Alwashi 1 1 2

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 177

® *_HASKE WRITERS ASSO_*

( _Home of expert & perfect writers_)

*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

_Sakon fatan alkhairi gareki k'anwata Feedohm marubuciyar ZAN RAYU DAKE,ina
yimiki fatan alkhairi aduk inda kike, indeed i have no words to thank u, am deeply
grateful....! The first page is belong 2 u dear!_

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI.

*1*

****Gidane na marayu mai d'auke da tangamemen gate sannan ga katanga babba


zagaye da gidan wanda tsawonta ma abin kallone,haka shima cikin gidan yake
wawakeken gaske mai dauke da gine gine masu yawa wadanda suka hadar da ofisoshin
ma'aikatan gidan da kuma wurin kwanan marayun da kuma duk wani abu na bukatarsu,

Duk inda ka hanga yarane zaune sunyi group group, masu wasa nayi sannan masu hira
sunayi yayinda wasu kuma suke yan aikace aikacensu na yau da kullum,

Wasu yanmata ne guda biyu acan gefe su kadai wadanda akalla shekarunsu zasu kai
shekaru 23,

Daya daga cikinsu tayi tagumi tana sanye da kodadden hijabi da wata kodaddiyar
atamfa ajikinta haka itama dayar kayan jikinta duk sun gajiya,

"Hafsat wai wannan tagumin da kikayi na menene? Yau naga gaba daya yanayin naki sai
ahankali tamkar wata marar lafiya..." Daya daga cikin yanmatan tafada bayan ta dafa
kawar tata,

"Amina wallahi lafiyata kalau kawai dai ina tunanin makomar rayuwarmu ne acikin
gidan nan, ba kasafai mutane suka fiya kulawa damu ba, hatta gwamnati tayi watsi da
rayuwarmu sai lokaci zuwa lokaci take tunawa damu..." Wadda aka kira da suna hafsat
tayi magana cikin karyewar zuciya,

"Amma dai hafsat wannan ai ba bakon abu bane awajenmu duba da tsawon shekarun da
muka diba acikin wannan gida gashi har yau Allah bai kawo wanda zai daukemu ya
fitar damu daga cikin gidan nanba ko muma mazamo yaya kamar kowa.."
"Amina kenan tayaya zamu zamo yaya kamar kowa alhalin babu wanda yasan asalinmu,
Allah ne kadai yasan tushenmu dan haka kinga maganar amaida mu 'yaya ma bata taso
ba.."

"Hmmm babu komai koma dai yayane Allah yana tare damu..."

"Kai yanmatan nan kutaso kuzo muje.." Muryar daya daga cikin ma'aikatan gidan
marayun ta ratsa kunnuwansu wanda hakane yayi sanadiyyar katse musu hirar da suke
yi,

Mikewa sukayi suka karasa inda take,

"Yawwa kuzo muje, wannan bawan Allahn ne yauma yakawo muku agaji kamar yadda
yasaba..."

Batare da sunyi magana ba suka bi bayanta, gaba daya an tattaro yaran gidan
antarasu wuri guda gefe kuma wata babbar motace anata sauke kaya daga kanta wadanda
suka hadar da buhunhunan kayan abinci da tufafi,

Wuri amina da hafsat suka samu suka tsaya suna kallon irin uba uban kayan da ake
saukewa,

Kowacce acikinsu addu'a take acikin zuciyarta kan Allah yasakawa koma wanene wannan
mutumin da alkhairi domin yajima yana yi musu hidima,

Kayan da aka sauke daga kan wannan katuwar motar ba dan kadan bane domin bayan
kayan abinci da kayan sawa harda barguna da katifu,

Suna nan zaune sunyi tsuru suna ganin tulin kayan da aka kawo musu har aka kammala
sauke kayan nan wakilin wanda yabada kayan akawo ya mike yadanyi jawabi,

_Kamar yadda muka sani kuma muka saba, wannan bawan Allah Wanda mukafi sani da suna
baya goya marayu akoda yaushe yana iya kokarinsa wurin ganin ya kyautatawa rayuwar
marayu sannan kuma ya sadaukar da dukiyarsa wurin taimakon musulunci, kamar yadda
nadade ina fada muku shi wannan bawan Allah matashine ba tsoho ba kawai dai Allah
ne ya albarkaceshi da halin manya dan haka muyita yimasa addu'a akan Allah ya
albarkaci rayuwarsa da dukiyarsa da kuma iyayensa...._

"Amin..."

Dukkan jama'ar dake wurin suka amsa cikin farin ciki domin wannan bawan Allah ba
karamin taimako yake yiba saboda kusan agarin ma shine lamba daya wurin taimakawa
rayuwar marayu.

Saida aka gama rabawa marayun kayayyakin da aka kawo musu akan idon wakilin wannan
bawan Allahn dake basu gudun mawa wanda suka dade da rada masa suna da baya goya
marayu,bayan gama rabon kayan tsaf sannan wakilin baya goya marayu yatafi, sukuma
yaran kowa ya kinkimi kayanshi ya nufi wurinda zai adana su, haka suke gudanar da
rayuwarsu cikin wannan gida wanda a lokuta mafiya yawa sukan shafe sama da watanni
biyu batare da sun samu wani tallafi ba indai ba wannan bawan Allahn ne ya aiko
musu ba gashi kuma duk wannan hidimar da yake yi musu basu taba ganinsa ba balle
har su gane kamanninsa.

***

Kamar bazai taka k'asa ba haka yake tafiya, sanye yake cikin jar t shirt mai
dogon hannu yasha d'amara da jar belt wadda ke d'amare ajikin bakin trouser din
dake jikinsa, duk da wai ahakan sauri yake amma baisashi sauya salon tafiyar tashi
ba,bak'in face din dake idonshi yadan gyara bayan ya maida hankalinsa kan agogon
azurfar dake d'aure a tsintsiyar hannunshi, kamar koda yaushe fuskarshi babu alamun
fara'a atare da ita,

K'ofar da zata sadashi da falon mahaifiyarshi ya bude ya shiga fuskar nan kamar
zaice wayyo Allah dan tsananin fushi,

Ganin babu kowa aciki yasashi kara yin gaba, awani tsararren falo wanda aka tanada
musamman domin hutawa ya isketa, tana zaune saman kujera daga ganinta bazata haura
shekaru 45 ba aduniya, farace jajur mai dan jiki, tana sanye da wani leshi mai
tsadar gaske, wuyanta da hannuwanta gamida kunnenta duk gwala gwalai ne sai walwali
suke, haka yan yatsun hannunta ma duk sunsha zubunan gold,gefenta kuma wata yar
matashiyar budurwa ce wacce zata kai shekaru 23 tana kwance tayi matashi da cinyar
matar,

Sallama yayi wadda ba lallai su iya jiba domin aciki ciki yayita,

Dukkansu hankalinsu yana ga drama din da suke kallo atashar tauraron dan adam wanda
har saida ya zauna sannan suka farga dashi.......

*_Ummi Sha® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI.....!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to Miss Xoxo_

*2*

***Fuska cikeda annashuwa mahaifiyar tashi ta kalleshi cikin fara,a yayin da


shikuma sai faman cijar lebenshi nakasa yake yi fuska babu annuri,

"Yusleem.... Har anshigo?"

Mahaifiyar tashi ta tambayeshi da fara,a akan fuskarta,

Saida yasake hade rai idanuwansa na bisa screen din hadaddiyar wayar dake hannunshi
sannan ya amsata dakyar,

"Ehh Mami..."
Wata fara,ar tasake yi sannan tayi magana,

"Nima dama tun dazu nake jiranka kazo saboda ina son ka sama mana visa nida surayya
zuwa kasar chairo zan kaita medical check up..."

Shiru yayi batare da ya amsa ba yaci gaba da latsa wayarshi, idan da sabo to kowa
nagidan ya saba da wannan mummunar dabi'ar tashi tayin shiru idan ana yimasa
magana, ko mahaifiyarshi ce tayi masa magana sai yaga dama zai amsa gashi da shegen
girman kan tsiya kamar shi yafi kowa,

Saida ya dauki fiyeda mintuna goma sannan ya daga manyan idanuwanshi wadanda suke
tamkar kwai domin round eyes gareshi,surayya kanwarshi ya kalla wacce ke kwance
akan cinyar mami tana sanye da English wears riga da skirt bakake kanta babu dan
kwali,

Baiyi magana ba yasake mayar da kanshi kan screen din wayarshi,

"Mami...am dama ina son infada miki.."

Tattaro hankalinta gaba daya Mami tayi zuwa gareshi,

"To yusleem ina jinka.."

"Mami nasaki khadija yau da safe.."

Zaro idanuwa Mami tayi gamida dafe kirji, surayya kuwa dake kwance akan cinyarta
zunbur tayi ta mike zaune, dukkaninsu kallonshi suke cikeda tuhuma gamida zargi iri
iri,

"Nashiga uku ni siyama, innalillahi wa inna ilaihir raji'un...." Mami tafada tana
tafa hannuwanta,

"Haba yusleem wai kai wanne irin mutum ne? Anya kuwa ba aljana ce ta aureka ba?
Karfa ka manta ko watanni uku cikakke ba ayiba da bikinku kaida khadija amma shine
yau kazo kake fada min wai ka saketa?

Yusleem mai ka dauki aure ne? Ka daukeshi ne a matsayin wasa, ko kuma abin wasa ko
wasan yara?

Yusleem duk fa wannan dukiyar da kake ganin kana da ita bazata taba iya siya maka
darajar da aure zai siya maka ba...!"

Dan jan numfashi tayi sannan ta dora,

"Kana yaronka dakai amma acikin shekaru biyar kayi aure sama da guda goma, haba
yusleem wannan wacce irin mummunar dabi'a ce, ka mayar da sakin aure ba
komaiba,saki da Allah ma baya sonsa amma kai kuma shine ka mayar tamkar sana,arka,

To agaskiya nidai nagama gajiya da wannan halin naka na auri saki, babu damar ka
zauna da mace na koda shekara dayane?"

"Gaskiya Yaya bamuji dadin wannan labarin ba, yanzu anty khadijan ma ka saketa?"

Surayya ta fada idonta dauke da kwalla,ko kallonta baiyi ba bare tasa ran zai bata
amsa,

Fada mami tasoma balbala masa ta inda take shiga bata nan take fitaba,

"Ni narasa gane kan wannan hali naka yusleem, kwata kwata baka dauki aure da daraja
ba, sam baka son zama da mace, wannan wacce irin rayuwa ce,

Kuma bafa kowa kake watsawa kasa a idoba face ni tunda nice nake aura maka matan,
yanzu abinda kayi ka kyauta kenan?"

Dan kishingida yayi kadan ya tsurawa wayarshi ido batare da yace komai ba,

"Dakai nake magana kayi min shiru, ka fada min dalilinka na auri saki, akalla ba a
kasaru ba yusleem ka auri mata dai dai dai har guda goma sha..., baka da lafiya ne
ko yaya?"

Saida ya dan shafi sajen fuskarshi sannan ya kalli mami,

"Mami ni lafiyata kalau sannan dama ai ban taba cewa ga wacce nake so ba, duk matan
da nake aure kece kike samo min su ki aura min.."

"Wacce irin magana kake fada min yusleem? Dan bakai kagansu kana soba shikenan
bazaka zauna dasu ba? Wannan dalilinne yasa ka dauki auri saki ba abakin komai ba?

Sau nawa ina baka dama domin ka fito da matar da kake so in aura maka amma sai kayi
biris da maganar, kuma ni ai aganina nagama yimaka duk wani gata wanda yadace ace
uwa tayiwa danta domin na nemo maka mata yan mutunci, yan asali, masu aji wadanda
suka dace dakai amma daga karshe duk dai labarin iri dayane cewa ka sakesu, yanzu
kaduba kaga yarinyar nan khadija da ka saketa ka rabu da ita, yarinya ce mai hakuri
mai nagarta mai sanin ya kamata, yarinya kyakkyawa yar asali yar mutunci yar kawata
hajiya fa'iza,ko wata biyar ba ayiba da bikinku amma kasaketa..."

Dan tsagaitawa mami tayi tana dubanshi cikeda bacin rai, har tsawon mintuna biyar
babu wanda yasake magana acikinsu,

"Yusleem wai da me kake takama ne da har kadauki auri saki ba abakin komai ba?

Idan dan kyawun dakake dashi ne yasaka kake yin haka to ya kamata fa kasani akwai
wadanda suka zartaka kyau amma basa yin haka,

Idan kuma dan arzikin dakake dashi ne to kasani akwai big millionaires suna nan ba
irinkaba young millionaire ba kuma basa aikata wannan wulakancin dakake yi,

Inkuma kuruciyar da kake tare da itane yasaka yin wannan cin mutuncin to wallahi ka
gaggauta farkawa daga wannan dogon baccin da kakeyi domin akullum shekarunka sake
yawa suke bawai raguwa ba.."

Shiru mami tayi cikeda bacin rai tana huci saboda babatun da tagama yanzu,

Mikewa yayi sannan yayi magana ahankali,kamar mai ciwon baki yace,

"Kiyi hakuri mami.."

Ko amsa masa batayi ba yasaka kai yafice daga cikin falon, nan mami da surayya suka
rakashi da idanu....

_*Ummi Shatu*_👌🏻[12/14, 9:21 PM] Ummu A'isha: ® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of
expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*4*

aishaummi.blogspot.com

***Tashi mami tayi tabi bayan hajiya fa'iza zuwa dakin da khadija ke kwance
tagama cin kuka ta koshi dan tsabar kuka yanzu ko hawayen ma bata iyayi,

Zama mami tayi agefen gadon da khadijan ke zaune ta dafata jikinta asanyaye,

"Khadija kiyi hakuri kinji, insha Allah komai zai daidaita sannan zaki koma gidan
mijinki"

D'aga jajayen idanuwanta wadanda suka rine tayi ta kalli mami,

"Mami bazan iya komawa gidansa ba, nahakura da aurenshi, bazan sake iya zaman aure
dashi ba wallahi"

Gaban mami ne yashiga dukan tara tara saboda jin abinda khadija tafada,

"Khadija wani abu yayi miki?"

"Mami ni babu abinda yayi min kawai wulakancinshi ne bazan iya cigaba da jurewa ba"

Dafata mami tasake yi,cikin sigar lallashi tace,

"Nasani khadija, kuma nasan kinada hakuri amma daurewa zakiyi kisake yin wani
hakurin ki koma dakinki..."

"Mami bazan iya komawa ba wallahi nidai nahakura"

"To kuma khadija idan Allah ya kaddaro da rabo a tsakaninku fa? Bana son ayi
gaggawar yanke hukunci daga baya kuma azo ana dana sani"

Sai a lokacin hajiya fa'iza mahaifiyar khadija tayi magana,

"Ai hajiya siyama maganar rabo a tsakaninsu ma babu shi saboda tunda akayi auren
bai taba shiga dakinta ba, ko kallo bata isheshi ba bare har ya kulata"
Tagumi mami ta rafka taci gaba da sauraron bayanin da hajiya fa'iza take yimata na
irin zaman da yusleem yayi da khadija ta rufe maganar da cewa,

"Kawai dai muyi addu'a Allah yasa hakane mafi alkhairi, nanda sati biyu kuma zamuzo
mu kwashe kayanta ki fada masa"

Ita dai mami jiki babu kwari ta mike bayan tagama bawa khadija da mahaifiyarta
hakuri, jakarta ta dauka ta fita ranta babu dadi zuciyarta cike da bacin rai,
wannan karon kam yazama dole ta nunawa yusleem fushinta akan abinda yajima yana
aikatawa na sakin mata babu gaira bare dalili, babu laifin tsaye babu na zaune.

Har kofar gida hajiya fa'iza ta rakata suna cigaba da bawa juna hakuri musamman ma
mami da take ganin laifin na yusleem ne domin shine yake nema yaja mata lalacewar
zumuncinsu da matar da suka dade atare,

Mota Mamman driver ya bude mata tashiga ta zauna ya rufe suka tafi domin tuni
hajiya fa'iza tajima da shigewa cikin gida.

Da tunani kala kala acikin zuciyarta suka karasa gida, cikeda damuwa take zayyanewa
surayya abinda yafaru, suna tsaka da yin maganar sukaji shigowar yusleem,

Bai karaso cikin falon ba yatsaya a dining area, sanye yake da jar t shirt mai
gajeren hannu sai black trouser, kamshin turaren lailatul abyad da na real oud ne
yake tashi daga jikinsa, fuskarshi tayi fes sai annurin kyaune yake fita daga
gareta,

D'aga murya Mami tayi tayadda tasan zai iya jiyota,

"Kai..."

"Na'am ma..." Ya amsa yana kokarin bude jeren flasks din dake ajiye asaman table
din,

"Zo nan.." Mami tafada bayan ta daure fuskarta, fasa diban abincin yayi ya tasamma
cikin falon inda su Mami suke.

***

Rayuwar Hafsat haka taci gaba da tafiya agidan marayu, yanzu haka ta maida
hankali sosai wurin koyon sana'o'in hannu domin ana zuwa akoya musu, musamman aka
ajiye musu wadanda zasu rinka koyar dasu,

Cikin lokutan da babu yawa ta kwarance wurin sak'a sannan tafara iya dinkin
keke,haka kawarta Amina itama tana yi daidai gwargwado,

Kullum cikin yin sak'a suke itada Amina suna warwarewa sai su sake saka wani abun
nadaban kamar hula, safa, ko riga,

Yau ma kamar kullum suna zaune a inda suka saba zama suna yar hirarsu kowaccensu
tana rikeda koreshi tana yin saka,

Hirarsu ce ta katse saboda gano wasu manya manyan motoci da sukayi suna kokarin
shigowa cikin harabar gidan,

Amina ce ta zunguri Hafsat da hannunta,

"Hafsat yauma da alama munyi baki, watakila mai girma governor ne yakawo mana
ziyarar bazata.."
"Nima dai abinda nake tunani kenan Amina, koma dai menene kinga tashi muje ayi damu
kin san bahaushe yace wai gani ya kori ji..."

Mikewa sukayi atare kowaccensu ta tukunkune zaren kulunta da koreshi suka nufi inda
suka hango mutanen gidan suna tafiya....

*_Ummi Shatu_*👌🏻
[12/14, 9:21 PM] Ummu A'isha: ® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect
writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*5*

aishaummi.blogspot.com

***Ahankali yake ratsawa har zuwa cikin falon mami inda suke zaune itada
surayya,

Tunda yaga fuskarta yasan tana cikeda bacin rai,

Zama yayi acikin daya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun dake girke acikin
falon,

Tamkar basarake haka yajingina da jikin kujerar ya kishingide,

"Yusleem kana son inyi maka mugun baki..?"

Mami tafada ahasale cikin fada, shiru yayi bai amsa ba hakan yasake tunzurata,
cikin tsawa tasake yin magana,

"Ba dakai nake yin magana ba?"

Dan kallonta yayi,


"Mami laifin me kuma nasake yi?"

"Ban saniba, ohhh watonma tambayata kake me kayi? Harma ka manta abinda kayi
kenan..?"

Jijjiga kai mami tashiga yi ta maida dubanta ga surayya wacce ke zaune tana jinsu,

"Lallai surayya gaskiyarki ne dole sai an binciki kwakwalwarsa, kinji yanzu wai
tambayata yake me yayi, watonma shi har ya manta, dole ka manta mana tunda ka cimin
mutunci a idon duniya, sannan ka nunawa duniya ban isa dakaiba, ka cuci yar mutane
ka mayar da ita bazawara.."

Nunashi da yatsa tayi,

"To wallahi kaji tsoron Allah yusleem, ina fada maka kaji tsoron Allah domin
wallahi bazai barka ba indai kaci gaba da wannan mummunar dabi'ar taka ta auri
saki"

"Mami yanzu shikenan anty khadijan tatafi bazata dawoba?" Surayya tayi tambayar
tana kallon mami,

"Surayya ai babu macen da za ayiwa irin wannan wulakancin ta yarda tasake dawowa,
yayanku bashida hali mai kyau mugun mutum ne.."

Da sauri ya kalli mami, sai lokacin yayi magana,

"Mami muguntar me nayi? Ita khadijan ce tace miki ni mugune?"

Kallonsa mami tayi cikeda masifa,

"Ai basai ta fada minba, kai yanzu acikin halayenka har sai wata tafada min? Acikin
halayenka wanne ne bansani ba?

Kai cikakken mugune, miskili, mai shegen tinkahon tsiya da girman kai,

To bari kaji infada maka, komai tinkahon mutum da girman kansa idan yashiga wurin
matarsa kaskantar da kansa yake komai sarautarsa da kudinsa, amma kai hatta matarka
wannan shegen kasaitar taka da girman kai kake nuna mata.."

Shiru yayi bai sake maganaba, yayinda mami taci gaba da zuba masa fada har saida
tayi mai isarta sannan ta sassauta,

"Yusleem nakasa gane damuwarka, tun kana karami kai mutumne mai zurfin ciki, amma
ai bakada wanda zaka iya fadawa damuwarka sama dani da na haifeka, idan wani abune
yake damunka kasanar dani.."

"Nifa lafiya lau nake mami, babu abinda yake damuna" yabata amsa,

"Karya kake, tayaya zan yarda dakai bayan kana yin abu irin na marassa lafiya,
tunda bazaka fada minba to ya zama wajibi agareni inkaika adubaka, yanzu maganar
zuwa chairo da nayi maka dazu to harda kai zamuje, zan kaika kaima su bincika min
kwakwalwarka agani domin inajin kasamu tabin kwakwalwa a wannan accident din da
kukayi da mahaifinku.."

Murmushi yadanyi saboda maganar ta mami dariya taso bashi,

"Mami tabin hankali kuma? Nidin?"


"Kai kuwa, ai ni har yanzu ban tabbatar da cewa kanada cikakken hankali ba har sai
kikitoci sun tabbatar da hakan.."

Mikewa yayi domin yunwa yakeji, dining ya nufa nan mami tabishi abaya,

"Kullum kai kenan azuwa cin abinci gidan nan, yanzu da kanada matarka kuma ka
riketa da daraja da ba kana can ta hada maka dinner mai ban sha'awa ba"

Baiyi magana ba yaja kujera ya zauna yafara bude flask din dake jere agabanshi,

Surayya ce ta kwaso da gudu,

"Yaya Karka taba wannan nawane.."

Daure fuska yayi yabude flask din, farfesun dankali ne da hanta da kwai da alayyahu
yasha curry sai kamshi yake,

Kamar bazaiyi magana ba,daga ido yayi ya kalli surayya sannan ya mayar da dubanshi
ga mami,

"Mami zan fasa bakin yarinyar nan.."

"Akan me? Abincinta fa ka taba, da kayi zuciya ka rike aure ka rike matarka hannu
bibbiyu ai da duk ba akai ga hakaba" mami tace dashi tana kokarin zuba tuwon accah
miyar egusi,

Bai tanka ba ya debi farfesun dankalin acikin flate ya fara tsakura yana ci,

Cigaba da yi masa gugar zana mami tayi shi dai bai kulaba, wannan yana daya daga
cikin abinda yasa mami take ganin ba kowacce macece zata iya zama dashi ba domin ko
zaka shekara kana yi masa magana sai ya gadama zai amsa idan bai gadama ba har kayi
ka gama bazai amsa maka ba, yusleem miskili ne nagaske,ahaka ya karaci cakule
cakulen abincin yagama yatashi ya nufi gidanshi wanda ke can wata unguwa daban bata
su mami ba.

***

Daga can baya su Hafsat suka tsaya itada amina suna hangen bakin dake fitowa
daga cikin motocin da suka zo yanzu,

Wata bakar jeep mai dauke da glasses masu duhu aka bude nan wani matashin saurayi
ya fito, yana sanye da suit blue colour da bakin face idanuwanshi sakaye aciki
wanda ya karawa fuskarshi haiba,ashekaru bazai wuce shekaru 30 ba zuwa 31,

Dan yatsina fuska yake kamar wani mace ko kuma kamar wanda yaga kashi,

Kallon hafsa amina tayi,

"Hafsat kalli wancan mutumin, yanzu dama aduniya akwai irinshi?"

"Uhm amina kenan, mu ai kinsan muna nan akumshe dan haka baza mu san me duniya take
cikiba"

Jin anfara bayani akan bakin nasu da suka Kawo musu ziyara yasasu maida hankulansu
can.
Bayani akayi sosai tareda gabatar musu da mutumin da ya jajurce wurin basu gudun
mawa akoda yaushe, har akayi aka gama baice ko uffan ba, shugaban gidan marayun ne
yayi jawabin godiya a madadin marayun tareda mika wasu tarin bukatunsu wadanda suke
son gwamnati tayi musu ko kuma masu hannu da shuni,

Take awurin matashin saurayin Wanda suka sanya masa suna da baya goya marayu yabada
gudun mawar naira biliyan goma, yana gama saka hannu ajikin cheque din da yabada
yabude motarshi yashiga batare da yatsaya yaji karshen jawabin godiyar da jama'ar
wurin keyi masa ba,

Shiru Hafsat da amina sukayi acikin zuciyoyinsu suna tambayar kansu to shi wannan
wanne irin mutum ne mai alheri wanda baya bukatar godiya?.

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*6*

***Suna tsaye suna kallonshi motar tashi ta lula tabar wurin yayinda yan
rakiyarsa suka yi hanzarin shiga nasu motocin suka mara masa baya,

"Mutumin nan Allah yasaka masa da alkhairi, dan haduwa ya hadu amma kuma nidai
banji dadin yanda ya karbemu ba lokacin da ana gabatar masa damu.." Amina tace da
Hafsat tana girgiza kanta,

"To in banda abinki amina mudai ina ruwanmu da yanda ya karbemu,mudai dama
taimakonmu kawai muke so yayi kuma yana yi iya daidai gwargwadonsa sannan dama kin
san masu kudi ance wulakanci garesu"

"Hakane Hafsat amma kuma ai daraja mutum ma wani abune mai muhimmanci.."

"Kedai amina korafinki kullum baya karewa, dadina dake kenan"

"To shikenan Hafsat nayi shiru.."


Amina tafada tana kokarin jan hannunta.

***

Tunda yashiga cikin lafiyayyen gidan nasa yaja burki acikin kasaitaccen falonsa
na alfarma wanda za a iya kira da aljannar duniya,

Kasa zama yayi dan haka ya mike yafara yin sintiri yana kaiwa da kawowa acikin
falon nasa,

Yau kwata kwata baya jin barci sannan yasan barcin ma dama bazai zo gareshi ba
saboda halin da yake ciki,

Maganar mami ce ta fado masa nacewa zata kaishi domin a binciki kwakwalwarshi,

Shi dai a iya saninsa yasan lafiyarshi kalau bashida wata lalura wacce keda alaka
da tabin hankali,

Haka yaci gaba da ire iren wadannan tunane tunanen har dare ya raba, saida yayi
sallar asubah sannan yasamu bacci yayi awon gaba dashi,

Misalin karfe 10 daidai nasafe yatashi, wanka yayi ya shirya yafito cikin bakaken
suit wadanda sukayi mutukar karbarshi domin rigar da yasaka aciki ja ce shikuma red
colour tana mutukar amsarshi,

Fita yayi zuwa wurinda aka tanada musamman domin adana motoci, motocine gasu nan
ajere kala daban daban tamkar wurin saida motoci,

Wata dark blue ya bude yashiga yayi mata key yafita daga gidan, kamar ya biya ta
gidan mami yayi breakfast sai kawai yawuce batare da yabiya ba domin yasan idan
yaje ma fadan dai da take ta yi zata dora daga inda ta tsaya,

Kamfaninshi na sarrafa takalma da jaka ya nufa domin yana da meeting da ma'aikatan


company din nan yabata lokaci mai tsawo bashi ya tashi ba sai 5 na yamma dan haka
agajiye ya tasamma gidan mami,

Yana tafe yana kokarin cire necktie din dake wuyanshi daf da zai shiga falo su
surayya suka fito itada kawarta wacce ta Kawo mata ziyara,

"Barka da zuwa yaya.." Surayya tace dashi lokacin da saka zo daf dashi, ko kallonta
baiyi ba bare ya amsa mata sannun da take yimasa,

Dayake tasan halinshi sai ko damuwa batayi ba maimakon hakama sai murmushi da
tadanyi ta waiwaya lokacin har yashige cikin babban falon,

"Sury wannan kuma waye?"

Kawar tata ta tambayeta tana dafa kafadarta,

"Wallahi billy brother nane.."

"Au wai dama kinada wani brother din bayan Abdul da khalifa?"

Murmushi surayya tayi,

"Wannan shine first born namu ai sunanshi yusleem"


Kada kai billy tayi tana dan murmusawa,

"Masha Allah, amma duk yafiku kyau, inama ace zaki bani shi.."

"A'a billy bazanyi Fatan ki auri yaya yusleem ba domin daga karshe kawancenmu dake
sunanshi kararre"

"Meyasa kikace haka?" Billy ta tambayeta,

"Kedai kawai mubar maganar, idan mun koma school zamu karasa, nidai bazan samu
komawa next week ba sai dai upper week"

"To shikenan Allah yakaimu"

Sallama sukayi billy tatafi ita kuma surayya tashiga cikin gida, akan dining ta
iske yusleem yana cin abinci,

"Yaya wallahi kayi kasuwa.."

Banza yayi mata yaci gaba da cin abincinsa, bedroom din Mami ta shiga ta fara
tsegunta mata maganar kawarta billy, ahaka yusleem yasamesu,

Agefen gadon mami yazauna yadan kishingida,

"Mami maganar visa dinnan inaga kawai kufara shiri domin nanda kwana 4 zata iya
zama ready.."

"Allah yakaimu, Allah yayi maka albarka yusleem.."

"Amin mami".

Cikin kwanaki hudu visa tafito suka shirya suka tafi kasar chairo, bincike sosai
mami tasa ayi mata a kwakwalwar yusleem dan agano mata abinda ke damunsa, cikin
kwanaki 2 likitocin suka kammala sakamako yafito...

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_


*7*

aishaummi.blogspot.com

***Mamaki ne ya kama mami saboda ganin sakamakon dake jikin takardar, wurin
surayya taje ta mika mata bayan ta zauna agefenta,

Itama surayyan mamaki ne ya bayyana akan fuskarta ganin wai yusleem lafiyarsa kalau
bashida matsalar komai,

"To yanzu mami menene mafita kuma?"

Surayya tayi tambayar tana kallon mamin,

"Surayya mujira tukunna mu koma gida sai asamo mafita"

"To Allah ya kaimu".

Satinsu biyu suka koma gida nigeria, bayan sun hutane mami tasake sakashi agaba
ta koro masa jawabi kamar haka,

"Tunda munje asibiti sun tabbatar mana da cewar kwakwalwarka lafiya lau take tofa
akwai sauran bincike domin yanzu kuma malamin rukiyya zan samo yazo yayi maka
rukiyya ya rabaka da wannan aljanar data aureka.."

Ware ido yayi ya kalli mami,

"Rukiyya kuma mami? Ni me ya hadani da rukiyya kuma?"

"Kai kuwa keda hadi da rukiyya yusleem domin dukkan alamu sun nuna cewar kana
tareda aljana..."

"Wallahi mami ni banida wata aljana, lafiyata lau.."

"Ai bazan yarda dakai ba har sai masu bincike sun bincika sun tabbatar"

Mikewa yayi yafita, tun daga nan bai sake komawa gidan ba sai ranar da surayya zata
koma makaranta,

Acikin kitchen ya iske mami itada kukunta suna soya dambun kifi da nama wanda
surayya zata tafi dashi makaranta,

"Mami barka da aiki.."

Kallonsa mami tayi ta dauke idonta taci gaba da aikinta,

"Sai yau zaka zo gidan? Akan ina nemamaka lafiya shine kuma zaka daina zuwa gidan
nan? Yayi kyau"

Shiru yayi baice komai ba dama kuma tasan ba komai din zaice ba,

Wucewa yayi zuwa cikin falo inda surayya take zaune tanata harhada kayanta wadanda
zata wuce school dasu,

"Yawwa yaya dama kai nake jira, pls ka bani kudi zan sai phone wallahi kaga wannan
din ta fashe jiya ina..."

Bai bari ta karasa ba yayi saurin katseta,


"Nawa kikeso?"

"Yaya duk abinda nasamu"

"Kijira zan turo miki anjima harda kudin karatunki, inyaso idan kikaje can sai
kisiya"

"Nagode yaya, Allah yabaka mata tagari"

Wata uwar tsawa ya daka mata,

"Ke....."

Saurin rufe bakinta tayi tai shiru, mami ce ta shigo tana rikeda dambun nama akan
flate, yusleem ta ajiyewa agabanshi ta samu wuri ta zauna tana kallonshi,

"Gobe idan Allah yakaimu malamin da zai yimaka rukiyya zaizo zaku fara"

Baiyi maganaba illa idanuwansa da ya tsayar akan tv din dake kafe abangon falon
tana aiki,

"Ko bakaji ne? Ina yimaka magana"

"Inaji.."

"Yawwa dan haka gobe da safe inganka agidan nan"

Dambun naman yaja yafara tsakura yana ci har surayya ta kammala shiryawa nan ya
daukesu a motarshi itada mami ya kaisu airport, saida sukaga tashin jirginsu sannan
suka dawo gida, bai shiga gidan ba ya juya ya nufi gidansa.

Washe gari kamar yadda mami tace haka ya nufi gidan, lokacin har mai yin rukiyyar
yazo, tun aranar aka fara amma shiru babu alamun aljanu atare dashi,

Tsawon kwana 7 aka dauka ana gudanar da rukiyyar amma babu abinda ya canja dan haka
malamin yacewa mami daga ranar angama kuma lafiyar yusleem kalau,amma bai saniba ko
aljanar kin bayyana tayi,

Shiru mami tayi tai tagumi tarasa abin fada amma har lokacin zuciyarta bata amince
mata da cewar yusleem baya tareda aljana ba.

Sallamar malamin mami tayi ta zubawa yusleem ido,

"Yusleem ka fada min abinda ke damunka saboda ni har yanzu jikina yana bani da
akwai wani abu"

"Mami babu abinda yake damuna"

"Da akwai yusleem, akwai abinda yake damunka, kafada min gaskiya idan baka da
lafiya a matsayinka na d'a namiji?"

Dan sunkuyar da kai yayi yasoma shafa sumar kanshi saboda nauyin da maganar ta mami
tayi mishi,

"Mami nifa banida kowacce irin matsala wallahi lafiyata lau"

"To shikenan tunda kafadi haka amma ina son daga yau dinnan kafara duba matar aure
domin agaskiya bazan juri ganinka ahaka babu mata ba"
Kallonta yayi amma sai yayi shiru baiyi magana ba domin shi ba kasafai ya fiya son
yayita magana ba, nasiha mami tashiga yimasa sai da tayi tagama sannan yatashi ya
fita,

Tun daga ranar mami tashiga nemar masa matar aure domin acewarta bata son ganinshi
haka babu aure,shikuma tasan ba samowa zaiyi dakanshi ba ko tabashi dama tunda
abaya tasha gwada irin hakan amma abun ya faskara.

Cikin sa'a aka samo mata wata yarinya mai hankali Nusaiba yarinyar bazata wuce
shekaru 20 ba domin ko jami'a bata shiga ba, duk da iyayenta sunji labarin irin
auri sakin da yusleem yakeyi hakan bai sasu yunkurin hanashi aurenta ba domin suna
ganin kamar wannan wata damace da suka samu wadda zasu dandani zakin arziki.

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*8*

aishaummi.blogspot.com

***Tamkar zaiyi kuka yasa mami agaba yana rokonta akan ta janye maganar
auren nan domin bashida burin sake yin aure nan kusa,

"Mami tunda dai sakin nan da nakeyi bakya so, shi yafi komai daga miki hankali to
kiyi hakuri kibar maganar auren nan domin bana bukatarsa.."

"Kai ka isama? Ai ko bakaso sai nayi maka wannan auren domin cikar kimarka shine
aganka da iyali, haba yusleem wacce irin rayuwa kake son yi ne? Haka kake so inzuba
maka ido ka zauna babu mata atare dakai? Ina abinda bazai yuyu ba kenan.."

Bai sake cewa komai ba yaciro wayarshi dake cikin aljihun wandonshi yafara latsawa,

"Aikinka kenan latse latsen waya, babu dama ayi magana ta minti 5 dakai, ai dole ka
rasa macen da zata zauna dakai..."
Nan dinma dai shirun yayi baice komai ba, nan mami taci gaba da mita tana tayi
shidai yayi shiru har tayi tagama ta tashi takoma bedroom dinta bai sake cewa koda
uffan ba,

Yadade zaune acikin falon kafin ya mike ya fita, washe garin ranar yan uwan
tsohuwar matarshi khadija suka zo suka kwashe kayanta kaf basu bar koda cokali ba,

Ita kuwa mami shirye shirye nema masa aure taci gaba dayi, tuni har tabada sautin
ahado masa lefe tun daga kasar dubai, amma har yau yusleem bai san koda kalar
yarinyar da Mami keson aura mishi ba,

Neman auren saida yayi karfi sosai sannan Mami tace ya shirya yaje yaga yarinyar,

Baiyi musu ba yace to zaije amma kuma baije dinba, shiru shiru baije gidansu
nusaiban ba har aka wuce sati biyu, kiranshi Mami tayi tace yazo ya sameta,

Lokacin da yatashi daga office yawuce kiran da mamin keyi masa, a falo ya sameta
itada sa'ade mai yimata kitso da kunshi domin Mami irin matan nanne yan gayu
shiyasa koda wasa bazaka taba cewa itace ta haifi yusleem dinba domin jikinta bai
nunaba gayunta ya boye tsufan,

Zama yayi acikin daya daga kujerun falon yazaro wayarshi yasoma latsawa,

Gaidashi sa'ade mai kitso tayi ya amsa dakyar, saida mami ta sallami sa'aden tatafi
sannan ta juya ta fuskanceshi.

"Yusleem meya hanaka zuwa wurin matar da zan aura maka? Tunfa rannan nace maka kaje
ku gaisa amma shine bakaje ba?

To lallai lallai kaje yau"

"Mami yarinyar shekararta nawane? Tayi 22?"

Girgiza kai mami tayi, "banajin zatafi 20 gaskiya"

"To agaskiya Mami ni tayi min kankanta da yawa, ina laifin ma yar 23 zuwa 25,amma
kawai ni akawo min wata karamar yarinya tazo tana yimin yarinta.."

"Kajishi sai kace wani abun arziki yake yiwa matan idan ankai mishi, ina ruwanka da
kankantarta? Kaida duk aure auren nan da kayi bana jin akwai mace kwaya daya da
zakace kunyi rayuwar aure da ita, duk fa sakinsu kake yi kafin wani abu yashiga
tsakaninku..."

Kawar da kanshi yayi bai kalli bangaren da mamin takeba,

"Koba haka bane..?"

"Mami wai sune suka fada miki hakan?" Yafada yana kallon wani wuri,

"Kai kasani dai,nidai kaji abinda nafada maka yau dinnan kaje wurinta ku gaisa"

Bai amsa ba yatsiri danne dannen waya,

"Wai idan ana yimika magana sai ka hau danne dannen waya, kaji abinda nafada?"

"Naji mami..."
"Ba maganar kaji bane, dama ai nasan kaji, so nake ka aikata abinda nasaka, sannan
idan kasan kanada matsala ka fada min tunda wuri sai in nemo maka magani..."

Sunkuyar da kanshi yayi yana murmushi, shi baya son yaji mami tana irin wannan
maganar,

"Kaji abinda nace?"

"Naji, mami dan Allah kibar maganar nan nifa lafiyata kalau"

"Yusleem ai dole inyi wannan maganar domin tazama dole, idan ba marar lafiya ba
wanne namiji ne za arinka aura masa kyawawan yanmata yazauna yana kallonsu sai
ankwana biyu ka sakesu? Nidai har yau ina nan akan bakana nacewar kana tareda
aljana dan haka ya zama wajibi inci gaba da nemar maka mafita"

Sajensa yafara shafawa kansa asunkuye idanuwansa akasa,

"Yanzu katashi kaje kaci abinci inyaso sai ka karasa gida ka shirya kaje can
gidansu nusaiban"

Tashi yayi yaje yahau kan dining ya dan fara dudduba abubuwan da aka dafa, tuwon
shinkafa da miyar ganye ya saka yadan ci ya mike, har lokacin mami na zaune acikin
falo, lekata yayi yai mata sallama yafita,

Shi dai adole zaije wurin yarinyar nan, yasan tunda mami takafe akan sai anyi auren
nan to ko me zaiyi bazata fasaba ba, da wannan tunanin yashiga cikin gidansa yaje
yayi wanka ya shirya,

Kananan kaya yasaka dark blue din t shirt mai gajeren hannu da bakin jeans, fuskar
nan ahade babu alamun fara'a,kamshin turaren albahrainil madina ne ke ta faman
tashi daga jikinsa,

Saida yayi sallar magrib a masallacin dake kofar gidanshi sannan ya dauki mota
yafita lokacin gari yasoma dan yin duhu,

"Mtswwww.." Yaja dogon tsaki, tsakin yayi tayi yana bin kwatancen da mami tayi masa
har yasamu ya gano gidansu nusaiba,

Yana hakimce acikin motarshi ya tura yaro ya kirata, gidan yaketa bi da kallo yana
daga cikin motar, gidan ba wani babba bane sai dai rufin asiri,

Yana daga ciki azaune ya hango ta tana fitowa daga ciki, kawar da kanshi yayi daga
kallonta sannan kuma bai fito daga cikin motar ba har ta karaso,

Glass din motar ya zuge yayi kasa dashi yana kallonta fuska ahade....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*8*

aishaummi.blogspot.com

***Tamkar zaiyi kuka yasa mami agaba yana rokonta akan ta janye maganar
auren nan domin bashida burin sake yin aure nan kusa,

"Mami tunda dai sakin nan da nakeyi bakya so, shi yafi komai daga miki hankali to
kiyi hakuri kibar maganar auren nan domin bana bukatarsa.."

"Kai ka isama? Ai ko bakaso sai nayi maka wannan auren domin cikar kimarka shine
aganka da iyali, haba yusleem wacce irin rayuwa kake son yi ne? Haka kake so inzuba
maka ido ka zauna babu mata atare dakai? Ina abinda bazai yuyu ba kenan.."

Bai sake cewa komai ba yaciro wayarshi dake cikin aljihun wandonshi yafara latsawa,

"Aikinka kenan latse latsen waya, babu dama ayi magana ta minti 5 dakai, ai dole ka
rasa macen da zata zauna dakai..."

Nan dinma dai shirun yayi baice komai ba, nan mami taci gaba da mita tana tayi
shidai yayi shiru har tayi tagama ta tashi takoma bedroom dinta bai sake cewa koda
uffan ba,

Yadade zaune acikin falon kafin ya mike ya fita, washe garin ranar yan uwan
tsohuwar matarshi khadija suka zo suka kwashe kayanta kaf basu bar koda cokali ba,

Ita kuwa mami shirye shirye nema masa aure taci gaba dayi, tuni har tabada sautin
ahado masa lefe tun daga kasar dubai, amma har yau yusleem bai san koda kalar
yarinyar da Mami keson aura mishi ba,

Neman auren saida yayi karfi sosai sannan Mami tace ya shirya yaje yaga yarinyar,

Baiyi musu ba yace to zaije amma kuma baije dinba, shiru shiru baije gidansu
nusaiban ba har aka wuce sati biyu, kiranshi Mami tayi tace yazo ya sameta,

Lokacin da yatashi daga office yawuce kiran da mamin keyi masa, a falo ya sameta
itada sa'ade mai yimata kitso da kunshi domin Mami irin matan nanne yan gayu
shiyasa koda wasa bazaka taba cewa itace ta haifi yusleem dinba domin jikinta bai
nunaba gayunta ya boye tsufan,

Zama yayi acikin daya daga kujerun falon yazaro wayarshi yasoma latsawa,

Gaidashi sa'ade mai kitso tayi ya amsa dakyar, saida mami ta sallami sa'aden tatafi
sannan ta juya ta fuskanceshi.

"Yusleem meya hanaka zuwa wurin matar da zan aura maka? Tunfa rannan nace maka kaje
ku gaisa amma shine bakaje ba?
To lallai lallai kaje yau"

"Mami yarinyar shekararta nawane? Tayi 22?"

Girgiza kai mami tayi, "banajin zatafi 20 gaskiya"

"To agaskiya Mami ni tayi min kankanta da yawa, ina laifin ma yar 23 zuwa 25,amma
kawai ni akawo min wata karamar yarinya tazo tana yimin yarinta.."

"Kajishi sai kace wani abun arziki yake yiwa matan idan ankai mishi, ina ruwanka da
kankantarta? Kaida duk aure auren nan da kayi bana jin akwai mace kwaya daya da
zakace kunyi rayuwar aure da ita, duk fa sakinsu kake yi kafin wani abu yashiga
tsakaninku..."

Kawar da kanshi yayi bai kalli bangaren da mamin takeba,

"Koba haka bane..?"

"Mami wai sune suka fada miki hakan?" Yafada yana kallon wani wuri,

"Kai kasani dai,nidai kaji abinda nafada maka yau dinnan kaje wurinta ku gaisa"

Bai amsa ba yatsiri danne dannen waya,

"Wai idan ana yimika magana sai ka hau danne dannen waya, kaji abinda nafada?"

"Naji mami..."

"Ba maganar kaji bane, dama ai nasan kaji, so nake ka aikata abinda nasaka, sannan
idan kasan kanada matsala ka fada min tunda wuri sai in nemo maka magani..."

Sunkuyar da kanshi yayi yana murmushi, shi baya son yaji mami tana irin wannan
maganar,

"Kaji abinda nace?"

"Naji, mami dan Allah kibar maganar nan nifa lafiyata kalau"

"Yusleem ai dole inyi wannan maganar domin tazama dole, idan ba marar lafiya ba
wanne namiji ne za arinka aura masa kyawawan yanmata yazauna yana kallonsu sai
ankwana biyu ka sakesu? Nidai har yau ina nan akan bakana nacewar kana tareda
aljana dan haka ya zama wajibi inci gaba da nemar maka mafita"

Sajensa yafara shafawa kansa asunkuye idanuwansa akasa,

"Yanzu katashi kaje kaci abinci inyaso sai ka karasa gida ka shirya kaje can
gidansu nusaiban"

Tashi yayi yaje yahau kan dining ya dan fara dudduba abubuwan da aka dafa, tuwon
shinkafa da miyar ganye ya saka yadan ci ya mike, har lokacin mami na zaune acikin
falo, lekata yayi yai mata sallama yafita,

Shi dai adole zaije wurin yarinyar nan, yasan tunda mami takafe akan sai anyi auren
nan to ko me zaiyi bazata fasaba ba, da wannan tunanin yashiga cikin gidansa yaje
yayi wanka ya shirya,
Kananan kaya yasaka dark blue din t shirt mai gajeren hannu da bakin jeans, fuskar
nan ahade babu alamun fara'a,kamshin turaren albahrainil madina ne ke ta faman
tashi daga jikinsa,

Saida yayi sallar magrib a masallacin dake kofar gidanshi sannan ya dauki mota
yafita lokacin gari yasoma dan yin duhu,

"Mtswwww.." Yaja dogon tsaki, tsakin yayi tayi yana bin kwatancen da mami tayi masa
har yasamu ya gano gidansu nusaiba,

Yana hakimce acikin motarshi ya tura yaro ya kirata, gidan yaketa bi da kallo yana
daga cikin motar, gidan ba wani babba bane sai dai rufin asiri,

Yana daga ciki azaune ya hango ta tana fitowa daga ciki, kawar da kanshi yayi daga
kallonta sannan kuma bai fito daga cikin motar ba har ta karaso,

Glass din motar ya zuge yayi kasa dashi yana kallonta fuska ahade....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*9*

aishaummi.blogspot.com

***Fuska adaure yusleem ke karewa nusaiba kallo aranshi yana mamakin wai
shine zai auri wannan yar karamar yarinyar domin shi aduk matan da mami ke aura
masa ma babu wacce take kasa da shekaru 23,

Muryar nusaiba ce ta katse masa tunaninsa,

"Ina wuni..?"

Sai da yayi kamar bazai amsa ba sannan ya amsa gaisuwar tata da kyar,
Daga nan yayi shiru itama shiru din tayi domin bata da abin cewa, kallonshi nusaiba
keyi yana cikin mota a zaune ita kuma ya barta awaje atsaye saboda tsabar mulki,

Wayarshi ya dauka yafara latsawa zuwa can ya dan kalleta kamar wanda akayiwa dole,

"Sai anjima..."

Glass din motar yayi sama dashi nan ta matsa tabashi wuri yaja motarshi yayi gaba,
bin motar da kallo nusaiba tayi acikin ranta tana yaba kyawun siffarshi amma kuma
akwai iya tsare gida da dan karen wulakanci nan da nan taji auren nashi ya fice
mata arai,

Shikam yusleem tun lokacin da yabar gidansu nusaiba yayi watsi da maganar aurenta
domin gaba dayanta bata yimasa ba,

Bai samu zarafin zuwa gidan mami ba sai washe gari da yamma,

Acikin bedroom dinta ya sameta tana yin waya da su khalifa,

Wuri yasamu yazauna akan stoll din mudubinta yana kallonta,

Sallama tayi dasu khalifa ta juya tana fuskantarshi,

"Barka da hutawa mami.."

"Yawwa sarkin taurin kai.., yanzu kai haka dama ake yin zance? Kaje ka tisa yarinya
agaba da harara, fuskarka adaure kamar mala'ikan mutuwa.."

Zamanshi ya gyara,

"Mami shiyasa nace maganar auren nan kibarshi kawai, yanzu ahakura da maganar auren
wannan yarinyar, ki bani lokaci zanyi miki magana da kaina kuma da kaina zan
gabatar miki da yarinyar da zan aura.."

Shiru mami tayi tana dan nazari,

"To yanzu baka jin idan nace afasa iyayenta zasu yimana kallon kananan mutane? Kuma
ma duk ba wannan ba, kai dinnan ba tabbas garekaba, nasan ko na baka shekara azuwan
ka fito da matar aure ba lallai ne ka iya yin hakan ba"

"Mami kidai bani damar ki gani nidai burina yanzu ki hakura da maganar auren nan
wallahi yarinyar nan tayi min karama kofa surayya batayi ba ashekaru.."

"Ehhh to, bari dai sai nayi shawara"

"To shikenan mami Allah yasa ki amince da bukatata.."

"Ai bukatar taka ne bata alkhairi bace amma tunda ka dage zan duba nagani.."

"To mami.."

Mikewa yayi yafita Mami ta rakashi da ido ita yanzu tausayi ma yake bata saboda
takamaimai ba asan abinda ke damunsa ba,

Aminiyarta hajiya fa'iza ta Kira wato mahaifiyar khadija matar yusleem tada wacce
yasaka,

Shawararta mami ta nema dangane da auren da take nemarwa yusleem, ajiyar zuciya
hajiya fa'iza ta ajiye sannan cikin sanyin murya tafara magana,
"Hajiya siyama nidai aganina ki rabuda yaron nan karki sake yimasa wani auren har
nan da wani lokaci,

Abinda yasa kikaji nace haka shine, kinga dai nafarko sakin auren da yusleem yakeyi
yayi yawa kuma hakan yana haifar da bacin sunansa acikin al'umma sannan kuma suma
yaran da yake sakin kinga yana rage musu wata kima da daraja a matsayinsu na
yanmata domin koda babu abinda yataba shiga tsakaninsu tofa da zarar ya sakesu
sunansu zawarawa sannan iyayensu kamar fa anshiga hakkinsu shiyasa ni nake ganin
ahakura da batun auren nan inyaso sai kici gaba da lallabashi har yasamu ya sanar
dake matsalarshi..."

Itama mami ajiyar zuciyar ta sauke,

"Hakane hajiya fa'iza, hakika gaskiya kika fadi shikenan insha Allah zanyi yanda
kikace"

"Babu komai siyama,Allah dai yabamu mafita"

"Amin ya Allah"

Sallama sukayi mami ta katse wayar, tabbas tasan abinda hajiya fa'iza tafadi
gaskiya ne shiyasa ma ta kuduri niyyar zuwa gidansu nusaiba da kanta domin tayiwa
iyayenta bayani,

Aranar da yamma taje gidan, lokacin da ta shiga dama ta iske Baban nusaiban da
mahaifiyarta sun sakata agaba sai fada suke ta inda suke shiga bata nan suke fitaba
saboda tace bazata auri yusleem ba ita tsoranshi takeji,

"Ko zaki mutu kuwa dolenki sai kin aureshi.." Inji mahaifin nusaiba, ganin mami
yasa suka dakata daga fadan da suke yiwa nusaiba, nan mami ta sanar dasu anjanye
maganar aure amma dukiyar aure wacce aka kai anbar musu,

Bacin rai da tashin hankalin da iyayen nusaiba suka shiga ba kadan bane itada dai
mami nan tayi musu sallama tatafi tabarsu da mita.

***

"Hajiya kubra dan Allah ki hakura kidaina kukan nan haka, haba kamar wadda aka
yiwa mutuwa? Karfa ki manta tafiya ba mutuwa bace"

Dago da jajayen idanuwanta tayi tana kallon mai gidan nata wanda ke zaune kusa da
ita,

"Haba Alhaji, dole nayi kuka ai, yanzu bazan sake ganin amal ba sai nanda shekara
daya.."

"Haba hajiya kubra sai kace yarinya, ya kike abu irin na yara ne, ai naga ga waya
nan akoda yaushe zaku rinka gaisawa.."

Cigaba da kukanta tayi bata amsa ba, yana shirin sake yi mata magana wayarshi dake
aljihunsa tafara ringing nan yacirota yaduba, ganin Wanda ke kiran nashi yasashi
saurin mikewa yana kallonta"

"Hajiya kubra ina zuwa, Alhaji Abubakar ne yazo,dama munyi dashi zaizo yanzu, ina
zuwa"
Bai jira amsarta ba yayi azamar ficewa daga cikin bedroom din nata yafita zuwa part
dinshi...

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*10*

aishaummi.blogspot.com

***Gidan Alhaji sa'id tawagar mai girma mataimakin gwamna suka wuce direct,
hafsat tana zaune abayan mota sai zazzare ido take yi domin bata ma san inda suka
nufa ba kasancewar ba fitowa sukeyi ba,

Wani kayataccen gida taga sun shiga wanda ya tsaru mutuka fadin girman gidan kuwa
bata baki ne,

Bude mata kofar motar akayi tafito tana bin gidan da kallo,

Wurinta alhaji sa'id ya karasa bayan sunyi sallama da aminin nashi wanda tuni har
tawagar tashi tafara fita daga cikin gidan,

Atsorace hafsa take binsa da kallo saboda rashin sabo gashi kuma uwa uba bata taba
ganinshi ba,

"Zo mu karasa ciki.." Yace da ita lokacin da yakarasa kusa da ita,

Kamar kurma haka tayi domin bata iya amsawa ba illah bin bayanshi da tayi tana mai
cigaba da karewa gidan kallo,

Tana biye dashi abaya har zuwa cikin wani hamshakin falo wanda ya kayatu mutuka da
kayan alatun more rayuwa,
Tunda suka shiga cikin falon alhaji sa'id yake kwallawa matarshi kira,

"Hajiya kubra.... Hajiya kubra...,hajiya kubra ko bakya kusa ne?"

Amsawar da yaji hajiya kubran tayine ya dakatar dashi daga kwalla kiran da yake yi
mata, falon tafito tana magana muryarta adashe saboda kukan da ta dade tanayi,

"Alhaji gani, har kun dawo?"

"Mun dawo kuma munyi farar tafiya tunda harda tsaraba nakawo miki.."

Hafsat ya nuna mata da yatsanshi, ido ta zaro ta bude baki cikeda mamaki domin da
lokacin da ta fito sam bata lura da Hafsat dinba sai yanzu da ya nuna mata ita,

"Alhaji a ina kasamo amal? Dawo da ita kasa akayi?"

Dan murmushi alhaji sa'id yayi, "kidai kalleta dakyau kigani.."

"Alhaji ai naganta, amal ce, ai bai kamata kace adawo da itaba tunda karatunta
karuwarmu ce gaba daya.., amal meyasa kika dawo?"

"Hajiya kubra wannan fa ba amal bace mai kamada amal ce, ganin kin tada hankalinki
kina neman tayar da nawa hankalin shiyasa na Kawo miki ita.."

Sai a lokacin hajiya kubra tafara bin Hafsat da kallo tun daga kafarta zuwa kayan
dake sanye ajikinta, ko shakka babu wannan ba amal bace amma kuma bata da banbanci
da amal din sai ko gayu da wayewa wadda amal din zata fita dashi amma hatta kalar
fatarsu da komai iri dayane kawai hutu da jin dadi fatar amal zata nunawa ta
Hafsat,

"Ikon Allah baya karewa,tabbas wannan babu abinda zai hanani karbarta a matsayin
amal domin kamar tasu ta isa.." Hajiya kubra tafada tana takawa har izuwa wurinda
Hafsat ke tsaye nan tashiga kare mata kallo,

"Yawwa tunda bukatata tabiya shikenan dama burina ki cire damuwar dake ranki akan
amal ki karbi wannan amadadinta"

"Alhaji ina kasamo min ita? Wallahi yarinyar nan batada maraba da'yata.."

"Hajiya kubra zanyi miki bayani daga baya saboda kinga yanzu lokacin sallar magrib
yakawo kai, amma abinda nake so dake shine wannan yarinyar nakawo miki ita amana
duk da cewar nasan zaki kula da ita tamkar yar da kika haifa saboda tayi kama da
jininki amal, yanzu kije kibata duk abinda ya kamata.."

Narai narai da ido hajiya kubra tayi ta kalleshi,

"Amma dai alhaji ba aro aka bani itaba ko? Saboda bana son itama kwana biyu azo ace
za arabani da ita"

"Kisha kuruminki hajjaju wannan yarinyar babu abinda zai rabaki da ita domin
tazama'yarki halak malak.."

Farin cikine ya bayyana akan fuskar hajiya kubra wanda har saida takasa boye hakan,

"To alhaji, amma naji dadin wannan maganar,nayi mutukar farin ciki.."

Juyawa yayi yanufi kofar fita, cikin farin ciki hajiya kubra ta kama hannun Hafsat
tana kallonta,
Tana rikeda hannunta har suka fice daga cikin falon suka shiga wani tafkeken dakin
bacci wanda ke dauke da Italian bed pink colour,haka komai na cikin dakin kalarshi
pink domin hatta bed sheet din dake shimfide akan gadon pink colour ne,

"Ya sunanki?" Hajiya kubra ta tambayi Hafsat har lokacin tana rikeda hannunta,

Sai a lokacin Hafsat tayi magana tun shigowarta gidan,

"Sunana Hafsat.." Tabata amsa,

"Hafsat, kamarku daya da tilon 'yata kwaya daya amal shiyasa lokacin da naganki
naji ina sonki har cikin zuciya..., nan dakinta ne ina so ki daukeshi a matsayin
naki, kiyi amfani da duk wani abu wanda kika ganshi acikin dakin nan ko kuma cikin
gidan nan.."

Sakin hannunta hajiya kubra tayi tajuya tafita, kan Hafsat adaure tafara bin dakin
da kallo tana yaba irin haduwar da yayi domin kamar akasar turai, kan gadon ta
kalla nan taga wasu jibga jibgan teddies guda biyu a jingine, kan mirror din dake
cikin dakin kuwa kayan make up ne jere tamkar wani dan karamin shago,

Kananan frames ta hango guda hudu ajiye akan bedside drewar nan ta nufi wurin domin
tahango kamar akwai hoton wata budurwa ajiki, nan ta nufi wurin da Sauri......

_*Ummi Shatu*_👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*12*

aishaummi.blogspot.com

***Gaban frames din hafsat ta karasa da sauri ta mika hannu ta dauki guda
daya ta kura masa idanuwa tafara kallo,

Gabanta ne yafara faduwa zuciyarta tana bugawa da karfi da karfi Wanda har saida ta
kaita da zama asaman gadon dake gefenta,
Ko shakka babu badan rayuwarta agidan marayu tayita ba to da zata iya yarda da
cewar wannan ta jikin hoton itace, sake kallon hoton tayi akaro na biyu wanda
yarinyar jiki ke sanye da english wears pink din riga da farin wando, kanta sanye
da hula pink colour,

"Ikon Allah..." Tafada ahankali tana mai sake dauko wani hoton tafara kallo, nan ta
lalace wurin kallon hoton batare data kosa ba.

Kasa koda zama hajiya kubra tayi illah kaiwa da kawowa da take ta faman yi dan
tsananin farin ciki, tabbas wannan wani al'amari ne daga Allah Wanda shi kadai
yabarwa kansa sani,

Ganin zama yagagara yasata fita ta nufi part din alhaji, shima shigowarsa kenan
daga masallacin dake kofar gidansa,

Zama tayi akan kujerar dake makotaka da tashi,

"Alhaji nidai kaganni tsabar farin ciki nakasa zaune nakasa tsaye.."

Murmushi alhaji sa'id yayi,

"To in banda abinki hajiya menene abin kasa tsaye da kasa zaune? Yanzu ina ita
yarinyar take?"

"Alhaji dole inkasa zaune in kasa tsaye mana,ai farin cikin da nake ciki bazai
barni inyi hakaba, tace min sunanta hafsat, tana can dakin amal nakaita tayi wanka
ta shirya sai tafito muyi dinner.."

"Hakan yayi daidai hajiya kubra,nidai abinda nakeso dake shine dan Allah ki rike
yarinyar nan bisa amana duk danasan zaiyi wuya ki gallaza mata tunda bata da maraba
da amal to amma wani lokacin ku mata ana ganin kamar kunfi kowa tausayi da rauni
sai dai akan gallazawa yaran da ba nakuba kunfi kowa nuna rashin tausayi da rashin
rauni, dan Allah ki riketa amana tunda kinga daga gidan marayu na daukota wannan
yana nuna cewar ita maraya ce..."

"Haba alhaji ai basai kayi min wannan nasihar ba domin ko wanine yakawo min wannan
yarinyar wanda bakai ba wallahi zan kula da ita..."

"Nasani hajiya kubra, Allah yayi miki albarka, yanzu ina tunanin ai tagama ko?"

"Ehh to bari indubo ingani"

Tashi tayi tafita takoma part dinta, dakin amal ta tura tashiga nan ta iske hafsat
zaune ta kurawa hotunan amal ido ko kifawa bata yi,

"Hafsat..." Ta kira sunanta bayan takarasa kusa da ita, dagowa hafsat tayi ta
kalleta,

"Na'am"

"Ya bakiyi wanka kin canja kayan jikinki ba? Tashi ki shiga bathroom kiyi wanka
indan kin fito ga drewar din kayan amal nan ki duba duk wanda yayi miki kisaka.."
Ta karasa zancen tana nuna mata drewar din da dan yatsanta,

"To" hafsat ta amsa har lokacin tana cike da mamaki domin ganin abubuwan dake
faruwa take yi tamkar acikin mafarki,
Fita hajiya kubra ta sake yi ganin haka yasa hafsat tashi ta shiga cikin bathroom
din, komai wanda ake bukata akwaishi acikin bathroom din babu bata lokaci tayi
wanka ta fito, man da zata dan shafawa fatarta ta shiga nema domin duk wadanda ke
kan dressing mirror din lotion ne dan haka dakyar tasamu wani me dan kama da
Vaseline tashafa,

Gaban drewar taje ta bude nanfa mamaki yacikata domin kayane iya ganinta shake
acikin drewar din,

Wata doguwar riga kalar ruwan hanta ta zaro da dan kwalinta tasaka ta dauki
hijabinta tayi salla,tana saman abin sallar azaune a inda aka kebe musamman domin
yin salla hajiya kubra tasake shigowa fuskarta dauke da murmushi,

"Hafsa kin idar ne?" Tajiyo muryar hajiya kubra na tambayarta,

"Ehh na idar.." Tabata amsa tana kokarin mikewa,

"Yawwa to taso kizo muje wurin alhaji"

Bin bayanta tayi suka fita, tiryan tiryan tana biyeda ita har suka shiga falon
alhaji sa'id Wanda ke zaune yana kallon labarai a tauraron dan adam,

Ganinsu yasashi rage volume din tv din ya fadada murmushinsa yana kallonsu domin
sai yake ganin kamar hajiya kubra ce da amal suke dososhi kamar yadda suka saba
akowanne dare domin yin hira,

"Alhaji...,labarai kake kallo?"

"Wallahi kuwa hajiya, keda 'yar takine?"

"Ehh amma har yanzu dai banga alamar zata sake ta saki jiki damu ba saboda ganinmu
take baki agareta" hajiya kubra tafada fuskarta da yar damuwa,

"To wannan kuma dama ai sai ahankali,kin san ai yau tafara ganinmu,sai asannu ko
Hafsat?" Yakarasa zancen cikin barkwanci,

Hafsat kam shiru tayi takasa koda kallonsu, sai dai wani lokacin ta dan saci
kallonsu ahaka har lokacin sallar isha yayi nan alhaji sa'id yafita masallaci
yabarsu a cikin falon nashi,

Anan Hafsat da hajiya kubra sukayi sallarsu,suna nan zaune har alhaji sa'id yadawo
dan haka hajiya kubra ta mike domin gabatar musu da abincin dare,

"Hafsat zo muje kitchen.."

Mikewa Hafsat tayi suka fita zuwa cikin kitchen wanda kallo kawai Hafsat ta bude
ido tanayi saboda ita ba taba ganin irin shi tayiba,

Akan babban faranti hajiya kubra ta jera flasks din abincin nan Hafsat din ta karba
ita kuma hajiya kubra ta debi filet da sauran abubuwan da suka kamata,

Zama Hafsat tayi bayan ta ajiye farantin, acikin dan madaidaicin filet hajiya kubra
ta zuba musu abincin, tuwon semo miyar danyar kubewa,

"Hafsat zo muci abincin.."

Matsawa hafsa tayi tasa hannu ita a zatonta iya ita da hajiya kubran ne kadai
zasuci amma sai taga sabanin haka domin shima alhajin saka hannu yayi saboda
al'adarsu tare suke cin abincin tare dashi da hajiya da amal, Hafsat ji tayi
kaunarsu ta fara darsuwa acikin zuciyarta, duk da cewar taki dan sakin jiki dasu
amma hajiya kubra sai sakota take acikin hirar tasu dahaka suka kammala cin
abincin.

Suna falon alhaji sa'id azaune har misalin karfe 9 nadare lokacinne hajiya kubra
ta mike ta kalli Hafsat,

"Hafsa taso muje ki kwanta naga kamar bacci kikeji ko?"

Dan murmushin yake Hafsat tayi ta tashi ta kalli alhaji sa'id,

Dan rissinawa tayi, "Alhaji saida safe"

Cikeda fara'a ya amsa tabi bayan hajiya kubra suka fita,

"Abba zaki rinka cewa alhaji kinji, nikuma ummi saboda haka amal ke kiranmu, kinga
tunda yanzu kema mune iyayenki.."

Hajiya kubra tace da ita akan hanyarsu ta zuwa part dinta,

"Tohh Ummi.."

Dadi hajiya kubra taji jin Hafsat ta kirata da Ummi,

Sai da safe Hafsat tayiwa hajiya kubra tashiga daki,zama tayi akan gado tana mai
bin dakin da kallo.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*13*

aishaummi.blogspot.com
***Kasa bacci Hafsat tayi illa tunanin rayuwarta da take ta faman yi,

Ji tayi kamar ta fashe da kuka a sakamakon fadowa ranta da kawarta Amina tayi,

Duk da tasan abin atayata farin cikine saboda canjin rayuwar data samu amma duk da
haka tana jin radadi acikin zuciyarta na rabuwa da gidan marayu da tayi domin
tariga da ta saba da mutanen ciki,

Wadannan tunane tunanen da tarinka yi sune suka hana idonta bacci har aka fara
kiran assalatu, a kunnenta aka shiga sallar asubah nan ta tashi tashiga bathroom ta
dauro alwala tafito, salla tayi tareda addu'o'i masu yawan gaske, anan inda tayi
sallar anan bacci ya kwasheta.

Misalin karfe shida da rabi na safe hajiya kubra ta shiga cikin dakin ganinta
kwance tana bacci yasata juyawa tafita batare data tasheta ba domin ta fahimci
cewar tayi sallar asubah,

Hafsat dai bata samu damar tashi daga wannan baccin ba mai cikeda mafarkai iri iri
wadanda takasa tuno koda guda daya daga ciki lokacin data farka, ba ita tatashi ba
sai misalin karfe 10 zuwa da rabi, hajiya kubra kuwa ta leka dakin yafi sau akirga,

Zama tayi tana bin dakin da kallo kamar yanzu ne tashigo ciki, daga bisani ta sauke
idonta kasa ta mike, fita tayi acikin falo ta hango hajiya kubra tasha kwalliya
cikin wata shadda kamfala tana faman jejjera abin Karin kumallo akan dining table,

Sam hajiya kubra bataji fitowarta ba har saida tayi magana,

"Ummi ina kwana.."

Cikeda farin ciki hajiya kubra ta juyo ganin Hafsat atsugunne yasata kamo kafadunta
ta tada ita tsaye tana murmushi,

"Lafiya lau Hafsat, sai yanzu aka tashi? Ai na shisshiga dakin kinata bacci"

Murmushin yake Hafsat tayi,

"Ummi akwai abinda za ayi ne?"

"Kamar mefa Hafsa na?"

"Na aikin gida.."

"A'a Hafsa babu abinda za ayi, har ankammala gyara gidan ai, inada ma'aikata na
masu yimin komai da kika sani, girki ne kadai nake yin abuna dakaina, yanzu kije
kiyi wanka ki shirya ki fito mu karya lokacin abbanku shima ya fito"

"Toh" ta amsa tareda juyawa takoma cikin daki, wanka tayi ta shirya ta fito
zuciyarta cikeda mamaki na irin tarba da soyayyar da hajiya kubra ke nuna mata
wadda abisa dukkan alamu zata riketa amana kamar itace ta haifeta,

Atamfa ta saka dinkin riga da zanine pieces kalar atamfar kalar ruwan hoda,
hijabinta da tazo dashi tasa ta fita,

Lokacin data fita tuni har su hajiya kubra sun hau kan table suna jiranta, durkuwa
tayi tagaida Alhaji sa'id,

Fuska asake ya amsa gaisuwarta yakare maganar da fadin,


"Tashi, tashi, zo ga kujera ki zauna"

Mikewa tayi taje ta zauna akusa da hajiya kubra wacce tafara kokarin hadawa Alhaji
tea,

"Hafsa babu wasu hijaban ne akayan amal naga kinata saka wannan?"

"A'a ban duba ba"

"To ai kuwa inajin tabar hijabai dan bata tafi da komai nataba duk agida
tabarsu..."

"Ashe yar uwarta tabarwa bata saniba" Alhaji sa'id ya karbe zancen,

Dariya hajiya kubra tayi,

"Ai so nake idan ta sai sim ta kira inyi mata albishir"

"To ai kuwa da dai nine naso inyi albishir dinnan amma naga kina nema ki rigani.."

Dariya sukayi dukkaninsu inbanda Hafsat wacce dan murmushi kawai tayi,

Abinsu gwanin sha'awa suna karyawa suna hirarsu har suka kammala nan Alhaji sa'id
ya mike yana gyara babbar rigar dake jikinsa domin wurin aiki zai fita,

"Adawo lafiya, Allah ya kiyaye hanya" Hafsat tace dashi tana rakube ajikin kujera,

"Amin Hafsat, nidai abinda nakeso dake shine ki saki jikinki ki dauka cewar nan
gidanku ne sannan kuma mu iyayenki ne, kinji? Allah yayi miki albarka"

"Amin, amin..." Hajiya kubra ta amsa tana murmushi,

Juyawa yayi yafita hajiya kubra tana biye dashi ganin haka yasa hafsat tattare
kayan da sukayi amfani dasu wurin karyawa ta nufi kitchen, tana tsaka da daurayesu
hajiya kubra ta dawo daga rakiyar da ta yiwa alhaji,

"Ahh hafsat ai ban sakiba, waye yace ki wankesu? Nafada miki akwai masu aiki zasu
yi har wanke wanken"

"Babu komai Ummi nima gani nayi babu abinda zanyi shiyasa nace bari in wanke.."

"To shikenan ai kin kyauta, ke baki da son jiki ba irin amal ba, amal bata son
motsi nan da can koda yaushe tana nade akan gado kamar wata mage.."

'Yar dariya Hafsat tayi taci gaba da wanke wanken yayinda ita kuma hajiya kubra
taci gaba da bata labari akan amal wannan yasa Hafsat sake fahimtar cewar ba
karamin so hajiya kubra ke yiwa yar tata ba domin magana daya biyu sai ta sako
zancen amal,

Tsaf Hafsat ta gyare kitchen din bayan ta kammala wanke wanken, falo suka koma suka
zauna suka fara kallo atashar tauraron dan adam,

Wannan zaman da suka yi shine yabawa Hafsat damar sakin jiki sosai da hajiya kubra
domin ta dan warware suna yin hira har tana bata labarin irin yanda rayuwarta ta
gudana agidan marayu.....
_Fatan alkhairi ga masoya masu bibiyar labarin..!._

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*14*

aishaummi.blogspot.com

***Sosai hafsat ta sake da hajiya kubra domin hatta girkin rana tare suka
yi suka shiryashi akan table saboda alhaji sa'id yana dawowa cin abinci daga
office,

Har dare suna tare suna hira afalon alhaji sa'id wanda kusan rabin hirar ta amal
ce, yauma kamar jiya atare suka fita ita da hajiya kubra suka yiwa alhaji sai da
safe,

Yauma saida tayi karfin hali sannan tasamu bacci ya dauketa domin har lokacin tana
kewar gidan marayu da kuma kewar kawarta amina,

Washe gari da safe suna kan table suna karyawa amal ta kira mahaifinta,nan hajiya
kubra ta shiga murna domin bakinta yaki rufuwa,

Mikawa hajiya kubra wayar Alhaji sa'id yayi bayan sun kammala gaisawa shida amal
din, cikin farin ciki hajiya kubra ta fara yiwa amal albishir na zuwan Hafsat
gidan, Hafsat tana zaune tanaji bata dai jiyo abinda amal din taceba kawai dai taga
hajiya kubra ta mika mata wayar tana fadin,

"To shikenan bari abata.."

Karbar wayar tayi ta kara akunnenta nan taji muryar amal din kamar zata fasa mata
dodon kunne dan tsananin kara,

Tamkar dama sun san juna haka suka gaisa gamida yin sallama,

Cikin fara'a Alhaji sa'id ya mike domin fita adawo lafiya Hafsat tayi masa, zama
tayi shiru bayan fitarsu shida hajiya kubra,tunani tafara aranta na yanda kowa
agidan ke sonta da kaunarta tabbas ta yarda Allah shine kadirun ala man yasha'u
domin ya sauya rayuwarta ya kuma juyata acikin lokaci kankani,

Yanzu kam ta warware sannan tagama sakewa da hajiya kubra, abu dayane kawai ke
damunta shine kewar Amina tare da sauran jama'ar da ta dade da sani arayuwarta,

Haka dai ta rinka boye damuwarta taci gaba da zama tareda su hajiya kubra har tayi
sati biyu agidan, kullum da daddare sai hajiya kubra ko Alhaji sa'id sun kira amal
angaisa da ita, ita kuwa idan aka bata wayar domin su gaisa amal cewa take tana ta
dokin ganinta saboda taji yanda su umminta ke zuzuta tsananin kamanninsu da Hafsat
din,

Duk da cewar tana jin dadin zaman gidan kuma babu abinda ta nema tarasa amma hakan
bai hanata shiga damuwa ba, tana yawan tuna rayuwarta ta baya wadda tayita acikin
rashin gata da rashin galihu sannan uwa uba cikin maraici,wannan dalilin ne yasa
take burin ta bada tata gudun mawar domin aganinta wannan wata damace ta samu wurin
taimakon yan uwanta marayu,

Ganin kamar tana cikin damuwa yasa hajiya kubra tambayarta koda akwai abinda ke
damunta, bata boye mata ba ta sanar mata da gaskiyar bukatarta na son zuwa kaiwa
kawarta Amina wacce ke gidan Marayu ziyara,

"To ai duk wannan mai sauki ne Hafsat, idan kin shirya kiyi min magana sai insa
driver yakaiki.."

"Toh Ummi nagode madalla Allah yasaka da alkhairi, Allah ya..."

Dakatar da ita hajiya kubra tayi,

"Bana son godiyar nan Hafsat, duk abinda nayi miki kaina nayiwa, yanzu me zaki
kaiwa kawar taki?"

"Ummi girki kawai zanyi mata inkai mata domin wallahi hatta abinci wahala yake mana
acan.."

"To shikenan gashi nan sai ki zabi abinda zaki dafa mata,duk abinda zaki bukata da
akwai kuma kin san wurinda yake.."

Daga haka hajiya kubra ta juya tawuce cikin falo domin lokacin acikin kitchen suke
Hafsat tana wanke wanke saboda sam bata son zama batare da tayi dan wani aiki ba,

Shinkafa da miyar kaji Hafsat ta dafawa Amina cikin manyan food flaks guda biyu,
wanka tayi ta shirya cikin wata shaddar amal kalar ruwan toka,farin hijab tasa
tafito ta iske hajiya kubra zaune tana karanta wani English novel,

"Hafsat anfito?"

"Ehh Ummi nashirya"

"To driver yana waje yana jiranki, yanzu idan kin tafi sai yaushe zaki dawo?"

"Ummi zan dan jima saboda kinga rabona da Amina an kwana biyu.."

"To shikenan sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya.."

"Amin" ta amsa tareda fita ta shiga kitchen ta debi girkin da tayiwa aminan tafita
compound din gidan inda salisu driver yake jiranta,
Har wani nushadi takeji yau haka kawai saboda zataje taga Amina da sauran mutanen
dake gidan marayun.

****

Tunda yusleem yaji mami tace masa anjanye maganar aurenshi shikenan yasaki jiki
yayi watsi da maganar bai kara bi takanta ba amma ita mami abun yana nan aranta
domin har yanzu kullum cikin tanadin kayan aurenshi take, duk inda taji ankawo kaya
masu kyau ko masu tsada na mata sai ta siyo kuma zata nuna masa tace matarsa ta
siyawa wacce zai auro nan gaba, shidai baya magana sai dai yayi shiru amma kuma
shine zai biya kudin kayan da ta siyo wannan kam ko nawane baya shayin biya kuma
bai taba musu ba,

Yauma hakance tafaru lokacin da ya shigo gidan ya isketa afalo ita da wata mata
wacce ta Kawo mata kaya daga dubai, wasu dogayen riguna ne masu adon stones ajiki
hadaddu,

Daga rigunan mami taci gaba dayi tana jujjuya su, bayan sallamar da yayi bai sake
yin magana ba yasamu wuri ya zauna,

"Yusleem kaga rigunan nan daga dubai aka kawo kuma sunada kyau nayi sha'awarsu
mutuka ko zaka siyawa matarka..?"

Yaji sarai abind mamin tace amma bai amsaba, kasancewar tasan halin abinta yasata
daukar kala biyu, ja da kuma baka mai adon golden ajiki,

"Gashi na daukar maka guda biyu, duk guda daya 35 thousands ahakanma ragi tayi min
amma bahaka take sayarwa ba.."

Gyada kai yayi har lokacin baice komai ba saboda shidai baiga amfanin kayan nan da
mami ta dage taketa siya ba,

Saida mai kayan tatafi sannan yadubi mami wacce ke zaune har lokacin tana ta
dudduba rigunan tana yaba kyawunsu,

"Wai mami dan Allah meye amfanin wadannan kayan da kiketa siye?"

"Amfaninsu? Amfaninsu kake tambaya? Kaifa mukayi dakai zaka nemo matar aure, ko
kamanta? Ai zuba maka ido nayi ka gama zagaye zagayenka ka Kawo min wacce kakeso
idan kuma hakan ya faskara to ni bazan gajiya ba wurin sake nemo maka wata.."

Shiru yayi ya lumshe manyan idanuwansa tareda jingina da jikin kujerar da yake
zaune batare da yayi magana ba....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_

*15*

***Lokacin da Hafsa takarasa gidan marayun ba karamin dadin ganinta Amina


tajiba domin bata taba tsammanin sake yin tozali da itaba acikin rayuwarta,

Kebewa sukayi suka samu kasan wata bishiyar darbejiya suka zauna suka fara
tattaunawa,

"Hafsa har kinyi kyau, ki ganki yanda kika sauya lokaci daya" Amina tace da Hafsat
tana bin jikin Hafsat din da kallo,

"Amina kema insha Allah canji yana nan zuwar miki ai tunda mukayi hakuri da rayuwar
da muka samu kanmu to da izinin Allah zamu dace da samun babban rabo.."

"Hmmm abar kaza dai kawai acikin gashinta hafsa, yawwa baki bani labarin yanda
akayi ba rannan da kika tafi.."

Kwashewa duk yadda akayi hafsat tayi tafadawa amina da irin gatan da take samu
yanzu,

Sun dade suna hira domin sai da la'asar liss sannan hafsat tatafi nan dinma kamar
kada su rabu da amina saida hafsa tace ai zata rinka zuwa akai akai sannan hankalin
amina ya kwanta.

Lokacin da hafsat takoma gida har alhaji sa'id yadawo daga office yana zaune a
falon hajiya kubra shida ita bayan ya kammala cin abinci kasancewar yau bai dawo
yin lunch ba,

Sallama tayi tashiga bayan sun amsa mata,

"Hafsa yau kuma ziyara aka kai?" Alhaji sa'id ya tambayeta yana murmushi,

"Ehh Abba" tabashi amsa,

"To ai yayi kyau, kin kyauta mutuka wannan ya nuna min cewa bazaki manta dasu ba
duk abinda kika zama nan gaba"

"Ai da alama kam hafsat bazata manta dasu ba" hajiya kubra ta karbe zancen ta
hanyar bawa alhajin amsa,

Zama hafsat tayi acikin falon tana sauraren hirar da su alhaji keyi wanda basu suka
tashiba sai da sukaji anfara kiran sallar magrib.

Satin hafsat uku agidan amma kai idan kaganta zakace wata uku tayi domin tayi
kiba tayi bul bul sosai, domin tana samun kulawa sosai daga iyayen rikon nata ga
gata da suke nuna mata kamar sune suka haifeta,

Malamai guda biyu musamman alhaji sa'id ya daukosu domin su rinka koyar da ita
karatun boko da na Arabic, sannan kuma yayi mata register a wata center ta mata
wacce ake koyar da sana'o'i saboda tana son tasake samun kwarewa sosai akan sakar
da ta iya,

Wadannan abubuwan da tasaka agaba sune suka saka bata da lokacin kanta yanzu koda
yaushe tana da abinyi amma hakan bai hanata ware lokaci na ziyartar kawarta amina
ba,

A fannin sakar ma tafi maida hankali domin hajiya kubra tafada mata cewar idan har
ta gwanance to zata siyo mata keken saka kuma tanada shagon saida kayayyaki zata
bata jari tafara saka kaya ana kaiwa shagon ana sayar mata wannan dalilin ne yasa
ta bada himma sosai har ta samu kwarewa kamar yadda hajiya kubran keso,

Satinsu shida aka yayesu domin sun iya sosai, alkawarin da hajiya kubra ta daukar
mata ta cika ta hanyar siyo mata keken saka harda sabuwar wayar hannu dambasheshiya
mai kyau kirar kamfanin LG,

Murna wurin hafsa sai wanda yagani, samun keke da tayi sai yasake rike lokacin ta
koda yaushe tana kai tana aiki acikin satittika kadan ta saka kaya masu yawan
gaske, kayan sanyi na yara da towel da safa da hula,

Diban kayan akayi aka kai shagon hajiya kubra na kasuwa acikin satin aka Kawo kudin
kayan domin har sun kare,

Kiranta hajiya kubra tayi itada alhaji sa'id domin suji ra'ayinta dangane da kudin,

"Hafsat kudin naki ajiyewa zakiyi a banki ko kuma wani abu zaki siyo ki ajiye?"
Alhaji sa'id ya tambayeta,

"Abba ba ajiyewa zanyi ba, kaya nakeso insiya inkaiwa gidan marayu gudun mawa"
tabashi amsa idonta yana kallon kasa,

Murmushi Alhaji sa'id yayi,

"Allah sarki hafsat hakika ke tagari ce kuma kinada hankali da nutsuwa, Allah yayi
miki albarka, yanzu abinda za ayi shine, gobe idan Allah yakaimu zan hadaki da
driver sai yakaiki kasuwa ki siyi duk abubuwan da kike ganin zaki siya sai kuje ki
kai musu.."

"Allah yabaki lada ya biyaki da gidan aljanna kinji.." Hajiya kubra tayi magana
cikin marerecewa,

Tashi hafsa tayi tafita domin malamin dake koyar da ita karatun arabi duk yamma
yazo yana jiranta.

Washe gari kamar yadda alhaji sa'id ya alkawarta haka yasa driver ya dauketa
yakaita kasuwa tayi siyayya wadda saida ta karar da kudin tass ko kwandala baiyi
saura ba, daga nan gidan marayu suka wuce, koda sukaje kuma akaga irin gudun mawar
da takai saida kowa yayi mamaki domin kayane na amfanin yau da kullum irinsu
sabulun wanka da na wanki, omo, sugar, man shafawa da makamantansu,

Rungumeta Amina tayi tana kukan farin ciki tareda yi mata addu'ar alkhairi, bama
Amina kadai ba kowa addu'ar da yake yi mata kenan....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*16*

***Haka rayuwar Hafsat taci gaba da tafiya akoda yaushe burinta shine taga
ta taimakawa yan uwanta marayu wadanda basu samu gataba suke zaune acikin gidan
marayu,

Rikon da hajiya kubra keyi mata kuwa rikone na tsakani da Allah wanda ko yar
cikinta iya abinda zata iya yimata kenan,

Kasancewar Hafsat din ta maida hankali akan karatuttukan da ake koya mata yasa
malamin dake koyar da ita fadawa Alhaji sa'id cewar lokaci yayi wanda yadace asata
a makaranta duk da cewar bata faro karatun daga tushe ba amma yana kyautata zaton
cewar zata iya, shawarar malamin Alhaji sa'id yabi aka sa Hafsat din awata
makaranta ta day,

Zuwanta makaranta yasata sake samun gogewa da wayewa domin ta hadu da yan mata
irinta wadanda suka fita wayewa,

Haka rayuwarta taci gaba da gudana sannan duk da ta shiga makaranta hakan bai
hanata cigaba da yin saka ba tana saidawa idan ta hada kudin sai taje kasuwa tayi
siyayya kamar yadda tasaba ta kai kayan gidan marayu.

Kwanci tashi har Amina kawarta ta samu mijin aure daya daga cikin ma'aikatan gidan
marayun ne zai aureta,ba karamin dadi Hafsat tajiba domin Amina itama zata bar
rayuwar kunci da talauci gamida maraici, tareda ita aka gudanar da komai aka daura
aure suka rakata gidan mijinta wanda keda makobtaka da gidan marayun.

Akwana atashi ahaka Hafsat tashiga aji biyar na secondary domin dama a aji hudu
aka sakata, kuma acikin wannan lokacin ne amal tazo gida hutu daga kasar Malaysia,
kai idan kagansu kamar wasu yan biyu domin ko Alhaji sa'id dakyar yake iya banbance
su musamman ma idan suka saka kaya iri daya domin hajiya kubra tun zuwan Hafsat
gidan iri daya take yimusu dinki tareda amal bata taba banbantawa ba,

Saida amal tayi wata uku sannan takoma makaranta tana cike da kewar Hafsa domin
komai tare suke yi gashi jininsu ya hadu sosai, itama Hafsat din tana mutukar
kewarta.

***
Abangaren yusleem kuwa har yanzu bai fitar da matar aureba duk kuwa da irin
Matsin lambar da Mami keyi masa akan ya zabo matar aure amma shiru to shi girman
kanshi ma bazai barshi ya tunkari mace da maganar soba,

Kullum idan yaje gidan Mami sai ta tisashi agaba da tambayoyi amma sai dai yayi
mata shiru daga karshe ma sai cemata yayi shifa har yanzu bai samu budurwar ba,
kyaleshi Mami tayi ta zuba masa ido domin ta dade da sanin cewar aljana ce ta
aureshi.

***

Misalin karfe 2:30 narana agogon hannunta ya nuna, dan karamin tsaki taja ta fito
daga cikin motar tata ta kulleta ta tsaya bakin titi tana jiran adaidaita
sahu,kallo daya kawai zaka yimata ka fahimci ko wacece ita domin sanye take cikin
atamfa exclusive purple colour da mayafi shima purple sai takalmi da jaka duk
purple colour,

Bakowa bace face Mami wadda ta dawo daga al hikima clinic dubiyar yar kawarta
hajiya maryam wacce aka yiwa cs adaren jiya, ganin motarta ta bata matsala yasata
tsayawa tanata kiran driver dinta amma bata sameshi ba wannan dalilin ne yasata
barin motar awurin ta zabi tasamu adaidaita sahu yakaita gida inyaso daga baya sai
drivern yazo ya dauki motar,

Adaidaita sahu ta tare tashiga yaja suka tafi, akan hanyarsu ne daidai queen ihsan
restaurant akofar wata private school ta hangi wata yar budurwa tana tsaye sanye da
uniform wanda yayi mutukar karbarta tana tare adaidaita sahun,

Da a niyyar Mami ta dauki drop yakaita gida kawai amma ganin budurwar wacce da
alama itama agajiye take sannan ga rana yasa mami barin mai adaidaita sahun ya
tsaya yadauki budurwar,

Lokacin da budurwar ta shigo ciki saida tagaida mamin, binta da dan kallo mamin ta
yi tana yaba hankalinta,

"Hajiya ina zan saukeki..?" Mai adaidaita sahun ya tambayi budurwar,

"A titin fahad mangul zan sauka.."

"Ok to sai nafara sauke wannan hajiyar kenan saboda ita a madaci road zata sauka"

"Babu damuwa" inji budurwar,

Suna tafe dukkaninsu sunyi shiru saiko karar radio din da mai adaidaita sahun ya
kunna dahaka suka karasa gidan mami, hand bag dinta ta bude ta fito da karamar
jakar hannunta ta fiddo naira dari biyar ta mikawa mai adaidaita sahun, key din
motarta da yafadi ta dauka ta fita tana gyara mayafinta,

Saida sukaje kofar gidan su wannan budurwar tana shirin fita bayan tabawa mai
adaidaita sahu kudinsa sai kawai tayi ido hudu da yar karamar jakar hannun Mami
wacce ta Jefarta aciki bata kulaba lokacin da zata dauki key din motarta,

Batayi magana ba tasa hannu ta dauki jakar tafita batareda tabari mai adaidaita
sahun yaganiba....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_Dedicated to MISS XOXO_

*17*

***Tana makale da jakar acikin hijabinta ta shiga gida, afalo ta iske


ummi tana lissafin wasu kayan yara da aka Kawo mata domin ta sara,

Ganinta yasa ummin yin murmushi,

"Hafsa na yau kam nayi miki laifi driver baije ya daukoki ba na aikeshi bakin
kasuwa shagona yaje yakai kayan nan da aka Kawo jiya kinga shine har yanzu bai
dawoba.."

Murmushi Hafsat tayi tazauna tana cire takalmi da safar dake kafarta,

"To ai babu komai ummi tunda gashi nadawo.."

"Ame kika dawo?"

"Adaidaita sahune dama kuma inada canji acikin jakata, kinga ma har na tsinci jakar
wata mata wacce muka zauna tareda ita aciki" takarasa maganar tana nunawa ummin
jakar,

"Yarwa tayi? To yanzu taya zaki ganta har abata, kodai cikiya zamu kai gidan
radio?"

"Ai naga gidanta ummi, naga gidan data shiga koda ace ba gidanta bane tunda dai nan
taje idan naje ai zan sameta"

"To shikenan tunda kinga gidan da taje sai kije ki kai mata koda gobe ne"

"To ummi Allah ya kaimu"

"Amin, kije kicire uniform din ki shiga kitchen akwai abinci yana nan"

"Toh" ta amsa tareda mikewa ta shiga bedroom dinta.

Washe gari da yamma ta shirya bayan tayi wanka, wani jan leshi tasa mai adon blue
ajiki, farin hijab tasa tafito tana rikeda jakar data tsinta,

A balcony tasamu hajiya kubra zaune ta dan kishingida tana sauraren radio,

"Ummi bari inje indawo"


"To hafsa sai kin dawo, zaki gane gidan dai ko?"

"Ehh zan gane, to kije ku tafi da salisu driver sai yakaiki"

"Toh ummi" ta amsa tareda wucewa,

Abakin gate ta iske drivern yana zaune wurin mai gadi suna hira, ganinta yasashi
tasowa domin yagane unguwa zasu fita, gidan baya yake kokarin bude mata taki
tahanyar bude gidan gaba tashiga ta zauna.

Mami kuwa tunda ta koma gida take faman duba yar karamar jakarta domin makudan
kudi ne aciki sannan uwa uba akwai muhimman abubuwanta aciki irinsu katin shaidar
dan kasa, gashi ATM card dinta yana ciki,

Ganin bata ganta ba ya tabbatar mata da cewar jefarwa tayi, zama tayi tasoma kiran
wayar yusleem amma shiru bai daga ba har takatse tasake kira, saida ta kirashi sau
uku bai dauka ba,

Tana kokarin tashi taji shigowarshi domin shi shigowarsa cikin gidan ma daban banci
dana kowa saboda awani hankali yake bude kofa ya rufeta,

Yana shigowa ko zama baiyi ba tafara magana,

"Kana inane haka nayita kiranka bakai picking ba? Nafita da mota ta dazu tabani
matsala akusa da al hikimah clinic naje duba yar gidan hajiya maryam"

Saida ya zauna yadan jingina kanshi da jikin kujera sannan ya kalli mamin yayi
magana,

"To amma mami meyasa zaki fita ke kadai? Meyasa baki tafi da driver ba? Saboda irin
wannan na ajiye miki driver fa"

"Yusleem drivern ai baya nan yatafi gareji gyaran daya motar tawa shine naga basai
na jirashi ba gara kawai naje nadawo"

"To meye matsalar motar?"

"Ina zan sani, tana can nabarta awurin ai saboda taki tashi, ni duk ma ba wannan
ba, jakata na yar ahanya ko akofar gidan nan ko kuma acikin adaidaita sahun da
nahau.., Kiran da naketa yi maka dama shine so nake kayi maza kaje bank kakai repot
saboda ATM card dina yana cikin jakar"

"Mami shiyasa ai nace kidaina yawo dashi.."

"Babu komai, kai ai ba a ketarewa kaddara"

"To Allah ya rufa asiri, bari naje"

Tashi yayi yafita ita kuma ta mike zuwa cikin bedroom dinta.

Har mami ta fidda rai da samun wannan jakar kwatsam washe gari da yamma tana falo
zaune tana kallo gabanta kuma snacks ne ajiye tana dauka jifa jifa tana ci taji
sallama,

Amsa sallamar tayi tadan gyara zamanta tana jiran wanda keyin sallamar yashigo,

Wata yar budurwa tagani wacce kamar ta dan san fuskar amma dai bazata iya tunawa
yanzu ba,
Ciki Hafsat ta shiga ta tsugunna tagaida mamin,

"A'a tashi mana, tashi ga kujera nan ki zauna" ita Mami ma duk tunaninta ko kawar
surayya ce,

"Hajiya dama jiyane bayan mun saukeki a adaidaita sahu mun tafi yakaini gida sai
naga jakarki kin mantata aciki shine nakawo miki yanzu..." Hafsat ta kammala zancen
tana mikawa mami jakar.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*18*

***Cike da mamaki Mami take kallonta bayan ta amshi jakar tata daga
hannunta,

Tabbas wannan jakar tace nan tayi hanzarin bude jakar tafara duba kudinta da
abubuwanta dake ciki,

Tsawon mintuna biyu tayi tana duban cikin jakar kafin ta dago fuskarta kunshe da
mamaki saboda yanda ta yasar da jakar haka take babu abinda aka taba bare har
acanja masa muhalli,

Ita kam Hafsat komawa tayi ta zauna bayan tabawa mami jakar, hankalinta kwance
lokacin da taga mamin tana kokarin duba jakar saboda yanda ta tsinceta haka ta
ajiyeta bata kara koda tabawa ba sai yau dinnan da zata Kawo mata,

"Yan mata ya sunanki?" Mami ta tambayeta fuskarta dauke da fara'a,

"Sunana Hafsat hajiya"

"Hafsat gaskiya kadanne irinku yanzu aduniya domin ba kowane zai tsinci makudan
kudi da sauran muhimman abubuwa ya mayarwa mai kayanba sai wanda yake mutukar jin
tsoron Allah, dama ni tun farkon ganin da nayi miki wallahi nayaba da hankalinki da
nutsuwarki sannan lokaci guda naji kin shiga raina,nagode madalla..."
Dan murmushi hafsa tayi akaro nafarko domin jin dadin yabon da mami tayi mata,

"Ai babu komai hajiya, nima nagode Allah yabar zumunci"

"Ai nice da godiya hafsa, wallahi naji dadi mutuka domin ATM card dina yana ciki
niduk dashi nafi damuwa ma wallahi saboda yarana sun koma makaranta last week to
kuma yayansu account dinshi yadan samu problem babu damar ya tura musu kudi shine
yasaka musu kudin a account dina inyaso sai atura musu tanan..."

"Ayya Allah sarki Allah yabasu sa'a"

"Amin amin, ai da har natura shi ma bankin yaje yakai musu report saboda kar asamu
matsala sai gashi kuma kin Kawo min, wallahi nagode miki mutuka"

"Hajiya wallahi babu komai dama tunda naganta nace taki ce domin mu biyu ne
aciki.."

"Allah sarki, kuma sai kika gane gidan nawa ma"

"Ehh dama nace koda ace banan ne gidan nakiba to zan Kawo saboda nasan kila idan
nayi musu kwatance su ganeki.."

Murmushi mami tayi ta mike cikeda fara'a akan fuskarta,

"Allah sarki,Allah yayi miki albarka.."

Dining area taje,jimm kadan sai gata ta fito rikeda dan madaidaicin farantin
silver,

Agaban Hafsat ta ajiye farantin tasake komawa ta dauko mata cup da juice na roba
takawo mata,

Kallon farantin Hafsat tayi taga dambun nama ne da snacks,

"Ga lemo nan kisha kinji 'yata, ai ni danaga kin shigo nazaci kawar yatace surayya"

"Au Allah sarki ai inajin ma banma santa ba.."

"Ehh gaskiya bazaki santa ba saboda ba anan takeba tana can akasar Malaysia tana
karatu yanzu haka saura shekara daya da yan watanni ta kammala, akwai kuma yayunta
maza guda biyu Abdul da khalifa suma suna outside suna karatu sai babban yayansu
shi yana nan anan.."

"Allah sarki" Hafsat tafada tana kallon agogon wayarta,

"Hajiya bari inje intafi saboda mamana tace kar injima"

"To ai hafsa bakici snacks dinba kuma ko juice dinma baki shaba"

"Babu komai hajiya, akoshe nake wallahi nagode madalla"

"To tsaya, ina zuwa" mami tafada tareda mikewa tashiga bedroom dinta tafito,

Kitchen ta wuce Jim kadan ta sake fitowa,

"Hafsat to ai sai ki fada min a inda gidanku yake ko saboda inason zan hadaki
kawance da yata surayya, koda yake bari sai insa driver yakaiki kinga sai yagano
min gidan ko"
Fuskar hafsa da murmushi tace,

"Hajiya nima driver ne yakawoni, kuma gidan namu ma bashida wuyar kwatance"

"To duk da haka dai zansa driver yabiku ya gano gidan naku"

"To shikenan hajiya nagode"

"Yawwa ga wannan babu yawa"

Dan tsorata Hafsat tayi saboda ganin girman ledar da mami ke mika mata,

"A'a hajiya bazan karba ba, nagode madalla amma kibarshi"

"Haba Hafsat karki maida hannun kyauta baya mana"

Dakyar dai mami tasamu har Hafsat ta karbi kayan, rakiya mami tayi mata har
compound din gidan, nan sukayi sallama Hafsat tashiga mota drivern mami yana biye
dasu suka fice daga gidan,

Kallon Salisu driver Hafsat tayi bayan sun hau titi sakamakon wasu kaya da tagani a
sit din baya,

"Wannan kayan fa?"

"Nakine, daga ciki wannan matar tasa aka fito dasu tace asa miki acikin mota"

Sake waiwayawa Hafsat tayi ta kalli kayan nan taga katan din juice guda daya sai na
biscuit shima guda daya sai snacks da dambun nama cikin wata leda mai dan kyalli,
murmushi tayi tana yaba kirkin mami acikin zuciyarta wato duk abinda takai mata da
bataci ba shine saida aka biyota dasu,

Har gida drivern mami yarakasu saida yaga shigarsu ciki sannan yajuya yakoma....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*19*
***Da murna akan fuskarta ta shiga cikin falon hajiya kubra, zaune ta
sameta akan carpet tana goge wata doguwar rigarta mai dan santsi,

"Ah Ummi akan kibari nadawo sai ingoge miki shine kike yi da kanki?"

Hafsat tafada bayan tayi yozali da hajiya kubran,

"A'a Hafsat to ai bawani aiki ne mai yawaba, zaman kadaici ne ya isheni shine
nadauko ina gogewa, abbanku ma kinga har yanzu bai dawoba nayi masa waya yace yana
gidan abokinshi sunje meeting"

"To Kawo in karasa miki.."

Mika mata iron din hajiya kubra tayi tana cewa,

"Abinda yasa ban hada da ita acikin kayan gugar nanba bana so akona min itane tunda
kinga tanada santsi..."

"Wannan kam sai anbita ahankali"

Bude kofa akayi aka shigo, Salisu driver ne yashigo bakinsa dauke da sallama,

Kayan da Mami tabaiwa Hafsat yashigo dasu ya ajiye yafita,

Saida Hafsat tagama goge duguwar rigar sannan ta tashi taje ta kinkimo kayan takawo
gaban ummin tana fadin,

"Ummi kinga wai daga zuwa shikenan matar nan ta hadoni da wadannan kayan.."

Cikin fara'a hajiya kubra tafara bude babbar ledar da mami tabawa hafsan,

Manyan turarruka ne masu kamshi guda biyu irin na larabawa sai mansu da sabulai
suma masu kyau sai abin hannu da sarka fation amma kuma mai mutukar kyauce,

Kallon kayan Hafsat keyi cikeda mamaki haka itama hajiya kubra mamakin ne ke
bayyane akan fuskarta,

"Hafsa anya kuwa duk murnar mayar da jakar nan zatasa matar nan tabaki wadannan
uban kayan? Anya kuwa?"

Murmushi Hafsat tayi ta gyara zamanta,

"Wallahi Ummi nima dai haka nace to amma yanda naga ta sake dani tanata yimin hira
tana bani labarin yaranta sai nima nadan saki jiki domin harfa cemin tayi wai
tanada yarinya budurwa tana kasar waje tana karatu idan ta dawo zata hadamu
kawance.."

"Kawance...?" Hajiya kubra ta tambayeta tana dariya,

"Wallahi haka tace Ummi, kinga fa har drivern ta taturo ya biyomu wai yazo yagane
mata gidanmu.."

"Allah sarki ai akwai mutane masu kirki a duniya, wasu sunada son jama'a.."

"Wannan kam tanada son mutane wallahi Ummi, kinga snacks din wai dan banci ba shine
ta hado min dashi"

Jan kayan sukayi suka ciro suna dubawa, cake ne da meat pie da sauran tarkacen
snacks,

Ajiyewa kayan sukayi har saida Alhaji sa'id yadawo suka nuna masa, tun daga wannan
rana ita hafsa tama manta da batun mami amma ita kam mami Hafsat tana makale
aranta,

Ranar alhamis da rana ta dawo daga super market siyayyar kayan amfanin gida ta biya
ta gidansu Hafsat,

Hajiya kubra tana kitchen tana kokarin sauke girkin rana da tayi taji sallamar
mami, da fara'a ta karbeta tamkar dama ta santa tayi mata jagora zuwa cikin
falonta,

Ruwa da abinci da juice takawo mata sannan tazauna suka fara gaisawa,

"Hmm nace yarinyarki kuwa tana nan?"

"Wacce daga ciki?"

Murmushi mami tayi ta daga kanta takalli hoton amal wanda ke kafe ajikin bangon
dakin wanda sak bashida maraba da Hafsat,

"Wannan, gata nan ajikin hoto" mami tafada tana murmushi,

"Ayya to ai tana makaranta, tatafi school tun watanni hudu da suka wuce"

"A'a, anya kuwa? Ai naga last week takai min jakata dana yar acikin adaidaita
sahu.."

"To ai shiyasa nace miki wacce aciki domin su 2 ne kuma duk kamanninsu daya,wannan
wacce kika nuna amal ce.." Hajiya kubra tafada tana dariya,

"Allah sarki to ba wannan nake nufiba, dayar nake nufi wacce taje gidana tace min
sunanta hafsat"

"Ehh,itama tana makaranta amma karfe 2 zata taso.."

Kallon agogon hannunta mami tayi, karfe 12:30 narana,

"To gashi nikuma sauri nakeyi, idan tazo agaisheta, zanje intafi"

"Insha Allah zataji, gashi bakici abincin ba"

"Alhamdulillah, nagode sosai"

Tashi tayi tafita nan hajiya kubra ta bi bayanta ta rakata har bakin gate mami kuwa
sai jaddadawa take cewar agaida Hafsat idan tazo,

Koda hafsat tadawo hajiya kubra tafada mata murmushi kawai tayi batace komai ba,
ita harkokin gabanta kawai takeyi yanzu daga makarantar boko sai makarantar
islamiyya kuma cikin hukuncin ubangiji duk tana fahimtar karatun nako wanne fanni,

Bayan sati biyu da zuwan mami tasake komawa ranar laraba da yamma amma ranar ma
bata samu hafsat ba domin tatafi islamiyya,

Sam bataji dadin wannan sabanin da suke yiba wanda har hajiya kubra saida ta
fahimci haka,

"Hajiya kiyi hakuri insha Allah zan turo miki ita gobe ko ranar juma'a, hafsan ce
wallahi uzururrukanta yawa garesu amma insha Allah zata zo miki.."

Sai lokacin damuwar dake kan fuskar mami takau har ta maye gurbinsa da murmushi,

"To ina jira amma dai dan Allah hajiya kicika alkawari kuma ranar juma'a ma
yakamata ki turo min ita yanda zamu dade muna hira.."

"To insha Allah zata zo, agaida mutanen gida"

Sallama sukayi mami tafita tatafi, kamar yadda hajiya kubra ta alkawartawa mami
haka ta cika alkawari ta hanyar saka driver yakai Hafsat gidan ranar juma'a da
musalin karfe 1 narana,

Lokacin da Hafsat taje gidan mami tana cikin bedroom dinta zaune agefen gado suna
yin waya da surayya jin sallama yasata fita ganin Hafsat dince tace ta karaso, har
cikin bedroom dinta takaita tace ta zauna agefen gado amma fur hafsa taki zama sai
akasa ta zauna kan dan madaidaicin carpet din dake shimfide akusa da gadon,

Wayar hannunta ta mikawa Hafsat,

"Ungo amshi ku gaisa da yar tawa surayya, ina zuwa bari inkawo miki ruwa kafin ku
gama"

Karbar wayar Hafsat tayi tana murmushi tafara kallon screen din wayar saboda video
call ne, surayyan ma daga can kurawa screen din ido tayi tana kallon Hafsat nan
suka shiga gaisawa kamar dama can surayya tasanta domin hira sosai take yimata,

Mami tana cikin kitchen tana warming din abinci yusleem ya shigo yana sanye da
farar shadda mai mutukar tsada kai idan kaganshi zaka dauka sabon ango ne saboda
tsananin kyawun da yayi dama kuma shi haka ka'idarshi take baya taba saka manyan
kaya sai ranar juma'a sai ko wani babban muhimmin abu,

"Har kadawo daga masallacin?" Mami ta tambayeshi tana kokarin sauke tukunya daga
kan wuta,saida yaje yadan jingina da jikin bango sannan ya amsa mata da,

"Ehhh, ina kukun naku yake naga kina girki dakanki mami?"

"Ba girki nakeyiba dumame ne nayi bakuwa ne shine zan kai mata abinci"

"Ok" shine kawai abinda yace yajuya zai fita, dakatar dashi mami tayi,

"Bazaka shiga ku gaisa da bakuwar tawa ba?"

"Ina zuwa mami, ai ba tafiya nayiba" daga fadin haka yasaka kai yafice,

Filet mami ta dauko ta zubawa Hafsat abincin, macaroni da miyar danyen kifi sai
abinsha da fruits, har mami takoma su Hafsat suna ta hira itada surayya wani dadi
mami taji wanda ita kadai tasan ma'anarsa acikin zuciyarta,

Saida mami ta karbe wayar tace Hafsat taci abinci sannan hirar tasu ta katse, kasa
cin abincin tayi saboda kunyar mami wanda har mamin saida ta fahimci haka, dakyar
dai tadan ci ta tattara kayan zata fitar mami ta hanata,

Wuni guda tayi domin sai la'asar sannan hajiya kubra taturo driver yadauketa, mami
kam wannan karon kaya sosai ta hada mata domin acikin kayan da take ajiyewa na
auren yusleem ta dauko mata duguwar riga dark blue da takalmi da turarruka,

Kin karba Hafsat tayi amma mami saida tasaka mata acikin mota tatafi da kayan,

Lokacin da takoma gidan hajiya kubra taga kayan rasa abin cewa tayi sai can ta nisa
tayi magana,

"Hafsat wannan matar haka zatayi ta miki hidima batareda wani abu aranta ba? Nifa
ina tsoron rayuwar yau domin wallahi akwai ayar tambaya aciki"

Murmushi Hafsat tayi,

"Wallahi Ummi babu komai sai alheri domin yau munyi waya ma sosai da yartata.."

"To shikenan tunda hakane"

Koda suka nunawa Alhaji sa'id kayan fada yashiga yi sannan yace kar Hafsat takara
zuwa gidan shi bai yadda da mami ba,

Tun daga wannan rana Hafsat bata sake zuwa ba amma da aka kwana biyu ita mamin sai
gata tazo, ranar kuma tayi Sa'a Hafsat din nagida tana kan keken sakarta tana
dinki,

Kyakkyawar tarba hajiya kubra da Hafsat din sukayi mata, ta dan jima agidan kafin
tayi musu sallama tatafi, sai bayan tafita ne maigadi yashigo da kaya wanda
takawowa Hafsat,

Kayan makulashe ne da turaruka masu tsada, ita kanta hajiya kubra yanzu tafara kuma
wani tunani akan mami Wanda dai tabarwa zuciyarta bata furta ba.

Lokuta zuwa lokuta mami kanzo ganin Hafsat kuma duk lokacin da zatazo bata zuwa
haka sai ta Kawo mata kayan makulashe irinsu biscuit, chocolate, sweet da sauransu
banda mayukan shafawa da turaruka, akwai wani lokaci da taje dubai tadawo tsarabar
da takawowa Hafsat abin ba acewa komai domin akwati guda medium ta ciko mata taf da
kayan sawa,

Shiyasa tun su ummi na zargin akwai wani abu aran mami har sun dawo sun daina daga
ita har Alhaji sa'id din,

Haka mami taci gaba da yiwa Hafsat hidima baji babu gani, lokacin da watan azumi
yakama kaya sosai mami tabada aka kai mata kamarsu fruits, madara, sugar da dai
sauran kayan hada tea da tarkacen kayan da akafi amfani dasu a lokacin azumi,

Ranar da aka kai azumi na 10 bayan ansha ruwa Hafsat ta shirya taje yimata sannu da
shan ruwa, suna zaune ita da yusleem yatashi yafita, yana fita Hafsat ta shiga, ba
karamin dadin ganinta mami tajiba nan ta cikata da kayan abinci iri iri,

Har Hafsat tabar gidan tatafi yusleem bai dawoba, da salla tazo kuwa mami kaya ta
dinkawa Hafsat kala biyar daya materia, daya leshi daya shadda biyu atamfa super
masu kyau da tsadar yan gaske kuma kowanne da takalminsa da mayafinsa banda turare
da sarka da abun hannu, wannan sallar saida Hafsat tasamu kaya kala goma domin
agida ma kala biyar Alhaji sa'id yayi musu itada amal,

Ranar salla kwalliya Hafsat taci bayan sun gama aikin Gida da hajiya kubra tace
mata zataje gidan kawarta Amina nan tatafi mata da abincin sallar da Ummi tayi
wainar shinkafa da miyar agushi,

Acan gidan Amina tawuni sai bayan sallar magrib driver yaje ya dauketa yamayarta
gida tana zuwa taga wasu sabbin food flasks zama tayi tafara budewa tana gani,
fried rice ce da kaza guda daya akai gasasshiya sai sinasir da miyar ganye wanda
yaji kaji,

"Ummi wannan abincin fa?"

"Daga gidan mamanki hajiya siyama aka Kawo miki abincin salla"

Murmushi tayi ta mike,

"Allah sarki mami kinga ni namanta ma ban kai mata abincin salla ba"

"Gobe ai sai ki kai mata idan zaki mayar mata da kwanukanta"

Washe gari hajiya kubra tayi girki musamman saboda mami shinkafa da miyar kaji
Hafsat ta shirya bayan taci kwalliya tatafi kai mata,

Da murna mami ta tareta tayi mata iso har cikin dakinta,

Zama tayi suka fara hira kamar yadda tasaba yi da Hafsat idan tazo mata, wuni cur
Hafsat tayi sai yamma tatafi.

Ahaka rayuwa taci gaba da wakana mami tana mutukar kaunar Hafsat kuma tana
kyautata mata wanda harsu hajiya kubra sun yarda da hakan adalilin hakanne ma
zumunci mai karfi yashiga tsakanin hajiya kubra da mami domin kawance sukeyi sosai,

Sannu sannu Hafsat ta kammala makarantar secondary wannan dalilinne yasa yanzu bata
zuwa ko ina sai makarantar islamiyya saiko dinkin sakarta wanda tasaka agaba,

Cikin weekend tashirya takaiwa mami ziyara,

"Hafsat ankammala karatu ko? Yanzu kuma me kikeda ra'ayin yi?"

Murmushi hafsat tayi,

"Mami karatu zanci gaba dayi"

"To hafsat banki ba amma dai da zakiyi aure shiyafi, idan kikayi aurenki sai kiyi
karatunki agidan mijinki"

"Hakane mami amma to wazan aura? Nida ko zance banay.."

"Dana zaki aura hafsat, yarona nakeso ki taimaka min ki aureshi, dan Allah kiyi min
wannan taimakon....!.

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*20*

***Cikeda mamaki Hafsat ta kalli mami saboda jin abinda tafada,

"Kidaina mamaki Hafsat sannan kuma narokeki dan girman Allah kada ki k'i amsar
bukatata domin yin hakan na iya zama dalilin faruwar abubuwa da dama ciki kuwa
harda dawwamar bacin rai da bakin ciki acikin zuciyata..."

Sunkuyar da kai Hafsat tayi tai shiru takasa yin magana acikin zuciyarta kuwa
tunani takeyi shin shi yaron mamin da take burin hadata dashi shine yaganta yake
sonta ko kuwa kawai mamin ce keda burin yin hakan a matsayinta na mahaifiyarsa
domin ita tunda take zuwa gidan bata taba ganin daya daga cikin yaran mamin ba kuma
surayya kadai ta sani har suke yin waya da ita,

"Hafsat ya naji kinyi shiru? Kodai bakya son dan nawa?"

Muryar mami ta katse mata tunaninta da takeyi,

"Mami to ai bai taba ganina ba kuma nima ba taba ganinshi nayiba.."

Murmushi mami tayi,

"Hafsat kenan ni awurina duk wannan ba wani abu bane kuma abune mai sauki domin na
isa da dana duk abinda nasashi baya k'in bin umarni na, matsalar dai kawai kece
idan baiyi miki ba,ga hotonshi nan akafe abango ta bayanki, juya ki gani..."

Waiwayawa Hafsat tayi cikeda mamaki ta kalli wurin domin tunda take shigowa bedroom
din mami Allah bai taba bata ikon damar kallon wurinba bare har taga hoton,

Hadadden saurayi tagani zaune akan kujerarshi ta office wanda abisa dukkan alamu
acikin office dinshi akayi masa hoton,

Farine kyakkyawa mai daukar hankali wanda baduk macece zata ganshi takau da idonta
a lokaci guda ba,fuskarshi zagaye take da saje mai hadeda kasumba,bakaken suit ne
ajikinshi wadanda sukayi mutukar amsarshi domin sun sake haska farar fatarshi,

Manyan idanuwanshi farare tatass ta zubawa ido har ta gangaro izuwa kan dogon
hancinshi mai tsini wanda yake daf da bakinshi dan madaidaici mai dauke da
zagayayyun lips wadanda suka kasance jajaye jur,

Ita kanta bata san tsawon mintunan data dauka tana karewa halittar yusleem kallo
ba,

"Masha Allah, tsarki ya tabbata ga ubangijin halittu wanda ya kawata halitta da


surar wannan bawan nashi.." Ta fadi hakan acikin zuciyarta wanda har lokacin takasa
dauke idanuwanta daga kallon hoton,

"Hafsat..." Taji mami takira sunanta sai lokacin ta iya tunawa ma da ashe mamin na
zaune wurin, cikin sauri ta dauke idonta daga kan hoton ta sunkuyar da kai cikeda
jin kunya,

"Hafsat ko baiyi miki bane?"

Shiru Hafsat tayi bata amsaba tasake sunkuyar da kanta kasa,

Juyin duniya haka mami tayi tana tambayar hafsat amma taki amsawa tayi shiru,

Murmushi mami tayi,

"To Allah dai yasa hasashe na yazama gaskiya hafsat idan har kuwa hakan ya tabbata
to nasan zanfi kowa farin ciki....."

Dan murmushi hafsat ta kuma yi cike da kunya,

"Insha Allah zanzo gidan gobe goben nan muyi maganar da umminki kafin asan ta inda
za afara kuma"

Mami tafadi hakan cikin jin dadi, ita hafsat yanzu sai taji tana jin kunya da kuma
nauyin mamin shiyasa taji duk zaman ta takura,

"Haba hafsat ai tsakaninmu babu yar surukunta, ki dauka cewa kece yata ba yusleem
ba, ko aurenku ya tabbata karkiji kunyar sanar dani laifinsa matsawar yayi miki ba
daidai ba.."

Shiru hafsat tayi takasa cewa komai,har mami takaraci maganarta ta gama bata iya
daga ido ta kalleta ba daga karshe ma sai cewa tayi zata tafi duk kuwa da cewar ba
wannan lokacin tayi niyyar tafiyar ba amma wannan maganar da sukayi da mamin itace
ta tilasta mata barin gidan.

Ko drivern gidansu bata zauna zaman jiraba sai mami ce tasa drivern ta yakaita
gida,

Hatta ummi saida tayi mamakin ganinta a lokacin saboda bata zaci zata dawo dawuri
hakaba,

Tambayarta ummin taringa yi akan dalilin dawowarta da wuri haka bayan kuma ba haka
tasaba dawowa ba idan taje,

"Hafsat ko unguwa hajiya siyaman zataje ne shiyasa kika dawo?"

"A'a Ummi babu inda zataje tana nan.."

"To meya faru?" Tasake tambayarta,

"Babu komai, tace zatazo wurinki gobe ma"

"Amma dai lafiya ko?"

"Ehh lafiya lau"

"To shikenan Allah yakaimu.."

Acikin zuciyarta ta amsa amin din bata bari ummin tajiba,


Ita kanta bazata iya fassara yanayin da zuciyarta ta karbi yusleem ba kawai dai
tanajinta cikin nishadi wanda bata san dalili ba,

Daren ranar tayishi ne batare da tayi isasshen bacciba.

Washe gari da safe misalin karfe 11 daidai nasafe mami tayiwa gidan sammako lokacin
Alhaji sa'id na nan ko fita baiyiba,

Jin zuwanta yasa Hafsat jin wata irin faduwar gaba duk sai taji jikinta yayi sanyi
dan dakyar ma ta iya zuwa suka gaisa daga nan ta koma daki ta kule bayan ta gabatar
mata da ruwa,

"Hajiya kubra yau dai zuwana yasha banban da wanda nakeyi ada domin dalilin zuwana
yau shine neman auren yata nazo.. Wato Hafsat"

Murmushi hajiya kubra tayi ta kalli mami,

"To ai bakiyi min gwari gwari yanda zan ganeba"

"Kamar yadda nafada miki nazone in nemarwa dana yusleem auren yarki Hafsat idan har
babu alkawarin wani akanta domin wallahi ina mutukar kaunarta kuma ina son inhada
jini da ku.."

Murmushi hajiya kubra tayi,

"To ai kema yarkice, amma yanzu abinda nake ganin za ayi shine abbanta yana nan bai
fitaba bari inje insanar masa"

"To shikenan"

Tashi hajiya kubra tayi tafita zuwa part din Alhaji sa'id mintuna Kadan sai gata
tadawo,

"Hajiya to bismillah zo mu karasa wurin alhajin"

Tare suka shiga suka iskeshi zaune kan kujera hannunsa rikeda jaridar weekly trust,

Gaisawa sukayi da mami tayi masa bayani kamar yanda tayiwa Ummi nan Alhaji sa'id
yace babu komai indai har Hafsat din ta amince domin ba za ayi mata doleba kawai
abinda za ayi shine suje su daidaita ita da yaron,

Cikeda farin ciki mami tayiwa Alhaji sa'id godiya ta mike tafita acikin ranta tana
ganin yanzu saura abu daya yarage shine tashawo kan yusleem....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*21*

***Falon hajiya kubra mami takoma tazauna tana jiranta zuciyarta cikeda
farin ciki wanda kana iya gane hakan karara idan har ka kalli kan fuskarta,

Tana nan zaune har ummi tafito daga sashen alhaji nan sukayi sallama ta rakata
tatafi, saida Hafsat taji fitar mami sannan tafito daga daki tazauna akusa da ummin
tana dan kallonta domin jin karin bayani amma kuma sai dai kunya takeji,

"Mamin naku tatafi yanzu nakaita wurin abbanku sunyi magana akanki keda danta,
abbanki yace yaron yazo ku daidaita mutukar kun amince kuna son juna to shi bashida
wata matsala..."

Shiru Hafsat tayi ta dan sunkuyar da kanta kasa tana murmushi,

"Nida naso kema kiyi karatu kamar yar uwarki amal to amma kin san kowa da yadda
Allah yake tsara masa rayuwarsa.., sai dai muyi fatan Allah yasa hakan shine yafi
alkhairi"

Har dai ummi tayi maganarta tagama Hafsat bata iya cemata ko uffan ba.

Cikin farin ciki marar misaltuwa mami taje gida tana shiga ta nemi wurin zama
ta zauna tafara lissafin abubuwan da ya kamata ta siyo ko ta hado domin bata
bukatar bikin nan yawuce watanni biyu masu zuwa kacal,

Paper da pen ta dauko ta zauna tana rubuta abubuwan da takeso tasiyo da adadinsu,

Yusleem ne yaturo kofar falon ya shigo yana sanye da farar riga jersey da blue din
trouser hannunshi rike da key din motarshi,

A kusa da mamin ya zauna ya jingina kamar yadda yasaba domin shi haka dabi'arshi
take kamar wani mai sarauta akoda yaushe cikin iko yake,

"Mami ina kwana..?"

Dagowa tayi ta kalleshi bayan tacire farin medical glass din dake kan fuskarta,

"Sai yanzu katashi ko? In ba hakaba yaushe za akira karfe 12 da safiya..." Takarasa
maganar tana murmushi,

"To ai mami weekend ne.."

"Ehhh tunda weekend ne sannan kuma kai kadaine baka da mata ai dole kayita bacci
har rana ta fito"

Murmushi yayi yana shafa kasumbar dake fuskarshi,

"Mami yunwa nakeji wallahi dan yunwar ce ma tafito dani daga gida"

"To me zakaci?"

"Abani tea banda bread, soyayyiyar agada da dankali amma banda egg"

Murmushi Mami tayi tana kallonsa,

"Ai matarka zata sha tsaraba kai idan katashi karyawa baka karyawa da abu guda biyu
kuma abin haushinma idan anbaka ba na kirki zakaci ba"

"Mami wallahi nima ina son infara cin abinci dayawa amma narasa meyasa bana iyawa,
but ina tunanin nanda 2 weeks zanje london so zan biya ta chairo naga dr dina"

"Da dai yafi maka amma mutum yarinka cin abinci kamar wani karamin yaro..."

Bai kara maganaba yaciro wayarshi daga aljihu yasoma latsawa, mikewa mami tayi
tafita takira kuku ta fada masa aikin da zaiyi tadawo wurin yusleem tazauna,

"Wai mami rubuce rubucen me kikeyi ne haka?"

"Ai zan fada maka, kwantar da hankalinka.."

Murmushi yayi yatashi yakoma kan 3 sitter ya kwanta,

Mintuna kadan kuku yashigo dauke da faranti wanda ya dorowa yusleem kayan breakfast
din akai,

Akan center table ya dora mishi yajuya yafita, tashi yusleem yayi yaja table din
gabanshi ya hada tea yasoma karyawa yanayi yana kallon mami wacce ta dukufa akan
rubutun da takeyi,

Saida ya kammala sannan mami ta dago ta kalleshi,

"Yusleem ya maganar auren da nace ka nemo, har yanzu baka samo yarinyar da tayi
maka ba ko kuma yaya?"

Dama tun shigowarshi saida jikinsa yabashi maganar aure mami zatayi masa,

Sai da yadan ja lokaci sannan yace,

"Mami meya faru kuma?"

"Babu abinda yafaru inaso ne inji idan har kasamo sai afara maganar auren idan kuma
baka samoba to ni nasamo maka..."

Sunkuyar dakanshi yayi yana nazari batare da yace komai ba, tabbas shikam yanada
farin jinin yanmata domin babu wahala yanzun nan budurwa tace tana sonshi sai dai
kuma sam shi baya bukatar auren ne,

"Yanaji kayi shiru?"

"To mami ai nazaci mun gama maganar nan"

"Dawa? A'a bamu gamaba, nidai ina son kasani nasamo maka yarinyar da zaka aura
nanda watanni biyu dan haka saika fara dukkan shirye shiryen da yadace amma wannan
karon kasani banyi maka aure dan ka sakar musu yarinya ba,

Sannan kuma inaso ka sama mana visa mutafi umarah domin muje inyi maka addu'a akan
Allah yarabaka da wannan aljanar da take tareda kai kuma yasa ayi auren nan cikin
sa'a yasaka albarka aciki"

Tunda mami tafara maganar baice uffan ba har tagama,

"Ina fata kaji maganganun da nayi maka kuma sun shiga cikin kunnenka?"

"Ehh naji"

"Yawwa to Allah yayi maka albarka Allah yasa ayi cikin nasara"

Bai amsaba yatashi yafita mami tarakashi da ido,

Kamar yadda mamin tafada acikin lokaci kankani yasamo musu visa suka tafi umarah
addu'a sosai mami tayi masa kan auren da zatayi masa bayan sun kammala umarah ne
yawuce London yabarta anan bayan tafiyarshi da kwana uku itama tawuce dubai domin
karasa hada lefenshi da siyan sauran abubuwan da za ayi amfani dasu abikin dan
hatta kayan da amarya zata saka duk saida tasai mata,

Saida ta kammala siyayyarta tsaf sannan tadawo Nigeria shikuwa yusleem har lokacin
bai dawoba, dawowarta babu jimawa tatura wakilan yusleem sukaje nemar masa auren
Hafsat agidan Alhaji sa'id wanda basu tahoba saida ranarsu, domin Alhaji sa'id ya
yanke ranar aure saboda ya fahimci cewar Hafsat din tana son yusleem,

Wannan abu ba karamin dadi yayiwa mami ba dan tsananin dadi aranar da daddare taje
gidan tayi godiya,

Aminanta da kawayenta ta gayyato suka kai lefen Hafsat wanda tsayawa fadar kayan
ciki bata lokaci ne, domin mami ta yiwa Hafsat lefe na alfarma irin lefen da tunda
yusleem yake aure ba ataba yin irinshi ba,

Yanzu gidajen guda biyu ko ina shirin biki sukeyi gadan gadan, Alhaji sa'id ya
sakarwa ummi kudi domin yiwa yartata siyayya, ita dai Hafsat bata katabus saboda
har yau bataga angonba kuma shima bai gantaba tana jin tsoron kar yaganta ya
rainata yace batayi masa ba domin tasan dama auren hadin mami ne,amma shikam bata
tunanin akwai wata ya macen da zata ce baiyi mataba,

Yusleem kuwa tunda ya Lula yatafi bai dawoba gyaran gidanshi ma wanda za ayi sai
yaronshi na office yasa yatsaya akai akayi aka gama aka gyara gidan tsafa aka sake
fenti,

Saida biki yarage saura kwana takwas sannan yadawo lokacin hatta kannenshi su Abdul
da surayya har sun zazzo daga makaranta, mami taso tayi masa fada amma kuma dayake
acikin farin ciki take sai ta shareshi taci gaba da harkokinta,

Surayya kam kanwar yusleem tattarawa tayi takoma gidansu Hafsat saboda acewarta ita
abangaren amarya take ba bangaren ango ba, Hafsat ba karamin dadi tajiba domin dama
ita kadaici kwal agidan take harkokinta domin Alhaji sa'id bai bar amal tazo ba duk
da tayi niyyar zuwa amma yahana,

Surayya ce taraka Hafsat akayi mata komai kama tun daga kunshi gyaran jiki da
gyaran kai wanda duk mami ce tadauki nauyin yin hakan,

Ana igobe daurin aure yusleem yaje gidansu Hafsat din wanda wannan dinma mamice ta
tilastashi, kamar zaiyi kuka yashirya yatafi bayan sallar isha,
Surayya yayiwa waya tana dauka taji yace,

"Ke turo min wannan yarinyar"

Sarai surayya tagane abinda yake nufi amma sai tayi fuska tace,

"Uhm yaya wafa?"

"Oho miki" yafadi tareda katse wayar,

Kallon Hafsat tayi tana murmushi,

"Angonki ne yazo yana waje yana jiranki"

Saida gaban hafsa yafadi saboda jin abinda surayya tace,hijabi tadauka ta kalli
surayya,

"Zo ki rakani dan Allah"

"Zan dai kaiki amma ina zuwa dawowa zanyi"

"Nayarda"

Fita sukayi gaba dayansu, afalo suka iske su ummi ita da jama'arta wadanda sukazo
suna yan aikace aikace,

Kanshi yana durkushe akasa yana latsa wayarsa dan haka ko fitowarsu bai ganiba bare
yaga zuwansu, surayya ce ta kwankwasa masa glass din dake saitinshi hakan yasashi
yin kasa da glass din yana kallonta, gaban Hafsat ne yashiga dukan tara tara haka
kawai domin gani tayi yusleem yafi kyau afili kuma tabbas shine mutumin da yake
taimaka musu lokacin da tana gidan marayu domin yataba zuwar musu sau daya sun
ganshi,

"Ina wuni.." Hafsat tace dashi tana kallon kasa,

Ko kallonta baiyiba ya amsa da "lafiya"

Daga haka babu wanda yakara magana acikinsu ganin haka yasa surayya tajuya zata
tafi dominated tabasu wuri nan yadakatar da ita yadauko rafar yan dubu dubu guda
daya ya mika mata yaja motarshi yayi gaba,

Hafsat ji tayi ko ajikinta balle abin ya dameta,

Washe gari aka daura auren Hafsat da yusleem da misalin karfe 2 narana akan sadaki
naira dubu hamsin.

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*22*

***Aranar da aka daura auren aranar alhaji sa'id yace aje akai Hafsat
gidanta duk da hajiya kubra bata so hakaba domin ita taso ace sai washe gari za
akaita amma tunda ga abinda alhaji sa'id yace dole babu yadda ta iya dan haka aka
fara shirin kai amarya dakinta,

K'arfe 9 daidai aka fito da Hafsat din daga sashen alhaji sa'id bayan ya kammala
yimata nasihar da ta dace duk wani uba yayiwa'yarsa a lokacin da za akaita gidan
miji, haka itama hajiya kubra ba abarta abaya ba wurin yiwa Hafsat fada akan tabi
mijinta kuma ta kyautata masa,

Inbanda kuka babu abinda Hafsat keyi domin tasan su hajiya kubra sunyi mutukar
kokari akanta kuma sun taka muhimmiyar rawa acikin rayuwarta wanda har abada bazata
manceba kuma bata da abinda zata iya biyansu da shi,

Wata tsadaddiyar mota ta alfarma kirar Lexus new series 2017 aka bude mata tashiga,
nan kannen hajiya kubra suka sakata atsakiya yayinda surayya kanwar yusleem tashiga
gaban motar,

Direct gidan mami aka wuce da ita inda mamin nacan ita da jama'arta suna zaman
jiran zuwansu,

Yanayin farin cikin da mami ke ciki abin bazai misaltu ba domin kana ganinta zaka
gane irin dunbin farin cikin da take ciki,

Har tsakiyar bedroom dinta aka shigar da Hafsat wacce ke tukunkune cikin wani
babban mayafi dark blue kalar leshin dake jikinta,

Rungumeta mami tayi tana fara'a,

"Barka da zuwa cikin zuri'ata 'yata,ubangiji Allah ya baku zaman lafiya ya kauda
fitina da duk wani sharri daga gareku, Allah yabaku zuri'a dayyibah, nidama tun can
a matsayin 'ya na daukeki kuma yanzun ma kina nan ahaka baki sauya ba, insha Allah
zamu rikeki amana"

Jin abinda mami tafada yasa kawayenta dake baibaye da ita sakin guda,basufi minti
talatin agidan mami ba aka wuce da Hafsat gidanta wanda ke can wata unguwa da ake
kira da babbar inuwa domin gaba daya mazauna unguwar shaharrun mutane ne wadanda
sukeda hannu da shuni,

Shi kanshi yusleem fadin girman gidansa da tsarinsa abune mai wahala domin gidan
yatsaru iya tsaruwa,
Cikin babban bedroom dinta aka shigar da ita ta zauna akan gefen makeken gadonta
samfurin Italy,

Saida yan Kawo amarya suka fita sannan Amina kawarta da surayya suka shiga cikin
dakin,

"Amarya kinsha kamshi, nidai bari inje intafi.." Inji Amina,

Dago jajayen idanuwanta Hafsat tayi ta kalleta,

"Haba Amina bazaki bari angwayen suzo ba?"

Dariya surayya tayi tareda bararrajewa akan gadon,

"Waye zai Kawo miki angwaye? Indai yaya yusleem ne Allah shi kadai zai zo gidan nan
garama kibarmu muje mu tafi, nidai dama kin san gobe da sassafe zanyi miki
asubanci..."

Jin abinda surayya tace yasa Amina tashi tsaye,

"To shikenan bari intafi, Hafsat sai nadawo ganin gida lokacin kin dawo cikin
nutauwarki domin nasan yanzu bakya tareda ita..."

"To Amina nagode, Allah yabar zumunci, nagode"

Tashi surayya tayi tabi bayan Amina suka fita tare,

Tsuru Hafsat tayi tana bin dakin da kallo wanda yasha furniture's na alfarma
kalarsu dark purple, duk tsoro yabi ya cikata saboda babu motsin komai agidan, ta
wuri daya hankalinta ya kwanta shine tasan akwai masu gadi acikin gidan wanda yanzu
haka suna can gate suna aikinsu,nan tazauna taci gaba da zuba idon ta Inda zataga
shigowar angonta.

K'arfe 10:30 yusleem yashiga gidan mami kasancewar yan biki suna nan basu
tattafi ba yasa gidan inbanda hayaniya babu abinda kakeji kamar dare baiyi ba,

Fitowa mami tayi wurinshi ta tsaya tana kallonsa, gaba daya ta fahimci bashida wata
walwala,

"Yusleem..." Ta kira sunanshi tana kallonsa,

"Na'am.."

"Kasan abinda nakeso dakai? Na hadaka da girman Allah yusleem ka rike Hafsat amana,
dan Allah karka cutar da ita, sannan ka taimaka ka rufa min asiri karka sakar musu
'ya, yusleem idan ka aikata daya daga cikin wadannan wallahi bazan yafe makaba
sannan ka nemi wata uwar amma baniba, Allah yayi maka albarka ya baka zuri'a
tagari"

Hannayenshi duka suna cikin wandon farar shaddar dake jikinsa yana tsaye yana jin
mami har ta kammala,

Gyada kai yayi batare da yace komai ba ya sunkuyar da kai,

"To kaje katafi mana"

"Ehh yanzu zan tafi, inasu Abdul suke? Ko shi ko khalifa wani yazo muje yayi
dropping dina saboda dama shu'aibu yaron office dinane yakawo ni kuma yawuce"
"To bari nakira maka daya daga cikinsu, ina zuwa"

Juyawa mami tayi ta nufi sashen samarin,da khalifa tafara yin arba dan haka shi
takirawo ta nuna masa yusleem a inda yake tsaye ya cire hularshi yana lanlankwasa
ta,

Batare data koma wurinshi ba tawuce zuwa ciki shikuma khalifa ya nufi wurinsa daga
nan wurin da aka tanada domin adana motoci sukaje khalifa yadauko guda daya yusleem
yabude yashiga suka fita daga cikin gidan,

"Yaya ka siyi yan abubuwanne?"

Kallon khalifa yusleem yayi,

"Mefa?"

"Wai da yaya ina nufin dan nama haka da sauransu.."

"Kaima yanzu bakada kunya kamar Abdul ko?" Yafada yana kallon titi,

"A'a yaya bahaka bane,nayi tunanin ko kamanta ne shine natuna maka"

Bai sake cemasa uffan ba har sukaje gidan nan yabude kofa yafita ya nufi ciki yana
takawa ahankali.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*23*

***Ahankali yaci gaba da takawa yana tafiya tamkar wani marar lafiya ko
kuma wanda yake jin tausayin kasar,

Hularshi yatura baya zuwa keyarshi ya zuba hannuwanshi acikin aljihun wandonshi
domin wani dan dari dari yakeji,

Babban falon dake girke atsakiyar part din guda biyu yabude yashiga, hanyar da zata
sadashi da bedrooms din Hafsat yabi har ya isa ga dakin da take ciki,tana
kishingide ta dan fara gyangyadi amma ba bacci takeyi ba,

Ahankali yatura kofar dakin yashiga, daga bakin kofa ya tsaya bayan yasake zuba
hannuwanshi acikin aljihun wandonshi,

Dan gyaran murya yayi kadan wanda hakan yayi sanadiyyar bude idon Hafsa ta tashi
zaune da hanzari,

"Zo...." Shine kawai abinda yace da ita cikin sanyayyiyar muryarshi yajuya yafara
tafiya, tashi tayi tasauka daga kan gadon tabi bayanshi,

Saboda irin yadda yake daga kafa dakyar yana tafiya ahankali yasa harta cimmashi
awani dan madaidaicin corridor, cikin falonta suka shiga,

Kan dining ya nuna mata,

"Ga abinci can idan kina jin yunwa.."

Daga haka bai sake cewa komai ba yajuya yafita ya nufi part dinshi,

Cikeda mamaki Hafsat take binshi da kallo, lallai wannan yusleem din ba kanwar lasa
bane yanzu dama akan kawai zai nuna mata abinci ne yasa yatasota?

Kan dining table din takarasa, bakaken ledodi ne cikeda fruits daya ledar kuma kaji
ne gasassu guda uku sai juice da fresh milk,

Dan yunwa kam tabbas tana jinta domin rabonta da cin abinci tun lokacin da aka fara
hidimar bikin nan bata iya zama taci abinci ta koshi ba,

Zama tayi ta bude ledar tafara yagar kazar tana ci saida taji ta koshi sannan ta
mayar ta rufe ta tashi,

Bedroom dinta takoma tashiga bathroom ta wanke hannunta da bakinta tadawo ta


kwanta, Sam bata kara jin duriyar yusleem ba har asuba tayi gari ya waye,

Wanka tayi ta shirya tayi kwalliya tasaka wani jan Swiss material,

Fita tayi zuwa falo tana bin ko ina da kallo domin dukiyar da aka zuba afalon da
shi kansa tsarin falon ba kadan bane,

Haka taci gaba da zama shiru har surayya tazo, shigowa tayi tana dauketa kulolin
abinci,

"Amarya bakya laifi.." Surayya tafada cikeda tsokana,

"Ni dan Allah zubo min abincin nan inci yunwa nakeji"

"Ai dole kiji yunwa amaryar mu, yanzu kuwa zan Kawo miki.."

Kitchen ta shiga ta dauko filet tazubo mata wainar shinkafa da miyar agushi wacce
taji kaji domin inbanda kamshi babu abinda takeyi,

"Ga abinci, ina yayan? Ko bai tashiba?"


Shiru Hafsat tayi saboda ita bata sanma me zatace ba domin rabonta da ganinshi tun
jiya da daddare,

"Duk yunwar ce ne ta hanaki magana?"

Murmushi Hafsat tayi ta gutsuri wainar tafara aikawa cikinta, kan dining table
surayya takoma taje ta kinkimo ledar kajin da yusleem yakawowa Hafsat jiya,

"Ai wannan baku ci bama, kun tsaya jin kunyar juna ko? To ni bari inci"

Hafsat najinta bata tankaba domin ita yusleem yayi bala'in daure mata kai saboda ko
atarihi bata taba jin angon da yayiwa amaryarshi hakaba, ace kazar ma bata da
darajar da zai dauka yakai mata har sai ya kirata tazo ta dauka da kanta,

Abincinta taci ta koshi ita kuma surayya tana faman yagar kazar da ta rage jiya,
bayan sun gama ne surayya tajata,

"Zo muje kiga sauran bedrooms din"

Fita sukayi daga falonta suka shiga corridor din da zai sadaka da dakunan baccinta
wadanda suke guda biyu ajere sai can gaba dasu daga karshe wata kofa ce itama
daban, bayan sun gama dudduba dakunan ne suka shiga wannan kofar, wani lafiyayyen
falo Hafsat tagani mai mutukar kyau wanda yasha kaya masu tsada sannan akwai wata
babbar kofa wacce tafita tawaje har zuwa kan wata katuwar balcony,

Coffee & milk colour ne gaba dayanshi sai wani kamshi yake na musamman,

Zama surayya tayi acikin daya daga cikin kujerun falon,

"Wash kafata, kinga bedroom din can leka kigani saboda wallahi nikam nagaji.."

Batare da tunanin komai ba Hafsat ta nufi bedroom din ta murda kofar ta shiga,
dakine babba wanda girmansa zaiyi girman falo, wani babban royal bed ne agirke
aciki sai kamfacecen mudubi da sauran kayayyaki, kamar ance ta kalli gefenta tana
kallon wurin taga wata babbar kujera mai kamada dan karamin gado, yusleem ne kwance
akai ya rungume pillow akirjinsa idanuwansa arufe abisa dukkan alamu bacci yake yi,

Tafi minti biyu tana kallonshi kafin tajuya zata fita harta bude kofar taji
maganarshi cikin muryarshi mai mutukar sanyi da zaki,

"Zo nan..."

Cikin tsoro ta waiwaya ta kalleshi, bude idanuwanshi yayi yana kallon sama bai
kalleta ba,

Mayar da kofar tayi ta rufe takarasa inda yake,

"Gani.."

"Menene ya kawoki?"

"Babu komai.."

Shiru taji yayi baiyi magana ba sannan har lokacin bai daga ido ya kalleta ba
maimakon hakama sai yajuyar da kanshi da yayi yana kallon wani wuri,

"Ina kwana..?" Tace dashi saboda tunawar da tayi bata gaidashi ba,

"Lafiya.." Taji ya amsa,


Tana nan tsaye shiru bai sake yimata magana ba dan haka tajuya tafita,

Gani tayi surayya bata inda tatafi tabarta, wucewa tayi takoma part dinta acan ta
iske surayya ta kunna makekiyar tv din dake manne abangon falon ta kamo tashar zee
world,

Ganinta yasa surayya fara yin dariya kasa kasa,

"Amarya da alama dai jiya yaya bai gayyaceki dakin nashi ba shiyasa har nakaiki
baki san can bane"

Zama Hafsat tayi tana yamutsa fuska,

"Dama kin san dakinsa ne shine kika ce inshiga ko?"

Dariya surayya tayi,

"To ba gashi kinyi gaisuwar safe ba.."

Kyaleta Hafsat tayi batace komai ba amma yanzu ta fahimci miskilin mutum Allah ya
hadata zama dashi,

Haka suka cigaba da zama itada surayya har yan uwan hajiya kubra suka zo suka tafi
suna tafiya yan uwan mami da kawayenta suma suka zo, duk wanda yazo gidan sai yasa
albarka kuma sai yaji yayi sha'awarsa domin yayi sosai, amma wasu daga cikin
kawayen mami da sukazo suka ga gida sannan suka ga Hafsat saida tausayinta yakamasu
domin sun san itama kwana nawane yusleem zai tarkatata yakorata da saki dai dai dai
dai har uku.

Har dare surayya tana gidan sai bayan sallar isha dasu khalifa suka zo tace zata
bisu tatafi,

Hafsat kallon samarin tayi wato Abdul da khalifa duk da bata taba ganinsuba amma
tasan dai kannen yusleem ne domin ga kama nan sai dai duk cikinsu shine fari domin
har surayya batafi Hafsat din fariba shikuwa yusleem farine sol,

"Kinga kannen yaya, yakika gansu? Sunfishi kyau ko?"

Murmushi Hafsat tayi, "ke kika sani"

Gaisawa sukayi daga nan sukai mata sallama suka tafi,

Tunda suka tafi kuma tazauna shiru ita kadai daga karshema taji tsoro yafara
shigarta dan haka ta tattara takoma bedroom dinta tayi shirin bacci ta kwanta.

Tun daga wannan ranar bata sake saka yusleem acikin idonta ba,kullum tareda
surayya suke wuni har dare, da haka har tayi sati daya agidan,

Rabonta da ganin yusleem kuwa tun ranar da surayya tazo last wanda yashigo falon
yace mata gobe kukun da yasamo mata zai fara zuwa tace a'a zata rinka girkinta da
kanta, juyawa yayi gurin surayya tatashi ya maida ta gida, tun daga ranar Hafsa
bata kara ganinshi ba gashi yanzu surayya bata nan sati biyu kenan da tafiyarta
Kaduna gidan kanwar mami,

Haka take wuni ita kadai babu abokin hira, bata san fitar yusleem ba bare tasan
dawowarsa.
Ranar alhamis da safe misalin karfe 11 saiga mami tazo gidan,

Da murna Hafsat ta karbeta, bayan sun gaisa mamin ke tambayarta yusleem din tashi
tayi tafita tace bari ta kirashi,

Faduwa gabanta yafara yi lokacin data doshi dakin nasa, ahankali ta tura ta shiga,
tayi sa'a kuwa yana nan,

Yana kan gado akwance yana bacci,

"Yaya... Yaya.." Tafara kiranshi, bude idonshi yayi, kallo daya yayi mata ya maida
idanuwanshi ya rufe,cikin sanyayyiyar muryarshi mai dadi yace,

"Menene?,idan ina bacci ba a tashina"

"Mami ce tazo shine tace inkira ka,amma kayi hakuri"

Ganin bashida niyyar amsa mata yasata juyawa zata fita, har takai bakin kofa taji
muryarsa,

"Zo.." Komawa tayi wurinshi,

"Bude drewar dinnan ki miko min t shirt dina"

Budewa drewar din tayi ta dauko masa t shirt guda daya ja ta mika masa,

"Ajiye anan"

Ajiyewa tayi ta juya zata fita,

"Kinga..."

Dawowa tasake yi,

"Kin iya dafa tea?"

"Ehh na iya"

"Ki dafa min, kicewa mami ina zuwa"

Da "to" ta amsa tajuya tafita tana mamakinshi acikin ranta domin sam bashida
alkibla tarasa gane inda yasaka gaba......

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_

*24*

***Wurin mami Hafsat takoma tafada mata cewa yusleem din yace yana zuwa
daga nan ta tashi ta shiga kitchen domin dafa masa tea din,

Dama indai fannin girki ne to bata da matsala domin zaman da tayi agida bawai zama
tayi ta zuba ido sai dai adafa abata taci ba, tare suke yin komai da hajiya kubra,
wata rana ma ita kadai ce keyin girkin,

Dankali ta fere ta soya masa bayan tagama dafa tea din sannan ta dan jajjaga kayan
miya kadan ta yimasa sos din kwai, akan babban faranti ta dauki kayan tafita,

Zaune ta iskesu shida mami ya sunkuyar da kai yana zaune akan kujerar dake facing
din ta mamin abisa dukkan alamu wata maganar suke yi mai muhimmanci, agabanshi ta
ajiye tiren tajuya ta koma kitchen ta dauko na mami ta Kawo mata itama ta ajiye,
sai binta da kallo mamin keyi cikin farin ciki tana yi mata sannu,

Ganin kamar maganar da sukeyi mai muhimmanci ce yasata kin zama awurin dan haka
tana kammala ajiye musu abincin ta juya takoma kitchen ta hada yan kayayyakin da
tayi amfani dasu tasoma wankewa,

Acan falo kuwa koda Hafsat ta fita mami kallonshi tayi,

"Yusleem anya kuwa kana zama tareda yarinyar nan kuyi hira kuyi wasa da dariya a
matsayinku na ma'aurata?"

Sunkuyar da kai yayi,

"Mami me kika gani?"

"To ai gani nayine kamar tana dan dari dari dakai, dan ko lokacin da nace ta kiraka
saida naga tayi wani dan jimmm"

Murmushi ne ya kwace masa saboda abinda yaji mami tace wanda har hakan yayi
sanadiyyar ajiye cup din dake hannunsa,

"Mami kenan, wallahi babu komai kuma ki tambayeta kiji"

"Ehh ai zan tambayeta din, amma kasani wallahi muddin naji kana takura mata ko wani
abu mai kamada haka to sai ranka ya baci..."

Murmushi yayi ya dauki shayin yaci gaba da kurba domin ba karamin dadi yayi ba
kasancewar da kayan kamshi Hafsat ta dafashi shiyasa in banda kamshi babu abinda
yake yi,

"Kaci dankalin mana gashinan, kai mai son dankali.." Yaji muryar mami tana yimasa
magana, shifa sam bai taba cin a abincin Hafsat ba, bama wannan ne abin mamakin ba
abin mamakin shine har yau baisan kamanninta ba domin ko kallon minti 1 bai taba
yimata ba bare har yaga yadda take,
Bude flask din data zubo masa dankalin yayi yadiba a filet yadebi sos din yadora
akai yafara ci,

Yana ci suna maganar da suka fara da mami har saida ya cinye dankalin domin baifi
kwaya biyar ba wanda yabari acikin flask din,

Hafsat kam tana kitchen bayan tagama aikinta ma wuri ta samu ta zauna saboda bata
son taje tasaka su mami agaba ta hanasu sakewa suyi zancen da suke,

Tana zaune akan kujera ta jingina da jikin deep freezer taji kamshin turarensa na
oud abyad,sam bataji shigowarsa ba bare tafiyarsa,

Akanta ya tsaya kamar wani soja yana kallon wani wuri,

"Me kikeyi?"

"Aiki nagama yanzu shine nazauna ina hutawa.."

"To zo.."

Yace da ita tareda juyawa yayi gaba, tashi tayi tabi bayansa tana kallon irin yanda
jar rigar da yasaka ta kara haskashi,

"Hafsat kizo ki zauna ki huta mana, inata kiranki bakiji ba,sannu kinji, tunda nazo
gidan nan baki zauna ba sai aiki kike tayi..."

Murmushi tayi saboda jin abinda mami tace, akasa ta zauna kusa da kujerar da mamin
ke kai,

"Mami ai aikin bashida yawa..."

"Duk da haka dai Hafsa ai kina kokari, gashi kin hadu da miji mai tsirfa Wanda ba
kowanne abinci yake ciba, kin ganshi nan haka yake kamar wani marar lafiya sam
bashi son cin abinci..."

"Uhm.." Kawai Hafsat tace ta danyi murmushi domin ita kwata kwata ma yusleem bai
taba cin abincinta ba,

"Bari intashi inje intafi, akwai ta wurin da zan biya dama cewa nayi bari inkaraso
inganku, Hafsat ai babu matsalar komai ko?"

Takarashe maganar tana dafa kafadar hafsa,

"Wallahi mami babu komai.."

"A'a hafsa idan da wani abu ki fada min saboda nasan halin yusleem sarai, bahagon
mutum ne koni da na haifeshi ban fiya gane mishi ba.."

"Allah mami babu komai da ace akwai wani abu ai zan fada miki.."

"To shikenan, taso muje akwai abinda nakawo miki"

Mikewa mami tayi itama Hafsat din ta tashi, kallon yusleem mami tayi,

"Kai kayi zamanka basai ka tasoba saboda ina son zan ganta ita kadai.."

"To mami asauka lafiya" yusleem ya amsa mata yana kokarin kishingida ajikin kujerar
da yake zaune,
Kama hannunta mami tayi suka fita,

"Hafsat kikace babu komai? Idanfa akwai wani abu ki sanar dani"

"A'a mami babu komai"

"Baya takura miki?"

"Wallahi mami babu abinda yake min"

"To shikenan dama haka nake son ji, bari ga wani sako da na Kawo miki,turare ne na
tsugunno tun daga chadi wata kawata ta aiko miki dashi,ki tsugunna akai kamar saura
awa biyu ko uku kafin kije dakinsa"

Jin abinda mami tace yasa hafsa taji kunyar duniya ta rufeta,

"Hafsat ai ni babarki ce menene abin kunya? Ki dauka haifarki ne kawai banyi ba


amma babu abinda bazanyi mikiba a duniya"

Karbar turaren tayi tana yiwa mamin godiya,

"To mami nagode Allah yakara girma"

"Amin, ai babu komai Hafsat"

Har gaban motar mamin tarakata ta bude ta shiga, tana tsaye har saida taga fitarta
sannan ta juya ta koma ciki,

A wurinda suka fita suka bar yusleem yanzun ma anan ta tarar dashi ya kwanta akan
doguwar kujera ya kunna tv yana kallon ball, har zata wuce tatafi bedroom dinta
taji k'asa k'asa yace,

"Zo nan.."

Dawowa tayi tazo inda yake,

"Gani..."

Shiru yayi mata baiyi magana ba, tafi minti biyu atsaye, ganin yaki magana yasata
fadin,

"Intafi ne?"

"Tafi in bazaki rage tsawo ba, kinzo kin wani tsaya min aka.."

Zama tayi akujerar dake makotaka da tashi,

"Bani inga abinda mami tabaki.."

Kallon mamaki ta wurga masa nan taga idanuwanshi suna kan tv,

"Ni babu abinda tabani.."

"Karya kike yi.."

Shiru tayi saboda jin abinda yafada domin dama tun lokacin da zata shigo ta cusa
kullin turaren acikin zaninta,
"Muga hannunki.."

Dagasu tayi babu komai aciki,

"Idan baki baniba tashi zanyi in cajeki fa"

"Ehh nayarda.."

"Tashi kije"

Mikewa tayi tawuce bedroom dinta taje ta bude drewar din madubinta ta jefa aciki
tafito ta shiga kitchen.

Girkin rana ta dora ta dafa shinkafa da taliya da miya, abin mamaki har ta kammala
girkin ta fito daga cikin kitchen yusleem yana nan awurin da yake kwance yana
kallon ball da alama yau babu inda zaije domin ko shirin fita baiyi ba,

Kan dining table taje ta jere abincin data girka tazo inda yake kwance akan doguwar
kujera,

"Yaya ga abinci angama"

Kai kurum ya daga mata alamun yaji, bedroom dinta tawuce taje ta watsa ruwa tayi
alwala domin taji anfara kiraye kirayen sallar azahar,

Bayan ta shirya ne ta koma falon, yusleem baya ciki amma ga filet nan da spoon
alamun ya danci abincin data dafa,

Murmushi tayi taje ta zubo abincin tadawo ta zauna tana cin abincin tana kallo, tun
da yafita kuma shikenan bata sake jin duriyarsa ba har akayi kwana biyu,

Jin shirun yayi yawa yasata nufar part dinshi domin dubashi,

Lokacin da ta shiga atsaye taganshi gaban mirror yana gyara necktie din da yasaka
da alama shirin fita yakeyi domin lokacin karfe 9:30 nasafe,

Sallama tayi ya amsa mata aciki ciki batare da ya kalleta ba,

"Ina kwana yaya.."

"Lafiya" yabata amsa,

Shiru tayi ta tsaya tana kallonshi, sanye yake cikin bakaken suit yasaka blue din t
shirt mai kwala ta ciki,

Agogon azurfa na Gucci yadauka ya daura ahannunshi yafesa turare ya zo ya raba ta


gefenta yawuce batare da yayi mata magana ba,

"Adawo lafiya..." Tafada ganin yayi hanyar fita,

Bata fita daga cikin dakinba saida ta gyarashi ta wanke toilet ta goge ko ina
sannan ta rufe tafita,

A falonta tasamu surayya baje tana jiranta,

"A'a saukar yaushe?"

"Jiyan nan nadawo shine naga bazan iya zamaba har sai nazo naganki"
"Sannu da dawowa, kin jima da zuwane?"

"Ehh to nadai fi 20 minutes amma abinda yasa ban damuba shine naga kina turakar mai
gida..."

Murmushi Hafsat tayi mai ciwo,

"Surayya yaya yusleem narasa wanne irin mutum ne shi wanda sam bai damu da iyalinsa
ba..."

Katseta surayya tayi,

"Da jira kikeyi yadamu dake? Tab ai bari kiji wallahi garama ki tashi daga wannan
dogon barcin da kikeyi domin yaya yusleem yanada manyan matsaloli,

Bafa akanki yafara aureba kuma wallahi sakin mata yake, auri saki gareshi dan babu
wacce ya taba aura tayi shekara agidansa shiyasa nake son ki zage ki kamashi ahannu
dumu dumu kuma wallahi karki raga masa ki azabtar dashi idan kika tsaya jin
tausayinsa kika raga masa sunanki sorry domin shi azabtar dake zaiyi..."

Jin abinda surayya tace ai Hafsat bata San lokacin data zamo daga kan kujerar da
take zaune ba tadawo kasa,

"Auri saki fa kikace?"

"Tabbas domin ya auri mata sunfi goma sha..."

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un.."

"A'a nifa ba fada miki nayi dan ki tada hankalinki ba, kawai fada miki nayi dan ki
tashi atsaye kisan duk yanda zakiyi ki karkato da hankalinsa gareki"

Tagumi Hafsat tayi tana lazimi acikin zuciyarta......

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_


*25*

***Tagumi Hafsat tayi tai shiru tama rasa abin cewa domin bata san ta inda
zata faraba,

"Baiwar Allah karki tashi hankalinki, nidai kawai abinda nakeso kisani shine yaya
yusleem fa ba dutse bane mutum ne dan haka duk taurin kansa wata rana dole ya
bukaci mace, dan haka daurewa zakiyi ki zage kiyita shisshige masa har yazo hannu
kin gane ai?

'Yar rangwadar nan, kwalliyar nan, tsabtar nan..." Surayya tafada tana dariya,

Kallonta Hafsat tayi idanuwanta har sunyi ja,

"Surayya kenan da alama baki gama fahimtar yayan naki ba, yaushe ma ya zauna agidan
bare har insamu damar yi masa wadannan abubuwan? Kedai kawai Allah yabani mafita"

"Amin, zaima baki cikin ikonsa"

Haka suka cigaba da tattauna maganar har tsawon wani lokaci,yauma kamar koda yaushe
saida da daddare sannan surayya taja motarta ta tafi,

Tafiyarta yasa Hafsat jin gidan yayi mata tsittt, part din yusleem ta shiga baya
cikin falon dan haka ta nufi bedroom dinshi nan dinma baya ciki, har zata fita
tajiyo motsin ruwa acikin toilet alamun wanka yake nan tajuya tafita,

Bata kara sashi a idonta ba tun daga ranar,dan haka kullum wunin kadaici takeyi
wannan dalilin ne yasa tayiwa Ummi waya tace a Kawo mata keken sakarta domin ko
babu komai zai rinka dan debe mata kewa idan babu abinda takeyi sai tarinka hawa
tanayi,

Washe gari hajiya kubra taje gidan takai mata keken da sauran kayan da zatayi
amfani dasu wurin sakar, wannan shine karo nafarko da ummin taje gidan nata shiyasa
murnarta takasa boyuwa,

Ita ason ranta ma ummin ta zauna ta wuni amma fur taki ko minti talatin batayi ba
tatashi zata tafi,

Bin bayanta Hafsat tayi ta rakata anan hajiya kubran ke fada mata cewar ai yusleem
sau biyu yana zuwa gida gaishesu bayan bikin, mamaki ne ya kama hafsa saboda bata
zaci zai iya zuwaba duk da tafi zaton cewar mami ce zata tilasta shi yaje, sallama
sukayi da ummin tatafi ita kuma takoma cikin gida.

Samun keken sakar nan akusa da ita shine dalilinta yanzu na rage zaman tunani duk
da wani lokacin tana ganin anya kuwa rayuwarsu ita da yusleem zata yiyu ahaka? A
matsayinsu na mata da miji ace sai suyi kwana 3 basu ga junaba, sannan bai damu da
yaci abincinta ba balle har magana ta shiga tsakaninsu,

Gama wannan tunanin keda wuya ta mike ta nufi falonshi, baya ciki dan haka takarasa
dakin baccinsa can dinma baya nan amma ga laptop dinshi nan a ajiye akan gado,
karasawa tayi ta dauke laptop din ta gyara gadon daga nan ta zarce da gyara dakin
gaba daya,

Bathroom tashiga nan taga ya jika kananan kayanshi acikin bocket da dukkan alamu so
yake su jiku yasa acikin washing machine yawanke domin tasan bazai taba yin wanki
da kansa ba tunda itama da ba kowan kowaba an ajiye mata injin wankin sai dai ita
bata ma fiya amfani dashiba tafi ganewa tayi abinta da kanta,

Tsayawa tayi ta wanke masa kayan tass tadauka tafita ta shanya, tana cikin shanyawa
yadawo yana sanye da kananan kaya jeans da t shirt,

Binshi cikin falon tayi bayan ta kammala shanyar kayan,

"Sannu da zuwa..."

"Yawwa..." Ya amsa mata aciki ciki daga nan bai kara koda kallon bangaren da takeba
bare tasa ran zaiyi mata sannu na aikin da tayi masa,dan haka tawuce takoma part
dinta,

Wadannan abubuwan dake faruwa sune suka hanata bacci adaren yau har misalin karfe
daya idonta biyu, tanata juyi tajiyo kamar alamun tafiya atsakar gida a tsorace ta
tashi taje gaban window ta daga labule tafara lekawa ahankali, kasancewar tsakar
gidan akwai haske tal kamar rana shiyasa tasamu damar hango yusleem din wanda ke
kokarin bude kofar motarshi,

"Ina yaya yusleem zaije acikin daren nan?" Ta tambayi kanta,

Kafin ta iya bawa kanta amsa tuni har yashiga motar mai gadi ya bude masa yafice,
ita tsoro ne ma ya kamata domin duk atunaninta agidan mami ne wani abu yafaru nan
takoma ta zauna jugum tanata nazari amma motsi kadan sai tatashi ta leka ko yadawo
amma shiru,

Haka takasa bacci sai sake sake da haka har asubah tayi a lokacin ne taji
dawowarshi da kamar taje wurinshi taji abinda yafaru sai dai tafasa,alwala taje ta
dauro tazo ta tada salla.

Misalin karfe 8 tashiga falonshi bayan taci kwalliya cikin wata dark purple din
shadda,

Kwance ta sameshi yana bacci akan doguwar kujera yana sanye da farar t shirt da
bakin boxer, karasawa dakinshi tayi ta gyara masa tafito, lokacin da ta fito kuma
yana zaune yana danna wayarshi, gaisheshi tayi ya amsa daga nan yaci gaba da abinda
yake yi, jin baice mata komai ba yasata fita takoma falonta taci gaba da
harkokinta,

Tana kan kekenta tana karasa hada rigar data fara jiya taji sallamar Amina kawarta,
da murna ta tari aminan wacce ke daga kafa dakyar domin cikinta yadan fara tsufa,

Ba karamin dadin ganin aminan tajiba nan suka baje a falonta suka hau hirar yaushe
gamo, wuni cur Amina tayi mata sai yamma ta tafi,

Haka taci gaba da zaman kadaici agidan domin surayya ma takoma makaranta kuma
bazata sake dawowa ba har saita kammala, yau watanta biyu da wani abu agidan kuma
tunda tazo bata taba fitaba shiyasa yau ta kuduri niyyar tambayarshi zuwa ganin
gida,

Yana kokarin fita tayi gaggawar tsayar dashi, tsayawa yayi batare da yajiyo ba,

"Yaya dama yau ina son zuwa gidanmu ne"

"Allah kiyaye hanya, idan kin shirya akwai driver"

Daga haka yayi gaba abinshi, shiryawa taje tayi tafito tana dauke da rigunan
jariran da ta saka wanda zata tafi dasu takaiwa Ummi domin asayar mata,
Kamar yadda yusleem yace haka ta tarar da driver yana zaman jiranta nan ya dauketa
yakaita gida, murna wurin hajiya kubra abin ba acewa komai nan tashiga yin nan nan
da ita, Hafsat ba ita tabaro gidanba sai dare domin saida tajira alhaji sa'id
yadawo suka gaisa,

Daren yauma kamar rannan kasa bacci tayi can taji fitar yusleem daga gidan agogo ta
kalla karfe 2 saura na dare,

"To wai shi wannan ina yake zuwa cikin talatainin dare haka?"

Sake saken zuci tayita yi har saida asuba takawo kai, awannan lokacin ne taji
dawowarsa azamar sauka daga kan gadonta tayi tanufi part dinshi da sauri domin tana
son taga awanne yanayi yake,

Acikin falonshi ta buya a bayan labule, ahankali taji ya bude kofa yashigo, lekashi
tayi nan taganshi acikin nutsuwarshi yake ita tayi zaton zata ganshi cikin maye ko
makamancin haka, zama yayi ya bude wani dan karamin akwati nan taga kudi fall kuma
duk daloli ne ba naira ba,

Mayarwa yayi ya rufe ya tashi yashiga bedroom dinshi, sadadadawa tayi tafita takoma
dakinta tana tambayar kanta to daga ina yaya yusleem yake?

Wasa wasa kullum cikin dare sai taji fitarsa kuma bashi zai dawoba sai aubah ashe
dama can haka yakeyi sanine batayi ba saboda lokacin da zai fita tayi bacci shiyasa
har yaje yadawo bata saniba, kasa gane inda yake zuwa tayi domin fitar tasa kusan
kullum ne tamkar ibada kuma baya tashi fita sai tsakiyar dare,

Yau kam ta daura aniyar binshi taga inda yake zuwa domin tunaninta yanzu yafara
bata cewar ko yaya yusleem dan fashi ne?

Hana idonta bacci tayi har karfe dayan dare tana jira taji motsin fitowarsa amma
shiru, karfe biyu shiru har da rabi duk shiru, hakura tayi ta kwanta nan bacci ya
dauketa can cikin baccinta taji dirin motarshi agigice ta tashi ta leka abin haushi
wai sai ganinshi tayi yafito daga cikin mota alamun yadawo daga wurinda yaje,

Da haushin wannan abun ta wuni da yamma sai gashi ya shigo cikin part dinta yana
sanye cikin farar shadda mai mutukar kyau da tsada dinkin tazarce sai jar hula da
yasaka,hannunsa daure da agogon fata fari kafarshi kuma yasa farin takalmi half
cover tsaf dashi fadin irin kyan da yayi abun ba acewa komai,ita bama tafiya
ganinshi da dogayen kayaba sai dai idan ranar juma'a ce tayi wannan kam yanasa
manyan kaya amma idan bahaka ba kullum cikin kananan kaya yake,

"Zanyi tafiya zanje America daga can zan wuce India saboda akwai likitan da zan
gani acan,idan akwai abinda kike bukata ki duba cikin bedroom dina akwai kudi..."
Yace da ita cikin muryarsa mai sanyi,

"Allah ya kiyaye hanya yadawo dakai lafiya"

Bai amsaba yajuya yafita,bayan tafiyarshi part dinshi taje ta shiga bedroom dinshi
tahau binciki wai ko zataga wata alama wacce zata tabbatar mata da gaskiyar abinda
take zargi amma babu abinda tagani haka ta hakura ta mayar da dakin ta gyara ta
fita,

Washe garin tafiyarshi mami ta turo driver ya dauketa can ta zauna har tsawon sati
2 sai ana gobe zai dawo sannan takoma gidanta kuma sosai taji dadin zama tareda
mami domin tana mutukar kaunarta tareda kulawa da ita,

Tunda yadawo take bibiyarsa tana fakonsa saboda so take sai tagane inda yake zuwa
cikin dare da abinda yake yi, kullum bata bacci har tsawon kwana biyar da dawowarsa
saida ta sakankance ranar da tayi bacci aranar ya fita daf da asuba kuma sai gashi
yadawo,

Wani haushine ya cika mata ciki gashi kuma tun daga ranar bai kuma fitaba, duk da
haka bata hakura ba haka taci gaba da saka masa ido,

A wata ranar lahdi har zata kwanta sai tajiyo motsinsa, tashi tayi ta sadada tafita
har yabude motar zai shiga ko me ya tuna oho sai yafasa yanufi ciki amma dai yabar
motar a bude, ganin haka yasata lallabawa tabude bayan motar tashiga ta makure ta
buya,

Tafi mintuna talatin aciki bai dawoba, tana shirin fita sai taji alamun tahowarsa
nan takoma tasake makalewa ta yadda bazai ganta ba,

Shiga cikin motar yayi yatadata ahankali ya murza ya doshi gate din fita.......

_Sakon fatan alkhairi ga yan group din Duniyar littattafan Hausa, tabbas kunfi
kowa son alwashi..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

_Kuna ina? Members na zauren karatu group, wannan page din yau nakune ku kadai
domin jin dadinku, soyayyarku gareni ta musamman ce, ina yinku kamar yadda kuke
yina....!_

*26*

***Sake lafewa Hafsat tayi a lungun kunjerun baya wato wurinda ake ajiye
kafa, tana jinsa yana driving din yana dan jan karamin tsaki, titin emirs palace
yahau,

Gaba daya garin tsitt yake babu motsin kowa sai haushin karnuka wadanda idan sun ji
motsi suke kaurewa da yi,

Wayarshi ce tadanyi kara nan taga ya dauka yakara a kunnensa, cikin sansanyar
muryarshi taji yace,

"Am on my way...." Wani dan tsakin yaja bayan ya kammala wayar ya ajiye,

Haka yaci gaba da yin driving ahankali shi kadai atsakiyar titi domin hatta jami'an
tsaro masu yin patrol sun gama aikinsu sun tafi,ita mamakinshi ma takeyi ganin ko
tsoro bayaji shi kadai a titi kamar aljani,

Wata hadaddiyar atishawa ce ta tahowa Hafsat batare data shirya ba nan tayi
hanzarin toshe bakinta da hancinta amma duk da haka saida yar kararta ta fita,

"Atshhh..."

Jin sautin yasa yusleem wanda ke yin driving dan juyowa nan tayi saurin sake
kwantawa abayan kujerar, maida kallonsa titi yayi yaci gaba da tukinshi,

Jin alamun yatsaya yasata dan dago kanta domin ganin ko inane, bata san ko ina bane
amma tana dan iya jiyo maganganun mutane, dukar da kanta tayi har saida taji
fitarsa sannan ta dago tafara kallon wurin,

Wani babban hotel ne mai tsananin kyau wanda yakeda fiyeda hawa 20,harabar wurin
kadai ta isheka nishadi da kallo domin itama kawace take da abubuwan saka nishadi,
wurin haske ne tarwal kamar rana sannan ga mutane nan sunata hada hadarsu mata da
maza,

Hango yusleem tayi ya nufi cikin hotel din nan tayi yunkurin binshi amma abin
haushi ya kulle motar kuma babu yadda zatayi ta iya budeta domin motar tashi ba
kamar sauran motoci bane, motarshi motace mai tsada wacce ta amsa sunanta domin ko
a zagayen garin bata tunanin akwai wanda yake da irinta,

Dukan kujera tayi cikeda haushi, damuwa gamida bacin rai domin taso ace tabishi
abaya taga karshen gudun ruwansa,

Tana nan zaune tana kallon yanda mata da maza ke zuwa suna shiga cikin hotel din
kamar bazasu kareba domin maimakon ma su ragu sai sake karuwa suke,

Tagumi Hafsat tayi aranta tana tunanin ko mahukunta suna ina hakan take faruwa?,

Tana nan zaune tana jiran taga ta inda yusleem zai bullo amma shiru sai misalin
karfe 5 saura sannan ta hangoshi yana fitowa daga cikin hotel din, saurin komawa
maboyarta tayi ta lafe, saida yadan jima awaje bata san me yatsaya yiba sannan
yabude motar yashiga ya tadata,

Tana jinsu suka hau titi suka nufi unguwarsu, karar bude gate taji alamun sun iso
gida lokacin anfara shiga masallaci sallar asubah,

Kasancewar gidane yasa yusleem bai kulle motar ba fita kawai yayi yatura kofar
yanufi ciki, saida yajima da fita sannan hafsat ta lallaba ta fita,

Ganin kamar giftawar mutum yusleem yayi lokacin da yake tsaye agaban window dinshi
bayan yadauro alwala, da sauri yafita yabi ta kofar da zata sadashi da part din
hafsat,
Bai taba shiga bedrooms dinta ba sai yau, wannan shine karo nafarko da yataba
takawa zuwa dakunan barcinta,

Bedroom din farko yafara shiga nan babu kowa aciki har cikin toilet yaduba amma
babu kowa, rufe dakin yayi yakarasa dayan yana shiga tana fitowa daga bathroom da
alama alwala tayi,

Ganinta yasashi juyawa yafita, dan lekashi Hafsat tayi,

"Ohh Allah, Allah kasa dai ba ganewa yayiba.." Tafada acikin zuciyarta,

Tana idar da salla ta kwanta ramuwar baccin da bata samu tayiba tunda ta kwanta
kuma ba ita ta tashiba sai misalin karfe 10 nasafe, wanka tayi tashirya tasaka wata
doguwar riga ta leshi pink colour da stones ajiki, kitchen tashiga ta dora
breakfast sannan ta dafawa yusleem tea tanayi tana addu'ar Allah yasa karya
gwasaleta,

Saida ta kammala yin breakfast dinta taci sannan ta dauki nashi ta nufi part
dinshi,

Yana kwance akan tsakiyar fankamemen gadonshi yana ta bacci, abisa dukkan alamu har
yanzu bai tashiba,

Dan karamin stoll tajawo ta dora masa akai ta tsaya tana kallonsa,

"Menene kika tsaya min aka kina kallona??" Taji yafada batare da ya bude idonsa ba,
ita tsorata ma tayi saboda ganin tun lokacin data shigo dakin idanuwanshi a rufe
suke,

"Ahhh babu komai..., dama breakfast nakawo maka.."

Murmushi taga yayi akaro nafarko tsakaninta dashi domin tun ranar data fara ganinsa
bata taba ganin murmushinsa ba sai yau,

"Shiga toilet ki hada min ruwan wanka.."

Taji yasake fada ahankali,

"Toh" bude bathroom dinshi tayi tashiga, saida tafara dauraye toilet din sannan ta
hada mishi ruwa acikin bathtub tasaka salt nawanka da turaren wanka domin duk gasu
nan tanade asaman wata yar madaidaiciyar kanta wacce ke daure ajikin bangon toilet
din,

Lokacin da tafito atsakar dakin ta sameshi yana tsaye yana yin mika nan tabashi
hanya yawuce yashiga ita kuma tasoma gyaran dakin tana yi tana yan kalle kalle ko
Allah zaisa idanuwanta su gane mata wani abu, har kasan gado ta leka amma babu
abinda tagani,

Tana kammala gyara dakin shi kuma yana fitowa fita tayi tabashi wuri domin
yashirya, a falonshi ta zauna tana nan zaune har yafito,zama yayi ya dauki remote
ya kunna tv,

Ita dai Hafsat tana zaune tana binsa da kallo duk inda ya motsa, har azahar tayi
bata bar falonba saida taga yafita salla sannan taje takwashe kayan da ta kawo masa
breakfast aciki takoma part dinta amma data kammala lunch ma can tasake komawa
sukaci gaba da zaman kurame.

Abin mamaki tamkar yasan shirin da Hafsat keyi akansa ko kuma yanada masaniyar
abinda take shirin yi sai ya canja taku, acikin kwanakin gaba daya baiyi fitar
dareba sai dai amma idan yafita kafin sallar magrib baya dawowa sai 1 ko 12:30,kuma
ranakun suna dan sassabawa domin wata ranama da rana yake fita to bazai dawoba sai
1 wata rana kuma tun safe idan yafita office baya dawowa sai 12 wata rana kuma sai
yayi zamansa agida ko nan da kofar gida bazai fitaba sai dai idan time din salla
yayi yafita yaje masallaci yadawo, gaba daya yasa Hafsat acikin wani yanayi domin
takasa fahimtar ta inda zata gano abinda yake aikatawa aboye wanda abisa dukkan
alamu babu Wanda yasani,

Yafi sati biyu yana wannan shifting din daga rana zuwa dare ko kuma daga yamma zuwa
dare,

Ganin kamar idan aka cigaba da haka Hafsat bazata samu abinda takeso ba yasata
yimasa dabara,

Tea ta dafa masa takai mishi ta zauna acan nesa dashi, saida yadawo daga sallar
azahar sannan yasha, nan yaji duk kasala ta rufeshi, wannan dalilin ne ya hanashi
fita gaba daya ranar domin har salla agida duk yayi,

Karfe 2 nadare daidai yayi shirin fita nan yaje wurin da yake ajiye keys din
motocinshi yasoma dubawa, yayi neman duniya amma baiga na BMW dinshiba shikuma yafi
son yaje da ita domin sabuwar motace dan haka ba kowa bane yasanshi da itaba
sabanin sauran motocinshi,

Wani key din yadauka yafita, Hafsat da tun jimawa take cikin bayan motar a boye
tasake gyara buyan da tayi ganin ya nufo parking space din amma abin haushi koda
yazo sai taji ba motar da take ciki yashiga ba wata daban yabude yashiga yayi
reverse zai fita haushi ne ya cika mata ciki domin fa saboda haka ta dauke key din
BMW dinshi ta boye saboda kar taje yasake kulleta kamar yadda yayi mata rannan
tanaji tana gani yafice daga gidan batare data bishiba,

Ciki takoma tana cizon yatsa wato duk shirin data dade tanayi Yatashi abanza
kenan,tsabar takaici bata ma san lokacin da yadawo ba.

Ganin tarasa mafita yasata tambayarshi cewar zataje gidansu bai hanataba kamar
yadda tayi tsammani dama, koda taje gidan acan tawuni amma yamma tanayi tacewa Ummi
tafiya zatayi, nan ummin tayi tayi da ita akan tajira salisu driver yadawo yakaita
amma taki,

A perfect guys & ladies hotel ta sauka ta biya mai adaidaita sahu kudinsa tatafi
can cikin wasu shuke shuken flowers ta tsaya, har akayi magrib bataga alamun daya
daga cikin motocin yusleem ba tana nan tsaye har akayi isha alokacin ne ta saddakar
da bazai zoba,

Fitowa tayi takama hanya zata fita tana zuwa gate din hotel din tahango motarshi
tana dosowa kamar a mafarki babu shiri tajuya tabi ta bayan wasu bishiyoyi ta nemi
mafaka duk da tasan ba lallai ne yaganeta ba saboda bazai taba tsammanin ganinta
awurinba,

Tana ganinshi yafito bayan ya rufe motarshi ya nufi ciki yana yin waya yana sanye
cikin kananan kaya, lababawa tayi tasoma binsa abaya abaya har zuwa ciki, akofar
wani daki taga yatsaya mintuna kadan aka bude masa yashiga,batayi kasa agwiwa ba
tabishi har kofar wannan dakin,

Tsayawa tayi tana tunanin ta ina ya kamata tafara, tafi minti goma atsaye daga
karshe kawai ta nufi kofar ta murda abin mamaki abude tajita nan tashiga ahankali,
wani dan madaidaicin falone wanda yacika da sanyin air condition, leken cikin
bedroom din tafara yi amma kuma bata iya hango komai nan tadan tura kofar ahankali
ta zira kanta ta leka, abinda tagani shine yayi sanadiyar sulalewarta awurin ta
suma bayan ta kwalla kara mai mutukar firgitarwa.....
_Tofa ko me Hafsat tagani? Nidai Ummi Shatu banida wannan amsar..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*27*

***Ahankali tafara bude idanuwanta wadanda suka yi mata nauyi ga wani irin
ciwo da kanta ke faman yimata kamar zai tsage,

Dishi dishi take gani kafin daga bisani ta dan fara ganin dishi dishin yana washewa
har ya b'ace gaba daya,

Mami ta hango zaune saman wata kujerar roba ganin ta bude idonta yasa mamin matsawa
gareta,

"Sannu Hafsat..., sannu kinji, Allah yabaki lafiya..."

Runtse idanuwanta tayi take wasu zafafan hawaye suka gangaro daga cikin idanuwanta,
ko kadan bata burin ta sake ganin yusleem ayanda taganshi dazu kuma ko tunawa bata
son ta kara yi domin wannan shine mafi munin gani da idanuwanta suka taba yi tunda
tazo duniya,

"Sannu Hafsat, kukan me kikeyi kuma?" Mami ta tambayeta tana dafata,

"Kukan ciwo mami, kukan ciwo nakeyi mami ba kukan komai ba domin kaina wani nauyi
naji yayi min banda azabar ciwon dake addabata..."

"Sannu, sannu Allah yabaki lafiya, ina zuwa bari inkirawo likita saboda yace idan
kin bude idanuwanki inkirashi.."

Fita mami tayi daga cikin dakin nan Hafsat tasake mayar da idanuwanta ta rufe tana
hawaye, a hakikanin gaskiya abinda tagani ne yasata wannan kukan bawai ciwon kan da
take tareda shi yanzu bane,

Tana nan kwance tana hawaye taji shigowar mami da dr,

Gaban gadonta likitan yakarasa yakai hannunsa kan goshinta ya taba,

"Sannu, yanzu me kikeji yafi damunki?"

"Dr ciwon kai ne kadai ke damuna.."

"To insha Allah shima zai daina nan da dan wani lokaci.."

Dukufa likitan yayi yafara rubutu ajikin wani dan madaidaicin file saida ya kammala
sannan yadago ya mikawa mami takardar,

"Ga magungunan da za asamo mata tasha bayan taci abinci, Allah yakara bata
lafiya.."

Karbar takardar mami tayi shikuma likitan yasaka kai yafice daga cikin dakin,

Wayar yusleem mami tasoma nema ringing biyu zuwa uku ya dauka,

"Kana inane? Kai nake jirafa.."

Kashe wayar tayi batare da Hafsat tajiyo abinda yusleem din yafada ba,

Ba afi mintuna biyar da gama wayarsu da mami ba sai gashi ya turo kofa yashigo,
kawar da kanta hafsat tayi daga gefen da yake ta mayar zuwa wani gefen,

"Wannan shine mijin kaddara..." Tafada acikin zuciyarta,

"Wai kai me yasameta? Inata tambayarka abinda yasameta harta suma haka amma kaki
yimin bayani.."

"Yanzu dai mami ai ba lokacin yin wannan maganar bane, abinda kuke bukata nake son
ji"

"To kaga dai magungunan da dr yace asiyo tasha bayan ta ci abinci amma gaskiya ni
ina ganin idan har takara kwana biyar bataji sauki ba gara ka kaita chairo..."

Dan sajenshi ya shafa ya karbi takardar dake hannu mami,

"To shikenan bari nasamo drugs din indawo.."

Yana fita hajiya kubra na shigowa hannayenta dauke da babban basket din abinci,

"Hajiya siyama ya mai jikin? Nifa kalau muka rabu da ita saida ma nayi nayi da ita
tajira salisu yadawo yakaita amma furr taki ashe tsautsayi ke janta.."

"Ehh haka Allah yake ikonsa ai, nima wallahi sai waya kawai yusleem yamin wai
yakaita asibiti..."

Ajiye kayan hannunta hajiya kubra tayi ta matsa wurin Hafsat tana yimata sannu,

"Wai ya akayi haka tafaru? Hafsat garin yaya..?"

"Ummi kaddara da tsautsayi, nima ban san abinda ya sameni ba kawai jina nayi
nafadi,shi lokacin da abin yafaru ma yana office inajin sai wayata aka dauka aka
kirashi..." Ta karashe maganar hawaye na bin kuncinta,

"To Allah ya rufa asiri ya kiyaye gaba.."

"Amin summa amin, Allah yatashi kafadunta yabata lafiya..." Inji mami,

"Tashi kici abincin to, tuwon shinkafa ne miyar zogale.."

Dakyar Hafsat ta iya tashi ta zauna saboda irin yanda kanta ke tsananin sarawa,
tafara cin abincin kenan yusleem ya shigo dauke da magungunan da likita ya rubuta
mata,

"Mami gashi..."

"Yawwa ansamo, to bari tagama cin abincin sai tasha, ashe kaima baka gida lokacin
da abun yafaru? Tace kana office sai awaya aka kiraka.."

Kallonshi Hafsat tayi domin taga irin yanda zai karbi maganar,

Shiru yayi baiyi magana ba saima bude kofa da yayi yafita,

Tunda yafita bata sake jin motsinshi ba,ita kanta tasan daren ranar bazata iya
bacciba ba don Allah ya taimaka anhada mata da magungunan bacci ba acikin maganin
da aka bata,

Tareda mami suka kwana a asibitin ita kuma ummi tatafi sai da safe ta dawo takawo
musu abincin karyawa,

Kwananta uku a asibitin dr yace zasu iya tafiya gida, duk da ta dan samu saukin
ciwon kan dake addabarta amma ta gagara daina kukan da takeyi wannan kam yazame
mata kamar ibada wani lokacin sai suna zaune kalau sai kawai aga tana hawaye gashi
daga mamin har Ummi sunyi tambayar duniya amma taki fada musu damuwarta wacce ke
sata kukan,

Yanzun ma da zasu bar asibitin hawaye ne ke faman bin kuncinta ganin haka sai mami
tace kawai hajiya kubra tatafi da ita gida ta dan sake warwarewa,

Tunda suka koma ummi ta tisata agaba tana yimata tambayoyi,

"Hafsat kin dai san yanzu aduniyar nan bakida wanda yafini daga ni sai Alhaji, ki
sanar dani abinda yake damunki, idan baki fada minba wa kike dashi wanda zaki
fadawa?"

Murmushin karfin hali Hafsat tayi,

"Ummi wallahi bafa kukan wani abu nakeyiba, kawai wani abin mamaki da ban tausayi
nagani ranar da nabar gidan nan..."

"Me kika gani?"

"Ummi wata matace suke tafiya da yarta, tana rike da hannun yar fa yarinyar ta
kwace ta ruga da gudu zata dauko wani abin wasa da ta hango ashe tsautsayi ne saiga
mota tabi takanta gaba daya ta tanitseta, wannan abun shinefa ya hadda samin wannan
suman da nayi..."

Dafata hajiya kubra tayi,

"Allah sarki Hafsat to ai dama idan ajali yayi kira ba makawa sai antafi, Allah
yajikanta mukuma yasa mucika da kalmar shahada.."
"Amin Ummi"

Tashi hajiya kubra tayi tafita, tana fita Hafsat ta kifa kanta ajikin pillow tasoma
kuka mai sauti domin da duk kukan zuci take yi wanda yafi nafili ciwo,

Kwananta biyu agida amma kullum sai mami tazo dubata yusleem ne kadai bai taba zuwa
ba, aranar da tayi kwana uku mami tace tashirya su tafi inyaso idan takarasa
warwarewa awurinta sai takoma gidanta, shiryawa tayi suka tafi gidan mamin nan mami
tasoma bata dukkan kulawa domin dakin surayya tabata ta zauna aciki wanda yake
dauke da dukkan abubuwan jin dadi irin wadanda ba agidan kowa ake samuba sai gidan
wadanda suka amsa sunansu masu naira,

Dukkan abinda take so shi ake Kawo mata domin ga ma'aikata nan agidan kashi kashi
ita kanta mamin babu abinda takeyi sai dai idan tana bukatar abu tayi waya kawai
akawo mata shiyasa koda yaushe cikin ado zaka sameta tasha kwalliyarta ta zubawa
jikinta gwala gwalai,

Dawowarta gidan mamin ma bai hanata daina kukan da ya zame mata jiki ba domin
kullum cikin yinsa take,

Kwananta biyar agidan mamin amma bataga yusleem ba nan tafara tunanin to kodai
tafiya yayi ne?

Tana cikin wannan tunanin tajiyo maganar mami a falo kuma da alamu yusleem dinne
yazo, runtse idonta tayi tafara zubar da hawaye wanda har mami tashigo bata san
tashigo ba,

"Hafsat, wai me yake damunki ne, kukan nan naki yayi yawa kuma nasoma zargin cewar
akwai abinda ke saki kukan, ki fada min gaskiya karki boye min.."

"Mami babu komai, wallahi babu abinda ke damuna, wannan kukan ni kaina ban san
meyasa nake yinsa amma nasan bazai rasa nasaba ba da accident din da naga anyi
rannan ba"

"To hafsat ai sai hakuri, haka rayuwar take sai dai Allah yasa mucika da imani, ki
shirya anjima mijinki zai zo ya daukeki ku tafi.."

"To mami.."

Ai mami nafita hafsat ta rushe da kuka saboda yanzu ita bata son ganin yusleem
kwata kwata kuma da alama shima yagane haka domin tun rannan bai sake rab'ar inda
takeba.

Misalin karfe 8 nadare yazo daukarta, kuka mami ta sameta tanayi nan hankalinta
yatashi ta fara tambayarta,

"Hafsat ko wani abun yusleem din yake yi miki?"

Jijjiga kai tayi, "a'a mami babu abinda yake min"

"To ko bakya son komawa gidan nashi ne yabarki anan?"

"A'a mami zan koma"

Zama mami tayi agefenta,

"Hafsat kar muyi haka dake, ki fada min gaskiya idan har akwai abinda yusleem yake
yimiki karki boye min"

"Wallahi mami babu komai, ni babu abinda ya taba yimin muna zaune lafiya
dashi,kukan rabuwa dake kawai nakeyi mami da kuma irin soyayyar da kike nuna min
nasan duk duniya nafi kowa yin sa'ar surika tagari mai sona"

Rungumeta mami tayi tasoma shafa kanta,

"To hafsat ai kema surakace tagari shiyasa dole in kaunaceki kuma wallahi ina sonki
irin soyayyar da nake yiwa 'yayan da na haifa,yanzu dai shikenan tashi kizo muje
dan yazo yana jiranki share hawayenki daina kukan"

Akwatin kayanta tadauka tareda yin karfin halin tsayar da hawayen dake zuba a
idonta tafito suka fita da mami domin shi har yajima acikin motarsa,kasancewar
ranar juma'a ne shiyasa yake sanye da dogayen kaya na ash colour din shadda mai
tsadar gaske,

Gaban motar tashiga batare da ta kalleshiba amma kamshin turarensa na beautiful oud
sai cika hancinta yake sallama sukayi da mami tanaji mamin nace masa yakula da ita
sosai sannan banda matsanta mata,kuma indai taji yayi mata wani abu to sai ransa
yabaci, kasancewar yan miskilancin suna kusa ko amsawa baiyi ba,

Jan motar yayi suka fita suka nufi gidanshi babu wanda ya kalli wani bare har yayi
magana nan tafara tunanin to ko shima fushin yake?

Lokacin da suka karasa gidan, trolley dinta taja ta nufi ciki batare data dubi side
din dayake ba,gidan tsaf tsaf taganshi kamar tana nan, a bedroom dinta tazauna kan
bed side drewar tayi tagumi sai kuma tafara kuka,

Handbag dinta wacce tafita da ita ranar data bishi hotel ta suma ya dauko yabita
dakinta, cilla mata jakar yayi saman kan bed dinta yajuya zai fita,

"Yaya yusleem..."

Takira sunanshi, cak yatsaya batare da yajiyo ba,

"Meyasa ka zabi wannan mummunar sana'ar acikin rayuwarka? Duk sana'o'in duniya
karasa wacce zakayi sai wannan? Kasan kuwa irin mummunan tanadin da Allah yayiwa
masu irin wannan sana'ar? Meyasa ka zabi duniyarka akan lahirarka?"

Ahankali yajuya yafara takawa ya nufi inda take tana zaune hawaye nafaman bulbula
daga idonta kamar anbude fanfo.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_

_Gaisuwa da babbar murya ga masoya masu karanta alwashi..._

*28*

****Agabanta ya tsugunna yana kallon fuskarta karo nafarko a zamantakewarsu


da ya tsaya ya kalleta,

"Yaya yusleem ko kasan kuwa tarin zunubin da yake kan duk wani wanda yake aikata
irin wannan dabi'ar? Irinfa wannan laifin al'umar wani annabi sukayi Allah ya
halakar dasu sannan acikin littafinsa mai tsarki ya sanar damu nau'o'in azabar da
ya tanadarwa duk wani wanda ya kasance yana aikata irin wannan halayyar...."

Tausassun hannayensa yakai yadora akan nata har lokacin dai idanuwansa suna kan
fuskarta sannan sun juye daga farare zuwa jajaye,

"Ba laifina bane, karki ga laifina, komai yana faruwa ne da dalili, wallahi irin
rayuwar da na tsinci kaina abaya ta kunci, talauci, tsangwama, tsana da kuma kyara
itace tayi sanadiyyar fadawata cikin wannan mummunan halin..."

Kallonta yayi da jan idanuwanshi tareda kwantar da kanshi bisa cinyarta yanajin
zuciyarshi tana yi masa zafi wanda bai taba jin irinsa ba,

"Yaya yusleem nikuma sai nake ganin wannan ba dalili bane ko hujja da har zaka jefa
kanka cikin halaka..."

"Wannan daliline mai karfi NANAH...."

"Nikuma agareni ba dalili bane domin wannan abun da kake aikatawa yafi dukkanin
abubuwan da ka zayyano muni,haba yaya yusleem kamanta labarin wani mutum da annabi
yafada mana mai tsawaita tafiya yana mai gizo mai k'ura k'ura yadaga hannayensa
zuwa sama yana cewa ya ubangiji ya ubangiji amma annabi yace ba a amsa masaba
saboda abincinsa haramun ne,abin shansa haramun, tufafinsa haramun sannan yayi
guzuri da haram...."

Dago da kanshi yayi ya kalleta sakamakon jin saukar hawayenta akan wuyanshi,

"NANAH arayuwar baya na tsinci kaina cikin mawuyacin hali, mahaifinmu Alhaji Ahmad
Mela mu Goma Sha biyar ya haifa sannan matanshi uku kowacce tanada yara biyar,

Ya mutu ya barmu tun muna kanana, acikin yaransa mu ukune manya daga Shu'aib sai
Mukhtar sai ni, dukkaninmu kanmu daya, kasancewar dama gidan ba azaman lafiya yasa
tun rasuwar mahaifinmu kowa ya kama 'yayanshi yarike bayan anraba gado,kuma kin
san zumuncin yanzu yanda yake na ganin ido ne,

Nanah a lokacin wallahi duk da ni yarone ban wuce shekara 24 ba ina yin iya bakin
kokarina wurin nemowa mahaifiyata da kannena abinda zamuci amma mami bata gani
kullum cikin kusheni take da zagi cewar ni banida zuciya zan bari wai talauci ya
kasheta,
Nayi iyakar iyawata ganin na fahimtar da ita amma taki fahimta ita kawai burinta
lokaci daya inyi kudi inzama millionaire dan kawai ta bawa kishiyoyinta haushi,

Idan kinga irin sana'o'in danayi makaskanta sai kin tausaya min, har turin baro
wallahi nayi, na saida pure water, nayi kanikanci,nayi jiran shago duk wai dan
inrufawa kaina da yan uwana asiri amma mami bata gani koda yaushe bata da magana
sai nacewa, ita bazan burgeta ba muddin ban tashi nanemo kudi duk inda yake nazama
mai kudiba,mami duk tabi ta tsangwameni ta tsaneni akan kawai ban zama mai kudiba,

Da wannan kananan sana'o'in nasamu nakammala degree amma abin haushi babu aikin yi
dole nakoma gareji naci gaba da gyaran mota,

Sau da dama ku mata kune kuke cusawa mutum ra'ayin da baiyi niyyaba nanah, a
lokacin idan nasiyowa mami abu nakawo mata ko atamfa ko takalmi sai ta raina kiri
kiri zata nuna min ban burgeta ba kuma bata ji dadiba wani lokacin ma har takara da
fadin "ni ba irin wannan harkar tsiyar nakeso kayimin ba, ni so nake karinka Kawo
min kaya masu tsada akwati akwati yanda nima zan fantama, amma kai kullum abubuwa
ba arziki kaki katashi kayi arziki yanda mahaifinku ya mutu bai bar muku komaiba
kaima haka zaka mutu baka bar komai ba?"

Irin Wadannan maganganun da mami kemin sune suke tsaya min araina inji zuciyata
takasa samun nutsuwa saboda ni aganina ina iyakar kokarina amma komai nayi bata
gode min kuma bazata samin albarka ba,

Acikin wannan yanayin wan mahaifinmu yabani yarsa Rahina in aura, sam Rahinan bata
sona saboda kawai banda abin hannu sai rufin asiri,

Dakyar ita da uwarta suka amince akayi auren saboda babu yanda zasuyi, bayan
aurenmu da Rahina nashiga matsanancin hali saboda zan siyo mata kayan cefane in
aiko mata dashi daga gareji amma wallahi nanah yanda aka Kawo kayan nan haka zan
dawo insamu kayana tabarshi awurin bata taba ba, idan abin lalacewa ne to sai dai
ya lalace, bazata yimin girki ba idan nayi magana tace ita bazata dafawa matsiyaci
abinci ba mai k'ashin tsiya wanda bashida rabon arziki,

Bazata yi sharaba,baza tai wanke wanke ba babu abinda takeyi abinci ma mahaifiyarta
ce ke aiko mata daga gidansu batare da mahaifinta yasaniba, kullum idan naje gaida
mami dakyar take amsawa, idan nadawo gida Rahina ta tareni da masifa da bakaken
maganganu wani lokacin ma sai tace bazan shiga dakinta ba ita ubanta bai siya mata
gado da katifa dan matsiyaci ba dama kuma tunda akayi auren bata barni na kusanceta
ba domin kullum da wuka akasan pillow take kwana wai duk ranar da nayi yunkurin
zuwa inda take sai ta kasheni,

Kullum a falo nake kwana ita kuma tana cikin daki wata rana ma idan bata gadamaba
rufe kofa take sai dai inkwana awaje idan nafadawa mami sai ta goyi da bayanta
tamkar ba itace ta haifeni ba, duk da irin wannan abubuwan da Rahina kemin bai hana
zuciyata fara sonta ba amma ita hankalinta ba akaina yakeba domin haka mahaifiyarta
zata zo har gida su hadu su zageni tass suna kirana da matsiyaci marar arziki,

In takaice miki zance daga karshe sakani agaba sukayi saida nasaki Rahina duk da
ina sonta ashe wani mai kudi tasamu suke soyayyarsu da aurena, aranar da nasaketa
sukazo suka kwashe kayanta Hafsat nayi kuka irin kukan da ban tabayiba domin ina
sonta duk da rashin kyautatawar da take yimin,

Kwana biyu nadauka agida ban fitaba saboda damuwa, da daddare ina kwance ni kadai
adaki na dauki wayata nashiga facebook nan naga wani yaturo min da friend request
babu bata lokaci nayi accepting,

Bayan mun gaisa yake cemin a ina nake nafada masa, sai yacemin wai ina dan harkoki
nace masa ehh to ana dan tabawa saboda ni ban gane abinda yake nufiba haka mukaci
gaba da yin hira yace shi dan majalissa ne awani gari yakamata inje in sameshi,

Wallahi nanah ban taba sanin mutumin nan bana kirki bane saboda nayi tunanin ko
aiki zai bani tunda nafada masa nagama karatu babu aikin yi,

Sallama nayiwa mami nashirya natafi wurinsa da takardu na amma koda naje sai labari
yasha banban lokacin da yanuna min karara abinda yake son yi dani ashe gay ne ban
saniba, a lokacin ban aminceba amma koda nazauna nayi tunani nahango irin
tsangwamar da mutane kemin akan bani da arziki da irin halin ko inkula da mami ke
nuna min da kuma yadda aka rabani da rahina sai kawai na amince shiyasa nace miki
amafi yawan lokuta ku mata kone kuke zama silar faruwar komai domin dayawa daga
cikinku bakuda godiyar Allah burinku kawai mutum yayi arziki batareda kun damu da
sanin halalcin arzikin ko haramcinsa ba,

Kwanana uku awurinshi aranar da zan dawo yabani wata kyakkyawar mota banda tsabar
kudi dubu dari biyar,

Tunda mami taga nafara arziki shikenan tahau murna tana cewa burinta yakusa cika
sukuma mutane sai cewa suke Allah ne yayi min nasibi dare daya ya azurtani, wallahi
nanah ko sau daya mami bata taba tambayata a ina nake samun kudiba ita kawai tunda
nace mata wani uban gida nasamu yake buda min shikenan tahau murna tana saka min
albarka,

Kuma har yau dinnan da nake miki magana mami bata taba tuhumata akan arzikin da
nake dashiba gashi kuma acikin lokaci kankani na mallaki komai na jin dadin rayuwa
kama tun daga gidaje, kamfanoni, motoci da komai da kika sani na jin dadin rayuwa
domin mutanen dake cikin harkar nan masu fada ajine daga senators sai Reps sai
Governors...."

Zamowa daga kan bedside drewar din Hafsat tayi tazauna dirshan akasa cikeda tashin
hankali, matsawa kusa da ita yayi yasake dora kanshi akan cinyarta yafashe da wani
kuka mai ban tausayi,

"Yaya yusleem daina kuka dan Allah, shi Allah mai yawan gafara ne domin yace yana
gafarta zunabai gaba daya komai yawansu mutukar muka tuba kuma muka nemi gafararsa,
nidai dan Allah so nake kabar aikata wannan dabi'ar domin bata dace dakai ba,
kazanta ce, masu aikatata sun tabe duniya da lahira.."

Hannunta yakama ya matse cikin nashi,

"Nanah na daina, amma nasan rayuwata tana cikin hatsari domin wallahi sawa zasuyi
akashe ni saboda zasuga kamar zan tona musu asiri ne kuma mafi yawansu manyan
mutane ne.."

"Yaya yusleem insha Allah babu abinda zai sameka, insha Allah Allah zai kareka..."

Baiyi magana ba illah kukan da yaci gaba dayi mai tsuma zuciya,

Rarrashin duniya Hafsat tayi masa amma baiyi shiruba, ranar haka suka kwana azaune
ido biyu har gari yawaye,

Alwala yayi yafita masallaci idanuwansa akunbure sunyi jajur, ita kanta Hafsat din
kukan da tayi ba kadan bane,

Acikin sujjadarta kuwa tajima tana yimasa addu'a, tana zaune akan abin sallar tayi
tagumi ta jingina da jikin gado sai gashi yashigo akusa da ita ya zauna yajingina
da jikinta, hannu tasa ta rungumeshi,
"Yaya yusleem kadaina kukan nan haka dan Allah.."

"Hafsat wallahi natsani kaina, natsani rayuwata, ni yanzu mutuwa kawai nake s...."

Saurin rufe masa baki tayi,

"Yaya yusleem babu kyau fatan mutuwa, karkayi sabo dan Allah kayi shiru.."

"Nanah mami ta illata rayuwata, bata min adalciba.."

Sake rufe masa baki tayi, "kadaina fadin haka, mami mahaifiyarka ce bata cancanci
haka daga gareka ba domin tafi kowa sonka.." Shiru yayi baice komai ba saboda jin
abinda tace.

Haka suka ci gaba da zama har rana tafito karfe 12 narana yayi, tashi Hafsat tayi
taje kitchen ta dafa musu indomie da kwai ta hado tea takawo musu, ko kallon
abincin yusleem baiyi ba bare tasa ran zaici, ta rarrasheshi iya rarrashi amma yace
bazai iya ciba,

Haka suka wuni da yunwa har dare,

Yau ma bacci baiga idonsu ba sai jikin asubah ya daukesu yana kwance akan cinyarta.

Karfe 8 nasafe suka farka, salla sukayi tace bari takawo masa tea, girgiza mata
kai yayi alamun bazai sha ba, dawowa tayi tazauna akusa dashi takamo hannunshi,

"Yaya yusleem haka zaka zauna jiya bakaci komai ba yauma kaki ci?"

"Nanah bazan iya cin komai ba musamman ma wanda aka siya da wannan kazamin
kudin ..."

"To idan nabada aka siyo maka wani abun nadafa maka zaka ci?"

Girgiza kai yayi alamun a'a, tashi tayi taje cikin drewar din gadonta ta dauko dari
biyar,

"Wallahi wannan ba irin kudin ka bane, ranar da naje gidane Abba yabani 5000,gashi
zan bawa mai gadi ya siyo maka indomie indafa maka"

Baiyi magana ba tasaka kai tafita, tunda tafita bata dawo cikin dakinba har sai da
tadafo indomie din,

Agabanshi tazauna ta diba takai saitin bakinshi, kawar dakai yayi,

"Please yaya yusleem..."

Dakyar yayarda yayi 5 spoon daga haka bai karaba, ita kanta cokali biyu kacal tayi
tabari tature gefe.

Har kwana uku suna cikin wannan hali yusleem dai dai da ruwan gidan yaki sha bare
yaci abinci, aranar tun sassafe yafice daga gidan batareda yasanar da itaba, bashi
yadawo ba sai la'asar,

Tana falo tayi tagumi yazo ya sameta, hannunta yakama ya matse cikin nasa,kallonshi
tayi cikin tausayawa domin har ya dan fada yayi wani iri kamar bashiba,

"Yaya yusleem ina katafi haka tun safe,lafiya kuwa?"

"Zan fada miki, yanzu kitashi kije ki debo kayanki gidan nan zamu bari, yau bazamu
kwana agidan nan ba.."

"Lafiya?" Ta tambayeshi tana zaro ido,

"Kidai je ki kwaso kayanki kifito mu tafi, nasayar da gidanne bama shi kadaiba
komai nawa da kika sani nasayar.."

"To me zakai da kudin?"

"Nasaka acikin asusun marayu, yanzu banida ko kwandala nanah, banida komai yanzu,
su kansu kayan sawata wallahi dan babu yanda zanyi dasu ne amma da bazan kara
sakasu ba.."

Hawayen dake makale acikin idanuwanta sune suka silalo tajuya ta nufi cikin bedroom
dinta,

Lokacin da tafito rikeda babbar trolley dinta shima har ya fito yana kulle part
dinshi, jakarta yakarba yahada da tashi yaja suka fita,

A bakin gate taga wasu mutane guda 3 suna jiransu, kulle gidan yayi da wani babban
padlock yamika musu key din yarike daya awurinshi domin yafada musu da sauran
kayansu aciki,

"Ina mai gadin kuma?" Ta tambayeshi,

"Na sallameshi tun safe"

"To yanzu ina zamuje?"

"Allah ne yasani domin nikaina ban saniba gashi nafada miki babu ko naira daya
atare dani domin hatta account dina na rufeshi..."

Trolley dinsu yasoma ja yayi gaba nan tabi bayanshi suka fara tafiya batare da
sunsan inda zasuje ba.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_


*29*

***Bin bayanshi tayi suka fara tafiya batare da sun san inda zasuje ba har
saida suka danyi nisa da gidansu sannan Hafsat ta dakatar dashi,

"Yaya yusleem yanzu ina wai muka nufane takamaimai?"

"Ai nafada miki ni kaina banida masaniyar inda zamuje..."

"To tsaya inkira ummi inada kudi awurinta sai inje in karbo kaga ko babu komai zai
dan rage mana wani abun.."

Shiru yayi baice komai ba illah tsayawa da yayi akarkashin wata bishiyar mangwaro,

Wayarta ta zaro tasoma kiran Ummi, saida suka gaisa sannan tayi mata maganar kudin
kayan sanyin da ta saka kashi biyu,

"Hafsat kin san ban fiya son in ajiye kudi agida ba amma anyi sa'a ga dubu talatin
zan bawa Salisu yakawo miki yanzu..."

"To shikenan Ummi dan Allah kice yayi sauri saboda amfani zanyi da kudin yanzun
nan..."

Sallama sukayi ta katse wayar takarasa kusa da yusleem ta tsugunna,

"Yi dan hakuri kadan yanzu ummi zata aiko min da kudin"

Daga mata kai yayi baiyi maganaba da alama miskilancin ne ya motsa kuma hakan bazai
rasa nasaba da irin damuwar da yake ciki ba,

Bayan kamar mintuna 15 suna zaune sai ga motar gidansu ummin tana dosowa da sauri
hafsa ta tashi ta tsayar da salisu driver ta karbi kudin tana kallonsa sam bata son
ya fahimci wani abu bare idan yakoma yafada,

"Kaga nima baki nayine yan uwan mijina ne suka zo daga can wani kauye kuma baya nan
shine zan basu kudin mota"

"Allah sarki to Allah ya kiyaye hanya"

"Amin"

Saida taga bacewar motarsa sannan takoma wurin yusleem wanda ke zaune shiru yana
tunani,

"Yaya yusleem tashi mutafi to.."

Mikewa yayi yaja akwatunansu suka fara tafiya,

Adaidaita sahu suka samu suka tare bayan sun fara tafiya mai adaidaitan ya
tambayesu wurinda zai kaisu,

"Bawan Allah idan akwai unguwar da kasani wacce za a iya samun dakin haya ayanzu
kawai kaimu can..." Inji Hafsat,
"Ahh za asamu mana hajiya, unguwar da nake akwai gidajen haya sosai bari muje..."

Yar tafiya mai tsawo kadan sukayi sai gasu cikin wata unguwa, kallon yanayin
unguwar dukkansu suke yi domin da alama ta talakawa ce saboda ko titi babu gashi
gidajen awani cunkushe suke babu tsari,

"Yawwa ga gidan alhaji Bashari yanada gidajen haya har guda uku bari inyi muku
sallama dashi"

"Yawwa mun gode"

Kafin dan adaidaita sahun ma yafita saiga mai gidan yafito,

"Yawwa ga alhajin ma"

Fita Hafsat tayi mai adaidaita sahun yana biyeda ita,

"Alhaji barka da yamma, dama wadannan ne suke neman dakin haya.."

Dan jimm alhajin yayi sannan yace,

"Ai inajin dukka gidajen nan akwai mutane aciki.."

"To alhaji yanzu ya za'ayi?" Inji Hafsat,

"Yawwa natuna jiya wani yafita sakamakon transfer da akayi masa ta aiki amma gidan
ba anan layin bane a layin gabane"

"Alhaji nawane kudin dakin"

"Dubu ishirin ne"

"To shikenan yanzu zamu baka dubu goma, nanda kwana biyu sai mu cika maka"

"To babu laifi, babu laifi Kawo"

Kirgar kudin Hafsat tayi tabashi suka koma cikin adaidaita sahu suka nufi layin da
gidan yake,

Fitowa sukayi suka shiga cikin gidan nan suka ganshi babba domin dakuna sun kai
goma sha biyar can gefe kuma rijiya ce gefenta wasu mata ne kimanin su 8 zaune suna
hira masu kitso kuma sunayi,

Dakin da zasu zauna aciki gashi nan abude duk sumintin ya dan farfashe,kayansu
suka shigar ciki takalli dan adaidaita sahun,

"Bawon Allah a ina zamu samu motar da zata debo mana yan kayayyakinmu?"

"Hajiya nima ai ina yin dakon kayan, bari inje indauko akori kura.."

Fita yayi ita kuma ta tsaya tana karewa dakin kallo wanda yake da dan girma amma ba
canba, gabanta ne yafadi sakamakon tunawa da tayi da matan da ta hango atsakar
gidan ita fatanta daya Allah yasa ba bathroom guda daya bane agidan,

Ji tayi andafa ta, ahankali ta juya, yusleem tagani,

"Tunanin me kikeyi?"

"Yaya yusleem fata nake Allah yasa bathroom din gidan nan ba guda daya bane"
"Idan guda dayane mezai faru?"

"Takura zamuyi, kuma bana son idan kafito daga wanka mutane suyita kare maka
kallo.."

Kafadarta ya dafa yayi mata nuni da hannunsa bayan yadan saki murmushi,

"Kinga bathroom nan acikin dakin nan.."

Sai lokacin ma ita takula da kofar bathroom din amma sam da hankalinta bai kai
nanba, zuwa tayi ta bude nan taga bathroom din dan kuf dashi,

"Wannan dinma duk da haka babu laifi.." Tafada acikin zuciyarta.

Babu jimawa dan adaidaita sahun nan yadawo da mota ta diban kaya fita tayi suka
koma gidansu ta bude tashiga yan kayayyakin da tasan zasu bukata ta debo musu
irinsu kwanukan cin abinci tukunyar girki, bargo, bedsheet,labule sai katifarta
sannan bata bar keken sakarta ba shima ta hado dashi,

Wurin biyar da rabi suka koma gidan hayar nan aka sassauke kayan ta biya kudin
diban kaya Dubu biyar, har ciki mai adaidaita sahun nan ya taimaka musu suka shigar
da kayansu,

Share dakin tayi ta karkade ko ina suka shigar da katifar ta shimfidata wacce ta
cinye fin rabin filin dakin gashi babu ko leda atsakar dakin sai simintin dake
shimfide kawai,

Yar madaidaiciyar dardumar data dauko musu ta shimfida agaban katifar sannan ta
shimfida bedsheet akan katifar tajera musu filillika guda biyu,

Yusleem ta kalla wanda ke kokarin kafa musu labule,

"Yaya yusleem bari indebo ruwa inwanke mana toilet din.."

"Kibari ingama sai na debo"

"A'a kayi wannan din idan kagama sai ka yi alwala kaga fa ko salla bamuyi ba"

Bucket ta dauka ta fita taje bakin rijiya inda matan nan ke zaune,

"Sannunku.."

"Yawwa sannu da zuwa.." Matan suka fada har suna hada baki,

Ruwa taja ta cika bucket din ta dauka ta koma daki, wanke toilet din tayi tasake
komawa ta debo wani ruwan ta cika daya bucket din sannan ta ciko wannan din ta
ajiye,

Alwala sukayi sukai salla,

Kan katifa taje ta kwanta saboda gajiyar da take tareda ita, shikuma yana kan
carpet azaune yana tunanin rayuwa domin ko a mafarki bai taba tunanin wai zai yi
irin wannan rayuwar ba amma dayake Allah shine mai cancanja al'amura sai gashi
rayuwa ta canja ya tsinci kanshi acikin wannan halin,

"Yaya yusleem baka jin yunwa ne?"

Juyawa yayi ya kalleta,


"Inaji amma sam bana sha'awar cin komai"

"Duk da haka daurewa zakayi kaci, bari ayi sallar magrib sai mufita mu samo abinda
zamu ci"

Har bayan sallar magrib Hafsat takasa tashi saboda gajiyar da tayi, saida akayi
sallar isha sannan ta iya mikewa,dakin duhu didim yake saboda babu wuta ga uban
sauro banda zafi da yake addabarsu,

"Gaskiya yaya yusleem muyi sallar nan muje mu samo abinda zamu ci daga nan sai mu
taho da maganin sauro.."

Suna idar da sallar suka fita, gasasshiyar kaza Hafsat tace asiya nan yusleem ya
kalleta,

"Yanzu fa ba lokacin cin abin dadi bane, kibar kazar nan muje shagon can mu sai
gari da sugar.."

"A'a yaya yusleem, gaskiya gari bazai shiga ba wallahi, mudai siyi kazar.."

Son ranta yabi suka siyo gasasshiyar kazar daga nan suka karasa shago suka siyi
maganin sauro da candle guda biyu da ashana sai sabulun wanka give sinki daya da
soson wanka da brush da maclean sai man shafawa Vaseline,

Gida suka koma ya kunna candle din ya ajiye sannan ya kunna musu maganin sauro,

Kasancewar yunwar tasu taci ta cinye yasa baifi rabi suka ci kazar ba, Hafsat ce
tafara tashi ta bude trolley dinta ta dauki zani tadauki soso da sabulun wanka da
brushes dinsu da maclean ta shiga bathroom, wanka tayi tafito ta dauki kayan
baccinta takoma cikin bathroom din,Riga da wando ne red colour masu santsi, rigar
tana da dan guntun hannu yayinda wandon yake dogo,doro hijabinta tayi akan kayan
tafito tahau kan katifa ta kwanta,

"Bari nima inje inyi wankan tunda kin fito" yusleem yafada tareda tashi tsaye ya
shiga cikin toilet din, yajima aciki kamar wanda zai sake fata dama Hafsat tasan
dadewarshi a wanka shiyasa tafara shiga,

Saida yayi kusan minti 30 sannan yafito yana rikeda rigarshi yana tsane ruwan
kanshi,

Gaban kayansu ya karasa ya bude trolley dinshi yaciro yar t shirt da boxer,

Ta dan hasken candle din da suka kunna Hafsat take kallonshi lokacin da yake
kokarin sauya kayan jikinshi,

Rufe idanuwanta tayi saboda wannan shine karo nafarko da zata kwana dashi akan
katifa guda daya,

Juyowa yayi ya kalleta bayan yaje ya dauke kakkauran labulen kofar dakin yabar mai
shara sharan,

"Ko ke bakya jin zafin ne?"

"Inaji mana yaya yusleem, wallahi akwai zafi kila hadari ne agarin"

Candle ya dauka yakarasa gefen katifar yazauna,

"Bama kila bane ga gari nan anata yin walkiya, kalli waje ki gani"
Sai lokacin talura da ashe asaitin kofar daki ta kwanta nan ta mirgina takoma barin
da yake,

"Anan zan kwanta, kai kakoma can barin"

Tashi yayi yakoma bayan yakashe candle din,duhu didim dakin yayi,

"Shine ni kika turo ni kofar daki ko inyaso abin tsoron idan yazo ni ya kamani"

Murmushi tayi ta zare hijabin dake jikinta,tana jinshi ya kwanta agefenta bayan ya
matso da filonshi jikin nata filon sabanin da dayake ajiye acan karshen katifa.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*30*

***Dukkaninsu shiru sukayi kowa da abinda yake tunani acikin zuciyarsa,

"Nanah..." Taji yusleem yakirata, dan juyawa tayi acikin duhun ta kalleshi,

"Yaya yusleem menene?"

"Babu komai dama nayi zaton ko kinyi bacci ne"

Juyawa tayi ta dan gyara kwanciyarta,

"A'a banyi ba"

"To kiyi.."

Lumshe idanuwanta tayi,


"Saida safe"

"Allah ya tashemu lafiya"

Shiru suka sakeyi wanda har bacci ya dauke Hafsat amma shi yusleem sam yakasa
baccin inbanda sake sake babu abinda zuciyarshi keyi masa, yasaka wancen ya kunce
yasaka wancan har garin yayi tsit dare ya raba bai iya yin bacci ba,

Hafsat kuwa cikin barcin da takeyi tafara wani mafarki marar dadi domin wasu manyan
mutane tagani suna bin yusleem aguje kowannensu rikeda katuwar wuka mai kaifi sai
kyalli take zuwa can yusleem din ya fadi daya daga cikinsu ne ya cimmasa ya daga
wukar zai daba masa tayi firgigit ta farka,

Cikin duhun tafara lalubenshi akan katifar amma bata jishiba hakan yasata rudewa,

"Yaya yusleem,yaya yusleem...!"

Shiru tayi sakamakon jin ya amsa daga bakin kofa inda yaje domin saukar da labulen
dakin domin yanzu garin yadauki sanyi duk da ba ayi ruwa ba amma wata iska mai
sanyi ake kadawa,

Karasowa yayi kan katifar, tun kafin yakarasa hawowa taje ta rirrikeshi,

"Yaya yusleem babu abinda yasameka...?"

Riketa yayi ya kwantar da ita awurinda take kwance dafarko,

"Menene yafaru nanah? Lafiya lau nake.. Mafarki kikayi?"

Hannuwanshi ta makalkale cikin nata,

"Yaya yusleem wani mummunan mafarki nayi wallahi..."

"To ai mafarki ba gaskiya bane nanah, ki koma kiyi baccinki kinji..."

D'aga mishi kai tayi kamar yana ganinta tareda tallafe kumatunta da hannunshi guda
daya,

Duk da taga azahiri babu abinda ya sameshi amma sai takasa komawa baccin, shi
kanshi yusleem din shima yakasa yin barcin,

"Yaya yusleem.."

"Na'am..."

"Tunda mun kasa yin bacci katashi muyi alwala muyi sallar nafila watakila sai Allah
ya amsa ya rangwanta mana masifun da suke tunkaro mu..."

"To nanah, bari natashi naje.."

Saurin rikeshi tayi, "yaya yusleem mu tafi tare"

Taren suka shiga toilet din kasancewar duhu ne alwala sukayi suka fito suka fara
sallolin nafila wanda har saida suka yi sallar asuba sannan suka kwanta bacci,
bacci sukayi sosai sai 12 saura sannan Hafsat ta farka, yusleem takalla wanda ta
rirrikeshi yana kwance agefenta,

Tashi tayi tashiga wanka har tafito ta shirya bai tashiba tunanin abinda zasu karya
dashi tafara, mikewa tayi tashiga bathroom ta dauko bucket domin debowa yusleem
ruwan wanka,

"Nanah ina zaki..?" Taji yace da ita idanuwanshi suna rufe,

"Ruwan wanka zan debo maka..."

Tashi zaune yayi,

"Dauko wani bucket din inbiki mu debo tare"

"Kabarshi zan debo"

Tashi yayi dakanshi yaje yadauko bucket din yabita domin ita tuni tajima da fita,
kamar jiya yauma matan gidan suna zazzaune akofar dakin daya daga cikinsu, ganin
Hafsat tafito duk sai suka maida kallonsu gareta, gaishesu tayi kamar jiya sannan
takarasa bakin rijiyar,

Gugar yusleem ya karba daga hannunta,

"Kawo inzuba miki.." Yayi maganar ahankali duk da dama maganarshi bawai cika karfi
tayiba,sakar mishi tayi yafara janyo ruwan yana zuba mata acikin bucket din,

Ganin hankalin matan ya komo garesu yasa duk taji ta tsargu musamman ma dataga
kamar sunfi karkata ga kallon yusleem, saida ta jirashi ya cika nasa bucket din
sannan suka dauka suka tafi,

Acikin bathroom din tabarshi bayan ta ajiye ruwan tafito,

Keken sakarta ta kinkimo ta zauna agefen katifa tasoma saitashi domin so take
tafara yin sakar kayan sanyi, jin tafiyar yusleem yasata juyawa ganinshi tayi babu
riga sai iya boxer dan haka tayi saurin maida kanta ta sunkuyar,

Kanta yana sunkuye har yagama shiryawa yasaka kayanshi yadawo kan katifar ya Zauna,

"Yaya yusleem ga guntun naman jiya can bari indauko mana.."

Kafin yabata amsa har tatashi taje ta dauko,

"Kaga cewa nayi ko inje insaida kujeru na sai insiyo zaren bulu da sauran kayan da
zamu bukata, kaga dole sai mun siyo risho da kayan abinci.."

Shiru taji yayi baice komai ba, dagowa tayi ta kalleshi,

"Yaya yusleem bakace komai ba"

"Nanah gaskiya akaina bazaki rabu da kayanki ba, karki saida ko cokali naki"

Murmushi tayi,

"To ai ba saboda kai zan siyarba, saboda nida kai zan siyar"

"To ban goyi baya ba"

"Shikenan tunda baka amince ba"

"Ba amincewa ne banyiba kawai dai idan narabaki da kayanki ne banyi miki adalci ba"

"To magana tawuce,yanzu kasan me? Kafadawa mami cewar zakayi tafiya ta gaggawa zuwa
wani state din mai nisa saboda kasan zata nemeka idan kuma har ta nemeka bata
sameka ba hankalinta tashi zaiyi, idan tayi maka maganata kace tare zamu tafi kaga
hankalinta zaifi kwanciya sannan tunaninta bazai taba Kawo mata cewar da akwai
matsala ba.."

"To amma iyayenki fa? Sukuma me zan fada musu"

"Sudinma hakan zan cemusu munyi tafiya zuwa wani gari mai nisa, koma kawai muce
Niger muka tafi.."

Hadaddun wayoyinshi dake ajiye akasan trolley dinshi hadeda laptop dinshi yadauko
ya kunna,

Number mami yayi dialing babu bata lokaci ta dauka, dakyar ya saita nutsuwarshi
yayi mata bayani bayan sun gaisa, fatan alkhairi tayi musu daga nan sukayi sallama,

"Nima bari inkira Ummi infada mata kaga shikenan daga nan mun gama da matsalar gida
sai mu fuskanci wata rayuwar kuma"

Tata wayar itama ta dauka ta kira Ummi ta sanar mata daga nan takashe wayar amma
shi yusleem tashi wayar abude yabarta saboda yasan abokan harkarshi zasu nemeshi.

Misalin karfe 2 narana ta dauki dan madaidaicin food flask, fita tayi domin yusleem
bacci yakeyi, tsakar gida taje inda matan nan ke zazzaune ta tambayesu inda ake
sayar da abinci,

"Me kike so? Kawo amir yasiyo miki" inji wata mata wacce ahaife da alama bazata
girmeta ba,

"Yawwa nagode dan wanke nakeso"

Naira dari tabayar yaron yatafi siyo mata, daki takoma tazauna tana lissafi domin
kudin da yayi saura yanzu baifi dubu goma sha daya da yan canji ba gashi kuma
bukatunsu nada yawa domin basuda kayan abinci kuma zasu cikawa mai gidan haya
kudinsa gashi tana son ta siyo zaren saka,

Yanke hukuncin zata sayar da kujerunta kawai tayi batareda yusleem yasaniba, jin
muryar amir yana sallama yasata tashi taje ta karbo abincin ta danka mishi naira
goma,

Bata tashi yusleem ba saboda tasan daren jiya bai samu bacci ba har saida ya tashi
dan kanshi lokacin karfe 3:32 na yamma,

Dan waken tasa musu suka ci bayan sun gama tace mishi zata fita kasuwa domin siyo
zaren kulu da dan abubuwan da ba arasa ba, acikin dakin tabarshi tafita,

Direct wurin wasu kafintoci tawuce tayi musu tallen kujerunta sukace zasu siya amma
sai sun gansu nan tace to zuwa gobe zatazo suje sai sugani,

Daga nan kasuwa tawuce tasiyo zarirrukan kulu kala kala sannan ta siyo musu dan
karamin risho ta hado musu kayan tea da babban bread guda daya,

Ana kokarin yin sallar magrib tadawo gida, akan katifa tasamu yusleem yana zaune,

"Sannu nanah.."

"Yawwa yaya yusleem sannu nabarka kai kadai ko"


Murmushi yayi, "ai kece da sannu"

"Kaga abubuwan da nasiyo, ga risho amma kalanzir dinne na dari biyu kawai nasiyo
nasan zai ishemu mu rinka dan dafa ruwan zafi"

Tausayinta yaji yakamashi saboda irin rayuwar da suka samu kansu aciki yanzu wacce
yasan shine silar jefata aciki,

"Allah yayi miki sakayya da gidan aljanna.." Shine abinda yafada kawai ya mike
yashiga toilet domin yin alwala,

Tea tadafa musu da daddaren suka sha suka kwanta, wayarshi ce ta hau vibrating nan
yadaga,

"Yusleem kayi gaggawar kashe wayarka domin su oga nemanka suke ido rufe, idan baka
kashe wayarka ba zasuyi tracing wurinda kake..." Wannan shine abinda kunnuwan
yusleem suka ji wanda bai gane ko muryar waye ba kitt yaji wayar takatse nan
yakashe wayar gaba daya,

Sam baya son Hafsat taji bare hankalinta yatashi nan yaki fada mata gaskiyar abinda
yake faruwa domin tun lokacin data fita suke fafatawa shida abokan harkar tasa
domin sun ce mutukar yace yabar wannan harkar to sai dai wani bashi ba saboda sun
san tona musu asiri zaiyi,

Jin baice komai ba yasa Hafsat bata Kawo komai acikin ranta ba daga karshema tashi
tayi ta kunna candle tahau keken sakarta tafara saka kayan sanyi na yara, sai wurin
12 sannan ta hakura ta kwanta.

Washe gari dakyar da dabara yusleem yabarta tafita, wurin masu siyan kayan nan da
sukayi alkawarin siyan kujerunta ta nufa daga can suka wuce gidan yusleem nada
tabude musu sukaje suka gani, ganin kyawun kayan da irin tsaruwar gidan sai masu
siyan kayan suka nemi fasawa domin gani suke kamar karya take banata bane ko kuma
ba mallakinta bane dakyar tashawo kansu akayi cikini dubu 50 suka siya duk da kayan
sun wuce haka,

Fita sukayi da kujerun tamayar gidan ta rufe ta nufi kasuwa da kudin, komai da
tasan zasu bukata na kayan abinci saida ta siya musu, data gama siyayyar kuwa
adaidaita sahu ta nema ta zuba kayan yakaita har kofar gida.

Yusleem na kwance agefen katifa bayan ya kammala dafa musu ruwan zafi wanda zasu
sha tea sai gata tashigo niki niki da kaya, manyan idanuwanshi yazuba mata,

"Daga ina haka?"

"Ina zuwa yaya yusleem ai zan fada maka"

Tashi yayi ya taimaka mata suka karasa shigo da kayayyakin,

Kudin hannunta ta ajiye ta zare hijabin jikinta ta zauna,

"Yaya yusleem nagaji sosai gashi ina jin yunwa"

"Bari inhada miki tea.."

Kafada ta makale,

"Gaskiya ni bazan sha tea da wannan uban zafinba, tunda ga kayan abinci sai ka dafa
min abinci inci"
"To ai baki fada min a inda kika samo wadannan kayan abincin ba.."

"Zan fada maka kafara bani abinci inci tukunna mana"

"Nifa ban iya girki ba sai dai kiyi guiding dina"

"To fara kunna risho din ka mayar da ruwan zafin can ka dora.."

Kamar yadda tace haka yayi, yanayi tana kwatanta mishi har yadafa musu farar taliya
yasoya mai,

Acikin filet ya zuba musu yakai gabanta inda take kwance, hannunshi ya mika mata
amma sai tayi kamar bata ganiba ta tashi zaune cikeda kunya,

Saida suka gama cin abincin sannan ta fada mishi duk yanda akayi,

"Yanzu ga 10 thousands din wannan alhajin cikon kudin hayarshi idan yazo sai
abashi, wannan kuma 9 thousands din sai mu ajiye.."

Rasa abinda zaice yayi yatsaya kawai yana kallonta saboda yasan acikin mata dari
dakyar za asamu irinta guda goma, Hafsat tayi masa halacci acikin rayuwarsa, ta
rufa masa asiri, tayi sanadiyyar fitarshi daga cikin halaka, gashi tana zaune dashi
a lokacin da bashida madafa har tana salwantar da abubuwan data mallaka saboda shi,

"Nanah banida bakin da zan gode miki illah..."

Tashi tayi tabar dakin ta wuce toilet saboda bata son yayi mata godiyar abinda
tayi,

Cikin dare ta tasheshi tana makale da cikinta saboda wani irin ciwo mararta keyi
mata, riketa yayi acikin duhun da suke yana tambayarta menene,

"Yaya yusleem cikina ne yake ciwo"

"Ciki kuma? Sannu to yi hakuri"

"Bani ruwa insha.."

Ruwa ya Kawo mata takarba tasha takwanta, candle ya kunna yajata jikinshi yadora
kanta akirjinshi ya rungumeta yasoma rarrashinta hannunshi yakai kan cikin nata nan
tayi saurin ture hannun,

Kwanciya luff tayi ajikinshi sakamakon duk gabobinta ciwo suke yimata, tambayar
duniya yayi mata akan tafada mishi abinda yasa mata ciwon cikin amma tayi shiru
saboda kunya takeji tace mishi period pain ne,

Ajikinshi ta kwana har asuba tayi sai lokacin tasamu saukin ciwon da marar tata
keyi bacci yadan dauketa kwantar da ita yayi ya nufi toilet,

Sai wurin karfe 6 sannan tatashi daga baccin nan tarasa yadda zatayi tana son
tafada mishi kuma tana kunya, komawa tayi ta kwanta ta kalleshi,

"Yaya yusleem kira min amir dan gidan maman amir.."

"Meya faru?"

"Aikenshi zanyi.."

"Toh bari naje"


Tashi yayi yafita ita kuma ta rakashi da ido...

*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*31*

****Bai wani jima da fitaba sai gashi yadawo, kusa da ita yakarasa ya
tsugunna agabanta,

"Su maman amir din basu bude kofar su ba inaji basu tashiba.."

Gyada mishi kai tayi taja bargo zata lulluba, rike bargon yayi,

"Kitashi kiyi salla mana kafin kisake kwanciya"

Shiru tayi masa tasake yunkurin lulluba, kara maimaita maganarshi tafarko yayi,

"Ba yanzu ba.."

Ganin ta dage taki tashi yasashi rabuwa da ita tasake lulluba takoma barci, gefenta
yaje ya kwanta,

K'arfe 8 tafarka ta kalli yusleem wanda ke gefenta akwance,


"Yaya yusleem dubo min ko su Maman amir din sun tashi.."

Tashi yayi yafita jim kadan sai gasu sun dawo tareda amir din,

"Yaya akwai biro awurinka?"

"A'a babu"

"Amir jeka wurin ummanka kace tabani aron biro da yar paper kaji"

Tafada tana ciccije lebenta, fitar amir tasa yusleem komawa wurinta,
"Har yanzu ciwon ne?"

Daga mishi kai tayi,

"To ko asibiti zamuje?"

"A'a"

Shigowar amir yasa sukayi shiru dukkaninsu, karbar takarda da biron tayi tana daga
kwance ta rubuta mishi abinda zai siyo mata ta kalli yusleem,

"Yaya yusleem bashi dari biyu acikin kudin nan"

Tashi yusleem yayi yadauko kudin yabashi, sake gyara kwanciyarta tayi ta tukunkuna
har amir yadawo kasancewar yusleem yana tsaye bakin kofa yasa amir bashi ledar pad
din,karba yusleem yayi ya leka cikin ledar, sai yanzu ya fahimci abinda yake
damunta,

Tana kokarin tashi domin yin wanka ya dakatar da ita,

"Tsaya indafa miki ruwan zafi sai kiyi wankan dashi zaki fi jin dadin jikinki"

Komawa tayi tasake kwantawa shikuma ya dora mata ruwan zafin bayan ya kunna risho,

Bathroom yashiga ya dauko bucket yazo ya juye mata ruwan aciki yakai mata cikin
toilet tareda sirka mata shi,

"Ga ruwan wankan can nakai miki, tashi kije kiyi"

Dakyar ta tashi tajuya ta dan kalleshi ganin ba ita yake kalloba hankalinsa yana
kan ruwan da zai sake maidawa ya tafasa yasata saurin tashi bayan taja zanin
wankanta tashige cikin bathroom.

Bata dade sosai ba tafito lokacin har yusleem ya kammala hada musu abinda zasu
karya dashi, kallonshi take kasa kasa saboda duk yau atakure take,shi kansa ya
fahimci haka shiyasa ma yajuya mata baya bayan ya kwanta bisa katifa,

Ganin baya kallonta yasata dan sakewa tashirya tasaka wata blue din atamfa dinkin
riga da skirt wanda dayane daga cikin irin dunkunan da mami tayiyyi mata,

Zama tayi abakin katifa wanda yayi sanadiyyar juyowar yusleem,

"Kin gama?"

"Uhm" tabashi amsa,

Tashi yayi ya debo mata tafasasshen ruwan zafi acikin cup,

"Kisha wannan ruwan zafin zai dan rage miki radadin ciwon da marar taki keyi"

"Ni ba ciwon Mara nakeba ciwon cikine"

Murmushi yayi ya mika mata cup din,

"Ashe dai ke dinma kin iya karya ban saniba, meye hadin period da ciwon ciki? Ai
nazaci mahaifa a mara take ba acikin cikiba ko ke taki acikin ciki take?"
Karbar cup din tayi tasoma kurbar ruwan zafin batare da tayi magana ba har saida ta
shanye,

"To ga abinci kuma taliya"

Girgiza masa kai tayi ta kwanta babu jimawa sai bacci, rasa abinda zaiyi yayi
saboda dama idan tana ido biyu ne suke yin yar hira, shi dinma kwanciyar yayi tun
yana yan tunane tunane har bacci ya daukeshi,

Hafsat ce tafara farkawa yanzu taji dadin jikin nata sannan kuma ciwon ma yaragu
sosai sai kadan kadan, ganin yusleem din bacci yake yasata zuba abincin ita kadai
ta danci tana gamawa yatashi, fita tayi tace mishi zataje wurin maman amir,

Dayake mata babu wuyar sabo tunda taje suke hira da maman amir din kasancewar itama
mijinta baya nan dama kuma police ne,

Yau duk taki sakewa ta zauna wuri daya da yusleem saboda kawai yagane abinda ke
damunta, da tashiga dakin zata fice takoma wurin maman amir shi kanshi yusleem din
ya lura da ita,

Tun azahar da tashiga wurin maman amir sai yamma lis tadawo wannan dinma dan wanka
zatayi ne, yana kwance ta shigo taki kallon inda yake tadauki abinda zata dauka
tashiga wanka bakar ledar da tasaka pad din data cire da rana taga ya dauke yadora
akan window din bathroom din, acikin toilet din tashirya dan haka koda tafito iya
kaya kawai tasa tashafa dan mai tagama tafita.

Wasa wasa har karfe 8 nadare tana dakin maman amir saboda ita so take sai yusleem
yayi bacci sannan zata koma dakin, shi kuma yau duk kadaici yakeji saboda bata
cikin dakin ganin har 8 ta dan gota yasashi fita yanufi dakin maman amir daidai
lokacin da aka dan fara yayyafi yif yif alamun ruwa yana daf da tsinkewa,

Abakin kofar dakin yatsaya,ahankali yayi magana,

"Nanah..!"

"Na'am"

Hafsat ta amsa tareda tashi, kallonta maman amir tayi,

"A'a keda wa? Banji magana ba sai ji nayi kawai kin amsa"

"Yaya yusleem ne yake kirana"

"Anya kuwa? Kodai kunnenki ne"

"Wallahi shine, bari inje"

Duk da haka maman amir bata yarda ba saida ta leka nan taga ashe shidinne kuwa yana
tsaye akofar dakin,

"Lahh ashe dagaske shine, kinga kuwa ni banji maganarshi ba, mijin naki ne ma ni
sai inga kamar baya magana"

"Dama ai nafada miki shine, bari inje, saida safe"

Fita tayi lokacin har ruwan yadan soma karfi, wucewa yayi tabishi abaya, suna shiga
daki yajuya ya kalleta,

"Da ban kiraki ba sai yaushe zaki dawo?"


"Sai anjima"

"To ke haka akeyi mata da mijinta kije ki zauna musu adaki tun rana"

"Mijin nata fa baya nan"

"To amma ai ke naki mijin yana nan ko? Shine zaki kama hanya kitafi kibarshi"

Shiru tayi bata amsaba, maimakon ma tazauna sai kawai ta dauki kayan baccinta
tanufi toilet, shi yau yarasa wacce irin kunya takeji sam taki sakewa dashi shikuma
yafi son tasaki jiki dashi sosai tadaina jin kunyarshi,

Yana nan zaune tafito sanye da rigar bacci wacce tadora zani da hijab akai,

"Ga abinci nan ko zaki ci"

Girgiza masa kai tayi, "Allah nakoshi tun abincin da naci da rana"

Maimakon tazo ta kwanta sai yaga tadauki candle ta tafi kan keken sakarta, nan ta
farayi babu ji bare gani, yana kwance yana kallonta har 11 nadare kuma har lokacin
ba adauke ruwan da ake tsugawa ba,

Lumshe idanuwanshi yayi yabudesu akanta take zuciyarshi tafara kissima mishi
siffarta, baka ce yar doguwa sannan ita ba ramammiya bace kuma bata da kiba can,
tanada round face mai dauke da madaidaitan idanuwa sai dan dogon hanci wanda yake
daf da dan karamin bakinta, tanada gashin gira sosai da gashin ido haka kuma gashin
kanta ma yanada dan yalwa,

Ido ya tsura mata domin ta dade da cire hijabin dake jikinta dan haka daga ita sai
wata rigar bacci cotton mai hannun shimi milk colour mai digon fari da ja da baki
da pink da blue duk dai kaloli ne aka diddiga ajiki, sai hula mai santsi kalar
ruwan siminta dake kanta saboda duk tunaninta yusleem yayi bacci, sakarta takeyi
bil hakki da gaskiya tana son ta kammala rigar da tafara kafin ta kwanta bacci
gashi har candle din data kunna yakusa cinyewa shiyasa taketa sauri takarasa kafin
ya mutu,

Tashi yusleem yayi sadaf sadaf ya nufi wurinta baki yasa ya hure candle din take ya
mutu ita kuma ya daukota cak daga inda take zaune, tsorone ya ziyarceta hankalinta
yatashi domin bata taba zaton yusleem bane kokarin kurma masa ihu take yayi saurin
rufe mata bakinta da hannunshi ahaka suka karasa kan katifa ya kwantar da ita,
laluben hannunshi tafara domin tananne kadai zata gane idan shine cikin sa'a ta
lalubo zobenshi na azurfa wanda ke sanye cikin babban dan yatsanshi na tsakiya,

Duk da tagane shine gabanta bai daina faduwa ba sannan kuma jikinta bai daina
rawaba domin tayi mutukar tsorata,

Pillow yaja yadora kanta akai,cikin maganarshi mai sanyi ahankali yace,

"Ke yau bazaki yi bacci bane?"

Dan matsar da jikinta take kokarin yi amma ya hanata saboda irin yanda ya manne
gefen jikinshi da nata domin hatta kanshi yau akan pillown ta yake,

"Yaya yusleem wata riga naso da inkarasa kafin inyi baccin.."

"To kiyi hakuri kibari sai gobe.." Yayi maganar asaitin kunnenta ahankali,

"Amma wallahi kabani tsoro, kaji yanda na tsorata kuwa?"


"Kin zaci wanine yazo saceki?"

"A'a nazaci ko aljanine saboda fa lokaci daya naga candle din ya mutu sannan anyi
sama dani.."

Murmushi yayi yaja bargo ya lullubesu,

"Sanyi akeyi ne kuma wallahi inajinsa sosai kekuma kin tafi da dumin kin barni
shiyasa na dauko ki"

Shiru tayi saboda kunya bata amsa ba, sarai yagane kunyace ta hanata magana,

Jikinta taji ya shige sosai yadora kanshi atsakiyar kirjinta,

"Yaya yusleem...." Takira sunanshi,

"Na'am nanah.."

"Gaskiya to banda juye juye ka ajiye kanka wuri daya dan wallahi kirjina ciwo yake"
tayi maganar cikeda shagwaba kamar zatayi kuka,

Murmushi yayi saboda yagane abinda take nufi,

"Nasani ai, bazan fama ki ba, kiyi barcinki"

Shiru tayi takasa magana,shi dinma shirun yayi amma dai aranshi yana jin cewar
kullum haka zai rinka yi mata har tasamu tasake dashi yadda ya kamata,

Saida yaji tayi bacci sannan shima yasamu zarafin yi. Dayake kusan kwana akayi ana
ruwa sai karfe 6 harda wani abu ya iya tashi,

Yana zaune bayan ya idar da salla Hafsat tatashi, brush tashiga bathroom tayi
tafito ta kunna risho ta dora ruwan wanka,

Sam takasa kallon koda gefen da yake zaune,

"Masak'iya babu magana? Ya saka?"

Murmushine ya subuce mata saboda jin abinda yace sai yanzu tagane ashe shidinma ya
iya tsokana,

"Ai wallahi jiya ka tsoratani"

Murmushi yayi yakoma ya kwanta,

"Ke dince ai gani nayi kinfi bawa sakarki muhimmanci fiyeda barcinki.."

Ruwan wankanta ta juye ta dora wani tashiga wanka.

Duk da dai yanata janta da magana amma bata sake dashi ba sosai saboda yanzu har ma
tafi jin kunyarshi fiyeda jiya, tashi tayi da niyyar fita zuwa dakin maman amir,

"Ina zakije?" Taji ya tambayeta,

"Dakin maman amir zanje"

"Shikenan to nima bari intashi inleka kofar gida inzauna tunda kema fita zakiyi"
Murmushi tayi tafita, tashi shidinma yayi yasa takalminsa yafita kofar gida wanda
bama wai taba fitowa yayiba tun zuwansu unguwar sai yau,

Kan wani dan dutse yasamu yazauna, yana zama ko minti 5 baiyi ba wasu mutane
sukazo a mota kimanin su biyar suka kamashi suka saka a mota suka tafi dashi......

*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

_Kuna ina? Group members na Duniyar makaranta group 1&2 wannan shafin mallakinku
ne domin jin dadinku...!_

*36*

***Kafin ta k'arasa wurin yusleem tayi karfin halin tsaida hawayen dake yi
mata ambaliya akan kuncinta,

Murmushin karfin hali ta kakaro tayi lokacin da ta isa wurin yusleem,

"Yaya yusleem tashi muje..., anjima zan dawo na sai maka maganin saboda yanzu kudin
hannuna bai kai ba"

Kallonta yayi yana jingine ajikin kujerar dake jere acikin reception din,

"Nawa ne?"

"Ka tashi muje kawai yaya yusleem..."

Bai sake yin magana ba yatashi, hannunshi ta rike suka fita, suna fita suka samu
keke napep suka shiga,

Lokacin da suka koma gida ruwan zafi kadai ta dafa mishi domin baya iya cin abinci
komai yaci sai yayi amansa, tana kokarin fita maman amir ta aiko mata da dan wake,
Kasa zaunawa taci tayi saboda idan har ba kudin nan taje ta nemo ta siyowa yusleem
magani ba hankalinta bazai taba kwanciya ba,

Wurin kafintocin da suka siyi kujerunta takoma tasake kai musu tallar dayan kujerun
nata na babban falo babu bata lokaci suka tafi gidan taje ta bude musu,

Duk haduwar kujerun nan da kyawunsu amma sai kafintocin sukayi mata tayin wulakanci
wai dubu 60 zasu siya, kin siyarwa tayi nan suka kara dubu goma yazama dubu
saba'in,ganin kudin basu cikaba yasata fito musu da wani show glass dinta wanda aka
zuba mata humra da turaren wuta aciki, dubu goma sha biyar suka siya,

Saida suka fitar da kayan sannan ta rufe gidan tatafi, kai tsaye asibitin da sukaje
da yusleem ta koma taje pharmacy ta siyo mishi maganin sachet daya,

Lokacin data koma gidan samunshi tayi yana bacci dan haka ta ajiye mishi maganin ta
shiga wanka tafito, harta shirya bai tashi ba sai da ta idar da salla sannan taji
motsinshi, juyawa tayi ta kalleshi,

"Sannu yaya yusleem"

"Yawwa, kin dawo?"

"Nadawo lokacin kana bacci.."

Mikewa tayi taje kusa dashi ta zauna,

"Yaya yusleem ga maganin nasiyo maka"

Kallonta yayi bayan ya gyara zamansa,

"A ina kika samo kudin da kika siyo?"

"Yaya yusleem kujerun nan naje nasiyar, lafiyarka yanzu ni tafi min komai.."

Hannunshi ya dora akan nata,

"Amma meyasa kika zabi sayar da kayanki? Ba ga nawa kayan ba wayoyina da laptop
dina"

Girgiza masa kai tayi,

"Nawa kayanma naka ne, sannan nasan yanzu aduniya baka mallaki komai ba sai wayarka
da laptop wannan dalilinne yasa bazan bada goyon bayan mu siyar dasu ba.."

"Nanah agaskiya ban san da wanne baki zan yimiki.."

Saurin rufe masa baki tayi bata barshi yakarasa ba,

"Inbaka maganin kasha yanzu ko zaka dan ci abincin da Maman amir ta Kawo min?"

"Bazan ci komai ba, bani maganin kawai nasha"

Tashi tayi ta dauko mishi ta hado da ruwa, abin mamaki kwata kwata kwayoyin maganin
kwallo 6 ne aciki bamasu wani yawa bane sai dan karen tsada abinda yayi mutukar
tayar da hankalin Hafsat,

Saida taga yasha maganin sannan ta dauko dan waken da maman amir takawo mata taci,
Hannu ya mika mata bayan tagama cin abincin ya kwantar da ita akusa dashi, kasa
kasa yake yi mata magana suna yin yar hira.

Tunda Hafsat taga yakusa shanye maganin hankalinta yatashi nan tasake komawa wurin
kafintoci ta sayar musu da gadajenta gaba daya taje ta siyo mishi magunguna saboda
sam bata son ta doshi umminta ko abbanta da lalurar yusleem domin tasan asirinsu
yana iya fallasa,

Haka taci gaba da daga kayanta tana sayarwa tana siya masa magani wanda yanzu haka
bata da komai domin hatta su fridge dinta da sauran kayan kallonta duk ta siyar ta
hada kan kudin ta ajiye wani kuma ta saiwa yusleem magani, yanzu abu dayane ke
damunta shine kullum yusleem yana shan magani amma sauki baya samuwa kuma har yanzu
baya iya cin abinci sai ruwan zafi gashi kusan 3weeks da zuwansu asibitin,

Sake shiryawa sukayi suka koma asibiti ganin dr sufyan, bayan yagama dudduba
yusleem sun kama hanyar fita har sun kai kusa da gate Hafsat ta dakatar da yusleem,

"Yaya yusleem tsaya zo mukoma wurin dr akwai abinda nake son fada mishi"

"To Nana shiga kifito mana, bari injiraki anan"

Komawa office din dr sufyan Hafsat tayi, zaune tasameshi yana rikeda cup yana
kurbar tea,

"Madam ya akayi?"

"A'a babu komai likita dama cewa nayi ko zaka sauya mana wani maganin saboda wannan
din yayi tsada da yawa kuma har yanzu bai warkeba gashi baya iya cin abinci..."

Tunda tafara jawabi ya kura mata ido baya ko kiftawa har saida ta gama, ajiye cup
din dake hannunshi yayi ya dora hannuwanshi akan table,

"Wato madam abinda zaki fahimta shine mijinki dan homo sexual ne wanda kusan
lalurar ma taci karfinsa so dole sai magani mai karfi zai rinka sha, wannan maganin
ba ako ina ake samunsa ba saboda tsadarshi dan inajin ma gaba daya garin nan baifi
chemists guda uku zaki samu ba wadanda suke kawoshi, amma ni zan taimaka miki zan
rinka baki maganin free mutukar zaki amince da abinda zan fada miki.."

"Likita ni sassauci nake son kayi mana ka sauya mana wani maganin wanda bai kai
wannan tsada ba.."

"To ai madam condition din da mijinki yake ciki yanzu dole irin wannan maganin zai
rinka sha,amma ni zan taimaka miki.."

"To nagode dr, nagode madalla.."

"A'a ai ba wani abu bane, zan baki card wanda yake dauke da address din gidana dake
cikin G. R. A. Governor road.." Yakarashe maganar yana lasar lips dinshi,

Sai lokacin Hafsat ta fahimci inda maganar tashi ta nufa,

"Dr aini ba yar iska bace sannan banyi kamada matan banza ba wadanda zasu iya cin
amanar mazajensu ba..."

Hannu ya daga mata,

"Amma shi mijin naki meyasa yaci taki amanar yaje maza suka bata masa rayuwa? Shifa
da maza yan uwanshi ma yarinka alaka,Bari infada miki gaskiya kidaina wahalar da
kanki akan mijunki domin situation din da yake ciki yanzu bazai taba kallonki a
matsayin mace ba bare har ya iya kusantarki saboda lalurar dake tare dashi, gaba
daya bayanshi yakusa lalacewa domin sperm din dake shiga ciki babu wurinda zai fice
shine sai yarinka taruwa yana taruwa har idan yakai wani stage sai wurin ya lalace
har tsutsotsi su rinka fita ta wurin dan haka kidaina wahalar da kanki abanza, ni
zan rinka bashi magani kyauta duk da tsadarshi mutukar kin amince da bukatata domin
nan asibiti nane wadannan magungunan kuma tun daga India nake iyo ordersu ake kawo
min.....!"

Sassauta muryarshi yayi cikeda yaudara da son janyo hankalinta,

"Kinga maimakon ki zauna kina yimasa wahala bayan bazai iya amfana miki komai ba
gara kisamu wanda zai rinka debe miki kewa duk lokacin da kika so...!.

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

_Kuna ina? Group members na Duniyar makaranta group 1&2 wannan shafin mallakinku
ne domin jin dadinku...!_

*36*

***Kafin ta k'arasa wurin yusleem tayi karfin halin tsaida hawayen dake yi
mata ambaliya akan kuncinta,

Murmushin karfin hali ta kakaro tayi lokacin da ta isa wurin yusleem,

"Yaya yusleem tashi muje..., anjima zan dawo na sai maka maganin saboda yanzu kudin
hannuna bai kai ba"
Kallonta yayi yana jingine ajikin kujerar dake jere acikin reception din,

"Nawa ne?"

"Ka tashi muje kawai yaya yusleem..."

Bai sake yin magana ba yatashi, hannunshi ta rike suka fita, suna fita suka samu
keke napep suka shiga,

Lokacin da suka koma gida ruwan zafi kadai ta dafa mishi domin baya iya cin abinci
komai yaci sai yayi amansa, tana kokarin fita maman amir ta aiko mata da dan wake,

Kasa zaunawa taci tayi saboda idan har ba kudin nan taje ta nemo ta siyowa yusleem
magani ba hankalinta bazai taba kwanciya ba,

Wurin kafintocin da suka siyi kujerunta takoma tasake kai musu tallar dayan kujerun
nata na babban falo babu bata lokaci suka tafi gidan taje ta bude musu,

Duk haduwar kujerun nan da kyawunsu amma sai kafintocin sukayi mata tayin wulakanci
wai dubu 60 zasu siya, kin siyarwa tayi nan suka kara dubu goma yazama dubu
saba'in,ganin kudin basu cikaba yasata fito musu da wani show glass dinta wanda aka
zuba mata humra da turaren wuta aciki, dubu goma sha biyar suka siya,

Saida suka fitar da kayan sannan ta rufe gidan tatafi, kai tsaye asibitin da sukaje
da yusleem ta koma taje pharmacy ta siyo mishi maganin sachet daya,

Lokacin data koma gidan samunshi tayi yana bacci dan haka ta ajiye mishi maganin ta
shiga wanka tafito, harta shirya bai tashi ba sai da ta idar da salla sannan taji
motsinshi, juyawa tayi ta kalleshi,

"Sannu yaya yusleem"

"Yawwa, kin dawo?"

"Nadawo lokacin kana bacci.."

Mikewa tayi taje kusa dashi ta zauna,

"Yaya yusleem ga maganin nasiyo maka"

Kallonta yayi bayan ya gyara zamansa,

"A ina kika samo kudin da kika siyo?"

"Yaya yusleem kujerun nan naje nasiyar, lafiyarka yanzu ni tafi min komai.."

Hannunshi ya dora akan nata,

"Amma meyasa kika zabi sayar da kayanki? Ba ga nawa kayan ba wayoyina da laptop
dina"

Girgiza masa kai tayi,

"Nawa kayanma naka ne, sannan nasan yanzu aduniya baka mallaki komai ba sai wayarka
da laptop wannan dalilinne yasa bazan bada goyon bayan mu siyar dasu ba.."

"Nanah agaskiya ban san da wanne baki zan yimiki.."


Saurin rufe masa baki tayi bata barshi yakarasa ba,

"Inbaka maganin kasha yanzu ko zaka dan ci abincin da Maman amir ta Kawo min?"

"Bazan ci komai ba, bani maganin kawai nasha"

Tashi tayi ta dauko mishi ta hado da ruwa, abin mamaki kwata kwata kwayoyin maganin
kwallo 6 ne aciki bamasu wani yawa bane sai dan karen tsada abinda yayi mutukar
tayar da hankalin Hafsat,

Saida taga yasha maganin sannan ta dauko dan waken da maman amir takawo mata taci,

Hannu ya mika mata bayan tagama cin abincin ya kwantar da ita akusa dashi, kasa
kasa yake yi mata magana suna yin yar hira.

Tunda Hafsat taga yakusa shanye maganin hankalinta yatashi nan tasake komawa wurin
kafintoci ta sayar musu da gadajenta gaba daya taje ta siyo mishi magunguna saboda
sam bata son ta doshi umminta ko abbanta da lalurar yusleem domin tasan asirinsu
yana iya fallasa,

Haka taci gaba da daga kayanta tana sayarwa tana siya masa magani wanda yanzu haka
bata da komai domin hatta su fridge dinta da sauran kayan kallonta duk ta siyar ta
hada kan kudin ta ajiye wani kuma ta saiwa yusleem magani, yanzu abu dayane ke
damunta shine kullum yusleem yana shan magani amma sauki baya samuwa kuma har yanzu
baya iya cin abinci sai ruwan zafi gashi kusan 3weeks da zuwansu asibitin,

Sake shiryawa sukayi suka koma asibiti ganin dr sufyan, bayan yagama dudduba
yusleem sun kama hanyar fita har sun kai kusa da gate Hafsat ta dakatar da yusleem,

"Yaya yusleem tsaya zo mukoma wurin dr akwai abinda nake son fada mishi"

"To Nana shiga kifito mana, bari injiraki anan"

Komawa office din dr sufyan Hafsat tayi, zaune tasameshi yana rikeda cup yana
kurbar tea,

"Madam ya akayi?"

"A'a babu komai likita dama cewa nayi ko zaka sauya mana wani maganin saboda wannan
din yayi tsada da yawa kuma har yanzu bai warkeba gashi baya iya cin abinci..."

Tunda tafara jawabi ya kura mata ido baya ko kiftawa har saida ta gama, ajiye cup
din dake hannunshi yayi ya dora hannuwanshi akan table,

"Wato madam abinda zaki fahimta shine mijinki dan homo sexual ne wanda kusan
lalurar ma taci karfinsa so dole sai magani mai karfi zai rinka sha, wannan maganin
ba ako ina ake samunsa ba saboda tsadarshi dan inajin ma gaba daya garin nan baifi
chemists guda uku zaki samu ba wadanda suke kawoshi, amma ni zan taimaka miki zan
rinka baki maganin free mutukar zaki amince da abinda zan fada miki.."

"Likita ni sassauci nake son kayi mana ka sauya mana wani maganin wanda bai kai
wannan tsada ba.."

"To ai madam condition din da mijinki yake ciki yanzu dole irin wannan maganin zai
rinka sha,amma ni zan taimaka miki.."

"To nagode dr, nagode madalla.."

"A'a ai ba wani abu bane, zan baki card wanda yake dauke da address din gidana dake
cikin G. R. A. Governor road.." Yakarashe maganar yana lasar lips dinshi,

Sai lokacin Hafsat ta fahimci inda maganar tashi ta nufa,

"Dr aini ba yar iska bace sannan banyi kamada matan banza ba wadanda zasu iya cin
amanar mazajensu ba..."

Hannu ya daga mata,

"Amma shi mijin naki meyasa yaci taki amanar yaje maza suka bata masa rayuwa? Shifa
da maza yan uwanshi ma yarinka alaka,Bari infada miki gaskiya kidaina wahalar da
kanki akan mijunki domin situation din da yake ciki yanzu bazai taba kallonki a
matsayin mace ba bare har ya iya kusantarki saboda lalurar dake tare dashi, gaba
daya bayanshi yakusa lalacewa domin sperm din dake shiga ciki babu wurinda zai fice
shine sai yarinka taruwa yana taruwa har idan yakai wani stage sai wurin ya lalace
har tsutsotsi su rinka fita ta wurin dan haka kidaina wahalar da kanki abanza, ni
zan rinka bashi magani kyauta duk da tsadarshi mutukar kin amince da bukatata domin
nan asibiti nane wadannan magungunan kuma tun daga India nake iyo ordersu ake kawo
min.....!"

Sassauta muryarshi yayi cikeda yaudara da son janyo hankalinta,

"Kinga maimakon ki zauna kina yimasa wahala bayan bazai iya amfana miki komai ba
gara kisamu wanda zai rinka debe miki kewa duk lokacin da kika so...!.

*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*38*

***Kallon mamaki Hafsat ke yiwa khadija lokacin da ta fita kofar dakin domin
ganin ko wacece ke sallama ganin khadijan yasata shiga cikin mamaki domin bata taba
ganinta ba,

Dan gyara tsayuwarta kadan khadija tayi bayan ta zubawa Hafsat idanuwanta tana
yimata kallon kurulla domin tun daga kafarta tafara kallonta har zuwa samanta,

"Baiwar Allah wakike nema?" Hafsat ta katse shirun nasu ta hanyar tambayar khadija,

"Ammm yusleem nagani shine nabiyoshi saboda ina son yin magana dashi.."

Shiru Hafsat tayi kafin tasake yin magana,

"Ok to amma daga ina kike kuma wa zance mishi?"

"Anan garin nake, kice mishi khadija mu'az ce.."

"To ina zuwa.." Hafsat tace tareda juyawa takoma cikin dakin,

Bin dukkan lungu da sako na gidan khadija keyi da kallo tana mamakin yanda akayi
har yusleem yake iya yin rayuwa acikin wannan gidan na haya wanda babu komai na
alatun more rayuwa aciki,

Acan cikin daki kuwa koda Hafsat takoma wurin yusleem zama tayi agefenshi gabanta
yana faduwa,

"Yaya yusleem watace tazo nemanka wai sunanta khadija.."

Dan damm taga yayi kafin ya yunkura yatashi zaune,

"Yanaji kayi shiru ko akwai matsala ne? Ni tsoro nakeji kar asirinmu ya tonu,kar
taje tafadawa mami.."

"Babu abinda zai faru insha Allah, ki shigo da ita"

Tashi Hafsat tayi ta sake lekawa inda khadija ke tsaye tana faman touching din
phone dinta,

"Yawwa bismillah shigo.."

Tare suka shiga cikin dakin, ganin yanda dakin yake awani takure yasa khadija sake
shiga cikin tsananin mamaki,

"Yusleem... Dagaske kaine anan? Me yafaru? Lafiya kuwa? Me yakawoka rayuwa a irin
wannan gidan?"

Duk wadannan tambayoyin khadija ta jero sune cikeda mamaki lokacin da take yunkurin
zama akasan carpet din dake dan shimfide agaban katifarsu,

"Yusleem wai dagaske kai dinne kodai idanuwana ne kemin gizo.."

"Khadija nine nan.." Yusleem yabata amsa yana kallonta,

Jijjiga kai tayi tagyara zamanta,

"To meya faru dakai har kazo nan? Saboda ni ban san wani abu yafaru dakaiba domin
ko jiya agida da yamma muna tareda mami agidanmu.."

"Khadija wata matsala aka samu babba wadda ta tilasta min dawowa nan.."
"Amma dai mami bata saniba ko?"

"Ehh to gaskiya ban bari tasani ba har yanzun nan danake yimiki bayani saboda wani
dalili.."

"To amma yusleem meyasa zakazo nan wurin kazauna? Irin wannan rayuwar sam bata dace
dakai ba, dubi yanda duk kabi kasauya ka dawo wani kala..."

Murmushi yusleem yayi,

"Khadija kenan kin san dai ai komai yana faruwa ne da dalili, kawai dai ki kalli
wannan a matsayin wata kaddara wacce take tawa kuma dole saita sameni.."

Jijjiga kai tayi,

"Hakane, to Allah ya rufa asiri.. Sannan insha Allah nayi alkawari zan baka gudun
mawa dari bisa dari acikin rayuwarka.."

"Nagode khadija amma ni babu wata gudun mawa da nake nema daga gareki.."

Jin abinda yace yasa Hafsat saurin kallonshi, tashi khadija tayi tai musu sallama
tafita, har kofar daki hafsat ta rakata bayan taga fitarta ne takoma wurin yusleem,

"Yaya yusleem gaskiya banji dadin abinda kafada ba, ai ni sai nake ganin ko babu
komai wanda ya nuna yanayi dakai yafi..."

Bai barta takarasa ba yajata jikinshi ya rufe mata baki da hannunshi yana kallonta,

"Nanah akwai dalilin dayasa kikaji nafadi haka, wallahi ba dan Allah khadija zata
taimaka mana ba, akwai wata manufa atare da ita.."

"Taya kasani?"

"Saboda khadija matatace ada, saida muka rabuda ita sannan na aureki.."

"To ai ba lallai bane abinda kake zargi yazama gaskiya ba, nidai dan Allah idan
tasake dawowa next time karka yi mata irin wannan.."

Kura mata ido yayi saboda jin abinda tafada, lallabashi takoma yi har ya amince,

Washe gari da safe misalin karfe 11 saiga khadija tasake dawowa gidan lokacin
hafsat na gyarawa yusleem farcenshi, da fara'a Hafsat ta karbeta suka gaisa, fuskar
yusleem kuwa babu yabo babu fallasa,

Cigaba da yimishi gyaran farcen Hafsat tayi yayinda ita kuma khadija ta zauna tana
kallonsu aranta tana tunanin yanda akayi har Hafsat tasamu irin wannan damar awurin
yusleem domin abisa dukkan alamu tasamu fada mai girman gaske awurinshi sabanin su
da ko kallo basu isheshi ba lokacin da yana tareda su,

Ajiyar zuciya ta dan sauke sannan ta kalli yusleem wanda idonshi ke kan hannayensu
shida Hafsat wanda ta rike nashi cikin nata acikin zuciyar shi kuwa dan murmushi
yakeyi saboda ganin yanda kalolin fatarsu guda biyu ta hadu tashi fari tata kuma
bak'a,

"Uhmm yusleem dama cewa nayi bari nabiyo na dubaku saboda naga kamar baka da lafiya
ko? Domin duk ka sauya"

Kafin yayi magana Hafsat ta amsa,


"Ehh wallahi zazzabi yake fama dashi amma hakanma da dan sauki.."

"Ayya Allah yakara bashi lafiya.."

"Amin.."

Kallo na tsanaki khadija ta rinka bin dakin dashi aranta tana mamakin tayadda akayi
wai yusleem yadawo haka duk da cewar jiya yayi mata bayani amma gaskiya har yanzu
bata gamsu da bayanin dayayi mata ba duba da irin tarin dukiyarshi da matsayinshi
ada,

Mikewa tayi tsaye tana murmushi,

"Yawwa bari naje na tafi sai wani lokacin idan nadawo.."

Cikeda fara'a Hafsat ta kalleta,

"Zaki tafi? To mun gode madalla Allah yasaka da alkhairi.."

"Nagode khadija, sai anjima" yusleem ya fada yana damke hannun hafsat acikin nashi,
fita khadija tayi tana fita yusleem yaja hafsat jikinshi yana murmushi, lakuce mata
hanci yayi,

"Yau fa banga kinci abinci ba?"

"Kaima ai bakaci ba, gara ma ni amma kai yaushe rabonka da abinci"

Murmushi yayi ya matse kanta akan kirjinshi tayanda har tana iya jiyo bugun
zuciyarshi,

"Hafsat wani tunani nafara gameda ke da rayuwarki..., ni ina ganin kodai in sawwake
miki ne kitafi gidanku kije kici gaba da rayuwarki cikin kwanciyar hankali saboda
nasan na takura rayuwarki da yawa ba kadanba..."

Jin abinda yafada yasa gabanta mummunan faduwa bayan zuciyarta ta harba da karfi,
dagowa tayi ta kalleshi idanuwanshi sun danyi ja kadan, ganin ta kura mishi ido
abinda bata taba yiba yasashi sake mayar da kanta ya kwantar bisa kirjinshi,

Daga shi har ita shiru sukayi babu wanda ya iya cewa uffan domin kowa da abinda
yake sakawa acikin ransa.

Abangaren khadija kuwa bayan tafita daga wurinsu yusleem tafi minti goma sha
biyar tana tsaye ajikin motarta takasa shiga, tunani take anya kuwa yadace tabar
yusleem acikin wannan halin?

Girgiza kai tayi,

"Am sorry yusleem dan gaskiya yazama dole nasan abinyi..."

Shiga motarta tayi tai mata key tafita daga unguwar, fitarta keda wuya bata zame
ako inaba sai gidan mami mahaifiyar yusleem, cikin sa'a kuma mamin na gida bata
fita ko inaba,

Lokacin da khadija ta shiga kawataccen falon na mami mamin na cikin bedroom dinta
tana shiryawa kamar me shirin zuwa unguwa, jin sallamar khadija yasata fitowa falo,

Kallo khadija ta dan bita dashi, tana sanye cikin wani swiss les dan gaske golden
colour sannan tasaka sarka da earrings da warwaro duk golden gashi tasha jan lalle
kai idan kaganta bazaka taba cewa ta ajiye samarin yara ba,zama mamin tayi tana
murmushi saboda ganin khadija......

_Fans kuyi hakuri da wannan please,ina cikin hidima ne..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*Sakon fatan alkhairi gareku members na haske writers asso fans, this page is
for u...*

*39*

***Gaisar da mami khadija tayi bayan sun gaisa ne khadijan tafara tunanin
ta inda ya kamata ta bullowa da mami maganar yusleem, zuwa can dai ta dan nisa
tace,

"Mami nikuwa yusleem yana kasar nan..?"

Murmushi mami tayi,

"Yusleem baya nan khadija, nikaina rabon da inyi magana dashi kota wayane anjima,
daga yin tafiya shikenan shine har yau..."

Jijjiga kai khadija tayi,

"Ai kuwa Mami naga yusleem, yana nan agarin nan babu inda yaje domin naganshi da
idona kuma har magana munyi dashi jiya da yau, yanzu ma daga wurinshi nataho nan.."

Mamakine ya bayyana akan fuskar mami,

"A ina kika ganshi khadija? Yaushe yadawo..?"


"Ai dama mami babu inda yusleem yaje yana cikin garin nan kawai dai wurin zama ya
sauya, agaskiya mami na tausayawa halin da naga yusleem aciki.."

"Meya sameshi khadija? Dan Allah fada min idan wani abune ya sameshi" mami tayi
maganar cikin rudewa,

"Ba wani abun tada hankali bane mami, kawai dai muje inkaiki gidan da yake ki
ganshi da idonki.."

Da hanzari mami ta tashi tashiga bedroom dinta ta dauko mayafi ta fito jikinta har
wani yar tsuma yake saboda taraddadin halin da zataje taga yusleem aciki,

Acikin motar khadija suka fita, ganin irin yanayin unguwar da khadija ke kokarin
shigar dasu yasanya mami fara kokwanton anya kuwa khadija yusleem dinta tagani
kuwa? Kasa hakuri mamin tayi har saida tayi magana,

"Khadija anya kuwa idanuwanki sun gane miki gaskiya?, me yusleem zaizo yayi anan?
Sannan tayaya za ace waima yadawo kasar nan amma ni a matsayina ta mahaifiyarshi
inkasa sani..."

"Mami ai magana kam takare tunda gamu munzo kofar gidan da yusleem ke ciki, zaki
ganewa idonki komai"

Shiru kawai mami tayi amma bawai dan ta yarda da khadija bane a'a sai dan dai kawai
ba abokiyar yin mahawararta bace shiyasa bazata yita jayayya da itaba,

Bude kofa kowaccensu tayi ta fito daga cikin motar, nan suka tasamma cikin gidan
gadan gadan bayan khadija tarufe motarta,

Wani mamakin ne yasake lullube mami lokacin da suka shiga cikin gidan saboda yanda
taga tsarin gidan yake dakuna ratata banda kaca kacan da gidan yayi sannan ga mata
nan atsakar gidan kowacce tana harkar gabanta, watama ko riga babu saiko daurin
kirji,

Kofar dakin da su yusleem suke khadija ta karasa dasu suka tsaya khadija tafara
doka sallama,

Cikin barcin da ya daukesu sama sama kunnuwansu suka fara amsar sallamar da khadija
keyi,

Hafsat ce ta dan bude idonta gamida sake kankame yusleem wanda take kwance
ajikinshi,

Jin ansake kwada sallamar da karfi yasanyata tashi tana jan dan karamin tsaki, shi
kanshi yusleem din shima baiji dadin wannan katse mishi baccin da akayi ba, juyi
yayi yasake gyara kwanciyarshi ita kuma Hafsat ta dauki dan kwalinta tafita,

Tana yaye labulen tayi arba da mami da khadija wadanda ke tsaye akofar dakin,
tamkar acikin mafarki haka Hafsat tagani, take kuma gabanta yashiga faduwa,

Tunda mami taga Hafsat tasan abinda khadija tabata labari gaskiyane dan haka yanzu
bata da sauran kokwanto kuma,

Cikin rawar baki Hafsat tace,

"Mami..."

"Na'am Hafsat, ashe dagaske kuna nan kuna rayuwa batare da sanina ba..?" Mami tayi
maganar cikin sanyin jiki,

"Mami shigo daga ciki"

Shiga cikin dakin mami tayi bayan tacire takalminta, cikeda mamaki take bin kowacce
kusurwa ta cikin dakin da kallo wanda take ganinshi kamar dakin girki irin na
kauye,

Har lokacin da suka shigo yusleem baisan cewar mami bace domin baccinshi yakeyi
hankali kwance amma jin maganarta yasashi juyowa da sauri bayan yatashi,kallon
mamin yakeyi fuskarsa dauke da mamaki gamida al'ajabi,

"Mamie..." Yakira sunanta yana mutsutstsuke ido,

"Yusleem wacce zuciyarce tabaka wannan mummunar shawarar har kazo nan kake rayuwa
batare da sanina ba? Meyasa zakayi min karya?"

Wadannan sune tambayoyin da mami ta jefo masa batare da ta amsa kiran da yayi mata
ba, fuskarta kunshe da fushi da bacin rai take kallonshi.......

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*40*

***Rasa abinda zaice yusleem yayi illa kallon mamin da yakeyi wadda itama
shi take kallo kafin daga bisani ta mayar da kallonta kan Hafsat wacce ta sunkuyar
da kanta kasa,

Dakin nasu mami takoma tafara kallo kusurwa bayan kusurwa,


"Mami dan Allah kiyi hakuri wallahi akwai kwakkwaran dalilin da yasa kikaga hakan
tafaru, zamuyi miki bayanin komai...." Hafsat tayi karfin halin yin magana,

Mami bata bawa Hafsat amsar maganarta ba illa sake balbale yusleem da fada da tayi,

"Ka dauko yarinyar mutane kazo ka ajiyeta anan kana wahalar da ita, dubi yanda
takoma, kalli kaima yanda ka zama duk kabi ka rame kayi baki daga gani kana cikin
mawuyacin hali, to da ace khadija bata ganku taje ta fada minba da sai yaushe zaku
nemeni? Da sai ka kashe musu 'ya sannan zakaje min da mummunan labari? Yayi kyau"

Mikewa mami tayi ta kalli khadija wacce ke zaune ta sunkuyar da kai tana sauraren
duk abubuwan dake faruwa,

"Tashi mu tafi khadija"

Kallon yusleem mami tayi,

"Kai kuma na baka nanda mintuna 20 ku tattaro duk kayanku kuzo gida ku sameni, idan
kuka wuce haka to ina mai tabbatar maka ranka sai ya baci.."

Fita mami tayi daga cikin dakin khadija ta rufa mata baya,

Kallon yusleem Hafsat tayi bayan mami tafita,

"Yaya yusleem katashi mu bita, idan munje gidan sai muyi mata bayani atsanake kaga
kamar fa tayi fushi..."

Dafe kanshi yayi wanda ke yimasa wani irin ciwo,

"Kibari kawai muci gaba da zama anan idan ta huce sai muje mu bata hakuri"

Girgiza kai tayi bayan ta rike hannunshi cikin nata,

"A'a yaya yusleem, mubi umarninta mu tattara kayanmu muje, bai kamata muyi watsi da
maganarta ba.."

Tashi tayi batare da tajira abinda zaiceba ta shiga tattara kaya dama kuma kayan ba
wadansu masu yawa bane, cikin toilet ta shiga ta kwaso inner wears dinsu dake
shanye tazo ta zuba acikin trolley, har lokacin yusleem na zaune baiko motsa ba,

Kayan da tasan bazai yiyu su tafi dasu yanzuba ta tattara wuri daya ta adana sannan
tafita daga dakin taje dakin maman amir tayi mata sallama, kasancewar sunyi sabo
maman amir harda kuka, ita kanta Hafsat din da hawaye tadawo cikin dakin,

Tashi yayi ya rungumota jikinshi yana murmushi,

"Menene na kukan kamar ance bazaku sake haduwa ba..., sorry.."

Har lokacin hawayen basu bar zuba a idonta ba,

"Ya isa haka, kiyi shiru dan Allah"

Dakyar ta iya tsayar da hawayen yusleem ya dauki trolley dinsu suka fita acikin
ranshi yana mamakin mata su babu wuya yanzun nan zasuyi maka kuka,

Har waje mutanen gidan suka rakasu duk da ba wai wani zumunci mai zurfi sukeyi ba,

Adaidaita sahu suka shiga yakaisu har gidan mami,


Gidan yana nan kamar da babu abinda ya sauya sannan ga ma'aikata nan kowa yana
aikinsa kamar yanda suka saba, ganin su yusleem yasa masu gadin gidan saurin amsar
kayan dake hannunsu suka shigar musu dashi ciki,kowa sai sannu da zuwa yake yiwa
yusleem domin duk atunaninsu daga doguwar tafiya yadawo,

Acikin falo suka iske mami tana zaune tana shan ruwan lipton sannan ga soyayyen
chips with kidney sos tana dan tsakura kadan kadan tana ci da dukkan alamu sai
yanzu take yin breakfast,

Jin sallamarsu yasanyata dagowa ta kallesu bayan ta amsa, akasa Hafsat ta zauna
yayinda yusleem yazauna akujerar dake kusa da ta mami,

"Hafsa ga abinci can maza tashi kije kici kinji..."

"Wallahi mami munci abinci sai dai idan anjima.."

Shiru mamin tayi batace komai ba taci gaba da kurbar ruwan tea dinta, suna nan
zaune shiru babu wanda yasake magana har mami ta kammala cin abincin,

Sunkuyar da kai Hafsat tayi tasoma bawa mami hakuri,

"Mami dan Allah kiyi hakuri da abinda yafaru, wallahi ba laifinsa bane laifina ne
domin nice nabashi wannan shawarar kuma nima nayi hakanne dan gudun kada mu tayar
miki da hankali, amma dan Allah kiyi hakuri.."

Ajiyar zuciya mami tayi ta kalli yusleem sannan ta kalli Hafsat,

"To shikenan Hafsat nahakura, amma meyake faruwa? Nasan dai duk yanda akayi akwai
abinda ke faruwa daku"

"Ehh mami da akwai, bashin banki yaya yusleem yaci sukuma kin san dokarsu idan baka
biyasu ba sai sun sayar da komai naka, to shima yaya yusleem din hakance tafaru
kuma lokacin nasan idan kikaji hankalinki tashi zaiyi shiyasa nace mubari tukunna
sai zuwa wani lokaci sai mu fada miki..."

Tafa hannuwa mami tashiga yi tana salati,

"To garin yaya?"

Kallon yusleem tayi,

"Kai agarin yaya kaciyo bashin banki batare da sanina ba?"

"Mami tsautsayi da kaddara, saboda dama tun asali da wannan bashin nasu nayi
arziki, komai da kika sani nasune, nikuma nayi hakanne dan incika burinki inzama
mai wadata kamar yadda kike muradi..."

Katse shi mami tayi cikin fada tace,

"Ungo nan.." Dakuwa tayi masa sannan ta dora da cewa,

"Shikenan kuma dan ina son kayi arziki sai kaje ka aikata ba daidai ba? Ai ni bance
kayi kudi kota halin kaka ba, haba yusleem meyasa zakabi shawarar zuciya? Ko dan
gaba karka sake aikata makamancin wannan, yanzu da ace sun kamaka sunje sun daureka
me gari yawaya?"

Dan zamewa yayi ya jingina bayanshi da jikin kujerar ya lumshe idanuwansa,

Kallon Hafsat mami tayi,


"Bashida lafiya ko?"

"Ehh mami amma da sauki, matsalar dai baya iya cin abinci"

Shiru mami tayi ta danyi tagumi,

"Hakika wannan wata jarrabawa ce daga Allah, domin ni dinma duk kudaden dake cikin
account dina na turawa yan makaranta domin sun kusa dawowa, gashi na sissiyo kayan
abinci wadanda zasuyi mana 1 month,ma'aikatan gidan nan ma wallahi wannan watan ko
albashi ban biyasu ba nace suyi hakuri sai yusleem yadawo.."

"To ai babu komai mami duk wannan ba wani abu bane Allah zai bamu mafita" inji
Hafsat,

"To hafsa rashin lafiyar tashifa? Ni duk ita tafi daga min hankali"

"Mami babu komai insha Allah zai samu lafiya, gobe zamu sake komawa asibitin ma ayi
masa test..."

"To wai menene ke damunsa?" Mamin ta tambaya cikin damuwa,

"Mami harda ulcer dai saboda baya cin abinci wallahi"

"To Allah yabashi lafiya, goben sai muje asibitin mugani"

Shi dai yusleem yana jinsu baiyi magana ba da zaman kujerar ya isheshi ma dakin
surayya yashiga wanda yake makotaka da na mami yaje ya kwanta akan gadonta,

Ita kuma mami afalo duk tabi ta damu sai jajanta rashin lafiyar yusleem takeyi,
Hafsat dince ma mai karfin halin kwantarwa da mamin hankali tana cewa babu komai,

Saida lokacin salla yayi sannan Hafsat ta dauki kayanta ta nufi bedroom din
surayya, akwance ta samu yusleem amma ba bacci yakeyi ba,

"Yaya yusleem tashi kayi salla..."

Tashi yayi yana kallonta,

"Hafsat meyasa baki fadawa mami gaskiyar abinda yafaru ba? Saboda ko dan nan gaba
ya kamata ace tasani"

Zama tayi kusa dashi,

"A'a yaya yusleem fadar bata da alfanu hakan dai da akayi shine daidai"

"Shikenan.." Abinda yace kenan yatashi zai fita, bin bayanshi tayi zuwa falo ta
dauki trolley din kayanshi tabishi, part dinsu Abdul ya bude yashiga, bedrooms biyu
ne aciki sai falo domin suma samarin kowa da dakinshi, dakin khalifa yashiga tana
biye dashi, juyawa yayi ya kalleta,

"Wai kina nufin ke adakin surayya zaki zauna?"

"Ehh mana"

Murmushi yayi ya karbi trolley din hannunta,

"Ashe dama karya kike da kikace bazaki iya kwana babu niba.."
Murmushi ne ya kwace mata tajuya zata fice yayi hanzarin rikota,

"Debo kayanki kidawo nan"

"Tohm" ta amsa amma bawai aikatawar zatayi ba domin tana jin nauyin mami ba
kadanba,

Sakinta yayi tafita shikuma ya nufi cikin toilet.

Koda takoma part din mami salla tayi tafito falo nan ta hango kuku yana shirya
lunch akan table, fitowar mami ne ya katse mata tunaninta,

Kan table suka hau, fried spaghetti da salad kukun yadafa sai kunun shinkafa, suna
ci suna hira har suka gama, kunun Hafsat ta dauka tatafi kaiwa yusleem ko zai iya
sha,

Akan carpet din salla ta sameshi yana tura sako ta email dinshi ackin laptop,

"Yaya yusleem ga kunu.."

Dagowa yayi ya karba ya dan kurba, zama tayi agefen gado, babu laifi yadan sha
kunun ganin haka yasa taji dadi sosai, maganinshi ta dauko mishi ya karba ya hadiya
daga nan tatashi tafita.

Wayarta ta Kunna bayan ta koma, ko minti biyu ba ayiba Ummi takirata, cikeda zumudi
ta dauka suka gaisa nan take fadawa ummin cewar yau suka dawo amma suna gidan mami,

Suna gama waya da ummin kiran Amina yashigo, ita dinma korafin bata samunta awaya
tayita yimata gashi ta jima da haihuwa mijinta yanata zuwa gidan domin yafada mata
amma baya samunsu, Allah yaraya Hafsat tayi mata tace sunyi tafiya ne amma tunda
sun dawo tana nan zuwa,

Komawa wurin mami tayi bayan sunyi sallama da Amina, nan take fadawa mami yusleem
yadan sha kunun da takai masa tunda hakane zata rinka dama masa kullum.

Misalin karfe 8:30 nadare suna zaune afalo suna kallon tashar zee world itada mami
sai gashi yashigo da cup din kunun data kaimasa, zama yayi yasoma kurbar kunun,
Hafsat da mamine ke dan yin hira lokaci zuwa lokaci yana zaune yana jinsu,

Yana kallo hafsat ta shige daki bayan tayi musu saida safe, itama mami ba ajima ba
tashiga nata dakin suka barshi afalo shi kadai, sai wurin 11 yakashe tv da sauran
kayan wutar dake cikin falon, dakin surayya wadda Hafsat ke ciki ya shiga ya maida
kofa ya rufe, gani yayi harta jima da yin bacci, bargon yabude yashiga yayi
kwanciyarshi tareda mannuwa ajikinta.

Said a asubah sannan Hafsat tasan yana cikin dakin, tashi tayi tashiga bathroom
tayi alwala tafito, ahankali tafara tashinsa saboda bata son mami ta jiyo,

Tashi yayi yana lullumshe ido alamun baccin bai isheshi ba,

"Yaya yusleem katafi saida safe..."

Hammar da yafara ya karasa sannan ya kalleta,

"Ina zan tafi?"

"Masaukinka..."

Baice komai ba yasauka daga kan gadon yanufi toilet, lokacin da yafito har ta idar
da raka'atanul fijr tana kokarin tada ikamar sallar asubah,

Tashi yayi yakoma kan gadon ya kwanta bayan ya idar da sallar, yana kokarin lulluba
da bargo Hafsat ta bazamo tazo tana masa magana kasa kasa,

"Dan Allah yaya yusleem katafi.."

"Ina?"

"Dakinka mana, bana son mami tazo taganka"

Kafin yabata amsa suka fara jiyo knocking abakin kofa da sauri Hafsat ta diro,
maganar mami tajiyo tana cewa,

"Hafsat, Hafsat kitashi asubah tayi.."

"Na'am mami"

"Au ko kin tashi ma?"

"Ehh mami"

"To shikenan.."

Daga nan tajiyo alamun tafiyar mami,hannu ya mika mata yana daga kwance,kafada ta
makale ta kwabe fuska, shi dinma hakan yayi kamar yadda tayi,

"Zo dan Allah"

Kan gadon ta hau ta mika masa nata hannun, kama hannun nata yayi yajata ya kwantar
da ita yaja musu bargo.

_Fatan alkhairi ga Hajjaju, Chuchu, Maman sultan, pheey, Maman humy, Anty sis,
Dshanty, Reane_Gh,meela adeel,meernah parrot,khadija sadeeq,Billy s fari, Billy s
jega, ummu abrar, anty Baraka, Maman mujahid da duk wadanda ban ambata ba, wannan
shafin nakune kyauta domin jin dadinku._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*
_DEDICATED TO MISS XOXO_

*Yau shafin nakune kawayena, Lubabatu mai tafsir, fiddausi sodangi,phertymah


xarah Maman khadija, cwt Kausar Luv, Teemah Cool,Khaleesat Haidar, Hafsat bunza,
Zee Rumah,Maman Shakur Benaxir oamar,Billy Galadanchi, ina yimuku fatan alkhairi
aduk inda kuke...*

*41*

_Ina cikiyar RIRI TURAKI marubuciyar halal dina, idan sakona ya riskeki ni Ummi
Shatu ina nemanki urgently._

***Misalin karfe 9 Hafsat tafarka daga bacci, juyawa tayi ta kalli yusleem
wanda ke rike da hannunta yana kanannade da ita, dakyar ta iya tureshi daga jikinta
ta tashi,

Wanka tashiga tayi tafito ta shirya agurguje, falo ta leka tagani ko mami tafito
domin sam bata so mamin ta fahimci cewar yusleem awurinta ya kwana, ganin mami bata
fito ba sai masu aiki dake faman mopping din falon yasata sakin ajiyar zuciya,

Juyawa tayi tasake komawa cikin dakin, tashinsa tasoma yi tana dan bubbuga gefen
pillow din da kanshi ke kai,

"Yaya yusleem...,yaya yusleem katashi"

Ido guda daya ya bude ya kalleta,

"Me zan yi miki?"

"Safiya fa tajima dayi dan Allah katashi"

Mayar da idonshi yayi ya rufe yajuya mata baya yasake jan bargo ya lulluba, tashi
tayi tafita, kuku ta hango yana jera musu breakfast akan dining,

Zama tayi acikin falon tama rasa me zatayi, ajiyar zuciya tayi aranta tana fadin
dama matsalar gidan masu kudi kenan ko katashi da wuri karasa abinda zakayi,

Tana nan zaune tana kallon shirin gari yawaye a tashar arewa 24 har mami tafito,
kamar kullum mamin tasha kwalliya kamar me shirin zuwa gidan biki,

Sauka kasa tayi tagaida mami, cikin fara'a da sakin fuska mami ta amsa domin tana
jin son Hafsat tamkar na yar da ta haifa,

Kan dining suka dunguma suka fara karyawa,suna daf da gamawa mami ta kalleta tace,

"Shi wannan sarkin baccin bai tashi bane? Ai da yatashi saboda maganar zuwa
asibitin ko"

"Ehh gaskiya kam, bari nagama sai inje in tasoshi.."

Kafin Hafsat ta rufe baki sai gashi ya bude kofa yafito yana yamutsa fuska,
sunkuyar da kai Hafsat tayi kamar ruwa ya cinyeta, mami kuwa dubanshi tayi ta kawar
da kai,

"Ka manta da maganar zuwa asibitinne kaki tashi da wuri?"

"Wallahi ina sane mami, ban manta ba" yakarasa maganar yana kallon Hafsat ta gefen
ido wadda yasan ba haka tasoba,

"To ai sai kaje kashirya.."

Wucewa yayi yafita zuwa part din su khalifa, wanka yayi yafito ya zauna domin shafa
mai, yana zama Hafsat tashigo hannunta rikeda jug dan madaidaici,

"Ga kunun..."

"Babu gaisuwa?"

Yafada lokacin da yake shafa man a hannayenshi,

"Ina kwana?"

"Ni bazan amsa ba, zo nan.."

Dan sake matsawa tayi tana kallonsa,

"Gani.."

"Kinsa Mamie tana yimin fada ko, bayan kuma kece kikayi sanadiyyar makarata saboda
dumin jikinki da naji"

Juyawa tayi zata fita daga dakin fuskarta dauke da murmushi,

"Zo nan, Allah karki fita"

Dawowa tayi ta tsaya, tana nan tsaye har yagama shiryawa ya dauki kayanshi yasa,

Kunun da ta Kawo mishi yasha sannan suka fita domin Tafiya asibiti,

Afalo suka iske mami cikin shiri nan suka dunguma domin tafiya amma kuma suna
fitowa compound din gidan sai ga motar khadija ta kunno kai kuma tareda
mahaifiyarta suke wannan dalilinne yasa mami fasa zuwa asibitin tace da yusleem da
Hafsat kawai suje driver yakaisu ita kuma takoma ciki itada hajiya fa'iza da
khadija,

Ganin irin gaisuwar da yusleem sukayi shida khadija yasa Hafsat yimasa magana domin
daurewa khadija fuska taga yakeyi bayan kuma ita bataga laifinta ba, ganin baya son
maganar yasata yin shiru ta kyaleshi.

Lokacin da sukaje asibitin Hafsat kin shiga office din dr sufyan tayi tai zamanta
awaje sai yusleem ne yashiga shi kadai, ya dan jima aciki kafin yafito,

"Yaya yusleem ya kukayi?"

"Yace nanda 4 days nakara dawowa lokacin result din taste din da yayi min yafito.."

"To Allah dai ya jiyar damu alkhairi"

"Amin, muje mu tafi gida tunda babu abinda yayi saura, Dr din yana tambayarki wai
yau banzo da matata ba nace tare ai muke kina waje wai ai dama yasan bazaki barni
nazo ni daya ba..."
Dan murmushin yake tayi batace komai ba amma acikin ranta fadi take "Dan iskan Dr",

Lokacin da suka koma gida sai mami ita kadai domin su khadija sun tafi, ganin sun
dawo da wuri mami tace Hafsat ta shirya taje driver yakaita gidansu tagaisa da
iyayenta,

Garin dakakkiyar busasshiyar kubewa da kuka da daddawa wanda Maman khadija ta Kawo
wa mami su mamin tabawa Hafsat tace takaiwa umminta tsaraba,

Yusleem yana kwance akan kujera mami na kujerar kusa dashi Hafsat din tafito zata
tafi,

"Mami idan nadawo zan biya ta gidan amina kawata, haihuwa tayi shine zanje inga
babyn.."

"To sai kin dawo, Allah ya raya.. Ki gaida hajiya kubran"

"To mami zataji"

Fita tayi nan yusleem yatashi yabita, tana daf da fita daga cikin kitchen yayi
saurin rikota,

"Mami zaki tambaya unguwa saboda itace take aurenki ko? To gidanku kadai na amince
kije daga nan karkije ko ina"

Juyawa yayi zai koma falo tayi saurin rikoshi,

"Dan Allah kayi hakuri yaya yusleem.. Kaji"

Shiru yayi mata ita kuma taci gaba da yimasa magiya, dakyar ya amince yace taje.

Acikin kitchen ta iske Ummi lokacin dataje gidan, ba karamin dadin ganinta hajiya
kubra tajiba nan suka baje suka fara hira irinta uwa da 'ya da haka har Alhaji
sa'id yazo ya samesu yadawo daga buga bugarsa domin shima ya haduda jarrabawa
irinta rayuwa sai dai ita Hafsat bata saniba har saida ummi tayi mata bayanin
abubuwan da suka faru na iftila'in da ya afkawa alhaji sa'id din bayan ya sayar da
kadarorinsa ya tura asiyo masa kayayyaki amma har yau kayan basu fitoba gashi
saboda rashin kudi kwangilar ma ba samuwa takeyi ba dan dai kawai yanada amini ne
mai fada aji,

Kuka Hafsat tayi ba kadanba dalilin jin wannan labarin da hajiya kubra ta bata amma
kuma tasan jarrabawa ce daga Allah shiyasa ma bata daga hankalinta ba,

Dayake sun dade basu hadu da umminba yasa Hafsat takasa tafiya da wuri har saida
aka kira sallar magrib, bayan tayi sallane tatafi lokacin driver yazo daukarta, ko
gidan aminan ma bataje ba gida ta wuce direct,

Mami kadai ta tarar afalo tana waya da surayya nan ta zauna har mami ta kammala
wayar itama tabata suka gaisa domin rabonsu da juna tun lokacin da surayyan takoma
school,

"Hafsa kin dawo? Ya kika baro mutanen gidan?" Mami ta tambaya tana kokarin ajiye
wayarta,

"Lafiya lau mami, suna nan lafiya, Ummi tana gaidaki tace ayi miki godiya..."

"Babu komai wallahi, kayan ma nawa suke.."


Zama sukayi dan shiru suna kallon tv zuwa can Hafsat ta mike ta nufi bedroom, tana
shiga ta iske yusleem akwance,

"Lafiya kuwa yaya yusleem?" Ta tambaya,

"Wallahi zazzabi ke damuna hafsa"

Ahanzarce takarasa kusa dashi jin jikinsa zafi zauuu tayi gashi yana dafe da
cikinsa wanda ke ta faman murda masa,sannu ta shiga yimasa yana amsawa dakyar, zuwa
can taji ya kamo hannunta ya dora akan cikin nasa,

Jikinta rawa yafara saboda ganin yanda yusleem yake yin murkususu gashi bata son
taje tafadawa mami hankalinta yatashi,

Ruwan sanyi ta dauko tasoma shafa masa acikin nashi nan yaji ciwon yafara lafa masa
ahaka har bacci ya daukeshi, ganin yasamu bacci yasa ta fita wurin mami wadda take
zaune akan abin salla ta idar da sallar isha tana jan carbi,

"Hafsa ga tuwo can, wallahi yau shi naji ina sha'awa shine nace kuku yayi.."

Murmushin yake Hafsat tayi ta girgiza kai,

"Kafin nataho ma agidan Ummi saida naci abinci,wallahi na koshi.."

Wuri tasamu ta zauna amma lokaci zuwa lokaci tana dan shiga bedroom din taduba
yusleem sai dai har 10 tayi bai tashiba, har sukayi sallama da mami tashiga dakinta
itama ta shiga daki yusleem bacci yake,

Akusa dashi ta kwanta tana kallonshi yana rike da cikinshi, sai wurin 11 sannan
yatashi yayi sallar magrib da isha wadanda ke kanshi domin bai samu damar yiba,

Kalau yayi sallar ya idar tana zaune tana kallonshi yana idarwa kuma yace sai ta
dama masa kunu yasha yunwa yakeji, tare suka fita zuwa kitchen din ta tafasa ruwa
ta dama masa kunun suka koma daki, saida yagama sha sannan suka kwanta, tana ji
yafara tsokanarta kamar bashi bane dazu yake murkususu kamar zai mutuba,

Bata San lokacin da yagama tsokanar tataba domin bacci tayi tabarshi, can tsakiyar
dare kuma kamar acikin mafarki take jin kakarin amai nan tatashi taganshi kwance
yana juyi yana rikeda cikinsa, ruwan sanyi ta debo tafara shafa masa amma yanzu ji
yake kamar ruwan zafi tafasasshe take Shafa masa, kunun da yasha kuwa saida yayi
amansa gaba daya,rikeshi tayi nan ya kuwa kankameta kamar zai koma cikin cikinta
daga shi har ita babu wanda yasake runtsawa har asuba tayi ita dai agaba tasashi
tana hawaye,

Ganin abin yayi yawa gashi yana yin wani irin amai kore kore yellow yellow yasa
hafsa zuwa ta sanarwa da mami lokacin karfe 5:30,

Driver mami tayiwa waya kasancewar a B/Q yake zaune, nan da nan yafito suka kama
yusleem suka nufi asibitin Dr sufyan dashi,

Kallo daya zaka yiwa mami da Hafsat kagane acikin tashin hankali suke domin
kowannensu fuskarshi kunshe take da tashin hankalin,

Emergency aka kai yusleem bayan kamar mintuna 30 Dr mufid yafito dauke da file din
yusleem domin lokacin Dr sufyan bai fitoba,binsa mami da Hafsat sukayi abaya domin
jin abinda zaice,

"Hajiya in my opinion ni ina ganin cewar is better for u idan kuka fitar da patient
dinku kasar Cairo ko kuma India saboda sincerely speaking yana cikin bad condition
domin cutar dake tattare dashi itace take cousing din wannan ciwon cikin da yake
fama dashi, and kuma akwai wani aiki da zasuyi masa wanda mu bazamu iyaba, so idan
zai yuyu in the next 3 days ku samar masa visa sai ku fita dashi domin magana
tagaskiya bama karbar patients wadanda lalurarsu tazama chronic kuma worst saboda
kinga nan is private hospital dole sai mun zama muna him takatsantsan..."

Yana ida wannan bayanin yagyara farin glass dinshi yayi gaba, sororo mami da Hafsat
sukayi kowannensu yana tunanin hanyar da za abi har akai ga fitar da yusleem kasar
waje....

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

_Fatan alkhairi ga yan kungiyar haske writers association, shafin yau nakune ku
kadai domin jin dadinku..._

*42*

***Daga mami har Hafsat ji sukayi kamar ruwa ya cinyesu dalilin jin
bayanin da dr yayi musu nan hankalin kowanne acikinsu yakai kololuwar tashi,

Mami ce tafara magana fuskarta cikeda murmushin yake,

"Hafsat babu komai kinji, karki daga hankalinki insha Allah zamu samu yanda
zamuyi..."

Wasu hawaye ne suka zubowa Hafsat tasa gefen hijabinta ta share batare da tayi
magana ba,

Kama hannunta taji mami tayi suka bar wurin suka koma reception,

"Yanzu Hafsat ina zuwa bari naje gida nadawo kinji..."

"To mami sai kin dawo, Allah kiyaye hanya.."


Tashi mami tayi tafita, yayinda ita kuma Hafsat taci gaba da zama awurin zuciyarta
kunshe fal da tarin tunani.

Tana nan zaune tarasa abinda yake mata dadi tahango dr sufyan yana kokarin
shigowa cikin reception din hannunsa dauke da wata yar madaidaiciyar bag, ko
kallonsa batayi ba ta dauke kanta takaishi can gefe, shikuwa kura mata ido yayi har
ya bace ya nufi office dinshi,

Kimanin mintuna 30 da tafiyar mami sai gata ta dawo, tun kallon farko da Hafsat
tayi mata ta fahimci cewar akwai damuwa a tattare da ita amma dai sai batayi magana
ba domin daga ita har mami din kowa ba son yin maganar yake ba,

Emergency suka shiga wurin da yusleem ke kwance yana bacci, gaban gadon sukaje suna
kallonsa,

"Ni wannan abu ya daure min kai, wai menene takamaimai abinda yake damunsa ne? Ni
duk ban fahimci bayanin da Dr yayiba hafsat..." Mami tayi maganar idanuwanta na kan
yusleem wanda yake kwance yana fitar da numfashi,

"To nima dai mami maganar dr ta daure min kai amma a iya sanina dai wannan ciwon
cikin shine ke damun yaya yusleem"

"To ko komawa zanyi wurin Dr din insake tuntubarsa inji?"

"A'a mami da dai mun hakura kawai munyi yanda yace din.."

"To yanzu hafsat ina zamu samu kudaden da zamuyi hakan? Hafsat yanzu ba babu abinda
muka mallaka inbanda wannan motar kwaya daya da nake hawa sai ko gidan da muke
ciki..."

"Babu komai mami ki kwantar da hankalinki insha Allah komai zai zama daidai saboda
Allah baya taba dorawa bawansa abinda bazai iyaba"

Ajiyar zuciya mami ta yi suka fita daga cikin emergency room din suka koma waje
suka zauna,

Wuni guda cur yusleem yana bacci sai yamma yafarka, hafsat ce ta karasa wurinsa
domin ita mami tatafi gida ta dawo wanda tafiyar tata bazata rasa nasaba ba dayin
wanka sannan da shiryo abinci,

"Sannu yaya yusleem.."

Kai ya daga mata ya lumshe idanuwansa,

"Yaya yusleem zaka sha kunun?"

Girgiza mata kai yayi bayan ya bude idonsa, kicin kicin yaga tayi tabata fuska
kamar zata saka kuka, ganin haka yasashi daga mata kai alamun zaisha,ita kanta tana
lura dashi sam yanzu baya son yaga bacin ranta,

Dan murmushi tayi ta tsiyayo masa kunun acikin cup ta zauna agefen gadon, yunkurawa
yayi yafara kokarin tashi ta taimaka masa, duk da cewar dakin basu kadai bane akwai
mutane da yawa aciki amma haka ta rinka bashi abaki yana kurba idan kuma ya disa
sai ta lashe, kallonta kawai yake yi da idanuwanshi wadanda suka dan firfito har
tagama bashi duk da dai bai shanyeba amma yadan sha dayawa,

Taimaka masa tayi ya kwanta ta gyara masa kwanciyar, ta zauna tana kallonshi,
hannunta taji ya riko acikin nashi tareda lumshe idanuwanshi ahaka har wani baccin
ya sake daukarshi.

Zuba mishi ido tayi takai hannunta bisa kuncinshi tasoma shafawa ahankali tana jin
wani irin tunani yana ratsa zuciyarta, ahaka Mami ta dawo ta isketa jikinta sukuku
wanda daga gani ranta abace yake gaba daya,

Jugum sukayi babu wanda yake yin magana acikinsu har tsawon wani lokaci domin kowa
shi yasan tunanin da yakeyi,sai can Mami tayi karfin halin yiwa hafsat magana,

"Hafsa kitafi gida kije kiyi wanka sai kidawo.."

Duk da bata son tafiyar amma bata musawa Mami ba haka tayi mata sallama tatafi
bayan ta leka yusleem ta window nan taganshi har lokacin bacci yakeyi ga drip nan
ahannunshi wanda ba ajima da daura masa ba domin duk jikinshi yayi yaushi,

Mami saida ta tabbatar da cewa hafsat tatafi sannan tatashi ta nufi office din Dr
sufyan,

Kimanin mintuna samada arba'in mamin ta shafe acikin office din na dr sufyan sannan
daga bisani tafito, tana zama hafsat nadawowa,

Zama suka cigaba dayi har zuwa dare, lokacin ne aka fito da yusleem daga emergency
aka kaishi wani daki wanda gado ne guda daya aciki irin na marassa lafiya sai
fridge dan karami sannan ga yar karamar tv nan daure ajikin bango sai dan
madaidaicin bathroom aciki,

"Hajiya wannan dakin kwana uku kadai zamu bashi muna treating dinshi domin dama
narigada nafada miki cewar fitar dashi outside shine kadai solution agareku,
therefore nan da 3 days zamu baku sallama so sai kuje gida kuci gaba da kula dashi
idan kuma before time din kun sami kudin fitar dashi outside sai ku fitar dashi.."
Dr mufid yafada yana sunkuye yana rubutu ajikin file din yusleem,

Kallonshi Mami da hafsat sukayi har ya kammala jawabin sannan yafita,

"Hafsat wuce kije kitafi gida ki kwanta inyaso idan Allah ya nuna mana gobe sai
musan abinyi.."

Girgiza kai hafsat tayi ta kalli mami,

"A'a Mami kibarni anan din ke kitafi gida, ni zan kwana tare dashi.."

"Hafsat kije ki huta kinji, babu komai"

"Dan Allah mami kibarni kitafi, wallahi ko naje gidan ba iya barci zanyi ba"

"To shikenan tunda kinki, bari ni naje natafi, Allah yabashi lafiya"

"Amin mami"

Saida mamin tasake duba yusleem din sannan tayiwa hafsa sallama tatafi,tana fita
harabar asibitin tahango dr sufyan tsaye ajikin motarshi kirar Benz new series 2017
yana sanye cikin kananan kaya, wurinshi mami takarasa dama abisa dukkan alamu ita
yake zaman jira, bude mata kofar motar yayi tashiga tazauna sannan yazagaya side
dinshi bayan yarufe yaja motar suka bar harabar asibitin.

Cikin dakin hafsat tashiga ta zauna akan wata kujera tana kallon yusleem wanda keta
faman barci, lokaci daya ta tashi zunbur ta isa gefen gadon ta zauna, bude idonshi
taga yayi,
"Sannu yaya yusleem"

Kai ya daga mata sannan yadanyi murmushi,

"Yaya yusleem ko kana bukatar wani abu ne..?"

Kanshi ya girgiza har lokacin fuskarshi tana dauke da murmushi, shiru tayi ta dan
jingina da jikin bango, gyangyadi ta dan soma yi amma da zarar baccin yafara
daukarta zatayi firgigit ta bude idonta,

Matsawa yusleem ya danyi yakamo hannunta, idonta Wanda yake cike da barci ya bude
domin daren jiya bata samu tayi ba,

"Kizo ki kwanta..."

"Bari inshinfida hijabina akasa kawai sai in kwanta saboda kar intakura maka"

"Gashi na matsa miki"

Girgiza kai tayi zata sauka daga kan gadon, tashi shima yayi da niyyar sauka tayi
saurin rikeshi,

"Haba yaya yusleem kaida bakada lafiya,dan Allah kakoma ka kwanta"

Dakyar ya kwanta din hannunshi rikeda ita dole ta hakura ta kwanta akusa dashi,

Sassafe saiga mami tazo, office din dr sufyan tafara zuwa amma lokacin bai fitoba,
wurinsu hafsa taje, hafsat din tana zaune akan kujera shikuma yusleem yana kan gado
akwance,

Tare da mamin suka cigaba da zama har karfe 9 tayi lokacinne driver yakawo musu
abinci amma ita mami bata samu damar cin abincin ba domin hankalinta yana can
office din Dr sufyan, hajiya kubra da alhaji sa'id ne suka zo duba yusleem din
bayan an dan gaggaisa mami ta zare jikinta ta fita, office din Dr sufyan tashiga
wanda yake abude alamun yana ciki,

Lokacin da hafsat tafito domin raka su hajiya kubra sukayi kicibus da mami, godiya
mami tayiwa su hajiya kubra sukayi sallama suka wuce ita kuma tanufi dakin da
yusleem yake,

Hafsat kam saida ta rakasu har wurinda motarsu take sannan tajuya ta takoma, tana
shiga cikin dakin ta iske mami tana shirya kudi rafa rafa sabbi kal yan dubu dubu
acikin jakarta wadanda zasu doshi samada naira dubu dari tara, cikeda mamaki hafsat
ta karasa gaban mami wacce ke zaune akan kujera.....

_Fans kuyi hakuri da jina shiru da kukayi kwana biyu, kun san jiki da jini amma
alhamdulillah naji sauki sosai, hakika bani da bakin da zan gode muku,duk wadanda
suka kirani suka gaisheni da wadanda suka min text nagode Allah yabar zumunci._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*43*

***Gaban Mami hafsat takarasa ta tsugunna fuskarta cikeda mamaki,

"Mami wannan kudin fa?"

Fadada murmushi mami tayi batare da ta dago ta kalli hafsat ba domin hankalinta
yanaga kan kudin da take lissafawa,

"Hafsat wani al'amari ne ya gudana wanda yayi sanadiyyar samuwar wannan kudin,
kinga dr kwana uku kacal yabamu yace daga nan sallamace zata biyo baya to shiyasa
naga gara fa intashi atsaye innemo kudi duk inda yake domin mu fitar da yusleem
kasar Cairo.."

"Hakane mami, amma yanzu kin san kudi yana wuyar samuwa shiyasa nace garin yaya aka
samo wadannan kudaden masu yawa.."

Rufe handbag din mami tayi ta maida hankalinta gurin hafsat da niyyar yimata bayani
amma kafin takai ga farawa sukaji anturo kofar dakin da suke ciki anshigo,
dukkaninsu maida idanuwansu wurin sukayi domin ganin wanda zai shigo,

Khadija ce ta shigo hannunta rikeda basket din abinci, tana sanye cikin bakar
doguwar riga ta yane kanta da mayafin rigar inbanda kamshi babu abinda take zubawa,

"A'a khadija ce? Sannu da zuwa" mami tayi maganar tana fadada fara'arta,

"Yawwa sannu mami" khadija tafada tareda ajiye basket din hannunta ta durkusa kasa
tagaida mami,

"Mami ina kwana? Ya mai jikin? Allah yabashi lafiya"

Cikin raha mami ta amsa gaisuwar, kallon khadija hafsat tayi tayi mata sannu da
zuwa sannan suka gaisa,

Gaban gadon yusleem khadija takarasa amma har lokacin bai tashi daga bacci ba dan
haka tadawo wurinsu mami ta zauna suka cigaba da zaman tare,

Zuwa can bayan yan wasu mintuna nurse tashigo ta dan dubashi tayi rubutun da zatayi
tafita, fitarta babu wuya yusleem din yatashi, idanuwansa fess yasaukesu akan
hafsat wacce ke zaune kusa da khadija, ita kuma khadijan sai danne dannenta takeyi
awayarta,

Tashi hafsat tayi taje wurinda yake itada mami,

"Hafsat taimaka min inje bathroom.."

Ba iya hafsat dince kadai ta rikeshi ba harda mami suka taimaka mishi yasauko daga
kan gadon suka rirrikeshi,

Tasowa khadija tayi tana cewa mami,

"Ayya mami barshi, kawo intayata.."

"Lahh babu komai khadija da kinyi zamanki kin huta" inji mami,

"A'a mami dan Allah barshi kije ki zauna"

Hade fuska yusleem yayi bai bari khadijan takai ga rikeshi ba yafada cikin toilet,
dukkansu sororo sukayi banda khadija da ke yin dan murmushin yake,

Dukkansu komawa sukayi suka zauna hafsat ce kadai ta tsaya tana jiran yafito, bai
jima sosai ba yabude kofa yafito yana faman bin bango, rikeshi hafsat tayi har zuwa
gefen gadon,

"Salla fa nake son yi" yace da hafsat,

"To bari in shimfida maka dan kwalina sai kayi.."

"A'a inada carpet acikin mota bari inkawo.." Khadija tace sannan ta mike tafita,
dan satar kallonshi hafsat tayi har lokacin fuskarshi kicin kicin take babu
walwala,

Karbar dardumar hafsa tayi bayan khadija ta Kawo ta shimfida masa,yahau yatada
salla,

Tashi yayi yakoma kan gadon bayan ya idar da salla, gaishe da mami yayi tai masa
sannu sannan suka gaisa da khadija,

Tea Hafsa tatashi ta hada masa takai masa,

"Yaya yusleem wannan bata fuskar duk na menene? Ka saki ranka mana"

Hannunta yariko tareda cup din ruwan zafin yana dan murmushi,

"Ai kece kika sani yin fushin..?"

"Saboda me?" Tafada tana dan zame hannunta daga nashi,sake rike hannun yayi yaki
saki,

"To ai gani nayi kunyi min rufdugu alhalin ke daya ma zaki iya rikeni..."

Murmushi tayi ta dan kalli wurin dasu mami ke zaune nan taga hankalinsu ma kwata
kwata ba akansu yakeba domin hirarsu sukeyi itada khadija,

"Yaya yusleem kenan..."


Cup din da hannunta yahada yarinka kaiwa tea din bakinsa yana kurba har yakusa
kammalawa, muryar mami ce ta katsesu,

"Hafsat ina zuwa bari mu fita tareda khadija tayi dropping dina saboda ayau zuwa
gobe nake so agama komai na tafiyar yusleem ban son abun yadauki lokaci.."

"To shikenan mami sai kin dawo, Allah yasa adace"

Sallama sukayi da khadija suka fita tareda mami, kwanciya yusleem yayi ya tallafe
kumatunsa da hannunsa guda daya yana kallonta,

"Kici abincin ki tayani wanka"

Sunkuyar da kanta tayi taci gaba da tsiyayo tea acikin cup,

"Uhmm, ko bakiji ba?"

"Naji yaya yusleem"

Ido ya tsura mata lokacin da tafara kurbar ruwan tea din, ganin ya kafeta da ido
yasata tashi ta bar wurin ta matsa can nesa dashi, murmushi yayi ya lumshe
idanuwansa.

Tunda mami tatafi bata samu dawowa ba har yamma abincima sai khadija ce takawo
musu kuma yanzun ma kamar da safe bataga sakin fuska awurin yusleem ba amma hafsat
ita kam ta karbeta hannu bibbiyu domin bataga aibunta ba,

Alla Alla hafsat tarinka yi mami tadawo domin ta kosa taji hanyar da mamin tabi
tasamo makudan kudade haka masu wuyar samuwa.

Mami bata samu dawowa ba sai bayan sallar isha, lokacin Dr yazo ya rubuta musu
sallama bayan mami ta bibbiya kudaden da yakamata su biya asibitin,

Driver ne ya daukesu suka nufi gida kuma dama jikin yusleem din yadanyi sauki ba
kamar ranar da sukazo ba domin yanzu ko aman yadaina,

Afalo suka zauna dukkaninsu hafsat tagama matsuwa da son jin abinda mami zatace
amma taji mamin tayi shiru sai lissafe lissafen kudi taketa faman yi,

"Yusleem nasamu munyi nasara komai ya kammala insha Allah nanda kwana biyu zaka
tafi kasar Cairo domin ance visa din kasar tafi saurin samuwa fiyeda ta kasar
India.."

"To mami Allah yasaka da alkhairi Allah yakaimu lokacin"

"Amin, Allah yasa asamo abinda akaje nema Allah yabaka lafiya"

"Amin mami, bari inyi wanka" yace da mami bayan ya mike yana yiwa hafsat kallon zo
ki rakani, taganshi sarai amma saita dauke kanta tayi kamar bata ganiba dolenshi
yajuya ya fice shi kadai,

Bayan fitarshi hafsat ta kalli mami,

"Mami kodai gwala gwalanki kika siyar?"

Dakatawa mami tayi daga yin abinda take ta kalli hafsat,

"Hafsa ai ni yanzu banida gwalagwalai, jiya darana bakiga nakoma asibiti raina
abace hankalina atashe ba?
Wallahi infada miki dawowa nayi na iske safe dina wurin da nake ajiyar gold din
abude an kwashe babu komai aciki, koda nakira mai gadi na tambayeshi sai yace min
wai bakuwa nayi kuma yace mata babu kowa agidan amma tace ehh zata shigo ta jirani,
ban san wacece ba amma duk yadda akayi itace ta sace min wadannan gold din kuma
dama iya saiti daya gareni sauran duk nasayar bana gasken bane.."

Zaro ido hafsat tayi saboda jin satar da akazo har gida aka yiwa mami,

"Mami Allah ya kiyaye gaba, Allah yamayar miki da alkhairi, yanzu kuma ya akayi?"

"Shine naje nasamu shi shugaban asibitin wannan yaron sufyan nace masa zan sayar da
kodata (kidney)guda daya sannan suma su khalifa shida Abdul idan sun dawo za aciri
tasu guda dai dai tunda dama guda dayace ke amfani ajikin dan adam.."

Zabura hafsat tayi ta zazzaro ido, cikin rawar baki tace,

"Haba mami, ya za ayi kisayar da kododinku? Ai bai kamata dan za agyara wani kuma
abata wani ba.." Takarashe maganar hawaye nabin kuncinta,

"Ai magana takare hafsat tunda shima sufyan din yabani shawara ta hanyar cewar idan
inada wata kadara kamar gida ko fili gara insiyar akan insaida kodata data yarana,
to kinga yanzu bamuda wasu kadarori inbanda wannan gidan kwaya daya shine yace to
mahaifinsa zai sai gidan kuma insha Allah zaiyi mana taimako ta hanyar bamu aron
gidan muci gaba da zama har zuwa ranar da zamu mallaki namu,adaren jiya mukazo muka
ga gidan bayan ya debo dillalai kuma sunyiwa gida kudi, ansiya miliyan daya.." Mami
takammala maganar tana dan murmushin yake domin zuciyarta wani zafi takeyi mata.

Hafsat ji tayi tasamu yar nutsuwa saboda jin bayanin mami,

"Allah ya rufa asiri mami, Allah yasa adace kuma"

"Amin hafsat, kinga yanda rayuwa ta juya mana ko? Mun kawoki kinata faman shan
wahala"

"Dan Allah mami kidaina fadin haka, ai yanda Allah ya tsara min kenan.."

"Allah yayi miki albarka, insha Allah gobe zamu yi signing atakardar gidan daga nan
sai inbasu copy.."

Shiru hafsat tayi tana jin tausayin mami yana kwaranya acikin ranta domin tasan
karfin hali kawai mamin keyi amma ita kadai tasan yanayin da take ciki,

Ganin mami ta tashi tashiga cikin bedroom dinta yasa itama hafsat tatashi tashiga
dakin surayya,

Kayan jikinta ta cire tashiga wanka, lokacin da tafito ta hangi yusleem kwance
saman gado yayi d'ai d'ai, hijabinta ta janyo ta saka tana kallonshi, shi dinma
juyawa yayi yana kallonta daga kasa har sama......

_Fatan alkhairi ga aminiyata maryam Qaumi, Amira zango,zeebells tareda Xarah b~b_

*_Ummi A'isha_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*44*

***D'auke kanta tayi daga kallon yusleem taje gaban mirror tafara shiryawa,
shikuwa sai faman binta da idanuwa yake domin duk wani motsi da zatayi akan idonshi
ne,

Tashi tayi da niyyar ta dauki kaya tasa amma ganin ya kafeta da ido yasata shiga
bathroom tasa kayan sannan tafito,

"Yaya yusleem dan Allah katashi katafi,ni wallahi bacci nakeji, kaga dai 2 days
banyi bacci ba..." Tafada cikin shagwaba bayan ta zauna agefen gadon, hannunta ya
kamo yarike cikin nashi,

"To ai yanzu ba hanaki baccin nayi ba, zo ki kwanta"

"Ni gaskiya katafi, bana son mami ta..."

Saurin katseta yayi ta hanyar jawota jikinshi,

"Karyar kunya kikeyi nanah, saboda Kinga mami fa tajima da sanin cewar tare muke
kwana tunda ko lokacin da tararmu agidan haya muna zaune adaki daya ta tarar damu
ba dakuna biyu ba.."

Jin ya ambaci gidan haya yasa taji Maman amir ta fado ranta,

"Kaga kuwa dazu da rana Maman amir ta kirani tana gaisheka tace inyi maka sannu..."

"Ina amsawa kawar Maman amir..."

Murmushi tayi tafara kokarin zamewa daga jikinsa amma ya riketa gam,

"Ba kince bacci zakiyi ba, to kiyi mana"

Shiru tayi domin dama bawai baccin takeji ba ita dai kawai tana kunyar mami tasan
anan yake kwana,
"Ya kukayi da mami? Ta fada miki a inda tasamo kudaden nan kuwa? Saboda wallahi sam
hankalina yaki kwanciya" yayi maganar cikin raunin zuciya yana shafa kanta,

"Ehh ta fada min yaya yusleem, wannan gidan ta saida kasan lafiyarka tafi komai
muhimmanci agaremu yanzu..."

"Hakane to amma..."

Katseshi hafsat tayi ta hanyar kai hannu ta rufe masa baki, shiru yayi yana jin
yanda take shafar kasumbarshi dake baibaye a fuskarshi,

"Ai yaya yusleem babu abinda yakai uwa dadi, kowacce uwa tana son danta acikin
kowanne irin yanayi koda kuwa duk duniya zata ki shi to ita zataso kayanta, kasan
meyasa nafadi haka?"

Girgiza kai yayi alamun a'a,

"To da mami kidney dinta tayi niyyar sayarwa da tasu Abdul..."

Gani tayi idanuwanshi sun firfito waje ya yunkura yana kokarin tashi, mayar dashi
tayi ya kwanta takoma jikinshi ta dora kanta akirjinsa,

"Ka kwantar da hankalinka ai bata sayar ba, gidan nan ta siyar shine aka samu
kudaden da zaka tafi Cairo..."

Ajiyar zuciya yayi yakai hannu ya rungumeta,

"Dole hankalina yatashi hafsat, idan mami da yan uwana suka sayar da kidney dinsu
menene ribar? Babu riba at all saboda nan gaba za azo ana facing problems a
lot,tunda kinga akwai kidney disease ko wani abu mai kamada haka"

"Hakane amma tunda Allah ya takaita abin ai shikenan karka daga hankalinka, Allah
yabaka lafiya, ni yanzu babban burina shine inga kasamu cikakkiyar lafiya kamar
kowa"

Murmushi yayi ya kamo hannuwanta,

"Kin kosa insamu lafiya ayi wacce za ayi ko?"

Dariya tayi ta boye fuskarta akirjinsa,

"Kai yaya yusleem ni wallahi ba abinda nake nufi ba kenan"

"To me kike nufi?"

"Ni kawai inganka lafiya kadaina wannan zazzabin da amai da ciwon ciki shine kadai
burina"

Kanta yafara shafawa yana murmushi,

"Nikuwa kin ga babban burina shine idan nasamu lafiya inbawa matata dukkan hakkoki
wanda addini ya rataya min awuyana, sannan inmaidata mace sosai..."

Boye fuskarta tayi tana dariya,

"Kai yaya yusleem.."

"Kai nanah hafsat, da kin zaci zamu zauna ahaka ne? Uhm"
Shiru tayi masa tana dariya har lokacin bata bari yaga fuskarta ba,

"Uhmm?" Yasake tambayarta, shirun tasake yimasa, hannunta yakama yakai bakinsa yayi
kissing dinshi, ji tayi ya rungumeta tsam tsam,

Kunyace ta lullubeta domin abin na yusleem yau yagirmama duk da dai dama yasaba
rike hannunta ko ya dafa kafadarta ko yaja mata yan yatsun kafarta ko kuma yadafa
kafadarta amma bai taba yunkurin kissing dinta ba sai yau,

Wasu wasanni masu nauyi yau yake yimata wanda bai taba yimata ba, sun jima cikin
wannan yanayin kafin ya rungumeta yana fitar da numfashi ahankali, kwanciya tayi
luf ajikinsa da haka har bacci ya dauketa domin dare yayi sosai.

Tunda tafara baccin ba ita ta tashi ba sai karfe 7,ita kanta tayi mamakin makarar
da tayi, dudduba gefenta tayi nan taga babu yusleem babu alamunsa,

Wanka tashiga tayi agurguje tafito tayi salla taci gaba da zama shiru, tana zaune
akan abin sallar taji shigowar mami,

"Hafsat yau makara kikayi ne? Naji shiru baki fitoba"

Tashi Hafsa tayi tana ninke dardumar da tayi salla,

"Ehh wallahi mami, ina kwana?"

"Lafiya lau, idan kin shirya kifito ga breakfast nan yana jiranki"

"To mami bari inzo.."

Fita mami tayi ita kuma ta tsaya tana nazarin ta yadda zata fita falo domin bata
son su hadu da yusleem, ta dade tsaye akofar dakin tana ta tunani kafin daga bisani
tayi kuru tafita,

Akan kujera ta hango yusleem kwance yana kallon tv ita kuma mami tana zaune tana
hada ruwan zafi,

Kin kallon yusleem tayi taje kusa da mami ta zauna itama tasoma hada ruwan zafin,

"Kai yusleem bazaka yi breakfast din bane?"

"Mami sai zuwa anjima yanzu ruwan zafi kadai zan Sha"

"To bari akawo maka"

Hada masa tea din hafsat tayi ta dauka takai mishi, zaune yatashi yana kallon
fuskarta amma saita kawar da tata fuskar,

"Yaya wankan safe...?" Yafadi lokacin da zai karbi cup din, shiru tayi masa tayi
hanzarin barin wurin aranta tana tunanin yanda akayi yazama marar kunya tsakanin
daren jiya zuwa yau,

Misalin karfe 10 nasafe suna zazzaune acikin falon sai ga khadija tashigo, tana
sanye da orange colour din atamfa da mayafi kalar atamfar da yar karamar hand bag,

Duba yusleem tayi tatafi bayan sun gaggaisa, bayan tafiyar khadija mai gadi yashigo
yace anyi baki wai masu siyan gidane suka zo, mamice tafita bayan ta dauki wasu
takardu,

Wasu mutane guda biyu tasamu tsaye a compound din gidan suna jiranta amma yau babu
dr sufyan,

"Sannu alhaji, wadannan sune takardun gidan gashi.."

Karbar takardun wani dan dattijon mutum yayi yafara dubawa, yajima yana nazarin
takardun kafin ya dago yana kallon mami,

"Hajiya wannan wanda sunansa yake jiki shine mai gidan?"

Jijjiga kai mami tayi,

"Ehh shine yarona ne"

"Yana ina yanzu?"

"Yana ciki"

"Zan iya ganinsa?"

"Me zai hana, bisimillah zo mu karasa"

Yusleem yana zaune a falo ya tisa Hafsa agaba yana tsokanarta sai gasu mami sun
shigo tashi yayi daga kusa da Hafsa yakoma wata kujerar ya zauna,

"Yusleem ga bakinka" inji mami, cikeda mamaki ya kalli mutanen nan yaga babu wanda
yasani acikinsu, zama wannan dattijon yayi ya kalli yusleem,

"Yusleem baka ganeni ba ko?"

Daga kai yusleem yayi alamun eh,

"Zaka iya tunawa shekaru shida da suka wuce kaje neman aiki a wata ma'aikata ta
yada labarai? A lokacin anyi maka interview daga baya kadawo akace maka baka samu
aikinba"

Murmushi yusleem yayi alamun ya tuna,

"Ok sai yanzu natuna ai dayake shekarun an dan kwana biyu"

"To yusleem tun lokacin da kayi interview kasamu wannan aikin kuma abangarena wato
department dina, nine nan nahanaka aikinka nace baka samuba amma gwamnati ta
daukeka sannan duk watan duniya tana biyanka albashi na naira dubu hamsin da biyar
banda allowances d sauran alkhairan da baza arasaba, nine na rinka rike kudin ina
harkokin gabana dasu har lokacin da zaka samu promotion daga grade level 9 zuwa
grade level 12,haka na rinka ninke kudinka ina kasafin gabana har saida naji wani
malami yayi wa'azi akan mutane masu aikata laifi irin nawa, to tun daga nan nasoma
binciken hanyar da zanbi insadu dakai inbaka hakkinka da aikinka amma kuma duk
lokacin da nakira wayarka bata shiga, daga karshe danaga narasa yanda zanyi inganka
sai narinka tara maka albashinka ina ajiye maka kuma ina juya maka acikin kudadena
na kasuwanci wanda yanzu haka duk dukiyata tamuce nida kai, kayi hakuri yusleem ka
yafe min domin na danne maka hakkinka kuma na cutar dakai..."

Jin maganar yusleem yayi kamar acikin mafarki, bashi kadaiba hatta su mami abin
yabasu mamaki mutuka amma kuma duba da irin zamanin da muke ciki yanzu sai mamakin
nasu baiyi yawa ba domin yanzu zalunci awurin mutane ba abune mai wahala ba,

"To ai alhaji ni banma san me zance ba domin gaba daya kaina yagama daurewa.."
Yusleem yayi maganar yana kallon mami wadda ita dinma shi take kallo zuciyarta
kamar kankara dan farin ciki domin arzikin danta da alama yakusa dawowa,
"yanzu tashi zakayi kazo muje inkaika kamfanoninmu da gidajenmu da kuma shagunanmu
wadanda ake sayar mana da kayayyakin da kamfanin mu yake sarrafawa, yusleem wallahi
kullum da kai nake kwana acikin raina inata addu'ar Allah yasa sai mun hadu nabaka
hakkinka kafin na amsa kiran ubangijina, gashi yau burina yacika, zan sauke babban
nauyi, zan baka albashinka na shekaru shida sannan kuma zan raba dukiyata gida biyu
inbaka taka, haka kuma zamuje can ministry of information domin abaka office dinka
wanda yake can yana jiranka.., yanzu tashi mu hanzarta mu tafi"

Farin cikine ya lullube Hafsa nan tasoma yiwa ubangiji godiya acikin zuciyarta, ji
take kamar ta zuba ruwa akasa tasha dan farin ciki,

Alhaji musa mori bai bar yusleem yasake wata magana ba yasashi agaba suka fita yace
zaije ya sauke nauyi,

Har tsakar gida mami da hafsat suka rakasu saida suka ga fitarsu sannan suka koma
ciki cikeda farin ciki da murna, dan murna ko abincin rana kasa ci sukayi suna
jiran suga dawowar yusleem amma har dare bai dawoba gashi kuma washe gari da safe
zai tafi kasar Cairo,

Yusleem kuwa tunda suka fita basu samu zamaba suna can sunata yawo ana nunnuna masa
filayensa da gidaje da shaguna da kamfanoni, basu suka samu Kansu ba sai karfe 9
nadare nan alhaji musa yagayyaceshi suje gidanshi suci abinci amma yusleem yaki
yace gida zaije domin gobe da safe zai tafi kasar Cairo nan suka rabu da alhaji
musa akan sai bayan yadawo sannan zasu karasa duk wasu abubuwa wadanda suka dace,
suka kawoshi gida suka ajiyeshi.

Afalo yasamu su mami zaune suna sauraron zuwanshi kowannensu da gani babu tambaya
yana cikin walwala da farin ciki, zama yayi agajiye kusa da hafsat yana murmushi,

"Wallahi yau nasha wahala mami, munyi tafiya sosai har wasu yan kauyuka mukaje.."

"Ikon Allah, Allah mai yadda yaso, Allah yasanya alkhairi dai" inji mami,

"Amin" ya amsa mata tareda kwashewa yadda akayi yasanar da ita, murna dukkansu suka
rinka yi sai lokacin suka iya cin abinci, faten wake da kifi yaji albasa da manja,
acikin faranti babba hafsat ta zuba musu suka hadu gaba dayansu sukaci harda mami,

Mamince tafara tashi tawuce bedroom dinta tabarsu awurin, kallon hafsat din yakeyi
yanda taketa wani sussunne kai ita adole kunyarshi takeji, bai kulata ba yatashi
yafita, wanka yaje yayi ya duba kayanshi yasa domin har hafsat ta hada masa yan
kayan da zai tafi dasu,

Saida yashirya tsaf sannan yanufi part din mami, dakin da hafsat take ciki yatura
yashiga, tana tsaye gaban mirror tana shafe jikinta da turare mai dan karen kamshi
da dadi,

Abayanta yatsaya yana kallonta yana shakar kamshinta wanda yatasamma rikita masa
kwakwalwa,

"Ashe nidinma dan gatane tunda gashi nan ana shirin yimin tarba ta musamman" yafada
cikin tsokana,

Shiru tayi bata tanka ba, ji tayi yadauketa yayi saman gado da ita, rungumeta yayi
yana bata labarin abinda yafaru tun daga fitarsa har Kawo dawowarsa,

"Yaya yusleem ai Allah yaga sadaukarwar da kayi kuma yaga irin tuban da kayi
shiyasa bazai taba barinka katabe ba.."
"To ai da taimakonki hakan yafaru madam, Allah yayi miki albarka.."

Kasa amsawa tayi domin tuni taji yasoma yunkurin irin wasannin da yayi mata adaren
jiya,

Duk da yanata maganar yagaji yagaji yau amma hakan bai sashi yayi barci ba, yanda
sukaga rana haka sukaga dare har asuba tayi, saida sukayi salla sannan suka kwanta
bacci.

Itace tafara tashi lokacin karfe 9 nasafe tayi wanka tafita wurin mami, bayan sun
gama breakfast tana shirin taje ta tasoshi sai gashi yafito, kamar ta nitse dan
kunya duk da tasan yanzu mami tagama gane adakin yake kwana, tagefen ido ta
kalleshi lokacin da yana gaida mami,

"Yusleem karfe 11 fa zaku tashi, kayi sauri kashirya muje mu rakaka" mami tayi
maganar tana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, tea kawai yasha yatafi
shiryawa,

10:30 daidai yafito tsaf cikin shirinsa natafiya, yasha kananan kaya, iya hafsat ce
kadai acikin falon tana jiran mami tafito tana tsaye gaban wani console tana ganin
fuskarta, abayanta ya tsaya, yariko kugunta nan tayi saurin juyowa,

Murmushi yayi yakai mata kiss saman bakinta tayi saurin gocewa, hannunta yariko,

"Jiya baki ki ba yau kuma tsabar gulma ce tasaki kin yarda?"

Hannu tasa tarufe fuskarta, jin mami na kokarin fitowa yasashi sakinta nan suka
dunguma suka tafi, motar mami suka shiga driver yaja suka fita daidai lokacin motar
khadija ta Kawo kai nan tayi reverse tabi bayansu.....

_Gaisuwar fatan alkhairi ga Anty A'isha (mama 4),Anty Aisha (maman minal),Maman
sultan, & Hawy yanmata_

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_


*45*

***Ta cikin mirror din saitinshi yake hango fuskar hafsat wacce ke kunshe da
abubuwa guda biyu wato farin ciki da kuma sabanin haka,

Mami kuwa tamkar tafi kowa farin cikin wannan tafiyar ta yusleem domin zaka gane
hakan idan har ka kalli fuskarta,

Tafiyar mintuna 15 zuwa 20 ne yakaisu airport din suna yin packing saiga khadija
itama tayi packing din tata motar akusa dasu dan haka kusan atare suka firfito,

Cikeda fara'a ta karaso wurinsu tasoma gaisar da mami, cikin fara'a mami ta amsa
domin acikin farin ciki take, dan kallon yusleem tayi taga hankalinsa ai bama anan
yakeba domin yana tsaye shida hafsat suna yin magana,

Tsayawa dukkaninsu sukayi ajikin mota suna jiran su,

Hawayene suke kokarin zuba a idon hafsat yusleem yayi saurin kama hannunta suka bar
wajen, can dan nesa dasu mami sukaje yafara rarrashinta,

Hannuwanta duka biyu yarike yana kallon fuskarta,

"Haba nanah karki zama raguwa, kiyi hakuri kinga da ace tun farko kudin nan sun
fito dawuri to da tare dake zan tafi..."

Hawayen da taketa kokarin hana zubowarsu ne suka zubo sharr nan yakai hannunshi ya
goge mata,

"Daina kuka, me kike so inkawo miki idan zan dawo..?"

Shiru tayi idanuwanta na kallon kasa,

"Abin dadi?, ko kayan kwalliya?", taji yasake tambayarta, girgiza masa kai tayi
alamun a'a,

"To me kikeso?"

Nunashi tayi da dan yatsa,

"Ni kaina...?" Yayi maganar murya kasa kasa,

Kai ta daga masa,

Hannuwanta taji ya matse tareda janta zuwa kirjinsa bata fargaba tajita rungume
ajikinshi,

"Yaya yusleem su mami..." Tafada tana kokarin zamewa, sassauta rikon da yayi mata
yayi yana murmushi,

"Ki kwantar da hankalinki idan nadawo zaki sameni har sai ma kin gaji dani"

Murmushi tayi ta zame jikinta tana kallonshi, shi dinma kallon fuskarta yake yana
murmushi, wurinsu mami suka koma yayi musu sallama ya dauki yar jakar kayanshi
yawuce,
Saida sukaga tashinsu sannan suka bar airport din suka dunguma suka koma gida har
khadija.

Bayan komawarsu gida harkokinsu sukai tayi amma da zarar hafsat tashiga daki sai
taga kamar zataga yusleem, haka taitajin kewarsa har dare yayi, duk irin baccin da
yacika mata ido amma lokacin da tazo ta kwanta sai taji ta kasa baccin kwata kwata,
sai uban juyi data rinka yi tana tuno mijinta, dakyar tasamu bacci ya dauketa bayan
dare ya raba.

Washe gari da safe bata samu damar fitowa da wuri ba sai wurin misalin karfe 11
lokacin da ta fito mami na shiri fita dama ita take jira,

"Hafsa ga breakfast can ni fita zanyi, ina son zanje gidan hajiya Sarah amma ba
dadewa zanyi ba"

"To mami Allah ya kiyaye hanya sai kin dawo"

Fita mami tayi tatafi ita kuma ta nufi dining area, zama tayi ta karya duk da
abincin bawani mai yawa taciba, falo tadawo tazauna ta kamo tashar b4u tana kalla
domin zaman shiru babu dadi,

Har bacci yadan fara daukarta sama sama taji sallamar khadija wacce abisa dukkan
alamu yanzu ta mayar da zuwa gidan kullum tamkar ibada,

Tashi zaune hafsat tayi tana murmushi,

"Sannu da zuwa.."

"Yawwa hafsa, ko mamin bata nan" inji khadija wacce ke sanye cikin wata doguwar
riga ta atamfa,

"Ehh mami ta dan fita wallahi" hafsa tabata amsa bayan tatashi zaune,

Zama khadija tayi, bayan sun gaisa suka dan fara hira kadan kadan,

"Hafsa kowa yayi mamakin yadda akayi kika samu kan yusleem har kuka kai wannan
lokacin tare, saboda yusleem baya iya zama da mace.."

Murmushi hafsa tayi,

"Baya zama da mace kamar ya? Aini ban san wannan labarinba ko a mafarki"

"To kuwa a lissafi kece mace ta fiyeda goma da ya aura, kuma saida ya sakeni sannan
ya aureki, ni kinga bamufi wata biyarba tare"

Jijjiga kai hafsa tayi alamun tausayawa,

"Allah sarki, Allah yarufa asiri kin san ai dama lamarin aure sai hakuri domin
shima rai gareshi..."

"Hakane amma nida ina zargin ko aljanu gareshi ko kuma da saninsa tsabar cin
mutunci ne, shiyasa ma ni yanzu wallahi auren yagama fitar min daga raina domin kin
san naji dadi shine gari bawai nasaba ba.."

"To ai ba duk aka taru aka zama dayaba khadija, sai kiga nan gaba kin samu inda
zakiji dadin hankalinki ya kwanta..."
"Kayya hafsa, kin san ai duk wanda miciji ya sareshi to idan yaga tsumma gudu yake,
hafsa arayuwar aurena tafarko ban tsinci komai ba face bakin ciki da bacin rai da
takaici, shiyasa ko zan kara wani auren gaskiya ba yanzu ba sai zuciyata ta nutsu
tukunna"

"Ubangiji Allah yazabi abinda yafi alkhairi, babu komai ai jarrabawa ce daga Allah"

"Amin.."

Haka sukaci gaba da yin hirarsu har azahar tayi sai lokacin khadija tatafi, tun
daga wannan rana kuma kullum zatazo susha hirarsu da hafsat wani lokacin ma harda
mami, ita hafsa tausayin khadija takeji domin irin labaran da take bata na kuncin
rayuwa da rashin samun farin ciki wanda ta rinka fuskanta agidan aurenta nafarko,
shiyasa take tausayinta domin tasan irin wannan rayuwar tunda itama tashiga
makamanciyarta abaya, koda yaushe yanzu khadija tana gidan haka kuma idan bataje da
safe ba to zataje da rana ko da yamma wani lokacin harda daddare ma zuwa take
tamaida gidan mami kamar gidansu haka ta dauki hafsat a matsayin yar uwa kuma
abokiyar shawara domin ko sabon bazawari tayi saita fada mata,

Yauma kamar kullum hafsa tana zaune tana tsifar kai ita kuma mami tana gyaran
farcenta saiga khadijan tashigo da alama daga sch take domin karfe 2 saura narana,

Da mami kawai suka gaisa tahaye dining ta zubo tuwon shinkafa miyar zogale tadawo
wurin hafsat ta zauna,

"To inbanda abinku kuma ga tsifar gashi ga abinci?" Mami tafada tana murmushi,

Dan kwali hafsat ta dauka ta rufe kanta, "bari inbarshi anjima na karasa idan
tagama"

Tashi mami tayi ta shiga kitchen domin tajiyo buruntun kuku aciki,

Mami natashi khadija ta dubi hafsa dama da labari tazo mata,

"Hafsa inata son inbaki labarin wani guy Al'amin, saurayi ne fa amma yadage sai ya
aureni duk da nace masa nataba aure"

Murmushi hafsat tayi, "to kibashi dama mana kigani, wallahi khadija kiyarda indai
kinga baida problem"

Murmushi khadija tayi ta yanko laumar tuwo tasa abakinta,

"Shikenan zan gwada ingani, bari inyi sauri ma domin munyi dashi zaizo da yamma"

"To Allah ya tabbatar da alkhairi"

Saida khadija taji tayi nak sannan ta hada nata yanata tatafi, kullum hakace take
faruwa domin acewarta dama gidan mami gidansu ne domin dama aminiyar mahaifiyarta
ce.

Tunda yusleem yatafi basuji duriyarsa ba saida yayi sati biyu sannan yakira su
murna ranar awurin mami da hafsa ba acewa komai, sun jima suna hira dashi yana
yimusu bayanin abubuwan dake faruwa sannan sukayi sallama,

Haka da daddare ma saida ya kuma kira suka kwashe awanni shida hafsat suna hira,
yanzu har tasan lokacin kiranshi domin kullum sai yakirasu da safe da daddare,

Satinshi 7 acan yafara shirye shiryen dawowa amma idan yadawo bayan wani lokaci zai
sake komawa,

Hafsat tunda taji zai dawo tarasa inda zata cusa kanta dan murna wanda hatta mami
saida ta fahimta, saloon mami takaita aka wanke mata gashinta aka gyarashi, bayan
sun dawo gida mai kunshin dake yiwa mami tazo ta zane mata kafafunta da hannaye da
bakin lallai mai adon ja,

Tarba ta musamman mami da hafsat suka shiryawa yusleem,karfe 3:30 jirginsu yasauka
nan mami da driver suka tafi daukoshi banda hafsa wacce tazauna domin karasa girke
girken da aka dora sabodayau tace itace zatayi girkin da yusleem zaici.....

_Gaisuwa da fatan alkhairi ga takwarata A'isha D/sabo..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*46*

***Lokacin dasu mami suka dawo gidan hafsat tana cikin daki tana shiryawa,
saida ta kammala sannan tayi sallar la'asar domin lokaci yayi,

Tana tsaye gaban mirror tana gyara fuskarta bayan ta idar da sallar ta hango
wulgawar mutum ta cikin mirror atsorace ta juya amma abun mamaki bataga kowa ba,
tsorata tayi takama hanya zata fita daga dakin taje falo wurinsu mami,

Ji tayi anyi mata wata irin damka, tuni numfashinta yafara neman daukewa, ajikin
mutum tajita anrugumeta tabaya tayadda bazata iya ganin fuskar mutumin ba, kara
taso fasawa amma ina bata samu zarafin yin hakanba domin ji tayi anrufe mata baki
da abinda bata san ko menene ba sai daga baya sannan ta fahimci cewar da bakinshi
ne,

Wani sanyayyen kamshi ne mai dadi yake ratsa kofofin hancinta gaba daya,

Sassauta rikon da yayi mata yayi ya dago da fuskarta yana kallonta,

"Nanah hafsat..."

Firgigit tayi tabude idanuwanta akan fuskarsa ganinshi yasata daka tsalle ta
rungumeshi na tsawon wasu mintuna,

Riketa yayi yana dan juyi da ita ahankali, dago da fuskarta tayi ta kalleshi,
tabbas yaya yusleem dintane amma kuma tamkar wanda aka canjashi domin farar
fatarshi tasake haskawa farin yakaru, gashi fatar tashi tasake laushi lubus kamar
ta jarirai, kyakkyawar fuskarshi kuma tasake cika da kyau, annuri, da farin ciki,

Ji tayi gaba daya tagama raina kanta saboda yusleem yafita tako ina ita sai take
ganinma ayanzu haka ai bata da wani abu atare da ita wanda take ganin zata iya jan
ra'ayinshi domin yafita kyau yafita komai na rayuwa,

Hancinta taji yaja domin har lokacin tana dale ajikinshi hannayenta sakale
awuyanshi,

Bude idanuwanta tayi daga dogon tunanin data lula ta kalleshi, ji tayi ya rike
fuskarta yana kokarin sake saita bakinshi akan nata, shi kansa bakin nashi da lips
din dake jiki da fararen hakoran dake jere aciki tasan abin kallone, lumshe idonta
tayi tana jiran taji saukar lips dinshi akan nata amma sai taji sabanin haka
maimakon yayi kissing din bakinta sai tajishi asaman kirjinta, saurin tureshi tayi
tasoma kokarin kwacewa tana dariya,

Riketa yayi shidinma yana yin dariyar kasa kasa,

"Bakiyi min ko sannu da zuwa ba.."

Tana shirin yin magana suka jiyo maganar mami tana nufo kofar dakin,

"Hafsa har yanzu baki idar da sallar bane? Idan kin idar kifito ki hada salad din
saboda nace kuku yahada yace kece kika ce karya taba sai kin fito..."

Bude baki tayi zata amsawa mami amma takasa saboda shakewar da muryarta tayi, rufe
mata baki da hannunshi yayi yabawa mami amsa da,

"Mami har yanzu fa bata idar da sallar ba.."

"To idan ta idar kafada mata, sannan ku fito muci abincin..."

"To mami..."

Saida ta tabbatar da cewar mami tatafi sannan ta kalleshi,

"Kuma da tashigo taganmu fa gashi kace mata wai salla nake yi.."

Murmushi yayi ya lakuce mata hanci,

"Ai bazata ma shigo ba saboda tasan nidake yau tamkar tif da taya zamu kasance...."
"To kazo muje kar taga mun dade tayi zargin ko wani abu muke yi.."

Murmushi yayi ya dauketa nan tasoma mutsu mutsu, ajiyeta yayi ta fice shikuma
yashiga toilet yayi alwala yafito yayi salla,

A falo ya samesu ita da mami sun baje girke girken da aka wuni anayi saboda shi,
akusa da mami ya zauna yana kallon hafsa wacce ke tsugunne tana hada salad wanda
zasu ci abincin dashi,sai lokacin wai ya lura da kunshin dake hannunta duk hidimar
dazu idonshi bai kai kan kunshin ba,

Tashi mami tayi zuwa kan dining domin debo wasu kwanuka,

Hannunshi yakai kan na hafsa,

"Ya akayi dazu banga kunshin nan ba sai yanzu? Koda yake ai ni yau dinne gaba daya
amaryar tawa tagama rudani, ta dauke hankalina"

Murmushi hafsat tayi saboda jin abinda yace, janye hannunta tayi daga jikin nashi
saboda taga mami na kokarin fitowa ganin haka shikuma ya wayance da lakuto salad
din yakai bakinsa,

Kamar koda yaushe a cikin babban faranti yauma suka zuba abincin suka hadu suna ci,
idan yusleem yafaki idon mami sai ya kwace abincin hafsa ya kai bakinsa,

Tun daga yanayin cin abincinsa mami da hafsa suka gane cewar lafiya ta samu domin
yau yaci abinci sosai wanda rabon da yaci irinshi har anmanta,

Komai da suka girka saida yaci, kallonshi kurum hafsa keyi saboda ganin yanda ya
bude ciki ya narki abinci,

Kan kujera yaje ya mike, mami na zaune kusa dashi suna dan yar hira dangane da
tafiyarsa da dawowar tashi yana sanar da ita abubuwan da suka wakana,

Hafsa kam wurin da suka gama cin abinci tashiga gyarawa tana kwashe na kwashewa
tana kaiwa kitchen ba zuwa tayi tasasu agaba ba domin tasan tsakanin d'a da mahaifi
dole akwai abubuwan da zasu tattauna atsakaninsu,

Saida ta kalkale wurin tass sannan ta kunna turaren wuta lokacin har 6 tayi, tashar
zee world ta kunna tazauna tana kallo bayan ta dora dan karamin pillow din kujera
akan cinyarta,

Tana ta kallonta sam hankalinta baya kansu mami, pillown taji anzare an kwanto akan
cinyarta,

Saurin kallon wurin dasu mami ke zaune tayi nan taga mamin bata nan, kallonshi tayi
lokacin da yake kara gyara kwanciyar kanshi akan cinyarta,

"Wai yaya yusleem yau da me kazo ne? So kake sai mami tafito ta ganmu?"

"Mami bazata fito yanzu ba ai, tashiga bedroom dinta kuma kin san idan tashiga bata
fitowa sai bayan tayi salla"

Shiru tayi, hannunta ya kamo ya hada da nashi yana gani,

"Kinyi kyau..."

Shiru tasake yi domin sai tana ganin kamar gatse yake yi mata, shikuma tsakaninshi
da Allah har cikin zuciyarshi yake fada,
"Yanaji kinyi shiru? Uhm"

"Babu komai"

"Ban yarda ba" yafada yana murza babban dan yatsanta,

"Lokacin salla yayi fa.."

Tashi zaune yayi yana kallonta,

"Tashi muje to muyi"

Tashi tayi tabi bayanshi zuwa cikin bedroom din,

"Kishiga ki fara yin alwalar"

"Nifa inada alwalata"

Murmushi yayi ya matsa kusa da ita,

"Allah karya kike, infada miki gaskiya? Wallahi ko tsarki bakida shi garama kije ki
sake kiyi alwala.."

Tamkar kasa ta tsage ta shige haka taji dan kunya, ganin yana kokarin sake yimata
wata tabargazar yasata juyawa da sauri ta fada cikin bathroom din ta turo kofa,
murmushi yayi ya cusa hannuwanshi cikin aljihun wandon jeans din dake jikinsa......

_Fans aci gaba da yimin uzuri domin har yanzu ban gama warwarewa ba, fatan alkhairi
agareku all..._

_*Ummi Shatu*_👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*Kina ina Hawwa Jidda Aliyu? Page din yau nakine tawan, Allah yakara miki basira
da hangen nesa...ina yinki hawwa kulu..!*

*47*

***Yana tsaye ya bawa kofar bathroom din baya hafsat ta fito hannunta
rikeda dan kwalinta tana kokarin daurawa,

Juyowa yayi yana kallonta, ganin gashin kanta wanda yasha gyara da yayi yasashi
karasawa gabanta ya rike dan kwalin,

"Yanmata harda su gyaran gashi shine ba anuna min tuntuni ba?"

Hancinshi yakai kan gashin wanda har hafsat na iya jin dumin numfashinsa wanda ke
sauka akan gashin nata,

Hannunshi tarike tana mai bata fuska,

"Yaya yusleem dan Allah kabari, Allah lokacin salla zai wuce.."

"Da yaushe ma aka kira sallar? Da sauran lokaci ai baby.."

Ribom din dake daure da gashin nata ya warware yasoma baza mata shi akan
kafadarta,tamkar mai yimata tafiyar tsutsa haka taji,

Rike hannunshi tasake yi,

"Nikam gaskiya yaya yusleem alwalata..."

Murmushi yafara wanda yakarashe shi da dariya,

"Ta karye?"

Girgiza masa kai tayi alamun a'a,

"A'a dai baby hafsa fada min gaskiya, ta karye?"

Runtse idonta tayi tana rikeda hannunshi,

"Dan Allah kabari kar time din salla yakure mana.."

"To bari naje masallaci..."

Har yasaketa yasake rikota,

"Bari kawai nakarasa karyata inyaso sai kisake sabuwa"

Kafin takai ga yin magana har ya kama lips dinta,

Mintsininshi tayi a hannunshi nan yasaketa yana dariya, fita yayi daga cikin dakin
zuwa bathroom din dake cikin falo anan yayi alwala yatafi masallaci.

Koda hafsa ta idar da sallar magrib kin fitowa tayi anan inda tayi salla ta kwanta
har saida lokacin sallar isha yayi sannan tatashi ta gabatar da sallar isha da
shafa'i da wutri,
Batare da ta cire hijab din da tayi sallar ba tafita falo wurin mami,

Mamin nazaune da carbi a hannunta tana ja sannan kuma tana kallon labarai a tashar
BBCW,

Tana zama yusleem yana shigowa, kin kallonshi tayi tamaida idonta kan tv, a kusa da
mami ya zauna wato kujerar dake kallon ta hafsa,

"Hafsa akawo abinci ko?" Mami tayi maganar tana kallonta,

"To mami bari nakawo muku nidai nakoshi.."

"Nima gaskiya na koshi amma zansha kunu" yusleem yayi maganar yana zaro wayarshi
daga aljihun jeans dinshi,

"To shikenan adama mana kunun gaba daya sai musha" inji mami,

Tashi hafsa tayi zuwa kitchen, mintuna kalilan ta damo kunun ta dawo falo dauke
dashi,

A cup ta zuzzuba musu ta dauko sugar da madara tasa musu,da kafarshi ya tabota
kasancewar tana zaune akasa kusa da kujerarshi, dagowa tayi ta kalleshi,

"Wannan na waye kike zubawa?"

"Nakane.." Tabashi amsa,

"Yayi yawa ai, rage"

Sauka kasan shima yayi kusa da ita,

"Bar sugar dinnan haka, amma ki kara milk da yawa"

"Duk wannan wadda nasa batayi ba?"

"Nifa ke nake yiwa gata yarinya, ko bakya so indaina?" Yayi maganar cikin rada rada
tayadda mami bazata jiyo ba domin tana dan nesa dasu,

Shiru tayi masa saboda tagane abinda yake nufi, ita yau mamaki yake bata domin
kamar zuwansa Cairo dinnan rashin kunya yaje ya koyo domin tunda yashigo cikin
gidan yau yaketa yimata abubuwa masu nauyi,

Tura masa gwangwanin madarar tayi gaba daya da kunun nashi tadauki na mami takai
mata tadawo ta zauna tasoma shan nata kunun,

Tana jinshi yanata dungurinta tarabu dashi daga karshe ma tashi tayi tawuce cikin
daki tayi kwanciyarta, wayarta ta jawo nan taga miss called din umminta, kiranta
tayi suka gaisa suka dan taba hira daga nan sukayi sallama.

Tana kwance lullube cikin bargo taji shigowarshi, rufe idonta tayi kamar mai yin
bacci, akusa da kafarta ya zauna yakama yan yatsun kafar yasoma jansu daya bayan
daya suna yin kara, duk da tanajin zafi shiru tayi masa ita adole bacci take yi,

Jin tayi shiru yasashi haurawa saman gadon, abayanta ya kwanta bayan ya dan ture
bargon da take ciki,

Kamshin turarenshi da taji shine ya haifar mata da kasala, luf tayi tana jinshi
yana baza mata gashin kanta,

Juyo da ita yayi tana fuskantarshi, jikinta ne yabata cewar kallonta yake domin
tsawon mintuna biyar zuwa shida tajishi shiru baiyi koda motsi ba kuma tasan ba
bacci yake yiba, ahankali ta bude idonta guda daya kadan ta kalleshi ai kuwa kamar
yanda ta zarga ganinshi tayi ya zubawa halittar kirjinta manyan idanuwanshi ko
kiftawa bayayi, ganin yana kokarin kai hannu yasata saurin juya masa baya kamar mai
bacci, juyo da ita yasake yi,

Rike masa hannu tayi tabude idonta,

"Keda kike yin barci ya akayi kikasan abinda ke faruwa?"

"Dan Allah nidai ka kashe hasken nan"

Murmushi yayi ya kalleta,

"Bakya son inganki ahaske? Nikuma da nafi son inkare miki kallo sosai"

Jan bargo tayi ta rufe har kanta, sauka yayi daga kan gadon yaje yakashe hasken
yadawo amma abin mamaki koda yahau kan gadon ji yayi babu ita babu alamunta nan
yafara shashime amma bai jitaba,

"Hafsa, hafsa, dama wayo zakimin kenan.."

Jin bata amsaba yasashi sauka daga kan gadon yafara bin bangon dakin yana lalubenta
domin bai zo da wayarshiba,

Shiru bai jitaba sai can yajiyo kamar motsinta awurin gaban mirror, ahankali yataka
yaje wurin, hannayenshi ya mika da niyyar damkota amma sai aka samu akasi suka
sauka akan abunda yaketa zumudin samu yanzu,

"Wai wai yaya yusleem..." Tace dashi tana rike hannunshi,

Rikota yayi ya dagata yadorata akan kafadarshi ya lulubi gado ya hau har lokacin
tana kan kafadarshi,

"Allah ne yaga zuciyata shiyasa yabani cikin sauki.." Yace da ita yana kokarin
kawar da sleeping gown dinta,

"Dan Allah kayi bacci kaga daga tafiya kadawo..."

Murmushi yayi mai sauti wanda har sai da ita kanta taji,

Bata kara jin muryarshi ba har tsawon wani lokaci,

Duk da cewar bacci yacika mata ido amma haka tahakura,

A tsakiyar kirjinta ya kwantar da kanshi ahaka bacci ya daukesu,

Dakyar ta iya tashi da asuba saboda tsabar bacci, komawa tayi ta kwanta bayan ta
idar da salla,tana kwanciya yazo ya matseta ya kwanta abayanta.

K'arfe 10 tatashi, wanka tayi ta shirya tasa atamfa blue ta fita, iya mami ce
kadai a falon tana duba jaridar daily trust, durkusawa tayi tagaida mami sannan
tahau kan dining tahada tea tasha,
"Yafada miki yafita ko?" Mami ta tambayeta,

"A'a mami ai sai yanzu natashi"

"Hakane kuma, can yatafi gidan alh musa mori zasu karasa wannan yawon ganin
kadarorin nasu wanda suka fara rannan"

"To Allah yadawo dashi lafiya"

"Amin amin".

Koda yusleem yafarka daga barci bathroom yashiga yayi wanka yafito, ganin hafsat
bata tashiba yasashi fita zuwa part dinsu Abdul, acan yashirya cikin farar shadda
kal da ita yasa agogon azurfa yafito bayan yashafe jikinsa da turare, sauri sauri
yashiga part din mami yasha tea domin alh musa nacan yana jiranshi, wurin hafsa
yakoma har lokacin bacci take gagarumi bata da ranar tashi, yan yatsun kafarta
yaja, ganin ko motsi batayi ba yasashi yiwa dan madaidaicin bakinta kiss da
wuyanta,shi baisan dalilin da yasa baya iya dauke idonshi daga jikinta ba musamman
ma kirjinta idan yazuba mata ido shagala yake, saida yakai hannunshi wurin sannan
ya iya kwantar da kwalamarshi yafita,

Yana fitowa daga dakin itama mami nafitowa daga nata,

Keyarshi yadan fara sosawa sannan ya durkusa yagaida mami, sallama yayi mata
yakarbi key din motarta yafita,

Lokacin da yaje gidan alh musa dake unguwar millionaires estate aharabar gidan ya
ajiye motarshi wadda tafito a matsayin bare acikin sauran motocin dake farfajiyar
gidan domin duk sunfi tashi aji da matsayi,

Wata zukekiyar budurwace tafito sanye da wata hadaddiyar bakar gown, hannunta
rikeda hand bag da key din mota tasha takalmi mai mutukar tsini tasa bakin face
afuskarta, ashekaru zata kai 30 sai kamshinta ne ke kai kawo acikin iskar dake
kadawa a compound din gidan, hango yusleem tayi yana fitowa lokacin da take kokarin
bude motarta sabuwa dal,

Fasa shiga cikin motar tayi ta tsaya tana karewa yusleem kallo domin ko acikin
finafinan India tasan ba kasafai aka fiya samun handsome, classic guy kamarshi
ba.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_DEDICATED TO MISS XOXO_

*48*

***Tsayawa yusleem yayi ajikin motarshi bayan yafito, wayarshi ya zaro daga
cikin aljihun wandon shaddarshi yasoma kiran hafsat saboda yasan yanzu may be
tatashi daga baccin da yataho yabarta tanayi,

Har tayi ringing takatse bata dauka ba da alama bata kusa, sake kira yayi domin
yasan bazai samu nutsuwa ba har sai yaji muryarta,

Kiranta yaci gaba dayi amma shiru bata dauka ba domin bata cikin bedroom din tana
falo tareda mami, saida yayi mata 5 miss called, ana 6 dinne tashiga cikin bedroom
din, wayar na daf da tsinkewa ta daga tareda zama agefen gado,

"Yaya yusleem lafiya...?" Tace dashi bayan ta kara wayar a kunnenta,

"A'a..." Yabata amsa yana murmushi,

"To meyake faruwa?"

"Ji nayi ina tsananin son jin muryar matata saboda nabarota tana bacci, ko har
yanzu baki tashiba?"

Murmushi tayi najin dadi,

"Natashi, gashi har naci abinci naje wurin mami muna hira"

Murmushin shima yayi,

"To nima idan nadawo za ayi hirar dani"

"Allah yadawo dakai lafiya, Allah ya tsare ka ya kare mana kai"

"Amin, sai nadawo"

Katse wayar yayi yana murmushi, wayar tashi yamaida cikin aljihu ya nufi kofar da
zata sadashi da falon bakin alh musa mori,

Duk wadannan abubuwan da yusleem keyi akan idon wannan matashiyar budurwar ne domin
tamkar tv haka ta tsaya tazuba masa ido tana kallonshi, ganin ya shige tadaina
hangoshi yasata fasa fitar da zatayi ta juya takoma cikin gida domin har ga Allah
tanada bukatar sanin ko waye wannan kyakkyawan saurayin, gentle mai aji,

Ta kofar dake cikin part dinsu ta bi tashiga falon mahaifin nata,

Shi kam yusleem baima san da itaba domin lokacin da yagama wayarshi kansa tsaye
yanufi wurin alh musa,

A falo ya iskeshi yana karyawa, durkusawa yusleem yayi yagaida shi sannan yatashi
yazauna akan kujera,

"Yusleem ga abinci kazo kazuba kaci, ina so kadauki nan gidan a matsayin gidanku
domin bakada shamaki atare dashi"

Murmushi yusleem yayi,

"To alh nagode, Allah yasaka da alkhairi"

Duk da bashida sha'awar cin abincin amma yadan hada ruwan zafi rabin cup yana
kurba,

Wani kamshine mai mutukar ratsa zuciya ya dokeshi kafin zazzakar muryarta ta cika
kunnuwansu,

Cikin nutsuwa tashigo cikin falon mahaifin nata ta durkusa agabanshi tana gaidashi
kanta akasa,

"Hafsat baki fita ba yau?" Alh musa yayi maganar cikeda kulawa, jin an ambaci
hafsat yasa yusleem kallonta, kyakkyawa ce iya kyau saida yaji gabansa yafadi,

"Ehh abba dama saboda naji umma tace katashi baka jin dadi shiyasa ma ban fitaba"

"To ai babu komai kin san jikin tsufa dama hakane.."

Gaida yusleem tayi cikin nutsuwa da ladabi, ya amsa mata fuska asake,

Dauke idonshi daga garesu yusleem yayi yana sauraren tattaunawar tasu har suka
gama,

Mikewa tayi tafita yayinda alh musa yajuya ga yusleem,

"Yusleem wannan itace babbar yata hafsa, itace babba tanada kanne guda hudu daya
mace uku maza"

"Allah sarki.." Yusleem yafada yana murmushi,sake kallon alh musan yayi yace,

"To alh ni ina ganin tunda baka da lafiya ma kawai mubari gobe idan Allah yakaimu
sai nazo muje, dama dan ban san bakada lafiya bane da bazan zo ba sai gobe"

"To shikenan Allah yakaimu, nagode yusleem"

Sallama sukayi yusleem yafita, gaba daya kamshin turaren nan dayaji yatada masa da
kwalamar hafsanshi,

Shiyasa yake sauri yasamu yaje gareta ko zaiji sauki, bude motar tashi yayi cikin
sauri yashiga yayi mata key yafita daga gidan,

Tun daga fitowarshi har fitarshi duk akan idon hafsat hakan yafaru saida taga
fitarshi sannan takoma ciki.

Lokacin da yusleem yakoma gida, afalo ya iske hafsat da khadija suna hira da alama
mami bata nan, gaidashi khadija tayi ya amsa batare da yatsaya ba yawuce dakin
hafsa,

Kallon hafsa khadija tayi,

"Bari nakarasa tunda maigidanki yadawo sai wani lokacin zan sake dawowa.."

"To shikenan Allah yadawo dake khadija, nagode"


Rakata kofar falo hafsa tayi tajuya ta nufi wurin yusleem, a kwance tasameshi yayi
rigingine yana kallon sama, hannu ya mika yarikota zuwa jikinsa ya kwantar da ita,

"Harka dawo? Amma kamar fa kadawo dawuri..."

Shiru yayi mata yana laluben zip din rigarta,shirun itama tayi aranta tana tunanin
to ko dama abinda yadawo dashi kenan?

D'an dukan kirjinshi tayi, "yaya yusleem kayi magana mana"

Sake rungumeta yayi yana shakar kamshin dake tashi daga jikinta,

"Matata naji ina bukata shiyasa nadawo gareta..."

Murmushi tayi aranta tana mai jin farin ciki yana ratsata sai dai kuma har yau
takasa banbance shin halaccin da tayi masa ne yake sashi kyautata mata ko kuma
zuciyarshi ce tafara kaunarta?

Kasa lalubo amsa tayi dan haka tayi gaggawar kawar da tunanin acikin ranta,
mirginata kasa taji yayi shikuma yana samanta,

Soyayya mai mutukar sanyi yashiga nuna mata cikin nutsuwa domin komai nashi dama a
nutse yake aiwatar dashi babu baragada, kissing dinta yajima yanayi har zuwa wani
lokaci,wasu wasanni masu sanyaya zuciya yashiga yimata wanda saida yaji yasamu
nutsuwa sannan ya sarara mata,

Rungumeta tsam tsam yayi yana jin wata irin nutsuwa tana saukar masa, fatar
kunnenta yakama da hakorinshi yana ciza ahankali yana hura mata iska awurin,

"Wai yaya yusleem dama abinda yadawo dakai kenan?"

"Hafsa sau nawa zan amsa miki ne? Nace miki eh, eh, ehhhh..."

Murmushi tayi tarike hannunshi duk kunya tagama baibayeta kawai daurewa takeyi,

"Ina mami tatafi?"

Sai lokacin hafsat ta tuna da cewar mami na iya dawowa ako wanne lokaci dan haka
tafara kokarin zame jikinta, riketa tsam yayi,

"Mami fa ba nisa tayiba dan Allah kabari karta dawo ta samemu..."

"Kin kusa ai kibar mamin dan wallahi daukeki zanyi inkaiki inda zamu rayu mu biyu
babu mai katse min hanzarina.."

Murmushi tayi tasamu ta zare jikinta dakyar tatashi tana yimasa dariya kasa kasa
saboda ganin yanda duk shaddar jikinsa tayi wani arnen squeezing,

Rikota yayi lokacin da take kokarin sauka daga kan gadon, hannuwanta duka biyu tasa
ta kare fuskarta tana yin wata dariyar ahankali.....

_Gaisuwar fatan alkhairi ga maman fati, ina mutukar kaunarki mamana..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

_Fatan alkhairi ga yan zauren babie isah, hakika ina mutukar yinku kamar yadda
kuke yina,shafin yau nakune kyauta..._

*49*

***Ahankali ya tashi zaune har lokacin yana rikeda ita,

"Menene kike yimin dariya?"

"Babu komai.."

"Ban yarda ba"

Wata dariyarce tasake subuce mata,

"Nasan abinda kike yiwa dariya shikenan, anjima ki shirya zaki rakani unguwa"

Dadine taji ya kamata shiyasa fuskarta tasake fadada da farin ciki,

"Tom Allah yakaimu, amma ina zan rakaka?"

"Zance..." Yabata amsa tareda kokarin sauka daga kan gadon, saurin rikoshi tayi
saboda jin abinda yace,

"Zance?" Ta maimaita abinda yace cikin sigar tambaya,

"Ehh ko bakya son inyi miki kishiya?"

Shiru tayi masa tasakeshi, dan kwalinta da rigarta da sauran kayanta wanda yayi
mata fatali dasu tabi ta tattara ta nufi wurin drewar kaya ta tsaya,

Dan kallonta yayi yasaki murmushi domin bai taba ganin fushinta ba sai yau,
Tashi yayi yaje gabanta tana tsaye tana kokarin saka riga, kunnuwanshi duka guda
biyu ya rike,

"Am sorry nanah hafsat..."

Bata kulashi ba taci gaba da abinda takeyi, hannuwanta yarike,

"Nace kiyi hakuri wallahi dawasa nake yi miki.."

"Ni kadaina bani hakuri saboda ba fushi nayiba"

Rungumeta yayi gaba daya ajikinshi yana murmushi,acikin kunnenta yafara yimata
rada,

"Gidan su Ummi fa nake son ki rakani daga nan sai muje gidansu kawarki Maman amir"

Duk da taji dadin zata je gidansu da gidan su maman amir hakan baisa ta saki
fuskarta ba,sassauta rikon da yayi mata yayi,

"Baby ashe haka kike da kishi shine ban saniba?"

Sake bata fuska tayi ta zame daga rikon da yayi mata, fita tayi gaba daya daga
cikin dakin tanufi falo tana tafiya tana kokarin zuge zip din rigarta, tana zama
mami na shigowa,

Sannu da zuwa tayi mata ta karbi kayan dake hannunta, kinkimar kayan da mamin tazo
dashi hafsat tayi takai cikin dakin mami tafito lokacin har yusleem yafito yana
zaune kusa da mamin,

Ko kallonshi batayi ba tawuce tazauna, dan kallonta yayi ya rausayar dakai alamun
ban hakuri, dauke kanta tayi taki kallonshi,

"Mami dan Allah kibawa yarinyar nan hakuri naga sai fushi take dani daga yimata
wasa....." Tajiyo yusleem yana fadawa mami,

"Ahh fushi kuma?" Mami ta tambaya, juyawa tayi ga hafsa,

"Hafsa meya faru??"

Murmushi hafsa tayi cikeda jin kunya tace, "Allah mami ni babu komai ba fushi
nakeba"

"Wallahi mami karya take yi fada mukayi saboda wai kawai nayi mata wasa nace zata
rakani zance wurin budurwata..."

Jin abinda yace yasa mami yin murmushi tatashi ta wuce kitchen wurin kuku tabarsu
afalon saboda ta fahimci maganarsu ce ba tataba,

Ganin mami tafita yasa yusleem kallonta yana gyarawa hularshi karinta,

"Wallahi Allah hafsa wasa nake yimiki, wallahi ni banida wata budurwa kin san dai
bazan rantse miki akan karya ba.."

Jin abinda yace yasata sakin ranta kadan amma bawai dan ta huceba sai dai ko babu
komai zuciyarta ta danyi sanyi domin ta tabbatar da gaskiyar abinda yafada tunda
har ya rantse mata,

Tashi yayi yafita saboda jin batayi masa magana ba, tunda yatafi bata kara jin
motsinshi ba har karfe 2 narana, suna zaune suna cin abinci taji yakira mami
awaya,

"To shikenan bari mugama sai tazo, ehh tana nan zuwa" mami tafada sannan takatse
wayar tajuya tana kallon hafsa,

"Yusleem ne wai idan kin gama kije ki karbo mana kayan tsarabarmu, kiji wani
kinibibi tun dasafe bai bamu ba sai yanzu..."

Murmushi hafsa tayi saboda tagano wayonshi kawai son ganinta yake shine ya bullo
tanan,

Saida mami tasake tuna mata bayan sun gama cin abincin sannan ta tashi tatafi, baya
cikin falo dan haka tawuce ciki, akan gado ta hangoshi zaune yana daddanna
wayarshi,

"Mami tace kana kirana, gani.."

"Zo..."

Karasawa tayi gaban gadon ta tsaya batare data kalleshiba tun bayan kallon farko da
tayi masa saboda daga shi sai gajeren wando da farar vest iya shaddar da yasaka
kawai yacire,

Hannunshi ya mika ya kamo nata ya fisgota da karfi, babu zato tajita tafada kanshi,
matseta yayi yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi, sam baya gajiya da
lalubarta dan haka nan take yafara,

Duk da tana dan fushi dashi amma hakan baisata juya masa baya ba,soyayya ya nuna
mata sosai ita har mamakinshi ma tayi,

"Baby wallahi bana gajiya dake,kefa kina gajiya dani...?"

Shiru tayi masa ta dauke kanta cikeda kunya,

Hancinshi yagoga ajikin nata,

"Uhm...?"

Shirun tasake yimasa, hancinta yaja tareda lakuce mata shi yana murmushi,

"Bacci nake son ki dan tayani baby zuwa anjima sai kitafi wurin mamin ko?"

Bai jira amsarta ba ya rungumeta tsam tsam ajikinshi yana shafa sumar kanta wacce
tasha gyaran saloon......

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

_Fatan alkhairi ga yan zauren babie isah, hakika ina mutukar yinku kamar yadda
kuke yina,shafin yau nakune kyauta..._

*49*

***Ahankali ya tashi zaune har lokacin yana rikeda ita,

"Menene kike yimin dariya?"

"Babu komai.."

"Ban yarda ba"

Wata dariyarce tasake subuce mata,

"Nasan abinda kike yiwa dariya shikenan, anjima ki shirya zaki rakani unguwa"

Dadine taji ya kamata shiyasa fuskarta tasake fadada da farin ciki,

"Tom Allah yakaimu, amma ina zan rakaka?"

"Zance..." Yabata amsa tareda kokarin sauka daga kan gadon, saurin rikoshi tayi
saboda jin abinda yace,

"Zance?" Ta maimaita abinda yace cikin sigar tambaya,

"Ehh ko bakya son inyi miki kishiya?"

Shiru tayi masa tasakeshi, dan kwalinta da rigarta da sauran kayanta wanda yayi
mata fatali dasu tabi ta tattara ta nufi wurin drewar kaya ta tsaya,

Dan kallonta yayi yasaki murmushi domin bai taba ganin fushinta ba sai yau,

Tashi yayi yaje gabanta tana tsaye tana kokarin saka riga, kunnuwanshi duka guda
biyu ya rike,

"Am sorry nanah hafsat..."

Bata kulashi ba taci gaba da abinda takeyi, hannuwanta yarike,

"Nace kiyi hakuri wallahi dawasa nake yi miki.."

"Ni kadaina bani hakuri saboda ba fushi nayiba"


Rungumeta yayi gaba daya ajikinshi yana murmushi,acikin kunnenta yafara yimata
rada,

"Gidan su Ummi fa nake son ki rakani daga nan sai muje gidansu kawarki Maman amir"

Duk da taji dadin zata je gidansu da gidan su maman amir hakan baisa ta saki
fuskarta ba,sassauta rikon da yayi mata yayi,

"Baby ashe haka kike da kishi shine ban saniba?"

Sake bata fuska tayi ta zame daga rikon da yayi mata, fita tayi gaba daya daga
cikin dakin tanufi falo tana tafiya tana kokarin zuge zip din rigarta, tana zama
mami na shigowa,

Sannu da zuwa tayi mata ta karbi kayan dake hannunta, kinkimar kayan da mamin tazo
dashi hafsat tayi takai cikin dakin mami tafito lokacin har yusleem yafito yana
zaune kusa da mamin,

Ko kallonshi batayi ba tawuce tazauna, dan kallonta yayi ya rausayar dakai alamun
ban hakuri, dauke kanta tayi taki kallonshi,

"Mami dan Allah kibawa yarinyar nan hakuri naga sai fushi take dani daga yimata
wasa....." Tajiyo yusleem yana fadawa mami,

"Ahh fushi kuma?" Mami ta tambaya, juyawa tayi ga hafsa,

"Hafsa meya faru??"

Murmushi hafsa tayi cikeda jin kunya tace, "Allah mami ni babu komai ba fushi
nakeba"

"Wallahi mami karya take yi fada mukayi saboda wai kawai nayi mata wasa nace zata
rakani zance wurin budurwata..."

Jin abinda yace yasa mami yin murmushi tatashi ta wuce kitchen wurin kuku tabarsu
afalon saboda ta fahimci maganarsu ce ba tataba,

Ganin mami tafita yasa yusleem kallonta yana gyarawa hularshi karinta,

"Wallahi Allah hafsa wasa nake yimiki, wallahi ni banida wata budurwa kin san dai
bazan rantse miki akan karya ba.."

Jin abinda yace yasata sakin ranta kadan amma bawai dan ta huceba sai dai ko babu
komai zuciyarta ta danyi sanyi domin ta tabbatar da gaskiyar abinda yafada tunda
har ya rantse mata,

Tashi yayi yafita saboda jin batayi masa magana ba, tunda yatafi bata kara jin
motsinshi ba har karfe 2 narana, suna zaune suna cin abinci taji yakira mami
awaya,

"To shikenan bari mugama sai tazo, ehh tana nan zuwa" mami tafada sannan takatse
wayar tajuya tana kallon hafsa,

"Yusleem ne wai idan kin gama kije ki karbo mana kayan tsarabarmu, kiji wani
kinibibi tun dasafe bai bamu ba sai yanzu..."

Murmushi hafsa tayi saboda tagano wayonshi kawai son ganinta yake shine ya bullo
tanan,
Saida mami tasake tuna mata bayan sun gama cin abincin sannan ta tashi tatafi, baya
cikin falo dan haka tawuce ciki, akan gado ta hangoshi zaune yana daddanna
wayarshi,

"Mami tace kana kirana, gani.."

"Zo..."

Karasawa tayi gaban gadon ta tsaya batare data kalleshiba tun bayan kallon farko da
tayi masa saboda daga shi sai gajeren wando da farar vest iya shaddar da yasaka
kawai yacire,

Hannunshi ya mika ya kamo nata ya fisgota da karfi, babu zato tajita tafada kanshi,
matseta yayi yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi, sam baya gajiya da
lalubarta dan haka nan take yafara,

Duk da tana dan fushi dashi amma hakan baisata juya masa baya ba,soyayya ya nuna
mata sosai ita har mamakinshi ma tayi,

"Baby wallahi bana gajiya dake,kefa kina gajiya dani...?"

Shiru tayi masa ta dauke kanta cikeda kunya,

Hancinshi yagoga ajikin nata,

"Uhm...?"

Shirun tasake yimasa, hancinta yaja tareda lakuce mata shi yana murmushi,

"Bacci nake son ki dan tayani baby zuwa anjima sai kitafi wurin mamin ko?"

Bai jira amsarta ba ya rungumeta tsam tsam ajikinshi yana shafa sumar kanta wacce
tasha gyaran saloon......

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_DEDICATED TO MISS XOXO_


*51*

***Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi,

"Ina sauraronka ya yusleem"

"Hakuri zan baki akan rashin baki hakkinki da banayi wannan yana faruwane bisa
umarnin da likita yabani saboda har yanzu akwai sauran bacteria atare dani so idan
nace zan baki hakkinki to zan iya cutar dake ta hanyar maidaki victim, shiyasa nake
mai baki hakuri da kikara dan bani lokaci har zuwa time din da zan koma Cairo naga
likita nasan insha Allah lokacin komai yazama normal ina dawowa abinda zan fara yi
shine insauke hakkinki inbaki kayanki..."

Juya masa baya tayi cikeda kunya tana murmushi saboda ita dataji yace zasuyi magana
a tunaninta wata muhimmiyar magana ce ashe wai wannan zai sanar da ita,

Rungumeta ta baya yayi hancinsa yana shakar daddadan kamshinta,

"Banji kince komai ba Nana hafsa"

Jin tayi shiru yace,

"Uhm?"

"To yaya yusleem me zance? Ni wallahi nazaci wata muhimmiyar magana zaka fada ashe
wannan zakace.."

"Wannan ba muhimmiya bace? Wannan maganar ai ni aganina tafi kowacce magana da zan
fada miki ayanzu"

"Ni bahaka bane gaskiya"

Murmushi yayi ya juyo da ita,

"Tsakaninki da Allah bakya son inbaki hakkinki?"

Zame jikinta tayi zata fita daga cikin dakin yasake rikota,

"Ai babu inda zakije sai kin amsa min tambayar da nayi miki"

"Kai yaya yusleem, nifa yunwa nakeji"

"Ehh zakice min ko a'a"

"To ehh"

"Ohh dagaske bakya so din kenan ko? Shikenan to bari Indaina wahalar da kaina na
sai nasamu lafiya, basai nakoma Cairo dinba sai kawai inzauna muci gaba da zamanmu
haka"

Dasauri ta dago ta kalleshi bayan ta zaro idanuwa,


"Haba ya yusleem, haka zaka yita zama da cuta ajikinka?"

Murmushi yayi yaja hancinta,

"Dama ashe karya kike ba gaskiya kika fada ba"

"Nifa ba wannan nake nufiba"

"Ai nariga da nagane wayonki"

"Allah ya yusleem ni bahaka nake nufi ba"

"To naji, ke bakya bukatata kenan?"

Kwacewa tayi daga jikinshi tajuya tana bubbuga kafa, "nidai Allah yaya yusleem
kabari"

"Shikenan nabari amma gaskiya ni kullum acikin bukatarki nake"

Hannayenta tasa tarufe fuskarta taki juyowa,

"Tunda ni ba a bukatata bari natafi.."

Juyawa yayi zai fita tabi bayanshi,

Tea tahada masa sannan tazuba mishi sauran kayan soye soyen wanda aka tanada dan
karin kumallo,

Har yagama karyawa mami bata fito ba, kallon hafsa yayi,

"Nabar hulata adakinki, jeki dauko min"

Tashi tayi tanufi cikin dakin taje ta dauko hular tadawo,

Hannu ya mika zai karba ta hanashi,

"Zan gwada sa makane ingani ko na iya"

"Tom gwada ingani..."

Wayarshi yazaro saboda jin yar tsuwwarta daga cikin aljihunsa, ganin alh musa mori
ne yasashi saurin dagawa, saka masa hular tayi tazaro turaren data boyo tasoma fesa
masa ajikinshi, hannunta yarike bayan tagama fesa masa turaren yajata kan
cinyarshi, kokarin kissing dinta yake duk da bai gama yin wayar ba, kanta ta ajiye
akan kafadarshi tana shafa kasumbarshi, hannun yarike yakai bakinshi,

Zumbur ta mike daga kan cinyarshi saboda jiyo maganar mami da tayi tana kokarin
fitowa daga bedroom wanda da alama waya take yi,

Akan kujera tazauna itama mami tazo ta zauna har lokacin bata gama wayarba, saida
yusleem yajira tagama sannan yagaidata yafita yana yiwa hafsa wani kallo, "adawo
lafiya" tafada ahankali wanda shi kadaine yaji, binshi da kallo hafsa tayi har
yafice daga cikin falon.

Acikin mota yazauna yana kallon fuskarshi tajikin mirror, hular da hafsa tasaka
mishi yake kallo domin ba karamin kyau yayi ba, tada motar yayi fuskarshi kunshe da
murmushi har yaje gidan alh musa,

Kamar jiya yauma hafsa yar gidan alh musa tana tsaye asaman upstairs awani dan
corridor tana jiran ganin zuwan yusleem cikin sa'a kuwa saiga motarshi ta kunno
kai, murmushi tayi lokacin da taga yafito daga cikin motar yana duba agogon dake
daure a hannunshi,

"Fine boy" tafada ahankali tana kallonshi, bata iya dauke idonta daga kanshiba har
saida taga kulewarshi sannan ta nufi hanyar saukowa.

Kamar jiya yauma yusleem afalon alh musa ya sameshi yazauna bayan sun gaisa, tashi
alh musan yayi yashiga ciki yabar yusleem zaune afalon,

Hafsa ce tashigo dauke da wani kyakkyawan faranti sai fitinannen kamshine ke fita
daga jikinta,

Doguwar riga tasa ja mai gajeren hannu tayafa dan karamin bakin mayafi akanta,

Agaban yusleem ta ajiye abincin,

"Ina kwana...?"

"Lafiya lau, yagida"

"Alhamdulillah,bismillah ga abinci"

"Alhamdulillah"

"Haba dai, dan Allah kaci ko babu yawa, please" ta karashe maganar kamar zatayi
kuka,

"Ok to nagode"

Juyawa tayi tafita baiyi niyyar cin komai ba amma yahada coffee yasha yana gamawa
alh musa na fitowa dan haka babu bata lokaci suka dunguma suka fita.

Karfe 8 nadare suka dawo domin daga yau sun gama zagayen da yakamata suyi saboda
duk inda ya dace suje sunje kuma yusleem zai fara fita aiki nanda sati mai zuwa
domin alh musa ya gabatar dashi,

Gaba daya hankalin yusleem yayi gida saboda yau wuni guda baiga hafsanshi ba dan
haka suna dawowa yaso tafiya gida amma alh musa yahana yace sai sunyi dinner haka
ya zauna ba don yasoba, hafsa ce takawo abincin yanzu blue din doguwar rigace
ajikinta da dan mayafi, tuwon semo miyar ogu ta kawo musu,

Filet ta dauka ta zuzzuba musu sannan tafita, kadan yusleem yaci yayiwa alh musa
sallama yafita,

Abin mamaki koda yaje motarshi saiyaga tayoyin gaba daya sun sace babu iska motar
tayi kasa, tsayawa yayi yana duban motar cikeda mamaki,

"Ya yusleem lafiya kuwa?" Yajiyo zazzakar muryarta daga bayanshi,juyawa yayi ya
kalleta,

"Lafiya lau, tayoyin motar ne suka sace..."

"Ayya to yanzu ya za ayi? Gashi dare yayi balle inkira maka bakanike dinmu.."

"Ah babu damuwa bari kawai zanje insamu keke napep so gobe sai nazo da bakanike"
"A'a kabari inyi dropping dinka mana ko kuma inbaka motata sai katafi da ita gobe
ka Kawo min"

"Karki damu babu komai"

"A'a wallahi gaskiya bazaka hau keke napep ba da daren nan,ka karbi motata dan
Allah katafi da ita, haba mana ya yusleem yaushe da ajinka da komai zaka wani tafi
a keke napep..."

Tsayawa yayi yana kallonta yanda ta tubure sai yatafi da motarta, shi abinma dayafi
bashi mamaki yanda akayi ta rike sunanshi tamau abakinta tamkar itace ta rada mushi
ga wata shagwaba da take yimasa,

"Ya yusleem please say something.."

"Am ina ganin basai na karbi mot...

"Please ya yusleem don't say bazaka karbi motata ba, please ban son wani abu yafaru
dakai"

Daga mata kai yayi alamun takawo key din, juyawa tayi zuwa cikin gida mintuna kadan
sai gata tafito, yana tsaye yana bin tangamemen tsakar gidan da kallo wanda ya
wadatu da shuke shuke da hasken fitilu kamar rana,

"Gashi" ta mika masa tareda dan rissinawa, karba yayi yana jiran ta nuna mishi
motar,

"Ga motar can, the last one din"

Parking space din yaje wanda ke dankare da lafiyayyun motoci hadaddu, takarshen ya
bude kamar yadda tafada, ash colour ce motar kirar Mercedes Benz mai bakaken
glass,shiga yayi yabawa motar wuta ya fito, tana tsaye tana kallonshi har yazo
saitinta, kasa yayi da tintac glass din yaleko,

"Nagode sai goben, thank you"

"Don't mention it, Allah yakaimu"

Sai da taga fitarshi daga cikin gidan sannan tanufi ciki cikeda murna domin dama
tana neman hanyar da zata samu tayi magana dashi sai gashi tasamu cikin sauki....

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

_Fatan alkhairi ga kawata Billy Galadanchi ina mutukar yinki..._

*52*

***K'arfe 8:30 yusleem yashiga cikin gidansu daidai lokacin da yashiga


yahango hafsat itada khadija suna tsaye jikin motar khadijan suna hira,

Fitowa yayi hannunshi rikeda robar ruwa, jikinshi gaba daya ya kamu da daddadan
kamshin dake cikin motar Hafsat domin wani irin fitinannen kamshi ne shi ba turaren
wuta ba shi ba perfume spray ba,

Ganin yusleem yasa hafsa jin mamaki domin a iya saninta yanzu basuda mota irin
wannan,

Wani kallo khadija tabishi dashi lokacin da yazo daidai kusa dasu, gaisheshi tayi
ya amsa batare da yatsaya ba bare ya kalli inda take, dan jijjiga kai tayi tana
mamakin takamarshi domin har yanzu wannan jijji da kan nashi yana nan bai sauka ba
saima karuwa da yasake yi,

Sallama sukayi tatafi ita kuma hafsat tawuce ciki, a bakin kofa taganshi tsaye da
alama ita yake jira, tana zuwa kusa dashi taji ya rungumeta, kissing dinta yafara
yi,

"Ya yusleem daga dawowa?"

"Ehh mana barka da dawowa nake baki ko bakya so?"

Murmushi tayi tarufe fuskarta, hannunshi yasakala a kugunta yana fuskantarta,

"Yau wuni guda ban gankiba, ke amma babu ruwanki ko, ko ma damuwa bakiyi ba"

"To ai nasan duk acikin aikine, naganka ma da sabuwar mota tawaye?"

Shiru yayi yarasa amsar da zai bata domin yasan idan yafada mata gaskiyar abinda
yafaru kila za a iya samun matsala,

"Uhm yaya yusleem?" Tafada tana wasa da clips din dake jikin rigarshi,

"Motar gidan alh musa ce na aro saboda ta mamin da naje da ita tayoyinta sun
sace.."

Murmushi yaga tayi tareda jan dogon hancinshi abinda bata taba yiba,
"Ban yarda dakaiba" shine abinda tace tareda kokarin tafiya, sake kankameta yayi
yana sinsina wuyanta,

"Duniya tazo karshe tunda gashi hafsa tafara karyata ni"

Dariya ce tazo mata saboda jin abinda yace

"Ni ban isa inkaryata yaya yusleem ba, yanzu ni duk bama wannan ba zo muje kayi
wanka sai kafito kaci abinci"

Jin abinda tace yasashi dan murmusawa,

"Yawwa Nana hafsa na, zo muje tare to"

Tana makale ajikinshi suka nufi part din su Abdul, suna zuwa balcony yayi sama da
ita yabude part din suka shiga, har cikin bedroom yaje da ita ahaka, asaman gado ya
ajiyeta tareda binta,

"Gaskiya wata yarinya tafara nauyi, mami tana bata abinci tana koshi"

Murmushi tayi tashafo kanshi wanda ke kwance bisa kirjinta,

"Kuma kaga ko rabinka banyi ba fa"

"Ahh karya kike da ace akwai scale da angwada"

"To agwada"

"To agwada mana" yafada tareda dago kanshi yana kallon fuskarta,

"Tayaya?" Ta tambayeshi,

"Zamuje agwada kibari sai nasamu lokaci, yanzu tashi ki hada min ruwan wankan..."

Tayar da ita zaune yayi tashiga cikin bathroom shikuma yasoma cire agogon
hannunshi, fitowa tayi tasameshi tsaye yana jiranta bayan tahada mishi ruwan,

"Sauranki cire wannan.." Yayi maganar yana nuna mata kayan jikinshi, kunya taji ta
kamata domin bata taba cire mishi kayaba amma saita daure, clips din rigarshi
tasoma cirewa nan taji ya matseta ajikinshi har suna jiyo bugun zuciyar junansu,

"Yaya yusleem easy mana.."

Sassauta rikon da yai mata yayi,cire mishi kayan tayi tabarshi da na ciki kadai.

Ahankali taji yafara zuge zip din dake jikin rigarta,saurin kallonshi tayi,

"Lafiya?"

Langabar da kanshi yayi,

"Tare zamuyi dan Allah karkice a'a"

Kasa tayi da kanta nan ya kinkimeta yayi cikin bathroom din da ita, duk jinta tayi
atakure saboda sam bata shiryawa wankan ba shiyasa abin yazo mata kwatsam,

Dadewar da sukayi acikin bathroom din ba kadan bace daga karshe dai shine yarigata
fitowa yazo yatsaya agaban mudubi yafara goge sumar kanshi da dan karamin towel,
Yana cikin shafa turare yahangota tana fitowa,sunkuyar da kanshi yayi yana murmushi
yaci gaba da bulbulawa jikinshi turare domin shi arayuwarsa yana tsananin son
kamshi ko nawane zai iya kashewa ya siyi turare komai tsadarshi,

Ji tayi gaba daya dakin ya kaure da kamshin turarukan da yake shafawa wanda
yawancinsu oil ne masu karfi,

Ta gefenshi tabi ta dauki turaren zata shafa,

"To kinga ai na taimaka miki kinyi wanka yanzu kina zuwa sai dai kawai kisa kayan
bacci ki kwanta"

Turo baki tayi tana harararshi, kunnenshi guda daya ya kama,

"Nadauki laifin, yi hakuri..."

Murmushi tayi batace komaiba har ta gama shiryawa tasa kayanta, koriyar t shirt
yasa da boxer, ba karamin kyau taga yayiba wanda harta shagala tana kallonsa bata
saniba, hure mata ido yayi da bakinshi,

"Ko wankan bai isheki ba akara wani?"

Makale kafada tayi,

"Kyau kamin"

"Kema haka"

"Nagode"

Murmushi yayi bai bata amsaba illa kama hannunta da yayi suka tasamma kofar fita,
shirun itama tayi aranta tana jin wani irin babban lamari agame dashi, jin har suka
fita baiyi magana yasata fahimtar yan miskilanci nashi sun motsa,

Har saida sukaje cikin part din mami sannan yayi magana,

"Zo inji cikinki kinci abinci kuwa?"

Zame hannunta tayi tagudu tarigashi shiga cikin falon,

Mami nazaune tana cin tuwon shinkafa miyar lalo,

"Yau hira tayi muku dadi keda khadija, sai yanzu tatafi?" Mami tace tana murmushi,

"Ehh mami.."

"Mami karya take tun dazu khadija tatafi" yusleem yafada lokacin da yake
shigowa,harararshi hafsat tayi ita kuma mami tace,

"Kajishi ko taya yasani shida baya nan"

Murmushi hafsa tayi gamida yimasa gwalo,

Tuwon hafsa tazuba yazo yazauna akusa da ita yasa hannu aciki, duk da tasan sun
saba cin abinci tare amma saida taji kunyar mami sai dai ita mamin babu ruwanta
bata ma san sunayi ba domin ta maida hankakinta akan labaran da take kallo atashar
NTA hausa.
Hafsat tariga kowa tashi daga falon saboda ciwon da taji cikinta yanayi, kwanciya
taje tayi acikin bedroom,

Daga mami har yusleem babu wanda yakawo wani abu dan haka suka cigaba da hirarsu
har wani lokaci, sai wurin 10 sannan mami tashiga dakinta, saida yusleem yabari
bayan shigar mami kamar da mintuna 15 sannan shima yatashi yanufi wurin hafsa,

Akwance ya sameta dafe da cikinta zuwa mararta,

"Lafiya?"

Girgiza masa kanta tayi, "cikina ne ke ciwo"

"Da kuma mararki ko?"

Daga mishi kai tayi bayan tarufe idonta, zama yayi yadauketa yadorata ajikinshi
yasoma shasshafa mata cikin nata har zuwa mararta ahaka suka raba dare har saida
bacci yadauketa sannan ya kwantar da ita shima ya kwanta.

Washe gari tariga shi tashi har ta shirya bai tashiba,

Tana tsaka da fesa turare ya bude idonshi ya kalleta,

"Har kin tashi? Marar taki tadaina ciwo?"

Kai ta daga mishi, "tadaina, naji sauki"

"Har yazo kenan"

Shiru tayi masa,

"Zo inji kamshin wannan turaren saboda wallahi kamshinne yatada ni..."

Ajiye turaren tayi takarasa kusa dashi, cusa fuskarshi yayi ajikinta har na tsawon
wani lokaci, dakyar yabarta yatashi yafita,shiryawa yaje yayi yafito yazo tabashi
breakfast yaci wanda kusan ma tare suka ci, zama yayi suka fara yin game din temple
run awayarshi, saida yajira mami tafito suka gaisa sannan tarakashi zai tafi,motar
yabude yashiga bayan yaja hancinta, ramawa itama tayi ta hanyar jan nashi, zama
yayi acikin motar yasauke glass yana kallonta, leka cikin motar tayi nan tahango
takalmin mata mai tsini ajiye akan kujerar gaba,

Dauke kanta tayi ta daga mishi hannu yaja motar yafice, tunda taga wannan takalmin
sai kuma taji hankalinta yakasa kwanciya, wani irin zafi takeji acikin zuciyarta,
da wannan takalmin tawuni aranta.

Yusleem kuwa lokacin da yaje gidan alh musa mori samu yayi har angyara mishi
tayoyin motarsa an wanke motar tas sai wani sheki takeyi, packing yayi yafito yana
kokarin rufe motar yasoma jiyo takun tahowar hafsat domin dama tana tsaye tana
sauraren zuwanshi, juyawa yayi,tana sanye da bakar doguwar riga da dan mayafi kamar
kullum wannan fitinannen kamshin nata yana yawo acikin iska,

"Barka da zuwa ya yusleem"

Dan murmushin yak'e yayi, "yawwa, ga motar nagode fa,thank you"

Karbar key din tayi ta dan shagwabe fuska,

"Ni ya yusleem kadaina yimin godiya dan Allah, saikace wanda nayi maka wani babban
abu?"
Murmushi yayi yajuya yafara tafiya,

"Duk da haka nagode"

Tsayawa tayi tana kallon yanda yake tafiya yasa hannunshi guda daya cikin aljihun
wandonshi, akan idonta yashige cikin sashen Alh musa mori....

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*


_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*53*

***Tsaye tayi tana kallonsa da murmushi akan fuskarta,har ya bacewa ganinta


bata iya yin kwakkwaran motsiba,

Tana nan atsaye har yafito daga sashen mahaifin nata sai lokacin ta dauke idonta
daga kallon kofa tamayar kan kyakkyawar silbebiyar wayar dake rike a hannunta,

Har ya nufi motarshi sai yafasa yanufi wurinta,

"Sai yanzu nakula ashe ma angyara min tayoyin..."

Batare da ta dago ta kalleshi ba tayi magana cikin aji da yauki,

"Uhm karka damu.."

"To nagode, bari naje"

"Am bakaji ba, phone number dinka nake so saboda wata rana"

Murmushi yayi, "babu damuwa"

Wayarta ta mika masa ya amsa ya rubuta mata sannan ya wuce, motarshi ya dauka wacce
keta faman tashin daddadan abin kamshin da aka saka aciki,

Kansa tsaye banki yawuce wanda kusan acanma yau yabata lokaci domin sai bayan
sallar azahar sannan yagama dasu, duk wasu kudadensa wadanda ke hannun alh musa
ayau yaturo masa kayanshi sannan zai mallaka masa takardun gonakinsu da na filaye,

K'arfe uku da yan mintuna ya koma gida, iya mami kadai ya tarar afalo tana
kishingide tana hutawa, samun wuri yayi yazauna cikeda alamun gajiya atare dashi,

"Ya akayi naganka duk kayi la'asar?" Inji mami,

"Mami wallahi nidinne agajiye nake, yanzu haka daga banki nake"

"Sannu, bari akawo maka abinci"

"To mami, ina yar taki tayi naji banji motsinta ba?"

Dan murmushi mami tayi bayan ta tashi domin Kawo masa abinci,

"Tana ciki inajin bacci ma take yi"

"Lallai tana hutawa"

Murmushi mami tayi bata sake magana ba tawuce dining area ta zubo masa abinci ta
Kawo masa, fried rice with chicken salad sai coconut juice mai dan banzan sanyi,

Diban abincin yayi acikin filet ya nufi cikin bedroom din hafsa, tana kwance akan
gado tana bacci, agefenta ya zauna yaja babban yasanta na kafa,

Har yagama cin abincin bata motsa ba, yana shirin ja mata hanci yaga tana kokarin
yin juyi, riketa yayi nan ta bude idonta ta ganshi,

"A'a yaushe ka dawo?"

"Tunda jimawa, nazo kinata bacci"

Murmushi tayi ta mika masa hannunta yarike ta tashi zaune,

"Yau kadawo da wuri"

"To ai yawon yau bai kai najiya ba"

Murmushi tayi tai shiru saboda tarasa ta inda zata fara,

Ji tayi ya matsa gareta sosai,

"Sai naga kamar akwai abinda kike son fada,hakane?"

Murmushi tayi,

"Hakane amma bana son fada yanzu"

"Saboda me?"

"Saboda kar ka ga kamar banda juriya"

Murmushi yayi yasa hannuwanshi duka ya tallafo kumatunta,

"Bazan yi wannan tunaninba dan haka karki ji tsoron komai fada min"
Shiru tayi tasaki fuskarta ta kawatata da murmushi,

"Dama cewa zanyi har ka mayar mata da motar tata?"

Dan dam yayi jin abinda tace, cikeda mamaki ya kalleta,

"Wacece?"

"Ita wadda ta baka aron motar mana"

Murmushi yayi yasake matsarta,

"Kece kika santa amma nidai ban san wata mai bada aron motaba"

"Ohh dama nima hasashe nayi saboda naga takalminta aciki shiyasa nazaci ko..."

"Ko me? Ni ban san motar ko ta macene ko ta namiji ba saboda nidai kawai bani aro
akayi"

Murmushi tayi ta kalleshi,

"To shikenan magana tawuce,kuma har hankalina ya kwanta"

Murmushin shima yayi ya kalleta yana nazarin maganganunta duk da bata fito fili ta
fada ma amma yafahimci kishi ne fal zuciyarta saboda takalmin hafsat dataga acikin
motar,

"Yanaji kayi shiru?"

"A'a babu komai, kawai dai tunanin fara fita aiki inbarki ke daya nake"

Murmushi tayi, "to basai muna tafiya tare ba"

"Hakama za ayi"

"Ko?" Tace tana murmushi,

"Ehh mana"

Zamewa tayi zata kwanta ya riketa ya langabe Kai, babu yanda ta iya dole sai tare
suka kwanta.

Acikin yan kwanakin ya dauketa suka fita ta zazzabo masa kayan sawa nafita office
tun daga kan kananan kaya, suit, shaddodi,yadika da takalma, banda turaruka da
sauran kayan bukata,

Cikin lokaci kankani yusleem yadawo yusleem dinshi na ainihi dan gaye mai ji da
kwalisa,

Wata Lafiyayyiyar mota sabuwa mai tsada yasa aka Kawo masa yasiya saboda zuwa
office,

Ranar Monday yafara fita bayan mami da hafsa sunyi masa addu'o'i masu tarin yawa,
ciki suka koma bayan sunga tafiyarshi, laptop dinshi hafsat tadauka wacce yabar
mata aro tayi game domin debe kewa kafin yadawo,

Tana cikin bedroom azaune tana yin game din wizo taji sallamar khadija,da murna
tatareta domin yanzu khadija yar gidace ba bakuwa ba nan suka bude babin hira har
hafsat ke sanar da khadija yusleem yafita office,

K'arfe 3 hafsa tashiga kitchen da kanta ta hadawa yusleem abinci, shinkafa da salad
da miyar dafaffen kwai,

Shirya masa abincin tayi akan table taje tayi wanka tafito tashirya bayan ta hade
jikinta da turaruka masu kamshi,doguwar riga ta atamfa tasa wacce ta tsuke daga
kirji sannan ta baje daga kasa,

Yusleem bai samu dawowa gidanba sai karfe 5:30,tana tsaye cikin falo taji kamshin
turarensa, cikin nutsuwa da jan hankali tajuya ta kalleshi tana yimasa murmushi,
shi dinma murmushin ya aika mata dashi,dauke kanta tayi taci gaba da abinda takeyi
har ya karaso kusa da ita, kafadarshi yasa ya bugi tata,

"Babu sannu da zuwa baby nanah..?"

Murmushi tayi ta dubeshi,

"Da akwai mana, sannu da zuwa..."

Hular kanshi yacire yana shafa sumarshi,

"Mami fa?"

"Yanzu tafita, baku haduba?"

"A'a bamu haduba, kuma naji dadin jin hakan domin ko babu komai zan dan sake da ke
before tadawo, kima fara shiri mun kusa barin gidan nan.."

"Ko zamu bari amma ai kabari kaje Cairo kadawo tukunna ko?"

Murmushi yayi ya lakuce mata hanci,

"Kafin sannan dinma inada bukatar kasancewar mu mubiyu.."

Kawar da zancen tayi ta hanyar fadin,

"To zo muje kayi wanka sai kazo kaci abinci..."

Bai musa mataba yabi bayanta suka nufi part din da yake, itace ta taimaka masa yayi
wanka yashirya cikin kananan kaya bakar t shirt round neck da bakin boxer,part din
mami suka koma tazuba mishi abinci tasoma bashi abaki, hannunta yarike cikin nashi
yana yin wasa dashi domin har acikin ranshi yana yaba irin kulawar da take bashi
batare da nuna gajiyawa ba,

"Baka bani labarin office ba"

Hadiye abincin dake bakinshi yayi,

"Zan baki amma ba yanzu ba sai dare yayi idan munzo yin bacci"

"Kai wai ya yusleem baka da magana sai ta dare"

"To ai lokacin ne nafi samun nutsuwa"

Kawar da kanta tayi ta ci gaba da bashi abincin har ya koshi nan kuma ya kinkimeta
ya dorata bisa cinyarshi suka fara buga game,

"Meyasa aka yimiki wannan zip din tabaya? Arinka yimiki tagaba.."
Hannunshi tarike cikeda kunya,

"Ta gaba kuma sai kace wata mai shayarwa..."

Dariya yadanyi ya hade hannuwanshi da nata,

Ahaka mami ta dawo ta iskesu, bayan sallar magrib yakirata wai ta rakashi unguwa, a
motarshi suka fita domin zaga gari kawai, basu suka koma gidaba sai 9, kullum haka
ce take faruwa kamar doka sai sun fita yawon zaga gari da daddare,

Tuni cikin kankanin lokaci harkokinshi suka soma mikawa suna hababbaka, alh musa
kuwa ya maidashi tamkar mahaifinshi domin har mami yadauka taje ta gaidashi, kusan
kullum sai yaje gidan saboda yazama tamkar dan gida, hafsa kuwa akullum da
tunaninsa take wuni take kwana saboda zuciyarta da ruhinta sun yaba dashi kuma sun
aminta da nagartarsa,

Yau kam kasa daurewa tayi dan haka ta kuduri aniyar sanar dashi sirrin dake cikin
zuciyarta wanda ya jima yana azabtar da ita,

Waya tayi mishi tace abbanta na son ganinshi domin yau throughout baizo gidan ba,
cemata yayi gashi nan zuwa nanda 20 minutes, cikin sauri tafada bedroom dinta
tasoma shirin tarbarshi.....

_Fatan alkhairi ga Zarah B~B & Ummu Bashir, yau shafin nakune ku kadai batare da
kowa ba...._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*54*
***Sauke manyan idanuwanshi yayi masu mutukar haske akan fuskar hafsa wacce
ke zaune tana hada masa green tea,

"Yaya yusleem ina zakaje?" Ta tambayeshi tana juya tea din da spoon,

Kafarshi ya dora akan hannunta dake ajiye yadan taka ahankali,

Yar kara tasaki ta runtse idonta,

"Ahh sorry, zo mugani" yace da ita yana murmushi kasa kasa,

"Ya yusleem Allah da saninka ka takani.."

"Bada sanina bane baby nanah, zo ingani"

Tashi tayi tana yarfe hannun taje wurinshi inda yake zaune agefen gado, riko
hannunta yayi ya zaunar da ita bisa cinyarshi yakama hannun yana hurawa,

"Yi hakuri bazan sake ba"

Daga masa kai tayi,

"Ina zakaje? Naji kamar kana yin waya kana zaka fita"

"Ehh ba jimawa zanyiba, gidan alh musa zanje, yau banje na gaidashi ba shine yake
nemana"

"Zan bika..."

Murmushi yayi yasoma shafa bayanta,

"Ai nima ba jimawa zanyiba, yanzun nan zaki ganni nadawo"

Makale kafada tayi,

"Nidai ban yarda ba zan bika"

"Kai nanah irin wannan rigima haka, ashe kema rigimammiya ce"

"To kace zakaje dani"

"Bazaki bani tea din bane insha sai yahuce?"

"Lahh mantawa nayi..." Zumbur tayi taje ta dauko masa tea din takawo tazauna a inda
tatashi, abaki tarinka bashi yana sha har ya shanye,

Wata mika yayi sannan yasauke idanuwanshi akanta,

"Ga lafiya iya lafiya ga karfi amma sai dai inyita kallonki..."

Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi,

"Bawani kallona da kakeyi bayan akwai abunda kake y..."

"Wannan ma ai sake takurani yake idan baki saniba... Danke fa nakeyi, tsaya ma
yanzu..."
Yunkurin tashi tagudu tayi yayi saurin riketa yana dariya,

"Daga magana sai gudu?" Yayi maganar yana shafa cikinta daga nan yafara yimata
cakulkuli babu shiri tafara dariya tana kokarin kwacewa,

Tashi yayi da ita ajikinsa ya isa gaban drewar, ajiyeta yayi,

"Canja min kaya saboda wannan sunyi kananu da yawa bazan iya zuwa dasu ba"

Wata ash colour din shadda sabuwa fil ta ciro masa, tayashi sakawa tayi taciro masa
hula tasa masa, gaban mirror sukaje ta dauki turare ta fesa masa,

"Irin wannan kwalliya haka baby nanah kamar mai shirin zuwa zance?" Yafada yana
rungume da ita agefen jikinshi bayan ya kalli mudubi,

"Ina sone duk inda mijina yaje arinka jin yana kamshi kuma aganshi fes fes, nafi
son kafi kowanne namiji kyau da kwalliya.."

Murmushi yayi ya manna mata kiss a goshinta,

"Allah yayi miki albarka, Allah yasaka miki da gidan aljanna"

"Amin,muje katafi karka yi dare, dan Allah karka juma"

Sake rungumeta yayi suka fita, har gaban motarshi ta rakashi, saida taga fitarshi
sannan ta juya takoma cikin gida.

Yana driving ahankali yana wani tunani acikin zuciyarsa,

Kome yatuna oho sai kawai yadan saki murmushi, yau jinsa yake acikin farin ciki
banda nishadin da yake ciki,

Kamar koda yaushe yauma kansa tsaye yatura hancin motarsa cikin gidan yanufi
parking space, saida yadan jima acikin motar sannan yabude kofa yafito yana fitowa
yashaki daddadan kamshinta wanda ya yakawowa harabar wurin sumame babu bata lokaci
ko ina yadauka,

Ahankali take takowa Kwas kwas cikin takunta na hamshakan mata masu ji da aji,

"Barka da zuwa jarumin maza..." Tafada daidai lokacin data karaso gab dashi,

Dan bude lumsassun idanuwanshi yayi ya kalleta, yau wani kyakkyawan leshi purple
colour tasa dinkin riga da skirt ta yafa purple din mayafi marar nauyi atakaice dai
irin shigarsu tayi ta yaran masu kudi,

"Waye yace miki ni jarumi ne?..." Yace da ita yana kokarin rufe motarshi,

"Ai basai anfada minba domin zan iya tabbatar da hakan batare da wani yafada ba..."

Murmushi yayi yajingina ajikin motar ya zuba hannuwanshi cikin aljihun rigarshi,

"To yau dai na fuskanci tsokana kikeso.."

"Ko daya bahaka bane, gaskiyata dai nafada maka.."

Dan murmushi yayi,

"To yagida lafiya?"


"Lafiya lau, ya aiki?"

"Aiki babu dadi hafsat"

"To ko zaka kawo intayaka?"

Murmushi yasakeyi ya kalleta,

"Me zai hana idan har zaki iya"

"Zan iya mana, ka kawo kagani"

"To shikenan, yanzu dai bari inshiga wurin abba saboda naga idan nabiyeki anan zan
bata lokaci"

"To ai abban baya nan, yau baima wuni agari ba..." Tafada tana danyi masa dariya,

"Amma da ai kece kika fada min yana nan"

"To ai son ganinka nake yi kuma nasan idan ba hakan nayiba yau bazan samu ganinka
ba bayan kuma ni zuciyata bazata iya jurewa ba"

Idanuwa yazuba mata yana kallonta tsawon mintuna biyu yayinda ita kuma ta sunkuyar
da kanta tana wasa da zobunan gold din dake sanye cikin yan yatsunta.

Saida ya sauke ajiyar zuciya sannan yayi magana,

"Sai dai kuma hafsa ban gane abinda kike nufiba.."

Kunyace ta dan kamata har tasa mayafinta ta rufe gefen fuskarta,

"Wallahi har cikin zuciyata naji kana burgeni tun farkon ganin da nayi maka wannan
dalilinne ma yasa na kuduri niyyar baka amanar zuciyata.."

Bugun da zuciyarsa keyi yaji ya tsananta batare da yasan dalili ba,

Kafin yayi mata magana wayarshi dake cikin aljihunsa tafara kara, zarota yayi nan
yaga hafsat ce,

Cikin sanyin murya ya daga,

"Hello baby ya akayi?"

"Ya yusleem kaje lafiya?" Hafsat tafada daga can bangaren,

"Lafiya lau, yagidan"

"Lafiya, dama mami ce tace ka taho mata da maganin tari idan zaka dawo, nima kuma
ina son ka taho min da maganin ciwon mara"

"Toh, dama har yanzu baki warware ba amma kika ki fada min?"

"Saura kadan amma naji sauki, sai kadawo dai"

"Korata kike yi hafsat?"

Jin yakira hafsat yasa hafsat din dake tsaye kusa dashi tayi saurin dagowa ta
kalleshi,
"A'a ba korarka nakeyi ba, sai kadawo dai"

"Toh sai nadawo"

Katse wayar yayi ya maida cikin aljihu yayinda hafsat tunani fal yacika zuciyarta
banda tarin tambayoyin dake ta faman kai kawo acikin kwakwalwarta,

"Wannan hafsat din da yusleem yakira wacece ita? Meye alakarshi da ita? Wanne
matsayine da ita awurinsa? Sonta yake? ...." Wadannan tambayoyin su taketa jerowa
acikin ranta har maganar yusleem takatse mata tunani,

"Hafsat am..., bawai fahimtarki ne banyiba, na fahimci abinda kike nufi sannan kuma
babu wani namijin da zai ki karbarki a matsayin matarsa, sai dai kuma ni ahalin
yanzu inada mata..."

Dagowa tayi da sauri ta kalleshi idanuwanta jajur,

Girgiza mata kai yayi alamun sake jaddada mata abinda yafada,

"Inada mata hafsat, sunanta hafsat"

"To ni yanzu menene makomata da matsayina agareka? Baka sona? Baka kaunata? Bazaka
aureni ba?..."

Batare da tajira amsar tambayoyin da tayi masa ba takwasa gudu gudu sauri sauri ta
nufi cikin gida, tana jinshi yana kiranta amma bata tsaya ba,

Yajima tsaye awurin kafin yashiga motarsa jikinsa asanyaye yafita daga gidan, tukin
ma kawai yana yinsa ne cikin wani irin yanayi wanda shi kansa bai san abinda ke
damunsa ba, a wani chemist ya tsaya yasaiwa su mami magungunan da suka bashi sako
sannan yawuce gida,

Kasancewar mami bata jin dadi mura tasakota agaba shiyasa lokacin da yakoma gida
bai sameta afalo ba iya hafsat kadai yatarar tana zaune tana kallon wani Indian
film kites,

Jiki asabule yazauna akusa da ita ya mika mata maganin ta karba tana kallonsa bayan
tahada ledar maganin da hannunsa ta ruke,

Jingina da jikinta yayi ya ajiye kansa bisa kafadarta......

_Gaisuwa mai tarin yawa ga besty na Phertymarh Xarah._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*55*

***Hular kanshi ta cire tasoma shafa sumarshi ahankali, dan lumlumshe ido
yafara yana sake nanuka jikinta domin wani kamshine yake fusgarsa,

"Yaya yusleem lafiya kuwa?" Tace dashi tana rike hannunshi,

"Lafiya lau baby, kamshinki ne yake neman tada min da hankali..."

Saurin juyowa tayi ta kalleshi,

"Meyayi? Ko kamshinsa ne baiyi maka ba?"

Murmushi yayi yadafa kafadarta,

"Easy, ba abinda nake nufi kenanba, tsananin dadin kamshinshi ne ke neman juyar min
da kwakwalwa..."

Murmushi tayi ta tureshi ta tashi tanufi dakin mami domin kai mata maganin da
yasiyo mata,

Mintuna kadan tafito ta dauki ruwa roba daya tasake komawa, wannan karon ta dan
jima sannan tafito, amike taganshi kwance kan doguwar kujera,

Durkusawa tayi akasa ta dora hannuwanta ajikin kujerar,

"Ba yanzu zaka shiga ka kwanta ba?"

Hannuwanta duka ya riko yajata kan ruwan cikinshi,

"Gani nayi kinje wurin mami kinyi zamanki shiyasa na kwanta anan..."

"To ba gashi nafito ba"

Yana kokarin kai hannunta guda daya bakinshi mami tafito,

Tashi hafsat tayi gaba daya kunya tagama lullubeta domin tasan mami tagansu, sum
sum tawuce cikin bedroom batare da tayi magana ba,

Zaune yatashi yana kallon mami wacce tawuce dining area batare da ta kalli wurin da
yakeba,
Handset dinta yaga ta dauko wanda da alama mantata tayi awurin,

"Sannu mami, yajikin naki"

"Yawwa sannu, dasauki"

Mami tace dashi tareda wucewa bedroom dinta, yajima zaune awurin kafin ya mike ya
nufi bedroom wurin hafsat, tana gaban mirror daure da zani tana shafa wasu dadadan
turaruka, khalta maryam,da musk altahara,

Ajiye mata ledar maganinta yayi yatsaya kawai yana kallonta,

Juyawa tayi ta kalleshi itama,

"Ya yusleem ya akayi?"

Hannunta yariko cikin nashi yazauna agefen gado ya zaunar da ita ajikinshi,

"Yau basai kinsa sleeping dress ba" yarada mata acikin kunnenta, kunyace ta rufeta,
dan dukan kirjinshi tayi ahankali, ta cusa kanta agefen wuyanshi,

"Kaga dazu ma haka kasani naji kunya"

"Da nayi me?"

"Da ka sa mami tazo taganmu mana"

Mikewa yayi ya kwanta ya kwantar da ita ajikinshi yana murmushi,

"Ai ba laifina bane"

"Laifin waye?"

"Laifinki mana"

"Laifina fa kace"

Lumshe idanuwanshi yayi yana sake matseta ajikinshi,

Sun jima ahaka zuwa can bata san meya faruba sai ji tayi ya sassauta rungumar
dayayi mata yafada kogin tunani,

Kin bari yayi ta fuskanci cewar akwai abinda yake damunsa nan ya lallabata bacci ya
dauketa, kwantar da ita yayi yatashi zaune yayi shiru yana nazari,

Jin zaman ya gundureshi yasashi tashi tsaye yafara kai kawo acikin dakin, sam yau
bayajin bacci sannan yarasa dalilinsa na damuwa da lamarin hafsat yar gidan alh
musa, haka kuma yana jin wani irin abu mai kamada tausayi tausayi yana yimasa yawo
akirjinsa gameda ita,

Kukan da yaga tatafi tanayi shine yafi komai tsaya masa arai,kusanma shine
makasudin rashin baccinsa, yarasa ta inda zaibi ya bullowa wannan al'amari domin
shi dai ara'ayinsa baida niyyar kara aure, yafi son ya zauna da Hafsat ita kadai ya
nuna mata soyayyar da sauran mata basu samuba to amma kuma ita rayuwa kana nakane
Allah yana nashi kuma komai mukaddarine daga gareshi,

Bude idanuwanta tayi nan taganshi tsaye yayi shiru abisa dukkan alamu baiyi bacci
ba,
Sauka tayi ahankali daga kan gadon tanufi wurinshi, dafa kafadarshi tayi nan yayi
saurin juyowa yana kallonta,

"Ya yusleem...., meke damunka? Menene ya hanaka bacci? Tunanin mekakeyi?"

Kago murmushin dole yayi yasa tausasan yan yatsunshi ya kamo nata,

"Babu abinda nake tunani baby nah, baccin ne naji yaki daukata shine kawai nataho
nan nake dan zagayawa"

Murmushi tayi ta dan sake yin kasa da muryarta,

"Kafada min gaskiya dai, kodai?"

Murmushin shima yayi mata ya dauketa cak yanufi makwancinsu da ita,

"Kema kindai san idan nace miki bata damuna karya nake yimiki...."

Mayar da fuskarta gefe daya tayi tana murmushi aranta tana tunanin abinda zaije
yazo duk ranar da aka tabbatar masa da yagama samun lafiya domin shima taga kamar
fitinanne ne,

"Yanaji kinyi shiru?"

"Ehh bacci nake son komawa"

Mirginata yayi takoma kasa yayi pillow da kirjinta, tun tana dan shafa sumarshi har
yaji shiru alamun tayi bacci, shikam dakyar yasamu ya iya bacci cikin wannan dare.

Tunda wannan maganar ta shiga tsakaninsu da Hafsat shikenan bai sake ganinta ba
koda yaje gidan sai dai kusan kullum yana ganin massage dinta taturo mishi,

Bayan kamar sati biyu da faruwar al'amarin da wani yammaci yaje gidan bayan sun
gaisa da alh musa yafito ya hangeta tsaye jikin motarshi tana wasa da key din
motarta wanda da alama dawowarta kenan taga motarshi,

Dan hade rai yayi yanufi wurin,

Ganinshi haka yasata yin dan murmushi,

"Ya yusleem menene abin bata ran? Dama kawai tsayawa nayi mugaisa sannan in tambayi
lafiyar takwarata da na yaranta"

Batare da yasaki fuskarshi ba yace,

"Tana lafiya"

Bashi wuri tayi ta tsaya tana kallonshi bata kara maganaba yashiga motarsa yafita
daga gidan, yana cikin driving yaji karar shigowar text massage,

_Ya yusleem insha Allah sai na aureka kuma zakace nafada maka..._

Cilla wayar kan kujera yayi yaci gaba da driving dinshi bayan yagama karanta sakon.

Akasalance ya karasa gida,babu kowa afalon mami dan haka kai tsaye yawuce cikin
bedroom dinta nan dinma bata nan sai lokacin yatuna da cewar baiga motarta ba
lokacin da yashigo, dakin hafsat yawuce ita dinma bata ciki, fitowa yayi yana
tunanin to kodai tareda mamin suka fita da wannan tunanin yakarasa cikin bedroom,
Zaune yaganta tana goge mishi kananan kayanshi data wanke ta kunna laptop dinshi
tana sauraren wakar dayake muradin so wadda kusan koda yaushe sai yajita,

Tsaye yayi yana kallonta yana dan murmushi domin yasan bata san yashigo ba,

Ahankali ya sadada yarufe mata ido da hannuwanshi ai kuwa ta kurma wani uban ihu
tana salati,

Dariya ce taci karfinshi ya fada jikinta yanayi bayan ya bude mata idanuwan,

Kashe iron din tayi tahau dukanshi, hada hannayenta duka guda biyun yayi ya rike
yana yimata dariya,

"Allah ya yusleem sai nafawa mami abinda kayi..."

"Yi hakuri hafsat, ke dince kika bani dariya sosai"

"To bakaine ka tsorata ni ba"

"To kiyi hakuri, kinga anjima dama ina son ki rakani anguwa"

Fadada murmushinta tayi,

"Tom shikenan, yanzu bari inhada maka ruwan wanka idan ka shirya sai muje kaci
abinci"

"To tashi ki hada min"

Tashi tayi tashiga bathroom kafin tafito yayi sauri ya cire kayan jikinshi yabita
ciki dole sai tare sukayi suka fito tanata kumbura fuska,

"Shikenan bazan karaba tunda bakya son ladan, kiyi hakuri"

Kin kallonshi tayi yayinda shikuma ya kafeta da nashi manyan idanuwan, bai san
daliliba bakar fatarta tana yimasa kyau,

"Gaskiya koda ace mata hudu zanyi to duk bakake zan aura"

Dan harararshi tayi taci gaba da shafa masa mai,

"Kullum kuma sai kaita ganin kala daya babu canji?"

"Ehh mana ai tafi kyau"

Shiru tayi masa takarasa shiryashi takoma shirya kanta, kananan kaya yasa dark blue
din t shirt da blue din jeans iya gwiwa,

Tattarawa sukayi suka nufi part din mami lokacin tadawo tana zaune tana waya dasu
Abdul wadanda zasu dawo wani satin,

Zama sukayi takawo masa abinci yaci sannan suka yiwa mami sallama suka fita,

Ac ya kunna musu acikin motar ya rufe gaba daya glasses din ya kunna wata waka ta
turanci _you are my African queen..._,ahankali wakar take tashi yanabi yana makale
da hannun hafsat guda daya acikin nashi yana driving da dayan,

Wata hamshakiyar unguwa tamasu fada aji taga yakaisu, wani tangamemen gida suka
shiga mai manya manyan part har guda hudu sannan kowanne upstairs ne,kuma daga can
gefe B/Q ne,
Nafarkon yabude suka shiga nan taga tangamemen falo da kitchen da store sai dining
area, saman kuma bedrooms ne guda biyu masu dauke da bathroom acikin kowanne,

"Kinga gidan da na sai mana zamu dawo nan bada jimawa ba domin har nabada asiyo
furniture's,nafi son ina dawowa daga Cairo insauka anan"

"Wai amma gidan ya hadu yaya, ga girma komai awadace.."

Murmushi yayi yariko hannunta suka fito, "kin dai k'i zancen ko?"

Murmushi tayi,

"To amma yanaga part din guda hudu?"

"Daya namu, daya na mami, daya nasu Abdul"

"To dayan fa?"

"Na amarenki"

Duka takai mishi,

"Allah kabari"

Dariya yayi yabude musu motar suka shiga batare da sun shiga sauran part dinba
domin gaba daya parts din tsarin gininsu da komai iri dayane,

Saida suka gama yawonsu agari sannan suka koma gida.

Washe gari hafsat gidan umminta tatafi tawuni acan, misalin karfe 2 narana mami
nazaune tana yin lunch taji sallama, har cikin falon mai sallamar tashiga sai faman
budada kamshi take nan ta durkusa tagaida mami,

"A'a tashi ki zauna, sannu da zuwa"

Saida mami ta gabatar mata da abinci da abubuwan sha sannan ta dubeta da fara'a,

"Sai dai kuma ban ganeki ba" inji mami,

"Ehh ai momy baki sanni ba, sunana hafsat kuma ni yar gidan alh musa ce ubangidan
ya yusleem"

Sake fadada fara'arta mami tayi ta dubeta....

_Fans kuyi min uzuri zakuji ni shiru kwana biyu saboda wani uzuri da ya taso min na
gaggawa amma insha Allah nanda sati daya zaku cigaba da jina ina fata zaku yimin
afuwa..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

You might also like