tana kallonta cause taga babu alamar karya a tare da ita,
iya gaskiyarta kawai take fada, can Aunty Maryam tace "Ikon Allah, to kuma a gida
an san kina bin wa ennan kawayen har ma ki bi su duk inda xa su?" Nihad ta girgiza
kai tace "Stepmom dita ce kawai ta sani, ta ma san gaba dayansu" Buda baki Aunty
Maryam tayi, sai kuma tace "Kuma bata hanaki alaqa da su ba?" Nihad tace "Aa, tace
min in rikesu baxan samu kamarsu ba don suna sona sosai, kuma tana kare ni yanda
yan sauran yan gidan baxa su gane ba, idan na dawo da daddare ita take bude min
kofan parlon mu idan an kulle" Aunty Maryam was really shock jin abinda Nihad tace,
taji zufa na keto mata, tace "Mamarki fa?" Nihad ta girgiza kai a hankali tace
"Bata sani ba ai, dama a bangaren stepmom dina nake, so akwai distance tsakanin
part din stepmom din tawa da na Mum dina...." Aunty Maryam tace "Wa ya ce ki koma
part din stepmom din taki?" Nihad tace "Aa wai tun ina karama ta dawo da ni wajenta
shi ne har na girma" Aunty Maryam tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to ina
jin ki, idan ta bude maki kofar da daddare sai tace maki me??" Nihad tace "Kawai
cewa xata yi inyi sauri in wuce kar a gan ni" Aunty Maryam bata san sanda hawaye ya
kawo idonta ba, nan ta kara tsorata da lamarin kishiya, bata san sanda ta dafe
kanta da yayi mata nauyi ba, can ta dago da kyar tace "Bata da yara ne?" Nihad ta
girgiza kai a hankali tace "Tana da yarinya mate dita, her name is Nihal, ita kuma
tana side din Mumy na, sannan akwai Amina da Aunty Kamila that is married" Aunty
Maryam tace "Kuma duk su ma yaran nata dake gidan suna fita su kai dare ta bude
masu kofa?" Nihad ta girgiza kai da sauri tace "Aa babu inda suke zuwa su, ba ma su
da friends" Aunty Maryam tace "Nihad" Nihad ta daga kai ta kalleta, Aunty Maryam
tace "Ku nawa ne wajen mamanki?" Nihad tace "Mu uku ne, ni ce first born" Aunty
Maryam was so heartbroken, tace "Ita kuma fa?" Nihad tace "Babban yayanmu ya Farooq
sai ya Usman, sai Aunty Kamila, Nihal da Amina" Aunty Maryam na girgiza kai tace
"Yanzu a tunaninki duk gidan wa yafi sonki? Yake maki duk abinda kike so?" Nihad ta
sunkuyar da kai a hankali tace "Umma" Aunty Maryam tace "Wacece Umma?" Nihad tace
"My Stepmom" cike da takaici Aunty Maryam na girgiza kai tace "Ta cuci rayuwarki,
ta cuceki, ta cuci mahaifiyarki, ita
kuma salon nata kishin kenan?? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, da wannan abun
da ta maki da gwara ta fuskanci mahaifiyarki su xuba kishin yanda ya kamata, bata
maki adalci ba, kuma ko tantama babu da sa hannun wannan matar a video din naki,
Nihad wani masoyinka ne xai dinga supporting dinka kana bad things, kana abubuwan
da basu dace ba? Wani masoyinka ne xai xuba maka ido ka fita ka kai har dare shi
bai maka fada ba kuma ya kareka ta yanda wasu baxa su sani ba balle su maka fada?
Wani masoyinka ne xai ce ka rike yan iska masu shaye shaye a matsayin kawaye har
yana ikirarin baxa ka samu kamar su ba, sannan ya daure maka kugu ka dinga bin su
duk inda xa su? Nihad me yasa ita nata yaran basu da kawaye sannan basa fitan
dare?" Shiru Nihad tayi tana kallon Aunty Maryam ko kiftawa babu, Aunty Maryam tace
"Ba shiru xa kiyi min ba bude baki ki bani amsa yanzun nan?" Tunda Nihad take bata
ta6a zaunawa tayi wannan tunanin ba balle har ta gane komai tayi reasoning a kai,
ita dai Aunty Jamila kawai rabata take da Umma ta karfi da yaji amma bata ta6a
zaunawa ta zayyano mata abubuwan nan da Aunty Maryam ta zayyano mata ba yanzu, to
ai bata ma san abinda take yi da sanin Umman ba balle har ta zayyano mata wannan
abubuwan tunda komanta a boye take yi, Umma ce kawai ta sani... Aunty Maryam bata
yi interrupting Nihad a duniyar tunanin da ta fada ba, kana kallon fuskarta zaka
fahimci she is slowly trying to comprehend duk wani abinda Aunty Maryam ta fada ne,
babu kuma abinda ya fado ran Nihad sai karyan da suka yi ma yan gida wai zata bi
Aunty Kamila kebbi alhalin hostel xata koma da zama, Umma da Aunty Kamilar ne kadai
suka san gaskiyar maganar, kuma har ta gama zamanta hostel din for more than 3
months Umma bata ta6a zuwa inda take ba, har ita Aunty Kamilan, alhalin idan mutum
na hostel kuma iyayensa na garin ko bayan sati uku ne su kan kai masa ziyara.
Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and ur evidence via

07087865788...
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

38

Khalil bai kuma ce ma Mami komai ba sai kallonta kawai yake lokaci daya duk jikinsa
yayi sanyi, juyawa Mami tayi ta fice daga dakin ta zauna second parlonta, a hankali
Khalil ya zauna kan kujeran dake dakin yana jin kansa na mugun sara masa, gaba daya
he is confuse, dafe kansa yayi thinking of where to start from, where will he begin
now? Damuwar Mami ya ninka wanda shi ya ji ya shiga a lkcn, daga karshe taji ta
kasa zaman ɓangaren nata, she just can't imagine Khalil ya sake barin gida for the
second time saboda wannan issue din, tafi kowa sanin halin mahaifinsa, this time
around also he won't take it likely with him, tashi tayi tana jin wani sabon
tashin hankali ta fita daga parlon, Nihad na nan zaune yanda take a first parlor
din, Mami bata yarda ta kalleta ba amma jin yanda take kuka sai ta kasa fita daga
parlon duk da ta bude kofa, kulle kofar tayi gently ta juya ta kalleta, sai kuma ta
nufeta walking slowly tace "Kina ji na, ki daina wannan kukan ya isa haka, ga
breakfast dinki ki tashi kiyi" Nihad bata iya ta ce mata komai sai kuka take kamar
ranta zai fita, sai a yanzu maganganun Aunty Jamila ke dawo mata and it seems this
is just the beginning of what she's talking about.... Mami tayi karfin halin cewa
"Taso muje can parlon ki karya, kuma nace ki daina wannan kukan haka nan" Daga haka
Mami ta daukar mata abubuwan karin ta kai other parlor dinta ta ajiye, bayan ta
dawo parlon tana kallon Nihad tace "Baxa ki bar kukan nan haka ba? Taso mu je can
parlon" Sai a sannan Nihad ta mike da kyar, har sannan kuma ta kasa daina kukan da
take, Mami ta rike hannunta har zuwa daya parlon ta zaunar da ita tace "Eat now"
Zaunawa kawai Nihad tayi, her heart is so heavy, and she is now beginning to feel
useless, juyawa Mami tayi ta fita daga parlon, Visitor room dake bangaren nata ta
shiga kawai ta zauna cike da damuwa. Khalil ya mike daga karshe jin kukan da Nihad
take ya fito parlon don Mami a bude ta bar kofar bedroom din nata da ta fita,
Zaunawa yayi kan kujeran dake kusa da inda take zaune, he is speechless at first,
after few seconds ya kalleta, a hankali yace "It's okay, and...." Sai kuma yayi
shiru, Can yace "Kiyi hakuri" Ta hade kai da gwiwa tana kuka sosai, yace "Baki ji
me nace ba" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa da idanuwanta da suka yi jajir, ya
kasa ci gaba da kallonta ya sauke idonsa yace "Kiyi hakuri, take ur breakfast now"
A hankali ta dinga subsiding kukan da take amma tana jin xuciyarta na mata zafi, Ya
sauka ya koma inda take without looking at her ya dau cup ya zuba mata ruwan shayi,
ya haɗa mata shayin, ya ajiye side dinta, ita dai goge hawayen da yaki tsaya mata
kawai take tana kallonsa, Bude kofa yaji anyi a other parlor din, ya dau shayin
yace "Tashi mu je ciki kiyi breakfast din" Mikewa tayi da sauri ta bi bayansa zuwa
bedroom din Mami, ya ajiye mata shayin sannan ya koma zai dauko sauran abincin,
Mami ce ta shigo parlon, ganin Nihad bata parlon ta sauke ajiyar xuciya, juyawa
khalil yayi bayan ya dau abincin ya nufi Bedroom da sauri saboda muryoyin wa enda
yake ji, Mami ta zauna parlon har Hajiya Amina ta karaso ta zauna, Sai Hajiya
Hassana ma ta shigo ta zauna, Hajiya Amina tace "Yanzu tun jiya dama Khalil ya dawo
gidan nan aka ki sanar mana? Sai kace wani mugun abu, sannan kuma ya ki zuwa ya
gaida mu?" Mami tace "Jiyan ai ba da wuri ya dawo ba" Hajiya Amina tace "Toh ai bai
wuce duk mu yi barka ba, mu bama bakin ciki da abun alkhairi, daxu su Farhana ke ce
min ya dawo nace to ai haka dama ake so" Hajiya Hassana dake girgiza kafa tace
"Yana ina yanzu?" Mikewa Mami tayi ta wuce bedroom dinta, duk suka kalli juna suka
ta6e baki a tare, Mami na shiga dakin ta kulle kofar, Khalil na zaune ya sa Nihad a
gaba tana shan shayin hannunta da kyar, yana ganin Mami ya mike ɗan yana durkushe a
gabanta ne, Mami tace "Ka fito ku gaisa" khalil ya kalleta ya ɗan hade rai yace "In
gaisa da wa?" Mami tace "Ka rufa min asiri, minti nawa ne kun gaisa ka juyo" Ya
girgiza kai yace "Aa kiyi hakuri Mami, wallahi baxan fita ba" kasa cewa komai Mami
tayi tana kallonsa, ya koma saman kujera ya zauna yace "Saboda me xan gaisa da su,
sanda xan tafi sallama muka yi da su balle mu gaisa yanzu da na dawo, i am sorry
Mami i am not going out" Mami sai kallonsa take, can tace "Toh ko bakin kofa ai sai
ka tsaya Khalil, kai baka gudun abun magana ko?" Yace "Aa gaskiya bana gudu Mami, i
am not moving an inch from here, ita Aunty Hassana dama a shirye nake da ita na
dawo gidan nan, she shouldn't dare cross my part" Mami dai duk jikinta yayi sanyi
ta kasa ce masa komai, daga karshe Khalil ya tashi ya bude bandaki ya shige, A
hankali Mami ta juya ta fita ta koma parlon tana kirkiran murmushi tace "Shiryawa
yake, idan ya gama duk xai je ya gaishe ku" Hajiya Hassana ta daga mata hannu ta
dakatar da ita da sauri tace "Aa ba sai kin karesa ba Fatima, ai bamu isa ya fito
ya gaida mu ba ne, mu a su wa?" Mikewa tayi tana kallon Hajiya Amina tace "Taso mu
je Amina" Hajiya Amina ta mike suka nufi kofa Mami ta bi su da kallo har suka fita,
Mami ta sauke ajiyar xuciya ta zauna. Daga karshe ta mike ta fita daga parlon nata,
ba a dau lokaci ba ta dawo rike da kayan Mimi, ta shiga dakinta ta ajiye gefen gado
tana kallon Nihad tace "Shiga bandaki kiyi wanka yanzu" Khalil dai na zaune yana
kallon Mami, Nihad ta tashi ta shiga bandakin, Mami ta fito parlor, biyota yayi ya
zauna kujeran kusa da ita yayi kasa da murya yace "Don Allah ki saurareni Mami"
Mami tace "Sauraran me xan maka Khalil" Yayi gathering courage xai yi magana aka
bude kofa duk suka juya, Farhana ta shigo parlon tana kallon Khalil tace "Yayanmu
wai kaje Abuu yana kiranka" Yayi shiru yana kallonta, Mami ta hadiye abu da kyar
tana kallon Farhana tace "Ki je yana zuwa" Juyawa tayi ta bar wajen, Mami ta
kallesa da damuwa tace "Ka je kaji kiran da yake maka" Khalil bai iya yace komai
ba, can ya mike ya fita, slowly yake tafiya har ya isa bangaren Abba, yayi sallama
sai da aka amsa masa sannan ya shiga, Abba na tsaye ya shirya alamar zai fita,
Khalil yayi ma Aunty Hassana kallo daya ya zauna kasa, a hankali yace "I am here
sir" Abba yana nuna masa Aunty Hassana yace "Who is she to me?" Khalil bai iya yace
komai ba, Calmly Abba yace "Tambayarka nake" Khalil ya kallesa yace "Ur sister"
Abba yace "Good, kasan da haka ka dawo gidan nan baka je ka gaida ita da Hajiya
Amina ba" Khalil yayi shiru, Aunty Hassana tace "Aa yaya, uwar ce ta sa shi hakan
ba kowa ba, ita ce xata hanasa ya shigo ya gaida mu saboda ba mu isa ba, sannan
still mun tashi mun je har can bangaren nata don ganinsa amma kememe yaron nan ya
ki fitowa ta wani fito tana karesa, ita Amina da abu kadan ke sa ta kuka muna
fitowa ta kama kuka wai ai wannan cin mutunci ne, ni kuma kasan halina bana daukar
nonsense shine yasa ma na zo na sameka yanzu, yaron da a haife na haifesa? Sau nawa
nake saka ka a gaba ina cewa kayi hakuri ka bar sa ya dawo gidan nan, shine zai
dawo ya saka min da haka?" Abba dai yayi shiru yana safa da marwa a babban parlon
nasa, Khalil ya jefa mata wani kallo ta gefen ido, Can Abba ya juyo yana kallonsa
da kyau yace "Bata hakuri, sannan duk ka bi su bangarensu ka gaishesu kace masu ka
dawo" Khalil ya kalleta a takaice yace "Yi hakuri" Daga haka ya mike ya fice daga
parlon, Da ido Abba ya bi sa, Anty Hassana ta saki baki ita ma ta bi sa da kallo,
Can ta kalli yayan nata xata yi magana yace "Tashi ki je Hassana, xan nemesa anjima
idan na dawo" Aunty Hassana ta dinga kallonsa da mamaki, sai ma taga ya nufi wajen
takalmansa ya zauna yana kokarin sa wa, tashi tayi daga karshe ta fice daga parlon
kamar xata tashi sama, Khalil na fita ya koma bangaren Maminsa, Mami na tsaye tana
kallon Nihad dake sa mayafin Mimi da ta amso mata, Mami ta fesa mata turaren
hannunta tana kallonta tace "Baki taho da dankunne ba?" Nihad ta girgiza mata kai
kawai, Gaba daya in ka kalleta sai ta baka tausayi, duk ta fita hayyacinta, Khalil
dake tsaye bakin kofa kallon Mami kawai yake ya ma rasa abinda xai ce mata, lokaci
daya jikinsa yayi sanyi don bai san what she is up to ba, Mami ta dauko ma Nihad
wani dankunnen gwal mara nauyi ta mika mata tace "Sa wannan" Nihad ta kai hannu a
hankali ta amsa tace "Nagode" sannan ta saka dankunnen, Mami ta dau nata mayafin ta
yafa a shoulder tana kallon Nihad tace "Mu je" Nihad ta nufi kofar ta bi gefen
Khalil ta fita, Mami na isa bakin kofar ya matsa a hankali ya bata hanya, makullin
motarta ta mika masa tace "Mu je" Yayi karfin halin cewa "Where Mami?" Mami tace
"Amshi makullin a hannuna ko?" A hankali ya kai hannu ya amsa, Mami ta fita Nihad
na biye da ita. Har suka fito compound din gidan babu wanda suka hadu da a hanya
kamar dai babu kowa gidan, Nihad ta dinga bin compound din da kallo, it's soo
beautiful and big, Khalil ya nufi Ride din Maminsa yana tafiya a hankali, gaba daya
ya rasa tunanin da xai yi, Mami ta dinga amsan gaisuwan da securities din cikin
gidan ke mata, Nihad dai sai binta take tana satan kallonsu, back seat Mami ta bude
tana kallon Nihad tace "Shiga" Nihad ta shiga motar a hankali, Mami ma ta shiga
sannan ta kulle motar, bayan few minutes Khalil ya ja motar ya fita compound din
bayan an bude masa wagegen gate din gidan, slowly khalil ke driving din har suka
fita anguwan, sai a sannan yana kallon Maminsa ta madubi cikin sanyin murya yace
"Where are we going Mami?" Mami tace "Take me to Maryam's house" Ya d'an sauke
boyayyen ajiyar zuciya sannan ya nufi gidan Aunt dinsa, Nihad sai kallon anguwanni
masu kyau take, amma kana mata kallo daya zaka san she is worried, suna shiga
estate din su Aunty Maryam basu dade suna tafiya ba suka isa gidan, Khalil yayi
horn bayan an bude gate din ya shiga yayi parking, Mami ta sauka tana kallon Nihad
tace "Sauko" Nihad ta sauko, ta bi bayan Mami zuwa gidan, Aunty Maryam ta rungume
Khalil tana welcoming dinsa cike da farin ciki tace "Idon son dina kenan nake gani
haka?? Alhamdulillah ya Allah, Alhamdulillah" Murmushi kawai yayi ya gaisheta, ta
amsa tana
kallonsa daga sama har kasa, Lokaci daya er fara'ar fuskarta ya bace tace "Welcome
son, Allah Ubangiji ya saka maka abinda aka maka" Murmushi kawai shi dai yake,
Aunty Maryam na rike da hannunsa ta nufi parlor tana gaida Mami da ladabi, murmushi
dauke fuskarta tace "Har kinyi Kumari yar uwa, Allah Ubangiji ya raba mu da mugun
ji da mugun ganin" Murmushi kawai Mami tayi, Nihad dai sai kallon Aunty Maryam take
don ita ma kana kallonta kasan halfcast ce, fara ce kal kamar Mamin khalil, sannan
ita ma ga gashinta da tayi packing har kusan gadon baya, Aunty Maryam ta kalli
Nihad don sai sannan ta lura da ita tace "Sannu da zuwa yan mata, shigo ki zauna"
Nihad ta sauke kanta ta zauna kasa a hankali ta gaisheta, Aunty Maryam ta amsa tana
Zaunawa gefen yayarta, tuni mai aikin Aunty Maryam ta cika gabansu da ruwa da lemo
da kayan maqulashe, Aunty Maryam ta kasa daina kallon Khalil tana murmushi, she is
so happy seeing him, can dai ta kalli Mami tace "Ya gida Aunty?" Mami tace
"Alhamdulillah, kira mai aikinki ta shiga da bakuwar nan ciki ta bata breakfast
naga bata wani yi a can gida ba" Aunty Maryam ta kalli Nihad tace "Ayya, to bari in
kirata ta zo" Aunty Maryam ta kira mai aikinta a waya sai gata ta taho tace "Gani
Hajiya" Aunty Maryam tace "Ki shiga da bakuwar nan guess room ki hada mata
breakfast yanzu" Yarinyar tace "Toh Hajiya" Aunty Maryam ta kalli Nihad tace "Tashi
ku je yan mata" Nihad ta mike a hankali ta bi bayan mai aikin da tayi wani bangaren
daban da ita. Mami na kallon Khalil tace "Ko da za ayi sati admission letter din
bai fito ba xata zauna nan har ta karba sannan ta koma gidansu" Khalil ya dinga
kallonta ya kasa cewa komai, Aunty Maryam tace "Who is she Aunty?" Mami tace "Tare
ya zo da ita" Aunty Maryam ta kallesa tace "Wacece ita din" yayi kasa da murya yace
"Yarinyar mai gidan da na zauna a kano" Aunty Maryam tace "Allah sarki, Admission
take nema nan din?" Ya gyada kai kawai, Aunty Maryam tace "Lallai ya yarda da kai
tunda har ya bar ka da yar sa har ku ka taho tare, Allah Ubangiji ya saka masa da
alkhairi" Khalil dai bai ce komai ba, Mami tace "Ameen" Mami ta kalli Aunty Maryam
tace "Yaushe tafiyar naku, naji shiru baki ce komai ba" Tace "Ohh wllh yace sai
yayi settling a can kafin mu bi sa, may be nan da sati biyu in sha Allah" Mami tace
"Toh Allah ya kai mu" Aunty Maryam tace "Ameen" Khalil yayi kasa da murya cike da
karfin yace "Mami about that video.... yan dakinsu ne a makaranta suka mata bata
sani ba, sannan suka saki a social media... the Case is silently in court now,
mahaifin nata yayi sueing dinsu gaba daya, so that's why zai canza mata makaranta
yanzu, since the incident yake processing admission dinta a nan garin so
coincidentally xan taho sai yace mu taho tare da ita" shiru yayi cause he him self
knows he sounds so stupid, there is nothing making sense in what he is saying, Mami
tace "Toh ni ka ji nace wani abu Khalil? Allah dai ya tsare mana zuri'a gaba daya,
kawai ta zauna nan har sanda xa ta amshi abinda ta zo amsa sai ta koma gida, ae
shikenan ko...." Aunty Maryam dake ta kallonsu tace "Wai me ke faruwa?" Mami ta
sauke ajiyar zuciya briefly tayi mata bayanin abinda ya faru daxu da safe da yara
suka shigo, Aunty Maryam ta saki baki da mamaki looking speechless, can ta kalli
Khalil tayi kasa da murya tace "Wai kana nufin wancan ita ce yarinyar da video
dinta yayi trending weeks ago?" Khalil bai iya yace komai ba, Aunty Maryam ta
girgiza kai hankali tashe tace "Amma ta bata wayonta, tayi tarnishing image dinta a
idon duniya, ta kuma yi ma kanta ta6on da goguwansa sae wani ikon Allah, duk yanda
aka yi bata ji, banda bata ji meye zaki zauna daga ke sai skimpy inner wears a daki
har maki video kina dariya, kai ai abun nan bai min dadi ba wallahi, Allah Ubangiji
ya tsare mana zuri'a, amma wannan ta6on ai baxai gogu ba har tsawon rayuwarta sai
ma ta tashi aure zata gane hakan barin idan tana da mahassada" Kallonta kawai
Khalil yake baya cewa komai, Aunty Maryam ta rike ha6a cike da jimami tace "Kaii,
sai kawai naji bata burgeni ba don bana son yaro mara kamun kai, don da tana da
kamun kai da babu yanda xa ayi tayi abinda tayi, babu yanda xa ayi hakan ya faru da
ita, wallahi ranan da naga videon ta sai da nayi tashin dare nayi addu'a Allah ya
kare mana xuri'a da al'ummar Musulmi baki daya, abun sam babu dadi, gashi babu inda
wannan videon bai je ba, kuma kun ga wllh ban ganeta ba ni banda kun yi magana, to
ma banda abun uban nata ai aurar da ita kawai ya kamata yayi a yanzu ba wai ya sake
biya mata makaranta a wani wajen ba, tana kanon ma a gabansu tana shakiyanci ina ga
ta hadu da yan matan garin nan ai kuma sai abinda hali yayi, gata wata sumu sumu
kamar bata magana... To kai garin yaya kasan mahaifin nata?" Khalil ya sauke idonsa
kasa, Mami dai sai kallonsa take, Aunty Maryam tace "Kayi shiru" Ya dago ya kalleta
a hankali yace "A sanda na sauka a kano bani da kowa bawan Allahn ya rike ni tamkar
dan sa, yayi accomodating dina, yayi feeding dina without knowing who i am,
mahaifiyarta mace ce mai kirki warce saboda ita nayi dadewar da nayi a tare da su,
ina jin ta kamar ke da Mamina a gidan, yayyinta maza kuwa zaman mutunci da girmama
juna muka yi da su, basu ta6a nuna min ni ba dan gidan bane, haka sauran yan
uwanta mata dake gidan, abinda nake so ku gane, ba wai na je masu da real identity
dina bane, i went der as a nobody, babu wanda yasan wanene ni har yanzu da nake
maku magana banda ita yarinyar yanzu, amma suka min karamci a irin wannan zamanin
da muke ciki, i know i can never repay them their good deeds, kuma yace in taho
tare da yarinyarsa ta amshi admission letter saboda wani mistake nata sai in ki?"
Aunty Maryam ta sauke ajiyar xuciya tace "Baxa ka ki ba kam, amma surutun yan gidan
nan naku ake gudu" Mami ta kalli Aunty Maryam tace "That is it dear, abinda na guda
kenan na kawota nan gidan har ta gama abinda ya kawota ta koma, banda mu da muka
san wannan labarin da ka fada a kan gidansu yarinyar waye ya sani? Nobody, kai ko
sun ji cewa xa su yi karya kake, don haka duk abun magana gudunsa nake nan da ka
gan ni, daxun ma da suka shigo ba saboda Allah bane, gulma ce ta kawosu, yarinyar
kawai suka zo gani, ita kuma wannan yarinya ta bata wayonta don waje daddaya ne
xata je aki ganeta, Allah dai ya kiyaye ya tsare mana zuri'a, ya bata mijin da xai
aureta yayi overlooking mistakes dinta ya rufa mata asiri duniya da lahira, da da
mijin ma da auren kawai yayi mata ta ci gaba da karatun nata a dakin mijinta don
hakan zai fi mutunci, Allah dai ya takaita mata gori a duk inda xata kasance"
Khalil dai kallonsu kawai yake, Aunty Maryam tace "Ameen, da ganin wannan lamari
kasan influence na bad friends ne hade da rawan kai irin na yaran yau, saboda haka
ne ya kamata mu kara sa ma yaranmu ido sosai" Wayar Mami ya fara ring ta daga ta
kai kunne, bayan sun gaisa tace "Lahh ai gani a gidan Maryam, kin fito ne?" Mami
tace "Yauwa to, kawai ki taho nan din idan kin fito, shima yana nan ai" Daga haka
ta katse wayar, Aunty Maryam na kallonta tace "Wacece?" Mami tace "Hajiya Safeenah
ce" Aunty Maryam tace "Allah sarki, taji sauki kenan" Mami tace "Aa da sauki sosai,
3 days ago ma ai taje can gida wajena" Aunty Maryam ta mike tace "Bari inje in
sanar ma mai aikin can tayi mata wani abun kafin ta iso" Daga haka ta bar parlon,
Mami na kallon Khalil tace "Wai fasa tafiyar kayi yau Khalil?" khalil na danna
wayarsa yace "Sai na shirya Mami" Aunty Maryam ta ɗan tsaya kitchen din tayi
assisting mai aikinta bayan da ta gama hada komai ta bar mata ta fito parlor, duk
bata tarar da su a parlon ba, har zata wuce sama sai kuma tayi bangaren guess ta
kara ganin Nihad, don kawai abun ya tsaya mata a rai tun daxu, bude kofar dakin
tayi ta shiga ta ganta zaune kasa ta jinginar da kanta da gado, Aunty Maryam na
kallon abincin dake ajiye tace "Baki yi breakfast din ba?" A hankali Nihad tace "Na
koshi" Aunty Maryam tace "Toh fito parlor kiyi kallo, yara sun jogane kayan kallon
nan din sai an gyara" Nihad dai bata ce komai ba ganin Aunty Maryam ta juya ta mike
a hankali ta bi bayanta, har suka fito parlor tare, nan din ma a kasa ta zauna,
Aunty Maryam ta tafi ta kulle kofa sannan ta wuce sama wajen Mami, Khalil na kwance
saman kujera Mami na basa labarin abubuwan da suka faru baya nan, Aunty Maryam ta
zauna kenan aka kira Mami, Mami ta daga tace "Kin iso ne?" Sai kuma Mami tace "To
bari a bude" Katse wayar tayi tace "Kin kulle kofar parlon ne Maryam?" Aunty Maryam
ta kalli Khalil da sauri tace "Dr ka bude mata kofa, yanzu kuma na kulle kafin in
hauro" Ya mike ya fita daga parlon ya sauka downstairs, Nihad na zaune ta k'ura ma
Tv ido duk da ba fahimtar abinda ake yi a ciki take ba, kallo daya yayi mata ya
nufi kofar parlon ya bude, Da ladabi ya gaisheta yayi mata sannu da zuwa, da fara'a
tace "Maa sha Allah, ka dawo lafiya Khalil?" Yace "Alhmdlh mum" Tace "Toh
Alhamdulillah, sannu, Allah Ubangiji yayi maka albarka" Yana murmushi yace "Ameen"
Sannan ya koma gefe ta shigo parlon, ya juya ya nufi inda remote yake ya dauka don
rage volume din Tvn, a hankali Nihad ta gaisheta ta amsa da fara'a, Khalil Yace
"Suna sama Mumy" Upstairs ta nufa, Kamar ance ya juya ya ganta ta jingina da kofar
parlon tana kallonsa tana murmushinta me kyau, wara ido yayi kafin yace komai ta
taho da sauri ta rungumesa ta lumshe ido a hankali tace "I have missed you so much"
Daga kai Nihad tayi ta kalleta, shi kam yayi stiff a wajen da yake duk ya daburce
cause she took him unaware, Lokaci daya ta lura da Nihad dake wajen da sauri ta
sakesa ta koma baya tana mata murmushi tace "Sannu, sorry i just badged in,
Assalamu alaikum" Nihad dake kallonta daga sama har kasa ta dauke kai kawai, Khalil
ya bude palm dinsa with surprise yace "But you didn't say u are coming with Mum" Ta
langwabar da kai smiling at him tace "Surprise" Kallonta kawai yake, a hankali
hawaye na taruwa idonta tace "I missed u so much..." Ya mata wani kallo yace "Come
off it dear" Lokaci daya
Nihad ta mike ta fice daga parlon zuwa guess room da take ciki daxu, Nadeeyah ta
bi ta da kallo, sai kuma ta kallesa tace "Dear Wacece ita? Ko dai taji haushin
yanda na shigo ko? Wallahi i was just overwhelmed" Khalil ya daga kafada yace "No,
kece dai kika ga haka...." Tace "Ohk, tayi hakuri in ma taji haushina ne, where is
Mami?" Ya nuna mata sama tace "Let me go and greet her" yace "Ohk dear" Tana barin
wajen ya bi ta da kallo har ta haura sama.....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

Assalamu alaikum manyan mata!!

For your Egyptian Abaya's, mad gowns, laces and handbags and all sort of
jewelries... Give me the privilege to be ur plug plss, and u will never regret it🥰

Join my WhatsApp group for beautiful samples.

Contact https://wa.me/c/2349090591769
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

40

Aunty Maryam ta kai hannunta saman shoulder din Nihad ta dafata a hankali tana
kallonta don har sannan tunane tunane take with shock written all over her, da
sauri Nihad ta daga kai ta kalleta, lkci daya hawaye ya cika idonta, ta hadiye abu
da kyar, cike da karfin hali tana girgiza kai tace "Ni ba wanda ya taba gaya min
abubuwan nan, ni ban sani ba, you are just telling me now" Aunty Maryam tace "And
hope you've realized what i am saying?" Nihad ta gyada kai hawaye na sauka idonta,
sai kuma ta fashe da kuka tana kallon Aunty Maryam tace "Ni ban san bata so na ba
Aunty, Lokacin wani saurayina yace iyayensa xa su xo gidanmu shine na gaya mata sai
tace min kar in gaya ma kowa har Mumyna, ita da kanta xata je ta gaya ma Abba, na
gaya mata da few days aka saki Video dina a internet shine yayi blocking dina" Buda
baki Aunty Maryam tayi tana kallonta and she was speechless, Nihad na kuka sosai
don sai sannan abubuwan ke dawo mata, sai yanzu ƙwaƙwalwarta ya fahimci abubuwa da
dama, Tana kuka sosai tace "Da Abbana ma ya koreni bata ce komai ba" Aunty Maryam
ta dafata da sauri tana kallonta da mamaki tace "Ya koreki daga ina?" Cikin raunin
murya Nihad tace "Gidanmu, yace baya son ya sake ganina har abada, she was standing
at the door bata ce masa komai ba, and she saw me leaving the house" Sai ta kara
fashe da kuka sosai, she is so pained, bata ta6a kallon Umma from this perspective
ba, ga dai komai vividly a bayyane amma bata ta6a ganewa ba, Aunty Maryam tayi
karfin halin cewa "Kina nufin he sent you away from his house?" Nihad ta gyada mata
kai tana kuka, Aunty Maryam ta kasa rufe baki, can ta kalleta da kyau tace "Dalilin
kawo ki garin nan da Khalil yayi kenan dama?" Sai a sannan Nihad tayi realizing she
just said what she's not suppose to say to her, ta dakatar da kukan da take da
sauri ta hadiye abu da ya tokareta a throat, ta kalli Aunty Maryam, sai kuma ta
fara kame kame "Aa Aunty kawai dama.... Dama, makaranta...." Aunty Maryam da tuni
ta ganota tace "Kar ki min karya" Nihad ta hade kai da gwiwa tana kuka a hankali,
Jikin Aunty Maryam yayi sanyi sosai, wato dalilin kawota Abuja da Khalil yayi
kenan? But ai Mami tace mata Abba ne ya bukaci ya dawo kuma, she became so confuse
at this point, Can ta kalli Nihad tace "Ya isa haka, ki daina wannan kukan, ki tafi
bandaki ki wanke idonki ki kwanta kafin Asuba ya karasa" Nihad ta kasa ce mata
komai, Aunty Maryam tace "Tashi" Tashi tayi da kyar tana jan kafa ta shiga bandakin
ta wanke fuskarta ta fito, Aunty Maryam tace "Ki kwanta, kuma bana son ki sake
wannan kukan kin ji me nace?" Nihad ta gyada mata kai ta kwanta saman gadon, Aunty
Maryam ta mike ta fita daga dakin ta kullo mata kofar. Kwanciyar da Aunty Maryam
bata sake yi ba kenan har gari ya waye, lamarin Nihad ya tsaya mata cak a zuciya,
taji tausayinta da mahaifiyarta ainun, ta kuma ji mata takaicin wannan baƙin taɓon
da aka mata da xai bibiyeta har karshen rayuwarta, this is soo painful, ta kuma
tsine ma Umma ta la'anceta yafi a kirga, ta jima bata ji labarin irin wannan
zaluncin da aka ma Nihad ba, ta kara tabbatar da cewa kishiya bala'i ce kuma masifa
ce. ƙarfe takwas saura ta kira Khalil, yana bedroom dinsa kwance yayi nisa a
tunanin da yake, he is so confused and looking for a way out a kan wannan lamarin,
gaba daya kansa ya daure on what next to do, ko jiya da daddare sai da Mami ta sake
masa magana yayi kokarin ganin Nihad ta amshi admission letter din nata ko gobe ne
kar a shiga weekend, idan yaso idan ta amsa ko ranan sai ta bi jirgi ta koma gida,
ita dai duk ta damu ace Nihad ta tafi gida, ga Abba a jiyan shi ma yayi masa
maganan business din da zai yi a zanzibar, which he will be leaving Nigeria in 2
days time, that is on Sunday, kiran Aunty Maryam ya kara rikita masa lissafi ya
mike zaune da sauri yana kallon wayar, Allah ya sa ba wani maganan Nihad tayi mata
ba dai, sai da wayar ya kusa katsewa ya daga ya kai kunne, yayi composing kansa
yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Lafiya lau, idan baka komai ka taho yanzu ina
jiranka" Nan yaji gabansa ya fadi sosai, Ya dake yace "Hope all is well Aunty?"
Tace "Nace dai ina jiranka" Yayi gathering courage yace "Toh" Daga haka ta katse
wayar, duk da sanyin Ac dake dakin ji yayi zufa na keto masa ta ko ina, he just
can't Imagine ace Nihad tace mata ai an daura mata aure da shi, yayi saurin kawar
da tunanin don bai ma son yayi, ya sauka daga saman gadon da kyar ya shiga bandaki
yayi wanka ya fito, cikin few minutes ya gama shiryawa ya dau perfumes dinsa ya
fesa sannan ya dau makullin motar Mami dake wajensa ya fita, ko part dinta bai tafi
ba ya fita zuwa compound, har Khalil ya isa gidan Small mum dinsa ba shi da nutsuwa
babu tunanin da bai zo ransa ba, tunda ya san ba wani saiti gare Nihad ba nan da
nan zaka bugi cikinta ta bude maka komai, yana parking compound din Aunty Maryam ya
kashe motar ya sauka sannan ya nufi parlonta, xuciyarsa na bugawa ya kwankwasa
kofar parlon, mai aikin ta bude, ta gaishesa ko amsawa bai yi ba ya karasa ciki ya
zauna ya jinginar da kansa da kujera, sai ga kiran Aunty Maryam a wayarsa ya daga
ya kai kunne tace masa ya hauro sama, ya mike yana kallon mai aikin yace "Ke ina
bakuwar da take gidan nan?" Da ladabi mai aikin tace "Tana guess room" Direct can
ya nufa da sauri maimakon sama da Aunty Maryam tace ya hau, ya bude kofar dakin ya
shiga, tana zaune gefen gado daure da zanin da Aunty Maryam ta bata bayan ta fito
wanka tana shafa mai, har sannan idanuwanta a kumbure suke don har gari ya waye
bata rintsa ba, Umma tayi mugun tsaya mata a rai, bata ta6a viewing dinta from the
this perspective ba sai yanxu with the help of Aunty Maryam, she wish ana iya maida
hannun agogo baya, wani tsanar Umma kawai taji take ji a ranta idan ta tuna wasu
abubuwan da ta sa ta dinga yi a boye, tunda Nihad ta juya da sauri bayan an bude
kofa suka hada ido da Khalil ta dauke kai ta ci gaba da shafa man da take a
hankali, ya nufota kirjinsa na heaving yace "Kee, me kika gaya ma Aunty Maryam?" Ta
ɗan kallesa, sai kuma ta ci gaba da abinda take taki kulasa, jin bata ce komai ba
ya hade rai yace "Magana nake maki" Tace "Toh ba ga ka a gidan ba kaje ka tambayeta
mana" Sake baki yayi yana kallonta, ganin yanda ya tsaya mata a kai ta mike ta dau
cream dinta xata bar wajen ya fixgota ta dawo dab da shi yana mata wani kallo, ta
zaro ido tace "Ni wallahi ka kyaleni, ai ba ni kadai xaka tambaya ba ita ma sai ka
je ka tambayeta" Khalil ya dinga kallonta sai kuma ya zaunar da ita gefen gadon
strictly yace "Ina me tabbatar maki cewa in har kika gaya mata anything pertaining
to relationship dina da ke, ko kuma dalilin da ya sa muka zo garin nan tare dake, i
have no choice then to divorce you right in front of her, a nan take a gabanta xan
sakeki" Nihad ta wani kyabe baki tace "Toh kayi ta saki na mana, dama ni ai ban san
ina da wani aure a kaina ba, sannan Alhamdulillah tunda duk iskanci na ba a ta6a
ganin ina rungume rungume ba, kawai dama in ka gama sakin nawa ka kai ni tasha ka
saka ni a mota in tafi gun dangin mamata tunda ina da su kuma suna so na" Kallonta
ya dinga yi babu ko kiftawa, kawai ji tayi magana da Aunty Maryam ya sa mata
courage da tayi loosing few days ago, taji ta kara samun kwarin gwiwa sosai,
because at least tayi magana da warce ta fahimceta ta yarda da ita, sannan warce ta
ganar da ita abubuwan da duk bata sani ba bata kuma ta6a kawowa a kai ba a baya,
Tashi tayi ta koma can daya bangaren gadon ta zauna tana shafa cream din a kafa,
Wayarsa dake hannunsa ya fara ring ya kalli screen din sai kuma ya nufi kofa ya
fita daga dakin, direct sama ya haura yaga Aunty Maryam zaune parlornta, ta dinga
kallonsa ya kasa barin su hada ido har ya karaso ya zauna, yace "Ina kwana Aunty?"
Aunty Maryam na kallonsa a hankali tace "Lafiya lau" Sai a sannan yayi karfin halin
daga kai ya kalleta, ta sauke wani boyayyen ajiyar xuciya tace "Ka gaya min gaskiya
Khalil, dama saboda ka kawo Nihad garin nan ne ka dawo gida ko da gaske kiranka
Abbanka yayi?" Khalil yayi karfin halin cewa "Aunty ai da Abba bai min izinin shiga
gidansa ba kema kinsan babu ta yanda xan shiga, kawai coincidentally ne...." Sai
kuma yayi shiru ya sauke kansa kasa don bai ma san me xai ce mata ba tunda bai san
abubuwan da Nihad ta gaya mata ba, he don't want to say something different, bayan
few minutes yaji Aunty Maryam tace "Me ka fahimta game da kishiyar Mamarta tunda
kace ka zauna a gidansu" Da sauri Khalil ya daga kai ya kalleta, sai kuma yayi kasa
da murya yace "A wolf in sheep's clothing, a green snake under the green grass...."
Aunty Maryam ta girgiza kai cike da takaici tace "I was shock at Nihad's story
Khalil, nayi matuƙar girgiza da labarinta, kishiyar Mamarta bata mata adalci ba, ta
cuceta ta gurbata mata rayuwa" Khalil ya lumshe ido ya bude bai dai ce komai ba,
Aunty Maryam tace "Me yasa kace admission letter xata amsa a garin nan bayan ba
haka bane?" Sai da khalil yayi stiff a inda yake zaune, Aunty Maryam tace "She told
me her dad sent her away from his house" Sosai gaban khalil ya fadi jin abinda
Aunty Maryam ta kara cewa, shikenan ya ma san ta riga tace an masa aure da ita
tunda har ta iya buda baki tace an koreta a gida, jin tayi shiru Khalil yayi karfin
halin cewa "Sai me kuma ta gaya maki Aunty?" Aunty Maryam tace "Iya abinda ta sanar
min kenan, sai kuma wanda kai zaka kara min, sannan tace video dinta bata san garin
yaya aka mata ba har ya fita.... Na kuma yarda da ita don babu alamar karya a duk
zantuttukan ta" Khalil dai kallonta kawai yake, can ya sauke wani boyayyen ajiyar
zuciya da ya fahimci iya abinda ta sanar ma Aunty Maryam kenan da gaske, yayi kasa
da murya yace "Haka ne Aunty, but bansan ta ina xan fara gaya ma Mami all this ba,
ni kuma mahaifinta yayi min halaccin da baxan iya kyaleta ta shiga duniya ba bayan
ya koreta gidansa saboda offense din da ba yin kanta ba, her stepmom is behind all
that happened to her amma bata sani ba ta kuma ki kwantar da hankalinta ta gano
hakan,
makira ce matar kuma azzaluma, ta lalata mata rayuwa ta dora ta a kan abubuwa da
yawa da basu dace ba, wanda ita nata yaran bata basu wannan tarbiyar ba, duk
nutsattsu ne babu na banza a yaranta, farkon faruwan incident din ai mahaifin nata
bai koreta daga gidan ba amma matar nan ta san yanda tayi har ya koreta after
almost one month da faruwar incident din, and i am telling you ba directly take
abubuwanta ba, ni nasan mahaifinta baya cikin hayyacinsa ya koreta daga gidansa,
coincidentally kuma nima na masu sallama xan bar gidan kenan in taho Abuja bayan
Abba ya kirani, kawai naga baxan iya barin ta tafi wani wajen ba, And you know what
Aunty.... bamu ta6a shiri da yarinyar ba duk tsawon xamana a gidan, amma sbda
kirkin mahaifiyarta na tausaya mata muka taho nan Abuja tare" Aunty Maryam ta sauke
wani ajiyar xuciya tace "Dangin mahaifiyarta fa?" Ya girgiza kai yace "Babu su a
nan" Aunty Maryam tayi shiru cike da tausayin Nihad, can tace "Kai yanzu menene
next plan dinka Khalil?" Ya girgiza kai yace "I don't know Aunt, i am confuse, ban
san ta yanda xan yi convincing Mami har ta zauna nan zuwa sanda mahaifinta xai huce
ba, gashi jiya da daddare ma sai da tace min ta amshi abinda xata amsa yau ta tafi
sbda gobe weekend" Aunty Maryam tace "Kar ma kace mata komai don ba lallai ta
fahimta ba, kawai dai ko da zata sake maganar admission letter din kace still fa ba
a samu ba.... Nihad have to stay here kafin a samu wani solution din gaskiya, she
is too young for this trauma at her age, kishiyar uwarta bata mata adalci ba, gashi
ni kilan nan da sati biyu xamu yi tafiya" Khalil yayi shiru sai kuma a hankali yace
"Aunty to me yasa baxan samar mata admission din ba kawai, sai ta zauna Abujan a
zuwan dai karatu take" Aunty Maryam tace "Eh wannan ma shawara ce mai kyau kuwa,
amma wani makarantar xaka samar mata?" A hankali yace "Nile or Baze University...."
Buda baki Aunty Maryam tayi tana kallonsa da mamaki tace "Did you know the tuition
fees of those Universities kuwa?" Ya ɗan yi dariya yace "Ohhh nawa ne ma?? shi su
Mimi ke zuwa i think?" Tace "In ba dai ko Abbanku ya hada har ita ya dinga biya ba,
tunda kowa ma biya ma kudin makaranta yake ai naga" Khalil yayi murmushi yace "I
will process the admission for her as soon as possible in sha Allah" Aunty Maryam
tace "Toh Allah ya rufa asiri, kaga dai dai kenan ma tunda sabon session xa su
shiga" Bai ce komai ba, Aunty Maryam tayi shiru tana ta nazarin abubuwa iri iri,
can ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Yanzu duk wani hanya da xa a bi a gano ta
inda wannan video din nata ya fita babu shi kenan? Ai bai kamata ayi shiru babu
bincike ba, kamata yayi anyi ta bincike har Allah ya sa a gano wanda yayi wannan
ta'asar, duk da babu tantama ni nasan da sa hannun matar ubanta, sannan ina zargin
kawayenta ma, don ta gaya min ko su waye" Khalil dai bai ce komai ba, Aunty Maryam
tace "Amma tunda har ta iya tashi cikin dare ta kai ma Allah kukanta ni nasan komin
daren dadewa wataran gaskiya zai bayyana, ta yanda komai ya faru duk Allah xai nuna
ya tona asirin koma wanene, Allah Ubangiji ya kare mana zuri'a ya sa mu fi karfin
zuciyarmu" Sai wajen karfe goma Khalil ya sauko downstairs daga parlon Aunty
Maryam, Babu kowa parlon kasa ya nufi guess room da Nihad take, ya bude kofar dakin
a hankali ya shiga ya ganta kwance tana bacci, for almost 4 days sai yau take bacci
peacefully kuma me nauyi, ya karasa cikin dakin yana kallonta, juyawa yayi daga
karshe ya fita ya kulle dakin. Ba laifi throughout ranan Nihad ta saki jikinta a
gidan Aunty Maryam she really felt at home, Aunty Maryam bata barta ta zauna ita
kadai ba, har fita suka yi tare da yamma ta rakata xata yi siyayya a shopping mall
sae dai ta bata nikaf ta saka saboda yan kwakkwafi masu gane mutum farat daya,
Aunty Maryam ta bata baki sosai a kan kar ta wani damu kanta in Allah ya yarda
asirin wa enda suka mata haka zai tonu, kuma xata ga yanda Allah xai yi da stepmom
dinta, hakan yasa damuwan Nihad ya ragu sosai ta samu relieve, bayan sun dawo daga
shopping Mall din Aunty Maryam ta ware mata nata abubuwan da ta siyo mata ta bata,
Nihad ta amsa a hankali tace "Nagode Aunty, Allah ya saka da alkhairi" Daki ta kai
ta dawo ta zauna parlon, Aunty Maryam na ba Mus'ab dinta abinci Nihad tayi kasa da
murya tace "Aunty don Allah xaki iya ara min wayarki in kira Mumyna?" Aunty Maryam
ta dau wayar ta mika mata, Nihad tayi dialing number Mumy sannan ta kirata, lkci
daya jikinta yayi sanyi jin wayar a kashe, ta mayar ma Aunty Maryam tace "Wayar a
kashe yake" Aunty Maryam tace "Anjima sai ki sake trying" Nihad tace "Toh" Wayar
Aunty Maryam ya fara ring ta dauko ganin Mami ce ke kiranta ta daga, bayan sun
gaisa Mami tace "Ya ake ciki ta amsa kuwa Maryam?" Aunty Maryam tace "Kinsan sabon
session ne Mami, so ina jin sai zuwa next week xa su fara badawa gaskiya, har yanxu
bata samu ba kam" Mami tace "Wai wani makaranta ne?" Aunty Maryam tace "Toh ban dai
sani ba gaskiya" Mami tace "Toh Allah ya kyauta, amma na so ace ko yau ko gobe ta
koma gida" Aunty Maryam tace "Toh tunda Allah bai nufa ba sai mu saurari yanda ya
tsara" Mami tace "Yana nan gidan naki ne Khalil din?" Aunty Maryam tace "Aa" Mami
tace "Ohk tun safe ya fita naga kuma bai dawo gida ba" Aunty Maryam tace "Kilan
yana can gidansu budurwarsa" Mami tace "To a gaida Mus'ab" Aunty Maryam tace "Xai
ji" Daga haka suka yi sallama ta katse wayar, Aunty Maryam ta dinga tunanin ta
yanda xa su bullo ma yayartata. Aunty Hassana ce xaune bangaren Hajiya Amina tana
kallonta rai a dagule tace "Yanzu dai kin kara tabbatar da cewar bayan malaman da
fatima ke bi na kasar nan har kasansu ma malamai yi mata aiki suke ko?" Da sauri
Hajiya Amina tace "Aa na yarda wallahi...." Aunty Hassana tace "Wai ni yau yaya zai
buda baki yace in bar masa parlonsa sbda na kawo masa shawarar kar ya tura Khalil
Zanzibar, yaushe har ya dawo gidan balle a san ko ya sauya hali ko bai sauya ba,
har zai kara yarda da shi ya daura sa kan miliyoyin kudinsa, kar ki dada kar ki
raga shine yaya ya hayyako min har yana cewa in bar masa parlonsa cikin tsawa"
Hajiya Amina tace "Toh wai yanzu me malamin yace maki da ku ka yi waya" Aunty
Hassana tace "Ta lalata mana aiki, kuma da tsafi aka lalata aikin" Hajiya Amina ta
rike ha6a tace "Aikin kusan miliyan daya fa?" Aunty Hassana ta sauke ajiyar xuciyar
takaici tace "Wato an bata sa'ar dai dai sanda xata gaya masa ya shigo gidan babu
wanda xai hanasa, shine ya shigo kansa tsaye asiri kuma yayi tasiri aka xuba masa
ido babu wanda ya dakatar da shi, uban ma ya kasa cewa komai har yanzu shine ya
billo da turasa Zanzibar yayi masa business" Hajiya Amina tace "Toh ni ance ba shi
kadai ya dawo ba, kuma har yanzu ban ga yarinyar da aka ce ya dawo tare da ba,
kinga ai ko yau naje bangaren, kuma har dakin Hajiya Fatiman na shiga kai tsaye ko
yarinyar na ciki amma ban ganta ba" Aunty Hassana tace "Farhana tace fa bata gidan,
tun da suka gane ita ce me wannan video din na kwanaki ya fitar da ita wai daga
gidan, kinga tabbacin tsiyarsa kawai yaje ya tsula a duniya ya dawo, babu tantama
kuma karuwarsa ce" Hajiya Amina tace "Wai daxu baki ga uwar yarinyar da ake son
makala masa ta zo ba kuwa??" Aunty Hassana tayi wani dariya tace "Ai ko zata mutu
baxai auri er ta ba sai dai in har ba Hassana sunana ba, Nadiya take ko wa? Toh
wallahi baxai aureta ba, ba dai dukiyar yayana ake hari ba? to sai dai su gani su
hanga daga nisa, ita fatima ta zaci ta fi kowa wayo shine take kokarin xata makala
masa yar aminiyarta tunda kasarsu daya su hadu su wawushi dukiya ta ko ina su ci
karensu ba babbaka, su yi wandaka son ransu su gayyato jajayen danginsu da abokai
ayi biki a ci uban kudi, to kuwa xan ga ta yaya, don da dai in bari ya auri
yarinyar nan gwara ya dauwama babu auren har ya mutu, yanzu in zai yi auren ai
dukiya ne ba ta wasa ba yaya xai kashe, don har lefe shi xai yi masa, toh kiyi
imagine nawa xai basu su yi lefen, ai miliyan 10 ma albarka" Hajiya Amina tace "To
ke yanzu baxa ki yi ma Malam magana ayi duk yanda xa ayi ya auri ko Farhana ko
Sajida ba? Ai gwara yan gida su mora da yan waje" Aunty Hassana tayi wani dariya
kawai ta kyabe baki bata ce komai ba, Hajiya Amina tace "Allah kuwa da dai ya auri
yarinyar nan gwara anyi haka kawai mu san har yanzu mu ne" Aunty Hassana na girgiza
kafa tana wani Murmushi tace "Ke kin zata a banza ne har yanzu ba ayi auren nasa da
Nadeeyah ba, sai yayi ta ce masu ba yanzu ba har ya bar gidan nan?" Hajiya Amina
tace "Toh yanzu gashi ya dawo ga kuma uwar yarinya har ta fara mana sintirin gida"
Aunty Hassana tace "Xata yi ta gama, baxai auri er ta ba, balle wata kuma can"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

41

Umma ta shigo dakin da taga Nihal ta shiga for almost ten minutes bata fito ba,
wato dakin Nihad, dube dube ta sameta take yi a dakin, tun da Nihal taga shigowar
Umma ta dakatar da abinda take ta zauna gefen gado, da mamaki Umma tace "Me kike
nemar mata a daki tun daxu?" Nihal dai bata ce komai ba, Umma ta kyabe baki tace
"Ke idan fa kika ce xaki tafi makaranta a haka ba tare da kin saki ranki kin dawo
yanda kike harkokinki da ba to ina me tabbatar maki zaki samu matsala a makaranta
wannan time din, abinda baki ta6a ba, eh ansan er uwarki ce kuma ba dadi to amma so
kike ki targada naki future din ne? Ko damuwar nan ne xai dawo maki da Nihad, to ma
ta dawo ta maki me? yarinyar da ke can kauyen mijinta" Ita dai Nihal bata ce komai
ba still kuma bata kalli Umma ba, Umma ta kara kyabe baki ta karaso ta zauna gefen
gado tace "Ba kwanaki can kina da number shi dreban ba, ni da ma kin kirasa in ji
ko kauyen nasu na nan garin suka tafi ko Zarian ya tafi kauyen uwarsa da yace"
Nihal dai bata ce komai ba, Umma tace "Ba da ke nake ba kika min shiru Nihal?"
Nihal ta daga kai ta kalleta, sai kuma tace "Bani da number sa" Umma tace "Toh amma
ai farooq bazai rasa ba tunda shi ma Allah ya zuba masa shisshigi kira min shi ki
tambayesa yanzu ina jira" Nihal ta dau wayarta tayi dialing number Ya Farooq ta sa
handsfree, yana fara ringing ya daga bayan ta gaishesa tace "Yaya wai kana da
number Khalil?" Farooq yace "Wa ke tambayar numbersa?" Duk da alamar da Umma ta
dinga yi mata kan cewar kar tace ita ce ke tambaya amma Nihal bata kalleta ba tace
"Umma ce" Farooq yace "Noo bani da shi, sai anjima" Tace "Toh sai anjima" Katse
wayarsa yayi, Umma ta hade rai tace "Akan meyasa xaki ce masa ni ce ke nema?" Nihal
tace "Nima na tambayesa Shekaranjiya yace bashi da, don ki tabbatar da hakan yasa
na sake kiransa amma ni nasan bashi da number" Umma tace "Toh ai shikenan, dama wai
da sai mu ji kauyen da suke, in ya kama mu je sai mu je kafin ki koma makaranta"
Daga haka ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin, Nihal ta mike ta ci gaba da duba
takardun da take. Ranan asabar da rana khalil na zaune parlon Mami sai ga kiran ya
Farooq gaba daya ya mance sun yi waya few days ago yace masa xai shigo zaria, Ya
ɗan kalli Mami dake parlon, bai daga wayar ba har ya katse, Ya farooq ya sake kira,
mikewa yayi ya nufi kofa yace "Mami sai later" Daga haka ya fita daga part din gaba
daya sannan ya kira Ya farooq, ya farooq na dagawa bayan sun gaisa ya sanar masa
zai taho zaria from kaduna, Khalil yace "Ohk amma kaga muna gidan wata kanwar
Baabata mun je gaisheta" Farooq yace "A ina kenan?" Khalil yace "A Abuja take"
Farooq yace "Ohk, babu damuwa Usman na Abuja, so xai je inda ku ke in sha Allah"
Khalil bai iya yace masa komai ba da farko, can kuma yayi saurin cewa "Toh Allah ya
kai mu" Farooq yace "Zan tura maka numbersa yanzu ko da xai kiraka" Khalil yace "Ba
damuwa" Daga haka suka yi sallama, kamar ance ya daga kansa ya ga Farhana a tsaye
tana sauraron wayar da yake, ya hade rai yace "Ke ya kika tsaya min a kai?" Bata ce
masa komai ba tana rungume da laptop dinta ta wuce tana ta6e baki, ya bi ta da wani
mugun harara. Khalil na shirin xai fita da yamma sai ga kiran number da Farooq ya
turo masa daxu, wato number Usman, yayi jim yana kallon wayar, can ya daga ya kai
kunne, gaisawa suka yi, Usman yace "Yauwa wani anguwan ne a Abuja?" Khalil ya ɗan
buda ido sai kuma yayi saurin cewa "Bari in tambaye Kanwar Baabar tawa" Usman yace
"Ohk ina jira" Katse wayar yayi yana tunanin abinda xai yi next, bayan ya gama
shiryawa ya fito zuwa bangaren Mami sannan ya kira Usman, yana dagawa yace "Tace
Suleja ne" Usman yace "Ohk, akwai tazara sosai tsakaninmu, amma idan na shirya zuwa
zan kiraka" Khalil ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Toh Allah ya kai mu" Usman
yace "Ba Nihad din wayar mu gaisa" Khalil yace "Idan na shiga gida xan kiraka yanzu
ina waje" Usman yace "Alright" Daga haka ya katse wayar, Mami da ta fito parlon
tana kallonsa tace "Waye a Suleja?" Yace "Wasu ne" Tace "Ohk" Sannan ta zauna saman
kujera a hankali tace "Ina son za mu yi wata magana da ke damuna Khalil" Ya kalleta
yace "Toh ina ji Mami" Tayi kasa da murya tace "It's High time kayi settling down
son, tun baka bar gidan nan ba almost 2 years ago Abbanka ke maka magana har Allah
ya kaddara tafiyarka, babban burina a rayuwa a yanzu shine in ga kayi aure...."
Khalil ya sauke ajiyar xuciya yace "Mami kinsan fa she aure lokaci ne, idan time
din yayi sai kika nayi Mami...." Tace "I am not talking about you settling down wai
saboda ina son ka auri Nadeeyah, No son, idan da wata warce kake so daban fine,
present her to us xa mu yi accepting as far as tana da tarbiyya, i can never force
u on marriage son, kar kaga ko Nadeeyah yar aminiyata ce shi sa nake so ka aureta,
a'a idan dai kasan da wata warce kake so da aure go ahead ka nemi aurenta just make
sure yar gidan mutunci ce me tarbiyya ce like i said, sannan she should be from a
reputable family, ka dai san halin Abbanka ai" Khalil yayi murmushi yace "Toh Mami
ai ba ke kika hada mu da Nadeeyah ba, i met her abroad without knowing she is ur
friends daughter, ba ta dalilin ke da Mumy muka san juna da ita ba, kawai Allah ne
ya hadamu..." Mami tace "Haka ne, amma kaga ai yan sa ido gani suke mu muke cusa
maka ita ka aura, don ta Hajiya Safeenah ma ta fi son Nadeeyah tayi aure a can
Yemen tunda danginta suna can, kuma dama ita a can din ta tashi" Khalil yace "In
sha Allah, as soon as i come back from this business trip xan kai ma Abba batun
Mami.... Nima ina son settling down" Mami tace "Toh Allah ya nuna mana, amma kwana
nawa xaka yi a can?" Yace "It depends, but nasan baxan wuce wata daya ba, but duk
sati xan dinga shigowa Nigeria" Da mamaki Mami tace "Duk sati kuma? Me xaka dawo yi
kai da ya kamata ka zauna can har ka gama abinda ya kai ka" Khalil yace "Bana son
xama can har na wata daya, duk weekend xan dinga dawowa" Mami tace "Toh shkkn, amma
ka sanar ma Abban naka?" Ya girgiza kai yace "He said i should do what suite me"
Mami tace "Toh Allah ya tsare ya baka nasara" Yace "And one more thing Mami, ki
amsar min Cv's dina and my assets that he clutch" Mami tayi kasa da murya tace "No,
kai ya kamata kayi masa maganan wannan idan ka dawo, kuma ina ga ko ka dawo din ma
kar ka masa magana kawai ka zuba masa ido ka gani" Khalil yace "Aa i am asking him
Mami" Shiru tayi bata ce komai ba, ganin ya mike tace "Toh shikenan son, Allah ya
daura ka a kansa, Allah kuma ya kai ka lafiya ya dawo min da kai lafiya" Yace
"Ameen" Daga haka yayi mata sallama ya fita daga parlon. Khalil na fita gidan Aunty
Maryam ya nufa, can sama ya tafi ganin babu kowa a parlon kasa, ta fito daga
bedroom dinta ta shigo parlor ta zauna ya gaisheta ta amsa tace "Ya su Mami?" Yace
"Lafiya lau" Tace "Toh maa sha Allah, ya ake ciki?" Yace "Gobe ne zanyi tafiyar
Aunty" Aunty Maryam tace "Toh Allah ya kai mu, sai ka dawo yaushe?" Yace "Nan da
wata daya xan gama komai" Tace "Waii, ai ba lallai xaka dawo ka tarar da ni kilan a
kasar nan ba, yanzu ya ake ciki maganar admission din?" Yace "In sha Allah an fara
processing tun jiya" Sai kuma a hankali yace "But Aunty ya za mu yi da Mami yanzu?
Kinsan halinta fa, and i don't want her to be angry with me as a result of this
issue" Aunty Maryam tace "I will think about that khalil, in sha Allah xan san
yanda xa ayi, har yanzu nima tunanin ta inda xa a billo nake wallahi, da ina nan
babu abinda xai hanani riketa a gidan nan" Bai kuma cewa komai ba, amma tunani
yake, how will Mami be convinced, shi kuma he will neva let her stay in the
hostel.... Bai wani jima ba yayi ma Aunty Maryam sallama kan zai je gidansu
Nadeeyah, yana sauka parlor ya ga Nihad a parlon da mai aikin Aunty Maryam dake ta
bata labari, ita dai tayi tagumi tana kallonta don ta gaji da surutunta gashi ko
gane labarin bata yi, tun suna girki a kitchen take bata wannan boring labarin,
wannan yasa ta tuna nasu mai aikin a can gida, warce ko magana bata son ya hadasu
da ita ba kuma ta zama inda take saboda tana ganin ta fi karfin hakan kamar yanda
Umma ta ke yawan sanar mata, and for the first time Nihad felt bad at the way she
treated Hafsah back then, yau dai ga ta ita ma a gidan mutane ba gidansu ba tana
cin arziki.... Khalil ya sauko downstairs yana danna wayarsa, yayi dialing number
Usman, yana fara ring Usman ya daga, ya nufeta ya mika mata wayar, tuni Murja ta
gaishesa ta bar parlon da sauri, Nihad ta amshi wayar ba tare da ta kallesa ba tana
kallon screen din amma bata gane number waye ba, ta kai kunne, jin muryarsa a
hankali tace "Ya Usman" Yace "Ya kike Nihad?" Tace "Lafiya lau, ina yini" yace
"Alhamdulillah, hope you are doing fine, babu matsala dai ko?" Ta sunkuyar da kai
cikin sanyin murya tace "Eh" yace "Ohk are you still using ur account?" Tace "Bani
da atm card ne" yace "Toh ya kaiki banki ki amsa wani" Tace "Toh" Yace "Xan maki
transfer a ciki yanzu" a sanyaye tace "To yaya Nagode" Katse wayar yayi, hawaye ya
cika idonta ta rufe fuskarta jikin kujera hawayen na zubo mata, bata son taji tana
jin haushinsu a rai sbda Umma because she love all of them, basu ta6a nuna mata
ubansu ne kawai daya ba, shi dai Khalil na tsaye don bata basa wayarsa ba, bayan
few minutes ta dago tana goge idonta ta mika masa wayar ba tare da ta kallesa ba,
kallonta yake, zata ajiye masa kan kujera ganin yaki amsa yace "Kee" Sai a sannan
ta kallesa babu yabo babu fallasa, yace "Da xan baki wayar saman kujera na ajiye
maki?" Ita dai bata ce masa komai ba, ya amshi wayar ta mike ta bar wajen, ya bi ta
da kallo har ta bace sannan ya fita daga parlon, washegari kuma ya bar Nigeria for
Zanzibar in the morning. Ranan Talata Mami ta kira Aunty Maryam, bayan sun gaisa
Mami tace "Maryam bakuwar nan ta tafi kuwa?" Aunty Maryam tace "Ehh ta tafi jiya"
Mami tace "Toh maa sha Allah, banda dai yace a gidansu ya zauna ai yarinyar nan bai
kamata a gansu tare ba balle har ya kawota nan gidan" Aunty Maryam dake sauraronta
tace
"Saboda me Mami?" Mami tace "Kika ce saboda me?" Aunty Maryam tace "Au... Toh
Allah dai ya kyauta, Allah ya tsare mana zuri'a" Mami tace "Ameen" Aunty Maryam
tace "Ai ko yan gidansu suna ta godiya" Mami tace "Allah sarki, yanzu hostel din
zasu kama mata ta zauna kenan?" Aunty Maryam tace "Toh ban dai sani ba" Mami tace
"Toh idan ba nan din ba suna da yan uwa a Abuja ne? In basu da kowa ai sai dai
hostel din dama" Aunty Maryam tace "Haka ne" sallama Mami tayi ma Aunty Maryam ta
katse wayar, Aunty Maryam ta fara tunanin ta ina za a fara convincing Mami?? Tun
bayan tafiyar Khalil Zanzibar duk sanda Mami taje gidan Aunty Maryam a daki Aunty
Maryam ke sa Nihad ta zauna har sai Mami ta bar gidan, idan kuma ita ke son xuwa
gidan yayartata ita kadai take xuwa da Mus'ab ta bar Nihad da mai aikinta a gida,
unlike before da har da mai aikinta take zuwa gidan, a cikin wannan kwanakin kuma
mijinta ya sanar mata nan da kwana biyar xa su taho kasar da yake, ta rasa ta inda
xata billo ma yar uwarta a kan Nihad. Ranan friday ta shirya taje can gidan, bayan
sun gaisa da Mami a bedroom dinta, it took her like five minutes kafin ta samu
kwarin gwiwan yi ma yayartata magana, Mami tace "Wani magana kuma ke tafe da ke? To
Allah ya sa lafiya, ina jin ki" Aunty Maryam tace "Mami dama iyayen yarinyar nan ne
suka kira jiya, suna neman alfarman ta zauna wajenmu don basu son xamanta a hostel,
and i think lectures will be commencing in 2 weeks time" Mami dai kallon Aunty
Maryam kawai take, Aunty Maryam tace "Toh ni kuma gashi nan da kwana biyar xa mu yi
tafiya" Mami tace "Ikon Allah, to Maryam ke ko da ba tafiya xa kiyi ba ina ke ina
rike yarinyar nan dama? Kuma ma da suka gaya maki haka ai sai kice barin kasar ma
xa ki yi, sannan ni kuma da kika zo nan kika gaya min me kike son ince maki? Meye
nawa a ciki?" Aunty Maryam tace "Amma Mami ke kam ba me mance alkhairi bace, bansan
ki da manta alkhairi ba komin kankantarsa, ko albarkacin xama da suka yarda Khalil
yayi a gidansu har na shekara daya ai bakya ce haka ba" Mami tace "Yanzu ya kike
son ayi Maryam, ni dai kinsan baxai ta6a yiwuwa ince yarinyar nan ta zo gidan nan
ta zauna ba, tsangwama da hantaran yan gidan ma kadai ya isheta balle aje ga shi
matsalar da Khalil din xai shiga in har Abbansa ya samu labarin shi ya kawota gidan
nan, a ina ya santa da har xai kawota gidansa, ku na lura yin abu ku ke kanku tsaye
duk wani abun magana bakwa gudunsa, ke kinga da sararin zamanta nan gidan, kwana
daya kadai da tayi kina ganin abinda ya faru" Aunty Maryam tace "Ni wallahi idan
kina nuna shakkan matsiyatan gidan nan a fili abun kona min rai yake yaya, ita
tsinanniyar Hasanar kike tsoro ko kuma Aminar? Haba Mami ko sau daya ke baxa ki
kwatar ma kanki yanci ba, ke kenan baki son fitina ke kenan gudun abun magana, A
haka rayuwar xai ci gaba? Yo Abun magana na nawa? Dubi tuggun da suka hada ma danki
suka sa ya bar gidan nan kina ji kina gani baki iya buda baki kin tsaya kinyi
defending dinsa ba shi da gidan ubansa, nima kika hanani magana a sannan, wannan
wace irin rayuwace? Toh wallahi mu ba butulu bane, kuma ba mu mance alkhairi komin
kankantarsa, in sha Allahu yarinyar nan bata da wajen zama tayi karatunta da ya
wuce nan gidan, kuma wajenki tunda har iyayenta suka nuna mu ma sun yarda damu,
sannan da iyayen nata basu rike shi khalil din ba Allah kadai yasan depression din
da xai fada a lokacin, kana ji kana gani a kwace duk wani abu naka da ka mallaka, a
amshe takardunka akan laifin da baka aikata ba, a toshe duk wani hanyar samun
kudinka, sannan ace ka bar gidanku ba a son ganinka, infact garin ma gaba daya kada
a samu information din kana ciki, ka tafi duk inda xaka tafi, me kike tunanin zai
samu mutumin da aka ma hakan idan bai fada hannun na gari ba? Ni nasan zamansa
gidansu really contributed wajen rage masa damuwarsa banda haka da baki gansa a
yanda kika gansa ba yanzu, ai Allah ya tsine ma Hasana da Amina, ya walakanta su
dai dai gwargwado, wato tunda ta kashe aurenta yau shekara kusan ashirin to bari
naki ma ta kashe maki, ga agololinta ta cika gida da su suna ta baza mulki son
ransu, wani abun ma sae ayi masu ba ayi ma naki yaran ba, to ai ni da xata burgeni
ta auri Janar din kawai mana mu ga, for 20 good years kina daukan cin kashin matan
nan kin kasa ta6uka komai, don dai kawai ni xamana ba steady bane a Nigeria amma
wani abun da ba ayi ba wallahi, to gaskiya it's high time kema ki kwaci kanki ki
daina shirun nan Mami, yarinya kuma duk shegiyar da tace Khalil ne ya kawota gidan
nan kice karya take, bai santa ba bai ma ta6a ganinta ba, babu sa hannunsa a
zuwanta gidan, dama ai kowa ya sanki da taimako to wannan ma duk cikin taimakon da
kika saba yi ne, amma babu ta inda khalil ya santa, kawai haka za ki ce masu,
sannan hantara da tsangwama da kika ce baxa ma su ganta ba balle su yi mata, dakin
baki na nan bangaren xata zauna, da safe ta tashi ta tafi makarantar ta, ta dawo da
yamma to a ina za su ganta? Duk sanda na shigo Nigeria yin wani abu ta dawo wajena
har sanda xan koma, ba shikenan ba?" Mami dai kallon Aunty Maryam kawai take ta
kasa cewa komai, sallama aka yi a parlon duk suka daga kai.
*Not too okay, ayi manage pls*
wa enda suka yi payment ban masu reply ba har yanzu su yi hakuri xan yi kokari inyi
pls, those that checked on me i do really appreciate, Allah ya bar zumunci.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via

07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

42

Aunty Maryam na kallonsa tace "Saukan yaushe kJay?" Yace "Shigowata kenan, ina yini
Aunty" Da murmushi tace "Lafiya lau, ya hanya?" Yace "Alhmdlh" Kallon Mami dake ta
kallonsa yayi yace "Good evening Mami" Ta sauke ajiyar zuciya tace "Ka dawo
lafiya?" Yace "Lafiya lau" juyawa yayi ya fita daga parlon, Aunty Maryam tace "Ni
zan koma gida Mami, ana gobe xan tafi xan kawota nan din da kayanta" Daga haka ta
mike tana gyara gyalenta ta nufi kofa tace "Sai anjima" Mami dake ta kallonta ta
rasa ma me xata ce mata ta bi ta da ido kawai har ta fita daga parlon. Aunty Maryam
na shigowa main parlor din gidan don ita bata yarda ta bi ta bayan bangaren Mami ba
tunda ba shakkar yan gidan take ba, taga Aunty Hassana a parlon da er ta Farhana,
Aunty Hassana tace "Ashe kina gidan Haj. Maryam" Aunty Maryam tace "Eh fa ina ciki,
sannunku da shan AC" Daga haka ta nufi kofa, Aunty Hassana ta bi ta da wani shegen
kallo tana kyabe baki, Farhana tayi kasa da murya xata yi magana kawai taga Khalil
ya shigo parlon, ko kallon ita da uwarta bai yi ba ya bi bayan Aunty Maryam, Aunty
Hasana ta rike haɓa tana biye da shi da ido, wato ya ma daina gaisheta kenan yake
nufi??? Farhana ta tabe baki tace "Toh har Mum din Hanan fa baya gaidawa in gaya
maki ba ke kadai ba" Aunty Hassana tace "Haka tace min ranan, ki kyaleni da ɗan
iska, zan kuma sauke masa abinda ke kansa, shi din banza" Har Aunty Maryam ta shiga
motarta amma ganin khalil ta jira har ya karaso, ya jingina da motar yana shafa
kansa kafin yace komai tace "Shigo mu je can gidan kawai" Zagawa yayi ya bude daya
side din ya shiga ta ja motar, Securities dake bakin gate suka yi saurin bude mata
gidan, Sai da suka bar anguwan tace "Uhn na shawo kan Mami da kyar, ko jiran
opinion dinta ban yi ba na fito" Yayi kasa da murya yace "Yanzu zata iya zama nan
gidan ta dinga zuwa makarantar kenan?" Aunty Maryam tace "Kwarai kuwa, zata zauna
nan guess room dake bangaren Mami, kaga bata shiga cikinsu ba ma balle su hantareta
ko su tsangwameta, sai ta so ganinsu xata gansu, balle na lura ita ma miskila ce ta
bala'i gashi ya hade mata da nukurci" Murmushi kawai khalil yayi, Aunty Maryam tace
"Kaga ko Murja bata wani sake ma komin surutun da yarinyar take janta da shi, tana
da aji sosai" Calmly Khalil yace "To ta fi haka da kika ganta, wannan abinda ya
faru da ita ne ya ɗan fara koya mata hankali, dalilin sanyin nata kenan, but..."
Sai kawai yayi murmushi bai ce komai ba, Aunty Maryam tace "Allah sarki, dama kace
bakwa shiri ai duk zamanka gidan..." Yace "Yeah, ni kinsan bana daukan raini, so
tana ji da girman kanta nima ina ji da nawa, i just use to forget she exit in the
house, beside she's her dad's favorite" Dariya Aunty Maryam tayi tace "Ikon Allah,
kai da kake ra6e gidansu kuma kake mata girman kai?" Er dariya Khalil yayi yace "I
don't want to talk about that Aunty, amma da stepsister dinta kawai muke shiri, her
name is Nihal she is nice" Aunty Maryam tace "Allah sarki, wato she being her dad's
favorite shine aka hada mata wannan tuggun saboda bakin ciki" Khalil yace "Yea,
tunda kinga ita kadai ke zuwa Maryam Abatcha a gidan, and komai take so shi ake
mata komin tsadarsa, ban ta6a ganin mace me kissa irin stepmom dinta ba, she really
got them, komin abunki baxa ki ta6a gano cewar ba sonta take ba, at first i thought
ita ta haifeta yanda take tsaya mata a kan komai kamar gaske" Aunty Maryam ta
girgiza kai cike da tausayin Nihad tace "Allah sarki, Allah Ubangiji ya gaggauta
saka mata, Allah ya tona asirin duk masu hannu a wannan abun, Allah ya walakanta su
tun a nan gidan duniya kowa ya shaida" Khalil dai bai ce komai ba, Aunty Maryam
tayi shiru sai can tace "Dama akwai wata makociyarmu a can Yemen, nasan kai baxaka
ganeta ba tunda yaushe rabonka da can ina jin tun kana 20 years, matar tana da wani
yaro bai wuce ka a shekaru ba, yana fita kasashe ne, mugun mai kudi ne yaron, ya
sha zuwa Nigeria kuma idan ya zo har nan gidana yana zuwa, bai ta6a shigowa kasar
nan bai zo gidana ba, mun dai zama kamar yan uwa, wajen Mami ne kawai baya zuwa
saboda securities din nan naku na jaraba tun daga farkon unguwa, wallahi yaron nan
Ayman a ko da yaushe burinsa in samar masa mace yar Nigeria Hausa fulani ya aura,
gashi fa ko hausar ma shi baya ji sai turanci da larabci, da nayi ma Mami maganar
Noor tace min a'a bata son tayi nisa da ita, ni kuma kaga su Zeenah basu isa ayi
xancen aure ba su ma kuma babansu naga kamar baxai so suyi nesa da shi ba, banda
haka da xan basa su koma can gida tunda kakarsu na can ai, ai sun ma fi rike aure,
To kuwa wallahi tun da aka yi haka xan hadasa da Nihad in sha Allah, a can kasar
waye xai wani san abinda ya sameta ko wani xancen video dinta can?" Kallonta kawai
Khalil yake, can yayi dariya yana girgiza kai bai dai ce mata komai ba, tace "Au
dariya ma na baka, u think i am joking right? Wallahi i am very serious, kuma ina
me tabbatar maka zai aureta saboda ya kwallafa rai sai bahaushiya zai aura, yana
aurenta su bar kasar kawai tayi komawarta can gaba daya, dama ita ma tana zubi da
larabawan ai" Khalil na Murmushi yace "Gaskiya ne, Allah ya rufa asiri" Aunty
Maryam tace "Ameen, ina komawa gida da daddare xan yi chatting dinsa up, har
hotonta idan ya kama sai in tura masa gobe, ai ɗa na kowa ne bawa sai mai shi, in
sha Allah sai Allah ya daukakata ko don saboda wannan jarabawan da take kan ci"
Khalil ya kalleta yace "Toh amma ai kya bari ta samu karatu ko Aunty?" Aunty Maryam
tace "Aa xata yi karatunta confirm, idan kuwa ya shirya auren yanzu kawai ya aureta
idan sun je can ya samar mata makaranta, mu ma duk ba can muka yi karatun ba"
Khalil na gyada kai yace "Haka ne" Aunty Maryam tace "Yauwa, kaga ta haka har
zuciya sai stepmom din nata ta hadiya saboda bakin ciki, bayan asirinta ya tonu
kenan a idon duniya" Khalil dai bai kuma cewa komai ba har suka iso gidan Aunty
Maryam, tana parking ta sauka shi ma ya sauka, Nihad ta fito tare da Mus'ab dake
wajenta tun fitar mamarsa, tayi masa wanka ta canza masa kaya, yana jin motar
uwarsa ya fito compound da gudu zuwa wajenta, Nihad dai na tsaye bakin kofar
parlon, ko lura da Khalil din ma bata yi, shi ko tunda yayi mata kallo daya yaga
wani haske da tayi, wanda dama shine ainahin haskenta, wahala da tashin hankali ne
ya boyesa, Aunty Maryam na rike da hannun yaronta bayan ta tambayesa wa yayi masa
wanka ta nufi kofar parlon, Khalil ya bi bayanta, sai a sannan Nihad ta gansa,
Nihad na tsaye har Aunty Maryam ta Karaso ta yi mata sannu da zuwa, Aunty Maryam
tace "Yauwa gwara da kika masa wankan kafin in dawo don da baxai yarda ba, hope kun
gama girkin?" Nihad tace "Ehh mun gama" Aunty Maryam ta shiga parlon, Nihad ta
kalli Khalil daga sama har kasa ta juya ta bi bayan Aunty Maryam, da mamaki ya bi
ta da kallo yana tsaye, Aunty Maryam ta juya ta kalleta jin bata ji ta gaidasa ba
tace "Kin gaishesa kuwa Nihad?" Ta ɗan yi yake ta juya da sauri ta kallesa tace
"Ohh, ban gansa ba, ina wuni" tana fadin haka da sauri ta bar wajen ya bi ta da
ido, Aunty Maryam dai ta zauna parlor tana amsa gaisuwar Murja, ya karaso cikin
parlon ya zauna, tuni Murja ta tafi kawo masa ruwa da lemo, Nihad kuma dama dakin
da take tayi wucewarta, Aunty Maryam na kallonsa tace "Wallahi har ka kara wani
fresh fitar nan da kayi kwana biyu, halan sanyi ake a kasar?" Ya ɗan yi murmushi
kawai ya dau bottle water ya bude yana sha, sai kuma ya ciro wayarsa ya shiga
number Mumy yayi dialing, tunda suka zo Abuja yake kiranta baya samunta, luckily
yanzu ya shiga, tana dagawa ya gaisheta, yayi mata ya jiki sannan ya tambayeta su
Sudais, daga haka yace "Bari in ba Aunt dina ku gaisa" Mumy tace "Toh..." daga haka
ya mike ya kai ma Aunty Maryam wayar, suka gaisa, nan Mumy tayi mata godiya sosai
kamar tasan issue din da ake kai, Aunty Maryam tace "Ahh ba komai Hajiya ai ɗa na
kowa ne, ke dai ki kwantar da hankalinki in sha Allah komai xai daidaita, kawai
kiyi ta bin ta da addu'a domin kuwa addu'an ki gareta baxai ta6a faduwa kasa ba,
Allah Ubangiji ya rufa mana asiri ya kara daura mu akan makiyyanmu" Mumy taji dadin
wannan furucin na Aunty Maryam, nan kuma ta kara jin hankalinta ya kwanta ta samu
relieve, suka yi sallama Aunty Maryam ta mika masa wayar, ya amsa Aunty Maryam tace
"Ka ba Murja ta kai mata wayar su gaisa ko yau tayi trying kiranta da wayana bai
shiga ba" Khalil ya mike ya nufi dakin da Nihad take, ko kwankwasa kofar bai yi ba
ya bude, ta juya da sauri don ko Aunty Maryam kafin ta shigo tana mata Knocking
haka ma Mus'ab ko mai aikin gidan, ta ci gaba da game din da take a Ipad din
Mus'ab, ya karaso cikin dakin ya sake dialing number Mumy yana fara ring ya mika
mata wayar, ta amsa tana kallon screen din ganin Number Mumy ta kai kunne da sauri,
you can tell how happy she is da take magana da Mumy, Mumy ma ta kara samun nutsuwa
jin how lively her daughters voice is, Nan dai Mumy ta kara mata nasiha a kan ta bi
mijinta, Nihad dai tayi shiru har Mumy ta gama, sannan tace "Toh nagode Mumy, Allah
ya saka da Alkhairi" Mumy tace "Yauwa ki gaida yan gidan gaba daya" Nihad tace "Toh
Mumy a gaida min da su Sudais" Daga haka ta katse wayar ta mika masa without
looking at him, ya rungume hannunsa bai amshi wayar ba yana kallonta da kyau yace
"Wato kin dawo da rashin kunya da fitsaran da kika saba yi ma mutane ko?? Kuma i am
hoping kin dai tabbatar ni ba sa'anki bane yanzu in all aspect" Ta juya ido tace
"To dama ai ba dainawa nayi ba" Sake baki yayi yana kallonta, Ta jefa masa wani
kallo tace "Kuma da kake wani daddaga min shoulder 2 days back naga dai babanka ne
mai kudi ba kai ba, kuma gidan babanka ne ba naka ba, duk motocin gidan nan na
babanka ne not urs, all those securities are for ur father not you, don haka ka
jira sai kayi naka kudin kafin ka dinga daga min shoulder kana forming, thinking u
are not my mate in all aspect...." Kallonta ya dinga yi da mamaki, ya dake yace "Ke
me yasa baki jira kinyi naki kudin ba kike daddaga naki shoulders din da kudin
babanki a gidanku" Ta turo masa
baki tace "Toh ai ni macece, kuma ni yarinya ce yar karama ban san abinda nake ba"
ya kai hannu xai yi squeezing bakinta yace "Sha'awar gado ce ba yar yarinya ba" Ta
koma baya da sauri tana kallonsa, ya hade rai yace "Na maki iya abinda xan iya maki
albarkacin mahaifiyarki da mahaifinki amma ba don halinki ba domin baki cancanta
ba, it's now left for u ki zauna gidan mutane kisan ba gidanku kike ba yanzu, ki
kwantar da kanki, ki gane you are now a NOBODY, kina gida ne wanda level dinki bai
kai nasu ba, baki wuce kiyi wanke wanke a gidan ba a biyaki, shi ma by luck xaki
samu don mu masu degree muke dauka suyi mana aiki a gida.... Dai dai nan aka bude
kofar dakin, Aunty Maryam na tsaye bakin kofa tace "Basu gama wayar bane?" Nihad ta
mika masa wayarsa tana kallonsa, ya amsa shi ma yana kallonta, dauke kai tayi ta
nufi kofa, Aunty Maryam tace "Pls ki yi feeding din Mus'ab, ko na basa ni ba ci xai
yi ba" a hankali Nihad tace "Toh" Sannan ta fita, Aunty Maryam ta juya ta bi
bayanta, sai a sannan shi ma ya fito parlor, Aunty Maryam tace "Ji Ayman da nake
maka magana dazu ina buda WhatsApp yanzu naga message dinsa wallahi" Khalil dai
kallonta kawai yayi ya zauna, sai kuma yace "Toh Allah ya baku nasara" Aunty Maryam
tace "Ameen" Yace "Xan je gidansu Nadeeyah, sai da safe Aunty" ta gefen ido Nihad
dake ba Mus'ab indomie ta kallesa, Aunty Maryam tace "To a gaisheta" Ya mike yace
"Xata ji" Daga haka ya nufi kofa ya fita. Har Khalil ya koma Kasar Tanzania ranan
lahadi bai koma gidan Aunty Maryam ba, ya dai mata forwarding admission letter da
komai na Nihad ta e-mail dinta ranan lahadin kafin ya tafi, Aunty Maryam tayi murna
sosai ganin Nile din ya samar mata kuma ta samu, Aunty Maryam ta fito parlor tana
kallon Nihad looking so happy for her tace "Congratulations Dear, ga admission
letter dinki...." Nihad ta amshi wayar da Aunty Maryam ke nuna mata, ta dinga
kallon sunan makarantar as if she wants to be sure, wannan ai Nile take gani, can
ta kalli Aunty Maryam tace "Aunty wani makaranta ne?" Aunty Maryam tace "Nile
University my dear" Sai da Nihad tayi shock jin da gaske sunan da take gani jikin
screen din wayar ne, Nihad tayi karfin halin cewa "Aunty na ina?" Aunty Maryam tace
"Wanda dai kika sani" Nihad ta zaro ido tace "Aunty waye ya biya min makarantar?"
Aunty Maryam na Murmushi tace "Khalil, he paid the tuition fees and everything, don
haka it is good to be good, as a result of the goodness ur father did to him, he is
also doing u good by sponsoring you to one of the costliest university...." Lokaci
daya Nihad taji bata son zuwa makarantar kuma baxata je ba, amma bata ce ma Aunty
Maryam komai ba, Aunty Maryam tace "Anjima xan kirasa in baki waya kiyi masa
godiya" A hankali Nihad tace "Toh" Da daddare kuwa Aunty Maryam ta zo har daki ta
kawo mata wayar, Nihad ta amsa Aunty maryam ta juya ta fita, ko sallama bata yi
masa ba a takaice yace "Bana bukatar godiyarki ba don ki gode min na maki ba,
sannan ba don kinyi deserving nayi maki ba...." Nihad tace "Toh ai ba godiyar xan
yi ba dama, da ka kwantar da hankalinka kaji abinda xan ce maka kafin ka yanke
hukunci.... If you are lucky xa su maka refunding ka sanar masu suyi maka, don
baxan je ba"
Abba ne xaune parlonsa da Umma dake yanka masa lemo, yace "Kamila ta zo gida ne?"
Umma ta kallesa tace "Aa bata zo ba, rabonta da gidan nan ai xai yi sati daya" Abba
yace "Ohk na fito masallaci yanzu mijinta ya kirani" Umma ta ajiye wukar hannunta
tace "Lafiya dai ko?" Abba zai yi magana aka doka sallama bakin kofa, duk suka
kalli kofar, Umma ta amsa ta mike, Inna ta shigo parlon Umma na mata sannu da zuwa
da fara'a tace "Saukan yaushe Inna?" Inna ta saki baki tana kallonta, can tace "Da
naje ina?" Sai kuma ta ja tsaki bata kara sauraronta ba tana kallon Abba tace "kai
Ibrahim kira sabon drebanka maza ya taso ya kai ni wajen jikata ba kashe mutum tayi
ba da xan yanke alaka da ita haka kawai, balle babu laifin tsaye balle na zaune
sharri ne aka mata, abinda wasu haka zaka ga an masu bedion da mamansu saɓaɓar
saɓaɓar a titi, sannan babu dan kamfai a jikinsu mazaunansu mala mala, matancinsu
duk a titi, sai ita da idan ba ido mutum yasa sosai ba baxai san babu kaya a
jikinta ba, wallahi wani ma tunani xai yi yar shekara shidda ce a bedion indai
bedion da aka nuna min ne, bashi da wani aibu da har za a kullace yarinya a
banzatar da lamarinta haka, bayan an aura mata gansameme da bamu san isilinsa ba ko
ɗan yankan kai ne, ko ɗan kinnafin ne, ko ɗan fashi, oho duk dai bamu sani ba, duk
da haka kuma mu fita harkarta? to na dawo hayyacina maza maza a kai ni gidan jikata
in ga halin da take ciki yanzun nan"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

44

Mikewa Nihad tayi bayan ta tuna wayar da Aunty Maryam ta bata, ta sauko daga kan
gadon ta tafi inda empty bags din suke ta duba wanda wayar ke ciki bata gani ba,
mamaki ne ya cikata ta dinga kallon jakar, ta duba second bag din nan ma taga babu
wayar babu alamarsa, Knocking aka yi a kofar dakin ta mike tsaye da sauri tana
kallon kofar, can ta karasa ta bude taga Mimi a tsaye, Mimi tace "Ki fito mu ci
abinci" Nihad tace "Toh" Mimi tace "At Mami's parlor" Nihad ta gyada mata kai, Mimi
ta bar bakin kofar, komawa dakin Nihad tayi ta dau mayafinta tana kallon agogo,
karfe sha biyu saura ake cin abincin rana kenan a gidan, ta dai nufi kofa ta fita
zuwa parlon Mami tana tafiya a hankali, Mimi na zaune with 3 different foods a
gabanta, Nihad ta karasa tana kallon abincin, Mimi ta nuna mata wajen da zata
zauna, Nihad ta zauna, Sai ga mai aikin Mami ta shigo da ruwa me sanyi da drinks a
hannunta ta ajiye masu tana kallon Mimi tace "Za a kawo fruit Salad din ne?" Mimi
ta kalli Nihad tace "Will you take fruit Salad?" Nihad ta girgiza kai alamar a'a,
Mimi ta kalli Bilkisu tace "No need" Bilkisu ta juya ta fita, Mimi ta zuba abinda
xata ci a abincin gabansu, tayi ma Nihad alamar ta diba, Nihad ta dau plate ta debi
shinkafa da miya, daga Nihad har Mimi cakalkala abincin kawai suke yi, ita Mimi sae
danna wayarta take, daga karshe ta mike tana kallon Nihad dake mamakin wai har ta
gama cin abincin kenan, Mimi tace "Let me go and brush My teeth" Nihad ta gyada
mata kai kawai, Mimi ta fita daga parlon, ba a dau lokaci ba Noor ta shigo parlon
kallo daya tayi ma Nihad ta dauke kai ta nufi dakin Mami ganin Mami bata nan ta
juya ta nufi kofa zata fita, Nihad ta bi ta da ido har ta fita, Mimi na dawowa
parlon ta kira Bilkisu ta waya ta zo ta fitar da sauran abincin daga parlon.... Har
yamma Nihad na parlon Mami, wayar da bata gani ba yayi mugun tsaya mata a rai, kuma
ta ma san wa zai dau wayar, Lokaci lokaci Mimi ke shigowa wajenta a parlon, seems
basa wani zama nan bangaren sae Mami ta kirasu ko kuma sun shigo gaisheta, shigowar
Mimi na karshe tace "Pls mu je ki rakani saloon xan yi gyaran gashi" Nihad tace
"Toh" Mimi ta jirata har ta dauko Hijab dinta sannan suka fito Main parlor din
gidan, Nihad sai estimating uban tafiyar da suka yi kafin su shigo ainahin parlon
gidan wanda girmansa ya wuce misali take, the house is really huge, Tun da suka
shigo parlon Aunty Hassana dake waya ta bi su da ido, can ta katse wayar da take
tace "Ke Mardiyya zo nan" Mimi ta dawo tana kallonta, ko kadan Nihad wasn't
comfortable at the way the woman was looking at her, Aunty Hassana tace "Wacece
wannan?" Mimi ta kalli Nihad da tayi tsuru tsuru tace "Aunty bakuwa ce" Aunty
Hassana tace "Bakuwar wa?" Mimi ta buda hannu tace "Bakuwar Mami" Nihad tayi karfin
halin cewa "Ina yini" Aunty Hassana na kallonta daga sama har kasa tace "Lafiya"
Mimi ta jawo hannun Nihad suka bar parlon, Sajida da shigowarta parlon kenan ta
kalli Aunty Hassana tace "Wallahi Mama she is the one" Aunty Hassana tace "Anya
kuwa? Naga wannan fara ce sosai fa" Sajida tace "I am telling you the fact, ita ce,
bari in dauko wayata ki gani" Daga haka ta tashi da sauri ta tafi ta dauko wayarta
ta shiga video tayi playing ta mika ma Mamarta wayar, Aunty Hassana tace "Toh ba
cewa ku ka yi tare da wannan ɗan iskan suke ba? Kun ce shi ya kawota gidan" Sajida
tace "We are not sure, kawai muna shiga parlon Mami muka ganta a zaune, kilan er
uwarsu ce saboda yau da Aunty Maryam xata tafi ne ta sake dawowa gidan nan, all
those while tana gidanta" Aunty Hassana tace "Kaiii, da yar uwarsu ce xan santa, da
kyar dai in ba shi ya kawota gidan nan ba, idan kuwa ba shi bane ya aka yi sai da
ya dawo ita ma muka ganta a gidan, amma ba komai xan samu yaya anjima idan ya dawo,
ae dai baxa a kawo masa yarinya gidansa bai sani ba, xai min bayanin ko wacece"
Nihad ta dinga kallon motar da wani mutumi sanye da camouflage yayi parking dai dai
inda Mimi ke tsaye, ya sauka ya bude masu back seat, kana ganin shigar da Mimi tayi
na English wear ga baƙin shade dinta a ido sannan ga wani jaka da ta rataye xaka
san ba karya, she looks so cute and beautiful, Nihad bata ta6a jin da akwai wanda
xata ji ya fita komai a rayuwa ba sai yanzu, ita da ganin kanta take babu ya ita,
har University da take zuwa ma kallon kasa kasa take masu ba kowa take ma magana ba
ko da kuwa an mata, don tana ganin ba class dinta bane su, sai gashi yanzu kawai
taji ta raina kanta, Mimi na kallon Nihad ganin yanda ta ja gefe ta tsaya tace
"Shigo" Nihad ta shiga motar ta kulle a hankali, mutumin ya ja motar aka bude gate
suka fita daga gidan, Mimi ta ajiye wayarta da take dannawa tana kallon Nihad tace
"Here is a question for you Nihad" Nihad ta dinga kallonta ba ko kiftawa, Mimi tace
"How did u come to know my broda?" A hankali Nihad tace "Wanne?" Mimi ta ɗan yi jim
tace "Yayana fa nake nufi, wanda ku ka dawo tare da shi dazu da safe" Nihad tace
"Ohk, Yayanki ne?" Mimi ta buda ido tace "Yea he is my senior brother, we are
having same father and same mother, Mami is our Mum, Noor is my senior sister, she
is his immediate but ya girmeta sosai, ya bata 12 years, xan nuna maki ita idan mun
koma gida kilan baku hadu ba har yanzu" Nihad sai kallonta take don truly Mimi na
nugun kama da shi, both the nose and eyes, a hankali Nihad tace "Pls ki gaya min
gaskiya gidansu ne wannan gidan da muka fito?" Mimi ta wara manyan Idonta tace
"That's funny, he is the first and only male child of our father, did he tell you
ba gidansu bane?" kallonta kawai Nihad take tana jin ita fa yanzu da ta ga ainahin
cikin gidan da irin girmansa da kyau ta kasa yarda gidansu Khalil ne, ita kawai
yanxu gani take kamar rikonsa ake a gidan ko kuma gidan ɗan uwan babansa ne, abinda
ta saka a ranta kenan don she is beginning to get confuse ta yaya ma xa ace wannan
gidan nasu ne, mutumin da yaje gidansu yake driving ana biyansa for almost a year,
sannan har kauyensu ya kai ta, to me yasa xai kawota irin wannan gidan yanzu ta
yarda nasu ne, Mimi da ke ta kallonta ta katse mata tunaninta tace "What are u
thinking about?" A takaice Nihad tace "I am finding it hard to believe, and I don't
think i will believe" Mimi tayi murmushi tace "Now i understand, he acted like he
is a nobody right?" Nihad tayi shiru tana kallonta, Mimi ta shiga gallery dinta
taje inda take ajiye hotunan yayan nata, wanda sun fi dari ta shiga ta mika ma
Nihad tana kallonta, farkon hotonsa da Nihad ta gani ta dinga kallo babu ko
kiftawa, sanye yake da farin labcoat with stethoscope round his neck, ta tafi next
hoton, ta gansa cikin private jet an masa unaware picture, yayi crossing kafa yana
danna waya with a serious face, ga tsadadden non-alcoholic wines a gabansa,
designers ne kayan jikinsa, irin kyan da yayi kuwa a hoton ba ace wa komai, Nihad
ta dinga kallon hoton don karya ne mutum ya kalli hoton bai sake kallo ba, bata san
sanda tayi zooming ba still wanting to confirm and be sure shi din ne dai, taga
wallahi shi ne, da zaka shiga zuciyarta kaga mamaki da shock da ya cika sa, a
hankali ta tafi next picture din ta gansa a Newyork, then another in Los Angeles,
Paris and another in United kingdom, infact duk yawanci hotunan a kasashen waje ne,
wasu hotunan da turawa, wasu larabawa, she is really shock at all what she is
seeing, sai kuma ta fara ganin hotunansa da Nadeeyah, a hotonsu na uku tare ta ki
ci gaba da kallon, ta ɗan kalli Mimi dake danna second phone dinta giving it all
her attention, tayi tapping dinta ta mika mata wayarta, Mimi tace "Are you done?"
Nihad ta gyada mata kai, amsar wayar Mimi tayi ta mayar cikin jaka ta ci gaba da
abinda take da dayar wayarta, har suka isa saloon din Nihad bata sani ba don tayi
nisa tunanin da take, Mimi ta kamo hannunta tace "Dear" Firgit Nihad ta dawo, Mimi
tayi murmushi tace "Mun iso" Nihad ta kalli mutumin da ya bude masu motar yana
jiran su sauko, ta sauka daga cikin motar, sannan Mimi ma ta sauka, kallon wajen
Nihad ta dinga yi tana imagining duk nan saloon ne? How big and beautiful, ganin
yanda ta tsaya Mimi tace "Mu je" Nihad ta bi bayanta ta kasa daina kallon saloon
din har suka shiga ciki, nan taga fararen mata ne masu gashi har gadon baya ke zuwa
gyaran gashi wajen, har turawa da larabawa, kana ganin cikin saloon din kasan ba
karya, Mimi tace "Ke ma kiyi gyaran gashinki" Nihad dai bata ce komai ba, da Mimi
ta sake mata magana tace "Ohk" sai da suka 6ata kusan awa daya da rabi a saloon din
daga karshe suka fito, har sannan kuma wanda ya kawosu na jiransu a motar, har suka
isa gida Nihad na duniyar tunanin da ta fada, mamakin Khalil kawai take.... why
then did he disguise himself and come to their house as a driver? What might be his
mission? And who were those villagers he took her to and claimed they are his
parent? Tambayoyin da take ta ma kanta kenan amma babu amsa, ta kuma rasa amsan,
kenan Nihal ta san wanene shi shiyasa take kulasa har da exchanging number? Nan
abubuwa da yawa da suka faru tsakaninta da shi a gidansu suka hau dawowa mata
vividly, lkci daya tayi saurin kawar da tunanin daga xuciyarta don ko tunawa bata
son tana yi, a haka har suka isa gida... Basu tarda kowa a Main parlor ba Mimi ta
raka Nihad har dakin da aka sauketa, Nihad na kallonta a hankali tace "Thank you"
Murmushi kawai Mimi tayi mata ta juya zata fita, Nihad tace "Wait plss, ina son xan
maki tambaya" Mimi ta juyo tana kallonta tace "Ohk" a hankali Nihad tace "I have
this female friend, a guy came to stay in their house... he showed he was a nobody,
i mean he disguised him self, he hide his identity, so all through his stay a
gidansu yana mata abubuwa gadara gadara, sannan he don't have an atom of respect
for her as per somebody that came to stay and work under them, shikenan ita kuma
sai bata raga masa, shi ma kuma bai fa sa walakanci da gadara da yake mata ba, to
cut everything short har dai ya bar gidan, ita kuma it now happens tana nasu gidan
da zama for just a while, and he wasn't what
she took him to be, she saw him a different person in his parents house, idan ke
ce a shoes din kawar nan tawa tell me how u will handle everything...." Mimi ta
fashe da dariya sosai, ta zauna gefen gado tana kallon Nihad still laughing tace
"Really?" Nihad dai fuskarta babu yabo babu fallasa tace "Tell me how u will handle
it" Mimi ta sauke ajiyar xuciya tana murmushi tana gyada kai tace "Ohk, if i should
be in this shoe gaskiya xan ji kunyarsa sosai...." Nihad tace "Mind you, sanda yake
gidansu baya respecting dinta sannan walakanci da gadara kawai yake mata da gaya
mata bakar magana, ya sha hadata da parents dinta har ya kai ya kawo nobody is even
supporting her again in their house, shi kuma ba a ganin nasa laifin, kullum shine
me gaskiya ita kuma ayi ta mata fada" Mimi dai murmushi kawai take tana kallon
Nihad tace "Amma ita bata masa walakanci ko cin mutunci ko cin zarafinsa ba, or
even gori during his stay?" A takaice Nihad tace "Tayi mana, tunda ae shi ya ja
komai" Mimi dai ta kasa daina murmushi, can tace "Ohk in ni ce, to make peace reign
xan samesa a gidan nasu in basa hakuri ince let by gones be by gones plss, we just
misunderstood ourselves amma yayi hakuri komai ya wuce" Nihad ta katse ta tace
"Idan baxa ta iya basa hakurin ba fa?" Mimi tace "Then ko hanya baxan dinga barin
yana hadani da shi a gidan nasu ba, i will try all possible best to be avoiding him
sbda duk sanda na gansa a gidan xan dinga tuna abubuwan da suka faru a baya and i
might be feeling guilty for everything.... So idan ni ce i will prefer in basa
hakuri a wuce wajen, saboda with all that have happen baxan samu peace of mind din
xama a gidan ba" Mimi na Murmushi ta kare maganar, Nihad tace "Ai shima duk abinda
yake mata bai ta6a bata hakuri ba" Mimi tayi dariya tace "Toh shikenan, sai kawai
tayi ta avoiding dinsa, that's just it" Nihad tace "Thank you for ur advice to her"
Mimi tace "Welcome dear" Daga haka ta juya ta fita, Nihad ta koma gefen gado ta
zauna a hankali. Bayan Magriba Nihad ta tafi bangaren Mami ta dalilin kiran da Mimi
ta shigo tayi mata wai Mami na kiranta, kwance ta ga khalil a parlon farko waya na
kare kunnensa, ta kalli Mimi ganin ta shiga next parlor din, ta nufesa trying her
possible best to be calm tace "Ka bani wayata da Aunty Maryam ta bani...." Ko
kallonta bai yi ba, from the way yake magana har ta gane da warce yake wayar, ganin
yayi banza da ita tace "Magana nake maka" Ya katse wayar da yake ya mike zaune yace
"Why are interrupting my call?" Taki ce masa komai, mikewa yayi ya bar ta a wajen
ya fice daga parlon ta bi sa da wani kallo, can ta shiga daya parlon. Mami na
kallon Nihad bayan ta shigo ta gaisheta tace "Ba dai wani matsala ko? And i hope u
are comfortable a dakin?" Nihad tace "Eh Mami nagode" Mami tace "Good, if there is
anything u let me know" Juyawa Nihad tayi ta fita. Washegari da safe Nihad ta fito
wanka kenan Mimi tayi Knocking, ta saka hijab dinta ta tafi ta bude mata kofar,
Mimi ta sakar mata murmushi tace "Good morning Neehad" Nihad ta mayar mata da
murmushin tace "How was ur night" Mimi tace "Alhamdulillah, Aunty Maryam wants to
speak to you on phone" daga haka ta mika mata wayar tace "Idan kun gama ki sameni
parlon Mami" Nihad ta gyada mata kai ta juya ta koma cikin dakin, wani farin ciki
taji jin muryar Aunty Maryam, bayan sun gaisa Aunty Maryam tace "Ina wayar da na
baki Nihad?" Nihad tace "Ban kara ganinsa ba Aunty" da mamaki Aunty Maryam tace
"Baki gansa ba kuma? Ba a jakarki kika sa ba?" Nihad tace "Ehh na duba kuma ban
gani ba" Aunty Maryam tayi shiru, can tace "Waye ya dau maki jakar?" A hankali
Nihad tace "Shi...." Aunty Maryam tace "Khalil?" Nihad tace "Ehh" Aunty Maryam tace
"Ohk, shikenan xa mu yi magana" daga haka tayi mata sallama ta katse wayar, Aunty
Maryam na katsewa Khalil ta kira, bayan ya daga ko amsa gaisuwarsa bata yi ba tace
"Bawan Allah akan wani dalili ka dauke wayar da na ba Nihad?" Khalil dake kwance ya
mike zaune ya buda ido yace "Waya kuma... Ita tace maki haka? Beside Aunty ai ni
ban ma san da wata waya ba" Ta dakatar da shi tace "Kar ka raina min hankali Malam,
babu wanda zai dau wayar nan sai kai, yanzu dalilin da ka dauke wayar kawai nake
son ji, period" Ya koma ya kwanta yace "Because kamata yayi tayi concentrating a
kararunta yanzu ba ta rike waya ba...." Aunty Maryam ta saki baki tana sauraronsa,
sai da ta bari yayi shiru sannan tace "Toh dauki wayar ka mayar mata, xan kirata da
shi nan da minti goma...." Shiru yayi bai ce mata komai ba tace "Baka ji abinda
nace bane?" Yace "Na ji" Tace "In kuma kana son mu samu matsala da kai ka kara
dauke wayar nan daga wajenta ka ga, ai kana ji sai da nace maka na ba wani number
layin shine xaka wani kama waya ka ɗauke, jaririya ce ita da baxata rike waya ba ko
kuma waye ya ta6a xuwa jami'a ba waya?" Khalil dai bai ce mata komai ba, tace
"kamar yanda nace nan da minti goma zan kira wayar bana son jin sa a kashe, sannan
kuma ita nake son jin ta daga kiran" Daga haka ta katse wayarta ya taɓe baki, bayan
few minutes ya sauka daga saman gadonsa fuskarsa babu yabo babu fallasa ya dau
shirt dinsa ya saka ya dau wayar sannan ya fita. Nihad ta gama shiryawa ta dau
gyalenta ta fita zuwa parlon Mami, dai dai corridor that will lead to the parlor
suka hadu da shi yana zuwa ta opposite dinta, taki yarda su hada ido har ta iso
kofar xata bude taji ya fixgo hannunta ya bar bakin kofar, zaro ido tayi tana bin
sa tace "Meye kake ja na haka?" Bai saurareta ba yana ta tafiya da ita, Balcony din
part din ya shiga tare da ita, Ta dinga bin domain din wajen da kallo, kai baxaka
ce ba a kasar waje bane, can ta kallesa tace "Why will you drag me this way??" Yace
"Bana jin wannan yaren" Ta wani kyabe baki ta dauke kai tana kallon titi, a takaice
yace "Zan baki waya kamar yanda aka ce in baki, amma ina son tunasar maki cewa shi
aure ko ma wani iri ce daraja ne da shi sannan ba abar wasa bace, ba ruwan Allah da
auren soyayya ko auren kiyayya ko auren hadi, so abu kadan zaki yi yanzu ki sa6a ma
Allah, ki ja ma kanki fushinsa...." Da mamaki Nihad ke kallonsa har da bude baki,
bai bata space din cewa komai ba ya ci gaba yace "Dama kawai ina mutunta iyayenki
ne shi yasa har yanzu ban raba auren da ke tsakanina dake ba ina jiran appropriate
time din yin hakan, sannan i have conscience baxan iya sakin ki a halin da kika
shiga days back, don a sanda mahaifinki ya nuna baya bukatar ni dake a garin da
yake, a sannan ya kamata ace na rabu dake na kama gabana don dama saboda shi nake
zaune dake, amma ban yi hakan ba, tausaya maki da nake ne dalilin da yasa har yanzu
aurenki ke kaina.... So a halin da ake ciki yanzu bazan so a rubuta maki zunubi ta
dalilina ba, don haka idan na lura baxa ki daraja martaban aure ba kuma zaki janyo
ma kanki fushin Allah to zan raba auren dake tsakaninmu don sama maki sauki, dama i
was hoping to do that in the rightful time a lokacin da ya kamata, probably idan
kinyi nisa karatunki kin kusa kammalawa, kinyi reconciling da mahaifinki, kinyi
kokarin amending few damages that u did to ur self, kin kuma sake fahimtar rayuwa,
kin fahimci duniya da mutanen dake cikinta da kyau, but i Sense duk wannan won't be
possible saboda hanyar da aka daukar maki na rike waya, and communicating with a
guy...." Nihad dai kallonsa kawai take, yace "So how ever u chose it to be is left
to u, ina maki abubuwa da yawa ne ba don kin cancanci in maki ba, sai ɗan darajan
iyayenki..." Yana gama fadin haka ya ciro wayar aljihunsa ya mika mata yana
kallonta yace "I will decide on what to do in few days time" ta sa hannu ta amshi
wayar, ya juya ya bar wajen.... Nihad ta shiga parlon Mami ta tadda Mimi na jiranta
su yi Breakfast, bayan ta zauna shayi kawai ta iya sha sai irish kadan, ta na dai
zaune idonta na kan tv abubuwan da Khalil ya gaya mata na ta dawo mata, tabe baki
kawai tayi, aka bude kofar duk suka daga kai, Aunty Hassana ce ta shigo parlon,
bata amsa gaisuwar Nihad ba tana kallon Mimi tace "Ke ina uwarki?" Mimi ta mike ta
shiga dakin Mami, Aunty Hassana ta dinga hararan Nihad, a hankali Nihad ta mike ta
nufi kofa ta fita daga parlon don haka kawai ta ji tana tsoron matar, Aunty Hassana
ta bi ta da harara, tana ta tsaye har Mami ta fito, Mami na kallonta tace "Mun
tashi lafiya Aunty Hassana" Aunty Hassana ta dakatar da ita tace "Ba wannan ya kawo
ni ba, ina ce ai ko ba komai Hajiya Fatima yanda xa ki mutunta uwar mijinki da tana
raye haka nima ya kamata ki girmamani ki mutunta ni don ni din ba banza bace, Da
mijin nan naki da kike takama ya sha nono ni ya sakar ma, amma naga baki da warce
kika raina sama da ni, yanzu ace wannan yarinyar da ta zo gidan nan tun jiya har ta
kwana zuwa yau ya dace ace baki turata ta gaidani ta gaida Amina a gidan nan ba?
Idan ita Amina bata isa ba nima din ban isa ba kenan? Kawai yarinya ta shigo gidan
mutane tsabar ba a nuna mata matsayin wa enda ta samu a gidan ba sai ta wuce ka
wuce bata gaida ka ba, ko daga kai baxata yi ta kalleka ba, to akan wani dalili?"
Mami ta kalli Mimi tace "Mimi je ki kai ta ta gaishesu" a fusace Aunty Hassana tace
"Aa bama bukata, taje ta gaida wa? kawai dai ina kara baki shawaran ki daina abinda
kike, in raini kike ji a gidan nan to karki matso da shi inda nake, don ni ba
abokiyar yin ki bace Fatima" tana kai wa nan ta fice daga dakin kamar iska, Mimi ta
kalli Mami tace "Why is she always creating issues out of nothing? From this to
that, is she normal?" Mami tace "Jeki ki kaita nace ta gaishesu ban iya wahala da
safen nan Mimi, da nasan abinda ya kawota kenan ma ni cewa xanyi kice mata ina
bacci" Mami na kai wa nan ta juya ta koma dakinta. Khalil na zaune parlon Abbansa,
ya jira har ya gama wayar da yake na kusan minti goma, Abba na kallonsa bayan ya
gama a takaice yace "May i help you?" Khalil ya gyara zama yace "My Curriculum
vitae, the key to my houses and their written document, my land title, my car....
Ina bukatarsu gaba daya, and I also want my business account unfrozen" Kallonsa
kawai Abba yake, can ya mike yana kallonsa da kyau yace "Till u pay ur debt of
800m, idan ba haka ba duk assets din nan da ka lissafo ina me tabbatar maka siyar
da su zan yi, kuma basu kai biyan bashin ba ma, shi kuma Cv din in kona, after all
i sponsored you...." Khalil ya dinga kallon mahaifin nasa, Abba yace "So Now get
out before i shoot ur leg" mikewa Khalil yayi ya nufi kofa kamar xai tashi sama ya
bude, sai kuma ya juyo yace "But dad, I can't pay for what I know nothing
about...." Yana fadin haka ya fice daga parlon, direct bangaren Mami ya tafi, Mami
na ganinsa ta mike tace "Lafiya" Yana huci yace "Mami me yasa har yanzu Abba ke
danganta 800m dinsa da ni?? Ina zan kai har 800m" A hankali Mami tace "Saboda kai
ya ba, a hannunka yasan kudinsa" A fusace Khalil yace "Toh ni ban san komai kan
kudin nan ba, why is he not believing me?" Mami tace "Yanzu me ya kawo maganar
kudin?" Yace "Naje na samesa xan amshi abubuwa na da ya amshe min" Mami tace "Amma
ai na hanaka ko? What are you lacking now without them?" Khalil na girgiza kai yace
"Baxan iya ci gaba da zama bana aiki ba Mami, ya sa anyi sacking dina a inda nake
aiki, to ya bani Cv dina in nemi aikin a wani waje mana?" Mami tace "Idan da ka
saurareni da baka je masa da maganar wani Cv ba Khalil, me kake bukata da baka samu
a yanzu haka? Baka fi wani me aikin samu ba duk da haka? Every month ina tura maka
300k banda wanda kannena ke baka, so me xaka yi da Cv yanzu" a fusace Khalil yace
"Ni neman auren Nadeeyar ma bana son yaje min, xan samu kawu kawai su je" yana
fadin haka ya nufi kofa a fusace, Mami ta buda baki, sai kuma tace "Toh ai mun yi
magana da shi jiya yace next week xai tura representative nasa su je neman auren,
kar ka fara xuwa wajen kowa idan ba ɓacin ransa kake son gani ba" Tuni khalil ya
fice daga parlon. Hajiya Amina ta shigo bangaren Aunty Hassana tace "Aunty Hassana
kin ji abinda Oga yake ce min daxu kuwa?" Aunty Hassana tace "Me yace?" Hajiya
Amina tace "Wai satin da xa a shiga xai tura a nema ma Khalil auren yarinyar nan
dai, ita fatimar ta masa maganan hakan..." Aunty Hassana ta gwalo ido tace "Da
gaske?" Hajiya Amina tace "Wallahi, kafin ya fita yake sanar min" Aunty Hassana
tace "Ai ko bai gaya min ba kuma na shiga gaishesa daxu" Hajiya Amina tace "Toh dai
shine nace bari in zo in sameki" Aunty Hassana tace "Toh bari inyi wanka zan fito
yanzu" Hajiya Amina tace "Toh sai kin fito" Daga haka ta juya ta fita, Aunty
Hassana ta mike da sauri ta dau wayarta ta shiga daki tayi dialing number
aminiyarta, tana dagawa tace "Ke kuma haka ake Chamo daga cewa kina zuwa sai in ji
shiru" Daga daya bangaren aminiyar tata ta kece da dariya tace "Ke dai bari na
shiga rububi ne, ai da ma sai dai ki gan ni yau to kuma sai tafiya Kaduna ya
kamani, ya gida ya su Sajida" Aunty Hassana tace "Lafiya lau, ni baki gaya min
yanda ku yi da mutumin nan kan maganar da muka yi dake ranan ba har yanzu" Chamo
tace "Wallahi yace daga dubu dari tara da hamsin ko biyar baxai sake ragewa ba,
kuma ke ma dai kin shaida aikinsa, ba fa kowa yake ma aiki ba don shi aiki ma yawa
yake masa" Aunty Hassana tace "Shikenan, don wallahi yanzu Amina ta shigo take gaya
min satin da xa a shiga ma xa aje neman auren yarinyar" Chamo tayi wani dariya irin
ta bosawa tace "Wuyarta ba a tura masa kudi an fara aiki ba, ke dai turo kudi kawai
aminiya" Aunty Hassana tace "Toh Sadiya, yanzu kuwa zan saka maki, so nake da kansa
zai birkice masu yace ya fasa bai sonta, kuma dab da xa a kai kudin" Chamo tace "An
gama, sako kudi yanzu" Aunty Hassana ta katse wayar ta tura mata kudin.

ki biya ki karanta cikin salama hankali kwance.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788....


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

43

*This pages is dedicated to Safiyya Usuman uwar Sultan, sauran kuma duk su ci kansu
kandas ba mai ba yaji* 🤓

Umma tace "Ayya inna ai suna can garinsu da ita" a tsorace Inna tace "Garinsu? Ina
ne garin nasu? Buzu ne fa, ba shi da wani gari da ya wuce Nijar, Nijar din ya
kinkimi jikata ya kai kuna gani baku hanasa ba? ta ina zata fara da zafin saharar
su, ga shi ance mana ana ta juye juyen mulki a can yau kwana da kwanaki, ni da
Abubakar muna ta jimami" Umma tace "Aa Inna, garin zaria ya tafi da ita" Inna ta
saki baki, can tace "Kan uba, ku ka bar sa ya tafi da ita wannan garin, ai duk ɗan
kano yafi karfin zama a can, Sannan da xai kai ta can din wani shegen ya bi su a
cikinku??" Umma tace "Haba Inna, ai sun je sun dawo ya fi a kirga, Nihad fa ta sake
fiye da yanda kike tunani Inna" Inna tace "Kai nima dai wallahi da na tsaya nake
biye maki kamar wata er wiwi, maganina ma kenan, matsa ki ban waje wajen Ibrahim na
zo ba wajenki ba, kai kuma Ibrahim wajenka na zo ba wajen Sumayya ba" Abba yace
"Toh ya kike son ince Hajiya? Dama ana zuwa cigiyar wanda kulawarsa da komai nasa
ya fita daga hannun iyayensa? Ai ni tuni na mikata garesa, alaqarsa da ita ya fi
namu yanzu, don haka duk inda ma ya kai ta dai dai ne, ba ruwana, ba ruwanki, ba
ruwan kowa" Inna da ta saki baki tana kallonsa tace "Yau ba lafiya, kace ba ruwanka
Ibrahim?" Yace "Toh hanasa tafiya da ita xan yi?" Umma na murmushi tace "Banda
abunki Inna mata da mijinta ki zo cigiyarta a gidansu, ita da gidan nan kuma ai sai
dai ta kawo mana ziyara, idan aka ganta gidan nan yanzu ai ba lafiya kenan, kuma
wallahi ko sati ba ayi ba sun zo gidan nan da shi sun mana sallama kafin su tafi
Zarian wai garin mamarsa ce, kawai dai ba ku da rabon ganawa ne, amma yace ba
jimawa xa su yi ba za su dawo, suna dawowa kuma da kaina xan je can gidan in dauke
ki in kaiki gidan nasu" Inna tace "Toh wai ni shikenan nuna masa ku ka yi bani da
matsayi ne da tun da aka aura masa ita daga shi har itan babu wanda ya taka yaje
inda nake yace min ci kanki? duk da dai naje Bauchi kwanan nan na dawo" Umma tace
"Au ashe dai kinyi tafiyar dai, to ki dai yi hakuri Inna, sun je ne baki nan, ki
tambayi yan gidan kilan basu gaya maki bane da kika dawo" Inna tace "Kai Ibrahim
fito za mu yi magana" Daga haka ta juya ta nufi kofa tace "Don ban ga xan iya
magana gaban kwaɓeɓiyar nan ba" Abba ya mike ya bi bayanta suka fita, Umma ta bi ta
da harara, can ta ja tsaki tace "A haka dai"
Ranan alhamis Aunty Maryam suka fara shirye shiryen barin Nigeria tare da mai
aikinta da yaranta mata biyu da ke wani boarding school a nan Abuja, duk sai jikin
Nihad yayi sanyi, the present of Aunty Maryam use to make her feel strong, it's
making her move on with life, tana kara samun kwarin gwiwa har ta mance duk wata
damuwar da take ciki and now she is leaving her, Aunty Maryam na lura da sanyin da
Nihad tayi, and she felt really sorry for her, she wish she could do something
about it, she wish xata iya tafiya da ita inda xa ta, daren Thursday Aunty Maryam
ta idar da sallahn da take a sama ta sauko kasa ta karasa sauran kintse kintsen da
bata yi ba a gidan don ranan Asabar za su tafi, har xata koma sama sai kuma ta tafi
ta bude dakin Nihad duk da taga jiya bata yi tashin daren ba da ta leka ta, zaune
ta ganta kan darduma ta hade kai da gwiwa, ta dago kai jin an bude kofar dakin,
Aunty Maryam ta shigo dakin ganin idonta tace "Kukan me kuma kike Nihad?" Wasu
sabbin hawayen suka ciko idonta ta kasa cewa komai, Aunty Maryam tace "Talk to me,
why are you crying?" cikin rawar murya Nihad tace "Aunty you are leaving me... idan
kika tafi kika bar ni i don't have anybody here" tana fadin haka ta fashe da kuka,
Lokaci daya jikin Aunty Maryam yayi sanyi ta dagota ta zaunar da ita gefen gado
tana kallonta cikin sanyin murya tace "Ke da zaki fara makaranta Nihad, sannan
wajen yayata fa za ki zauna, she is also nice, you will like her so much, and
Khalil is also there for you always" kuka kawai Nihad take don tasan idan Aunty
Maryam ta tafi shikenan she might go back to her former self, there will be no one
to encourage her anymore, har ranta bata son gidansu Khalil, she don't think she
can cope staying there, ganin yanda take kuka Aunty Maryam ta jawota jikinta cike
da tausayinta tace "Kiyi hakuri Nihad, bana son kina wannan kukan, ni ma ina son mu
zauna dake kawai bani da yanda xan yi ne, but even with my absence baxa kiyi
lacking komai ba" Kai kawai Nihad ta daga mata hawaye na sauka idonta, Aunty Maryam
tace "Je ki wanke fuskarki ki zo ki kwanta" Tashi tayi a hankali ta tafi bandaki ta
wanke fuskarta ta fito ta hau saman gadon amma wasu hawayen ne ke zuba idonta,
mikewa Aunty Maryam tayi jikinta a sanyaye ta fita daga dakin, ita kanta tasan in
dai ba khalil na gidan ba zaman gidan ba lallai yayi ma Nihad sauki ba, duk excuses
da Mami ta kawo a kan dalilin da baxata riketa ba gaskiya ne, amma saboda babu wani
option yasa Aunty Maryam duk tayi shunning excuses din. Washegari friday tana
dakinta tayi dialing number Khalil, yana fara ring ya daga bayan sun gaisa tace
"Baxa ka dawo weekend ba?" Yace "Ina airport yanzu haka, in sha Allah yau xan dawo"
Aunty Maryam tace "Toh kana sauka ka daure ka fara biyowa ta nan gidana" Yace "Ohk,
hope all is well?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Yaushe ne tafiyar Aunty?" Tace "Gobe
in sha Allah" Yace "Ohk, sai na dawo in sha Allah" Sallama suka yi ta katse wayar,
gaba daya ta kasa sauka gun Nihad don har ranta bata son ganin kukanta. Wajen karfe
biyu zeenah ta shigo wajenta a daki tace "Ummi why is ur visitor crying since
morning?" Aunty Maryam ta kalleta tace "Go and mind ur business please dear" Ta
zaro ido tace "No i was only trying to show concern" Aunty Maryam tace "Je ki kira
min ita" juyawa tayi ta fita daga dakin, Bayan wani lokaci sai ga Nihad ta shigo
parlon Aunty Maryam tana tafiya a sanyaye, bata yarda sun hada ido ba ta zauna
kasan Carpet, Aunty Maryam ta dinga kallon idanuwanta da suka kumbura, can ta sauke
ajiyar zuciya tayi kasa da murya tace "Wajen yayata ne baki son zama Nihad?"
Girgiza mata kai kawai Nihad tayi bata ce komai ba, Aunty Maryam tace "Toh ki gaya
min inda kike son zama" cikin sanyin murya Nihad na wasa da gefen gyalen jikinta
tace "Bani da inda zan zauna" Aunty Maryam tayi shiru tana kallonta cike da
tausayinta, irin wannan yarinya karama haka ace wai an koreta daga gida, why? to
yanxu da ba don Khalil din ya taho da ita ba da ya zata yi kenan, sai da ta shiga
duniya kenan tunda gashi wai dangin mamarta basa nan, what a cruel world we are in,
how comfortable is this her step mum now da tasa aka kori yar teenager haka daga
gida saboda selfish interest dinta, lallai duniya abun tsoro, bayan few seconds
Aunty Maryam tace "Je ki zuba abinci ki ci" Tashi Nihad tayi ta nufi kofa ta fita
daga parlon. Karfe hudu saura Khalil ya shigo gidan ya tarar da Aunty Maryam dake
parlonta a zaune, tayi welcoming dinsa ya zauna sannan ya gaisheta tace "Ya hanya?"
Yace "Alhamdulillah" Kallonta kawai yake yana jiran ya ji kiran da take masa, Ta
sauke ajiyar zuciya tace "Kjay, ina tunanin halin da Nihad xata shiga idan na tafi
na bar ta a kasar nan, she's been crying since 2 days ago, i feel really sorry for,
she is too young to be passing through all this, tana bukatar tausayawa da soyayya
irin ta uwa, ban san yanda xan yi ba...." Kallonta kawai khalil yake, can a hankali
yace "Aunty ba wajen Mami za ki bar ta ba?" Aunty Maryam ta girgiza kai tace "Kai
ma kasan mun banbanta da Mami ta ɓangarori daban-daban, yanda na jawota jiki har ta
sake ta buda min cikinta Mami baxata yi haka ba, sanyinta baxai bari tayi hakan ba,
ko me xa ayi mata a gidan kuma nasan iyaka Mami tace tayi hakuri, toh da wanda ya
dameta zata ji ko da na yan gidanku KJay?" Khalil dake ta sauraronta yace "Toh meye
shawararki Aunty?" Aunty Maryam tace "I am thinking of telling Abu Zeenah sai mu
tafi tare da ita ƙasar da za mu" Khalil was speechless at first, can yayi karfin
halin cewa "Aunty karatun nata fa?" Aunty Maryam tace "Sai a samar mata a can ta
fara" Yayi kasa da murya yace "But i have paid all the fees, kuma kinga ai na kashe
kudi da yawa, ni kuma baxan wani iya bin processes din refund ba" Aunty Maryam tayi
shiru tana kallonsa, ya kwantar da murya yace "Kar ki damu Aunty in sha Allah she
won't be uncomfortable as you are thinking, beside Mimi na gidan, nasan baxata bari
ana ci mata fuska ba, sannan nima next week zan gama abinda nake a can in dawo
Nigeria gaba daya" Aunty Maryam still ta kasa cewa komai but deep down her tausayin
Nihad kawai take ji kawai tana jin da kawai ya bari sun tafi da ita, shi dai
kallonta kawai yake hoping she is convinced, daga karshe tace "Shikenan, Allah yayi
mana me kyau, Allah ya bata ikon kwantar da hankalinta a gidan naku" a hankali
Khalil yace "Ameen" Aunty Maryam tace "Ba komai, ka tafi gida kawai, gobe da safe
za mu hadu a airport" Yace "Allah ya kai mu" har ya tashi tace "And one last thing
xan bata waya, kar kuma kace zaka amshe, kawai dai ka sa mata ido wajen ganin da su
wa da su wa take communicating" Yayi shiru yana kallonta, tace "Sannan na ba Ayman
layin da na sa mata a wayar da xan bar mata" Shi dai Khalil kallonta kawai yake,
tace "Ka ji abinda nace?" Yace "Na ji" tace "Sai anjima" juyawa yayi ya fita daga
parlon nata. Khalil na sauka downstairs ganin Zeenah a parlor yace "Ina Moon?" Tace
"She is sleeping upstairs" Yace "Ohk, ya preparation din tafiya?" Tace "Mun gama
tun jiya" yace "Good" Ya fi minti biyar tsaye a parlon, daga karshe kawai ya fita
compound, nan gidan ya bar motarsa don akwai wani abokinsa a layin da xa su je wani
wajen tare yanzu. Washegari da safe Khalil ya nufi airport tare da Mami da Mimi
with Noor, Aunty Maryam ta tafi da motarta da yaranta uku da mai aikinta da Nihad,
don tun da taga motar khalil a gidanta ta sanar masa xata taho da motarta airport
sai ya maido mata gida ya dau nasa, Noor kuma tayi driving dinsu Mami su koma gida,
har suka isa Airport Nihad bata daina kukan da take ba, she felt everything is over
for her, it's just like they are sending her away from home for the second time,
she felt insecure without Aunty Maryam, she won't have anyone to confide in
anymore, bayan Aunty Maryam ta isa airport din tayi parking, har ma ta daina ba
Nihad baki ganin ba sauraronta take ba, ta dau waya ta kira khalil, ya sanar mata
sun kusa isowa, tana ta jira har ya shigo airport din with escort, murmushi tayi
don tasan babu abinda ya tsana kamar wannan escort din, kawai dai babu yanda xai yi
don escort din na Mami ne sae in ita tace masu bata bukata, wannan kuma sai in ba
waje me nisa xa ta ba, tuni aka masu providing wajen parking babu 6ata lokaci,
bayan few minutes Mami da su Mimi suka sauko daga motar, Aunty Maryam ma ta sauka
ta tafi ta gaida Mami, yaranta ma duk suka sauka xuwa wajen, Noor ta rungume Aunty
Maryam tace "Ohh i feel like crying Aunty, xa mu yi missing dinki sosai" Mimi ma ta
marairaice tace "Me too Aunty" Mami na murmushi tace "Toh ba sai ku tafi gaba daya
ba" Noor tayi dariya tace "We wish" Nan mai aikin Aunty Maryam ta durkusa ta gaida
Mami, Mami ta amsa tace "Murja sai Uk ko?" Murmushi tayi tace "Za mu yi kewanku
Mami" Mami tace "Toh Allah ya tsare, Allah ya kai ku lafiya" Nihad bata yarda ta
sauka daga motar ba ta hade kai da gwiwa tana shesshekan kuka, Aunty Maryam bata yi
forcing dinta ta sauko ba cause she feel sad seeing her cry that way, Mami tace
"Toh ina yarinyar?" Aunty Maryam ta ɗan yi murmushi tace "Kuka take a motar shi sa
ma ban bari ta sauko ba" Mami tace "Kuka kuma? Kukan me?" Aunty Maryam tace "Sabo
mana Mami" Mami tace "Allah sarki" Tuni aka sauke kayansu zuwa cikin airport din,
Khalil dai na tsaye ya jingina da motarsa ya rungume hannu, lkci lkci yake kallon
motar Aunty Maryam, Sai da xa su shiga cikin airport din bayan sun yi sallamar
karshe da su Mami Aunty Maryam ta koma gun motarta ta bude back seat ta dafa
shoulder din Nihad a hankali tace "Be a good girl dear, Allah ya tsare ki, Allah
kuma yayi maki albarka, in sha Allah xa mu dinga waya sosai duk abinda ya dameki
kar ki boye min ki dinga gaya min kin ji, kuma kar ki fasa addu'a da tashin daren
da kike kamar yanda kika saba in sha Allah xaki ga sakayya cikin gaggawa, sannan ki
dinga daukan kiran mutumin da na ba numberki banda walakanci my dear, he is a good
guy, and u will enjoy communicating with him" Nihad ta kasa ce mata komai sai kuka
take, Aunty
Maryam ta juya cike da karfin hali ta bar wajen duk Khalil na kallonsu, Ta mika
masa makullin motarta yace "Allah ya tsare Aunty" Ta gyada masa kai ta nufi cikin
airport din su Mami na daga masu hannu, Khalil ya mika ma Noor makullin motar Mami
dake wajensa, Ta amsa tace "Till we meet home yayanmu" Juyawa yayi ya nufi motar
Aunty Maryam ya bude driver seat ya shiga ya tada motar, ya riga su Noor fita daga
airport din, har sannan Nihad bata daina kukan da take ba kamar ranta zai fita, shi
ma kuma bai ce mata komai ba, har ya isa gidan Aunty Maryam, bayan an bude masa
gate ya shiga yayi parking motar a parking space, Nihad ta kasa dago kanta, ya
sauka daga motar ya jingina jiki, bayan few minutes ganin ba bude motar xata yi ta
sauko ba ya bude mata, da kyar ta sauko daga motar xata bar wajen tana harde kafa
tana kokarin danne kukan da ya taho mata taji ya jawota kusa da shi, lkci daya ta
fashe da kukan ta rufe fuskarta a jikinsa, drawing her more closer to himself yayi
kasa da murya yace "Da kin bi ta ai" Ya bar ta ta ci kukanta bai hanata ba, har ta
gaji tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta rufe ido tana shaƙar daddadan
kamshin jikinsa, tana kuma jin yanda zuciyarsa ke bugawa. They stood in that way
for almost 5 minutes, lokaci daya yaji ta sakar masa duk jikinta, yayi saurin
rungumeta sosai kar ta zame kasa, he could feel her breathing calmly, kamar kuma
warce aka tsikara ta bude ido da sauri ta janye jikinta shi ma yayi saurin saketa,
ta koma gefe tana murza ido, shi kuma yayi keeping straight face.... she is so
sleepy don jiya ba wani baccin kirki da tayi, ya ciro makullin motarsa ya bude tasa
motar, ya shiga yana warming dinsa tana kallonsa tace "Kayana" Ya daga kai ya
kalleta, ta koma gun motar Aunty Maryam ya bude booth din da makullin, ta ciro
jakunkuna biyu, daya na wasu kaya da Aunty Maryam tayi mata, daya kuma wanda ya
siya mata, ta zuba kayan a booth dinsa ta kulle sannan ta shiga back seat, bayan ya
gama warming motar suka bar gidan, Nihad ta ɗan shinshina Hijab din jikinta jin
kamshin dake tashi a jiki, a hankali ta kwanta jikin motar ta lumshe idonta, har
suka isa gidansu bata sani ba tana bacci, bayan yayi parking ya kashe motar ya
sauka still Nihad bata farka ba, ya bude back seat din yana kallonta, patting din
kujeran motar yayi still bata bude ido ba, sai kuma ya kai hannu jikinta yana
tashinta, sae a sannan ta bude ido da sauri tana bin inda suke da kallo, ganin
compound din jikinta yayi sanyi, ya zaga ya bude booth ya fiddo jakunkunanta, ta
sauko daga motar tana kallon securities din bakin gate din, ya kulle motar yana
rike da jakunkunan nata biyu ya fara tafiya, ta bi bayansa tana jan kafa tayi kalan
tausayi da fuskartar, ta inda ya shigo da ita gidan ranan farko da suka zo ya bi da
ita yanzu ma, har suka isa bangaren Mami, ya kai mata kayanta guess room dake
bangaren, tana tsaye bakin kofar har ya karaso ya shiga parlon Mami sannan ta bi
bayansa, Mimi ce kadai zaune parlon, Mami kuma na bedroom dinta, ya zauna saman
kujera Nihad dai ta koma gefe ta tsaya, kana ganinta kasan she isn't happy being
here, ya ɗan hade rai ya nuna mata kujera, ta sauke kanta kasa ta zauna saman
kujeran, Mimi na kallonta tace "Hi" Nihad ta daga kai ta kalleta, Mimi na murmushi
tace "I am Mardiyya, and you?" Nihad dai sai kallonta take jin yanda tayi
pronouncing R din sunan alamar dae bata cikakken R 😜, Khalil ya juya ya kalli Nihad
jin tayi shiru, Nihad ta kalli Mimi tana ɗan murmushi tace "I am Nihad" Mimi ta
wara ido tace "Waow, You have a nice name, ina da wata fwend with ur name" Khalil
na kallon Mimi yace "Hey take her to the guess room ta kwanta, she is sleepy" tashi
Mimi tayi tace "Ohk mu je" Nihad ta tashi tana kallonsa, sai kuma ta bi bayan Mimi
har zuwa dakin, babba ne dakin sosai sai kace ba guess room ba, furnitures din
dakin ma kadai abun kallo ne, sannan ga bandaki shi ma babba a ciki, har da kayan
kallo akwai a dakin, Yanda aka gyara dakin kuwa ga zanin gado sai sheki yake kai
kace akwai mutum a ciki ne, Mimi tace "An wriga an gyara dakin yau, so za ki iya
kwanciyarki" Nihad tayi murmushi cause her intonation and most especially how she
pronounces her letter R is very funny to her, can dai tace "Thank you" daga haka ta
kwanta saman gadon, Mimi ta juya ta fita, nan da nan bacci ya dauke Nihad... After
sleeping for many hours ta bude ido a hankali, tsaye ta ga Khalil a dakin yana jera
mata kayanta a press din dake dakin, Kallonsa take kawai don bai san ta tashi ba,
duk Abayas din ya jera su waje daya, haka Hijab da atamfofi da Aunty Maryam tayi
mata kusan kala takwas, tana ganin xai ta6a inner wears dinta ta sauko daga kan
gadon da sauri ta turo baki tace "Ka bar min xan yi kayana da kaina" ya juya ya ɗan
kalleta, sai kuma ya kwashi duk inners din ya mayar da su cikin jakar ya koma gefe
ya tsaya yana kallonta, taki Kallonsa, a takaice tace "I need space" Daga sama har
kasa ya kalleta sai kuma ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita daga
dakin, duk sai da tayi seperating inners din nata, sannan ta koma ta kwanta tayi
lamo saman gadon tana tunanin Mumy.

I really appreciate ur patronage lovely fans, Allah ya biya maku bukatun alkhairi,
ya saka ma iyayenku da gidan aljanna.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

And you show ur evidence via


07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

45

Da daddare Mimi na parlon Mami tana ta danna wayarta bayan sun gama cin abinci da
Nihad, kallo daya zaka ma Nihad ka gane she is moody, gaba daya she is
uncomfortable da zaman gidan, Noor ta shigo parlon tana kallon Mimi tace "Hey Madam
Dad yana kiranki..." Mimi tace "Ohk" Daga haka ta mike ta kalli Nihad tace "I am
coming" Nihad ta gyada mata kai, ta nufi kofa Noor na biye da ita, Nihad ta bi su
da kallo, a hankali ta kwantar da kanta jikin kujera tana jin kewar nata Abban,
bayan sun fita Noor na kallon Mimi tace "I don't like her" Mimi ta buda ido tace
"Why?" Noor tace "Baki ga wani kallo da take ma mutane ba, beside bata iya gaisuwa
ba sai bin mutum da ido, who does that" Mimi tayi murmushi tace "But she is nice,
kawai bata son magana ne" Noor tace "Toh wa xata nuna ma rashin son magana, what's
even the reason of her staying here? Na zata kwana biyu xata yi ta wuce" Mimi ta
buda hannu bata ce komai ba tana ci gaba da tafiya. Mikewa Nihad tayi daga karshe
ta nufi kofa xata bar parlon, kafin ta bude kofar aka riga ta budewa, suna hada ido
ta koma gefe without looking at him tana jiran ya wuce, ya shigo yana kallonta,
tayi ficewarta ta bar wajen ba tare da ta kallesa ba, ya bi ta da kallo... Nihad ta
shiga dakin da take ta dau wayar da ya bata daxu, maganganunsa ne suka dinga dawo
mata, ta tabe baki, kawai advice din Mimi ta dauka banda haka da tace masa to ya
saketa din mana what is he even waiting for, though it's better that she kept
silent, miss call ta gani da foreign number, ta dinga kallon number, xata mayar da
wayar ta ajiye sai ga wani kiran da same number, dagawa tayi ta kai kunne tayi
shiru, sallama taji ya mata da accent dinsa na larabci, ta amsa yace "Is this Nihad
pls?" Tace "Who am i speaking to?" Yace "I am Ayman Fadlullah, i got ur digit from
Ukhti Maryam" Nihad tace "Ohk" Yace "So how are you?" Tace "I am fine" Yace "Can we
chat on WhatsApp plss?" Tace "Ohk" Yace "Thank you, i appreciate" Daga haka ya
katse wayar, ita bata ma san ko da WhatsApp a wayar ba, ta dai shiga ta duba taga
an ma bude WhatsApp din da number, but ba a fara chatting ba, sai shi kadai da yayi
mata sallama few hours ago, tayi replying sallaman, with pure English ya shiga yi
mata introducing kansa as the first son to his parent, yana da kanni maza biyu, sai
autansu mace, ya kara mata da cewa he is from Yemen but now resides in America inda
yayi studying Accounting... Ita dai Nihad karanta chat din nasa kawai take bata
cewa komai, har ta mance rabonta da chatting almost 5 weeks now, ganin she is not
replying yace "Are you der Nihad?" Tace "Yeah... " Yace "Ohk good, tell me more
abou you" Kamar dai baxata ce komai ba sai kuma tayi masa introducing kanta a
takaice a chatting din, yace "Waow, that's nice... I will be flying to Nigeria soon
to meet with you in sha Allah, i have already beginning to feel comfortable with
you" duk hiran yawanci shi yake yi, sai dai tayi masa reply da ok ko kuma tayi
shiru har sai ya tambayeta is she there, and she noticed he is jovial and very
friendly sannan wayayye ne sosai, he chatted her for almost an hour, babu abinda ya
boye mata game da kansa, ya tura mata hotansa da iyayensa with his siblings, ta
gansu kyawawan larabawa kamar su suka yi kansu, da yayi requesting ta tura masa
nata hoton bata ta6a fuskantar low self esteem a kanta ba sai yan kwanakin nan da
suka gabata, da kuma yanzu da Ayman ya bukaci hotonta, jin bata ce komai ba yace
"Nihad" ajiye wayar tayi ta koma a hankali ta kwanta, bayan kusan minti sha biyar
sai ga wayar ya fara ring daukan wayar tayi tana kallon screen din, sai kuma ta
daga ta kai kunne tayi shiru, yace "Did i hurt you in anyway pls?" Tace "Not at
all" Yace "Ohk sorry about me asking of ur picture" Tace "Ohk" Ya ɗan yi shiru sai
kuma yace "I won't be asking u anymore" Tace "Good" Hiransa kawai ya ci gaba da yi
mata, ta kalli agogo dake nuna sha daya da wani abu tace "I will be going to bed
now" Nan yayi mata sallama ya kuma yi mata godiyan basa lokacinta da tayi, ta jira
har ya katse wayar sannan ta kwanta ta lumshe ido, nan da nan bacci ya dauketa.
Washegari da safe Mimi na dakinta ta fito wanka tana shiryawa gaban mirror aka yi
Knocking kofar dakin tare da budewa, ta daga kai tana kallon kofar ya shigo tace
"Yayanmu ina kwana?" Yace "Cool, are you having lectures today?" Tace "Yeah, yau
muka yi resuming ai" Yace "Good, Nile ne makarantar naki ko Baze?" Tayi er dariya
tace "Yanzu yaya har ka mance makarantar da nake, to su Noor ke zuwa Baze, but i
and Farhana NUN ne" Yace "Ohk i now remember, did you have idea on when Jamb is
commencing this year?" Mimi tace "Registration is still on progress, an kusa zana
jamb din ma ai" Yace "Good, that girl... Ta samu admission a makarantar ku but she
have to present her jamb result, don haka you take her with u zuwa center din da ku
ka yi jamb registration tayi register" Mimi tace "Ohk, but that will be after my
today's lectures right? May be around 2" Yace "Ohk, ku tafi makarantar da ita
kawai" Mimi tace "Ohk then" yace "But do not tell Mami about the jamb registration,
xan baki admission letter dinta kiyi mata presenting kice zaku tafi makaranta da
ita kawai shikenan" Mimi tace "Ohk" Juyawa yayi ya fita daga dakin, Bayan Mimi ta
gama shiryawa ta tafi can dakin da Nihad take, ta tarar ita ma tayi wankan har ta
shirya tana zaune gefen gado tayi shiru, yau din ma she is moody, gaba daya taji
bata son zaman gidan nan, she isn't comfortable, Mimi na kallonta tace "Good
morning Neehad, yayanmu yace za mu je kiyi registering jamb yau, so xa mu fara zuwa
school cause ina da lectures, after my lectures sai mu je wajen" Nihad na kallonta
tace "Ohk"Juyawa Mimi tayi ta fita. A parlon Mami suka yi breakfast, daga nan Mimi
ta sanar ma Mami tare za su tafi makaranta da Nihad, Mami tace "Wani makarantar ne
nata?" Mimi tace "Makarantar mu daya" Mami tace "Really?" Mimi tace "Yeah, this is
her admission letter" Mami tace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Mimi ta fito tare da
Nihad daga parlon Mami suka kusa cin karo da khaleel, daga sama har kasa yake
kallon Nihad that's putting on veil, though ba karami bane, don yawanci duk medium
veils Aunty Maryam ta siya mata ba irin wanda ta saba sa wa a gida ba, Mimi tace
"Za mu tafi yayanmu" Yace "Ohk" Nihad ta wucesa, Mimi na biye da ita ya bi su da
kallo har sai da suka yi nisa yayi saurin cewa "Hey Mimi" Mimi ta juyo tana
kallonsa, Nihad dai tsayawa kawai tayi bata juyo ba, shima abinda yasa ta tsaya
bata son tafiya zuwa main parlor din ita kadai ne, ya nufesu har ya isa inda suke
yana kallon Mimi yace "Erm sorry wayana zaki dauko min a dakina" Mimi tace "Ohk" Ta
mika ma Nihad laptop dinta dake hannunta tace "Rike min pls" Nihad ta amsa, Mimi ta
juya ta bar wajen, yana ta tsaye har ya daina hango Mimi, Nihad dai ta hade rai
tayi backing dinsa taki juyowa, ya zaga ya tsaya a gabanta fuska daure yace "Baki
da hankali ne zaki fita da gyale?" Bata san sanda tace "Saboda me baxan fita da
gyale ba???" Yana kallonta da kyau yace "Saboda dama ke kina da baƙin taɓon da duk
inda kika shiga dole xa a ganeki sai dai wanda bai san labarinki ba" Shiru Nihad
tayi tana kallonsa babu ko kiftawa, lkci daya zaka iya ganin yanda jikinta yayi
sanyi, ya buda hannu yace "So however u wish to dress is ur business not mine, kuma
naga ai har nikab da hijabs Aunty Maryam ta sa maki a kayanki, but saboda ke kin
saba tallan jikinki baxa ki iya sa su ba, to nan ba inda zaki yi abinda kika ga
dama babu me sa maki ido bane" Ta sauke Idonta daga kallonsa tace "My dressing, my
choice!!!" Tana fadin haka ta kara juya masa baya, Kallonta yake ko kiftawa babu, a
haka Mimi ta dawo ya nufeta da sauri ya amshi wayarsa yace "Thank you" daga haka ya
juya ya tafi parlon Mami, Mimi xata amshi laptop dinta Nihad ta ɗan kirkiro mata
murmushi tace "I will hold it for u" Mimi tace "Oh thank you" a haka suka ci gaba
da tafiya, luckily babu kowa parlon har suka fita compound, tuni wanda zai kai Mimi
makaranta ya taso, ta fara shiga bayan motar sannan Nihad ma ta shiga, ya tada
motar ganin Nihad bata kulle motar ba Mimi tace "The door Nihad" Nihad ta kalleta
sai kuma a hankali tace "Plss baxan bata maki lokaci ba idan na koma ciki for just
some minutes?" Mimi tace "Mantuwa kika yi?" Nihad ta sauke idonta daga kallonta
tace "I am not comfortable with my dressing" Da mamaki Mimi ta dinga kallonta daga
sama har kasa tace "What's wrong with it? But you look smart dear, there is nothing
wrong with you dressing, or is the veil too big?" Nihad ta ɗan yi murmushi tace "I
will prefer i change" Mimi tace "Ohk then, xa mu jira ki" Sauka tayi daga motar ta
koma cikin gidan. Da sauri ta wuce main parlor ta haura Upstairs har zuwa bangaren
Mami sannan ta shiga dakin da take, she is just changing because kamar yanda ya
fada xa a iya ganinta a ganeta amma ba don wai ya mata magana ba, hijab dinta ta
dauka har kasa ta saka sannan ta dau nikab ta daura, baka ganin komai sai fararen
hannunta da manyan idanuwanta with long lashes ta cikin nikab din, dama kuma Aunty
Maryam tace mata ta dinga yawan saka Nikab in xata fita, tana fitowa ta sauko main
parlor da sauri, Aunty Hassana da ke kokarin haurawa sama ta dayan stairs din ta bi
ta da kallo, tadai san duk gidan babu me saka Nikab, sai kuma tace "Keee" Da sauri
Nihad ta juya amma bata tsaya ba, Aunty Hassana ta sauko daga matakala biyun da ta
hau ta nufota, hakan yasa Nihad ta tsaya gabanta na faduwa tana kallonta, Aunty
Hassana ta isa har gabanta ta fizge Nikab din tace "Ke wa ya kawo ki gidan nan?"
Nihad ta sunkuyar da kanta, a fusace Aunty Hassana tace "Baki jin ina maki magana
ne" cike da karfin hali Nihad tace "Karatu nake yi" da mamaki Aunty Hassana tace
"Karatu a ina? Wa ya kawoki kiyi karatu? Ke yar uwarsu Maman Mimi ce?" Nihad ta
daga kai da kyar alamar eh, Aunty Hassana ta dinga kallonta daga sama har kasa,
Mimi ce ta shigo parlon jin shiru shiru Nihad bata fito ba, Mimi na kallon Aunty
Hassana tace "Good morning
Aunt" Aunty Hassana tace "Wace makarantar take?" Mimi tace "Makarantar mu daya?"
Aunty Hassana tayi shiru tana nazarin anya ba yayanta bane aka daura ma biyan kudin
makarantar? Anya ba kawota gidan aka yi don yayanta ya dinga biya mata kudin
makaranta ba, Aunty Hassana tayi mitsi mitsi da ido tace "Daga wani garin take?"
Mimi ta buda hannu tace "Nima ban sani ba Aunty, Mami ce ta sani" Aunty Hassana
tace "Ke baki ta6a saninta a er uwarku ba?" Mimi tace "Yan uwanmu suna da yawa wa
enda ban sani ba, so she might be among them" Aunty Hassana ta gama nazare
nazarenta sannan ta kara kallon Nihad ta juya ta bar wajen, Mimi ta kama hannun
Nihad suka fice daga parlon. The day was so hectic for Nihad don ta mance rabon da
ta fita, NUN ya wuce yanda take tunaninsa, and it has always been one of her dream
school don shi ta gaya ma Abba tana so amma yace Abuja yayi nisa sai yayi
suggesting mata Maryam Abatcha and yayi assuring dinta she will like the school,
though babu wanda ya san sunyi hakan, amma sai da taje ta gaya ma Umma which she is
regretting right now, sai gashi yau she is going to be a student of her dream
university amma kuma bata farin ciki da hakan, Ayman really whiled away her time a
makarantar kafin Mimi ta gama lectures, sun dade suna magana da shi a waya tun bata
son amsawa har dai ta fara amsa masa, shi ma saboda teasing dinta da yake ne sai
tace sai ta rama, and she really enjoyed conversing with him caused he is so
friendly and jovial, still tana makarantar Aunty Maryam ma ta kirata, sun kusa
minti sha biyar suna waya, Aunty Maryam ta kara jaddada mata kada dai tace xata ma
Ayman walakanci ta basa chance baxa kuma tayi da na sanin hakan ba, Nihad tace "Toh
nagode Aunty" Daga haka Aunty Maryam tayi mata sallama, Nihad tace "A gaida min
Mus'ab" Aunty Maryam tace "In sha Allah" Daga haka ta katse wayar. Sai bayan
la'asar suka koma gida, tun da drivern motar yayi parking a parking space Khalil
dake zaune karkashin wasu bishiyu da suka kawata makeken compound din yake kallon
motar, Mimi ta sauka daga motar ta nufesa tana murmushi tace "Yayanmu good evening"
Yace "How are you" tace "Alhmdlh, we are done with the registration, nan da sati
biyu ne exam din ma ashe" Khalil yace "Ohk..." Juyawa tayi tace "Let me go in and
take a shower" Daga haka ta juya taga har Nihad ta isa entrance din shiga cikin
gidan, ta bi bayanta da sauri. Sai da suka fara shiga parlon Mami su gaisheta,
kallo daya Nihad tayi ma Nadeeyah dake zaune parlon da Noor, ta dauke kai ta juya
ta fita daga parlon, Nadeeyah ta kalli Noor da mamaki tace "Who is she?" Noor was
speechless and astonished, ke baki yi sallama ba, kin shigo kin tadda mutane a
parlor ba gaisuwa ba komai kin masu kallon tara saura quarter kin juya kin fita,
Mimi ta sauke ajiyar xuciya tace "She is tired, yanzu muka dawo, it's an
hectic...." Noor ta daka mata wani tsawa ta dakatar da ita tace "Pls get lost, ke
da kika shigo baki yi mana sallama ba? Ko baki gaishemu ba? How dare she? Who did
she think she is?" Mimi dai bata sake cewa komai ba, Noor ta ci gaba da jaraba
kamar xata ari baki, Nadeeyah ta sauke ajiyar xuciya tace "Calm down Noor, kilan
kamar yanda Mimi ta fada ta gaji ne, so kiyi mata uzuri...." A fusace Noor tace
"Baxan yi ba, kuma wallahi na sake ganin ta shigo inda nake tayi repeating nonsense
din nan da tayi i won't take it likely with her" Mimi dai ta karasa ta leka bedroom
din Mami, ganin bata cikii ta juya ta bar masu parlon, Noor was still fuming with
rage, Nadeeyah tace "Easy pls Noor, ya riga ya wuce ko? Stop the nagging pls" Noor
tace "Nahhh bai wuce ba, i could slap her if she should repeat such kuma ba abinda
xai faru" Nadeeyah tace "But who is she? Ranan na ganta gidan Aunty Maryam" Noor
tace "How will i even know who she is, ni ban ma damu insan wacece ba tunda ba
gabana take ba, i hate nonsense, na dai ji Aunty Maryam na ce ma Mami ai gidan
iyayenta Yaya Khalil ya zauna when he was in kano, they were kind to him, they did
that, they did this, bla bla bla, ita kuma tana so ta fara karatu ba a son ta zauna
hostel, shine wai zata zauna nan gidanmu, cause at first Mami bata amince da
zamanta a nan ba, but Aunty Maryam insisted, ta dinga kawo silly backups har sai da
tayi forcing Mami yarinyar ta zauna gidan nan" Kallonta kawai Nadeeyah take babu ko
kiftawa, can tayi karfin halin cewa "But who brought her here?" Noor ta karyar da
kai tace "We saw her a day after yayanmu came back, which means tare kenan suka zo
gidan, yes tare ma suka zo" Nadeeyah ta hadiye abu da kyar tace "Tare??" Noor tace
"Yeah, and you know what?" Nadeeyah ta girgiza kai, Noor tace "You remember the
video of a lady with undies that went viral last month?" Nadeeyah tayi shiru, Noor
tace "Wani video that's all over social media na wata yarinya babu kaya jikinta?"
Nadeeyah tace "Yeah, i heard about the video amma i didn't bother watching, so ban
ta6a gani ba" Noor tace "Toh yarinyar ce" Nadeeyah ta zaro ido with surprise tace
"Wace yarinya?" Noor tace "Yar rainin wayon da ta fita yanzu, ita ce a video din
sure" Buda baki Nadeeyah tayi tace "Wai da gaske?" Noor tace "I mean it, bani da
video din da na nuna maki, su Sajidah da Hanan ne ke da shi a waya" Nadeeyah was
over shock, tayi karfin halin cewa "Kuma gidansu Kjay ya zauna a kano?" Noor tace
"Yes, she was once a student of Maryam Abatcha" Nadeeyah ta sauke ajiyar xuciya
tace "Toh Allah ya kiyaye" Noor tace "Waow its been long i hala this way, har kaina
ya fara ciwo wallahi, shi sa bana son magana da yawa amma wannan yar kauyen ta sa
ni magana, As i was saying...." Nan ta ci gaba da ba Nadeeyah labarin da take bata
cikin nutsuwa irin na big babes, but gaba daya Nadeeyah was absentminded, Nihad ta
tsaya mata a rai sosai, abinda ta mata ranan da suka hadu gidan Aunty Maryam ya
fado mata, ita kuma a ranan bata dauka as komai ba, sai yanzu brain dinta ya
tunatar da ita cewa warce suka hadu a mall a can kano ce fa da Kjay, mamaki da
fargaba ya cikata, but why did he have to bring her all the way from kano to his
parent house, sannan even for once bai ta6a ce mata tare suka dawo ba gashi yau
satinsu uku, Noor dake ta magana ta lura gaba daya hankalin Nadeeyah baya wajen ta
kai hannunta fuskarta tana waving, da sauri Nadeeyah tayi blinking idonta, Noor
tace "What are you thinking of?" Nadeeyah bata ce komai ba amma kana ganinta kasan
there is something bothering her, she looks so disturbed, Noor ta kamo hannunta
tace "Tell me plss, me ya faru" Lkci daya Nadeeyah taji hawaye ya kawo idonta ɗon
saurin kuka ke gareta, tana kokarin ganin bata fashe da kuka ba tace "He neva told
me he came all the way from kano with her, even for once bai gaya min ba" Noor ta
zaro ido tace "Ohh that? Meye abun damuwa a nan bayan dai kinsan aurenki zai yi? In
3 days time fa xa a kai kudin aurenku da shi, and baxa a sa ya wuce sati biyar ba,
so why bother ur self about one filthy lady that's all over social media half
naked? ke sai kace baki san halin KJay ba? Ba abinda ya hada sa da yarinyar banda
gidansu da ya zauna don ni tunda ta dawo gidan nan ma ko magana bana ganin yana
hadasa da ita, you know he have class" Nadeeyah ta sauke ajiyar zuciya bata dai ce
komai ba tana share idonta, Noor tace "C'mon chill plss, wannan bata kai ta sa ki
shiga damuwa ba har ki zubda hawayenki a banza, me xai yi da ita? Da akwai wani abu
tsakaninsu ma ai baxai fara kawota gidan nan ba, kuma saboda mugun abinda tayi shi
yasa ma ba a son ta zauna hostel may be parent dinta suka yi requesting ta zauna a
nan, shi sa ma kika ganta a nan" Nadeeyah ta gyada mata kai kawai, Noor ta ci gaba
yi mata hiran da take mata a nutse..... Har karfe biyar khalil na zaune inda yake a
cikin compound din yana danna waya, so yake ya maida Nadeeyah gida kafin ya je inda
yake son zuwa, wayarsa dake hannunsa ya fara ring, ya dinga kallon number wanda ke
kiransa, ya dai yi picking daga karshe yakai kunne, bayan sun gaisa Farooq yace
"Dama wani aiki ne ya shigo da ni Abuja yau, so gobe da safe in sha Allah xan koma
kd, shine nake son inji wani wajen ku ke a Abujan?" Khalil ya sauke idonsa yace
"Ohk, maa sha Allah, goben za ka zo kenan?" Farooq yace "No, na gama abinda nake yi
yanzu, goben da sassafe nake son tafiya" at first khalil ya rasa abinda xai ce
masa, Farooq yace "Hello" Khalil yace "Eh ina jin ka, xan tura maka address din
yanzu" Farooq yace "Toh ina jira" Daga haka ya katse wayar, Daga nisa ya dinga
kallon Nadeeyah har ta iso inda yake, ta dauke kai tace "Xan tafi gida" Ganin mood
din ta yace "What happened Nady? Are you okay?" Ta ki ce masa komai, ya mike yana
kallonta, lokaci daya hawaye ya cika idonta, da damuwa yace "Talk to me plss, me ya
faru?" Cikin rawan murya tace "But you neva told me ba kai kadai ka dawo Abuja ba"
Yace "Shit... Toh menene tsakanina da warce na dawo da? There is nothing Nady kawai
karatu ta zo yi a garin nan, and she have no where to stay shine take zaune gidan
nan, bayan nan babu wani abu kuma trust me" Ta goge Idonta tace "Naji, I want to go
home" yace "Noo, not in this manner pls, but ta maki wani abu ne?" Nadeeyah tace
"Kawai shigowa tayi ta hararemu ta fita babu sallama balle gaisuwa" Khalil yayi
wani sigh yace "But you guys shouldn't have taken it personal, she is a
sociopath...." Nadeeyah ta tabe baki dai bata ce komai ba, khalil ya kalli wayarsa
dake ring da sauri, ganin Farooq ne ya daga yace "Ina tura maka ne" Farooq yace
"Ohk" Daga haka ya katse wayar, Khalil yace "Look Ki koma ciki yanzu, i will be
having a visitor immediately, idan ya tafi sai muje ki sha ice cream sannan in
maida ki gida" Murmushi kawai tayi ta juya ta fara tafiya, yea dama murmushin kawai
yake son yaga ta yi which means komai ya wuce kenan, ya sauke ajiyar zuciya ya
zauna ya shiga sending ma Farooq address.....

*Nihad* is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence of payment via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

47

Mikewa Khalil yayi ya tafi har bakin kofa ya tsaya ya rungume hannu yana kallon
yanda take kuka, calmly yace "In da gaske kina son bin sa me yasa tun zuwansa baki
ce masa xaki bi sa ba kika zo nan kina min kukan munafurci, tunda kinsan tafiya zai
yi ba nan zai kwana ba" Nihad ta hadiye kukan da take ta daga kai tana kallonsa
fuska daure, can ta mike tsaye tace "Ina ruwanka da ni? Kaga dai ba ruwana da kai a
gidan nan, don yayana yace in daina kulaka duk abinda xaka min, kuma ni dai naji
maganarsa, don haka kai ma ka fita harkata because bana son inyi disobeying yayana,
idan baxa ka iya cewa inyi hakuri ba dole sai ka min maganan" ta karasa maganar
kamar xata fashe da sabon kuka, kallon bakinta kawai yake, can yace "Ohk yace ki
daina kulani kenan?" Tace "Ehh, kuma ko kana daga min shoulder dinka baxan san kana
yi ba tunda ba ruwana da kai, I will pretend I don't know" Tana kai wa nan ta
nufosa fuska daure tace "Ka matsa min ni in fita" ita haushinta maimakon yace tayi
hakuri shine yake neman tsokanarta kuma, Yace "Aa bari dai a baki kudin mota ki bi
sa kawai, ai yana nan Abuja bai yi nisa ba" Wani kallo ta dinga masa, ya sa hannu
cikin aljihun 3 quarter din jikinsa ya ciro 100 dollar ya mika mata yana kallonta,
ta dinga kallon kudin sai kuma ta kwace ta cukuikuye ta jefar kasa, tana kallonsa
da kyau tace "Kudin da ba naka ba" Kallonta ya tsaya yi baki bude, can yace "Kinsan
hukunci warce ke ma namiji rashin kunya, namijin ma wanda aka aura mata daga
gidansu?" Ta wani kallesa tace "Ohh dama kai mijina ne? Ai ban san ina da miji ba,
kuma ai shi namiji baya neman tsokanar mace" Jin yayi shiru bai ce mata komai ba ta
dauke kai ta turo baki, a hankali ya kai hannu ya kashe switch din dakin ta juya da
sauri ganin duhu ya gauraye ko ina sai ɗan hasken screen din Iphone dinsa da ya
ajiye saman gado, taji kuma yana sa makulli a kofa, komawa baya tayi a tsorace tana
zaro ido tace "Meye haka kake yi?" Ba abinda ta ji yace mata, Ganin he is advancing
toward her ta fara komawa baya da sauri cikin rikicewa tana cewa "Wayyo don girman
Allah kayi hakuri, duk abinda na fada ba da kai nake ba don Allah kayi hakuri, dama
yayana yace in daina maka rashin kunya kuma na daina tun...." Wani kara tayi a
tsorace jin saura kadan ta fada saman gado don bata san har ta iso wajen gadon ba,
zata tashi da sauri ya mayar da ita ta fada kan gadon, zaro ido tayi a mugun
tsorace ganin he just lied directly on her, cikin rawan murya ko ina na jikinta na
ɓari tace "Don girman Allah kayi hakuri, wallahi baxan sake maka rashin kunya ba
har abada, kaji na rantse..." Gaba daya ta gigice tana kokarin turasa amma ta kasa,
cause his weight is out of the world, nan kuma ba duk weight din nasa ya sakar mata
ba, ta fashe masa da kuka tana sauke numfashi da kyar ga kamshinsa da ya cika ko
wani breathing dinta, yayi kasa da murya still adjusting on her yace "Baki san kina
da miji ba ko?" Cikin kuka tace "Wallahi na sani, kawai wasa nake maka, don Allah
ka yafe min kayi hakuri baxan kara ba.... Wallahi numfashina zai iya daukewa" a
hankali yace "Ya dauke mana" Bata san sanda tayi wrapping hannunta a bayansa tana
kuka sosai tace "My chest is paining me plss" ai ko ya lumshe ido ya kara sakar
mata weight hakan da tayi masa, as if he is going to sleep, sae kuma yayi placing
forehead dinsa kan nata, joining his nose directly with hers, cike da karfin hali
tace "I am sorry plsss" murda kofar dakin aka yi, yayi brushing lips dinsu ya mike
da sauri ya sauka saman gadon, Nihad ta ja wani numfashin wahala ta mike da sauri,
jikinta na rawa ta silalo kasa hawaye na sauka idonta, ya tafi gun switch din dakin
ya kunna, ya fara dube duben Jallabiyarsa a dakin ya dauka ya daura kan kayan
jikinsa sannan ya tafi ya bude kofar dakin, Mimi dai sai bin su take da ido ya
amshi cup din hannunta da sauri yace "Thank you dear... Zata bi yayanta inda ya
tafi shine na kulle kofar har ki zo, may be u can tell her not to" Nihad dai ta
kasa dago kanta daga inda take durkushe a kasa har sannan bata ji kirjinta ya dawo
dai dai ba, ga wani bugawa da zuciyarta yake alamar ba karamin tsorata tayi ba,
Mimi ta karasa ciki ta durkusa gabanta soothingly tace "Kiyi hakuri, tunda yasan
gidan definitely zai dinga zuwa wajenki ai, so ba sai kince zaki bi sa ba" Nihad
taki yarda ta kalleta kamar munafuka, Khalil dake tsaye bakin kofa yace "Kawai ki
tafi ki kyaleta idan ta gama kukan sai ta fita...." Zumbur Nihad ta mike har sai da
ta ba Mimi tsoro, Mimi ta mike tana kallonta ganin she looks so afraid tace "Are
you alright Neehad?" Nihad tayi karfin halin gyada mata kai, Mimi tace "Toh mu
tafi" Tana makale bayan Mimi suka nufi kofa, taki yarda ta kalli inda yake tsaye,
ya bi ta da ido har suka fita sannan yayi wani murmushi ya kulle kofarsa... Duk
zaman da Nihad tayi part din Mami bayan sun koma da Mimi she is so silent duk da
dama can ba wai tana magana bane amma na yanxu yayi worst, gaba daya ta kasa cire
abinda yayi mata a zuciyarta, abincin ma kasa ci tayi wai ta koshi, Mimi duk
tunaninta ai tafiyar farooq ne ya sa ta zama haka, shi yasa ma bata yi bothering
dinta ba. Wajen karfe tara Khalil ya shigo parlon wearing on his pajamas, sai da
gaban Nihad ya fadi ganinsa da tayi taki yarda kuma su hada ido, yana kallon Mimi
yace "Mami na ciki?" Mimi tace "Aa tana downstairs tun dazu" Yace "Ohk, ni bani da
abinci yau a gidan kenan?" Mimi ta ɗan zaro ido tace "Yayanmu wanda muka kai maka
daki fa?" Yace "I called Noor ta fita da shi ban ci ba, ai wannan yayi yawa sosai"
Mimi tace "Ohk sorry pls, should i get you another one now?" Yace "Yeahh, but ba
nan zaki kawo min ba, and ki ɗan kara hada min irin wannan coffeen da kika yi min"
Sosai gaban Nihad ya fadi da ta lura Mimi fita zata yi daga parlon, sai zazzare ido
take uwa warce tayi ma sarki karya, Mimi ta dau after dress dinta ta daura kan
sleeping dress din jikinta tace "I am coming Nihad" Nihad was shocked and confused
on what to do, haba ai bata san sanda ta mike da sauri xata ce mata tana son bin ta
amma tuni Mimi har ya fita, kamar munafuka ta fara tafiya zuwa kofa, Khalil dake
kallonta yace "Kee" Ta tsaya a tsorace ta kallesa kamar zata yi kuka tace "Ni
rakata zan yi" Bata jira me xai ce ba ta karasa kofar da gudu ta bude ta shige next
parlor amma taga Mimi har ta fice daga nan ma ta kulle kofar, bin bayanta Khalil
yayi tana ganin haka ta kwasa a guje ko kusa da kofar bata kai ba ta take dogon
hijab din dake jikinta na Mimi, sai ga tim a kasa ta zaro ido tana yarfe hannu, dai
dai nan aka bude kofar parlon, Mami ta koma baya tana kallonta tace "Subhanallah,
garin yaya?" Nihad ta mike tsaye da sauri xuciyarta na bugawa tace "Zan tafi in
kwanta ne, shine na fadu" tuni khalil ya koma daya parlon, Mami na kallonta tace
"Toh ki dinga yi a hankali, Hope you are not injured?" Ta gyada mata kai da sauri,
Mami tace "Toh sai da safe" Nihad tayi saurin fita daga parlon, Mami ta bi ta da
kallo, sai kuma ta karasa next parlor din, zaune ta tadda khalil yana waya, the way
he is talking on the phone xaka yi zata ya kai minti talatin yana wayar, Mami tayi
wucewarta cikin bedroom dinta. Sai da Nihad ta shiga dakin da take taji knees dinta
na mata zafi, ta zauna gefen gado tana dubawa taga ba ciwo amma zafi yake mata, da
kyar ta samu ta shiga bandaki tayi wanka ta fito, ta saka kayan barci bayan ta
shafa turare ta kwanta saman gado tayi lamo, incident din daxu ne ya dinga dawo
mata, but what's the meaning of that?? Lokaci daya ta kawar da tunanin ta jawo
wayarta a hankali tana dubawa, taga miss calls din Ayman har biyu, zata ajiye wayar
sai ga wani kiran nasa, dagawa tayi ta rufe har kanta da duvet, ko minti goma basu
yi da fara wayan ba taji an kwankwasa kofar dakin, da sauri ta mike zaune ta katse
wayar tana kallon kofar, aka sake Knocking sauka tayi a hankali ta tafi gun kofar
tace "Waye?" Mimi tace "It's me" Daga haka Mimi ta bude tana kallonta tace "Mami
said i should ask if u are okay?" Nihad tace "Sure, thank you" Mimi tace "Ohk good
night" Nihad ta dan mata murmushi ta gyada kai kawai, daga haka Mimi ta juya ta bar
wajen Nihad ta kulle kofarta ta koma ta kwanta. Washegari Khalil na tare da Mami a
parlonta Aunty Hassana ta shigo da sallama, Khalil na jin muryarta yayi saurin kara
waya a kunne yana maganan da babu shi, Mami dai bata ce komai ba, har Aunty Hassana
ta karaso, shi kuma ya mike ya fice daga parlon still making fake call, Mami tace
"Mun tashi lafiya Hajiya Hassana" Aunty Hassana da ta bi sa da kallon gefen ido
tayi saurin cewa "Lafiya lau, ya yaran?" Mami tace "Alhamdulillah, ya su Sajidah"
Aunty Hassana tace "Toh ni naji kin min shiru, baki ce ga abinda ake ciki ba, don
last week naji Abbansu yace xa a kai kudin auren yaron nan, to mu ba wani shirye
shiryen da xa muyi a nan ne?" Mami tace "Ai gobe ne idan Allah ya kai mu" Aunty
Hassana tayi shiru tana kallonta da mamaki, can tace "Gobe goben nan amma ba
labari?" Mami tace "Ni ai na zata Amina ta gaya maki don muna tare da ita a parlon
Yallabai ya saka lokacin, and that was last week" Aunty Hassana ta hade rai tace
"Saboda Amina ce tafi kusanci da ni ko me?" Mami tace "Ba dai ta yanda xa ayi kice
baki ji daga bakinta ba Hassana, ko ita bata gaya maki ba ai yaci yayan naki ya
gaya maki, yaushe rabon mu hadu dake cikin gidan nan balle maganar ya hadu mu? Ai
mun kwana biyu bamu hadu ba" Aunty Hassana tace "Gaskiya ne, kya yaɓa min magana
son ranki ai, ba laifin ki bane" Bude baki Mami tayi tana kallonta tace "Meye abun
ɓacin rai a zancena Hassana?" Tuni Daga Hassana ta mike fuuu ta fice, tana komawa
bangarenta ta dau waya ta hau kiran kawarta Chamo, ta yaya za ace gobe xa akai kudi
ita da ta zata Mami zata ce mata an daga lokacin kai kudin, Chamo na dagawa Aunty
Hassana tace "Ke gobe fa naji ana cewa xa a kai kudin auren, yaya haka?" Chamo tace
"Toh in kai kudin aure sai aka yi yaya? Baki ta6a ganin inda aka fasa aure ranan
daurin auren bayan an tara jama'a ba?" Aunty Hassana tace "Haka ne, to amma idan
kuma
hakan bata kasance ba fa? Ai risk ne wannan Chamo, kamata yayi ko kudin ma kar a
kai balle a saida rana" Chamo tace "Ke dadina dake gajen hakuri wallahi, sai kace
yau aka saba maki aiki kiga aikin ya ci Hassana?" Aunty Hassana ta sauke ajiyar
xuciya tace "Aa ba haka bane Chamo, ni dai kawai ina ga ba sai an wani je ga ranan
daurin aure a fasa ba, kawai tun ba aje ko ina ba a fasa gaskiya hankali na zai fi
kwanciya" Chamo tace "Toh ai abinda baki sani Malam yace min dole ne xa a kai kudin
amma a banza tunda ba auren za ayi ba, daga sanda aka kai kudin matsaloli xa su
dinga billowa daga both part har aure ya ruguje daga karshe" Aunty Hassana dai tayi
shiru don ita fa bata gamsu ba, tasan karkari aka kai kudin nan a sa wata daya in
dai yayanta ne, can tace "Toh daga ina ne xa su bukaci a fasa auren Chamo?" Chamo
tace "Shi da kansa Khalil din xai ce ya fasa, ke ni bari kiji wllh malamin ma ce
min yayi bai ga auren ba kwata kwata, xa dai ayi ta kashe kashen kudi, a siya
wancan a siya wannan na biki amma fa ba auren" Aunty Hassana tace "Toh yanzu
Sajidar ce ko farhana?" Aunty Hassana tace "Toh ai kya bari maganar auren ya ruguje
tukunna ki kawo wannan ko?" Aunty Hassana tace "Toh shikenan, sannan abu na karshe
kinsan ɗan iskan yaron nan ko gaisheni ya daina yi a gidan nan?? Wallahi tun da ya
dawo ga maciji bai hadani da shi balle yarana, iyaka yayi da kanninsa ko Hanan"
Chamo tace "Shi khalil din??" Aunty Hassana tace "Wallahi nake gaya maki" Chamo
tace "Wannan ai abu ne me sauki, xan kira malamin in gaya masa xa a san yanda xa
ayi...." Aunty Hassana tace "Toh Nagode, za mu yi magana zuwa anjima" Daga haka ta
katse wayar tana ta tunane tunane, ita wallahi ko kudin auren ma bata son ya shiga
hannunsu, don tasan ba amsa xa ayi ba idan aka fasa auren ai, ga kudi ba na wasa ba
xa a kai ta sani. Throughout ranan Nihad taki fito dakinta don ko by mistake bata
son haduwa da Khalil, wani sabon tsoronsa take ji har cikin zuciyarta, saboda yanda
ta sa abinda yayi mata jiya da daddare a ranta sai da tayi mafarkinsa cikin dare,
wajen karfe shidda na yamma Mami ta shigo dakin nata tana tsaye bakin kofa tace
"Why are you inside throughout?" Nihad ta ɗan yi yake tace "Aa ina kallo a waya ne"
Mami tace "Ohk, ga can takalmi Noor ta siya har da ke" Nihad ta dinga kallon Mami
jin wai Noor, ko dai Mimi take son cewa, da sauri tace "Toh Mami, xan fito yanzu"
Mami ta juya ta fita, a hankali Nihad ta mike ta dau mayafinta sannan ta fito daga
dakin. Tana shiga parlon Mami taga Mimi zaune tana operating laptop dinta, Mimi
tace "Kinyi scarce yau fa, hope you know you are having lectures tomorrow" Nihad ta
ɗan yi murmushi kawai ta zauna ta gyada mata kai, Mimi ta dau takalmi ta mika ma
Nihad tace "Noor got this for us all, same color same design" Nihad ta amsa tana
kallon takalmin tace "I appreciate it" bude kofar parlon aka yi Khalil ya shigo,
Mimi tace "Awnn Yayanmu you look good daga wajen Sis Nadeeyah kake ko?" Yace "Yeah,
ina Mami?" Tace "She went in not too long" Ya ɗan kalli Nihad suka hada ido, ta ɗan
daburce tace "erm... Good evening" Yace "Evening" Daga haka ya nufi dakin Mami
yana murmushi, Mimi ta wara ido tace "That's sweet of u Nihad, kuma naji dadi da
kika ji maganata" Nihad dai bata ce komai ba, can kuma dai ta dau takalminta tace
"Zan je inyi sallah, it's almost magrib" Mimi tace "Ohk" Daga haka Nihad ta mike ta
fice daga parlon don bata ma son ya fito ya sameta. Tare Khalil da Mami suka tafi
bangaren Abba ta dalilin kiranta da Abban ya aika khalil yayi, Mami ta gaishesa
bayan sun samesa a parlor tare da Aunty Hassana, Mami tace "How was the trip?" Yace
"Alhamdulillah" Mami tace "I was thinking ba sai ka dawo ba, representative dinka
kawai zaka aika goben" Abban ya ajiye takardun hannunsa yace "Ni ba saboda shi na
dawo ba ai, kuma i think gobe xan yi tafiya portharcourt..." Mami tace "Allah ya
kai mu" Shi dai khalil na zaune nesa da su yana danna wayarsa, Abba na kallon Mami
yace "Dama i want to confirm if ke ce ke aikosa ya zo nan yayi min rashin da'a"
Aunty Hassana ta sauke wani ajiyar xuciya, Mami ta kalli khalil da sauri, Khalil ya
ajiye wayarsa yace "But i see nothing wrong don na tambayi hakkina Abba, i am
asking you for my property, i seriously need them" Abba ya mike yace "Toh daga yau
ka sake shigo min nan da wannan maganar i am promising u i won't take it likely
with you..... Nace baxan bayar ba kuma i mean it" da mamaki Khalil yace "But why? I
have all right to ask Abba" cike da damuwa Mami tace "Me yasa idan na maka magana
baka ji Khalil? Me yasa kake daukan maganata for granted pls" Khalil ya mike yana
jin ransa na ɓaci yace "Mami to saboda me za a rike min abubuwana akan laifin da
ban aikata ba? Akan something i knew nothing about, why???" Aunty Hassana ta bude
baki tace "Akan laifin da baka aikata ba? Ehh lallai ka cika mara kunya kuma
fitsararre, Sannan da ka mike a zabure haka dukan uban naka za kayi ko yaya?" A
fusace yace "Kee ni ban sa bakinki ba Hajiya, babu ruwanki da issue dina da
mahaifina, stay in ur lane and stay out of family issues da bai shafe ki ba" Aunty
Hassana ta fashe da kuka ta rufe fuskarta da gefen gyalenta tana girgiza kai, sake
baki Abba yayi yana kallon Khalil, ya juya ya nufi kofa ya fice daga parlon fuuu,
Mami dai ta ma rasa abun cewa, wato khalil baxai ta6a canzawa ba kenan, Abba ya hau
kai komo a parlon fuskarsa a murtuke, cike da karfin hali Mami na kallon Aunty
Hassana tace "Kiyi hakuri Hassana zan je in...." Wani tsawa ta daka ma Mami tace
"Bana bukata, duk ba ke ke sa shi yake raina mu ba, kiri kiri yaron nan ya daina
gaishe da ni da Amina a gidan nan, yaron da a haife na haifesa, yanzu kuma rashin
kunyar tasa da fitsara har ya kai kan ubansa, kayi laifi amma kafi kowa bakin
magana, miliyan dari takwas wasa ne yanzu? An daga maka kafa albarkacin tausasa
yaya da muke tayi ka dawo gida amma kace mune makiyanka? Yanzu da nawa ɗan nan zai
yarda da abinda khalil yayi min yanzu? Ba tashin hankali xa ayi ba kenan??" Abba
yace "Ki bar zancen nan, i know how to handle it, ke Fatima yarinyar da kika kawo
gidan nan without my knowledge wacece? Kuma daga ina take??" Mami ta kallesa da
mamaki, sai kuma tace "Sauran yaran da ake kawowa gidan nan su karaci zamansu su
wuce ka ta6a tambayar daga inda suke ko wa ya kawosu Yallabai? Yaran da har kudin
makaranta kai ke biya masu sai wannan da ko biyar dinka babu a makarantar da aka
biya mata?" Hassana ta mike a fusace tace "Kar ki kuskura kice zaki masa magana
yanda kika ga dama a gabana Fatima, ke kiyi ɗan ki yayi, to baku isa ba, kuma
wallahi baxan dauka ba don kiji in gaya maki" Mami ta daga kai tana kallonta, can
ta kalli Abba tace "To er ɗan uwana ne, kuma karatu ya kawota gidan...." Mami na
fadin haka ta mike ta fice daga parlon, Aunty Hassana tace "Toh wa yaki zamanta a
gidan nan dama? Abinda Allah kadai yasan ladan ciyar da ɗan mutum, ai mu bamu ki
tayi ta zama har abada ba ma, kawai damuwar mu kamar yanda na gaya maka Yaya,
kwanaki can wani videon yarinya tsirara na ta yawo a kafofin sada zumunta, to ita
ce yarinyar" Abba na kallonta da kyau yace "Ke kin tabbata Hassana?" Aunty Hassana
tace "Zan maka karya ne yaya? Wallahi ita ce yara duk sun shaida mu ma kuma mun
shaida, babu amfanin nuna video din ne yanzu da sai in nuna maka, sannan tun da
yarinyar ta zo gidan nan bata gaida mu, sai dai mu wuce ta wuce saboda ta isa" Abba
ya dinga zaga parlon yana nazari bai dai ce komai ba, ran Aunty Hassana yayi fari
tass don duk hanyar da zata kuntata ma Mami nemansa take ido rufe.....
Mumy ce ta shigo bangaren Umma ta sameta a parlor tare da Kamila, Mumy tace "Dama
kina gidan nan Kamila?" Da sauri Umma ta amshe tace "Daxu ta zo, yanzu ma mijin
take jira wai" Mumy tace "Ohk, dama tambayarki zanyi kinji daga Nihal kuwa? Tun
jiya bana samunta a waya wallahi" Da damuwa Umma tace "Yanzu ma abinda muke
jajantawa kenan, har na gaji da kiran wayartata wallahi, na kira farooq yace min
yana Abuja amma gobe zai shiga kaduna sai ya karasa Zaria yaga ko lafiya" Mumy tace
"Toh duk yanda aka yi sace mata wayar aka yi" Kamila tace "Nima abinda nace kenan,
amma Umma duk ta daga hankalinta, babu tantama an dauke wayar ne" Umma tace "Sai ta
rasa wayar da xata kira mu da shi a kawayenta tace an dauke mata waya?" Mumy tace
"In sha Allahu lafiya lau take" Umma tace "Toh Allah ya sa" Juyawa Mumy tayi ta
fita daga parlon, Kamila tace "Ke abu indai ya shafi Nihal duk ki daga hankalinki
ki daga na wasu, ni gashi na kawo maki damuwata ko bin ta kaina baki yi ba sai
korata kike in bar gidan nan tun jiya" ko kulata Umma bata yi ba ta mike ta fita
daga parlon.

Littafin Nihaad na kudi ne, ki biya ki karanta cikin salama, idan ba haka ba akwai
dari biyar tsakaninmu.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

46

Farooq was perplexed bayan yayi parking dai dai inda Khalil yace ya tsaya ya
jirasa, yana kallon sojojin dake opposite dinsa amma nesa da shi, ya dinga bin area
din da kallo with mouth agape, ina ne nan din khalil yace ya zo? And why will he
tell him to come and wait here? He could see 3 of the soldiers advancing toward his
car with haste, and bai san me xai masu ya kawo shi nan ba idan sun karaso, can
nesa ya hango khalil na tahowa ta inda sojojin suka yi creating barriers, sojoji
ukun suka karaso har inda yake suna masa alamar ya sakko fuskarsu a murtuke babu
rahama, Farooq ya kashe motarsa ya sauko with calmness ya gaishesu, Maimakon su
amsa strictly suke tambayarsa where is he from kuma tsayuwar me yayi a nan? Farooq
yayi karfin halin nuna masu khalil dake tahowa yace "I was waiting for him...." Da
sauri khalil ya fito daga wajen barrier din ganin sojojin da suka tsare farooq, ya
daga ma sauran soldiers din dake wajen a zaune hannu ya nufi gun farooq, sojojin
dake gaban farooq na ganinsa suka juya suka koma position dinsu, Khalil na Murmushi
yace "Yi hakuri na bar ka a tsaye, barka da isowa yallabai" farooq dai sai kallonsa
yake still surprise, can dai yace "Ina ne nan din Khalil?" Khalil ya zaga daya side
din motar not wanting to answer him yace "Mu karasa can ciki Yallabai, ba a tsayawa
a nan...." Farooq ya shiga motarsa har sannan mamaki ne shimfide a fuskarsa Khalil
yace "Mu je can gaba" da wani expression Farooq ya masa wani kallo yace "Mu je
ina??" Cause ta wajen barriers din da sojojin ke tsaye yaga Khalil na nuna masa wai
su bi, Ba tare da Khalil ya kallesa ba yace "Gaba xa mu yi, kuma hanya ce ai"
Farooq yace "Ta gaban sojojin can xa mu bi kake nufi?" Khalil yace "Ba komai, nace
maka hanyar kowa da kowa ne" Bayan few seconds Farooq dai ya tada motar yana
driving din a hankali yaga sojojin sun daga masa karfen da ya rufe layin, ya wuce
ciki still driving careful, Bayan sun shiga Farooq na kallon Khalil yace "Wai ina
ne nan din Khalil?" Khalil na nuna masa gaba yace "Can gaba xa mu karasa, ba nisa
sosai" Farooq dai ya ci gaba da driving din amma carefully cause the security in
there isn't funny, very tight security, gasu fuskarsu babu rahama duk a murtuke,
Farooq dai na driving yana kare ma anguwan kallo, bayan tafiyar few minutes, Khalil
ya nuna masa gate yace "Baƙin gate din can xaka yi horn" Farooq ya juya yana kallon
Khalil, Khalil bai yarda ya kallesa ba ya danna horn din da kansa, Sojojin wajen
suka taso zuwa gun motar, tuni khalil ya sauke glass ganinsa suka koma, aka bude
gate din, sai da Khalil yace "Mu shiga yallabai" sannan Farooq ya ja motar zuwa
cikin compound din, Khalil ya nuna masa inda xai yi parking, kai kana ganin farooq
kasan abun ya gama daure masa kai, he is more than confuse, Khalil ya sauka daga
motar ya zaga yana kallon farooq, farooq ya sauko daga motar shi ma yana kallonsa
amma ya kasa cewa komai, Khalil na dan murmushi yace "Ya kwana da yawa Yallabai?
It's a pleasure meeting with you after a while" A hankali Farooq yace "Now tell me,
why did u chose to hide ur Identity? Why?" Khalil ya sauke idonsa kasa yace "I was
left with no choice Farooq, but the beautiful part of all is that i meant no harm
to your family, something's are better left unsaid, and mind you this is my
father's house not my house, kuma shi namiji ai baya tutiya da gidan ubansa, all
what u are seeing in here is for my dad, and i am not him in anyway" Khalil bai
jira abinda Farooq xai ce ba yayi gripping hannunsa yace "Mu shiga ciki" Daga haka
suka bar wajen, Farooq couldn't stop looking at Khalil, babban tambayar da yaji
yake bukatar amsarta shine me khalil yaje yi gidansu? meye manufarsa na zuwa
gidansu yace zai yi driving? Driving fa?? Shi dai From day one yasan there is
something about Khalil that is hidden, he knows that, and here is what was hidden
today, Suna shiga Main parlor Khalil ya sake hannunsa, Farhana dake parlon ta bi su
da kallo, Daga khalil har Farooq da yake tafiya with calmness babu wanda ya kalli
inda take har suka haura sama, Farooq couldn't hide how amazed he was with all what
he is seeing, and he felt so happy for his Lil sis, har suka iso parlon Mami,
Khalil na kallonsa yace "This is my mum's part, za ku gaisa da ita" Farooq na
murmushi yace "Sure" Suka shiga first parlor sannan second, Nadiya dake zaune ita
kadai tana danna waya ta daga kai jin an bude kofa, Farooq yayi sallama ya shiga
bayan Khalil yayi taking lead, Nadiyah ta kalli Khalil sannan farooq, Khalil yayi
mata murmushi yace "Meet my frnd Farooq" Da fara'a Nadeeyah ta gaida Farooq ya amsa
with calm smile written all over his face sannan ya zauna saman kujera, Tuni Khalil
ya shiga dakin Maminsa, bayan few minutes sai ga shi ya fito tare da Mami, da
fara'a Mami suka gaisa da Farooq dake ta kallonta saboda resemblance dinta da
khalil is very obvious, khalil ya zauna gefen Farooq yana kallon Mami yace "Yayan
Nihad kenan Mami, he is Farooq by name...." Mami tace "Maa sha Allah, you are
welcome son" Khalil na Murmushi yana patting shoulder din Farooq gratefully yace
"They are the most nicest family i have met so far in life, they really made my
stay with dem a memorable one, they made me felt at home all through my stay with
them, and i owe them for that..." Farooq dai kawai yayi murmushi, Mami tace "Allah
sarki Allah Ubangiji ya karfafa zumunci, Allah ya saka da alkhairi.... This is so
beautiful to hear" Farooq wish he could express how happy he is for his Lil sis at
this moment, a ko da yaushe addu'arsa ga Nihad shine Allah ya dauwamar da ita cikin
farin ciki bayan all What she's gone through, yana mata addu'ar Allah yasa aurenta
da Khalil ya zama sillar farin cikinta na har abada, he sees her as a strong young
girl, don yau ace Nihal ce abubuwan nan suka faru da yasan she is definitely going
to break, yasan she can never endure it for long, duk abubuwan da Khalil ke fada
akan karamcin da suka masa a kano Farooq hankalinsa ba nan yake ba, ganin komai
yake kamar a mafarki, tuni Mami ta kira Bilkisu ta kawo masa drinks and small
chops, Mimi ta shigo parlon rike da laptop dinta zata dau charger da ta bari, Mimi
na kallon Farooq tace "Good evening" With smile on his face yace "Evening dear" Ta
dau charger xata fita Khalil na kallonta yace "Can you pls call ur new friend?"
Mimi ta ɗan juya tace "You mean Neehad?" Yace "Yeah" Ta gyada kai tace "Sure" Daga
haka ta juya ta fita daga dakin.... Kwance ta tadda Nihad kan gado, Nihad ta juya
tana kallonta, ganin yanayinta Mimi tace "Are you okay?" Kai kawai Nihad ta gyada
mata ta mike zaune, Mimi tace "But there is tears in ur eyes" Nihad ta girgiza mata
kai trying not to break cike da karfin hali tace "I am fine, kawai ciwon kai
nake...." With concern Mimi tace "Eyya Allah ya sauwake, i will get u drug, ki zo
parlorn Mami ana kiranki" Nihad ta hadiye abinda ya tokare mata cikin karfin hali
tace "Ohk" duk zaton ta Mamin ce ke kiranta, Ta sauka daga saman gadon ta bi bayan
Mimi tana tafiya a hankali suka fita daga dakin.... A hanya suka hadu da Noor,
ganin she is dressed up Mimi tace "Are you going out big sis?" Banza Noor tayi mata
saboda tana tare da Nihad, ta wuce su kamar xata bangaje Nihad din, Nihad dai ta bi
ta da kallo bata ce komai ba, Mimi tayi kasa da murya bayan Noor ta wuce su tace
"Sorry.... she is angry at you may be because u just badged into the parlor when we
came back from school, baki yi masu sallama ba kuma sannan baki yi recognizing
dinsu ba, which isn't right" Nihad ta dinga kallonta tace "Ta yaya zan shiga waje
ban yi sallama ba, sai dai in basu ji ba, ko kuma nice ban yi yanda xa su ji ba,
beside they were discussing ta ya za su ji?" Mimi tace "You just have to raise ur
voice za su ji, and why didn't you recognize them?" Nihad ta ɗan buda ido tace "Do
i have to?" Mimi tace "Yeahh, as far as ke kika shiga kika samesu a wajen, sai kiyi
acknowledge din haka" Nihad ta tabe baki tace "Sai dai in yi ma yayarki amma ita
dayar i have no business with her don ban santa a gidan nan ba, why will i
recognize her?" Mimi tayi letting sigh tace "But fiancee din yayanmu ce" Nihad ta
buda ido sosai tace "Ohh ashe fiancee ce kawai!!" Mimi tace "Yeah, and she is going
to be his wife soon" a takaice Nihad tace "Then i will wait till she becomes his
wife if that's possible, before i can recognize her...." Mimi tace "Now accept that
u are wrong Neehad" Nihad tace "I accept, but by not recognizing only ur sister"
Mimi ta daga kafada tace "Ohk then, and can i ask u one more thing" Ba tare da
Nihad ta kalleta ba tace "Ohk" Mimi tace "I noticed u don't greet my brother, why?"
Nihad ta kalleta da mamaki, can tace "But u advised i should be avoiding him
totally" Noor halted with mouth wide open tana kallon Nihad, bata san sanda ta
fashe da wani dariya ba, she laughed for some seconds kafin tace "But u neva told
me it's you, u said ur friend" Nihad ta ɗan zaro ido tace "Oh, oh... I.... I mean
to say...." Sai kuma ta rasa abinda xata ce lokaci daya taji kunya, Noor na dariya
tace "You are so funny Nihad, ni bance kar ki gaishesa ba, i only said u should be
avoiding him, but not ignore greeting him" Nihad dai ta ki cewa komai, Mimi ta
langwabar da kai tace "Yayana na da kirki sosai fa, you only misperceived him, just
try turning friends with him zaki gane hakan, he is a simple and sweet person....
Give what i said a trial pls" Nihad taki cewa komai ta ci gaba da tafiya Mimi na
biye da ita har suka iso parlon Mami, khalil kadae Nihad ta gani zaune saman
kujera, sai Nadeeyah dake parlon ita ma, bata ma lura da Noor dake tsaye daya side
din ba, ta juya zata kalli Mimi ta tambayeta wa ke kiranta tayi ido hudu da ya
farooq dake tsaye side din kofa ya rungume hannunsa yana kallonta with smile
written all over his face, Kasa kwakkwaran motsi tayi a inda take, don kawai sai
abun yayi mata kamar mafarki take, ta dinga kallonsa babu ko kiftawa, ganin haka
kawai ya nufeta yana murmushi ya rungumeta, he understands
she is shock and neva expect seeing him at that time, Nihad ta kankamesa ta fashe
da kuka, tana son magana amma ta kasa cewa komai, Khalil da Nadeeyah dai kallonsu
kawai suke, haka Noor dake tsaye, lkci daya Mimi dake murmushi ta fahimci yayanta
ne, haka Noor da ta kasa barin inda take a tsaye, ganin kukan da Nihad take farooq
yayi kasa da murya yace "Ain't you happy seeing me Lil sis?" A hankali cikin rawan
murya tace "Don girman Allah kar ka tafi ka barni a nan yaya, wallahi baxan iya
zama a nan ba, take me back home in roki Abba yayi hakuri ya yafe min" Farooq kadai
ke jin abinda take cewa, yayi kasa da murya yace "You are a married woman now
Nihad, you have to stay where ever ur husband is staying" Nihad ta kara rushe masa
da kuka, ya kama hannunta ya tafi da ita suka zauna saman kujera yana kallonta,
kuka kawai take tana share hawayen da yaki tsaya mata, shi dai khalil kallonta
kawai yake, Farooq yace "Now stop that cry ko inyi tafiyata, and i am serious" Da
sauri ta fara goge idonta tana kallonsa ta hadiye kukan da take ta jinginar da
kanta kan shoulder dinsa.

Umma na kallon Kamila cikin fada tace "Magana nake maki kika kauda kai" Kamila dai
danna wayarta kawai yake, Umma tace "Ke yanzu kina nufin ban isa in gaya maki kiji
ba? Zaman gidan nan yafi maki ki koma dakinki kike nufi? To wai ma uwar me kike
tsinana min a nan da kika zo kika jaɓe min?" A fusace Kamila tace "Umma ni wallahi
baxan koma in zauna da manemin mata ba, baxan iya ba wallahi" Umma ta buda baki
tace "Duk da baki san yana neman mata ba sai yanzu Kamila?" Kamila tace "Nace maki
yanzu ya fara Umma, don wannan abun da nake gaya maki ko wata biyu ba ayi ba da ya
fara... Sannan the worst part of all is that guilty conscience ya sa ya dau zargi
ya daura min, kwata kwata na lura yanzu bai yarda da ni ba, ban isa in motsa ko nan
da can ba, ba dama yaga wayana yayi ring, to a kan me?" Umma tace "Toh duk ba
ruwana da wannan wallahi, tunda har ya kira ki tattara ki koma dakin ki, banda
iskanci shekaranku biyu tare baki san yana neman mata ba sai yanzu? Dariya kike son
a min a gari ko me? Kina zaune da mijinki lafiya ga arziki sai yanda kika yi da shi
amma saboda shaidan na maki ganga a kai shine xaki billo da wannan iskancin? Ko duk
matan duniyan yake bi ma ina ruwanki? Balle wannan sharri ne kawai kika masa"
Kamila ta mike fuuu ta fice daga dakin a fusace, Umma tace "Wallahi baxaki kwanar
min a gidan nan yau ba, maza dau jakarki ki koma dakinki, na gaji da boyeki haka
kuma"

Nihad ta dade bata shiga farin cikin da ta shiga a yau ba, a haraban gidan take
zaune ita da yayanta bayan sun fito parlon Mami, Farooq dai sai kallonta yake ganin
yanda ta kara haske tayi kyau sai dai ta rame sosai, he just can't wait to go back
home and break this amazing news to His stepmom ko xata samu peace of mind, a
hankali tace "Ya farooq yanzu Abba baxai yafe min ba? Wallahi i know nothing about
all what that has happened to me" Farooq ya wara ido trying his best ya kwantar
mata da hankali yace "Xai yafe maki mana Lil sis, amma sai kin zauna lafiya da
mijinki, kin masa biyayya... I am assuring you wannan ne kadai zai sa Abba ya yafe
maki, don ya gaya min haka" Nihad tayi shiru tana kallonsa, yace "Yea, when i
begged him on ur behalf abinda yace min kenan, don haka kiyi kokari ku zauna
lafiya, and accept him as ur husband" Hawaye ya cika idonta tace "But shi ma baya
sona fa Ya farooq, we don't like each other" Farooq ya girgiza kai yace "Da baya
sonki baxai kawoki har nan gidan iyayensa ba, ke dai ce baki son zaman lafiya
Nihad, ko da baya sonki ke ba mace bace, teach him how to love" Hawaye kawai Nihad
take bata ce komai ba, Farooq yace "I know it's hard dear, amma kiyi hakuri, komai
xai daidaita wataran, za kuma kiyi farin cikin Kasancewarsa mijinki" Cikin rawan
murya tace "Bayan sai yayi ta daga min shoulder saboda yaga suna da kudi" Dariya
sosai farooq yayi yace "Ke sanda kika dinga daga masa naki shoulder din a gidanku
fa?" Nihad ta hade rai tace "Aa ni ban daga masa shoulder ba, kuma shine sai yayi
ta tsokanata" Farooq yace "Toh yanzu dai duk ba wannan ba, all i want from u is to
love and accept him Nihad" Nihad dai ta ta6e baki bata ce komai, nasiha sosai
Farooq ya dinga mata kuma yawanci duk sun shigeta kadan ne taji baxata iya abinda
yace ba, bayan khalil ya basu at least 40min ya fito yayi joining dinsu tare da
Mimi, at last dai Driver tare da Noor ne suka maida Nadeeyah gida, Nadeeyan kuma
bata damu ba ganin yana da bako, Mimi sai mamakin Nihad take don bata ta6a tunanin
tana magana har tayi dariya haka ba, shi dai Khalil sai dai ya kalleta ta gefen ido
jefi jefi, sai da aka kira sallah sannan Khalil suka shiga ciki su yi alwala farooq
before going to mosque, Nihad da Mimi suka koma parlon Mami, Bilkisu ta kawo
abincin farooq nan parlon Mami ta ajiye ta fita, Mimi ta kalli Mami tace "Mami
yayanmu yace in kai masa can dakinsa" Mami tace "Toh kai masu can din" Mimi ta mike
tana kallon Nihad tace "I can't take this all alone" Nihad da kamar jira take ta
tashi da sauri, don dama tun da suka shigo ciki jikinta yayi sanyi duk da ya farooq
din ya ce mata ba tafiya zai yi ba amma zuciyarta ya kasa yarda da hakan, Ta dau
wani tray din ta bi bayan Mimi zuwa dakin Khalil, Khalil kadai suka tarar cikin
dakin, Nihad bata yarda sun hada ido ba ta durkusa ta ajiye abincin hannunta a
hankali tana bin dakin da kallo, Mimi tace "Yayanmu ga abincin visitor dinmu"
Khalil yace "Wani visitor?" Mimi ta mike tana kallonsa, Nihad dai ta kasa tashi
daga durkushen da tayi a kasa ita ma tana kallonsa babu ko kiftawa.... a takaice
khalil yace "Ai ya tafi" Nihad bata san sanda ta zauna nan kasan tiles ta fashe da
wani kuka kamar yar yarinya ba, Khalil na kallon Mimi yace "Go and make me coffee"
Mimi ita ma jikinta yayi sanyi, but he should have at least say even a goodbye
mana, juyawa tayi a hankali ta fita daga dakin ta kulle kofar....

Nihad is 500 via 3276052919 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

49

Nihad ta fito bandaki kenan taga mutum zaune edge din gado wayarta a hannunsa yana
dube duben wayar with full concentration, lokaci daya mamaki da tsoro suka cikata,
gashi bata san for how long yake dakin ba don tana dawowa daga amso charger wajen
Mimi ta jona wayar sannan ta shiga wanka, tana tafiya a hankali taje inda Hijab
dinta yake ta dauka ta saka don towel ne kadai jikinta, ta juya tana kallonsa, she
don't think ya san ta fito daga bandakin ma don gaba daya fa hankalinsa na kan
wayarta, tana jan kafa ta tafi can karshen gado ta tsaya tana ɗan leka wayar trying
to see what he is doing with it, a kan WhatsApp ta gansa yana duba duk chat dinta
da Ayman tun daga farkon sa, sosai taji gabanta ya fadi, and she started thinking
of what to do next, though ba wai dirty chat suke da Ayman din ba, but he use to
chat romantically sometimes saboda wayayye ne gayen, ta kalli fuskarsa taga babu
yabo babu fallasa yana ta scrolling chat din slowly, a hankali Nihad ta nufi kofar
dakin gabanta na faduwa ta murda taji a kulle sannan ba makullin a jiki, ta juyo
tana kallonsa kamar zata yi kuka, gaba daya hankalinta yayi mugun tashi, har at
last ya gama karance kaf chat din ya ajiye wayar staring at the wall still fuskarsa
babu yabo babu fallasa, hankalin Nihad ya kara tashi, she wish kofar a bude yake da
tuni ta fice ta koma parlon Mami, shi kam for the next 2 minutes bai ko kalleta ba,
ko tunanin me yake oho, sai kuma taga ya tashi ya dau wayar ya saka aljihu ya nufi
kofa, ta bi sa da kallo har ya isa kofar yana kokarin budewa, da sauri tace "Ina
zaka je da waya...." Bata kai karshe ba ya juya ya sauke mata wani lafiyayyen mari
a fusace, ta dafe kuncinta da sauri with shock tana kallonsa baki bude, sai a
sannan taga idonsa da ya koma kamar garwashi, ya fasa bude kofar ya fixgota ya
hadata da bango cikin husky voice yana mata wani mugun kallo yace "I thought
iskancin da kika yi a baya ya isheki ai? I thought it was enough for you ashe i was
mistaken, ta waya kika ci gaba da iskancinki daga inda kika tsaya...." Nihad ta
fashe da kuka sosai tace "Ni ban ta6a iskanci ba, ni ba er iska bace...." Ya daka
mata tsawan da ya firgitata yace "Meye ban sani ba a kanki? Tell me, meye ban sani
ba akan kazamin rayuwar da kika yi a baya? Idan zaki ma wani karyan baki bi maza ba
don baki da kunya har ni za ki ma? Ke din da kika mayar da kanki taxi no garage,
leaving home at night and returning back early dawn, kece warce naga kayan maye da
Prophylactics a jakarki, what were you doing with them??? bayan haka har alcohol
you do take..., bana tunanin akwai hotel ko club din da baki sani ba a garin kano,
At times if i think of ur past life i regret my destiny of having to accept ur
marriage for the sake of ur parents, i so regret that, ƙyamarki nake don ma ki ji
ki sani babu yanda xan yi da aurenki ne, you are not worth being married to me, na
fi karfinki ta ko ina, and i can never be comfortable to present you to anybody as
someone i am marrying, kwanciyar hankalina kawai shine in dinga kawar da tunanin
akwai aure tsakanina da ke, no responsible person will be proud to have u as the
mother of his kids..... You have a dirty past, still not considering that shine
kike chatting da wani katon banza har kina ce masa you have neva kissed all ur
life, telling him no one have ever touched you before, ain't you ashame of lying?
Ke da kika gama rabar da mutuncinki a hotels? Ina ce garin haka ne har aka samu
wanda ya maki video ya sakar ma duniya, nasan duk zaman da kike yanzu u are
uncomfortable without a man tunda kin riga kin saba, shine kike biye wani namijin
da aure a kanki ku ke chatting har da phone calls saboda ke baki san darajan aure
ba" Nihad ta daga kai hawaye na sauka idonta tana kallonsa tace "Duk na ji, ka
rubuta min takardata ka bani" Ya wani fizgota yana mata mugun kallo yana huci yace
"Who are you to tell me what to do?? To baxan bayar ba, idan kin isa ki rubuta ma
kanki takardan" Yana fadin haka ya turata har sai da ta kusa faduwa, ya nufi kofa
kamar zai tashi sama ya bude kofar ya fice daga dakin. Hajiya Amina na parlonta
tare da Aunty Hassana dake cin fruit salad, Hajiya Amina tace "Ke kin ta6a jin inda
aka kai kudin aure har dubu dari bakwai, ba wai sadaki ba, sannan a hada da
buhunhunan shinkafa? Wallahi abun yayi mugun daure min kai" Aunty Hassana ta ajiye
bowl din hannunta tace "Toh ke kuwa ba mayunwata bane, ai ita fatiman ce xata ce a
hada da shinkafar, ni fa ko a gyalena batun auren nan, don in dai wannan auren ne
wallahi baxa ayi sa ba ina da assurance din hakan, don da dai Khalil yayi aure a
waje gwara ya dauwama haka ba aure, in ma duniyanci xai yi shi yafi komai sauki
wallahi" Hajiya Amina dai ta tabe baki bata ce komai ba, Aunty Hassana tace "Banda
babana ya tsaya shiririta ai shi zai fara auren a gidan, kuma yanzun ma bai baci ba
ya dawo shima yayi auren kawai shi ma ayi masa abinda xa ayi masa" Hajiya Amina
tace "Ba gobe kika ce yana hanya ba?" Aunty Hassana tace "In sha Allahu kuwa"
Hajiya Amina tace "Toh kuwa baxai juri ganin sabon walakancin khalil a gidan nan
ba, dama can kinsan ba jituwa suke ba" Aunty Hassana tace "Ai dalilin da yasa na
takurasa kenan ya dawo, Babana ne zai raga masa? Sai dai in bani na haifesa ba
kuma" Hajiya Amina ta kyalkyale da dariya tace "Yana dawowa ki takura masa ya fiddo
mata shi ma a masa auren tunda abun en aure aure ne" Aunty Hassana tace "Ke dai ki
zuba ido mana, gwara shi auren zai yi, can kuwa kashe kudin xa ayi a banza babu
zancen auren" Sallama aka yi bakin kofar duk suka yi shiru. Umma ce zaune dakinta
tana magana da Nihal, Umma tace "Ke in zaki bude baki ki min magana ki bude, meye
kuma ana maki magana kiyi ta amsawa mutane ciki ciki, ko baki da lafiya ne dai?"
Nihal tace "Ce maki nayi ya turo min daxu" Umma tace "Nawa ya tura maki?" Nihal
tace "Dubu hamsin" Umma ta tabe baki tace "Me dubu hamsin xai maki, ko dai baki ce
masa kayan abinci xa ki siya ba?" A hankali Nihal tace "Na gaya masa" Shiru Umma
tayi, don da Nihad ce ai dubu dari zai saka mata ko fiye da haka, shi sa fa ita
bata jin ko dar akan abinda ta aikata, don akan Nihad sun ga abubuwa iri iri a
wajen Abba a gidan nan ita da yaranta, haka ya kwashi kudi ya kai ta Maryam Abatcha
dab da bikin Kamila bayan ga kayan gadon da kamila ta zaba ya ki siya mata wai yayi
kudi, wanda a lokacin ko dubu dari takwas kayan gadon basu yi ba, tana ji tana gani
kuma ya tura mata Nihal dinta Zaria, kuma ko nunawa a fuska Umman bata yi ba balle
a gane taji haushi, Umma tace "Toh ai Shikenan, kawai ki kira farooq ko Usman su
kara maki, ita er son ma ko biyar ta daina samu ai yanzu, wa ma yasan isilinta"
Nihal dai bata ce komai ba, Umma tace "Ke in fa baki da lafiya ne nasanki da zurfin
ciki ki dawo gida a maki treatment kar kije ki jaza min jaraba, lafiyarki kuwa?"
Nihal tace "Lafiya ta kalau ni" Umma tace "Toh ai shikenan, Kina da labarin Nihad?"
Nihal ta girgiza kai tace "Aa" Umma tace "Allah sarki, kamar ba ayi ta ba, ko ana
wani kauyen yanzu kuma, yanzu kenan wayar dreban baya shiga?" Nihal tace "Ehh" Umma
tace "Toh Allah ya kyauta, ya wannan saurayin naki ɗan senator, in ji dai kin ci
gaba da kulasa banda walakanci ko?" Nihal tace "Eh" Umma tace "Yana zuwa wajen
naki?" Nihal tace "Eh" Umma tace "To madallah, ki dai kula banda cewa xaki bi sa ko
ina komin takuraki da zai yi, kuma ban amince da tadi a mota ba, sannan iyakan ku
cikin makaranta, ko wajen makaranta ban yarda ki bi sa ba, banda dai mata sun zama
abinda suka zama da sai ince ko hira xaki fita in ya zo ki dinga fita da roommate
dinki wannan da kika raka garinsu, to yan matan ne sai su maka snatching" Ita dai
Nihal bata ce komai ba, Umma tace "Ki dai kula don Allah kin ji Nihal?" Nihal tace
"Toh" Umma tace "Naga kamar bacci kike ji sai da safe" a hankali Nihal tace "Allah
ya tashe mu lafiya" Umma tace "Ameen auta" Daga haka ta katse wayarta, ta shiga
neman number Husnah, ita kam tana son taji wani hali Nihad take a kauyen da dreba
ya kai ta, yana fara ring Husnah ta daga, Bayan sun gaisa Umma tace "Kwana biyu ko
leko mu kun daina" Husnah tace "Wallahi kuwa, nima ai banji dadi ba kwanaki, na ma
kwana biyu a asibiti da kamar xa a min aiki a ido sai kuma Allah ya takaita,
wallahi ban dade da fara fita ba yanzu haka, don idan na fita cikin rana idon kamar
ya cire don azaba" Umma tace "Subhanallahi, to Allah ya tsare, Allah ya kara
lafiya, gashi bamu da labari ai da ko dubaki ne sai in zo inyi" Husnah tace "Ameen
Umma, ya mutanen gidan?" Umma tace "Lafiya lau wallahi, nace dai yau bari in kiraki
in ji ko kina ji daga wajen kawarki, kamar anyi ruwa an dauke yau wata daya kenan
ni Sumayya" Husnah tace "Wallahi jiya jiya su Naf suka gama wannan zancen, Umma
kinsan wani abun mamaki kuwa??" Umma tace "Aa me ya faru?" Husnah tace "In gaya
maki kafin su bar garin nan ina kwance asibiti sun je dubani, turanci a bakin
dreban nan kamar bature" Umma tayi shiru, can tace "Turanci kuma?" Husnah tace
"Wallahi" Umma tace "Aa to ai dama yace yayi sakandari, dama dole xai iya turanci
ai in dai ba dakiki bane, amma tabbas iyakarsa dai sakandari" Husnah dai tayi
shiru, can tace "Yanzu ko Abba baxa kice ya tuntubi...." Da sauri Umma tace "Aa ko
xancen su bai so gaskiya, yanzun nan hawan jininsa sai kiga ya tashi, shi yasa na
daina gaba daya, dama wai inji inda suke ne" Husnah tace "Shekaranjiya saurayin
Nihad din ɗan janar jikamshi ya kira Naf asking for her whereabout, muka ce ai mu
ma bamu sani ba gaskiya..." Umma tayi shiru, can tace "Shikenan dai, shi banda
abunsa ko da ba a mata aure ba ta ina iyayensa xa su amince da auren wata Nihad, ai
da ko Aminata ce sai ya nema tunda ita Nihal na da wani saurayi, ko ɗan minister ne
ko sanata ni dai na manta yanda tace min, kuma yana sonta sosai sai kinga kudin da
yake kashe mata, don da bata ma kulasa ni ke ta tursasata ta dinga kulasa bata san
waye mijinta ba, kwanaki har mota yace xai bata taki, nima kuma ban goyi bayan
hakan ba" Husnah tace "Gaskiya kam"
Umma tace "Shikenan, sai dai yanda ta yiwu" Husnah tace "Muna nan dai muna
binciken inda xa mu samota in sha Allah" Umma tace "Toh don Allah ku kokarta" Nan
suka yi sallama Umma ta katse wayarta. Da safe Mimi ta gama shiryawa zata tafi
makaranta wajen karfe goma, bayan ta sallami Mami ta kalli Khalil dake parlon yana
danna wayarsa tace "Yayanmu sai na dawo" ya kalleta yace "Isn't ur frnd going to
lectures?" Tace "I met her lying down tace baxata ba, i don't think she is even
okay" Bai ce komai ba har ta fita daga parlon, Bata jima da fita ba Noor ma ta
shigo parlon ta je ta sallami Mami sannan ta fito, tana kallonsa tace "Yayanmu amma
dai yau zaka je wajen Nadeeyah ko? You know u didn't try yesterday, she made all u
requested but u ended up not coming, you just spoilt her mind" Yace "Zan je" Tace
"Better, cause she is so sad" Shi dai bai kara ce mata komai ba har ta fita daga
parlon, wayarsa ne ya fara ring ya duba yaga Nihal ce, tun jiya da daddare ya
kirata to check on her ya ji ta on another call kuma bata kirasa ba sai yanzu,
Bayan sun gaisa jin she sounds dull yace "Are you okay Nihal? You sound stressed
out" Nihal tace "I am fine, i just woke up, ya Nihad?" Yace "Alhamdulillah, yaushe
za ku fara exam?" A hankali tace "There is still time, CA muka gama yanzu" Yace
"Are you sure baxa ki je gida ko weekend ba so that u can get enough rest? Naga
kamar wannan semester din da zafi" Nihal tace "Toh xan je" Yace "Or will you like
to come over to ur sister?" Nihal ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "I will love that"
Yace "Ohk then, i will talk to farooq about it later, idan ya amince sai in zo
Zarian gobe in daukeki" a hankali tace "Okay, i am grateful" Yace "Take care dear"
Tace "Sure" Daga haka ya katse wayar, Mami ta fito, Khalil na kallonta yace "Mami
are you going out?" Tace "Ehh xa mu fita da su Amina, xa mu je wani gaisuwa ne..."
Yace "Ohk, are you staying long" Tace "Not at all, but i might branch Hajiya
Safeenah's place" Yace "Ohk Allah ya tsare" Tace "Ameen, ina da magana da kai idan
na dawo" Yana kallonta yace "Maganar me Mami?" Tace "Sai dai na dawo" Ya bi ta da
kallo har ta fita daga parlon, yana jin fitarsu daga gidan with escort bayan kusan
minti sha biyar, mikewa yayi ya fita daga part din Mami. Dakinsa ya koma ya kwanta,
deep in his thought, kiran Nadeeyah ne ya shigo wayarsa, ya dinga kallon wayar har
ya katse, can ya dauka ya kirata, kamar me bacci yace "I will call u later
Nadeeyah, i am still on bed..." Jin bata ce komai ba yace "Hello" Tace "Ohk" Katse
wayar yayi ya mike zaune, bayan kusan minti biyar ya kalli agogon dakin dake nuna
karfe goma da rabi, tashi yayi ya dau wayar Nihad dake gaban mirror dinsa ya fita,
daren jiya Ayman ya kirata yayi sau biyar, yau da safe ma still sai da ya kira duk
Khalil na kallon kiran, direct ya nufi dakin da Nihad take ya bude kofar ya shiga,
kwance ya sameta ta rufe har kanta da duvet, ya karasa ya cire duvet din ya jefa
mata wayar a gefenta, fuska daure yace "Kirasa yanzun nan kice kada ya sake
kiranki, do that immediately...." Ko bude ido Nihad bata yi ba balle ta kulasa, ya
wani hade rai yace "Ba dake nake ba?" Tashi tayi ta sauka daga kan gadon zata nufi
bandaki ya fizgota, ta fashe da kuka tana turasa da dashashiyar muryarta tace "Ni
ka kyaleni wallahi, kai me bakinka yake yi da baxa ka gaya masa da kanka ba sai
ni??" Yana mata wani kallo yace "Ni kike gaya ma haka?" Cikin tsawa tace "Na fada
maka din, tell him ur self and stop bothering me, ko kuma ka kira Aunty Maryam ka
gaya mata ita ta gaya masa" Sai kuma ta fashe da kuka ta durkushe wajen, tayi me
isanta duk yana kallonta sannan ta mike ta figi Hijab dinta zata fita ya fixgota,
ta buge hannunsa cikin rawan murya tace "Ni ka kyaleni, baxan sake kwana a gidanku
ba, gwara in tafi wajen grandma dita nasan she will accept me, it's not as if I
don't have anywhere to go...." Yana mata wani kallo yace "Da izinin wa zaki je
wajen nata??" Cikin kuka tace "Wallahi idan baka barni na tafi ba sai na gaya ma
kowa a gidan an mana aure da kai, kaji har na rantse" Da mamaki yake kallonta baki
bude, xata kwace kanta ya riketa gam yace "Ohk, kinsan an mana auren kike kula wani
farin katon banza a waya har kike ce masa you love him too?" Ta hadiye kukan da
take ta kallesa tace "Kai kuma da kake kula wata farar katuwar banza fa? Sai ni ce
baxan kula wani ba...." Duk da dariyar da ta basa ya kara murtuke fuska yace "Ohh
kika ce sai kin kulasa?" Tace "Kuma baka isa ka hanani ba, don bansan da auren kowa
a kaina ba, i neva accepted ur marriage even for one second, nasan kuma da shi ne
he is too gently and calm to raise his hand on my face, and dole ka sakeni in
auresa because i am beginning to love him...." Kuka take sosai tana son kwace kanta
amma yaki saketa yana kallonta babu ko kiftawa, ta fara kai masa duka a kirji ganin
ya ki saketa, lokaci daya ya dauketa cak ya nufi saman gado da ita ya jefata kai,
ta hadiye kukan da take tana kallonsa tana komawa baya ganin yanda ya daure fuska
yace "I will show you ni mijinki ne yau, and you have nothing to do about it" Kawai
taga ya juya ya yaje ya sama kofar dakin key, ta yi wani tsalle xata shiga bandaki,
yayi hanzarin fizgota kafin ta shiga.....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖💖 NIHAAD 💖💖

48

Washegari wajen karfe tara na safe kiran Farooq ya shigo wayar khalil dake bacci,
bude ido yayi a hankali ya jawo wayar yana kallon screen din, ganin Farooq ne ya
daga ya kai kunne, bayan sun gaisa Farooq yace "Pls kwanakin baya kace min kuna
gaisawa da Nihal, when last ku ka yi magana da ita on phone?" Khalil ya ɗan yi
shiru, sai kuma yace "Not too long mun yi magana da ita, ta turo min waec result,
birth certificate, i mean all those stuffs saboda makarantar da nake nema ma er
uwarta...." Farooq yace "When was that pls?" Khalil yace "It was just last week,
Though bana iya reaching dinta a line dina so i used my other line shine na kirata
muka yi magana, hope all is well?" Farooq yace "For 2 days yanzu ba a samunta a
waya, i just arrived zaria but bani da contact din any of her Coursemate as i am
talking to you now...." Khalil ya mike zaune yace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un, or did she lost the phone?" Farooq yace "Ko ma haka ne ai ya kamata tayi
using ko wayar Coursemate dinta ta kira ta sanar, her problem is that she neva get
close or mingle with frnds" Khalil yace "Haka ne.... I am hoping she is fine in sha
Allah" Farooq yace "Shikenan, sae mun yi magana, thank you" Khalil yace "In sha
Allah... Nima xan yi ta trying line dinta" daga haka suka yi sallama, khalil yayi
amfani da daya wayarsa yayi dialing numberta don bata yi unblocking dinsa ba har
sannan daga main line dinsa, shima yaji wayar a kashe, he felt a bit tensed, then
what happened to her? Tambayar da yayi ma kansa kenan, after trying her line for
like 3 times ya ajiye wayar a hankali ya sauka daga saman gadon ya shiga bandaki.
Har kusan karfe sha biyu Khalil na trying line din Nihal also, he is just restless,
and he prays she is okay... Yana zaune parlon Mami wajen karfe uku Mami ta fito
daga dakinta ganinsa tace "Dama kana nan har yanzu?" yace "Eh" Mami tace "Wai har
sun kai kudin, ai kunyi magana da ita ko?" Khalil ya daga kai da sauri yace "Ohh
really, ni nama manta..." Mami tayi masa wani kallo da mamaki tace "Ka manta? I
don't understand ka manta" Yace "Wallahi i am disorganized ne gaba daya yau Mami"
Mami tace "Me ya faru?" Da har zai gaya ma Mami what is happening sai kuma ya fasa
cause bai san ta sigar da zata dau lamarin ba, bai san daga wani perspective zata
yi viewing issue din ba, kar tayi tunanin gidan ba tarbiya or something like that,
Mami tace "Kayi shiru" Ya sauke ajiyar zuciya yace "I am having a terrible headache
tun dazu" Da damuwa Mami tace "Subhanallah, toh Allah ya sauwake, ka sha magani?"
Yace "Yanzu xan je in sha" Tace "Do so immediately pls, ko da abinda kake so a
girka maka?" Yace "No, i am okay" daga haka ya mike ta bi sa da kallo har ya fita
other parlor din, dai dai nan Mimi da Nihad suka bude kofar parlon dawowarsu kenan
daga makaranta, Hijab ne har kasa jikin Nihad with Nikab, she looks so cute in
them, Mimi tace "Yayanmu ina yini" yace "Lafiya lau" Nihad ta sunkuyar da kai ba
tare da ta kallesa ba slowly tace "Ina yini" ya ɗan kalleta yace "Lafiya lau" Daga
haka ya nufi kofa ya fita daga parlon, suka karasa can parlon, Mimi ta zauna saman
kujera looking very tired ta gaida Mami, Nihad ma ta gaisheta, Mami tace "Sannunku
da zuwa" Mimi tace "Mami Noor bata dawo ba har yanzu?" Mami tace "Tana gidansu
Nadeeyah, kinsan yau aka kai kudin" Mimi ta zaro ido tace "Seriously? Yaushe aka sa
auren?" Mami tace "4 weeks in sha Allah" Mimi tace "Awwnn maa sha Allah, Allah
Ubangiji ya nuna mana lafiya, nasan it won't exceed that... I am so happy for the
love birds" Mami dai ta juya zuwa dakinta ta dalilin wayarta dake ring, Nihad dake
ta kallon Mimi ta mike daga saman Carpet da ta zauna, ta dawo gefenta ta cire Nikab
din fuskarta tana kallonta tace "Who is getting married?" Mimi ta wara ido tace "I
thought i told u yesterday, Yayanmu is getting hitched, yau aka kai kudin aurensa
with sister Nadeeyah...." Tana murmushi ta kare maganar, Kallonta Nihad take babu
ko kiftawa, Mimi tace "U remember me telling you?" Nihad ta sauke idonta tace
"Sure" Tashi tayi tace "Xan je inyi wanka" Mimi ma ta mike tace "I too, i need warm
shower" Tuni Nihad ta rigata ficewa daga parlon ta nufi dakin da take, ta fi minti
2 tsaye bakin kofar dakin bayan ta shiga ciki, can ta karasa inside of the room ta
zauna gefen gado a hankali.... Khalil na komawa dakinsa yaga miss calls din
Nadeeyah har hudu a babban wayarsa, ya zaune gefen gadon ya jingina bayansa da
pillow yayi dialing numberta, yana fara ringing ta daga, a hankali yace "How are
you Nadeeyah?" Kamar xata yi kuka tace "Why ain't you picking ur calls, ina ta
kiranka no response" Yace "Bana kusa ne" Tace "Ta yaya zaka ce min baka kusa, i
called almost 2 hours ago" yayi kasa da murya yace "Kina da son korafi da yawa
Nadeeyah, why?" shiru tayi, yace "Kinsan baxan ƙi daga kiranki just like that ba
ai, so why not believe bana kusa and have rest of mind" Nan ma bata ce komai ba,
yace "Hello, nasan kina ji na" a hankali tace "Shikenan, Allah ya baka hakuri, only
called to say Hi, na ji ka shiru all through" yace "Ina parlon Mami tun daxu, i am
sorry i missed your call, it wasn't intentional....." Ta gyada masa kai kawai bata
ce komai ba, yayi murmushi sanin da kyar if she is not in tears already, yace
"Karfe biyar xan zo in sha Allah, ki min wannan drink din da pancake me dadi da
kika min the other day, immediately after Magrib kuma we will be going out for
shopping" A hankali tace "Ohk" Calmly yace "I love you" Tana goge hawayen idonta
tace "Love you too" Yayi murmushi kawai ya katse wayar. Khalil ya sake trying wayar
Nihal for the countless time but a kashe, as at 2pm dazu ya kira farooq yaji if
there is any positive news, farooq yace har yanzu ba labari, ya ma je har
department dinsu wajen malaman, and an dubo few of her Coursemates sunce ai tun
jiya bata yi attending lectures ba, wannan batu ya sa hankalin Khalil ya tashi.
Biyar saura minti sha biyar Khalil ya shirya zai je wajen Nadeeyah kamar yanda yayi
mata alkawari, yana fita ya nufi bangaren Mami xai je yayi mata sallama, a hanya ya
hadu da Mimi tace "Yauwa yayanmu pls kana da paracetamol a dakinka?" Yace "Check my
room, who is taking paracetamol?" Tace "Neehad ce tace min kanta na ciwo, so i want
to give her to take" Yace "Where is she?" Tace "tana daki" Bai kuma ce mata komai
ba ya karasa parlon Mami ya zauna, after like 15 minutes Mimi ta dawo parlon ya
daga kai yana kallonta, tace "I have given her ta sha, yayanmu fita zaka yi kayi
dropping dina gidansu frnd dita Aziza pls? Today is her birthday...." Yace "Aa, ki
je driver ya kai ki" Tace "Ohk, tot u were going out" Ta figi jakarta don dama ta
shirya tace "Bye" Yace "Wait kin gaya ma Mami?" Tace "Yeah i told her kafin su fita
da Mom, i will be back in sha Allah after Magrib" Yace "Ohk, stay safe" murmushi
tayi masa ta gyada kai sannan ta fita da sauri daga parlon, wayarsa dake hannunsa
ya fara ring ya duba ganin farooq ne ya daga da sauri, farooq yace "I just reached
her minutes ago, the stupid girl wai ta raka wata roommate dinta garinsu bata da
lafiya a nan Zaria, i still don't get dalilin da yasa bayan ta rakata bata dawo a
ranan ba, wai kuma babu wuta and bata je da power bank ba...." Khalil ya sauke
ajiyar zuciya yace "Toh Alhamdulillah, but you have to take it easy pls, kasan ba
halinta bane, baxata zauna haka kawai babu dalili a can ba" Farooq yace "That's so
stupid of her, tasan mutane nawa ta daga ma hankali a can gida, har yanzu maganar
da nake maka bamu sanar ma Abba ba, we don't even have the courage to do so, and
God being so kind dama basu waya da shi kamar yanda yake da Nihad, sai in tana
bukatar abu suke waya da shi" Khalil yace "Take it easy pls, it's well in sha
Allah" Farooq yayi masa sallama ya katse wayar, sauke ajiyar zuciya Khalil yayi don
sai yanzu yaji hankalinsa ya kwanta, Nihal have a special place in his heart cause
she's one of the kindest soul he have ever met, ita ma baxai taɓa mance kindness
dinta toward him ba, dialing numberta yayi ya fara ring, bayan some seconds ta
daga, a hankali tace "Hello" Khalil yace "Me yasa kika yi abinda kika yi Nihal?" Ta
fashe da kuka kamar jira take bata dai ce komai ba, yace "Are you okay?" Ta gyada
masa kai kamar yana ganinta amma ta kasa cewa komai, yace "Nihal" tayi karfin halin
cewa "Na'am" Yace "Don't try that again pls, idan ma zaki je wani waje ki sanar
before doing so, ur parents trusted you so well shi yasa har suka bari kika yi nesa
da su kike karatu, ita er uwarki me gathering bad friends ai kinga they didn't
allow her move an inch from kano" Nihal dai kuka kawai take bata ce komai ba, a
hankali yace "Kin ji abinda nace maki?" cikin rawan murya tace "In sha Allah" yace
"Take care of ur self pls" a hankali tace "Ka gaishe min da Nihad" Yace "I will in
sha Allah" Daga haka ya katse wayar ya mike ya fita daga parlon Mami, dakin da
Nihad take ya nufa ya bude kofar dakin gently, kwance ya sameta ta rufe har kanta
da duvet, ya karasa bakin gadon ya janye duvet din a hankali yana kallonta, she is
just wearing a short gown, ta bude ido da sauri, suna hada ido ta hade rai ta juya,
yace "Ni kika ma wannan kallon?" Ta fashe da kuka ta sake juyowa tace "Ni ba da kai
nake ba" Yace "Tashi zaune" Ba musu ta mike zaune, zai cire duvet din daga jikinta
ta rike da sauri tace "Ni ban sa kaya ba" ya daure fuska yace "Sake" A hankali ta
sake ya cire ya mayar gefe, ta sunkuyar da kanta, yana kallonta yace "What's wrong
with you?" Taki ce masa komai, sai kuma hawaye ya hau zuba idonta, Kallonta kawai
yake ba ko kiftawa, ta hade kai da gwiwa ta fashe da kuka sosai, bai san sanda ya
zauna gefenta ba ya dagota da mamaki yace "Are you okay?" Kuka kawai take ta ki
cewa komai, ta sauke kafanta daga saman gadon zata sauka ya jawota ta fado jikinsa,
sai ta kara sautin kukanta, ya rungumeta yana kallonta amma bai sake ce mata komai
ba, ta gaji don kanta tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya tana shaƙar kamshinsa,
for almost 10 minutes suna nan a haka,
jin ta sakar masa jikinta gaba daya tana sauke numfashi a hankali ya sunkuya yana
kallon fuskarta, bacci yaga tana yi, ya dinga kallon lips dinta for almost a
minute, sai kuma ya dago a hankali ya jinginar da kansa jikin gadon ya lumshe
idonsa.... Da sauri khalil ya bude ido ta dalilin wayarsa da ke ring, he realized
he just slept off also, shi da baya baccin rana balle na yamma, ya kalli Nihad dake
kirjinsa tana ta bacci kamar warce ta samu lafiyayyen katifa, ya ciro wayarsa da
sauri jin ana sake kiransa, yaga Nadeeyah ce, kallon agogon wayar yayi yaga har
shidda da minti arba'in just few minutes to magrib, he was shocked and surprise at
the same time, ya sake kallon Nihad sai bai daga wayar ba har ya katse, still
Nadeeyah ta sake kira, Nihad ta bude idonta da sauri, dagowa tayi tana kallonsa, ya
wani hade rai, ta fara kalle kalle kamar munafuka, sai kuma ta matsa daga kusa da
shi, mikewa yayi yana rike da wayarsa ya fita daga dakin, sae a sannan ya daga
kiran Nadeeyah, a hankali tace "But you said 5pm" Ya sauke wani ajiyar zuciya yace
"I am sorry Nadeeyah, i slept off without knowing i did...." Tace "Which means bani
da muhimmanci ko?" Ya ɗan hade rai yace "kin fara da korafinki again" a hankali
tace "Shikenan, sae anjima" Daga haka ta katse wayar, dakinsa kawai ya wuce ya
shiga bandaki.... Wajen karfe tara Khalil na zaune parlon Mami tare da Mimi da
Noor, Mimi na basu labari, Nihad ta bude kofar parlon a hankali, duk suka daga kai
suna kallonta, can ciki ciki tayi sallama that isn't audible, gaisuwan ma can ciki
tayi Noor dai sai kallonta take, Nihad ta nufi Mimi ta duka gabanta tana kallonta
murya can kasa tace "Pls kina da Android charger? I can't find mine" Mimi tace "Ohk
let me check" Tashi tayi Nihad ma ta mike ta bi bayanta Khalil ya bi su da kallo
har suka fita daga parlon, Ganin Nihad zata koma dakin da ta fito, Mimi tace "Mu je
sai in baki na Bilkisu" Nihad ta bi ta har zuwa bedroom din Bilkisu, Mimi na kallon
Bilkisu tace "Pls xaki ɗan mata lending charger dinki" Bilkisu tace "Ohk toh" daga
haka ta tashi ta dauko chargern ta ta mika ma Nihad, Nihad ta amsa tace "Thank you"
Bilkisu ta mata murmushi tace "My pleasure" Daga haka suka fito daga dakin, Nihad
ta wuce dakin da take, Mimi kuma ta koma parlon Mami, tana kallon yayanta da Noor
tace "Yauwa as i was saying" Nan ta ci gaba da basu labarin da take kafin ta fita,
ganin yanda Khalil ya lumshe ido Mimi tace "Yayanmu you are not listening bacci
kake" ya bude ido a hankali yace "I am sleepy" Mimi tace "Labari fa nake baka" Yayi
kasa da murya yace "Bacci" Noor ta kallesa tace "When did u start sleeping early?"
Mikewa yayi yace "Idan Mami ta shigo ku ce na tafi in kwanta sai da safe" daga haka
ya fita daga parlon....

*You people should manage this small one pls I know it's small, nayi tafiya ne*

07087865788
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

50

*Those that paid for Nihad and are complaining of too much lingua franca suyi
hakuri after today xan rage kame kamen turancin da nake yi a littafin kamar wata
kanwar mungo park, wa enda basu biya ba kuma su ji da bashin dari biyar dake kansu
kar su sake min complain din turancin da nake, ba ruwansu*😏😏

Nihad ta fashe masa da kuka hankalinta a tashe ganin babu alamar rahama a tare da
shi, ta hade hannunta pleadingly tace "Don girman Allah kayi hakuri, wallahi
tallahi na maka alkawarin baxan sake ba, i am promising you this" Ko sauraronta bai
yi ba ya sake mayar da ita saman gadon, tana ganin ya fara cire shirt dinsa ta hau
zaga kan gadon tana cewa "Don girman Allah ka yi hakuri, wayyo na shiga uku" Bata
kara tsorata da shi ba sai da taga ya cire both his singlet, bata san sanda ta kara
sauka daga kan gadon ba da nufin sake attempting din shiga bandaki da gudu, ya kara
fincikota ya mayar kan gadon, forcefully ya fara kokarin cire mata rigar baccin
jikinta wanda dama iyakarsa knees dinta, ta zaro ido ta fasa wani ihu a tsorace
tace "Wayyo na shiga uku, don Allah ka bari, wallahi ban saka komai ba..." bai ko
saurareta ba har ya fixge rigar da karfi, ta kara gwalo ido cikin rikicewa ta jawo
duvet tana kokarin rufe jikinta yana kallonta don bai yi zaton babu Bra a jikinta
ba, cause the way they are firm and pointed babu wanda xai ce bata saka Brassiere
ba, lokaci daya ya kwace duvet din yayi cilli da shi gefe daya yana ci gaba da
kallonta, tunda take bata ta6a tsayawa haka gaban kowa ba, hakan yasa duk ta rikice
taki barin ma ya kare mata kallo ta takure waje daya jikinta na rawa, tana ganin
zai dagota and that will give him access to seeing her bare chest fully, kawai tayi
saurin rungumesa ta fashe masa da kuka tace "Don Allah kayi hakuri ina rokonka, i
am ashame plssss" Ba a tsaye yake ba but he just loose his stamina all of a sudden,
ya tafi luuu ya fada kanta, bata damu da weight dinsa ba ta kara rungumesa sosai
tana kukan tashin hankali, ita a dole kar ya tashi yaga jikinta, runtse ido yayi
cause he is beginning to loose his mind, he is gasping heavily for breath, kawai
taga ya fara canza salon rungumar da tayi masa to something else and at the same
time trying to make her go completely naked before him, bata san sanda ta wani zaro
ido ta fara turashi da duk strength dinta tana kokarin tashi amma yaki bata wannan
daman, sai ta fara ganin abun da yake mata kamar a mafarki, tayi karfin halin wage
muryarta ta fasa wani ihu tana girgiza masa kai a gigice tana cewa "Don girman
Allah, don darajan iyayenka ka yafe min duk abinda na maka tun sanda ka fara
sanina, wallahi sharrin shaidan ne, don Allah kar ka min haka, wallahi baxan sake
rike wayar ba xan bar shi a wajenka...." Ko sanin abinda take cewa bai yi ba balle
kalmomin nata su ceceta, idanuwansa suka yi matukar tsorata ta, bata taɓa ganinsa a
haka ba, infact komai nasa ma ya tsoratata a lokacin nan, kamar ba Khalil da ta
sani ba, he wasn't even ready to waste anytime, he wasn't wanting to be careful in
anyway, ko kwakkwaran motsi yaki barinta tayi saboda yanda ya gwada mata ba
karfinsu daya ba, shi dai kawai ya cika burinsa a lokacin, tayi karfin halin cewa
"Wallahi ban ta6a ba, don Allah Khalil kar ka min haka xan iya mutuwa, wallahi ban
ta6a ba" a karo na farko yayi magana cikin kaushin murya yace "Baki taɓa me ba?"
Cikin tashin hankali tace "Abinda zaka min" Cikin muryar da bata san sa da shi ba
"Karya kike" Kasa ce masa komai tayi kawai tayi give up, but she is so shock, lkci
daya taji kamar numfashinta na neman dauke saboda yanda ta tsorata, kawai ta fasa
masa ihu a wahale yaga tana kokarin jawo numfashi and she immediately passed out,
duk yanda ya so ya hakura ya kyaleta bayan ya fahimci wani abu kasawa yayi, instead
yaki yin abinda yayi niyya da farko, amma still bai kyaleta ba har sai da yaji
hankalinsa ya dawo, ya koma gefenta yana kallonta babu ko kiftawa breathing
heavily, he is a doctor but he is confuse at this moment ba wai suman da tayi bane
confusion dinsa, he couldn't stop looking at her for almost 30 seconds kafin ya
tashi ya shiga bandaki ya fito da karamin towel, bayan ya gama abinda xai yi ya
zauna yana kara kallonta, ya sake duba inside of her da kyau yaga ta kankame
jikinta upon she is unconscious wanda hakan ke nuni da she is in severe pain hakan
da yayi mata, and the smallest of his finger couldn't gain access comfortable into
her, balle kuma shi da kansa, jin siren tun daga nesa ya mike da sauri yana kallon
agogo, ya dau singlet dinsa ya saka sannan ya sa shirt din, ya mayar mata da
kayanta gaba daya, ya shiga bandaki ya debo ruwa ya fito, zaunawa yayi gefenta ya
dagota yana kallonta yayi rubbing ruwan gently on her face, sai da yayi hakan sau
biyu, ta fara kokarin bude idonta kamar warce tayi bacci me nauyi sai kuma ta kara
kulle idon, jin an bude gate ya kwantar da ita kawai ya dau karamin towel din ya
bude dakin da makulli ya fita ya kulle kofar.... Ya fito wanka kenan sai ga Mami ta
shigo dakinsa, tana Kallonsa tace "Wanka kayi" ba tare da ya kalleta ba yace "Eh,
sannu da dawowa" Tace "Yauwa, kayi breakfast din?" Still bai kalleta ba yace "Nayi,
Mami baki je gidansu Nadeeyan ba?" Tace "Ehh xamu yi maganar da Hajiya Safeenah ta
waya, idan ka shirya ka sameni parlor" Yace "Toh Mami" Daga haka ta juya ta nufi
kofa ya bi ta da kallo. Khalil na gama shiryawa ya fito xai sauka downstairs ya sha
ko tea ne don wani irin yunwa yake ji, karo suka kusa ci, ya koma baya yana
kallonsa, kamar yanda shi ma yake kallonsa from head to toes, Khalil ya bi ta
gefensa ya bar wajen fuskarsa daure yayi hanyar kitchen, a nan dinning table dake
kitchen din ya zauna yana sha shayin da tunani iri iri a zuciyarsa, kawai yaji ya
ma kasa shan shayin, daga karshe ko shanyewa bai yi ba ya bar cup din a wajen ya
haura sama, direct bangaren Mami ya nufa, a hankali ya murda kofar dakin da Nihad
take ya shiga, zaune ya ganta saman gadon ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan
kuka, ta dago kai da hawaye shabe shabe a fuskarta tana ganin shine tayi saurin
mayar da kanta bisa gwiwanta wani sabon kukan na taho mata, ya karasa ya zauna
gefenta a hankali yana kallonta, amma ya rasa me xai ce, can ya mike ya shiga
bandaki ya hada mata ruwan wanka sannan ya fito ya dawo gabanta yace "Go and take
ur bath" Taki dago kai tana ci gaba da kukanta kamar ranta zae fita, ji tayi ya
dauketa kamar wata er yarinya, ta bude ido da sauri cikin kuka tace "Don Allah ka
bar ni" Bai saurareta ba har ya shiga bandakin da ita ya ajiyeta dai dai jacuzzi
dake ciki, ta durkusa da sauri ta rintse ido tana kuka, yayi kasa da murya yace
"Are you okay?" Ta kasa kallonsa don ita yanzu da gaske take tsoronsa, cire mata
rigar jikinta ya fara kokarin yi tana son hanasa amma tana tsoron yin hakan, banda
hawaye babu abinda take, tana ji tana gani ya cire mata kayan taki yarda su hada
ido, ruwan dumi da ya tara a bathtub din ya dauketa ya sakata ciki, wayarsa ya fara
ring ya ciro a aljihu ganin Mami ne ya mayar da sauri ya durkusa dai dai fuskarta
ya rada mata magana sannan ya mike ya nuna mata clean water da ya tara a wani bowl
daban, daga haka ya juya ya nufi kofar fita bandakin, sai a sannan ta bi sa da
kallo hawaye na zuba idonta. Khalil na shiga parlon Mami ya sameta zaune, ya zauna,
a hankali yace "Ga ni Mami" Mami tace "Hope kayi breakfast din?" Yace "Na yi" Tace
"Ohk, ranan kana parlon Abbanka kanwarsa ta kawo maganar yarinyar nan dake karatu
gidan nan ko?" Khalil dai yayi shiru yana kallonta, Mami tace "I am asking" a
hankali yace "Ina jin na fita sannan" tace "Toh, I covered up everything that day,
kuma nayi iya kokarin ganin i defend the girls stay in this house, na nuna masa
lallai nan zata zauna tayi karatu tunda ae ana kawo wasu ma su zauna su yi karatun
a nan babu wanda ya taɓa cewa don me, to ko sauraronsu ban yi ba ma na bar parlon,
to ban san me er uwar ta kitsa masa ba bayan fita na, Allah kadai ya bar ma kansa
sani, jiya da daddare kafin in kwanta ya kirani akan maganar dai still, and ya nuna
lallai lallai baxata zaunar masa a gida tayi karatu ba, da na nuna hakan baxai yiwu
ba naga xai xama mana ɓacin rai kawai na tashi na bar masa parlon, amma nasan Allah
baya bacci, duk me nufina da sharri a gidan nan in sha Allahu zai kare masa, zai
gani a kwaryarsa, tunda ni ban nufi kowa da sharri ba" Khalil dake ta sauraronta
yace "Mami she is staying here, ni da kaina xan samu Abban, What if here is the
rightful place for her to stay? What if she have every right to live in this
house?" Mami ta hade rai tace "Ka samesa akan wani dalili bayan na nuna masu ni na
kawota gidan nan ba wani ba, kai duk abun magana baka gudunsa a rayuwar ka ko
Khalil? Duk sun sa kayi baƙi wajen ubanka amma duk da haka kai baka gani, baka
tsaya ka gama saurarana ba xaka yanke hukunci just like that, quite alright
iyayenta sun maka kirki to tunda abubuwa suka kasance a haka ba sai mu nemi wani
solution din ba for the mean time" Khalil yace "Noo Mami, akan me zaki bari wannan
matar ta maidaki so low a gidanki, meyasa zata dinga maki abubuwa haka and u are
doing nothing about it" Mami tace "Ka saurareni pls khalil" Yace "Ina jin ki" Mami
tace "I want to show them that ko da gidan nan ko babu zata yi karatunta lafiya a
garin Abuja, kuma koma ina zata zauna she will be comfortable, wannan dalilin ne
yasa na kira Hajiya Safeenah kuma ta amince zata zauna gidanta, ba wai xata yi ta
zama gidan bne amma ina son in san ta inda xan billo ma lamarin ne, nima kaina
hakuri na ya kare a gidan nan...." kallonta khalil ya dinga yi babu ko kiftawa,
gashi ya kasa cewa komai, can yayi karfin halin cewa "Mami gidansu Nadeeyah kuma??"
Mami tace "Ehh ko ina da sama da uwar Nadeeyan ne a garin nan tunda Maryam bata
nan? Sannan i am not saying she will be staying there har ta gama karatun, kawai
dai i want to sort out things yanda ya kamata, don naga mahaifinka is taking this
issue so personal, he isn't even giving me a listening ear" khalil was speechless,
ya kasa daina kallon, Mami tace "Yanzu zan je in samu ita yarinyar ince mata zan yi
tafiya, zata koma gidan kawata kafin in dawo..." Khalil dai ya kasa cewa komai,
Mami ta mike zata fita, kamar wanda ya tuna abu yayi saurin tashi yace "Mami xan
sameta ni, i know how to talk to her about it" Mami
tace "No, kawai ka kira min ita ta zo nan" Bai ce komai ba ya nufi kofa ya fita,
yana shiga dakin da Nihad take ya ganta ta dukunkune cikin duvet ta kulle idonta,
ya zaune gefenta ya duka yana kallonta amma bata bude idon ba, ya dagota ta bude
ido da sauri, tana ganinsa ta fara ja baya taki barin su hada ido, gaba daya
jikinta a sanyaye yake and she looks so afraid, ya jawota jikinsa murya can kasa
yace "Are you okay?" Taki cewa komai and he could feel the way her heart is beating
so fast, ya kalli dogon gashinta dake a jike, ya jawo karamin towel din da yaga ta
ajiye gefe ya shiga goge mata gashin, ita dai taki yarda ta kallesa balle su hada
ido, bayan ya gama goge mata, a hankali yace "Kinyi breakfast?" Ta kasa ce masa
komai hawaye na zuba idonta, ya kara rungumeta yana patting bayanta a hankali, ya
kai bakinsa dai dai kunnenta murya can kasa yace "Why are you crying?" Still taki
ce masa komai, bayan few minutes ya saketa ya mike ya nufi inda kayanta suke ya
bude yana duba wanda xai daukar mata, dai dai nan aka bude kofar dakin, juyawa yayi
da sauri yaga Mami ce, sai da heart dinsa is skipping, yace "Erm em Mami, bama ta
jin dadi ashe tun jiya, i just came in and realize that" Mami ta kallesa ta
kalleta, Nihad dai ta kara dunkune jikinta cikin duvet don towel kawai ta daura,
Mami na kallonta tace "Me ya sameki?" Cikin karfin hali Nihad tace "Kai na ke min
ciwo" Mami tace "Toh Allah ya sauwake" Khalil ya nufi kofa ya fita daga dakin da
sauri, Mami na kallonta tace "Wanka kika yi ne?" Nihad ta gyada mata kai, Mami tace
"Toh sauko ki saka kaya sai in baki magani" Nihad ta cire duvet din, ta jawo hijab
dinta ta saka kam towel din jikinta ta sauko daga saman gadon tana tafiya a hankali
ta nufi wajen kayanta, Mami na kallonta tace "Kinji ciwo ne a kafar?" Ta gyada kai
da sauri tace "Bugewa nayi tun jiya" Ji take kamar ana mata azaba idan ta taka
kafarta da kyau, she is feeling pain down there but not terrible pain, kawai tana
jin haka ne sbda attempt da yayi, wanda ita in ance bai mata komai ba baxata ta6a
yarda ba, duk tunaninta ya mata wani abu, Mami tace "Idan kin sa kayanki ina
jiranki a parlor" a hankali Nihad tace "Toh" Bayan ta shirya ta fito tana tafiya a
hankali zuwa parlon Mami, tun da ta shigo parlon yake kallonta, shi ya ma kasa
daina mamaki seeing how she is walking, and he did nothing to her, ya kalli kofar
dakin Mami ya mike da sauri ya isa kusa da ita don a kasa ta zauna ya durkusa
gabanta yana kallonta

*Adai dinga manage pls for the meantime kun san ban koma gida ba har yanzu, thank
you*

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

52

Nihad ta dinga kallon Nadeeyah dake tahowa tare da Mimi ko kiftawa babu har suka
karaso parking space din, Nadeeyah na kallonta murmushi dauke fuskarta cikin
sanyayyen muryarta tace "Sannu da zuwa" Babu yabo babu fallasa Nihad tace "Yauwa"
daga haka kuma ta dauke kai, Khalil ya kulle motar yana kallonsu ya ɗan yi murmushi
yace "Hi Nadeey..." Nadeeyah taki yarda ta kallesa tace "Welcome" Mimi ta nuna ma
mai aikinsu Nadeeyah da ta taho trolly dinsu dake cikin mota, yarinyar ta saukar da
su daga booth din ta dauka ta wuce ciki, Nadeeyah ta dau wani karamin jaka ta bi
bayan mai aikin, Mimi na kallon Khalil tace "Yayanmu xaka shigo ne?" Khalil yace
"Yeahh, ki tafi ina zuwa xan yi waya tukun..." Mimi ta kalli Nihad tace "Let go in
Neehad" Nihad ta ki ce mata komai, Mimi ta kalli Khalil da ya fiddo wayarsa yana
danne danne kamar zai yi sending call, Ta sake kallon Nihad sai kuma kawai Mimi ta
juya ta bi bayan Nadeeyah, bayan sun yi nisa Khalil ya mayar da wayarsa aljihu yana
kallon Nihad ya dawo kusa da ita yace "Why are you not going in?" A takaice Nihad
tace "I am not staying in this house" Ya dinga kallonta, sai kuma yace "Why??" Ba
tare da ta kallesa ba tace "Ban ga zan iya ba" Shiru yayi yana kallonta, ta jingina
da motar ta rungume hannunta ta hade rai alamar she isn't moving an inch, Ya
jingina gefenta yayi kasa da murya yace "Ohk, How about we spending the night at
the hotel together" Ta kallesa da sauri, ya dage mata gira, ta dauke kai tana jin
gabanta na faduwa, ya kamo hannunta a hankali yace "Kinsan Mami ce tace ku zo nan
yau, so it won't make sense in maida ke gida ince kince baxa ki zauna ba for now
reason, so kawai mu tafi hotel" yana gama fadin haka ya bude mata back seat yana
kallonta yace "Ur usual spot" Nihad dai ta kasa cewa komai kuma ta ki shiga motar,
wayarsa ne ya fara ring ya duba yaga Mimi ce, dagawa yayi tace "Yayanmu Kai Mumy ke
jira fa bata wuce sama ba, or ain't you coming in again" Da sauri yace "Ohk, ohk
I'm coming" Daga haka ya katse wayar, yana kallon Nihad yace "Bari in je mu gaisa
da mutanen gidan, idan na fito sai mu tafi hotel din" yana fadin haka ya nufi cikin
gidan, Nihad ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, lkci daya hawaye ya cika idonta,
why will they bring her to this house, gidansu wannan er iskar yarinyar, tasan
baxata bi sa hotel ba but she will surely not stay in this house... Khalil na shiga
ya tadda Mum din Nadeeyah xaune a parlor, ya gaisheta da ladabi ta amsa da fara'a
tace "Ina bakuwar?" Yace "Yayanta ne ya kira take magana da shi a waje" Nadeeyah
dai sai kallonsa take, Mumy tace "Allah sarki" Khalil ya kalli Nadeeyah dake zaune
saman kujera suna hada ido ta dauke kai, tunawa yayi bai yi sallah ba ya mike da
sauri yace "Mumy xan yi sallah in dawo yanzu" Mum din Nadeeyah Tace "Toh je kayi...
Ga abinci xa a zuba maka kafin ka dawo...." Kofa ya nufa ya fita yana kallon
parking space, bai ga Nihad a wajen da ya bar ta ba, yayi still yana bin compound
din da kallo amma babu alamarta, cikin few seconds ya karasa gun mai gadi dake
bakin gate yana kallonsa da sauri yace "Wata ta fita gidan nan yanxu ne Malam?" Mai
gadin yace "Ehh bata dade ma da fita ba" Khalil ya zaro ido with shock yana kallon
mai gadin ya kasa ce masa komai, sai kuma ya fice da sauri daga gate din, at first
ya ma rasa ina zai bi don hanyoyi ne daban daban a area din, kawai ya dau hanyar
titi, cikin minti kadan ya iso main road din duk da nisan shi, amma bai ga alamar
Nihad ba, ya dinga bin ko ina da kallo zuciyarsa na bugawa, lokaci daya yaji wani
xufa na keto masa at the same time ƙafafuwansa suka masa nauyi.... Sai da Nihad ta
tabbatar tayi nesa da anguwan sosai sannan ta tsaya, ta cikin layuka tayi ta tafiya
har ta ganta a wani babban titi, wanda hakan yasa ta gane she is very far away from
the area she just left, tana ta tsaye bakin titi tana bin lafiyayyun motocin dake
wucewa da kallo ta rasa next step din da xata dauka, she stood there for more than
15min a bakin hanyar kafin wani mota yayi parking kusa da inda take tsaye, ta koma
baya tana kallon motar, wani mutumi da baxai wuce shekara 55 ba ya sauke glass yana
kallonta yace "Yan mata ina zuwa? Ki shigo in rage maki hanya mana kina ta tsayuwa
a nan" Nihad dake ta kallonsa taki cewa komai, yace "Haba yan mata ya kika yi
shiru, naga tun daxu kike ta tsaye a nan, har na shiga wancan supermarket din na yi
siyayya na fito" Sai a sannan Nihad tace "Bani da kudin mota ne, na yar da jakata"
Yace "Subhanallahi, to shigo in ajiye ki inda za ki ko, Allah ya tsare gaba" Nihad
tace "Sai dai ka bani kudin motar" Dariya yayi yace "Toh nawa ne kudin motar" Ta
ɗan yi shiru sai kuma tace "Ko nawa ne ka bani" Yace "Toh amma me yasa baxa ki
shigo in ajiye ki ba, ba fa ɗan yankan kai bane ko ɗan Kidnapper, Kinga dare yayi
bai kamata mace kamarki na tsaye bakin hanya a wannan lokacin ba" Tayi shiru ta ki
cewa komai, yace "Toh bari a baki kudin motar tunda baki yarda da ni ba, amma wani
anguwa kike?" Tace "Can gaba ne" Ya ciro kudi ya mika mata hade da wayarsa yace "To
sa min number wayarki yan mata" Ta amshi kudin ta ajiye masa wayarsa kan kujera me
zaman banza tace "Nagode, amma bani da waya wallahi" Tana gama fadin haka ta ci
gaba da tafiyarta da sauri, ya bi ta da kallo baki bude. Tafiya kawai Nihad take
amma bata ga alamar adaidaita sahu ko daya unguwar ba, gashi ta gaji sosai abun ka
da bata saɓa da tafiyar kafa ba, har lokacin kuma bata duba nawa mutumin ya bata
ba, daga karshe ta ganta a gaban wani babban supermarket, a nan taga wani me
adaidaita ta nufesa da sauri tace "Tasha zan je" yace "Wani tasha?" Tace "Inda ake
hawa motar kano" yace "Toh mu je" tace "Nawa ne?" Mutumin yace "Dubu biyu" Nihad ta
kalli kudin hannunta ta fara kirgawa taga dubu biyar ne, ta shiga adaidaitan, ya
tada suka bar wajen, Nihad na isa tashan bayan ta ba mai adaidaita sahu kudin ta
shiga ciki, ai ko ta samu mota da xai kama hanyar kano a lokacin, nan ta tambayi
nawa ne kudin mota aka ce mata dubu takwas, tayi kuri da ido ta kasa ce masu komai
don dubu uku kadai ne a hannunta, can ta koma gefe ta tsaya kamar munafuka, dreban
motar yace "Hajiya nawa xaki bada?" Tayi shiru sai kuma tace "Ni bani da kudi amma
idan na baka wannan xaka karba?" Tana magana tana kokarin ciro dankunnen kunnenta,
duk da akwai haske a wajen sai da mutumin ya kunna fitilar wayarsa yana haska ɗan
kunnen da kyau, can ya kira wani abokin aikinsa shi ma ya duba, Mutumin na kallonta
yace "Ai kawai ki fadi nawa zaki siyar ba cuta ba cutarwa sai a baki kudinki ki
cire kudin mota" Nihad tace "Ai ban san nawa zaka siya ba" Yace "Kin siyar dubu
talatin?" Nihad dai tayi shiru sai kuma tace "Toh" Mutumin yace "Toh ina zuwa" Can
sai gashi da cash din dubu talatin ya mika mata, Nihad ta amsa ta kirga dubu takwas
ta basa, sannan ta shiga motar wanda duk maza ne a ciki, suka bar mata jikin window
ta zauna.... Mami ce tsaye parlor tare da Mum din Nadeeyah suna kallon Khalil dake
zaune saman kujera ya ki ce masu komai, kana ganinsa kasan yana cikin tashin
hankali, Mimi sai hawaye take, Noor dai na zaune saman kujera don tare da Mami suka
zo gidan, Nadeeyah kuma na tsaye can kusa da dinning area, Mami tace "Magana fa
nake maka ka min shiru Khalil, ina kake tunanin yarinyar mutane zata tafi da
daddaren nan? Lokaci fa na wucewa" Mikewa yayi without looking at them yace "Nima
ban sani ba" Daga haka ya nufi kofa, Nadeeyah ta bi sa da kallo har ya fice daga
parlon, Mumy ta saki salati tace "Wallahi duka duka ko minti goma fa basu yi da
shigowa gidan ba, har nake tambayarsa tana ina da naga ita bata shigo parlon ba
yace tana waje tana waya da yayanta, ina yar mutane ta shiga ni Safeenah" Mami dai
ta kasa cewa komai don hankalinta ya tashi ita ma, where are they going to start
from, kasa ci gaba da tsayuwa tayi ta nemi kujera ta zauna tana furta innalillahi
wa inna ilaihi raji'un a zuciyarta.... Ko barin Abuja Nihad basu yi ba bacci ya
dauketa a motar, Khalil bai jin ya taɓa shiga tashin hankalin da ya shiga a wannan
lokacin, ko abinda Abbansa yayi masa bai daga masa hankali irin wannan ba, ganin
abun yake kamar a mafarki fa, ya ma rasa wani tunanin zai yi, sai da yaga karfe
goma yayi tashin hankalinsa ya fara fitowa sarari, tun takwas su Mami suka koma
gida don barinsu ma yayi a gidan yayi wucewarsa, amma saboda yanda hankalin Mum din
Nadeeyah ya tashi haka ta sake bin su gidan tare da Nadeeyah, Duk suna zaune
parlorn Mami wajen karfe goma da yan mintuna khalil ya shigo parlon ta dalilin
kiran da Mami tayi masa, Mami tayi karfin halin cewa "Nace ka kira gidansu ka ki,
nace ka kira yayanta ka ki, to wai ya zan yi da kai, in ma baxa ka kira ba ni ka
bani numbersu mana, wannan wani irin tashin hankali ne" Khalil that was trying all
possible means to be calm yace "In kirasu ince masu me Mami? I should call and tell
them I can't find their daughter cikin daren nan? In kirasu ince masu an kasa rike
yar su a gidanmu saboda kanwar Abbana tace baxata zauna ba kuma Mamina bata da
abinda xata iya yi game da hakan? Mami ni na zata akan yarinyar nan sai inda
karfinki ya kare, i thought zaki yi repaying good deeds din da iyayenta suka min ta
hanyar riketa just like su Mimi, ina ce you will always be there for her, if not
for her family i would have been depressed by now, right in front of u Abbana sent
me away from his house and u couldn't do anything about it, kina gani na bar gidan
nan baki iya yin komai a kai ba, naje inda suka rikeni ba tare da sun san ni ba har
suka damka min amanar dukiyarsu amma ta haka za muyi repaying dinsu mu kasa rike
masu tasu er?" Mami dai kallonsa kawai take ta rasa abinda xata ce amma duk jikinta
yayi sanyi, juyawa yayi ya fice daga parlon Nadeeyah ta bi sa da kallo babu ko
kiftawa, Hajiya Safeenah ta nemi kujera ta zauna tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un" Wajen karfe biyu da rabi na dare Nihad suka shigo garin Kano, tayi bacci
har ta gode Allah a hanya, mamaki ya cikata ganin adaidaita har sannan a tasha,
tana kallon
wanda ke tambayarta inda xata tayi shiru, tana tunanin ko dai kawai taje hotel ta
kwana tunda tana da kudi kuma tasan prices din hotels na Kano, nan ta gaya masa
hotel dai dai kudinta ya tafi da ita kuwa, tana sauka ta basa kudinsa ta shiga
ciki, ta biya kudin daki aka bata makulli ta wuce zuwa dakin, wanka ta fara yi a
bandaki sannan ta dauro alwala tayi magrib da isha ta kwanta, amma ta kasa bacci
sai juye juye kawai take, babu wanda ke ranta kuma a lokacin sai Nadeeyah, she just
hate her with passion, bata son ganinta kwata kwata, da tasan gidansu zasu je da
tun daga gidansu Khalil ta gudu don ko haduwa da ita bata so har cikin ranta....
Karfe takwas saura na safe Nihad ta tashi daga baccin da ta koma bayan tayi sallan
asuba, ta fita waje zuwa supermarket dake kusa da hotel din ta siyo brush da
maclean ta koma ciki, kafin karfe tara har ta gama shiryawa ta fito ta tare
adaidaita yana tambayarta inda xata tayi shiru, don sai a sannan gabanta ya fara
faduwa don bata san me xata je ta tarar a gida ba, kilan ma Abba ya koreta idan
taje, amma a haka ta dake ta gaya masa inda xata sannan ta shiga adaidaitan a
sanyaye, ya kama hanyar gidansu, tunda suka dau hanya gabanta bai daina faduwa ba,
bayan tafiyar kusan minti talatin suka iso gidan, at first kasa sauka tayi daga
cikin adaidaitan ganin ya juya yana kallonta, tayi karfin halin sauka ta basa
kudinsa ta nufi gate tana tafiya a hankali, she is so afraid, daurewa kawai take,
bude gate din tayi taga Aminu zaune bakin gate da er radio a hannunsa, yana ganinta
ya zare ido ya mike da sauri yace "Hajiya" Ta ɗan yi murmushi tace "Aminu" Bakin
Aminu har kunne ya dinga mata sannu da zuwa, sai kuma ya nufi waje da gudu duk
zatonsa tare take da Khalil, Nihad dai ta ci gaba da tafiya gabanta na faduwa ganin
motar Abbanta a parking space, taga motar ya Usman ma alamar yana gidan, har ta isa
balcony dinsu ta kasa daga kafarta da kyau, tsoro ne fal zuciyarta, ta kusa minti
daya a tsaye kafin ta murda kofar a hankali ta shiga ciki tana kallon parlon, Umma
ta fito kitchen kenan rike da breakfast din da ta hada ma Nihal tayi sororo bakin
kofa tana zaro ido tace "Wa zan gani kamar 'ya ta Nihad?" tun da Nihad ta mata
kallo daya ta dauke kai ta nufi bangaren Mumy tana tafiya a hankali, Umma ta buda
baki with shock ganin abinda tayi mata ta bi ta da kallon mamaki, tuni Nihad ta
bude kofar Parlon Mumy a hankali ta shiga, Mumy ta fito dakinta kenan tayi ido hudu
da Nihad, still tayi bakin kofar dakin tana kallonta with surprise, Nihad ta tafi
da gudu ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Mumy dai ta kasa motsi, can tayi
karfin halin dago kanta tace "Daga ina?" Nihad na Murmushi tace "Gida Mumy" Mumy
tace "Ke da wa??" Nihad tace "Ajiyeni yayi yaje ya dawo" Bude kofar Parlon aka yi
duk suka daga kai, Umma ta shigo, Nihad na ganinta ta shige dakin Mumy ta kulle
kofar, Umma tayi kasake a inda take tsaye, Can tayi karfin halin cewa "Ko ba Nihad
bace?" Mumy ta kirkiri murmushi tace "Ehh wallahi, yanzun nan ta shigo na ganta
nima" Umma tace "Allah sarki, to sannunta da zuwa, ina jin ta gaji ne" Daga haka ta
juya ta fita daga parlon, Mumy ta juya ta koma dakinta da sauri tana kallon Nihad
tace "Me yasa kika yi mata haka ta zo ganinki Nihad? Why did u leave the parlor"
Nihad dai tayi shiru bata ce komai ba, Mumy tace "Why didn't u greet her?" A
hankali Nihad tace "I need rest, and beside ke na zo gani" Mumy dai ta kasa cewa
komai ta dinga kallonta, Nihad tace "Mumy ina jin yunwa" A hankali Mumy ta juya ta
fita daga dakin don kawo mata breakfast, Mumy na fita ko minti uku ba ayi ba Nihal
ta shigo dakin....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

51

Nihad ta ki yarda su hada ido da shi, ya dinga kallonta don duk a tsorace take, ya
kamo hannunta zai yi magana aka bude kofa Mami tayi ta fito daga dakinta, Khalil
yayi saurin tashi daga kusa da ita ya nufi kujera, Mami ta kallesa ta kalleta, ita
dai Nihad kanta na kasa, Mami tace "Ya ciwon kan? Kin sha magani?" Nihad still bata
dago kanta ba tace "Na sha" Mami tace "Toh Allah ya sauwake, je kiyi kwanciyarki
kawai...." Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita, Mami na kallon Khalil fuska daure tace
"Ban gane ma'anar shisshige ma yarinyar nan da kake ba Khalil?" Ya zaro ido da
sauri, sai kuma ya xauna yace "Mami shisshige mata kuma? I just saw she is sick
and...." Mami ta katse sa rai bace tace "If she is sick ni baxan iya mata abinda ya
kamata ba sai kai? Sannan who did she tell she is sick? i see no reason da xai sa
kana shiga dakin da take at the first place ita ba muharramarka ba, meye ma'anar
hakan? to gaskiya bana so, don't ever try it again, idan wani abu ya dameta ta zo
ta gaya min bana son wannan shige matan da kake we are not pagans" Khalil ya mike
yace "Mami ai baki taɓa gani na...." Dakatar da shi tayi tace "Bana son jin komai,
na dai gaya maka abinda xan gaya maka, khalil ya dinga kallonta ya kasa cewa komai,
ta juya tayi komawarta cikin dakinta, a hankali ya koma ya zauna ya jinginar da
kansa jikin kujera ya lumshe ido, kansa bai taɓa kullewa yanda ya kulle ba yanzu,
ya ga alama it's not going to be easy, it doesn't look Mami will take things easy
kafin aje ga Abbansa, sai a sannan ya fara tunanin he wished bai boye ma Aunty
Maryam komai ba tun farkon dawowarsu, may be she will have understood him, yasan
yanzu its too late ita kanta baxata fahimcesa ba yanxu, it's just too late, bayan
wani lokaci Mami ta fito daga dakinta ko kallonsa bata yi ba ta nufi kofa zata
fita, ya jima bai ga ta hade masa rai haka ba, wannan yasa jikinsa yayi sanyi, he
don't think she will ever support him in any way, Mami xata bude kofar parlon aka
bude before her, hakan yasa ta daga kai suka yi ido hudu da shi, da fara'a tace
"Aa, Aliyu yaushe ka dawo?" Yace "Not too long Mami" Khalil ya wani murtuke fuska
yana danna wayarsa, Mami ta koma ta zauna tana kallon Aliyu tace "Sannu da zuwa, ai
ban san ka dawo ba wallahi" Ya zauna saman kujera yace "Ina yini Mami" Tace
"Alhamdulillah, ka dawo lafiya?" yace "Lafiya lau Alhamdulillah" Mami tace "To maa
sha Allah, gaskiya ka dade sosai wannan karan" ya ɗan yi murmushi da iyakarsa baki
yace "Na shigo ne in gaisheki dama...." Tace "Toh Nagode Aliyu, i will be coming
downstairs later, you are welcome dear" Yace "Alright" Mikewa yayi ya nufi kofa ya
fita daga parlon, Mami ta kalli Khalil da damuwa tace "Why didn't u speak to him
Khalil?" Khalil kamar jira yake yace "Why will i speak to him Mami?" Mami ta
girgiza kai tace "No.... gaskiya bana son haka, tunda ya shigo har nan ya gaisheni
menene a ciki don ka gaisa da shi? Me yake yi som" Khalil yace "Am i his mate da
xan fara gaishesa Mami? or da can ya saba shigowa gaisheki a nan idan ba hypocrisy
ba, look Mami i am begging you to stop forcing me do what isn't necessary, babu
abinda ya hadani da su" Mami tace "No Khalil, me yasa kake daukan komai da zafi a
rayuwarka ne? ko kaki ko ka so ɗan uwanka ne fa" Khalil ya mike yace "Ba ɗan uwana
bane ban hada komai da shi ba..." Mami ta daure fuska tace "Kace min ba ɗan uwanka
bane" Yace "I want to excuse my self plss" Kallonsa Mami ta dinga yi, yace "I said
i want to excuse my self Mami" Mami ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "Ohk"
Juyawa yayi ya fice daga parlon a fusace, Mami ta girgiza kai irin zuciyar Khalil
na damunta, he is the one always causing problem for himself, sai yace baya tsoron
kowa, hatta mahaifinsa tasan yanda duk suke shakkarsa shi baya yi, shi yasa yana ce
masa ya bar masa gida ko minti goma bai kara ba a gidan yayi gaba, bayan few
minutes ta girgiza kai ta mike ta fita daga parlorn ta nufi dakin da Nihad take don
ce mata ta hada kayanta, Khalil yayi stiff a bakin kofar dakin don zai fito kenan
sai ga Mami, Kallonsa Mami take babu ko kiftawa ta ma kasa ce masa komai,
confidently yace "I left my phone in here, so i came to pick it up" Daga haka ya
bar ta tsaye bakin kofar without waiting for her reply, ta bi sa da kallo, Can ta
shiga cikin dakin, Nihad na kwance ta rufe ido kamar me bacci, Mami ta dinga
kallonta for some seconds, sai kuma ta karasa kusa da gadon, Nihad ta bude ido da
sauri, ganin Mamin ta mike ta zauna tana murza idonta, Mami tace "Are you feeling
better now?" Nihad tace "Alhamdulillah" Mami stood for almost a minute looking at
her, Sai kuma ta juya ta fita daga dakin. Khalil na komawa bedroom dinsa yaga miss
calls din Farooq, zaunawa yayi gefen gado yayi dialing number, yana fara ring
Farooq ya daga, suka gaisa sannan farooq yace "I think Nihal will be going to kano
for the weekend don dazu Umma ta kirani tace in tura mata Tp ta ce mata ta taho
Kano, after exams ai xata iya zuwa Abujan ko?" Da sauri khalil yace "Sure ba
damuwa, i think that will even be better" Farooq yace "Toh maa sha Allah" Daga haka
suka yi sallama khalil ya katse wayar. Mimi na dawowa makaranta Mami ta shigo
dakinta, Mimi dakw goge jikinta da towel tace "Mami good afternoon" Mami tace
"Afternoon dear, kina ji na" Mimi ta kalli Mami tace "Ina ji Mami" Mami tace "Za ku
je gidansu Nadeeyah ke da Nihad ku yi 2 days a can" Da mamaki Mimi tace "Why Mami?
Me ake yi a gidan?" Mami tace "Ba komai, but you have to do as i say" Mimi tace
"Ohk" Mami tace "Idan kin huta kin ci abinci anjima sai kice mata ta shirya
kayanta, kema ki shirya naki" Mimi tace "Toh" Juyawa Mami tayi ta fita daga dakin.
Nihad na kallon Mimi dake zaune gefenta a kan gado tace "Ina za mu je?" Mimi ta
wara ido tace "Somewhere, gidan sister din Mami" Nihad felt a bit relieve jin haka,
don dama har cikin ranta ta gaji da gidan nan, and har zuciyarta taji bata son tana
ganin Khalil don wani tsoronsa take ji, da ta tuna abinda yayi mata sae taji hawaye
ya zubo mata, ita duk tunaninta ae ya santa fa, a hankali Mimi tace "But pls tell
me Neehad, why are u always unhappy, ur eyes are often swollen, u are always
silent, ko baki son gidanmu ne?" Nihad ta sauke idonta bata ce mata komai ba, Mimi
tace "Or are you not comfortable here? Am i not nice to you? Kinga ai bakya haduwa
da cousins dina da step sister dita Hanan, basa shigowa part din nan so it's rear
ku hadu, and idan kika saki jiki da Noor xa ki ga she is also nice, u misunderstood
her ne kawai from the beginning" Nihad dai ta kasa ce mata komai she wish she can
tell her abinda khalil yyi mata ko zata samu saukin abinda ke damunta a zuciya,
Ganin haka Mimi ta sauke ajiyar zuciya tace "So now kawai ki hada kayanki, nasan
you won't get boring gidan da za muje cause they are not strict, we will be having
enough freedom there to go anywhere unlike here, and i will be taking u out to many
places in Abuja" A hankali Nihad tace "Okay thank you" daga haka ta sauka daga
saman gadon ta tafi wajen kayanta, Mimi ta bi ta da kallo, seeing how she is
walking tace "Are you injured?" Da sauri Nihad ta kalleta tace "I am getting better
now" Mimi tace "Ohk"

Umma na jera kayanta da Isiya me wanki da guga ya kawo mata dazu a Press aka bude
kofar dakinta, daga kai tayi tana kallon kofar ganin Amina tace "Wai baki tafi
islamiyyar ba?" Amina tace "Umma, Aunty Nihal ta dawo" Umma ta ajiye kayanta da
sauri tace "Kai haba, oyoyo oyoyo" Daga haka ta fice daga dakin da sauri ta tafi
can bangaren Mumy ta shiga dakin Nihal, Kwance ta ganta Mumy na zaune gefenta, cike
da farin ciki Umma tace "Oyoyo autana, sannu da zuwa, sannu da zuwa" Sai kuma ta
karasa bakin gadon tace "Aa baki da lafiya ne?" Nihal ta girgiza kai tace "Aa
lafiyata qlau" Mumy tace "Nima tambayar da nayi mata kenan, ina jin gajiyar hanya
ce kawai" Umma tace "To taso mu je, ga favourite dinki can na maki" Nihal tace
"Umma bana jin yunwa sai anjima" Umma tace "Ni dallah taso, dubi yanda kika rame
kamar baki cin abinci a makarantar, ni wallahi wannan jarabbaben makarantar ya
isheni Allah ya so shekaran karshe kike ki huta mu ma mu huta" Mumy tace "Tashi
kije Nihal" Nihal ta sauka daga kan gadon ta bi bayan Umma suka fita daga dakin,
Mumy dai ta bi su da kallo, at times ganin Nihal na sa ta mance duk wani damuwarta,
yana rage mata kewar Nihad da take, tana jin Nihal kamar Nihad a zuciyarta, sannan
tun bayan da Farooq ya kirata ya sanar mata yaje har inda Nihad take a Abuja, Mumy
ta samu rest of mind, duk da yace sauran bayanan sai ya shigo Kano zai mata amma ta
kwantar da hankalinta Nihad is fine and comfortable where she is. Umma ta cika ma
Nihal abinci a gabanta, ita dai Nihal ta daura chin dinta a saman gwiwarta tana
kallon abincin, Umma ta dawo ta zauna tace "Toh deba ki ci mana" A hankali Nihal ta
jawo plate ta fara zuba abincin, Umma dai sai kallonta take don ta rame sosai ba
kadan, sannan ba lively Nihal dinta take gani a nan ba, Umma tace "Nihal" Da sauri
Nihal ta dago ta kalleta, da damuwa Umma tace "Did you have any problem?" Nihal ta
girgiza kai da sauri tace "Aa Umma, i am okay" Umma tace "Na ganki a sanyaye kamar
kina da damuwa daughter" Nihal ta girgiza mata kai kawai tace "Ba komai Umma" daga
haka ta ci gaba da dibar abincin da take, Umma na ta kallonta tace "Ko dai Nihad
kike tunani har yanzu Auta?" Lokaci daya taga hawaye ya kawo idon Nihal, nan da nan
hankalin Umma ya tashi, ta mike don a duniya babban tashin hankalinta kukan Nihal
ko kuma damuwar Nihal, Umma tace "Yanzu meye abun kuka? Wallahi in dai Nihad ce ni
sai in sa duk inda take a samota in hakan ne xai sa ki daina damuwa, in ma kauyen
xaki je ki masu kwana biyu sai kije in dai wannan ne damuwarki Nihal" Nihal dai ta
kasa cewa komai sai goge hawayen da yaki tsaya mata take, nan Umma ta hau
lallashinta tana jin kukan nata har cikin ranta. Da yamma Umma ta dau makullin mota
ta fita sai gidan Hajiya Turai, bayan sun gaisa Umma tace "Anya turai baxa ki sake
rakani gidan malamin nan ba a sassauta abin nan da yayi" da mamaki Hajiya Turai
tace "Saboda me?" Da damuwa Umma tace "Toh Nihal ce har yanzu na rasa gane kanta
wallahi, duk ta sukurkurce, kinsan sun shaku sosai da er uwar, wallahi daxu da naga
test script dinta sai da hankalina yayi mugun tashi, Nihal da bata taɓa faduwa a
makaranta ba, gashi shekaran karshe take, a'a gaskiya mu je a sassauta abin nan
Turai" Hajiya Turai tace "A karya asirin kenan nufin ki?" Umma tace "Aa, a karya
kuma?? Cewa nayi fa a sassauta yanda dai Uban zai bar Nihad din ta shigo gidan amma
babu yabo babu fallasa sannan ko sisinsa baxai shiga hannunta ba balle na dreban,
kin dai gane ai, ni dai in samu hankalin 'ya ta ya kwanta, ta ci gaba da karatunta
cikin aminci" Hajiya Turai tace "Amma abun da mamaki, tun da can bata daga hankali
haka da abun ya faru yana zafi zafi ba sai yanxu?" Umma tace "Ke kuwa sabo, nima
dai farko naga bata yi haka ba duk da ta damu gaskiya, amma wai daga zuwa makaranta
shkkn abu ya lalace, Sai ma kiyi ta kiranta a waya bata son dagawa, gaba daya tayi
sanyi yanda kika san an zare mata laka, wallahi abun na damuna, kuma nasan saboda
er uwarta ne, gashi yanzu naga uban ma yana jan ta jiki tunda ba Nihad din, ko
Shekaranjiya ce min yayi xai canxa mata laptop, to taki kwantar da hankali" Hajiya
Turai tace "Toh sai mu koma gobe" Umma tace "Yauwa Hajiya turai, sannan ita ma
Kamila ina son a kara aiki akan mijinta, don suna ta samun matsala kwanan nan, ita
kuma Nihal wani da minister ya fito yana sonta shi ma sai ayi aiki a kai" Hajiya
Turai tace "Duk Allah ya kai mu goben" Umma bata jima a gidan ba tayi mata sallama
ta kama hanyar gida.
Dab da magrib Nihad ta gama shiryawa tana tsaye gaban mirror tana daura Nikab dinta
sai ga Mimi ta shigo ita ma ta shirya, Mimi ta wani ɓata fuska tace "C'mon plss
where r u going with this mask, ba fa school xa mu je ba" Bata jira me Nihad xata
ce ba ta kwace Nikab din, Nihad ta juya tana kallonta don khalil ne yace ta sa
Nikab din, da tayi niyyar baxata sa ba amma kuma kawai ta dauko daga karshe, Mimi
na girgiza kai tace "Don Allah ki dau mayafi ki yafa mu fita, we are not going to
school fa, beside this is evening" Nihad tace "I am more comfortable with the Nikab
Mimi" Mimi tayi shiru tana kallonta, Nihad ta mata murmushi ta amshe Nikab din a
hannunta ta shiga daurawa, Mimi ta daga kafada ta fita daga dakin xuwa parlon Mami,
ganin Khalil zaune parlon tace "Yauwa yayanmu pls ka kai mu mana since u are
around, i don't want to be escorted" Ya kalleta sai kuma yayi kasa da murya yace
"Tell Mami so" Da sauri ta shiga daki wajen Mami tace "Mami since yayanmu yana nan
ya kai mu can gidan mana" Mami tace "Ohk" Mimi tayi murmushi ta juya ta fita ta
kulle mata kofa, Tana kallon Khalil tace "She said ohk" Daga haka ta fice daga
parlon. Mimi ta sauka downstairs tare da Nihad bayan Bilkisu ta kai masu kayansu
waje, dai dai stairs din karshe Nihad ta makale jikin rail din staircase din tana
kallon wanda ta gani zaune parlor ko kiftawa babu, yana tare da 3 of his frnds ga
drinks da kaza with small chops a gabansu, they were all gisting suna dariya, Mimi
ta kalleta ganin kamar she is shock tace "What happen Nihad?" Nihad tayi backing
parlon da sauri kamar xata koma sama tana zaro ido ta cikin Nikab din fuskarta,
Mimi ta kama hannun Nihad da mamaki tace "Are you alright?" Nihad ta kasa cewa
komai xuciyarta na heaving, Mimi na rike da hannunta tace "Nihad" Da sauri Nihad ta
kalleta, with confusion Mimi tace "What happen?" Nihad tayi karfin halin cewa
"Nothing, nothing" Mimi ta kama hannunta suka sauka daga stairs din, kin kallon
inda su Aliyu suke tayi tana makale da hannun Mimi tana shige mata kamar xata harde
ta fadi, gaba daya mamaki ya cika Mimi, Can dai Mimi ta kalli su Aliyu da suka bi
su da kallo tace "Yaya sai mun dawo" Yana kallonta yace "Ohk" Daga haka suka fita
daga parlon tana rike da hannun Nihad, Mimi ta kulle kofa tana kallonta tace "Kin
san wani a cikinsu ne?" Nihad ta hadiye wani abu da kyar ta girgiza mata kai, Mimi
dai ta dinga kallonta, Nihad tayi karfin halin cewa "Who is the guy in white?" Mimi
tace "He is my cousin brother, did u know him?" Nihad ta kasa ce mata komai tana
kallonta babu ko kiftawa, lokaci daya taji komai ya tsaya mata ga wani jiri da ke
dibanta, ta dinga nanata kalmar cousin da Mimi ta furta mata a zuciyarta, Can Nihad
tayi karfin halin cewa "Can i know his name pls??" Mimi tace "Aliyu, his name is
Aliyu Iliya, yayansu Sajida and Farhana" a hankali Nihad ta dinga gyada mata kai
amma ta kasa cewa komai, Mimi tace "But don Allah ki gaya min, kin san sa ne? U
reacted as if kin ta6a saninsa" Da sauri Nihad ta girgiza kai amma ta kasa cewa
komai har sannan, bayan few seconds tayi karfin halin cewa "What is his
relationship with ur brother?" Mimi tace "Of course they are cousins, my brother is
Ibrahim Khalil Jikamshi, while he is Aliyu Iliya, mum dinsa ita ce Aunty Hassana ai
kin santa...." Nihad was Baffled, taji zuciyarta na wani irin bugawa tace
"Jikamshi?" Mimi tace "Yeah, that's my father" Mimi ta wara ido tace "You mean all
this while baki san gidan da kike ba?" sunkuyar da kai Nihad tayi a hankali tana
jin jikinta kamar an zare mata laka, Mimi dai sai kallonta take, can dai Mimi tayi
murmushi ta kama hannunta suka bar wajen, Har suka isa mota Nihad jan kafa take
tana ganin komai kamar a mafarki, a ranta kuwa ta fadi Aliyu Iliya ya fi sau goma,
for the first time she felt life had never been nice to her, she's been deceived in
so many ways by so many people, Umma, her frnds, and now Aliyu, nothing was in her
favor during her pass, a yan kwanaki kadan taga abubuwan da bata ta6a zato ba a
lkcn da bata ta6a tunani ba, a yan kwanakin nan ta fahimci not everything is as it
seems, she felt so stupid of her self at this point, tayi da ta sanin abubuwa da
yawa na rayuwarta a baya, she wish she can amend things, but how will that be
possible, Mimi ta dinga kallonta bayan ta bude mata back seat amma taga bata shiga
ba alamar tayi nisa tunanin da take, kamar ma bata san sun kai parking space din
ba, a hankali Mimi ta dafata, firgit Nihad ta dawo duniyar tunanin da ta tafi, Mimi
ta nuna mata motar, Nihad ta shiga da sauri trying all possible best kar ta bar
hawaye ya taru idonta balle har ya kai ga zubowa, why she?? Why is all this
happening to her?? Mimi ta zaga ta shiga gaban motar, sai a sannan Nihad ta daga
kai suka hada ido da khalil dake kallonta ta madubi, sosai gabanta ya fadi, kuma
bata taɓa jin kunyar duk abubuwan da tayi masa ba sai yau, she felt so ashame of
her self, yau ne taji kunyarsa na gaske, a kwanakin baya tana jin guilt a xuciyarta
na abubuwan da suka faru amma na yau ya wuce misali, and she remembered vividly
ranan da ya kai ta Wellcare wajen Aliyu da abinda ya faru, yanda ta cakumesa a
wuyar riga raining all sort of insult on him, bata san sanda ta hade kai da gwiwa
ba wasu hawaye masu zafi suna sauka idonta, many things are not as they seem, truly
not everything is as it's seems, ta yaudari kanta sosai a baya, Khalil ya tada
motar suka bar gidan, sai da suka yi nisa ya kalli Mimi yace "Ba ki bukatan komai?"
Mimi ta ɗan buda ido tace "In dai expenses din na kanka" Ya ɗan yi murmushi yace
"Ohk, where are we going now?" Ta kira masa wajen wani shopping, nan ya dau hanyar
zuwa wajen, suna isa yayi parking ya ciro Atm card dinsa ya mika mata, ta amsa tace
"I thought tare xa mu shiga" Yace "Nahh, ke kadai za ki shiga, i have done my part
by giving u my card" tace "Can i shop for two?" Ya gyada mata kai, kulle motar tayi
ta juya ta bar wajen yana ganin ta shiga ciki ya sauka ya shiga bayan motar, shi da
yake bai biyo ta main parlor ba bai san su Aliyu na parlon ba ma, Nihad taji wani
kukan ya taho mata jin ya shigo bayan motar, ya dago kanta a hankali yace "Now tell
me what's ur problem" ta kasa kallonsa tana shesshekan kuka sosai, she wish many
things didn't happen, she wish she was so kind to everyone back then, bata taɓa
sanin Umma bata sonta ba sai da Aunty Maryam ta ganar da ita, she encouraged her to
be mean to everyone, ya cire nikab din fuskarta yana kallonta, ta boye fuskarta da
sauri wani kuka ya taho mata, kunyar hada ido da shi take, ya jawota jikinsa ya
rungumeta a hankali yana kokarin kai hannunsa in between her legs yace "Does it
hurts har yanzu?" Bata san sanda ta zaro ido ba ta rike hannunsa da sauri, closing
her leg tightly tace "Aa" Yace "Then what?" Shiru tayi bata ce komai ba tana sauke
ajiyar zuciya a jikinsa, she felt a bit relieved, tana jin breathing dinsa a
fuskarta kamar me rada yace "You need the phone?" Shiru tayi Idonta a rufe bata ce
komai ba tayi lamo a jikinsa, Shi ma bai kuma ce mata komai ba ya lumshe idonsa
yana sauke numfashi a hankali, Nihad ta bude ido tayi karfin halin cewa "Me ya
kawoka gidanmu?" Bai bude ido ba still yana taɓa kafarta yace "We should ask Habibu
that" Da sauri ta daga kai ta kallesa, da sauri Khalil ya saketa ganin Mimi ta fito
daga mall din rike da just er leda, ya bude motar ya sauka ya koma front seat, tana
karasowa ta shiga gaban motar ta ajiye ledan hannunta tana Murmushi tace "just 2
perfumes" Yace "You are not serious" Dariya tayi, ya tada motar suka bar wajen. Har
suka isa anguwansu Nadeeyah Nihad bata daina tunanin abinda yace mata ba wai they
should ask Habibu, how did he know Habibu, gari yayi duhu suka iso gidansu Nadeeyah
don har an idar da magrib, bayan yayi parking ya sauka motar, Mimi ta sauka ita ma
tana rike da ledan turaren da ta siyan ma ita da Nihad, Nihad ta sauka daga cikin
motar, Mimi tace "Bari in kira me aiki ta dau mana kaya" Daga haka ta wuce ciki,
Nihad ta bi ta da kallo, sai kuma ta kalli Khalil taga kallonta yake da sauri ta
sunkuyar da kai ta juya zata bar wajen ya fizgota ya hadeta da mota yana kallon
lips dinta, gaba daya ta rikice don mai gadi na zaune kusa da gate, ta fara turasa
zata bar wajen sai ga Mimi ta fito tare da Nadeeyah, da sauri ya saketa ya bude
driver seat kamar zai dau wani abu.

Kika karanta min littafi baki biya ba bashin dari biyar a kanki har duniya ta nade.
Ehe 😌
Nihaad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

53

Nihal ta karasa har inda Nihad take tana kallonta ta zauna gefenta with smile all
over her face, a hankali tace "Welcome sis" Nihad ta sauke idonta tace "Thank you
Nihal" Nihal tace "Ina Khalil din?" Nihad ta kalleta tace "He is fine" Nihal tace
"Ohk ba tare ku ke ba?" Nihad tace "Ajiyeni yayi kawai" Nihal tace "Ohk, kinyi kyau
sosai sis" Ta karasa maganar tana murmushi, Nihad dai bata ce mata komai ba, Nihal
ta kamo hannunta cikin sanyin murya tace "And i miss you so much" Nihad tace "Same
here" Nihal tace "I am happy u are home" Shiru Nihal tayi bata ce komai ba, can
Nihal ta mike a hankali tace "Zan je inyi wanka" Nihad tace "Ohk" Daga haka ta nufi
kofa Nihad ta bi ta da kallo har ta fita, Tana fita da few minutes Mumy ta shigo
dakin rike da tray, Hafsah na biye da ita da flask, cike da murna Hafsah tace
"Sannu da zuwa Aunty Nihad" Nihad ta kalleta tana ɗan murmushi tace "Ya kike
Hafsah" Hafsat tace "Alhamdulillah Aunty" Nihad tace "Ya aiki?" Hafsah na washe
baki tace "Lafiya lau, munyi kewarki sosai Aunty" Nihad dai tayi murmushi kawai,
Mumy dai ta zauna sai kallon Nihad take cike da mamaki, yaushe har ta wani san da
zaman Hafsah a gidan balle har ta mata fara'a haka har da tambayarta ya aiki,
Hafsah ta juya ta fita daga dakin, Nihad ta sauko ta zauna saman Carpet ta dau cup
ta debi ruwan zafi, bayan ta gama hada shayin ta daga kai ta kalli Mumy taga
kallonta take, Nihad tace "Mumy Nihal tayi rashin lafiya ne?" Mumy tace "Me kika
ga?" Nihad tace "Aa kawai naga ta rame" Mumy tace "Tun dai kwanaki a school but
she's better now, kawai stress din makaranta ne, you know she is in her final year"
Nihad bata ce komai ba, bayan few seconds cikin sanyin murya tace "Su sudais sun
tafi school?" Mumy tace "Ehh..." Shiru Nihad tayi tana juya shayin gabanta, Mumy
tace "Ya yan uwan mijin naki gaba daya?" Nihad tace "Duk suna nan lafiya, suna
gaishe ku" Mumy tace "Toh maa sha Allah, shi xai shigo nan ne a hada masa
breakfast?" Nihad ta girgiza kai tace "Aa sai anjima" Mumy tace "Toh shkkn" Mikewa
tayi ta fita ta bata waje don ta karya comfortably don taga kamar duk a ɗari ɗari
take. Nihad na gama breakfast din ta dau tray din ta fita main parlor, har ta mance
yaushe rabon tayi breakfast cikin dadin rai haka, Zaune ta ga Nihal da Mumy a
parlor, Hafsah dake goge goge ta taso da sauri tace "Bari in kai maki kitchen
Aunty" Nihad tace "Aa Nagode, ci gaba da aikinki xan kai" Daga haka ta wuce kitchen
din Nihal ta bi ta da kallo haka ma Mumy, Dai dai nan Umma ta shigo parlon daga
bangarenta kamar warce aka hankado rike da makullin mota, ko lura da Mumy bata yi
ba tana kallon Nihal tace "Idan Abbanku ya fito kice masa jikar Hajiya Turai ta
fada cikin ruwan zafi yanzu aka kirani na tafi gidan, bana son tashinsa yana bacci,
sannan don Allah ki tafi dakina zaki ga kayana saman gado duk na birkito ki jera
min, sauri nake shi sa ban maida su ba" Nihal tace "Toh Allah ya sauwake" Mumy dake
ta kallonta tace "Subhanallahi, ayi masu sannu don Allah" Tuni Umma ta fice daga
parlon cikin hanzari ba tare da ta ma san Mumy na wajen ba. Nihad ta fito kitchen
kenan sai ga Abba ma ya fito daga parlonsa jin tashin motar Umma don ba bacci yake
ba, hada ido suka yi da Nihad, Sosai gabanta ya fadi ta makale jikin kofar kitchen
din ko ina na jikinta ma rawa, Ita kanta Nihal dake zaune sai da gabanta ya fadi,
Mumy dai ta sunkuyar da kanta kawai, Abba dai kallon Nihad kawai yake babu ko
kiftawa, Nihad ta sauke idonta kasa, lokaci daya taji hawaye ya cika idonta, Abba
ya dauke idonsa daga kallonta yana kallon Nihal yace "Ina Baabarki ta tafi?" Nihal
tace "Wai jikar Mama Turai ce ta fada cikin ruwan zafi shine ta tafi" Juyawa Abba
yayi ya koma parlonsa, Nihad ta bi sa da kallo hawaye na sauka idonta, mikewa Mumy
tayi ta bar parlon ta shiga nata duk jikinta a sanyaye, Nihal ta karasa kusa da
Nihad ta kamo hannunta a hankali tace "Mu je ki gaishesa" Nihad dai bata ce komai
ba hawaye sai bin fuskarta suke, haka Nihal ta nufi parlon Abba da ita tana rike da
hannunta, Zaune suka gansa parlon ya jinginar da kansa jikin kujera, Nihad ta ki
barin su hada ido ta durkusa daga nan bakin kofar tayi gathering courage muryarta
na rawa tace "Abba ina kwana" Yana kallonta bayan few seconds yace "Me ya kawo ki
gidana?" Ta girgiza kai hawaye me zafi na sauka idonta tace "Kayi hakuri Abba" Bai
kuma ce mata komai ba sai dauke kansa da yayi daga kallonta, staring at the Ac in
his parlor, Nihal ta juya ta fita daga parlon hawaye cike idonta, mikewa Nihad tayi
da sauri ta bi bayanta tana goge hawayen da ya ki tsaya mata, Abba ya bi ta da
kallo lokaci daya yaji hawaye ya kawo idonsa, mikewa yayi ya shige bedroom dinsa,
Nihad ta koma bangaren Mumy ta shiga bedroom dinta ta ga Mumy zaune gefen gado
looking so worried, fadawa kan gadon Nihad tayi tana kuka a hankali, Mumy tayi
karfin halin cewa "Me yace maki? Yace ki bar masa gidansa ko?" Nihad ta kasa cewa
komai sai kuka take sosai, Mumy bata san sanda ita ma ta fashe da kukan ba, taji
zuciyarta na mata zafi, Nihad na ganin haka ta mike da sauri ta rungumeta tana kuka
sosai tace "I am sorry i never listened to you mum, kiyi hakuri ki yafe min
plsss..." kasa ci gaba tayi saboda kuka da ya ci karfinta, Mumy tayi karfin halin
cewa "Baki min komai ba Nihad, na yafe maki duniya da lahira, babu abinda kika min,
haka Allah ya tsara maki rayuwarki babu kuma wanda ya isa ya canza hakan" Nihad na
kuka bitterly tace "Amma Mumy baki taɓa ce min Umma ba so na take ba, u never told
me she is misleading me, nobody was there to tell me all this, Umma caused me all
what i am passing through now" Mumy ta dakatar da kukan da take tana sauraronta
babu ko kiftawa, Cikin kuka sosai Nihad tace "Duk abinda nake yi a baya Umma ce
take sa ni inyi, she neva gave me the chance to differentiate what's good or bad,
she is always supporting me in every aspect, i don't know she was just ruining my
life, ta cuci rayuwata, me yasa baki taɓa gaya min bata sona ba, me yasa baki gaya
min ba masoyiyata bace? mumy me nayi mata?" Mumy ta girgiza kai kawai wasu hawayen
na sauka idonta ta kasa ce mata komai, A hankali Nihad na girgiza kai sounding
bitterly tace "Ita ta karfafa min gwiwa wajen yin kawance da su Husnah, she
encourage me to follow them everywhere, ta nuna min duk wani dake aiki a gidanmu
bashi da value i should treat them harshly idan ba haka ba za su raina ni...." Mumy
tayi shiru sai sauraron Nihad take, Nihad tace "Mumy ba wani gidan Aunty Kamila da
naje, duk watanni hudu da nayi bana gidan nan ina hostel tare da su Husnah, i never
went to Auntt Kamila's place Umma planned it for me...." Mumy bata san sanda ta
mike tana kallon Nihad babu ko kiftawa ba, Nihad na share hawayen da yaki tsaya
mata cike da karfin hali tace "Ita tace ma Kamila ta kira Abba tace za mu je kebbi
amma babu wani kebbi da muka je, all those while i am staying in the hostel with my
frnds, duk wani hotel da party da su Husnah za su Umma tasan ina bin su ita ke
encouraging dina in bi su, duk sanda na fita da daddare zuwa party Umma ce ke bude
min kofar parlor babu wanda xai sani, tun da na taso muke haka da Umma....." Tana
kai wa nan ta hade kai da gwiwa tana kuka me ban tausayi, she is deeply regretting
everything now, tayi da ta sanin abubuwa da yawa da tayi a baya, nobody was there
to tell her Umma ba sonta take ba all that while, wasu abubuwan ma baxata iya gaya
ma Mumy ba amma Umma ta cuceta ta cuceta iya cuta, sannan ta nuna mata da ma duniya
gaba daya babu wanda take so sama da ita, Mumy dai ta kasa cewa komai sae kallonta
take babu ko kiftawa, kana ganinta kasan she is shock, don duk bata san da abubuwan
nan da Nihad ke fadi yanzu ba, ta dai san komin laifin da Nihad xata yi a gidan
Umma bata barin a mata fada sai ta nuna ai yarinya ce babu abinda ta sani, sannan
ko me take so wajen Abba Umma ke taimaka mata wajen amsa, ko kai maye ne baxaka ce
Umma bata son Nihad da gaske ba, sai ta siya ma Nihad abu sau goma bata siya ma er
ta Nihal ba, wannan ne ma ya sa Mumy ta kara jawo Nihal jikinta sosai.... Nihad ta
zamo kasa muryarta na rawa tace "Don Allah ki yafe min Mumy, amma ban taso na gan
ni a wajenki ba, i never knew u were my mother at first, Mumy me yasa kika bar ma
Umma ni? Why did u hand me over to her?" Tana kai wa nan ta hade kai da gwiwa tana
kuka sosai, Wani kuka ya taho ma Mumy bayan memory din yanda Umma ta rabata da
Nihad ta karfi da yaji tun tana 5 years ya dawo mata vividly.... Mumy tayi duk iya
kokarinta na ganin Abba bai dauke Nihad daga wajenta ya damka ma Umma ba har hakan
sai da yayi sanadin igiyar aurenta daya a gidan, babu irin bakaken maganganun da
Inna bata gaggaya mata ba a wancan lokacin wai bata da kara bata da kunya akan yar
ta ta fari, ina ruwanta da er ta na fari da har zata zakalkake a kanta tana nuna
tafi kowa iko da ita sae kace ba bafillatana ba, banda zamani ya lalace, su
zamaninsu babu macen da ta isa tayi haka, har inna ke kara tunatar mata cewa Umma
bata rike ɗan ta na fari da na biyu ba bata ma san ta yanda suka girma ba ta kauda
kai a kansu kamar ba ita ta haifesu ba, Ya Farooq da ya Usman basu taso wajenta ba,
tun daga yaye inna ta daukesu suka koma wajenta a Bauchi kuma Umma bata taɓa cewa
don me ba, yawancin rayuwarsu duk a wajen Inna suka yi a lokacin ma kakansu na da
rai, sae ya kasance Kamila ce kawai gaban Umma and she never complained for once,
har dai ta zo ta haifi Nihal, washegari kuma Mumy ta haifi Nihad, wanda sai da Mumy
tayi shekara goma a gidan kafin ta haihu, duk tana gidan aka haifi Usman da Kamila
amma ita Allah bai bata haihuwa ba, dalilin da yasa da ta haifi Nihad Abba ya dau
son duniya ya daura mata gashi fara ce kal kamar zaka latsa ta jini ya fito, ga
masifar kyau kamar er larabawa, dama shi farin yaro da shegan shiga rai yake, ita
kuma Nihal baƙa ce amma suna kama sosai da Nihad, sai ya dau Nihad sau goma bai dau
Nihal sau daya ba don Nihal tana da kiwiya sosai shi sa ma bai bin ta kanta, ba ta
yarda da kowa sai Umma, hakan
yasa yafi shakuwa da Nihad da ko muryarsa taji ta dingi kuka kenan sai ta gansa ya
dauketa, shakuwa me tsanani ya shiga tsakaninsu ya dau soyayya mara iyaka ya daura
mata, har cikin ransa yake jin Nihad, wanda Mumy na lura da Umma kamar hakan baya
mata dadi don bata iya boye hakan a fuska, ga kuma er ta Nihal shegen kiwiya da
kuka, Mumy kan ce ma Abba ya daina bambanta su kar a samu matsala, nuna banbancin
bashi da amfani don duk daya suke a wajensa, amma sai yace mata ai Nihal kiwiya
gareta bata yarda da kowa, haka rayuwa ya ci gaba har aka yayesu, tun Nihad na
shekara uku Umma ta fara nuna tafi damuwa da ita akan Nihal kamar yanda taga Abba
ke yi, ta sha attempting mayar da Nihad dakinta gaba daya amma Mumy taki bada
fuskar hakan, don babu Alkunya take shiga ta dauke er ta ko da kuwa bacci take a
dakin Umma komin dare kuwa, ko hularta bata yarda ta bari a dakin Umma, Umma bata
hakura ba har sai da ta san yanda ta hada makircin da ta hada tare da goyon bayan
Inna Nihad ta dawo wajenta, Wanda har sai da Abba ya saki Mumy akan issue din wai
tana son raba masa kan gida, ga inna ta saka ta gaba da gore gore wai ai ba da ita
ta zo gidan ba sannan ina ruwanta da er ta ta fari idan ba rashin kunya ba, karfi
da yaji dai aka raba Mumy da Nihad, babu yanda Mumy ta iya tana ji tana gani ta
cire hannunta akan wasu lamarin Nihad ta bar ma Umma gaba daya, and that was the
genesis of the whole problem.... Mumy ta kasa ci gaba da zama dakin ta fita kawai
ta koma parlor tana jin xuciyarta na mata zafi, Umma ta cuceta ta cuceta, ita kuwa
bata ma er ta irin rikon da tayi ma Nihad ba, Nihal da kanta ta koma bangaren Mumy
a lokacin ma tayi shekara goma, tana ji tana gani sae Umma ta hana Nihad shigowa
wajenta, babu kusanci kwata kwata tsakaninta da Nihad, to amma ya zata yi, tunda ga
abinda mijinta da uwar mijinta suka ce, kawai sae ta rungume Nihal tana ganinta
kamar yar cikinta. Nihad ta ci kukanta ta koshi ta mike ta koma saman gadon Mumy ta
kwanta ta rufe idonta a hankali tana jin kanta na ciwo, a haka har bacci ya dauke
ta. Wajen karfe goma da wani abu Nihad ta bude ido a hankali ta dalilin tashinta da
aka yi, ta mike zaune tana kallon Nihal dake zaune gefenta, Nihal tace "Ana kiranki
a parlor" Nihad na murza idonta tace "Waye?" Nihal ta mike tace "Ki fito" Daga haka
ta mike ta fita daga dakin, Nihad ta mike da kyar ta nufi kofa ta fita Parlon Mumy,
zaune ta gansa duk ya wani birkice yana kallon kofar dakin eagerly, suna hada ido
ta sunkuyar da kai a hankali, Nihal ta juya ta fita ta rufe kofar parlon, sai a
sannan ya mike da sauri, Nihad tayi saurin juyawa zata koma dakin yayi hanzarin bin
ta har ciki ya fizgota, zaro ido tayi tace "Don Allah ka bari kar wani ya shigo"
kin yarda su hada ido tayi taki dago kanta, da taga he is trying to raise her head
up kawai ta kwanta saman kirjinsa tayi lamo, she could feel how fast his heart is
beating, ta lumshe idonta a hankali, ya rungumeta sosai, Underneath his breathe
taji yayi maganan da ita kanta bata ji ba, jin hawayenta a jikinsa ya dago kanta da
sauri yana kallonta, kasa barin su hada ido tayi, cikin rawan murya tace "I am...
Am sorry, i..." sai kuma ta kasa ci gaba ta fashe da kuka, Lokaci daya ya saketa
jin an bude kofar parlor, ta goge idonta da sauri ta fito parlon sai ta ga Nihal ce
ta shigo rike da ruwa da lemo, Khalil ya fito parlon shi ma ya zauna, Nihal dai
bata yarda ta hada ido da su ba. Tashin hankalin da Mami ta shiga ba a cewa komai
da ta shiga dakin Khalil da sassafe taga baya ciki, kuma bata ga alamar ma a dakin
ya kwana ba, tun sannan take kiran duk layinsa taji su a kashe, ta ma rasa
takamaiman abinda zata yi, tun cikin dare take Allah Allah gari ya waye ta samesa
tace masa ko za su je can kano ne gidan iyayenta ko Allah ya sa can ta tafi, sai
gashi ta shigo babu shi a dakin, ta dawo bangarenta cike da damuwa, tana zaune tare
da Mimi a parlon tace "Kuma ko number yayanta baki da shi ko?" Mimi ta girgiza kai
a hankali tace "Bani da shi" Bude kofar parlon aka yi, duk suka daga kai, Mami ta
dinga kallonsa da mamaki don in ba dai tana kwance ba lafiya ba baya shigowa
bangarenta kai tsaye haka, sannan ko minti ashirun bai yi da dawowa gidan ba, kuma
ba ita ce ma da girki ba, Mimi ta mike ita ma tana kallonsa tace "Good morning sir"
Bai amsa mata ba ta nufi kofa ta fita, Mami na ganin yanayinsa ta san ba lafiya, to
me kuma ya faru, ta dai mike cikin dakewa tace "Lafiya kuwa Yallabai? Is everything
alright" Yana huci yace "Stop asking me that, Ina Ibrahim? Provide him now" Mami
sai da gabanta ya fadi, tayi karfin halin cewa "Is everything alright" tsawa ya
daka mata yace "Ina maki tambaya kina amsa min da tambaya?" Ta koma ta zauna bata
sake ce masa komai ba, ya sake jefo mata tambayar ina Ibrahim, a fusace tace "Tunda
dai ba goya Ibrahim nake ba ta ina xan san inda yake da sassafen nan? Ba dai ka san
hanyar dakinsa ba" Yana muzurai yace "Ohh haka kika ce?" Tace "Ya kake son ince?
Naga dai ba nan yake kwana ba da ka zo nemansa a nan, za ka wani zo ka isheni ina
Ibrahim" Ya fi second ashirin yana kallonta yana gyada kai, kafin ya juya ya fice
daga parlon almost ripping the door off, tagumi tayi tana tunanin to me kuma yaron
nan yayi? Wannan wani irin fitina ne ita kam, Noor ce ta shigo parlon tana kallon
Mami a sanyaye tace "Mami kin san me Yayanmu yayi?" Mami da taji gabanta na faduwa
sosai tace "Me yayi Noor?" Noor ta zauna cikin sanyin murya tace "He broke into
Abba's room and collected all what Abba seized from him, lalata makullin dakin ma
fa yayi" Buda baki Mami tayi ta kasa cewa komai zuciyarta na bugawa, Noor tace "Ina
jin cikin dare kowa na bacci yayi haƙan, he scattered everywhere in the room" Mami
ta saki salati ta rafka uban tagumi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" sai
ga Aunty Hassana ta shigo parlon babu ko sallama cike da rashin mutunci tace "Ke
kam fatima kin haifar mana fitina a gidan nan, don Khalil fitina ne wallahi...."
Mami ta dakatar da ita tace "Ban haifi fitina ba sai in ke kika haifi fitina
wallahi"

*Thanks for being patient with Khaleesat*

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

54

Mami bata tsaya ta kara sauraran Aunty Hassana ba ta mike ta shige dakinta ta
shirya ta fice ta bar masu gidan daga ita har yayan nata zuwa gidan Hajiya
Safeenah. Tana zaune parlon Hajiya Safeenah abun duniya ya isheta, Hajiya Safeenah
tace "Na fa ce ki kwantar da hankalinki Hajiya Fatima, yarinyar da har nude video
dinta yayi yawo a gari ai kinsan dama can idonta a bude yake kome aka ce ta aikata
to zata iya aikatawa, ke dai kawai Allah ya shirya mana zuri'a, kuma babu tantama
kila gidan nasu ta koma, ke kuma kina nan duk kin bi kin daga hankali" Mami dake ta
kallonta tace "You have a point, sai yanzu da kika yi maganan nan na tuna wacece
yarinyar, duk yaron da idonsa yayi budewar da nata yayi koma meye zai iya aikatawa
gaskiya kika fada, ni fa wallahi bani da yanda xanyi ne amma ni ba wai son zamanta
nake a gidana ba, haka kawai taje ta kara aikata wani abun da ba shikenan ba, gashi
baka gane gabanta balle bayanta, nukurcinta yayi yawa, sannan kwana biyun nan ina
ta lura da yanda Khalil din ke shige mata, sam bana son haka...." Hajiya Safeenah
ta rike haɓa tace "Au, ashe kema dai kin lura, jiya bayan mun dawo gida zancen da
Nadeeyah ta kawo min kenan...." Mami tayi shiru da tunani iri iri a ranta, can ta
sauke ajiyar zuciya tace "Wallahi abun ya dameni, to yace mana wajen iyayenta ya
zauna a kano ya zanyi masa, ga Maryam me goyan bayansa, tukunna ma dai wasu irin
iyaye ne xasu hada yar su da gandameme kamar Khalil wai su taho Abuja tare sannan
ya bar ta a gidansu wai zata yi karatu? A ina aka taɓa haka kamar dai garin gaɓa
gaɓa aka taso? Idan ma haka ne ai kamata yayi uwar ko uban wani ya biyota sai a
damka mana ita a hannu ace gata nan don Allah zata yi karatu a sa mata ido, to wai
sai aka hadata daga ita sai khalil ya kawo mana ita, ko marasu addini baxa su yi
haka ba, ni wallahi na rasa yanda zanyi ne, i have a big question mark on this
issue, ga Maryam tayi ɓake ɓake kan lamarin sai goyan bayansa take wai sai an
riketa tunda iyayenta suka rike shi, to shi ba namiji bane ko da da kafafuwansa
yaje gidan nasu shi kadai, ita kuwa ai sai cikin iyayen wani ya rakota saboda halin
rayuwa, komai fa na son tsari a rayuwar nan, amma sam wannan lamarin ba tsari, a
hada baligi da baliga wa enda ba muharraman juna ba" Hajiya Safeenah tace "Gaskiya
abun dubawa ne wannan, kuma kika ce kwanaki yayanta yaje gidan ko?" Mami tace "Ehh
yaje kam, amma ko da iyayen ma baxa su biyota ba ai sai su ba yayan nata ya kawota
ba Khalil ba, it's making no sense to me now, tun farko ya kamata inyi masa wannan
tuhumar amma hankalina bai je ba, sannan ban taɓa jin an kirata daga can gidan nasu
ba ko kuma ita ta kirasu" Hajiya Safeenah tace "Toh dai ki kara kiran layukan
Khalil din ko xaki samu, aji in gidan ta koma kin ga hankalin kowa sai ya kwanta,
sai kuma a koma next issue that's on ground" Mami ta sake dialing number Khalil,
luckily ya fara ring, gyara zama tayi ta sa handsfree tana jiran ya daga, sai da ya
kusa katsewa sannan ya dauka, tace "Khalil me ya kai ka dakin Abbanka?" Khalil ya
ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ajiyata na dauka Mami" Mami ta bude baki tana kallon
Hajiya Safeenah, can tace "Ajiyarka? Wato khalil duk yanda zaka daga min hankali
shi kake nema a rayuwarka ko? Ba nace ka fita batun abubuwanka da ke hannun Abbanka
ba? Me yasa baka jin magana ta ne fisabilillah" Khalil yayi kasa da murya yace
"Mami i did nothing wrong, bayan takarduna babu wani abu da na taɓa masa a dakinsa,
i seriously need them Mami, tunda ke baxa ki iya dauko min ba shine fa na dauka da
kaina Mami...." Mami ta buda baki, ta ma rasa abinda xata ce masa, can tayi karfin
hali tace "Duk inda kake ka dawo ina nemanka immediately, sannan kada kayi making
mistake din zuwa gida ka zo nan gidan Hajiya Safeenah ka sameni" Ya ɗan yi shiru,
sai kuma yace "Toh" Mami zata katse wayar, Hajiya Safeenah tace "To baki tambayesa
batun yarinyar ba" Mami da har ta manta tace "Ohh, Sannan ita kuma yarinyar can ina
fatan gidansu ta tafi?" Khalil yayi shiru kamar baxai ce mata komai ba, sai kuma
yace "Eh" Mami tace "Toh madallah, sai ka gaya ma iyayen nata taki zama Abujan,
it's better kawai su nema mata transfer ta koma Kanon da karatu ya fi" Khalil dai
bai ce mata komai ba, tace "Baka ji na ne?" A hankali yace "Ina ji" Tace "Then do
as i say, kai kuma immediately ka taho gidan Hajiya Safeenah ina jiranka" Yace "Ni
bana Abuja yanzu" Buda baki Mami tayi tace "Kana ina?" Yace "Ina kano" Tace "Ohh
kanon ka bi ta? Kana nufin kanon ka kama hanya ka tafi ko gaya min baka yi ba? To
ka kyauta, maza maza ka nemi next flight ka taho Abuja yanzu" Yace "Ba jirgin da
zai tashi yau saboda weather" rai bace Mami tace "To wannan kai ta shafa ka biyo
mota kawai ka dawo na gaya maka" Daga haka ta katse wayarta, cike da fada tace
"Banda ma lalacewa tunda yarinyar ta zo gidan daga uwar har uban babu wanda ya taɓa
kira muka yi magana da su, don su ma ji ya yarinyar take, kawai ga ta nan dai kamar
bata da iyaye, kana da ya mace har hankalinka zai kwanta idan bata gabanka, babu
wanda fa ke bibiyar lamarinta nake gaya maki, duk ina lura da komai, kinga ai
saboda tsabar yanda idonta ya bude ai Kano ta kama hanya tayi wucewarta daren jiya,
wanda bai saba ba ai baxai yi haka ba, ko tsoron dare bata ji ba, dama can ta saɓa
abunta ne, Allah ya shirya" Hajiya Safeenah ta sauke ajiyar zuciya, Mami tace "Tun
farko da ya samu matsala da uban Yemen nace ya tafi ya ki, na dawo nace ko zai je
Uk nan ma yaki, all that while ban san yana kano ba na dai san yana Nigeria, to
gidan wasu irin mutane ne ya zauna wa enda basu da kula haka? Ka sakar ma duniya
yar ka mace a wannan zamanin, sannan ga dai abinda yarinyar nan tayi ko wata uku ba
ayi ba amma har ku sakankance baku bibiyar lamarinta, a'a ban taɓa ganin haka ba
tun da nake" Hajiya Safeenah tace "Yanzu dai Hajiya Fatima kiyi hakuri, a bi komai
a sannu ki kirasa ya bar zuwan nasa gobe tunda yace ba jirgi, biyo mota daga kano
zuwa Abuja ai aiki ne babba yanzu, kawai ki masa hakuri ya bari har gobe, bari in
kirasa" Daga haka Hajiya Safeenah ta kira Khalil, nan ta sanar masa kawai ya bari
gobe sai ya biyo jirgin safe, bayan ta katse wayar Mami tace "Dama yana dawowa duk
zan amshe takardun in mayar ma uban baxan iya fitina ba, idan jiƙawa zai yi ya
shanye sai ya jika ya shanye, babu abinda zai raga Khalil da shi" Hajiya Safeenah
tace "Aa kar kiyi haka, ki bar wannan issue din tsakaninsa da ubansa kawai kar kiyi
involving kanki, gaskiya kar kiyi haka, kamar yanda ya fada ke baki amsar masa ba
kuma ya amsa sai kice xaki mayar?" Mami tace "Wallahi mayar masa shine kadai mafi
alkhairi gare mu gaba daya, sai kace baki san General ba, ni duk wani abun tashin
hankali bana so wallahi, har fargaban zuwa asibiti nake yanzu yanda nake ji a
jikina sai ya iya yiwuwa jini na ya hau" Hajiya Safeenah tace "Allah ma baxai sa
hakan ba, kawai kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki Hajiya, komai zae zo da sauki"
Mami ta taɓa baki tace "Ya batun programs na bikin, kun gama shawaran da Hajiya
Hauwa?"

Bayan Azahar ganin Khalil bai shigo ba Mumy na kallon Nihad tace "Ki je kiyi masa
magana ya shigo ya ci abinci" Nihad da tunda tayi sallah take zaune saman darduma a
bedroom din Mumy ta mike ta dauke darduman ta linke sannan ta fita, Hijab ne har
kasa jikinta don ta shiga bedroom dinta ta kwaso sauran kayanta ta kawo bangaren
Mumy ta ajiye, har zuwa sannan kuma Umma bata dawo gidan ba, babu kowa main parlor
din ta fito compound ta gansa zaune tare da Aminu, ɗan zaman da Khalil yayi a wajen
babu abinda Aminu bai sanar masa ba da ya faru a gidan bayan tafiyarsu sai wanda ya
manta, dawowar Kamila gida, matsalar da Usman ya samu wajen aikinsa, rashin
walwalan Abba a ko da yaushe tun tafiyarsu, yanda Umma ke fita ta dawo dab da
magrib kafin Abba ya dawo motarta duk jan laka, zuwan karshen da Inna tayi gidan ta
zauna nan compound tana ta tikar kuka wai an rabata da Nihad an daura mata aure da
ɗan kauye tana can ita ma ta zama er kauye, sabon dreba da aka kawo me warin baki
da warin hammata ga shegen gulma, murmushi kawai khalil ke yi yana kallon Aminu da
ke basa labaran nan with passion babu abinda yake tsallakewa a labarin, in details
yake badawa, he is so good in it, in wanda xai yi demonstrating ne sai ya tashi
yayi demonstrating sannan ya koma ya zauna, yana cikin basa labarin yanda banki
suka zo suka kulle gidan dake can karshen layi saboda bashinsu da ya ci na fitar
hankali sai ga Nihad ta karaso, duk abinda Aminu ke cewa Khalil baya apprehending
tun fitowar Nihad, don ainahin kamshin da ya santa da shi ne ya cika wajen still
dai bai daga kai ya kalleta ba, Aminu ya mike yana washe baki yace "Sannu Hajiya,
sannu da karasowa...." Nihad tace "Sannu Aminu" Daga haka ta kalli khalil tace
"Mumy tace ka shigo ka ci abinci" Sai a sannan ya kalleta kamar baxai ce komai ba
sai kuma yace "Kawo mana nan" Tayi shiru tana kallonsa, can ta juya ta bar wajen ya
bi ya da ido har sannan kamshin na dukan hancinsa, sai da tayi nisa Aminu ya koma
ya zauna yace "Kai mutumina, amma kayi jahadi wajen dawo da yarinyar nan hanya mai
bullewa, wallahi duk jikina yayi sanyi kamar ba Nihad din da na sani ba a baya,
dubi fa yanda ta zama ta gari, ko da dai dama wannan matar uban nata ce ke zugata
duk mun sani, wani nutsuwa na musamman fa take da shi yanzu, shi yasa jiya da
naganta ta dawo ita kadai na maza na kiraka inji ina kake don na zata guduwa tayi,
ashe dai ta nutsu, sannan ga...." Khalil ya dakatar da shi ta hanyar cewa "Ina
jinka, sai bankin suka kulle masa gidan" Aminu ya gyara zama yace "Wallahi kuwa in
gaya maka, bawan Allahn ya fito yayi ta birgima a layin nan duk muka taru kansa, ga
matansa da ya'yansa a gefe abun dai zar tausayi, an fa ce caca yake yi, kuma ɗan
giya ne....." Khalil ya dinga kallon Nihad da ta fito, hakan yasa Aminu yayi shiru
yana ɗan murmushi ganin Khalil bai ma san me yake cewa ba, har ta iso inda suke da
tray din abincin ta durkusa gabansa ta ajiye, shi dai kallonta kawai yake, ta mike
tace "Me sanyi ruwan za a kawo?" Sae a sannan ya dauke idonsa yace "Duk wanda kika
kawo" Juyawa tayi ta bar wajen still ya bi ta da ido, the perfume is just something
else, Aminu dai sai wani murmushi yake irin na rubabbu, yau wai Nihad ce ke kawo ma
Khalil abinci har ta durkusa ta ajiye masa a gabansa yarinyar da har hana a basa
abinci tayi a gidan, Aminu ya rike haɓa uwa ɗan daudu yana nazari... Sai bayan
la'asar Khalil ya shiga cikin gidan shi ma Sudais ne ya zo yace masa Mumy na
kiransa, parlor ya samu Mumy, Mumy tace "Kana ta zama a waje Ibrahim" Ya ɗan yi
murmushi yace "Muna tare da Aminu ne" Tace "Kuma ba rana" Yace "Aa babu" Tace "Toh
ko bayan magrib ne sai ku tafi can gidan Inna ku gaisheta" Yace "Toh Allah ya kai
mu" Bai wani jima a parlon ba tunda ba wai hira suke da Mumy ba ya fita ya koma gun
Aminu, Mumy ta koma parlonta tana kallon Nihad tace "Me yasa baki je dakin er
uwarki ba Nihad?" Nihad dake game da wayar Mumy tace "Naga kamar bata son magana
ne, i don't want to inconvenience her" Mumy ta zauna tana kallonta tace "Amma ai ta
shigo nan har sau nawa saboda ke Nihad" Nihad tace "Ko ta shigo ba magana take ba,
i don't know why she is silent" Mumy bata kuma cewa komai ba, bayan few minutes
tace "A ina kuke a Abujan?" Nihad tayi shiru, sai kuma ta daga kai ta kalli Mumy
ganin kallonta take, ta sauke idonta a hankali tace "Maitama" Mumy ta ɗan bude ido
tace "Maitama kuma? Akwai wani maitaman ne bayan wanda na sani?" Nihad ta girgiza
mata kai tace shi wannan din ne, da mamaki Mumy tace "Wajen wa a Maitama?" Ita dai
farooq yayi assuring dinta sosai yace ta kwantar da hankalinta Nihad is doing very
fine, idan ya zo kano za su yi magana, iyakar abinda ya gaya mata kenan amma bai
gaya mata anguwan ba ko inda take, Mumy tace "Kin yi shiru" Nihad ta ajiye wayar
hannunta a hankali tace "Gidan iyayensa" Mumy look so confuse, tace "Wani iyayen
nasa kuma?" Nihad ta sauke idonta tace "He is the son of General Jikamshi" Kallonta
kawai Mumy take, can tace "Are you okay Nihad?" Nihad ta kalli Mumy, a hankali tace
"He disguise himself, I don't know his reasons, I don't know.... but they are rich,
he is the son of General Abubakar" Mumy da duk kanta ya daure tace "Ke ban gane ba,
wani general din? Sannan ba Aliyu bane ɗan gidan General? Kanki daya kuwa Nihad, ko
dai zaki je ki kwanta ne...." Nihad tayi wani murmushi kawai, can ta girgiza kai ta
goge hawayen da ya taru idonta tace "Aliyu lied to me, ba shine yaron jikamshi ba,
Jikamshi is just his uncle which is Khalil's father" Sai kuma ta fashe da kuka
cikin sanyin murya tace "Mumy naga abubuwan iri iri in just 3 months from every
angle, Khalil isn't who we thought him to be, i don't know his intent of coming to
our house, I don't know his intent of coming here as a driver, they are super rich,
his father is a General, his mum is from Yemen, i don't just...." Sai kuma ta hade
kai da gwiwa tana kuka a hankali bayan ta tuno abubuwa da yawa, Mumy was
speechless, ta ma rasa me xata ce, sai kallon Nihad din take inna State of
confusion, kuma har cikin ranta taji bata yarda da abinda Nihad ta fada ba, seems
bata da lafiya, Mumy ta mike ta dagata tace "You need rest, go and have some rest"
Har dakinta ta kai ta ta kwantar da ita saman gado, Mumy na ta kallonta har ta rufe
ido sannan ta juya ta fita daga cikin dakin.
Bayan Magrib Nihad ta gama shiryawa ta sa Hijab dinta har kasa, tun labarin da ta
ba Mumy da la'asar Mumy bata dawo dai dai ba kuma ba wai ta yarda da zancen Nihad
bane, a'a kawai gani take kamar ƙwaƙwalwarta ya fara taɓuwa ne as a result of all
what she passed through, gani take she isn't in her right senses, gani take kawai
sambatu take ba wai don tasan abinda take fada ba, Mumy ta nuna mata inda Makullin
motarta yake, Nihad ta dauka, a hankali tace "Sai mun dawo Mumy" Mumy bata iya ta
ce mata komai ba ta bi ta da kallo har ta fita daga dakin, Mumy ta jingina da
kujera rai ba dadi, ita dai tasan Nihad bata da lafiya don sanyin nata ma yayi
yawa, Mumy bata san sanda ta fashe da kuka ba tana fatan kada ace ƙwaƙwalwarta ne
ya samu matsala. Khalil na tsaye parking space bayan ya gaisa da Abba, sae dai Babu
yabo babu fallasa Abban ya amsa masa har ya shiga ciki, yana ta jiran Nihad har ta
karaso ta mika masa makullin motar ya amsa yana kallonta, ita dai bata bari sun
hada ido ba duk da ta dai ga ya canza kayan jikinsa, ta zaga ta bude kofar gaba
zata shiga yace "Aa koma normal spot din ki...." Ta ɗan yi jim sai kuma ta sauka ta
koma back seat, ta madubin mota yake kallonta har ya tada motar yayi warming suka
bar gidan, She doesn't look like the normal Nihad anymore, seems abubuwa da yawa
suna damunta a zuciya, this is a new Nihad he is seeing for 2 months now, har suka
isa gidan Baffanta bata sani ba don tayi nisa a tunanin da take, yayi parking yana
kallonta, ta dago kai ta kalli anguwan da suke da sauri, sai kuma ta bude motar ta
sauka shi ma ya sauka. Tana gaba yana bin ta har suka shiga gidan, Hamid na zaune
parlor Nihad bata kallesa ba ta shiga bangaren da Inna take, Khalil ya karasa har
inda yake ya basa hannu sannan ya juya ya nufi bangaren Inna, Inna ta tsaya rike da
darduman hannunta tana ta kallon Nihad, sai kuma ta fashe da kuka kamar yar yarinya
ta ajiye darduman hannunta a gefen gado, ta zauna kasa tace "Allah ya isa tsakanina
da duk wanda yayi sanadin rabani da ke, ko ma waye Allah ya saka min, Allah ya
walakanta shi...." Sai kuma ta kalli Khalil da ya durkusa bakin kofa, ta wani tsuke
fuska tace "Kai kuma haka ake yi kawai ka dau yar mutane ka tafi da ita kauyen
Nijar saboda Allah ya ci da kai an aura maka ita babu ko sisinka, yau ga karfin
hali ni patu, kai ba kowan kowa ba dillalin kashi a leda zaka dau min jika ka mayar
kauyenku? Ashe haka buzaye suke basu da kamun kai basu da lissafi bamu sani ba, yau
ko da kudinka aka aura maka ita zaka dauketa ka kaita kauyen ku balle babu
kwandalarka, ina ma kaga kudin aurenta, wato ka samu xukekiyar yarinya a bagas
shine ka tafi kana ta fafa da ita a kauyenku kai ga ɗan banza" Shi dai khalil kansa
na kasa sai ɗan murmushi yake, Nihad kuwa banda hararanta babu abinda take tana
turo baki, Inna ta rike haɓa tace "Tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin wannan
azababben karfin halin ba, banda kaddara me Nihad zata yi da kai ɗan nan, ai kai ba
ajinta bane tafi karfinka ta ko ina, iyaka kayi aikinka na dreba ka kama gabanka
amma ina kai ina auran yar masu gida banda ƙaddara da ta riga fata, ɗan gidan
Habubakar Jikamshi ne saurayinta fa wannan dai da kayi ma walakanci kwanakin baya,
wanda da ba don mutuncina da na ubanta ba da ya daureka har karshen rayuwarka ka
rube a gidan yari, wallahi mun sha gaisawa da shi yafi a kirga ta waya, abinda idan
bashi da number mutum ma baya samunsa ba ko wani gaja yake waya da ba, sai in shi
ya yi niyyar kiran mutum" Nihad tayi karfin halin cewa "Dama gaisheki muka zo yi"
Inna tace "Toh ya tashi ya tafi sai kin huta haka kuma, wato ga ki ya sameki a
banxa sai dai Ibrahim ya tura masa kudi kaca kaca, shi gashi ai sai kyau yake yana
kara budewa uwa kirjin zai yage, ke kuma duk kin tsamure kin kanjale ke da kudin
ubanki, da kyar idan kina samun abinci ma kina ci sau uku a rana" Khalil ya daga
kai yana kallon Inna, a hankali yace "Toh bari muje ta debo kayanta Inna" Inna ta
masa wani shegen kallo tace "A ina??" Yace "Gidan da muka ajiye kayan" Tace "Wani
gidan ne?" Yace "Nan cikin gari" Tace "Toh wai da daga ina ku ke?" Yace "Kauyenmu"
Ta buda baki tana kallonsa, can tace "Toh maza maza tafi ka debo mata kayanta,
kauyen uban wa, kaga tayi kalar yar kauye banda dai baka tsoron Allah duk girmanka,
kaiii Ibrahim ma dai sai Allah yayi masu hisabi da Nihad, don ya cuceta ya gurbata
mata rayuwa, wallahi ya cuceta" Khalil ya mike yana kallon Nihad dake ta kallonsa,
yace "Za muje ki debi kayan ne, don ban san wanda zaki bukata ba" Mikewa tayi, Inna
tace "Ta debi me, Bawan Allah dukka zaka tafi ka kwaso mata ka kawo nan inyi jinyar
jikata ko zata marmaro, shi kuma Ibrahim yaje hakkinta ma baxae bar sa ba duk da ni
nace na yaɓa da hankalinka kawai a aura mata kai, bansan kai ma mugu bane, ashe
kauyen da dadi ka gudo ka dawo birni ka nemi tukin mota, maza tafi ka kwaso mata
kayanta" Nihad tace "Toh ai ni xan je in xaba kayan, ba dukka nake sa wa ba fa"
Inna tace "Duk da haka kuje ki kwaso su gaba daya, baki ji yace wajen ajiya kayan
suke ba, idan aka kwashe maki kaya ta ina za a fara...." Nihad tace "Toh" Khalil na
kallon Inna yace "Sai anjima" da sauri tace "Toh" Juyawa yayi ya fita ta bi sa da
harara, Nihad ta bi bayansa, Inna tace "Maza kiyi ki dawo" Har suka iso mota babu
wanda yace komai cikinsu. Bayan sun bar layin ya juya ya kalleta yace "Kala nawa
zaki debo kayan?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Ko dukka za a debo?" Ta hade
rai tace "Ni nace maka zan koma ne?" Yace "Ai ban sani ba" bata kuma ce masa komai
ba bayan tafiyar kusan minti talatin ta gansu gaban wani hotel, ta kallesa, ya
fiddo wayarsa dake ring ganin Mami ke kiransa ya jinginar da kansa jikin kujeran
motar, can dai ya daga ya kai kunne a hankali yace "Ina yini?" Daga daya ɓangaren
ba tare da ta amsa ba a takaice tace "Karfe nawa zaka taso goben?" Yace "Da safe"
Tace "Ai dai ka ji inda nace kaje idan ka sauka ko?" Yace "Toh saboda me?" Mami
tace "Ohh kace saboda me? To in baka da hankali ka shigar masa gida idan ka shigo
Abuja, wai ma in tambayeka kana da wani kudurin na daban ne a ranka da yasa ka dage
sai ka amshi takardunka dake wajensa bayan babu abinda ka rasa yanzu?" Ya ɗan yi
shiru, sai kuma yace "Ba komai, just in case of necessity" Mami tace "Toh kana
sauka Abuja xaka bani in mayar masa kuwa" Khalil ya bude baki yace "Ki mayar masa
kuma Mami?" Tace "Haka nace" Shiru yayi, yana jin ta kashe wayar ya ajiye, bayan
few seconds ya kalli Nihad yace "Mu je ki dau wasu kayan naki da kika bari a Abuja
na taho maki da su" Yana fadin haka ya bude motar ya sauka, ta bi sa da kallo sai
kuma ta sauka, sai da ya kulle motar sannan ya nufi cikin hotel din ta bi bayansa,
makullin dakin ya amsa tana biye da shi har zuwa dakin da ya sauka dazu da safe, a
hankali take tafiyar har ta shiga cikin dakin ya kulle kofar, taga ya shiga bandaki
ya dauro alwala ya fito, nan dakin ya shimfida darduma zai yi sallan don an idar a
masallaci, Nihad dai ta dinga bin dakin da kallo don bata ga alamar jaka balle kaya
ba, can dai ta nufi bandakin ita ma tayi alwala ta fito, ta dau wani darduman ta
shimfida xata yi sallan...
Bayan ta idar da sallan ta kallesa don kwanciya yayi kan gadon ya rufe idonsa kamar
me bacci nan ko ba bacci yake ba, kawai neman mafita yake na chakwakiyar nan da
yake ciki, he don't even know where to start from, it's doesn't look easy at all,
definitely yasan ko harbesa Abba zai yi baxai mayar masa da takardunsa ba, to shi
wannan ma ba damuwarsa bane, babban tashin hankalinsa daban yanzu, wanda da ya tuna
sai gabansa ya fadi, throughout ranan kuma Nadeeyah bata kirasa ba, a hankali ya
bude idonsa daga karshe yana kallon Nihad yaga ta kwantar da kanta saman gadon tana
daga zaune kan darduma tana bacci, mikewa zaune yayi still yana kallonta, can ya
sauka daga saman gadon, ya nufi switch din dakin ya kashe, sannan ya dawo gabanta
yayi patting dinta, bude ido tayi da sauri amma taga ko ina duhu ta gyara zamanta
da sauri tana gwalo ido, yayi kasa da murya yace "Tashi...." Gabanta na faduwa tace
"Ni baxa ka kai ni gida bane?" Ji tayi ya dagata ta zaro ido kafin tace komai ya
cire mata hijab din jikinta kamshinta sai da ya kusa Knocking dinsa down yaji ya
kasa tsayuwa da kafafuwansa, gaba daya ta rikice zata duka ƙasa yaki barin ta,
instead taji ya ja ta suka fada saman gadon, ta sauka kansa da sauri, cikin rawan
murya tace "Don Allah kayi hakuri mu tafi gida kaga dare yayi" Kamar wanda ya sha
wani abu yana lumshe ido yace "Saboda me?" Ta hadiye abu da kyar tace "Za a neme
ni" Yace "Ke da wa ku ka fita?" Ta kasa cewa komai sai zaro ido take xuciyarta na
bugawa, murya can kasa yace "I am asking you, ke da wa ku ka fita?" Still taki cewa
komai tana neman sauka daga saman gadon, taji ya danneta, zaro ido tayi, kamar me
rada yace "Answer me" jikinta na rawa tace "Mijina" Bata rufe baki ba ya daura lips
dinsa kan nata giving her a deep snog...

*Domin jin sunan turaren Nihad🥰 a tuntuɓa ta wannan number


http://Wa.me/+2347065525409* Saboda wannan turaren Barrister ya mallaka min gidansa
gaba daya don ma ku ji😁😜
Da za ku ji kamshin turaren nan xa ku gane i am not exaggerating wallahi.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

55

It took Khalil a while kafin ya iya controlling urge dinsa a lokacin, it wasn't
easy for him, duk da dama babu abinda yayi niyyar mata, amma sai da ya kai
zuciyarsa nesa kafin ya iya hakura ya kyaleta, ya koma can gefe ya kwanta breathing
rapidly, jin yanda take kuka kamar warce aka ma duka ya mike zaune da kyar ya kunna
switch din dake kusa da gadon yana kallonta, da sauri ta boye fuskarta da gadon
tana ci gaba da kukanta, har sannan jikinta bai daina rawa ba, she is so afraid, he
realized bakuwa ce gaba daya a lamarin, she is not use to it, ya koma kusa da ita
ya dagota ya rungumeta ya lumshe ido yana jin yanda zuciyarta ke bugawa, ita dai
taki yarda su hada ido jikinta sai rawa yake, ya kai bakinsa kunnenta a hankali
yace "Toh me aka maki?" Tayi shiru bata ce masa komai ba, suna nan a haka for
almost 10mins har yaji she is completely calm, a hankali yace "Nihad" Da sauri ta
daga kai ta kallesa saboda yanda ya kira sunan nata, yana kallon kwayar idonta yace
"Me ke kai ki hotels a baya?" Sauke idonta tayi bata ce masa komai ba, lokaci daya
hawaye ya cika idonta, still taki ce masa komai, shi ma bai sake ce mata komai ba,
ya dauko rigarta ya mika mata sannan ya sauka daga kan gadon ya shiga bandaki,
kafin ya fito har ta shirya, ta jinginar da kanta jikin gadon tayi nisa tunanin da
take, har ya karaso kusa da ita yana kallonta bata sani ba, wayarsa da ya fara ring
ne ya dawo da ita duniyar tunanin da ta tafi, ya dau makullin mota yace "Tashi mu
tafi" Mikewa tayi tana kallonsa, ya nufi kofa ta bi bayansa, har suka isa gida babu
wanda yace komai a cikinsu, tunanin da yake a zuciyarsa daban, ita ma haka, yayi
parking a compound sai a sannan ya juya ya kalleta yace "Kina da National ID card?"
Ta ɗan kallesa, sai kuma ta gyada masa kai, yace "In kin shiga ki dauko min" Bata
ce komai ba ta bude motar ta sauka, ya bi ta da kallo ta nufi entrance din gidan
walking slowly, jinginar da kansa yayi da kujeran motar ya lumshe ido, he wish
things won't go as hard as he is seeing it now, he wish his parents will understand
him, Nihad bata tadda kowa main parlor ba ta tafi bangaren Mumy, Mumy na kallonta
bayan ta zauna tace "Ina Ibrahim din?" Tace "Yana waje" Mumy tace "Kun samu Innar?"
Nihad tace "Ehh" Mumy tace "Bata dai yi fada ba ko?" Girgiza mata kai kawai Nihad
tayi, Mumy tayi shiru, bayan wani lokaci ta kalli Nihad tace "Bayan kun fita zuwa
gidan Inna daxu Umma ta shigo wai kina ganinta baki gaisheta ba shine hakan ya
dameta shi yasa ma ta bar gidan, bana son ki nuna mata komai Daughter, pretend as
if everything is okay, kar ki nuna mata komai har ku bar gidan nan kin ji?" Nihad
dai sai kallon Mumy take, Mumy tace "Kwana nawa yace za ku yi?" Nihad ta sauke
idonta a hankali tace "Nima ban sani ba" Mumy tace "Toh kiyi hakuri kar ki nuna
mata komai, idan kun hadu ki gaisheta yanda kika saba" Nihad dai ta kasa cewa Mumy
komai but deep down her tasan she will never greet her, don duk duniya babu wanda
take jin tsanarsa a zuciyarta irin Umma. Khalil na zaune tare da Aminu wajajen
karfe goma Amina ta iso wajen tana kallonsa tace "Abbanmu yana kiranka" ya ɗan
kalleta wanting to make sure da shi take ko Aminu, Aminu yace "Tace Alhaji na
kiranka mutumina" Khalil yace "Toh" Juyawa tayi ta bar wajen ya mike ya saka ID
card din Nihad da Sudais ya kawo masa a aljihu sannan ya nufi cikin gidan, Umma na
zaune parlor ta kafe ma TV ido duk da gaba daya hankalinta ba kan kallon yake ba,
malamin nata da suke zuwa wajensa tare da Hajiya Turai sun ƙona man mota a banza
sun je har kauyen da yake a kusa da Zaria amma wai bashi da lafiya an kawosa
asibiti cikin kano, haka nan suka juyo a hanya kuma mota ta lalace masu, sai da ta
kashe ya fi dubu saba'in wajen gyaran motar, suka ɓata awa kusan uku kafin aka gama
gyaran ta kamo hanyar gida a wahale ga yunwa.... suna hada ido da khalil bayan ya
shigo parlon ya dauke kai ya nufi kofar parlon Abba, ta bi sa da kallon mamaki don
haduwarsu na farko kenan tun zuwansu gidan, Ya tsaya bakin kofar parlon yayi
sallama, sai da yaji Abba ya amsa sannan ya shiga, Umma ta kalli Amina tace "Ko dai
ya gaisheni ni ce ban ji ba Amina?" Amina tace "Ba wani gaisheki da yayi wallahi"
Mikewa tayi ta nufi parlon Abban da sauri ita ma, Khalil na zaune kasa ya sunkuyar
da kansa bayan ya kara gaida Abba, Abba yace "Wani garin ku ke?" Khalil zai yi
magana Umma ta shigo, Ta nemi waje ta zauna parlon tana ɗan murmushi, Abba ya
kalleta, can kuma yace "Is there any problem?" Da sauri tace "Aa babu komai, sannu
Khalil, fatan kun zo lafiya?" Khalil ya kalleta yace "Alhamdulillah" Tace "To
madallah" Abba ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Idan zaka kwanta ka tafi dakin
Farooq, dakin nasa a bude yake..." Khalil da kansa ke kasa yace "Toh Nagode" Abba
yace "Shikenan you can leave" Mikewa yayi ya fita daga parlon, Umma dai sai
murmushin yake take tace "Allah sarki, sun dawo nan garin kenan?" Abba ya dau
wayarsa dake ring ya daga ya kai kunne. Nihad na kwance saman gadon Mumy bayan tayi
shirin bacci Mumy ta shigo dakin tace "Baxa kije ki ji ko yana bukatar wani abun ba
Nihad?" Nihad ta daga kai tana kallon Mumy, Mumy tace "Duk da nasan akwai komai
dakin farooq but ki je kiji if he is comfortable" Nihad ta mike zaune, Mumy ta juya
ta fita daga dakin, Nihad ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fita, bata gansa a
dakin ba hakan yasa ta dawo tayi kwanciyarta kawai. Washegari bayan khalil ya shigo
gaida Mumy ya sanar mata za su koma a ranan, Nihad dake zaune dai sa kallonsa take
tana tunanin inda za su koma, Mumy tace "Toh ka samu Alhajin ka sanar masa?" Khalil
yace "Na ɗan fita dazu, kafin in dawo kuma ya fita" Mumy tace "Toh ka kirasa a waya
sai ka gaya masa" Khalil yace "Toh in sha Allah" mikewa yayi ya fita daga parlon,
Mumy na kallon Nihad tace "Toh ki tashi ki fara shiri" lokaci daya jikin Nihad yayi
sanyi, amma saboda bata son Mumy ta fahimci komai ta mike ta shiga bedroom dinta
kawai kamar zata shirya, zaunawa tayi kan gado ta hade kanta da pillow hawaye na
sauka idonta, Umma tayi sallama ta shigo parlon Mumy, Ta zauna saman kujera bayan
sun gaisa da Mumy tace "Ina er tawa?" Mumy ta mike tace "Yanzu ta shiga ciki bari
in duba" Daga haka ta shiga daki Umma ta bi ta da kallo, Nihad na jin muryar Umma
dama ta shige bandakin Mumy ta sa makulli, Mumy ta ɗan yi jim a dakin, can ta juyo
ta fito tana kirkiran murmushi tace "Kamar wanka take, tana bandaki...." Umma tace
"Toh, ni sai naga kamar ta kullaceni, tana ganin na watsar da al'amarinta bata san
Alhaji babu me iya masa ba sai Allah, kuma Allah shine shaida, nayi bakin kokarina
kema shaida ce amma hakan ya so ya zame mana ɓacin rai da Alhaji, har yake ga kamar
ina goyon bayanta ne, Nihad gani take kamar nayi shiru naki cewa komai akan abinda
ya sameta nan kuma ba haka bane Allah ya ga zuciyata, babu yanda na iya ne abun ya
fi karfi na" Tana magana tana matsar kwalla, Mumy dake ta kallonta babu ko kiftawa
ta kasa ce mata komai, Umma tace "Toh idan ba kullatata tayi ba menene? Ni Nihad
bata taɓa min haka ba wallahi, a jiyan nan da da tashigo da wajena zata fara shiga
kafin ma ta zo nan, amma bata yi hakan ba, to kinga ai ta kullaceni kenan, duk sai
jikina yayi sanyi na fita na bar gidan" Mumy ta sauke idonta kasa don bata da
abinda xata ce ma Umma, banda zafi babu abinda zuciyarta yake, da Umma bata gurbata
ma 'er ta rayuwa haka ba, da zagewa tayi kawai su zuba kishi amma da bata ma er ta
abinda tayi mata ba, daure kawai Mumy take a zaune a wajen, Umma ta sauke ajiyar
zuciya jin Mumy ta ki cewa komai, tace "To amma zasu kwan biyu ai ko?" Mumy tayi
karfin halin girgiza kai tace "Anjima za su koma" Umma ta buda ido sosai tace "Yau
din nan? Ikon Allah, ni na zata sun zo su kwana biyu ne? Toh a wani kauyen suke ne
halan?" Mumy tace "Ban sani ba gaskiya" Umma tace "Allah sarki, Allah me yanda ya
so...."
Nihad na shirya sauran kayanta dake gidan a cikin Trolly Mumy ta shigo dakin tana
mata wani kallo tace "Ke kika kirata kika ce kin zo??" Nihad ta daga kai tana
kallon Mumy tace "Wacece?" Mumy tace "Ban sani ba" Nihad tace "Mumy ni ban kira
kowa ba ni da bani da waya, kuma ai kinga ban yi amfani da wayarki ba" Mumy tace
"To wa yace mata kina nan?" Nihad tace "Ai ban san wacece ba" Mumy tace "Sai kije
ki duba" Nihad ta mike tsaye ta nufi kofa ta bude ta fita parlon Mumy taga babu
kowa, can main parlor ta fita, tsaye tayi parlon tana kallon Husnah dake zaune ta
sha baƙin glass, Husnah ta mike da sauri ta rungumeta cike da murna tana kare mata
kallo tace "Besty, meye rayuwa? yanzu da sai dai mu ji kin zo kin tafi babu daga
hannu? Haba Nihad, amana bata ce haka ba ai, nafi karfin haka a wajenki" Nihad ta
karasa ta zauna parlon tace "Wa yace maki na zo?" Husnah tace "Wallahi na zo wucewa
ta anguwar nan ne nace bari dai in shigo mu gaisa da su Umma da Mumy, kawai sai na
samu labarin wai kina nan, nace what?? abun ya daure min kai nace kina nan shine
babu notice, yanzu ko ta waya kin daina neman mu Nihad, Duk kusancinmu ace kin ya
da mu haka?" Nihad dai sai kallonta take, Husnah na gyara zama tace "Toh yanzu ya
ake ciki? Naga kin yi haske amma kin rame, ina mijin naki?" Nihad tace "Lafiya lau"
Husnah tace "To wai wani garin ku ke?" Nihad na kallonta tace "Ban san sunan wajen
ba" Husnah tayi kasa da murya tace "Kar kice min kin hakura kin zauna da shi Nihad
har abu ya shiga tsakaninku Nihad" Nihad tace "Do you have any problem with that?"
Shiru Husnah tayi tana kallonta, Can tayi yake tace "Aa kawai tambaya nake kawalli,
kinsan har yanzu Aliyu Jikamshi bai daina damun Naf a waya ba shi yasa ma nake maki
wannan tambayar, wallahi Aliyu bai hakura ba har yanxu" Nihad dai bata ce mata
komai ba, Husnah tace "To wai har yanzu baki da waya?" Nihad tace "Bani da shi har
yanzu" Husnah tayi kasa da murya ta bude jakarta tana kokarin ciro waya tace "Toh
ko in baki karamar wayata ki saka layi kawai, sai mu dinga magana...." Nihad tace
"Aa yanzu bana bukatar waya" Shiru Husnah tayi tana kallonta da mamaki, Nihad tace
"Toh naji dadi nagode da ziyara Husnah, ina son zan je in ci gaba da abinda nake yi
a ciki" Husnah ta buda baki tana kallonta ta kasa cewa komai, Nihad ta mike tace
"Toh sai anjima, nagode" Kai kawai Husnah ta iya gyada mata, Nihad ta juya ta bar
ta a parlon ta koma parlon Mumy, Husnah ta mike da sauri ta shige bangaren Umma...
Bayan Azahar Khalil na zaune balcony tare da Nihal, Hira suke amma gaba daya
hankalinta baya jikinta, she is carried away with her thought, sannan tun dazu ake
kiran wayarta amma bata dagawa daga karshe yana lura da ita ta sa wayar a silent,
yace "Nihal" Firgit ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta kirkiri murmushi tace
"Na'am" Yace "Pls tell me what ur problem is, Or don't u trust me?" Nihal dai sai
kallonsa take, can ta ɗan kirkiri murmushi tace "Sure i do... but i told u nothing,
I don't have any problem...." Khalil dai kallonta kawai yake, Da sauri tace "Yaushe
xa ku koma?" Yace "Today" Ta wara ido tace "Yau din nan? Amma ai rana yayi" Ya
girgiza kai yace "Bai yi ba" Tace "Ohk, nima next week zan koma makaranta in sha
Allah" Yace "Allah ya kai mu, but if there is anything feel free to call and talk
to me Nihal" a hankali tace "In sha Allah" Yace "Bani account number din ki" Ta ɗan
buda ido tace "Ahh haba wallahi Nagode, ka bar shi" yace "I asked for it" shiru
tayi bata ce komai ba, ya ciro wayarsa yace "Gaya min" Ta kallesa tace "Amma..." Ya
dakatar da ita yace "Ki bani nace" Ta sunkuyar da kai ta karanto masa account din,
cikin few seconds taji alert a wayarta ta duba taga dubu hamsin ya sa mata, ta daga
kai tana kallonsa, ya mike yace "Ki duba min ko ta gama shiryawa, lokaci na wucewa"
Tace "Nagode sosai Allah ya saka da Alkhairi" Shi dai bai ce mata komai ba, ta
tashi ta shiga ciki, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta fito da trolly din Nihad,
wanda duk hijabs dinta da wasu kayanta ne a ciki da turarrukanta, daurewa kawai
Nihad take kar ta fashe da kukan da ke cin ta, Mumy ta gama mata nasihar da zata
mata sannan tace "Ki je kar ki bata masa lokaci, Allah ya tsare, in kin samu waya
ki dinga kirana kin ji?" Nihad ta gyada mata kai kawai tana goge hawayen idonta ta
nufi kofa, Mumy ta bi ta da kallo ita ma hawayen har ya cika idonta, Aminu ya taho
ya saka jakar Nihad a bayan motar yana kallon sabon drivern gidan cike da tsangwama
yace "Kwata kwata baka san aikinka ba Iliya, kana ganin an fito da jakar ai da gudu
zaka dauka ka saka a booth, haka ake yi ba wai ka tsaya kamar soja ba" Dreban yace
"Wai kai ina ruwanka da ni a gidan nan ne bawan Allah" Aminu yace "Oho dai ka ji da
warin bakinka" Daga haka ya koma gate, shi dai khalil na jingine jikin motar yana
kallonsu, sai kuma kawai ya shiga ciki don yi ma Mumy sallama, Mumy tace "Toh Allah
ya tsare Ibrahim, ayi ta hakuri da ita don Allah, idan tayi maka ba dai dai ba kar
kayi kasa a gwiwa ka kirani kaji" Kansa na kasa yace "Nagode Allah ya kara girma"
Tace "Ameen, Allah ya maku albarka" Ya amsa da "Ameen" sannan ya bar parlon ya
fita zuwa compound, ba a dau lokaci ba Nihad ta fito tare da Nihal, Nihal ta bude
mata back seat tana kallonta tace "Allah ya tsare sister...." murmushi Nihad ta
mata tace "Ameen" Daga haka ta kulle motar tana kallon Khalil tace "Safe trip"
Khalil yace "Thank you Nihal" ya bude front seat ya shiga ya kulle, drivern ya ja
motar suka bar parking space, Tun bayan barin Husnah gidan Umma ma ta fita shine
har yanzu bata dawo ba, Aminu na tsaye gate tun kafin motar ya karaso yake daga ma
Khalil hannu baki har kunne, suna isa gate khalil ya sauke glass din motar ya mika
masa cash din dubu dari, Aminu yayi washarere da baki yana kallon tulin kudin da
khalil ke mika masa ya kasa amsa, Shi kansa dreban sai gwale ido yake yana kallon
kudin don dari biyar biyar ne sababbi, ita dai Nihad na bayan motar tana kallonsu,
Khalil ya kamo hannunsa ya damka masa kudin sannan ya kulle glass din yana kallon
drivern yace "Mu je" Drivern ya ja motar suka bar Aminu tsaye galala da kudi a
hannu, Bayan sun hau saman titi drivern na kallon Khalil cike da ladabi yace "Ina
muka nufa ranka shi dade?" Khalil yace "Airport" Nihad ta daga kai ta kallesa,
drivern yace "Toh Yallabai yanzu kuwa" Daga haka ya nufi airport da su, suna isa
Aminu kano bayan yayi parking Khalil ya sauka daga motar, da sauri Drivern ya zaga
ya sauke kayan Nihad dake bayan motar, ta bude motar ta sauka ta tafi ta amshi
trolly dinta a hannun drivern, Khalil ya ciro dubu biyar ya basa yace "Mun gode"
Drivern har da risinawa ya dinga masa godiya, Khalil ya amshi trolly din hannunta
ya nufi cikin airport din ta bi bayansa tana tafiya a hankali.... Suna shiga cikin
airport din bayan ya amsar masu Boarding pass sai ga kiran Mami, sai da gabansa ya
fadi, yau ta kirasa yafi a kirga, ya dai daga kiran yana sauraronta don bata basa
space din magana ma, can yace "Calm down Mami, ina airport yanzu haka" Yana fada
mata haka ta katse wayarta, sai da suka jira for almost 30mins kafin jirgin ya
tashi zuwa Abuja.. kamar jira Nihad take jirgin ya tashi ta fara bacci, ya jawota
kusa da shi a hankali ya kwantar da kanta saman shoulder dinsa, shi dai yasan banda
Mami babu abinda zai kai sa Abuja, but he just have to go because of her, jirgi na
sauka a Abuja bayan sun fito daga cikin jirgin hankalin Nihad ya tashi, yanzu
gidansu zai sake mayar da ita kenan, tunanin hakan yasa taji kamar ta fashe da
kuka, suka dau cab a airport din bayan khalil ya sanar masa inda zai kai su,
tafiyar kusan minti arba'in suka yi, Nihad taga wani anguwan daban suka shigo, ta
dinga bin ko ina da kallo har mai cab din yayi parking dai dai wani gida wanda ya
haduwa iya haduwa, duk manyan gidaje ne a layin kamar wannan, Khalil ya sauka daga
cab din don tun a hanya yayi masa transfer, mai cab din ya bude booth ya ciro
trolly din Nihad, Khalil ya amsa yana kallonsa yace "Ka jirani zaka ajiye ni wani
waje yanzu" Mai cab din yace "Ok sir" Daga haka ya nufi gate din gidan ya ciro
makulli a aljihunsa ya bude sannan ya juya yana kallon Nihad dake tsaye, karasowa
tayi a hankali kusa da shi ta tsaya, ganin jira yake ta shiga gidan kawai ta shiga
shi ma ya shiga sannan ya kulle gate din, ta dinga bin compound din da kallo, it
looks so beautiful, duk gidajen da taje a Abuja daga gidansu sai wannan a kyau, don
ko na Aunty Maryam bai kai wannan kyau ba balle nasu Nadeeyah, kuma sabon gida ne
kamar ba kowa ciki, yana gaba tana biye da shi har suka iso entrance din shiga
cikin gidan, ya bude kofar da makulli ya shiga ta bi bayansa, waow the parlor is
breathe taking, komai na ciki sabo ne dal, ya ajiye jakarta yace "Ki tafi sama kiyi
sallah, i will be going out now" ta marairaice tace "Ni kadai a katon gidan nan?"
Yace "Ke yarinya ce?" Ta dinga kallonsa gabanta na faduwa amma ta kasa ce masa
komai, daukar jakar yayi ya wuce sama ta bi bayansa da sauri, ya bude wani daki ya
ajiye jakar a ciki ya juya yana kallonta, ta shigo dakin tana bin ko ina da kallo
yace "Ki shiga bandaki kiyi alwala" Daga haka ya juya ya fita sannan ya sauka
downstairs, ya fita daga gidan ya kulle gate din da makulli ya shiga cab din dake
jiransa don baya son Mami ta sake kiransa.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

56

Khalil na isa gidan Hajiya Safeenah, ya ga motar Mami a compound din alamar tana
ciki, ya karasa har kofar shiga parlon gidan yayi Knocking, ba a dau lokaci ba aka
bude kofar suka yi ido hudu da Nadeeyah, juyawa tayi zata bar wajen ya bi parlon da
ido ganin babu kowa ciki ya jawota da sauri yace "C'mon Babe, did i offend you in
anyway?" Nadeeyah dai bata ce masa komai ba, ya karaso cikin parlon ya kulle kofar
still yana rike da ita yayi kasa da murya yace "Haba Nadeey, nayi maki wani laifin
ne? In ma nayi kiyi hakuri don't punish me plss" Taki kallonsa, a takaice tace "Pls
aiki muke yi a kitchen, let go of me" Ya sake bin parlon da kallo sannan ya
rungumeta a hankali yace "I am sorry dear, I'm deeply sorry...." Kamar jira take ta
fashe masa da kuka tace "Saboda ga budurwarka ta gudu shi yasa zaka daga hankalinka
haka har ka dinga shareni ko?" Da sauri yace "Noo Nadeey, budurwata kuma? Haba...
Kawai ya zama dole in daga hankalina saboda parents dinta trusted me har suka bari
na taho da ita Abuja ta zauna a gidanmu, Kinga idan wani abu ya sameta i don't know
how to explain to her parents, bansan da wani idon zan kallesu ba, wannan shine
dalilin da yasa kika ga hankalina ya tashi Nadeeyah, but Alhmdlh she is home now,
ba shikenan ba" Hawaye na bin kuncinta tace "Ko farin cikin sa mana rana da aka yi
baka yi ba, u are not even saying anything about the wedding, balle mu yi wani
shirye shirye, You've been ignoring me for at least 2 weeks now...." Ya wara ido
yace "Ko ba wata daya aka sa ba? ina fa lissafi Nadeey, i know yau saura 15 days in
sha Allah, and kinsan ni bana son duk occasions din nan da ake yi ko events a biki,
i told u that years back, so ba wani abu da xa ayi, just wedding fatiha sai walima
a gida, but if su Mami za su yi wani program fine za su iya, kema in za kiyi da
frnds dinki it's okay the expenses will be on me, but count me out of any
event....." Nadeeyah dai bata ce komai ba, ya share mata hawayen idonta a hankali
yace "You know i love you always dear, kuma baxan so ranki ya baci saboda ni ba....
Don Allah kiyi hakuri kin ji wife" Jin bude kofar kitchen yasa ya saketa da sauri
ya koma baya, ya wara ido yace "Ina su Mami?" Bata kai ga basa amsa ba ya jiyo
muryarsu, Ya kashe mata ido yace "Bari in karasa ciki Baby" Daga haka ya nufi kofar
parlon Hajiya Safeenah, Nadeeyah ta bi sa da kallo, yana shiga parlon da sallama
Mami ta dinga kallonsa, ya zauna ya gaida Hajiya Safeenah da ladabi ta amsa da
fara'a tana tambayarsa ya hanya, yace "Alhamdulillah" Ya ɗan kalli Mami da ke
kallonsa har sannan yace "Ina yini Mami" Mikewa Hajiya Safeenah tayi ta fita daga
parlon ta basu waje, Mami na masa wani kallo tace "Ban ga komai a hannunka ba bawan
Allah" a hankali yace "Kamar me fa Mami?" Ta jefa masa wani kallo tace "Kar ka
raina min hankali mana, ina takardun da makullan da ka kwashe?" Khalil yayi shiru
bai ce mata komai ba, Mami tace "Na lura baka son kwanciyar hankali na Khalil, duk
wani abu da zai daga min hankali baka gudunsa a rayuwarka, banda haka what are you
lacking in this life? Rasa motar hawa kayi ko rasa gidan zama kayi? Nawa ne salary
din naka dukka? Sannan nawa kake samu currently a wata? Ka gaya min ko banbancin da
wani tazara, ko kuma rashin godiyar Allah ne ke damunka?" Kallonta kawai Khalil
yake ya kasa ce mata komai, A fusace Mami tace "Instead of you to sit and plan ur
wedding cikin tsari sai ka ɓuge da dauko mana magana, Is this the rightful time da
zaka amshi abubuwanka khalil in ba dai kana da wani kuduri na daban a zuciya wanda
mu bamu sani ba, are u even okay? A kan bikinka that's by the corner zaka yi
concentrating yanxu ko takardunka?" Yayi kasa da murya yace "Kiyi hakuri Mami, ni
ban yi hakan don ranki ya ɓaci ba, i am very sorry Mami...." Mami tace "Aa kayi ne
don raina ya ɓaci don sarai kasan kaina komai zai dawo, you are lacking nothing,
akan me zaka damu da takardu ko makullin gida? Yanzu maganar da ka jawo min dai dai
ne?" Shi dai yayi shiru bai ce komai ba, tace "Toh duk inda ka kai su ma kaje ka
kawo min su ina jira, duk da ba shiri ku ke da shi ba but he is planning on sending
6million da za a hada maka lefe shine kaje ka aikata wannan shirmen, sannan da ka
kwantar da hankalinka nasan dole xai baka makullin gidanka idan anyi auren tunda
nan din dai amarya zata tare.... Amma ban san meye manufarka nayi abinda kayi ba"
Khalil ya daga kai ya kalleta, Mami ta girgiza kai tace "I am very disappointed
Khalil" A hankali yace "Kiyi hakuri Mami, i am so sorry" Mami tayi shiru, can tace
"Sannan ita Maryam akan wani dalili take kiranka for many days now baka daga
kiranta?" Ya ɗan buda ido yace "No ban ga kiranta ba, or may be ban lura ba, but
zan kirata" Mami tace "Ita kuma yarinyar can wato gidansu ta koma ko" Khalil ya
sauke idonsa yace "Ehh" Mami tace "Ikon Allah, toh Allah ya kyauta, dama can ba wai
ta saki jiki bane a wajen nawa, gwara ta koma gaban iyayen nata su kara sa mata ido
don har ga Allah hankalina bai kwanta ta zauna wajen mu ba, kada taje ta ci gaba da
abubuwan da take a makaranta mu muna nan gida bamu sani ba, so i am happy da ta
koma gida" Shi dai Khalil bai ce mata komai ba, Mami tace "Don yarinyar na bukatar
sa ido sosai, a shekarunta in zata iya aikata abinda ta aikata a social media to
komai ma zata iya yi, dubi dai yanda babu tsoro ta bi dare ta kama hanyar kano,
abun nan yayi mugun daure min kai wallahi" Still Khalil dai bai ce komai ba, Mami
tace "Toh ya ku ka yi da iyayen nata da kaje can din?" Ya girgiza kai yace "Ba
komai, the most important part is that gida ta koma ko da dai bamu iya mun rike
masu ita ba" Mami tace "Aa baka masu bayanin yanda mu ka nemeta muka rasa bane? Ae
ba wanda ya ki riketa, kin zama tayi instead" Yace "It's not necessary Mami, kinga
sanda take gidan Aunty Maryam ai bata taɓa attempting barin gidan ba, she was sad
and cried all throughout bayan tafiyar Aunty Maryam" Mami dake ta kallonsa tace
"Toh me kake nufi yanxu?" Yace "Aa ba komai" Nadeeyah ta shigo parlon da sallama ta
ajiye masa tray me dauke da ruwa da lemo a kai, tana kallon Mami tace "Sannu Mami"
Mami tace "Sannu Nadeeyah, kun gama girkin" ta girgiza kai tace "Aa da saura" Daga
haka ta mike ta nufi kofa, khalil ya dau ruwan gora ya bude ya sha, Mami tace
"Tashi zaka yi ka tafi ka dauko min takardun yanxun nan" Yace "Toh, amma ki bari
sai gobe Mami, it's almost magrib yanzu" Mami tace "Why not today?" Yace "Baya nan
kusa sai naje na dauko" Mami tace "Toh Allah ya kai mu, da baka aikata wannan abun
ba ko ni zan same Abban naku ince ya bada makullin gida za aje kai kaya ina da
tabbacin baxai hana ba wllh, amma ka zo ka ɓata sha'anin" Khalil dai yayi shiru
yana kallonta, don yanzu gaba daya hankalinsa yayi can gida bai son gari ya fara
duhu bai koma ba, Mami tace "Ka ɗan samo min fruits masu kyau idan na koma gida xa
a min fruit salad" Yace "Babu a gida ne?" Tace "No, i need fresh fruits" Yace "Ohk"
Daga haka ya mike yace "But ba fa mota a gurina Mami" Tace "Ka amshi makulli wajen
driver na yana waje, i will call him ya baka" Mikewa Khalil yayi ya nufi kofa ya
fita, Nadeeyah na zaune parlor ya karasa kusa da ita yace "Zan je grocery in dawo
yanzu Babe" Ta daga kai ta kallesa tace "Can we go together?" Yace "Sure" Ta mike
tace "Bari in gaya ma Mumy" Daga haka ta tafi dakin Mumy, shi kuma ya fita ya samu
sojan dake tsaye compound kusa da Motar Mami, yana isa ya mika masa hannu babu yabo
babu fallasa yace "Bani makulli" Sojan ya mika masa don Mami ta riga ta kirasa
kafin Khalil ya fito banda haka da baxai basa ba, in akwai wanda Khalil ya tsana a
rayuwarsa bai wuce soja ba, ji yake kamar ya makuresu, he detest the sight of them,
ga shi sun fi goma a gidansu, fuska daure ya bude motar ya shiga, yana ta zaune
driver seat har Nadeeyah ta fito looking so cute, kallo daya yayi mata ya dauke
kai, ta karaso ta bude gaban motar ta shiga sannan mai gadi ya bude masu gate suka
bar gidan, Khalil na Driving din yace "So where did u suggest i should rent an
apartment for us??" Tace "Amma wannan gudun na meye kake yi haka?" Yace "Abokina na
jirana before magrib kinga ai it's almost magrib now shi yasa nake sauri" tace "Toh
amma ka rage speed din pls...." Yace "Ohk" Tace "Duk inda kaga ya dace nan za mu
zauna ai ko?" Yayi Murmushi ya gyada mata kai kawai, bayan ya siya ma Mami fruits
Nadeeyah tace "Pls ina son zan ɗan yi shopping amma ba me yawa ba" Yace "Ki bari
gobe Nadeeyah kinga sauri nake yanzu" Ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Toh Allah ya
kai mu" Bai fasa gudun da tace ya daina ba har suka iso gida, bayan yayi parking ta
bude motar ta sauka, ya ɗan zaro ido, don shaff ya mance bai mata tayin ice cream
ko pizza ba tunda tana so sosai, kuma basu taɓa fita tare suka dawo bai siya mata
komai ba sae yau, Yayi kasa da murya yace "Nadeeyah" Juyawa tayi ta kallesa, a
hankali yace "I am sorry na mance i didnt get you anything, but let me order...."
da sauri tace "Noo it's fine, ai sauri kake shi yasa, gobe idan mun fita sai mu
siya in sha Allah" Yayi mata murmushi yace "Thank you" a mota ya bar fruits din
Mami ya sauka ya ba drivern makullin sannan ya bi bayanta suka shiga gidan, Yana
tsaye parlon Mum din Nadeeyah ya sanar ma Mami fruits din suna mota, Mami tace
"Baxa ka tsaya ka ci abinci ba? Saurin meye haka kake yi" Da sauri yace "Aa Mami,
ni a koshe nake" Tace "Toh wai saurin me kake haka?" Ya ɗan buda ido yace "Aa ni ba
sauri nake ba kawai bana son a kira magrib ina nan ne" Mami tace "Toh gidan naka ka
bude ka shiga??" Sai da yaji gabansa ya fadi, lokaci daya ya girgiza mata kai da
sauri yace "Not at all, ina gidan abokina ne fa" Mami tace "Gobe karfe nawa zaka
kawo takardun?" Yace "Da safe" Tace "Toh Allah ya kai mu" Daga haka yayi mata
sallama tace "Ka jira mu fita tare mana sai mu ajiyeka inda zaka, nima yanzu zan
tafi gida" Yayi karfin halin cewa "Noo i am fine Mami, Bolt na jira na a waje tun
dazu" a hankali Mami tace "Toh Allah ya tsare" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga
parlon ta bi sa
da kallo, Ko sallama bai yi ma Nadeeyah ba balle Mum dinta ya bar gidan. Ana idar
da magrib Khalil ya isa gidansa don sai da ya tsaya eatry ya siyo abinci with
drinks da bottle water, 3 houses away from his house yaga sojoji hudu a tsaye kofar
gidan, nan ya fara imagining gidan waye wannan kuma har da sojoji masu gadinsa, ya
tsani yaga an cika ma gida sojoji a bakin gate, ya ciro Makullin gidansa a aljihu
ya bude ya shiga ciki, yana bude kofar main parlon Nihad ta mike tsaye da sauri, ya
kulle kofar ya karasa ciki yana kallonta don kana ganinta zaka san ta ci kuka ba
kadan ba, taki yarda su hada ido ta koma ta zauna saman Carpet ta dauke kai ta wani
hade rai, ajiye ledan hannunsa yayi ya wuce sama ta bi sa da harara, har bayan
minti goma bata ga ya sauko ba, ta jawo ledan da ya ajiye a hankali tana duba ciki,
taga jollof rice ne da fried rice a takeaway daban daban sae kaza, jollof rice din
ta dauka ta fara ci, har kuma ta gama cin abincin bai sauko ba, ta mayar da empty
takeaway din sannan ta matsar da ledan daga kusa da ita, sae gashi ya sauko sanye
da jallabiya bata taɓa ganinsa da jallabiya ba sai yau, ya karaso cikin parlon ya
bude ledan ganin empty takeaway ya daga kai ya kalleta for like 20 seconds, sai
kuma yace "Ke fa hana mutane abincin kike a gidanku, nan ba a hanaki ba an siyo
baki jira a baki ba kin dauka, who does that?" Sai a sannan ta kallesa kamar baxata
ce komai ba sai kuma tace "Toh me mutum yayi kafin aka hanasa abincin a gidan
namu?" As if that was what he was waiting for ya zauna yace "Ba abinda yayi kawai
baƙin hali yasa aka hanasa" Ta masa wani kallo tace "Aa ya dai tuna abinda yayi"
Kallonta ya dinga yi, ta turo baki ta mike ta dau goran ruwan da ta rage, ta koma
can jikin wani kujera ta zauna, sai kuma yayi murmushi, ya bude fried rice din da
ta bar masa ya fara ci, lokaci lokaci yake daga kai sai su hada ido don kallonsa
take, da sauri kuma take dauke idonta, sun yi hakan kusan sau uku, a na hudun ne ta
mike da sauri, yace "Ina za ki?" Bata bari sun hada ido ba ya ga ta wuce sama ya bi
ta da kallo, nan parlon yayi isha ya kai sauran abincin kitchen ya ajiye, babu
abinda babu a katon kitchen din kamar da mace a gidan, komai kuma sabo ne, ko gas
din gidan ba a taɓa kunnawa ba, ya kashe wutan kitchen din ya fito, ya haura sama,
master Bedroom ya shiga ya yi wanka sannan ya saka pajamas dinsa yana zaune gefen
gado ya dau wayarsa ganin kiran Nadeeyah ya kirata, tana dagawa yace "Hello dear"
Tace "Shine ka tafi ba ko sallama Dr?" Yace "Ai nace maki sauri nake ana jirana" a
hankali tace "Ohk, ya hanya?" Yace "Alhamdulillah, Mami ta tafi gida ai ko?" Tace
"Yea tun daxu" Yace "Ohk, ya ake ciki?" Tace "Dama ina son zan maka maganar kayan
da za muyi fitar biki ne...." Yace "Ohk, kawai kiyi shawara da frnds dinki sai ki
gaya min" Tace "Alright?" Yace "Shikenan maganar?" Da mamaki tace "Are u eager to
cut the call?" Da sauri yace "Noo, kawai dai i am tired ina son zan kwanta ne da
wuri" tayi shiru, yace "Hello?" A hankali tace "Ohk, good night" Yace "Hope u ain't
taking it personal?" Har hawaye ya cika idonta tace "Yaushe rabon da mu yi magana a
waya, kai idan ban kiraka ba baka kirana, kuma na kiraka yanzu kana ce min bacci
zaka yi, shikenan kayi baccinka kawai ba damuwa" Ya sauke wani ajiyar zuciya yace
"I am sorry Nadeeyah, to yanzu meye labari?" Tace "Noo, kawai kayi kwanciyarka sai
da safe" Yace "I will sacrifice that because of you my love" Taki ce masa komai,
sarai yasan kuka take.... A hankali yace "Nadeeyah" taki amsawa, yayi kasa da murya
yace "Ke komai kuka, duk randa na maki kishiya shikenan haka zaki dinga mata kuka
ita ma har ta raina min ke?" Diff yaji ta katse wayar, ya wara ido, nan ya dinga
kiranta taki dagawa, ya kirata ya kusa sau hudu bata daga ba, ya ajiye wayar sai ga
kiran Aunty Maryam, sai da gabansa ya fadi, for almost 3 days now yake ignoring
kiranta don yasan dalilin kiran nata, yana ta kallon wayar har ya kusa katsewa can
dai ya daga a hankali ya kai kunne, yayi gathering courage yace "Hello Aunty" Daga
daya bangaren tace "Shaye shaye ka fara yi ne kana ganin kirana baka dagawa Khalil?
Kiran na wa kake ignoring??" Da sauri yace "No ba haka bane Aunty, kawai i am not
my self this days ne shi yasa, amma kiyi hakuri don Allah" Aunty Maryam tace "Yanzu
dai ina Nihad? Mami tace min ta koma gidansu, garin yaya hakan ta faru Kjay? And
did the parent accept her??" Yace "Gidansu Nadeeyah Mami tace ta koma saboda su
Aunty Hassana, ita kuma a ranan ta bar garin which means bata son zaman gidan...."
Aunty Maryam ta bude baki cike da mamaki tace "Ikon Allah, kaga kuma Mami bata gaya
min haka ba wallahi, ce min kawai tayi an nemeta an rasa, daga baya aka gano ashe
gidansu ta koma" Khalil dai yayi shiru, Aunty Maryam tace "Amma Mami bata kyauta
ba, yanzu saboda su Aunty Hassana ta ki rike baiwar Allahn nan? Me yasa Mami tayi
haka kai me baya? Gaskiya ban ji dadin jin haka ba, ka tabbatar kuma gidan nasu ta
koma Khalil? Kar fa wani wajen daban ta tafi" Khalil yace "Can ta koma Aunty, naje
har gidan nasu, i came back today" Aunty Maryam tace "Allah sarki, to me ya samu
wayar da na bata ba a samunta, Ayman ma har ya gaji da kiranta" Khalil yace "I
think charging point din ne ya lalace" Aunty Maryam tace "Toh ai kana da number
Mamarta ka turo min yanzu" Khalil yace "Oh ohk, amma ba a wannan wayar nake da
number ba, idan na kunna wancan wayar zan tura maki" Aunty Maryam tace "Toh yau
nake son ka turo min Malam, don't keep me waiting" A hankali yace "Ohk" tace "And
lastly Mami tace min ka kwashe takardunka da Cv a dakin Abbanku, ta kuma ce zata
amsa ta mayar masa, to shawaran da zan baka kada ka kuskura ka bata ko me zai faru
kuwa, ban san me ke damun Mami ba kwata kwata wallahi, don't make that mistake of
giving her na gaya maka, idan ma ya kama ka bar masu garin ne ka bari gaba daya, ta
yaya ita bata kwatar maka hakkin ka ba ka kwata da kanka kuma take neman amsa ta
mayar masa, wannan wace irin rayuwa ce?" A hankali Khalil yace "Ban san yanda zan
yi ba Aunty, and she is taking the issue so personal" Aunty Maryam tace "Kaga idan
ya kama kawai ka taho inda nake kayi zamanka cikin kwanciyar hankali, with ur
qualifications zaka samu aiki me kyau a nan, kada ka wani tsaya biyewa Mami...."
Khalil yayi murmushi yace "Nagode Aunty" Tace "Toh ni dai na gaya maka, kuma ina
jiran number Maman Nihad" Khalil yace "Toh Aunty" Daga haka ta katse wayar, ya
sauka ajiyar zuciya ya ajiye wayar yana nazari, bayan few minutes ya mike ya fita
daga dakin, dakin da Nihad ke ciki ya nufa ya bude a hankali, zaune ya ganta gefen
gado ta daura sabon towel da ta gani cikin press din dakin tana shafa turarurrukan
ta alamar wanka tayi, tana ganinsa ta jawo hijab dinta ta rufe duk jikinta, ya
tsaya jikin mirror ya rungume hannunsa yana kallonta ga kamshinta da ya cika masa
hanci, bayan few seconds ta daga kai ta kallesa tace "I need space" Ya ki ce mata
komai kuma yaki barin dakin, ganin hakan ta mike ta dau doguwar rigar baccinta zata
shiga banɗaki yayi saurin riketa, zaro ido tayi tace "Ni wallahi ka sakeni in je in
sa kayana, meye haka mana" Ya janye hijab din ya jefar saman gado dama tana ganin
haka ta rike towel dinta gam tana zazzare ido, hankalinta a tashe kamar zata yi
kuka tace "Meye haka kake yi don Allah? It's not proper plss" Ya kai bakinsa
kunnenta ya rada mata magana a hankali, sannan ya kalli fuskarta to see her
reaction, ta marairaice zuciyarta na bugawa amma ta kasa hada ido da shi, maganar
nasa yayi mata nauyi sosai, mamakin yanda baya jin kunya ko kadan take, murya can
kasa taji yace "Agreed?" Still taki kallonsa balle ya sa ran amsa, zai dago kanta
taki barin yayi hakan gaba daya a tsorace take, ya kai hannu towel din ta rike
hannunsa da sauri muryarta na rawa tace "Why are you doing this plss? Ni fa ba er
iska bace" Ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Toh ni ne ɗan iska?" Ta kasa ce
masa komai banda bugawa babu abinda zuciyarta yake, amma kuma a ranta taji gwara ta
amince da abinda yace mata tunda iya hakan ne kawai, bata hanasa ci gaba da kwance
towel din ba amma kafin ya cire ta rufe fuskarta jikinsa da sauri jikinta na rawa
tace "Ni akwai haskeee" yanda tayi maganan just turned him on the more, ga
kamshinta da ya gama rikitasa, Yana rike da ita ya nufi wajen switch din duk da
yanda kafafuwansa suka masa nauyi, ya kashe wutan dakin, tun tana nonnoke masa har
bata san sanda ta sakar masa jiki gaba daya ba kamar ba ita ba, he made sure she
savour every bit of that moment, he let her forget the global she was in, lokaci
daya hankalinta ya dawo jikinta bayan kusan minti sha biyar, tana zaro ido ta fara
turasa tace "Kace min banda shi, wayyo na shiga uku, You excluded that..." cikin
shaky voice yace "Plsss" ta fashe masa da kuka tace "Nooo, baxan iya ba wallahi"
Bashi da option haka ya kyaleta cike da karfin hali ya koma gefe yayi kwanciyarsa
upside down, har sannan jikinta rawa yake ta jawo hijab dinta da sauri ta saka,
tashi taga yayi wanda hakan sai da ya tsoratata ta koma edge din gadon da sauri
jikinta na rawa, sai taga ya sauka daga kan gadon, ta bi sa da kallo cikin duhun
har ya shiga bandaki, sai da ya kusa minti ashirin kafin ya fito taga ya kwanta a
kasan dakin, ita dai tana ta kallonsa cikin duhun, har dai ta gaji ta kwanta a
hankali ta rufe idonta amma ta kasa bacci, tana ta kwance har kusan sha biyu, tana
jin yanda yake juye juye a kasa da yake kwance, ta mike zaune tana kallonsa, can
kuma dai ta sauka daga kan gadon ta koma inda yake ta durkusa dan nesa da shi duk
da ba sosai take ganinsa ba saboda duhu tace "Are you okay?" A hankali taji yace "I
am not" Bata san sanda ta isa dab da shi ba ta durkusa tace "Baka da lafiya ne?"
You could tell from her voice that she is worried, taji ya jawota jikinsa with
trembling voice yace "I promise i won't hurt you, i promise, i promise" Sae da taji
wani mugun faduwar gaba, ta fara kokarin tashi daga jikinsa ya ki saketa yana maida
numfashi yace "Plsss,
i promise it won't hurt, trust me Nihad" Bai bata damar cewa komai ba ya cire
hijab din jikinta ya jefar.

Mami ta kasa bacci tun da taji fitar motocin operation biyu na sojoji dake gidan
wajen karfe biyun dare, kuma General na gidan, gaba daya ta kasa samun nutsuwa, ta
kira Khalil yafi sau goma bai daga ba, kuma tasan bashi da nauyin bacci, ko karfe
nawa ka kirasa na dare zai daga, sai ta fara tunanin to ko yana zaton maganar
takardun zata masa yasa ya ki dagawa, ita kuma so take taji inda yake, daga karshe
ta kira Aunty Maryam, Aunty Maryam na dagawa Mami tace "Maryam yanzu naji fitar
motocin operation a gidan nan, to gaba daya hankalina yaki kwanciya, you know how
cunning general can be, to na kira Khalil baya daga kirana, ki kirasa ki ji yana
ina, though ni dai yace min ba gidan nasa yake ba, amma ki kirasa pls" Aunty Maryam
tace "Toh bari in kirasa" Ba a dau lokaci ba Aunty Maryam ta kira Mami tace "Mami
wallahi baya dagawa" Mami taji hankalinta ya kara tashi, a hankali tace "Toh
shikenan Maryam" Aunty Maryam tace "In sha Allah babu abinda zai faru Mami ki
kwantar da hankalin ki, balle ai General din ba sanin inda yake yayi ba" Mami tace
"Toh shikenan, sai mun yi magana" Daga haka ta katse wayar ta ajiye tana ma ɗan
nata addu'ar neman tsari daga Abbansa.

*Ayi kokarin sauke bashin dari biyar ayi karatu cikin aminci hankali kwance*

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

58
Mami ta koma bangarenta da sauri ta shiga dakinta, Noor dake parlor ta bi ta da
kallo ganin yanayinta ta mike ta bi bayanta zuwa dakin, zaune ta ganta gefen gado
kamar warce taji wani mugun abu, she look shock, Noor ta karasa kusa da ita da
sauri tace "Mami are you alright?" Mami ta kasa ce mata komai sai kallonta take,
cike da damuwa Noor tace "Pls Mami ki kwantar da hankalinki kar ki fara rashin
lafiya, everything will be alright in sha Allah, don Allah kar ki sa damuwa a
ranki" Still dai Mami babu bakin magana, furucin khalil na karshe ne kawai ke ta
yawo a kanta, she is trying all possible best tayi apprehending din furucin nasa,
Noor ta zauna gefenta ganin kamar ma bata san abinda take cewa ba, ko kadan bata
son ganin Maminsu cikin tashin hankali, Noor ta kamo hannunta cikin sanyin murya
tace "Plss Mami calm down, everything will be okay in sha Allah...." Sai a sannan
Mami ta kalleta cike da karfin hali tace "Dauki wayata ki kira min Maryam...." Noor
ta tashi ta dau wayar Mami dake gaban mirror tayi dialing number Aunty Maryam ta
kai ma Mami bayan ya fara ring, Mami ta amsa tana kallonta tace "Ki je zan yi waya
Noor" Noor ta juya ta fita daga dakin, Aunty Maryam na dagawa tace "Ya ake ciki
Mami? Nayi ta kira baki daga ba, Is he alright?" Mami tayi karfin halin cewa
"Maryam i wish kina kusa da ni...." Aunty Maryam da taji gabanta ya fadi tace
"Lafiya Yaya? Hope all is well?" Mami ta kasa ce mata komai, she is just
speechless, hankali tashe Aunty Maryam tace "Hello.... talk to me, me ya faru
Mami?" Mami taji kanta ya sara mata, ta dafa kan tace "Zan kira ki Maryam" Bata
jira me Aunty Maryam zata ce ba ta katse wayar kawai ta mike ta dau Hijab dinta ta
saka ta fita.... Aunty Maryam ta gaji da kiran wayar Mami, daga karshe ta kira
Noor, Noor na dagawa Aunty Maryam tace "Noor me ke faruwa?? Ina Mamin?" Noor tace
"Wallahi ban sani ba, kawai tace min zata je wajen yayanmu a guardroom, kuma da ta
dawo naga mood dinta gaba daya sae a hankali" Aunty Maryam tace "Ta samu ganinsa
kuma?" Noor tace "Toh ban dai sani ba, kawai naga ta shigo wani iri, i asked what
the problem is bata ce min komai ba" Aunty Maryam tace "Abban naku na gidan ne??"
Noor tace "Baya nan tun jiya" Aunty Maryam duk hankalinta ya tashi, tace "Ina Mamin
yanzu take?" Noor tace "Yanzun nan ta fita" Aunty Maryam tace "Kai mata wayar da
sauri don Allah" Noor ta mike ta fita da sauri, har ta iso main parlor bata ga Mami
ba sai Aunty Hassana dake zaune ta cika parlon da kas kas din cingam, Noor na
fitowa compound ta gan Mami cikin mota za su fita with 3 soldiers, tsaye tayi tana
kallon motar har suka fita daga compound din, Noor ta koma ciki ita ma duk jikinta
yayi sanyi, ta kira Aunty Maryam tace "Aunty naga ta fita a mota kuma yanzu" Aunty
Maryam taji hankalinta ya kara tashi sosai, ta ji kamar tayi tsuntsu ta ganta a
Nigeria, Aunty Maryam tace "Kin tabbata kuma Khalil na guardroom din?" Noor tace
"Da asuba fa suka shigo gidan nan, i am sure yana ciki, kuma na tambayi wani soja
dazu yace min yana ciki" Aunty Maryam ta katse wayar kawai, babban damuwarta rashin
maganar da basu yi da Mami ba har ta fita gidan, to ina zata? Ko gidan Hajiya
Safeenah?
Gaba daya hankalin Mami baya jikinta har suka iso gidan Khalil, ta bude motar ta
sauka tana kallon gate din gidan dake a kulle, daya daga sojojin ya karasa ya bude
mata gate din da makulli, har bakin kofar shiga main parlor suka rakata, cike da
karfin hali tana kallonsu tace "Ku jira ni nan" Suka tsaya bakin kofar ta shiga
ciki tana bin parlon da kallo, mutuwar tsaye tayi ganin takalmin mace dake kofar
parlon, she became weak lokaci daya, taji kafanta sun mata nauyi, banda faduwa babu
abinda gabanta yake, tana tafiya a hankali ta nufi staircase dake parlon ta haura
sama kamar me counting stairs din, ta fi second ashirin tana bin kofofin dakunan
dake sama da kallo, master Bedroom din Khalil ta fara shiga taga ba kowa ciki sai
pajamas dinsa dake saman gado, ta fi minti daya tsaye a dakin kafin ta juyo a
hankali ta fito daga dakin, ta tafi ta bude wani kofar very gently, gabanta ya
yanke ya fadi, komai ya tsaya mata cak ganin mace kwance saman gado ta takure cikin
duvet sae dai ba a ganin fuskarta sbda ta rufe da duvet sae gashin kanta dake baje,
Mami ta ji ta kasa ci gaba da tsayuwa zuciyarta ya dinga bugawa babu kakkautawa, is
this for real or she is dreaming, yanzu abunda Khalil ya fada gaskiya ne kenan, ta
juya da sauri ta fita daga dakin ta koma corridor ta dafa bango, bata san sanda ta
fashe da kuka sosai ba tana furta "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" yanzu da
gaske aure Khalil yayi duk basu sani ba? aure yayi without the knowledge of his
parent? What came over him? does that mean bai daukesu a bakin komai ba kenan, duk
yanda take kokarin ganin ta kyautata masa saboda abinda ubansa yayi masa ta haka
zai saka mata, yanzu abinda Khalil zai mata kenan, da bata san waye ɗan nata ba da
sai tace karya yake kawai macen banza ya kawo gidan nasa ya ajiye, amma tasan
halinsa tasan abinda zai aikata da wanda baxai aikata ba, tunda yace matarsa ce
definitely matar tasa ce, amma a ina yaje yayi auren nan? Lokaci daya tunaninta ya
tafi kan Hajiya Safeenah, da wani idon zata kallesu ma dai tukun? Kuka kawai Mami
take ta rasa wani tunanin zata yi, wannan wani irin jarabawa ne astagfirullah, me
ya samu khalil haka? how is everybody going to take this barin ma Abbansa,
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ita kanta bata lamunta da auren nan ba kuma
baxata taɓa lamunta da shi ba, bata taɓa jin takaicin ɗan nata ba sai yau, yau taji
haushinsa da bata taɓa ji ba, yayi disappointing dinta ta yanda bata yi tunani ba,
zata nuna masa ita ta haifesa ba shi ya haifeta ba, za kuma ta nuna masa yanda bai
yi shawara da su wajen zuwa yayi aurensa ba haka babu shawaransu zai rabu da
yarinyar cikin gaggawa ko ya ki ko ya so, idan ko ba haka ba sae dai ya nemi wata
uwar ba ita ba, this time around she is going to show him bai isa yayi controlling
dinta ba, she isn't going to take it likely with him, ba don tasan babu ta inda
yarinyar zata fita ba da kawai juyawa zata yi tace ma sojojin su mayar da ita gida
yarinyar tayi ta dauwama a gidan, kuma bata ga dacewar fita tace ma sojojin su
shigo su tasheta ba, da abinda xata yi kenan da dai ita ta shiga ta taso ta, ta
share hawayenta zuciyarta na ƙuna ta koma cikin dakin tana kallon Nihad, ko motsawa
Nihad bata yi ba a yanda take kwance, sabida takaici Mami taji baxa ma ta iya
karasawa tace zata tasheta ba, she just can't, kawai ta juya hawaye na sauka idonta
ta fita daga dakin tana girgiza kai, downstairs ta sauka tana goge idonta ta tafi
waje, har sannan sojojin suna tsaye balcony ta amshi wayar daya daga cikin sojojin
ta koma parlor tayi dialing number Noor, Yana fara ring Noor ta daga, Cike da
karfin hali Mami tace "Ki dau driver ku taho gidan Khalil yanzu" Noor da hankalinta
ya tashi tace "Mami hope all is well?" Mami tace "Kiyi abinda nace yanzu, ina jiran
ki" Daga haka ta katse wayar, Zaunawa tayi saman kujera a parlon zuciyarta a
dagule, takaici baxai bari ta iya tashin yarinyar ba, gwara kawai Noor taje ta
tasheta idan ta karaso, Mami na ta zaune lokaci lokaci hawaye ke sauka idonta, bata
taɓa expecting haka daga Khalil ba, she least expect this from him, bayan kusan
minti talatin Noor ta iso gidan, tana shigowa parlon ta karaso wajen Mami da sauri
duk hankalinta a tashe tace "Mami me ke faruwa?" Mami tace "Tafi sama ki taso
yarinyar dake daki a kwance" Noor ta zaro ido tace "Yarinya kuma? Me ya kawota
nan?" Ganin Mami tayi shiru bata ce komai ba, fuskarta zar takaici, Noor ta nufi
sama gabanta na faduwa, direct dakin da Nihad ke ciki ta fara budewa, ai ko taga
mutum a kwance, still tayi bakin kofar gabanta na bugawa, can dai ta karasa cikin
dakin tana tafiya a hankali tana kallon saman gadon, tapping gefen gadon tayi,
Nihad ta bude idonta a hankali amma ta kasa sauke duvet din fuskarta don ko ina na
jikinta ciwo yake mata na fitar hankali, ko kwakkwaran motsi bata son yi, a
tunaninta kuma Khalil ne, Noor ta sake buga gadon amma Nihad bata motsa ba, hakan
yasa tayi karfin halin yaye duvet din tana kallon fuskarta, bata san sanda ta mike
a kidime ta dafe kirjinta ba tana zaro ido ganin warce ke kwance saman gadon, tana
in ina tace "You????? What are you doing here??" Sae a sannan Nihad tayi kokarin
daga kanta jin muryar warce take ji, Nihad ta kasa ci gaba da kallonta, Noor dai
gabanta sai faduwa yake tana kallon Nihad, ganin abun take kamar a mafarki, wato
Yayansu gidansa ya dawo da ita da zama ashe?? Wayar hannunta ya fara ring ta duba
da sauri ganin number da Mami ta kirata da shi dazu ne ta kalli Nihad, tace "Ki
tashi" Nihad ta kalleta amma she couldn't say a word, Noor na ganin yanayinta ta
ɗan yi jim, don daga lips dinta har idonta sunyi ja sosai, and she looks so sick,
can tace "Are you okay?" Nihad bata ce mata komai ba, Noor na kai hannunta jikinta
tayi saurin janye hannun, bata taɓa sanin temperature din mutum na irin wannan
zafin ba, ta koma baya tana kallonta, sai ga Mami ta sake kiran wayarta, Noor ta
daga daga daya bangaren cikin fada Mami tace "Uban me kike yi a dakin ne? Baxa ku
fito a kulle gidan ba" Noor ta kasa cewa komai da farko ita duk tunaninta Mami
tasan Nihad ce a kwance, Mami tace "Hello, baki ji na ne..." A hankali Noor tace
"Mami she is very sick fa" Mami taji wani sabon faduwar gaba, tace "Sick? Toh
baxata fito ba kenan?" Noor dai ta kasa cewa komai, Mami ta katse wayarta, Noor ta
karasa saman gadon ta kamo hannun Nihad tace "Ki daure ki tashi, za a kulle gidan
as instructed by our father" Nihad ta girgiza mata kai amma ta kasa cewa komai,
Noor ta cire duvet din gaba daya wanda shi ma duk ya dauki zafi, dai dai nan Mami
ta bude kofar dakin, and she met the shock of her life, don sai da numfashinta ya
dauke na yan dakikai saboda bugun da zuciyarta yayi, ta dinga kallon Nihad da
idanuwanta kamar zasu fito bata ko kiftawa, lokaci daya taji komai ya tsaya mata
cak, at yhe same time kanta ya kulle, zuciyarta ya canza bugun da yake yi, wait....
raina mata hankali Khalil zai yi?? wannan din ce zai ce ma matarsa saboda ya fara
shan wiwi, dama gidansa ya kawota all this while, shine yake kokarin covering up
yace matarsa ce tunda yasan babban laifi yayi, a fili tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, me zan gani haka?" Nihad dai ta kasa ci gaba da kallon Mami, Mami
ta daka mata wani tsawa tace "Me kike yi a nan? Amma dai babu tantama daga sama
kika fado babu iyaye...." Noor ta kalli Mami, sannan ta kalli Nihad, sai a sannan
ta fahimci Mami bata ma san ita ce a dakin ba, da sauri Noor ta nufi Mami tace
"Mami she is very sick" ko sauraronta Mami bata yi ba cikin bacin rai tana kallon
Nihad tace "To zo ki fita...." Duk da Nihad na jin ko tashi zaune bazata iya ba,
haka tayi karfin hali ta yunkura zata sauka daga saman gadon, abu biyu taji a
lokaci daya, wani mugun jiri sannan kuma taji kamar ta taka allurai a kasan kafarta
har zuwa laps dinta, bata san sanda ta fasa kara ba, sai kuma ta tafi luuu ta fadi
kasan dakin, Mami dai sai kallonta take, controlling temper dinta kawai take kada
ta fadi abu da zai yi affecting ɗan nata taje tayi masa baki, bata taɓa jin ɓacin
rai irin na yau ba, Noor ta durkusa gaban Nihad sai taga kamar bata motsi, ta kalli
Mami da sauri tace "Mami kamar fa suma tayi" a fusace Mami tace "Dauki Hijab dinta
ki bata ta fitar min daga nan, idan taje waje sai ta suma...." Noor ta mike ta
kalli Hijab din Nihad dake saman gado ta dauka, kallon bedsheet ta dinga yi sai
kuma ta kalli Mami dake kallon saman gadon ita ma, Mami ta karaso dakin tana kara
kallon zanin gadon, Noor dai sai kallon Mami take, bayan few seconds Mami tace
"Ajiye Hijab din kije ki ce ma sojojin nan they should be patient muna fitowa" Noor
ta nufi kofa ta fita, Mami ta sake kallon saman gadon sannan ta kalli Nihad dake
kasa, dukawa tayi gabanta cike da karfin hali tace "Me ya sameki?" Nihad ta bude
idonta da yayi ja a hankali tana kallonta amma ta kasa cewa komai, Mami ta dake
tace "Tashi zaune" Hawaye ya fara gangarowa idonta ta girgiza mata kai kawai, Mami
ta kai hannu jikinta taji sa kamar wuta, ta dagota tace "Hau saman gadon" Nihad ta
girgiza kai da sauri cikin muryarta da baya fitowa tace "Baxan iya tashi ba...."
Mami ta kasa hada ido da ita, sai da ta fara cire zanin gadon sannan ta taimaketa
zuwa saman gadon, kamar warce aka zare ma laka ta fita daga dakin ta sauka kasa
tana kallon Noor dake zaune parlon tace "Kina da number Dr Rukayya?" Noor tace "Eh
ina da shi" Mami tace "Kira min ita" Noor ta shiga neman number bayan tayi dialing
yana fara ring ta mika ma Mami, Mami ta amsa ta kai kunne Dr Rukayya na dagawa suka
gaisa Mami tace "Hajiya Fatima ce ke magana Dr" Dr Rukayya tace "Na gane Hajiya, ya
yaran?" Mami tace "Alhamdulillah, pls za ki zo ki duba mara lafiya ne amma ba can
gida ba, will send u the address right away" Dr Rukayya tace "Ohk Ma" Mami ta katse
wayar ta tura mata address din gidan Khalil, daga haka ta mika ma Noor wayarta ta
koma sama duk jikinta ya mutu, tsaye tayi corridor tunani kala kala na yawo a
ranta, she is confuse, meye hakan ke nufi kenan? Tana safa
da marwa a corridor din for almost 20 minutes don hakan kadai ke sata jin relieve
din abubuwan da suka tunkushe a zuciyarta, har dai likitan ta iso gidan, Noor ta
kai ta sama ganin Mami na corridor ta sauko kasa ta bar su, Mami suka kara gaisawa
da Likitan sannan suka shiga dakin tare, likitan na kallon Nihad tace "Me yake
damun ki yan mata?" Nihad dai kallonta kawai take ba bakin magana, duk gaba daya
tayi laushi, Likitan tayi considering haka ta kalli Mami dake tsaye tace "Hajiya
what's wrong with her, and for how long is she sick, naga ta jikata da yawa..."
Mami ta hadiye wani abu da kyar tace "I don't know precisely Dr, amma dai ki dubata
ki ga" Likitan na kallon Nihad cikin kwantar da murya tace "Just indicate duk inda
kike jin ciwo...." Nihad ta nuna mata kanta sai kuma kafarta, Likitan ta dinga
kallon kafar tace "Daga ina zuwa ina?" Nihad ta nuna mata daga lap dinta har kasa,
Mami dai ta jingina da bango don tsayuwar taji yana neman ya gagaranta, Likitan
tayi shiru tana kallonta, can ta kalli Mami tace "Is she a new bride?" Rasa abun
cewa Mami tayi lokaci daya taji kamar ta fashe da kuka, Likitan ta na kallon kayan
baccin jikin Nihad da kyau sai ta lura da few blood stain, Kallon Mami likitan
tayi, kawai sai Mami ta juya ta fita daga dakin hawaye na zuba a idonta, hakan ya
daure ma likitan kai ta kalli Nihad tace "Are you married??" Nihad tayi karfin
halin gyada mata kai, Tashi likitan tayi ta shiga bandaki, tana ganin zanin gadon
dake bandakin ta tabbatar da zarginta, ruwan zafi kawai ta hada a bathtub, ta fita
xuwa wajen Mami tana kallonta tace "Za a samu gishiri Hajiya?" Mami tayi karfin
halin girgiza mata kai kawai, Likitan ta koma ciki, dole ta ɗan ɗiga disinfectant
dake bandakin sannan ta fito, sosai taji tausayin Nihad kafin su karasa bandakin,
she is in so much pain, sai ta fara imagining where is the husband that is this
heartless, wannan ma yana da imani kuwa, duk yanda tayi da Nihad ta shiga ruwan kin
shiga tayi tana kuka kamar yanda tayi ma khalil jiya, bata mance wahalan jiya ba,
Sun bata minti kusan biyar a haka likitan na fama ta shiga ta ki, likitan ta kara
ruwan zafi a bathtub din ta fita daga bandakin taje ta samu Mami, tana kallon Mami
tace "Tana bukatar ta shiga ruwan zafi, ban san ko zaki mata magana taji ba, she
isnt co-operating" Mami was lost of words, kawai ta gyada ma Likitan kai, likitan
tace "Zan fita yanzu in siyo mata drugs da allura" A hankali Mami tace "Toh" Daga
haka Likitan ta sauka downstairs, Mami ta shiga dakin sannan ta karasa bandakin, ta
fi minti daya tsaye kafin ta tura kofan, Nihad tayi da ta sanin da bata hakura duk
azaban da zata ji ta shiga a haka ba, bata yi zaton Mami likitan ta tafi ta kira
ba, ga kunyan yanda Mami ta shigo ta ganta, ta kasa yi ma Mami musu banda hawaye
babu abinda take, haka nan ta shiga ruwan, bata san daga inda dauriya ya zo mata ba
a wannan lokacin, Mami ta canza mata ruwan ya kai sau uku, daga karshe ta tara mata
ruwan wanka, duk wannan abun karfin hali kawai Mami take amma her heart is so
heavy, bata yarda su hada ido da Nihad all through ba, kamar yanda ita ma Nihad din
bata iya ta hada ido da ita ba saboda kunya, Nihad na wanka Mami ta wanke bedsheet
din ta fita daga bandakin, zaunawa Mami tayi gefen gado ta rike kanta, ita Khalil
yayi deceiving haka? Tunanin abinda zata masa taji sanyi a ranta kawai take, ta ina
za a fara wannan babban lamarin? Hawaye ya hau sauka fuskarta tana girgiza kai, she
wish all this is nothing but a dream, daga karshe ta mike ta fice daga dakin ta
shiga wani dakin daban, Nihad na fitowa bathtub din taji dama daman abinda take ji,
amma har sannan zazzabin na jikinta, tana dingishi cike da karfin hali ta fito daga
bandakin daure da towel ta kwanta saman gado ta takure waje daya tana jin sanyi.
Bayan wani ɗan lokaci Mami ta goge idonta ta sauka downstairs tana kallon Noor tace
"Ki duba ko akwai yanda zaki dafa mata shayi a kitchen, idan babu kuma ki fita ko
restaurant ne ki siyo mata abinci kafin likitan ta dawo" Noor tace "Toh" Mami ta
juya ta koma sama tana jin jikinta babu dadi kwata kwata, kofar dakin da Nihad ke
ciki ta bude ta ganta kwance har ta fara bacci, Mami ta karasa cikin dakin tana
kallonta tunani iri iri na yawo a zuciyarta, press din dakin ta nufa ta bude taga
babu kaya a ciki, ta kalli akwatinta dake dakin tana tafiya a hankali ta nufi gun
akwatin ta bude tana duba kaya a ciki, wata doguwar riga ta fiddo mata da underwear
sannan ta mike ta karasa kan gadon, bude akwatin da Mami tayi ya tada Nihad, Mami
ta ajiye mata kayan a gefen gado ba tare da ta kalli idonta ba tace "Tashi ki sa"
Nihad ta mike zaune, Mami ta fita daga dakin, hawaye kawai Nihad take, all her
thought was that Khalil left her upon the condition she is in, bai duba halin da
take ciki ba yayi tafiyarsa ya kyaleta haka, rabon da taji haushinsa yanda take ji
yanzu tun farkon zuwansa gidansu.....
Har kusan azahar Nihad bacci take tun bayan da Dr Rukayya tayi mata allurai ta bata
magani, ita ma Mamin maganin bacci ta sha don truly bata jin dadin jikinta, tasan
da kyar idan jininta bai hau ba, nan spare room dake gidan tayi bacci har kusan
azahar din ita ma, har a lokacin kuma Noor na gidan, ana idar da azahar Mami ta
sauko downstairs tana kallon Noor tace "Zan kiraki zuwa anjima, xan je gida yanzu"
Noor tace "Toh Mami, Allah ya kiyaye" Daga haka Mami ta fita tare da sojoji biyu
suka maida ta gida, tana sauka compound direct Guard room ta nufa wani soja yayi
saurin bin bayanta yace "Hajiya Oga ya dawo ai an fito da shi" Mami da gabanta ya
fadi don sai da yayi magana taga motar Janar a gidan, ta juya tana kallonsa cikin
karfin hali tace "Yana ina?" Sojan yace "Yana ciki" Mami ta karasa cikin gidan da
sauri, tana shiga main parlor Aunty Hassana na kyabe baki tace "Plan din naku yayi
aiki...." Mami ta kalleta sai kuma kawai ta tafi part din Khalil, bata gansa a
dakinsa ba, ta fito kenan sai ga Mimi ta biyota, Mimi tace "Mami yana part din
Abba, he is very sick" Mami tace "Me yake yi a can?" Bata jira abinda Mimi xata ce
ba ta nufi bangaren Janar, bude kofar parlon tayi, taga Aliyu a tsaye Janar dake
zaga Parlon yana ma Aliyun magana, don shi bai iya tsayuwa waje daya, Ta dinga bin
parlon da kallo bata ga Khalil ba, Aliyu yayi kasa da kai yace "Ina yini" Mami tace
"Where is Khalil" Wani kallo Janar yayi mata ya ci gaba da gaya ma Aliyu abinda
yake gaya masa na zuwa Germany da zai yi akan wani business, Aliyu ya nuna mata
inda Khalil yake, ta karasa ta bude kofar da sauri, kwance ta gansa saman gado yana
bacci, ga allurai da drugs a kan bedside drawer, sai kuma drip da aka sa masa, har
sannan kuma hannunsa daya akwai handcuff, ya bude ido a hankali jin an bude kofar
dakin don baccin nasa sama sama ne, ganin Mami sai da gabansa ya fadi, ya mike
zaune da sauri kusan a firgice, Mami ta dinga kallonsa kafin ta karasa cikin dakin
ta tura kofar tana girgiza kai cike da takaici tace "Wato ni zaka raina ma hankali
Khalil? Ni ka maida yar iska tsohuwar banza, ni zaka raina ma wayo kamar kai ka
haifeni, ka ban mamaki wallahi, ka ban mamaki, dama kuma tun farko ni ce ban tsaya
nayi nazari ba, amma da na tsaya nayi nazari da na gano cewar babu iyayen arziki da
za su hada 'yar su da namiji wai ya kai ta karatu, a da ina alfahari da tarbiyan da
na maka amma banda yanzu, i can't count on you now, ban taɓa tunanin akwai ranan da
zaka saɓa ma Allah ta hanyar zina ba" Khalil ya katseta da sauri yana girgiza kai,
zuciyarsa na bugawa yace "Keep on counting on me Mami, i am not a fornicator, ban
taɓa ba, kuma baxan fara ba, i am sorry ban san ta yanda zan billo ma lamarin bane,
amma Nihad matata ce ta sunna... Da aurenmu na kawota gidan nan, kamar yanda kika
fada da ba don aure ba babu abinda zai sa iyayenta su bari in taho masu da yar su
daga ni sai ita...." Mami kallonsa take babu ko kiftawa with new shock, lokaci daya
ta fashe da matsanancin kukan takaici tana girgiza kai ranta na mata zafi tace "Sai
dai in bayan raina zaka zauna da ita a matsayin matarka... amma matukar da raina a
doron kasa to wllh babu aure tsakaninka da yarinyar nan, wallahi baza ka zauna da
ita ba...." Tura kofar dakin aka yi Mami ta juya da sauri tana share Idonta, Janar
na kallon Khalil with the expression of soldiers yace "Wacece matar taka???" Mami
ta fashe da kuka sosai tana girgiza kai tace "Ban taɓa dana sanin haifanka ba sai
yau Khalil, kuma ina me tabbatar maka sai dai ka zaɓi ko ni ko yarinyar, baxan taɓa
hada zuri'a da ita ba wallahi tallahi, this time around duk abinda ubanka zai maka
yayi maka sannan nima ka jiraye nawa hukuncin, sai na nuna maka ni na haifeka ba
kai ka haifeni ba" Daga haka ta fice daga dakin, zufa ya dinga keto masa yaji kansa
yayi masa mugun nauyi, lokaci daya zazzabinsa ya dawo masa sabo, Janar dake ta
kallonsa yace "Wace yarinya kenan take magana a kai??" Lokaci daya hawaye ya kawo
idon Khalil idan Mami tayi masa haka waye kuma zai tsaya masa, yana kallon Abbansa
ya kasa cewa komai saboda shock, Abba ya masa tsawa yace "I am talking to somebody"
Khalil ya rike kansa with shaky voice yace "A gidan da na zauna a kano suka bani
aurenta, ni kuma na amsa saboda sun amsheni a lokacin da aka nuna ba a bukatata a
gidanmu, i can't tell them no" Janar na ta kallonsa yace "So now, where is the
girl?" Khalil ya kasa dagowa yace "Tana gidana" Janar ya hau safa da marwa a dakin
kamar me pareti, can yace "Sai suka ce kuma ka boye mana ko?" Khalil ya dago a
hankali yana kallon Abbansa with tears in his eyes, Janar na gyada kai yace "Zaka
kai ni har kanon gidan iyayen yarinyar to make confirmation, and if i should find
out u are lying sai na karya maka kafa i promise, idan kuma din da gaske matarka ce
that's fine...." Daga haka ya juya ya nufi kofa Khalil ya bi sa da kallo zuciyarsa
na bugawa.......

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

https://instagram.com/ruuscollections?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==
Ruuscollections turaren wuta and more we got you everything scent,long lasting
fragrance at very affordable price, change or complete refund if you don't like any
of our product in Sha Allah
Arabian,Traditional,English,Khumra ,Oil
perfumes,Koleccha,Morphingmist,Roomfreshener,
Armpit powder, Mouth freshener,Laces ,Shoes,
Bags,Atamfa, 07025393114
[8/15, 8:24 AM] Maman Al'ameen VIP: 💖 NIHAAD 💖

57

*This page is dedicated to my one and Only Deejah me lamurje, she is a sister from
another Mother, ina kuma sonta har cikin raina, Allah ya bar xumuncinmu har
aljanna*🥰😍
Hajiya Zahrah Me gari naji labarin Najar Jikamshi ya siya maki sabon kasuwar cikin
garin dutse, to su kuma yan dutse su yi yaya? Ko da yake ga dai kasuwar Hakimi. 🤔

Khalil na zaune gefenta ya jinginar da kansa jikin gado yana kallonta ko kiftawan
kirki bai yi, gaba daya a sanyaye yake kamar ba shi ba, bai taɓa jin haushin kansa
irin yau ba, he know she will ever trust him again because he never fulfilled the
promise he made to her, he can't tell what came over him that way, he didn't take
it easy on her, and all this is making him feel so bad, duk motsin da Nihad zata yi
idonsa na kanta, even in sleep she doesn't look alright, baccin karfin hali kawai
take, duk tayi laushi saboda wahala, wani mugun tausayinta yake ji har ransa, a
karo na farko kuma yaji yana son sanin ta yanda video dinta ya fita, yaji yana son
yasan who is behind the leakage of that video of her, da kuma a inda aka yi sa,
this he is going to find out by all means.... Bacci take amma restlessly, kana
ganinta kasan she is in severe pain, he wish he can help her more than the way he
did, but babu wani abinda xai iya mata bayan wanda yayi mata don ko kwayar magani
babu a gidan, ji yake dama zai iya mayar da pain din nata zuwa jikinsa, duk ya kagu
gari ya waye ya bata full care din da take bukata, ya kamo hannunta a hankali ganin
ta kasa kwanciya guri daya sai juye juye take, he is been sitting there for almost
an hour now, and bai damu ya zauna a hakan har gari ya waye ba just to keep an eye
on her, hannunsa ya kai goshinta yaji temperature dinta is gradually getting so
high, hakan da yayi yasa ta bude idonta da suka kumbura a firgice tana kokarin
tashi zaune ya kwantar da ita, cikin sanyin murya me cike da damuwa yace "I am only
feeling ur temperature" Taki bari su hada ido ta juya kanta tana sauke numfashi a
hankali ta kulle idonta, ya duka dai dai kunnenta cikin sanyin murya that is full
of remorse yace "I am sorry Nihad, i never meant to hurt you this way.... Don Allah
kiyi hakuri.... I was just..." Sai kuma ya kasa ci gaba, he felt so bad because he
is making her pass through much pain, ya kife kansa saman gadon ya kasa cewa komai,
Ita dai bata bude idonta ba duk da hawayen dake zuba ta gefen idon nata a hakan,
bayan few minutes ya dago kansa a hankali yana kallonta da idanuwansa da suka kada,
ya ga alamar ta koma baccin, ya kalli agogo da yayi strucking karfe biyu da minti
sha biyar, ya sake kallonta yaga baccin take yi, a hankali ya kai hannu ya goge
hawayen dake fuskarta sannan ya mike duk jikinsa ba kwari ya nufi kofa, karfin hali
kawai yake don ji yake kamar zazzabi na neman rufesa, har ya fita ya dawo ya dau
Hijab dinta ya ajiye saman bedsheet din sannan ya juya ya fita daga dakin ya kulle
kofar a hankali, nasa dakin ya koma, ya shiga bandaki ya tara ruwan dumi yayi wanka
sannan ya fito, a daddafe ya goge jikinsa ya saka Jallabiyarsa sannan ya kwanta ya
rufa da duvet feeling feverish, ga wani sanyi da yake ji, yana son tashi ya koma
dakin nata to check on her amma ya kasa tashi, lokaci daya zazzabi ya rufesa, yana
ta kwance cikin duvet yaji kamar tsayuwar motoci a waje, ya bude fuskarsa wanting
to be sure of what he heard, Bai san sanda ya yunkura ya mike ya nufi windown
dakin da sauri ya bude curtain din, sosai gabansa ya fadi jin ana taɓa gate din
gidan, da hanzari ya shiga parlornsa ya bude kofar balcony dake wajen don ta nan ne
kadai zai iya hango kofar gidan da kyau, still yayi yana kallon motocin wa enda
yake hangowa a kofar gidan, lokaci daya hankalinsa yayi mugun tashi, ya juya da
sauri ya fito ya koma bedroom dinsa ya dau wayarsa zuciyarsa na bugawa, nan ya ga
missed calls din Mami ya kusa sha biyar, Ga kuma na Aunty Maryam duk few minutes
ago, he was just confused at this stage, gaba daya ya rude, ya koma dakin da Nihad
take da sauri, rasa yanda zai yi yayi, ya jingina da bango zuciyarsa na bugawa
sosai, da shi kadai ne gidan sai dai su shigo su dau hotonsa da za su gani manne a
parlor amma ba dai shi ba, definitely sai ya sami hanyar fita cikin lokaci kankani,
he will surely find a way out for himself, but yanzu bazai yi hakan ba ga Nihad,
yaji kafafuwansa sun kasa daukansa ya karasa da kyar ya zauna gefen gadon ya rike
kansa da yayi masa nauyi sosai, duk wani tunaninsa ya kwance a lokacin, bai kuma
sannua zai yi ba, his father really caught him unaware, yana jin suna ta kokarin
bude gate din gidan babu kakkautawa, can yayi karfin halin tashi ya tafi dakinsa ya
dauko duvet ya fito ya dawo dakin da Nihad take, lulluba mata duvet din yayi a jiki
a hankali, don riga ce iya gwiwa da ya sa mata daxu a jikinta, ta bude jajayen
idonta da sauri tana kallonsa, yayi kissing goshinta yaji jikinta yayi mugun zafi,
ya lumshe idonsa yayi kissing lips dinta a hankali yace "I don't want you to be
cold.... I am sorry i made u sick Nihad" Ta rufe idonta don muryarta ma a dashe
yake, bata taɓa sanin akwai irin wannan wahalan ba a duniya sai dazu, ya mike a
hankali ya fita daga dakin, ya zura wayarsa a aljihu sannan ya sauka downstairs duk
da yanda kansa ke juya masa, ya nufi kofar parlor ya bude ya fita, direct gate din
ya nufa, ya ɗan tsaya for few seconds, can ya runtse ido lokaci daya ya bude gate
din yana kallonsu, Sojoji ne sun kai su goma a bakin gate din, daya daga cikinsu
yayi gripping din hannunsa yana kallonsa, Khalil ya hade rai yace "Easy Mr Man, kai
ka kamani ko ni na kawo kaina??" Tuni wani ya miko handcuff, shi dai kallonsu kawai
yake kirjinsa na sama da kasa, ganin yanda sojan ke kiciniyar saka masa handcuff
din kamar wanda yayi sata, Khalil yaki bari ya saka, yana huci yace "Ce maku aka yi
nayi sata ku zo ku daureni?" Duk cikinsu babu wanda ya kalli fuskarsa balle su ce
masa komai a wajen, har sai da suka makala masa suka yi hanyar mota da shi, wani
sojan ya tafi ya kulle gidan Khalil na kallonsa, anyi masa ire iren haka ya fi a
kirga don haka ba sabon abu bane wannan a wajensa, kuma yanda Janar ya basu umarni
su yi haka suke yi, shi sa duk bakaken maganar da Khalil zai gasa masu basa daga
kai su kallesa balle su ce masa komai, don ko dungurinsa Najar bai basu umarni su
yi ba, iyaka su saka masa handcuff su kawo masa shi har gida.... (au Janar xan ce
wai Najar
😂)
wajejen karfe hudu na asuba suka isa gida da shi, direct Guard room dake cikin
compound din suka kai sa suka turasa ciki sannan suka rufe wajen da kwado, leaving
him all alone, Khalil ya rike kansa dake sara masa, why didn't he think twice kafin
ya shiga gidan, he just forgot who his father is, babban damuwa da tashin
hankalinsa yanzu bai wuce Nihad ba, she needs to be taking care of, she needs him
by her side, yasan baxata iya yin komai ba, wannan tunanin yasa yaji zazzabinsa ya
dawo da karfinsa, har aka yi kiran sallah na biyu ko gyangyadi khalil bai yi ba, ga
sauro sai abinda suka manta ne basu masa ba a jikinsa, ko kwanciya mutum bashi da
damar yi a guard room din, wajen ne ɗan tsut da shi, ana tada sallan asuba sojoji
uku suka zo suka bude karfen Guard room din, fitowa yayi da kyar yana jin kansa na
juya masa, ya dafa bango da sauri, ɗan cell ne wajen kafin ainahin guard room din,
shi cell din ba laifi yana ɗan da sarari duk da shi din ma dai ba babba bane, a
cell din kuma har da bandaki a ciki, yasan dalilin budesa da suka yi bai wuce ya
fito yayi alwala a cikin bandakin dake cell din ba yayi sallah, yayi namijin kokari
wajen shiga bandakin, ko kafin ya fito ya ga darduma an ajiye masa nan cell din, ya
dauka ya shimfida, suna ta tsaye bakin kofa har sai da ya idar da sallah, suka sake
maida sa cikin guard room din suka kulle sannan suka kulle cell din ma daga waje,
Khalil ya hade kansa da karfen Guard room din, duk da yanayin da yake ciki Nihad ce
kawai a ransa, he is so worried because of her, banda ita he don't mind being in
the guard room for weeks tunda dai ya saba zama ciki, kuma yanda Abba yasa aka
ajiyesa a nan zai iya tafiyarsa ya mance da batunsa har sai randa Allah ya dawo da
shi, iyaka a dinga kawo masa abinci da ruwa, for the sake of Nihad yaji zai iya
mayar masa duk abinda yayi seizing, duk da zafin da guardroom din shi sanyi yake
ji.... Yana nan a haka har wajen karfe takwas ya ji ana bude kofar cell din, ya
daga kansa, sojan na gama bude cell din Mami ta shigo ciki tana kallon ɗan
guardroom din, Sojan ya karaso ya bude karfen guardroom din... Khalil ya kasa
fitowa saboda zazzabin da ya ci karfinsa, Mami ta karasa tana kallonsa, cike da
karfin hali ya fito, Mami na ganin yanayinsa taji hankalinta ya tashi tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Yanzu meye amfanin haka khalil, kaga abinda
nake ta gudar maka ka kasa ganewa...." Sai kawai ta fashe da kuka, Da sauri taga ya
shiga bandakin cikin cell din wanting to throw up, ta bi bayansa hankalinta a mugun
tashe, tana rike da hannunsa suka fito daga bandakin don ya kasa aman, ya zauna nan
kasan cell din ya jinginar da kansa jikin bango ya lumshe ido yana sauke ajiyar
zuciya, Mami dai sai hawaye take barin yanda taji jikinsa yayi zafi, it's rare aga
yana rashin lafiya shi yasa ma hankalinta ya tashi yanzu, to kiran Abban nasa zata
yi tace bashi da lafiya yanzu kenan, tana yin hakan kuma zai ce ita ke supporting
dinsa yayi duk abinda yake yi, gaba daya she is confused, ta durkusa gabansa tace
"Abinda nake ta gudu kenan, kasan waye Abbanka Khalil, kasan abinda zai iya
aikatawa, ban san me yasa zaka shiga gonarsa ba..." Sai kuma ta fashe da kuka, ya
kamo hannunta cikin sanyin murya yace "I am sorry Mami...." Tace "Ka fada min wani
maganin za aje a siyo maka idan kayi breakfast yanzu sai ka sha" Ya girgiza mata
kai kawai, tace "You don't look okay, so kake ciwon ya kwantar da kai a nan? Ka
gaya min maganin da za a siyo maka in je yanzu a siyo" Yayi kasa da murya yace "I
am not sick, i am just worried, i am disturbed, not because ina cikin guard room"
Mami na kallonsa tace "What is making you worried then?" Ya kasa hada ido da ita,
sai ma sunkuyar da kansa da yayi, da damuwa tace "Talk to me son, meye damuwarka?
Ni mahaifiyarka ce kar ka boye min" Lokaci daya idanuwansa suka kada ya dago kai
cike da karfin hali yace "Na maku laifi during my stay in kano" Mami ta dinga
kallonsa tace "Laifi? Laifin me son?" Ya kamo hannunta gathering all sort of
courage, muryarsa na rawa yace "I got married while in kano" da wani expression
Mami ta dinga kallonsa kamar me son fahimtar abinda yace, can tace "Ban fahimta ba,
menene married?" Ya kasa kallonta with shaky voice yace "I am sorry Mami, Allah ne
ya kaddara min haka, but i never bargained for it" Mami ta janye hannunta daga
rikon da yayi mata ta mike tana kallonsa with a weird expression tace "Zazzabin ne
yasa kake wannan sumbatun Khalil? Kasan me kake cewa kuwa" Hawaye ta gani idonsa,
cike da karfin hali yace "Mami i am in my right senses, i am telling u the fact,
kuma tana can gidana yanzu haka" Mami na zare ido tace "Ita wa?" A hankali yace
"Matar, kuma sojojin sun kulle gidan, she is inside the house" Mami ta fi minti
daya tana kallonsa with shock, shi dai ya kasa hada ido da ita, burinsa kawai aje
wajen Nihad a bata kulawar da ya kamata a bata, A hankali Mami ta juya ta nufi
kofar cell din, kana ganinta kasan jikinta yayi mugun sanyi and she is speechless,
ya bi ta da kallo zuciyarsa na bugawa har ta fita......

*kuyi manage yau ruwa aka yi tayi in gaya maku a kano* 😯

*Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah*

Ur evidence via 07087865788

https://instagram.com/ruuscollections?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==
Ruuscollections turaren wuta and more we got you everything scent,long lasting
fragrance at very affordable price, change or complete refund if you don't like any
of our product in Sha Allah
Arabian,Traditional,English,Khumra ,Oil
perfumes,Koleccha,Morphingmist,Roomfreshener,
Armpit powder, Mouth freshener,Laces ,Shoes,
Bags,Atamfa, 07025393114💖 NIHAAD 💖

59
Mami na fitowa bangaren Janar Aunty Hassana ta bi ta da kallo ganin yanda take
kuka, can ta kalli Aliyu da shi ma ya bi ta da kallo yana tsaye parlon, Aunty
Hassana ta bude hannu murya kasa kasa tace "Lafiya na ganta haka?" Aliyu ya daga
kafada yace "I don't know...." Aunty Hassana tayi shiru, can ta mike ta nufi
bangaren yayan nata da sauri, A parlonsa ta samesa yana dube duben wasu takardu, ta
nemi waje ta zauna da damuwa tace "Yaya lafiya naga Aunty fatima ta fito tana
kuka?" Janar ya daga kai ya kalleta yace "Toh me ya hanaki bin ta ki tambayeta? Ko
ita ta turo ki ki tambayeni?" Aunty Hassana ta ɗan yi yaƙe tace "Haba ai bata ma
tsaya ta saurareni ba, kawai dai i was just worried ganinta da nayi cikin wannan
yanayin shi yasa na fara shigowa nan, amma bari in je in sameta" Tana fadin haka ta
mike har ta nufi kofa sai kuma ta dawo tace "Ya jikin Khalil din Yaya?" maimakon ya
amsa mata sai ya daga wayarsa dake ring wanda wani babban sojan ne ke kiransa, kofa
ta nufa ta fita daga parlon duk kanta a daure, to lafiya ta fito tana irin wannan
kukan kamar warce uwarta ta mutu, ko dai sakinta yayi? Tunanin hakan ba karamin
dadi yayi ma Aunty Hassana ba, da ace bata yaɓa mata magana bane dazu da ta shigo
parlon da sai ta bi ta bangaren nata, amma yanzu da kunya ai ta bi ta, kyaɓe baki
tayi a ranta tace "In ta yi wari ma ji dai" Daga haka ta tafi bangarenta don Aliyu
ma ya bar parlon. Mimi na zaune gefen Mami duk hankalinta a tashe ganin yanda Mamin
ke kuka, tace "Ko ma menene don Allah ki daina kukan nan Mami for the sake of ur
health" Mami dai ta kasa daina kukan da take, she still can't believe abubuwan da
Khalil ya gaya mata, ita in particular zai yi fooling haka? Ita zai yaudara haka ya
kawo yarinya for almost 2 months tana gidan sai yau ne zai bude baki yace wai
matarsa ce, ta ina hakan zai yiwu? Ai bazai taɓa yiwuwa bane tunda ba film ake
acting ba, zata nuna masa ita ta haifesa ba shi ya haifeta ba, Ta jawo wayarta for
the 4th time ta kira Aunty Maryam amma bai shiga ba, har ta tashi zata dau mayafi
zuwa gidan Hajiya Safeenah sai kuma ta tuna to idan ma taje can din kukan me zata
ce mata tana yi? Me zata ce mata ya faru? Ai bata jin zata iya sanar mata da wannan
mugun abu da Khalil ya aikata, haba wannan ai abun kunya ne, Mimi ta fashe da kuka
tace "Mami na tambayeki me ya faru kin ki gaya min, kuma sai kuka kike, don Allah
kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki koma menene" Mami ta fashe da sabon kuka tana
fatan da ma ace duk wannan abun mafarki ne..... Tun bayan fitar Mami khalil ya kasa
komawa ya kwanta, gaba daya hankalinsa yayi mugun tashi, bai ki ya ga fushin
Abbansa ba, amma baya wasa da fushin Mami, he strongly detest anything that will
make her angry, bai taɓa zaton haka zata dau al'amarin nan da zafi ba, he never
expect that from her, he was thinking Abbansa ne idan yaji zai kusan harbesa, sai
yaga Abba ma bai dau issue din personal ba, sai Mami da ya dau hope ya daura mata
yana ganin ko wani bai goyi bayansa ba ita zata goyi bayansa dari bisa dari, A
hankali ya zare drip din hannunsa ya sauka daga saman gadon duk da yanda yake jin
jikinsa ya nufi kofa ya fita, Janar ya daga kai yana kallonsa, tunda khalil ya
kallesa sau daya ya dauke kai ya nufi kofar fita daga babban parlon, Janar yace
"Hey Mr Man, koma ka kwaso drips din da magunguna da ka bar min a dakin...." Khalil
ya juya ya koma dakin ya kwaso duk kayan treatment din nasa ya fito, Janar ya bi sa
da kallo sai kuma yace "Ita yarinyar da ake magana akai tana ina?" Tsayawa khalil
yayi kamar baxai juya ba sai kuma ya juyo yace "Can gidana" Janar yace "Tana ciki
aka kulle gidan?" Khalil yayi shiru, Janar ya dau wayarsa zai kira daya daga manyan
sojojin dake tare da shi, Khalil yace "Daga gidan Mami take yanzu" Janar yace "Toh
wa ya bata izinin zuwa? Sannan wa ya kai ta har ya bude mata gidan?" Shi dai khalil
bai ce komai ba, can dai ya juya ya fita daga parlon. Hajiya Amina ce tayi sallama
cikin parlon Mami, Mimi tayi saurin tashi don kofar bedroom din a bude yake ta nufi
kofa ta fito tace "Ina yini Mama?" Hajiya Amina na kokarin kutsa kai ta shige dakin
tace "Lafiya lau ina Hajiyar?" Mami tayi kamar bacci take, hakan bai hana Hajiya
Amina karasawa cikin dakin ba, tace "Hajiya rasuwa aka min nace in zo in gaya maki"
Babu yanda Mami ta iya haka ta bude idonta ta mike zaune tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, wa ya rasu?" Hajiya Amina na kallonta tace "Makociyar kanwata Nana,
kinsan muna mutunci da matar, yau ta rasu wajen haihuwa" Mami tace "Allah sarki,
Allah ya ji kan musulmi" da mamaki Hajiya Amina tace "Lafiya na ganki haka Hajiya?"
Mami tayi yake tace "Wallahi bana jin dadi ne" Cike da damuwa Hajiya Amina tace
"Naga idanuwanki sun kumbura kamar warce tayi kuka? Kukan me kike haka" Mami tace
"Har da baccin da bana samu yanzu" Hajiya Amina tace "Ayya, Allah ya sauwake, ya
Khalil ya kara ji duk da na shiga bangaren Janar din ban gansa ba" Mami ta daga kai
da sauri tace "Baya can?" Hajiya Amina tace "Aa ya fita gaskiya kuma ai ruwan bai
ci ace ya kare ba" Mami bata kuma cewa komai ba, Hajiya Amina ta nemi waje ta
zauna, duk wani salon bugan ciki babu wanda bata yi ma Mami ba ko zata samu hint
din abinda ke faruwa a gidan amma Mami sai kaucewa take, gashi ita dai bata ga ana
hada kaya ba alamar anyi saki, ta dai gaji da zama ta mike tace "Toh Allah ya kara
lafiya Hajiya, bari in je in ci gaba da abinda nake yi" Mami tace "Toh Nagode" Daga
haka ta fita daga dakin, Mami ta dau wayarta da sauri ta shiga kiran Noor, har ya
katse Noor bata daga ba sai ga shi ta biyota, Mami ta daga tace "Khalil yaje gidan
ne???" Noor tace "Aa, amma muna hanya Mami, Sojojin ne suka ce Abba yace su maida
mu gida" Mami tayi shiru ta ma rasa abinda zata ce, can ta katse wayar kawai, ta
kara dialing number Aunty Maryam ko zata sameta amma still baya shiga, to ina ta
shiga haka??? Tun da Nihad ta ga anguwan da suka shigo jikinta ya kara yin sanyi
taji kamar ta fashe da kuka, a duniya babu inda take jin bata son ganin kanta irin
wannan gidan da za su, har cikin ranta bata son gidan, ta dinga kokarin ganin
hawayen dake taruwa idonta bai zubo ba amma ina, sai da ya zubo, ita dai Noor na
zaune ta daya end din tana ta danna wayarta, har suka iso gidan bayan an idar da
sallan magrib, Noor ta bude motar ta sauka tana kallon Nihad dake dannar kanta kar
ta fashe da kuka, A hankali Nihad ta bude motar ta sauka, Noor ta nufi entrance din
gidan Nihad na biye da ita tana tafiya a hankali tana goge idonta, har sannan zafi
take ji sosai idan tana tafiya, Noor ta jira ta har ta shigo parlon don Abba ya
sanar mata suna isowa direct su nufo bangarensa, babu kowa main parlor din, Nihad
na biye da Noor walking slowly har suka shiga bangaren Abba, Noor tayi sallama
kafin ta shiga Nihad ta ki shiga ta tsaya bakin kofar gabanta na faduwa, Noor ta
juya ta kalleta, Nihad ta sunkuya da kanta, sai kuma ta shiga cikin parlon, Sojoji
ne su hudu a tsaye parlon Janar na basu instruction, Noor ta tafi saman kujera ta
zauna don in dai ka shigo parlon Janar baya barin ka zauna a kasa, Nihad dake bin
parlon da kallo ta rakube jikin tsadadden kujeran dake parlon tana kallon katon
hoton Janar dake manne jikin bangon parlon yana sanye da kayan soja da hularsa,
daga kasa an rubuta Lieutenant General Abubakar I Jikamshi, lokaci daya sojojin
suka juya suka nufi wani kofar daban wanda ba sai sun bi ta babban parlon gidan ba
zasu fita compound, Noor ta kalli Abbanta tace "Good evening Sir" maimakon ya amsa
sai ya kalli Nihad yace "Ke ya sunanki?" Nihad sai da taji gabanta ya fadi don
muryarsa kadai ma ya isa firgita mutum, Ta hadiye abu da kyar tace "Sunana Fatima"
Yace "Yar wace gari ce?" Tace "Kano" Janar ya kalli Noor yace "Go and call me
Ibrahim immediately" Noor ta mike ta fita daga parlon, ba a dau lokaci ba sai ga ta
ta dawo bayan taje ta sanar ma Khalil Abba na kiransa, ta zauna tace "Abba yana
zuwa" Janar na nuna ma Nihad kujera yace "Have a sit" Da kyar ta girgiza kai tace
"Zan zauna a nan" A bit strict yace "Tashi ki hau kujera" Da sauri ta mike ta zauna
saman kujeran ba tare da ta shirya hakan ba.... Khalil da ya fito part dinsa yana
ganin Aunty Hassana ta daya staircase din tana saukowa ya rage pace dinsa, tun
bayan da ya fito daga bangaren Abba ya shiga dakinsa bai fito ba sai yanzu, sallan
magrib ma a dakin yayi, kuma har zuwa sannan banda shayi da Mimi ta kai masa babu
abinda ya ci, Daga sama har kasa Aunty Hassana ke kallonsa, shi ko ya ki kallon
direction dinta, can kawai ta nufi bangaren Janar ganin can din shi ma za shi,
Khalil ya tsaya ya bi ta da wani kallo yaji kamar ya juya ya koma dakinsa, bude
kofar Main parlor din aka yi, sai ga Aunty Maryam ta shigo da karamin trolly dinta,
Khalil ya zaro ido yana kallonta ko kiftawa babu, Aunty Maryam ta sauke ajiyar
zuciya ganinsa don duk tunanin ko Janar yayi masa wani abun ne da taji Mami na ta
kuka a waya, ta nufosa da sauri tace "Ina Mami??" khalil ya kasa ce mata komai don
ba karamin girgiza yayi da ganinta ba, ta karaso tana kallonsa kafin tace komai ya
wara ido, cike da karfin hali yana murmushi yace "Aunty saukan yaushe? Ko dai dama
kina kasar ne" Aunty Maryam ta galla masa harara tace "Ehh ina kasar, Mami idan
bata daga ma mutum hankali ba bata jin dadi ai, ga dai ni Allah ya kawo ni lafiya,
tana ina?? Shi kuma ya ga daman fitowa da kai daga guardroom din kenan...." Khalil
dai sai zufa yake yana kirkiran murmushin yake ya kasa ce mata komai, duk maganar
da take yi ma shi ba fahimta yake ba, Aunty Maryam tace "Ji wai ina maka magana
kana min Murmushi kamar sha sha sha, tambayarka nake ina Mami??" Ya hadiye wani abu
da ya tokaresa da kyar yace "Upstairs..." Dai dai nan Noor ta fito daga bangaren
Abba, ta zaro ido ganin Aunty Maryam ta taho da gudu ta rungumeta tace "Aunty daga
ina kike haka?" tace "Wallahi daga Uk, tun bayan da muka yi wannan wayar dake
hankalina ya kasa kwanciya kawai nayi ma Abbansu Zeenah magana ya kuma bar ni na
taho, me yasa
Mami take haka don Allah, yanzu ba ga Khalil din ba, duk ta bi ta daga min
hankali, haka kawai taje cutarta ya tashi a banza, komai baxata bi sa a sannu ba"
Noor ta amshi jakarta tana Murmushi tace "Mu tafi sama Aunty, sannu da hanya" sai
kuma ta kalli Khalil da sauri tace "Lahh Abba is waiting for you tun dazu fa
yayanmu..." Bai ce komai ba ya nufi parlon yana tafiya a hankali, Aunty Maryam ta
bi sa da kallo sannan ta kalli Noor tace "Tun yaushe ya sa aka sake sa?" Noor tace
"Tun da safe, da Abban ya dawo ya sa a fiddo shi, kinsan ba shi da lafiya so he is
under medication now" Aunty Maryam ta girgiza kai a ranta tana Allah wadai da mugun
halin janar, sai kace ba ɗan da ya haifa ba, Sama ta nufa Noor na biye da ita a
baya rike da karamin akwatin ta, dai dai kofar shiga parlon Mami suka hadu da
Mamin, Aunty Maryam taji gabanta ya fadi ganin idanuwan Mami and how weak she
looks, hankali tashe tace "Subhanallahi Mami, lafiya?? Me ya sameki haka?" Mami ta
kasa cewa komai ganin er uwartata kawai ta fashe da kuka sosai tana girgiza kai,
Aunty Maryam ta rungumeta hankalinta a mugun tashe tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un, Yaya me ya faru? Don Allah ki min magana What's happening?" Cike da karfin
hali Mami tace "Janar ya kira yana jirana a parlonsa, mu tafi can din...." Iyakar
tashi hankalin Aunty Maryam ya tashi a lokacin, ita kanta Noor jikinta yayi sanyi
sosai ta koma gefe ta dinga kallon Mami, Aunty Maryam ta kama hannun Mami ranta a
dagule tace "Mu je parlon" yau ta dau alwashin sai ta ma Janar wankin babban bargo
in har dalilinsa Mami ta shiga wannan damuwar take kuka haka, dama tara sa kawai
take, tana rike da Mami zuciyarta na bugawa tace "Mu je parlon nasa" Mami dai na
biye da ita kawai. Tun da Khalil ya shigo parlon yayi ma Aunty Hassana kallo daya
ya nemi kujera ya zauna, Aunty Hassana bata fasa maganar da take ma Janar ba tace
"Shine fa ta kirani wai bata sani ba ko ta maka wani laifin ne, kasan halin
kauyawan nan da rashin wayewa yanzu yanzu sai su juya wannan lamarin, barin suna
ganin ba uwa daya uba daya bane, to wani tsiyar suka taɓa kullala mana har Allah ya
kawo mu iyanzu? ni nasan duk a kullace suke da kai tun da muka tare nan gidan
shekara kusan shidda kenan babu wanda ya san inda muke iyaka idan zaka masu aike ka
bani in tura masu, toh su ai ba haka suka so ba, sun fi so su yi ta maka zarya wasu
in sun zo ma sai su shekara basu tafi ba ga ka shugaban kasa, Ya dikko ma ta kirani
jiya...." Janar ya dakatar da ita yace "Kee Hassana, maganar da ta kawo ki kenan??"
tayi shiru, yace "Toh bana son zancen, kowa ya dade bai yi tunanin dake ransa ba,
clear??" Sai kuma ya dauke kansa ya kalli Khalil da idonsa ke kan Nihad, ita kuwa
taki barin su hada ido ta sunkuyar da kanta gabanta na faduwa, Aunty Hassana ta
gyara zama tana kare ma Nihad kallo tana mamakin ita kuma uban me take yau a parlon
Janar, ita dama ba zancen da take ma Janar bane ya kawota, aa dalilinta na shigowa
daban amma sai ta fake da wannan zancen, dai dai nan Mami da Aunty Maryam suka
shigo parlon, Tsabar tashin hankali Khalil ji yayi dama kasa ta bude masa kawai ya
shige, ya kasa hada ido da su biyun, Aunty Maryam tayi mugun mamakin ganin Nihad
zaune parlon, can ta kalli Khalil sannan ta sake kallon Nihad din cike da mamaki,
to me ke faruwa, ba Mami tace mata ta koma gidansu ba, yaushe kuma ta dawo nan,
sannan me take yi a parlon Janar, Aunty Maryam ta kalli Janar dake kallonsu lokaci
daya ta ɗan hade rai, babu yabo babu fallasa tace "Barka da dare Janar" Yace
"Barka" Tana rike da hannun Mami suka tafi 2 seater suka zauna, Aunty Hassana sai
kallon ikon Allah take, yaushe ita kuma wannan galallawar ta dawo kasar, Can dai
tace "Sannu Maryam, yaushe a gari" a takaice Aunty Maryam tace "Daxu na sauka, ya
yaran?" Aunty Hassana tace "Lafiya lau, sannu da zuwa" Daga haka duk suka yi shiru
a parlon, Nihad dai sai kallon Aunty Maryam take, she don't know if she should be
happy or not, duk da damuwan da ya cika xuciyar Aunty Maryam haka ta mata murmushi,
Nihad ta mayar mata da murmushin amma na karfin hali, cikin sanyin murya tace
"Sannu da zuwa Aunty" Aunty Maryam tace "Sannu Nihad" Janar ya nisa, sai kuma yana
kallon Nihad ya nuna mata Khalil yace "Wanene wancan?" Khalil yaji gabansa ya wani
fadi, he wish rana irin ta yau baxai taɓa zuwa ba, amma dole ne ya zo, ya jinginar
da kansa jikin kujeran da yake zaune zuciyarsa na bugawa, gashi dai duk da wannan
tashin hankalin nasa yana jin takaici yanda za ayi magana a gaban Aunty Hassana,
Ita kuwa Aunty Hassana sai gwaggwale ido take a parlon tana son jin dai me ke
faruwa, Nihad ta kalli Khalil ta sunkuyar da kanta a hankali, ita ma har sannan
gabanta faduwa yake sosai, a ɗan tsawace Janar yace "Ke magana nake maki, or are
you deaf?" Lokaci daya hawaye ya kawo idon Nihad ta daga kai tana kallon Khalil,
duk a tsorace take, da zaka kalli yanda kirjinta ke heaving sai ka tausaya mata,
Janar ya kula da she is afraid kuma a rude take, Sai yayi calming voice dinsa yace
"Fatima ko??" Nihad ta kallesa da sauri ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta,
ya nuna mata gefensa calmly yace "Dawo nan" A hankali ta tashi ta dai daita
tafiyarta ta nufesa walking slowly, ta durkusa inda ya nuna mata, ya nuna mata
saman kujeran yace "No, nan zaki zauna" Kasa kallonsa tayi ta mike a hankali ta
zauna gefensa gabanta na faduwa kamar zai fito, Aunty Hassana dai sai kallon ikon
Allah take, yau ga sabon salo, Mami dai kanta na kasa, Aunty Maryam kuwa sai kallon
Janar take kamar ta shakesa ta huta.... Speaking Calmly Janar yace "Kinsan wancan
mutumin dake zaune Fatima?" Nihad ta kara kallon Khalil ta gyada kai, Janar yace
"To wanene?" Tana tsoron tayi shiru Janar ya mata ihu, sannan kuma ita bata gane
kan tambayar Janar ba, she is just confuse, kamar ya gane she is confuse yace "I
mean, meye tsakaninku Fatima?" Ta sake Kallon Khalil with her heart beating so
fast, shi dai idonsa na kan Ac dake tsaye parlon baya ko kiftawa, a hankali tace
"Ya zauna gidanmu" Janar na gyada kai yace "Good... What took him there?" Cikin
sanyin murya tace "He was our driver...." Ba Janar ba har Aunty Hassana da su Mami
sai da suka kalli Khalil da sauri, shi dai idonsa na kan Ac, Janar look a bit
confused ya dinga kallonsa, can yace "Kamar yaya fatima?" Ta sunkuyar da kanta tace
"Driving dinmu yake yi, Abbana na biyansa kudi" Janar yayi shiru for almost 30
seconds, can ya daga kai ya kalli Khalil, wanda shi ma Khalil din kallonsa yake
this time around, su Aunty Maryam kuwa sai kallon Khalil din suke da mamaki, Janar
ya dauke kansa ya sake kallon Nihad yace "For how long?" Nihad na jan fingers dinta
a Hankali tace "For almost a year" Janar ya sake yin shiru, sai kuma yace "A gidan
naku yake zama kuma?" Nihad ta gyada kai tana wasa da yatsunta tace "A chalet din
gidanmu yake tare da sauran masu aiki a gidanmu" Lokaci daya hawaye ya kawo idon
Aunty Maryam, Khalil ya rike kansa..... Janar dai yayi shiru kamar iyakar
tambayoyin da zai ma Nihad kenan, bayan wani ɗan lokaci ya sake kallonta yace "Did
u have an idea of nawa Abban naki ke basa?" Nihad ta kalli Khalil, a hankali ta
girgiza kai tace "Nima ban sani ba" Janar yace "Sai kuma me ya faru da har ya taho
dake garin nan?" Hawaye ya cika idon Nihad a hankali cikin sanyin murya tace
"Abbana ya min aure da shi" Sai kuma ta rufe fuskarta jikin kujera tana kuka a
hankali, Aunty Maryam tayi mutuwar zaune a inda take saboda yanda ta girgiza da
abinda Nihad tace, ta dinga kallon both Nihad and Khalil a tare, with her mouth
agape, Aunty Hassana bata san sanda ta mike tsaye tana kallonsu ba ita ma, Mami dai
sai hawaye take ta kasa dago kanta, Janar ya dafa shoulder din Nihad yace "Wani
anguwan ku ke a Kano?" Ta dago kanta hawaye caɓa caɓa a fuskarta cikin rawan murya
tace "Nasarawa GRA" Janar yace "Ya sunan Abbanki?" A hankali Nihad tace "Alhaji
Ibrahim Sadeeq" Janar yayi shiru yana gyada kai, can ya mike ya shiga bedroom dinsa
sai ga shi ya dawo rike da Makulli a hannunsa, ya ajiye ma Khalil Makullin yace
"Dauketa ku tafi can gidan naka, ku shirya gobe xa mu tafi kanon gaba daya" Khalil
ya dinga kallon Abban nasa, Janar ya ɗan masa tsawa yace "Baka ji me nace bane"
Khalil ya mike yana kallon Mami da ke ta hawaye, Ita kuwa Aunty Maryam tsabar shock
ta kasa fa rufe baki, Janar ya kalli Nihad yace "Ta shi ku tafi Fatima, Allah ya
tashe mu lafiya" A hankali Nihad ta mike har sannan hawaye na makale idonta, Khalil
ya kalli Mami da kanta ke kasa, Sai kuma ya kalli Abbansa, Wani kallo Janar yayi
masa, ya nufi kofa Nihad ta bi bayansa har suka fita daga parlon, Aunty Hassana
dake ta wurga ido, tana rawan baki tace "Yaya, ban gane ya tafi da ita gidansa ba,
kai ka yarda....." Janar ya dakatar da ita yace "Fita ki ban waje Hassana"

*Kiyi kokarin sauke nauyin 500 akan ki Aunty and Mama*


Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Via 07087865788

https://instagram.com/ruuscollections?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==
Ruuscollections turaren wuta and more we got you everything scent,long lasting
fragrance at very affordable price, change or complete refund if you don't like any
of our product in Sha Allah
Arabian,Traditional,English,Khumra ,Oil
perfumes,Koleccha,Morphingmist,Roomfreshener,
Armpit powder, Mouth freshener,Laces ,Shoes,
Bags,Atamfa, 07025393114💖 NIHAAD 💖

60

Tun da Nihad ta hango Aliyu tsaye bakin kofar Main parlor bayan sun fito bangaren
Janar ta rikice ga shi ba abun tace zata juya ba ko zata canza direction, in ma
tayi hakan ina zata? Ga khalil sai tafiyarsa yake duk da ya gansa, lokaci daya ta
fara bobboye fuskarta da hijab dinta tana sisinne kai kamar munafuka, gaba daya ta
daburce ta rikice, shi ko khalil tunda yayi ma Aliyu kallo daya ya dauke kansa
walking Majestically, Aliyu ya dinga kallon Nihad don reaction dinta ne ma ya fara
jan hankalinsa gareta, at first he didn't even care to notice who she was, amma
yanda yaga take yi ya sa ya dinga kallonta, Khalil ya kai hannu ya bude kofar
parlon, Aliyu ya cire wayar kunnensa a hankali ya mayar aljihunsa yana kallon Nihad
keenly kamar wanda ya gano abu, her eyes, her scent, the way she walks, Nihad dai
taki yarda ta kallesa kuma bata fasa rufe fuskarta da hijab ba ga wani faduwa da
gabanta ke ta yi, sai harde kafa take tsabar rudewa, tana isa dai dai kofar bata
san sanda ta daga idanuwanta suka hada ido da shi ba, ta sauke idonta da sauri tana
kokarin fita yayi hanzarin fizgota ya janye Hijab din da ta rufe fuskarta da shi,
ya wani zaro ido yana komawa baya yace "Nihad????" Ko rufe baki bai yi ba yaji an
wani tura sa yayi baya kamar zai fadi, Khalil na masa wani kallo cikin husky voice
yace "Do not ever try that again...." banda zare ido babu abinda Aliyu yake with
confusion yana bin Nihad da kallo, ita dai Nihad tuni ta fita compound a rikice har
tana neman faduwa, Aliyu ya cakumo Khalil yana masa wani kallo yace "How dare you??
A ina ka santa kake warning dina?" Wani wawan naushi Khalil ya kai masa, Aliyu yayi
saurin kaucewa yana zare ido, Aunty Hassana da ta fito daga bangaren Janar rai a
dagule ta zaro ido tana kallonsu ganin abinda ke faruwa tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, Meye haka???" da gudu ta nufesu ta shiga tsakaninsu ganin ana
kokarin kai naushi, Khalil na ganin haka ya fice daga parlon kamar zai tashi sama,
Aunty Hassana na kallon Aliyu idanuwanta kamar za su fito tace "Ina ruwanka da ɗan
wiwin nan zaka tsaya kana ɓata lokaci a kansa har ku ke neman ba hammata iska? Ina
kai ina shi? Responsible somebody like you, kai da zaka fita Germany ma gobe meye
na biye mara aikin yi wanda ake tsoron daurasa kan harkokin arziki?" Aliyu na zare
ido cikin wani yanayi yace "Mum, mum budurwata ce na gani a gidan nan, ita ce
wallahi, Nihad ce, what is she doing here?" Aunty Hassana tayi galala tana kallonsa
tace "Budurwarka kuma? A ina budurwar taka?" Aliyu na nuna mata waje yace "He just
left with her now, wa ya kawota gidan nan? Wajen wa ta zo?? Mum Nihad ce fa" Aunty
Hassana dai ta saki baki tana kallonsa, can tace "Wai yarinyar nan da ya fita tare
da yanzun nan kake magana?" Da sauri Aliyu yace "Ita Mum, ita nake nufi, wajen wa
ta zo a gidan nan??" Aunty Hassana tace "A'a, anya kanka daya kuwa Aliyu, yanzu fa
yarinyar ke cewa ya zauna a gidansu a kano...." Aliyu da kansa ya gama daurewa ya
dinga kallon Aunty Hassana babu ko kiftawa, a hankali yace "Gidansu kuma? Me yaje
yi gidansu?" Aunty Hassana tace "Wai driving, yanzun nan da bakinta take gaya ma
Janar wallahi....." Still Aliyu yayi yana kallon mum din tasa baki bude, Aunty
Hassana tace "Kaga ka fitar da ni a duhu Aliyu, kai a ina kasan yarinyar?" Yayi
karfin halin cewa "A kano na santa, budurwata ce kuma ita nake son zan aura,
wallahi budurwata ce" Aunty Hassana ta rike haɓa a hankali tace "Budurwarka? Wai fa
matarsa ce an daura masu aure, da bakinta yanzu take gaya ma Janar wai ubanta ya
daura mata aure da shi" Aliyu ya dinga kallonta babu ko kiftawa, a hankali yace
"Shi ya aureta dama??" Aunty Hassana tace "Wallahi haka nan ta ce" A hankali Aliyu
ya juya mata baya with different thought running his mind all at the same time,
Driver? Khalil ne sabon drivern gidan nasu da take gaya masa dama? girgiza kai yayi
da sauri not wanting to believe that, sai kuma ya tuna encounter dinsa da so called
sabon drivern a ranan da yaje ya sameta a Mall, Aliyu ya dinga jin zuciyarsa na
bugawa, wait!! is this really happening??? Aunty Hassana dake ta kallon ɗan nata
tace "Naji kayi shiru, ko dai kawai kaga kama ne Aliyu, amma me zai kawo budurwarka
gidan nan ana zaune lafiya, kamar dai a wasan kwaikwayo...." Lokaci daya Aliyu ya
juyo yana kallonta da karfi yace "Budurwata ce Mum, duk duniya kuma babu macen da
nake so sama da ita, ita fa nake ce maki zan aura kwanaki, ita ce fa, dalilin da na
zo nace maki na fasa auren a lokacin Video dinta with just Underwear aka yi leaking
a internet...." Aunty Hassana ta buda baki hangangan, murya kasa kasa tace "Ita ce
dama da gaske a videon??" Aliyu bai ce mata komai ba, Aunty Hassana ta gyada kai a
hankali tace "Ai ko Janar bai sani ba sun boye masa... Na gaya maka yarinyar fa
cewa tayi Khalil din ya zauna gidansu a matsayin dreba na shekara daya, ashe duk
tsawon lokacin da baya gidan yana can gidansu, sannan ta dawo tace ubanta ya aura
mata shi, da yake asirinsu ya fara ci Janar ko kallon banza bai yi ma Khalil din a
parlon ba, ita kuwa uwar sai kukan munafurci take, yanzu kana nufin ka taɓa soyayya
da yarinyar???" Aliyu na kallon Mum dinsa yayi wani murmushi, calmly yace "Idan
kuwa da gaske shi aka aura ma Nihad, to ina me tabbatar maki in dai ina numfashi
wallahi baxai yi rayuwa da ita a matsayin matarsa ba, yanda naki jininsa baxan taba
bari yayi rayuwa tare da warce nayi soyayya da ba, ko da kuwa ba aurenta xan yi ba,
he is Mad...." Yana kai wa nan yayi hanyar dakinsa kamar zai tashi sama, Aunty
Hassana dai ta bi sa da kallo, can ta gyada kai a hankali kamar me nazari, sai kuma
ta bi bayansa da sauri. Tun barinsu gidan Khalil ke driving yana kallon Nihad da ta
kauda kanta taki kallon inda yake gaba daya, wani mugun haushinsa take ji har
ranta, a tsorace tayi wani kara bayan ya kauce ma wani motar da ya kusa colliding
ma a gabansa, duk da haka kuma sai da ya gurji motar, ta juya da sauri tana
kallonsa tana zaro ido, bude motar yayi ya sauka ya nufi motar don me motar ma yayi
parking ya sauko, hakuri ya dinga ba mutumin, Allah kuma ya so me saukin kai ne, ya
koma motarsa kawai, Khalil ya koma nasa motar ya shiga, ya jinginar da kansa jikin
kujeran motar ya sauke ajiyar zuciya, Nihad dai sai kallonsa take, irin kamar wanda
baya ganin gabansa din nan don ma Allah ya takaita, ya juya a hankali ya kalleta,
sai ta wani hade rai ta dauke kai, murya can kasa yace "Will u mind driving the car
pls?" Sai kuma ta juyo ta kallesa, ya girgiza mata kai a hankali yace "Baxan iya
ba" Shiru tayi bata ce komai ba, Sai taga ya bude motar ya sauka, a hankali ta bude
side dinta ta sauko ita ma, suka yi exchanging seat, ya sa mata driving direction
din a Google map a wayarsa ya ajiye mata, sai daga baya Nihad ta fahimci dalilin
kasa tukin nasa, don kuwa har suka iso gida kallonta yake, even for a second bai
daina kallonta ba as if his life depends on that, Ita dai tayi concentrating kan
driving da take kawai, ganin bai sauka ya bude gate din ba duk da sun iso gida ta
juya ta kallesa, wani murmushi me narka zuciya ya sakar mata, ta kasa daina
kallonsa, ya kamo hannunta a hankali, sai kuma ya saketa ya sauka daga motar ya
bude gate din gidan ta shiga ciki da motar tayi parking a parking lot, Bata jirasa
ba ta nufi kofar shiga gidan da sauri, sai dai dole ta tsaya ya zo ya bude kofar,
yana budewa kuwa ta shige ciki ya bi bayanta da sauri ya rikota, bata san sanda ta
fashe masa da kuka ba, ya rungumeta jikinsa sosai, yana jin kukan nata har cikin
zuciyarsa, murya can kasa yace "I am so sorry Nihad, i am very sorry, i am sorry i
hurt you much...." Kuka take tana tuna irin azaban da yayi mata, bata ankara ba
taji ya dauketa ya wuce sama da ita, ta kankamesa saboda tsoro, bai direta ko ina
ba sai saman makeken gadonsa dake master Bedroom ya hau aikin lallashin da bai samu
yayi mata all through that day ba, da ya ga ta hakura da kukan ya shiga bandaki ya
hada mata ruwa a bathtub dinsa, ya dawo ya dauketa zuwa bandakin, he did everything
for her, ita dai ta kasa hada ido da shi..... Daren ranan Khalil bai wani rintsa ba
all his thought was with Mami, kukan da yaga tana yi ya tsaya masa a rai, tun kafin
su kwanta ya so kiranta amma bai ma san me zai ce mata ba, infact ba ma shi da
courage din kiran nata, kawai ya hakura da kiran, all through the night Nihad na
jikinsa bai saketa ba, and she slept soundly. Karfe takwas na safe Khalil ya kira
Ya farooq bayan kiran da Janar yayi masa na cewa su shirya shi da Nihad before 9:30
za a zo a daukesu, wayar na fara ringing Farooq ya daga, bayan sun gaisa farooq ya
tambayesa ya Nihad, Khalil yace "She is fine Alhmdlh, ya Kaduna?" Farooq yace "Ina
kano ai" Khalil ya fara tunanin ta ina ma zai fara sanar masa, can dai yace "Erm...
dama Dad dina ne za su je kano wajen Abba yau su gaisa, so i don't know how it's
going to be...." Farooq yace "Ohk, ba damuwa zan sanar masa in sha Allah, Allah ya
kawo su lafiya" A hankali Khalil yace "Ameen" Don har ya fara jin kunyan Abban
Nihad da Mum dinta, Farooq yace "Kamar karfe nawa kenan?" Khalil yace "Zuwa sha
daya in sha Allah" Farooq yace "Allah ya kai mu" Daga haka suka yi sallama Khalil
ya ajiye wayarsa ya jinginar da kansa da kujera, yau kam bai ma san da idon da zai
kalli Abban Nihad ba, he wish Abbansa zai yarda yaje gidan without convoy, but that
will never be possible, can kuma ya ji dama Abban ya bar sa shi kadai yaje gidan ba
sai anje da shi da Nihad din ba, ya sauke wani ajiyar xuciya ya mike daga karshe ya
nufi sama ya shiga dakinsa, har sannan Nihad bacci take, kana kallonta kasan it's a
peaceful one, ya zauna gefen gadon a hankali yana kallonta ko kiftawa babu, abubuwa
da yawa ne suka hau dawo masa tun farkon da ya fara zuwa gidansu, and he couldn't
help it but smile and he wish she will go back to her former Nihad me tsiwa, wauta,
fada, masifa, amma banda walakanta d'an Adam da bin kawayen banza. Aunty Maryam na
zaune gefen gado a dakin Mami ta jingina jikin gadon tayi
shiru bata cewa komai, can ta sauke ajiyar zuciya a hankali tace "Aa Mami kar ki
ce baza ki ba tunda har Janar din da kansa yace ki shirya...." Mami ta dakatar da
ita a fusace tace "Akwai wanda zai tilasta ni in je ne idan nace baxan je ba? To
nace baxan je ba, kuma baxan je din ba" Aunty Maryam ta girgiza kai tace "Ni health
dinki nake jiye maki Mami, don Allah ki kwantar da hankalinki abi komai a sannu,
tun jiya nake gaya maki haka amma kin ki fahimtata" Mami ta kalleta tace "Wallahi
ban ga amfanin zuwanki ba Maryam, na zata da kika zo za ki tayani a san ta inda za
a billo ma lamarin nan, amma sai dai ki zauna ki kura ma mutane idanu baki cewa
komai...." Aunty Maryam ta sauke wani ajiyar zuciyar tace "Ni so nake abi komai ne
a sannu Mami, ni kaina i am shock, i am really shock don yarinyar bata taɓa ce min
ae da aure tsakaninsu ba kuma ta bude min cikinta sosai during her stay a gidana,
amma dae na fi tunanin shi ne ya hanata fadi ita kuma babu yanda zata yi, ni sai
nake ganin tunda auren yayi ba shashanci ba ae da sauki da dai ace neman mata yake
Mami..." Mami ta dinga kallonta ta ma rasa abinda zata ce mata don takaici, Aunty
Maryam tace "That is just it Mami, wannan ne ma yasa na sa ma kaina nutsuwa ban
daga hankali ba, duk da lamarin akwai shock, but one have to try and reason, though
i am not in support of what khalil did da har zai yi aure babu knowledge dinku,
amma ai sai abi komai a sannu" Mami bata tanka ta ba ta dalilin wayarta dake ring,
ta dau wayar nata, ganin Hajiya Safeenah ce ta dinga kallon screen din wayar, can
dai ta daga ta sa handsfree kawai, nan suka gaisa faram faram, Mami tace "Kina ta
kirana jiya da daddare ban samu dagawa ba Hajiya, wallahi maganin bacci na sha,
bana ɗan jin dadi" Hajiya Safeenah tace "Subhanallah, ya jikin yanzu?" Mami tace
"Aa Alhamdulillah naji dama dama" Hajiya Safeenah tace "Toh zuwa karfe sha daya zan
shigo in sha Allah" Mami ta ɗan yi shiru sai kuma da sauri tace "Koh??? kuma gashi
za mu je kano tare da Janar amma yau din za mu dawo" Hajiya Safeenah tace "Ahh to
shikenan, sae dai kun dawo kenan, ita Nadeeyan sae ta tafi ita kadai kawai, dama
tace min zata gun Noor anjima maganar anko" Mami tace "Allah sarki, to in sha
Allahu muna dawowa zan kira ki" Nan dai suka yi sallama Mami ta ajiye wayar a
hankali, lokaci daya jikinta yayi sanyi, Aunty Maryam dake ta kallon Mami tace "Kin
ga gwara da kika ce mata haka kar ta zo ta ganki a wannan yanayin da kike ciki"
Mami dae bata ce komai ba, Aunty Maryam tace "Ga kuma Nadeeyah tace zata zo wajen
Noor, kar kuma ta zo ta ga kina nan, ba gwara kawai ki shirya a tafi kanon ba, na
tabbatar idan kika je kanon zaki fi samun nutsuwa da kwanciyar hankali, sai kuma a
san next step da za a dauka" Aunty Maryam na fadin haka ta mike ta shiga
bandaki.... Farooq yayi sallama kofar parlon Abba ya shiga ciki, ya zauna kasa ba
tare da yayi interrupting din Inna dake ma Abba magana ba, Umma ma na zaune parlon
ta rafka uban tagumi sai kallon innar take, Inna na kallon Abba a ɗan fusace tace
"Ya kake kallona haka Ibrahim, ni fa ba kai nace ka dauko masa yan sandan ba, to wa
ma zai sa ka ka lalata mana al'amarin, ni da kaina zanje gidan yan sandan in gana
da ogansu daga nan ya sa a cika min mota daya da kurtaye mu je har gidan nasa su
nakada masa shegen duka shi ma, kafin mu tafi da shi.... Ai ni da kaina zanje ko
ɗan rakiya bana so, don ma dai kaf zuri'a bamu da soja ai da shi zan aika ya ci min
ubansa kafin a kai sa gidan yan sanda" Farooq dai sai kallon Inna yake, Inna tace
"Sai kace er banza ya samu ya doka da za a yi shiru a kyalesa, to ni ba gantalaliya
bace, wallahi sai an bi ma jikata hakkinta" Farooq yace "Duk wannan abun fa
bangarenta kawai aka ji ba aji nasa bangaren ba Inna, ku daina saurin zartar da
hukunci daga jin bangaren mutum daya" Inna ta wani jefa masa shegen kallo tace
"Allah ya tsine masa shi da bangaren nasa, ya nakada mata shegen duka ya hadata da
saki daya kace mu jira mu ji bangarensa?? Anya farooq? to wai ko dai kai ka sa shi
yayi mata wannan abun ne bamu da labari farooq??" Shi dai Abba bai ce komai ba a
parlon, Umma ma ta kasa cewa komai abun duniya ya isheta, Inna tace "Toh kuwa bai
doki Kamila a banza ba sai inda karfina ya kare a wannan kes din wallahi, ga duka
ga saki??" Farooq ya dauke kai yana kallon Abba yace "Abba dama Khalil ne ya kirani
yanzu wai mahaifinsa zai zo gaisheka yau, zuwa karfe sha daya" Inna tace "Waye kuma
Khalil?" Umma ta daga kai daga tagumin da tayi tana kallon Farooq, Farooq na kallon
Inna yace "Mijin Nihad" Sake baki Inna tayi kamar warce ta ji mugun abu, can tace
"Lallai duniya ta tara marasu lissafi, yanzu su yan kauyen zai zauna jira baxai
fita aikinsa ba? Yau ga dai fitina kiri kiri" Abba na kallon Farooq yace "Allah ya
kawo su lafiya" Mikewa Farooq yayi ya fita daga parlon, Inna ta kalli Abba tace
"Kai kuma zaunawa zaka yi ka jira kauyawan?" Shi dai Abba bai ce mata komai ba,
Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "Yanxu inna ya kika ce za ayi?" Inna tace "Kamilar
ta zura Hijabi muje har gidan yan sandan su ga abinda matsiyacin yayi mata, daga
nan su bani mota daya muje su ci ubansa, sannan mu tafi kotu..." Umma tace "Toh ai
bata iya ko tashi Inna" Inna tace "Sai a min hotonta in kai masu su gani"

Wani soja ne ya bude ma Nihad kofar motar dake parke kofar gida, ta juya ta kalli
Khalil dake kulle gidan, yayi mata alamar da ta shiga, a hankali ta shiga cikin
lafiyayyen motar, Khalil ya karaso ya shiga motar shi ma, suka bar anguwan, direct
airport motar ya nufa da su, kusan kuma a tare suka isa airport din da Convoy din
Janar, Nihad dai sai kallon ikon Allah take, Lounge na manyan kasar aka yi
Conveying dinsu kafin tashin jirgi.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788💖 NIHAAD 💖

61

Farooq na fitowa parlon Abba ya tafi bangaren Mumy, Mumy ta fito daga dakinta jin
sallamarsa yace "Bacci kike ne?" Tace "Aa ba bacci nake ba farooq, ya gajiyan
hanya, jiya sai baka shigo ba har nayi bacci" Yace "Wallahi na gaji ne, i had
issues with my car" Mumy tace "Haka kace, Allah Ubangiji ya tsare" Yace "Ameen"
Mumy tace "Ka samu mijin Kamilar a waya?" Farooq yace "Eh na samesa amma bai daga
ba kuma bai biyoni ba" Mumy ta ɗan yi shiru, can tace "Toh Allah ya kyauta, amma da
ka je gida ka samesa ko?" Ya girgiza kai yace "Aa bazan je ba, duk yawancin abinda
take masa dama ai ni yake kira, kuma sai dai in basa hakuri, so this time around
ban san me tayi masa ba, tunda gashi har ya ga kirana bai biyo ni ba" Mumy tace
"Kai abun ba dadi wallahi, Allah Ubangiji ya daidaita su" Farooq yace "Mumy dama
Khalil ne ya kirani yace yau Mahaifinsa zai zo su gaisa da Abba...." Mumy tace "Yau
din nan?" Farooq yace "Ehh, shine na shigo in gaya maki ko za ayi masu ko da snacks
ne, tunda lokaci ya kure balle ace za ayi girki, yace min zuwa 11 za su zo and this
is past 9" Mumy tace "Toh shikenan, dama Jamila na garin amma yau tace min zata
koma, bari in kirata ko zata bari da yamma" Farooq yace "Ohk to, sai a karo drinks
da ruwa" Mumy tace "Toh shkkn" Yace "Zan siyo drinks din da ruwa" Daga haka ya fita
daga parlon Mumy ta dau wayarta ta shiga kiran Aunty Jamila, babu ɓata lokaci kuwa
Aunty Jamila ta iso gidan suka shiga kitchen da Mumy, Hafsah na taya su, Umma ta
fito ɓangarenta jin yanda kamshin soye soye ya cika gidan ta tsaya kofar kitchen
tana kallon Mumy tace "Wai!! Sannunku da aiki, toh dai Allah ya sa su iya ci, yan
kauye suka san wani Samosa da spring rolls banda abun ki Maryam, dama dai tuwo
miyar kuka kika masu da wannan wahalan ai" Ko kallonta Aunty Jamila bata yi ba tana
ci gaba da aikin da take, Mumy tace "Toh gashi nan dai muna yi, ya jikin Kamila?"
Umma tace "Da sauki...." Daga haka ta juya ta bar kitchen din, sai a sannan ta tabe
baki ta koma bangarenta. Nihad ta kasa hada ido da Aunty Maryam da Mami dake zaune
Lounge din, sai Aunty Hassana da bata yi shawara da kowa ba ta dau gyalenta ta
shige daya daga motocin Convoy, kuma daga Mami har Aunty Maryam babu wanda yace
mata komai, Ita kuwa Hajiya Amina dama sai yanda Aunty Hassana tace mata to bata ce
mata ta taho ba balle ta biyosu, Wani waje sak parlor Nihad ta hango Janar zaune da
wani mutumi sanye da kayan soja suna magana, Nihad bata iya ta dago kanta ba, ta
gaishe da su Mami a hankali, Mami ta amsa ba tare da ta kalleta ba, Aunty Maryam
dae sae kallonta take bayan ta amsa gaisuwan, can ta nuna mata kujeran dake side
dinta ganin gefe ta koma ta tsaya, a hankali Nihad ta karasa ta zauna kan kujeran,
Aunty Hassana ta dinga kallon Nihad tana nazarin abinda Aliyu ya gaya mata, Khalil
dama kin shiga Lounge din yayi, ya zauna a Departure Lounge din kowa da kowa...
first class passengers suka fara boarding din plane din, wanda iyaka ahalin Janar
ne a first class din, sai da Aunty Maryam ta nuna ma Nihad inda zata zauna cikin
jirgin sannan ta zauna, kamar yanda Khalil ke ta avoiding eye contact da Mami ita
ma haka ta dinga avoiding, wani kunyarta take ji, Khalil ne karshen shigowa ya
zauna, Aunty Maryam ta taɓe baki ganin yanda yake wani sinne kai, ita kam ta gama
tsorata da lamarinsa bata jin zata sake yarda da ko wani maganarsa, duk yanda take
da shi amma ya boye mata wannan lamarin..... Karfe sha daya da kusan rabi jirgin ya
sauka a Aminu Kano international airport, sai da suka fara sauka daga jirgin before
the rest class, Nihad ta dinga kallon jerin motocin dake jiransu har da na sojoji
da suka yi bake bake a airport din, tuni wani soja ya bude ma Janar da babban sojan
dake tare da shi motar da za su shiga, Khalil dai sai nesa nesa yake da su kamar
baya son a san tare suke, kai kace karere ne shi a wajen, Aunty Hassana kuwa sai
daga kafada ake ana taku dai dai uwa ita ce matar Janar din, Nihad ta daga kai a
karo na farko ta kalli Khalil tun barin su Abuja, taga ko kusa kusa da family din
nasa bai son matsowa, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, wasu abubuwan da tayi
masa a baya ne suka hau dawo mata vividly, irin humiliating dinsa da tayi a
gidansu, and even for once bai taɓa attempting nuna mata ya fi ta komai na rayuwa
ba, yawanci duk abinda take masa sai dai yayi kamar bai san tana yi ba, bata san
sanda hawaye ya kawo idonta, and because of him today she is among this elite,
standing in the midst of them, kamar ya san kallonsa take shi ma ya kalli direction
din da take, suna hada ido tayi saurin kauda kanta, Aunty Maryam ta bude daya daga
motocin dake jere tana kallon Nihad tace "Shiga" Nihad ta shiga mota sannan ita ma
ta shiga, Mami ta shiga wani motar daban, Aunty Hassana ta shiga motar da Mami ta
shiga don me shegen tsada ne, nan suka bar airport din, Khalil da zai yi directing
dinsu zuwa gidan ya hau motar dake gaba, tafiyar kusan minti talatin suka yi suka
iso Nasarawa GRA.... Nihad na ganin sun shigo layinsu gabanta ya dinga faduwa, Tuni
Aminu ya taso da sauri yana leko gate jin jiniya kamar tashin duniya, ganin jerin
motocin sannan ga na sojoji a gaba ya gwale ido yana jiran yaga sun yi gaba sannan
ya ga gidan wa za su amma sai ya ga sun jeru dai dai kofar gidan, kan kace me
sojojin sun sauka sun zagaye layin, a hankali Aminu ya tura gate din ya rufe ya
saka lock yana zaro ido, to meye kuma suka tsaya masu a kofar gida, ko dai ɓatan
hanya suka yi, A mugun tsorace Aminu ya kalli gate din jin ana bubbugawa, haba kan
kace me sai ga Aminu har cikin parlon gidan ba tare da yasan ya iso ba, Inna da
dawowarta kenan daga police station tana bada labarin yanda aka je har gidan Kamila
ba a tadda tsinannen mijin ba, ta saki baki tana kallon Aminu tace "Me zan gani
haka? waye wannan kuma??" Jiki na rawa Aminu yace "Hajiya wallahi sojoji ne sun fi
hamsin a kofar gidan nan, yanzu haka su ke bubbuga gate din, ban san wa suke nema
ba" Farooq ya mike yana kallon Aminu, Inna tace "Sojoji? Meye su din?" Umma dake
zaune parlon ita ma tana kallon Aminu tace "Sojoji fa kace Aminu" Zufa na keto ma
Aminu yace "Wallahi su Hajiya, da manyan bindigu na gansu sun sauka kofar gidan
nan" Inna tace "Aa to ko dai bariki za su suka yi ɓatan hanya suka shigo ma mutane
anguwa, da ba sai ka leka kace masu ba hanya ba" Abba ya fito daga parlonsa jin
bubbuga gate din da ake ta yi ba kakkautawa, shi dai Farooq na ta tsaye yana kallon
Aminu ya kuma kasa fita waje, ganin Aminu a parlon Abba yace "Lafiya" Aminu ya
durkusa ya makale jikin kujera yace "Wallahi Alhaji sojoji ne sun kusa dari ban san
wa suke nema ba, ni dai shine na kulle gate din na taho, ga su can suna ta buga
gate din" Ai ko rufe baki bai yi ba Farooq ya nufi kofa da sauri, a tsorace Inna ta
mike tace "Ina za ka farooq??" Umma ma ta daka masa tsawa amma tuni ya fice daga
parlon, da gudu Inna ta bi sa tana kiransa a gigice, yana tafiya ya fiddo wayarsa
dake ring a aljihu yaga Khalil ne ke kiransa, dagawa yayi khalil ya sanar masa suna
waje, Farooq ya karasa bakin gate din ya bude, Khalil ne tsaye bakin gate din sai
sojojin dake kewaye wajen ko wanne da bindiga a hannu, sai a sannan Janar ya sauko
motar tare da abokinsa, Inna ta gwale ido uwa munafuka ganin Khalil ga sojoji sun
zagayesa, sai kuma ta fashe da kuka ta saki salati tace "Dama sai da na fada, sai
da nace ɗan kinnafa ne su Ibrahim suka gwaleni suka maida ni wawa....." Sai kuma ta
kalli Janar da sojojin dake wajen suna kallonta tace "wallahi ranka shi dade bamu
taɓa saninsa ba, ce maku yayi ya san mu? Ɗan Nijar ne fa" Sai kuma ta juya da gudu
taje ta gaya ma Abba ya buya, gaba daya ta rikice ta gigice, Farooq sai kallon
Janar yake wondering if Lieutenant General Abubakar I Jikamshin da ya sani ne
wannan yake gani a gabansa or just kamanni ne, shi dai Janar was patiently
standing, su Mami kuma basu kai ga sauka daga motar ba, Khalil yayi kasa da murya
yana kallon Farooq bayan ya shiga compound din da sauri yace "He is my Father"
Muryan sojan dake tare da Janar suka ji yace "Is this how u treat ur guess?" Yana
kallon Farooq yayi maganar babu yaɓo babu fallasa, Da sauri Farooq ya gaishesu a
daburce yana welcoming dinsu ya bude gate din sosai ya basu hanya, nan su Mami da
Aunty Maryam suka sauko daga motar, Khalil dai kansa na kasa, walking fast ya fara
leading din Janar da abokin nasa zuwa entrance din main parlor ganin kamar Farooq
ya rikice and at anytime Janar zai iya exploding ya masu kwarkwar gaba dayansu a
wajen barin yanda aka barshi a tsaye, Nihad taji kamar taje ta rungume yayan nata,
she is so happy seeing him, A balcony Khalil ya hadu da Abban Nihad, a bit confuse
Abba ya dinga kallon Janar dake tahowa like the soldier he is, Abba ya kalli Khalil
sae kuma ya sake kallon Janar with his friend, kamar Janar Jikamshi yake gani a
gabansa, ko idonsa ne ke masa gizo, lokaci daya sojojin da suka biyo bayan Janar da
abokinsa suka nemi each and every angle of the compound suka tsaya, hakan dai bai
sa Abba ya fasa ba Janar hannu ba yana masa sannu da zuwa, sannan ya ba daya sojan
ma hannu kafin yayi leading dinsu har cikin Main parlor, Saminu da Isiya sai
wuwwurga idanuwa suke daga Chalet suna jiran suga an fara kwashe kowa na gidan har
su, har sannan kuma Aminu na makale a inda ya durkusa a parlon tun dazu, Hajiya
Inna kuma na can kuryan dakin Mumy bata ma san sanda ta isa nan ba tsabar gigicewa
sai salallami take tana cewa ya cucemu ya cucemu, dama sai da nace masu ban yarda
da shi ba hankalina bai kwanta da shi ba aka maida ni wawa.... Khalil ya daga kai
ya kalli Umma da ta koma bayan kujera ita ma sai zare ido take a tsorace, Mumy na
tsaye kofar kitchen da Aunty Jamila, ko wanne zaka ga Fargaba karara kwance a
fuskarsa, sunkuyar da kansa yayi kawai, Bayan Janar da abokinsa sun zauna ya nuna
ma Abba ganin bai zauna ba yace "Bismillah Alhaji" Abba ya kirkiri murmushi ya
zauna yace "Barkan ku da zuwa, amma sai dai ban san me ke tafe da ku ba, ina kuma
fatan Allah ya sa
lafiya" Nihad ce ta shigo parlon su Aunty Maryam na biye da ita, duk suka zauna a
parlon, Mumy da Aunty Jamila suka dinga bin su da kallo, lokaci daya gaban Mumy ya
fadi, what's happening??? Umma dai kamar idanuwanta za su fito tsabar yanda take
gwalesu tana bin sabbin occupant din parlon da kallo, Farooq ne kawai ke ta masu
sannu da zuwa a parlon da fara'arsa, ya tafi ya dinga jido pack din ruwa da lemo,
Nihad ta kasa ci gaba da zama kawai ta tafi da sauri ta rungume Mumy cike da farin
cikin ganinta duk da basu wani dade da ganin juna ba, but she is having a new
strong love for her mum now, Mumy ta hadiye wani abu da kyar, murya can kasa kasa
tace "Su waye wa ennan Nihad? Why are they here??" Yanda zaka san kowa a tsorace
yake ko gaida su Mami da Aunty Maryam babu wanda yayi a parlon ana dai jiran aji
abinda ke tafe da su, most especially Abba da hankalinsa ya tashi sosai, kawai dai
bai nuna bane a fuska, Muryar Janar dake kallon Abba suka ji yace "Babu wani abu
dake tafe da mu sae alkhairi Alhaji, kuma muna me ba kai da iyalanka hakurin yanda
muka shigo maku gida kai tsaye, may be without any notice.... and most important of
all, i hope kai ne Alhaji Ibrahim??" Abba ya gyada kai yace "Kwarai ni ne" Janar
yace "Sunana Abubakar Ibrahim Jikamshi...." A hankali Abba yace "Lieutenant...
General.... Abubakar Jikamshi" Janar yace "Haka ne" Umma ta dafa kujeran kusa da
ita tana sake kallon Janar da kyau kamar idanuwanta za su fito, kwarai kuwa sai
yanzu ta ganesa, Ita kanta Mumy da Aunty Jamila kallonsa suke babu ko kiftawa with
shock, Janar ya nuna ma Abba Khalil yace "Few abinda ka sani game da wancan mutumin
nake son kayi briefing dina Alhaji..." Sosai gaban Abba ya fadi, ya daga kai yana
kallon Khalil da ya sunkuyar da kansa kamar mara gaskiya, lokaci daya har hawaye ya
kawo idon Mumy..mm Kasa cewa komai Abba yayi, Janar yace "Muna sauraronka Alhaji" a
hankali Abba yace "Toh, ya dai zo gidan nan yau shekara daya da yan watanni, ya
nemi aikin driving na kuma basa, yana kai min yarana makaranta, sannan duk wani
aike na cikin gida ana aikensa" Cike da karfin hali Abba ke maganan, only Farooq is
looking so calm a parlon, Janar ya gyada kai cikin gamsuwa yace "Shikenan?" Abba ya
girgiza kai yace "Na kuma basa auren 'ya ta, bayan da naga shi me gaskiya da rikon
amana ne, sannan na yaɓa da hankalinsa da nutsuwarsa...." Janar ya dinga gyada kai,
Shi dai Abba kallonsa kawai yake, Janar yace "Amma kai ta yaya kasan yana da
gaskiya da rikon amana?" Abba yace "Ehh to, na sha gwadasa ta fanni daban daban
akan abubuwa da yawa da suka shafi kudi, and i never find him guilty of any, a
yanda ma yayi min maintaining motar da na basa ban taɓa driver da yayi min haka
ba...." Janar yace "Nawa ne Albashin da kake basa?" Abba yace "Na kan basa dubu
hamsin ko dubu sittin duk wata...." Janar yayi shiru sai kuma yace "Amma kai baka
bukaci sanin iyayensa ba kafin ka basa auren yar ka?" Abba yace "Har wajen iyayen
nasa naje a kauyen getso, kuma da yardansu na aura masa 'ya ta ba kai tsaye aka yi
hakan ba ranka shi dade" A tare Janar da su Mami suka daga kai suna kallon Khalil
with surprise, shi ko ya ki dago kansa, Janar dai ya kasa daina kallon sa, wato har
feigning iyaye yayi a kauye, Janar ya kalli remote dake gefen kujeran da yake
zaune, dauka yayi lokaci daya ya harbi Khalil da shi, duk yanda Khalil ya so
dodging remote din sai da ya taɓa sa, ni ko nace ya mance ba Major bane ya harbesa
da yake kokarin dodging, Nihad ta rufe bakinta da sauri don wani dariya ne ya kusa
taho mata, Khalil ya sosa kansa with a smile on his face, wai fa duk wannan abun da
ake Inna na makale jikin kofa ta kasa fitowa, banda hawaye babu abinda take, ta
tsine ma Khalil yafi sau hamsin, su Saminu da Isiya na tsaye bakin window ta waje
suna jiyo komai, Aminu dai har ya gaji da gwale ido kamar wanda yayi ma sarki
karya, Janar na kallon Abba bayan shirun few seconds da yayi yace "To ɗa na ne
Ibrahim, ni na haifesa.... Ba komai kuma ya sa na xo nan ba sae don in tabbatar da
gaskiyan lamarin auren nasa, ina kuma farin cikin hada zuri'a da kai Alhaji
Ibrahim, na kuma ji dadin yanda ka yarda da shi har ka basa auren er ka, and I will
forever be grateful for that" Ba Abba ba kowa na parlon sae da yayi stiff a inda
yake for some seconds, da wani expression Abba yace "Ɗan ka kuma??" Janar yace "Ɗa
na ne, and he is my only son" Aunty Hassana da ke ta girgiza kafa a parlon ta kalli
Janar da sauri jin da tayi yace his only son, Abba ya daga kai yana kallon Khalil
babu ko kiftawa, Aunty Jamila tayi saurin riko Mumy wanda ta ji wani jiri tayi baya
kamar zata fadi, Aunty Maryam dai sai kallom Mumy take cike da tausayinta don taga
kamanninsu da Nihad, Khalil bai iya ya dago kansa ba ya karaso har cikin parlon ya
durkusa gaban Abba cikin sanyin murya yace "I am sorry i wasn't truthful to you
sir, i had no choice but to hide my identity.... Ina kuma neman yafiyarka, i never
took u for a fool, bani da option ne...." Inna da ta kusa minti daya baki a bude ta
fito parlon da sauri bayan ta goge hawayenta tana kallon Janar tace "Wai ɗan da ka
haifa a cikin ka ko kuma yaron aikin gidanka kake nufi?" Janar na kallonta yayi
murmushi ya nuna mata Mami yace "Ga Mahaifiyarsa can, ita ce uwargida na" Mumy da
Aunty Jamila suka daga kai da sauri suka kalli Mami, hawaye masu zafi ne suka hau
sauka idanuwan Mumy ta jingina jikin kanwarta saboda yanda taji tsayuwar na neman
gagararta, ganin abubuwan take kamar a mafarki, Umma ta dinga bin kowa na parlon da
kallo babu ko kiftawa tana ta wani irin murmushi kamar warce tayi recovering daga
hauka, Inna ta rike kai tace "Habaa waaa, to kalleni nan" Janar dai sai kallonta
yake, ta nuna masa Abba tace "Ni na haifi Ibrahim, kuma tsakanina da Allah tun da
yaron nan Halilu ya xo gidan nan na gaya masu ba banza yake ba, wallahi tun ranan
da na fara ganinsa hankalina ya kwanta na amince da shi, yaushe ake samun mutum da
nutsuwa da ladabi da sanin ya kamata haka a zamanin nan, uwa uba ga kyauta, wallahi
apple ya siyo min ranan ya fi na dubu biyar daga cewa yaje yaji nawa nawa ake
siyarwa, Allah ne ya kaddara zaman sa a gidan nan amma ni ce sanadi, kuma ni na
bada goyon baya aka aura masa jikata ka tambayi kowa, amma dai kai ko wani lalacewa
ya sameka kamar me bakin uwa kana babban soja a kasa zaka bar ɗan ka a gantale?
Yanzu da bai shigo hannunmu ba fa? Ayi magana ta tsakani da Allah fa" Juyawa duk
suka yi da sauri jin an fadi timm a kasa, Mumy da Aunty Jamila da Farooq suka
karasa gun Umma da sauri, Abba ya mike, Mami ta nufi wajen tace "Subhanallah, is
she okay" Aunty Maryam dai ko motsawa bata yi ba don tuntuni take lura da yanayin
da Umma ta shiga a parlon, kuma a kan idonta ta tafi luuu sannan ta fadi timm, tuni
jini ya fara bulbulowa daga goshin Umma tsabar yanda ta buge da tiles, Farooq da
Khalil suka yi waje da ita bayan Janar yayi instructing sojan dake bakin kofa a
tafi da ita hospital with the convoy....

Waje aka yi da Umma za a saka ta a mota zuwa asibiti don jini ba na wasa bane ke
zuba a goshinta kamar an bude pampo, Inna tayi gate da gudu tana ce ma sojojin dake
bakin gate din su bude su bude, Kasake inna tayi ta bude baki ganin layin ba
matsaka tsinke da jama'a, ke kya ce rabon daloli ake, Inna ta toshe hancinta da
sauri don tear gas kawai sojojin ke sakar masu ba kakkautawa amma sun ki gudu, ashe
duk yan Khaleesat palace ne da suko taho ayi komai a gabansu, shine sojoji suka
hanasu shigowa gidan Abba, can na hango Mrs Bello ta ci damara, Mom twins da Aunty
Zahrah rike da katon Banner an rubuta masu gudu su gudu, Daga daya bangaren kuma
Chamo na hango tayi bake bake a gaba tana tura masu son mata overtaking ga Fu'ad
goye a bayanta duk ta hada zufa, Deejah me lamurje kuwa sai bi take tana rabon
lamurje a gora, ashe abinda yasa basa jin zafin tear gas din kenan, A kusa da Chamo
na hango Aunty Inna sanye da hulan lauyoyi tana cewa sai tayi sue din sojojin idan
basu bari sun shiga gidan ba, they have no right, turanci dai har da wanda ban taba
ji ba a bakin inna in gaya maku, Sai kuma na hango Mardiyya rike da microphone
cikin daga murya take cewa ita ewr jarida ce, ita fa ewr jarida ce, don haka tana
da right din shiga ta dau wrahotu, they have no wright to stop her, Safiyya Usuman
da Aunty Amzaj kuwa babu abinda suka mance basu gaya ma sojojin ba na cin mutunci
ga hawayen tear gas sai zuba yake a idonsu, Damsel, Aisha Bela, da Aneesah da Mom
Asas, kuwa na rike da speaker da ya cika anguwar da wakar rarara ta masu gudu su
gudu, daga can bayan yan Khaleesat palace na hango yan Nihad conversation su ma
suna ta nasu taɓarar su, a bayansu kuma ashe yan bati ne ko wacce da banner dinta a
hannu, duk suka tare layi babu ta inda za a fitar da Umma dake ta zuban jini xuwa
asibiti, ji kake tas tas tas tas tas a sama, kamar kiftawar ido layin ya dawo ba
kowa sai gorunan Lamurje, warin takalmin jama'a da zanin goyon chamo a kasa, sai
hular lauyoyin inna, sai banners din yan bati, sai a sannan aka samu aka yi asibiti
da Umma....
🥸🥸

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788💖 NIHAAD 💖

62

Ana fita da Umma zuwa asibiti Inna ta dawo parlor, tana kallon Aminu dake zaune
jikin kujera sai cilla ido yake, cike da mamaki tace "Kai baka da hankali ne kake
zaune tsamo tsamo cikin manyan mutane kana kallon bakinsu, tarbiyarka kenan? aa to
baka da tsoron Allah" Aminu ya mike da sauri ya fita daga parlon, Inna ta bi sa da
wani kallo, can ta karasa gun Janar tace "Mu ma kawai ba mu suman bane saboda
taurin zuciya amma gaskiya mun girgiza da wannan lamari, kishiyar uwarta ce fa amma
tafi uwar sonta, ita ta raineta tun tana karama har kawo girmanta, yanda take sonta
ma ko ya yan da ta haifa a cikinta bata so, kaga kuwa dole ta girgiza saboda farin
ciki har ta suma" Janar yace "Ikon Allah... To Allah ya bata lafiya" Nihad dake ta
kallon Inna ta mike ta bar parlon, Inna tace "Ameen ameen, to alfarma ta farko da
nake nema a wajenka a matsayinka na ɗa na shine a hadani da sojoji ko da basu kai
ashirin ba, wani tantiri aka aura ma jikata sai kaga yanda ya bi ya canza mata
halitta da duka, don da a hanya na ganta bazan fahimci jikata bace...." Abba dai ya
kasa dago kansa saboda takaici, a ransa kuwa yaji dama bata zo gidan ba baƙin suka
zo, ita kanta Mumy kanta a kasa yake, Aunty Hassana ta dinga ma Inna wani kallon
rainin wayo, can tace "Toh Hajiya banda abunki mu ga abinda ya kawo mu daban sai
kuma ki shigo da wani al'amari...." Inna ta juya tana kallonta da sauri tace "Amma
dai daga jin wannan zancen naki ba lallai kina da alaka da Janar ba, to ke kuma a
wa? Ina ce yace mana ga matarsa can wato uwar Halilu wancan kuma dake zaune kusa da
ita ko makaho ya shafa yasan kanwar matarsa ce, to wacece ke kuma?" Janar yace "Shi
mijin a ina yake Baaba?" Inna ta juyo tace "Ina dai zuwa" Daga haka ta tafi dakin
Umma don can Kamila ta makale duk budurin nan da ake saboda yanda fuskarta ya
kumbura suntum, ga bakinta da ya dawo kamar na rakumi, kana ganinta kasan tana jin
jiki, Inna tace "Daure ki tashi mu je parlor, ga sojoji nan Allah ya kawo mana daga
sama ba ko sisinmu, mu je su ganki don a san irin dukan da xa a ma matsiyacin,
Kamila ta wani kalli Inna tace "Baxan je ko ina ba" Inna tace "Amma dai ke
walakantacciya ce, ga dai za a bi maki hakinki kina neman gantalar da ni, tun dazu
nake ta wahala a kanki" Kamila ta kwanta ta juya mata baya, Inna ta dinga kallonta
can ta fita, kafin Inna ta dawo parlon Abba yayi saurin ce ma Janar ai mijin baya
nan amma ya riga ya gama magana da yan uwansa ba wani abun tashin hankali bane,
they will sort everything out, tana fitowa Janar yace "Shikenan Baaba, mun gama
magana za aje a samesa in sha Allah" Inna tace "Toh Allah yayi maka albarka, Allah
ya sa ka gama da duniya lafiya, mu kuma Allah ya bamu ladan rikon da muka ma ɗan
ka, rikon amana babu ha'inci, cin sa, shan sa, suturarsa, wajen kwanansa, duk bamu
gaza ba, kai har mota sai da muka basa yana zuwa duk inda ya ga dama kansa tsaye,
ni kuma duk sai na gwammaci Halilu a kan jikokina maza don ya fi jin kai na a
kansu, yanzu sai aje a ajiyeni gidan babban ɗa na in taho da shi har nan ya
gaisheka shi ma cikin girmamawa" Janar yace "Eh toh yanzu dai ana jirana Baaba,
kafin dai in koma Abuja za mu hadu da shi in sha Allah" Wani hararan tsana Hassana
ta dinga yi ma Inna, duk ta kagu taga sun fice daga gidan taje ta san ta inda zata
fara don wannan duk bata mata lokaci kawai ake, su Mami da Aunty Maryam dai sai
kallon Innar suke su ma kamar sun ga alien, Mumy kuwa kunya kamar ta nutse a wajen,
inna ba kamun kai, Masallaci Janar suka fita tare da Abba da abokinsa saboda
lokacin azahar yayi.... Mumy na kallon su Aunty Maryam tace "Mu je ciki ku yi
sallah Hajiya" Aunty Maryam ce ta fara tashi ta bi bayan Mumy, Inna ta lallaba ta
bi bayan Aunty Maryam bayan sun shiga parlon tace "Amma ita wancan figaggiyar da ku
ka zo da wacece ita? Naga babu ta inda take kama da ku ko Janar din, amma kuma take
son kawo min raini" Aunty Maryam na murmushi tace "Kanwarsa ce kaka" Inna ta gwale
ido tace "Kanwarsa kuma? To na ganta baka shi kuma fari, babu kuma kamanni in za a
fadi saboda Allah" Aunty Maryam tace "Uwarsu ce daya, amma gun dangin ubanta ta
taso" Inna ta rike haɓa, Mumy ta leko parlon tace "Hajiya karaso kiyi alwala" Aunty
Maryam na kallon Inna tace "Bari in yi alwala" daga haka ta ajiye mayafinta ta
shiga bedroom din Mumy, inna tace "Ashe tsinanniya ce take neman kawo min raini"

Umma bata yi awa biyu a asibitin ba aka sallameta suka nufo gida don tun kan ma su
isa asibitin ta farfado, dressing din mata ciwon da taji a goshi kawai aka yi sae
hannunta da ta samu dislocation shi ma aka gyara sannan magunguna da aka bata to
relieve the pain, Har cikin compound motar da aka kai ta asibiti da shi ya shiga
yayi parking bayan sun dawo gida, sojan dake tuka motar ya sauka ya bude ma Umma
kofa, Umma ta sauko daga motar a hankali da katon bandage a goshinta ga hannunta da
take lallabawa kar ta fama, ta dinga bin gidan da kallo kamar bata taɓa ganin gidan
ba, yanda take yi da idanuwa zaka ce tayi wata da watanni a kwance ba lafiya sai
yanzu aka fara samo kanta, Farooq ya sauka motar don a tare yake da ita a back seat
din, Khalil ya bude front seat shi ma ya sauko yana rike da drugs din nata dake
cikin leda, Farooq na rike da hannun Umma mara ciwon suka nufi entrance din cikin
gidan Khalil na biye da su, Mami da Aunty Maryam ne kawai a gidan, Inna ta shiga
gari sanar da yan uwa da abokai abun arxikin da ya samesu, Aunty Hassana kuwa tana
ganin Janar ya bar gidan ita ma ta shiga garin kano ko zata fara nemo solution
dinta a nan, Janar bai bar gidan ba sai da ya dire ma Abba miliyan daya, wanda yace
ya ba inna 300k sauran kuma ya raba ma duk yan gidan.... Tun bayan da aka kai Umma
asibiti Mumy ke bedroom dinta tare da Aunty Maryam da Aunty Jamila, Mami ce kadai
ta ki shiga dakin duk yanda Mumy tayi da ita kuwa, har abinci ma bata ci ba balle
small chops din banda bottle water kawai da ta dauka shi ma ba sha tayi ba kawai a
gefenta ta ajiye, Aunty Maryam ko ta ci abincinta ta koshi, ta kara da snacking,
yanda take hira da Mumy kamar ta taɓa saninta, Aunty Maryam bata boye ma Mumy duk
abubuwan da suka faru can Abujan ba kan yanda Khalil ya rufa cewar Nihad matarsa ce
for almost 2 months din da suka yi a can, ita dai Mumy ta ma rasa abun cewa, Aunty
Maryam ta kawo maganar Video din Nihad dake cin ta a rai kenan su Umma suka shigo
gidan daga asibiti, hakan yasa Mumy ta mike tace ma Aunty Maryam bari taje duba
jikinta, Mumy ta bi Umma har bedroom dinta tare da Farooq, Umma ta lallaba ta
kwanta saman gadon kar ta fama hannunta, Farooq ya ajiye ledan maganin da Khalil ya
basa a bedside drawer, Kamila kuwa na kwance can end din gadon, Mumy ta kalleta
tace "Sannu Kamila, na shigo dazu kina bacci" Kamila dai ba bakin magana, Mumy na
kallon Umma tace "A kawo maki abinci ne?" Umma ta girgiza kai da sauri amma ta kasa
cewa komai, Mumy tace "Toh Allah ya sauwake" Daga haka ta juya ta fita daga parlon,
tana komawa ɓangarenta ta kalli Mami dake parlonta tace "Hajiya ko dai kina son a
maki wani abun ne na ci?" Mami tace "No it's okay, mara lafiyar ta dawo mu dubata?
Don za mu koma Abuja yanzu" Mumy tace "Ehh yanzu suka shigo" Mami tace "Toh Maryam
ta fito mu je mu dubata mu kama hanya" Mumy ta shiga dakinta tayi ma Aunty Maryam
magana, Aunty Maryam ta fito, Mami tace "Janar yace akwai jirgin sojoji da zai koma
Abuja yau and it can contain us all" Aunty Maryam tace "Yaushe jirgin zai tashi?"
Mami tace "Soon" Tana fadin haka ta mike tana kallon Mumy tace "Ina bangaren mara
lafiyan?" Mumy ta kai su har bangaren Umma, Umma ta dinga bin su da ido tun da suka
shigo, ko sannun da suke mata ta kasa amsawa, Mami tace "Allah ya sauwake ya sa
kaffara ne Hajiya" Cikin rawan murya Umma tace "Ameen" Aunty Maryam dai sai
kallonta take ta tuna abubuwan da Nihad ta gaya mata a kanta, can ta taɓe baki ta
juya ta fita daga dakin. Mami bata koma bangaren Mumy ba ta zauna main parlor tana
jiran Convoy da suka tafi da Janar su dawo daukansu, babu dadewa kuma suka iso,
Mumy tayi masu packaging sauran small chops din, Aunty Maryam tayi ta mata godiya,
Mami na kallon Aunty Maryam tace "Ki kira Hassana" Aunty Maryam ta ciro wayarta ta
kira Hassana, tana dagawa Aunty Maryam tace "Za mu tafi airport yanzu Hajiya" Aunty
Hassana tace "Gaskiya nayi nisa, ku tafi kawai ko flight din dare idan na samu sai
in biyo" Aunty Maryam bata ce mata komai ba ta katse wayarta. Nihad ta fito daga
dakin Nihal da take ciki tun dazu bayan Mumy taje ta taso ta tayi masu sallama,
Aunty Maryam na kallon Nihad da murmushi fuskarta tace "Zaku taho tare da Khalil
din Daughter...." Nihad dai ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Sai da taga za
su fita tayi ma Mami sallama, Mami ta amsa sannan ta fita daga parlon, Mumy ta
rakasu har gate, sai da suka bar layin sannan ta dawo ciki, zaune taga Aminu kan
benchi kamar mara lafiya duk yayi sanyi, tana kallonsa tace "Lafiya Aminu?" Aminu
yayi kasa da murya yace "Ina ta tuna ko wani abu ya taɓa hadani da Halilu ne,
kinsan zaman tare zo mu zauna zo mu saɓa, ni dai a sanina baxan tuna ga abinda nayi
masa ba gaskiya, sai dai ko cikin rashin sani, amma lafiya na zauna da shi wllh, ni
dai dama in ta tsoron inda yake samun kudi kullum sai mun ci tsiren kusan dubu
biyar a nan da daddare, ga lemon kwali me tsada, wani lokacin ma ni yake aika in
siyo mana shi kuma ya tsare gate din, har ta kai ta kawo na daina cin abinci da
daddare saboda yanda muke cika cikinmu da nama, cakulate da manyan biskit kuwa har
yanzu ina da ledojinsu da na tara a dakina, muna zaune lafiya wallahi da shi har ya
bar gidan nan, haka kawai sai in ga ya mun kyautar dubu biyu dubu uku, ni duk
tunanina kudin albashin tukinsa yake ci, ashe ga zance ga magana, dama su isiya ne
suka masa azababben walakanci zuwansa gidan nan, Allah kadai kuma yasan yanda zai
yi da su yanzu" Mumy dake ta kallonsa tayi murmushi kawai ta bar sa wajen ta koma
ciki, Aunty jamila na zaune tare da Nihad a parlon Mumy, Mumy ta shigo ta zauna
tana kallon Nihad, Aunty jamila tace "Sai nake ga kamar uwarsa bata yi farin ciki
da auren nasu ba Aunty" Mumy ta ɗan yi murmushi kawai amma bata ce komai ba, Ita
dai Nihad wasa take ta yi da yatsunta, a hankali Mumy tace "I noticed that too, na
ga alamar hakan..." Aunty jamila ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Nihad tace
"Wani irin zama kika yi a gidansu can Abuja Nihad?" Nihad ta daga kai tace "Ita
dama haka take, she doesn't talk much, and... She isn't friendly, but she is nice"
Aunty jamila tace "Amma bata nuna maki komai ba sanda kike gidan?" Nihad ta girgiza
kai tace "Aa" Aunty jamila tace "Toh Allah ya kyauta" Mumy ta rasa me yasa she
isn't happy about how everything turns out, ko don saboda reaction din Mami ne she
can't tell. Babu yanda Mumy bata yi da Nihad ta shiga duba Umma ba amma kememe
taki, Aunty jamila tace "Aa kar ki takurata Aunty Maryam, ke dai ba kinje kin
dubata ba" Dab da magrib Khalil ya iso gidan, yana bude gate Aminu ya mike da
sauri, ya ɗan duka cike da ladabi yace "Barka da isowa ranka shi dade..." Khalil ya
fara kalle kallen abinda zai dauka ya jefe shi da shi....

Ana idar da sallan magrib Farooq ya tafi kai Kamila asibiti, Umma dama tun dazu
take jiran su tafi asibitin, suna tafiya kuwa ta mike da sauri ta shige bandakinta
ta tura kofar, Hajiya Turai ta shiga kira a wayarta, Turai na dagawa cikin kuka
Umma tace "Dazu muna magana Maryam ta shigo shi sa na katse Turai" Tsabar tashin
hankali zaman dirshan tayi a bandakin ta sa wayar a handsfree ta ajiye a kasa tana
kuka wiwi ta rike kanta tana cewa "Turai na shiga uku, turai na shiga uku na
lalace, wallahi tunda nake ban taɓa girgiza irin ta yau ba Turai, ban taɓa shiga
tashin hankali irin na yau ba, Shi fa Janar jikamshin da kansa ya shigo har gidan
nan namu yau da matansa, convoy kuwa tun daga farkon layin nan har karshensa, ga
sojoji yanda kika san za ayi yaki, Turai dama kin taɓa ce min anya ba basaja Khalil
din nan yake ba saboda jikinsa bai yi kama da wanda ya san wani abu wai shi wahala
ba, ni ko na dage maki cewar har kauyensu Yallabai yaje kawai farin fatar tasa ce
yasa kike ganin haka, Turai ashe duk karya mutumin nan yake, turai ɗan babban mutum
ne, turai ɗan jikamshi guda ne" Sai ta kara fashewa da kuka kamar warce aka yi ma
mutuwa, Turai da ita kanta tayi mugun girgiza da wannan labarin aminiyar tata tace
"Jikamshi? Janar jikamshi fa kika ce, ni wallahi duk kin rikitani, wannan saurayin
nata Aliyu ba shine ɗan jikamshin ba? Ko ya abun yake?" Cikin kuka Umma tace "Ince
maki yau ga mu ga Janar jikamshi da bakinsa kuma yace Khalil din ɗansa ne ki wani
kawo zancen Aliyu, ai tunda kika ga haka karya Aliyun ya sharara ma mutane kenan,
irin yan iskan makaryatan yaran nan ne masu amfani da sunan manya su yaudari yan
mata, kuma Allah ya isa tsakanina da shi don da ba don wannan karyan da yayi mata
ba a ina har za a ga wani video dinta na yawo balle har uban ya mata aure? Wllh duk
Aliyun nan ne ya ja min wannan bala'i, ya cuceni, ya cuceni, da ba don shi ba ai
kawai gantalinta zata ci gaba da yi da bin hotels babu wanda ya sani, ni dai mafita
zaki nemar min kawata, wallahi zuciyata zai iya fashewa in har Nihad ta ci gaba da
auren Khalil, Shine fa ainahin ɗan Janar din nake gaya maki, uwarsa kuwa da kyar
idan ba balarabiya bace, jikinsu duk gwala-gwalai Turai...." Ta fashe da wani
matsanancin kuka tana girgiza kai tace "Kuma fa wallahi da Nihal yaron suke shiri a
gidan, har zama suke yi gu daya su yi fira, amma nasan yanda nayi na sa ta fita
harkansa, har waya fa suke yi na hanata ta karfi da yaji, da na sani me zai sa in
shiga tsakaninsu Turai? Me zai kai ni?? Ai wallahi da sai inda karfina ya kare
wajen tabbatar da cewa ya aureta, amma duk tunanina mara galihu ne shi din" Turai
tace "Tashin hankali.... Yanzu sun koma Abuja da Nihad din kenan?" Umma na
shessheka tace "Ina na sani, tun dazu ni dai ban ji duriyarsu ba kinga ai sun koma
kenan, ita kanta Nihad din har yanzu zancen nan da nake maki bata shigo ta dubani
ba, Yallabai da ya shigo dazu kafin magariba yake gaya min miliyan daya Jikamshin
ya bada a raba ma yan gidan" Turai ta zaro ido tace "Toh baki ga ta kuka ba gaskiya
Sumayya, kuka ba naki bane yanzu, amma dai su ba su da labarin videon da yayi
leaking a gari ne kwanaki?" Umma tayi shiru, sai kuma tace "Kai bana jin sun sani
gaskiya, wa zai so ɗan sa ya auri irin wannan yarinyar? Ai da sun gani da tun a
Abujan za su sa ya saketa" Turai tace "Toh kawai kudi zaki bada a ba popular
bloggers kamar biyar haka su sake dawo da labarin da zafi zafinsa, nan da nan zaki
ga ya karade duniya" A hankali Umma tace "Ko??" Turai tace "Kwarai kuwa" Umma na
share hawayenta tace "Kamar nawa zan turo yanzu?" Turai tace "Ko dubu dari uku ce a
kacalcala masu, kyau a samu bloggers kamar shidda lafiyayyu" A hankali Umma tace
"Turai zoben fa saura kwaya daya yanzu, duk mun siyar an kai ma malamai" Turai tace
"Amma ai kuma bukata na biyuwa idan ba yanzu da aka samu cikas ba, yanzun ma rufe
ido zaki yi ki siyar kawai a biya bukata da shi, Allahn da ya baki shi zai sake
baki" Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh shikenan Turai, Nagode sosai Allah ya
bar zumuncinmu, in sha Allah gobe xan aiko Amina da shi, ni kinga bazan iya fitowa
goshi a fashe, ga hannu nayi targade" Turai tace "Ba damuwa goben ma zan shigo ba
sai kin aiko Amina ba" Umma tace "Toh nagode sai kin zo" Daga haka Umma ta katse
wayar, nan taji hankalinta yayi mugun kwanciya, ai da Nihad ta zama surkar jikamshi
gwara ko tsirara ne tayi yawo a duniya, sai tasan yanda tayi ta rabata da Khalil
wallahi, mikewa tayi ta nufi kofa ta jawo zata fita taga Abba tsaye bakin kofar
bandakin, Sake wayar hannunta tayi cikin daburcewa tace "Yall.. yallabai yaushe ka
shigo?? Bayan gida na shiga inyi...." Abba dai kallonta kawai yake, can ya juya ya
bar bakin kofar bandakin, walking slowly ya fita daga dakin gaba daya, jikin Umma
ya dau rawa ta dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a zuciyarta, da kyar
ta karasa fitowa daga bandakin taga ledan fruits da ya kawo mata ajiye a kasa....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

*CONGRATULATIONS*🥳🥳
*For taking this smart move to growing your business....*

I am zainab Suleiman you can save my contact ummu shaheed or kabzee 08033242995

* I will be giving you the opportunity to connect to Over 80 direct suppliers and
major dealers of various products in Nigeria, where you will be getting goods at
factory prices without Importation and reselling as an wholesaler to make great
profit.*🤑🤑🔥🔥

*This is for everyone that wants to start getting products at good purchase
price/factory prices and become a major wholesalers that other business owners can
buy in bulk from*🔥🔥

*This suppliers contact bundle has solved 70% of the problem of startups, small
business owners, distributors, dropshippers etc...which is the inability of getting
goods at good affordable prices to resell...*

*But the *GOODÑEWS is I will allow Only 20 people access this contact bundle at
a discount rate of N5000 ONLY*

*Ps: this offer is available for just 24 hrs.* ‼️


‼️
*After that price goes back to the usual price of N7,000* ✅✅💖 NIHAAD 💖

63

Nihad ta gama shirin kwanciya a bedroom din Mumy wajen karfe tara da rabi, Aunty
jamila da bata yi tafiyar tata ranan ba sai bin ta take da kallo tana ganin ikon
Allah, sai da ta bari ta kwanta sannan tace "Ke kam ashe har yanzu baki da saiti
ban sani ba Nihad" Nihad ta juya ta kalleta, Aunty jamila tace "Mijinki na gidan
nan tun dazu amma common kije ki ga ko ya ci abinci ma baki je, ko yana da bukatar
wani abu ke duk ba damuwarki bane, babu ruwanki sai harkan gabanki kike, to kuwa
idan kina nuna i don't care attitude din nan naki akan miji kya samu warce kina ji
kina gani zata kwace maki miji" Nihad ta mike zaune tana kallon Aunty jamila, a duk
maganar da ta mata na karshen ne ya tsaya mata a rai, Aunty jamila tace "Shi namiji
in gaya maki riritasa ake, wasu na can a waje suna harinsa ke kuma kina nan kina
shashanci, tun daxu da ya shigo gidan nan sai kije ki samesa ki ji ko yana da
bukatar wani abu tunda nasan Mumy dole zata basa abinci...." Dai dai nan Mumy ta
bude kofar dakin ta shigo, tana kallon Nihad tace "Ke baza kije kiji ko yana da
bukatar wani abun ba?" Aunty Jamila tace "Maganar da nake mata kenan yanzu Aunty"
Nihad ta sauka daga saman gadon a hankali ta dau hijab dinta ta sa, har ta nufi
kofa sai kuma tace "Toh ai ni ban san inda yake ba fa" Mumy tace "Yana dakin
Farooq" Bude kofar tayi ta fita, Aunty Jamila ta rike haɓa tace "Aa gaskiya tana
bukatar counselling akan auren ma gaba daya, don ban ga alamar tasan komai ba" Mumy
tace "Toh idan ba ke ba wa zai mata Jamila" Aunty Jamila tace "Allah ya kai mu
gobe" Mumy tace "Ke baza ki ci abincin ba?" Aunty Jamila tace "Aa na sha shayi...
Uhmm Aunty bamu samu mun yi magana ba har yanzu" Mumy na kallonta tace "Magana akan
me fa?" Aunty Jamila ta rike haɓa tace "Me suma daga ji da ganin abun arxiki, ke
kiji hassada kiri kiri, zuciya ta kasa adana hakan har sai da ya fito fili cikin
bainar jama'a, duk me hangen nesa a parlon nan yasan shock din al'amarin ne ya
sumar da ita ba wani abu ba, and shock in the sense that she wasn't expecting
things to turn out that way, wallahi she never expect that kamar yanda mu ma bamu
yi expecting ba kawai a bazata abun ya zo mana, wato Sumayya ta gina ramin mugunta
without considering zata iya dawowa ta afka ciki ko wani nata ya afka, yau ai ga
Kamilar da take takama tana auren mai kudi a gida ba wai farin ciki nake da hakan
ba don babu wanda zai yi farin ciki da mutuwar auren wani, amma ishara ta fara gani
tun a nan duniya, sai ga Nihad da ta so lalata ma rayuwa tana auren wanda ko a
mafarki bamu taɓa kawo hakan a kai ba, na sha gaya maki da akwai wani boyayyen
lamari game da Khalil din nan, tun ran da na fara ganinsa a gidan nan..." Mumy dai
ta sauke ajiyar zuciya ta ma rasa abinda zata ce ma er uwartata. Nihad na tafiya a
hankali ta nufi dakin Ya farooq, ta tsaya bakin kofar tayi sallama hade da
Knocking, bude kofar dakin aka yi taga Khalil tsaye, ta shiga cikin dakin tana
kallonsa tace "You need anything?" Ya kafeta da ido, sai kuma ya kulle kofar dakin
ya jawota, ta zaro ido tace "What are you doing??" murya can kasa yace "I need
nothing, but you...." Ta wani turo baki tace "Ni ka sakeni kar Ya Farooq ya shigo,
dama su Mumy ne suka ce in zo in tambayeka ko kana da bukatar wani abu shi yasa na
zo...." Kallon lips dinta kawai yake tana magana kuma ya ki sakinta, ganin haka
tace "Ni don Allah ka sakeni, meye haka...." Bai bari ta rufe baki ba ya hade
bakinta da nasa giving her a deep kiss, lokaci daya ta ji tana neman faduwa tsabar
yanda ta kasa tsayuwa da kafarta ya jinginar da ita da bango, kissing her
romantically, knocking din kofar dakin aka yi ya saketa da sauri zai koma baya amma
tuni Farooq ya shigo, yana shigowa kuma yayi kasa da kansa ya juya ya fita daga
dakin, Nihad ta marairaice tana kallon Khalil wanda shi ma kunyar Farooq ya cikasa,
wani harara ta galla masa ta nufi kofa da sauri, ya bi ta da kallo yana shafa kansa
har ta fita daga dakin, sai sunkuyar da kanta take wai ko zata ga farooq a hanya,
amma har ta koma bangaren Mumy bata gansa ba, ta sauke ajiyar zuciya ta shiga
parlon, ƙin karasawa bedroom din Mumy tayi don gani take suna ganinta za su gane
abinda Khalil yayi mata, ta kwanta saman 3 seater tayi lamo zuciyarta na bugawa,
har sannan tana jin kamar bakinsa na cikin nata, the imagination is making her
whole body weak, a hankali ta kai hannu soft lips dinta tana taɓawa. Farooq na bar
masu dakin na Usman kawai ya wuce yayi kwanciyarsa a nan, dama daga bangaren Umma
yake wanda taki fadin dalilin kukan da take kamar warce ta amshi sakon mutuwa, ba
yanda bai yi da ita ba amma taki gaya masa daga karshe tace masa ai hannunta ne ke
damunta, babu yanda ya iya ya fito dakin nata kawai. Daren ranan yanda Umma ta ga
rana cike da bakin ciki haka ta ga dare cike da fargaba, Kamila bar mata dakin tayi
ta koma na Nihad daga karshe tsabar irin kukan da take yi, Umma bata taɓa shiga
tashin hankali irin wannan ba, can kuma wata zuciyar ta dinga assuring dinta ai
Abba bai ji wayar da take ba fa, ta yaya zai ma ji bayan ta tura kofar bandakin,
kawai dai abinda ya ɓata masa rai yanda take magana cikin bandaki, wannan tunanin
yayi contributing wajen calming dinta down, amma fa bata runtsa ba har asuba, ga
dislocation dinta yayi tsami sai azaba yake mata, goshinta ma sai yanzu yake mata
fitinannen ciwo... Da safe Mumy ta shigo duba jikinta, Umma ta ki bari su hada ido
tace "Jiki Alhamdulillah" Mumy tace "Toh Allah ya sauwake, ya sa kaffara ne" Tace
"Ameen Ameen" Mumy ta ɗan zauna a parlon na wani mintuna kafin ta tashi tace mata
zata shiga kitchen, Umma na ganin ta fita ta lallaba ta saka Hijab dinta ta fito
main parlor don Mumy ce da girki kuma tun dazu take jiran ta ji ta a kitchen kafin
ta tafi parlon Abba, bata tadda kowa parlon ba don it is still early, ta nufi
bangaren Abba da sauri ta bude kofar parlon ta shiga, bata gansa a parlonsa ba
which is very rare, yana dawowa masallaci parlonsa yake zama har zuwa lokacin da
zai fita office sannan ya shiga bedroom dinsa ya shirya, hankalin Umma a tashe yake
sosai, gabanta sai faduwa yake, tayi karfin halin nufa kofar dakinsa a hankali ta
murda, zaune ta gansa saman gadonsa ya jingina da pillow yayi nisa tunanin da yake,
ya daga kai ya kalleta, gabanta ya fadi sosai, cike da karfin hali ta karasa cikin
ta zauna saman kujeran dake dakin ta dake tace "Ina kwana yallabai" Abba ya kalleta
kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Lafiya lau" Umma ta ɗan ji hankalinta ya
kwanta jin ya amsa, nan ta fara kame kame ta marairaice tace "Yallabai jiya, kawai
ina bandaki... Dama kuma kasan...." Dakatar da ita Abba yayi yace "Ni ban tambayeki
komai ba Sumayya" Bude kofar dakin aka yi, Mumy tayi turus bakin kofa ganin Umma a
dakin, sai kuma tace "Ohh ban san ma kina nan ba ai..." Umma dai tayi wuri wuri ta
kasa cewa komai, Mumy zata kullo masu kofar Abba yace "Ya aka yi Maryam?" Mumy tace
"Aa tambaya zan yi ko yanzu kake son black tea din" Yace "Aa sai anjima" Tace "Toh"
Daga haka ta juya ta kulle masu kofar dakin, Umma ta rasa abun cewa suna ta zaune
haka for almost 3 minutes duk jikinta yayi sanyi, yanxu da gaske ya ji wayar nan da
take? Abba yayi breaking silent din yace "Sumayya" Gabanta yace rassss, ta daga kai
da kyar tana kallonsa amma ta kasa amsawa, Yace "Za ku ba Bloggers 300k don su sake
dawo da Video din Nihad ke da kawarki a social media, kin nuna kina baƙin ciki da
gidan da Nihad ta samu, kin nuna you can't even withstand seeing her married to her
current husband kawai saboda selfish interest dinki, kika ce duk kun siyar da
zobenki na gwal kin kun kai ma malamai, baxan tsaya bin diddigin abubuwan da
malaman suka maku ba Sumayya, baxan yi hakan ba, kawai dai nayi farin ciki da na
gano duk wani abu da kike ma Nihad ba da zuciya daya kike ba, ke kina da wata
manufar taki ta daban ne a zuciya, this is so unfortunate Sumayya, idan kuma aka ce
min da hadin baƙinki video din 'ya ta yayi yawo a gari, kuma da sa hannunki wajen
yin video din ma baxan musa ba, kin gurbata mata rayuwa kin bar mata taɓon da baxai
taɓa gogewa a rayuwarta ba, kin cuceta" Umma ta fashe da wani matsanancin kuka tace
"Wallahi wallahi wallahi Yallabai ban san ta inda wannan video din ya fita ba kaji
har na rantse, believe me wallhi i know nothing about the video, idan kuwa karya
nake Allah ya dauki raina a nan" Kuka take sosai tana kallonsa, Abba yace "Ba komai
Sumayya, koma dai menene bana jin bayan abubuwan da naji kuna fada a waya dake da
kawarki kuma a hakan ma ba daga farko na tsinci wayar naku ba, bana jin zan iya ci
gaba da zama da ke, all what u are saying on phone ya nuna baki son Nihad, baki
taɓa sonta ba, fuska biyu kika dinga mata Sumayya, idan har tun ba yanzu kika fara
cutarta ba kuma kece sillar duk abubuwan da suka sameta Allah Ubangiji ya saka mata
cikin gaggawa, kuma kije na sake ki amma zaki iya ci gaba da zama gidan nan, don da
girmanki bazan ce ki bar min gidana ba, zaki ci albarkacin zuri'an dake tsakaninmu,
zaki ci gaba da zaman yaranki, ki ci gaba da duk harkarki a gidan nan amma babu
aure tsakaninmu, and this should be just between i and you, sai Maryam wanda ita ma
dole ta sani ne for some reasons, amma ko yaranki ni ban baki goyon bayan ki sanar
masu komai ba balle wani a waje, ki ci gaba da duk yanda kike a gidan nan, aure ne
dai babu tsakanin ni da ke" Bitterly Abba ke maganar, Tsabar shock Umma ta kasa
cewa komai ta dinga kallon Abba babu ko kiftawa, Abba yace "Ki je na sake ki
Sumayya" Wani kukan tashin hankali Umma ta fashe da tace "Ka sakeni fa kace
Yallabai, wallahi yallabai sharrin shaidan ne amma kasan ba halina bane, ban taɓa
nufin Nihad da sharri ba dai dai da rana daya, wallahi rudin shaidan ne, don girman
Allah ka rufa min asiri ka janye batun sakin nan, tsofe tsofe da ni kace ka sakeni,
ko albarkacin yara baxan ci ba Yallabai" Abba yace "Albarkacin nasu yasa nace kiyi
zamanki gidan nan kiyi harkarki yanda kika saba, sannan ko Mahaifiyata ni baxan je
ince mata na sakeki ba,
i am leaving it to my self, sai in kece kika je kika fadi a gari...." Kuka Umma
take kamar ranta zai fita tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, saki da
tsufana Yallabai, saki fa kace" Abba yace "Kin ga ki tashi ki je kar ki ja mana
attention a nan, you can leave pls Sumayya" Tashi tayi tana kuka sosai ta nufi kofa
ta fita daga dakin nasa..... Umma na komawa dakinta ta dinga kuka ba ji ba gani,
Kamila dake ta kallonta tace "Toh wai baki kira Hajiya Turan bane" Umma tayi banza
da ita tana rusa kuka uwa yar yarinya.

Aunty Maryam ta girgiza kai tana kallon Mami tace "Mami i am not supporting Khalil
in anyway, ki fahimce ni Mami, yanzu ko Janar ne yace bai yarda da auren nan ba ba
sai inda karfinki ya kare ba Mami? Ki daure ki dinga duba halacci irin na iyayen
yarinyar wllh sai kiga kin samu rest of mind kin rungumi auren nasu hannu bibbiyu,
uban yarinyar fa cewa yayi saboda kyawawan halin Khalil ya aura masa 'yar sa, ki ga
fa kauye yaje yayi hiring mutane a matsayin iyayensa ya kai ma uban yarinyar, amma
hakan bai sa uban ya kyamacesa ba ya basa er sa, mun dai je gidan kinga babu alamar
tsiya tare da su, kuma da ganinsu kasan yan babban gida ne, Mami in dai Nadeeyah ce
damuwarki to ki kwantar da hankalinki babu wanda yace Khalil bazai aureta ba, ai
Janar bazai ma yarda ya mayar da shi karamin mutum ba dole ce masa zai yi ya hadasu
gaba daya, kai idan ma tsoronki idan Khalil ya dawo zai iya cewa ya fasa to ko ni
kadai na ishesa wallahi, balle kar ki manta Mami muna nan duk bamu san da aure
tsakaninsa da Nihad ba amma kuma ai bai fasa shirye shiryen aurensa da Nadeeyah ba,
ya yarda har aka kai kudi aka sa masu lokaci, da bai da niyyar auren nata ai
kakkaucewa kawai zai dinga yi...." Mami ta dakatar da ita tace "Bana son ki dinga
kawo min maganar shirme Maryam, ko min rashin sona da auren nasa ba sai dai in zuba
ido inyi shiru ba tunda aikin gama ya riga ya gama, kina ganin zance ya saki
yarinyar ne? Ni takaicin dake damuna yanda har ni ya iya boye ma auren, Maryam babu
ranan duniyar da bana kiran Khalil fa, a rana nakan kirasa sau uku sau hudu, ko
kece ɗanki ya maki haka baza ki ji dadi ba Maryam, yasan dai ko da za a juya masa
baya akan batun auren nan ni bazan juya masa idan ma zan yi fushi na ɗan lokaci ne,
amma yayi min haka saboda bai daukeni a bakin komai ba wai har ni ya boye ma, kinga
kuwa ai babu ruwana da wani aurensa da yarinyar yaje can ya karata, babu ruwana"
Aunty Maryam ta kwantar da murya tace "Babu dadi amma kiyi hakuri kada fushin nan
da kike da shi ya shafesa Yaya, gaskiya yayi babban kuskuren boye maki ko da zai
boye ma kowa, but plss forgive him Mami, sannan ki sa ma auren nasu albarka don
Allah, ki rungumi Nihad a matsayin surkarki ko don halaccin da iyayenta suka ma ɗan
ki, kin dai ga uwarta mutuniyar kirki mara son hayaniya, ubanta ma kin ga babban
mutum ne da yasan darajan ɗan adam, ki duba wannan kiyi hakuri ki ja ta jiki
matsayin surkarki pls Mami" Mami ta mike ta dau gyalenta tace "Hajiya Safeenah na
jirana, sai na dawo Maryam" Daga haka ta nufi kofa Aunty Maryam ta bi ta da kallo.
Karfe shidda da yan mintuna na yamma Nihad ta gama shiryawa don Khalil ya sanar ma
Aunty Jamila Flight din nasu na karfe takwas din dare ne, Aunty Jamila ta nuna mata
gefen gado ta zauna tana kallon gorunan dake gabanta wanda a jiki duk aka rubuta
KMZ (Kayan Matan zuru 08033308307) Nihad dai ta sunkuyar da kanta taki yarda ta
sake kallon Aunty Jamila, Aunty jamila sai dai ta mika mata cup tace ta kwankwade,
Nihad ba halin mata musu, da ta shanye kuma take maida mata cup din ta kara mata
wani hadin, har zuman KMZ sai da ta bata, a karshe ta bata gumbar kwakwa ta ci,
sannan Aunty Jamila ta fita daga dakin, Sosai gumbar yayi ma Nihad dadi wanda bata
ma san sanda ta cinyesa tass ba, Amina ta leko dakin tace "Wai ana jiranki a waje
Aunty" Nihad ta mike da sauri ta shiga bandaki ta wanke bakinta da mouth wash
sannan ta fito, tun da tayi wanka dazu ta saka er gown bayan ta shafe duk jikinta
da turare, sai yanzu da ta sa Hijab har kasa ta fito, parlon Mumy ta shiga ta
sameta tare da Aunty Jamila, ta durkusa jikin kujera ta kasa kallonsu, a hankali
tace "Za mu tafi" Aunty jamila tace "Toh Allah ya tsare Nihad, babu kayan da zaki
dauka?" Nihad ta girgiza kai tace "Akwai kaya a can" Aunty jamila tace "Toh
shikenan, shi ma yanzu ya fita, yana can waje yana jiranki, saura kiyi watsi da duk
abubuwan da na gaya maki dazu" Nihad dai bata ce komai ba, can ta daga kai ta kalli
Mumy taga kallonta take, Mumy ta sauke idonta tace "Allah ya tsare, sai ayi ta
biyayya, Allah ya maku albarka gaba daya...." A hankali Nihad tace "Ameen" Mumy
tace "Jamila kiyi mata magana taje ta duba Umma kafin su tafi tunda ni na mata taki
ji" Aunty jamila tace "Wace Umma, baki ji fitarta ba dazu?" Mumy tace "Au haba?"
Aunty Jamila tace "Ai ko ta fita bayan la'asar da katon bandage a goshi ni na zata
ma asibiti zata amma kuma naga bata dawo ba har yanzu" Mumy tace "Toh shikenan
tashi ki je, kin bar sa a waje yana jiranki" Nihad ta mike kanta a kasa ta kara
masu sallama sannan ta nufi kofa ta fita duk suka bi ta da ido, A compound ta tar
da Khalil bakin gate yana zaune kusa da Aminu, Ga Iliya driver a cikin mota yana
jiransu, Aminu sai washe baki yake yana kallon Khalil kamar ranan ya fara ganinsa,
Khalil ya ciro dubu dari cash ya ajiye masa gefensa a kan bencin da suke yace "Ka
ci gaba da cin tsirenka da lemon kwali duk dare, idan kuma kaji da inda ake yankan
fili a unguwa me kyau ka kirani ka gaya min" Aminu ya kasa cewa komai sai kallonsa
yake kamar wawa, Isiya da Saminu dake makale jikin kofar dakin Aminu don wani Cele
suka mayar da khalil sai sinne kai suke kamar munafukai, Khalil ya mike ya ciro
dubu hamsin ya mika masu su biyu sannan ya bar wajen zuwa parking space, Nihad dake
tsaye ganin ya taho ta bude back seat ta shiga, shi ma back seat din ya bude ya
shiga, Aminu dake matsar kwallan farin ciki ya bude masu gate, ba bakin magana ya
dinga daga masu hannu yana jijjiga kai har suka bar gidan, Isiya da Saminu suka hau
raba kudi, Aminu na kulle gate din ya juya ya kallesu bayan ya share guntun hawayen
idonsa yace "To ai dai kun ga amfanin mutunta ɗan Adam a rayuwa, kiri kiri ku ka
hanasa daki farkon zuwansa gidan nan, ku ka dinga masa rashin mutunci sai da ya
nuna maku shima fa ɗan banza ne sannan ku ka shiga taitayinku amma ko ga maciji
bakwa yi da shi, to da nine shi wallahi da alawa ko biscuit zan hada ku yau" Sai
kuma ya tuntsire da dariya har da kyakyatawa, banda hararansa babu abinda suke yi,
horn yaji na katon mota, ya koma gate din da sauri yana leka waje, Katuwar mota ce
shake da kayan dakin Kamila da komai nata na gidan mijin ya turo a kawo alamar babu
komawa, Aminu ya saki baki sai kuma ya wangale gate din da sauri motar ta shigo
gidan.
Har suka kusa airport Khalil kallon Nihad yake, ita kuwa taki barin su hada ido,
can dai yayi kasa da murya yace "Ko mu bar tafiyar gobe kawai?" Sai a sannan ta
kallesa amma bata ce komai ba don gaba daya she is feeling her body so weak and
she's been sopping tun barinsu gida, ya kara yin kasa da murya yace "Ai baki gaji
da kanon ba ko?" Ta gyada kai a hankali tace "Ehh" Yace "Mu koma kawai a bari gobe
in sake wani booking din kenan?" Nan ma a hankali tace "Ehh" Yace "Ohk" Sai kuma ya
kalli Iliya yace "Baba juya kan motar kawai" da ladabi Iliya yace "Zuwa ina ranka
shi dade??" Khalil yace "Kawai nemi waje kayi parking kada a baka wahala, bari inyi
driving din da kaina" Yace "Ahh haba ranka shi dade ai mun saba, shekaru talatin da
suka wuce trailer nake ja daga nan arewa zuwa legas" Khalil yace "Kai dai yi
parking kawai Baba" Ba musu yayi parking gefen hanya, Khalil ya sauka ya tafi
driver seat din, Iliya ya koma daya gefen, Khalil ya ci gaba da driving din.... Da
mamaki Nihad ta dinga kallon dai dai inda Khalil yayi parking bayan tafiyar kusan
minti talatin da biyar da suka yi, Yana kallon Iliya yace "Nan za mu sauka baba,
sai ka koma gida" Dubu goma ya ciro ya basa, Iliya ya amsa ya dinga godiya ya sauka
daga motar ya dawo driver seat bayan khalil ya sauko, Khalil ya bude back seat yana
kallon Nihad, ta wani hade rai tace "What is the meaning of this?" Yace "Kina bata
ma Baba lokaci" Zata yi magana ya kamo hannunta zai sauko da ita daga motar, ganin
haka ta sauko da sauri, ya kulle motar ya daga ma Iliya Hannu, Iliya ya ja motar ya
bar wajen, Nihad ta daga kai tana kara kallon Bristol Hotel wanda ta zo sau ba
adadi da su Husnah, ji tayi ya kama hannunta ta bi sa zuwa cikin hotel din tana
tafiya a hankali......
Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

*Ina kuke ma'abota kamshi?😁😁 To Ku matso kusa, Albait Al Sahal sunzo muku da
hadaddun turarukan wuta na gida, na jiki da kuma ns kaya. Akwai perfumed body oils
masu dadin kamshi da sanyaya zuciya. Akwai spritz Wanda Ko bakiyi turaren wuta ba
ya isheki ga yana dadewa a wuri bai fita ba, Maza ku garzayo Albait Al sahal domin
Ku Sami naku Cikin sauqi domin yanxu suna sales komai ya sauqaqa.... Duk wacca ta
siya beyi mata ba ta dawo dashi # we trust the quality of our products# contact me
via WhatsApp 09084473900*💖 NIHAAD 💖

64

Nihad na shiga dakin hotel din ta zauna gefen gadon dakin a hankali, ya ajiye
wayoyinsa ya kalleta yace "Will be right back" Ita dai bata ce masa komai ba ya
nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita dakin, bin dakin da ba bakonta bane ta
dinga yi da kallo, memories da bata son tunawa suka dinga dawo mata, lokaci daya
tayi saurin kauda tunanin cause it's making her sad, ta jinginar da kanta a hankali
jikin gadon ta lumshe ido... Can dai ta gyara zamanta da sauri, ita dai tasan ba
lokacin period dinta bane but she is feeling as if her period just came, beside sai
tayi wata hudu ma bata yi period ba ita, tashi tayi ta tafi bandakin amma sai ta ga
opposite dinsa, bayan few minutes ta fito ta dawo ta zauna gefen gado, wayarsa da
ya ajiye side drawer ya fara ring, ta juya tana kallon wayar taga Nadeey a jikin
screen din, ta dinga kallon wayar ko kiftawa babu, lokaci daya ta wani hade rai,
sai kuma ta dau wayar tayi rejecting kiran, sake kira tayi nan ma ta kara
rejecting, sun yi hakan sau uku, ganin bata sake kira ba ta mayar da wayar ta
ajiye, wani sabon tsanarta kawai take ji a zuciyarta duk da dai bazata ce ga abinda
ta taɓa mata ba, but she hate her with passion, dai dai nan aka bude kofar dakin ta
daga kai tana kallonsa har ya shigo, ya ajiye ledan hannunsa ya cire agogon wrist
dinsa sannan ya shiga bandaki, alwala yayi ya fito, ta bi sa da ido har ya sake
fita daga dakin don an kira isha, mikewa tayi ta shiga bandakin ita ma tayi alwala
ta fito tayi sallahn, tana idarwa ta jawo ledan da ya ajiye ta bude, gasasshiyar
kaza ce sae kamshi take, ga fresh yoghurt me sanyi da kwalin lemo a wani ledan
daban, babu bata lokaci ta fara aika kazar inda ya kamata, tana ci tana korawa da
chilled drink din, sai da taji ya fita kanta tsabar cin da tayi masa sannan ta
ajiye wanda ta rage ta shiga bandaki ta kuskure bakinta ta fito ta hau gado ta
kwanta. Wajen karfe tara ya shigo dakin da karamin akwati wanda ke dauke da sabon
abaya da ya siya mata guda biyu da duk wani abinda zata bukata gobe kafin su tafi
Abuja, sae na shi kayan shima, ya ajiye akwatin yana kallonta don rufe ido tayi
kamar me bacci, ya zauna gefenta ya kai fuskarsa nata, murya can kasa yace "Are you
sleeping?" Bude ido tayi a hankali tana kallonsa, ya dagota ta zauna sannan ya jawo
ledan kazar da ya ajiye yace "I bought..." Kallonta yayi da sauri ganin ɗan abinda
ta rage a ledan, ta turo baki ta juya masa baya ta koma ta kwanta, ɗan murmushi
yayi ya mike ya tafi bandaki bayan ya dau sabulun da ya siyo, babu yanda Nihad ta
iya haka ya tilastata sai da ta sake yin wanka ita ma, tana fitowa bandakin ta ga
kayan baccin da ya ajiye mata gefen gadon shi kuma yana zaune daya side din gadon
sanye da wandon pajamas kawai, yana danna wayarsa with full attention, kana ganinsa
kasan text yake rubutawa, bata sake kallon kayan da ya ajiye mata ba, ta jawo
handbag dinta ta dau turarrukanta ta shafa sannan ta dau hijab dinta ta saka ta yi
kwanciyarta ta juya masa baya... Ya gama rubutun text din da yake ya tura sannan
yasa wayar a flight mode ya daga kai yana kallon Nihad, mikewa yayi ya kashe wutan
dakin ya dawo inda take facing ya kwanta, da sauri ta mike zata bar wajen amma ya
jawota jikinsa murya can kasa yace "Bayan kazata da kika cinye? Who told u it's for
free??" Ta marairaice tace "Ni kaina ciwo yake min, ina son inyi bacci" Yace "Ohk
zaki yi bacci, but we need to talk now" Bata ce masa komai ba, a hankali yace "Are
you ready?" Duk da ba ganin fuskar juna suke ba sai saukan numfashinsa da take ji a
fuskarta ta daga kai tana kallonsa cikin duhun, kwantar da ita yayi a faffadan
kirjinsa yayi wrapping dinta da hannunsa, bata san sanda ta lumshe ido ba tana
numfashi a hankali, yayi kasa da murya yace "Few months ago, i saw u in Bristol...
ke da wani gaye, me ya kawo ki?" Nihad ta bude idonta da sauri, tayi shiru tana
nazarin abinda yace, gaye kuma?? wani gayen? Ita dai tasan duk yawonta da tayi a
baya bata yi da maza sai dai su Husnah, then wani guy din yake magana akai? Ya
katse mata tunaninta yace "Answer me" a hankali tace "I can't remember" Yace "You
just have to remember..... He is tall and dark" Tayi kokarin tuna guy din amma
hakan ya faskara, ta girgiza masa kai cikin sanyi tace "Na manta, i am always
coming here together with Husnah and her clique... I don't know the guy are talking
about, or probably suna ciki zanje in samesu ne" Yace "I see, amma me ke kai ku
hotels? All the hotels in kano babu wanda baki taɓa zuwa ba" Ta ɗan yi shiru,
lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, yace "Ina jin ki" Ta rufe idonta don kawai
sai taji kunyar tambayar nasa, how did he know tana zuwa hotels bayan ita dai bai
taɓa kai ta ba, yaushe ma har ta tsaya suka yi shiri da shi balle ya kai ta hotels,
Habibu ne me kai ta hotel wani lokacin har ya jirata ko kuma yaje ya dawo, she felt
so ashame of his question, cike da karfin hali ce "Ba komai, kawai dai wani lokaci
Naf tana kama daki sai mu je can saboda constant Power, and ita tana son waje me
Ac, after that babu wani abinda ke kai mu hotel" Yace "Kema saboda constant Power
din da Ac kike bin su bayan na gidan ku?" Tayi shiru kamar baxata ce komai ba, sai
kuma tace "Ai dai ba wajen maza mu ke zuwa ba...." Yace "Babu warce bata zuwa wajen
maza a kawayen naki, kema kuma kin sani" Tace "Ehh, but that's their life, ni nasan
ba wajen maza nake zuwa ba Allah ma ya sani...." Yace "The Codeine,
Prophylactics...." Ta runtse ido da sauri gabanta na faduwa, lokaci daya taji kunya
ya rufeta, girgiza masa kai tayi tace "Na Husnah ne, kuma ban san ta sa a jakana ba
ranan, they are not mine i promise u...." Yace "Alcohol???" Ta bude ido a hankali,
he could feel how her heart is beating so fast a kirjinsa, tayi karfin halin cewa
"They lured me into taking it, amma bana sha wallahi, kuma ban taɓa sha ba, Allah
shine shaidata" Muryarta na rawa ta kare maganar, yayi shirun kusan minti daya, sai
kuma yace "What did u know about that Video?" Ta girgiza masa kai cikin sanyin
murya tace "I know nothing about it" Yace "Amma kinsan inda aka yi Video din ae"
Tace "I saw it just once, so i can't even remember how it is..." Yace "Ohk, idan
mun koma Abuja you will still have to see it for the second time because u need to
figure out where d video was done" lokaci daya hawaye ya cika idonta tace "Ni bana
son in sake gani, na bar ma Allah komai, koma waye yayi min na bar shi da Allah"
Yace "No zaki sake gani, sannan zaki duba da kyau kiga a ina ne aka yi video din"
Bata kuma ce masa komai ba, yaji saukan hawayenta a kirjinsa, lumshe ido yayi, ta
dinga shessheka a hankali a jikinsa.... abubuwan da take ta ignoring a zuciyarta
daxu su yake tambayarta yanzu and she have no choice then to give him answers to
his question, she wish mutum na iya gyara past dinsa, she wish zata iya amending
past mistakes dinta na rayuwa, but it's just too late, Bai hanata ba ya bar ta tayi
kukanta for few minutes kafin ya fara cire mata Hijab din dake jikinta a hankali,
da sauri ta dago don she is wearing just undies, ta rike hijab din taki bari ya
cire, murya can kasa yace "Take ur hands off it" sae da ya sake maimaita
instruction din nasa sannan ta sake Hijab din a hankali, ya cire ya ajiye gefe, and
he made sure he left her with nothing, ta dinga nonnoke masa tana son stopping
dinsa amma ta kasa, daga karshe she realized her body is just too weak for her to
stop him, and her body is welcoming duk abinda yake mata, ta gane cewar she is
liking it, Romance irin wanda ke nuni da akwai tsananin so na gaske between the
couples ya shiga yi mata as if his life depends on it, ba kowa ke samun matsayin
kalan romance din ba sai wanda ake so har cikin zuciya, ai ko ta sakar masa jiki
gaba daya ba tare da ta ma san ta yi hakan ba, he made sure she savor every bit of
it, duk sai da ya birkita mata lissafi ya rikitata kamar yanda shi ma ya rikice
telling her all what his mouth can, kyauta kam sae wanda ya manta ne bai mata ba a
wannan moment din, kiris ya rage bai bata kanon gaba daya ba a kora su Chamo Zaria,
and that night will always be a memorable night for them both, a night that will be
worth remembering.....
Har kusan karfe daya yana aikin lallashin shagwabar da take ta zuba masa tana kara
narke masa a jiki, daga karshe ya samu dai tayi bacci, mikewa zaune yayi bayan ya
kwantar da ita ya kunna wutan dakin yana kallonta feeling so blessed, a karo na
farko yaji kamar babu wani sauran damuwar dake tare da shi a rayuwa, he felt so
relieve kamar ya sauke wani burden daga kansa, yaji ya kara samun kwarin gwiwan
yanda zai tunkari sauran challenges dinsa babu fargaba, they all slept like a baby
throughout the night suna makale da juna. Da safe Nihad ta kasa hada ido da shi
tana zaune far end of the bed bayan ta gama shiryawa, wani mugun kunyarsa taji take
ji, she just don't know what came over her yesterday night duk da dai farkon
lamarin ta wahala sosai amma daga baya sai ya zama opposite of it, idan ta tuna
yanda ta dinga masa expressing feelings dinta sai taji kamar ta nutse, Khalil na
lura da ita, ya dai gama shirinsa ya dawo kusa da ita ya zauna yana kallonta with
smile all over his face, still taki bari su hada ido sai ma sunkuyar da kanta da
tayi, she wish kasa zai bude mata ta shige, yayi kasa da murya yace "Ko mu bari sai
gobe?" Ta daga manyan fararen idanuwanta tana kallonsa, they stared at each other
for almost 30 seconds babu ko kiftawa, ko wanne da tunaninsa a zuciya, kuma babu
wanda ya dauke idonsa a cikinsu, a hankali ya hade goshinsa da nata breathing
slowly, yayi pressing nose dinsa to her's, bata ankara ba sai jin bakinsa tayi a
nata, nan kuma labari ya canza, ashe jiya da daddare bata ga komai ba, don kuwa
this time around sai da yaga she can't take it anymore duk tayi laushi sai hawaye
take masa sannan ya hakura ya kyaleta, ya rungumeta sosai ya ja masu duvet yana
lallashinta, daga ita har shi a haka bacci ya daukesu, sai kusan Azahar Khalil ya
farka, ya zaro ido yana duba agogo a wayarsa don flight din karfe sha daya yayi
masu Booking, shikenan kuma sai dai wani flight din don yasan sunyi missing wannan,
ya kwantar da ita a hankali ya sauka daga kan gadon ya shiga bandaki... Still that
same day ya sake masu Booking wani flight din karfe shidda na yamma. Nihad ta daga
kai tana kallonsa bayan ya shigo dakin wajen karfe hudu da rabi, ya karaso ya zauna
gefenta ya ajiye ledan hannunsa yace "Baza ki sake cin abinci ba?" Girgiza masa kai
tayi tana avoiding eye contact da shi, ya dau ledan da ya ajiye ya mika mata yana
kallonta, kallon ledan ta dinga yi babu ko kiftawa, can ta sa hannu ta karba ta
ciro abinda ke ciki, kwalin latest iphone ta gani wanda bai jima da fitowa ba, ta
daga kai da sauri ta kallesa cike da mamaki, ya sakar mata murmushi me narkar da
zuciya, ta ma rasa me zata yi, amsar kwalin yayi ya bude yayi emptying dinsa, ya
daura mata sabuwar wayar a cinyarta, lumshe ido tayi, kana ganinta kasan she is so
happy, kawai sai gani yayi ta rungumesa tightly, murya can kasa tace "Thank you so
much" ya kai bakinsa kunnenta as if whispering yace "I... I.. love u" Lokaci daya
hawaye ya cika idonta amma bata iya ta ce masa komai, they remained like that for
almost 5 minutes, can ya saketa ya mike yace "Let not miss our flight again" Yana
fadin haka ya fara tattara kayansu dake dakin cikin trolley, cikin minti kadan ya
gama ya dau wayarsa yace "Bolt will be here in few minutes" Ya dau sabon wayar ya
saka mata a jakarta, kwalin kuma ya saka a trolley, sannan ya mika mata hannunsa,
ta daga kai ta kallesa sai kuma ta mika masa nata hannun ya dagota suka nufi
kofa.... Karfe bakwai da rabi suka sauka airport din Abuja, nan da nan Mood din
Nihad ya canza, bata sake shiga tashin hankali ba sai da ta ga unguwan da suka
shigo, shi dai yana rike da hannunta a cikin motar, lokaci daya hawaye ya kawo
idonta amma bata bari ya gani ba, me bolt din ya tsaya dai dai kofar gidansu
Khalil, Khalil ya bude motar ya sauka, ita ma ta fito daga motar, Mai bolt din ya
sauke masu trolley dinsu, Khalil ya dauka yana rike da hannunta suka shiga gidan,
basu tadda kowa babban parlon gidan ba har suka iso bangaren Mami, ba mood din
Nihad kadai ya canza ba har shi mood dinsa ya sauya, ga wani faduwa da gabansa
yake, wani shakkar Maminsa yake ji a ransa, ya shiga parlon Nihad na biye da shi,
har zuwa second parlor din Mami, ya ajiye trolly din hannunsa ya karasa bedroom
din, Nihad ta rakube jikin kujera feeling so sad, a hankali yayi sallama kofar
dakin amma bai shiga ba, Mami ta bude kofar jin sallama, ta tsaya tana kallonsa, ya
sunkuyar da kansa gabansa na faduwa, da ladabi yace "Ina yini Mami" a takaice tace
"Lafiya lau" Daga haka ta juya ta koma bedroom dinta, duk Nihad na kallonsu, ita ma
jikinta yayi sanyi lokaci daya, ya ɗan tsaya for few seconds a bakin kofar kafin ya
karasa cikin dakin ya kulle mata kofar a hankali, saman kujera ya ganta zaune ya
karasa har gabanta ya durkusa yace "I know i wronged you Mami amma don Allah kiyi
hakuri ki yafe min, kar fushinki ya shafeni" Mami tace "I don't have any problem
with ur stupid act Khalil, kuma bana ma son zance.... Don haka spare me!!!" Ya kasa
dago kansa, bayan wani lokaci yace "Kiyi hakuri don Allah Mami" Tace "Baka ji
abinda nace maka bane?" Yayi shiru bai ce komai ba, can ya mike a hankali ya juya
ya fita daga dakin, yana fitowa parlor ya kalli Nihad dake kallonsa yace "Ki shiga
ciki ki gaida Mami" Bata ce komai ba ta mike tana tafiya a hankali ta isa kofar
dakin tayi sallama, Sai da Mami ta amsa mata sannan ta shiga ciki, dai dai inda
Khalil ya durkusa ta duka kanta a kasa tace "Mami ina yini?" Mami tace "Lafiya lau,
ya kika baro mutan gidan?" Nihad tace "Lafiya lau" Mami tace "Toh madallah,
sannunku da zuwa" Nihad bata kuma cewa komai ba, Mami ma haka, tana ta durkushe
kasan, Mami tace "Kinyi sallah ne?" Ta girgiza kai ba tare da ta dago ba, Mami tace
"Ki je kiyi" Mikewa tayi ta juya ta fita daga dakin, bata ga Khalil a parlon ba, a
sanyaye ta shiga bandakin dake parlon ta dauro alwala.... Tana idar da sallah ta
mike zata dauke sallayar Mimi ta shigo parlon, Mimi ta wara ido ta nufeta da sauri
ta rungumeta cike da farin cikin ganinta tace "Welcome Nihad" Nihad ta mata
murmushi tace "Nagode"
Khalil na fita parlon Mami dakinsa ya tafi yayi alwala yayi sallan Magrib sannan
yayi wanka ya shirya ya dau makullin motarsa ya fita daga gidan zuwa gidansu
Nadeeyah... Yana ta zaune compound bayan yayi Knocking ya gaya ma mai aikin gidan
tayi masa sallama da Nadeeyah, don dama in yaje gidan a waje suka fi zama, amma for
almost 30 minutes bata fito ba gashi ya kira wayarta a kashe, mikewa yayi daga
karshe ya sake komawa kofar parlon gidan ya bude a hankali yayi sallama ya shiga,
babu kowa parlon ya zauna saman kujera, yana jiran fitowar mai aikin, bai jima
zaune parlon ba sai ga Hajiya Safeenah zata kitchen, da mamaki take kallonsa, suka
gaisa sannan ta tafi dakin Nadeeyah, bayan almost 5 minutes sai ga Nadeeyah ta
fito, Ta karaso cikin parlon kanta a kasa, ta zauna saman kujera bayan ta gyara
mayafin jikinta tana wasa da zoben hannunta, bata dai ce masa komai ba, yayi kasa
da murya yace "I am sorry Nadeeyah, this is all i can say to you" Lokaci daya
hawaye ya cika idonta ta girgiza masa kai tace "It's ohk" Dafe kansa yayi ya ma
rasa ta ina zae fara, infact he is just lost of words, can ya dago kai cikin karfin
hali yace "Kin dai san ina sonki ko Nadeeyah??" Ita dai bata ce komai ba sae
hawayen dake sauka idonta, yayi kasa da murya yace "Toh kiyi hakuri let accept
things the way God ordain it, i never bargained for all that has happened, Allah ne
ya kaddaro min duk wannan abun, albarkacin son da kike min kiyi hakuri ki taya ni
mu rungumi kaddarata tare Nadeeyah, in sha Allah kuma baxan mance halaccinki gareni
ba wannan alkawari ne na maki, i am begging you kiyi hakuri don Allah Nadeeyah"
Hawaye kawai ke sauka Idonta ta kasa cewa komai, lokaci daya jikinsa yayi sanyi,
Nadeeyah have sacrificed a lot because of him, tayi masa halaccin da ba ko wace
budurwa zata iya yi ma saurayinta ba, he knows she doesn't deserve this, mikewa
yayi ya dawo kusa da ita ya zauna, cike da damuwa yace "Plss ki daina kukan nan
haka Nadeeyah, u are making me feel guilty, nasan ban kyauta da na boye maki
abubuwan nan ba duk yanda muke dake, but ina son kiyi considering cewar even Mami
ban iya na gaya mata ba saboda ban son bacin ranta, kema gudun ɓacin ran naki ne
yasa na boye maki, but trust me Nadeeyah kina da special place a zuciyata har
kullum har gobe, kiyi hakuri ki tayani mu rungumi kaddarata kamar yanda kika saba
min a baya, ni kuma in sha Allah zan zamo me adalci gare ki, i am indebted to you
Nadeeyah.... Kamo hannunta yayi sanin fa baxata ce masa komai ba, don in har tana
kuka bata iya cewa komai, yayi kasa da murya yace "Send me the amount you need na
duk abinda za kuyi da kawayenki na biki in tura maki, if there is anything after
that ki gaya min" Mikewa tayi tana goge hawayen idonta tace "Zan yi isha'i" Tana
fadin haka ta juya ta bar parlon ya bi ta da kallo, gaba daya jikinsa yayi sanyi,
shi kansa yasan bata yi deserving haka daga garesa ba, but ya zai yi shi ma bai
taɓa tunanin things will turn out this way ba, yana ta zaune for almost 10 minutes,
can ya mike a hankali ya fita daga parlon duk jikinsa a sanyaye. Har khalil ya kusa
gida bashi da rest of mind, parking yayi jin Convoy din Janar sun shigo unguwan, ya
jira har suka wuce sannan ya ci gaba da driving dinsa a hankali, Ya jima zaune
cikin motar bayan yayi parking kafin ya bude ya sauka ya shiga ciki walking slowly,
direct ya tafi bangaren Mami, babu kowa first parlon ya karasa daya parlon ya bude
ya shiga, Nihad kadai ce zaune ga abinci a gabanta amma bata taɓa ba, daga sama har
kasa take kallonsa don fararen kaya ne jikinsa sae zuba kamshi yake, sai kuma ta
dauke kai, ya karasa cikin dakin yace "Why are you not eating" Ta hade rai bata dai
ce masa komai ba, ya durkusa gabanta ya bude abincin dake tiriri, plate ya dauka ya
zuba mata abincin with enough meat, ya dau cokali ya deba ya fara kai bakinsa ya ci
kadan sannan ya kai mata baki, dai dai nan Mami ta shigo parlon, makalewa yayi
wajen gashi ya kasa sauke spoon din daga kusa da bakinsa, ita kanta Nihad ji tayi
kamar ta nutse, ta kasa dagowa balle ta kalli Mami, wayarsa dake aljihu ya fara
ring ya ciro da sauri, yaga Abbansa ne ke kiransa, ya ajiye cokalin ya daga ya kai
kunne, Janar na gama fadin abinda zai fada ya katse wayarsa, Khalil ya juya a
hankali yana satan kallon Mami ya ga ankon lafiyayyen lace na su na iyaye take
kirgawa zata fita da shi, mikewa yayi kansa a kasa ya fita daga parlon, bangaren
Abbansa ya tafi, ya zauna saman Kujera yana kallon Janar yace "Good evening sir"
Janar yace "So now, how did my 800M vanish Ibrahim?" Khalil yace "I don't know"
Janar yace "U don't know? Kar ka manta u asked for 300M 2 days before and i refused
giving you, cause i am still yet to see the outcome of wa enda na baka a baya,
bayan kwana biyu kuma my 800M went missing, kai ka shigo min da shi gidan nan ba
wani ba, kai kadai kasan da kudin, ko uwarka da Amina basu sani ba, only you have
the access to my safe in this house, ba kuma wanda ke shigar min that particular
room banda kai, in kudi na baka for joint business sai dai kawai ka salwantar min
da kudadena, anyi hakan yafi a kirga, in dai zan dauraka akan Business tohh that
business will neva go smoothly...." Khalil yayi shiru yana kallonsa, can a hankali
yace "But it's always not my fault, i do use to try my best but ban san meke faruwa
ba" Janar yace "Shi Aliyu kai biyu garesa idan na daurasa kan kasuwancina
kasuwancin ke tafiya smoothly ban taɓa daurasa kan abu nayi asaran ko naira biyar
ba ko in ga ba dai dai ba, kai ko in sha Allahu sai ka salwantar min da kudade, and
now u want me to believe ba kai ka dau min kudina ba?" Khalil bai kuma ce masa
komai ba, Janar yace "Toh me kayi da 800M wanda u still have to end up driving daga
karshe?" Da sauri Khalil yace "Ni ban san komai kan kudinka ba, and ni ba don na
rasa kudi naje driving ba, i can fend for my self for years to come ko da ban yi
driving ba...." Janar dake kallonsa keenly yace "With whose money zaka yi fending
for ur self bayan ur account was frozen then?" Khalil yace "Mami never left me like
that, haka Aunties dina...." Janar ya tabe baki yace "Har gobe bazan daina cewa kai
ka dau min kudina ba...." Khalil dai kallonsa kawai yake, can yace "Toh shikenan,
ina fatan wataran gaskiya ta bayyana ka gane ban dau maka kudinka ba" Janar yace "I
am sending u 20M now, kudin lefen both matan naka..." Khalil na kallonsa yace
"Allah ya kara budi" Janar yace "Are they going to be staying together or
seperately?" Khalil ya sauke kansa yace "Duk yanda Mami ta ce" Janar yace "Oh ohk,
Mamin zata zauna maka da su kenan?" Ya girgiza kai yace "Kawai shawara zan yi da
ita" Janar yace "It's left to you... Zaka iya tafiya" Khalil yace "Nagode" Daga
haka ya mike ya fita daga parlon, direct dakinsa ya koma, yana zaune gefen gado
with different thought running his mind sai ga Alert din 20M daga Janar, shi bai ma
san yaushe ne bikin ba kuma bai san wanda zai tambaya da bazai yi misperceiving
dinsa ba, tashi yayi daga karshe ya koma bangaren Mami, ita kadai ya tarar a
parlonta tana waya da Aunty Maryam da ta tafi gun dangin mijinta dazu da yamma,
yana ta zaune har ta gama wayar ta ajiye, kallonta kawai yake ganin bata ko kalli
inda yake ba, can ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Mami Abba ya saka min 10M
yanzu na lefen Nadeeyah, toh ban san ko basu za ayi ba ko a nan za a hada kayan"
Mami tace "Baka da number Nadeeyan ne yanzu?" Yayi shiru yana kallonta, can ya
girgiza kai a hankali yace "No... kawai shawara nake yi da ke ne kafin in mata
magana" Mami tace "Toh kayi magana da ita ni ba maganar da zaka min" Bai kuma ce
mata komai ba, ta dau wayarta da ya fara ring ta daga ta kai kunne, hakan ya sa ya
mike kawai ya fita daga parlon, dakin da Nihad ke zama a gidan ya nufa ya bude
dakin yaga ba kowa ciki, yana ta tsaye yana imagining inda take, to ko tana bedroom
din Mami ne, can dai ya tafi bangaren Mimi to ask her yaushe ne bikin, Knocking
yayi kafin ya bude kofar yana kallon cikin dakin, Bai ga kowa dakin ba amma ga
trolley din kayan Nihad which means she is here, dai dai nan Nihad ta fito daga
bandaki daure da towel tayi wanka, ya karasa shigowa dakin ya kulle kofar, lokaci
daya ta hade rai zata dau Hijab dinta yayi saurin daukewa a wajen ya jawota jikinsa
murya can kasa yace "Kin ci abincin kuwa?" Taki ce masa komai fuskarta a daure, a
hankali yace "Ko an maki wani abu ne?" A takaice tace "Ina ka je da farin kaya
dazu?" A tsakiyar kansa yaji tambayar da ta jefo masa kamar dai ba ita ba, he
wasn't expecting such question from her, ya ɗan buda ido yace "Ba inda naje, i...
I... I met with a long time friend a cikin anguwan nan, ance maki naje wani waje
ne?" Lokaci daya hawaye ya kawo idonta tace "Ban yarda ba" Ya rungumeta so that she
won't see the smile on his face, yana murmushi sosai yace "Toh ina zan je bayan
kina cikin gidan nan?" Muryarta na rawa tace "Wajen budurwarka kaje ai na sani" Ya
dago kanta ya wara ido yace "Ina da wata budurwar bayan matar da aka aura min
dama??" Bai jira tace komai ba ya fara kissing dinta passionately, duk ta rikice
tana son kwace kanta ya ki saketa sai ma upgrading da yayi daga kiss din, muryarta
na rawa tace "Don girman Allah kayi hakuri kar Mimi ta shigo, yanzu zaka ga ta
shigo...." kamar me rada yace "Toh za ki bi ni dakina?" Ta marairaice tace "Ai
baxan iya ba, za a ganni" Bai kuma sauraronta ba ya ci gaba da abinda yake mata,
tun tana ce masa kar Mimi ta shigo har dai ita ma ta dauke light ta sakar masa
jiki. Daga ita har shi suka mance a ina ma suke.... kasa hada ido tayi da shi daga
karshe ta rufe fuskarta jikinsa cike da jin kunyarsa, murya can kasa yana rungume
da ita yace "U are the best thing that have ever happened to me, and i now
appreciate the reason i left home, i appreciate my pass...." Ita dai tayi lamo
jikinsa tana jin kamar bacci zai dauketa, Murda kofar dakin aka yi Nihad ta mike
zaune da sauri tana zaro ido, wani ajiyar xuciya ta sauke ba tare da tasan tayi
hakan ba, ashe yasan
ya saka ma kofar makulli shi yasa hankalinsa kwance yayi abinda yake so, ta
marairaice zata sauka daga kan gadon ya jawota yace "She is gone, plss tell me the
name of ur perfume" shiru tayi ta kasa bari su hada ido, ya dago kanta yana kallon
kwayar idonta murya can kasa yace "Tell me" a hankali tace "I will..." Tana fadin
haka ta jawo towel dinta ta sauka daga saman gadon ya bi ta da kallo babu ko
kiftawa har ta shiga bandaki ya sauke wani ajiyar zuciya yana sauke numfashi a
hankali, bai kara minti uku ba a dakin shi ma ya fita ya tafi dakinsa da sauri...
Ko da Mimi ta dawo dakin Nihad na kwance ta rufe har kanta da duvet, gani take
kamar Mimi zata gane wani abu, Mimi dai bata ce mata komai ba don dakin banda
kamshin turaren yayan nata babu abinda yake, ta koma daya side din gadon ganin
agogonsa a kasa ta dauka ta ajiye a hankali kan bedside drawer sannan tayi
Kwanciyarta ta kashe wutan dakin, Nihad ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya jin
bata mata magana ba, don da tayi ma bazata kulata ba she will pretend she is
sleeping. Washegari da safe Khalil ya shigo bangaren Mami don gaisheta, Bayan ya
gaida Mami ya kalli Aunty Maryam dake kallonsa, sunkuyar da kai yayi ya gaisheta
ita ma, ta taɓe baki ta mike tace "Mu koma dakin naka dama yanzu nake son in bi ka
can" Ya mike ya bi bayanta suka koma dakinsa, Ta zauna gefen gado tace "Kai yanzu
ka kyauta abinda kayi Khalil? Me zai kai ka kayi abu kanka tsaye?" Zai yi magana ta
dakatar da shi tace "Daga baya kenan Khalil, ba wani abinda zaka fada da zai yi
justifying foolishness dinka, ka riga dai kayi abun ka kai tsaye, ur father is
supporting you because he is a Man, kuma dama ku maza mentality dinku daya" A
hankali yace "Ku yi hakuri Aunty" Tace "Aa ni dama nayi, duk da yanda daga kai har
Nihad din kuka mayar da ni yar iska har nake hadata da wani saurayin su yi waya, to
laifi akan ku, don Allah ya gani ban sani ba" Khalil bai san sanda yayi murmushi
ba, Aunty Maryam ta jefa masa wani kallo, ya zauna gefenta a hankali yace "Wallahi
Aunty ban san ta yanda zan ce ma Mahaifinta a'a ba a sanda ya bani aurenta, kema
kinsan da nauyi, kuma kinga ai baxan ce zan kawosa gidanmu ba ga issue that is on
ground..." Aunty Maryam ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh Allah ya baku zaman
lafiya, Mami kuma sai kayi ta lallabata har ta hakura gaba daya, kasan fushin uwa
bala'i ne babba, don haka kayi ta bin ta har dai ta sauko, sannan kudin da Janar ya
tura maka na lefen Nadeeyah kawai ka tura masu su siya duk abinda suke so, yanzu
haka ake yi gaskiya" Khalil yayi shiru sai kuma a hankali yace "Aunty har da na
Nihad ya bada amma ban gaya ma Mami bane kawai" Aunty Maryam ta kallesa tace
"Nawa?" Yace "Ita ma 10M" Aunty Maryam tace "Maa sha Allah, hakan yayi kyau sosai,
ita ma ka tura ma iyayenta su yi mata lefen, ba sai ka sanar ma Mami ba may be daga
baya zaka iya gaya mata, but for now don't say anything to her" Yace "Toh Aunty,
and Abba yayi min magana ko hadasu zan yi nace sai nayi shawara da Mami" Aunty
Maryam tace "Aa gaskiya baza ka hadasu ba, noo it's not even possible, ita Nihad ka
bar ta a gidanka, Nadeeyah kuma ka nemi gida ka kama mata kawai, bikin ma ai an
kara 2 weeks dazu Mami ke gaya min" Yace "Ohk i don't know about it" Aunty Maryam
tace "How will u know dama bayan wannan gurmin da ka hada" Murmushi kawai yayi,
Aunty Maryam ta mike tace "Bari in je, za mu fita ne da Mami yanzu" Yace "Toh Allah
ya tsare" Tace "Ameen, sai ka kira iyayen nata ka tura masu kudin yanzu" Yace "In
sha Allah" Bayan Aunty Maryam ta fita daga dakin Khalil yayi dialing number Aunty
Jamila, Aunty Jamila dake zaune parlon Umma tare da Mumy ta shigo yi ma Umma
sallama zata koma Jigawa, Inna ma zuwanta kenan ta zo duba Umma da er ayabarta
kwaya uku da lemu daya, Jamila ta ciro wayarta ganin Khalil ke kiranta ta daga hade
da sallama, bayan sun gaisa Khalil ya sanar mata dalilin kiran nasa, Aunty Jamila
ta buda ido speechless at first, sai kuma tayi saurin cewa "Ahhh to maa sha Allah,
maa sha Allah, Allah ya kara arziki, zan tura maka account din Mumy" Daga haka suka
yi sallama ta katse wayar ta kalli Mumy cike da mamaki tace "Aunty Khalil ne ya
kirani yanzu, wai Babansa ya bada miliyan goma a hada ma Nihad lefe, shine zai turo
mu hada a nan" Umma tayi kuri tana kallon Aunty Jamila babu ko kiftawa, dama tunda
suka shigo ko um bata cewa balle um um, duk ta zama wani iri kamar warce ta dade
tana jinya, kana ganinta kasan hankalinta baya tare da ita, tana cikin tsananin
damuwa, hatta Mumy har lokacin Abba bai kai ga sanar mata babu aure tsakaninsa da
Umma ba don ita ce da girki banda yau da zata ajiye Umma ta dauka, kuma yau din ma
sai dare yake da intention din sanar mata, Inna ta mike tana kallon Aunty Jamila
tace "Waye Khalil?" Aunty jamila na murmushi tace "Mijin Nihad, wai babansa ya bada
miliyan goma a hada mata lefe shine zai turo mana mu hada a nan" Inna ta fashe da
kuka ta koma ta zauna, sai kuma ta saki kabbara da karfi tace "Allah mun gode maka,
Allah mun gode maka" Mumy na kallon Aunty Jamila tace "Jamila maimakon su hada
kawai a can har sai an turo kudi nan, ina ga ba gwara kice kawai su yi a can
ba...." Inna ta saki baki tana kallonta, can a fusace tace "Ke dai har yau baki da
wayewa Maryam, ai yanzu iyayen mace ake ba kudi su hada mata kaya, salon a bar masu
miliyan goma su cuceta su ki siya mata abinda ya kamata saboda bakin ciki? Yo ko
wannan figaggiyar baƙar shegiyar ta isa ta raba kudin biyu ta boye rabi, wannan din
nan da suka ce uwarsu ce kawai daya da Janar din, su turo kawai nan duk za mu siya
mata kaya na gani na fada na kece raini, wanda babu wanda zai ce Ibrahim ne ya
haifeta, ai tunda Allah ya tsameta daga cikinmu ya mayar da ita cikin masu
fitinannen kudi ita ma shiga zata dinga yi kamar yar sarki, in sha Allahu kayan da
za mu siya mata sai ya girgiza su wllh, yanda babu wanda zai raina min jikata a
gidan, ana gama hada kayan kuma a hadani da dreba in kai har Abujan, nima zan kara
dubu goma ta akan kudin a hada da miliyan goman duk a mata siyayya, da kyar idan ba
sai mun siye kwari ba" Aunty jamila tace "Kwarai kuwa Inna, kaya sai wanda bamu
gani ba a kasuwa ne baza mu siya mata ba, in sha Allah zamu hada mata kaya na gani
na fada...." Aunty jamila na fadin haka ta tura ma Khalil account din Mumy, babu
bata lokaci kuwa ya sako masu 10M din, Umma dai ta zama er kallo a parlon sai bin
su kawai take da ido ba bakin magana, a zaune take amma dishi dishi take gani.....
Wajen karfe sha daya khalil ya koma bangaren Mami, he still wants to tell her he is
sorry, fushin nan da take da shi ya sa ya kasa samun nutsuwa, ita kadai ya samu
bedroom dinta ya duka kasa ta juya tana kallonsa tace "Lafiya??" Ya marairaice mata
yace "Don Allah Mami kiyi hakuri ki yafe min, wallahi bazan samu nutsuwa ba idan
kika ci gaba da fushi da ni" Mami tace "Inyi fushi da kai a saboda me, a'a ni ba
fushi nake da kai ba, abinda kake so ne fa kayi, don haka bani da wata matsala da
wannan, kawai dai abinda na sani gida da Maryam tace maka zaka raba masu babu
wannan zancen, ban amince da haka ba, daƙuna biyar ne a gidanka banda biyu da ke
downstairs, don haka babu wani gida da zaka kama, they will be staying in the same
house...." Khalil ya daga kai yana kallonta ya kasa cewa komai.

*Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah*


Ur evidence via 07087865788

Assalamu alaikum
Barkanmu da war haka masoya Khaleesat da Nihad🥰. Nasan kowaccenku na cike da son
sanin turarukan da wadannan taurari namu guda biyu ke amfani dashi dake tafiyar da
xuciyar maxajensu ya rikita musu lissafi ya kuma goge masu hada😌.
Toh turaruka neh na oil masu kamshi sosai da rike jiki daga scentmania. Wadannan
turaruka sunfi kala goma. Dan mace ba'a Santa da xama da kamshi iri daya kullum ba.
Dole adinga jin kamshi ma banbanta ajikinta kullum. Ana hada wadannan turaruka biyu
xuwa sama asaka alokaci guda dansu bada sihirtaccen kamshin dake tafiyar da
hankalin duk wanda ya shaka.
Dan haka muka hada package na wadannan turaruka muna kiranshi da 'Nihad pack' 🔥 🔥
Akwai Nihad silver pack: ya kunshi turaruka kala biyar. 6mls guda biyu da 3mls
guda uku N5000.
Akwai Nihad gold pack: ya kunshi turaruka kala bakwai. 6mls guda uku da 3mls guda
hudu
Sannan akwai Nihad diamond pack: ya kunshi turaruka kala 8. 10mls guda daya 6mls
guda hudu 3mls guda uku.
Ga sunayen turarukan nan kamar haka
1. Love letter (na musamman akowani pack akwaishi)
2. Baccarat Rouge
3. Jadore
4. La vie est belle
5. Pink shiffon
6. Pure seduction redplum
7. Versace Eros woman
8. Black Opium
9. Kim Kardashian
10. Love spell
Note that turarukan package a discounted price aka bada, kuma ana hada scents din
da sukayi complimenting juna neh yadda xaifi tashin kai in anyi amfani dashi. Amman
in kinason kiyi maki choice dinki shima ana badawa standard price dinmu 3mls N800,
6mls N1500 10mls N3000
Akwai 20mls N5000, 30mls N7000 and 50mls N10000. Turaruka araha ina mai tabbatar
maki kikayi amfani dasu sai kin dawo. Mudae burinmu kowa tayi kamshi na musamman🥰🥰💖
NIHAAD 💖

65

Nihad na zaune dakin Mimi bayan azahar tana danna sabuwar wayar da Khalil ya siya
mata, har ta kira Mumy da ya farooq da wayar don ya saka mata layi da credit a
ciki, Mimi ta shigo dakin rike da ankonsu ita da Hanan ta diresu gefen gado, laces
biyu ne sai super uku uku, Nihad dai sai kallon kayan take, Mimi tayi wani sigh
tace "Ankon mu ne wannan.... Idan an siyo wani zan cire maki naki, Suhaila ma ba a
kawo nata ba" Nihad tace "Ankon mene?" Mimi ta kalleta zata yi magana amma kamar
warce ta tuna wani abu sai tayi shiru tana kallon Nihad din, can ta juya kawai ta
harhada ankon ta saka a press dinta ta nufi kofa, Nihad ta bi ta da kallo har ta
fita, Nihad ta ajiye wayar hannunta tana sake maimaita kalmar ankon da Mimi tace
mata a zuciya, a hankali ta koma saman gadon ta kwanta. Khalil na zaune first
parlor din Mami tare da Aunty Maryam, Mami kuma tana other parlon din nata tare da
bakuwarta, Aunty Maryam tayi kasa da murya tana kallon Khalil tace "Komai tace maka
kar ka mata musu kayi ta bin ta da toh, amma gaskiya baza ka hadasu gida daya ba"
Khalil dai yayi shiru bai ce komai ba, cause he don't get why Mami is making issues
complicated, Aunty Maryam tace "Yau saura kwana ashirin da daya cif cif, ita Nihad
din ta sani??" Ya daga kai ya kalleta ya girgiza kai yace "Ban gaya mata ba
gaskiya" Aunty Maryam tace "Aa ya kamata ka gaya mata, tun farko ma ya kamata ace
ka sanar mata kana da yarinya da kayi ma alkawarin aure kaga zata san da maganar a
kasa ba yanzu kawai taji sa kamar daga sama ba" Ya sauke ajiyar zuciya yace "Ko za
ki mata maganan da kanki Aunty?" Aunty Maryam ta rike haɓa tace "Ehh lallai, wato
ni ce ma zan gaya mata za a mata kishiya salon dai baiwar Allahn tayi ta kallona da
shi, kai dai zaka sameta kasan yanda zaka gaya mata cikin lallami, akan dai taji a
wani waje baka gaya mata ba, ba don Mami baxata fahimce mu ba da auren ma dagawa
kawai aka yi sai zuwa nan da wata uku tunda ai an kai kudi, ita kuma kaga bazata yi
tunanin don ba a sonta bane zaka sake aure, amma kuma naga bata da matsala, yarinya
ce, kaga bazata wani damu da kishi ba sai nan gaba" Murmushi kawai Khalil yayi bai
dai ce komai ba, Aunty Maryam tace "Allah kuwa bazata daga hankalinta ba yanda
babban mace zata yi, she is too young for that" Khalil yace "Toh Aunty nan gidan
zata yi ta zama kenan?" Aunty Maryam tace "Toh nayi ma Mami magana ka dauketa yau
ku tafi kawai tace ai duk rana daya za su shiga gidan da Nadeeyah, kaga sai nan da
sati uku kenan, to ya zan mata??" Da mamaki Khalil ya dinga kallonta, Aunty Maryam
tace "Kasan idan Mami ta ce ga yanda take son abu to fa kawai ayi hakuri a bi ta da
yanda take son din, that's just it" Aunty Maryam tace "Ni dai zaka kai ni airport
zuwa la'asar, kar kayi nisa" Yace "Toh yanzu idan kika tafi sai yaushe za ki dawo
Aunty?" Aunty Maryam tace "2 days before the wedding in sha Allah" Yace "Toh Allah
ya kai mu" Aunty Maryam tace "Ameen"
Mami na zaune parlonta da Aunty Maryam da dake rufe trolly dinta don la'asar din
ya kusa Hajiya Amina ta shigo parlon, Ta zauna da fara'a, bayan sun gaisa tace "Ina
amaryar, shiru shiru ni dai ban ganta ba tun da suka iso jiya, shine nace to ni
bari in biyota" Mami tace "Ayya, ai ko nace Mimi ta kai ta ta gaisheku ke da Aunty
Hassana tun dazu, ban san bata kai ta ba" Hajiya Amina tace "Allah sarki, ai ko
bata kai ta ba, ita ma Aunty Hassanar dazu ta dawo ai" Aunty Maryam ta dago kai jin
sai yau Aunty Hassana ta dawo daga Kanon, Mami tace "Allah sarki" Hajiya Amina tace
"Ya muka ji da shirye shiryen biki kuma?" Mami tace "Alhamdulillah" Hajiya Amina ta
mike tace "Toh Allah ya kai mu lokaci, dama dai cewa nayi bari in leko amarya" daga
haka ta fita daga parlon, Aunty Maryam ta taɓe baki ta ci gaba da abinda take tana
girgiza kai tace "Munafurcinsu dai zai kare masu idan kin bibiya Hassanar ce ta
turo ta, in sha Allahu sai mun ji su kaca kaca a rana nan ba da dadewa ba kuwa"
Mami dai ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba, ta dau wayarta ta shiga kiran
Mimi, Mimi na dagawa Mami tace "Dama baki kai ta bangaren Amina da Hassana ta
gaishesu ba kamar yanda nace maki Mimi?" Mimi ta zaro ido tace "Ohh da na shiga
dakin dazu na tarar bacci take, bari in duba yanxu Mami" Mami ta katse wayarta,
Aunty Maryam tace "Shi kuma Khalil daga cewa ba jimawa zai yi ba ya bar ni shanye a
nan gashi har lokaci ya kusa..." Mami tace "Ba ga driver ba sai ya kai ki mana,
dole sai shi Khalil din" Aunty Maryam dai bata ce komai ba.
Mimi na shiga dakinta ta tarar da Nihad kwance amma ba bacci take ba, Mimi tace "Ki
dau gyalenki mu je ku gaisa da stepmom dita Neehad" Nihad ta mike zaune, gaba daya
bata da walwala tun dazu, Mimi na kallonta ta mike ta dau Mayafinta sannan Mimi ta
fita dakin ta bi ta a baya, babu wani banbanci bangaren Mami da na Hajiya Amina sai
dai Hajiya Amina parlor daya ne babba, tun da suka shigo Hajiya Amina ke kallon
Nihad don ita fa duk zaman Nihad a gidan ba wai ta san ta bane, Nihad ta zauna kasa
ta gaisheta da ladabi, Hajiya Amina ta amsa faram faram tana mata sannu da zuwa,
Nihad dai bata dago kanta ba, bayan few minutes Mimi tace "Aunty Hassana ta dawo ko
Mum?" Hajiya Amina tace "Bata dade ma da fita nan ba, ku je tana can bangarenta"
Mimi ta mike tace "Toh bari mu je ta gaisheta" Hajiya Amina tace "Toh madallah"
Nihad ta mike suka fita daga parlon, da sauri Hajiya Amina ta dau waya tayi dialing
din number Aunty Hassana ta sanar mata ga su Mimi za su taho bangaren nata... Mimi
na isa ta bude kofar parlorn a hankali, ɗan matsakaicin parlor ne shi ma dai ya
hadu iya haduwa, amma bai kai na su Mami girma ba, Sosai gaban Nihad ya fadi ganin
Aliyu zaune parlon saman kujera daga kusa da bakin kofar parlon yana sanye da 3
quarter da polo, suna hada ido ta sunkuyar da kai, Mimi na ganinsa tace "Hi" Daga
haka ta karasa can cikin parlon zuwa kofar bedroom din Aunty Hassana tayi sallama,
Aunty Hassana tace "Waye?" Mimi tace "Mu ne, an zo za a gaisheki ne Aunty" Aunty
Hassana tace "Ina zuwa" Dawowa cikin parlon tayi tana kallon Nihad da ta rakube
waje daya a cikin parlon, duk ta ki sakin jiki, lokaci lokaci Aliyu dake danna waya
yake mata kallon kasa kasa, Sai ga Aunty Hassana ta fito tana kallon Mimi tace "Sai
kin wani rakota kamar za a cinyeta?" Mimi tace "Aa ai bata san hanyar ba" Aunty
Hassana tace "Toh ai yanzu ta ga hanyar ko?" Mimi tayi shiru bata ce mata komai ba,
can ta mike, sosai gaban Nihad ya fadi, ta dinga kallonta har ta nufi kofa ta fita,
Aunty Hassana tana kallon Nihad tace "Sannu ko, bari a kawo maki ruwa" Daga haka ta
nufi kofar parlon ta fita, Nihad da gabanta ke faduwa sosai ta kalli Aliyu taga
still wani irin kallo yake mata, mikewa tayi da niyyar ficewa daga parlon, taga ya
mike ya kulle kofar ya nufo ta yace "Munafuka, macuciya er cin amana.... Dama ashe
duk yaudarata kika dinga yi a baya ban sani ba? Ki rasa wanda zaki aura a karshe
sai makiyi na? And you are trying to make it look as if baki san hakan ba?" Nihad
dake kallonsa zuciyarta na bugawa tace "Kai ban kiraka da munafuki ba sai nice zaka
ce ma munafaka? Naga ai ban taɓa amfani da sunan mahaifin wasu a matsayin mahaifina
ba, i never lied to you about who my dad is, hasalima har gidanmu na kai....." Bata
kai karshe ba ya sauke mata mari, ta dafe kuncinta da mamaki tana kallonsa babu ko
kiftawa, yace "Sai kinyi da kin sanin sanina a rayuwarki, kuma duk sai na fanshe
bata min lokaci da kika yi ta hanyar da baki taɓa zato ba wallahi, i am promising u
this" Dai dai nan aka bude kofar parlon Aunty Hassana ta shigo rike da tray me
dauke da kwalin lemo da glass cup, tana kallon Aliyu da sauri ta ajiye tray din
hannunta tace "Me ke faruwa Daddy?" Kofa Nihad ta nufa da sauri hawaye na sauka
idonta, Aunty Hassana ta gwalo ido ganin haka ta bi ta tana kiranta amma tuni Nihad
tayi nisa, Aunty Hassana ta dawo parlon cike da masifa rai bace tace "Kai wani irin
shashasha ne mara lissafi Daddy? Kai me yasa baka jin magana ne? Nace maka a sannu
za a bi komai amma sai da ka yi mata magana? Toh yanzu ina kake son in bi ta in
bata lemon nan fisabilillahi? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, baka kyauta min
ba Daddy" Aliyu yace "Ke kika ga haka mum" Daga haka ya fice daga parlon kamar zai
tashi sama, Hankali tashe Aunty Hassana ta kira wata long time frnd dinta Maimuna
da ta hadu da ita zuwansu kano ta shige daki da sauri. Direct Nihad dakin Mimi ta
koma ta zauna gefen gado hawaye na sauka idonta sai kuma ta fashe da kuka sosai, ko
minti biyar bata yi da shigowa ba aka bude kofar dakin, Khalil ya shigo, da mamaki
yake kallonta ganin kukan da take, sai kuma ya nufeta da sauri yana kallonta yace
"What happened?" Hade kai tayi da gwiwa tana kuka sosai, ya zauna gefenta ya dagota
hankali tashe yace "Talk to me plss an maki wani abu ne?" Tana shesshekan kuka tace
"Aliyu slapped me" Khalil ya dinga kallonta ba ko kiftawa, as if counting his words
yace "Aliyu slapped you?" Nihad ta gyada kai cikin rawan murya tace "Mimi ta kai ni
mu gaisa da yan gidan shine muka hadu da shi a parlon warce muka je kano tare da
ita" Khalil bai jira ya gama sauraronta ba ya mike ya fice daga dakin kamar zai
tashi sama, direct dakin Aliyu ya nufa that is almost 5 minutes walk daga dakinsu
Mimi, a hanya ya ga wani vase din flower ya dauka yana ci gaba da tafiya kamar zai
tashi sama, bai kuma hadu da kowa ba har ya isa part din Aliyu, dai dai nan shi
kuma ya fito daga dakin sa babu wata wata khalil ya fasa vase din jikin bango ya
caka masa da karfi a kafarsa, Aliyu yayi wani kara ya dafe bango da sauri yana zaro
ido, kan kace me sai ga jini kamar an bude pampo, hakan bai sa Khalil ya fasa
shakesa ba yana huci yace "Stay away from my wife, idan kuwa ba haka ba, ni ne doom
dinka, i promise you" Yana gama gaya masa haka ya turasa da karfi ya juya ya bar
wajen kamar wani soja.... Mimi ta fita da trolly din Aunty Maryam zuwa mota ta dawo
kenan ta hadu da khalil tace "Yayanmu Aunty Maryam tana ta nemanka fa" Bai ce mata
komai ba ya fice daga parlon, Mimi ta tafi ta gaya ma Aunty Maryam yana parking
space yana jiranta..... Khalil na kai Aunty Maryam Airport ya dawo sai bai shiga
gidan ba, yayi parking kofar gida yayi dialing number Mimi, Mimi na dagawa yace
"Are you with me?" Tace "Yeah ina ji" Yace "I want you to come out now with Nihad
but kar ki gaya ma Mami, zata siya abu ne a Supermarket" Mimi tace "Alright" Daga
haka ta katse wayar, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta fito da Nihad, tun daga nesa
yake kallonsu har suka karaso, yana kallon Mimi yace "Thank you" cike da damuwa
Mimi tace "Yayanmu they just rushed Aliyu to the hospital now, i think ko kwalba ne
ya fadi a kafarsa i don't just understand, he is bleeding seriously" Khalil yace
"Ohh really" Bai jira me zata ce ba ya bude gefensa yana kallon Nihad yace "Shiga
mu je ki siyo abun" Nihad ta shiga motar, ya kalli Mimi yace "Za mu dawo yanzu but
don't say anything to Mami" Tace "Ohk" Yace "Noor fa?" Mimi tace "Noor na gidansu
Nadeeyah" Yace "Ohk" Daga haka ta kulle motar ta koma cikin gida shi kuma ya bar
layin, sai a sannan Nihad ta kallesa da damuwa tace "Me yasa zaka yi injure dinsa
haka?" Yace "Saboda ya taɓa Nihad" Tayi shiru tana kallonsa, can ya girgiza kai
yace "Dama i have been targeting him for so long, so this is just an opportunity
that comes but once" Nihad da hankalinta ya tashi tace "Mimi said he is bleeding
heavily" Khalil yace "Serves him right" ta daga kai da sauri ta kallesa ganin
gidansa ya kawota, deep down her she felt happy saboda bata jin dadin zaman gidan
nan nasu, bata son gidan har cikin ranta, ya sauka ya bude gate din ya shiga da
motar ciki sannan yayi parking, da kansa ya sauka ya bude mata side din da take, ta
sauke idonta sannan ta sauka daga motar, yana rike da hannunta suka shiga cikin
gidan, sama ya tafi da ita, yana kallonta yace "Which room will u prefer amongst
the room?" Nihad dai sai kallon dakunan take bata ce komai ba, yayi hugging dinta a
hankali ta baya yace "Ko in zabar maki?" Still dai tayi shiru feeling him at her
back, a hankali ta fara kokarin janye jikinta ya ki saketa dragging her closer to
him, murya can kasa yace "Na zabar maki this one" Ta kalli dakin da yake nuna mata
wanda yake kusa kusa da bangarensa na master Bedroom, rubbing her flat tummy yace
"Kina so?" Kai kawai ta gyada masa, wasu abubuwa ya dinga yi mata ita dai bata
hanasa ba sai kafafuwan ta ne kawai suka kasa ci gaba da daukanta, he could feel
how fast her heart is beating, he noticed jikinta ba shi da wuyar reacting to
stimulation, bata ankara ba sai ganinsu a bedroom dinsa tayi....
A hankali Khalil yayi kissing din goshinta yace "Wake up, it's almost Magrib...."
Nihad ta bude Idonta, ya dagota zaune yana kallonta, yana son sanar mata maganar da
Aunty Maryam tace ya gaya mata amma ya kasa don bai ma san ta inda zai fara ba,
Yayi kasa da murya yace "Za mu tafi can gida yanzu" Sosai gabanta ya fadi jin
abinda yace mata, ta kasa ce masa komai. Har suka sauka downstairs Nihad ji take
kamar ta fashe da kuka, ya dau wayarsa da ya ajiye a parlon, nan ya ga missed calls
din Janar har uku, sai na Mami kusan goma, shi gaba daya ya ma mance da wani abu da
ya aikata sai yanzu da yaga kiransu, ya mayar da wayar aljihunsa yana rike da
hannun Nihad suka fita daga gidan. Sai da suka isa gida Khalil yayi parking a layin
yana kallon Nihad, kamo hannunta yayi a hankali, gathering all courage yace "Kin
san kafin Abbanki ya hadani aure da ke ina da budurwata warce har da akwai maganar
aure tsakanina da ita right?" Nihad ta daga kai tana kallonsa kamar bata fahimce
abinda yake nufi ba, Ya lumshe ido ya bude amma ganin irin kallon da take masa
kawai ya fasa ci gaba ya ja motar yana driving din a hankali, ana bude masa gate
yayi parking a parking space, Nihad bata sake second daya a motar ba bayan ya bude
lock din ta sauka, ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gidan, ya sauke ajiyar
zuciya ya jinginar da kansa jikin kujeran motar. Sai da Khalil yayi sallah sannan
ya shiga gidan yana ciro wayarsa dake ring a aljihu ganin Abbansa ne ya daga, Janar
na gama maganar da zai masa ya katse wayar, Khalil ya nufi bangaren Aunty Hassana
kamar yanda Janar din ya umarcesa yana bude kofar parlon ya ga Janar a tsaye, ga
Aliyu zaune a kasa an nannade masa kafa da uban bandage wanda har yayi stain da
jini, sai zufan azaba yake, Aunty Hassana na zaune parlon sai kallon kafar Aliyu
take ta kankance ido zuciyarta na tafarfasa, Ga Mami a tsaye duk jikinta yayi
sanyi, ko magana bata yi, Hajiya Amina ma na dakin sai girgiza kai take cike da
alhini, Janar ya juya yana kallon Khalil cikin daga murya yace "I need an
explanation to this Ibrahim" Khalil yayi shiru bai ce komai ba, Janar yayi masa
tsawa yace "Magana nake maka" Khalil ya gyara tsayuwarsa jikin kofar yace
"Tsautsayi ne, amma ba da gangan bane" Janar na masa wani kallo yace "Tsautsayi??
Shaye shaye ka fara da zaka kira hakan da tsautsayi? Where u out of ur mind" Khalil
dai yayi shiru, can a hankali yace "Kayi hakuri" Janar ya hau zaga parlon fuskarsa
a murtuke, Can ya juya ya kalli Khalil yace "Sai ka shirya gobe ka tafi Germany ka
hadu da business partners dina na can" Aunty Hassana ta daga kai da sauri tana
kallon Janar baki bude, shi kansa Aliyu kallonsa yayi da sauri, Khalil yace "Ohk"
Daga haka ya juya ya fita daga parlon, Mami ta kasa dago kai don bata yi expecting
jin abinda Janar ya fada ba, Aunty Hassana ta kasa daurewa cikin ɓacin rai tace
"Yaya kasan kuwa illar da yayi ma kafarsa? Har fa ƙashinsa sai da ya tsage ya
dagargaje" Janar ya kalleta yace "Sai a fita da shi waje a sake duba kafar...."
Aunty Hassana na huci tace "Iya abinda zaka gaya ma ɗan ka kenan bayan illata min
ɗa na da yayi?? Amma yaya ka bani mamaki, wallahi ka ban mamaki, iya matakin da
zaka dauka kenan a kan wannan mugun raunin da Khalil ya ji masa??" Janar ya tsaya
kallonta bai dai ce komai ba, tana girgiza kai tace "Toh wallahi baxan yarda ba,
idan na yarda shegiya uwata da ubana suka haifeni, kafin in dau mataki dama sai na
fara kiran duk family sun san abinda ake ciki, duk sai na bi na tura masu video din
kafar Aliyu, Khalil ya nakasa min ɗa amma kai ta business dinka ma kake a Germany
ko?? To wllh bazan yarda ba samm, sai inda karfina ya kare a wannan abinda Khalil
yayi ma ɗa na" Janar yace "Ni kike gaya ma maganganun nan Hassana?" A fusace tace
"Na fada, ai ɗa bai fi ɗa ba, shekaru kusan ashirin baya haka nan yayi masa rauni a
baya har yau taɓon na nan a bayansa, a wancan lokacin ma babu wani mataki da ka
dauka banda asibiti da ka kai Aliyu, kawai ka dauki son duniya son jaraba ka daura
ma yaro yana ta abinda ya ga dama ya zama terror har da su sace sace a lamarinsa,
ohk don ba ubanmu daya ba shine zaka dinga fifita ɗan ka a kan ɗa na?" Janar ya
gyada kai yace "Ki sameni parlona Hassana" Daga haka ya fice daga parlon nata,
Aunty Hassana ta dinga bambami tana zage zage, babu abinda ta mance bata gaya ma
Mami da tayi shiru tana kallonta, daga karshe ta fice daga parlon nata ta bi bayan
Janar tana huci, dama ta saba fesa masu rashin kirkinta kuma ta zauna lafiya a
gidan, babu yanda har shi Janar din ya iya da ita, ita abinda ya kona mata rai
Germany da Aliyun bazai je ba sai Khalil, shine babban baƙin cikinta a yanzu, tana
isa parlon Janar ta ki zama tace "Ina jin ka" Bai ce mata komai ba banda zaga
parlon nasa da yake, bayan few seconds ya daga kai ya kalleta yace "Ki tattara
komai naki ki bar min gidana yau ba sai gobe ba Hassana" Buda baki tayi tana
kallonsa da mamaki babu ko kiftawa, can tace "In bar maka gidanka kace?" Yace "Ehh
ba sai gobe ba, dama da na duba wasu mugayen halayyenki a baya da yanda kika hadani
da mahaifiyata har ta koma ga Allah, to da ko anguwan da nake bazan bari ki karaso
ba balle ki shigo gidana har ki zauna zaman shekara talatin...." Aunty Hassana ta
dinga kallonsa ko kiftawa babu, yace "Ba hauka Ibrahim yake ba da zai raunata Aliyu
haka nan kawai, they must definitely be something, they must be a reason...." Aunty
Hassana na huci tace "Toh ai naga akwai cctv a gidan a duba mana a ga dalilin tunda
goyon bayan ɗan ka kake Abubakar" Janar yace "Cctv din da ku ke kashewa ko wanne
kike nufi a ciki? Hassana yau ba sai gobe ba ki bar min gidana kada in sa sojoji su
fitar min dake, wallahi karfin zumunci kawai nake dubawa nake zaune dake banda haka
a irin makircin da kika hada min a baya ko kusa da inda nake bazan bari ki zo ba"
Wani murmushin takaici tayi tace "Ohk" Daga haka ta juya ta fice daga parlonsa,
direct bangaren Hajiya Amina ta nufa, Hajiya Amina ta taso tace "Ya ake ciki
yanzu?" Hassana tace "Ragowar kudin nan na wajenki zaki turo min yanzu" Hajiya
Amina tace "Kudi kuma? Aa ni babu ko sisi a wajena, ai kudin sun kare" Wani
axababben kallo Aunty Hassana ta jefa mata tace "Me din suka kare?? Miliyan 15 din
nan da yayi saura fa nake nufi" Hajiya Amina tace "Aa, ni fa nace maki babu ko sisi
a tare da ni" Aunty Hassana tayi mici mici da ido tace "Kan uban can, to kuwa zan
maki rashin mutunci, ni zaki ce ma babu ko sisi?" Hajiya Amina tace "Yau ga ikon
Allah, kudin haihuwa suke ne, kwanaki kin san sa na tura ma sadiya miliyan 3, to
dama ai shikenan ya rage a kudin ko bakya lissafi ne??"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

Assalamu alaikum
Barkanmu da war haka masoya Khaleesat da Nihad🥰. Nasan kowaccenku na cike da son
sanin turarukan da wadannan taurari namu guda biyu ke amfani dashi dake tafiyar da
xuciyar maxajensu ya rikita musu lissafi ya kuma goge masu hada😌.
Toh turaruka neh na oil masu kamshi sosai da rike jiki daga scentmania. Wadannan
turaruka sunfi kala goma. Dan mace ba'a Santa da xama da kamshi iri daya kullum ba.
Dole adinga jin kamshi ma banbanta ajikinta kullum. Ana hada wadannan turaruka biyu
xuwa sama asaka alokaci guda dansu bada sihirtaccen kamshin dake tafiyar da
hankalin duk wanda ya shaka.
Dan haka muka hada package na wadannan turaruka muna kiranshi da 'Nihad pack' 🔥 🔥
Akwai Nihad silver pack: ya kunshi turaruka kala biyar. 6mls guda biyu da 3mls
guda uku N5000.
Akwai Nihad gold pack: ya kunshi turaruka kala bakwai. 6mls guda uku da 3mls guda
hudu
Sannan akwai Nihad diamond pack: ya kunshi turaruka kala 8. 10mls guda daya 6mls
guda hudu 3mls guda uku.
Ga sunayen turarukan nan kamar haka
1. Love letter (na musamman akowani pack akwaishi)
2. Baccarat Rouge
3. Jadore
4. La vie est belle
5. Pink shiffon
6. Pure seduction redplum
7. Versace Eros woman
8. Black Opium
9. Kim Kardashian
10. Love spell
Note that turarukan package a discounted price aka bada, kuma ana hada scents din
da sukayi complimenting juna neh yadda xaifi tashin kai in anyi amfani dashi. Amman
in kinason kiyi maki choice dinki shima ana badawa standard price dinmu 3mls N800,
6mls N1500 10mls N3000
Akwai 20mls N5000, 30mls N7000 and 50mls N10000. Turaruka araha ina mai tabbatar
maki kikayi amfani dasu sai kin dawo. Mudae burinmu kowa tayi kamshi na musamman🥰🥰

Ga number da za a tuntuba kamar haka. +2347065525409💖 NIHAAD 💖

66

Mami ta koma ɓangarenta tana hada sauran ankon da zata tura Drivernta ya kai ma
kawayenta da bata tura ma ba Noor ta shigo parlon, hankali tashe tace "Mami Aunty
Hassana da Mumy suna ta fada fa tun daxu" Mami ta mike tsaye tana kallonta da
mamaki tace "Fada kuma?" Noor tace "Wallahi har da dambe" Mami ta zaro ido tace
"Damben lafiya" Noor tace "They are fighting seriously fa a part din Mumy" Mami ta
nufi kofa ta fita da sauri, Noor ta bi bayanta, tun daga Babban parlon gidan take
jin muryoyinsu suna kunduma ma juna zagi kafin ma ta karasa bangaren Hajiya Amina,
tsaye ta ga Janar bakin kofa yana kallonsu, bai kuma yi attempting dakatar da su
ba, Suhaila da mai aiki na ta rirrike Aunty Hassana warce ke kokarin kara finciko
Hajiya Amina su fara wani sabon damben ga Attachment dinta yashe a kasa Hajiya
Amina ta tuge, Hajiya Amina na huci tace "Ku saketa don Allah ta zo, Banza kawai er
wahala, kafura...." Aunty Hassana na tura su Suhaila da karfi take cewa "Ku bar ni
in illata yar iskar, ni kike kira da er wahala? Ni? Toh wallahi zaki san ni kika ce
ma er wahala" Hajiya Amina na tafe hannu tace "An fada, er wahala, dama ba
wahalalliyar bace?" Cikin daga murya Aunty Hassana tace "Yanda nayi sanadin aka
aureki haka duk abinda zan yi sai nayi an sakeki Amina, wallahi karshenki ya zo a
gidan nan, ke banda na shiga na fita ko a er aikin gidan nan kin isa ki shigo balle
matar gidan? Waye bai san karuwancin da kika yi ba a baya ba?? Waye bai san har
madigo kin yi ba, ke da har London ana booking dinki ki ayi iskanci dake? Banda ni
din ina za ki san Janar ki auresa???" Hajiya Amina tayi wani shewa tace "Riiii, ai
abokin barawo barawo ne, madigo kuma tare muka fara da ke, kuma karuwancin ma duk
tare mu ke yi, gwara ni ba baƙin cikin karuwancin da nake bane ya kashe uwata har
lahira, lafiya lau muka rabu da ita, ke kuwa waye bai san har da bakin cikin
karuwancinki da kike yi tun da aurenki ne ya kashe taki uwar ba? Sannan uwa uba
alhakin mijinki Iliya da kika raba da 'ya yansa yau shekara ashirin kenan, kika
gudo daga kauyen da dangin ubanki suka maki aure da shi sbda shashancin da kike na
karuwanci, kika dawo garin Adamawa garin uwarki kika ci gaba da karuwancinki babu
kama hannun yaro, waye bai san Sajida a titi kika yi cikinta kika haifeta ba??"
Aunty Hassana tayi wani kukan kura tayi watsi da mai aikinta da Suhaila dake
rirriketa, tayi kam Hajiya Amina ta cakumota iya karfinta, nan suka fara sabon
dambe ba ji ba gani, Janar ya nuna ma Suhaila da Mai aikin kofa alamar su fita, sum
sum suka nufi kofar suka fice daga parlon, Mami da hankalinta yyi mugun tashi zata
karasa ciki da nufin rabasu, Janar ya dakatar da ita fuskarsa a murtuke, dambe iya
dambe suka sha har sai da suka kusa yi ma junansu zigidir a parlon, ga jini a bakin
ko waccensu, zuwa yanzu babu Attachment ko daya a kan Aunty Hassana duk Hajiya
Amina ta tugesu, Sai da suka gaji lilis sannan aka ci gaba da zage zage ta uwa ta
uba ana tsine ma juna, Aunty Hassana ta juya tana kallon Janar jini na zuba ta
hancinta tana huci tace "Ita ce ta dauke maka miliyan 800, ka tuhumeta, ba wani ya
dau kudin nan ba ita ce wllh, wallahi ita ce, sannan sai da tabi ta kashe duk cctvn
gidan kafin ta aikata mugun nufinta" Hajiya Amina tayi wani shewa tana tafe hannu
tace "Muka dauke dai tare Hassanaaa, banda kin masu labe shi da ɗan nasa a ina zan
san an shigo da kudi gidan?? Ai kece babban barauniya Hassana, kudi kuma suna
kugunki...." Hajiya Amina na kallon Janar tana huci tana nuna masa Aunty Hassana
tace "Ita ta saka na dauko mata kudin na bata wallahi, idan karya nake Allah ya dau
raina nan take, kuma ko miliyan 5 bata bani ba cikin kudin nan wallahi tallahi,
zuwa yanzu da zaka ji gidaje nawa Hassana ta siya da motoci daga ita har ɗan ta ai
sai Allah, sannan duk rashin ci gaban da kake gani a kasuwanci da kake daura Khalil
ita ke bin boka da Malamai kudin su tarwatse kar yayi nasara duk don a daura nata
ɗ'an, kuma hakan ne ya faru kusan shekara biyu a gidan nan in ba Aliyu ba baka
daura kowa kan harkokinka ɗan naka ma taje tayi asiri ta sa ka koresa gaba daya,
tunda ai sanda aka nemi kudin aka rasa baka koresa ba, ganin haka yasa ta banka
uban asiri har sai da ka koresa, Hassana bata sonka bata son ɗan ka tana tare da
kai ne kawai saboda abun duniya kuma kam ta tara don a yanzu Hassana ta mallaki
gidajen kanta ya fi takwas duk a kudin da ta saka na dauko mata, Kullum sunanka a
wajen Malamai yake don ta mulkeka son ranta duk abinda zata yi ka kasa yi mata
magana, ai ba a banza ta kori sojojin dake gadin bangarenka da kofar babban parlor
nan ba, a lokacin ta laka masu sharri wai suna kalle yan matan gidan idan sun zo
wucewa duk don ta samu ta ci ma mugun kudurinta, sannan babu me turning off din
Cctv din gidan nan sai ita, duk sanda take shirin yin mugun nufinta abinda take yi
kenan, da kasan da irin zuciyar da Hassana ke tare da kai ko, to ba uwa daya ba, ko
uwa daya uba daya ne wallahi sai ka nisanta kanka da zuri'arka daga Hassana, Matar
da ta hada maka tuggu gun mahaifiyarku an kamata dumu dumu tana zina sai tace ai
kai ka hadata da mutumin wai abokinka ne, alhalin shi abokin naka da ka hadata da
shi ko ta samu ya aureta tunda zawarcin ya ki ci yaki cinyewa sun rabu tun tuni,
amma tayi maka wannan sharrin, ko ka manta ne Janar????" Aunty Hassana ta shige
dakinta da gudu tana dube duben abinda zata dauko ta rotsa ma Hajiya Amina a kai,
Karasawa cikin parlon Janar yayi ya saka ma kofar dakin key ta waje, Hajiya Amina
dai sai huci take, yana kallon Mami da duk jikinta yayi sanyi qlau ta kasa
kwakkwaran motsi a inda take yace "Fita mu je" Mami ta juya ta fita daga parlon,
shi ma ya fito ya saka ma kofar parlon makulli ta waje. Bangarensa ya tafi ya kira
barracks a turo masa sojoji a mota, sannan a hada da mata ciki. Babu bata lokaci
sai ga sojoji sun iso gidan, Janar ya sa sojoji matan suka shiga suka fito da Aunty
Hassana da Hajiya Amina, duk aka kwama masu handcuff, Aunty Hassana na kallon Janar
tace "Yanzu yaya ni zaka sa a saka ma handcuff? Ni? Duk inda mahaifiyarmu take zata
yi alfahari da abun nan da ka min Yaya?" Ko rufe baki bata yi ba ya sauke mata
tagwayen mari wanda sai da taga stars, ya kuma umarci Sojojin da su zane su idan za
su kawo masu taurin kai, Ita dai Hajiya Amina ba abinda tace amma ranta fari kal ta
tona ma Hassana asiri, don shekara kusan 17 kenan Hassana ke amfani da ita a gidan,
don dai ita ma tana da wayo da sai dai ta tashi a tutar babu, Aunty Hassana ta juya
da sauri tana kallon Janar kafin a fita da ita daga parlon tace "Kuma wallahi
wallahi Hanan ba er ka bace, bata da gadonka, boka ne yayi mata cikinta don juya ce
ita bata haihuwaa...." Sojan ta kwada mata mari ta turata suka fita daga
parlon..... Kamar yanda Janar bai yi bacci ba daren ranan nan haka Mami warce ta ma
fi sa girgiza da wannan abu da ya faru, da ya tuna abinda Hassana ta fada na karshe
sai hankalinsa ya tashi, wai Hanan ba er sa bace, then there is need for a DNA
test.... Mami na idar da sallah da asuba Aunty Maryam ta fara kira don bata mance
furucinta a jiya da yamma kafin ta tafi airport ba, sai gashi hakan har ya faru,
amma bata sameta a waya ba, can ta mike a hankali ta fita daga bangarenta, dakin
Aliyu ta fara zuwa don duba kafarsa, amma taga dakin wayam kuma bata ma ga alamar
ya kwana a dakin ba, juyawa tayi ta fita ta karasa bangaren Janar, ta samesa zaune
saman kujera still pondering, bata taba ganinsa a yanayin nan da yake ciki ba sai
many years ago, kana ganinsa kasan abun ya tsaya masa a rai, ta gaishesa cikin
sanyin murya, ya amsa ba tare da ya kalleta ba, Ta kwantar da murya tace "Plss kar
ka sama kanka damuwa Yallabai, this isn't proper for ur health, sannan ina rokon ka
ka dubi albarkacin zumunci ka kyale Hassana, sai kaga Allah ya maka sakayya ta inda
baka zato...." Janar ya kalleta da sauri kuma a fusace yace "Amma ina ga baki da
hankali ko Fatima??" Mami dai tayi shiru, yace "Then if u have nothing good to say
ki bar min parlona kada ki kara bata min rai don Allah" Mami ta sauke ajiyar zuciya
bata dai sake cewa komai ba, Khalil ne ya shigo parlon da sallama, shi fa duk
abinda ya faru jiya a gidan bai sani ba don yana barin bangaren Aunty Hassana dama
gidansu Nadeeyah ya tafi kuma bai dawo ba sai kusan karfe goma saura, Ya zauna
saman kujera ya gaida Janar, Janar ya amsa without looking at him, he felt guilty
duk abubuwan da ya ma ɗan nasa a baya, Khalil ya gaida Mami ita ma ta amsa, bayan
few seconds Janar yace "When are you leaving?" khalil ya daga kai ya kallesa yace
"Later in the day in sha Allah" Janar yace "Da matar taka zaka tafi can din?"
Khalil ya ɗan yi shiru, he felt unhappy da bazai iya tafiya da ita ba, ya so ace da
ita zai yi tafiyar but it's not going to be possible in ba dai daga tafiyar zai yi
ba, a hankali yace "Ai bata da passport" Janar yace "Ohk, sai ayi kokari tayi, it's
important...." Khalil yace "Is the trip urgent sir?" Janar yace "It is, tun 5 days
ago ya kamata" Khalil yace "Ohk" Daga haka ya mike ya basu waje ya fita daga
parlon. Karfe takwas Janar ya shirya da escort dinsa suka tafi barikin da aka kai
Aunty Hassana da Hajiya Amina, ai ko ya tarar sojojin sun ci ubansu dai dai
gwargwado, tun karfe hudun asuba suke tsaye har zuwa yanzu da Janar ya zo, ga
tsallen kwadon da suka yi daren jiya na kusan awa biyu, banda azaba babu abinda
cinyoyinsu ke masu, ga sauro da zafi a inda aka ajiyesu, duk sun yi duhu kamar basu
taɓa shan Ac ba, Janar na kallon Hajiya Amina bayan ya shiga har inda suke ya ajiye
mata farin takarda a gabanta, Hajiya Amina taki daukan takardan, yace "Na sake ki,
saki daya, biyu, har uku, Hanan kuma zan kai ta ayi DNA test, if i should find out
that she isn't my daughter, you are to go with her" Yana gama fadin haka ya juya ya
fita ya shigo tare da sojoji murdaddu har biyar yana kallonsu ya nuna masu Aunty
Hassana yace "Ku bi duk hanyar da za ku bi sai ta furta maku inda takardun gidajen
da take siya da motoci suke" Suka ce
"Yes Sir...." Juyawa yayi ya fice daga babban guardroom din.

Inna ce tsaye tsakar parlon tayi mitsi mitsi da ido tana bin duk masu kallon
akwatunan kayan Nihad da kallo kada ko tag a nema a rasa cikin kayan, akwatuna 12
ne tsadaddu, 6 iri daya sauran shiddan ma irinsu daya, kayan ciki kuwa sai son
barka, Aunty Jamila da kawarta da wata kawar Mumy basu siya mata kayan banza ba,
kaya ne na gani na fada masu tsada, matan yayan Abba ne da yan uwa da abokan arziki
cike a parlon ana ganin kaya kowa sai sa albarka yake, Umma dai na zaune one sitter
sai bin kowa da ido take bata cewa komai, gaba daya tayi bakikirin kamar ba ita ba,
ita fa har yanzu gani take zata farka taga duk wannan abun mafarki take, da ko anyi
mummunan mafarki in haka ne, amma dae shiru shiru bata ga ta farka ba, gashi duk
dare da kyar take rintsawa saboda sai taji kamar an soka mata mashi a zuciyarta, ta
dingi juye juye kenan tana numfashi da kyar, Kamila ma na tsaye bayan kujera duk ta
rame saboda damuwa, sai bin akwatunan take da kallo, wanda ko rabin kayan ciki ita
bata samu ba, Inna na daga hannu tace "Toh a gaskiya idan ba ganin haramun ku ke
son yi ma kayan nan ba kuma ae ya isa haka, ganin kaya kusan minti ashirin yanzu
kamar wa enda aka ajiye ma kwari, ai yawansu bazae sa ma a gama ganinsu ba don ma
ku ji, kai wllh baza ma a sake bude kayan ba koma wa zai zo, iyaka ya ga akwati mu
ce masa kayan miliyan goma da dubu goma ne a ciki ya juya yayi tafiyarsa, idan ana
yawan bude akwatin ma ai sai su samu matsala mu shiga uku su ce sakwan muka
siyo...." Aunty jamila dake kan kujera tace "Gaskiya kam Inna" Inna tace "Toh kun
gani, ae ba ayi ma lefe kallon haramun haka, idan anyi saisa saisa sae a tashi
kuma" Wata er uwar Mumy dake zaune parlon tace "Toh yanzu yaushe za a kai kayan
Hajiya?" Inna tace "Aa wannan sai sanda Ibrahim ya sa mana lokaci, muna isa Habujan
dama sai ayi waya da Halilun ya sanar a gida ga fa mu nan zuwa da kaya niki niki,
kun ga ai kafin mu karasa sun mana girki irin tasu ko? tunda ance Abujan ma tana da
girma" Matar tace "Toh mutane nawa ne za su je kai kayan idan lokacin yayi?" Inna
ta kalleta daga sama har kasa, ta sake kallonta da kyau, can dai tace "Sirara ma za
a tafi da saboda matsi a cikin mota, dama daga ni sai Jamila da wannan da aurenta
ya mutu wato Kamila za mu je, kinga ai duk bamu da jiki, Ita Sumayya an barta ta ji
da jinyar goshinta da hannu kar a fama mata a hanya, amma dama ai ba gayya za ayi
ba" Matar bata sake cewa komai ba, bude kofar parlon aka yi Nihal ta shigo da
trolley dinta, Inna tace "Oyoyo yan makaranta"

Khalil bai ji dadin rashin ganin Nihad ba sanda zai tafi wajen karfe sha daya da
rabi na safe, wai Mami tace su tafi su yi gyaran gashi da Mimi, he don't know how
to ask Mami wani saloon din suka tafi, don yayi ta kiran layin Nihad din a kashe,
Mimi kuma bata picking, sai yayi tunanin ko Mimi bata tafi da wayarta ba, Har ya
isa airport mood dinsa was so dull.... Da yammacin ranan sojoji suka shigo da
Hassana gidan tana dingishi da kyar, kana ganinta kasan ta ci baƙar azaba hannunsu,
dama basu shigo gidan ba sai da suka Sanar ma Janar zuwansu, yana tsaye babban
parlor kuma suka shigo, har bangarenta ta kai su suna biye da ita babu rahama a
fuskarsu, Janar ya bi bayansu, tsabar yanda hannunta ke ciwo ta kasa daga wani
babban akwatinta dake dakin, wani soja ya sauke mata akwatin ta bude lock din ta
hau ciro atamfofi kusan kala talatin wanda bata dinka ba, yawancinsu super ne da
holland, can kasan akwatin ta ciro wani envelope, sojan ya dauki makeken sarka da
dankunnen gwal da zobe sun kusa biyar dake kasan akwatin, Tana zare ido tace
"Takardu fa ku ka ce, kuma ga su" Sojan ya fizge envelope din hannunta ya mika ma
Janar ya amsa ya bude ya ga takardun gida ne har hudu, Ya mayar cikin envelope din
yace "Akwai saura..." Hassana ta fashe da kuka tace "Ni su kenan wllh wllh, ba wani
takardan gida..." Wani naushi sojan kusa da ita ya kai mata a baki, Janar ya mika
masu envelope din yace "Ku mayar ku kulle akwatin ku fitar min da shi" Suka yi
yanda yace, Janar na kallon Hassana yace "Na baki awa daya ki tattara komai naki ku
bar min gidana dake da yaranki gaba daya" Ta fashe da matsanancin kuka ta durkusa
kasa tace "Yaya ka mance tsakanina da kai ne? Kanwarka ce fa ni, Yanzu duk inda
mahaifiyarmu take zata ji dadin wannan walakanci da tijaran da ka min Yaha" Yana
kallon sojojin strictly yace "Awa daya za ku jira ta hada komai nata ta bar min
gidana ita da yaranta, sannan ku yi alerting sojojin anguwan she is no longer
welcome in my house...." Yana gama fadin haka ya juya ya fita, babu bata lokaci
Aunty Hassana ta hau hada kaya tana kuka sosai kamar ranta zai fita, ga gwala-
gwalan nata ma duk suna akwatin, sai ma sun bude wani zip din za su gansu kaca kaca
sun yi na miliyan 40, duka duka account din nata ko dubu dari bakwai bai kai ba, ta
ina zata fara???? cikin minti arba'in ta dau iya abinda zata iya dauka a dakinta,
ta sa su Sajida ma duk suka hada kayansu suna kuka, sojojin suka tasa keyarsu aka
fitar da su daga anguwan gaba daya suka yasar da su bakin titi....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via

07087865788

Assalamu alaikum
Barkanmu da war haka masoya Khaleesat da Nihad🥰. Nasan kowaccenku na cike da son
sanin turarukan da wadannan taurari namu guda biyu ke amfani dashi dake tafiyar da
xuciyar maxajensu ya rikita musu lissafi ya kuma goge masu hada😌.
Toh turaruka neh na oil masu kamshi sosai da rike jiki daga scentmania. Wadannan
turaruka sunfi kala goma. Dan mace ba'a Santa da xama da kamshi iri daya kullum ba.
Dole adinga jin kamshi ma banbanta ajikinta kullum. Ana hada wadannan turaruka biyu
xuwa sama asaka alokaci guda dansu bada sihirtaccen kamshin dake tafiyar da
hankalin duk wanda ya shaka.
Dan haka muka hada package na wadannan turaruka muna kiranshi da 'Nihad pack' 🔥 🔥
Akwai Nihad silver pack: ya kunshi turaruka kala biyar. 6mls guda biyu da 3mls
guda uku N5000.
Akwai Nihad gold pack: ya kunshi turaruka kala bakwai. 6mls guda uku da 3mls guda
hudu
Sannan akwai Nihad diamond pack: ya kunshi turaruka kala 8. 10mls guda daya 6mls
guda hudu 3mls guda uku.
Ga sunayen turarukan nan kamar haka
1. Love letter (na musamman akowani pack akwaishi)
2. Baccarat Rouge
3. Jadore
4. La vie est belle
5. Pink shiffon
6. Pure seduction redplum
7. Versace Eros woman
8. Black Opium
9. Kim Kardashian
10. Love spell
Note that turarukan package a discounted price aka bada, kuma ana hada scents din
da sukayi complimenting juna neh yadda xaifi tashin kai in anyi amfani dashi. Amman
in kinason kiyi maki choice dinki shima ana badawa standard price dinmu 3mls N800,
6mls N1500 10mls N3000
Akwai 20mls N5000, 30mls N7000 and 50mls N10000. Turaruka araha ina mai tabbatar
maki kikayi amfani dasu sai kin dawo. Mudae burinmu kowa tayi kamshi na musamman🥰🥰💖
NIHAAD 💖

67

Bayan kwana biyu da tafiyar Khalil aka fara shirye shiryen biki a gidan, kai da
ganin irin IV din da aka buga kadai kasan bikin na masu kasar ne, kusan kullum Mami
sai ta fita for the wedding preparation, biki ne na gani na fada ake shirin yi, a
kwana a tashi dae har bikin ya rage saura sati daya, tuni Noor ta koma gidansu
Nadeeyah ta tare a can su ma suna nasu shirin da sauran kawayen Nadeeyah. Yau ma
kamar kullum Mimi ta gama shirin tafiya school ta juya tana kallon Nihad da ba ta
da wani aiki sai kwanciya all this days a daki, a ko da yaushe kuma zaka ganta babu
walwala tare da ita, she look so dull, abincin ma wani lokacin sai Mimi tayi mata
da gaske take dan tsakura, all this while kuma duk kiran da Khalil zai yi ma Mimi
ta bata waya, sai dai ta amshi wayar amma baxata masa magana ba don Mimi na mika
mata wayar take fita daga dakin ta bata space, har ya ma gaji da kiran ya daina,
wayarta kuwa dama ta kashe ta ajiye kusan sati biyu kenan, a daddafe ya iya yin
kwana sha biyu a Jamus don gaba daya hankalinsa yayi gida ba kuma wajen kowa ba
wajen Nihad, rashin maganan da take masa via phone call ya damesa sosai.... Mimi ta
ajiye handbag dinta ta zauna gefen gado tana kallonta tace "Nihad me yasa baki
maganar makarantarki ne yanzu?" Nihad ta daga kai ta kalleta amma bata ce komai ba,
Mimi tace "Soon za ki ji ance exams fa, for almost 2 month now baki shiga lectures
ba, kuma naga ma kamar makarantar ne baki so ko??" Nihad dai bata ce mata komai ba,
Mimi ta mike ta dau jakarta tace "Sai na dawo, zan bar maki breakfast dinki a
parlon Mami ba sai kin je downstairs ba" A hankali Nihad tace "Allah ya tsare" Mimi
na fita ɓangaren Mami ta tafi zata sallameta, Mami na kallonta tace "Breakfast din
fa?" Tace "Ehh xan yi before leaving" Mami tace "Toh ita fa?" Mimi tace "Idan ta
fito zata yi, she is still lying down, zan aiko Bilkisu ta kawo mata nata nan
parlon" Kafin Mimi ta tafi ta sa mai aikin Mami ta kawo breakfast din Nihad nan
parlon Mami ta ajiye, wajen karfe tara Mami ta fita zuwa wajen wata kawarta warce
ita ce tayi assigning lafiyayyun chefs da za su yi girki na bikin, sae kusan karfe
sha biyu ta dawo gida bayan an mata calculation din nawa kudin abincin zai kama
gaba daya kuma ta tura masu, don tuni Janar ya tura mata a account dinta, Babu kowa
gidan yanxu sae ita da su Mimi da Nihad sannan mai aikinta, Hanan kuwa na can gun
uwarta, Janar ma yau kwanansa uku da tafiya India for checkup, the house is so
empty duk da dama can gidan babu hayaniya, Mami na isa ɓangarenta taga breakfast
din Nihad har sannan a ajiye bata shigo ba balle ta dauka, mamaki ne ya cikata ta
fita zuwa dakin Mimi, sae da ta kwankwasa kofar dakin sannan ta bude, kwance ta
sameta saman gado ba kuma bacci take ba, Nihad na ganin Mami ta mike zaune a
hankali, Mami tace "Me yasa baki shigo kinyi breakfast ba?" ta sunkuyar da kanta
bata ce komai ba, Mami tace "Toh tashi ki fito kiyi...." Nihad tace "Toh" Juyawa
Mami tayi ta fita, ta kira Bilkisu ta sa ta fita da Breakfast din tace "Make a new
one immediately" Bilkisu ta amsa da ladabi sannan ta dau abincin ta fita... Ba a
dau lokaci ba Nihad ta shigo parlon Mami tana jan kafa..., Hijab ne har kasa
jikinta, Mami dake zaune parlon tana kallonta tace "Bari ta kawo maki wani yanzu"
Nihad tace "Toh" Zata zauna kasa Mami tace "Zauna saman kujeran" Ba musu ta zauna
kan kujeran ta jinginar da kanta jiki, Mami dae sai kallonta take, can ta ci gaba
da Chatting da sister dinta Hamida da zata taso jibi daga Yemen tare da
mahaifiyarsu da kanninta mata biyu, tana sanar mata abinda zata taho mata da shi
daga Yemen, Nihad na ta zaune har bacci ya ɗan fara daukarta Bilkisu ta shigo ta
ajiye tray din hannunta a kusa da ita sannan ta fita, Mami tace "Shiga bedroom za
ki ga carpet karami ki dauko sai ki zauna a kai, zuwa anjima za a kawo na parlon
nan dazu aka fitar da wanda ke kasa" Nihad ta mike ta nufi bedroom din Mami, juya
mata taga parlon ke yi, tayi baya zata fadi Mami dake kallonta ta mike da sauri,
amma tuni har ta kai kasa, Mami ta nufeta da hanzari ta dagota zaune tana kallon ta
da mamaki tace "Are you okay?" Kasa cewa komai Nihad tayi don har sanan kanta juya
mata yake, Mami ta dagota tsaye tana rike da ita ta kai ta bedroom din dinta, ta
taimaka mata ta zauna gefen gadonta tace "Sannu" Ita dai Nihad bata ce komai ba sai
sauke numfashi take a hankali, Mami ta juya ta fito parlor, shayi me kauri ta hada
mata a mug ruwan zafin ma ba da yawa ta zuba ba tayi diluting da Table water sannan
ta koma dakinta, kwance ta gan Nihad gefen gadon idonta a rufe, Mami ta ajiye mug
din shayin dake hannnunta ta dagota tace "Tashi ki sha shayin, it's already noon"
Nihad ta mike zaune a hankali, Mami ta dau mug din ta mika mata, amsa tayi ta kai
baki ta fara shan shayin. Mami ta juya ta fita daga dakin, ko rabin shayin Nihad
bata sha ba ta ajiye da sauri tana toshe bakinta, bata san sanda ta zabura ta mike
tsaye ba har ta nufi kofa ganin aman ya riga ya taho mata kawai ta dawo ta shige
bandakin Mami, nan ta dinga kwarara amai, Mami dake parlor ta mike da sauri ta koma
dakin don a bude ta bar kofar shi yasa ta juyo kakarin amanta, bandakin ta shiga ta
dafata tana kallonta tace "Sannu" Nihad ta kasa cewa komai, bayan ta wanke bakinta,
Mami ta cire mata Hijab din jikinta sannan ta koma dakin da ita ta zaunar da ita
gefen gado tana mata sannu, Nihad ta kasa ci gaba da zama kawai ta kwanta gefen
gadon, Mami ta koma bandakinta don ta gyara, ko da ta fito bacci ta tadda Nihad
take yi, ta fita parlor ta dau wayarta ta kira Dr Rukayya bayan sun gaisa tace mata
ta zo gida zata duba mara lafiya. Mami na ta zaune parlonta bayan minti talatin da
kiran Dr Rukayya aka bude kofar parlon, ta daga kai tana kallonsa, ya karaso ciki
da sallama, ya zauna saman kujera ya cire face Cap dinsa sannan ya gaisheta, Mami
ta amsa tace "Ya hanya?" Yace "Alhamdulillah, ya gida" Tace "Lafiya lau" Tace "Dama
tafiyar ta sati biyu ce?" Ya ɗan shafa kansa yace "Eh" Mami tace "Ohk" Yace "Naga
ba kowa a gidan Mami" Mami tace "Mimi ta tafi makaranta, Noor na gidansu Nadeeyah"
a hankali Khalil yace "Ok...." Mami bata sake ce masa komai ba, bayan few seconds
yace "What about Hanan?" Mami tace "Washegarin ranan da ka tafi ita ma ta tafi
kaduna" Yace "Ohk" Suna ta zaune parlon for almost 5 minutes, bai ce mata komai ba
ita ma haka, Wayarta ne ya fara ring tana dubawa taga Dr Rukayya ce, Mami na dagawa
ta sanar mata tana compound, Mami tace "Ohk, bari Bilkisu ta karaso ciki da ke"
Mami ta katse wayar ta kira Bilkisu, shi dai kallon Mami kawai yake, ya rasa ta ya
zai ce mata ina Nihad, don yana shigowa gidan dakin Mimi ya fara nufa amma yaga ba
kowa ciki, ya koma visitor room dake bangaren Mami nan ma yaga ba kowa ciki, har
Mimin ya kira yaji inda suka je amma tace masa ai ita tana makaranta Nihad kuma na
gida ta bar ta, Mami na gama waya da Bilkisu ta ajiye wayar a gefenta, Jinginar da
kansa yayi jikin kujera yana ta kallonta, Mami ganin kallon da yake mata tace "Toh
sai ka tashi kaje kayi wanka ka nemi abinda zaka ci ka bani waje ko??" A hankali
yace "I am okay" Mami tace "Toh ka bani waje za a shigo min da bakuwa yanzu" Cike
da karfin hali yace "Mami tare suka fita da Mimi ne?" Mami tace "Wa?" Sai kuma ya
kasa cewa komai, Mami tace "Baka da number Mimin ne?" Yayi shiru yana kallonta,
bata sake kallon inda yake ba har Bilkisu ta shigo da Dr Rukayya, Khalil ya dinga
kallonta, Ta gaida Mami da ladabi, Mami tace "Sannu da zuwa Dr" Dr Rukayya ta kalli
Khalil murmushi kwance fuskarta tace "Barka da rana ranka shi dade" Yace "Longest
time Dr" Tace "Ai kam ka buya" Mami ta mike tace "Mu je ciki Dr" Dr Rukayya ta bi
bayanta zuwa bedroom dinta, Khalil ya bi su da kallo har suka shiga, kasa daurewa
yayi ya mike ya bi bayansu, Tsaye yayi bakin kofar dakin yana kallon Nihad dake
bacci saman gadon Mami, Dr Rukayya dake duke dab da ita tana kallonta ta kai
hannunta a hankali goshinta to feel her temperature, sosai taji jikinta yayi zafi,
Dr Rukayya ta mike tana kallon Mami tace "Tun yaushe ne bata da lafiyan?" Mami tace
"I just noticed today, da yake ba bangaren nan take ba tana dakin Mimi ne" Dr
Rukayya ta gyada kai tana kallon Nihad da ta bude ido a hankali tana kallonsu, Mami
na kallonta tace "Ya jikin?" Kai kawai ta iya gyada mata, Mami tace "Toh ki dubata
Dr bari in baku waje" Tana fadin haka ta juya ta bar wajen, Khalil bai bari sun
hada ido da Mami ba ya juya da sauri shi ma ya bar bakin kofar dakin, ko da ta
shigo parlon bata gansa ba ya koma can first parlor, Dr Rukayya ta duka tana kallon
idon Nihad da kyau, ta dago hannunta tana kallon fingers dinta, calmly tace "When
last did u see ur period?" Nihad tayi shiru, sai kuma ta buda hannu alamar bata
sani ba, Dr Rukayya tace "Akwai abu a bakin ki ne da baki son bude bakin kiyi
magana Dear" Nihad ta girgiza kai cike da karfin hali tace "Aa" Dr Rukayya tace
"Good, now tell me how you r feeling?" Nihad ta jingina da gadon cikin sanyin murya
tace "Ina jin jiri idan na tashi, sannan in na ci abu sai in fara jin amai, i am
feeling dizzy..." Shiru tayi daga haka, Dr Rukayya tace "Tun yaushe kika fara jin
hakan?" Ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Not too long" Dr Rukayya tace "Good, koma ki
kwanta" Nihad ta kwanta a hankali, Dr Rukayya ta juya ta fita daga dakin zuwa
parlor, zaune ta tadda Mami ita kadai a parlon, ta zauna saman kujeran dake kusa da
Mami tace "Hajiya ina mijinta kuwa?" Mami tace "Shi kika tarar dazu ai da kika
shigo" Ta ɗan buda ido da mamaki tace "Wai Dr Khalil?" Mami tace "Eh" Dr Rukayya
tace "Maa sha Allah, ashe surkarki ce wallahi da na ganta fara na zata ko yarinyar
er uwarki ce, maa sha Allah that's nice, ashe Khalil yayi aure ba labari" Mami dai
kawai ta ɗan yi murmushi, Dr Rukayya na dariya tace "Yana matsayin likita amma
baxai duba matarsa ba sai an kira mata likita daga waje, ko rudewa yake... Kinsan
haka wasu likitocin suke" Mami tace "Toh yanzu dai me ke damunta?" Dr Rukayya na
murmushi sosai tace "Congratulations
Hajiya, u are going to be a grandmum soon, duk da na so sai anyi test kafin in
sanar maki but duk wani symptoms na ciki na gani a jikinta, ur in-law is pregnant"
Mami ta dinga kallonta ko kiftawa babu, can ta sauke idonta a hankali tace "Toh
Alhamdulillah" Dr Rukayya tace "Yanzu zan dauko Pt test strip a motata, don dake
tabbatar da hakan" Mami tace "Toh" Daga haka ta nufi kofa ta fita, ba a wani dau
lokaci ba sai ga ta da Urine specimen container da pt test stip, ta shiga dakin
Mami ta gaya ma Nihad yanda zata yi amfani da shi sannan ta kama hannunta zuwa
bandakin don ta kasa tsayawa sbda jiri, Dr Rukayya na ta jiranta a dakin bayan
minti shidda ta bi ta zuwa cikin bandakin, murmushi tayi ganin test din was
positive, bayan sun fito ta fita tayi discarding strip din da container, ta dawo
parlor ta sake congratulating Mami da ke zaune looking speechless. Bayan fitar Dr
Rukayya ta siyo drugs da alluran da zata ma Nihad, Mami dai na ta zaune parlor ta
kasa ma shiga ciki ta duba Nihad din, can dai ta mike daga karshe ta shiga cikin
dakin.... After Zuhur Khalil ya sake dawowa bangaren Mami, zuwa lokacin Dr Rukayya
tayi ma Nihad duk abinda ya kamata ta wuce, Babu kowa cikin parlon amma ya kasa
karasawa cikin bedroom din don bai san ko Mami na ciki ba, ya tsaya for almost 2
minutes contemplating kafin ya karasa ya tura kofar a hankali, Nihad ce kawai
kwance dakin tana bacci restlessly, ya sauke wani ajiyar zuciya ganin Mami bata
ciki ya karasa da sauri, ya zauna gefen gadon ya kai hannu forehead dinta yana kare
mata kallo keenly, he sat there looking at her for almost 2 minutes, sai kuma yayi
wani murmushi dai dai nan ta bude ido a hankali don baccin yin sa kawai take don
dole, All her body is just weak, gashi ko tunanin abinci tayi sai taji zuciyarta na
tashi amai na taho mata, Daure fuska tayi ganinsa, yayi kasa da murya yace "How are
you feeling?" Ta kara hade rai zata juya masa baya ya dagota zaune, yayi kasa da
murya cike da damuwa yace "To me na maki kike ignoring magana da ni for two weeks
now?" A fusace tace "Ni ka kyaleni don Allah" Yace "Ki gaya min laifin me nayi?"
Tace "Toh ai ba dole sai da ni kawai zaka yi waya ba tunda kana da warce ita ma
zaka iya waya da ita" Kallonta yake yi da mamaki, ta fizge hannunta zata juya masa
baya ya jawota ya rungumeta jikinsa yace "But ai ke kadai ce matata, ko da wacece
zanyi waya ai ba matata bace tunda ba aure tsakaninmu" A hankali ta sakar masa kuka
ya lumshe ido thinking of what to say to her don sarai ya gama gano ta, dai dai nan
aka bude kofar dakin kafin yayi saurin saketa har Mami ta shigo, Nihad taji kamar
kasa ya bude ta shige kawai ta huta, Ya mike da sauri ya kasa dago kai balle su
hada ido da Mami, sai kuma ya nufi kofa, Mami ta bi sa da wani kalloz a takaice
tace "Go back and take her to ur room" Tana fada masa haka ta juya ta bar dakin,
sai a sannan ya dago kansa yana sosa keya, can kuma ya koma wajen Nihad yace "Tashi
mu tafi" Wani kallo tayi masa tace "Wallahi baxan je ba ai ni ba fitsararriya bace"
Ya wara ido yace "Ni ne fitsararre?" Komawa tayi ta kwanta ta juya masa baya, yayi
murmushi ya juya ya fita daga dakin. Sanin Mami is watching his move ya sa ya
shirya bayan la'asar ya tafi gidansu Nadeeyah... Yana ta zaune compound din gidan
sai ga ta ta fito, shi dai ya ma rasa gane kanta for almost 3 weeks now, ta zauna
saman kujera without looking at him tace "Ina wuni" yayi shiru yana kallonta, ta
daga kai ta kallesa jin bai amsa gaisuwarta ba, yayi kasa da murya yace "Now tell
me ur problem pls Nadeeyah, is it Nihad? In dai ita ce u need not to bother plss ba
gida daya zaku zauna ba, sai ma ku yi wata da watanni baku ga juna ba i am assuring
you, pls ina son ki kwantar da hankali ki daina duk wani kokwanto a ranki, kuma ki
sa a ranki i owe u a lot saboda halaccin da kika min" Nadeeyah tace "And this is
the fifth time u are saying this to my ears, komai kace saboda halaccin da na maka
ba, ko kuma kace baza ka karya alkawarin auren da ka min ba... so what i want u to
make me understand now is that saboda abun da kake ganin na maka ne kake so ka
aureni so that it wont be like baka min adalci ba, ko kuma saboda alkawarin da kake
ikirarin ka min na aure shine zai sa ka aureni don ka zamo me cika alkawari or
whatt?" Khalil yayi shiru yana kallonta babu ko kiftawa, tayi wani murmushi tce "No
talk to me" Yace "Why are you complicating issues Nadeeyah? Me yasa zaki yi wannan
tunanin?" Ta girgiza kai tace "You are the one complicating issues Kjay, bana
mantawa kwanakin baya na tambayeka me ya kai ka gidansu Nihad driving, a ina kasan
su har kaje gidansu, but u told me that should be a story for another day, kaga sai
yanzu na fahimci cewar saboda ita kaje gidansu ka nemi driving don ka zauna a gidan
har ka aureta" Khalil ya zaro ido yana kallonta yace "Billah ban taɓa ganinta ba
sae da naje gidan, kin ji na rantse, kuma Nadeeyah na gaya maki times without
number mahaifinta ne ya hada aurena da ita, wllh at first bata san ni aka aura mata
ba mw" Nadeeyah ta mike tace "My frnds are waiting for me inside kuma wucewa suke
son za su yi" yayi shiru yana kallonta, can yace "Ohk sae mun yi waya, ki gaida
Mumy" Daga haka ya mike ya nufi motarsa ita kuma tayi wucewarta cikin gidan.

Inna ce zaune saman kujera a dakin Umma, ga Umman kwance saman gado ana kara mata
ruwa sai nishi take Kamila da Nihal na zaune gefenta, Zaune a dakin Mumy ce da
matan yayan Abba duk sun zo duba Umma, Hajiya Turai ma na zaune daga bakin kofar
dakin, Inna tace "Toh ni dai bamu san kan ciwon Sumayya ba gaskiya, abu kamar wasa
karamar magana ya zama babba, daga fasa goshi da targade a hannu, anya ba aljanu
suka shafeta ba kuwa" Babu me cewa komai dai a dakin, sallama aka yi can parlor
Inna tace "Kuma masu shigowa dubiyan nan ma ya kamata a hanasu haka don ba a san
zuciyar wani ba, banda haka ciwo yaki ci yaki cinyewa, ta ina zamu kama hanyar kai
akwati hankali ba a kwance ba, kila ma har sun gaji da jira a can Habujan kada ma
suyi tunanin cinye kudin aka yi" Husnah ce ta makale jikin kofar dakin ganin mutane
da yawa zaune ciki sai wuwwurga ido take, lokaci daya kuma tana sosa gabanta daga
cikin Hijabin jikinta, gaba daya tayi wani zuru zuru da ita kamar ba Husnah ba,
Hajiya Turai ta yamutsa fuska jin wani axababben doyi da ya bugi hancinta, Inna ta
toshe hanci da gyalenta a gigice tace "Wacece wannan kuma? Ba haya tayi a wando ko
me?" Husnah ta ɗan durkusa tana in ina tace "Aa wajen Umma na zo dama... Umma nake
nema" Umma dake fama da kanta ta ɗan bude ido daya tana kallon Husnah, Inna na kara
toshe hancinta a gigice tace "Wacece Umma, me zata maki?" Husnah ta fashe da kuka
tace "Ni dai dama inda zan samu Nihad nake nema, ko ta waya ne don Allah" Inna ta
mike da sauri ta koma can kofar bandaki tace "Wai wannan doyin meye haka yake
gigita ni...." Mumy na kallon Husnah jin abinda tace, tace "Me Nihad din zata maki
kike nemanta?" Umma ta mike zaune da sauri ba tare da ta shirya ba tace "Ke ya zaki
fado ma mutane daki haka kai tsaye?? Daga ina haka?"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

Assalamu alaikum
Barkanmu da war haka masoya Khaleesat da Nihad🥰. Nasan kowaccenku na cike da son
sanin turarukan da wadannan taurari namu guda biyu ke amfani dashi dake tafiyar da
xuciyar maxajensu ya rikita musu lissafi ya kuma goge masu hada😌.
Toh turaruka neh na oil masu kamshi sosai da rike jiki daga scentmania. Wadannan
turaruka sunfi kala goma. Dan mace ba'a Santa da xama da kamshi iri daya kullum ba.
Dole adinga jin kamshi ma banbanta ajikinta kullum. Ana hada wadannan turaruka biyu
xuwa sama asaka alokaci guda dansu bada sihirtaccen kamshin dake tafiyar da
hankalin duk wanda ya shaka.
Dan haka muka hada package na wadannan turaruka muna kiranshi da 'Nihad pack' 🔥 🔥
Akwai Nihad silver pack: ya kunshi turaruka kala biyar. 6mls guda biyu da 3mls
guda uku N5000.
Akwai Nihad gold pack: ya kunshi turaruka kala bakwai. 6mls guda uku da 3mls guda
hudu
Sannan akwai Nihad diamond pack: ya kunshi turaruka kala 8. 10mls guda daya 6mls
guda hudu 3mls guda uku.
Ga sunayen turarukan nan kamar haka
1. Love letter (na musamman akowani pack akwaishi)
2. Baccarat Rouge
3. Jadore
4. La vie est belle
5. Pink shiffon
6. Pure seduction redplum
7. Versace Eros woman
8. Black Opium
9. Kim Kardashian
10. Love spell
Note that turarukan package a discounted price aka bada, kuma ana hada scents din
da sukayi complimenting juna neh yadda xaifi tashin kai in anyi amfani dashi. Amman
in kinason kiyi maki choice dinki shima ana badawa standard price dinmu 3mls N800,
6mls N1500 10mls N3000
Akwai 20mls N5000, 30mls N7000 and 50mls N10000. Turaruka araha ina mai tabbatar
maki kikayi amfani dasu sai kin dawo. Mudae burinmu kowa tayi kamshi na musamman🥰🥰💖
NIHAAD 💖

68
Inna bata ba Husnah chance din magana ba ta daka mata wani tsawa tana kara toshe
hanci tace "Don Allah ki fita ki bamu waje, wacece kuma Nihad, Nihad da ke gidan
mijinta ɗan Janar Jikamshi, meye hadinki da ita" Umma da zuciyarta ke bugawa sosai
tace "Turai don Allah ki fitar mana da ita zuciyata tashi take...." Husnah ta
marairaice tace "Ko number...." Hajiya Turai ta mike da sauri cikin daga murya tace
"Fita ki bamu waje, fita" Juyawa Husnah tayi da sauri ta bar bakin kofar ganin
Turai ta yo kanta gata jibgegegiyar gaske, Nihal ta bi Husnah da kallon mamaki,
Umma ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya ta koma da kyar ta kwanta har sannan
gabanta na faduwa, Inna tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Da kyar idan ba
wani cutar bane ya kamata, amma wannan doyin gaskiya ba na lafiya bane, a bude mana
window a kara Ac...." Mumy ta ji kamar ta bi bayan Husnah taji neman me take ma
Nihad, tana ta nazarin maganan nata amma ta kasa tashi sai kallon kofar dakin take.
Ana idar da magrib Mami ta shiga dakinta, tun yamma take da baƙi a gidan basu tafi
ba sai dab da magariba, tana kallon Nihad dake kwance saman darduma tace "Me yasa
kika kwanta a kasa?" Cike da karfin hali tace "Sallah nayi" Mami tace "Toh koma
saman gadon" Nihad ta mike ta kwanta kan gadon, tun dazu zazzabin ya dawo mata
sosai amma a haka ta daure ta tashi tayi sallah, Mami ta dauke darduman ta ajiye
inda yake sannan tace "Me kike son za ki ci yanzu?" Nihad ta girgiza mata kai
kawai, Mami ta kashe Ac din dakin ganin kamar sanyi take ji, sannan tace "A kawo
maki Custard za ki sha?" Nan ma Nihad ta girgiza mata kai kawai, Mami ta juya ta
bar dakin, Bilkisu ta kira ta sa ta dama Custard din, ba a dau lokaci ba sai ga ta
ta shigo da shi a cup Mami ta amsa ta kai cikin dakinta tana kallon Nihad ta ajiye
Cup din a kasa tace "Bari ya ɗan huce sai ki tashi ki sha" Daga haka ta tafi ta
gyara curtains din dakin sannan ta rage hasken wutan ta fita.... Bayan minti goma
Mami ta sake komawa dakin, ganinta still a kwance tace "Ai ya huce haka, tashi ki
dauka ki sha" Nihad ta mike zaune, Mami ta dau cup din custard din ta mika mata,
amsa tayi amma tana kallon cikin cup din taji zuciyarta ya fara tashi, ta kauda kai
tace "Bazan iya sha ba" Mami tace "Toh me za ki ci?" Shiru tayi bata ce komai ba,
Mami tace "A kawo shayi?" Nan ma dai girgiza kai tayi, Mami tace "Kin dai san baza
ki kwanta da yunwa ba ko? Think of anything you want to take ayi a kawo maki yanzu"
Hawaye ne ya cika idonta, Mami ta karasa kusa da ita cikin kwantar da murya tace
"Shayin ma baki so?" Ta gyada mata kai, Mami tace "Toh a siyo maki abu a waje zaki
ci?" Nihad ta gyada mata kai, Mami ta juya ta fita daga dakin, wayarta dake parlor
ta dauka tayi dialing number Khalil, yana fara ring ya daga tace "Eatry zaka je
yanzu ka siyo abinci ka kawo min" Yace "Abinci? Wani irin abinci?" Mami tace "Idan
an samu pounded yam ko Semovita with vegetable soup" Yace "Ohk" Katse wayar tayi ta
zauna saman kujera. Ba a dau lokaci ba Khalil ya dawo rike da ledan takeaway din
abincin, ya ajiye parlon Mami yana kallonta, tace "Na manta ban ce ka hado da
fruits ba" Yace "Yanzu komawa za ayi a siyo fruits din?" Mami tace "Ehh" Juyawa
yayi a hankali ya fita daga parlon, ta dau abincin ta shiga dakinta da shi, ta kira
Bilkisu ta kawo mata plate, tana gama zuba pounded yam din a plate ta kalli Nihad
tace "Sauko kasa ki ci" Nihad ta mike zaune ta sauko kasa ta zauna kan rug da ta
shimfida mata tana kallon pounded yam din, it looks so enticing kuma bata ji
zuciyarta na tashi ba, Ta kalli ruwan wanke hannu da aka ajiye mata ta wanke
hannunta sannan ta fara cin pounded yam din, Mami tace "Do not rush it, idan kin ci
kadan ki rufe anjima sai ki ci sauran" Nihad ta gyada mata, Mami ta dauko mata
magungunanta ta ajiye gabanta sannan ta juya ta fita, Nihad bata wani ci da yawa ba
kamar yanda Mami tace mata, ta dau maganinta ta sha sannan ta rufe abincin ta tafi
bandaki ta wanke hannunta, ta dauro alwala ta fito tana idar da sallah ta kwanta
bacci ya dauke ta. Wajen karfe sha biyu saura Mami ta shigo dakin ganin idonta biyu
tace "Za ki sha kankana a kawo maki?" Nihad ta girgiza mata kai Mami ta dau abinda
zata dauka ta fita daga dakin.... Da kyar Nihad ta bude ido ta sauko daga saman
gadon Mami ta durkusa saboda daure mata da mararta yayi, Mami dake zaune saman
darduma ta kunna wutan dakin tana kallonta tace "Ya aka yi?" Tana yarfe hannu cike
da karfin hali tace "Cikina ke min ciwo" Mami ta mike da sauri tace "Ciki kuma?"
Kallon agogo tayi taga karfe uku saura na dare, ta zagayo side din da take tace
"Sannu, tashi zauna gefen gadon" Mami ta dagota zata zaunar da ita gefen gadon taga
stain din jini a rigar jikinta, cikin tashin hankali tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un" Nihad ta koma ta durkusa saboda murda mata da maran ke yi sosai,
Waya Mami ta dauko da sauri tayi dialing number Khalil, sai da ya kusa katsewa ya
daga, Tace "Ka taho part dina yanzu yanzu" Daga haka ta katse wayar, ta kara dago
Nihad tana mata sannu, duk ta rikice ta rasa abinda zata yi... Khalil na shigowa
dakin ya nufosu da sauri ganinta rike da Nihad yace "Me ya faru Mami?" Mami tace
"Wai cikinta ke ciwo and she is bleeding ko za mu tafi asibiti ne?" Ai bai san
sanda ya amshi Nihad daga hannunta ba hankali tashe yana kallonta yace "When did u
start bleeding?" Ta kasa ce masa komai sai sai hawaye ke sauka idonta, tuni Mami ta
dauko makullin motarta, ganin yanda ya tsaya shi ma ya rasa abun yi duk ya rude, ta
masa tsawa tace "Dallah ni ka fito min da ita mu wuce asibiti" Daga haka ta fice
daga dakin da sauri zata kai ma drivernta makullin mota kafin ya fito da ita,
Asibitin da ya fi ko wanne tsada a Abuja Mami ta sa suka tafi, kuma har suka isa
asibitin bata daina bleeding din ba, duk iya dauriyarta sai da ta fashe da kuka
sosai, likitocin suka shiga da ita emergency, tsabar rudewar da Khalil yayi har
mancewa yayi ashe shima fa likita ne, ya jinginar da kansa jikin bangon asibitin
with throbbing heart, he just cant say why he is bleeding that way, Mami ma ta kasa
zaune ta kasa tsaye a corridor din emergency ward din, she looks so disturbed,
lokaci daya Khalil jikinsa yayi mugun sanyi, he just can't imagine Nihad loosing
the pregnancy, ya kasa ci gaba da tsayuwa ya zauna kan kujeran dake wajen ya rike
kansa zuciyarsa na bugawa, bayan kusan minti arba'in wani baturen likita ya fito,
Mami na ganinsa ta nufesa da sauri, gabanta na faduwa da turanci take tambayarsa ya
ake ciki, yace ta samesa a office, sosai taji gabanta ya fadi, Khalil ya daga kai
yana kallon likitan har ya bar wajen, can ya kalli Emergency ward din, wani
bahaushe ne ya fito, Mami ta kara bin sa, cike da karfin hali tace "Likita ya ake
ciki don Allah??" Ya tsaya yana kallonta yace "Ki kwantar da hankalinki Hajiya, she
will be fine da izinin Allah, mu je office" Bin bayansa tayi zuwa office dinsa,
suna shiga ta zauna saman kujera ya kunna Ac din babban office din nasa ya zauna
yana kallonta kamar yanda ita ma take kallonsa, yace "Ki kwantar da hankalinki,
bleeding din ya tsaya amma there is high chances of her miscarrying the pregnancy
gaskiya" Mami ta dinga kallonsa babu ko kiftawa, sosai taji hankalinta ya tashi,
tayi karfin halin cewa "Cant anything be done about it pls Dr?? Babu abinda za a
iya yi?" Likitan ya girgiza kai yace "Kawai dai yanzu zan baku shawarwari ne ta
yanda za a tafiyar da cikin nata har Allah ya sa ta wuce stage din nan, she is just
4 weeks pregnant now, and she is having a cervical insufficiency kinga idan ba abi
a hankali ba sannan kuma ba wani iko na Allah ba she is going to loose the
pregnancy at anytime, bazai zauna ba..." Mami tayi shiru tana kallonsa ta ma rasa
abinda zata ce masa, he could see how worried she is, yace "Nan da sati biyu ya
kamata ku yi mata pre natal Ultrasound saboda its likely yan biyu take dauke
da...." Mami ta bude ido sosai tana kallonsa, ya gyada kai yace 'Yeah mun ga alamar
hakan but it's not as if we are 100% sure don at this stage ba a gani, Allah ya
bamu ikon gano hakan ne base on experience and how good we are" Yana murmushi ya
kare maganar, Mami dai ta kasa ce masa komai, Cikin kwantar da murya yace "In sha
Allah everything will be fine Hajiya, kar ki wani daga hankalinki, but nan dai da
sati biyu ayi Ultrasound din don tabbatarwa, by then she is 6 weeks pregnant" a
hankali Mami tace "Amma babu abinda ya samu cikin yanzu ko Dr?" Yace "Cikinta na
nan har yanzu, kawai dai yanzu zan baki measures da za a bi don gudun miscarrying
cikin, sannan we will keep her here for some days, Da farko well balanced meal,
kuma duk wani abu da zai dameta ya daga mata hankali da fargaba a gujesa gaskiya,
sannan she should be on bedrest, shi yasa nace za mu yi admitting dinta a nan na
yan kwanaki..." Sosai Mami ta basa attention dinta tana sauraronsa har ya kai
karshe, Bayan ya gama Mami tace "Idan aka bi duk abubuwan nan da ka fada ai
shikenan babu wani abu da zai samu cikin kuma ko Dr?" Ya ɗan yi shiru, sai kuma
yace "Hajiya to be sincere to u... the chances of keeping this pregnancy, and the
chances of loosing it is just 50/50, that's just the plain truth" Mami ta kasa ce
masa komai, can ta mike tace "Muna bukatar sallama zuwa da safe Dr" Ya daga kafada
yace "Alright then, Allah ya kai mu goben" Tace "Zan iya shiga in ganta yanzu?"
Yace "Sure, ai an maidata ward yanzu haka" Tace "Nagode" Daga haka ta fita daga
office din, wani likita ta tambaya ya gaya mata ward din da aka kai Nihad, tana isa
kusa da ward din ta tsaya ta ciro wayarta a jaka tayi dialing number Janar, hoping
he is going to pickup, yana fara ring kuwa ya daga, daga bangaren yace "Why are you
awake by this time??" Tace "Fatima ce bata da lafiya" Har Janar zai tambayeta
wacece Fatima kawai sai ya tuna warce take nufi wato Nihad, yace "Hasbunallah
what's wrong with her?" Mami tace "Na kira Dr Rukayya ta zo jiya ta dubata da na
fahimci bata da lafiya, bayan ta dubata ta tabbatar min tana dauke da ciki"
Janar ya ɗan yi shiru, can yace "Maa sha Allah, that's a good news, Allah ya bata
lafiya, maa sha Allah" Mami tace "Toh dazu Ina sallah wajejen karfe uku ta fara
bleeding, cause she is in my room" Janar yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,
kuna ina yanzu?" Tace "Muna asibiti, and they are telling me nonsense, that there
is high chances of her loosing the pregnancy, sannan cikin ma na yan biyu ne" Janar
yace "Take her away from that hospital immediately, i will make some calls now zuwa
gobe za ki fita da ita America....." Mami tace "Shi yasa dama na kiraka" Janar yace
"Ina khalil din?" Tace "Tare muka zo asibitin da shi, amma ni ban ga amfanin ma
zuwa da shi ba, yanzu na fito office din likitan wanda nake tunanin bai san abinda
yake ba gaskiya, har yana bani assurance akwai high chances of loosing the babies
who does that, i dont think he is okay" Janar yace "Ku koma gida ku fara shiri
kawai" Mami tace "Shikenan sai anjima" Daga haka ta katse wayar ta shiga ward din,
Khalil na zaune kusa da Nihad yana rike da hannunta yana kallonta, ita kuma tana
bacci, gaba daya ya zama wani iri kamar shi ne babu lafiyan, yana ganin Mami ya
juya yana kallonta, he doesn't look himself at all, gaba daya a sanyaye yake, Mami
ta nufi gadon tana kallonta ita ma, a hankali ya mike ya fita daga ward din zai je
gun likitan don jira yake ta fito dama. Da asuba Mami ta bar masu asibitinsu tare
da Nihad bayan ta biya bills din, dama sojan da ya kawota da motar soja guda daya
da ya biyosu suna cikin asibitin giving dem security tun a jiyan, gari ya fara
haske suka isa gida, Mami ta sauka daga motar tana kallon Nihad dake kokarin
saukowa tace "Ki fa yi a hankali" A hankali ta sauko daga motar Mami na biye da ita
a baya making sure ba sauri take ba suka shiga gidan, shi dai Khalil ya bi su da
kallo, Mami ta ajiye mayafinta ta shiga bandakinta ta hada mata ruwan wanka a
bathtub sannan ta fito dakin tace "Shiga kije kiyi wanka, and be careful as u do
so" Nihad ta tashi ta shiga bandakin, Mami ta koma parlonta ta tadda Khalil a zaune
tace "Ka hada mata kayan sakawanta da duk abinda zata bukata a jaka za mu tafi
asibiti..." Da mamaki yace "Asibiti kuma?" Wani asibitin?" Mami bata tsaya basa
amsa ba ta koma ciki ta dau wayarta, kanwarta Hamidah ta kira, yana fara ring
Hamidah ta daga, bayan sun gaisa Mami tace "Flight din naku yau din ne still
Hamida?" Hamida tace "Ummi fa bata gama siyayya ma jikokinta ba in gaya maki Yaya,
shi yasa ma bamu yanki ticket ba har yanzu" Mami tace "Toh ku bari ko nan da 2 days
ne don nima zan fita zuwa US yau" Hamida tace "Ohk me zaki yi a Us?" Mami tace
"Matar Khalil ce bata da lafiya za mu kai ta asibiti" Aunty Hamida tace "Ayya to
Allah ya bata lafiya, yarinyar da Aunty Maryam ta bani labari?" Mami tace "Ehh"
Aunty Hamida tace "Toh shikenan Mami zuwa jibin in sha Allah, Allah ya tsare hanya
ya shirye shirye?" Mami tace "Lafiya Alhamdulillah, ki gaida Ummi" Daga haka ta
katse wayarta. Ba laifi Nihad ta sha shayi har da dankali da safen kuma bata ji
amai ba, Mami dake dakin sai take ga kamar ko wani abu ya samu cikin ne tunda she
isn't looking sick anymore, ga kuma abinci ta ci sosai, this thought make her
palpitate, jiran kiran Janar kawai take duk da it's still 9am, Har ta gama hada
jakan kayanta ga na Nihad da ta ajiye a gefe bayan Khalil ya kawo mata, Nihad na
gama cin breakfast din sai bacci, Mami na ta zaune dakin bata fita ba har karfe
goma, sai ga kiran Janar Mami ta daga yace "Za a kawo mata B-2 Visa nan da karfe
sha biyu, zuwa da yamma za ku bar kasar in sha Allah" Mami tace "Toh Allah ya kai
mu" Yace "Ya jikin nata?" Mami tace "Toh da sauki, but i am hoping Allah ya sa ba
abinda ya samu cikin, yanzu dai bacci take" Janar yace "In sha Allah everything
will be okay" A hankali Mami tace "I hope so"Janar yace "Za mu yi magana zuwa
Anjima" Daga haka ya katse wayar, Mami ta juya tana kallon Nihad dake ta baccinta.
Mimi ce ta shigo dakin wajen karfe sha daya tana kallon Nihad da ke bacci har
sannan ta zauna gefenta tana kallonta, can ta kalli Mami tace "Mami tun baccin dazu
ne bata tashi ba?" Mami tace "Toh dole sai kusa da ita za ki zauna kiyi magana
Mimi, what if u wake her?" Mimi ta mike ta bar wajen ta koma kusa da Mami, Mami
tace "Kice ma Bilkisu da Sarah su gyara kajin nan Hajiya Safeenah zata zo anjima"
Mimi tace "Toh" Daga haka ta fita daga dakin... Bayan Azahar Hajiya Safeenah ta iso
gidan, Mami ta fito parlonta tace "Ni fa nayi tunanin tun dazu da kika kirani zaki
fito" Hajiya Safeenah tace "Sai da na fara biyawa wani waje kafin in zo nan" Mami
tace "Ya gajiya?" Hajiya Safeenah tace "Alhamdulillah, ya yaran?" Mami tace
"Lafiyansu Lau" ina Nadeeyah?" Hajiya Safeenah tace "Tana gida" Mami tace "Toh maa
sha Allah, wani magana kika ce za mu yi jiya kuwa" Hajiya Safeenah ta gyara zama,
bayan ta sauke ajiyar zuciya tace "Jiya da daddare dangin Baban Nadeeyah suka
kirani with different complaints..." Mami tace "Tohh, ikon Allah, me aka masu?"
Hajiya Safeenah ta girgiza kai tace "Wai mijin da Nadeeyah zata aura da babansa
basu je sun gaishesu ba anyi al'adun can, kawai ina ta iko da yarinya" Mami tayi
shiru tana kallon Hajiya Safeenah, can tace "Amma lokaci bai kure ba kuwa
Safeenah?" Hajiya Safeenah tace "Na gaya masu bikin saura sati daya suka ce ae
kawai a daga" Mami tace "Ikon Allah, to tun da basu fadi haka ba sai yanzu?" Hajiya
Safeenah dai bata ce komai ba, Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina ce mahaifin
Nadeeyah a Nigeria ya rasu?" Hajiya Safeenah tace "Toh yaushe rabonsa ma da Yemen
din kafin ya rasu, shekaransa kusan talatin a kasar nan, to idan ba tashin hankali
suke so ba meye na cewa sai anje an gaishesu bayan yana da ran ma ba damuwa suka yi
da shi ba" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh zan sanar ma Janar in sha Allah,
sai kawai a bi su a yanda suke so don a samu zaman lafiya" Hajiya Safeenah tace
"Wallahi ko bacci ban yi ba jiya, sun daga min hankali sosai, karamar magana ce
suka mayar babba" Mami tace "Kai, Allah dai ya kyauta" Hajiya Safeenah tace "Toh
Ameen" Mami tace "Dama dazu ce maki zanyi za mu je US ganin likita sae kuma kika ce
min ai zaki shigo yau ma" Hajiya Safeenah tace "Wa ye ba lafiya?" Mami tace "Matar
Khalil din ce ba lafiya" Hajiya Safeenah tace "Subhanallah, Allah sarki, Allah
Ubangiji ya bata lafiya, karfe nawa za ku tafi?" Mami tace "Zuwa la'asar in sha
Allah" Hajiya Safeenah tace "Toh Allah Ubangiji ya bata lafiya, tana ina yanzu?"
Mami tace "Tana ciki tana bacci" Hajiya Safeenah tace "Allah ya sa kaffara ne" Mami
tace "Ameen" Sun ɗan taɓa hira, Hajiya Safeenah ta ci abincin da su Bilkisu suka
kawo mata sannan tace ma Mami zata koma gida tana da baki, Mami ta rakata har Main
parlor, Hajiya Safeenah tace "In dai kun fita zuwa airport ki sanar min, sai in
hadu daku a can mu yi sallama Hajiya" Mami tace "Toh in sha Allah" Daga haka Hajiya
Safeenah ta bar gidan, Mami na komawa parlonta sai ga Khalil ya shigo, Ya zauna
yana kallonta yace "Ya me jikin Mami?" Mami tace "Alhamdulillah, ai kun yi waya da
Abbanka ko?" Khalil ya girgiza kai yace "Aa" Mami tace "Toh anjima za mu je USA da
ita a dubata da kyau" Ya sauke idonsa yayi shiru, can yace "Mami Visa fa?" Mami
tace "Yayi sorting komai out an kawo mata dazu" Yace "Amma na ganin likita ko?"
Mami tace "Ehh" Yace "Ohk" Mami tace "Yanzu Hajiya Safeenah ta fita gidan nan, wai
dangin mahaifin Nadeeyah sunce sai kai da Janar kun je sun sanku" khalil ya buda
ido sosai yana kallonta, Mami tace "Toh abinda suka ce kenan wallahi, ina ma son in
kira Janar din yanzu in fara gaya masa kafin mu fita kasar" Khalil dai bai ce komai
ba, can ya mike ya nufi dakinta ta bi sa da kallo, har sannan bacci Nihad take, ya
karasa kusa da gadon ya zauna gefen ya kamo hannunta, a Hankali ta bude ido tana
ganinsa murya can kasa tace "Yunwa nake ji?" Shima yayi kasa da murya yace "Me za
ki ci Dear?" Tace "Pounded yam" Yace "Ohk let me get u immediately" Da sauri ya
fita daga dakin Mami dai ta bi sa da kallo, kiran Janar ne ya shigo wayarta, tana
dagawa bayan sun gaisa yace "Ya jikin nata?" Mami tace "Alhamdulillah, bacci dai
kawai take yi" Yace "Toh Allah ya sauke, you should be cautious of time pls, kar
kuma kuyi missing jirgin" Mami tace "Ina duba agogo wllhi" Yace "Good" Tace "Kana
ji Janar?" Yace "Ina ji" Nan ta sanar masa abinda Hajiya Safeenah ta zo gaya mata
dazu, Janar yace "Waye zai kama ya tafi Yemen yanxu? Don't i have what to do??"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


Assalamu alaikum
Barkanmu da war haka masoya Khaleesat da Nihad🥰. Nasan kowaccenku na cike da son
sanin turarukan da wadannan taurari namu guda biyu ke amfani dashi dake tafiyar da
xuciyar maxajensu ya rikita musu lissafi ya kuma goge masu hada😌.
Toh turaruka neh na oil masu kamshi sosai da rike jiki daga scentmania. Wadannan
turaruka sunfi kala goma. Dan mace ba'a Santa da xama da kamshi iri daya kullum ba.
Dole adinga jin kamshi ma banbanta ajikinta kullum. Ana hada wadannan turaruka biyu
xuwa sama asaka alokaci guda dansu bada sihirtaccen kamshin dake tafiyar da
hankalin duk wanda ya shaka.
Dan haka muka hada package na wadannan turaruka muna kiranshi da 'Nihad pack' 🔥 🔥
Akwai Nihad silver pack: ya kunshi turaruka kala biyar. 6mls guda biyu da 3mls
guda uku N5000.
Akwai Nihad gold pack: ya kunshi turaruka kala bakwai. 6mls guda uku da 3mls guda
hudu
Sannan akwai Nihad diamond pack: ya kunshi turaruka kala 8. 10mls guda daya 6mls
guda hudu 3mls guda uku.
Ga sunayen turarukan nan kamar haka
1. Love letter (na musamman akowani pack akwaishi)
2. Baccarat Rouge
3. Jadore
4. La vie est belle
5. Pink shiffon
6. Pure seduction redplum
7. Versace Eros woman
8. Black Opium
9. Kim Kardashian
10. Love spell
Note that turarukan package a discounted price aka bada, kuma ana hada scents din
da sukayi complimenting juna neh yadda xaifi tashin kai in anyi amfani dashi. Amman
in kinason kiyi maki choice dinki shima ana badawa standard price dinmu 3mls N800,
6mls N1500 10mls N3000
Akwai 20mls N5000, 30mls N7000 and 50mls N10000. Turaruka araha ina mai tabbatar
maki kikayi amfani dasu sai kin dawo. Mudae burinmu kowa tayi kamshi na musamman🥰🥰💖
NIHAAD 💖

69

Mami tayi shiru tana sauraron Janar jin ya fusata sosai, ya ci gaba cikin fada yana
cewa "Me yasa tun farko basu kawo wannan batun ba sai yanzu da lokaci ya kure? Why
will they say this just a week to the wedding? Dama ita uwar yarinyar kadai ta
shirya abunta ta hada mu da masu amsan kudin auren yarinya ba tare da sanin dangin
ubanta ba, me yasa ku mata ku ke da karancin tunani ne wai?" Mami tace "Haba dai
ranka shi dade, aminin babanta ne fa, babanta ba shi da kamarsa har ya bar duniya,
tun a yemen suka san juna suka kuma ci gaba da zumunci har a nan, yau ko da uban
Nadeeyah na da rai ina tabbatar maka shi wannan Alhaji Mashkur din ne zai daura ma
Nadeeyah aure ba shi, dama tun asali dangin uban basu son Hajiya Safeenah saboda
Ubanta bafillatanin Nigerian ne uwarta ce er kasar yemen kaga ai ita bafullatana
ce, bayan ubanta ya rasu kuma mahaifiyarta ta koma yemen da ita, kawai dai suna son
daga ma Hajiya Safeenar hankali ne shi yasa suka billo da batun zuwa yemen gun
dangin Baban Nadeeyah, me yasa tun da aka sanar da su zancen auren basu ce haka ba
sai da lokaci ya zo, they knew nothing about the girls wellbeing, neman magana ne
kawai, don haka kayi hakuri tunda har sun ce a kara dagawa ai sai a daga din a bi
komai a sannu babu gaggawa, ayi making preparations na zuwa can Yemen din....."
Janar yace "Fatima" Mami tace "Ina jin ka" Yace "A dai nan kwana kusa daga sati
daya har zuwa sati biyar masu zuwa bani da time din zuwa Yemen to be frank with u,
i am occupied, nayi scheduling duk kwanakin nan, i don't have time, wait ma dai
tukun, idan ba rainin hankali ba ni me zanje yi masu a yemen, shi da yake neman
mata a can ai sai ya shirya yaje ya gaishesu, ni me zan je in masu?" Mami ta
girgiza kai tace "Aa mu ba haka ake a wajen mu ba gaskiya, da shi me neman auren,
da ubansa, da kawun uban nasa ne za ku je gaishe da dangin uban yarinyar, kai har
ma da dangin uwarta ko da a wani gari suke" Janar yace "I see" Mami tace "Ka daina
duba cewa ai shekaru 36 da suka wuce baka je can neman nawa auren ba, kar ka manta
a hannun wan mahaifina nake a kasar nan a wancan lokacin, you just have luck sai
bayan da aka yi aurenmu sannan suka koma can din gaba daya, banda haka da dole ne
sai kaje wallahi" Yace "To a sannan ina naga kudin zuwa Yemen?" Murmushi kawai Mami
tayi, sai kuma tace "Da da kudin ma ai danginka baza su bari kaje ba tunda ba sona
suke ba" Janar yace "Let me pick a call" Daga haka ya katse wayar, Mami ta sauke
wayar daga kunnenta tana tunanin ta inda zata fara convincing dinsa yaje gaida
dangin uban Nadeeyah, kallon agogo tayi ganin karfe uku ta mike da sauri ta shiga
daki don tada Nihad ta shirya su tafi airport, suna gama shiryawa ta kira Hajiya
Safeenah ta sanar mata ga su za su tafi airport, Khalil ya bi Mami da kallo babu ko
kiftawa, ta tafi ta dau Handbag dinta ganin kallon da yake mata tace "Kana kallona
haka, idan kuma in bar ka da ita ne to sai in bar ka ba sai naje ba, amma kada ka
kuskura in ganka a US ko a mafarki wallahi" Ita dai Nihad ta sa Hijab dinta Mami ta
saka ta a gaba suka fita daga dakin suka barsa nan tsaye kamar statue. Khalil na
zaune gaban motar Mami, ita kuma tana back seat tare da Nihad suka iso airport,
suka tarar da Hajiya Safeenah har ta isa airport din da wata er uwarta, Hajiya
Safeenah kadai Nihad ta gani ta dauke kai cikin dubara ta kuma ki sauka daga cikin
motar, Bayan Mami sun gaisa da er uwar Hajiya Safeenah tace "Ina Nadeeyah, tana
gida ne" Hajiya Safeenah tace "Aa tare muke, ta hadu da wata Coursemate dinta ce,
mun baro su can suna gaisawa" Mami tace "Allah sarki" Khalil ya zagoya ya gaida
Hajiya Safeenah da sister dinta suka amsa da fara'a, Hajiya Safeenah tace "Ya me
jiki? Tana ma ina ban ganta ba" Mami ta bude motar tana kallon Nihad da ta makale
ciki, sai ta fara kokarin saukowa daga motar Mami tace "Aa zauna ba sai kin fito
ba" Hajiya Safeenah na kallon cikin motar tace "Sannu kin ji, Allah ya sauwake, ya
baki lafiya" Nihad ta sunkuyar da kanta tace "Ina yini" Hajiya Safeenah tace
"Lafiya lau daughter, Allah ya baki lafiya kin ji" Ita dai Nihad bata ce komai ba,
sister dinta ma tayi mata fatan samun lafiya, daga nesa Nihad ta hango Nadeeyah na
tahowa haka kawai taji gabanta ya fadi, ta dai dauke kai daga kallonta har ta iso
inda suke, Nadeeyah ta gaida Mami da ladabi, Mami tace "How are you dear" Nadeeyah
tace "Alhamdulillah, ya me jiki?" Mami tace "Jiki Alhamdulillah" Hajiya Safeenah ta
koma gefe tare da Mami tace "Kinga ko da dangin Mahaifin Nadeeyah basu tado da
zancen aje can a gaishesu ba ai dole za a daga bikin nan har Allah ya ba takwararki
lafiya Hajiya" Mami tace "Toh yanzu na dai fara ma Janar magana amma bamu gama ba
gaskiya" Hajiya Safeenah tace "Aa da baki masa maganan yanzu ba ma, har sai Fatima
ta samu lafiya, lafiya ai yana gaba da komai Hajiya" Mami tace "Haka ne" Nadeeyah
na kallon cikin motar da Nihad take, har sannan da murmushi fuskarta ta ɗan saka
kai cikin motar cin sanyayyen murya tace "Hi, ya jikin, hope u are feeling much
better" Nihad ta ɗan kalleta, sai kuma ta mata wani kallo ta dauke kai ta tsuke
fuska tana kallon daya side din, duk Khalil na kallonsu but sai yayi saurin kauda
kansa, Nadeeyah ta bar jikin motar ta tsaya a gefe, gaba daya jikinta a sanyaye,
Khalil dai bai yarda ya kalli inda take ba, duk da yana son mata magana amma ya
kasa saboda Nihad, wanda ita ma sai kallo take taga ko zai mata maganan, Mami da
Hajiya Safeenah suna gama maganar da za su yi aka yi Conveying din Mami da Nihad
zuwa Lounge din da zasu jira har karfe hudu da rabi kafin tashin jirginsu, har
zagawa Khalil yayi zuwa daya side din mota kafin Nihad ta sauka zuwa Lounge yana
mata magana amma ta maka masa wani harara ta ki kulasa ta sauka Mami ta saka ta
gaba suka wuce, ya kalli Nadeeyah da har ta koma gun motarsu tana jiran Mum dinta
da Aunt dinta su karaso, yana kallon Drivern Mami yace "Bani makullin mota, ni zan
dawo da shi gida" Sojan zai yi magana Khalil ya ciro wayarsa yayi dialing number
Mami ya sa handsfree tana dagawa yace "Mami zan fita da motar ki" Mami tace "Ohk"
Bai sake kallon Sojan ba ya cire Makullin jikin motar ya kulle, ya nufi motar su
Nadeeyah, haka nan convoy da suka kawo Mami suka juya suka bar airport din leaving
Mami's Ride behind. Khalil na kallon Nadeeyah yace "Mu je in ajiye ki gida" ba tare
da ta kallesa ba tace "Nah don't worry za mu koma tare da su Mum" Aunt dinta ta
kalleta tace "Ki je mana" Ita dai Hajiya Safeenah bata ce masu komai ba, Nadeeyah
ta langwabar da kai tace "Na riga na shiga nan ne Aunty" Khalil yace "Ohk then,
later" Ta gyada masa kai, Yayi ma su Hajiya Safeenah sallama ya juya ya koma gun
motar Mami, Drivernsu ya ja motar suka bar airport din.
Umma ce zaune dakinta da ta kulle da makulli tana waya kasa kasa tace "Na gaya maki
tun ranan har yau... kin ga dai kusan sati uku kenan ko to ban sa shi a ido ba,
iyaka duk wani expenses na kudin magani da kika sani shi ke badawa bai taɓa cewa Aa
ba, dama Farooq ne ke kai ni asibiti tun da ya koma bakin aikinsa sai Kamila ta
rakani idan ta ga dama, wani lokacin da Amina nake zuwa...." Tana magana hawaye na
zuba idonta, ta ci gaba tace "Usman kuma ai na gaya maki sati biyu kenan da ya fita
Nijar yana buga bugansa a can, Turai duniyar ta min zafi, ji nake kamar zuciyata
zata iya fashewa a ko wani lokaci, ga Kamila babu zancen komawa dakinta mijin har
yayi wani auren, Ɗan nata guda daya ma ya amshe ya kai ma uwarsa, Nihal da nake sa
ran wannan ɗan ministan zai aureta tace min basa tare ai yanzu, da na tambayeta
waye kuma a kasa yanzu sai tace min babu kowa, to ina lafiya Turai? Gashi yau kusa
da wata uku kenan gata nan gata nan ne dai kawai kamar ba Nihal dita ba, har da
wannan sauyin nata ke damuna yanzu haka, sannan da na tuna Nihad ga gidan da fa
take aure sai naji zuciyata kamar ta tsinke, Turai kinsan bani da komai kuma yanzu
balle a ci gaba da neman taimako, zoben nan guda daya ne kawai ya rage min, ta ina
zan fara Turai?" Turai tace "Sumayya ki kwantar da hankalinki kada kije damuwa ta
sa maki ciwon zuciya, iya laluran hawan jinin da kika samu a kwanan nan ma ya isa
haka, in sha Allahu komai zai dawo dai dai Sumayya, yanzu abinda zai faru zan aiko
Fa'iza ta amsa zoben in siyar in je can Zaria gun malamin da ya fara mana aiki
shekaru takwas da suka wuce, kince saki daya Alhajin ya maki ai ko?" Hawaye na
sauka idon Umma tace "Ehh" Hajiya Turai tace "Toh babban abinda za a fara aiki a
kai yanzu shine duk yanda za abi Alhaji ya maida ki dakinki, bayan ya maida ki sai
a koma kan Nihad...." Da sauri Umma tace "Wacece Nihad, ga matsaloli kaca kaca a
gabana kina kira min Nihad Turai, bayan dai an maida ni ayi kokarin duk yanda za
ayi Kamila ma ta koma dakinta wallahi sai kinga rashin darajar da take min a gidan
nan yanzu, bata ma damu da halin da nake ciki ba, dazu da safe ke kyace dukana zata
yi daga nace tayi kokari ta rage baccinta ta dinga tashi tsakar dare tana gaya ma
Allah matsalolinta, Turai bata da aiki yanzu sai waya da manyan mata wanda ko ni
sun fi karfina, kusan kullum sai ta fita ta dawo da kayan ciye ciye tace Hajiya
wancan ce ta bata ko tace Hajiya wancan ce ta bata, har iphone ta dawo da shi gidan
nan wai macece er uwarta ta bata, idan ta fita tun safe sai dare take dawowa fa
wllh, ke dai kinsan irin tarbiyan da na basu Turai ko nan da gate idan ba
kwakkwaran dalili ba bana barin su fita, duk wani sa ido da uwa zata ma 'ya yanta
na masu bakin gwargwado Allah kuma ya gani, to wani hali ne wannan kuma Kamila ta
tsiro da? Wannan ai ba tarbiyata bane, tsorona ma kada taje su sakata harkan
lesbian, da farko ne mutuwar auren ke damunta har ta rame ta fita hayyacinta amma
yanzu kam manyan mata kawai take bi Turai, shine hankalina ya kara tashi wllh,
sannan sai a koma kan Nihal ita ma ayi duk kokarin da za ayi ɗan ministan nan ya
dawo ace yau ita ma tayi aure tana dakinta Turai, sannan Usman shi ma Allah ya
taimakesa ya samu wani aikin ko da ba na Abujan ba, wallahi yana cikin damuwa shi
yasa ma ya fita Nijar ba dangin uwa ba na uba a can, kinsan yanda samun aiki yake a
kasar nan idan ba kasan wanda ya san wani ba, Amina ma ayi addu'a Allah ya fiddo
mata da miji wllh babu me zuwa wajenta abun har tsoro yake bani, hatta Hafsat din
nan me aiki ana zuwa zance wajenta amma banda Aminata, abu na karshe wannan
yarinyar Husnah a yi duk me ma za ayi kada Allah ya kara kado ta gidan nan don
girman Allah, wllh wannan su ne babban matsalolin dake gabana a yanzu dai Turai, da
su nake kwana nake tashi" Hajiya Turai tace "Duk kar ki ji komai zan aiko a amshi
zoben, idan ma da ciko ni zan maki wallahi don kin fice haka a wajena Sumayya,
banda rashi ai da ba sai nace ki bada zobe ba ni me maki ne ko da miliyan zan
kashe, to bani da shi bani da dalilinsa Sumayya" Umma tace "Allah ya rufa asiri ni
dai ki min kokari Turai, bani da me min wannan abun banda ke" Nan suka yi sallama
Umma ta ajiye wayar ta jingina da gado abun duniya ya taru ya mata yawa, duk ta
rame tayi baƙi babu kyan gani. Kwankwasa kofar dakinta aka yi tace "Wanene?" Amina
tace "Ni ce" Umma tace "Ya aka yi? Ba nace kada wanda ya shigo min nan ba ina
bukatar hutu" Amina tace "Nihal ce zazzaɓin ya sake dawo mata Umma" Umma ta sauka
daga kan gadon da sauri ta tafi ta bude kofar tace "Tana ina?" Amina tace "Can
dakinta" Umma tace "Tun yaushe zazzaɓin ya dawo?" Amina tace "Abinci ta ci, sai
tace cikinta na ciwo sosai daga nan kuma sai amai" Umma tace "Wannan yarinya wannan
yarinya da shegen taurin kai take, nace mu je asibiti taki to ya zan mata, tana ta
zazzaɓi a tsattsaye yaki ci yaki cinyewa me maganin Chemist zai mata fisabilillahi"
Suna isa dakin Nihal suka tadda Mumy zaune gefen gadon tana mata sannu, Umma tace
"Me yasa kin fiye taurin kai ne Nihal, nace aje asibiti su maki treatment me kyau
kin ki, to ya kike son inyi dake?" Mumy tace "Nima yanzu maganan da nake mata
kenan, nace ta shirya mu je asibiti wai sai ta huta" Ko kallonta Umma bata yi ba
don tun bayan da Abba ya saketa ta daina kula Mumy a gidan, ko taje dubata a can
ɓangarenta duk sannun da zata mata ba um ba um um sai dai tayi ta sauke ajiyar
zuciya, Umma tace "Tashi sa Hijabinki mu tafi asibiti" Nihal ta daga kai ta kalleta
da kyar tace "Toh a bari anjima mana Umma" Umma tace "Anjiman ubanki, kin tashi kin
shirya ko kuwa, dubi yanda kika lalace kamar warce ta shekara tana zazzabi" Mumy
dai bata sake ce masu komai ba, Nihal ta mike zaune cike da karfin hali tace "Don
Allah ki bari Anjima Umma wllh bacci nake ji kuma yanzu" Umma tace "Toh tashi ki
koma bangarena ki kwanta" Nihal ta tashi tsaye ta fita daga dakin, Umma da Amina
suka bi bayanta, ta koma dakin Nihad dake bangaren Umma ta kwanta, Umma na kallonta
tace "In kin tashi daga Baccin sai Amina ta raka ki asibitin, ko dai kin ji za a
sakar maku result ne a makaranta, tunda ke haka kike da kinji za a saki result kin
fara zazzabi ba ji ba gani" Nihal ta gyada mata kai da sauri tace "Ehh" Umma tace
"Ko da naji, to Allah ya sa a ga alkhairi" Daga haka ta juya ta koma dakinta. Karfe
biyu da rabi na ranan Nihal ta shigo dakin Umma, Umma na zaune kan darduma rike da
carbi, tun da ta idar da sallahn azahar wajen karfe daya da wani abu take zaune
saman darduman take ta jan carbi, da taji hawaye ya zubo idonta sai tayi sauri ta
goge, Nihal ta zauna gefen gadonta, Umma na kallonta ganin yanda ta rame tace "Anya
baza kije asibiti a maki thorough Checkup ba Nihal? Kin ga yanda kika koma kuwa?" A
hankali Nihal tace "Toh ba final exams bane da muka yi Umma" Umma tace "Toh naga
ramar tayi yawa ne, and u look pale" Nihal tace "Umma zan je gidan Coursemate dita
dake rijiyar zaki, ita zata duba mana result din ni bazan iya ba" Umma tace "Har an
saki?" Nihal ta gyada kai a hankali tace "Eh" Umma tace "Toh Allah ya baku sa'a, ya
baku nasara ya rabaku da spill over" Nihal tace "Ameen" Umma ta jawo jakarta ta
ciro dubu daya daga cikin dubu sha biyar din da Farooq ya bata kafin ya koma aiki,
tace "Ki rike wannan a hannu, ai driver ne zai kai ki ko?" Nihal ta gyada mata kai
ta amshi kudin sannan ta mata godiya ta mike ta fita daga dakinta sai da ta fara
zuwa bangaren Mumy ta sanar mata zata fita sannan ta bar gidan, Raliya Coursemate
dinta ce kuma zata girmeta da kusan 4 years amma ko sau daya bata taɓa zuwa gidansu
ba sai dai Raliyan ta zo wajenta, duk da dai sai a level 4 ne ma suka saba da ita
har ta zo gidansu, bata da wata kawa da take zuwa wajenta a kaf garin kano, yawanci
ko yan islamiyyarsu sai dai su zo gida wajenta amma ita kam bata xuwa, Suna isa
kofar gidansu Raliya ta kirata a waya tace "Ina kofar gida" Raliya tace "Anya kin
gane address din da na tura maki kuwa Nihal?" Nihal tace "Toh ai driver ne ya kawo
ni" Raliya tace "Toh gani nan fitowa, Allah ya sa ba wani wajen daban ku ka je ba"
Sai ga Raliya ta bude gate din gidansu, Nihal ta sauka daga motar tana kallon
drivern tace "Kawai ka tafi idan na gama zan kiraka baba" yace "Toh Hajiya" Daga
haka ya ja motar ya bar layin, Raliya ta rungume Nihal cike da farin cikin ganinta
tace "Ya naga sai kara ramewa ma kika yi maimakon ki ciko da kika koma gida" Nihal
ta mata murmushi kawai, Raliya ta kama hannunta suka shiga cikin gidan nasu, babban
gida ne sosai, sai da Raliya ta fara kai ta ta gaida Mum dinta da Stepmom sannan ta
tafi dakinta da ita, Nihal ta zauna gefen gadonta, Raliya tace "Kinji result nan da
sati biyu za a saki?" A hankali Nihal tace "Allah ya kai mu" Mai aikinsu Raliya ta
kawo mata ruwa da small chops, Raliya tace "Naji dadin ganinki wallahi, dama baki
taɓa zuwa gidanmu ba sai dai ni in je naku, to yau dai ga ki a gidanmu and i really
appreciate it" Nihal tayi murmushi amma bata ce komai ba, Raliya tace "Na gan ki
wani iri, ko baki da lafiya ne dai Nihal?" Lokaci daya hawaye ya kawo idon Nihal,
Raliya ta koma gefenta ta zauna da mamaki tace "What's wrong dear?" Bayan few
seconds Nihal tayi karfin halin cewa "Ni bani da kawa, and i have no one to confide
with, kawai naji na yarda dake Raliya, For two months now.... ban ga period dina ba
Raliya" Raliya was shocked ta koma baya ta dinga kallon Nihal tsoro fal idonta, a
kaf department dinsu babu mutum da kana ganinsa zaka masa kallon holy somebody
kamar Nihal, ita ko magana da maza ma bata yi sai taga dama, sannan bata shigar
banza ko da bazata sa hijab ba bazaka taɓa ganinta da karamin gyale ba sai dai
babba da zai rufe jikinta, sannan she is one of the loveliest soul da ta taba
haduwa da warce bata san walakanci ba, abunta bai rufe mata ido ba sannan ga ta da
tausayi, Raliya ta sauka daga kan gadon tana kallon Nihal still shocked tace "Ban
gane ba Nihal? What are you trying to say now?" Kuka sosai Nihal take kamar ranta
zai fita tace "Kin dai
san halina duk da bamu wani dade tare ba Raliya, even male frnds i don't keep,
wallahi wallahi wallahi ni ban taɓa zina ba...." Sai kuma ta kasa ci gaba ta hade
kai da gadon Raliya tana kuka sosai, cikin rawar murya tace "I wish Allah zai dau
rayuwata yanzu, Allah ne shaidata ni ban taɓa zina ba, i was betrayed Raliya,
yaudarata aka yi...." Raliya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, amma don
baki ga period ba ai u don't have to conclude u are pregnant wani lokacin period na
haka, ko nima last 3 months sai da nayi kusan wata biyu banyi period ba daga baya
sai gashi ya zo, do not conclude Nihal" Nihal ta girgiza kai tace "Ni ban taɓa yin
haka ba" Raliya ta ma rasa abinda zata ce mata don gaba daya kanta ya kulle, can
tace "Abinda zai faru, ki tashi yanzu mu je mu siyo Pt test strip a chemist kiyi
amfani da shi don mu tabbatar" Nihal ta goge hawayen da yaki tsaya mata cikin rawan
murya tace "Toh" Raliya ta dau hijab dinta bayan ta je ta gaya ma Mum dinta za su
je siyo abu su dawo ta fita tare da Nihal, ba a chemist din unguwansu ta siya ba
sanin halin jama'a, sai da suka bar anguwan kwata kwata sannan suka samu wani
chemist suka siya, Raliya ta tare masu ɗan adaidaita ya maida su gida, ba Nihal me
test din ba, ita kanta Raliya gabanta faduwa yake sosai, ta dinga addu'a a
zuciyarta Allah ya sa negative za su gani, ai ko Nihal na gama dubawa suka ga
positive, Raliya was so shock ta zauna gefen gadonta ta kasa cewa komai, kuma bata
hana Nihal kukan da take ba kamar zata shide, Raliya ta dinga tunanin wani taimakon
zata iya ba Nihal wanda asirinta bazai tonu ba, gashi dai ita kanta ba wai idonta a
bude yake ba, tana dai cin life amma gaskiya bata shashanci, wata kawarta warce
tasan duniya, duniya ya santa ce ta fado mata, ta kalli Nihal cikin sanyin murya
tace "I have this friend Zaliha nasan zata hada mu da Dr da zai cire cikin...." Ko
rufe baki Raliya bata yi ba, Nihal ta dago da sauri ta girgiza kai hawaye na sauka
idonta cikin rawar murya tace "Bazan cire ba, laifi biyu a lokaci daya Raliya?"
Raliya tace "But kin ce yaudaranki aka yi Nihal, koma laifin ne astagfirullah sai
dai daya na cire ciki amma ba na zina ba since yaudaranki aka yi" Kuka Nihal sosai
take kamar ranta zai fita tace "Baxan cire ba, i can't" Raliya ta zaro ido da
mamaki tace "How did u want to face ur parents with this Nihal?? So kike ki sa masu
heart attack? Ya kike son mahaifiyarki tayi? Ta yaya zaki fuskanci mahaifinki idan
aka gano wannan cikin? Ohh no think about this plss" Kuka kawai Nihal take ta ma
rasa abinda zata ce ma Raliya amma ita dai tasan bazata taɓa cire cikin nan ba
Allah yayi fushi da ita, cire cikin will be the last thing she will do on earth,
Raliya tayi tagumi duk ranta babu dadi, this is so sad, bayan few seconds tace
"Since ni dai baza ki dauki shawarata ba, don't you have any other person that u
can confide in, ko namiji ko na mace wanda u are close with kiji shawaran da zata
baki ko zai baki??" Nihal tayi shiru tana goge idonta tana nazarin who will that
person be.....

*Manage this pls, bana jin dadi ina mura*

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788💖 NIHAAD 💖

70

Tun daga nesa Khalil ke kallonta har ta karaso ta ajiye masa tray din hannunta me
dauke da drink da glass cup sannan ta zauna tana danna wayarta, bayan few seconds
yace "Nadeeyah" Ta daga ido ta kallesa, yayi kasa da murya yace "Do u have anything
in mind that u are hiding away from me?" Tace "Iike?" Yace "You act strange this
days, i don't understand u anymore" Tace "Really?" Yayi shiru yana kallonta, ta
karyar da kai tace "I am not acting strange, kawai dai ina baku enough space da ku
ke bukata ne da kai da matarka" a hankali yace "But ai kema matata ce to be...."
dariya kawai tayi bata ce masa komai ba, sai kuma ta ci gaba da danna wayarta, yace
"Nadeeyah" Ta daga kai ta kallesa, yace "Seriously bana jin dadin abinda kike min,
you are making me feel kamar i am wronging u without me knowing" Ita dai kallonsa
kawai take, can tayi murmushi tace "Ohk sai yanzu ka gane hakan?" Yayi kasa da
murya yace "But how? Ta yaya nake wronging din ki?" Lokaci daya hawaye ya kawo
idonta bata dai ce masa komai ba, yace "Don Allah kiyi min magana" Ta daga kai ta
kallesa hawaye na sauka idonta tace "You should have told me to move on Kjay, da
baka ci gaba da ɓata min lokaci ba kana ce min in jira ka, you wasted my time for 4
years, i neva double dated because of u, da kayi aurenka da tun sannan ka gaya min
in ci gaba da rayuwata...." Ya dakatar da ita yace "Haba Nadeeyah, why are u saying
all this pls, how many times do i have to explain things to you, wallahi wallahi
ban je gidansu da niyyar aurenta ba, hasalima ni bn santa in person ba naje
gidansu, hadin mahaifinta ne aurenmu and i can't say no to him, kawai Allah ya
kaddara aurena da ita ne, i neva bargained for it" Cikin kuka tace "Yanzu ai da son
ranka kake zaune da ita, kuma kana sonta fiye da yanda kai kanka kake tunani yanzu,
saboda son nata da gudun bacin ranta yasa kayi kamar baka gan ni ba a airport ai"
Ya buda baki yana kallonta da mamaki, can ya kwantar da murya yace "Amma fa kinsan
ke na fara so Nadeeyah, kuma har a yanzu ina sonki fiye da tunanin ki, babu abinda
ya ragu a son da nake maki, don Allah ki cire Nihad a ranki Nadeeyah, you are my
first love and u will remain my first love, and kowa yana da matsayinsa a zuciya
ta" Ita dai kuka kawai take, ya dafe kansa don shi baya son wannan kukan nata, can
ya dago yana kallonta yace "If Nihad is just ur problem now shikenan ke zaki zauna
a nan Abuja ita kuma ta zauna either in kaduna or Kano, kinga babu ta inda za ku
fara ganin juna, is that okay by u?" Ta goge idonta tana kallonsa, yace "No say
something, idan da yanda kike son ayi sai ki gaya min" A hankali tace "I am not to
tell u what to do Kjay, and i will neva do that, kawai dai ni nasan i have no bad
intention against her, and i am trying my best to be friends with her amma she is
taking me for a foe, tun asali dama bata so na, even before i know she is ur wife"
Ya girgiza kai da sauri yace "Aa it's not that bata sonki Nadeeyah, kawai dai she
is a kind of person da bata sakin jiki lokaci daya da mutum, tana dadewa bata saba
da mutum ba, that is just it" Ɗan murmushi Nadeeyah tayi tace "No, ba haka bane,
tana min kallon kishiyarta, ni kuma bana mata wannan kallon har cikin raina, duk da
we were together before u met her, amma ni ban ji haushinta don ta aureka ba, i
have nothing against her" Yace "I will talk to her about that i promise, gradually
nasan zata saki jiki da ke in sha Allah" Murmushi kawai tayi bata ce masa komai ba,
yace "Ni nasan baki da matsala Nadeeyah, u are a good girl kamar yanda na san ki a
ko da yaushe...." Wayarsa dake ajiye ne ya fara ring, ya dauka yana duba me kiran
nasa, ganin Nihal ce ya daga ya kai kunne, ya amsa sallaman da tayi masa jin
yanayinta yace "Are you okay?" Daga daya bangaren tace "Alhamdulillah, ya Nihad?"
Ya ɗan yi shiru jin kamar her voice is shaking yace "Hope everything is fine
Nihal?" Tace "Lafiya lau, ina son zan maka magana ne...." Yace "Oh ok, zan kira ki
zuwa dare don bana gida yanzu" jin tayi shiru yace "Hello" Sai kuma tace "Allah ya
kai mu, Nagode" Daga haka ta katse wayar, Nadeeyah dai sai kallonsa take, Yace
"Hope everything is settled now dear?" Ita dai bata ce masa komai ba, yace "Can we
go out for shopping?"
Karfe shidda na ranan Nihal na kwance dakin Nihad don Umma ta hanata zuwa dakinta
yanzu, zazzaɓi ne me karfi ya rufeta, tun dawowarta daga waje Raliya bayan la'asar
take kwance dakin nata, da Umma ta shigo ta tambayeta result din makaranta sai ce
mata tayi ai ba a saki nasu ba, duk da tana jin zazzabin tun a lokacin amma bata
nuna ma Umma ba, kawai ce mata tayi bacci zata yi, Umma ta fita ta bar mata dakin
shine take ta kwance, Mumy ce ta shigo dakin ganin tun dazu bata ga ta fito parlor
ba, ta cire duvet din da ta kulle jikinta tace "Nihal jikin ne..." Shiru Mumy tayi
jin yanda jikinta yayi zafi qau, gashi sae rawan sanyi take, Mumy tace "Ke dae baki
jin magana Nihal, tun yaushe ake bin ki aje asibiti kin ki?" Nihal dae bata ce
komai ba, Mumy ta dauko mata Hijab dinta tace "Sa mu tafi asibitin yanzu" Lokaci
daya hawaye ya kawo Idonta tace "Ban son zuwa asibitin Mumy" Umma ce ta shigo dakin
ita ma jin shiru shiru Nihal bata fito ba, Ganin Mumy tsaye kanta ta karasa da
sauri tace "Menene, zazzabin ne ya dawo?" Mumy tace "Ehh shi ne nace ta tashi mu je
asibiti" Umma ta kwace hijab din Nihal a hannunta ta saka mata ta kamo hannunta
tace "Sauko in kai ki asibiti" Mumy dae ta koma gefe tana kallonsu, hawaye kawai
Nihal take Umma ta dagata daga kan gadon, da kyar tace "Umma amai nake ji" Umma
tace "Kin san yanda Malaria ke maki kika bar sauro suka cije ki a makaranta Nihal"
Nihal ta nufi banɗaki da sauri tana ganin jiri, nan ta dinga yunkurin aman amma
yaki tahowa don babu abinda ta ci, juyawa Mumy tayi ta fita ta koma bangarenta.
Umma ta saka ta gaba suka fita compound, ta kwalo ma Iliya dreba kira ya taho ya
bude masu motar bayan sun shiga, yayi hanyar asibiti da su, a hanya Umma ta ciro
wayarta a jaka tayi dialing number Abba, yana fara ring taji gabanta ya fadi don
tun bayan da ya saketa sai yau tayi dialing number sa, Ba a dau lokaci ba ya daga
yace "Ina jin ki" Zuciyarta na bugawa, murya can kasa tace "Dama Nihal ce bata da
lafiya mun tafi asibiti yanzu, saboda yanayin jikin nata ban san ko za su ce za a
kwantar da ita ba shiyasa nace in kira in gaya maka" Yace "Tun yaushe take rashin
lafiyar?" Umma ta gyara zama cikin sanyin murya tace "Tana tayi a tsattsaye wllh,
sai yau ne yayi tsanani, tun dai da ta dawo makaranta bata jin dadi gaskiya" Abba
yace "Allah ya sauwake, idan kun je asibitin duk abinda ake ciki a gaya min" Umma
tace "Toh in sha Allah, nagode" Katse wayar yayi, taji hankalinta ya ɗan kwanta tun
bayan da ya saketa, idan ko haka ne ai zata dinga son irin cases din nan su dinga
faruwa yanda za su dinga ko da magana ce ta waya da shi, kilan ta hakan sai Allah
ya daidaita su ya hakura har ya maida ta.... Har suka isa asibitin Nihal kuka take,
tun Umma na tunanin zafin ciwo ne har dai da taga irin kukan da take tace "Ke kukan
lafiya kike yi haka kuwa? Meye haka??" Nihal dai bata iya tace komai ba bata kuma
fasa kukan da take ba, she wish kafin su shiga asibitin Allah zai dauki ranta
kawai, a haka har Umma ta sa ta sauko daga motar tana rike da hannunta suka shiga
cikin asibitin, da yake asibitin da suka saba zuwa ne kati kawai Umma ta bada suka
biya kudin ganin likita, suna zaune reception wata nurse ta sanar masu turn dinsu
ne na ganin Dr, Umma ta mike tana rike da hannun Nihal tace "Kiyi ta yin abu kamar
ba mace ba Nihal, ni dai ki kama jiki mu shiga office din" ko rufe baki bata yi ba
taga yarinya ta sulale kafin ta kai kasa tayi saurin kamota tace "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un" Nurses din suka taso da sauri, nan aka yi emergency ward da
ita aka tafi kiran likita, Hankalin Umma yayi mugun tashi ta dinga salati tana zaga
reception din, Patient din wajen sai cewa suke ta kwantar da hankalinta Allah zai
bata lafiya, jakarta da ta bari kan kujera wata mata ta dauka ta kai mata tace "Ana
ta kiranki a waya Hajiya" Umma ta amsa da sauri, ta bude jakar ta ciro wayar taga
Abba ne ke kiranta, daga kiran tayi ta fashe da kuka tace "Yallabai muna shigowa
reception din asibitin ta suma yanzu haka an shiga da ita emergency ward" Abba yace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, bari in taho yanzu dama ina hanya" Daga haka
ya katse wayar, Umma ta mayar cikin jakan ta zauna tana share hawayen idonta....
Bayan kusan minti arba'in wani likita ya fito yana kallon Umma yace "Hajiya mu je
office" Umma ta mike da sauri ta bi bayansa zuwa office dinsa, Zaunawa tayi kujeran
dake gaban table dinsa tana kallonsa, ya gama kauda files din table din sannan ya
kalleta, hankali tashi tace "Ya jikin nata Dr?" Yace "Alhamdulillah, ina mijinta?"
Umma tayi kasake tana kallonsa sai kuma tace "Miji kuma?? Budurwa ce fa Dr, bata yi
aure ba, Ni mahaifiyarta ce kuma ni na kawota" Likitan ya dinga kallon Umma, can
yace "Kuma er cikinki?" Umma tace "Kwarai kuwa, second to the last born dita ce, ta
gama final exams dinta a Ahmadu Bello University ta dawo gida shine take ta zazzabi
sama sama, to dama idan sauro ya cije ta gaskiya tana wahala haka, nafi tunanin
fita karatun daren da take ne yasa ta kwaso malarian" Likitan ya girgiza kai yace
"I am sorry to say Madam, mun gano tana dauke da ciki wata biyu da sati biyu" Still
Umma tayi tana kallon bakin likitan kamar yare yake mata ba Hausa ba, Likitan ya
girgiza kai ya ajiye mata takardan test din yace "She is 2months 2 weeks pregnant"
zumbur Umma ta mike jin pregnant, tana kallonsa bakinta na rawa tana zaro ido kamar
zasu tuttulo waje tace "Meye kuma pregnant likita nace maka budurwa ce, ko dai
result din wata ka kawo min, meye haka kake gaya min don Allah, bata taba aure ba
fa, ta yaya zaka gaya min haka kamar kana shaye shaye?" Ya dau takardan da ya ajiye
mata ya mika mata yana kallonta yace "Ga test result din Hajiya" lokaci daya Umma
taji wani azababben jiri ya ziyarceta, kan kace me taga office din ya fara juya
mata, sai taga ko ina ya koma bakikirin, kafin likitan ya taso ya yo kanta ji kake
timmm a kasa ta kara buga goshi dai dai inda bai gama warkewa ba a tiles din office
din sai ga jini kamar an buda pampo, Likitan ya fita ya kira nurse biyu... Wani
dakin daban aka kwantar da Umma da har bayan minti ashirin bata farfado ba, sai
tsarkewa numfashinta yake kamar zai dauke har sai da aka saka mata oxygen, ga wani
bandage da aka tula mata a goshi inda ya kara fashewa, likitocin suka ji tausayinta
sosai bayan likitan da ya sanar mata Nihal na dauke da ciki ya gaya masu duk yanda
aka yi a office dinsa, duk suka dinga Allah wadaran Nihal. Tun shigowar Abba
asibitin yake kiran wayar Umma bata dagawa, hakan yasa ya kashe motarsa kawai ya
shiga cikin asibitin, bayan sun gaisa da nurses din yace "An kawo wata mara lafiya
yanzu, tare da Baabarta suka zo...." Wata nurse da ta ganesa don in dai Nihad bata
da lafiya shekarun baya yawanci shi ke kai ta asibiti, kuma duk tunaninta ma Nihad
ce aka kawo yanzu, Nurse din sai duk jikinta yayi sanyi tace "Ina zuwa sir" Wajen
likitan da yayi attending ma Umma ta tafi ta sanar masa ga mai gidan Umma ya zo,
yace tayi masa iso zuwa office dinsa, Nurse din ta kai Abba har office din likitan,
Abba ya zauna yana kallon likitan bayan sun gaisa yace "Jikin nata yayi critical ne
haka? I need to see her first pls" Likitan yace "It's okay sir, daughter dinka ce
ko?" Abba yace "Sure, she is my daughter" Likitan ya sauke ajiyar zuciya yace "I am
sorry to say sir, mun gano er ka na dauke da cikin wata biyu da sati biyu" Abba ya
dinga kallonsa babu ko kiftawa as if trying to apprehend what he just said, Likitan
ya ajiye masa result din yana kallonsa, Abba ya sauke idonsa kasa, the Dr can see
tension and shock written all over him, Likitan ya sauke ajiyar zuciya yace "Kar ka
daga hankalinka Alhaji, it shall be well in sha Allah, daga hankali da mahaifiyarta
tayi ya janyo tayi pass out dazu, yanzu haka ita ma tana kwance ba a kuma jima da
cire mata oxygen ba, kuma jininta ya hau, don haka kayi hakuri ka dauki dangana, ka
kuma kula da matarka har Allah ya bata lafiyarta, yaran yanzu ne ka haifesu baka
haifi halinsu ba, sae dae a bi su da addu'ar shiriya kawai" Duk wannan abinda yake
fada Abba bai ma san me yake cewa ba, Likitan ya mika masa bill din yace "This is
the bill sir, in kuma tare kake da dreba yayi kokari ya maida ka gida Alhaji, you
need to relax and accept this with good faith" Abba ya mike yace "It's okay, it's
okay" Kudi masu yawa ya ciro aljihunsa ya ajiye kan table din likitan ya juya,
Maimakon yayi hanyar kofar fita, sai yayi hanyar bandakin likitan, Likitan yace "Ga
kofar can Alhaji, don Allah ka kwantar da hankalinka saboda shekarun ka" Da sauri
Abba ya nufi kofar fita bai dai ce ma likitan komai ba har ya fita ko rufe office
din bai yi ba, likitan ya ga ya bi right maimakon left, Likitan ya girgiza kai with
pity, suna samun ire iren cases din nan sosai, but ya za ayi? Sai dai kawai Allah
ya kyauta ya shirya yan baya. Wata nurse ce tsaye kan Umma tana duba ko jininta ya
dawo dai dai amma taga har yanzu 180 ne, Umma ta bude Idonta da yayi mata nauyi da
kyar tana kallon nurse din ta cafko hannunta tana harhade magana tace "Nurse a ina
ake cire ciki a garin nan? Ko kuna cirewa a nan??" Nurse din ta girgiza kai tace
"Ba a cire ciki a asibitin nan Hajiya" Umma tayi karfin halin mikewa zaune cikin
rawan murya tace "Don Allah gaya min inda kika san ana cire ciki, don Allah ba don
ni ba, ki rufa min asiri ki gaya min er nan" Nurse din tace "Hajiya ban san
asibitin da ake cire ciki ba gaskiya, nima sabuwa ce a nan" Umma ta fashe da
matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace,
komai ya tabarbare min ni Sumayya, wayyo Allah na" Nurse din dai sai kallonta take,
Umma ta fizge ruwan hannunta ta sauka daga kan gadon tana share hawayenta da sauri
tace "Ina jakata, ina aka kai jakata" Nurse din ta nuna mata, Umma ta dauka da
sauri da nufin ciro waya ta kira Abba tace masa an sallamesu ba sai ya karaso ba,
ko ina na jikinta rawa yake ga wani ciwo da zuciyarta yake, sai hada zufa take ta
ciro wayarta taga miss calls din Abba har biyu, da
sauri tayi dialing kiran, yayi ring har ya katse bai dauka ba, ta kara kira nan ma
har ya katse no response, Nurse din dai ta juya ta fita tana girgiza kai, Umma ta
sauka daga kan gadon tayi zaman dirshan a kasa tana kuka kamar ranta zai fita tace
"Allah na tuba ka yafe ni, Allah na tuba, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na
shiga uku na lalace duniya tayi min zafi, na shiga uku ni Sumayya" Sai kuma ta mike
kamar mahaukaciya ta figi jakarta ta fice daga ward din, Nurses din ta sama a
reception jikinta na rawa tace "Tana ina?" Duk suka tsaya kallonta, wata nurse ce
ta kai ta ward din da Nihal take, zaune take ta hada kanta da gwiwanta tana kuka
kamar ranta zai fita, tun dazu take kukan amma daga nurses har Doctors din babu
wanda yace tayi shiru ko tayi hakuri, gaba dayansu ma haushinta suke ji, Umma ta
fashe da matsanancin kuka ta jingina da bango tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" Nihal dai ta
kasa dago kanta, har shidewa take saboda kuka, Umma tayi kukan har sai da taji ba
dadi sannan ta nufeta tace "Allah ya isa tsakanina dake Nihal, sakayyar da zaki min
kenan duk so da kaunar da na nuna maki cikin 'ya yana? Da cikin shege zaki biyani?
Me na maki zaki min haka Nihal?" Nihal dai bata dago kanta ba sai kuka kawai, Umma
ta goge idonta da sauri tunawa da tayi Abba zai iya karasowa yanzu, Da kyar tace
"Sauka mu tafi, munafuka matsiyaciya, Allah ya isa tsakanina dake wllh, sauko daga
kan gadon nan" Nihal ta sauko daga saman gadon tana kuka sosai, Haka Umma ta tasa
ta a gaba suka fice daga asibitin ita gaba daya tama manta ana biyan wani abu wai
kudin asibiti, bata ga iliya a haraban asibitin ba duk da tace ya jira su, bata
damu da hakan ba don hankalinta baya jikinta, a haka har suka isa titi Umma na can
gaba tana rusa kuka, Nihal na biye da ita a baya, suka samu adaidaita a haka har
suka isa gida, Kafin su karasa gate din gidan Umma ta goge hawayenta ta sa
adaidaitan ya saukesu ta basa kudinsa, Nihal dai na tsaye tana jin dama kawai a dau
ranta a wajen, Umma na kallonta da kyau tace "Don kaza kazanki ko wani tambaya aka
maki kice Malaria ne an maki allura gobe kuma za mu koma asibitin da safe" Ita dai
Nihal bata ce komai ba hawaye ne me zafi ke sauka idonta, a haka suka shiga
gidan....
Khalil na zaune bayan isha wayarsa na kare kunnensa yana magana da Mami, yana son
tambayarta Nihad amma ya kasa, gashi ita ma bata ce masa ga ta ba duk da ko minti
biyu basu yi suna wayar ba, Can dai yayi karfin halin cewa "Mami ya me jikin?" Mami
tace "Da sauki, gobe za mu taho in sha Allah...." A hankali yace "Toh Allah ya kai
mu" Tace "Ameen, sai anjima" Daga haka ta katse wayar, ya dinga kallon screen din,
he is missing his wife badly amma ko ɗan gaisawa Mami taki bata wayar su yi tun da
suka isa can, Number Nihal yayi dialing for the 3rd time yanzu, don tun bayan
magrib yake kiranta bata dagawa, yanzun ma har ya katse bata daga ba, ya ajiye
wayar ya fita zuwa parlon Abbansa don yana gidan, don yana son jin yaushe yayi
fixing na tafiyarsu Yemen din.... Kallonsa kawai Janar yake yi har ya gama tambayar
tasa, can Janar ya sauke glass din idonsa yace "Ka samu wani abokinka ku je, don
bani da lokacin zuwa kasar..." Khalil yayi shiru yana kallonsa, Janar yace "Sun ma
raina ma mutane hankali, kuma duk inda tsabga ta rainin hankali yake to babu ni a
ciki, tun asali me yasa basu kawo wannan zancen ba sai yanzu? So i don't think da
wani abu da zai kai ni kasar nan yanzu" Khalil ya sunkuyar da kansa kawai.
Umma na shiga parlor taga Mumy ta fito daga bangaren Abba, Mumy na kallonsu tace
"Ya jikin Nihal" ba tare da Umma ta kalleta ba balle taga idonta tace "Da sauki"
Daga haka ta tura Nihal suka yi gaba zuwa ɓangarenta, Mumy dai ta tafi ta zauna
parlor har family Dr din wan Abba wato Alhaji Abubakar da ta kira dazu ya iso
gidan, ta kai sa har ɓangaren Abba, tana kai sa dakin ta fito ta zauna parlor, ita
dai tasan lafiya ya fita yau babu ko alamar ciwon kai amma ya dawo a haka, a
zuciyarta kuma tace ikon Allah kenan, bayan kusan minti talatin likitan ya fito, ta
mike ta nufesa tana kallonsa tace "Dr ya jikin nasa?" Yace "Dole sai mun je
asibiti, jininsa ya hau over" Hankali tashe Mumy tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un" Mumy bata san sanda ta tafi ta dauko Hijab dinta ba a ɓangarenta da sauri.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788


Assalamu alaikum
Barkanmu da war haka masoya Khaleesat da Nihad🥰. Nasan kowaccenku na cike da son
sanin turarukan da wadannan taurari namu guda biyu ke amfani dashi dake tafiyar da
xuciyar maxajensu ya rikita musu lissafi ya kuma goge masu hada😌.
Toh turaruka neh na oil masu kamshi sosai da rike jiki daga scentmania. Wadannan
turaruka sunfi kala goma. Dan mace ba'a Santa da xama da kamshi iri daya kullum ba.
Dole adinga jin kamshi ma banbanta ajikinta kullum. Ana hada wadannan turaruka biyu
xuwa sama asaka alokaci guda dansu bada sihirtaccen kamshin dake tafiyar da
hankalin duk wanda ya shaka.
Dan haka muka hada package na wadannan turaruka muna kiranshi da 'Nihad pack' 🔥 🔥
Akwai Nihad silver pack: ya kunshi turaruka kala biyar. 6mls guda biyu da 3mls
guda uku N5000.
Akwai Nihad gold pack: ya kunshi turaruka kala bakwai. 6mls guda uku da 3mls guda
hudu
Sannan akwai Nihad diamond pack: ya kunshi turaruka kala 8. 10mls guda daya 6mls
guda hudu 3mls guda uku.
Ga sunayen turarukan nan kamar haka
1. Love letter (na musamman akowani pack akwaishi)
2. Baccarat Rouge
3. Jadore
4. La vie est belle
5. Pink shiffon
6. Pure seduction redplum
7. Versace Eros woman
8. Black Opium
9. Kim Kardashian
10. Love spell
Note that turarukan package a discounted price aka bada, kuma ana hada scents din
da sukayi complimenting juna neh yadda xaifi tashin kai in anyi amfani dashi. Amman
in kinason kiyi maki choice dinki shima ana badawa standard price dinmu 3mls N800,
6mls N1500 10mls N3000
Akwai 20mls N5000, 30mls N7000 and 50mls N10000. Turaruka araha ina mai tabbatar
maki kikayi amfani dasu sai kin dawo. Mudae burinmu kowa tayi kamshi na musamman🥰🥰💖
NIHAAD 💖

71

Khalil na tsaye balcony a sama yana kallon motocin suka gama shigowa babban
compound din, wani soja ya bude ma Mami motarta ta sauko, Nihad ma ta sauko suka
nufi entrance din shiga gidan, Mimi da Noor dake zaune main parlor suka yi
welcoming dinsu suka wuce Upstairs gaba daya zuwa bangaren Mami, Suna shiga parlor
Nihad ta zauna saman kujera, Mami ta sa Bilkisu ta tafi ta hada mata ruwan wanka a
bandakinta, Bilkisu na fitowa daga bedroom din Mami ta kalli Nihad tace "Shiga kiyi
wanka, sai ki kwanta ki huta, hope u are not hungry?" Nihad ta girgiza mata kai
tace "Aa na koshi" sannan ta mike ta shiga bedroom din Mami, Mami ta bi ta da
kallo, ko da ta fito wanka taga akwatin kayanta an kawo mata cikin dakin, ta dau
doguwar riga mara nauyi ta saka sannan ta kwanta gefen gadon.... Mimi na fito da
tsaraban da Mami tayi a Uk a cikin wani babban akwati Khalil ya shigo parlon, duk
yawanci kaya ne da ta siya ma Nihad irin English wears, su Mimi ma ta siyo masu
abubuwan da tasan sun fi so, Zaunawa Khalil yayi saman kujera yana kallon Mami yace
"Barka da isowa Mami" Ita ma ta kallesa tace "Yauwa" Yace "Ya hanya" tace
"Alhamdulillah" Bai sake cewa komai ba, Tace "Abbanka yace min ya samar maka aiki
ko?" Khalil yace "Ehh haka ne" Mami tace "Toh Allah ya sanya Alkhairi" Yace "Ameen"
yana ta zaune parlon yana kallon Mimi dake ta fiddo kaya tana waow, can kawai ya
mike ya nufi Bedroom din Mami, yana shiga ciki kuma ya kulle kofar, Nihad ta daga
kai ta kallesa don har sannan bata yi bacci ba, ya karasa kusa da ita ya zauna yana
kallonta, a hankali yace "How are you feeling dear?" Ta sauke idonta tace
"Alhamdulillah" Ya dagota zaune yana kare mata kallo as if wanting to see the
pregnancy with his naked eyes yace "Sure?" Ta kallesa dai bata ce komai ba, a nan
yaga yanda ta kara ramewa, sae dae kawai tayi haske sosai, yayi kasa da murya a bit
worried yace "I want you to go back to ur former Nihad pls, i don't like the new
you..." Murmushi kawai yaga ta yi ta dauke kanta, ya kamo hannunta yace "Plss...."
Ta sake kallonsa, yayi kasa da murya yace "Are you not comfortable being with my
household? Or do you have any problem staying here?" Ta girgiza masa kai, yace
"Then why are u always silent, always moody, and baki son ki saki jikin ki...." ta
daga kai ta kallesa tace "I am still recovering, and i am yet to recover fully, but
Alhamdulillah i am grateful to God for making me this strong in all situation i
found my self.... 1st ban samu proper coach from childhood ba which made me who i
am today, and i am still yet to recover from the shock of who i found out my
Stepmom was, Bad friends that led me astray, even in relationship i wasn't lucky,
babban damuwata kuma shine Abbana bai ce ya yafe min ba har yanzu, and i have many
people to ask for forgiveness from....." Tana kai wa nan ta daga kai tana kallonsa,
Har ransa yaji tausayinta, cikin sanyi yace "Forget ur past and face the future
Nihad, and i am assuring you the future is super bright, this is ur new life now,
ki manta da komai ki fara sabuwar rayuwarki...." Hawaye yaga ya cika idonta, sai
kuma tayi saurin gogewa, shi dai ya tsura mata ido, A hankali tace "And still yet
my challenges are not over..." Ya kamo hannunta yace "You think so? Wani challenge
ne kike gani a gabanki yanzu" Tace "Time shall tell, may be i will never be happy
in life..." Ya girgiza kai yace "Kar kice haka" Ta gyada kai tace "Ohk, but i will
love to ask for a favor" a hankali yace "Ina jin ki" Tace "Ina son zan je in ga
Mumy..." Ya ɗan yi shiru yana kallonta da mamaki, sai kuma yace "But ai bamu dade
da dawowa daga Kano ba, and baki da lafiya yanzu bai kamata kije ko ina and stress
ur self out ba" Tace "Ni na samu sauki, plss allow me" Yace "No Nihad, ki bari idan
kin kara samun sauki sai in kai ki kiyi 5 days a can...." Ta marairaice masa tace
"Nace maka na samu sauki, even if it's just for 2 days, i just want to see her
plss" A hankali yace "Ohk dear, i will talk to Mami" Tace "Thank you" Murmushi
kawai yayi mata yana kallonta, a ransa kuwa tunani yake if this is the right time
da zai kawo mata zancen Nadeeyah, bai taɓa ganinta speaking so calm with wisdom
haka ba, but kawai kuma dai ya fasa cause bai son mood dinta ya canza yanzu ta
dalilinsa, yace "Ain't you hungry?" Ta girgiza masa kai, yace "Ohk" Komawa tayi ta
kwanta tace "Ina son zan yi bacci" Daga haka ta rufe ido, yayi shiru yana ta
kallonta, can yace "Ohk dear" Gyara mata duvet yayi don dakin akwai sanyi sannan ya
mike ya nufi kofa ya fita ya kulle, Bai kalli Mami dake zaune parlon har sannan ba
ya nufi kofar fita daga parlon. Bayan Azahar Khalil na saukowa downstairs ya ga
Mami zaune main parlor suna kallon wani program da Bilkisu, tun da ta sauko raka
Hajiya Safeenah da ta zo yi masu sannu da zuwa ta zauna nan parlon bata koma sama
ba, wanda rabonta da zama parlon har ta manta saboda su Aunty Hassana, Khalil ya
karaso ya zauna parlorn, Bilkisu ta mike ta bar masu parlon, Mami tace "Abincin ka
na can dining din kitchen" Yace "Ohk" Mami bata sake ce masa komai ba ta ci gaba da
kallonta, Ganin bai tashi ba bayan wani lokaci ta kallesa tace "Ko kana da magana
ne kake ta kallona haka?" Yace "Ai baki gaya min yanda ake ciki ba batun zuwa ganin
likita da ku ka yi" Mami tace "To tunda ba kai ka aikeni ba ta yaya zan gaya maka
yanda ake ciki" Murmushi kawai yayi bai ce komai ba, tace "Alhamdulillah ba wani
matsala, sun rubuta mana drugs mun siya a can, sauran measures din kuma duk zan sa
ido tunda tana nan" Yayi shiru yana kallonta, can a hankali yace "Amma Mami tace
min tana son zuwa wajen Mum dinta, kwana uku kawai zata yi a can" Mami ta kallesa
tace "Yaushe ku ka yi hakan da ita?" Yace "U can ask her, nace mata a'a amma da
naga ta damu shine nace zan maki magana" Mami tayi shiru kamar me nazari, can tace
"Da dai ta bari nan da sati biyu kafin nan ta kara kwari" Yace "Toh ki mata magana
Mami, nima haka nace mata" Mami tace "I will talk to her" Mikewa yayi ya wuce
kitchen.... Wajajen karfe hudu da wani abu Bilkisu ta shiga bedroom din Mami da
abinci iri uku sai farfesun kayan ciki, Nihad dake zaune kan darduma ta bi ta da
kallo har ta fita, tana fita Mami ta shigo, Tace "Ki duba abinda zaki iya ci a ciki
sai ki diba" Nihad tace "Toh" mikewa tayi ta taho gun abincin ta bude, tuwo da
miyar kubewa ta zuba, Mami tace "Eat little at a time don kar kiyi amai kin ji?"
Nihad tace "Toh" Daga haka Mami ta fita daga dakin, bata wani ci abincin ba a haka
Mami ta dawo ta sameta ta jinginar da kanta da gado ga abincin a gabanta wanda bai
fi loma uku tayi ba, Mami ta zauna gefen gado tace "Ko kina son wani abu ne ba
tuwon ba?" Nihad ta sunkuyar da kanta tace "Na koshi ne" Mami ta dinga kallonta,
ganin kamar she is moody kamar ko da yaushe, tace "Kince ma Khalil za ki je wajen
Mum dinki ne?" Nihad ta kalleta tace "Ehh" Mami tace "Toh ki bari ko nan da sati
daya idan kin huta sai ki je, kinga yau muka dawo daga tafiya" Nihad ta kasa cewa
komai, lkci daya hawaye ya kawo idonta tace "Toh" Mami dai bata sake ce mata komai
ba ta mike ta fita, Nihad ta hade kanta da gwiwa hawaye na sauka idonta. Mami na
fita dakin ta tafi bangaren khalil don har sannan yana gidan bai fita ba, bayan ta
shiga dakin tace "Ta shirya gobe ka kai ta sai tayi kwanakin da take so a wajen
mamar tata, but za ku tafi da ko Mimi ko Noor" Khalil ya dinga kallonta tace "Sai
kayi maku booking flight ko na safe ne gobe" Daga haka ta juya ta fita daga dakin,
shi dariya ma ta basa, ya girgiza kai kawai. Washegari da asuba Mami ta shiga dakin
Mimi tace "Dear ki shirya kayanki ko kala biyu ne za ku je kano da yayanki, he will
be taking his wife home for somedays" Mimi tace "Ohh but am having presentation in
school today Mami, amma dai ba komai nasan excuse da zan bada" Mami tace "Aa, je
kiyi presentation dinki, you won't miss that, Noor will go with them" Mimi ta ɓata
fuska tace "Mami plss, i know how to cover up, beside Noor da take crams ai bata
zuwa ko ina" Mami tace "Ni dai nace kije makaranta kiyi presentation dinki" a
hankali Mimi tace "Ohk" Mami ta juya ta fita dakin ta tafi dakin Noor ta tarar tana
ciwon mara kamar yanda Mimi ta gaya mata, da taga dai dole babu wanda zai bi su
cikinsu ta tafi ta samu Khalil tace "Kar kayi booking flight din ka bari gobe idan
Allah ya kai mu, Mimi said she is having presentation today, Noor kuma bata da
lafiya" Khalil yace "I have done that since yesterday, flight din karfe sha daya
ne, na siya ticket ma" Mami tace "Ticket guda nawa?" Yace "Yanda kika ce a siya"
Mami tace "Toh Mimi isn't going kuma" Yace "Yeahh dama economy class ne, so we will
be more comfortable a 3 seat din" Babu yanda Mami ta iya haka ta juya ta fita daga
dakin, Nihad was so happy bayan da Mami tace mata ta shirya kayanta kala biyar da
duk abinda zata bukata, Karfe goma da rabi Mami ta rakasu har airport din, Ta sauka
bayan motar, Nihad ma ta sauka, Mami tace "Toh Allah ya tsare, ya kai ku lafiya..."
Nihad tace "Ameen" Mami ta kalli Khalil dake rike da trolly din Nihad tace "Yaushe
zaka dawo Malam? Yau ko?" Murmushi yayi yace "Idan na samu flight da zai taho
Abuja zan dawo yau din, idan kuma ban samu ba sai gobe" Mami tace "Ohk then"
Takardan hannunta ta mika masa, ya amsa yana kallonta don bai san na menene ba,
Mami ta kara yi ma Nihad sallama sannan ta koma cikin mota, bai bude takardan ba
yana rike da trolly din suka shiga cikin airport din, sai bayan da ya amsar masu
ticket suka yi following duk process da ya kamata suna zaune a Departure Lounge
sannan ya bude takardan da Mami ta basa, Measures din da likitan US yayi suggesting
ne Mami duk ta rubuta a takardan kanta tsaye, bai san sanda yayi dariya ba ya rike
kai, Nihad dai sai kallonsa take don bata san me ke basa dariya ba, ya daga kai
yana kallonta with smile on his face sai ya mika mata takardan, ta amsa tana duba
content din ciki, duk ta karanta comfortably amma tana kai wa na karshe ta ɗan
kallesa da gefen ido taga kallonta yake, mayar masa
da takardan tayi ta dauke kai, yayi dariya ya linke takardan ya saka a pocket, a
haka har suka yi boarding jirgin sannan yayi takeoff zuwa garin Kano, garinsu Aunty
Maryam din danladi nasidi..... Karfe daya saura Nihad suka iso kofar gidansu, bata
wani jira Khalil ya gama gaya mata cewar sai da yamma zai dawo gidan ba cause she
is too eager kawai ta gyada masa kai ta shige cikin gidan, Bayan sun gaisa da Aminu
da ya mike da sauri yana jiran ganin Khalil, ita dai ta nufi entrance din shiga
gidan, tayi mamakin ganin motar Abbanta a gida on a Tuesday, ta dai karasa cikin
parlor, wanda ta tadda babu kowa ciki, ta tafi side din Mumy, nan ma bata ga Mumy
ba ta shiga har bedroom dinta, kannenta dai tasan suna makaranta, Khalil bai bari
ta shiga da trolly dinta ba yace zai kawo mata anjima idan ya dawo, ta cire doguwar
rigar jikinta don zafi taji take ji, duk da suna samun wuta sosai a anguwansu amma
akan dauke wani lokacin, ita kuwa ta saba electricity 24/7 a gidan Janar, tana
kwance kan gadon Mumy bayan ta bude curtains din sai ga Mumy ta shigo dakin, tsaye
tayi tana kallonta da mamaki, Nihad ta mike zaune tana murmushi kafin tace komai
Mumy tace "Lafiya??" A hankali Nihad tace "Ina missing dinki ne shine Maminsa tace
ya kawoni in gaisheki" Mumy ta sauke boyayyen ajiyar zuciya ta karasa cikin dakin,
Nihad dai sai kallonta take ganin her eyes are swollen, and gaba daya a sanyaye
take, Mumy ta zauna gefen gadon amma bata ce komai ba, Nihad taji gabanta na faduwa
tace "Mumy are you okay?" Nan da nan hawaye ya fara sauka idon Mumy kamar jira
take, Hankalin Nihad ya tashi sosai, ta dawo kusa da ita tace "Mumy me ya faru?? Ki
gaya min meke faruwa?" Mumy na girgiza kai tace "Nothing dear, a kawo maki abinci?"
Nihad bata san sanda ta fashe da kuka ba tace "Mumy don Allah ki gaya min, is
everything alright" Mumy na share idonta tace "Tafi ki duba Abbanki kiyi masa ya
jiki sai ki dawo, he is sick" Sosai gaban Nihad ya fadi wanda har sai da taji wani
jiri, tace "Mumy what's wrong with him?" Mumy tace "He is getting better now, ki je
ki dubasa a dakinsa" Nihad ta mike jiki ba kwari ta dau rigarta ta saka ta nufi
kofa ta fita daga bangaren Mumy ta tafi na Abba, ba kowa a parlon nasa ta karasa
kofar bedroom dinsa har sannan gabanta bai daina faduwa ba, tayi sallama bakin
kofar aka amsa mata ta shiga ciki, Farooq ne zaune gefen Abban nasa, sai Hamid dake
daya side din da Alhaji Abubakar sai wani kawun Abba, tun da ta shigo duk suke
kallonta a dakin, ita dai idonta na kan Abba dake kwance saman gado, ta durkusa
gaban gadon gabanta na bugawa, can kuma ta tashi ta koma can kusa da shi muryarta
na rawa tace "Abba what's wrong with u?" Ya gyada mata kai kawai, muryarsa ko
fitowa baya yi sosai yace "I will be fine Nihad, how are you?" Bata san sanda ta
fashe da kuka ta hade kanta da gadon ba, Alhaji Abubakar yace "Taso ki dawo nan
Mamata" Ta tashi ta koma inda yake tana kallonsa hawaye na sauka idonta, cikin
kwantar da murya yace "Yaushe kika zo?" Muryarta na rawa tace "Yanzu" Yace "Ina me
gidan naki?" Tace "Yace zai shigo anjima" Yace "Toh maa sha Allah, he is recovering
in sha Allah, ki je ki huta" Ta kalli Abba da ya rufe idonsa, a hankali Farooq dake
kallonta yace "Ki je ki huta" Ta tashi kawai ta nufi kofa ta fita daga dakin ta
koma bangaren Mumy tana kuka sosai, Mumy bata hanata kukan ba, tayi me isarta
sannan ta kalli Mumy da kyar tace "Mumy me ya samu Abbana?" A hankali Mumy tace
"Yana samun sauki in sha Allah" Nihad tace "Toh amma menene ya samesa?" Mumy tayi
shiru kamar bazata ce komai ba, can tace "He had stroke, but he is recovering now"
Nihad ta zaro ido a tsorace tace "Stroke?" Mumy tace "Baki ga ya fara magana ba, ai
baya magana sai few hours ago ya fara, kuma da sauki sosai jikin yanzu, in 2 days
time za a fita India da shi" Kuka kawai Nihad take ta ma rasa me zata ce ma Mumy,
Mumy ta goge nata hawayen tace "Ai ba kuka za kiyi ba, addu'a za kiyi masa, he will
be fine in sha Allah" Tuni Nihad taji ta fara jin jiri ga sara mata da kanta ke yi
amma duk da haka bata fasa kukan da take ba, Mumy tace "Ke meye haka? Idan baza
kiyi masa addu'a ba meye amfanin kukan?" Mikewa Mumy tayi ta fita daga dakin, Nihad
ta dafa gado ta koma ta kwanta da kyar don ji tayi kamar zazzabi zai rufeta, Mumy
na fita kitchen ta tafi ta zubo abinci kadan a plate, miyan ma ba da yawa ta sa ba,
ta hada just milo a cup sannan ta dawo bangarenta, tana shiga dakinta taga Nihad ta
lullube har kanta da bargo kuma bata fasa shesshekan kukan da take ba, Mumy ta tafi
gaban madubinta ta dau makullin da ta ajiye bayan wani kwalban turare sannan ta
fita ta bude dakin Nihal dake bangarenta ta shiga da tray din shinkafar da cup din
milo, sannan ta kulle kofar, tana zaune at the very far end of the room kamar ko da
yaushe, Mumy ta ajiye tray din hannunta ta zauna gefen gadon tace "Ta so ki ci
abinci Nihal" Nihal ta daga idonta da yayi ja kamar garwashi tana kallon Mumy, Mumy
tace "In kuma baza ki ci shinkafar ba ki shanye ruwan milo din yanzu ki bani cup"
Mikewa Nihal tayi tana tafiya a hankali kamar iska zai hurata ta fadi, ta taho ta
durkusa gaban tray din abincin ta dau cup din milon, Mumy tace "Ba lokaci daya zaki
shanye ba, ki dinga bin sa bit by bit" Kamar yanda Mumy tace mata haka ta dinga
shan shayin wanda take jinsa kamar magani a baki, she don't want to say no to Mumy
ne shi yasa har ta daure take sha, amma ko sip uku bata yi ba taji ya dawo mata, da
sauri ta shige bandaki, Mumy ta mike ta bi bayanta, bayan tayi aman ta fito Mumy ta
sa ta kara shan kadan sannan ta hada mata ruwan wanka a bandaki tayi wanka, sai da
Mumy ta ɓata almost 35 minutes a dakin, bayan taga Nihal ta kwanta sannan ta dau
tray din ta fita ta sa ma kofar makulli ta tafi kitchen, Mumy ta zuba ma Nihad
abinci ta kai mata daki, kwance ta sameta har sannan kanta a rufe da duvet, Mumy ta
cire tana kallonta, Nihad ta bude ido da kyar Mumy tace "Sauko ki ci abinci" Nihad
ta girgiza mata kai tace "Na koshi" Mumy tace "Ban son iskanci ga abinci na kawo
maki kice min kin koshi, ki sauko ki ci abinci Hajiya" Nihad ta mike zaune da kyar
ta sauko da kafafuwanta daga saman gadon, kallo daya tayi ma shinkafa da miyan dake
dauke manyan nama, ta toshe hancinta da sauri, lokaci daya taji amai ya taho mata,
Mumy dai sai kallonta take da mamaki ganin reaction dinta, Nihad ta sauka daga kan
gadon da sauri ta tafi bandaki ta fara kwarara amai, Mumy ta bi bayanta ta kamata
tace "Are you okay?" Sai da ta amayar da ɗan shayin da Mami ta lallabata ta sha a
Abuja kafin ta samu nutsuwa, lokaci daya tayi laushi, Mumy ta taimaka mata ta wanke
bakinta ta fito da ita daga bandakin, Nihad ta kwanta gefen gado tana jin zazzabi
sosai, Mumy ta sauke idonta daga kallonta ta ja duvet ta rufe mata jiki tace
"Sannu"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788💖 NIHAAD 💖

72

Sai bayan Magrib Mumy ta tada Nihad dake ta bacci tun dazu, Nihad ta bude ido a
hankali, Mumy tace "Ki daure ki tashi kiyi sallah, anyi magrib" Mikewa zaune tayi,
cikin sanyin murya tace "Mumy ya jikin Abbana?" Mumy tace "Da sauki, je kiyi
alwala" sai da Mumy ta ga shigarta bandakin sannan ta fita daga dakin, Nihad na ta
zaune kan darduma bayan ta idar da sallahn tana son tashi ta tafi bangaren Abbanta
ta dubasa amma kasala ya sa ta kasa tashi, Mumy ta dawo dakin tana kallonta tace
"Ki tashi kije ki samesa a parlor" Mumy na fadin haka ta bar dakin, Nihad ta mike
da kyar ta fito parlon Mumy ta ga Khalil a zaune, Tun da ta fito yake kallonta don
gaba daya a sanyaye take, kana ganinta ka ga damuwa karara a tare da ita, ta zauna
saman kujera tana kallonsa amma bata ce komai ba, tashi yayi ya koma kusa da ita ya
zauna ya kamo hannunta cikin kwantar da murya yace "Abba will get better soon in
sha Allah, ki kwantar da hankalinki kin ji" Kamar jira take ta fashe masa da kuka
sosai, cike da damuwa yace "Noo pls, i am assuring you he will be fine in sha
Allah, trust me" Girgiza masa kai kawai tayi amma ta kasa cewa komai, ya rungumeta
yana lallashinta, har dai ya samu ta daina kukan, wayarsa ne ya fara ring ya ciro
ganin farooq ne ke kiransa yace "I am coming back now" Daga haka ya mike ya fita
daga parlon, Nihad ta bi sa da ido hawaye na sauka fuskarta, Khalil na fitowa main
parlor ya tafi bangaren Abba, yana cikin duba sabbin magungunan Abba da Farooq ya
siyo Inna ta bude kofar dakin ta shigo rike da katon cooler, Duk suka daga kai suna
kallonta ta ajiye coolern hannunta, sai kuma ta rushe da kuka tace "Allah ya tashi
kafadunka Ibrahim, Allah ya baka lafiya, saura kiris ina tahowa yanzu mota ta
bigeni saboda rashin nutsuwa, da yake babu wanda ma yasan na fito daga gida, da
kafa na zo gidan nan wllh" Farooq yace "Ba dazu kika tafi ba Inna ai da baki sake
dawowa ba sai gobe, kinga ai jikin nasa da sauki Alhamdulillah" Cikin kuka inna
tace "Ina zan ga nutsuwar jira har gobe in dawo Farooq? Ai gwara in dawo nan din
gaba daya kawai, Abincin da aka kawo min ko budewa ban yi ba na dauko kawai na saɓa
gyale na biyo hanya in kawo masa ko zai iya ci" Khalil ya ajiye maganin hannunsa a
hankali yace "Ina yini Inna?" Cikin rawan murya tace "Lafiya lau" Daga haka ta tafi
wajen Abba dake ta bin ta da ido ta zauna gefensa tace "Yanda baka kashe ubanka ba
ko uwarka to babu ɗan ɗa zai kasheka Ibrahim, in Allah ya yarda ba baƙin ciki bane
ajalinka, Allah zai baka lafiya kayi rayuwa me tsayi ka ci gaba da bauta masa,
sannan ka ci gaba da taimakon bayin Allah kamar yanda ka saba" Khalil ya mike kawai
ya fita daga dakin, Main parlor ya koma ya zauna, har sannan ya ji ya kasa yarda da
abinda Farooq ya sanar masa akan Nihal, he is still finding it hard to believe
this, Mumy ta fito daga kitchen rike da cup din kunu, ganinsa a parlon tace
"Ibrahim abincinku kai da farooq na can dakinsa" Khalil yace "Toh mun gode" Zata
wuce yayi karfin halin cewa "Mumy ina son ganin Nihal" Mumy ta juya tana kallonsa,
ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "To ina zuwa" Bangarenta ta tafi dama kuma dakin
Nihal din zata shiga ta dau makulli a bedroom dinta tana kallon Nihad da ta kwanta
gefen gado sai juye juye take tace "Za ki sha kunu ko?" Nihad ta kalli Kunun hannun
Mumy sai kuma ta gyada mata kai a hankali, Mumy tace "Ina zuwa" Daga haka ta fita
daga dakin ta tafi dakin Nihal, bayan ta bude ta shiga dakin, kwance ta sameta kan
gado idonta biyu, pillownta yayi jagab da hawaye, Mumy ta ajiye Cup din hannunta ta
zauna gefen gadon tace "Ibrahim wants to speak with you Nihal" Nihal ta dinga
kallonta alamar bata san wani Ibrahim din ba, Mumy tace "Mijin er uwarki" Nihal
bata iya tace komai ba, lokaci daya wasu hawayen suka cika idonta, Mumy ta juya ta
fita, bayan ta koma main parlor tana kallon khalil tace "Ka karaso Ibrahim" Mikewa
yayi ya bi bayan Mumy har zuwa bakin kofar dakin Nihal, sannan Mumy ta juya ta bar
wajen, a hankali ya murda kofar dakin hade da sallama ya shiga, Nihal dai na zaune
gefen gado, ya karasa har gaban mirror din ya rungume hannunsa yana kallonta, ita
dai ta kasa barin su hada ido, haka nan kawai yaji tausayinta ya dirar masa a
zuciya, a hankali yace "Nihal" Ta daga idanuwanta da suka kumbura tana kallonsa,
lokaci daya ta fashe masa da kuka, ya girgiza kai yace "Ba kuka na shigo ki min ba,
now tell me who is responsible??" Kuka kawai take bitterly ta kasa ce masa komai,
yace "Who is responsible Nihal?" Ta hade kanta da gado still crying loudly, sauke
idonsa yayi daga kallonta, yana jin tausayinta har cikin ransa, ya barta tayi kukan
me isarta sannan yace "Now tell me who is responsible" Ta dago kanta a hankali tace
"Abdallah" Yace "Who he is? And a ina kika san sa?" Cikin rawar murya tace "Babansa
Minister ne" Khalil ya ɗan yi shiru, can yace "Minister of what" ta girgiza masa
kai tace "Nima ban sani ba" Yace "Toh a ina ku ka hadu da shi?" Tace "ABU yaje
wajen wani abokinsa da yake masters a can" Yace "Sai me ya faru?" Bitterly tace
"Yana ta bi na a makaranta for like two days requesting for my phone number, he
said he only wants us to be friends, shine na basa amma ni bana son waya da shi,
har na dawo gida hutu sai yayi ta kirana bana dauka, Umma tayi noticing shine ta sa
na fara picking calls dinsa ba da son raina ba, har cewa take in bata su gaisa da
shi, sanda ya zo kano yace zai gaisheta sai ta tafi gidan friend dinta Mama Turai
ya sameta a can suka gaisa, tun daga sannan Umma take forcing dina sai na dinga
kulasa sosai" Kuka take sosai kamar ranta zai fita, khalil yace "Ina jin ki" Tace
"Dalilin da yasa na fara kulasa kenan, duk weekend yana shigowa Zaria wajena" Yace
"Daga ina yake zuwa" tace "Abuja" Khalil yace "Sai me ya faru?" Tace "He is always
requesting to take me out for shopping, dama Umma tace kada ince zan bi sa wani
waje kuma kar ince zan shiga motarsa, shine ranan ya kirata yace za mu je yayi min
shopping amma nace masa ta hana ni fita daga makaranta yana neman excuse to go out
with me for shopping, shine Umma ta amince ya fita da ni ranan" Shiru tayi tana
goge hawayen idonta, Khalil yace "Go on" tace "Muna shiga mota muka tafi yayi min
shopping, bayan mun fito daga shopping mall din ya dau drink a motarsa ya bani nace
masa am okay, sai ya nuna min bai ji dadi ba... Shine na amsa kawai, sai da muka
koma makaranta na sha drink din da shawarma dat he bought me" Khalil yace "A ina
kika sha?" Ta daga kai ta kallesa tace "A motarsa" Yace "Why did u eat in his car?"
A hankali tace "He insisted, shi ma a ciki ya ci nasa, shi yasa nima na ci" Khalil
ya gyada kai, a hankali yace "And then?" Wasu hawaye na sauka idonta tace "I don't
really know what happened after that, I don't understand" A hankali Khalil yace
"Did u pass out?" Tace "Noo, but i wasn't my self, i remember him telling me bari
mu siyo wani abu mu dawo, shine ya kai ni wani waje, i still can tell ko gida ne ko
ba gida bane...." Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka, Khalil ya kasa cewa komai
yana kallonta, ta goge hawayen idonta tace "Bayan wannan incident din sai yayi ta
threatening dina that he have my video if i should say no to him zai yi leaking
dinsa, i was confuse on what to do and who to tell.... I was so confused" Khalil
yace "Me yasa baki gaya min ba?" Ta kasa ce masa komai hawaye na ta sauka idonta,
tace "Shikenan, and i neva said no to him ko me yace min, saboda ina tsoron threat
dinsa" Khalil yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, and he kept on using u?" Ta
gyada masa kai, yace "Did u tell him about the pregnancy?" Ta gyada kai tace "He
blocked me bayan na gaya masa" Khalil yace "Kina da hotonsa?" Ta girgiza masa kai
tace "Na goge dukka har da numbersa, but i have his IG handle yana so hotunansa a
can" Ya ciro wayarsa yace "Gaya min handle din nasa" a hankali ta gaya masa, yayi
searching sunan a Instagram, yana fito masa ya fara shiga hotonsa, Still Khalil
yayi yana ta kallon hoton da mugun mamaki yace "This is Abdullahi" Nihal dai tayi
shiru tana kallonsa hawaye na sauka idonta, Khalil ya kasa rufe baki ya kalleta da
sauri yace "I know him, he is Aliyu's friend, is he the one u are saying about
now??" Nihal ta fashe da kuka ta hade kanta da gado tana shessheka, Khalil ya
girgiza kai sadly yace "He lied to you, ba ɗan minista bane shi kamar yanda ya gaya
maki, gaba daya Clique dinsu ba su da aiki sai na karyan identity da yaudaran yaran
mutane, makaryata ne na karshe... Aliyu is his very close frnd" Khalil yayi wani
murmushin takaici yace "In his next life bazai sake lalata kowa ba...." daga haka
ya juya ya fice daga dakin, Nihal dai ta bi sa da kallo hawaye na sauka idonta.
Khalil ya koma dakin Farooq ya zauna yana tunanin ta yanda zai billo ma lamarin
nan, banda tafarfasa babu abinda zuciyarsa yake, he is going to make sure Abdullahi
bazai sake moruwa a rayuwa ba, yanda ya lalata ma Nihal rayuwa shi ma sai inda
karfinsa ya kare na ganin ya lalata masa rayuwa kafin hukuma su shigo ciki, And he
felt so bad he didn't listen to her ranan da ta kirasa yana tare da Nadeeyah, he
wish yayi taking excuse daga gun Nadeeyah ya tafi gefe ya saurareta may be da
abubuwan sun zo da sauki, yana ta tunane tunanen nan Farooq ya shigo dakin, Farooq
ya ajiye wayarsa gaban mirror yana kallon Khalil yace "Ka zuba abincin ka ci"
Khalil ya kallesa yace "Ka ba ma Nihal listening ear?" Farooq ya girgiza masa kai
kawai ya shiga banɗaki alamar bai ma son zancen, Mikewa yayi ya fice daga dakin ya
tafi waje gun Aminu a bakin gate, tun shigowarsa gidan dazu da rana Aminu ya sanar
masa abinda ke faruwa a gidan, wanda sai da ya samu benchi ya zauna saboda shock,
yana shiga cikin gidan kuma Farooq ma bai boye masa komai ba ya sanar masa abinda
ke faruwa, Aminu na hango Khalil ya mike tsaye, har Khalil ya karaso, Aminu yayi
kasa da murya cike da damuwa yace "Jikin me gidan da sauki yanzu? Ni dai dazu da na
shiga dubasa bakin ya sake rufewa" Khalil yace "Da sauki Alhamdulillah" Aminu yace
"Allah
Ubangiji ya tashi kafadunsa, Allah ya basa lafiya, mutumin kirki wallahi" Khalil
yace "Bari in shiga Masallaci Aminu" Daga haka ya fita daga gate din zuwa
masallaci. Karfe tara saura Khalil yayi sallama kofar parlon Mumy, bayan ta amsa
masa ya shiga, Nihad na kwance saman kujera ga kunun da Mumy ta kawo mata ta kasa
sha, tayi amai kuwa ya fi a kirga, Mumy tace "Kun ci abinci dai ko?" Yace "Ehh,
Mamina ce zata maku magana" Mumy tace "Toh" wayarsa ya kai ma Mumy, Mumy ta amsa ta
kai kunne hade da yin sallama, Mami ta amsa daga daya bangaren bayan sun gaisa ta
tambayeta jikin Abba, Mumy tace "Jiki Alhamdulillah mun gode Allah, ya yaran?" Mami
tace "Alhamdulillah, Allah Ubangiji ya tashi kafadunsa, ya basa lafiya" Mumy tace
"Ameen Hajiya nagode" Mami tace "Zan sa ya tura min numberki inyi saving in sha
Allah" Mumy tace "Toh ba damuwa" Mami tace "Nihad na kusa?" Mumy tace "Eh ga ta"
Daga haka ta mika ma Nihad wayar, Nihad ta mike zaune bayan ta amshi wayar ta kai
kunne, suka gaisa da Mami, Mami ta tambayeta jikin Abba sannan tace "Hope kina ɗan
cin abinci?" Nihad ta gyada kai a hankali tace "Ehh ina ci" Mami tace "Toh maa sha
Allah, mu kwana lafiya" Nihad ta mata sai da safe sannan ta katse wayar Khalil ya
karasa ya amsa, bai jima a parlon ba ya fita. Wajen karfe sha daya saura Khalil na
wajen Abba tare da Farooq da Usman da ko awa biyu bai yi da shigowa gidan ba, sai
yayan Abba Alhaji Abubakar dake shirin tafiya gida, Inna ma na makale dakin taki
tafiya wai gidan zata kwana, Abba na ta kallon Alhaji Abubakar da ya mike yana
lallaba inna ta tashi su koma gida da kansa zai dawo da ita gobe da safe, a hankali
Abba ya buda baki yace "Akwai maganan da zan yi Alhaji" Alhaji Abubakar ya kallesa
sannan ya koma ya zauna, tun bayan da ya sha magungunan da Khalil yayi prescribing
din masa dazu da yamma yake ɗan iya bude baki yayi magana har ya fito, Alhaji
Abubakar yace "Ina jin ka Ibrahim" Mikewa Khalil yayi yana son barin dakin Abba
yayi masa alama da ya koma ya zauna, inna warce ke ta farin ciki ɗan nata ya fara
bude baki har aji abinda yake cewa ta kalli Khalil da sauri tace "Koma ka zauna
Halilu ai ka zama ɗan gida yanzu... Duk daya muke da kai" Khalil ya koma ya zauna,
Abba ya kalli Farooq yace "A kira min duk yan gidan, har Nihad da su Kamila" Farooq
ya mike ya nufi kofa walking slowly ya fita, Bangaren Mumy ya fara zuwa ya sanar ma
Mumy sannan ya juya ya fita, tun dazu Mumy ke son taje dakin mai gidan nata ta duba
jikinsa amma ta kasa saboda Inna da tayi bake bake a dakin sannan kuma Alhaji
Abubakar tun isha yake gidan, Nihad ma ita ta hanata zuwa saboda yanayin jikinta
duk da yanda ta damu tana son zuwa amma tsayuwan kirki bata iya yi for long balle
tafiya zuwa bangaren Abba, Farooq na fita side din Mumy ya tafi bangaren Umma, tana
zaune kan darduma can karshen bangon dakinta sanye da dogon hijab hannunta rike da
carbi, tun da tayi sallan asuba take wajen nan, sai dai taje ta sake alwala ta dawo
ta zauna, Farooq ya sanar mata kiran Abba sannan ya juya ya fita, shi ma duk kamar
ba shi ba, gaba daya a sanyaye yake, sosai gaban Umma ya fadi, amma haka ta dake ta
mike tana jin jiri idanuwanta sunyi bulu bulu, circle din idon yayi bakikirin
tsabar kuka da tashin hankali, duk ta fice hayyacinta ta dawo gata nan gata nan ne,
sai da ta shiga bandakinta ta sake dauro alwala sannan ta fito tana jan kafa ta
tafi bangaren Abba, har bedroom dinsa ta shiga da sallama, nan taga har Mumy da
Nihad a dakin, ga Inna da Alhaji Abubakar, Khalil da Usman, Kamila da Amina, Nihal
ce kadai bata dakin, Umma ta nemi gefe ta rakube amma bata bari ta hada ido da kowa
ba na parlon, Farooq ya karasa ya zauna inda yake, Abba dai bai ce komai ba sai
kallon ceiling yake, lokaci lokaci Inna ke sauke ajiyar zuciya take girgiza kafa,
Alhaji Abubakar yace "Ga su nan gaba daya Ibrahim, muna kuma sauraronka...." Abba
ya dinga bin su da kallo a parlon kafin a hankali yace "A da na so barin abinda zan
fada a yanzu ya zamo wani sirri tsakanina da Sumayya sai kuma Maryam, amma yanzu
hakan bazai yiwu ba saboda there is need for me to speak out, don haka nake sanar
da cewa for almost a month now babu aure tsakanina da Sumayya, zaman 'ya yanta
kawai take a gidana, na kuma bata dama ta ci gaba da duk harkanta kamar yanda ta
saba a gidan nan" Kowa na dakin sai da ya girgiza barin Farooq da ya kasa daina
kallon mahaifin nasa, Umma dai kanta na kasa taki dagowa, Inna ta saki salati ta
mike tana tafe hannu tace "Ka saki sumayya??" Alhaji Abubakar yace "Ki koma ki
zauna Inna" Ta koma ta zauna tana kallon Umma baki sake, Abba yace "Bayan ni da ita
babu wanda yasan dalilin sakin nata, don hatta Maryam ban sanar ma ba, ta dai san
babu aure tsakaninmu amma yanzu zan sanar ma kowa na dakin nan dalilin da ya sa na
saki Sumayya kafin in shigo da ainahin maganar da yasa na tara ku a dakin nan...."
Banda hawaye babu abinda Umma take, Nan Abba ya basu labarin wayan da ya tadda Umma
ke yi a bandaki da kuma abubuwan da kunnuwansa suka jiye masa a ranan, Inna ta
fashe da kuka ta mike jiki na rawa tana kallonsa tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'una, anya kunnuwanka sun jiye maka da kyau kuwa Ibrahim? Wannan sumayyar ko
wata daban dai kake nufi?" A hankali Abba yace "Ga ta nan ki tambayeta ko ba ayi
haka ba Baaba, ki tambayeta...." Umma ta fashe da kuka da karfi tace "Ko ma me nayi
kai ne silla Ibrahim, kai ne ka kai ni ga duk halakan da na shiga a rayuwa, babu
uwar da zata so taga ana nuna ma 'ya yanta halin ko in kula a kan 'ya yan
kishiyarta, babu warce zata iya daukan wannan masifar, ka fifita Nihad akan nawa
'ya yan da na haifa maka kafin a haifeta, ka nuna Nihad ita ce er ka sauran kuwa ba
naka 'ya yan bane hatta Nihal da take sa'arta baka damu da lamarinta ba sai na
Nihad, ka banzatar min da nawa 'ya yan duk a kan Nihad, ka nuna ita ce er so, kaf
gidan nan babu ɗan da ka cire kudi ka biya ma tsadadden makaranta tun daga Primary
har secondary sai Nihad, a kan Nihad Kamila bata samu cikakken kayan daki ba ka
gwammaci ka kai ta Private University bayan ni tawa er ka kai ta federal ka
ajiyeta, kafin ka biya ma 'ya yana bukatansu daya ka biya ma Nihad bukatunta goma,
shine nima na nuna nafi kowa sonta don ta haka ne kadai zan iya cimma burina na
rama duk abinda kayi ma 'ya yana a kanta, you caused everything Ibrahim, duk abinda
nayi ma Nihad kai ka jawo, barin ta zuwa hotels, clubs, party, bin kawayen
banza.... kai ka kaini ka baro Ibrahim" Inna da ta hangame baki kamar yanda Mumy
tayi ta dinga kallon Umma a tsorace, Kuka sosai Umma ke yi tana girgiza kai tace
"Gashi yanzu ta dalilin son kanka duk wani mugun abu da na so ma Nihad a duniya sai
da ya dawo kan nawa 'ya yan, ka cuce ni da yarana Ibrahim, ka cucemu...." Ta Kasa
ci gaba tana kuka sosai kamar ranta zai fita, a mugun fusace Inna ta nufeta tana
kunduma mata zagi tace "Allah ya tsine maki Sumayya, Allah ya isa tsakaninmu dake,
dama can zuciyar kafurai gareki kada ki laka ma ɗa na, dama can ke kafura ce mara
tsoron Allah, idan bai so Nihad ba wa zai so dama?? abinda uwarta sai da tayi
shekara kusan talatin bata haihu ba a gidan nan babu irin walakanci da cin kashin
da Maryam bata hadiya ba a wajenki, babu irin gorin haihuwan da baki mata ba sai
wanda kika manta amma matar nan ta mika lamuranta ga Allah kuma bata fasa zama
zuciya daya dake ba tana bin ki, kin xata duk mun manta wannan? sannan don ubanki
da kike cewa an banzantar da 'ya yanki, ke kika rainar min farooq da Usman?? Ba duk
wajena suka gama har sakandari ba kafin su tafi jami'a?? Wani abu ne na gata
Ibrahim bai masu ba wanda har ita Nihad din ban ga ta samu irinsa ba? Wani kula ne
Ibrahim bai ba yaran nan ba da suke wajena Sumayya?? Wani kudi ne bai kashe masu
ba? Kamila da kika ce kudin kayan dakinta bai cika ba karya fa kike son yi ya nuna
maki bazai iya ba, yar gwal ce ita da za a siya mata kayan daki kusan miliyan goma
a zamanin nan??? Sannan Nihal da kike cewa bai damu da al'amarinta ba ta ina ya
shaku da ita yarinya duk kiwuya kowa ta maida shi dodo?? Ina ce har ni bata yadda
da ni a sanda take karama? Kuma har yanzu da girmanta kin ga tana zuwa wajena? A
ina kika taba ganin yaro me kiwiya an shaku da shi? Ai sai dai uwarsa, don haka duk
sharrin da kika laka ma ɗa na Allah ya saka masa, Allah ya isa tsakaninsa dake,
Wato har bedio da aka ce yana ta yawo na Nihad har da sa hannunki kenan??" Sai kuma
ta fashe da matsanancin kuka ta koma ta zauna, Nihad dai sai kallon Umma take
hawaye na sauka idonta, shi kam Abba was speechless, Khalil ne ya fara tashi ya bar
dakin, Inna tace "Aa dole ka tashi ashe duk ga warce ta gurbata rayuwar matarka tun
yana er yarinya bamu sani ba" Sai kuma ta rushe da kuka tace "Allah na tuba ka
yafeni da hadin bakina fa aka dauke Nihad daga wajen uwarta aka ba Umma ashe matar
da sharri take nufinta bamu sani ba" Alhaji Abubakar sai share zufan da ke keto
masa yake yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" A hankali Abba ya lumshe ido
with tears in his eyes yace "I have failed as a father"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788💖 NIHAAD 💖

73

Khalil na fita dakin Abba ya kira Farooq, Farooq bai daga wayar ba ya mike kawai ya
bi bayansa, he is so heartbroken, main parlor ya samesa tsaye, ya tsaya shi ma yana
kallonsa bai ce komai ba, Khalil yace "This is not the rightful time for that
conversation saboda condition din sa, u have to stop it plss, it's not appropriate
for his health" Farooq dai bai iya yace masa komai ba sai kallonsa yake, Khalil ya
juya ya fita daga parlon, Farooq bai sake komawa dakin Abba ba, ya nufi dakinsa
walking slowly yana ganin kamar mafarki kawai yake. Inna na ganin hawayen da Abba
yake ta rushe da matsanancin kuka cike da takaici tace "Wallahi kin cuce mu
Sumayya, kin cucemu, Allah ya isa bamu yafe maki ba, ashe duk ke kika lalata masa
gidansa duk kokarin da yake na ganin ya ba 'ya yansa tarbiya nagari, duk kokarinsa
na ganin 'ya yansa sun zama na kirki kin tarwatsa masa, daga me Video dake yawo a
gari sai warce aure ya mutu an korota gida sannan uwa uba wai yau cikin shege a
zuri'armu, cikin shege fa?? ya ya zaki yi da wannan hakkin sumayya? Kuma saboda
karancin tsoron Allah kike nema ki alaqanta duk wannan abun da Ibrahim, dama can
kafura ce ke kawai wacce babu Allah a ranta, to bazan boye maki ba a gaskiya
zamanki ya zo karshe a gidan nan, ni kaina baxan jure ci gaba da ganinki ba balle
shi wanda kika cuta ga har ciwo ya kama sa, ki tattara yanaki yanaki ki kama
gabanki kawai Sumayya, ganinki kadai ya isa yasa Ibrahim yaki warkewa wallahi, ki
je duk inda za ki mu kuma baza mu hana yaranki zuwa gareki ba tunda ke kika
haifesu, alhakin abinda kika so ma Nihad ne ya sauka kan er ki, Sumayya kin cuci
Ibrahim don Nihal din ma er sa ce ba abinda zai canza hakan, shi yasa aka ce in
zaka gina ramin mugunta ka ginasa karami, ke ko baki yi wannan tunanin ba..." Umma
dai bata ce komai ba sai kuka take ta dafe kanta, Mumy ta kasa dago kanta ita ma
hawayen ne ke sauka idonta, Nihad kuwa gaba daya ta shiga rudani jin Inna ta ambaci
cikin shege, waye kuma yayi cikin shege, Nihal?? No it can't be Nihal, Tashi Usman
yayi ya fita daga dakin cause he can't endure it anymore, Umma ta mike tana share
hawayenta da zumar fita ita ma, taji muryar Abba a hankali yace "One more thing
Sumayya...." Ta juya ta kallesa, yace "Tell me what u know about Nihad's Video...."
Ta ɗan yi shiru na few seconds, sai kuma hadiye kukan da take tace "Kawayenta ne
suka yi drugging dinta sannan suka mata video din suka kuma saki a duniya..." Mumy
ta daga kai da sauri tana kallon Umma, Inna ta sake salati tana zaga dakin hankali
tashe, Alhaji Abubakar dai is totally speechless, a hankali Abba yace "U asked them
to do that?" Umma ta girgiza kai tace "Sai bayan da suka yi ni nasani, i never
asked them to do that..." Yace "Shikenan, Kije... ni kam na yafe maki, a duk zaman
mu idan akwai inda na kuskure maki ko yaranki ina neman gafara, Allah ya yafe mana
baki daya" Tana share Idonta tace "Ameen, ni baka taɓa min komai ba, Allah ya baka
lafiya" Daga haka ta juya ta nufi kofa inna ta bi ta da sauri tana hawaye tace "Ai
komin dare ana samun a kori kura, aje a samo ki kwashe kayanki Sumayya kada abu ya
lalace mana ni da ke cikin dare" Mikewa Kamila da Amina suka yi suka bi bayan
uwarsu ko warce da hawaye fuskarta, Abba ya kalli Mumy dake kallonsa tana hawaye
ita ma, cikin sanyin murya yace "I am sorry i never played my role well as a
father, i am sorry i broke my family..... I am sorry for everything" Alhaji
Abubakar yayi karfin halin cewa "Kar kace haka Ibrahim, komai kaga ya faru a duniya
Allah ne ya tsara hakan, stop thinking u failed ur family, u never failed them, u
were and will always remain a good father..." Da kyar Abba na kallon Mumy yace "Ki
kira min Nihal" Alhaji Abubakar ya dafasa yace "Noo, not now Ibrahim, sai ka kara
samun lafiya sosai, yanzu a bar wannan maganar haka, u need rest for now pls" Abba
bai kuma ce masa komai ba, Mumy ta share hawayenta ta mike ta nufi kofa a sanyaye
ta fita daga dakin, Nihad dai ta kasa tashi a inda take sai kuka take a hankali,
ganin Abba kallonta yake ta mike cike da karfin hali ta tafi can kusa da shi ta
durkusa cikin rawan murya tace "Abba kayi hakuri, all this is happening because of
me, i caused all this, i am sorry Abba, May be you shouldn't have...." Kasa ci gaba
tayi tana kuka sosai, Abba dai sai kallonta yake ya kasa cewa komai, nan kuwa tuna
irin yanda Allah ya dora masa sonta a zuciyarsa tun tana er yarinya yake, wanda tun
a sannan bai iya boye son nan ba har girmanta, kaf 'ya yansa babu warce yaji har
ransa kamar ita, and Umma used that against him by helping him to love her whereas
ba haka bane a zuciyarta, Umma used that to runined him and his family, Hawaye
Nihad ta gani a idonsa ta fashe da kuka sosai ta ma rasa abinda zata ce masa ta
daura kanta a jikinsa cikin rawan murya tace "I am sorry Abba, i am so sorry Abba"
murya can kasa yace "I will always love and Cherish u Nihad, you still remain my
favourite, Allah ya baki zaman lafiya da mijinki, Allah ya baki ikon yi masa
biyayya kamar yanda mahaifiyarki ta min, Allah ya baku zuri'a dayyaba, at last
everything turns out to be in ur favor.... " Ganin irin kukan da take yi Alhaji
Abubakar ya mike ya dagata yace "Tashi ki je Mamana, Allah ya maki albarka" Har
kofar fita parlon ya rakata sannan ya koma gun kanin nasa. Har kusan karfe sha biyu
Nihad bata hakura da kukan da take ba, gani take kamar saboda ita duk abubuwan nan
suka faru, and condition din da Mumy ta gaya mata Nihal ke ciki contributed wajen
kara daga mata hankali ta kasa daina kuka, tsabar yanda hankalinta ya tashi bata
iya ta je dakin Nihal din ba, she don't even know what to say to her, it's till
hard to believe wai she is pregnant, Mumy ta fito parlor ta dalilin wayarta dake
ring ta duba taga Khalil ne ke kiranta, dagawa tayi tare da yi masa sallama, daga
daya bangaren ya amsa yace "Mumy hope ban tashe ki bacci ba" Mumy tace "Aa ban
kwanta ba tukun" Yace "Dama zan ce maki magungunan ta na cikin akwati ne" Mumy tace
"Ohk bari in duba" Daga haka yayi ma Mumy sai da safe ta katse wayar, ta mike ta
nufi akwatin Nihad ta bude ta ciro magungunan sannan ta duba prescriptions din ta
bata ta sha,Tana shan maganin ba a dau lokaci ba bacci me nauyi ya dauketa. All
through the night Mumy bata wani rintsa ba, to ina ma taga kwanciyar hankalin
bacci, lokaci lokaci kuma take shiga dakin Nihal ta dubata sannan ta dawo ta ci
gaba da sallanta, Inna kuwa na parlon Abba a nan aka mata shimfida da bargo don
taki bin Alhaji Abubakar gida, ita ma dai bata yi baccin kirki ba sai sallah take
tana roka ma ɗan ta lafiya a wajen Allah, duk a daren ta yanke shawaran kawai ta
dau Nihal ta kai ta Bauchi wajen kanwarta har Allah ya sauketa a can don idan har
uban na ganinta a gabansa da kyar ya samu lafiya har ya tashi, gwara kawai ta
nesantata da shi, ta kai ta can inda bata san kowa ba tayi rainon cikin tunda taji
ance baza a zubar ba, Umma ma dai yanda taga rana haka taga dare nan babu ko digon
bacci a idonta, yanda take ji kuma a jikinta tasan jininta ya kara hawa, a daren
nan tayi mugun da ta sanin duk abubuwan da ta aikata, tayi da ta sani ya fi a
kirga, kamar yanda Inna ta fada babu abinda yaranta suka rasa gun Abba kawai son
zuciya ne ya kai ta ya baro, duk da baya nuna masu irin son da yake ma Nihad din a
fili amma basu taɓa kawo bukatunsu ya ki yi ba ko ya hanasu, Nihal ce dama bata iya
tambayarsa abu, komai take so sai ta bi ta hannun Umman, shi ko Abba idan baka
tambayesa ba he will assume u don't need it, Nihad kam kullum cikin tambaya take
kuma kullum cikin bata yake, Usman da Farooq throughout the night suna tare da
Abban nasu a dakinsa, Khalil dai lokaci lokaci yake shiga ya duba jikinsa a cikin
daren, idan ya dubasa kuma ya koma dakin Farooq, Mumy na son shiga ta duba Abban
amma ta kasa zuwa sanin Inna na parlon nasa sannan su Farooq na bedroom dinsa.
Karfe hudu da yan mintuna Mumy ta samu ta kwanta bacci ya dauketa, 4:30 Khalil ya
fito daga dakin Farooq ya nufi bangarem Abba, duk da an hour ago ya shiga ya dubasa
last, kwance ya samu Inna a parlon tana bacci har da minshari, wanda daxu da ya
shigo idonta biyu tana ta sallah, walking gently don kar ya tasheta ya nufi dakin
Abba, dazu da ya shigo Farooq ne kawai ke bacci Usman idonsa biyu, amma yanzu kuwa
duk bacci suke saman Carpet din dakin, ya karasa saman gadon yana kallon Abba don
ba a position din da ya bar shi dazu ya samesa ba ya karkace kansa dake kan pillow,
dukawa Khalil yayi murya can kasa yace "Abba ya jikin?" Abba bai ce masa komai ba,
ya kai hannu zai gyara masa kwanciyar saboda kar wuyarsa yayi ciwo sannan ya danne
hannunsa me matsala, Khalil ya fi 20 seconds yana kallon Abba babu ko kiftawan
kirki, can ya kwantar da shi da sauri ya cire pillow din da yake kai gefe yana duba
every pulse that he can check a jikinsa, ji yayi kafafuwansa sun kasa ci gaba da
daukarsa, bai san sanda yayi kneeling down nan kasa ba yana ci gaba da kallon
Abban, lokaci daya ya hade kansa da gefen gadon hawaye na sauka idonsa a hankali
yana furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un a zuciyarsa, Muryar Farooq yaji yace
"Ohh i slept off...." Khalil dai bai iya ya dago kansa ba, Farooq ya mike ya dawo
kusa da su yace "Ya samu baccin?" Hawaye kawai ke sauka idon Khalil ya kasa ce masa
komai, Farooq ya kalli position din da Abba yake sai kuma ya kalli Khalil da sauri,
lokaci daya yaji gabansa ya wani fadi, ya duka gaban Abba da sauri ya riko hannunsa
yana jijjigawa yace "Abba... Abba" Yaga ko motsawa Abba bai yi ba, kiran da Farooq
ke ma Abban ne da karfi ya tada Usman, ya tashi tsaye da sauri, Farooq ya kai kansa
chest din Abba jikinsa na rawa and he heard nothing like heartbeat, ganin abinda
Farooq yayi Usman ya nufosa hankali tashe yace "What is the meaning of that???" Shi
dai Khalil ya kasa dagowa ya kallesu, he was weak all over, hawaye ya kasa daina
zuba a idonsa, Farooq ya hade kai shi ma da jikin gadon hawaye na sauka idonsa yace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" hayaniyar
Usman ne dake ta jijjiga Abba yana kiransa ya tada Inna, da gudu ta shigo dakin a
rikice, jiki na rawa tace "Menene kake kiransa haka Usuman??" Usman ya fashe da
kuka ya durkusa nan kasan dakin, Inna ta tafi saman gadon da sauri ko ina na
jikinta na bari tana cewa "Ku gaya min me ya samesa, me ya samu ɗan nawa? Wayyo
Allah na ku gaya min don Allah" Ganin babu me shirin bata amsa, ga Khalil da Farooq
sun ki dago kai, Usman kuma yayi zaman dirshan a kasa ya rike kai yana kuka, ta
fashe da matsanancin kuka da gudu ta fice daga bangaren ta shigo main parlor a
gigice ta saki salati da duk karfinta, sai kuma ta fasa ihu ta daura hannu a ka
tana zaga parlon, Mumy ce ta fara fitowa da sauri daga ɓangarenta a tsorace, Sai ga
Umma ma ta fito da su Kamila, Nihad ma ta fito daga parlon Mumy, Inna na kallon
Mumy ta kara kwala ihu tana girgiza kai tace "Na shiga uku Maryam, wayyo Allah na
Maryam, na shiga uku na lalace, su ce min wasa suke min, Innalillahi wa inna ilaihi
raji'una...." Sai kuma tayi collapse nan kasa, Umma dai jikinta sai rawa yake ta
kasa karasowa cikin parlon, Mumy bata kara kallon Inna ba ta yi bangaren Abba duk
jikinta na rawa ta shiga, Nihad bata san sanda ta bi bayanta ba ita ma da sauri,
dai dai sanda Khalil ya mike ya ja ma Abba abun rufansa ya rufe har kansa Mumy ta
shigo dakin, Banda kuka babu abinda Farooq da Usman suke, Mumy taji wani jiri ya
debeta ta fadi a sume nan kasan dakin, wani kara Nihad ta kwala da karfi ita ma ta
sulale nan kasa.... Kafin wayewar gari gidan Abba ya cika babu masaka tsinke da
jama'a, ko wajen parking babu a layin, abokansa na wajen aiki, yan uwa da abokan
arziki, makota, wa enda ya taimaka a rayuwa, childhood friends duk dai gasu, babu
wanda bai ji mutuwarsa ba, da yawa al'umma sai da suka yi kwalla, shaidar da Abba
ya samu kuwa ba a cewa komai, an masa shaidan mutumin kirki me rike ibada sannan me
tausayi da taimakon talaka, Aminu kuwa kai kace Mahaifinsa ne ya rasu don can bayan
gidan ya tafi ya dinga kuka yana buga kai, haka Saminu da Isiya, karfe takwas saura
Janar da abokansa biyar suka iso gidan tare da Mami da su Mimi.... Mami was more
than shock ta kasa kallon Mumy ta nemi waje a parlon dake cike ta zauna tana nanata
Innalillahi wa inna ilaihi raji'una a zuciyarta zuwansu gidan da kuma position din
da Abban ya zauna cikin parlon yana magana cikin girmamawa cike da dattako kawai
take tunawa, irin kukan da Umma ke yi a parlon dole a tausaya mata, duk ta birkice
ta dawo kamar wata tabaɓɓiya, Mumy dai ba um ba um um sai hawaye don zuwa lokacin
sumanta uku, Aunty Jamila dake gefenta tana ɓata baki cikin nutsuwa ita ma dai
kukan take, haka frnds dinta su hudu da ko wacce kokarin kwantar mata da hankali
take, Karfe tara aka tafi kai Abba makwancinsa, a sannan ne Mumy ta kara realizing
da gaske tayi loosing mijinta forever and she couldn't endure it any longer, hakan
yasa su Aunty Jamila suka shiga da ita part dinta. Bayan an dawo daga kai Abba Mami
ta samu Khalil a compound tana tambayansa Nihad don tun da suka zo bata ganta ba,
tana son tasan halin da yarinyar take ciki, bai iya ya daga kai ya kalli Mami ba
yace "Tana asibiti tare da wata Aunt dinta, she miscarried the pregnancy...." Mami
ta kasa cewa komai tana kallonsa, can tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,
hope she is fine amma?" Yace "Yanzu zan je can din, an mata alluran bacci ne tun
wajen 6" Mami ta kasa cewa komai, she really pitied the family sosai, a hankali
tace "Toh ka je, Allah Ubangiji ya bata lafiya, ita ma mamarta da alluran baccin
aka samu aka yi mata" Yace "Bari dai in je asibitin in dawo, kakarta ma na asibiti"
Mami tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Juyawa Khalil yayi ya nufi gate, a
sanyaye Mami ta koma cikin gidan....

*Barrister yace harba masu haka nan ko ba yawa su yi maneji* 😟

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788💖 NIHAAD 💖

74

Nihad ta daga kai tana kallonsa har ya karaso cikin dakin, ya zauna kusa da ita
yana kallonta a hankali yace "My father wants to speak to you Nihad" Ta sauke
idonta hawaye na saukar mata bata ce komai ba, ya goge mata hawayen ya mike ya
dagota suka nufi kofa don da Hijab har kasa a jikinta, It is around 5pm na yamma,
kuma ranan aka yi sadakan ukun Abba, har a sannan kuma akwai jama'a sosai a gidan,
tana biye da shi kamar iska zai hureta ta fadi har suka iso parlon Abba, Janar na
zaune da frnds dinsa a parlon sai yan uwan Abba biyu da amininsa da wasu Colleague
dinsa, Nihad ta karasa har kusa da Janar ta duka kasa ta gaishesa cikin sanyin
murya hawaye na zuba idonta, yayi patting shoulder dinta cike da tausayinta ya
kwantar da murya yace "Kiyi hakuri daughter, take heart dear, a yanzu ur dad needs
nothing from u than prayers, baya bukatan wannan kukan naki, ki yawaita yi masa
addu'a that is all he needs now...." kai kawai ta gyada masa hawaye wani na bin
wani a fuskarta, ya dai yi mata nasiha masu kwantar da hankali da kara hope,
Sojojin dake parlon da abokan Abba na taya sa, shi dai khalil na tsaye bakin kofa
yana kallonta, he is full of pity for his wife, he wish he can take all her pain
away, so kawai yake ya samu space din lallashinta yanda ya kamata don har yanzu bai
mata lallashin da ya gamshesa ba, daga karshe Janar ya daga kai ya kallesa yace
"You can leave with her" cikin rawan murya Nihad tayi masu godiya ta mike ta nufi
khalil, Abba yace "I want to speak with the mum and her Co wife also before
leaving" Khalil yace "Alright sir" Daga haka ya bi bayan Nihad da har ta fita daga
parlon, Aunty Jamila ya samu don har sannan ya kasa facing Mumy, ya sanar mata
Janar zai yi magana da Mumy da Umma, Aunty Jamila tace "Toh bari in mata magana" Ta
tafi inda Mumy ke zaune da duk sisters dinta da Aunts suna amsan gaisuwa, Inna da
idonta yayi bulu bulu tana gefe zaune ita ma da wasu tsofaffin a kusa da ita, Aunty
Jamila ta durkusa kusa da Mumy tace "Baban Khalil na son magana dake da Umma yanzu"
Inna da taji abinda Aunty Jamila tace ta kalleta, a hankali tace "Wacece kuma Umma?
Meye hadinta da Baban khalil din har zata je Jamila?" Sai kuma ta fashe da
matsanancin kuka tana girgiza kai tace "Ban yafe maki ba idan kika je da ita, taje
tayi masa me Jamila? Ina ce matar marigayi aka ce ke kira? Yana da wata matar ne
bayan Maryam? jira fa nake yau da daddare idan kowa ya watse gidan nan Sumayya ta
hada kayanta ta tafi kuma haka, ai na mata kara na bar ta har aka yi uku kuma ban
ce komai ba, taje duk inda zata amma bana son ganinta a gidan nan, Allah ya hada mu
a darussalam" Aunty Jamila dai bata ce komai ba, Inna ta kalli Mumy a hankali tace
"Daure ki tashi ki je Maryam, Allah Ubangiji ya kara mana tawakali" Mikewa Mumy
tayi Aunty Jamila na biye da ita har zuwa parlon Abba, ta nemi gefe ta zauna a
parlon, Janar ya kara mata gaisuwa cikin nutsuwa, nan ya dinga bata baki yanda ya
kamata, ita dai hawaye kawai take kanta a kasa bata cewa komai, daga karshe Janar
yace "Allah Ubangiji ya gafarta masa, ya sa yana kyakkyawan masauki, mu kuma Allah
ya kyautata namu, Allah ya kara maki hakuri da dangana" A hankali Mumy tace "Ameen"
Abokansa ma suka kara mata gaisuwa, Janar ya dau wani fancy leda babba dake gefensa
ya mike ya tafi har gaban Mumy ya ajiye mata yace "Allah ya kara hakuri, we will be
communicating in sha Allah" Aunty Jamila ce tayi masa godiya tace "Allah ya kara
girma, ya saka da Alkhairi" Mumy dai bata iya tace komai ba, Wani abokin Janar ya
tashi shima ya ajiye mata wani ledan a gabanta yace "Allah ya kara hakuri Hajiya"
Sauran frnds din Janar suma suka har hada kudin wajensu waje daya duk suka ajiye ma
Mumy, Aunty Jamila ce ke yi masu godiya ita kam bata iya cewa komai, har suka fita
daga parlon, Janar na kallon Khalil da ya shigo yace "Where are all his children?"
Khalil ya juya ya fita, tare ya dawo parlon da Farooq da Usman, Abba ya kara masu
gaisuwa yana kallon Farooq ganin kamar shine babba yace "Kana aiki ai ko?" Farooq
ya gyada masa kai ya sanar masa inda yake aiki a kaduna, Janar yace "That's good"
Ya kalli Usman yace "Kai kuma fa?" Usman ya sauke kansa yace "I had issues with the
place i am working" Janar yace "Ka bani CV dinka kafin in bar gidan nan" Usman yace
"Toh Allah ya saka da Alkhairi" Janar ya mike yace "Bari inyi ma tsohuwa sallama za
mu koma Abuja yau in sha Allah" Har main parlor ya fita ya tafi gaban Inna ya duka
ya kara mata gaisuwa sannan ya sanar mata za su koma Abuja, Ta fashe da kuka sosai
tace "Toh Allah ya saka da Alkhairi, Allah bar zumunci, mun gode, ai ka kyauta ka
ture duk wani aikin tsaro na kasar nan ka jira har aka yi sadakan uku, ina ta
addu'a Allah yasa kada mutanen dajin su lura ba kai su kawo hari cikin gari kai
kuma baka baƙin aiki kaje ka samu matsala da gwamnati" Kuka take sosai tana
maganan, Yace "Kiyi hakuri Baaba, kuma ki rage kukan nan kiyi ta masa addu'a shi
kawai yake bukata daga gareki, kiyi ta masa addu'a" Cikin kuka tace "In sha Allahu"
Dubu dari biyu ya ajiye mata, abokansa ma duk suka karaso suka kara yi mata
gaisuwa, sannan ko wannensu ya ajiye mata dubu dari, ita dai sai kuka take kamar er
yarinya, a haka dai Janar suka bar gidan tare da frnds din nasa don Convoy na waje
tun zuwansu, Khalil ya samu Abbansa da har ya shiga mota, Janar ya juya yana
kallonsa, ya mika masa CV din Usman yayi kasa da murya yace "The first wife, baku
samu kun yi sallama da ita ba...." Janar ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ka bata
500k, i will make the transfer to you" Khalil yace "Alright sir" Janar na kallon
envelope din hannunsa yace "Wannan fa?" Khalil yace "CV din da kace a baka" Janar
yace "Ohh haka ne" Daga nan ya amsa ya mika ma abokinsa dake kusa da shi yace "Kar
in manta wannan pls" Abokin ya amsa, Khalil yace "Allah ya tsare" Daga haka ya juya
ya koma ciki, shi ko don saboda su Farooq bai son a walakanta Umma, ya kamata ta ci
darajarsu, mahaifiyarsu ce kuma uwa uwa ce ko ya take, beside kallo daya zaka yi
mata kaga tsantsan danasani da ladama a tare da ita, duk tayi zuru zuru kamar ita
kadai aka yi ma mutuwa, the thought of this is making him feel so sad. Wajen karfe
shidda Mami tace ma Mumy za su tafi, amma gobe kafin su tafi Abuja zata shigo, tun
ranan da suka zo sai yamma likis suke barin gidan da su Mimi su koma gidansu na nan
Kano, da safe kuma kafin karfe takwas suke isowa gidan, har dai aka yi sadakan uku
yau, cikin sanyin murya Mumy tace "Toh Hajiya, Allah ya saka da Alkhairi, Allah ya
bar zumunci" Mami tace "Ameen, Allah ya kara maki hakuri" Nan tayi ma Inna ma
sallama, sannan ta tafi tayi ma Umma dake can wani lungu a zaune da su Kamila da
kanninta biyu sallama, Mami bata bar gidan ba sai da ta karasa part din Mumy wajen
Nihad, ta sameta zaune tare da Aunty Jamila dake kara kwantar mata da hankali don
ko gajiya da kukan ma bata yi, Mami ta fi 15 minutes a dakin tana bata baki ita ma,
har dai Nihad tayi mata alkawarin bazata sake kuka ba kafin ta bar gidan da su
Mimi. Da daddare Aunty Jamila da sisters din Mumy Suwaiba da Khadija suka dauko
ledan da Janar da abokinsa suka ba Mumy suna dubawa, bundles of note ne masu yawan
gaske yan dubu dubu, kuma kusan kan kudin da abokin Janar ya bada daya ne da na
Janar din, da suka ga ba kudi bane da za su ce zasu iya kirgawa a lokaci kankani
kawai Aunty Jamila ta bude press din Mumy ta ajiye kudaden a ciki. Mumy na kallon
Aunty jamila a hankali tace "Don Allah ku duba jikin Nihal, ko kuma ki ce nace ta
dawo nan" Aunty Jamila tace "Naga basu dade da dawowa daga asibiti da Kawar Umma da
kanwarta ba ai" Mumy tace "Duk da haka ki duba min ita ko ta samu ta ci abinci,
kuma ta dawo nan" Aunty Jamila ta girgiza kai cike da tausayin Nihal tace "Idan zan
koma Jigawa ki bar ni in tafi da ita Mumy kar yarinyar ta samu matsala a
kwakwalwarta, she is already depressed amma har yanzu babu wanda ya gane hakan"
Mumy dai ta kasa cewa komai, don ita bata ma yi tunanin Nihal will make it har yau
ba, kuma gaskiya Aunty jamila ta fada ita kanta tasan ta shiga depression tun kafin
rasuwan Abba, yanzu kuma duk gani take he died because of her, Aunty Jamila dai ta
juya ta shiga dakin Nihal, duke ta ganta jikin gado kasan dakin duk ta hada zufa,
Aunty Jamila ta nufeta da sauri tace "Lafiya Nihal?" Kasa ce mata komai tayi but
kana ganinta kasan she is in severe pain, Aunty Jamila ta buda ido a tsorace ganin
jini me yasa a kasa, da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Sai kuma ta
juya da sauri ta koma dakin Mumy hankali tashe ta sanar mata abinda ta gani, Mumy
da sauran sisters dinta da Aunt dinta suka nufi dakin Nihal din da sauri, Mumy na
kallon Aunty Jamila bayan ta dago Nihal tace "Kira min Khalil da sauri" Aunty
Jamila tayi saurin komawa parlor daukan wayarta, makale taga Nihad jikin kofa ta
kasa shiga dakin, Aunty Jamila tayi saurin kiran Khalil.... Karfe sha daya saura na
dare Aunty Jamila ta kira Mumy da ta kasa zaune ta kasa tsaye damuwa kala biyu a
ranta, hawayen ma yanzu babu sai kukan zuci, cikin sanyin murya Mumy tace "Ya ake
ciki Jamila? Ya jikin nata?" Aunty Jamila ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai
tace "Cikin jikinta ya zube, da kyar likitocin suka samo kanta wllh, yanzu Yaya sai
da Turai da kanwar Umma suka san yanda suka bi aka zubar da cikin nan ba tare da
sanin yarinyar ba, to alhaki a kansu wllh, ni dama da suka ce za su kai ta asibiti
dazu sai da na zargi hakan, amma duba da halin da yarinyar ke ciki ai babu wanda
zai kawo abinda za su kai ta su aikata kenan, ba ma ta lafiyanta suke ba, burinsu
kawai ciki ya zube kuma sun zubar sai suje su san abinda za su gaya ma Allah" Mumy
dai ta kasa cewa komai sai hawaye masu zafi ke sauka idonta, she wish basu zubar da
cikin ba ko ita zata rike koma me Nihal zata haifa, ta so anji wasiyyan Abba na
cewa kada wanda yace zai xubar da cikin tun ana saura kwana biyu zai bar duniya,
Aunty Jamila ta sauke ajiyar zuciya tace "Shikenan yaya sai gobe, amma da sassafe
ki ba ko Suwaiba
kayanta ta kawo mana asibiti da ruwan shayi" Cikin sanyin murya Mumy tace "Allah
ya kai mu, ki kula da ita don Allah Jamila" Daga haka ta katse wayar. Washegari da
safe Mami tayi lafiyayyen farfesun kaji ta dafa white rice zata kai ma Nihad ganin
da tayi ko abinci bata ci ko ya za ayi da ita kuwa, ta gama shiryawa Mimi ta kai
mata abincin compound ta saka a mota, Mami ta dau gyalenta da jaka zata fita
wayarta ya fara ring, bude jakar tayi ta ciro wayar ganin Hajiya Safeenah ce ke
kiranta ta daga suka gaisa, Hajiya Safeenah tace "Ya karin hakuri?" Mami tace "Mun
gode Allah" Hajiya Safeenah tace "Toh Allah ya gafarta masa" Mami tace "Ameen,
zuwan naki na nan kuwa?" Hajiya Safeenah tace "In sha Allahu, in dai na gama abinda
ya kai ni zan kiraki... Incase ma baxa mu hadu ba sai ki turo min address kawai in
karasa in masu gaisuwa" Mami tace "Toh ba damuwa, Allah ya tsare" Daga haka suka yi
sallama ta katse wayar, Mimi ta rakata har bakin mota, Noor tun jiya dama ta koma
da su Janar, Mami tace "Sai na dawo, kafin in dawo kuma you make sure our boxes are
ready don Flight dinmu na komawa Abuja karfe daya ne" Mimi tace "Toh Allah ya kai
mu, ki gaida Nihad" Mami tace "In sha Allah" Daga haka Mimi ta juya ta koma cikin
gidan. Mumy na bedroom dinta tare da Inna dake rusa kuka kamar ranta zai fita tace
"Har hakura nayi na kai zuciyata nesa fa na bari aka yi uku Maryam, hakan da nayi
ban kyauta ba kenan?? idan ina ganin matan nan a gidan nan kin san me nake ji a
zuciyata kuwa? Wallahi kallon warce ta kashe min ɗa nake mata, akan me zaki dinga
bani hakuri haka Maryam? Kinsan zafin rasa ɗa kuwa? Har abada fa bazan sake ganinsa
ba ya tafi kenan" sai ta kuma rushewa da matsanancin kuka tace "Allah Ubangiji yayi
maka rahama Ibrahim, Halinka na gari ya bi ka, tun da muke bai taɓa saɓa min ba,
kullum cikin yi min biyayya da kyautata min yake, idan ma ya taɓa min laifi na yafe
masa duniya da lahira, Allah yayi masa Rahama, Allah Ubangiji ya basa sa'a" Mumy
dake zaune gefen gado ita ma hawayen kawai take ta ma rasa me zata ce ma Inna, tun
dazu take kokarin ganar da ita rashin amfanin ce ma Umma sai ta bar gidan, Cike da
karfin hali tace "Albarkacin yaranta za ki duba Inna, ko don su Farooq kar kiyi
haka don girman Allah, har yanzu ba wai mutane sun san me ke faruwa bane, ba wanda
yasan abinda ya faru, kuma kinga akwai sauran yan uwa da abokan arziki da basu tafi
ba, idan kika ce sai ta bar gidan nan yau ai kinga za su so sanin abinda ke faruwa,
ki rufa mana asiri tunda Allah bai tona mana ba don Allah inna" Kuka Mumy take yi
sosai, Inna na shessheka tace "Maryam ganinta na daga min hankali ne, idan ba dai
zama zan yi a dakinki in ki fita har sai duk an gama watsewa ba sannan in sa ta
tattara komai nata ta bar gidan nan ita ma" Mumy na girgiza kai tace "Nace ki dubi
su farooq kar kiyi haka Inna, ki bar su su ji da daya" Inna tace "Da can bata duba
su Farooq din ba tayi duk abinda tayi, ni dai wallahi don kin hanani ne Maryam
banda haka Sumayya bazata kwana a gidan nan nima in kwana ba yau" Mumy bata sake
cewa komai ba tana share hawayen da yaki yanke mata yau kwana hudu kenan, a kwanaki
hudun nan ba karamin rama tayi ba, kana ganinta kasan karfin hali kawai take amma
tana cikin tashin hankali da shock, Inna dake kallonta tana shesshekan kuka tace
"Ki daure ko ɗan ruwan shayi ne ki dinga sha Maryam, kar kije wani ciwon ya kama ki
kuma" Mumy dai bata ce komai ba, Aunty Jamila ta shigo dakin da sallama tana kallon
Mumy tace "Kawu Salisu sun iso Yaya" Mumy ta kalleta tana share hawayen idonta,
jikin Aunty Jamila yayi sanyi, bata son ganin yayartata a haka, hankalinta tashi
yake sosai, Karasowa cikin dakin tayi cikin sanyin murya tace "Plss i need u to be
strong Aunty, i know it's hard, it's painful but for the sake of ur little kids be
strong plss" Lokaci daya ita ma ta fara hawayen, Mumy dai ta rike kanta bata ce
komai ba hawaye na sauka idonta, Inna kuwa na can ta fada duniyar tunaninta tana
hawayen ita ma, Aunty Jamila ta goge idonta tace "Na kai su can parlon tun da akwai
mutane a naki, ki taso yaya" Kai kawai Mumy ta gyada mata, Aunty Jamila ta mike ta
fita daga dakin, Mumy ta kalli Nihad dake bacci tun wayewar gari, tun bayan rasuwan
Abban nata sai yau tayi bacci na kusan awa uku, amma yanda take ganin rana haka
take ganin dare, yau din ma alluran bacci Khalil yayi mata bayan da ya kirata ta
samesa a mota a waje, Mumy na kallon Inna a hankali tace "Bari in je inna, yayan
babanmu ne ya zo" To kawai Inna tace mata, Mumy ta fita daga parlon tana tafiya a
hankali, Mami dake zaune parlon tare da Aunt din Mumy ta bi Mumy da kallo tace
"Amma da kin samu ko shayi ne ki sha Hajiya" Mumy tace "Ehh nayi baki ne yanzu zan
dawo sai in sha" Mami tace "Toh je ki dawo" Aunt din Mumy ta sauke ajiyar zuciya
tace "Bata cin abinci kwata kwata, wannan kadai ma ya isa ya sa mata ciwo ai" can
parlon Abba Mumy ta tafi don can Aunty jamila ta sauke baƙin, Dattijo ne sosai don
zai yi shekara 87, sai kuma wani wanda bazai wuce 58 ba, da wata mata dake tare da
su, sauran sisters din Mumy da suka sun shigo parlon yi masu sannu da zuwa su ma,
Mumy ta zauna saman Carpet tana kallon dattijon a hankali tace "Sannu da zuwa Kawu"
Cike da alhini Dattijon na Girgiza kai yace "Sannu Maryam, sannu, Allah ya baki
hakuri, ashe Ibrahim sa'i yayi, toh Allah ya gafarta masa yayi masa Rahama, Allah
ya kara maki hakuri" A hankali Mumy tace "Ameen kawu, fatan kun zo lafiya" Yace
"Lafiya lau, saukan mu kenan, tun jiya muka so zuwa Mubarak muka jira ya iso
Abujan" Aunty Jamila ta shigo parlon da tray din ruwa da lemo, wata kawar Mumy na
biye da ita da warmer din abinci da plates, ta ajiye masu, matar ta juya ta fita
bayan sun gaisa, Aunty Jamila ta nemi waje ita ma ta zauna tana kara masu sannu da
zuwa, mutumin dake gefen Dattijon yayi ma Mumy gaisuwa shi ma, haka ma matar dake
zaune a parlon, Mumy tace "Ameen, Allah ya bada lada" Dattijon na nuna mutumin dake
gefensa yace "Baku san wannan ba ko?" Duk suka dinga kallon Mutumin da ya nuna
masu, Dattijon yayi murmushi yace "Xumunci yayi wuya yanzu, yaran yanzu bakwa
zumunci wai ku yan boko, to ɗan uwanku ne Mubarak, shine ɗa na na biyu" Aunty
Suwaiba tace "Allah sarki, zumunci kam yayi wuya kawu, wai ɗan uwanmu amma da za mu
hadu a hanya sai dai ya wuce mu ce" Dattijon yace "Toh dai kuyi ma kanku fada,
shikenan don iyayenku sun rasu sai aka ce a yanke zumunci, to Allah ya ji kansu ya
gafarta masu" Duk suka amsa da "Ameen kawu, kai kuma Allah ya kara maka lafiya, in
sha Allah za a gyara" Ya nuna masu matar dake zaune yace "Wannan ma ba sai na bata
bakina ba nasan baku santa ba...." Duk dai suka yi shiru suna kallonta, yayi
murmushi yana girgiza kai yace "Babanku Ahmadu bai taɓa baku labarin Kawunku
Abudurrahman ba? Wanda ya rasu shekaru kusan 30 da suka wuce yanzu" Aunty Jamila
tace "Lahh kawu Abudurrahman din ne bamu sani ba Kawu? Kawai dai muna yara ne
lokacin" Yace "Toh er sa ce wannan...." Duk suka dinga kallonta, Mumy tace "Allah
sarki, sannu da zuwa Hajiya" tayi murmushi tace "Sannu, zumuncin ne yayi wuya
yanzu, gashi duk bamu san juna ba...." Alhaji Mubarak yace "Kun ga cousin dinku ce
ta kut da kut amma duk ba a san juna ba" Aunty Jamila tace "Gaskiya kam, rayuwa
kenan, Allah ya ji kan kawu Abudurrahman, tunda Allah ya hada mu yau in sha Allah
za a ci gaba da zumunci yanda ya kamata, naji dadin haduwar mu da ita, muna da
labarinta amma bamu santa ba" Dattijon yace "Toh ga ta yau... Dama mu hudu ne kacal
gun iyayenmu duk kun sani, ni ne babbansu sai Abudurrahman Allah yayi masa gafara,
Sannan Ahmadu mahaifinku shi ma Allah ya ji kansa, Autarmu Asiya wajen haihuwar
fari ta rasu, Allah ya gafarta mata, to don haka ga yar uwarku ku ci gaba da
zumunci don Allah, dama Allah bai yi mu da yawa ba, kun ga ita kadai ce gare
Abudurrahman har ya koma ga mahaliccinsa, ni dama Mubarak ne sai Salaha da Asiya,
Ku kuma Maryam, Jamila, Suwaiba sannan Khadijah, ɗan autanku ya rasu, don haka
Allah ya ji kansu da rahama" Duk suka ce "Allah ya gafarta masu, kuma in sha Allah
za mu ci gaba da zumunci kawu...." Aunty Jamila ta mike tace "Mu je can parlon
Aunty" Ta mike Mumy ma ta mike duk suka fita parlon tare da bakuwar suka bar kawun
nasu da Mubarak su ci abinci, suka nufi bangaren Mumy.

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

*Ina kuke maabota kamshi? To Ku matso kusa, Albait Al Sahal sunzo muku da hadaddun
turarukan wuta na gida, ma jiki da kuma kaya. Akwai perfumed body oils masu dadin
kamshi da sanyaya zuciya. Akwai spritz Wanda Ko bakiyi turaren wuta ba ya i sheki
ga yana dadewa a wuri. Maza ku garzayo Albait Al sahal domin Ku Sami naku Cikin
sauqi domin yanxu suna sales komai ya sauqaqa. Duk wacca ta siya beyi mata ba ta
dawo dashi # we trust the quality of our products# contact me via WhatsApp
09084473900*💖 NIHAAD 💖

75

Tun da suka shigo parlon Mami ke kallon Hajiya Safeenah da mamaki, ko ba Hajiya
Safeenah bace take gani, ita ko Hajiya Safeenah bata ma lura da Mami ba har ta
zauna a parlon, Aunty Suwaiba ta fita dauko mata ruwa da abinci, Mami tayi karfin
halin cewa "Safeenah??" Hajiya Safeenah ta juya da sauri zuwa direction din da aka
kirata, buda baki tayi ita ma da mugun mamaki tana kallon Mami, Aunty Jamila tace
"Lahh ashe kun ma san juna" Mami tace "Wai dama nan gidan ne za ki zo gaisuwa?"
Hajiya Safeenah ta kasa cewa komai tsabar yanda mamaki ya cikata, Mami tayi er
dariya tace "Ikon Allah, what a coincidence..." Hajiya Safeenah tace "Lallai kam
ikon Allah" a hankali Mumy da ta zauna parlon tana kallonsu tace "Ashe kun san juna
kenan" Mami tace "Kawata ce sosai Safeenah" Mumy tace "Allah sarki, To maa sha
Allah" Babu wanda ya kara cewa komai a cikinsu, ko wacce da tunanin da take a
zuciya, can Mami ta kalli Mumy warce ita ma tayi nisa tunanin da ta fada tace
"Hajiya an kai maki kayan shayi daki, da kin daure kin je kin sha ko ba yawa, ki
daina zama ba cin abinci" cikin sanyin murya Mumy tace "Toh" Daga haka ta mike ta
wuce bedroom dinta, Aunty Jamila ta mike ta bi bayanta don hada mata Shayin, Mami
ta kalli Hajiya Safeenah tace "Toh ya hanya Hajiya?" Hajiya Safeenah ta sauke
ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, sai gashi mun hadu gidan rasuwar" Mami tace
"Wallahi kuwa, amma marigayin kika sani ko uwar gidan tasa?" Hajiya Safeenah tace
"Ita warce ta shiga ciki yanzu ita na zo ma gaisuwa" Cike da confusion Mami tace
"Warce ta shiga ciki? To ai ita ce uwar Nihad, amma kuma i don't understand, a ina
kika santa? And kin saba zuwa gidan nan kenan kuma baki san Nihad ba?" Hajiya
Safeenah ta kalli Mami ta kasa cewa komai da farko, can ta jinjina kai a hankali
tace "My late father and her late father have the same parent amma kuma bamu taɓa
sanin juna ba sai yau ta dalilin rasuwan mai gidanta na zo mata gaisuwa, ni dai
kinga tun bayan rasuwar mahaifina mahaifiyata ta koma kasar Yemen da ni, a can na
girma nayi karatu har nayi aure a can, i never had the privilege of knowing my
paternal relatives gaba dayansu sai babban yayansu wanda muka zo yanzu tare da shi,
shine ma ya kirani ya sanar min rasuwan nan yace min tunda ina Nigeria lallai in
shirya in je gaisuwa don er uwata ce ta kusa amma bamu san juna ba" Mami ta rike
haɓa cike da mamaki tana kallon Hajiya Safeenah, can a hankali tace "You mean
Nihad's mother is ur cousin??" Hajiya Safeenah dai sai kallon Mami take bata ce
komai ba, Mami tace "Ikon Allah" Throughout zaman nasu a parlor babu me cewa komai
cikinsu, Hajiya Safeenah ruwa kawai ta dauka ta sha a abincin da Aunty Suwaiba ta
kawo mata... Mumy ta daure ta sha shayin da Aunty Jamila ta hada mata shi ma don
Aunty Jamila ta tsareta ne a dakin, Nihad na zaune gefen gado ta tashi daga baccin
da take, Mumy ta juya ta kalleta, sai kuma ta hada mata shayin a cup din da ta sha
ta dauka ta mika mata tace "Ki sha, ki tafi parlor ku gaisa da bakuwa..." Nihad ta
amshi shayin ta ajiye kan bedside drawer, a hankali ta sauko daga saman gadon ta
nufi bandaki don wanke bakinta, Aunty Jamila tace "Ga abinci nan Maman Khalil ta
kawo maki, sai ki hada da shayin" To kawai Nihad tace ta shiga bandakin. Bata tadda
su Mumy da Aunty Jamila a dakin ba bayan ta fito, ta dau shayin amma ta kasa don
bata da appetite gaba daya, it's now completely dawning on her cewar da gaske ta
rasa beloved Abbanta har duniya ta nade, ta goge hawayen da ya taru idonta ta tashi
daga kan gadon ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fito parlon Mumy, a kan Hajiya
Safeenah ta fara sauke ido a parlon, ta sunkuyar da kanta ta karasa ta durkusa
saman Carpet tace "Ina wuni?" Cikin sanyin murya Hajiya Safeenah tace "Lafiya lau,
ya hakuri??" Nihad tace "Alhamdulillah" Hajiya Safeenah tace "Toh Allah ya ji kansa
ya gafarta masa" Nihad tace "Ameen" Mami dai sai kallon Nihad take, kamar yanda
Hajiya Safeenah ma ke kallonta, Aunty Jamila da Aunty Suwaiba sai wata frnd din
Mumy kadai ne a parlon, Mami tace "Kin ci abinci?" Nihad tace "Yanzu zan ci" Mami
tace "To tashi ki je ki ci" Ta shi tayi ta koma dakin ta kwanta gefen gado, bata
san sanda wani baccin ya sake dauketa ba alamar alluran bai gama sakinta ba. Karfe
biyu saura Mami ta bar gidan bayan an mayar da flight dinsu zuwa karfe uku, Hajiya
Safeenah kuwa dama sai gobe zata koma Abuja, Mami bata samu yin sallama da Nihad ba
don har ta bar gidan bacci take. Wajen karfe biyar Nihad ta fito kofar gida ta
dalilin kiranta da Khalil yayi ta wayar Aunty Jamila, tun da ta fito gate din yake
kallonta, tana tafiya a hankali ta karaso gun motarsa, ya bude mata front seat ta
shiga ta kulle motar, A hankali yace "When did u wake up?" Ba tare da ta kallesa ba
tace "30 minutes ago" Ya juyo da ita yana kallonta ita ma tana kallonsa, ya kama
hannunta murya can kasa yace "Nasan baki ci abinci ba ko?" Bata son yaga hawayen
idonta saboda alkawarin da tayi masa, ya tada motar ya bar layin, wani tsadadden
eatry ya kai ta, ya dau menu din wajen dake saman table bayan sun zauna ya mika
mata yace "Zabar mana abinda za mu ci, kiyi mana order" Ta ɗan kallesa, sai kuma
tace "Sai wa zai biya?" A hankali yace "Hajiyata" Murmushi kawai tayi, ya kira mata
server din wajen, ta nuna masa abubuwan da zai kawo masu, Khalil dai sai kallonta
yake har server din ya bar wajen, ta daga kai ta kallesa, ya kashe mata ido yace
"Naga abinci me tsada kika yi ordering hope aljihunki da nauyi?" Tace "Idan ma ba
nauyi u can wash dishes...." Murmurshi kawai yake bai ce mata komai ba, aka kawo
masu abincin cikin some minutes, haka ya dinga distracting dinta da zance suna cin
abincin, and he love the way she ate much, suna nan zaune Mami ta kirasa don tun
dazu ya kira yaji ko sun isa gida lafiya, bayan sun gaisa tace "Don Allah ka ɗan
dinga sa mata ido ta dinga cin abinci" Yace "Alright in sha Allah, ga ta nan ku
gaisa" Ya mika ma Nihad wayar, bayan ta gaida Mami tace "Kun isa gida lafiya" Mami
tace "Alhamdulillah, ki daure ki dinga cin abinci kin ji" Nihad tace "In sha Allah
zan ci Mami" Sallama suka yi ta mika masa wayar. Sai dab da magrib suka bar wajen
bayan ya biya bills din, yana parking dai dai kofar gida yace "Bari in shiga
Masallaci" Tace "Toh" Ta bude motar ta sauka ya dau ledan takeaway da suka yi ya
mika mata, ta amsa tace "Thank you" Ya sakar mata murmushi yace "You are welcome
love" Sauke idonta tayi ta juya ta nufi cikin gate, ya kashe motar ya sauka. Mamaki
ya cika Nihad ganin Hajiya Safeenah a parlon Mumy tare da Inna, ta gaishesu ta
shiga cikin daki tana kallon Mumy dake zaune tare da Aunty Jamila, sa mamaki tace
"Mumy bakuwar Mami bata tafi ba? Naga Mami ta tafi ita ai" A hankali Mumy tace "Ba
bakuwa bace, gwaggwonki ce, she is my sister...." Nihad ta dinga kallon Mumy cike
da confusion tace "I don't understand ur sister, frnd din Mami ce fa, she is also
staying in Abuja, and ta zo nan saboda Mami ne" Mumy bata sake cewa Nihad komai ba
don ko magana me tsayi bata so, Aunty Jamila tayi murmushi tace "She is our cousin
sister Nihad, ke may be kin santa a Abuja saboda Maman Khalil, mu kuma er uwarmu ce
ta kusa ma kuwa" Nihad ta karasa kusa da su kana ganinta kasan ta rikice sosai tace
"Ban gane ba Aunty" Aunty Jamila tace "Zauna ki ji yanda mu ke da ita" Nihad ta
zauna gefen gadon tana kallonta, nan Aunty Jamila tayi mata bayanin relationship
dinsu da Hajiya Safeenah, Nihad dinga kallonta babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa,
What?? Does it mean Nadeeyah second Cousin dinta ce kenan?? Duk a zuciyarta take
wannan tunanin, Da yake su Mumy basu san komai kan auren da Khalil zai yi ba shi
yasa basu fahimci abinda yasa Nihad ta daburce haka ba, Aunty Jamila tace "Ita ma
Maman khalil din yanda kika yi mamakin ganinta a gidan nan haka tayi, ke a
tunaninki saboda Maman Khalil ta zo gidan nan ko?" Nihad ta gyada mata kai a
hankali amma ta kasa cewa komai don she is speechless, Aunty Jamila tace "Toh ba
saboda ita bace, er uwarmu ce ta kusa sosai, kasancewar uwarta er yemen yasa bamu
taɓa saninta ba, don a can suke da zama bana jin sun jima da dawowa kasar nan"
Nihad dai ta ma rasa abinda zata ce masu, gaba daya jikinta yayi mugun sanyi, Aunty
Jamila tace "She said tana da yarinya kuma tare suke a Abuja, kin san yarinyar ko?"
Nihad ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Aunty Jamila tayi kasa da murya ganin
reaction din Nihad is weird tace "Ko dai wani abu ya taɓa hadaki da ita a Abujan
ne?" Nihad ta girgiza kai da sauri tace "Aa, kawai nayi mamaki ne" Mumy dai
kallonsu kawai take bata cewa komai don abinda ya dameta daban, Nihad ta mike ta
fita daga dakin still in shock, tana fitowa parlor suka hada ido da Hajiya Safeenah
warce ita ma tunani iri iri sun addabeta a zuciya tun bayan da ta san irin alaqarta
da Nihad, Nihad ta sunkuyar da kanta ta nufi kofa tana tafiya a hankali ta fita,
dakin Nihal ta shiga ta sameta tana bacci, zaunawa tayi gefen gadon dakin ta
jinginar da kanta a hankali jikin gadon. Washegari karfe goma Hajiya Safeenah ta
bar gidansu Nihad zuwa Abuja don ta kagu ta koma don ta hadu da Mami, kuma tun da
ta zo har ta koma bata hadu da khalil a gidan ba, infact bai ma san ta zo ba don ba
a gidan yake kwana ba. A kwana a tashi har Abba ya cika kwana ashirin da tara da
rasuwa, zuwa lokacin kuma duk Allah ya sa ma family dinsa wani dangana na daban,
sun amshi kaddaran rasa shi hannu bibbiyu, yan uwa da suka zo daga garurruka daban
daban duk sun koma garinsu, gidan ya rage daga su sai su kawai, sai Inna da har
sannan taki komawa gidan babban ɗan ta wanda kullum da daddare shi ma zai zo gidan
shi ma, Aunty Jamila ma dai bata koma ba tana wajen yayarta sauran kannin Mumy ne
suka koma gidajensu, Har a lokacin Umma na gidan amma zaman daki kawai take, ko nan
da parlonta bata lekowa, a ko da yaushe ka shiga dakin nata zaka ganta zaune at the
very far end a kan darduma da carbi a hannunta, Kamila kuwa kamar kar Abba ya rasu
ta dawo hankalinta duk sabbin halayen da ta tsiro
ta daina tunda dama ba bin jikinta yayi ba, Nihal ce kadai har yanzu bata daina
kukan Abbanta ba safe, rana, da dare, ita kadai ce taki hakura, kullum zaka ganta
babu walwala sai kuka, gwara Nihad ita cikin dare take nata kukan, duk don Nihal ta
kwantar da hankalinta Mumy har cewa tayi Abba ya bar mata wasiyyan ya yafe mata
duniya da lahira kawai Allah bai yi za su gana bane, amma Nihal taki yarda da
hakan, ga Umma ko magana bata son mata a gidan, su ya farooq ma sama sama suke
kulata, sai tayi kwana da kwanaki bata ga yayyin nata ba tunda yanzu dakin Mumy ta
dawo gaba daya take Rayuwarta, result din su na final exams ma da ya fito sai da ta
samu spill a almost duk courses din da ta dauka a semester din, ita da ko carry
over bata taɓa samu ba a makarantar, wajen Mumy da Aunty Jamila kadai take samun
relief a gidan, sae Nihad dake jan ta jiki ynzu, Aunty Maryam ta kira Mumy tun
sanda aka yi rasuwan yayi sau hudu yanzu, kuma duk sanda ta kira zata sa Mumy ta ba
Nihad su gaisa. Mumy ce zaune kan darduma da Hijab dinta har kasa hannunta rike da
carbi, Aunty Jamila da Nihad ma suna dakin sai Nihal dake kwance idonta a rufe
amma ba bacci take ba, Mumy ta kalli Aunty Jamila cikin sanyin murya tace "Ya
kamata kuma ta tattara haka ta bi mijinta su tafi gida ko Jamila?" Nihad ta daga
kai ta kalli Mumy da sauri sanin da ita take, Aunty Jamila tace "Gaskiya kam, tunda
anyi sati hudu har da kwana biyu yau, kuma nasan saboda ita ne ma bai bar garin nan
ba har yanzu, kar rashin hankalin namu yayi yawa" Nihad ta marairaice tace "Mumy ba
sai anyi 40 days ba?" Mumy ta ɗan kalleta tace "Me za kiyi har 40 days a nan din?"
Aunty Jamila tace "A duk inda kike kika ma Abbanki addu'a zai samesa ba sai lallai
gidan nan ba Nihad, kinga Allah ya baki miji wanda ba ko wace mace ke samun irinsa
ba a rayuwar nan, uwa uba ga danginsa mutanen kirki mutanen arziki, duk da
matsayinsu amma kowa nasu ne babu girman kai ba komai, to kada mu zama kananun
mutane mu yi ta ajiyeki a nan, gashi yau har sati hudu, don haka ki shirya gobe ya
daukeki ku koma..." Nihad ta dinga kallonsu har hawaye ya cika idonta, tsoronta kar
ta koma Abuja damuwar rasuwan Abbanta ya dawo mata sabo, don idan tana ganin Mumy
da yan uwanta tana jin relieve sosai, Ta goge hawayen idonta cikin sanyin murya
tace "Then can i go together with Nihal?" Aunty Jamila tace "Sai abinda mijinki
yace" Nihal ta buda ido tana kallonta, a hankali tace "I will come but not now"
Nihad bata sake cewa komai ba, haka Aunty Jamila ta sata gaba ta fara hada kayanta
a akwati, Usman yayi sallama kofar dakin, Mumy da Aunty Jamila suka amsa masa ya
shiga, bayan ya gaishesu yace "Mumy dama na shigo in gaya maki Abban Khalil ya
samar min aiki a Nnpc na garin kaduna" Mumy da Aunty Jamila suka hada baki wajen
cewa "Alhamdulillah" sosai suka taya sa murna, Mumy tayi masa addu'a sosai tayi
masa fatan alkhairi, Yace "Nagode Mumy, Allah ya kara girma" Mumy tace "Yaushe zaka
yi resuming aikin kenan?" Yace "Gobe lahadi za mu tafi kadunan tare da Farooq don
shi ma zai koma aiki, on monday in sha Allah zan fara aikin" Mumy tace "Toh Allah
ya bada sa'a, Allah ya tsare" yace "Ameen" Daga haka ya mike ya fita daga dakin,
Aunty Jamila tace "Allah sarki, na taya sa murna sosai, Allah ya saka ma General da
alkhairi" Tun da aka tura ma Usman offer din yaje ya nuna ma Umma a dakinta, ko
gani bata yi ba bayan ta masa addu'a ta tasa ya je ya nuna ma Mumy a bangarenta.
Aunty Jamila da Nihal na zaune parlon Mumy suna kallon wani movie Khalil ya kirata,
ta daga wayar bayan ya gaisheta yace "Aunty dama zan zo da wani bako ne yanzu zai
ma Mumy gaisuwa" Aunty Jamila tace "Toh sai kun zo" Nihad na can daki tare da Mumy
da tun yanzu har ta fara mata nasiha ta yi hkuri ta zauna lafiya da mijinta kar ta
basu kunya, gaba daya sun sa ta hada kayanta duk da dai basu ce ma khalil din gobe
ya dauketa su tafi ba, tana son gaya ma Mumy auren da zai yi amma ta kasa don
that's her only nightmare ynzu, Aunty Jamila ta shigo dakin tace "Yaya ki fito za a
maki gaisuwa" Mumy tace "Toh" daga haka ta mike ta nufi kofa, Nihad ta bi ta da
kallo, lokaci daya hawaye ya cika Idonta, Mumy na shigowa parlon ta zauna tana
kallon balaraben dake zaune, ya gaisheta da turanci ta amsa da fara'a, nan yayi
mata gaisuwa, ya kuma yi ma Abba addu'a sosai, cikin sanyin murya tace "Ameen,
thank you very much" Khalil ya gaida Mumy don duk ranan bai shigo gidan ba, Aunty
Jamila ta tafi main parlor dauko ma baƙon ruwa don in dai Nihal ce ba tashi zata yi
ba in ka bibiya ma hankalinta baya tare da ita, don a ko da yaushe zaka sameta
absentminded barin idan ana kallo, Baƙon ya daga kai yana kallonta yace "Hi Nihad,
i am so sorry for ur lost, may Allah SWT grant him aljannatul firdauss" Khalil ya
ɗan yi murmushi ya kallesa da turanci yace masa ba Nihad bace sister dinta ce, Mumy
ta tabo Nihal da bata ma san ana mata magana ba, Da sauri ta dawo duniyar tunanin
da ta tafi, Khalil yace "Yana maki gaisuwa...." Ta kallesa duk da bata san abinda
yace ba tace "Ameen nagode" Nihad ta fito daki don sarai ta dau muryarsa, ya daga
kai yana kallonta bayan ta fito, tana Murmushi tace "Hi Ayman" Da Fara'a ya amsa
mata, ta karaso ta zauna a parlon, nan suka gaisa yayi mata gaisuwa ta amsa ta masa
godiya, yana nuna mata Nihal da mamaki yace "The resemblance is obvious, just
complexion difference" Tana Murmushi tace "Yeah, she is my blood, her name is
Nihal" Ya sake kallon Nihal yace "Nihal" Nihal ta kirkiri murmushi bata ce komai ba
Yace "It's nyc meeting with you Nihal" Ta gyada masa kai kawai, don bata son magana
yanzu, Ayman bai wani dade a parlon ba, bayan ya sha ruwan da Aunty Jamila ta ajiye
masa, yayi ma Mumy sallama ya ajiye mata dollar dari biyar, Mumy da Aunty Jamila
suka yi masa godiya sosai, ya fita parlon tare da Khalil, Mumy na kallon Nihad da
mamaki ganin yawan kudin da ya ajiye mata tace "Who is he?" Nihad tayi murmurshi
tace "Sister din Mami namesake dinki ce ta hadani da shi farkon zuwana Abuja" Aunty
Jamila ta buda baki tace "Lokacin basu san da aurenki da khalil ba?" Dariya kawai
Nihad tayi bata ce komai ba, Aunty Jamila tace "Ikon Allah, to dama yasan khalil
din ne?" Ta girgiza kai tace "Kilan sai daga baya, nasan Aunty Maryam ce zata gaya
masa Abbana ya rasu shine zai ce zai zo gaisuwa, dama dai yana shigowa Nigeria but
a Uk yake zama" Mumy tace "Allah sarki, Allah ya saka da Alkhairi, Allah ya bashi
lada" Khalil bai dawo gidan ba sai dare, nan Aunty Jamila ta sanar masa gobe ya dau
Nihad su tafi gida, ya dai yi shiru bai ce komai ba, komawa daki tayi wajen er
uwarta, Khalil ya kalli Nihal dake juya abincin gabanta a parlon, yace "Ina wayarki
Nihal?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tace "Yana dakina" Yace "A kunne yake?" Ta
girgiza masa kai don for more than a month now bata kunna wayarta ba, Yace "Ki
kunna za a kiraki....." Ta dai yi shiru tana kallonsa, yace "Kin ji?" Ta gyada masa
kai kawai, Nihad ta shigo parlon rike da abinci ta kawo masa, ta ajiye gabansa ta
zauna tana facing dinsa sannan ta dau plate tana debar masa abincin, shi dai
kallonta kawai yake babu ko kiftawa, Nihal ta mike ta dau abincinta ta shiga dakin
Mumy, a hankali Nihad tace "Should i add more?" Yayi kasa da murya yace "I want to
feed on u, not rice and stew"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

Ina kuke maabota kamshi? To Ku matso kusa, Albait Al Sahal sunzo muku da hadaddun
turarukan wuta na gida, ma jiki da kuma kaya. Akwai perfumed body oils masu dadin
kamshi da sanyaya zuciya. Akwai spritz Wanda Ko bakiyi turaren wuta ba ya i sheki
ga yana dadewa a wuri. Maza ku garzayo Albait Al sahal domin Ku Sami naku Cikin
sauqi domin yanxu suna sales komai ya sauqaqa. Duk wacca ta siya beyi mata ba ta
dawo dashi # we trust the quality of our products# contact me via WhatsApp
09084473900💖 NIHAAD 💖

75

Tun da suka shigo parlon Mami ke kallon Hajiya Safeenah da mamaki, ko ba Hajiya
Safeenah bace take gani, ita ko Hajiya Safeenah bata ma lura da Mami ba har ta
zauna a parlon, Aunty Suwaiba ta fita dauko mata ruwa da abinci, Mami tayi karfin
halin cewa "Safeenah??" Hajiya Safeenah ta juya da sauri zuwa direction din da aka
kirata, buda baki tayi ita ma da mugun mamaki tana kallon Mami, Aunty Jamila tace
"Lahh ashe kun ma san juna" Mami tace "Wai dama nan gidan ne za ki zo gaisuwa?"
Hajiya Safeenah ta kasa cewa komai tsabar yanda mamaki ya cikata, Mami tayi er
dariya tace "Ikon Allah, what a coincidence..." Hajiya Safeenah tace "Lallai kam
ikon Allah" a hankali Mumy da ta zauna parlon tana kallonsu tace "Ashe kun san juna
kenan" Mami tace "Kawata ce sosai Safeenah" Mumy tace "Allah sarki, To maa sha
Allah" Babu wanda ya kara cewa komai a cikinsu, ko wacce da tunanin da take a
zuciya, can Mami ta kalli Mumy warce ita ma tayi nisa tunanin da ta fada tace
"Hajiya an kai maki kayan shayi daki, da kin daure kin je kin sha ko ba yawa, ki
daina zama ba cin abinci" cikin sanyin murya Mumy tace "Toh" Daga haka ta mike ta
wuce bedroom dinta, Aunty Jamila ta mike ta bi bayanta don hada mata Shayin, Mami
ta kalli Hajiya Safeenah tace "Toh ya hanya Hajiya?" Hajiya Safeenah ta sauke
ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, sai gashi mun hadu gidan rasuwar" Mami tace
"Wallahi kuwa, amma marigayin kika sani ko uwar gidan tasa?" Hajiya Safeenah tace
"Ita warce ta shiga ciki yanzu ita na zo ma gaisuwa" Cike da confusion Mami tace
"Warce ta shiga ciki? To ai ita ce uwar Nihad, amma kuma i don't understand, a ina
kika santa? And kin saba zuwa gidan nan kenan kuma baki san Nihad ba?" Hajiya
Safeenah ta kalli Mami ta kasa cewa komai da farko, can ta jinjina kai a hankali
tace "My late father and her late father have the same parent amma kuma bamu taɓa
sanin juna ba sai yau ta dalilin rasuwan mai gidanta na zo mata gaisuwa, ni dai
kinga tun bayan rasuwar mahaifina mahaifiyata ta koma kasar Yemen da ni, a can na
girma nayi karatu har nayi aure a can, i never had the privilege of knowing my
paternal relatives gaba dayansu sai babban yayansu wanda muka zo yanzu tare da shi,
shine ma ya kirani ya sanar min rasuwan nan yace min tunda ina Nigeria lallai in
shirya in je gaisuwa don er uwata ce ta kusa amma bamu san juna ba" Mami ta rike
haɓa cike da mamaki tana kallon Hajiya Safeenah, can a hankali tace "You mean
Nihad's mother is ur cousin??" Hajiya Safeenah dai sai kallon Mami take bata ce
komai ba, Mami tace "Ikon Allah" Throughout zaman nasu a parlor babu me cewa komai
cikinsu, Hajiya Safeenah ruwa kawai ta dauka ta sha a abincin da Aunty Suwaiba ta
kawo mata... Mumy ta daure ta sha shayin da Aunty Jamila ta hada mata shi ma don
Aunty Jamila ta tsareta ne a dakin, Nihad na zaune gefen gado ta tashi daga baccin
da take, Mumy ta juya ta kalleta, sai kuma ta hada mata shayin a cup din da ta sha
ta dauka ta mika mata tace "Ki sha, ki tafi parlor ku gaisa da bakuwa..." Nihad ta
amshi shayin ta ajiye kan bedside drawer, a hankali ta sauko daga saman gadon ta
nufi bandaki don wanke bakinta, Aunty Jamila tace "Ga abinci nan Maman Khalil ta
kawo maki, sai ki hada da shayin" To kawai Nihad tace ta shiga bandakin. Bata tadda
su Mumy da Aunty Jamila a dakin ba bayan ta fito, ta dau shayin amma ta kasa don
bata da appetite gaba daya, it's now completely dawning on her cewar da gaske ta
rasa beloved Abbanta har duniya ta nade, ta goge hawayen da ya taru idonta ta tashi
daga kan gadon ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fito parlon Mumy, a kan Hajiya
Safeenah ta fara sauke ido a parlon, ta sunkuyar da kanta ta karasa ta durkusa
saman Carpet tace "Ina wuni?" Cikin sanyin murya Hajiya Safeenah tace "Lafiya lau,
ya hakuri??" Nihad tace "Alhamdulillah" Hajiya Safeenah tace "Toh Allah ya ji kansa
ya gafarta masa" Nihad tace "Ameen" Mami dai sai kallon Nihad take, kamar yanda
Hajiya Safeenah ma ke kallonta, Aunty Jamila da Aunty Suwaiba sai wata frnd din
Mumy kadai ne a parlon, Mami tace "Kin ci abinci?" Nihad tace "Yanzu zan ci" Mami
tace "To tashi ki je ki ci" Ta shi tayi ta koma dakin ta kwanta gefen gado, bata
san sanda wani baccin ya sake dauketa ba alamar alluran bai gama sakinta ba. Karfe
biyu saura Mami ta bar gidan bayan an mayar da flight dinsu zuwa karfe uku, Hajiya
Safeenah kuwa dama sai gobe zata koma Abuja, Mami bata samu yin sallama da Nihad ba
don har ta bar gidan bacci take. Wajen karfe biyar Nihad ta fito kofar gida ta
dalilin kiranta da Khalil yayi ta wayar Aunty Jamila, tun da ta fito gate din yake
kallonta, tana tafiya a hankali ta karaso gun motarsa, ya bude mata front seat ta
shiga ta kulle motar, A hankali yace "When did u wake up?" Ba tare da ta kallesa ba
tace "30 minutes ago" Ya juyo da ita yana kallonta ita ma tana kallonsa, ya kama
hannunta murya can kasa yace "Nasan baki ci abinci ba ko?" Bata son yaga hawayen
idonta saboda alkawarin da tayi masa, ya tada motar ya bar layin, wani tsadadden
eatry ya kai ta, ya dau menu din wajen dake saman table bayan sun zauna ya mika
mata yace "Zabar mana abinda za mu ci, kiyi mana order" Ta ɗan kallesa, sai kuma
tace "Sai wa zai biya?" A hankali yace "Hajiyata" Murmushi kawai tayi, ya kira mata
server din wajen, ta nuna masa abubuwan da zai kawo masu, Khalil dai sai kallonta
yake har server din ya bar wajen, ta daga kai ta kallesa, ya kashe mata ido yace
"Naga abinci me tsada kika yi ordering hope aljihunki da nauyi?" Tace "Idan ma ba
nauyi u can wash dishes...." Murmurshi kawai yake bai ce mata komai ba, aka kawo
masu abincin cikin some minutes, haka ya dinga distracting dinta da zance suna cin
abincin, and he love the way she ate much, suna nan zaune Mami ta kirasa don tun
dazu ya kira yaji ko sun isa gida lafiya, bayan sun gaisa tace "Don Allah ka ɗan
dinga sa mata ido ta dinga cin abinci" Yace "Alright in sha Allah, ga ta nan ku
gaisa" Ya mika ma Nihad wayar, bayan ta gaida Mami tace "Kun isa gida lafiya" Mami
tace "Alhamdulillah, ki daure ki dinga cin abinci kin ji" Nihad tace "In sha Allah
zan ci Mami" Sallama suka yi ta mika masa wayar. Sai dab da magrib suka bar wajen
bayan ya biya bills din, yana parking dai dai kofar gida yace "Bari in shiga
Masallaci" Tace "Toh" Ta bude motar ta sauka ya dau ledan takeaway da suka yi ya
mika mata, ta amsa tace "Thank you" Ya sakar mata murmushi yace "You are welcome
love" Sauke idonta tayi ta juya ta nufi cikin gate, ya kashe motar ya sauka. Mamaki
ya cika Nihad ganin Hajiya Safeenah a parlon Mumy tare da Inna, ta gaishesu ta
shiga cikin daki tana kallon Mumy dake zaune tare da Aunty Jamila, sa mamaki tace
"Mumy bakuwar Mami bata tafi ba? Naga Mami ta tafi ita ai" A hankali Mumy tace "Ba
bakuwa bace, gwaggwonki ce, she is my sister...." Nihad ta dinga kallon Mumy cike
da confusion tace "I don't understand ur sister, frnd din Mami ce fa, she is also
staying in Abuja, and ta zo nan saboda Mami ne" Mumy bata sake cewa Nihad komai ba
don ko magana me tsayi bata so, Aunty Jamila tayi murmushi tace "She is our cousin
sister Nihad, ke may be kin santa a Abuja saboda Maman Khalil, mu kuma er uwarmu ce
ta kusa ma kuwa" Nihad ta karasa kusa da su kana ganinta kasan ta rikice sosai tace
"Ban gane ba Aunty" Aunty Jamila tace "Zauna ki ji yanda mu ke da ita" Nihad ta
zauna gefen gadon tana kallonta, nan Aunty Jamila tayi mata bayanin relationship
dinsu da Hajiya Safeenah, Nihad dinga kallonta babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa,
What?? Does it mean Nadeeyah second Cousin dinta ce kenan?? Duk a zuciyarta take
wannan tunanin, Da yake su Mumy basu san komai kan auren da Khalil zai yi ba shi
yasa basu fahimci abinda yasa Nihad ta daburce haka ba, Aunty Jamila tace "Ita ma
Maman khalil din yanda kika yi mamakin ganinta a gidan nan haka tayi, ke a
tunaninki saboda Maman Khalil ta zo gidan nan ko?" Nihad ta gyada mata kai a
hankali amma ta kasa cewa komai don she is speechless, Aunty Jamila tace "Toh ba
saboda ita bace, er uwarmu ce ta kusa sosai, kasancewar uwarta er yemen yasa bamu
taɓa saninta ba, don a can suke da zama bana jin sun jima da dawowa kasar nan"
Nihad dai ta ma rasa abinda zata ce masu, gaba daya jikinta yayi mugun sanyi, Aunty
Jamila tace "She said tana da yarinya kuma tare suke a Abuja, kin san yarinyar ko?"
Nihad ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Aunty Jamila tayi kasa da murya ganin
reaction din Nihad is weird tace "Ko dai wani abu ya taɓa hadaki da ita a Abujan
ne?" Nihad ta girgiza kai da sauri tace "Aa, kawai nayi mamaki ne" Mumy dai
kallonsu kawai take bata cewa komai don abinda ya dameta daban, Nihad ta mike ta
fita daga dakin still in shock, tana fitowa parlor suka hada ido da Hajiya Safeenah
warce ita ma tunani iri iri sun addabeta a zuciya tun bayan da ta san irin alaqarta
da Nihad, Nihad ta sunkuyar da kanta ta nufi kofa tana tafiya a hankali ta fita,
dakin Nihal ta shiga ta sameta tana bacci, zaunawa tayi gefen gadon dakin ta
jinginar da kanta a hankali jikin gadon. Washegari karfe goma Hajiya Safeenah ta
bar gidansu Nihad zuwa Abuja don ta kagu ta koma don ta hadu da Mami, kuma tun da
ta zo har ta koma bata hadu da khalil a gidan ba, infact bai ma san ta zo ba don ba
a gidan yake kwana ba. A kwana a tashi har Abba ya cika kwana ashirin da tara da
rasuwa, zuwa lokacin kuma duk Allah ya sa ma family dinsa wani dangana na daban,
sun amshi kaddaran rasa shi hannu bibbiyu, yan uwa da suka zo daga garurruka daban
daban duk sun koma garinsu, gidan ya rage daga su sai su kawai, sai Inna da har
sannan taki komawa gidan babban ɗan ta wanda kullum da daddare shi ma zai zo gidan
shi ma, Aunty Jamila ma dai bata koma ba tana wajen yayarta sauran kannin Mumy ne
suka koma gidajensu, Har a lokacin Umma na gidan amma zaman daki kawai take, ko nan
da parlonta bata lekowa, a ko da yaushe ka shiga dakin nata zaka ganta zaune at the
very far end a kan darduma da carbi a hannunta, Kamila kuwa kamar kar Abba ya rasu
ta dawo hankalinta duk sabbin halayen da ta tsiro
ta daina tunda dama ba bin jikinta yayi ba, Nihal ce kadai har yanzu bata daina
kukan Abbanta ba safe, rana, da dare, ita kadai ce taki hakura, kullum zaka ganta
babu walwala sai kuka, gwara Nihad ita cikin dare take nata kukan, duk don Nihal ta
kwantar da hankalinta Mumy har cewa tayi Abba ya bar mata wasiyyan ya yafe mata
duniya da lahira kawai Allah bai yi za su gana bane, amma Nihal taki yarda da
hakan, ga Umma ko magana bata son mata a gidan, su ya farooq ma sama sama suke
kulata, sai tayi kwana da kwanaki bata ga yayyin nata ba tunda yanzu dakin Mumy ta
dawo gaba daya take Rayuwarta, result din su na final exams ma da ya fito sai da ta
samu spill a almost duk courses din da ta dauka a semester din, ita da ko carry
over bata taɓa samu ba a makarantar, wajen Mumy da Aunty Jamila kadai take samun
relief a gidan, sae Nihad dake jan ta jiki ynzu, Aunty Maryam ta kira Mumy tun
sanda aka yi rasuwan yayi sau hudu yanzu, kuma duk sanda ta kira zata sa Mumy ta ba
Nihad su gaisa. Mumy ce zaune kan darduma da Hijab dinta har kasa hannunta rike da
carbi, Aunty Jamila da Nihad ma suna dakin sai Nihal dake kwance idonta a rufe
amma ba bacci take ba, Mumy ta kalli Aunty Jamila cikin sanyin murya tace "Ya
kamata kuma ta tattara haka ta bi mijinta su tafi gida ko Jamila?" Nihad ta daga
kai ta kalli Mumy da sauri sanin da ita take, Aunty Jamila tace "Gaskiya kam, tunda
anyi sati hudu har da kwana biyu yau, kuma nasan saboda ita ne ma bai bar garin nan
ba har yanzu, kar rashin hankalin namu yayi yawa" Nihad ta marairaice tace "Mumy ba
sai anyi 40 days ba?" Mumy ta ɗan kalleta tace "Me za kiyi har 40 days a nan din?"
Aunty Jamila tace "A duk inda kike kika ma Abbanki addu'a zai samesa ba sai lallai
gidan nan ba Nihad, kinga Allah ya baki miji wanda ba ko wace mace ke samun irinsa
ba a rayuwar nan, uwa uba ga danginsa mutanen kirki mutanen arziki, duk da
matsayinsu amma kowa nasu ne babu girman kai ba komai, to kada mu zama kananun
mutane mu yi ta ajiyeki a nan, gashi yau har sati hudu, don haka ki shirya gobe ya
daukeki ku koma..." Nihad ta dinga kallonsu har hawaye ya cika idonta, tsoronta kar
ta koma Abuja damuwar rasuwan Abbanta ya dawo mata sabo, don idan tana ganin Mumy
da yan uwanta tana jin relieve sosai, Ta goge hawayen idonta cikin sanyin murya
tace "Then can i go together with Nihal?" Aunty Jamila tace "Sai abinda mijinki
yace" Nihal ta buda ido tana kallonta, a hankali tace "I will come but not now"
Nihad bata sake cewa komai ba, haka Aunty Jamila ta sata gaba ta fara hada kayanta
a akwati, Usman yayi sallama kofar dakin, Mumy da Aunty Jamila suka amsa masa ya
shiga, bayan ya gaishesu yace "Mumy dama na shigo in gaya maki Abban Khalil ya
samar min aiki a Nnpc na garin kaduna" Mumy da Aunty Jamila suka hada baki wajen
cewa "Alhamdulillah" sosai suka taya sa murna, Mumy tayi masa addu'a sosai tayi
masa fatan alkhairi, Yace "Nagode Mumy, Allah ya kara girma" Mumy tace "Yaushe zaka
yi resuming aikin kenan?" Yace "Gobe lahadi za mu tafi kadunan tare da Farooq don
shi ma zai koma aiki, on monday in sha Allah zan fara aikin" Mumy tace "Toh Allah
ya bada sa'a, Allah ya tsare" yace "Ameen" Daga haka ya mike ya fita daga dakin,
Aunty Jamila tace "Allah sarki, na taya sa murna sosai, Allah ya saka ma General da
alkhairi" Tun da aka tura ma Usman offer din yaje ya nuna ma Umma a dakinta, ko
gani bata yi ba bayan ta masa addu'a ta tasa ya je ya nuna ma Mumy a bangarenta.
Aunty Jamila da Nihal na zaune parlon Mumy suna kallon wani movie Khalil ya kirata,
ta daga wayar bayan ya gaisheta yace "Aunty dama zan zo da wani bako ne yanzu zai
ma Mumy gaisuwa" Aunty Jamila tace "Toh sai kun zo" Nihad na can daki tare da Mumy
da tun yanzu har ta fara mata nasiha ta yi hkuri ta zauna lafiya da mijinta kar ta
basu kunya, gaba daya sun sa ta hada kayanta duk da dai basu ce ma khalil din gobe
ya dauketa su tafi ba, tana son gaya ma Mumy auren da zai yi amma ta kasa don
that's her only nightmare ynzu, Aunty Jamila ta shigo dakin tace "Yaya ki fito za a
maki gaisuwa" Mumy tace "Toh" daga haka ta mike ta nufi kofa, Nihad ta bi ta da
kallo, lokaci daya hawaye ya cika Idonta, Mumy na shigowa parlon ta zauna tana
kallon balaraben dake zaune, ya gaisheta da turanci ta amsa da fara'a, nan yayi
mata gaisuwa, ya kuma yi ma Abba addu'a sosai, cikin sanyin murya tace "Ameen,
thank you very much" Khalil ya gaida Mumy don duk ranan bai shigo gidan ba, Aunty
Jamila ta tafi main parlor dauko ma baƙon ruwa don in dai Nihal ce ba tashi zata yi
ba in ka bibiya ma hankalinta baya tare da ita, don a ko da yaushe zaka sameta
absentminded barin idan ana kallo, Baƙon ya daga kai yana kallonta yace "Hi Nihad,
i am so sorry for ur lost, may Allah SWT grant him aljannatul firdauss" Khalil ya
ɗan yi murmushi ya kallesa da turanci yace masa ba Nihad bace sister dinta ce, Mumy
ta tabo Nihal da bata ma san ana mata magana ba, Da sauri ta dawo duniyar tunanin
da ta tafi, Khalil yace "Yana maki gaisuwa...." Ta kallesa duk da bata san abinda
yace ba tace "Ameen nagode" Nihad ta fito daki don sarai ta dau muryarsa, ya daga
kai yana kallonta bayan ta fito, tana Murmushi tace "Hi Ayman" Da Fara'a ya amsa
mata, ta karaso ta zauna a parlon, nan suka gaisa yayi mata gaisuwa ta amsa ta masa
godiya, yana nuna mata Nihal da mamaki yace "The resemblance is obvious, just
complexion difference" Tana Murmushi tace "Yeah, she is my blood, her name is
Nihal" Ya sake kallon Nihal yace "Nihal" Nihal ta kirkiri murmushi bata ce komai ba
Yace "It's nyc meeting with you Nihal" Ta gyada masa kai kawai, don bata son magana
yanzu, Ayman bai wani dade a parlon ba, bayan ya sha ruwan da Aunty Jamila ta ajiye
masa, yayi ma Mumy sallama ya ajiye mata dollar dari biyar, Mumy da Aunty Jamila
suka yi masa godiya sosai, ya fita parlon tare da Khalil, Mumy na kallon Nihad da
mamaki ganin yawan kudin da ya ajiye mata tace "Who is he?" Nihad tayi murmurshi
tace "Sister din Mami namesake dinki ce ta hadani da shi farkon zuwana Abuja" Aunty
Jamila ta buda baki tace "Lokacin basu san da aurenki da khalil ba?" Dariya kawai
Nihad tayi bata ce komai ba, Aunty Jamila tace "Ikon Allah, to dama yasan khalil
din ne?" Ta girgiza kai tace "Kilan sai daga baya, nasan Aunty Maryam ce zata gaya
masa Abbana ya rasu shine zai ce zai zo gaisuwa, dama dai yana shigowa Nigeria but
a Uk yake zama" Mumy tace "Allah sarki, Allah ya saka da Alkhairi, Allah ya bashi
lada" Khalil bai dawo gidan ba sai dare, nan Aunty Jamila ta sanar masa gobe ya dau
Nihad su tafi gida, ya dai yi shiru bai ce komai ba, komawa daki tayi wajen er
uwarta, Khalil ya kalli Nihal dake juya abincin gabanta a parlon, yace "Ina wayarki
Nihal?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tace "Yana dakina" Yace "A kunne yake?" Ta
girgiza masa kai don for more than a month now bata kunna wayarta ba, Yace "Ki
kunna za a kiraki....." Ta dai yi shiru tana kallonsa, yace "Kin ji?" Ta gyada masa
kai kawai, Nihad ta shigo parlon rike da abinci ta kawo masa, ta ajiye gabansa ta
zauna tana facing dinsa sannan ta dau plate tana debar masa abincin, shi dai
kallonta kawai yake babu ko kiftawa, Nihal ta mike ta dau abincinta ta shiga dakin
Mumy, a hankali Nihad tace "Should i add more?" Yayi kasa da murya yace "I want to
feed on u, not rice and stew"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

Ina kuke maabota kamshi? To Ku matso kusa, Albait Al Sahal sunzo muku da hadaddun
turarukan wuta na gida, ma jiki da kuma kaya. Akwai perfumed body oils masu dadin
kamshi da sanyaya zuciya. Akwai spritz Wanda Ko bakiyi turaren wuta ba ya i sheki
ga yana dadewa a wuri. Maza ku garzayo Albait Al sahal domin Ku Sami naku Cikin
sauqi domin yanxu suna sales komai ya sauqaqa. Duk wacca ta siya beyi mata ba ta
dawo dashi # we trust the quality of our products# contact me via WhatsApp
09084473900💖 NIHAAD 💖

76

Nihad tayi murmurshi kawai ta sunkuyar da kanta bata ce masa komai ba ta kara masa
nama akan abincin da ta zuba, shi dai kallonta kawai yake kasa kasa, can yayi kasa
da murya yace "Baki ce komai ba...." Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa tana mika
masa abincin tace "Fara cin wannan" Dariya ta basa, a hankali yace "Are you
serious?" Ta gyada masa kai, ya amshi abincin ya fara ci, ta koma ta jingina da
kujeran ta kusa da inda yake zaune tana kallon tv dake aiki a parlon, lokaci lokaci
take satan kallonsa ta gefen ido sai taga shi ma kallonta yake, taji yayi kasa da
murya yace "When are we leaving tomorrow?" A hankali tace "Sanda kace" Yace "Da
safe?" Tace "Allah ya kai mu" Bai wani ci abincin da yawa ba ya ajiye ya dau ruwa,
ta daga kai tana kallonsa ganin ɗan abinda ya ci tace "Bai maka dadi bane?" Cikin
whisper yace "When it's not you...." Hararansa tayi ta gefen ido, yayi murmushi ya
sha ruwan da zai sha ya ajiye sauran yace "Let me not over stay my welcome, bari in
tafi sai da safe" Tace "Toh Allah ya kai mu..." Tashi yayi yace "Kice ma su Mumy na
tafi sai da safe" Nihad ta mike ta dau gyalen Nihal ta yafa a jikinta, shi dai
yana tsaye yana kallonta, ganin kallon da yake mata irin na mamakin nan ta ɗan buda
ido a hankali tace "Ko baka son rakiyan ne?" Ya wara ido yace "Idan baki rakani ba
ma ai bazan tafi ba sai dai in kwana parlon nan" Ta ɗan yi murmurshi ta dau wayarsa
dake saman kujeran, ya nufi kofa ta bi bayansa, sai bayan da suka fito daga main
parlor ya kama hannunta suka nufi gate walking slowly ko wanne da tunanin da yake a
ransa, Aminu na zaune bakin gate din har sannan shi fa bai gama dawowa dai dai ba
kai kace shine Farooq ko Usman, Nihad ta zame hannunta a hankali daga na Khalil
ganin Aminu, ta nufi gate ta fita, khalil ya tsaya wajen Aminu, ba a dau lokaci ba
Khalil ya fito kofar gidan ya ganta jingine jikin motarsa, ya karasa har kusa da
ita ya tsaya yana facing dinta yayi kasa da murya yace "Till tomorrow?" A hankali
tace "Allah ya kai mu lafiya" Yana kallon eye balls dinta yace "Ko mu tafi in dawo
dake gobe da safe?" Ta zaro ido tace "Aa ni dai bazan iya ba" Yayi murmushi yana
bin layin da kallo, wanda babu kowa cause it's few minutes to 10pm, murya can kasa
yace "Can i kiss you love?" Ta sunkuyar da kanta kawai tayi murmurshi, shi dai
kallonta kawai yake babu ko kiftawa da lumsassun idonsa, sai kuma yaga ta ɗan bi
layin da kallo, ganin babu kowa ta gyada masa kai a hankali, ya hade goshinsa murya
can kasa yace "With stew in my mouth" Daga haka ya fara kissing dinta, and he did
that for almost a minute, underneath his breathe yana lumshe ido yace "I love you
so much" Lumshe ido tayi, kawai yaga ta shige jikinsa a hankali tace "Same" Yace
"Same what?" Da sauri ta ajiye masa wayarsa kan motar ta juya ta nufi gate, dariya
ta basa sosai, ya bi ta da kallo har ta shige gidan ta kulle gate. Washegari Nihad
na tashi wajen karfe tara bayan tayi breakfast ta fara harhada duk kayanta dake
dakin Mumy, Aunty Jamila dai sai bin ta da kallon mamaki take don bata ce masu
komai ba kawai ta hau hada kaya kamar warce ake jira a kofar gida, Ita kanta Mumy
bin ta kawai take yi da kallo, tana kokarin rufe trolly dinta kamar ance ta daga
kai taga duk kallonta suke a dakin har Nihal dake dakin, kunya taji ya lullubeta ta
rufe fuskarta da trolly din da sauri tana turo baki, Aunty Jamila tayi dariya tace
"Duk wannan azarbabin tafiya ne haka kamar muna koranki Nihad?" Ita dai bata ce
komai ba kuma bata dago kanta ba but she is so ashamed, Aunty Jamila na murmushi
tace "Karfe nawa za ku tafi?" Ba tare da ta dago ba a hankali tace "Aa ni bai ce
min yaushe ba, kawai dai naga kayan are scattered ne shi yasa nake gyarawa fa
Aunty" Aunty Jamila nata murmurshi tace "Eh naga alama, kayan kam are scattered"
Fasa zuge zip din Nihad tayi daga karshe ta mike kawai ta fita daga dakin ta koma
dakin Nihal ta shiga bandaki tayi wanka ta shirya cikin kayan da ta cire a akwati,
riga da skirt ne da babban mayafi wanda Aunty Maryam tayi mata a Abuja, bata taɓa
sa shi ba dama sai yau, tana gama shiryawa ta kwanta gefen gado kawai... Karfe sha
daya Nihal ta shigo dakin, tana kallonta tace "Ur husband is around" Nihad ta daga
kai ta kalleta sai kuma ta mike zaune, Nihal tace "Bari in daura maki dankwalin"
Daga haka ta dau dankwalin ta tafi gaban madubi ta jawo stool tana kallon Nihad
tace "Dawo nan" Nihad ta mike ta tafi gaban mirror din ta zauna, eye pencil kawai
ta saka a idonta sai lip balm da ta saka a lebbenta amma zaka yi tunanin har powder
ta shafa, she looks so beautiful, ga shi ta ɗan marmaro daga raman da tayi, Nihal
tayi mata dauri me kyau ba kuma me hayaniya ba, ya zauna dass a kanta, sosai kyanta
ya kara fitowa, Nihad na kallonta a hankali tace "Thank you" Nihal na Murmushi tace
"You look beautiful sweet sis, nasan bazai gane ki ba" Nihad dai murmushin kawai ta
mayar mata, Nihal ta dauko mata gyalenta ta mika mata ta amsa sannan suka fita daga
dakin tare, tun da suka shigo parlon Mumy Khalil ke kallon Nihad babu ko kiftawa
don at first bai gane ita bace duk da na kwalliya tayi ba a fuska amma bai taɓa
ganinta da daurin dankwali ba, ta zaune tana kallonsa a hankali tace "Ina kwana" Ya
lumshe ido ya bude a hankali yace "You look beautiful dear, how was ur night?" Tana
wasa da fingers dinta tace "Alhamdulillah" Ita dai Nihal na zaune a parlon ta maida
hankalinta kan tv, Khalil yace "Ur box?" Nihal na jin haka ta mike ta tafi dakin
Mumy don dauko akwatin Nihad ta fita main parlor da shi, Aunty Jamila ta shigo
parlon tana kallonsu tace "Toh ku yi ma yan gidan sallama dai kafin ku fita" Khalil
yace "In sha Allah" Aunty Jamila tace "Kafin in koma Jigawa in sha Allah za mu taho
da lefen nata Abujan, inna ta kai su can gidan ta ajiye a dakinta" Khalil yace
"Allah ya kai mu Aunty" Aunty Jamila tace "Ameen, a gaida mana su Hajiya da
General, mun gode kwarai Allah ya bar zumunci" Khalil yace "In sha Allah" Nihad ta
mike ta tafi dakin Mumy, ta sameta zaune saman darduma, ta duka gefenta murya can
kasa tace "Mumy za mu tafi" Mumy na kallonta tace "Toh Nihad, Allah ya tsare, Allah
ya baku zaman lafiya, ki dau iyayensa tamkar naki sai ki zauna lafiya a rayuwa kin
ji, Allah ya baku zuri'a dayyaba" Ita dai Nihad kanta na kasa, Mumy tayi shiru bata
dake cewa komai ba, don bata son hawayen dake taruwa idonta ya zuba, she knows she
is so much going to miss her daughter most especially in this trying time, banda
Aunty Jamila na nan da bata san kuma ya zata yi ba, Nihad ta goge hawayen da ya
kawo idonta a hankali tace "Allah ya ji ƙan Abba ya basa aljanna...." Sai kuma ta
fashe da kuka, Mumy da hawaye ya fara sauka idonta tace "Ameen, ta shi ki je" Cikin
rawan murya tace "Idan su Sudais sun dawo ace masu na tafi" Kai kawai Mumy ta iya
gyada mata saboda bata son tayi breaking, Nihad ta mike ta nufi kofa Mumy ta bi ta
da kallo tana share hawayen dake sauka idonta, Aunty Jamila ta bi Nihad da kallo
bayan ta fito daga dakin, can ta mike ta tafi wajen Mumy, ba a dau lokaci ba ta
fito tare da Mumy da ta tsaya jikin kofar dakin nata tayi ma Khalil sallama cikin
sanyin murya, ya kasa kallonta yace "Ameen Mumy, Allah ya kara hakura" Ta amsa masa
da Ameen, sannan ta juya ta koma daki, Tare da Aunty Jamila suka fita main parlor,
Nihal na zaune main parlor din tana jiran fitowar su, ba don ran Nihad ya so ba
suka nufi bangaren Umma da khalil, shi ma kawai don Nihal na zaune ne bazata iya ce
masa a'a ba da yace mata za su shiga wajen Umma, banda haka da bazata ba wllh,
Kamila na zaune parlon Umma, ta gaida Khalil ya amsa mata da murmushi, ita dai
Nihad wasa kawai take da gefen mayafinta, Amina kuma ta shiga dakin Umma, sai ga
Umma ta fito ta zauna nan bakin kofar dakinta rike da carbi, Khalil ya gaisheta ta
amsa cikin sanyin murya, yace "Za mu koma ne yanzu in sha Allah Umma" A hankali
Umma tace "Toh Allah Ubangiji ya tsare hanya, Allah ya kai ku lafiya, ya kuma baku
zaman lafiya da zuri'a dayyaba, Allah ya rabaku da sharrin masu sharri" Kansa a
kasa yace "Ameen" Ita dai Nihad bata kalli Umma ba, Umma ta ɗan kalleta, sae kuma
cikin sanyin murya tace "Toh Nihad, Allah ya kai ku lafiya.... Allah ya ji ƙan
mahaifinku ya gafarta masa...." Ba tare da Nihad ta kalleta ba don har hawaye ya
cika idonta tace "Ameen" Khalil ya mike yace "Toh Allah ya ƙara hakuri Umma" Umma
tace "Toh Khalil, a yayyafe... Allah kuma yasa muna da rabon ganawa, Allah ya
kaddara saduwan mu" Yace "In sha Allah, Allah ya kara mana lafiya gaba daya" Nihad
ta mike ta nufi kofa ta fita, Khalil ya bi bayanta, Umma ta kalli Kamila tace "Toh
ki raka su ko" Mikewa Kamila tayi ta bi bayansu har zuwa main parlor, Khalil na
kallonta yace "What did u study in school?" Tace "Microbiology" Yace "Ohk maa sha
Allah, kuma duk Cv's dinki na nan ai" Tace "Eh suna nan" yace "Toh bari mu shiga
muyi ma Inna sallama kafin mu fito ki dauko min" Tace "Toh" Suna shiga dakin Inna
suka sameta ita kadai tayi backing kofar dakin tana ta faman aikin kirgan uban
kudaden da aka bata, har ta jawo zani zata boye ganin Khalil ne da Nihad ta bar su
a sarari, ta marairaice fuska tana kallon Khalil tace "Sannu Halilu" Ya zauna kasan
Carpet yace "Ina kwana inna?" A hankali tace "Lafiya lau Halilu, ya gajiya" Yace
"Alhamdulillah Inna" Nihad ta durkusa gefen gado tace "Ina kwana" Inna ta kalli
Khalil tace "Daga ita har Nihal sai sun ga dama suke shigowa su gaisheni su ce min
ya hakuri kuma sun san ina gidan nan, kai kace ni na kashe Ibrahim din" Khalil ya
ɗan buda ido yace "Aa gaskiya basu kyauta ba" Inna tace "Atohh bayan wanda ya hada
ma Allah ya daukesa ya bar duniyar da kalubalen dake cikinta kadai ta ishi bawa, ai
nasan in sha Allahu yana kyakkyawan masauki tunda shi din ba mutumin banza bane,
don haka tsakanina da su kawai kowa ya kama kansa, dama babu abinda na hada dasu
har ga Allah...." Khalil ya ɗan yi murmushi yace "Kiyi hakuri Inna" Nihad dai bata
kalli inda Inna take ba, Khalil yace "Dama za mu koma Abuja ne yau, shine muka
shigo mu yi maki sallama" Inna tace "Kai, kaga da anyi arba'in ai sai in bi ku
inje na musamman in ma Janar da mahaifiyarka godiya don ba ko wasu surkai ne za su
yi abinda suka yi ba, mutanen kirki wllh, sannan kuma duk abi da ni gidan abokansa
da suka zo har nan in masu ban gajiya, babu wanda bai ban dubu dari ba a cikinsu,
kaga yanzu nake ta hada kan kudaden ko rijiya ce in sa aje kauye a haka ma bayin
Allah, duk wanda ya sha ruwan Allah ya kai ladan gun Ibrahim dina" Khalil yace
"Gaskiya ne inna, hakan abu ne me kyau kuwa" Inna tace "Wallahi abinda nake so in
yi kenan, shi yasa na fito da kudaden yau nake kirgawa, sannan filayena biyu a
siyar a gina dankareren masallaci a bakin titi da sunansa, in sha Allahu abinda zan
yi kenan, idan Allah ya kara hore min har gidan marayu sai na gina da sunansa wllh,
to idan ban masa ba wa zai masa?? Sai dai ko yayansa Abubakar, balle ma Abubakar
din ya dauke nauyin karatun kananun yaran da ya bari wato Sudais da Fadil, ita
Amina naji ance ta gama sakandarin amma fa yace bazata jami'a ba, ni dai nace ko wa
aka samu kawai ayi mata aure ta bar gidan nan don babu ruwana kuma wllh, mai gadi
ma kaga Abubakar ne zai dinga biyansa albashi daga yanzu, da nace a kori ko me
gyaran fulawan da sharan tsakar gida a bar me wanki da guga kada kudin yayi ma
Abubakar din yawa sannan fa ga albashin dreba me kai kananun mazan nan boko da
islamiyya amma yace duk zai iya ba sai an kori kowa ba, cefanen gidan kuma Farooq
da Usman sai su dage, duk da buhunhunan shinkafa sun kusa goma yanzu haka a store
wanda abokan Marigayi da yan wajen aikinsa da yan anguwa suka harhada aka kawo, ga
jarkan mangyada manya manya har biyar, indomie ma da na kirga katan 11 ce wllh, ga
taliya, kuskus, macaroni, kai har fa da gero da masa ko wa zai ci?? Sannan ga
buhunhunan sugar, flawa, kai mu je ma in nuna maka store din ka gane ma idonka
kawai, wllh ko kwakkwaran spes babu a store din ya cika makil da kayan abinci"
Khalil yace "Duk na gani ai Inna, ina nan duk aka kawo" Inna tace "Toh banda shi
mutumin kirki ne waye zai ma iyalinsa haka? Ko nan da shekara biyu bana tunanin
kayan abincin nan za su kare, kawai fatana kada su yi espaya kawai" Khalil yace
"Baza su yi ba in sha Allah" Inna tace "Allah ya sa, sannan lefen matar nan in sha
Allahu idan zan taho godiya da bangajiya da su zan zo" Khalil na Murmushi yace "Toh
Allah ya kai mu inna, bari mu je kada jirgin ya tashi babu mu" Da sauri Inna tace
"Maza ku je, Allah ya tsare" Dubu hamsin ya ajiye mata, tayi ta godiya tana sa masa
albarka ta rakosu har main parlor, Kamila na tsaye tana ta jiransa da takardun
nata, ya nufeta ya amsa tace "Nagode Allah ya saka da Alkhairi" Yace "In sha Allah,
zan kai ma Abbana" Tace "Toh Allah ya kai ku lafiya" Gaba daya yan gidan suka
rakosu gun mota banda Mumy da Aunty Jamila sai Umma, Inna ta dinga cewa "Allah ya
kai ku lafiya, Allah ya kiyaye hanya...." Khalil ya bude motar yace "Ameen Inna,
Allah ya saka da Alkhairi" Aminu ya gwalo ido ganin wanda ke tahowa a mashin dinsa,
shi kansa khalil tsayawa yayi yana kallonsa, Inna tace "Waye wannan kuma da mashin
duk ya cika anguwa da ƙara" Yana isa dai inda suke ya kashe mashin din ya sauka ya
fashe da kuka sosai, Aminu ma ya rushe da kuka kamar jira yake, Inna ma sai ta
fashe da kuka tace "Habibu?? In gaya maka Habibu Allah yayi ma Ibrahim rasuwa"
Habibu ya nemi dakali ya zauna yana rusa kuka Aminu ya zauna gefensa yana tayasu,
Kamila tace "Don Allah meye haka, ku da za ku dinga bin sa da addu'a" Habibu yace
"Haka ne, Allah Ubangiji ya gafarta ma Alhaji, wallahi na shiga Nijar saro ma
yayana kaya sai jiya na dawo labarin nan ya riskeni, Allah sarki Alhaji har yau
gashi ina ta cin moriyar shagon da ya bude min har na gina gidana a birni" Inna
tace "Toh in kai me hankali ne sai ka duba marayun da ya bari kanana idan ko ba
haka ba Allah sai ya tsine maka wllh" Habibu ya dinga cewa "Haka ne inna, gaskiya
ne Inna" Kamila ta daga ma Nihad hannu ta juya kawai ta shiga ciki, Amina ma tace
"Allah ya kiyaye Aunty Nihad" Daga haka ita ma ta shiga ciki, Nihal ta mata side
Hug cikin sanyin murya tace "I will miss u sweet sis" Daga haka ita ma ta koma
cikin gida, Habibu ya taso yana kallon Nihad da ladabi ya gaisheta yace "Ya hakuri
Hajiya" Nihad ta sauke idonta tace "Alhamdulillah" Inna tace "Idan ka gama da su
sai ka shigo kayi ka su Maryam gaisuwa" Sai kuma ta kalli Khalil tace "Bari in
shiga Halilu, Allah ya kai ku lafiya" Ta juya ta shiga gidan, Habibu na kallon
Khalil yayi kasa da kai yace "Oga ya muka ji da hakuri?" Khalil yace "Hakuri mun
gode Allah Habibu" Habibu yace "Sau da yawa ina kiran layin nan naka da nake da shi
don in gaisheka amma bana samunka oga" Khalil yayi murmushi yace "Ina da numberka
ai, zan kiraka da main line dina" Da ladabi Habibu yace "Toh Oga godiya nake"
Khalil ya shiga mota don tuni Nihad ta shiga ta zauna, Habibu da Aminu na daga masu
hannu har suka bar layin, Nihad ta kallesa a hankali tace "Motar taka fa?" Yace "A
airport nake barinsa ai dama, but our flight is in the evening in sha Allah" Tayi
shiru tana kallonsa da mamaki don ta zata airport din za su yanzu, bata ce komai ba
shi ma bai kuma ce mata komai ba, tafiyar kusan minti talatin suka yi yayi horn
baƙin gate din hotel din aka bude masa ya shiga, Nihad na kallonsa tace "All this
while a nan kake dama?" Ya kashe mata ido yace "Yeah" Bata kuma cewa komai ba har
yayi parking ya kashe motar, yana kallonta kasa kasa yace "Kinyi breakfast?" Ta
gyada masa kai tace "Nayi" Yace "Ohk" Tace "Kai fa?" Yace "Done" Bude motar yayi ya
sauka, ita ma ta sauka sannan ya kulle motar, suka jera a tare suka shiga cikin
hotel din, ya amshi makulli a reception yana gaba tana biye da shi har zuwa dakin
da yake ciki, ajiye hand bag dinta tayi saman bedside drawer tana kallonsa a
hankali tace "Now tell me, where did u know Habibu?" Dariya yayi without looking at
her, ya ajiye wayarsa gaban mirror, ya cire shirt din jikinsa sannan ya hau saman
gadon ya kwanta yana nuna mata gefensa with smile all over his face yace "Dawo nan
ki ji inda na san Habibu" Ta dinga kallonsa, ganin taki tahowa yayi kasa da murya
yana kallonta yace "Then.... let forget about that question forever" Sauke idonta
tayi ta cire mayafin jikinta ta linke ta ajiye sannan ta cire dankwalin ma ta linke
ta ajiye, ta nufi saman gadon ta hau a hankali ta kwanta gefensa tana kallonsa....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

Ina kuke maabota kamshi? To Ku matso kusa, Albait Al Sahal sunzo muku da hadaddun
turarukan wuta na gida, ma jiki da kuma kaya. Akwai perfumed body oils masu dadin
kamshi da sanyaya zuciya. Akwai spritz Wanda Ko bakiyi turaren wuta ba ya i sheki
ga yana dadewa a wuri. Maza ku garzayo Albait Al sahal domin Ku Sami naku Cikin
sauqi domin yanxu suna sales komai ya sauqaqa. Duk wacca ta siya beyi mata ba ta
dawo dashi # we trust the quality of our products# contact me via WhatsApp
09084473900*💖NIHAAD💖*

*77*

A hankali yace "Come.... closer" Ta kafesa da manyan idanuwanta tana kallonsa babu
ko kiftawa, ya daga kafada yace "Ohk then" Yana fadin haka ya juya mata baya ya
kwanta, murmurshi tayi ta karasa kusa da shi a hankali ta daura kanta a bayansa
cikin sanyin murya tace "Ina jin ka" Juyowa yayi ya jawota jikinsa yayi pecking
lips dinta yana kallonta da kyau yace "What did u want to know?" Tace "Ina son
sanin menene alaqarka da Habibu, da kuma abinda ya kawoka gidanmu" Yana shafa dogon
gashinta a hankali yace "Only that?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk.... Bayan na bar
gidanmu Mami ta so in tafi Uk inyi zamana a can, but i refused saboda bana son
rayuwan turai, i then decided to come to kano, i love kano so much but occasionally
muke zuwa can, so ban taɓa rayuwa a garin ba.... i have a friend da muka fara
karatu tare da shi a India, ɗan nan kano ne, but mind u, we were among the few that
were privileged to get scholarship zuwa india to study medicine babu kosisin mu,
unfortunately he lost his Mum halfway muna cikin karatun, wanda hakan yayi
affecting performance dinsa badly, and sadly he was expelled from the school ya
dawo kano, all through our stay together in india ban taɓa nuna masa waye Abbana ba
don gaba daya Clique din namu opportunity ne ya kawo mu kasar, so kawai ina
rayuwata irin na kowa da kowa da muka taho karatun tare like i am also a
nobody...." Nihad dai sai kallonsa take, ya ja dogon hancinta yace "Zaki tsammanin
hancinki??" Murmushi tayi tace "Are you teasing me?" Yayi er dariya ya manna nasa
dogon hancin da nata yace "Toh naga naki ya fi tsayi" Tace "Ba wani nan naka ya fi"
Ya lumshe ido har sannan dogon hancinsa na manne da nata inhaling each other's
breathe, a hankali tace "Ka ci gaba" Ya buda idanuwansa da suka sauya kala murya
can kasa yace "Ohk" Ya kwantar da ita saman kirjinsa yana ci gaba da shafa gashinta
yace "Still after Mu'azzam left India muka ci gaba da mutunci sosai da shi, though
after going back to Nigeria shagon Abbansa ya koma zama a kasuwar kurmi inda
Abbansa ke siyar da magunguna irin na gargajiya, bayan na dawo Nigeria na so ya
zana jamb ya nemi admission ko a Buk but he told me the zeal to study has left him
since his mother's death, so nayi assisting dinsa in many ways that i can a sannan,
har ya bude nasa shago a nan kasuwar shi ma yana siyar da irin abinda Babansa ke
siyarwa but in a modernize way, After having issues with my dad wajen Mu'azzam na
tafi a kano, then yana hayan wani self contain a wani local unguwa, na dai manta
sunan anguwan, a wajensa nake kwana, a nan nake komai na, da safe mu siya abinci mu
ci sannan in bi sa zuwa noisy kasuwan mu zauna shagonsa tare, that almost affect me
mentally don ban saba ba, amma kuma bana son inje in zauna a hotel even though i
can afford it, ina bukatar zama tare da mutane for the sake of my mental health
because allegations din da Abbana yayi min is too much for me to bear" Nihad dai
sai kallonsa take babu ko kiftawa, yace "Habibu ya kan shigo kasuwan kurmi sosai,
don yana da wani aboki me siyar da kayan koli, shagon abokin kuma kusa da na
Mu'azzam ne, duk in Habibu ya zo wajen surutunsa ke announcing presence dinsa, a
haka dai har muka ɗan fara sabawa da shi don yakan leko shagon mu, and mind u har
sannan Mu'azzam bai san wanene mahaifina ba, don ni duk inda zanje bana show off da
Dad dina ko dukiyarsa.... i knew Habibu for like 3 months a kasuwar kurmi, har dai
muka saba sosai da shi, rana daddaya ne baya shigowa kasuwar, though shi Mu'azzam
baya wani kulasa fa, to saboda ni sai ya dade shagon Mu'azzam muna hira, so wataran
yake sanar min ai ya kusa komawa kauyensu na Getso gaba daya da zama don uban
gidansa ya bude masa shago a can, sai nake tambayansa waye uban gidan nasa, that's
how he started telling me about ur late dad, ya gaya min yayi serving dinsa for
almost 10 years now, and he was like ba don ci gaba bane da bazai bar gidan ba don
yana jin dadin aiki a gidan, yana jin yan gidan kamar yan uwansa, he told me they
are one of the nicest people he have ever met, ya kuma lissafo min workers din
cikin gidan da yanda ake basu 3 square meals everyday sannan ga wajen kwana, har
cewa yayi idan yana gidan mantawa yake ba gidansu bane...." Ya ɗan kalli Nihad dake
kallonsa with full attention, yace "As at then, i was missing the love at home, i
so missed my Family, i am not use to zaman kasuwa that is so noisy and polluted, i
imagined living with this nice family as a worker also, may be hakan zai rage min
kadaici da kewan nawa family din, ban yi kasa a gwiwa ba nace ma Habibu ko zai
taimaka min nima in fara tuki a gidan" Nihad ta sauke idonta kasa lokaci daya gaba
daya mood dinta ya canxa, Khalil ya lumshe ido ya bude a hankali yace "Habibu
refused, saying ya riga da yayi ma wani abokinsa alkawari, kuma ma Alhajin bai ce
ya kawo wani ba tukun, bluntly ya nuna bazai kai ni gidan ba, kin san yan kauye da
baƙin ciki at times, guess what i did..." Nihad ta daga kai ta kallesa a hankali,
yayi murmushi yace "I gave Habibu 200k just to get that Job, cause i need a new
family badly.... He was so shocked at first da na basa kudin, amma ko kwana biyu ba
ayi ba sai ga Habibu ya zo ya sameni wai yayi ma Alhajin magana yace ya kawo ni,
that was how everything started, a hanyar mu ta zuwa gidan yake sanar min ai ce ma
Alhajin yayi kauyenmu daya, ga gidansu ga namu, don haka kada inje in canxa baki, I
just smiled and said Ohk, kaf yan gidan Habibu bai min maganan kowa ba sai ke, He
told me idan ina son in dinga samun extra income in maki biyayya sannan duk inda
kika ce in kai ki kawai in kai ki sannan babu ruwana da kalan rayuwarki, komai zan
gani in yi shiru ni dai kawai in amshi kudi idan kin ban...." Nihad ta kasa barin
su hada ido, shi dai murmushi kawai yake yana kallonta, murya can kasa yace "And
you were the second person i met in that house after Aminu...." Nihad taki cewa
komai cause she remembered vividly ranan ganinsa tayi zaune a balcony wai yana
jiran Abba, tayi ta masifa don me zai zo nan ya zauna maimakon ya zauna kan benci a
bakin gate, daga nan kuma ta dinga tunano irin rashin mutuncin da ta dinga yi masa
kwando kwando babu ko tsoron height dinsa a gidan har zuwa sanda Abbanta ya daura
mata aure da shi, cikin sanyin murya yace "And i found the family i was looking for
in that great house, Aminu was more than kind to me tun farkon shigowata gidan,
wannan yasa i will make him great in life in sha Allah" Cikin sanyin murya khalil
yace "Abba!! Allah ya ji kansa ya gafarta masa, he took me in without second
taught, yayi accepting dina lokaci daya, har yayi min tayin zama a gidan if i wish,
apart from salaryn da yake bani a ko da yaushe cikin min ihisani yake, he trusted
me even with his Atm card a lkcn kuma ko wata hudu ban cika ba a gidan, and
Nihal... Duk sanda na ganta ina mata kallon Mimi, she made me feel free staying in
that house, she treated me with kindness.... Mumy kuma ina mata kallon mahaifiyata
cause she was so nice to me from the start, i still remembered her giving me one of
her expensive duvet and many other things, bata taɓa hana kananun yaranta zuwa inda
nake ba a gidan, Farooq!!! He ignored i was just a driver and we became friends,
idan yana gari tare muke zama da shi baƙin gate mu yi hira wani lokacin har zuwa
karfe sha biyun dare, na sha cin abinci a plate daya tare da shi da Aminu, Usman
kuma bai taba ganina ya wuce bamu gaisa ba duk da he is an Introvert, Fadil and
Sudais made me their new uncle and love me, even Amina bata taɓa wuceni bata
gaisheni ba....." Hawaye ya fara sauka idon Nihad ta kasa ce masa komai, shiru yayi
bayan yaji saukan hawayenta, can ya rungumeta a hankali yace "And you made my stay
a memorable one wife, i enjoyed almost every bit of ur altitude toward me, it made
my stay in the house worth remembering, duk sanda naga kinyi watsi da ni sai inji
kawai i need to find a way da zan jawo hankalinki gareni har kiyi min halin, i know
i am the cause of most of our fight, wani lokacin kuma ina yin hakan ne just for u
to react, sai kuma a hankali na lura u are being used and controlled, Lastly....
ban taɓa kawo kaddaran aure tsakaninmu ba, and i blessed the reason that made me
meet u Ummina...." Kuka take a hankali bata ce komai ba, ya rungumeta sosai wani
sabon sonta na kara shigarsa, cikin rawan murya tace "I.. i am sorry for
everything, i am sorry i treated u badly, i am sorry for all what i have done to
you, don Allah kayi hakuri" Whispering into her ears yace "I love you for all what
u did to me" Kuka kawai take tana ganin kamar ba haka bane a zuciyarsa, may be he
is only trying to calm her down, amma tasan bazai taɓa manta abubuwan da tayi masa
a gidansu ba. Sai bayan isha'i suka sauka garin Abuja, tun kan su iso dama Drivern
Mami ke jiransu a airport, Nihad bata san if she is happy coming back to Abuja ba
or she isn't, ita dai gata nan gata nan ne kawai, a haka dai har suka iso gidan
Janar, Mami ta ji dadi sosai ganin yanda tayi move on bayan rasuwan mahaifin nata
don har ta marmaro, nan ko bata san handwork din ɗan ta bane, har parlon Janar suka
tafi gaishesa don yana gidan, Janar ya tambayeta su Mumy da Inna, Nihad tace "Suna
nan lafiya" Basu wani jima parlonsa ba suka koma bangaren Mami, abinci iri iri Mami
ta sa aka ajiye masu a parlon nata kafin su dawo, sai da suka yi sallah sannan
Nihad ta fara zuba masa abincin don su biyu ne kadai a parlon, Mimi da Noor sun
koma dakinsu, ya sauko ya zauna kasa yana kallonta ta ajiye masa abincin a gabansa,
ya girgiza kai yace "Ae tare za mu ci, ba sai kin zuba wani ba" Ta zaro ido tace
"Aa ni bazan iya ba...." Yace "Toh return the food inside the warmer nima bazan ci
ba" Murmushi tayi murya can kasa tace "Mami fa zata iya shigowa yanzu" Yace "Ita ma
zuwa tayi ta ci abinci tare da mijinta" er dariya Nihad tayi bata dai ce masa komai
ba ta dau wani spoon din ta fara cin abincin a hankali, yayi murmushi ya dau nasa
cokalin ya fara ci, may be don suna ci
from the same plate ne yasa suka ci da yawa barin ita, bayan sun gama cin abincin
Nihad ta tafi kai sauran abincin kitchen Mami ta shigo parlon, ta zauna tana kallon
Khalil tace "Hope the family are doing better now" Khalil yace "Alhamdulillah" Mami
tace "To maa sha Allah, Allah ya kara masu hakuri da dangana" Yace "Ameen" He was
expecting Mami zata ce su tafi gidansu duk da yasan dare yayi amma bata ce haka ba,
sai ma wani hiran na daban da ta kawo masa, Nihad dakin Mimi kawai ta tafi don ta
hadu da Mami a hanya sanda zata kitchen. Washegari da safe Khalil na zaune parlon
Abbansa ya je gaishesa, Janar yace "So sun shirya maka sanda zaka tafi can Yemen
din kenan?" Khalil ya daga kai ya kalli Abbansa don nobody is even saying anything
to him about the wedding anymore, kuma ba wai basa waya da Nadeeyah bane don har
kusan karfe sha daya jiya yana waya da ita, a jiya da suka dawo ma ya zata Mami
zata yi masa magana don sun ɗan yi hira, amma har yayi mata sai da safe ya tafi
dakinsa bata ce masa komai game da bikin ba, Janar yace "Tunanin me kake?" Khalil
ya sauke idonsa yace "Abba na zata tare za mu je can din ai" Janar yace "No, of
course no, sai dai representative dina but my schedules are tight" A hankali Khalil
yace "Ohk sir" Janar yace "But let me ask you, Ibrahim kana ganin zaka iya adalci
tsakaninsu kuwa?" Khalil yayi shiru yana kallonsa, Janar yace "I am asking this
because, ita dama wannan da zaka aura yanzu choice dinka ce, and i know kuna tare
da ita for long, ita kuma wannan matar taka.... aure ne da Mahaifinta ya hada ba
kai kace kana so ba" Murya can kasa Khalil yace "Zan iya in sha Allah" Janar yace
"Toh Madallah, Allah ya baka ikon hakan, i will talk to ur Uncle sai ku tafi can
kasar tare da shi, may be this weekend in sha Allah, sai iyayen nata su sanar masu
da zuwan naku" Khalil yace "Toh nagode Abba, Allah ya kai mu" Janar yace "Ameen"
Bai jima a parlon ba ya mike ya fita ya tafi bangaren Mami ita dama duk asuba yake
shiga gaisheta, Abbansa ne dai sai kusan takwas ko tara yake shiga gaishesa, xaune
ya sameta a second parlor dinta tare da Mimi da Nihad, Nihad tayi shiru ganinsa, ya
kalli Mami da Mimi dake kallonta, Ya zauna saman kujera, Mimi tayi masa murmushi
tace "Ina kwana yayanmu" Yace "Lafiya lau" Nihad ta ɗan kallesa tace "Ina kwana"
yace "Lafiya lau" Mami na kallon Nihad tace "Ina jin ki" Sunkuyar da kanta tayi
kawai tayi murmurshi, sai kuma ta ɗan saci kallon Khalil amma ta kasa ci gaba da
maganan, Mami ta yi murmushin ita ma tace "Toh ku je ku shirya...." Nihad ta mike
ta nufi kofa, Mimi tayi dariya ta tashi ta bi bayanta har suka fita parlon, Khalil
ya kalli Mami yace "Me take gaya maki?" Mami tace "Ina ruwanka da abinda take gaya
min" Ya shafa kansa yace "Ohk then" Mami bata sake ce masa komai ba, shi ma yayi
shiru, bayan wani lokaci ya kalleta yace "Mami Abba yace da weekend sai mu tafi can
Yemen din, So sai su sanar masu a can din about our coming..." Mami dake ta
kallonsa tace "Toh ai can gida zaka je ka samesu ka gaya masu ko?" Ya ɗan buda ido
yace "Na zata zaki kira Mom din Nadeeyan ki gaya mata kawai Mami" Mami tace "Aa ka
dai je ka gaya masu da kanka ya fi" Yace "Toh" tace "Kayi breakfast ne?" Ya bi
flask da warmers dake parlon da kallo, sai kuma ya girgiza kai, Mami tace "Su Mimi
ne suka yi yanzu, and it's still hot" Ya sauko ya zauna saman Carpet yana bude
warmers din gaba daya, sai kuma ya debi abinda zai ci, ya hada Lipton, jefi jefi
suke magana da Mami har ya gama breakfast din ya mike zai bar parlon sai kuma ya
juyo yace "Mami naji kince su shirya ina za su?" Kallonsa kawai Mami take yi, hakan
yasa ya juya ya fita daga parlon, Direct dakin Mimi ya tafi ya ganta ita kadai a
dakin tana fiddo masu kayan da za su sa da Nihad, ita kuma Nihad na bandaki tana
wanka, yana kallon Mimi yace "Ina za ku naji Mami tace ku je ku shirya?" Tace "Nima
ban sani ba, amma tare za mu fita da ita" Ya ɗan yi shiru sai kuma yace "Ohk, let
me disturb you a little, can u pls make me a cup of coffee ki kai min daki" Tace
"Ohk" Daga haka ta nufi kofa ta fita, bandakin ya karasa ya bude, Nihad dake
kokarin fitowa daure da towel ta koma bandakin da sauri ta zaro ido tana kallonsa a
tsorace imagining ta inda ya bi ya shigo, ita dai tasan ta bar Mimi a dakin to ko
fita tayi, shigowa taga yayi ya kulle kofar, ta marairaice masa tace "What is this
u are doing, Mimi idan ta shigo fa, don girman Allah ka fita" Yace "Ina za ku?" Ta
girgiza kai da sauri tace "Wallahi ban sani ba, Mami ce tace in shirya, don Allah
ka fita Mimi kar ta shigo yanzu" Ya nufota zata koma baya yayi saurin kamota ya
kwance towel din, ta wani hade rai tace "Ni bana son haka, this isn't proper plss,
dakin Mimi ne fa" Yace "Ohk, me kike ce ma Mami dazu?" Ta turo baki tace "Ni dai
nace ka fita don Allah" Yace "Kin yi alkawarin idan na fito za ki shigo dakina ki
gaya min?" Da sauri tace "Ehh" Yace "Ohk" light kiss yayi mata ya juya ya fita,
tana jin ya kulle kofar dakin alamar ya fita, ta ɗan leka cikin dakin taga Mimi
bata nan, ta sauke wani ajiyar zuciya ta fito, ko da Mimi ta dawo dakin ta sameta
tana shiryawa, Mimi ta shiga bandakin don yin wanka ita ma, Nihad na gama shiryawa
ta fito ta tafi bangaren Mami da sauri don bata manta abinda ta gaya mata jiya da
daddare ba.... Mami na dakinta tana shiryawa Khalil ya shigo parlon, Nihad dake
zaune parlor ta sunkuyar da kanta, yayi kasa da murya yace "Ni kika yi ma wayo ko?"
Boye fuskarta tayi taki ce masa komai, sai ga Mami ta fito rike da makullin motarta
yace "Mami zan fita sai na dawo" Mami tace "Alright, mu ma yanxu za mu fita" Yace
"Toh Allah ya kiyaye" Daga haka ya juya ya nufi kofa, Nihad ta bi sa da kallo, Mami
ta koma dakinta don dauko handbag dinta, Nihad ta mike da sauri ta bi bayansa a
second parlor ta gansa har ya bude kofar zai fita, a hankali tace "Ina za ka?" Ya
juya ya kalleta yace "Nima ban sani ba" Tayi shiru tana kallonsa daga sama har kasa
don ba karamin kyau kayan jikinsa suka yi masa ba, lokaci daya mood dinta ya canza,
yace "Ba dai ni kika yi ma wayo ba, zaki shigo hannu ai" Juyawa tayi ta bar wajen
da sauri yace "Wait..." Amma tuni har ta koma first parlor, ya shafa kansa yana
murmushi, sai kuma ya juya ya fita. Gidansu Nadeeyah ya tafi yana zaune compound
din gidan yana jiranta bayan ya kirata a waya, ba a dau lokaci ba sai gata ta fito,
ta ja kujera ta zauna tana kallonsa da murmushi fuskarta tace "Sannu Kjay" Yace
"Sannu kamar wani mara lafiya" Tace "Ohk, weldone KJay..." Yayi mata murmushi yace
"How are you doing" Tace "Alhamdulillah, how is ur wife?" Ya ɗan kalleta, amma sai
bai ce mata komai ba, tace "Naji Mum tana cewa za mu je can gidan ma Anjima" Yace
"Ohk Mum na ciki?" Tace "Yeah, but tana da bakuwa" Yace "Ohk, we will be going to
Yemen on Saturday with my uncle don Abba bashi da lokaci, shine na zo in gaya maki
ki gaya ma Mum don ta sanar masu kafin Saturday din" Nadeeyah dai tayi shiru tana
kallonsa, yace "Ya kika yi shiru Madam?" Ɗan murmushi tayi tace "Kasan a rayuwa
muna namu Allah na nasa ne ko?" Yace "Sure..." Tace "And kasan policy dina a baya
da nake yawan cewa i will never marry someone's else Husband, kuma idan baka manta
ba a lokacin muna Uk da kaje kara karatu ni kuma ina year 1 farkon haduwarmu kenan
nayi wani saurayi me mata da yaro daya da yake zama a Uk, na kuma so sa but na ki
aurensa saboda yana da mata, ka tuna ko?" Ya sauke idonsa bai dai ce komai ba don
truly tana yawan fadin haka a baya, har tsokanarsa ta sha yi kan cewar duk ranan da
zai mata kishiya sai dai fa ita ya saketa yayi aurensa, Jin yayi shiru Nadeeyah
tace "Kayi shiru" ya daga idanuwansa ya kalleta but still bai ce komai ba, murmushi
tayi tace "To be sincere Kjay, after i found out u are married na sanar ma da Mum
dita ni baxan iya aurenka ba na hakura, my Mum tried persuading me inyi hakuri kada
ince haka ko don zumuncin dake tsakaninta da Mami, Mami won't be happy idan nayi
hakan, Few months back ai kaga er uwar Mum dita ta zo daga yemen, she came because
of the issue saboda i was serious nace bazan aureka ba ni na hakura, idan ka lura
har wayarka ai bana dagawa a sannan cause har zuciyata nasan na hakura da kai, amma
Mum dita da sister dinta suka saka ni a gaba for almost a week ana abu daya, har
yau kuma Mami bata sani ba, almost all my maternal relatives sai da suka min magana
a kan issue din nan, and at last babu yanda zanyi haka na janye kudurina na cewa na
fasa auren, but still idan ka lura har yau ni da kai ba kamar yanda muke a da bane,
kuma kai ma ka sha fadan haka...." Yayi kasa da murya yace "Kiyi hakuri Nadeeyah,
Allah ne ya tsara mana haka" Tayi murmushi tace "Haka ne, daga karshe ya kuma tsara
babu aure dama tsakanina da kai Kjay" Da mamaki yake kallonta, tace "Yeah, we were
not destined to live as husband and wife tun daga farko...." Yace "Why are you
saying this Nadeeyah?" Tace "I am saying this because Nihad is my second cousin,
kuma ni bazan iya auren mijin cousin dita ba duk da ba haramci a auren namu amma
bazan iya ba, Beside even if i should ignore the fact that Nihad is my Second
Cousin, in dai da mutunci Mum dita bazata bari in aureka ba ko don saboda Cousin
dinta warce ita ce Mahaifiyar Nihad" Cike da confusion Khalil ke kallonta don shi
har a lokacin babu wanda ya gaya masa meke faruwa, Yace "Ban gane ba Nadeeyah, u
are getting me confuse, what is happening" Ta mike tace "Ina zuwa..." Yace "Wait
plss ki fahimtar da ni Nadeeyah" Tace "I am coming" Ya bi ta da kallon mamaki har
ta shiga cikin gidan, ba a dau lokaci ba sai ga mai aikin gidan ta fito ta karaso
har inda yake ta sanar masa ance ya shigo ciki, tashi yayi ya bi ta zuwa cikin
gidan, nan ya tarar da Hajiya Safeenah a parlor, ya zauna ya gaisheta ta amsa da
fara'a tana tambayarsa ya ya baro mutanen kano, yace "Alhamdulillah" Tace "Naje har
kanon amma bamu hadu ba har na taho" Da mamaki yace "Wallahi ban sani ba Mum" Tace
"Ehh nasan baka sani ba Khalil" Bai sake cewa komai ba yayi shiru yana
jiran yaji kiran me tayi masa, tace "Kana ji na Khalil" Yace "Ina ji Mum" Tace
"Kasan komai ya faru a rayuwa mukaddari ne daga Allah ko?" Shi dai yayi shiru yana
kallonta, tace "Don haka ina son ka sa a ranka Allah bai kaddara aurenka da
Nadeeyah ba" Da mamaki yace "Mum me yasa kika ce haka?" Tayi shiru tana kallonsa, a
nutse ta shiga yi masa bayanin duk abinda ya faru da kuma alaqarta da Mahaifiyar
Nihad, he was just speechless and at the same time confuse, tace "Duk da aure
tsakaninku bai haramta ba amma sai mu yi masu kara, kuma er uwata ce ta kusa ba ta
nesa ba, daga kai har Nadeeyah ku yi hakuri, kai ka zauna lafiya da matarka ita
kuma Allah ya bata miji na gari, amma bazan iya barin 'ya ta ta auri mijin Nihad ba
albarkacin zumunci, Nayi ma Hajiya Fatima bayanin komai yau kusan sati uku kuma ta
gamsu da duk bayanai na ta kuma min uzuri...." Khalil dai tuni ya fada duniyar
tunani yana ganin abun kamar a mafarki, jin Mum tayi shiru ya kalleta yaga shi take
kallo, A hankali Khalil yace "Amma Mum babu haramci a aurena da Nadeeyah ai" Tace
"Kayi hakuri Khalil, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi, Allah ya ma Nadeeyah
zabin alkhairi" Sunkuyar da kansa yayi bai ce komai ba yana ganin kamar dole ma
Allah ya kamasa bayan jiran nan nasa da Nadeeyah tayi at the end ace bai aureta ba,
Mum tace "Bari in je ina da bakuwa khalil" Bai iya yace mata komai ba har ta mike
ta bar parlon, ya Jinginar da kansa jikin kujeran parlon, ba a dau lokaci ba
Nadeeyah ta shigo parlon tana kallonsa tace "Hope ka gane yanxu??" Yace "Ban gane
ba Nadeeyah.... Don ke da Nihad kun kasance Cousins ba wannan yake nufin babu aure
tsakaninmu ba ai" Tace "Toh babu, dama kawai iyayena nake kokarin yi ma biyayya
kuma i am happy things later turnout this way at last, and i pray it's just the
best for me"

*Thanks for the calls and messages to check on me, i am much better*

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788*💖 NIHAAD💖*

*78*

Khalil ya girgiza kai yayi kasa da murya yace "Kar ki ce haka pls Nadeeyah, don't
say that plss, it's a promise we made na auren juna, do not allow us break that
promise plss..." Nadeeyah tace "Plss kada mu ja issue din nan Kjay, Allah ya sa
hakan shine mafi alkhairi gareni, sannan kuma gareka, let's close this case forever
and ever, in dai ba ja kake son yi da mahaifiyata ba...." Kallonta kawai yake ya
kasa cewa komai, tayi murmushi tace "So what's up now?" Jinginar da kansa kawai
yayi jikin kujera a hankali yace "Ba wani mahaifiyarki Nadeeyah, dama kin riga kin
sa a ranki ke baza ki auri me mata ba, kuma kin fada just now, baxa ki aureni ba
saboda ina da mata yanzu, i understand u are just using this new issue to cover up"
Tace "I agree with what ever u think Kjay, ko da na aureka bazan samu rest of mind
ba i know, so i love the way things took a new turn, from henceforth u are the
brother i neva had, zan daukeka matsayin babban yayana that will always be there
for me" Shiru kawai yayi yana kallonta lokaci daya duk yanayinsa ya canza, tace
"Let me get u water and some slice of cake" Daga haka ta mike ta nufi cikin gidan
ya bi ta da ido babu ko kiftawa. Bayan la'asar Khalil ya shigo gida bangaren Mami,
gaba daya mood dinsa wasn't good, Parlor ya tadda Mami da Noor xaune suna kallo
tare, ya nemi waje ya zauna yana kallon Mami cikin sanyin murya yace "Ina yini" Ta
kallesa tace "Lafiya lau" Shiru yayi, bayan wani lokaci a hankali yace "Mami me
yasa baki gaya min abinda ke faruwa ba?" Mami tace "Yanxu dai ba ka je ka jiye ma
kunnenka ba Khalil" Jin bai ce mata komai ba ta kallesa, taga kallonta yake alamar
dai he is speechless, tace "Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi gare ku baki
daya, Allah ya bata miji na gari ita kuma" Mikewa kawai yayi ya bar parlon Mami ta
bi sa da kallo. Mami na zaune parlon Janar da shigowarsa gidan kenan wajen karfe
biyar na yamma, Apple ne da ta yanka masa a gabansa yake ci, ta ci gaba da maganar
da take masa a hankali tace "Toh yanzu suna son za su dawo maka da kudaden ne" Ya
kalleta da sauri yace "Inyi me da su? No they should keep it, it's okay ba damuwa,
haka Allah ya tsara" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh shikenan, zuwa Anjima
zan kira Hajiya Safeenar in gaya mata, kai kuma Allah ya kara girma" Wayarsa dake
gefensa ya dauka saboda kiransa da ake ya daga ya kai kunne a takaice yace "Basu
wayar kawai in masu magana idan ka iso..." Daga daya bangaren me kiran nasa yace
"Amma kana ji na Abubakar, dama ban maka bayani bane, zancen gaskiya bani kadai
bane, kuma muna isowa suka fara kora mu babu tantama kila ka gaya masu...." Janar
ya katse sa yace "Da kai da waye?" Yace "Da dai ka bugo masu waya kayi masu magana
su bari mu shigo sae kaga ni da wanene" Janar yace "Kaga Yaya ni ba kowa nake
kawowa gidana ba gaskiya, banda kai sai Abdulrazaq babu wanda yasan inda nake, ban
kuma ga dalilin da zaka kawo min wani gidana ba, kai baka ga irin security din
wajen bane" Yace "Kwarai na sani Abubakar amma don Allah kayi hakuri dole ce tasa
na taho ba ni kadai ba, amma...." Janar ya katse wayar kawai, ya dau wayarsa da
sojojin suka san sa da shi ya kira, ya kuma basu umarnin tahowa da Yayan nasa wanda
suke uba daya tare da bakon nasa har zuwa cikin gidansa ba sai anyi ta tsayar da su
a checking point ba, Mami na kallon Janar tace "Amma baka sanar min za kayi baƙi ba
a tanadar masu abu na musamman Janar" Yace "Tun last week yake ta son mu hadu to
kinga i am so busy, saboda shi ne ma nayi canceling tafiyata na yau, banda zuciyar
musulunci ni zan kalli Umaru ma kuwa balle in bar sa ya zo har gidana? Wuyarta dai
Allah ya daga mutum nan xai ga wa enda suka yi ta nufansa da sharri sun fi kowa son
su kasance da shi, ni fa nan da kike ganina na dawo daga rakiyar mutane wllh" Mami
ta girgiza kai cikin kwantar da murya tace "Ka daina kawo abubuwan baya da suka
wuce Janar, sannan yan uwanka ne su kuma hannunka baya taɓa rubewa ka cire ka yar,
ka dubi girma irin ta zumunci kayi hakuri duk ka yafe masu kai ne a gaba, su kuma a
baya, hakurin ka ne ya kai ka har wannan matsayin da su basu samu ko 5% dinsa ba,
don haka eraze all this off ur mind" Janar ya mike ya fita daga parlon zuwa parlon
baƙi don har sun shigo gidan don a mota yayan nasa yake, Mami ta bi sa da kallo sai
kuma ta mike ta bi bayansa, Janar na shiga parlon baƙin yaga Yayan nasa Umaru zaune
saman kujera, Alhaji Umaru yace "Ran babban soja ya dade" Kallonta kawai Janar yake
da mugun mamaki, ita kuwa ta sunkuyar da kai kamar munafuka, Janar ya kalli yayan
nasa rai bace yace "Yaya wacece wannan din ka kawo min gidana? Kuma a kan wani
dalili" lokaci daya ta fashe da kuka sosai tace "Don girman Allah yaya kayi hakuri
ka yafe min duk abinda nayi maka wllh sharrin shaidan ne, na tuba bazan kara ba
yaya, ka dubi girman Allah kayi hakuri, duk inda mahaifiyarmu take bazata ji dadin
wannan abinda ka min ba wallahi" Alhaji Umaru yace "Har gidana ta zo ta sameni tana
kuka Abubakar akan cewar in rakata ta zo ta baka hakuri domin idan taje ita kadai
sojojin koran karya suke mata ga kuma tsallan kwado da za su sa ta tayi ta koma
gida kafa duk a kumbure, dalilin da yasa nayi ta kiranka kenan nace maka lallai
lallai ina son mu hadu...." Janar yace "Amma baka kyauta min ba Umaru, kuma da
nasan da wannan shaidaniyar zaka shigo min gidana wllh bazan bari kai ma ka shigo
ba, wannan ai bai dace ba, ina ruwanka da tsakanina da Hassana?" Alhaji Umaru ya
marairaice yace "Ni fa gyara zan yi Abubakar, naga dai yarinyar nan uwarku daya
kamar yanda muke uba daya da kai, kaga kuwa nima ai er uwata ce kuma baxan ga wata
baraka in yi shiru ba" Mami ta shigo parlon da sallama don gaisawa da Alhaji
Abubakar, da mamaki ta dinga kallon Hassana warce tayi bakikirin kamar roban wanki,
wanda dama baƙin shine ainahin colour dinta amma man shafawa me shegen tsada da Ac
da ciye ciyen kayan dadi a gidan Janar yasa ta koma jajir kamar baturiya, Mami ta
dai karasa ciki ta zauna ta gaida Alhaji Abubakar sannan ta kalli Aunty Hassana
tace "Sannu Hassana ya kwana biyu?" A dakile Aunty Hassana tace "Lafiya lau" Sae
kuma ta kalli yayan nata cikin rawan murya tace "Wallahi kwayar abincin da za mu ci
babu a gidana Yaya, tun barinmu gidan nan nayi ma Aliyu kira yafi dubu amma wllh
yaki dagawa, ban san inda ya tafi yake rayuwarsa baya son mu rabesa ba ya bar mu
cikin wannan halin da muke ciki da kannensa, ni ba sisi ba, kuma bani da dalilinsa
tunda ba kasuwanci na iya ba, dama dubu dari bakwai ne a account dina bayan bari na
gidan nan, na kama mana hayan dubu dari shidda daki daya da parlor da bandaki a can
cikin gari, dubu dari din na siya mana kayan abinci, to yanzu ko kwayar shinkafa
babu a gidan, tunda muka shigo satin nan a wahale kawai muke wllh yaya, su Sajidah
ma babu kudin motar zuwa makaranta" Janar yace "Ina ubansu da zaki kawo min maganar
banza?" Tace "Ni dai kayi hakuri duk abinda nayi maka yaya, na maka alkawarin hakan
bazai sake faruwa ba, ai mun horu haka kusan wata daya da sati biyu, don Allah kayi
hkuri ka yafe min" Janar ya mata tsawa yace "Me kike nufi yanzu?" Daga ita har
Umarun sai da suka tsorata a parlon, Umarun yayi karfin hali yace "So take kayi
hakuri ka bata dama na karshe ta dawo nan da yaranta su ci gaba da zama Abubakar,
kuma in sha Allahu bazata sake yin abinda tayi ba" Janar ya girgiza kai yace "A
area din da nake ma Hassana bata isa ta zauna ba balle cikin gida na, abu daya zan
iya yi ma Hassana kuma shine na karshe wallahi kun ji na rantse kuma bazan yi
kaffara ba, Sannan bana son ko da wasa ta sake zuwa kusa da inda nake idan kuwa ba
haka ba zan sa sojoji su halbe min ita, Nauyin yaranta kuma ba a kaina yake ba ta
kwashesu ta mayar gun ubansu da ta rabasa da su tun suna yara, ita kuma albarkacin
zumunci zan tura mara miliyan biyar a account dinta taje ta koyi kasuwanci tayi,
iyakar abinda zan iya yi ma Hassana kenan, bayan nan kar ta sake making mistake din
zuwa kusa da inda nake idan ko ba haka ba bazata ji da dadi ba" Umaru yace "Yo ai
hakan ma ta gode, Miliyan biyar a wannan marran, aa wllh ta gode...." Janar ya fice
daga parlon, Mami dai na zaune parlon ta kasa cewa komai, Aunty Hassana ta daga kai
tayi mata wani kallo ta dauke kai, Mikewa Mami tayi ta fita daga parlon, Umaru yayi
kasa da murya tace "Toh yanzu nawa zaki turo min kenan Hassana? Kin ji fa har
miliyan biyar, ke ko kin haye wllh" Ta galla masa wani kallo tace "Ehh lallai amma
baka da tsoron Allah, kai da nace ka tursasa ka dage kayi min kokari wajen ganin ni
da yarana mun dawo gidan da zama, ni ban ma ga amfanin zuwanka ba, ko ni ai zan iya
zuwa ya bani miliyan biyar din ba sai ka rakoni ba Umaru" Umaru da ya bude baki
yace "Amma ke butulu ce Hassana, haka za ki ce min? Ba don ni ba ke kin isa ki zo
kusa da layin nan??" Ko kallonsa bata sake yi ba, Sai ga Janar ya shigo yana
kallonta strictly yace "Na tura maki miliyan biyar, yau ya zama rana ta karshe da
za ki shigo unguwar nan idan ba haka ba wallahi baza ki ji da dadi hannun sojojina
ba" Ta marairaice tace "Toh yaya nagode, Allah ya kara girma" Daga haka ta mike ta
dau Handbag dinta ta nufi kofa, Umaru ya bi ta da kallo baki bude har ta fita,
Janar yace "Na tura maka 100k ka kara mai a motarka" Yayi shiru da farko, sai kuma
yace "Toh, toh, to ba damuwa" Janar yace "Zan shiga ciki, ina expecting wasu baƙin"
Mikewa Umaru yayi ya nufi kofa, kana ganin reaction dinsa kasan ya raina 100k din,
har ya fice daga parlon babu sai anjima, Janar ya koma part dinsa, Aunty Hassana na
barin gidan ta kira wata kawarta da ta hadata da wani sabon malami dake cikin garin
Abuja, bayan sun gaisa tace "Sabira na samo kudi yanzun nan, nawa kika ce yace za a
bashi last price?" Sabira tace "Ke Allah fa ya sa ya samu lokacinmu, Kinsan yan
siyasa kawai yake ma aiki amma zan je har gidansa in lallabasa yayi mana aikin"
Aunty Hassana tace "Yanzu dai nawa za a bashi nake tambayarki?" Tace "Wallahi
miliyan biyu ma Allah ya sa ya kallemu, shi fa aikinsa kamar yankar wuka yake,
karamin kudi da yake amsa idan yayi aiki baya yin kasa da miliyan biyu" Aunty
Hassana tace "Toh zan tura maki yanzu, Don Allah ko ma me zai yi yayi kawai aga
cewar ba er sa bace a result din nan" Sabira tayi wani dariya tace "Sha kuruminki
Hassana, kawai dai ki hado min da miliyan daya da na ara maki kika kai ma wannan
munafukin malamin da har yau bakya samunsa a waya" Aunty Hassana ta ɗan yi shiru,
yanzu fa idan ta tura 3m kudin saura 2m kenan fa, a ranta tace to meye in dai
bukata zata biya, ana gamawa da case din Hanan, sauran miliyan biyun zata ba
malamin yayi mata aiki akan Janar, sanda zai ce ta dawo ba sani zai yi ba. Tun da
Khalil ya shigo corridor din part din Mami ya ji wani kamshin turaren wuta me
birkita hankali na tashi amma ya rasa ta wani direction ne, it's just past 9 now,
yayi ta bin ko ina da kallo, can ya nufi guess room dake part din don kamar ta nan
kamshin ke fitowa ya baza corridor din, bude kofar dakin yayi yana kallon ciki,
tana zaune gaban mirror tana shafa kwallacham, ga garwashin turaren wutan a kasa,
ta zaro ido tana kallonsa har ya tura kofar ya karaso cikin dakin ya nufota yana
kallon gashin kanta da yayi bakikirin sai sheki yake, tayi narai narai da ido tace
"Wallahi yanzun nan Mami ta fita kuma yanzu zata dawo, plssss ka fita kar ta shigo"
Ya jingina da bayanta yana jin wani fitinannen kamshi na tashi a jikinta hade da na
turaren wuta, ga wani laushi na musamman da yaji jikinta ya kara kamar ainahin
auduga, kasa magana yayi da farko, can dai ya dake murya can kasa yace "Ina kika
shiga duk yau ban ganki ba Baby? I have search everywhere ban ganki ba" yana fadin
haka taji chilled lips dinsa a wuyanta, ta marairaice tace "Na shiga uku, don Allah
ka bari pls, wllh Mami is coming back now" Ko rufe baki bata yi ba Mami ta bude
kofar dakin, da sauri ya saketa ya koma baya, kallo daya Mami tayi masa ta nufi gun
garwashin wutan rike da wani kwalban turaren wuta, Nihad dai ta kasa daga kanta ta
ci gaba da shafa kwallacham da take yi, Ya kasa kallon Mami shi ma don juya mata
baya ma yayi, can dai ya shafa kansa ya nufi kofa kamar munafuki har ya fita daga
dakin ya jawo kofar, Mami ta gama sa mata turaren wutan wanda na tsugunno ne, ta sa
mata stool din sannan ta gaya mata yanda zata yi, Mami na tsaye for almost 7
minutes kafin tace "Dau kayan baccin naki mu je ki kwanta" da a nan dakin zata
kwanta amma jin abinda Mami tace mata ta dau kayan baccinta ta saka sannan ta bi
bayan Mami zuwa ɓangarenta ta kwanta a bedroom dinta, ita kanta wani daban take jin
ta, tun da suka fita daxu da safe suka tafi wani tsadadden saloon wanda ya fi inda
Mimi ta fara kai ta farkon zuwanta gidan, bayan an gama mata gyaran gashi aka kai
ta wajen gyaran jiki duk a katon building din saloon din, ita kanta bayan an gama
gyaran jikin sai da jikinta ya bata sha'awa, luwai din kenan don sai wani glowing
take ko ina yayi sumul a jikinta, washegari da safe ma zata sake komawa saloon din
don ci gaba da gyaran jikin, tun da suka dawo kuwa Mami ta bata abubuwa sun fi a
kirga ta sha, shi yasa ko abincin dare ma bata iya ta ci da yawa ba, a haka har
bacci ya dauketa, da mafarkai iri iri na mijinta. wajen karfe sha daya sai da
khalil ya sake komawa dakin amma ya ga wayam, he felt like dying... Washegari da
safe ya shigo bangaren Mami, jiya da damuwa ya kwanta don ko baccin kirki bai iya
yayi ba, he just can't endure it any longer shi dai kawai a basa matarsa su bar
gidan nan, Bayan ya gaida Mami yayi shiru ya ma rasa me zai ce mata, Wayar Mami ya
fara ring ganin Janar ke kiranta ta mike ta fita daga parlon zuwa ɓangarensa, a
hankali ya mike ya nufi Bedroom dinta don tun da ya shigo kamshin Nihad na jiya
kawai yake ji a parlon, babu kowa dakin kawai ya juya ya fice daga bangaren rai
bace, don kafin ya shigo sai da ya fara shiga guess room nan ma babu kowa ciki, har
dakin Mimi ya shiga yaga ba kowa, kawai ya nufi dakin Noor ko amsa gaisuwarta bai
yi ba yace "Ina su Mimi?" Tace "Mami ta sa driver ya fita da su not too long" Kasa
cewa komai yayi, can ya juya fuu ya bar bakin kofar ya koma dakinsa, makullin mota
kawai ya dauka ya bar gidan ko zae samu relieve din walakancin nan da ake masa....
Mami na zaune parlon janar bayan ya sanar mata dalilin da yasa ya kirata har ya
bata takardan ta duba, cike da murna tace "Alhamdulillah, what a good news, Naji
dadin wannan lamarin wallahi, dama kai ne kawai ka sa kokwanto a zuciyarka tun
farko, amma ni har ga Allah naji a raina ba haka bane, to maa sha Allah tunda yanzu
zaka kauda zargi a ranka" Janar ya nisa yace "Abokina da ke kaduna will be coming
back together with her tomorrow don akwai jirgin sojoji da zai taho nan Abuja" Mami
tace "Toh Allah ya kai mu" Bata jima a parlon ba don ta bar wayarta a parlonta kuma
za a kawo mata turarrukan wuta da tayi order jiya da daddare, har ranta tayi farin
cikin kasancewar Hanan er Janar she is so happy with this good news. Sai kusan
azahar su Nihad suka dawo tare da Mimi glowing din yau har ya fi na jiya, gyara ne
na gaske aka mata wanda da zaka ji kudin da aka kashe zaka rike baki, bayan sun yi
wanka sun ci abinci Mami tace "Kin kira mum dinki yau?" Nihad tace "Ehh mun yi
magana da ita" Mami tace "Good, ki hada duk kayanki dake nan, zuwa da yamma za ku
koma can gidanku..." Nihad dai tayi shiru bata ce komai ba, Mimi ce ta hada mata
kayan nata duk a akwati biyu, bayan la'asar Mami ta sa ta taje tayi wanka ta shirya
cikin riga da skirt na atamfa da mayafinsa, sannan ta bata sauran magungunan nata
da suka rage ta sakata ta shanyesu tas, Ganin normal dankunne ne a kunnenta ta bata
na gold ta saka, Suna daki Khalil ya shigo parlon ta dalilin kiransa da Mami tayi
almost 2 hours ago, Mami ta fito ta gansa zaune, ya gaisheta can ciki ciki, Mami na
lura da yanda ya wani tamke fuska ta ci gaba da harkokin gabanta a parlon, can dai
yace "Gani Mami" Mami ta kirawo Nihad, Nihad ta fito parlon ta duka jikin kujera
tace "Gani" Mami tace "Fito da kayan naki ku wuce" Khalil ya daga kai ya kalli Mami
da sauri yana son sake tabbatar da abinda tace, Nihad dai bata ce komai ba kuma
bata dago kanta ba, Mami tace "Ko kuma bari in kira Mimi ta kai maki kayan mota" Ta
dau wayarta kan kujera tayi dialing number Mimi ta ce ta zo ita da Bilkisu su fitar
da kayan Nihad zuwa mota, Mikewa Nihad tayi a hankali ta koma dakin, Khalil ya ɗan
kalli Mami sai kuma ya mike ya nufi kofar dakin yana kallon Nihad yace "Ina kayan?"
Ta kallesa da sauri, shi yayi abun amma ita ta tayasa jin kunyan, tayi narai narai
da ido tana kallonsa kamar zata yi kuka, ko a jikinsa ya karaso ya dau duk akwatin
biyun ya fita, Mimi da Bilkisu na shigowa turarrukan wutan da Mami tayi order ma
Nihad suka dinga fitarwa zuwa motarsa, turarrukan wuta ne masu shegen tsada, da na
tsugunno, kwallacham, Humra, miski, infact duk wani abun kamshi dai da mace zata
bukata, Nihad dai na jikin kujera kanta a kasa, Mami tace "Toh Allah Ubangiji ya
baku zaman lafiya Nihad, ki kula da tsaftar jikinki da na gidanki... sannan kuma
kiyi hakuri ki zauna lafiya da mijinki kin ji?" Cikin sanyin murya Nihad tace
"Nagode Mami, Allah ya kara girma" Mami tayi mata murmushi tace "Ameen" Khalil ya
shigo parlon ya shafa kai yana kallon Mami yace "Za mu tafi Mami" Taɓe baki Mami
tayi tace "Allah ya tsare" Daga haka ta nufi dakinta tana kallon Nihad tace "Toh
tashi ku je, Allah ya kiyaye hanya" Nihad da har hawaye ya cika idonta ta mike a
hankali tace "Nagode Mami" Yana gaba tana biye da shi suka fito babban compound din
gidan, Mimi na tsaye har suka bar compound din tana daga masu hannu, sai bayan da
suka bar anguwan ya kalli Nihad dake share kwallar da yaki tsaya mata, ya gyada kai
yace "Na gasken zaki yi anjima, wannan ai ba kuka kike ba" Ta ɗan kallesa cike da
shagwaba tace "Toh ina ruwanka da kukana" Er dariya yayi yace "Kin ga kuwa Anjima
ai da ruwana da kukanki tunda ni zan sa ki"
*Toh a dai yi kokari a sauke hakki, idan baki sauke a nan ba to ban san kuma inda
zaki je ki sauke ba, cause my book is not free*

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788*💖 NIHAAD 💖*

*79*

Har suka kusa gida Nihad bata ce masa komai ba don tayi nisa duniyar tunanin da ta
tafi, da ta tuna Khalil is getting married soon sai taji gabanta ya fadi sosai,
amma idan ta duba yanda ta tsallake many challenges a rayuwarta sai taga wannan din
ma she will scale through it, Allah zai tsallakar da ita, amma fa in ta tuna wannan
challenge din is for ever sai taji duk jikinta yayi sanyi, may be Allah bai rubuta
zata ji dadi tayi farin ciki a rayuwarta ba, daga wannan sai wannan, ba a wata daya
sai taga sabon jarabawa, but Alhamdulillah for everything, ya ɗan kalleta yace
"Baby we need to get some foodstuffs" Ta juya ta kallesa a hankali tace "Ohk" wani
shopping mall ya tsaya suka shiga ciki a tare, siyayya suka yi sosai na kayan
abinci da kayan shayi, sae varieties of drinks, duk dai wani abu da yasan za a
bukata a gida sai da ya siya, ta zabi spices iri iri na girki, bayan yayi payment
aka kai masu kayan gaba daya bayan booth din motarsa, ana kiran sallan magrib suka
bar haraban mall din, still kafin su karasa gida sai da ya tsaya wani eatry ya siya
masu abinci da drink. karfe goma saura Nihad ta fito daga wanka kenan ya shigo
dakin da turarrukan wuta da Mami ta yi mata, ya ajiye mata su a kasa yana kallonta
yace "Kin kunna heatern bandakin ne" Ta gyada masa kai tace "Na kunna" Ya nuna mata
turarrukan wutan yace "To su wa ennan ya ake yi da su?" Murmushi tayi tace "Ci ake"
Ya zaro ido yana kallonta, tace "Zaka ce baka san turaren wuta ba?" Ya shafa kansa
yace "Can u pls make me a cup of tea after dressing up ki kawo min daki?" Tace
"Ohk" Juyawa yayi ya fita daga dakin, sai da ta gama shafe shafenta, kafin kace me
kamshi ya cika dakinta, ta dau kayan baccinta ta saka sannan ta dau Hijab har kasa
ta sa ta fito daga dakin, a tunaninta zata gansa downstairs zaune parlor amma bata
gansa ba, ta wuce kitchen kawai ta daura masa ruwan shayin, bayan ta gama ta wuce
sama da shayin, tana tsaye jikin kofarsa tayi knocking a hankali tare da sallama
sannan ta bude kofar, tsaye ta gansa a dakin with short alamar he just took his
bath too, banda kamshi me dadi babu abinda dakin yake ga sanyin Ac da har yayi yawa
a dakin, bata karasa ciki ba murya can kasa tace "Ga shayin na gama" without
looking at her yace "You can come in" Ta turo masa baki tace "Ni ban gama abinda
nake yi ba fa" Ya buda ido sosai yana kallonta yace "Idan kin ajiye ba sai ki wuce
ki ci gaba da abinda kike yi ba, i am not stopping you Love" Shiru tayi na few
seconds sai kuma ta karasa ciki a hankali ta tafi har bedside drawer ta ajiye cup
din shayin, sai kuma ta saci kallonsa taga kallonta yake, zata nufi kofa yayi
saurin jawota ya matseta jikinsa yace "Ni kika ce ma cin turaren wuta ake yi ko?"
Ta marairaice masa tana shigewa jikinsa tace "Toh kai baka san wasa ba, ni fa da
wasa na gaya maka haka" Ya cire mata Hijab din jikinta murya can kasa yace "Noo,
ban san sa ba, you have to tell me how i will start eating it when it's not
you...." Kawai gani tayi ya kashe switch din dakin, ya dauketa cak sai kan big bed
dinsa, rungumesa tayi ta fara masa kukan shagwaba tana cewa "Ni dai a'a pls" Nan ta
kara birkita mutumin.... Da asuba a nan dakin suka yi sallah tare saboda ruwan da
aka fara tun karfe hudu saura har zuwa lokacin sallah bai tsaya ba, bayan sun idar
ya juya yana kallonta taki barin su hada ido, murya can kasa yace "Good morning
Heart" ta sunkuyar da kanta bata ce masa komai ba, yayi murmushi ya dawo kusa da
ita a hankali ya dago kanta yana kallon idonta da ya kumbura, nan da nan hawaye ya
cika idonta, lokaci daya jikinsa yayi sanyi ya jawota jikinsa a hankali yace "I am
sorry wife, i am very sorry" Ita dai bata ce komai ba sai hawaye da take tana
shessheka a hankali, dagota yayi ya kwantar da ita saman gadon ya ja mata duvet don
garin yayi sanyin sosai, ya zauna gefenta yace "Get some sleep" Yana ta zaune gefen
nata har yaga ta fara bacci wajen karfe shidda, ya sauke ajiyar zuciya sannan ya
sauka daga kan gadon ya dauke pray mat din da suka yi sallah yayi folding dinsa.
Har da safe karfe takwas bata tashi ba, ya dau makullin motarsa ya fita zuwa
pharmacy don siyo mata magani ya dawo gida, ko da ya shiga dakinsa bai ganta a ciki
ba, ya fita zuwa dakinta jin wanka take a bandaki ya zauna dakin ya jira har ta
fito, suna hada ido ta sunkuyar da kanta ta karaso kan gadon ta kwanta ta lulluba
da duvet don sanyin take ji, ya koma kusa da ita yace "Maran ya daina ciwo gaba
daya?" Ta kallesa ta gyada masa kai, ya dagota yace "I can also make u warm not
only duvet" Yana fadin haka ya lullubesu da duvet din gaba daya yana rungume da
ita, kamshinsa yasa taji warmth din, ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace
"But.... did you know i love you?" Lumshe ido tayi, shi ma yayi hakan yana jin
sabon sonta na fizgarsa yace "Ina sonki, ina sonki my wife, fiye da yanda ni kaina
nake zato... I want to be with u till death do us apart....." As if whispering tace
"Me too, i love u" Kissing dinta ya fara yi, duk da tsoronsa da ya cika zuciyarta
amma bata hanasa ba, kuma daga karshe sai da tayi da ta sanin da bata hanasa din
ba, haushinsa da taji na yanzu yafi na jiya da daddare, ya gaji da lallashinta
ganin kamar tunzurata yake kara yi kawai yayi shiru ya kyaleta yana kallonta. Sai
da ya sauko downstairs ya kalli agogo yaga har sha daya saura minti biyar, ya tafi
kitchen ya hada mata shayi don shi kam babu abinda ya iya bayan wannan, ya kusa
minti daya tsaye bakin kofar dakin ya kasa shiga kamar dai yana shakkarta, daga
karshe dai ya tura kofar a hankali, durkushe ya ganta jikin gadon, ya karasa ciki
da sauri ya ajiye shayin yace "Are you okay?" Cikin kuka tace "It's paining me" Ya
dagota ya zaunar da ita gefen gadon yace "I am sorry dear, pls ki sha Shayin ga
magani na siyo maki nan" Da kyar ya lallabata ta sha shayin ƙadan sannan ya bata
maganin da ya siyo mata daxu ta sha, tayi ta juye juye har kusan 12 kafin bacci ya
dauketa, ya mike ya fita daga dakin zuwa nasa. Karfe uku na yamma bayan ya sa ta ci
abincin da ya siyo mata ya sauko downstairs tare da ita, gaba daya baya jin dadin
ganinta cikin yanayin da take ciki yanzu, and he promise him self zai kyaleta har
sai ya gano cause of ciwon maran nata, ta zauna kan kujera tana kallon tv dake
aiki, yayi kasa da murya yace "U are angry at me ko?" Taki ce masa komai, ya zauna
gefenta yace "Kiyi hakuri plss ba laifina bane Baby" Ta wani kallesa, murmushi yayi
ya ja hancinta yace "To mu je kiyi strolling compound for some minutes, you will
feel better" Bai jira cewarta ba ya dagota suka fita daga parlon, yace "kin taɓa
zaga Backyard din gidan nan kin ga flowers da na shuka maki kuwa?" Ta girgiza masa
kai, yace "Ohk now, zan rufe idonki in kai ki har wajen and u chose the best flower
da kika fi so, da kaina zan dinga watering din maki shi, sauran kuma masu aiki su
dinga yi" Ta ɗan buda ido tace "Toh idan naje na fadi kasa fa?" Tun da garin Allah
ya waye sai yanxu ta bude baki tayi masa magana, yaji dadin haka yace "Ta ya zaki
fadi bayan ga mijinki, ain't u secured when with me?" Ita dai bata ce komai ba,
bayan sun sauka matakalan bakin entrance din gidan ya zaga ta bayanta ya tsaya ya
rufe mata idonta a hankali da hannunsa, sannan ta tafiya a hankali yayi leading
dinta har zuwa Backyard din gidan, ita dai tafiya kawai take amma a tsorace gani
take kamar xata ji ta kume kanta da bango ko ta ci tuntube da wani abu ta fadi, sai
da suka kusa wajen yace "Now, let's stop here baby" Ita dai bata ce masa komai ba,
taga ya zame hannunsa a hankali daga idonta, ta gwale ido tana neman flowers din,
duk da akwai flowers din masu kyau a wajen amma idonta bai sauka kan komai ba sai
kan cages har hudu dake wajen.... Juyawa tayi da sauri ta kallesa, ya wara mata ido
yace "Hope za a janye Allah ya isan yanzu ko?" She was speechless, can kawai ta
karasa inda cages din suke tana kallon kyawawan colourful birds dake ciki, wa enda
ma suka fi nata tsada da kyau, ai kawai sai ta juya ta koma da gudy ta rungumesa
tightly cike da farin ciki tace "Waoww wllh i love them so much, naji dadi sosai,
are they for me pls?" Murya can kasa yace "Kin janye Allah ya isan yanzu?" Ta daga
kai tana kallonsa da sauri kamar me son gano wani abu, zaro ido tayi ta koma baya
hade da dafe kirji tace "Dama kai ne ka sakar min tsuntsaye na a gidanmu??" Ya
karyar da kai yace "Ai ban san naki bane na zata na makota ne" Kawai sai ta fashe
da dariya har da kyakyatawa ta durkusa wajen, ya dinga kallonta yana murmushi har
cikin ransa yaji dadin dariyar nan nata, tayi dariyarta me isarta, ta mike tsaye ya
jawota jikinsa murya can kasa yace "I love u so much dear" Ta kwantar da kanta
kirjinsa tana murmushi ta lumshe ido a hankali tace "I love you more Hubby" Yace
"Kin yafe min yanzu?" Tace "Baka min komai ba my dear, instead ni ce nayi maka" Tun
daga ganin birds din nan Nihad ta dawo lively suka zaga gaba daya gidan da ita tana
gaya masa how beautiful everywhere looks, sun kusa awa daya a compound din sannan
suka shiga ciki shi ma saboda la'asar da ake kira, yayi alwala ya fita xuwa
masallaci ita ma tayi sallan sannan ta shiga kitchen, tunanin abinda zata girka ta
shiga yi, cause she don't want him to be spending money buying food outside, cous
cous tayi deciding ta hada masu with sauce, ko da ya dawo masallaci ya ganta a
kitchen he was so surprise, shi fa kawai ya siya kayan abinci ne saboda ya kamata
ya siya amma ba wai don yasa ran ta iya girki ba balle ta girka masu, bai gama
kwasan mamaki ba sai da ta gama girkin wajen biyar da rabi ta zubo masu a tare, shi
dai yasan da baya gidan bazai taɓa yarda Nihad ce tayi girkin ba ko duk jikinsa
kunnuwa ne, wallahi yayi mamaki sosai, he never expect such taste from her food,
sai yake jin kamar Maminsa ce ma tayi girkin tsabar dadinsa, ita bata wani ci da
yawa ba amma shi kam ya ci har sai da ya kusa cinyewa, ya jawota kusa da shi yayi
mata whisper a kunnenta, turo baki tayi ta rufe fuskarta a jikinsa don maganar tasa
ya bata kunya, Yayi kasa
da murya yace "Amma fa kin fi abincin by far....." Suna ta zaune parlorn har aka
kira magrib ya tafi masallaci ita kuma ta dau plate din abincin ta kai kitchen,
basu taɓa zama su yi hira da Khalil ba sai ranan, they gisted about so many things
har kusan karfe goma da rabi, daga karshe ya sa suka tafi bandaki suka yi wanka a
dakinsa, ta gama shirin kwanciyarta ta kwanta saman gadon tayi lamo, bayan ya
shirya shi ma ya kwanta kusa da ita, banda faduwa babu abinda gabanta yake, ya
rungumeta ya kashe wutan dakin murya can kasa yace "Maran yayi sauki yanzu ko?"
Tayi shiru bata ce komai ba don tun bayan da ta fara shan maganin bata jin ciwon
kuma, duk iya daurewan da ya so yayi ya kauda kansa daga gareta yayi bacci amma ya
kasa, sai juye juye yake amma bai yi attempting komai ba, can dai ta dago kanta a
hankali tace "Are you okay?" Ya kasa ci gaba da daurewa kamar me rada yace
"Plss.... I..." Sai kuma yayi shiru, rubbing his chest a hankali tace "You what?"
Shkkn ta kara rikita al'amarin, she didn't stop him ta daure duk da condition din
nata, ganin she couldn't hold it anymore daga karshe ta fara masa kuka, amma ya
kasa kyaleta, daga karshe kuma ya dawo yana bata hakuri, bai yi baccin da yake ji
ba sai da ya tabbatar she is okay, ya jira har tayi bacci kafin yayi baccin shi ma
with sweet dreams of her. Tun da ya dawo masallaci sallan asuba basu koma bacci ba,
tana jikinsa yana danna waya a hankali yace "Amma ya kike jin ciwon maran naki
yanzu? Let me see if i should get another medicine for you" Ta girgiza kai tace "Ba
kamar na shekaranjiya bane ciwon" Yace "Na jiya fa?" Tace "It stopped immediately"
Yace "Kuma bai maki cikin dare ba?" Ta gyada masa kai, ya shafa gashinta yace
"Alright love, we will be traveling to Zanzibar hope u will welcome this idea, sai
mu yi like 3 weeks a can...." Nihad ta daga kai ta kallesa, yayi mata murmushi yace
"I promise u will love it there wife" A hankali tace "May be some other time, kaga
Abbana bai yi 40 days ba, sannan kuma ina son inyi settle down a nan so i can rest
and practice my duties as a housewife, i am tired of going from one places to
another, i will love to stay here for sometime..." Cikin sanyin murya yace "Haka
ne, shikenan anytime u feel like wanting to go for holidays u can let me know pls"
A hankali tace "Ohk and one more thing pls" Yana kallonta yace "I am all ears
sweetheart" Bata yarda yaga hawayen da ya taru idonta ba cikin sanyin murya tace "I
know u will be getting married soon, nasan ita budurwar ka ce warce ku ke tare tun
ba yanzu ba, ni kuma Abbana ne yayi mana aure da kai It's not as if i am ur choice
or u had the intention of marrying me, so pls i am begging for Allah's sake, do not
use my past mistakes against me, that might affect me mentally, i have already gone
through a lot in life do not break my heart pls I can't endure it, sannan don Allah
kar kace zaka hada mu gida daya ina rokon ka don Allah, i am saying this because i
know u can afford it...." Bai ce mata komai ba yana jin yanda hawayenta ke sauka a
jikinsa, ya rungumeta ya lumshe ido yana patting bayanta a hankali... Da yammacin
ranan Khalil ya san Nadeeyah zata zo gidan yi ma Nihad gaisuwa but ya rasa ta yanda
zai gaya mata cause shi yanzu da ranta ya baci gwara nasa ya ɓaci sau dubu, har dai
Noor da Nadeeyah suka iso gidan bai sanar mata ba, sai bayan da ya gaisa da su a
parlor sannan ya haura sama zuwa dakinta, kayanta ya sameta take gyarawa a press,
ya zauna gefen gado yace "Su Noor sun zo" Nihad na kallonsa tace "With Mimi?" Ya
girgiza kai kawai, sai kuma dai a hankali yace "With Nadeeyah" Sosai taji gabanta
ya fadi tayi shiru tana kallonsa, yayi kasa da murya yace "Gaisuwa ta zo maki ba
wani abu ba, don Allah idan kin fito kar ki nuna mata komai Baby, Nadeeyah is a
very nice gal, bata da matsala and kinga sai Allah ya kaddara cousin dinki ce ma,
nasan kinsan haka pls behave maturedly Wife" Nihad dai bata ce masa komai ba, ya
mike yace "Kar ki bata lokaci ki fito pls" Daga haka ya juya ya fita, Hijab kawai
Nihad ta dauka ta saka don skimpy dress ne a jikinta, har ta sauko kasa gabanta
faduwa yake, bata dai yarda sun hada ido ba ta karaso cikin parlon ta xauna, Noor
tace "Good evening sis" Nihad ta kalleta tayi murmushin karfin hali tace "Sannunku
da zuwa" Nadeeyah tace "Ya karin hakuri?" Ba tare da Nihad ta kalleta ba tace
"Alhamdulillah mun gode Allah" Nadeeyah tace "Allah ya ji kansa, Allah ya gafarta
masa" Nihad tace "Ameen" Mikewa tayi at first Khalil ya zata sama zata wuce, ya bi
ta da kallon mamaki, sai kuma ya ga hanyar kitchen ta nufa, ta dauko masu ruwa da
lemo ta kawo ta ajiye masu sannan ta tafi ta debo abincin da ta girka dazu shi ma
ta ajiye masu, ya ji dadin hakan da tayi, Drinks din kawai suka sha su ma kuma basu
wani dade a gidan ba suka tafi don driver na jiransu a waje, Khalil ya bi ta har
kitchen bayan taje ajiye tray din drinks din a hankali yace "Thank you Wife" Ita
dai bata juyo ba balle tace masa komai amma Allah kadai yasan abinda take ji a
ranta, and she is trying her best not to cry.

A satin Nihad hudu a gidan Khalil ya fahimci abubuwa da yawa game da ita wanda a da
idan aka gaya masa bazai taɓa yarda ba, babban abinda ya burgesa ya kara narkar
masa zuciya game da ita shine tsaftarta, she is neat in all aspects ba kuma na
ganin ido ba, she is just neat in nature, sannan ko kaɗan bata da son jiki don
kullum take gyaran babban gidan duk da su kadai ne a ciki, bayan ta gyara dakinta
ta wanke bandaki sannan ta shiga nasa ma tayi hakan, ga kuma parlon kasa da
kitchen, a ko da yaushe cikin kamshi me kwantar da hankali da zuciya zaka samu
gidan, ya zata kawai na kwana biyu zata yi ta gaji ta watsar but sai yaga ba haka
bane ways dinta ne tsaftace waje, bata son kazanta da gaske, another sweet thing is
that she can cook varieties, tun daga abincin gargajiya, na zamani, snacks, infact
all, ba kuma wajen kowa ta koya ba sai wajen Aunty Jamila, iya girkinta na kashesa
da mamaki, he never knew she had all this qualities a baya, hakan ya kara masa
sonta sosai ba kadan ba, ganin kansa yake the luckiest on earth da Allah ya mallaka
masa ita a matsayin matarsa, he just love her dearly, wannan yasa a ko da yaushe
duk sallan da zai yi yake saka Abbanta a addu'a don he gave him a gift that he
could never have found else where, yana alfahari da ita a matsayin matarsa, duk
bayan 3 days yake zuwa gida ya gaida Mami, idan Janar na nan shi ma su gaisa, kuma
baya wuce awa daya a gidan kamar ana mintsilinsa, ko da wasa bai taɓa attempting
din kai Nihad gidan ba don yana ganin Mami zata iya rike masa ita, shi ko a yanda
yake ji yanzu yasan bazai iya rayuwa without Nihad ba, har tunani yake ta inda zai
fara adjusting idan yayi resuming aiki. A yau Inna da Aunty Jamila da daya matar
Alhaji Abubakar tare da Kamila suka iso garin Abuja da kayan lefen Nihad, Khalil
bai sanar mata zuwansu ba kuma shine yayi masu jagora har zuwa gidan Janar, Mota
uku suka taho da, daya na Farooq, sai Jeep din Alhaji Abubakar, da kuma na haya da
suka yi chattering daga motor park, duk ukun kuma kayan lefen Nihad na ciki don
akwatuna sha biyu ne, sai uban turaren wuta da Humra da Mumy tayi mata, Aunty
Jamila kuma ta taho mata da products din KMZ, Inna sai salati take a zuciyarta
ganin lafiyayyen anguwan da suka shigo duk sojoji ta ko ina, har dai suka isa gidan
Janar, Inna ta kalli Aunty Jamila tana wuri wuri da ido tace "Nan din ma duk a
cikin Najeriya yake Jamila?" Aunty Jamila tayi murmushi tace "Haba tun yaushe muka
baro Najeriya Inna" Inna tace "Ko da naji, dama tun da muka sauka kan wani rubabben
titi kafin Halilu ya isko mu nasan mun bar Najeriya na dai yi shiru ne kawai" Sosai
Mami da Hajiya Safeenah, da wata kawar Mami suka yi welcoming dinsu dama an hada
masu abinci iri iri da drinks, Sojojin suka dinga shigowa da akwatunan zuwa babban
parlon gidan, bayan an gama gaisawa an cika masu gabansu da kayan ciye ciye su Mami
suka bar parlon, Inna ta kalli Aunty Jamila tace "Sai da nace ku bari ko kala
shidda ne in saka a akwatina aka ki aka ce sai dai kala biyu, to yanxu ga irinta
nan, kun dai ga gidan nan ba irin gidan da mutum zai sa kaya daya ya wuni da shi
bane, minti nawa ne kaya ya fara tsami a jikin mutum? Ni dai wallahi Habubakar bai
kyauta min ba, kafin dare ma sai in sanye kala biyun da na taho da shi ai" Hajiya
Hauwa dai sai murmushi take, Aunty Jamila taki ce ma Inna komai, babu abinda Inna
bata taɓa a abincin da aka ajiye masu ba, wani da ta ji taste din ba irin nata bane
sai tayi maza ta mayar cikin warmer din tana gwaggwale ido, Mami ce ta shigo parlon
bayan kusan awa daya, Inna ta mike tace "Hajiya a ina zan yi wanka in canza kayan
haka kuma" Aunty Jamila ta kalli Hajiya Hauwa da ta saki baki tana kallon Inna da
mamaki, Mami na Murmushi tace "Mu je sama Baaba" Inna tace "Naga ma an tafi da
akwatin nawa can sama" Mami tace "Ehh yana can dakina" Inna aka bi bayan Mami ana
daga shoulder sai kuma ta juya da sauri tana kallo Aunty Jamila tace "Ke jamila kin
saka min sarkata da dankunne a cikin akwatin kuwa?" Aunty Jamila da tayi tagumi
tace "An sa" Da sauri ta bi bayan Mami, Kamila ta tabe baki tace "Dama ai sai da
Baffa yace kar a taho da ita, yanzu ai ga irinta nan" Khalil na ajiye su Aunty
Jamila dama gida ya koma don tun safe ya baro gidan, hankalinsa duk ya koma can,
yana shiga parlon kamshin turaren da ya doki hancinsa sai da ya sa shi zaunawa a
parlon for some minutes yana bin ko ina da kallo, can ya mike jin alamar tana
kitchen, ya shiga kitchen din miyar vegetable ya sameta ta gama hadawa, tuwon ma ta
gama, rungumeta yayi ta baya yace "Baby wannan wani irin turaren wuta ne kika sa
haka a gidan nan? Yafi ko wanne dadin kamshi" Tayi murmushi tace "Tohm tunda shi ma
turaren wutan sai kayi santinsa to wata neighbor dinmu ce ta shigo ta kawo min
dazu, tace min ordering dinsa tayi...." Ya wara ido yace "I bet from dubai, or...
Saudi??" Dariya Nihad tayi tace "Aa fa a nan ne, A *Albaita-Al-sahal* tace min tayi
ordering turaren" Yace "Then we will order ours too" Ta kashe gas din tace "Sure"
Juyo da ita yayi yana kallonta yace "Guess what baby?" Tayi shiru tana kallonsa
tace "What?" Yace "Da farko dai Abdallah yana hannun hukuma yanzu haka, after
beaten blue black by soldiers.... That's my papa's handwork, and since he is
involve in sha Allah nasan dole za a hukuntasa yanda ya kamata" Nihad da farin ciki
ya cikata tace "Alhamdulillah, am so happy to hear this, maa sha Allah" For just a
week now aka fara neman Abdallah bayan Khalil ya buda ma Janar abinda yayi, at
first ya ki gaya ma Janar cause bai san ta yanda zai yi viewing issue din ba, kada
ace duk gidan kuma basu da kamun kai ne, but sanin Janar na saka baki duk inda
Abdallah yake dole sai an lalubosa a kasar, shine kawai dai yayi shahada ya sanar
masa duk abinda ya faru though yasan Abbansa baya tunani negatively, Janar yaji
tausayin Nihal sosai kuma yayi alkawarin za a hukunta Abdallah yanda ya kamata, ko
sati daya bai yi da gaya ma Janar ba sai ga Abdallah a garin gombe an kamosa har
zuwa garin Abuja bayan ya ci duka a hannun sojoji, Khalil yace "Ko da yake bazan
gaya maki na biyun ba, zaki gani ne kawai da idonki" Bai jira cewarta ba ya ja ta
suka bar kitchen din ya tafi sama da ita yace "I am pressed Baby" Nan da nan ta
hade rai ta wani turo baki.....

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

*Ina kuke maabota kamshi? To Ku matso kusa, Albait Al Sahal sunzo muku da hadaddun
turarukan wuta na gida, ma jiki da kuma kaya. Akwai perfumed body oils masu dadin
kamshi da sanyaya zuciya. Akwai spritz Wanda Ko bakiyi turaren wuta ba ya i sheki
ga yana dadewa a wuri. Maza ku garzayo Albait Al sahal domin Ku Sami naku Cikin
sauqi domin yanxu suna sales komai ya sauqaqa. Duk wacca ta siya beyi mata ba ta
dawo dashi # we trust the quality of our products# contact me via WhatsApp
09084473900**💖 NIHAAD💖*
*80*

Karfe hudu saura Khalil ya gama shiryawa ya fito dakinsa ya shiga na Nihad, kwance
ya sameta kan gado yanda ya bar ta amma idonta a rufe, ya zauna gefenta yana
kallonta, a hankali ya kamo hannunta ta bude idonta tana kallonsa, yace "How are
you feeling now?" Tace "Da sauki" Yace "Ya daina gaba daya?" Ta gyada masa kai,
yace "Anjima da magrib za mu je asibiti" Ta mike zaune tace "Ya fa daina, kuma ai
ba ko da yaushe yake min ciwon ba" Yace "No sweetheart, we need to go to the
hospital to know the cause of the pain" Shiru tayi bata ce komai ba, ya kai hannu
lower abdomen dinta, for almost 1 minutes bai cire hannunsa a wajen ba as if
feeling something, ita dai kallonsa kawai take, can ya daga kai ya kalleta, a
hankali tace "Ai ya daina ciwon gaba daya yanzu" Bai ce mata komai ba, bayan some
minutes ya mike yace "Anjima da daddare za mu je asibiti" Tace "Fita zaka yi
yanzu?" Yace "Yeah, amma bazan dade ba zan dawo" Ta mike zaune zata sauka daga kan
gadon tace "Toh bari in kawo maka abinci" Yace "Sai na dawo zan ci" Tace "Toh amma
baka ci komai ba fa" Ya ɗan kalleta sai kuma murya can kasa yace "Bayan na dazu?"
Ta ɗan buda ido tana kallonsa, sai kuma tayi murmushi a hankali tace "Allah ya
tsare Dear" Yayi pecking lips dinta yace "Ameen Baby" Sauka tayi daga saman gadon
ta rakasa har parking space, sai da ya bar gidan sannan ta koma ciki. Nihad na
zaune parlon sama tana waya da Nihal wanda sun fi 40 minutes suna wayan, kuma duk
labarin Ayman take bata, kwana daddaya ne basa waya kuma Nihal bata boye ma er uwar
tata komai akan relationship dinta da Ayman, tun bayan dawowar Nihad Abuja take
amfani da wayarta frequently bata kuma sake kashewa ba saboda Mumy da Nihal sai
yaya Farooq da suke yawan waya shi ma, babu ranan da zai wuce bata kira Mumy sau
biyu ko sau uku ba, ko yau ma sun yi waya da Mumyn amma bata sanar mata su Aunty
Jamila na Abuja ba, Jin shigowar motar Khalil tayi ma Nihal sallama ta ajiye wayar
tana kallon agogo dake nuna karfe biyar da yan mintuna, ko awa daya bai yi da fita
ba ya dawo, downstairs ta sauko ta tafi kitchen don saka masa abinci kafin ya shigo
cikin parlon, tana cikin hada masa abincin sai ga shi ya shigo kitchen din ya kulle
kofar yana kallonta daga sama har kasa saboda kananun kaya ne a jikinta yace "Kin
yi baƙi fa a parlor" Ta ɗan buda ido tace "Baƙi? Su waye?" Yace "Idan kin fito zaki
gansu...." Tace "Plss hijab dina a sama" Yace "Ohk, let me get you" duba tuwon da
ya rage tayi taga babu yawa, sai ga shi ya dawo ya mika mata Hijab din, Tace "Su
nawa ne?" Ya ɗan juya ido yace "Just 4" a hankali tace "Abincin ba shi da yawa
balle in basu, sai dai drinks" Yace "Ki hada masu har nawa ki basu" Ta zaro ido
tace "Sai kai kaci me?" Yace "Zan hakura in sha tea" Tace "Aa wallahi, kawai mu bar
su haka" Dariya yayi yace "Toh shikenan mu je" Ita ta fara fitowa daga kitchen din
ya bi bayanta, Still tayi a parlon tana kallon wa enda ke zaune da mugun mamaki, ta
wani doka uban kara da gudu ta tafi ta rungume Aunty Jamila cike da farin cikin
ganinta tace "Aunty yaushe ku ka zo?? Nobody told me u people are coming wllh" Ta
gefen ido Inna da ta hakikance a kan kujera take kallonta, Aunty Jamila na murmushi
tace "Ni dai daga ni... Ba gashi kin ganmu ba ko da ba a gaya maki mun zo ba" Nihad
ta rasa inda zata sa kanwar mum dinta don farin ciki, can tace "Don Allah Aunty me
yasa baku ce min za ku zo ba in maku special girki, kuma mun yi waya da Mumy ma
bata gaya min ba" Inna sai girgiza kafa take a parlon, Kamila kuwa sai kallon Nihad
take ganin yanda ta wani cicciko sannan tayi wani mugun haske tayi kyau kamar ba
ita ba, gaba daya Kamila ta kasa daina kallonta, kai kana ganinta kasan ta samu
kwanciyar hankali over, Aunty Jamila tayi kasa da murya tana tura Nihad da ta daura
hannunta saman cinyarta tace "Wai baki da hankali ne, baki ga su Inna ba?? Baza ki
je ki gaishesu ba" Da sauri Nihad ta juya sai kuma ta mike da gudu cike da farin
ciki ta nufi Inna da nufin rungumeta, Inna ta daga mata hannu da sauri ta dakatar
da ita ta tsuke fuska tace "Aaa, gaskiya har yanzu ban gama dawowa dai dai daga
wujijjigar mota ba, dama in za mu koma ma ai sai dai Jirgi, koma gun Jamila ai ita
kadai kika sani" Nihad ta turo mata baki ta tafi wajen Hajiya Hauwa ta durkusa
gabanta ta gaisheta da murmushi fuskarta, Hajiya Hauwa ta amsa tace "Fatan mun same
ku lafiya Nihad?" Nihad tace "Alhmdlh Ummi, ya su Billy?" Hajiya Hauwa tace "Duk
suna gaisheki" Nihad ta kalli Kamila da ta mayar da ita TV sai bin ta take da kallo
ganin har da wani hips da Butt tayi, Nihad tace "Aunty ina wuni" Kamila ta sauke
boyayyen ajiyar zuciya tace "Lafiya lau Nihad, ya gida?" Nihad ta sunkuyar da kanta
tace "Alhamdulillah, ya su Umma" Kamila tace "Lafiya lau, duk suna gaisheku" Mikewa
Nihad tayi ta koma kitchen da sauri duk suka bi ta da kallo, Inna tace "Tunda mun
zo mun ga gida har mun gaisa to a zo gaskiya a maida mu inda aka dauko mu, na fi
gane ma can" Aunty Jamila ta kalli Inna tace "Don girman Allah ki rufa mana asiri
Inna, duk wannan abinda kike yi wllhi bashi da amfani" Inna tace "Kar ki gaya min
maganar banza Jamila, banda marigayi da ya haifi Nihad din har ya aura mata Halilu
a gidan ubanwa za ku hadu da wannan daular har ku bar duniya? Ta dalilin jikata ce
fa har ku ka samu matsayin barin Najeriya, to ahir kar ki kawo min raini" Ita dai
Hajiya Hauwa ta ja bakinta tayi shiru, Kamila tace "Ai gaskiya Aunty Jamila ta
fada, mu dai ba duk inda aka bamu masauki nan za mu zauna ba, ina mu ina zabar inda
za mu zauna" Inna tace "Toh wallahi sai na zaba na darje, kuma ban ga masaukin da
zan zauna da ya wuce gidan Janar ba, banda lalacewa ina matsayin kaka ina ni ina
zama gidan yara? Kuma ai inda muka fara sauka nan ne masaukinmu a shari'ance ma,
kawai kawai ku yi ta abu ba wayewa kamar kauyawa, maimakon ku yi komai kanku tsaye
irin na wayayyu" Kamila tace "Ga ki ga gidan Janar din ai sai ki bi hanya ki koma"
Inna ta kunduma mata zagi tace "Dama na ji takaicin taho da ke da aka yi kawai na
ja bakina ne nayi shiru bance komai ba, amma banyi farin cikin biyomu da kika yi ba
wllh" Hajiya Hauwa tayi kasa da murya tace "Don girman Allah a bar maganar nan
Inna, gidan surki ne fa" Inna na huci tace "Toh nayi shiru" Nihad na shiga kitchen
taga Khalil ya cika masu tray da ruwa da lemo, tace "Yauwa my dear" Yace "Yanzu za
a basu abincin ko baza a basu ba?" Dariya tayi taki ce masa komai ta dau tray din
ta fita, ta kai masu parlor, ita dai Inna duk hankalinta yayi gidan Janar, kafin
Nihad ta koma kitchen din har ya sa masu abincin a plate, yace "Zan ɗan fita in
siyo abu yanzu, sai ki zaga da su gidan idan suka gama cin abincin" Nihad tace
"Toh" Daga haka ta dau abincin ta kai masu parlon, Khalil ya fito shi ma yace masu
yana zuwa sannan ya bar gidan, Duk yanda Nihad tayi da su Aunty Jamila su ci
abincin kin ci suka yi, wai sun ci abinci kafin su fito, Inna dai ta nemi plate ta
saka rabin tuwon da miyar vegetable ta debi isasshen nama ta zuba lemo a cup, Aunty
Jamila ta kyabe baki ta dauke kai, Nihad ta mika tace "Aunty mu je sai ku ga ko
ina" Sama duk suka wuce gaba daya har da Kamila da Hajiya Hauwa, dakin Khalil ne
kadai Nihad bata shigar da su ba, amma har parlonsa ta kai su, Kamila na nuna kofar
dakin tace "Shi kuma wancan fa?" Murmushi Nihad tayi ta sunkuyar da kanta bata ce
mata komai ba, Hajiya Hauwa tayi dariya tace "Dakin mijinta ne, kuma dama bai
kamata ma mu shiga ba, maa sha Allah gida yayi kyau Nihad, Allah ya sa gidanki ne
na har abada, Ya sa ki zama tsohuwar gida" Kamila tace "Ameen" Downstairs suka
sauko ta nuna masu dakin dake kasa da bandaki, sannan kitchen, dama dining area din
is open kuma sun gani, Sosai Aunty Jamila taji dadin yanda suka samu gidan so neat,
kuma ko ina kamshi yake, da Nihad ta san da zuwansu babu abinda zai hana ta cewa
sai da taji za su zo ta gyara ko ina, amma tasan Khalil bai gaya mata ba, Duk suka
dawo parlon Inna har ta handame tuwon ta koma gefe ta zauna, Hira suke ta yi a
parlon amma Inna bata cewa komai, can dai tace "Amma fa kada magariba tayi mana a
nan Jamila ki kirasa ki ji inda yake, tafiyar magariba babu dadi wallahi" Kamila
tace "Toh wai idan nan din za mu kwana fa? Kika san yanda suka yi da mamarsa?" Inna
ta kalleta tace "Kamila kike ko Kamilu? To wllhi ki fita harkata a kasar mutane
kada in maki tijara, ina ruwanki da lamarina ne komai nace sai kin tsomo min
bakinki me wari? A garin gaɓa gaɓa aka haifemu da za mu yarda mu kwana a gidan yara
kanana? Wannan ai sai ace lalacewa ta samemu, mu wallah bama haka a al'adanmu, ku
kira min Halilun ni in masa magana da kaina" Nihad tace "Toh meye a nan din da baza
ku kwana ba Inna?" Inna tace "To ai ni ba er iskar kaka bace da zan kwana cikin
yara" Kamila tace "Toh sai a kama maki hotel kawai, mu mu kuma sai mu kwana a nan,
washegari kuma mu tafi tashar motar" Inna ta dinga kallon Kamila alamar ta ma rasa
abinda zata ce mata, can dai tace "Ni dama ban taɓa mamakin mutuwar aurenki ba,
halinki ya kashe maki aure, shi ne zaki zo ki kashe na er uwarki saboda baƙin ciki,
to da wanda ya bada shawaran a taho dake, da wanda ya daure ma shawaran taho dake
kugu, dake kanki da kika biyo mu duk Allah ya isa tsakanina da ku bam yafe ba"
Nihad ta fashe da dariya har da kyakyatawa, Kamila dai ta kyabe baki ta dauke kai,
shigowar motar Khalil gidan ya sa hankalin Inna ya kwanta, yana shigowa parlon tace
"Halilu tafiya da magariba babu dadi wallahi, naga kuma karfe shidda har ya gota"
Yace "Inna baza ku kwana a nan ba?" Tace "Haba Halilu, sai kace tabaɓɓiya, ai da
kunya in kwana a nan, ni dai a nemo min duk inda zan kwana amma banda gidan nan"
Kamila ta bude baki a ranta tace sannu Mumy, shi dai Khalil murmushi kawai yake,
Kamila tace "Toh ko a sama maki hotel Inna?" Inna ta juya da sauri tana kallon
Kamila amma ta kasa cewa komai, Aunty Jamila sai danne dariyarta take, ita kanta
Hajiya Hauwa sai murmushi take, Khalil yace "Toh kawai bari a maida ke can gidanmu
Inna" Inna ta sunkuyar
da kai tace "Toh" Aunty Jamila tace "Mu kam zaka ajiye mu a gidan Hajiya Safeenah"
Da mamaki yace "Aunty me yasa baza ku kwana a nan din ba" Ita dai inna har ta mike
ta zuge zip din jakarta ta rataya ta nufi kofa, Aunty Jamila tace "Aa mun yi da
Hajiya Safeenah za mu je can gidan nata" Yace "Ku bari sai gobe kawai Aunty" Aunty
Jamila tace "Mun fa ga gida Khalil, Allah Ubangiji ya sanya Alkhairi, ya baku zaman
lafiya, kuma goben in sha Allah da safe za mu koma" Nihad taji ba dadi ganin da
gaske baza su zauna ba tafiya za su yi, nan da nan mood dinta ya canza, tana ji
tana gani suka bar gidan ta dawo parlor tana kuka a hankali. Bayan magrib Khalil ya
dawo gidan, yana dawowa kuma ya sa ta shirya suka tafi asibiti, da yake asibitin da
yake aiki ne kafin ya samu matsala da Abbansa nan da nan suka yi attending masu,
bayan kusan awa daya da zuwansu asibitin Khalil ya shiga ward din da Nihad take
kwance tana ta game da wayarta, tun bayan da aka dubata take wajen a kwance, ta
juya tana kallonsa har ya karaso kusa da gadon ta mike zaune a hankali tace "Are
they done?" Shiru kawai yayi yana kallonta, ta kamo hannunsa tace "Kayi shiru"
Zaunawa yayi gefenta ya sakar mata murmushi drawing her closer to himself murya can
kasa yace "I love you wife" Ta lumshe ido tace "I love you too" Yace "We can go
home now" mikewa tsaye yayi ya taimaka mata ta sauko daga kan gadon sannan suka bar
asibitin. Washegari Janar ya biya ma su Aunty Jamila flight za su koma kano amma
banda Inna, Flight din karfe daya ne na rana don haka karfe sha daya da rabi Khalil
ya tafi da Nihad can gidan don tayi masu sallama, a bangaren Hajiya Amina aka masu
masauki, ganin kowa ya gama shiryawa banda Inna Nihad tace "Inna ke baki shirya
ba?" Inna ta kalleta tace "Ai ba gidan Halilu nake ba da zaki min wannan tambayar
Nihad, kuma Janar din da kansa yace in zauna in ɗan kwana biyu in kara hutawa kafin
in koma, ni da ce masa nayi aa amma ya dage, da kyar dai na amince don dai kar
mutum yace baka ji maganarsa ba" Kamila tayi dariya tace "Lallai kam" karfe sha
biyu da wani abu aka kai su Aunty Jamila Airport, Nihad taji kamar ta bi su taje
taga Mumy, haka ta dinga daga masu hannu har suka shiga airport din, sannan Khalil
ya koma can gida da ita. Dakin Mimi Nihad ta tafi, shi kuma Khalil ya tafi bangaren
Maminsa, ita kadai ya samu a parlor tana kallo ya zauna yace "Innan fa" Mami tace
"Yanzun nan ta tafi taje tayi wanka" Yace "Ohk" Tace "Yanzu yau za ku tafi da kayan
nata gida?" khalil yayi shiru sai kuma yace "A dai bari ko zuwa gobe Mami" Mami
tace "Allah ya kai mu" Yace "Kwana biyu ma bata jin dadi tana lower abdominal pain"
Mami tace "Subhanallahi to dubata kayi ko asibiti ka kai ta?" Yace "Jiya da daddare
muka je asibiti, an yi mata Ultrasound sound scan and they found out she is 3
months pregnant" Mami ta dinga kallonsa with confusion, tace "Pregnant kuma?" Yace
"Yeah, i think she miscarried just one baby, dayan na nan" Mami da ta kasa rufe
baki tace "Ikon Allah, kai kuma kana matsayin likita duk baka ga hakan ba sai da ku
ka je asibiti?" Ya ɗan yi murmushi yana shafa kansa yace "Ni sai jiya naga symptom
shi yasa ma na kai ta asibiti amma ban taɓa lura ba" Mami tace "Toh Allah Ubangiji
ya raya mata wannan, Allah ya kara mata lafiya, maa sha Allah" Yace "Ameen" Mami
tace "Amma kuma tana cin abinci?" Yace "Tana cin komai, kuma babu aikin da bata yi,
there is nothing like sign of the pregnancy fa" Mami tace "Toh gaskiya ta rage
aikin ko ma ta bar yi gaba daya kar a samu matsala tunda kace tana ciwon mara, idan
baza ka samar mata me aiki ba sai Mimi ko Hanan suje su taya ta zama for sometimes
don a dinga taimaka mata da aikin gidan, don Noor ba wani abun kirkin da zata
taɓuka" Shi dai yayi shiru bai ce komai ba. Basu bar gidan ba sai wajen karfe
takwas na dare bayan Mami ta basu abinci su tafi da shi a warmer, Nihad har mamakin
yanda Inna ta saki jiki a gidan kamar ta taɓa zuwa take, ko aike zata yi a dauko
mata abu a bangaren Hajiya Amina sai dai tace aje bangarenta a dauka mata abu kaza,
kayanta kala biyu dama har ta jera cikin Siff, ga atamfofi kala biyar da Mami ta
bada a dinka mata don ma Mami ta bata dogayen riguna sababbi irin na Saudi.... A
kwana a tashi babu wuya wajen Allah sai ga cikin Nihad ya kai har wata biyar, Duk
watanni biyun nan Hanan na gidanta babu abinda bata mata, sai Nihad taga yanda Mimi
take haka Hanan din ma take bata da matsala kwata kwata, she is kind and nyc to be
with, a zaman Hanan tare da su kuma Hajiya Amina ta zo har sau biyu, kuma Khalil
bai taɓa nuna mata komai ba zai zauna su yi hira sosai in ta tashi tafiya kuma shi
zai kai ta tasha don a kaduna take rayuwarta, ya kuma hadata da kudi not less than
50k, Satin Inna biyu a gidan Janar aka yi mata passport suka tafi Makka tare da
Mami su yi Umra, Mami ta so tafiya da Nihad amma saboda condition dinta sai bata ma
kawo ma Janar batun ba, suna dawowa Umra kuma da yake ta kano suka sauka Mami ta
kai Inna har gida, bayan tafiyar Mami Inna har da matsar kwalla don gani take kamar
an dawo da ita wani kauye ne.... Cike da farin ciki Nihad ta gama hada kayanta kala
hudu zata Kano tare da Khalil da Hanan don yau Mumy ke fita takaba kuma a yau din
mutanen Ayman za su zo nema masa auren Nihal, tun a daren jiya suka tafi gidan
Janar suka sallami Mami, don haka karfe tara na safe suka kama hanyar airport don
jirgin karfe sha daya ne. Nihad bata damu da condition dinta ba tana shiga dakin
Mumy ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Mumy ta janyeta tace "Ke baki da
hankali ne?" Aunty Jamila da Aunty Suwaiba suka rike haɓa suna kallonta, Aunty
Suwaiba tace "Aa babu alamar hankali kam a nan Yaya" Nihad ta zame kasa tana dariya
tace "Wallahi nayi missing dinki Mumy" Sai kuma ta kalli Aunties dinta tace "Au
dukkan ku nayi miss" Murmushi kawai suka yi, nan ta gaishesu gaba daya, Hanan ta
shigo dakin da sallama duk suka amsa mata, ta durkusa saman Carpet ta gaishesu suka
amsa mata da fara'a suna tambayarta ya hanya.... Mumy na ce ma Nihad taje ta gaida
Umma bata mata musu ba ta mike ta fita zuwa bangarenta, tana shiga parlon taga ana
ta hada kaya, Ta gaida Kamila dake parlon, Kamila ta amsa tace "Kun zo lafiya?"
Nihad tace "Alhamdulillah" Sai ga Umma ta fito, Nihad ta dinga kallonta don kamar
ba ita ba ta rame sosai ba kadan ba kamar bata taɓa jiki a rayuwarta ba, Nihad ta
gaisheta, Umma ta amsa da fara'a tana tambayarta Khalil, Nihad tace "Sai anjima zai
shigo" Umma tace "Toh sannunku da zuwa" Nihad dai tayi shiru, can dai ta kasa
daurewa tace "Ina za aje da kayan?" Umma tace "Kaduna zan koma wajen yayata" Nihad
tayi shiru tana kallonta, Bayan wani lokaci cikin sanyin murya Umma tace "Toh duk
dai abinda ya faru a rayuwa rubutattce ne daga Allah, duk wayon ka da dubaranka
idan Allah ya rubuta ga kaddararka babu yanda zaka yi ka tsallake ta, sai in Allah
yayi ka me yawan ibada da addu'a sannan kuma me tsoronsa, sai ka ga Allah ya sauya
maka kaddararka mara kyau zuwa me kyau, to mu kam Allah Ubangiji ya yafe mana kura
kurenmu, ya sa mu yi tabbataccen tuba kafin mutuwa, sannan ina neman afuwanki
Nihad, ki yafe min...." Da sauri Nihad ta girgiza kai tace "Ni na yafe maki tuntuni
Umma, Allah ya sa mu dace duniya da lahira" Umma ta share hawayen da ya taru idonta
bata dai ce komai ba, babu yanda Mumy bata yi da ita kan ta zauna gidan ba amma
taki don in har ta ci gaba da zaman gidan nan tasan conscience will neva allow her
have peace of mind, a kullum sai abubuwan da suka faru a baya sun dawo mata,
memories iri iri sun ki barin ta na gidan, har inna dake koranta a baya sai da ta
sa baki ta zauna amma taki tace gwara ta koma gun yayarta kawai sai ta dinga kawo
masu ziyara, Kamila da Nihal kuwa su zauna gun Mumy, zata tafi da autarta Amina. A
ranan bayan an kawo kudin auren Nihal Umma ta shigo parlon Mumy, ta zauna saman
kujera a hankali tace "Toh Maryam, a yayyafe don Allah...." Inna dake zaune parlon
ta fashe da kuka tace "Kiyi zamanki cikin yaranki kin ki Sumayya" Umma ta girgiza
kai tace "Duk abinda zan masu nasan shi Maryam zata masu har ma fiye da yanda ni
zan masu Inna"

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788*💖 NIHAAD💖*

*81*
4 months later

Nihad ta fito bandaki Aunty Maryam na biye da ita a baya, Aunty Jamila ce tsaye
jikin press din kayanta tana duba mata kayan da zata sa, Aunty Maryam ta fita daga
dakin don dauko abu ta dawo, Aunty Jamila na juyawa taga Nihad durkushe gaban
Babynta dake kwance cikin cot dinsa sai kallonsa take babu ko kiftawa, Aunty Jamila
ta rike haɓa don bata da aiki sai kallon jaririn ko a gaban waye kuma, in ko bata
gansa ba irin anje masa wanka to sai ta bi sa, Aunty Jamila tace "Toh wai ko mayar
da yaron nan ciki za kiyi ne?" Da sauri Nihad ta bar wajen tana murmushi, Aunty
Jamila tace "Ikon Allah, Ke ko kunyar surkanki da sababbin ido bakya yi, toh kar in
sake ganin kina makale masa kina masa wannan kallon kamar zaki cinyesa, idan duk
aka watse daga yau zuwa gobe sai ki zauna daga safe har dare kina kallonsa babu me
hanaki, amma yanzu ki rufa mana asiri don Allah" Ita dai Nihad bata ce komai ba ta
sunkuyar da kanta, Aunty Jamila ta ajiye mata kayanta tace "Ta shi ki shirya, ina
Aunty Maryam take ajiye maki socks din naki?" Nihad ta nuna mata sannan ta mike ta
shirya cikin kayan da Aunty Jamila ta dauko mata, Aunty Maryam ta dawo dakin rike
da glass din ruwa da drugs dinta, tana bata ta sha ta fita da glass din, Yau kwana
sha biyar da haihuwan Nihad, a jiya kuma aka yi suna wanda za a iya cewa bikin da
ba ayi a baya bane aka samu privilege din yi yanxu, don kuwa sunan nan ya samu
halartar manya manyan kasar daga garurruka daban daban kai kace biki kawai ake, yan
yemen ma duk sun zo kwansu da kwarkwatansu don taya Mami murnan samun first
grandchild, Hajiya Safeenah dai abu nasu maganin a kwabesu, tayi kokari tayi
bajinta sosai don kaya na gani na fada ta hada ma jaririn bayan sun dawo US, Janar
ya kashe kudi me sunan kudi a sunan nan don a gidansa aka yi sunan, Nihad kuma ta
samu kudi iya kudi don kamar ba a son kudin aka dinga bata, kawayen Mami ne, Abokan
Janar, yan uwa da abokan arziki, kudi dai kam ta samu, shagali sosai aka yi a sunan
nan abinci iri iri da nama kuwa ba a cewa komai sai wanda ya gani, komai irin na
yan gayu aka yi a sunan, har Umma sai da ta zo sunan da autarta Amina ta kuma ga
abinda bata taɓa zato ba don ma dai Aunty Jamila na ta jan ta jiki duk don ta sake
ayi komai da ita kamar yanda dai matan Alhaji Abubakar suka saki jiki ana ta hidima
da su, Nihal tayi aurenta da Ayman wata daya da sati daya da suka wuce baya, wanda
Mumy na daga cikin wa enda suka kai ta har UK where Ayman is based, family dinsa
dake Uk din suka amshi Nihal hannu bibbiyu don duk abinda ɗan uwansu ke so su ma
suna so, Nihad taji takaicin rashin zuwanta bikin er uwartata saboda nauyin da tayi
a lokacin amma Su Mami da Noor da Khalil har Hajiya Safeenah da Nadeeyah duk sun
tafi, gashi har Nihal ta tafi bata san gidan Nihad na Abuja ba, don kwantar mata da
hankali Khalil yace idan ta haihu da wata uku zai kai ta har Uk din gun Nihal.
Kamila ma dai ba a bar ta a baya ba wajen zuwa suna duk da ita ma dai tana ta
shirye shiryen komawa gidan tsohon mijinta zai mayar da ita, Farooq zuwansa hudu
gidan Janar tun da Nihad ta haihu don ya dawo Abuja da aiki, Usman kuma sai ranan
sunan ya zo daga kaduna yaga Baby, ko wannensu was so happy for their lil sis, dubu
dari Usman ya bata ta siya duk abinda take so, Farooq kuma ya siya mata tsadaddun
atamfa har biyar da kayan baby iri iri, duk wanda ya ga Inna ranan sunan nan kuwa
sai yayi tunanin ita ta haifi Janar din gaba daya, Babu kayan fitan sunan da Khalil
yayi ma Nihad don Janar yayi mata yayi kala talatin a gidan kuma duk kayan da ta
saka babu na banza a ciki kaya ne masu sunan kaya, Mami ta siya mata jaka da
takalmi dai dai da kayan fitan sunanta, Aunty Maryam kuma ta siya mata jewelries
masu shegen kyau da tsada, Jaririn ma daga waje aka yi masa order din duk
kayayyakinsa banda wanda Khalil ya siya masa tun ba a haifesa ba, hakan yasa Khalil
ya siya ma Nihad dankareren dankunnen zinari da sarkansa don tana da zobuna da Mami
ke bata sun yi biyar ynxu, yaro ya ci sunan Abban Nihad za kuma a kirasa da Aaryan,
Inna kuka ta dinga yi wiwi jin sunan da aka sa ma yaron.. Tun kafin EDD din Nihad
ya cika dama suka fita US da Mami don sun bi duk process a can suke son ta haihu,
daga baya kuma Khalil ya bi su don kawai azarbabin Mami ya sa ta tafi da ita kafin
lokacin haihuwan, sai da ya dai dai ci saura few days EDD dinta sannan ya dau leave
a wajen aiki ya bi su, sun kusa kwana goma a US kafin Nihad ta haifo santalelen ɗan
nata, after 3 days bayan ta huta kuma suka juyo suka dawo Nigeria. Duk da 2 days
ago aka yi suna amma har yanzu da sauran baƙi a gidan da suka zo daga nesa. Nihad
na ganin Aunty Jamila ta fita, ta mike da sauri ta koma gun Babynta tana kallonsa,
yaron kamar ubansa yayi kaki, komai na Khalil ya dauko har hancin da bakin, the
baby is so cute and fair, with pink lips, ta durkusa kusa da shi tana kallonsa with
smile all over her face wani farin ciki na musamman take ji idan tana kallon yaron
nata, murya can kasa tace "Abbana" Yaron ya bude ido a hankali yana kallonta kamar
ya ji abinda tace, wani dadi taji har ranta har da kyalkyalewa da dariya, ta lumshe
ido ta manna masa kiss a soft cheeks dinsa tace "I love you so much" dai dai
shigowar Aunty Jamila, tsaye tayi bakin kofa tana kallonta baki bude, Nihad ta mike
ta bar wajen da sauri tana kame kame tace "Aunty na ji yana kuka ne shine na
dubasa" Aunty Jamila dai bata ce mata komai ba ta karasa cikin dakin, Nihad ta zaro
ido ganin warce ke bayan Aunty Jamila, da sauri ta tafi ta rungumeta cike da farin
cikin ganinta, Mami dake tsaye gefen Mumy tayi murmushi tana kallonsu, Mumy tace
"Menene haka Nihad? Ke baxa kiyi hankali ba har yanzu" Nihad was more than happy
seeing her mother don har ta cire ran zuwanta da ta ga har an yi suna bata zo ba,
Mumy ta dau jaririn bayan ta zauna tayi masa addu'a ta saka masa albarka sannan ta
maida shi cikin cot dinsa, Nihad dake ta kallonta tace "Wallahi nayi missing dinki
Mumy" Ita dai Mumy murmushi kawai tayi bata ce mata komai ba, Mumy bata wani dade a
gidan ba ta bi Hajiya Safeenah zuwa gidanta wai can zata kwana zuwa gobe kuma ta
koma kano, babu yanda Mami bata yi da ita a kan ta zauna gidan ba amma taki, kana
ganin reaction din Mumy kasan eh lallai jinin fulani ce... Daren ranan Mami na
guess room tare da Aunty Jamila da Aunty Maryam wanda ita ta kirasu zuwa dakin
saboda baƙin dake bangarenta kuma tana son masu magana ne, Mami tace "Jamila kin
tuna lokacin rasuwan mahaifin Nihad Janar yaje tare da wani amininsa a lokacin? Duk
da dai abokan nasa da suka je suna da yawa amma wannan idan dai ba mantawa kika yi
ba suna tare always..." Aunty Jamila tayi shiru sai kuma tace "Kamar na so in
ganesa, he is a bit fair nd tall ko?" Mami tace "Yauwa kin ganesa kuwa, to tun dai
sanda Hajiya Maryam ta fita takaba ya nuna interest dinsa na aurenta, shi ma dai
matarsa ta rasu yau shekara bakwai kenan, yaransa uku a duniya biyu maza sai mace
daya, Babban ɗan sa is 30 yanzu, me bi masa kuma is 28, kuma duk basa kasar yanzu
haka a waje suke aikinsu dukkansu, autarsa ce dai me suna Maryam she is just 17
years now kuma tana wajen matar kanin baban nata, to tun dai da ya nuna interest
dinsa bayan fitar ta takaba Janar ya sa na kira Hajiya Maryam a lokacin nayi mata
magana amma sai ta nuna ita kam ba wani auren zata yi ba tana son ta kula da
yaranta maza biyu babu aure a gabanta, sannan step children dinta ma duk a gabanta
suke ita ke rike da su, This man is also a Lieutenant General sunansa Ahmad, kuma
na tabbatar da yana da wani flaws that can't be tolerated Janar will neva take him
serious balle har ya sa nayi ma Maryam magana, to ban san ko ta maki maganar ba
this happened almost 3 months ago, kuma har yau Janar Ahmad bai hakura ba, ni kuma
gaskiya naki basa numberta don idan na basa ban san yanda zata dau hakan ba, to
zuwan da tayi gaida janar dazu ai suna tare da Janar Ahmad din a parlonsa, shine
Janar ya kirani ya sa in sake mata magana, na kuma yi mata kafin ta tafi gidan
Safeenah, but still abinda ta gaya min a baya shi ta sake maimaita min yanxu ma,
sai ban ji dadi ba da naga tana hawaye, i know it's not easy but dole life have to
go on, she have to move on, balle ma naga ita er uwar Nihad din ma ai tayi aure
bata ma kasar yanzu, ina ce ita kadai ce step daughter dinta da take rike da" Aunty
Jamila ta sauke ajiyar zuciya tace "In sha Allahu zan mata magana Aunty, ina ga can
gidan Hajiya Safeenar ma zan je in kwana duk za mu hadu mu yi mata magana" Mami
tace "Toh don Allah kiyi iya kokarinki, Janar Ahmad zai rike mata yaranta maza, he
said this tun farkon maganarsa da Janar, kuma kin ga shi ma a nan Abuja yake" Aunty
Jamila tace "In sha Allahu we will talk to her Aunty" Kamar yanda Aunty Jamila tace
gidan Hajiya Safeenah ta tafi ta kwana don yi ma yayar tata magana don tasan idan
Hajiya Safeenah ma tasa baki kilan su rinjaye ra'ayinta. Har kusan karfe biyun dare
Hajiya Safeenah bata hakura ba sai da ta cusa ma Mumy ra'ayinsu na son ta amince da
auren Janar Ahmad. Washegari duk aka gama watsewa a gidan Janar kowa ya koma
various destination dinsa, Duk yanda Mumy ta so tafiya ranan Hajiya Safeenah bata
barta ta tafi ba har sai da Janar Ahmad ya zo ya sameta a gidan. Rayuwa kenan, babu
yanda Mumy ta iya haka ta hakura da auren bayan shi kansa Janar Jikamshi ya zaunar
da ita yayi mata magana ta nutsuwa da fahimta, Inna ma ta saka baki, babu yanda
Mumy ta iya haka tayi accepting auren, a cikin sati biyu kacal aka daura mata aure
da Janar Ahmad, amma bata yarda ta tare ba sai da ta ga Kamila ta koma gidan
mijinta, Alhaji Abubakar duk shi yayi mata wasu sabbin kayan dakin don daga ita har
Umma suka siyar da tsofaffin kayanta, bayan kwana biyar da komawar Kamila gidan
mijinta, Mumy ta hada komai nata a kano ta bayar don Janar Ahmad yace mata babu
abinda babu a gidansa, a Private jet aka tafi da su Abuja ta tare da yaranta maza
biyu a Mansion din Janar Ahmad, daughter dinsa Maryam me sunan Mumy ta dawo wajen
Mumyn da zama,
dalilin rufe gidan Abba kenan aka sallami su Aminu, Isiya, Saminu da dreba, duk
aka rabu ana kuka, Aminu had nothing to loose don da taimakon Khalil ya gina
dankareren gidansa a kauyensu ke kya ce ba me gadi bane don gidan duk ya fi na yan
kauyen, sannan Khalil ya basa jarin miliyan daya ya fara kasuwancinsa a cikin garin
kano. During period din nan kuma aka sa ma Noor rana da babban ɗan Janar Ahmad dake
Turkey don dama shi ne saurayinta, as at that time Nadeeyah dake masters dinta tana
tare da wani Young Brigadier general wanda sun fi shekara biyu da sanin juna but
bata basa lokacinta ba sai yanzu and he and his family are fully prepared su je
gaida dangin Mahaifinta a Yemen, idan ba message din Khalil ta gani a WhatsApp ba
ita har mancewa take da shi a Abuja, gashi dai zumunci suke yi sosai da Nihad don a
lokacin da ta haihu kullum sai taje gidan har aka yi suna amma Khalil kam mantawa
take da shi wllh.... Sai da Nihad tayi 50 days a gidan Mami, bayan Mami ta tabbatar
tayi mata duk gyaran da ya kamata tayi mata Hajiya Safeenah da frnd din Mami suka
maida ta dakinta tare da Mimi that will be of help to her zuwa wani ɗan lokaci
saboda jego, da yammacin ranan suka bar gidan, Mimi made sure ta gyara ko ina na
gidan ta sa turaren wuta. Karfe biyar da rabi Khalil ya dawo aiki, he was so happy
to see his wife and son don bai san ranan za su dawo ba, Mami dai ta amshi spare
key din gidan nasa kusan kwana shidda da suka wuce a baya, kullum sai ya dawo aiki
yake zuwa can gidansu ganin family din nasa, kuma sai kusan karfe goma yake komawa
gidansa yau kam yana dawowa ya gansu a gidan and he was very happy, sai dai kuma
Farooq da ya gani a gidan nasa made him believe what he was thinking before, kusan
duk dare idan yaje can gidansu sai ya ga Farooq a gidan sai yanzu ya sake tabbatar
da cewa wajen Mimi yake zuwa ba Nihad ba amma sai ya fake da kamar gun er uwarsa
yake zuwa, ita kuwa Nihad tuni ta gano zuwan me Farooq yake kullum, sai bayan
magrib Farooq ya bar gidan, Mimi ta kai ma Yayan nata shayi a parlonsa kamar yanda
ya bukata, da sallama ta shiga parlon, Nihad dake zaune kusa da Khalil dake rike da
Aryaan ta amsa mata sallaman, bayan ta ajiye shayin Khalil na kallonta yace
"Wajenki farooq ke zuwa ko?" Ta wani zaro ido ta dafe kirji tace "Ni??" Dariya
kawai Nihad tayi tana kallon Mimi da ta daburce, Khalil ya jefa mata wani kallo
yace "Tafi ki bani waje with ur hypocrisy" Ta sunkuyar da kai kamar munafuka ta
juya tana murmushi ta nufi kofa. Daren ranan Khalil ya nuna ma Nihad yanda yayi
kewanta sosai, ita ma kuma tayi kewan mijin nata, she truly missed him soo much.
Washegari da ya kasance asabar Khalil baya fita aiki, wajen karfe goma na safe ya
fita shopping da Nihad leaving Mimi and little Aryaan at home, Nihad ta dau duk
wani abu da tasan za su bukata a gida, bayan ya biya kudi aka kai masu mota, tana
kokarin shiga mota taji ana kiranta, waigawa tayi taga wata mata ta nufota da sauri
fuskarta rufe da Face mask, matar na karasowa kusa da ita ta sauke Facemask din, ko
kusa Nihad bata gane ta ba, Matar tace "Nihad ni ce fa" Sai a sannan Nihad ta dau
muryarta ta zaro ido da mugun mamaki tace "Zully???" Shi dai khalil har ya bude
driver seat ya shiga yana kallonsu, Zully ta cire face mask din gaba daya tace "Ni
ce Nihad" Da mamaki Nihad tace "Me ya sameki haka? Where u sick??" Zully ta fara
kikkifta ido sai kuma ta fashe da kuka a hankali tace "Ehh wallahi na kwana biyu
bani da lafiya amma na fara samun sauki yanzu tunda gashi har ina fitowa" Nihad na
kallonta daga sama har kasa tace "Me kike yi a nan?" Zully ta sunkuyar da kanta
tayi shiru, daga sama har kasa Nihad ke ta kallonta don she look so tattered and
unkept, sae bugawa ma take, ga wani ramewa da tayi ta koma bakakirin maimakon fara
da Nihad ta santa a baya, dama can ita iyayenta talakawa ne sosai don uwarta ma a
kauye take ubanta kuma ya rasu, Naf ce dai er masu kudi a cikin su ukun, lokaci
daya jikin Nihad yayi sanyi, a hankali tace "Husnah fah?" Zully ta kara fashewa da
sabon kuka tana girgiza kai tace "Ai Allah ya mata rasuwa ko sati biyu ba ayi ba,
tayi fama da cancer ga kuma HIV daga karshe kuma rai yayi halinsa" Nihad ta dafe
kirji tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Husnah ta rasu??" Zully ta gyada
kai cikin sanyin murya tace "A gidansu ta rasu a garin kaduna don babu kudin zuwa
asibiti, kafin ta rasu ta damu tana son ganinki, kuma an je har gidan ku nemanki
amma aka tarar babu kowa a gidan an ma kulle da kwado" Hawaye na sauka idon Nihad
tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Zully ta kara fashewa da kuka sosai tace
"Don Allah ki yafe mana Nihad duk abinda ya sameki mu ne muka ja maki wallahi daga
karshe kuma sai gashi ya zame maki alkhairi, wannan video din naki Husnah ce tayi
sa amma ba da nufin ta yada shi a social media ba, lokacin da Aliyu zai turo
iyayensa gidanku Umma ta kira Husnah duk ta zuzzugata wai haka za mu sa ido ɗan
Janar guda ya zo ya aureki muna gani alhalin mu har yanzu ba mu yi aure ba duk kuma
mun girme ki, sai Husnah take ce mata ai ko me za mu ce maki baza ki ji ba don son
Aliyu ya rufe maki ido akansa har rashin mutunci kike mana a kansa, Umma tace to mu
bi maki ta karkashin kasa mana, da so tayi ma mu bi ta zuwa gidan Malamai amma ko
wacce xata kawo ɗan abinda za a ba ma malam don tace bata da kudi ita a lokacin,
shine Husnah ta tuna wannan video dinki dake wayanta wanda tayi maki sanda kika
koma hostel da zama, ranan mun je zaria mun sauka wani hotel za ayi Birthday din
wata kawar Naf, gaba dayanmu sai muka sa maki kwaya a drink dinki kin fita kiyi
waya da Abbanki, mu ma duk mun saka a namu tunda mun saba sha, wllh wllh ba don
video dinki ya tafi viral aka yi ba Nihad, mun yi sa kawai saboda nishadi, we did
it da wayar Husnah just for fun saboda yanda kika dinga reacting very drunk after
taking the juice, Da Umma ta kawo mana batun zaki yi aure ki bar mu and we are
doing nothing about it kuma ta nemi mu kawo kudi ta kai mu gidan malami sai Husnah
ta tuno da video din da tayi maki, wallahi Umma ce cause din sakin wannan video din
a social media, da mun bi ta Naf ma baza a saki Video din ba don she was against
that amma saboda son zuciya ni da Husnah sai da muka bi bloggers muka tura masu
video din duk don Aliyu yace ya fasa aurenki, don girman Allah ki yafe min Nihad,
ita dai Husnah ta rasu, ni ma dai kinga ga yanda rayuwa ta mayar da ni a yau, bani
da sauran gata a duniya mahaifiyata ma cewa tayi in koma inda na fito kar in kashe
mata aure da naje wajenta a kauyen da take, duk samarin sun gama amfani da mu sun
gujemu ga cuta mun kwaso ma kan mu, duk inda muka yi gudunmu ake yanzu, karatun ma
Naf kadai ce ta gama a cikin mu ita din ma dai da pass, tana gamawa kuma babanta ya
aura ma abokinsa me mata biyu ita..." Kuka Zully take sosai kamar ranta zai fita
kana ganinta kasan tayi nadama ainun, Khalil ya dinga kallonta fuskarsa daure yana
jin zuciyarsa na tafarfasa, Nihad ta kasa cewa komai banda hawaye babu abinda ke
sauka idonta abubuwa masu yawa na dawo mata, no wonder ta kasa gane inda aka yi
video din don in da a hotel dake garin kano ne dole zata sani, har kasa Zully ta
durkusa tace "Kiyi ma girman Allah ki yafe min Nihad, ya kai ya kawo sai ina bin
eatry da manyan malls ina baran abinda zan kai baki, duniya ta juya min baya ga
ciwo ina fama da shi kuma bazan boye maki ba wallahi nima HIV din gareni Nihad,
yanzu haka karfin hali kawai nake, da kinga inda nake kwana ma zaki san ta kare min
a rayuwa Nihad" Khalil ya kalli Nihad yace "Shigo mu tafi Baby" ta kallesa hawaye
na sauka idonta tace "Pls let help...." Wani tsawa ya daka mata wanda bai taɓa mata
irinsa ba, ba shiri tayi shiru, ya wani hade rai yace "Shigo mota nace" Zagawa tayi
ta bude motar a hankali ta shiga, Zully ta biyota da gudu tana kuka tace "Don Allah
ki ɗan taimaka min ko da kudin magani ne Nihad...." Khalil ya kulle motar ya sauke
glass yana kallonta da kyau yace "This should serve as a lesson to people with the
kind of ur heart" Yana fadin haka ya ja motarsa ya bar wajen Zully na kuka sosai
tana bin motar da kallo, Nihad dai sai share hawayen da yaki tsaya mata take, bayan
sun isa gida Nihad ta shiga dakinta duk jikinta a sanyaye maganganun Zully na dawo
mata, dama su suka yi mata video din nan har suka ba Bloggers suka baza shi a
duniya they cause all her pain in life, tunanin hakan yasa ta fashe da kuka sosai,
a haka Khalil ya shigo dakin ya sameta, ya rungume hannunsa yana kallonta a hankali
yace "Duk abinda ya faru ya faru ne in ur favor Nihad, and kin yarda cewa every
disappointment is a blessing in disguise?? Ur disappoinment was nothing but a
blessing to you Baby, da basu maki hakan ba u will end up marrying Aliyu, who is a
bloody liar and a gangster, his wicked mum will become ur mother inlaw, abinda baki
sani ba Aliyu ko 5 daily sallah baya yi, ba shi da aiki sai shaye shaye da neman
mata daga wannan kasar zuwa wancan kasar duk da kudin Abbana, we grew up together
na fi kowa sanin waye shi nasan mugayen halayyansa, babu kalan giyar da baya sha,
ya saukar maki da kai ne saboda ya gama cin duniyarsa yana neman mace warce yasan
ba a lalata ba ya aura yayi settle down, da ace kin auri Aliyu sai kin fi
regretting akan abun da ya sameki a baya, mahaifiyarsa bata san Allah ba, bata kuma
kadaita Allah ba, she is a devil in human form, amma kin ga da yake zuciyar Mum
dinki is clean and pure shi yasa Allah ya sauya maki jarabawan auren Aliyu zuwa
wani daban...." Nihad na goge hawayen da suka ki tsaya mata tace "Haka ne" Ya
karaso ya zauna kusa da ita ya jawota jikinsa, murya can kasa yace "Da duk abinda
suka faru basu faru ba, da ba mu yi aure har mun samu Aaryaan ba" Ta lumshe ido
tana shaƙar daddadan kamshin jikinsa cikin sanyin murya tace "Ina alfahari da
kasancewar ka mijina, Allah Ubangiji ya bani ikon yi maka biyayya in bi ka sau da
kafa har karshen rayuwata, Allah ya tsare min kai da tsarewarsa ya kara maka
arzikin da zae amfani al'umma mijina...."
Ya rungumeta sosai yace "Ameen my wife, Allah ya sa ki haifo min yan biyu sau
biyu" Ta lumshe ido tana murmushi a hankali tace "Ameen my world" ya dago kanta
yace "Aryaan na cika 3 months zaki yi resuming school, and in sha Allah har masters
sae kinyi Baby...." Nihad ta kasa ce masa komai tana jin sabon sonsa na shigarta,
cikin sanyin murya tace "Promise me duk sanda mu ka kara ganin Zully zaka taimaka
mata da duk abinda Allah ya hore maka kaga tace magani zata siya" Yayi shiru sai
kuma yace "I promise u my love" Tayi kissing dinsa tace "Thank you Abuu Aryaan"
kissing her also yace "U are welcome Ummu Aryaan, some other time xan baki labarin
encounter dina da Husnah when she came to spend the night at our place back in
kano" Daga kai tayi ta kallesa da sauri, taga yana murmushi.... lumshe ido yayi ya
fara kissing dinta passionately.

Mumy ta samu kwanciyar hankali fiye da yanda tayi zato a gidan Janar Ahmad, so na
hakikanin gaskiya bawan Allahn ke mata, taga yana da wasu dabi'u in common da
marigayi Abba, he is such a caring husband, and bai rageta da su Fadil da komai ba
a gidan, Ga er sa Maryam warce hankali har yayi mata yawa, Mumy ta dauketa kamar
ita ta durkusa ta haifeta, Mumy bata yanke alaqarta da Umma ba don suna yawan
gaisawa ta waya duk bayan wani lokaci, har ma Amina kan zo gun Mumy ta mata kwana
biyu a Abuja sannan ta koma, ba a cikakken sati biyu sai Nihad ta je gidan
mahaifiyarta, don wannan satin in taje gun Mami, to wani satin gun Mumy zata je,
lokaci lokaci kuma tana zuwa gidan Hajiya Safeenah, at times kuma saboda Nadeeyah
take zuwa gidan wanda suka zama very best of frnds yanzu.....

And every one of them lived happily ever after!!!😊

_Kar ki manta er uwa idan kinsan baki sauke hakkina na dari biyar dake kanki ba ina
me maki tunatarwar karshe ki sauke don na zo karshen littafin, idan kuma baki
biyani a nan ba to ban san inda za mu hadu ki biyani ba, and lastly ɗan abinda ka
raina might definitely be ur doom one day, i neva sold the copywrite of Nihad balle
kice ai wani ya siya ya baki, but no p we shall meet somewhere one time in sha
Allah_ Masu zagina without me knowing them kuma za mu hadu a inda ya kamata 🤗

Nihad is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah.

07087865788...

Gaisuwa ta musamman zuwa ga Hajiya Asabe Hassan, ina maki fatan alkhairi Aunty,
Allah ya jibanci lamarinki ya raya maki zuri'arki Ameen.

*Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! a nan na sauke littafina me suna


NIHAAD* darussukan dake ciki Allah ya sa mu amfana da su, kurakuren dake ciki kuma
Allah Ubangiji nake rokon ya yafe min.... *Na kuma sadaukar da littafin nan zuwa ga
Mijina Barrister Ibrahim Khalil, ina alfahari da kai ina kuma godiya da ara min
some of ur time to do what makes me happy... Allah ya saka maka da gidan Aljanna ya
daura ka kan makiyanka, Allah ya kara maka arziki da zai amfani al'umma, thanks for
the encouragement and support from the beginning of the book Nihad till the end, u
were always by my side all through the long journey, i appreciate you so much dear,
Allah ya kara mana zaman lafiya da kwanciyar hankali.....*
My *Mother* Hajiya Hajarah and my sweet *Dad* Alhaji Bello Ahmad.. Allah ya kara
maku lafiya da kwanciyar hankali, Allah ya saka maku da gidan aljanna, Allah ya
kara maku arziki da wadata ta inda baku zato, ina alfahari da kasantuwarku iyayena.
My siblings Allah ya raya min ku gaba daya, Maryam Bello ga gaisuwarki a kyauta!!!
My cousins ina kewanku gaba daya, Allah ya raya min ku....

Aunty Zahrah mai gari, Deejah, Chamo, Aisha Bela, Aunty Amzaj, Mom twins, Aunty
Maryam, Maman Farida, Aisha Abdul, Sis Safiyya, Aunty Inna, Damsel, Aneesah, Mrs
Bello, Rabi'ah, da duk members din Khaleesat palace da ya kamata in ambaci sunansu
a nan ina alfahari da ku wllh, ina kuma yi maku fatan Alkhairi duniya da lahira,
Allah ya raya maku zuri'a, kafin wasu su yi patronizing dina ku ne farko as usual,
Allah ya kara maku budi Ameen. Scentmania, KMZ, Albaita-Al-sahal, Sapna borno
incense Allah ya karo maku kasuwa ta yanda ba kwa zato.

And finally my lovely fans that patronized me, ku ne farko ku ne karshe as usual,
wallahi ina yin ku, without u all they won't be Khaleesat Haiydar, Allah ya jibanci
lamarinku, ya kara maku arziki from every angle, ya kara ma iyayenku lafiya da
wadata... Ameeen, Nagode Nagode Nagode ina alfahari da ku.

*I need 10 concrete lessons from this book, kuma duk wanda ya rubuto lessons din ya
turo min i will check the best and i promise 3000 recharge card to the person with
the best write up, idan kuwa wanda bai siya littafin bane na yafe masa karantawar
da yayi a kyauta sannan in kara masa da recharge card na 1500* Idan kuma mutum bai
son katin sai inyi masa transfer.... Goodluck😊

07087865788

Taku har ko da yaushe Hauwa Bello Jiddah AKA _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻

You might also like