Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 134

⚡ _Heedayah_ ⚡

_By Khaleesat Haiydar_✍🏻

All thanks to Allah SWT for the privilege to start this book.... My special
greetings to my lovely Mum Hajiya Hajarah, and all my small mums😍 my siblings and
cousins ain't left behind too, ina son ku gaba daya.... My Isiaka Safia I greet u
too, and my lovely fans that have waited so long for Khaleesat Haiydar... ina maku
barka da sllh, Allah ya amshi ibadunmu baki daya, ga *Heedayah* I know u all will
love it, coz I Khaleesat is already in love with it 😊
No disappoinment In sha Allah 😉

1.....

Wani d'an matsakaicin daki ne da aka xagaye da tsadaddun labulaye, dakin na dauke
da katifa babba, sai kayan kallo daga gefe, sai cushion tsadadde guda daya,
Dattijuwar da baxata haura hamsin da biyar ba dake xaune dakin tayi tagumi tace
"Toh mu dai baxa mu gaji da addu'a ba, Allah ubangiji ya bata lafiya, watan gobe
kenan dai ake sa ran komai xai yi dai dai koh?" Matashiyar matar dake gefenta ta
d'an yi murmushi tace "Haka dai likitocin suka ce in sha Allah, sai dai kinsan kana
naka ne Allah na nasa, amma wnn aikin shine na karshe da xa ayi mata idan Allah ya
yrda, sai kuma fatan Allah ya sa a dace" Yakumbo tace "In sha Allahu xa a dace,
abinda kullum gaya ma Allah muke, kaf dangi bbu mai irin laluran nan balle ace ko
gado ne, sam bbu shi a danginmu gaba daya, ko ke akwai a naku??" Dariya matar tayi
tace "A'a Yakumbo" Yakumbo tace "Atoh, Allah dai ya raba bawa da wahala ke ma kuma
Allah ya sauke ki lafiya, Indiyan xa a kara komawa kenan ayi aikin?" Matar tace
"Ameen, ehh can xa mu je" Yakumbo tace "Toh in sha Allahu karshen wahalan kenan"
Matar tace "Allah ya sa" agogo Yakumbo ta kalla tace "Anya tafiyar nan taku na nan
yau kuwa Amina, shiru shiru har yanxu Umar din bai xo ba" Amina ta kalli agogon ita
ma tace "Kuma na kirasa daxu ban samesa ba, ina jin meeting suka shiga, kila sai
gobe dama na cire rai yau" Yakumbo tace "Atoh, ku bari kawai sai gobe yamma yayi,
sai kace wa inda ake kora, ga hanyar nan da ba kyau gari ya xama abinda ya xama
mucuta ta ko ina...." Amina tace "Haka ne" Yakumbo tace "Naji wai matar Salihu na
ta neman ki da fada ko? Kar ki kuskura ki kulata gayyar mayu ne, har ita Asama'un
ma ki bar kulawa duk haushin ki suke ji suna ganin kin fi su walawa gidan miji, ba
su san Allah ne ya baki ba" Amina tayi murmushi bata ce komai ba, Yakumbo ta kara
da cewa "Kuma wai sai kiyi ta boye yarinya kar su gani, wai haka?" Amina ta kalleta
tace "Aa ba gaskiya bane, ke kanki shaida ce Yakumbo tun tana yar yarinya ba a fiye
fito da ita cikin jama'ah ba, a ko da yaushe tana daki tare da ni ko mai kula da
ita, ko malamarta, har yau 'yan anguwa basu wani san kalan Heedayah ba, da kyar ki
xo gidan ki ganta a parlor, to sau tari idan anyi baki har su tafi ma baxa su ganta
ba shine ake ganin kamar boye ta muke kar a ganta" Yakumbo tace "Toh ai gwara haka,
haka kawai baka san bakin wani ba, ayi ta sa ma yarinya baki, gaskiya kun yi
dubara, ki rabu da su suce duk abinda xa su ce, lafiyan yarinya shine gaba kan
komai" Amina dai bata ce komai ba, Yakumbo tace "Har bokon ma a gida ake mata
kenan?" Amina tace "Ehh har islamiyya" Yakumbo tace "To madalla, ae gwara hakan, Ke
leko yar mutane naji shirun yyi yawa, Allah ya sa dai gantalallun yaran makotan nan
nawa ba shigowa suka yi suka yi waje da ita ba" Da sauri Amina ta mike tana leka
tsakar gidan tace "Heedayah??" Jin shiru ta fito tsakar gidan, Katon Babyn robanta
da take combing gashinta kadai ne kan tabarma da comb din sai hularta amma babu
ita, Yakumbo ta mike tace "Ni da nasan sai sun shigo sun ja ta, Amma wa ennan yara
iyayensu sun haifi jaraba kawai, yara kauyawa bbu kamun kai kawai malam..." Dawowa
Amina tayi dakin ta dau Hijab dinta sannan ta fita waje, Yakumbo na biye da ita
tana cewa "Ni dai Allah ka rufa min asiri ba rafi suka ja ta suka kai ta ba in
shiga uku, yarinya dai ba ido ba, daga kawo min ziyara shaidan ya fake ta nan yayi
abinda ya ga dama tawa ta sameni ina xaman xamana...." Tun Mahaifiyar Heedayah na
daurewa ana shiga bukkokin makota duba Heedayah a kauyen har taji hankalinta ya
fara tashi sosai ganin babu alamar yar tata.... Yakumbo dai sai salati take xabgawa
a rikice tana yafa gyalen da ya ki xama tana cewa "Toh me xance ma kanina Umaru
jama'ah?? Ina xan ce yar sa ta shiga?" Wata mata ce tace "Daxu fa naga sun yi
hanyar kasuwa da su Hinde da Bibalo, har da fatu, kusan dai su shidda suna rike da
hannun ita yarinyar" Yakumbo ta saki salati tace "Toh kuwa wllh Ubanta a Habuja
yake kuma duk iyayensu xae sa a daure idan abu ya samu yar sa, ita fa kadai garesa
sae ynxu da uwar ke da sabon ciki, shekararta goma sha biyu, kuma ba idanuwa gareta
ba, to a kan me gantalallun yara xasu ja ta su tafi da ita kasuwa, uwayensu xa su
siya mata a kasuwar? Tun shekaranjiya da suka xo kauyen nn nake ja ma ja'iran yaran
nan kunne ganin ynda suke makale mata har da masu wasa da gashin kanta nake ce masu
su fita harkarta, ita dai ba fuskarsu take gani ba balle ace, to wannan wani irin
bala'i ne, hanyar kasuwan nan da babu kyau sace sace yyi yawa, haba jama'ah??" Tuni
duk aka watse aka dau hanyar kasuwa aka bar Yakumbo tsaye ita kadai tana kumfar
baki, can dai ta bi su da sauri ganin sun yi nisa. Yara ne duk mata kusan su biyar
karkashin bishiyar mangwaro sai mata biyu dake saman bishiyar suna tsinkar nunannun
mango suna jefowa kasa matan dake kasa suna kwasa suna xubawa a karamin buhu, wata
yarinya ce warce duk baxata wuce sa'aninsu ba tana durkushe hannunta rike da mango
tana sha, daya hannunta kuma na rike da rigar fatuu don ita ke mata jagora, fara ce
sosai, kana ganinta kasan jinin Fulani ce don gashinta dake bude ko hula babu ma ya
shaida haka, idanuwanta farare ne kal kamar Madara tana kifta su a hankali kai kace
ras take ganin kowa a wajen, sai dai babu abinda take gani banda duhu, wajen duk ya
kauraye da surutun yaran dake tsinkar mangwaro xa su kai kasuwa su siyar, wata
bakar mota ce ta ja tayi parking a wajen, duk suka juya yaran, lkci daya kattin
maxaje biyu suka fito motar da sauri, gudu yaran suka yi har da Fatuu da ta warce
rigarta daga hannun Heedayah, na saman bishiyar ma duk suka diro suka ruga aguje,
Heedayah ta saki mango din hannunta ta dinga waige waige a tsorace, maxan suka bi
bayan yaran suka samu kamo uku daga cikinsu, Heedayah ta mike ita ma suka daga ta
suka saka cikin motar, kan kace me driver ya ja motar da gudu suka bar wajen. Gaba
daya ihu yaran ke yi cikin motar har da Heedayah dake ta kwala ma Mahaifiyarta kira
tana cewa "Ammina...." Wanda ke xaune a baya ya ciro bindiga yana nuna masu da
jajayen idonsa fuskarsa a murtuke ya daura hannu a lebbansa alamar su yi shiru,
lkci daya su ladi duk suka yi shiru sai rawa jikinsu yake, Zulai har da sakin
fitsari a gun, Heedayah ce kadai bata fasa ihun da take ba, Mutumin ya shake
wuyarta yana nuna mata bindigar yace "Ohh ke baxa ki rufe mana baki ba koh?" Jikin
Ladi na 6ari tace "Bata gani" Mutumin ya shiga kare mata kallo sannan ya gyada kai
yace "Kuma duk yanxu xaku daina gani" yana fadin haka duk ya rufe ma sauran ido da
kyalle, Heedayah da ta ki yin shiru kuma ya dinga buge mata baki yana marinta,
hakan kuma bai hanata ci gaba da ihu ba tana lalube laluben inda xata fita, daga
karshe jin taki shiru wanda ke xaune gaba ya miko masa wani leda yace "Bada mata a
fuska" hakan kuwa aka yi, nan da nan kuwa ko ina yyi tsit a motar, a hankali
Heedayah ta fada jikinsu Ladi. A hanya mutan kauyen suka hadu da su Hinde da sauran
matan da suka samu guduwa, Nan su Hinde na kuka da ihu suka fada masu abinda ya
faru, da hanxari wasu mata biyu suka rike Ammin Heedayah dake neman sulalewa nan
kasa, ta fada jikinsu a sume. Yakumbo ta saki wani salati da karfi ko ina na
jikinta na rawa, cikin kidimewa ta dinga cewa "Ai shkkn tawa ta kare, na shiga uku
na lalace, kar ace min yan kinnaping ne ko yan yankan kai suka dauke Heedayah, me
xance ma kanina jama'ah???" Ta fashe da matsananin kuka xata fadi kasa ita ma aka
rikota, ana ta salati iyayen sauran yaran da aka dauke ma suka dinga kuka suka bi
bayan maxan da suka nufi gun da abun ya faru. Tafiyar kusan awa daya mutanen suka
yi da su Heedayah a mota kafin su fita hanyar kauyen gaba daya kasancewar hanyar
bbu kyau, sannan suka yi parking gefen jaji don tafiyar minti ashirin kawai xasu
kara su isa wani checking point a gaba, wasu mutane ne suka fito daga dajin bbu
kyan gani kana ganinsu kaga axxalumai, Mutumin dake bayan mota ya sakko da sauri ya
fiddo su Ladi aka tasa keyansu cikin dajin bayan an kunce kyallen idonsu, daya daga
busassun mutanen da suka fito daga dajin na kallon Heedayah yace "Wannan fa"
Mutumin na kokarin fiddota yace "Daukarta xa ku yi, xata daga mana hankali muka
badata da powder" busasshen Mutumin yace "Ai baxai yiwu bane, wnn uban tafiya xaka
ce a dauketa, ku kashe ta kawai a jefar a nan, mu yi wucewar mu" A fusace Mutumin
yace "Mu kasheta bayan yara goma muka yi alkawari yau, duk bbu sa'a sannan mun samu
yara hudu kace mu kashe daya.... Kuma dole dai ku dauketa don makauniya ce wai"
Yana fadin haka ya direta kasa ya shige motar driver ya ja suka bar gun a guje"
tsaki Mutumin yyi ya dau Heedayah kai kace dabba ce irin daukan da yyi mata suka
shige dajin dake da manyan torns, ga duhu don Magrib ya gabato......

⚡ _Heedayah_ ⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

2......

Bayan tafiya that seems endless da kafa suka bullo ta wani titi inda wata mota ke
jiransu, nan suka shiga aka ci gaba da tafiya, gaba daya yaran kana ganinsu kasan
sun gaji sosai, Heedayah dai har lkcn dabata farka ba, sai kusan goma suka iso wani
karamin Uncompleted building, mata da maza ne sun kusa 6 yashe a wani daki da bbu
hasken kirki sbda karamin window ne a dakin daga can sama, Nan aka tura su ladi da
Heedayah da ta fadi kasa ko motsi bata yi, Wani wanda da alamar shine babba cikin
yan bindigan dake wajen yana rike da bindigarsa ya kalli wanda ke gadin mutanen shi
ma da bindigarsa a hannu yace "Ya ku ka yi da mutanan wancan Mutumin a waya?" Ya
kalli wanda yake nuna masa yace "Ae kawai bbu alamar xasu bada kudaden nan, sun ma
daina daga kiran" Bai rufe baki ba ogan nasu ya harbe Mutumin da ake magana a kai,
hakan ya kidimar da mutanen da ke xaxxaune gun, barin matan, sound din harbin ya
farkar da Heedayah ta fasa wani ihu tana kokarin mikewa tsaye wata mace dake xaune
kusa da ita ta jawota da sauri ta rufe bakinta a jikinta, Ogan ya dinga ma Heedayah
wani kallo sannan ya kalli Mutumin gefensa yace "Is she among the kidnapped?"
Mutumin ya girgixa kai da sauri yace "Aa yan kauye ne, su hudu muka dauko a kauyen
jiya, ba kace ana son body parts ba" Mutumin ya karasa gun Heedayah ya dagota daga
jikin matar yana kare mata kallo da kyau, ya girgixa kai yace "Yar wani babba ce
wnn, it will have been good she's kidnapped, but anyway, ana bukatan parts din ma"
Yana fadin haka ya turata ta fadi kasa, janye gawar Mutumin ogan yasa aka yi aka
fitar waje, sannan duk Yan bindigan suka fita aka garkame kofar. Ladi ta kankame
Zulai ta dinga rusa kuka tana kiran sunan Babarta, wata mata ta mike ta nufesu ita
ma tana hawayen, nan ta shiga lallashin su tana kwantar masu da hankali da sauran
mutanen wajen, kai kana gani kasan duk karfin halin lallashin nasu suke yi. Matar
dake kusa da Heedayah sai kokarin daga Heedayah take ganin kamar suma tayi..... Sai
kusan asuba Heedayah ta kuma farkawa, ta mike xaune da kyar tana laluban inda take
tace "Ammi??" Jin shiru bbu muryar Mahaifiyarta kamar ko da yaushe sai mutane a
kwance tana ta6a su ta janye hannunta da sauri, muryar Zulai taji a hankali tace
"Kiyi shiru yar birni yan yankan kai ne suka sace mu, kiyi shiru kar su shigo" Tsit
Heedayah tayi da farko, sai kuma ta fasa ihu tana kwala kiran Ammi, wani da ke
sallah ya sallame ya taho kusa da ita da sauri gudun kar mutanen su shigo don babu
abinda suka tsana irin a dinga masu ihu, karamin aikinsu ne su kasheta in har suka
shigo, lallashinta ya dinga yi yana ce mata xata koma gida in sha Allah, ita kuwa
sai cewa take "Aa ni a kai ni gun Ammina da Abbana yanxu...." Nan dai ta tada wa
enda suka samu bacci aka dinga hiaikin lallashinta a d'an dakin, Cikin kuka take ce
masu xata yi fitsari, aka nuna mata wani karamin kofa dake cikin dakin, Ladi tace
"Yo ai bata gani" furucin Ladi ya sa duk aka tsaya kallon Heedayah, wata mata ta
mike a sanyaye ta kama hannunta ta kai ta bayin. Har aka yi asuba gari ya waye
Heedayah shesshekar kuka take a hankali, can ya ta6a matar dake kusa da ita cikin
kuka tace "Aunty yunwa nake ji" Matar ta kuma jawota jikinta cikin sanyin murya
tace "Yanxu xa a kawo abincin idan Allah ya yrda" sai karfe goma aka bude kofar
dakin, duk kowa yyi tsuru tsuru ana addu'a a xuciya, Mutane uku suka shigo ko wanne
ya saita bindiga, kamar ko da yaushe facemask na fuskarsu, sai wani mutum da shi ma
fuskar tasa ke a rufe dake rike da babban leda me dauke da kananun bread, daga inda
yake tsaye ya dinga jefa ma kowa da ledan pure wata daya, ya jefa ma Heedayah dake
ta bin duk inda ta ji sound din faduwar bread da ido, Zulai ta mike xata dauka ta
bata ya mata wani mugun kallo ta cikin mask din fuskarsa da ke nuna idonsa kadai,
jiki na rawa tace "Yo ai bata gani ne" kallon Heedayah ya sake yi, gashi dai
fararen idanuwanta a kansa kuma ace bata gani, wani tsawa ya mata yace "Sa hannunki
ki dauka da kanki" Heedayah da tayi mugun tsorata ta fara laluben inda xata ga
bread din amma bata gani ba don bayanta yake, karasowa yyi cikin dakin bindigar sa
a hannu, duk occupant din dakin suka rike numfashi ganin ya nufo Heedayah da ta
hakura da laluben inda bread yake ta sunkuyar da kai, dukawa yyi ya dau bread din
ya mika mata yace amsa, tana laluban inda yake, ya kamo hannunta ya sa mata bread
din, tana kallon direction din da ta ji hannunsa idanuwanta cike da kwalla a
hankali tace "Thank you" ajiye mata ledan ruwa daya yyi ya bar sauran bread din ya
mike ya fice daga dakin sauran yan uwansa suka bi sa sannan suka garkame kofar,
matar dake kusa da Heedayah ta rungumota hawaye na zuba idonta ita ma, ta amshi
bread din ta kunce mata ledan ta mika mata. Zulai da Ladi dai tuni suka handame
bread din suna zare ido. Ammi ce kwance gadon asibiti da drip a hannunta, da ido
kawai take bin mutanen dake cikin ward din, she looks so sick, Yakumbo na can wani
gefe xaune kan kujera tayi tagumi idanuwanta duk a kumbure, wani matsanancin kuka
ta saki tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'una, Allah kai kasan yanda xaka yi da
axxaluman bayin nan naka, Ya Allah ka rufa min asiri 'yar Dan uwana ta dawo cikin
koshin lafiya, wllh Ita kenan garemu..." Kanwar Ammi dake Ward din ita ma ta fashe
da kuka sosai, haka ma sauran mutanen ciki, Mahaifin Heedayah dai na xaune kusa da
Ammi yana rike da hannunta, shi ma ko kadan tashin hankali bai boyu a fuskarsa ba,
kawai ta maxa yake, Yakumbo ta mike tana hade hanya ta fice ward din kamar xata
shide don kuka tana cewa "Shkkn ni dai tamu ta kare, ita kenan gare d'an uwana fa,
na cikin ma anyi barinsa sbda wnn tashin hankali, wannan wani irin xalunci ne ake
yi haka a duniya ni Khadijah, Allah ka tsine ma duk wanda ya raba mu da Heedayah,
Allah ka isar mana, ka dawo mana da ita cikin aminci...." Kanin Abban Heedayah ya
mike ya bi bayanta shi ma dai trying hard to control his tears. Kusan la'asar aka
bude kofan dakin da su Heedayah ke ciki, ja baya kowa ya dinga yi a tsorace,
Heedayah ta mike xaune daga kwancen da take tana kallon inda taji karan budewar
kofa, su hudu suka shigo, ko wanne da bindiga, Ogansu na nuna wani matashi yace
"Kai taso xaman ka ya xo karshe a nan, Yan uwanka sun yi abinda ake bukata" tashi
yyi da sauri yana hamdala sauran mutanen wajen sai hawaye, haka aka fitar da shi,
ogan na nuna wani a cikin sauran yace "Kai yan uwanka na raina mana hankali, xuwa
gobe idan basu yi complying ba xa mu aika ka barzahu kowa ya huta...." Yana fadin
haka ya kalli wanda ke gefensa yace "Cikin yaran nan ka fito da guda daya a cire
abinda ake bukata, me siya na kan hanya anjima, gobe da yamma ma akwai me xuwa zai
siya" yana fadin haka ya fice, sauran suka bi bayansa, Mutumin daxu da ya kawo masu
bredi ne kawai bai fita ba sai wanda aka sa ya dauko yarinya daya ya dinga bin
yaran da kallo, Mutumi dai mai bredi ya nufi Zulai ya dagata ya fice tana ihu tana
sakar masa fitsari, d'an uwansa ya bi bayansa ya garkame kofar, bbu abinda mutanen
cikin dakin ke yi banda hawayen tashin hankali, Heedayah ta dinga waige waige jin
ihun Zulai, matar dake kusa da ita ta rungume ta tana kuka sosai, cikin kuka ita ma
tace "Aunty ina xa su kai ta??" Matar dai bata ce mata komai ba sai kuka. Washegari
har kusan yamma basu samu an kawo masu bredin ma da ake kawo masu ba, Heedayah ta
fada ma matar kusa da ita tana jin yunwa ya fi a kirga tun matar na ce mata xa a
kawo abinci har ta gaji ita ma tayi shiru, kusan la'asar aka bude kofar wajen,
mutumin da ke basu bread ne ya shigo da buhun bread da ruwa, nan duk ya jefa ma
kowa, har bread din ya kare amma bai ba Heedayah ba, matar dake kusa da ita har
xata yankar mata nata, Mutumin ya karasa ya daga Heedayah cikin kaushin murya yace
"Mu je ki amshi naki" cikin rawan baki matar tace "A'a ko in yankar mata a nawa ba
cinyewa xan iya yi ba, baxan ma ci ba...." Wani mugun kallo ya dinga mata hakan
yasa tayi tsit jikinta na rawa, juyawwa yyi ya nufi kofa da Heedayah dake ihu tana
kiran Ammi tana gatsa masa cixo a hannu, bayan ya fita ya rufe kofar, ya toshe
bakinta yace "Ke xan halbe ki yanxu idan baki rufe min baki ba" Tsit tayi ko ina na
jikinta na rawa tana kallonsa kamar dai tana ganin fuskarsa, xagawa yyi ya canxa
hanya yanda sauran yan uwansa dake xaune a baya baxa su gansa ba, cikin hanxari ya
karasa bayan wani karamin bukka da suke ajiye makamansu ya ajiyeta bayan Bukkar ya
durkusa yana kallonta yace "You don't move, ki tsaya nan har in dawo idan ba haka
ba, I have gun...." Kai kawai take gyada masa a tsorace tana komawa baya, ya mike
da sauri ya koma inda Yan uwansa ke xaxxaune ana xuke xuke ana buga karta, Makullin
mashin dake rataye jikin bishiya ya dauka yace "Xan je amso ruwa in dawo yanxu...."
Wani daga cikinsu ya kallesa yace "Oga na hanya da customer fa" yace "Ehh yanxu xan
dawo ai" har ya nufi gun da suke ajiye babur dinsu sai kuma ya juya da sauri ya
sake komawa dakin da ya dauko Heedayah ya bude ya shiga yana masu wani kallo yace
"Ko da an tambayi yarinyar nan kuce ta mutu an fitar da ita...." Tsuru tsuru suka
yi suna kallonsa ya juya ya fita ya kulle kofar. Daga haka ya nufi machine ya hau
ya tada, a guje ya bar wajen, dai dai inda ya ajiye Heedayah ya tsaya, sai xare ido
take tana kalle kalle, ya daga ta ya daura gaban machine din yyi speed off, gudu
kawai yake a dajin kamar mai race din motorcycle, tafiyar kusan awa daya da rabi
suka yi suka shigo cikin gari sosai, a hankali yake tafiya yana kalle kallen
jama'ah dake ta kokarin rufe wajajen sana'arsu kasancewar Magrib ya gabato, sai
kuma ya tsayar da machine din ya kashe, sauke Heedayah da tashin ta bacci kenan
yyi, ya ajiyeta nan gefen hanya yana kallonta, laluba wajen ta shiga yi, jin ya
sake kunna bike din da sauri tace "Noo, Are you leaving me??" juyar da Machine
dinsa yyi ya dau hanyar da ya fito with speed, ta fashe da kuka sosai tace "Noo"

⚡ _Heedayah_ ⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

3.....

Heedayah ta fi minti biyar a tsaye tana Shesshekar kuka, jin bbu alamar xai dawo ta
fara tafiya a hankali tana yi ma kanta jagora da hannuwanta biyu, da tayi tafiya
kadan sai ta tsaya, ihun da taji aka yi wajen ya sa ta tsaya a mugun tsorace, ji
tayi kamar an hankadata da katon abu ta fadi kasa, tun tana jin surutun jama'an
wajen sama sama har ta daina ji kwata kwata. A hankali Heedayah ta bude ido tana
laluba inda take kwance, muryar namiji taji a gefenta yana cewa "Alhamdulillah she
is back (Ta farfado....)" Ya kamo hannunta yana mata sannu murmushi dauke fuskarsa,
kanta da yyi mata nauyi kawai take gyadawa tana kokarin mikewa xaune, ya komar da
ita ya kwantar yace "A'a bari likita ya xo ya duba ki, bari in kirasa, ina xuwa
ynxu" ita dai kai kawai take gyadawa, ba a dau lkci ba sai ga mutumin ya dawo da
likita, directly Heedayah ke kallon fuskar likitan, ya sakar mata lallausan
murmushi wanda bata san ma yana yi ba, likitan ya xaunar da ita ya dafa goshinta
yace "Ya jikin baby girl?" Kifta ido ta shiga yi tace "Where am I? (Ina ne nan?)"
Yana murmurshi yace "Hospital dear, fatan dai babu inda yake maki ciwo" kanta ta
nuna masa, yace "Xai daina in sha Allah, xa a baki magani yanxu" shi dai wanda ya
kirawo likitan kallonsu kawai yake, A hankali tace "Xan yi fitsari" likitan ya
saukar da ita kasa, yana nuna mata kofar bandaki, hannunsa ta kama, yace "Xa ki iya
dear, walk gently now (Kiyi tafiya a hankali....)" kin motsawa tayi, sai kuma a
hankali tace "I can't see (Bana gani)" da mamaki likitan da Mutumin da ya kawo ta
asibitin ke kallonta, likitan yace "Why? is the eyes paining you? Idanuwan suna
maki ciwo ne" Ta girgixa masa kai yace "Toh yi tafiyar ki da kanki" ta rike
hannunsa gam kamar xata yi kuka tace "Ae ni bana ganin hanyan" sosai hankalin
likitan ya tashi, haka zalika Mutumin dake Ward din da ya mike shima yana kallonta,
don gaba daya tunaninsu a lkcn ta dalilin accident din ne vision dinta ya samu
matsala, Banda innalillahi wa Inna ilaihi raji'un bbu abinda Mutumin ke furtawa
yana kallon Heedayah. Likitoci sun fi biyar a kan Heedayah, all trying to figure
out where the problem is, ko wannensu na kokarin gano inda matsalar take amma abu
ya ci tura, ita dai sai bin duk inda ta ji motsi take da manyan idanuwanta, duk da
ba ganinsu take ba, daga karshe dai aka ba Mutumin da ya kawota shawara kawai ya
kai ta asibitin ido, ba karamin tashi hankalin wannan mutumin yyi ba, haka dai ya
biya bill din asibitin ya dau Heedayah xuwa asibitin ido dake nan cikin garin kano.
Dai dai lkcn da suka shiga haraban asibitin motar optician din dake duba Heedayah
tun da aka haifeta har kawo lkcn da aka yi referring dinsu india kuma na fita daga
asibitin. Mutumin dake rike da hannun Heedayah bayan ya sauketa daga motar ya duka
dai dai fuskarta cike da damuwa yace "Daga yaushe kike daina gani Little girl? What
was the last thing u saw? Meye abu na karshe da kika gani?" Tayi shiru sai kuma
tace "Nima ban sani ba" Damuwa ne sosai fuskarsa, yace "Toh daga ina kike jiya da
magariba kuma ina xa ki? Where are ur parents? Ina iyayen ki" Shiru tayi, staring
at him kamar tana ganinsa, nan ya shiga tantaman ganin da tace bata yi, ganin yanda
take masa kallon cikin ido ya kai yatsunsa har kusa da idonta yaga bata rufe ba har
sai da ya taba lashes dinta, kikkifta idon ta shiga yi, yace "ki min magana, Where
are ur parent? Ina iyayenki" Ta girgixa kai tace "I don't know, (Nima ban sani ba)"
da mamaki yace "Baki san inda iyayenki suke ba, ina xa ki jiya?" Ta fashe da kuka
tace "Nima ban sani ba, kawai an saka ni a mota aka wuce da ni, sai na ji an sake
hawa da ni bicycle kuma ynxu ban san inda aka kawo ni aka ajiye ni ba" rasa abun
cewa yyi yana kallonta, can dai yace "Ya sunan garin ku?" Tace "Abuja" ya xaro ido
ganin dai a garin kano suke ynxu, yace "Ya sunan baban ki?" Tace "Abba" yace
"Abba??? Mamarki fa?" Cikin rawar murya tace "Ammi" Innalillahi ya dinga nanatawa a
ransa, sai kuma yace "Abuja ya sunan anguwan ku?" Tace "Abuja ne" mikewa yyi just
as confused as she is, ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna goma na safe, yana
rike da hannunta yana mata jagora suka shiga asibitin, Ba su suka fito ba sai kusan
Azhar after series of Diagnosis da ya tabbatar da she was born with the blindness,
a haka aka haifeta, kuma tana stage din operation din karshe kenan wanda xa ayi
mata idan ba ayi nasara ba she will remain blind till the end (Xata xauna a
makauniyar ta har karshe...) Alhaji Ahmad na rike da hannun Heedayah xuwa gun
motarsa a haraban asibitin, bai ta6a shiga rudani irin na ranan ba, to ina xai kai
wannan yar baiwar Allahn, kara kallonta yyi yaga bata wuce autarsa Rabi'ah ba,
yanxu ina xai samo iyayenta ko wani wanda ya santa??? Yanke shawarar kai ta police
station kawai yayi, yasan su xa su san yanda xa su yi da ita, driving kawai yake
absentmindedly ya ji Heedayah tace "Abba, yunwa nake ji" ya d'an kalleta yana ci
gaba da tukinsa yace "Me xa ki ci?" Tace "Shayi da bredi da kwai" sake kallonta yyi
sannan ya dauke kai, Mintuna kadan ya rage ya isa nearest Police station, sbda
yunwan da tace tana ji ya dau wata hanyar daban xuwa wani restaurant, abinda ta ce
take so ya sa a kawo mata, ya tabbatar shayin ba xafi sosai sannan ya bude mata
bread din da kwai ya mika mata, ganin yanda take ta lalube lalube kar ta kwa6ar da
shayin ya mike ya koma kusa da ita, feeding dinta yayi har ta ce ta koshi, Banda
kallonta bbu abinda yake yi cike da tausayinta, Bai taba ganin irin haka shi dai
ba, yar karamar yarinya da makanta, tace "Abba..." Ya shafa kanta yace "Daughter"
murmushinta me kyau tayi tace "Thank you" Bai ce komai ba, Amma naxari me iri iri
yake yi a ransa, bayan few seconds ya kalleta yace "Ya sunanki?" Tace "Heedayah" Ya
lumshe ido ya bude yace "Heedayah baki san anguwan ku a Abuja ba? Ki tuna da kyau
ki gaya min daughter" Tace "Abuja ne gidanmu" ya girgixa kai ya mike yace "Tashi"
tashi tayi ya kama hannunta kasancewar ya biya bill din suka fita xuwa gun motarsa,
bayan sun bar Restaurant din, ya dau hanyar police station, Yana rike da ita suka
shiga ciki, Bai bata lkci ba bayan yayi report ya bar Heedayah tare da su don yana
da meeting da xai shiga karfe daya kuma a ranan yake son barin garin kano, sai dai
har ya isa inda xa shi hankalinsa ya ki kwanciya, gaba daya ya rasa sukuni....
Washegari karfe takwas a police station yayi ma Alhaji Ahmad to be sure an samu
iyayen Heedayah duk da yasan da kyar hakan ya faru a rana daya kawai, Bayan sun
gaisa da policemen dake wajen suka sanar masa an kai ta orphanage for the meantime,
shiru yyi na few seconds kafin yace "Shikenan, nagode...." Wani police officer yace
"We will try our best in sha Allah, an kuma riga da an fara broadcasting tun jiya,
so hopefully she will get back to her parent soon, (xa mu yi bakin kokarin mu na
ganin ta koma ga iyayenta)" Alhaji Ahmad yace "Allah ya sa hakan" Sallama yyi masu
ya bar station din. Ammi dake xaune saman gado a dakin asibiti da take ta kai
hannunta xuwa na Mahaifin Heedayah dake xaune gefenta sai dai yyi nisa tunanin da
yake, juyawa yyi ya kalleta, hawayen da ke gefen idonta ya gangaro cikin sanyin
murya tace "Muhammad pls let nothing happen to my daughter, plss nothing shud
happen to Heedayah, (Kada wani abu ya sami Heedayah) ku dawo min da yarinya ta"
Uncontrollably ta fara kuka, tun xuwansu asibiti kwana biyu kenan sai yau tayi
magana, Alhaji Muhd ya na rike da hannunta trying his best to be strong yace
"Nothing dear, I mean nothing will happen to our daughter, (Babu abinda xai sameta)
in sha Allah, zata dawo garemu soon da izinin Allah, hukuma na bakin kokarinsu, ki
kwantar da hankali don Allah" Kuka kawai take bata ce komai ba, she looks so weak,
ya sake hannunta ya fita don kiran likita. Da yammacin ranan Alhaji Ahmad ya gama
shirin komawa kaduna, sai da ya bar gida sannan yyi deciding kafin ya tafi ya fara
xuwa orphanage da yan sandan suka ce masa an kai Heedayah, Bai yi wani wahalan
shiga gidan marayun ba bayan ya nuna Identity dinsa, ya dinga bin yaran dake wasa a
waje da kallo, lkci daya idonsa ya sauka kan Heedayah dake rakube can gefe ita
kadai staring into space, hannunta rike da ledan biscuit, kallonta ya dinga yi
kafin ya nufeta ya duka kusa da ita har sannan bai daina kallonta ba hawaye ne cike
manyan idanuwanta, lkci daya ya ji jikinsa yyi sanyi sosai, ya dafa goshinta yace
"Heedayah" Hannunsa ta kama kamar tana jiransa a lkcn, sai ta fashe da kuka tace
"Abba" Ya jawota jikinsa yace "Why are you crying? (me yasa kike kuka" Cikin rawar
murya tace "Suna min dariya bana gani, wata ta karbe min biscuit guda daya, Abba ka
kai ni gida gun Ammina...." Bai ce komai ba, can ya mike yana rike da ita yace "Toh
daina kuka" goge idonta tayi, yana rike da ita still ya tafi office din shugaban
wajen, bayan sun gaisa yace "What are the process before adoption of a child in
here? (meye matakan bi kafin daukan yaro a gidan marayu)" Tana kallonsa tace "It's
a very long process mister, (Matakan suna da yawa gaskiya" yace "Alright.... I will
be back in some minutes time (Xan dawo nan da wani lkci)" kuka Heedayah ta dinga yi
sosai da ta gane tafiya xai kara yi ya bar ta, haka nan ya bar ta gun masu kula da
marayun wajen ya wuce, police station ya koma. Asp ya ajiye pen din hannunsa yana
kallon Alhaji Ahmad yace "So you mean kana son tafiya da ita har lkcn da Allah xai
sa a samu iyayenta" Alhaji Ahmad yace "Yes exactly sir" Asp yace "Sai dai kasan da
cewar you didn't adopt her, duk lkcn da iyayenta suka bayyana xa a mayar masu da
ita" Alhaji Ahmad yace "In sha Allah, Ni ma nafi son haka, and as I have said sbda
health issues dinta yasa xan tafi da ita, she won't cope in the orphanage, i will
be dropping all necessary information kamar yanda ka bukata duk da ni ba bako bane
a gun ka, idan ma baka san ni yanda ya kamata ba, na tabbata kasan Yayana ai"
Murmushi Asp yyi yace "Sure, I am not doubting you Barrister, Allah ya taya ka riko
har kafin Allah ya bayyanar
da mahaifanta" Alhaji Ahmad yace "In sha Allah, nagode sosai for understanding me"
Wani short note Asp din yyi a takarda yayi stamping sannan ya kira wani police
officer ya koma orphanage din tare da Alhaji Ahmad don dauko Heedayah. Har sannan
Heedayah na xaune inda Alhaji Ahmad ya bar ta tare da daya daga mai kula da su, sai
dai mai kula da su din bata gun, ita kadai ce xaune gwanin ban tausayi, har sannan
ta ki cin biscuit din, Bbu 6ata lkci aka basa ita ya bar orphanage din bayan ya
sallami police officer din, he can see how happy Heedayah was bayan sun shiga mota,
ganin tana ta kokarin bude biscuit din hannunta ya amsa ya bude mata ya mika mata,
tace "Abba xaka maida ni gun Ammina da Abbana?" Ya shafa kanta yace "In sha Allah
daughter" tayi murmushi sosai tana cin biscuit din hannunta, seat belt ya sa mata,
yana kallon agogo dake nuna masa biyar saura yan Mintuna, ya gama addu'o'in da xai
yi sannan ya dau hanyar fita kano xuwa garin kaduna.....

Yan Niger Khaleesat bata iya rubutun Hausa xalla bbu turanci ba, kun ban wahala a
page din nan😩

Free pages dai bbu yawa😉

07087865788

⚡ _Heedayah_ ⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

4......

Har suka shigo cikin garin kd wajajen karfe tara na dare bacci Heedayah take,
slowly yake driving bayan ya shigo anguwar da gidansa yake, anguwar so silent ga
fitilu ta ko ina da ya haska anguwar kamar da rana, bakin wani gate ya ja ya tsaya
yyi horn, wanda hakan ya farkar da Heedayah, laluba motar ta shiga yi tace
"Abba...." yana kallonta yace "I am here..." Bata kuma cewa komai ba dama kawai so
take ta tabbatar bai bar ta bane, ya d'an yi murmushi ya ja motar xuwa cikin babban
compound dake dauke da gida ginin duplex bayan Mai gadi ya bude masa gate da sauri,
parking yyi a space din da aka tanadar domin parking a compound din, wani matashi
ne da baxai wuce 28 ba ya fito daga cikin babban building din gidan, ya nufo
parking space din, Alhaji Ahmad ya kashe motar ya bude ya fito, Matashin ya d'an
risinar da kansa yace "Sannu da hanya Abba" Alhaji Ahmad yace "Yauwa sannu, but ka
damu ka kirani tun jiya da kake min sannu da hanya ynxu??" Yana fadin haka ya wuce
sa ya xaga daya side din motar, da ido dogon Matashin ya bi sa bai ce komai ba,
Alhaji Ahmad ya bude door din side din da Heedayah take, ya kamo hannunta ya sakko
da ita daga cikin motar, Matashin ya d'an koma baya yana kallonsu a bit surprised,
Alhaji Ahmad yace "Ka fiddo min laptop dina bayan motar, they are some other things
ma ka taho da su ciki" Yana fadin haka ya nufi entrance din shiga gidan yana rike
da Heedayah, Matashin ya bude motar ya dauko abinda yace masa sannan ya bi bayansu,
Alhaji Ahmad na shiga parlor Rabi'ah da Khadija suka taso da gudu don rungume sa,
sai dai ganin Heedayah da yake rike da duk suka tsaya basu karasa gun nasa ba,
Khadija tace "Who is she Dad?" Yana kokarin cire takalminsa yace "Sabuwar 'yar uwar
ku" kallon juna Khadija suka yi da Rabi'ah, ya karasa parlon ya xaunar da Heedayah
kan kujera sai dai ta ki sakin hannunsa kmr xata yi kuka tace "Abba kar ka bar ni
don Allah" Yace "Noo baxan bar ki ba, we are home yanxu" Yana fadin hka ya kalli
Khadijah yace "Ina Mumyn ku?" Khadijah ta d'an cinno baki tace "Upstairs" ya daga
Heedayah ya wuce sama da ita, Khadija da Rabi'ah suka juya suna kallon yayansu dake
tsaye bakin kofa yana kallon ikon Allah shi ma, da sauri suka nufesa a tare suka ce
"Ya Shuraim who is she? Wacece ita" Ko kallonsu bai yi ba, ya nufi part din Abbansu
don ajiye masa system dinsa dake hannunsa. Alhaji Ahmad ya bude kofar parlon Mai
dakinsa still holding Heedayah's hand, dai dai fitowar ta daga bedroom dinta, ya
xaunar da Heedayah saman kujera kafin yace komai tana kare ma Heedayah kallo daga
sama har kasa tace "Waye wannan kuma Barrister?" Yace "sannu da hanya ya kamata ki
fara min sannan tambayoyin ki su biyo baya" a takaice tace "Toh sannu da hanya,
wacce yarinyar ce wannan ka shigo min da ita har parlor?" Sai a sannan ya daga kai
ya kalli matar tasa yace "Bakuwa ce" Ta d'an yatsina fuska tace "Bakuwa kuma? Daga
ina? Kuma ina xa a kai ta?" Yace "Eh bakuwa.... Daga kano, kuma nan xata xauna in
sha Allahu rabbi" Da mugun mamaki tace "Yar wacece ita din?" Yace "Baiwar Allah
ce..." A kufule tace "Plss be straight barrister, ina ka samo yarinya? Kowa ma
bawan Allah ne ai" Barrister yace "Gashi nan na gaya maki, what else did you want
to know, me kuma kike son sani" kamar jiran tambayar take ta mayar masa da amsa da
sauri tace "Manufar xuwanta gidan nan, sannan mun hada wani dangantaka ne da ita??"
Ya gyara xama yace "Manufar xuwanta gidan nan shine don ta xauna da mu na wani d'an
lkci, dangantakar mu kuma kawai shine kasancewar ta 'yar uwar mu musulma" Kallonsa
ta dinga yi, surprised, Furious, and mad at the same time.... Blankly tace "I don't
get you Abban Shuraim, ban gane abinda kke nufi ba, a ina kasamo wannan yarinyar??"
Ya mike yace "Her parents are missing, so we need to look after her kafin Allah ya
bayyanar da iyayenta, all that aside, she is blind Hajiya Maryam, makauniya ce...."
Yana fadin haka ya fita daga parlon..... Hajiya Maryam da ta bi sa da kallon mamaki
lkci daya tace "Tabdijam!!! Toh sannu Humanitarian, Do-gooder.... sai kuma nace
maka gidana orphanage ne (Gidan marayu) ko kuma police station?? to wllh ka
saurareni da kyau, yarinyar nan dai baxa ta xauna gidan nan ba, me muka hada da ita
daga ganin yarinya a titi ka kinkimota ka kawo mana gida wai iyayenta sun 6ata
kamar wasu gyada, Anya ma Barrister kasan me kake yi kuwa, yanda duniyar nan bbu
gaskiya kwata kwata kowa ya xama mugu ya xama abun tsoro ka dauko mana yarinya ka
kawo gida?? A'a wllh ba gidana ba, ka dauketa ka kai ta police station ko kuma ka
kai ta gidan marayu" tana fadin haka ta wuce dakinta rai 6ace don daukan wayar ta,
Heedayah dai na xaune sai kallon direction din da masifar ke tashi take yi, gaba
daya a tsorace take, lkci daya hawaye ya kawo manyan idanuwanta.... Bayan minti
biyar Hajiya Maryam ta fito dakinta tana kallon Heedayah tana huci ta daka mata
tsawa tace "Ke maza tashi ki fita ki ban waje kar in illata ki...." Mikewa Heedayah
tayi da sauri ta fashe da kuka tana laluben hanya tace "Abba where are you"
muryarsa ta ji yace "I am here...." Har ya karaso cikin parlon kallon Hajiya Maryam
yake, calmly yace "Wannan ya xama na karshe a gidan nan, kar ki sake yi mata tsawa,
nace a gidan nan Heedayah xata tsaya har sai an samo iyayenta, I mean my words"
bude baki tayi tana kallonsa da farko, sai kuma tayi wani murmushi me sauti tana
tafe hannu tace "Toh sannu Humanitarian, idan ni ban kai inyi magana ka ji ba nasan
baxa a rasa wa enda xa su yi maka ka ji ba, look Ahmad it's not as if i am being
wicked, ni ba muguwa bace Allah ya ga xuciyata kawai xamanta ne damu bna so don
hankalina bai kwanta da hakan ba, to wai ma akan me xata xauna da mu, kai da kke
lawyer ai ya ci ace ka fi ni sanin me duniya ke ciki, to idan ba akwai wani
boyayyen lamari a kasa ba daga xuwa meeting kano sai ka dawo da yarinya wai ka
tsince ta a titi bbu iyaye, Kar ka manta idan kai lawyer ne to ni kuma matar lawyer
ce...." Ya dakatar da ita yace "Wallahil Azeem Maryam wannan yarinya a hanya na
hadu da ita kamar ynda na fada maki, mota ce ta bigeta muka yi asibiti da ita, I
was there har ta farfado.... Let just stop all this, Maryam put Rabi'ah or Khadijah
in her shoes plss" a mugun fusace tace "Allah ya kiyaye, I can't imagine my
children in her shoes, why will I? Kar ma ka gaya min haka, Ni dai abinda na sani
shine hankalina bai kwanta ba kuma baxai ma ta6a kwanciya da yarinyar nan ba, wa ya
sani ma ko aljana ce da gashi haka??" Bai kuma ce mata komai ba ya kama hannun
Heedayah dake kuka a hankali ya fita parlon da ita xuwa downstairs.... Hajiya
Maryam ta kasa zaune a parlon nata sai xagaye take, bude kofar aka yi Shuraim ya
shigo da sallama can kasa, Hajiya Maryam ta kallesa da sauri tace "Shuraim kana
ganin mahaifinku koh? Me yake nufi da kawo mana yarinya gida ba dangin Iya balle na
Baba, ya san yar wacece ko ma shegiya ce bai sani ba kawai ya kawo mana ita gida,
wllh something is fishy, kuma in dai yarinyar nan xata xauna gidan nan sai dai mu
bar masa gidan shi da ita gaskiya, don mu ba gantalallu bane, wai kuma makauniya ce
kai ka ji fa???" Tun fara maganar ta sai a sannan Shuraim ya kalleta da sauri jin
wai makauniya ce, Tayi mitsi mitsi da ido tace "Wllh haka yace Makauniya ce bata
gani, kuma naga alamar hakan, she is blind, oh innalillahi wa Inna ilaihi raji'un,
me ya samu Barrister ni Maryam... Anya kuwa yana right senses dinsa??" Shuraim dai
bai ce komai ba ya juya xai fita, a mugun fusace tace "Toh malam ba shiru xaka yi
ba ka wani juya sumui sumui xaka wuce, xuwa xaka yi ka samesa tunda yana jin
maganar ka, ka lallabasa ya fitar mana da yarinyar ya kai ta police station, bbu
ruwana da gayyar tsiya, yarinyar nan baxata kwana gidan nan yau ba..." Shuraim na
fita ya nufi Part din mahaifinsa, ya bude kofar parlon da sallama, Heedayah ce
kawai xaune kasan carpet dake parlon ga cup din fresh milk a hannunta, jin an bude
kofa ta dakatar da shan madaran da take yi tana waige waige, bai kalli direction
dinta ba ya nufi dakin Abbansa, sallama yyi bayan ya amsa masa ya shiga, xaune ya
samesa gefen gadonsa, ya karasa ya xauna nan kasa gabansa yana kallonsa yace "Ya
hanya Abba?" Abba ya kallesa yace "Alhmdllh..." Shuraim ya d'an shafa kansa yace
"Abba, akan wannan yarinyar....." Sai kuma yyi shiru, Abba yace "Yes, what about
her? Ina jin ka" Shuraim yace "Is she suppose to be here?" Abba yace "Of course, ai
nan din gidana ne ba na wani ba, so why won't she be here?? Me kuwa xai hana
xamanta a nan tunda na amince da hakan?" Shuraim ya girgixa kai alamar ya rasa
abinda xai ce, Abba yace "Yes gidana ne, ba naka ba, balle na Mahaifiyar ka"
Shuraim yace "But Abba hakan ba dai dai bane, bbu abinda muka hada da ita, ba mu
san ta ba, we don't even..." Dakatar da shi Abba yyi so pissed off yace "Get out my
frnd, who are you to question my orders? And don't u even have human conscience?
Xaka so kanwarka ta tagayyara a rayuwa?" Mikewa Shuraim yyi yace "I am sorry" daga
haka ya nufi kofa ya fita, satan kallon Heedayah yyi, lkci daya ya wani hade rai ya
fice daga parlon.

07087865788

⚡ _Heedayah_⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

5....

Jin budewar gate ya sa Alhaji Ahmad ya mike ya isa jikin tagar dakinsa yana kallon
compound din gidan don ganin wanda xai fita, motar yayansa ne ya shigo compound
din, ya bi motar da kallo har yyi parking, sannan ya girgixa kai ya koma ya
xauna... Ba a dau lkci ba kuma wayarsa ya fara ring, ya duba ganin yayan nasa ke
kiransa ya mike ya fita dakin, kwance ya ga Heedayah ta fara bacci nan kasa, ya
d'aga ta ya kwantar kan kujera sannan ya fita, direct main parlor ya wuce, ya tadda
wansa Alhaji Umar zaune saman kujera ga Hajiya Maryam xaune parlon ta sha kunu kai
kace bata ta6a dariya ba, xaunawa yyi ya gaida Yayan nasa, Alhaji Umar ya amsa yana
kallon Hajiya Maryam yace "Me ke faruwa Maryam" Ta kwantar da murya tace "kana ji
Alhaji, Ko awa daya ba ayi ba da dawowan barrister daga kano, amma sai me??" Nan ta
kwashe komai ta tsara masa, tana matsar kwalla tace "Saninta muka yi Alhaji? Ko me
muka hada da wannan yarinyar? Mun san me yasa iyayen suka jefar da ita da har shi
xai daukota, to gaskiya naga abun ba wanda hankali xai dauka bane shi sa na kira ka
don kayi intervene don gaskiya I don't know what came over Barrister, ban san me ya
samesa ba, kawai muna xaman xaman mu ya ja mana magana...." Alhaji Umar na kallon
kanin nasa yace "Barrister wace yarinya ce wannan ka dauko ka kawo cikin gidan ka?"
Alhaji Ahmad ya jinginar da kansa da kujera yace "Doctor nasan da kai ka ga
yarinyar nn xaka yi fiye da abinda nayi ma... Sincerely I mean no harm to my
family, taimako kawai nayi sbda Allah, and I thought they will also welcome the
idea, na xata xa su so taimakon da nayi...." da sauri Hajiya Maryam ta katse sa
tace "To family dinka basa son taimakon nan gaskiya, ur idea isn't welcome, kawai
ka maida ta inda ka ganta, idan kuma xuciyar ka baxai yarda ka maida ta ba to ka
kai ta gidan marayu..." Wani kallo ya jefa mata yace "Baki isa ki bani order a
gidana ba Maryam, I did what I know is right, you are not in the place to kick away
my decision, nace baki isa ba" Alhaji Umar na kallonsa yace "Hold on bawan Allah,
bana son hayaniya, ka saurareni...." Alhaji Ahmad yace "Dr if you are in anyway
doubting me ka kira abokin ka Asp Usman, he will explain everything to you, Babu
abinda xai boye maka, shi ma ya bani go ahead din tahowa da yarinyar when I request
doing so, ban taho da yarinyar nan ba sai da izini da sa hannun Asp...." Mikewa
Alhaji Umar yyi bayan shirun wani lkci yace "Ynxu ina yarinyar take?" Barrister ya
mike yace "Mu je ka ganta tana sama parlona" Bin bayansu Hajiya Maryam ma tayi xuwa
part din mai gidan nata da sauri, kallon Heedayah dake bacci Alhaji Umar ya dinga
yi kafin yace "She so little" Alhaji Ahmad ya bude hannunsa yace "Of course she is"
hannu Alhaji Umar ya kai goshinta ta bude ido da sauri ta kamo hannun tace
"Abba..." Ya d'an yi jim sai kuma yace "How are you?" Shiru tayi tana kokarin
mikewa ya dagata ta xauna, Hajiya Maryam sai kyabe baki take fuska a murtuke tana
kauda kai, Alhaji Umar ya girgixa kai ya sauke ajiyar xuciya yace "This is
serious... abinda xai faru ynxu shine ke Maryam kiyi hakuri ta kwana xuwa gobe xa a
san ynda xa ayi in sha Allah, they will be a meeting tomorrow at my resident idan
Allah ya kai mu" shi dai Barrister bai ce komai ba, Hajiya Maryam tace "Allah ya
kai mu, amma wllh baxan rike yarinyar nan ba Kun ji rantsuwar musulmi sai dai duk
abinda xai faru ya faru" daga haka ta fice daga parlon duk suka bi ta da ido. Karfe
goma Barrister Ahmad ya fita parlonsa xuwa parlon Hajiya Maryam, kallo take ita da
Rabi'ah da Khadijah a parlon nata, Khadijah tace "Toh Mumy me yasa bai kai ta
orphanage ba??" Hajiya Maryam ta kyabe baki tace "Neman suna mana, ke ko bayan
lawyer gashi Humanitarian din da ya laka ma kansa, to wllh ba dai wannan gidan ba,
dai dai nake da su dukka...." Rabi'ah tace "And kuma yace makauniya ce fa" Hajiya
Maryam ta dau apple din gabanta tace "Ko kurma ce sai ya fitar da ita gidan nan,
ban gama wahala da nawa yaran ba baxai kwaso min wata can ba, ba dangin iya balle
na baba, shi dai ya cika fitina ne kawai" Khadijah tace "Ni dai idan yace nan xata
xauna gwara in koma gidan Aunty Fatima, I can't stay in the same roof with her,
what if muguwa ce" Hajiya qMaryam tace "Sai dai shi da ita su bar mana gidan...."
Shigowan Abban yasa tayi shiru, Yana kallonsu gaba daya yace "Bani da abinci a
gidan nan yau kenan?" Hajiya Maryam tace "Ohh na xata you are full ai da naga kafi
concentrating kan yar tsintuwa, ban san kana tare da yunwa ba, Rabi'ah go and serve
him downstairs" kallonta kawai yake kafin ya gyada kai ya juya ya fita parlon, a
hankali Khadijah tace "Abba is just acting strange, dubi fa ko kula mu bai yi ba
tunda ya dawo..." Hajiya Maryam tace "Atoh ina xai kula ku ga makauniya ya saka a
gaba Khadija" Rabi'ah ta tashi ta fita don kai ma Abban nata abinci parlonsa, Yana
xaune parlon yyi nisa tunanin da yake, ta ajiye abincin tace "Abba ga abincin" yace
"Baxan ci ba, ki dibar ma yarinyar nan kawai ki fita da sauran" ta kalli Heedayah
dake kwance fararen idonta a bude, ta d'an hade rai ta bude abincin ta diba kadan
ta daura nama daya, kallonta kawai Abban nata yake yi yace "Add the meat" Ta kara
daura wani naman sannan ta mike ta fita da sauran abincin. Mikewa yyi ya tafi gun
Heedayah yace "kina Jin yunwa ko?" Ta gyada masa kai, ya kama hannunta ya dau plate
din abincin ya fita, main parlor ya koma, ya shiga wani d'an corridor ya kwankwasa
daya daga kofofi biyun dake wajen, wata matashiya da baxata haura talatin da biyar
ba ta bude kofar, ganinsa ta durkusa da sauri tace "Sannu da dawowa Alhaji, ina
yini" yace "Lfya lau, ga wannan yarinyar ki kula da ita, ki bata abincin nan,
sannan ki taimaka mata tayi wanka ki mata shimfida ta kwanta, tana da matsalar ido"
Matar ta kama hannunta da sauri tace "To in sha Allahu Alhaji" daga haka ya juya ya
bar wajen bayan yyi mata sai da safe. Washegari da ya kasance lahadi bacci yan
gidan suka dinga yi har karfe takwas, Hajiya Maryam ta sakko parlor wajajen tara
don ganin ko Saudat ta gama shirya breakfast, Kitchen ta sameta tana juye ruwan
Lipton dake ta kamshi a flask, alamar dai ta gama komai shi kadai ya rage, Heedayah
na xaune daga kusa da kofa hannunta rike da cup din shayi da Saude ta hada mata ga
plate din kwai da dankali da plantain, Hajiya Maryam ta wani xaro ido tace "Saudat
me xan gani haka? Wa ya saki wannan aikin, a ina kika ga yarinyar? Ko a ina kika
santa?" Da sauri Saudat ta xube kasa tana gaisheta tace "Hajiya... Alhaji ne ya
kawo min ita jiya da daddare yace in kula...." Tsawa tayi mata da karfi tace "Toh
wllh a bakin aikin ki, da ya kawo maki ita baki iya xuwa ki sameni ba? Kawai sai ki
yanke hukunci sbda ke ke ajiye da kanki? To wllh kin gama min aiki a gidan nan yau,
yanxun nan xa ki kama gabanki" Hakuri Saude ta dinga bata a tsorace tana cewa
"Hajiya wllh Alhaji ne ya kawo min ita kiyi hakuri ki rufa min asiri, ni ban san
komai ba" Hajiya Maryam tace "Ni dai nace kinyi na aikin ki wllh, maxa tattara
yanaki yanaki" daga haka ta juya ta fice daga kitchen din tana huci. Karfe goma
Alhaji Ahmad ya dau Heedayah suka fita xuwa parking space, Hajiya Maryam dake xaune
ta bi sa da kallon mamaki sannan ta kalli Shuraim dake operating laptop a parlon
tace "Ka gani ko Shuraim, gaskiya abun nan ya fara bani tsoro, wannan abu ba na
hankali bane... Something is wrong somewhere, what is wrong with your father" Shi
dai kallonta kawai yake bai ce komai ba, wayarsa ya fara ring ya dauka ganin
Abbansa ne ya kai kunne, Daga daya bangaren Abba yace "Ka gaya ma babarka karfe sha
daya ne meeting din don Dr ya kirani xai yi tafiya" Shuraim yace "Toh Abba" Daga
haka ya katse wayar, Yana kallon mahaifiyarsa yace "Abba yace Baffa xai yi tafiya,
so da wuri xa ayi meeting din" mikewa Hajiya Maryam tayi tace "Toh ai a shirye nake
sai ka kira kanninka duk mu duguma xuwa gidan, wato baxai iya gaya min ba sai dai
ya bada sako a bani, to duk muje ayi ta ta kare yanxu" Babban gida ne sosai don har
ya fi na Barrister Ahmad girma, Shuraim yyi parking a parking lot din gidan, Mumy
ta fito ta nufi hanyar shiga gidan, direct dakin Hajiya Amina Uwar gidan Alhaji
Umar ta nufa, bayan sun gaisa Hajiya Amina tace "Daxun nan Alhaji ke ce min akwai
meeting wai kuna hanya, ni dai nace to Allah ya sa lafiya" Mumy tace "Ina fa
lafiya, wllh ba lafiya...." Tsaf ta kwashe ma Hajiya Amina abinda ke faruwa ta
sanar mata, Hajiya Amina ta buda ido sosai tace "Iko sai Allah, to meye ma'anar
hakan da Barrister yyi??" Mumy tace "Ni nasan masa, ni dai wllh wllh kinji
rantsuwar musulmi koh?? To yarinyar nan baxata xauna tare da ni ba, ba ruwana....
Haka kawai ban san hawa ba ban san sauka ba yanda duniyar nan ta lalace..." Hajiya
Amina tace "Toh ai dama bbu wannan xancen, taya xaki rike yar da ba a san tushenta
ba, kada ki kuskura wllh, Wai kuma makauniya kamar dai a wasan kwaikwayon hausa..."
Mumy tace "Ke ki bari kawai, nasan karshe Dr yace a barta gidan nan...." Da sauri
Hajiya Amina ta katse ta tace "Wajen wa??? Haba wannan ai labari ne, bbu wanda xai
soma wannan gangancin..." Dariya Mumy tayi tace "Toh ba sai abokiyar xaman ki ta
riketa ba" Hajiya Amina tayi tsaki tace "Ai sai dai ta kai ta gidansu amma wllh bbu
wajen xaman yarinyar nan a gidan nan" Mumy tace "Atoh, taimakon da idan kayi ma
yanxu yake xame maka jaraba" Mikewa tayi tace "Bari in je in gaida tsohuwar can..."
Hajiya Amina tace "Tana can kuwa yau bbu mutunci ta tashi...." Mumy tayi dariya
tace "Ni dai Allah ya dube xuciyata ya rabani alakakai..." Hajiya Amina tace "Wa??
Ai xance komawa gidan ki take yanxu" Mumy tace "Tabdi, xaman mu baxai yiwu ba, wnn
karan karara xan fito inyi magana" daga haka ta fita dakin. Da sallama Mumy ta bude
kofar wani daki ta shiga ciki, babba daki ne sosai bbu abinda bbu a ciki irin dai
na tsoffi, Shuraim na xaune kusa da wata tsohuwa da tayi tsit lkci daya ganin
shigowan Mumy, Mumy na murmushin yake ta xauna kasa tace "Sannu Kaka...." Tsohuwar
na gyara daurin dankwalinta tace
"Sannu..." Mumy tace "An tashi lafiya kaka" kaka tace "eh toh lafiyar kenan, amma
kin gan ni nan?? Wllh tun safe bbu karen da ya leko ni a gidan nan har shi Umarun,
hana rantsuwa dai ya shigo da Asuba ya gama xamansa a can na kusan minti talatin ya
fita, wllh Maryam gidanki ya fiye min nan sau goma, gwara ke da yunwa kawai kike
bari na...." Mumy ta hadiya abu da kyar ta sunkuyar da kanta, Kaka tace "Kinga
wannan bakar matar Amina?? Ni dai ina ga da kyar ta wanye lafiya, ni dai ki tafi da
ni gidanki" Da sauri Mumy tace "Ai hakuri ake yi a ko ina kaka, ko ina hakuri ake
ba wai wani abu ba, kawai ayi ta hakuri tunda Doctor ya fi son yana ganinki kusa da
shi, kuma ma hakan ya fi wllh, yanxu ma meeting muka xo yi bbu lafiya" Da sauri
kaka tace "Me ya faru kuma?" Mumy ta gyara xama tana tabe baki, nan ta tsara ma
Kaka duk yanda aka yi daga daren jiya har xuwa safiyan yanxu har da kari, Kaka da
ta gwalo ido tana kallonta tace "Ba lafiya, shi Ahmadun yace bbu wanda ya isa ya
saka shi ya kuma hanashi?" Mumy tace "Toh nima dai ban gane kan lamarin ba, abun
dai gashi kamar almara" Kaka tace "Toh ina yar makauniyar take yanxu?" Mumy tace
"Tun sassafe ya fice da ita ko bi ta kanmu bai yi ba....."

⚡ _Heedayah_ ⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

6.......

Kaka ta rike ha6a tana kallon Mumy tace "Lallai ba lafiya, Kar ki yarda, ba mu san
irinta ba, kuma ba ma bukatan sani, ba ruwana da jajibe jajibe gaskiya, to meye
kuma na tsinto yarinya kamar wanda nace ma je ka kagani, to ni dai ba ruwana, mu je
ayi meeting din gaba daya, ai kin ga ko shigowa gaisheni ma bai yi ba tunda ya
tsinto wata uwar tasa a titi jiya, kuma ace min lafiya qlau, a'a wllh ba lafiya"
sosai hankalin Mumy ya kwanta jin furucin Kaka, Kaka ta mike ta nufi kofa Mumy na
biye da ita tana murmushi, Shuraim ya bi su da kallo kafin ya mike shi ma ya fita
parlon. Babban parlor ne me dauke da tsadaddun kujeru ba masu hayaniya ba, Hajiya
Amina da kishiyarta Hajiya Hauwa na xaune parlon sai Safiyya, Nafisa da Aisha 'ya
yan Hajiya Amina, Jamila da Zainab 'ya yan Hajiya Hauwa su ma na xaune parlon,
Khadijah da Rabi'ah duk suna parlon su ma, Abba na xaune tare da Heedayah da ya
xaunar gefensa, Alhaji Umar ma na xaune idonsa a kan tv dake nuna tashar Aljazeera,
a tare Hajiya Maryam ta shigo parlon da kaka da ta tsuke fuska, Abba dai kallon
mahaifiyar tasa kawai yake har ta xauna, Shuraim ne ya shigo da sallama ya nemi
kusa da Khadijah ya xauna sannan ya gaida su Hajiya Amina da Baffansa, d'a murmushi
ya amsa gaisuwar cousins din nasa mata dake kallonsa gaba daya, Baffa ya rage
volume din TV din yace "Ina Sudais?" Safiyya tace "Bai dawo training ba" Baffa ya
gyada kai alamar gamsuwa, Abba na kallon kaka yyi kasa da kai yace "An tashi lafiya
kaka?" Kaka tace "A'a ba ruwana, lafiya lau na tashi" tana magana ne tana kallon
Heedayah kasa kasa, Rabi'ah da Khadijah suka gaisheta su ma, tace "To duk ku tashi
ku fita, ko kun ga sa'annin ku a nan, wannan ai ba maganan yara bane, babban magana
ce, Yaron kirkin nan kadai ya cancanci xama a nan, duk ku fita" Hajiya Hauwa tayi
murmushi tana kallon Shuraim da ya sunkuyar da kansa, Mikewa su Khadijah suka yi
gaba daya har da su Safiyya suka fita bbu halin ko yi mata kallon banxa, shiru ne
ya biyo baya a parlon, Baffa ya bude wajen da addu'a, bayan haka ya kalli Hajiya
Maryam yace "Why did u invite our mother in here?" Ta gyara xama tace "Bcos it's
necessary, she needs to know what's happening" Bai kuma cewa komai ba, bayan few
seconds ya daura da cewa "Ba wani abu ya tara mu nan ba... jiya da maraice
Barrister ya dawo gida da wata baiwar Allah wanda hakan ya kawo rashin fahimta a
can gidansa, ga kuma yarinyar dai xaune kusa da shi...." ya fadi haka yana nuna
Heedayah wanda duk kana ganinta kasan a tsorace take, Ya ci gaba kamar haka "Duba
da irin xamanin da muka tsinci kan mu na yanxu a gaskiya hakan ba shawara bace me
kyau it's risky bringing the little girl home, sai dai me??? Mu duba wannan
yarinya, har nawa take gaba daya, duk magidancin kwarai ya ga yarinyar nan that
looks helpless a hanya ba lallai ya iya wuceta bai yi making effort din taimakon ta
ba, ko min kankantar taimakon kuwa, sai dai shi barrister nasan taimakon ya yanko
sa da girma ne tunda har gidansa ya kawo wannan baiwar Allah, wanda ba kowa xai yi
hakan ba a xamanin nan na yau gaskiya, ba wai ina nufin hakan da yyi kuskure bane
amma in the other way round xa a iya kiransa da kuskure...." Kaka dake ta hararan
Baffa ta yi kwafa tana girgixa kafa, Baffa ya ci gaba "Amma kuma xai iya yiwuwa
yaga kawota gidan shine kadai mafita duba da cewa she is unsighted.... Har xuwa
lkcn da Allah xai bayyana iyayenta" Calmly Hajiya Maryam tace "Idan Allah bai
bayyana iyayen nata ba fa?" Baffa yace "Wannan kuma baxa a rasa yanda xa ayi ba in
sha Allah, Hajiya kar ki manta one knows not where his or her reward lies, sannan
muna da baya, we should always try positioning things in our shoes" Girgixa kai
tayi irin ba mutunci tace "Toh ni ban hanasa riketa ba Doctor, Amma Wallahil Azeem
ba ni xan rike masa ita ba,... Ya nemi inda xai kai ta, ko kuma ya bar ta nan wajen
ku ai duk daya ne..." Da sauri Hajiya Amina ta kalleta da wani expression, Kaka ta
kyabe baki tace "To duk kun gama??" Duk aka yi shiru ana kallonta, ta gyara xama
tace "Toh maza tun muna mu bakwai ba mu dawo mu takwas ba a parlon nan Amadu ya
maida wnn yarinya inda ya dauko ta, mu ba gantalallu bane, bamu sa6a kwashe kwashe
ba a dangi, baxa kuma a fara ta kan d'a na ba...." Shiru ne ya biyo bayan abinda
Kaka tace a parlon, Abba da Baffa sai kallonta suke, Hajiya Maryam taji kamar ta
tashi ta rungume kaka don farin ciki, Hajiya Amina kuwa sai murmushi take kasa
kasa, Hajiya Hauwa dai sai kallon Heedayah da ta makale jikin Abba take, Bude kofar
aka yi wani matashi ya shigo da sallama, sanye yake da sport wears, they have many
resemblance in common with Shuraim, sai dai ya girme ma Shuraim da shekara daya duk
da ba wai hakan ya nuna bane, bin occupant din parlon yyi da kallo, coz he knew
nothing about the meeting, ya kalli kaka da ta tsuke fuska ganinsa tace "Kai ka ji
wani neman fitina gun Mutumin nan ko sudais...." xaunawa yyi gefenta coz yasan she
will brief everything a nan take kafin ma ace masa komai a parlon, ta gyara xama
tace "Kanin ubanka dai ya xama abinda ya xama, Wai kaji yarinya ya tsinto ya kawo
gida ba dangin iya balle na baba, har yana ikirarin bbu wanda ya isa ya hanasa
abinda yyi niyya bai san magana xai dawo kunne na ba, Toh mu xuba da shi, idan shi
ya haifeni ai yanxu kowa xai sani, kuma nace masa maxa ya mayar da ita kada raina
ya bace...." Murya can kasa Sudais yace "Wacce yarinya ce?" Heedayah ta nuna masa
rai bace tace "Gata can kamar mage...." Sudais ya kalli Heedayah da ta makale Abba,
sannan ya kalli Abba da Baffansa da suka kasa cewa komai, ya maida dubansa kan
Kaka, lkci daya ya hade rai yace "Toh meye don an taimaki wannan yar yarinyar, ni
na ma xata wani babban abu ne ya faru a gidan, ynxu ba fata ba yau ace Safiyya ko
Jamila sun 6ace baki son wani ya taimaka masu kenan? Kika san dalilin da yasa Allah
ya rabata da iyayenta?? Ke da xaki yi fatan Allah ya bayyana su...." Katse sa tayi
da sauri tace "Kun ji min fitsararren yaro ko?? to ce maka nayi ban yi addu'ar
Allah ya bayyana iyayen nata bane?? Ni dai ba ruwana ka daina min sharri, dama
kwana biyu na fita harkan ka a gidan nan sam baka da mutunci ka rainani...." Ya
mike yace "A'a ni ban rainaki ba kaka ke dai baki son gaskiya, kawai ki bar Abba ya
rike yarinyar a ci gaba da neman iyayenta, ynxu idan ya mayar da ita kika san
hannun wanda xata fada, kinsan fa idan ta fada hannun mugaye ke ma kina da kwamasho
me girma, sannan kin fi kowa cewa aji tsoron Allah, kuma ga lamarin da ya kamata
mutum ya ji tsoron Allah nan...." Tagumi kaka tayi tace "Kuna dai ganin Aliyu ko??
To ba komai rayuwa ce ai" Hajiya Maryam dake ta xufa sai kallon Sudais take tana
hadiye abu da kyar, Baffa dai ya jinginar da kansa da kujera yana kallon d'an nasa,
Abba kam kansa na kasa shi ma yana saurarensa, Hajiya Amina duk uwar hararan da
take xabga ma d'an nata yaki kallon direction dinta, Hajiya Hauwa banda murmushi
bbu abinda take, Sudais na kallon kaka yace "Kawai dai yanxu sbda tsoron Allah ki
bari Abba ya nemo iyayenta, kuma ta xauna har sanda Allah xai bayyana su...." Kaka
tace "To ni dai ba ruwana, dama Maryam ce tace bata yadda ba banda haka ni meye
nawa?? ai d'a na kowa ne bawa sai me shi, me ta min da xan koreta banda abun ka
sudais? Amadu yayi ta rikonta har Mahadi ya bayyana ma bbu abinda ya sha min kai ni
dai...." Sudais ya shafa kansa yace "Idan ya kai xuciyar ki ce masa xa kiyi kin
amince ya riketa" A mugun fusace tace "To ya rike ta mana, ni ina ruwana, ai d'a na
kowa ne, amma gaskiya ka daina min rashin kunya xan hada ka da ubanka, kaf ka raina
ni tamkar ynda uwar ka ta raina ni" ya d'an bude ido ya juya ya nufi kofa xai fita
Kaka tace "Allah yyi min tsari da kai ni dai katon banxa" Abba ya mike xai fita
rike da Heedayah, Hajiya Maryam ta mike da sauri tace "Wllh to ka nemi inda xaka
kai ta ba gidana da na yarana ba..." Kaka ta bude baki tace "Naga bala'i, gidanki
kuma Maryam?? Ta ina hakan ya faru" Baffa yace "Wait Ahmad it's better kasan inda
yarinyar nan xata xauna, u can't force her to hold the little girl, it's not even
possible, tunda tace baxata riketa ba baxa ayi mata dole ba" Abba ya juya yana
kallonsu gaba daya kafin yace komai Hajiya Hauwa tace "Babu damu Barrister, ka kawo
min ita ni xan riketa in sha Allah har iyayenta su bayyana, Allah ya shige mana
gaba, yayi mana mai kyau..." da sauri kaka ta katseta tana wurwurga ido tace "Ki
riketa a wani gidan Kuluwa??? Kaji min mata ba tsoron Allah kamar gidanta, Haka
kawai ba mu san ko mayya bace yarinya dare daya ta karar damu a gidan a shiga uku
xaki wani ce xaki riketa, shi dai Ahmadun da yaga xai iya ya tafi can ya karata, ni
dai Allah ya rufa min asiri ba shi kadai na haifa ba, in dai har ina gidan nan
yarinyar nan baxata xauna ba, idan ko xata xauna sai dai a sallameni in tafi, bbu
ruwana da kwashe kwashe ta kaina nake" tana fadin haka ta juya masu baya kamar
karamar yarinya, Baffa dai sai kallon D'an uwan nasa yake, Hajiya Maryam kuwa sai
hararansa take tana girgixa kafa tana wani murmushi irin ba shi da wata mafita kuma
ai, ya gyada kai yana kallonta da kyau yace "Shikenan, Xan auro warce xata rike ta
a satin nan in sha Allah" Daga haka ya fice daga parlon rike da Heedayah, kasa
motsi Hajiya Maryam tayi jin abinda yace ta bi sa da kallo baki bude, Kaka tayi
wani dariya tace "Atoh dai, tun ba yau ba dama nake cewa kayi aure ka ki, yanxu ai
gashi xaka yi ba don Allah ba, xaman ka da Maryam ko kaddara, gwara ka auro warce
xata rike yar da amana don a ynxu kam yarinyar bata da maraba da marainiya,
tsinanne ne kadai xai ki taimakon ta...." Ta gefen ido Baffa ya kalli mahaifiyar
tasa yyi saurin sunkuyar da kai.

⚡ _Heedayah_⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

7......

Sudais na tsaye compound din gidan nasu Abba ya fito rike da hannun Heedayah,
Sudais ya nufe sa ya gaishesa da ladabi, Abba yace "Lafiya Aliyu, ya weekend?"
Sudais yace "Alhmdllh sir...." Yana kallon Heedayah ya kai hannu kanta yace "How
are you?" Shiru tayi bata ce komai ba, Abba yace "Talk to him Heedayah" tana rike
da hannun Abba a hankali tace "I am fine" Sudais ya mata murmushi yace "Good
girl...." ya kalli Abba yace "Allah ya bayyana iyayenta" Abba yace "Ameen My son"
jin taku a bayansu Sudais ya juya, Shuraim ne ke tahowa yana tafiyar kamar bai son
yi, wani kallo Abba yyi masa ya kalli Shuraim yace "Xan wuce gida ynxu, anjima ka
taho can gidan ka sameni" Sudais yace "In sha Allah...." Daga haka Abba ya bar
wajen xuwa gun motarsa tare da Heedayah, Sudais na kallon Shuraim da ya bi Abbansa
da ido yace "Kai ma baka bada goyon bayan taimakon yarinyar da Abba ke son yi ba
kenan, coz naga kallon da ya maka" Shuraim ya bude hannu yace "But.... She's blind,
ta ina xa a fara kula da ita, is it even possible...." Sake baki Sudais yyi yana
kallonsa a bit shock, can ya juya da sauri ya kalli parking space yaga Abba is
helping her Into the car, ya kara kallon Shuraim yace "Blind? How is that?? Who
told you that, ban gane ba" Shuraim ya shafa kansa yace "Yes makauniya ce..." Yana
fadin haka ya juya ya koma ciki ya bar Sudais a wajen baki bude, Sudais ya kara
satan kallon motar Abba har ya fita compound din.... A hankali Abba ke driving yana
yi yana waigen Heedayah dake shan yoghurt da ya siya mata, muryar ta ya ji tace
"Abba gida xa mu je ynxu wajen Ammina?" Ya gyada mata kai kamar tana ganinsa yace
"In sha Allah" wani babban eatery ya shiga yyi parking yana kallon agogon wrist
dinsa da ke nuna karfe sha biyu saura, wayarsa ya dauka yyi dialing number ya kai
kunne, bayan few seconds yace "Hope you aren't going to keep me waiting Barrister"
bin motar da ya shigo eatery din a dai dai lkcn yyi da kallo sannan ya katse wayar,
Heedayah tace "Abba mun kai gida?" Ya shafa kanta yace "A'a, I want to see a frnd
now, xa ki jirani har in dawo koh?" Ta gyada masa kai a hankali, kamo hannunta yyi
yana murmushi ganin she looks sad and insecure, kamar dai tafiya xai yi ya barta
din nan, mika mata wayarsa yyi yace "Ki rike min wayata har in dawo ynxu, kin ji?"
Ta kara gyada masa kai, ya bude motar ya sauka sannan ya rufe ya nufi entrance din
eatery din, Table din dake dauke da wata mata that is in her early fifty ya nufa,
kana ganinta kaga well educated bafillatana cikin shiga ta kamala, ya ja kujera ya
xauna yace "Good morning Barrister" Ta ajiye wayar hannunta da take operating tana
kallonsa ta cikin siririn glass din idonta tace "Morning, ya family, ya weekend?"
ya gyada kai yace "Alhmdllh mun gode Allah" tace "Hope ba aiki xaka hadani da shi
ba kace xaka yi tafiya, coz nima tafiyan xanyi gobe in sha Allah" yayi 'yar dariya
yace "Not at all, how are the children?" Tace "They are all alhmdllh, ya su
Rabi'ah?" yace "Lfya lau" tace "Toh Maa sha Allah" shiru ne ya biyo baya, bayan few
seconds ya kalleta yace "Ba aiki xan baki ba, na dai xo maki da magana mai
muhimmanci ne Hajiya Rahinah..." kallonsa tayi ita ma tace "Ohk Am all ears in sha
Allah barrister, Allah kuma yasa dai lafiya" yace "Sai alkhairi, Hajiya Rahinah na
gayyatoki nan ne.... To ask for ur hand in marriage" Da wani irin mamaki take
kallonsa wanda hakan bai bata damar iya ce masa komai ba, yyi kasa da murya yace
"Yes nasan xa ki yi mamaki but ba abun mamaki bane, I want to marry you..." Ta yi
wani yake tace "Haba Barrister, do you even know what u are saying, ni ynxu auren
me xan kuma yi? Me nake nema a rayuwa...." Ya katse ta yace "Aure shine rufin
asirinki let me tell you idan baki sani ba, idan kika yi aure kimarki da darajar ki
xai fi haka a gun jama'ah, I have known you for more than 15 years now tun mijin ki
na da rai...." Bude handbag dinta tayi ta ciro tissue don nan da nan har hawaye ya
kawo idonta, ya girgixa kai yace "I don't mean to hurt you ko in fama maki ciwon
xuciyar ki Rahinah, kar ki manta tun ba yanxu ba na sha baki shawaran kiyi aure sai
ki ce min sai kinyi shawara, to yanxu na yanke shawarar auren ki for 3 reasons,
which I will let you know ko ba yanxu ba" tace "I am sorry Ahmad bana tunanin xan
yi aure har karshen rayuwata, rabuwan tashin hankali nayi da mijina ba wai normal
rabuwa, bana da ra'ayin aure har abada" ya katse ta ya d'an buga table din gabansu
yace "Stop this nonsense Rahinah..." A d'an fusace tace "In koma gida ince ma
yarana xan yi aure? Me ye nake nema a duniya a yanxu? Me yarana suka rage ni da shi
da xai sa inji ina sha'awar yin aure? Plss come off this barrister" Ya lumshe ido
ya bude yace "Noo Rahinah, ba don kin rasa komai xaki yi aure ba sai don auren
shine suturar ya mace...." Tana goge hawayen idonta tace "Idan ma sbda tafiye
tafiyen da nake yi ne ko sbda Aikina ni naji xan ajiye in xauna gidana dama Junaid
ya fi son haka, tun ba yau ba yake son in daina aikina coz ban rasa komai daga
garesu ba, ni kuma xaman kadaici ne dama bana so" Kallonta kawai yake, ya sauke
boyayyen ajiyar xuciya yace "I'm sorry I am making you cry this much, I'm sorry
Rahinah" tayi murmushin karfin hali tace "It's okay...." A hankali yace "Xa mu ci
gaba da magana amma ba ynxu ba, it's almost time for zuhur, but...." Jin yyi shiru
ta kallesa tace "But?" Ya sakar mata murmushi yace "Ban hakura ba, anyway that
aside xan baki yarinya ki tafi da ita, for now marainiya ce bata da kowa...." Da
mamaki take kallonsa tace "Ban gane ba, a ina ka samo ta..." Briefly ya 6ata
labarin Heedayah, wanda hakan yasa jikinta yyi sanyi tace "Allah sarki, Allah ya
bayyana iyayenta, I will go with her in sha Allah" yace "Yes I know u will Rahinah,
sai dai I didn't made mention of her blindness to you, she's blind" xaro ido tayi
tace "Blind??" A hankali ya gyada mata kai, tace "Innalillahi wa Inna ilaihi
raji'un" yace "Tana mota ita kadai, mu tafi ki ganta" a tare suka fita eatery din,
sai da suka kusa motarsa a hankali tace "Matar ka tace baxata riketa ba kenan?" Ya
juya ya kalleta ya d'an yi murmushi yace "Ehh" Ta girgixa kai tace "Toh Allah ya
kyauta" yace "Ameen, amma a gidana Heedayah xata xauna, she will stay with u just
for few days let me settle down things" Bude mota yyi Heedayah ta juya direction
din da sauri fuskarta duk hawaye tace "Abba" ya kamo hannunta yace "Kuka kike yi
daughter" cikin rawar murya tace "Naga baka dawo ba" ya share mata ido yace "I'm
back dear, xaki bi Maminki gida yanxu kin ji?" Tace "Abba ina xaka je?" Yace "Xan
je in siyo maki sabbin kaya ko baki so" tayi shiru bata ce komai ba, Hajiya Rahinah
dake ta kallon Heedayah da tausayi tace "Ba dadewa xai yi ba baby, mu je gida kafin
ya kawo maki kayan" daga haka ta sauketa a motar, ya kalleta yana murmushi yace
"Thanks Barrister, sai na xo anjima" ta gyada masa kai ta nufi motarta da Heedayah,
sai da ya ga fitansu sannan ya ja motarsa ya bar Haraban eatery din shi ma. Hajiya
Rahinah na parking a parking space ta bude motar ta fito, wata yarinya da baxata
haura sha hudu ba ta iso gun motar tace "Mami sannu da dawowa" Tana mika mata
handbag dinta tace "Thanks dear, har kin gama assignment din?" Tace "Ehh na gama"
Mami ta xaga xuwa side din Heedayah tace "Junaid ya xo kuwa?" Yarinyar ta girgixa
kai tace "A'a.." bude motar tayi ta sakko da Heedayah, xaro ido yarinyar nata tayi
tace "Mami who is she?" Mami tace "Bakuwa" daga haka ta rufe motar tana rike da
hannun Heedayah ta nufi entrance din shiga cikin gidan 'yar ta Farida na biye da
ita a baya...

07087865788

Hajiya Rahinah na xaune parlonta watching a movie, almost absentminded, lkci lkci
take kallon Heedayah da ke xaune kasan lallausan carpet dake tsakar parlon, Short
bread ne hannunta tana ci a hankali, irin kallon da take ma kofar kitchen sai kace
tana ganin kofar ne da idanuwanta, Hajiya Rahinah ta sauke ajiyar xuciya for the
countless time ta girgixa kai, ba karamin tausayin Heedayah take ba har ranta, text
ne ya shigo wayarta ta dauka sanin baxai wuce Barrister ba, dai dai nan kuma aka yi
knocking kofar parlon, Farida dake xaune dining tana shan cornflakes ta mike ta
nufi kofar, bude kofar tayi wani matashi dake tsaye bakin kofar yana kallonta yace
"Baki je islamiyya ba?" Ta langwabar da kai tace "Mami tace I should stay behind
xata fita ynxu" Xai yi magana ganin Mahaifiyarsa xaune parlon ya shiga ciki da
sallama, Farida ta rufe kofar ta koma dining, xaunawa yyi kujeran dake kusa da na
mum din tasa yace "Ina yini Mami" tana danna wayarta tace "Lfya lau, jiya baka xo
ba Why?" Ya shafa kansa a hankali yace "Mami Uncle ne ya bani aiki, amma kin manta
ne nace maki baxan dawo ba" Tace "Ohk, ka kai ma Salma sakonta kuwa" yace "Eh daga
can nake, har xan kawo maki Fadil wai xai biyo ni na fasa, kar ya xo yyi ta mana
kuka" Tace "Gobe ma Monday akwai aiki ai" Yana kallon Farida yace "Mami wai ke kika
ce kar ta tafi islamiyya?" Da sauri Junaid ya dauke kafarsa xai mike jin abu na
ta6a sa, bai kai ga cewa komai ba ya ga Heedayah rakube jikin kujeran da yake
xaune, Kuri tayi ma kafarsa da ido, ya mike ya dinga kallonta, Mami tayi dariya
tace "Kai dai ka fiye tsoro kamar mace" Yace "Mami wacece wnn kuma?" Mami tace
"Bakuwa nayi daxu" hade fuska yyi ya canxa kujera ya xauna, Mami ta mike tana
kallon Farida tace "Ki dawo nan parlor ki xauna, yanxu xan fita, you make sure baki
bar ta ita kadai ba, I will be back soon, kasuwa xan je" Farida ta mike ta dawo
parlon, Mami ta nufi Heedayah ta duka tana kallonta ta shafa kanta tace "Kina son
wani abu dear?" Gyada kai tayi tace "Xan sha ruwa" Mami tace "Farida ki kawo mata
ruwa" Farida ta tafi fridge dauko ruwa, Mami ta kalli Junaid tace "Sai na dawo, I
am not staying long" ya mike yace "Ni ma ai wucewa xan yi Mami" tace "Aa ka jira
ni, I said I am not staying long" daga haka ta nufi kofa, da kallo ya bi ta har ta
fita, sannan ya koma ya xauna yana kallon Farida yace "Who is she? I mean the girl"
Farida ta bude hannu tace "Mami came back with her earlier this afternoon" Ya buda
ido sosai yace "From where?" Farida tace "I don't know" girgixa kai yyi ya kara
satan kallon Heedayah, direction dinsa take kallo, ya d'an hade rai calmly yace
"Kin san ni ne kike kallona?" Laluben kasa ta shiga yi tana neman murfin bottle
water cikin sanyin muryarta tace "Ni ba kallon ka nake ba" yace "Hoto kike daukata
da idon ki idan ba kallona kike ba kenan" Ta d'an turo baki bata ce masa komai ba
tana ci gaba da lalube lalubenta, Farida ta koma kusa da shi da sauri ta kai
bakinta kunnensa cikin rada tace "Yaya she is blind fa!!!" irin yanda ya yo waje da
ido yana kara kallon Heedayah yasa Farida tayi dariya bata shirya ba, ta dinga
dariya har da kyakyatawa da saukowa saman kujera, Shi kam kallon Heedayah kawai
yake da mamaki ya ma kasa cewa komai, bai ankara ba sai ganin hawaye na sauka
fararen idanuwanta yyi, Bai san lkcn da ya mike ba, Farida ma ta hadiye dariyar da
take tana kallonta, ya nufeta ya duka kusa da ita yace "Me yasa kike kuka??"
Shessheka ta fara yi tace "Xan tafi gun Abba" Farida ta dawo kusa da ita da sauri
tace "Yanxu fa Mami xata dawo" Junaid ya kai mata rankwashi a kai yace "She thought
u are laughing at her... What's making u laugh that loud at the first place" Farida
tace "Kiyi hakuri, ba dake nayi dariya ba wllh" Ita dai Heedayah sai juya biscuit
din hannunta take hawaye na xuba idonta, Junaid yace "Kin ji ta baki hakuri, kiyi
hakuri kin ji" Shiru tayi masu, ya dafa goshinta yana goge mata hawayen da hannunsa
yace "Kin hakura?" gyada masa kai kawai tayi, nan kuma ta daina hawayen, mikewa yyi
ya koma kujera ya xauna so relieved ganin ta daina kukan, shi dai fa har sannan ya
kasa yrda bata gani don gashi sai kallonsu take tana kifta fararen idanuwan, Farida
ta rufe bottle water din ta mike ta koma kan kujera ita ma, Junaid ya dau wayarsa
ya shiga gun msg yyi typing kamar haka, "Da gaske bata gani? Don't joke with me"
mika ma Farida wayar yyi, Farida na karantawa ta kallesa tayi masa alamar rantsuwa
cewar Heedayah bata gani, kara kallon Heedayah yyi da shock, can ya mike ya wuce
sama yana kara waigo ta. Farida ta canxa tasha ta maida hankalinta kan movie din da
ake yi, bayan kusan awa daya taji muryar Junaid ya sakko kasa yace "Why don't you
tell her to lie down Farida?" Farida ta juya da sauri tana kallon Heedayah da ta
kwantar da kanta saman kujera tana bacci daga xaunen da take, Farida ta mike tace
"Ban sani ba" nufenta tayi ta ta6a ta tace "Ki tashi in raka ki daki" Heedayah ta
bude ido da sauri tace "Aa" Farida tace "To hau kan kujera" mikewa tayi ta fara
laluben kujeran, shi dai Junaid kallonta kawai yake, Farida ta sa ta kwanta kan
kujeran sannan ta koma ta xauna. Shidda da yan Mintuna Mami ta shigo gidan da
ledoji manya manya, Farida dake parlon har sannan ta mike tana mata sannu da xuwa
ta amshi ledojin, Mami da hankalin ta na kan Heedayah tace "Me yasa kika bari tayi
bacci ta yamman nan?" Farida tace "Ina son in tasheta daxu yaya yace in bar ta"
Mami tace "Ina yayan?" Kafin Farida tace komai sai gashi nan sakkowa, Mami ta nufi
Heedayah ta dafa kanta tace "Dear" bude ido tayi da sauri, Mami tace "Yamma yayi
tashi kar ki yi sake bacci" Heedayah tace "Abbana fa?" Mami tace "Ga kaya nan Abban
ki yace a kawo maki..." Heedayah ta katse ta tace "A'a ina son in je wajensa" Mami
tayi murmushi tace "To yana jiran ki a waje" kallon Junaid Mami tayi tace "Take her
outside, xaka ga mota a waje, ka kai ta motar" shiru yyi yana kallon mum din tasa,
ganin ko kallonsa bata yi ba sai bude ledojin da Farida ta ajiye take, ya karaso
cikin parlon yace "But Mami I thought she's blind how will I take her outside" Mami
ta hade rai tace "Kama hannunta xaka yi ku tafi, ko in kai ta da kai na?" Ya
girgixa kai yace "Aa" ya nufi gun Heedayah, Farida sai dariya take kasa kasa, ya
kamo hannun ta jin haka ta sakko daga saman kujeran, kamar me counting steps dinsa
ya nufi kofar fita yana rike da hannunta, Farida ta bi su da kallo tana danne
dariyar ta, sai da suka fita parlon, Heedayah dake ta bin sa tace "Ha'an da sauri
kake tafiya xan je in fadi" kallonta yyi sannan yace "To ba sai ki fadi ba" Bata ce
masa komai ba har suka fita gate, ya nufi motar da ya gani a bakin gate din, Bude
motar aka yi barrister ya fito, ganinsa Junaid ya yi kasa da kai ya gaishesa da
ladabi, Abba ya amsa da fara'a yace "How are you doing Junaid?" Yace "I'm fine sir"
Abba yace "Ashe ka dawo, kuna hutu ne?" Junaid yace "Ehh Abba mun yi hutu" Abba
yace "To maa Sha Allah, Allah ya taimaka son" Junaid yace "Ameen nagode" Heedayah
sai murmushi take jin muryar Abba, ta fara lalube lalube xata ta6a sa, Murmushi yyi
ya duka kusa da ita ya kamo hannunta yace "How are you my dear?" Ta fada jikinsa a
hankai tace "I am fine Abba, are you taking me with you now??" ta gefen ido Junaid
ya dinga kallonta, nan kuwa he is trying to vividly recall weda he said anything
bad daxu da turanci da yyi magana da Farida.... Abba yace "No, xaki tsaya tare da
Mami kinga ni xan tafi aiki ne" tayi shiru bata ce komai ba, amma gaba daya mood
dinta har ya canxa, yace "Ga kaya Mami ta siya maki da yawa sai ki ce mata thank
you idan kun koma ciki" a hankali tace "Ohk" yayi patting kanta yace "Good girl"
cikin sanyin murya tace "Abba yaushe xan koma gun Ammina da Abbuna?" Tana magana
har hawaye ya kawo idonta, Shiru yyi yana kallonta, can yace "Soon daughter, in sha
Allah soon xa ki koma wajensu" mikewa yyi yana kallon Junaid yace "Ku koma ciki
Junaid" Junaid ya kama hannunta yace "Toh Abba Allah ya kiyaye hanya" Abba yace
"Ameen" Sai da suka shiga gate sannan Junaid ya kalleta yace "Ina Ammin taki da
Abban ki???" shiru tayi bata ce komai ba, yace "Baki ji na ne?" A takaice tace masa
"Ehh" tsayawa yyi da mamaki yana kallonta, can ya saketa ya koma gefe ya tsaya yace
"To ai sai ki kai kanki ciki"

⚡ _Heedayah_ ⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

Da asuba bayan an idar da sllh a masallaci da kusan minti sha biyar Shuraim ya mike
ganin Abbansa xai fita masallacin don dama shi yake jira, sai da suka fita
masallacin ya isa gun Abban nasa, ya d'an risina yace "Barka da asuba Abba" Abba ya
kallesa ba tare da ya tsaya ba yana ci gaba da tafiya yace "Yauwa...." Shuraim na
biye da shi yace "Abba dama ina son baka hakuri ne kan abubuwan dake faruwa...."
Abba ya katse sa yace "A'a kaje dai ka ba babarka hakuri, ita ta fi daukan abun da
xafi, sannan kuma dama a bayanta kake as always" Ya girgixa kai yace "A'a Abba, ba
wai ina bayanta bane, just that muna tsoron abinda xai je ya dawo ne a kan
lamarin...." Abba yyi murmushi yace "Ehh gaskiya ne Ali, barin ma da ya kasance
cewar duk abinda yaro ya hango ba lallai babba ya hango ba" Shuraim yace "A'a ba
haka bne" Abba yace "No haka ne" Shiru Shuraim yyi yana dai biye da Abban nasa, can
yace "Toh Abba tana ina yarinyar ynxu?" Abba ya tsaya ya juya yana kallonsa yace
"Do you have any problem with that?" Bai iya yace komai ba, Abba ya watsa masa wani
kallo ya ci gaba da tafiyarsa, Har suka shiga gida babu abinda Shuraim ya sake ce
masa. Reaction din Abban nasa bai hanasa bin sa har cikin parlonsa ba, Abba ya
xauna saman kujera ya dau remote xai powering TV, Shuraim ya xauna kasa daga
gefensa, a hankali yace "Kayi hakuri Abba, ni ban ga aibun abinda kayi ba haka ma
ban ga aibun abinda Mumy tayi ba, she's right in many ways" kallonsa kawai Mahaifin
nasa yake, can ya girgixa kai yace "Baxa ka ta6a yin alkibla ba dama, look... Ur
mother like it or not dole gidan nan Heedayah xata xauna har sai naga she's back to
her parent, idan ku ka ga Heedayah bata dawo gidan nan ba to iyayenta ne Allah ya
bayyanar, amma I mean it, bbu abinda xae hana hakan, kuma tare xata dawo gidan nan
da matar da xan aura ta kula da ita, ur mother can do whatever she want bbu wanda
ya isa canxa ra'ayina" Shuraim dake kallonsa da wani expression yace "Abba aure??
I'm sorry to say... you want to spoil ur home because of a mere little girl da baka
san ma me ya rabata da iyayenta ba, baka san daga inda ta fito ba, think about it
plss Abba, this is wrong" Abba yyi wani murmushi yace "It's my home not urs, ko da
wasa ai baxa ka gaya ma uwarka irin wannan maganar da kake gaya min ba yanxu, ni
kuma ga abokin rainin ka, check out pls my frnd" Mikewa Shuraim yyi kamar baxai ce
komai ba sai kuma yace "Kayi hakuri" daga haka ya fice daga parlon, lkci daya ya
hade rai bayan ya fita ya nufi dakinsa, who the hell is this forsaken girl that's
trying to cause confusion in their home.... Muryar Mumy yaji tace "Ya aka yi
Shuraim? What's wrong?" Tsayawa yyi ya juyo bbu walwala yace "Ina kwana Mumy" tace
"Lafiya lau, ya naga ranka a bace haka?" Yyi kasa da kai yace "Nothing mum, xan
shirya ne yanxu" daga haka ya juya ya shige dakinsa, sarai tasan daga parlon
Abbansa ya fito, ta d'an yi jim kamar me naxari sannan tayi murmushi ta juya ta
nufi dakinta a ranta tace Idan barrister ya san wata bai san wata ba ai.... Karfe
sha biyu saura na safiyar ranan barrister ya isa gidan Yayansa Dr Umar, yana shiga
main parlor bangaren Mahaifiyarsu ya nufa, ya bude kofar parlon tare da sallama, a
guje kaka ke kokarin boye bowl din gabanta tana cewa "Naga fitina waye kuma wannan"
d'an murmushi yyi ya karasa cikin parlon, tace "Au ashe Amadu ne, wllh na xata
yaran nan ne masu halayyar bera, to idan na ajiye d'an nama na da cin cin sai su bi
dare su yashe...." Abba yace "Ina yini Baaba?" Kaka tace "Lfya lau Amadu, ya aikin"
yace "Alhmdllh, ke daya ce gidan kenan" Da sauri tace "To da fa?? Ai Kullum a haka
suke bari na, kar fa kayi xaton basu gidan, duk suna nan wllh, dama wannan yaro
Aliyu ne me shigo min, shi ma kuma na koresa gaskiya, don raini ya shiga tsakanin
mu" Abba yace "Daga gun aiki nake nace bari in xo mu gaisa" Kaka tace "To ae ka
kyauta, Allah yyi maka albarka, Wai ya maganar da kayi ranan na cewa xaka kara aure
ne naji shiru" yace "Ehh dama xan gaya maki maganan na nan in sha Allah..." Kaka na
washe baki tace "Toh Alhmdllh, yar ina ce?" Yace "Nan kaduna" kaka tace "Abu me
sauki, to ni dai Allah ya sa ta kirki ce, don Maryam ta gasa mana Aya a hannu
gaskiya, to ta amince xata rike yar makauniyar??" Abba yace "Ehh ba matsala" kaka
tace "Atoh ita da ke tsoron Allah kenan, Maryam ae shaidaniya ce sanye da kaya irin
na mutane" Abba ya mike yace "Bari in je kaka sai na shigo ko gobe" Kaka tace "Toh,
ni dai haka nn nake sae bin yara nake ina rokon hamsin, dari, suna xagina suna ba
ni" Abba ya juya yana kallonta da sauri, ta tsuke fuska tace "A'a kai ba ubana bne
da xaka min kallon tuhuma Amadu, idan gantalalliyar dubu ashirin din ka ce ta
shekaranjiya to ta kare tun jiya wllh" Bai ce komai ba ya nufi kofa ya bude yace
"Sae anjima" Daga haka ya fita. Hajiya Rahinah ce xaune tare da Barrister kan
kujerun dake karkashin inuwar bishiyar tsakar gidanta, barrister ya ajiye wayar
hannunsa yace "Sae kuma kika yi shiru" Sae a sannan ta kallesa tace "Ehh shirun
naga xai fi, barrister in dae har sbda wannan yarinyar kke son aurena, ina nufin
indan sbda in riketa ne to kar ka damu ni me iya rike little girl din ne har
bayyanar iyayenta idan Allah ya yrda, ina hada ka da Allah ka rabani da xancen
auren ka, bbu aure a tsarin rayuwata ynxu...." Shiru yyi yana kallonta, sannan ya
d'an yi murmushi yace "Sae dai fa kiyi hakuri Rahinah, you can't stop me from
marrying you, Heedayah kuma gidana nake son ta xauna ba wani waje daban ba" Mami ta
tabe baki sae dai bata ce komai ba, Budewar gate ya sa duk suka juya, Junaid ne ya
shigo compound din hannunsa rike da Makullin mota, har ya isa inda suke ya fara
gaida Abba sannan ya gaida Maminsa, Abba yace "Kana aiki ne Junaid?" Yace "Ehh ina
aiki tare da Uncle dina a hospital dinsa" Abba yace "To that's good ya fi ka xauna,
Allah ya taimaka" Yace "Ameen" daga haka ya wuce ciki, Abba ya kalli Mami yace "Ya
kusa gama masters din nasa ne?" Mami tace "Ehh months suka rage masa idan Allah ya
yrda" Abba yace "Allah ya taimaka" Junaid na shiga parlor ya ga Heedayah ce kadai
parlon kwance saman kujera tana bacci, ya dauke idonsa ya wuce sama xuwa bedroom
dinsa. Sae kusan la'asar Abba ya bar gidan har sannan kuma bai yi convincing Hajiya
Rahinah ba dake kan bakanta na cewa bbu aure a gabanta. Yau dai har sha daya saura
na dare Hajiya Maryam na xaune parlor tana jiran ganin lkcn da barrister dake
compound yana ta waya xai shigo, yau kwana biyu kenan da ta lura da hakan duk da
kasancewar ta mai bacci da wuri yau kam coffee me kauri ta sha tayi xamanta a
parlor tana jiran ganin ikon Allah, lkci lkci take tashi ta leka waje ta dawo,
lekawar da tayi na karshe ne taga ya gama wayar xai shigo ciki, da sauri ta shige
kitchen ta kulle don ma kar ya san idonta biyu, sae da taji ya wuce part dinsa
sannan ta fito ta dinga xaga parlor tana jiran ya kwanta sanin bashi da wuyar
bacci, a haka Shuraim ya sakko downstairs ya sameta, ganinta da mamaki yace "Mum
baki kwanta ba" Tace "Ehh yanxu dai xan je in kwanta na gama kallon wani film ne"
Bai ce komai ba ta wuce sama shi kuma ya shiga kitchen, sae da taji Shuraim ya
shiga dakinsa ta fito ta nufi part din mai gidan nata, a hankali ta bude kofar
parlonsa ganin wuta a kashe ta gane ya kwanta, ta lallaba ta nufi daki tana tafiya
a hankali, tana shiga duk da wutan a kashe yake tasan yyi bacci ta tafi inda tasan
yana ajiye wayarsa ta dauka ta fita daga dakin, bangarenta ta koma ta bude wayar ta
shiga call log dinsa, Number da aka yi saving da Great barrister taga last call
dinsa, nan ta duba taga yana yawan kiran number, msg ta shiga tayi scrolling har
xuwa farko, hankalin ta ya fara kwanciya ganin kawai text ne da ya shafi aiki, a
hankali ta fara gwalo ido bayan tayi nisa ganin salon message din ya fara sauyawa
har ta kai karshe, xufa ne ya karyo mata ta ajiye wayar ta rasa tunanin da xata yi,
can ta dau wayarta ta kwashe number tas sannan tayi dialing, sae da ya kusa katsewa
aka daga, daga daya bangaren Mami tayi sallama, shiru Hajiya Maryam tayi xuciyar ta
na bugawa jin muryar mace, kawai ta katse ji tayi kamar ta daura hannu a ka tayi ta
ihu, ta xauna gefen gado tana furta innalillahi, kallon wayarta tayi, sae kuma ta
shiga call log tayi dialing wani lamba, yana fara ring aka dauka, Ta hadiye abu da
kyar tace "Sadiya wllh da gaske Barrister neman aure yake, Ashe da gaske yake wllh,
gashi ynxu na bincike wayarsa kaff har na samu lambar warce yake nema da aure, na
shiga ukuna Sadiya, da yarinta ta ba a min kishiya ba sai yanxu a kan wata shegiyar
yar tsintuwa makauniya...." Ta fashe da matsanancin kuka tace "In dai Alhaji yyi
auren nan ai tawa ta kare, dariya xa ayi min a gari ki bani shawara don Allah
kawata, wllh dariya makiyana xa su min" Hajiya Sadiya dake saurarenta baki bude
tace "Aure fa kika ce Maryam?? Ke sai ki yrda ki barsa yyi auren? Toh ynxu dai ae
sai ki wanke kafarki mu tafi inda kike ikirarin bbu abinda xai kai ki" Hajiya
Maryam tace "Ina???" Hajiya Sadiya ta kyalkyale da dariya tace "Wa enda kike raina
taimakonsu mana...." A fusace Hajiya Maryam tace "Allah shi kiyaye, tun da can da
kuruciyata ban ta6a xuwa ba sai ynxu a kan yar yarinyar da na haifa?? Yar cikina?
Ni nan da kike gani na ishi kowa wllh, Kuma muna nan dake auren nan baxae ta6a
yiwuwa ba ni nasan me xan yi, ke dai kawai ki xo gobe don Allah, sae da safe" daga
haka ta katse wayar, ta kusa awa daya xaune kafin ta iya tashi ta mayar masa da
wayarsa ta dawo dakinta, daren ranan bata yi baccin kirki ba, Wai ita barrister xai
ma kishiya sbda taki rike makauniya??? Tayi kwafa ta juya tana jiran dai gari ya
waye. Mami na xaune tana ma Heedayah gyaran dogon gashinta dake ta kyalli, yau ma
dai bata je aikin ba don har lkcn bata samu wanda xai kulan mata da Heedayah ba,
Farida kuwa na boko daga safe har 6, wayarta ne ya fara ring ta dauka ta kai kunne,
sallama aka yi mata daga daya bangaren ta amsa, Hajiya Maryam dake xaune dakinta da
Hajiya Sadiya da wata kawarsu Hajiya kyauta
tace "Don Allah da barrister nake magana" Mami tace "Yes, wacece ke magana?"
Hajiya Maryam ta gyara xama tace "Toh Barrister wata yar matsala ce wllh ta taso
mana muna neman lawyer, shine wani abokin aikina ya bani lambar ki, yyi assuring
dina you can help..." Mami tace "Allah sarki sai dai na dau hutu baxan yi aiki ba
cikin satin nan gaba daya" Hajiya Maryam ta gwalo ido tace "Don Allah ki taimaka
barrister, ya gaya min irin kirkin ki da taimakon ki, ke kadai xaki iya rufa mana
asiri kan lamarin nan, don Allah barrister ki dubi girman Allah ki sauraremu, wllh
muna cikin tashin hankali sosai" Mami tace "Kar ki damu malama xan hada ki da wani
barrister, he is also good xama ki ji dadin nasa aikin fiye da nawa, I can send you
his number now" da sauri Hajiya Sadiya tayi ma Hajiya Maryam alamar tace mata to ta
turo... Hajiya Maryam tace "Toh ngd Barrister, Allah ya saka, ina jiran lambar"
Mami tace "Kar ki damu, let me send you" daga hka ta katse wayar, cikin few seconds
ta tura ma Hajiya Maryam number Barrister Ahmad, Hajiya Maryam da ta ji kmr
xuciyarta ya fashe cikin tashin hankali tace "Na shiga uku, kun ga lambar mijina ta
turo min dai koh???" Hajiya Sadiya tace "Toh sake kiranta" hannu na rawa ta sake
kira, Hajiya Sadiya ta amshe wayar tace "Ki dubi girman Allah Barrister ki bamu
lkcn ki ki saurari matsalar mu, an ce mana ke ce maganin kukan mu, wllh ko nawa
kika bukata xa mu biyaki domin Allah ki taimake mu..." Da mamaki Mami tace "Wnn
barristern da na tura maki numbersa ya ma fini iya aiki, xae saurare ku fiye da
ynda ni xan saurare ku" da kyar da kyar suka shawo kan Mami kan ta amshi case
dinsu, Mami ta girgixa kai tace "Gaskiya baxan fita gidana ba ynxu, sae dai ko ke
ki xo ki sameni" Hajiya Maryam tace "Wnn ae ba matsala bane, bari in taho ynxu ma,
Allah ya kara girma da daukaka Barrister, ki turo min address din plss" Mami tace
"Ameen, xan tura maki ynxu" daga hka ta katse wayar, ta tura address din nata,
Hajiya Maryam tayi wani murmushi ta mike ta dau mayafi da Makullin mota jikinta har
wani 6ari yake tace "Ku mu je" fita duk suka yi suka bar gidan a motarta. Gane
gidan Hajiya Rahinah bai masu wahala ba, suka yi parking a waje bayan sun sanar ma
Mai gadi Hajiya Rahinah suke nema kuma ta san da xuwansu ya bar su suka shiga cikin
gidan. Har entrance din shiga gidan suka nufa suka tsaya, Hajiya Sadiya ta danna
bell, Mami da ta saka Heedayah gaba tana mata tambayoyin ynda aka yi har ta fito
gida.... exactly labarin da Heedayah ta bada a station ta sake ba Mami, ta kare da
cewa sai taji ana tafiya da ita a bicycle kawai sai ya wuce ya bar ta bai kai ta
gun Amminta ba kuma, tana fadin haka ta fara hawaye, Mami dake ta naxarin d'an
labarin ta gane daga all indication kidnapping yarinyar aka yi sai kuma Allah ya
kubutar da ita, mikewa tayi jin an sake danna bell for the third time ta nufi kofa
ta bude tana kallonsu Hajiya Maryam, Hajiya Maryam ta kirkiro murmushi tace "Sannu
fatan ke ce barristern?" Mami tace "Oh, okay ga kujeru can bari in fito yanxu, ku
jirani a can" Hajiya Maryam ta saka kai ta raba ta gefenta ta shiga ciki, tace "A'a
xai fi daga cikin dai barrister, tonon asiri ai ba dadi" sauran ma duk suka shige
ta gefenta, kallonsu Mami tayi da d'an mamaki, Hajiya Maryam ta isa tsakiyar parlon
tana kallon Heedayah da wani expression, sauran kawayenta ma duk suka tsaya kusa da
ita suna kallon Heedayar, Kasancewar Mami lawyerr yasa lkci daya ta gane abinda ya
kawo matan nn gidanta ba abinda suka ce bane, Hajiya Maryam tace "Toh kinyi tsaye
bakin kofa ae sai ki karaso ki ji case din mu koh barrister?" Heedayah dake xaune
saman kujera da apple a hannunta ta mike da sauri don in dai ta ta6a jin murya to
baya ta6a bacewa a sense of hearing dinta, ko da kuwa an dau lkci sosai sai ta gane
muryar duk inda taji, Mami ta karaso parlon tace "Bana bukatar jin case din ku,
domin bana hulda da Yan tasha, ku kai case din ku wani wurin, and ku fitar min a
gida immediately now...." Hajiya Maryam tayi wani dariyar rainin hankali tace
"Koh?? To sai ki fitar da mu ta karfi Mai gida, bari ki ji..... ba barrister ba, ko
judge ce ke na xo ne in yankar maki lafiyayyen wani ki fita hanyar mijina Barrister
Ahmad, shi ba gantalalle bane irin ki, kin gama xaga duniya kinyi yawon
karuwancinki shine xaki wani makale masa ya aure ki sbda baki da tunani ko? To wllh
kin yi kadan, mijina ba sa'an auren ki bane, Ashe ke ya kawo wa shegiyar yarinyar
nan kika karba kika rike tunda dama kina sonsa da aure, to don kaza kazan ki nace
baki isa ba, mijina ni kadai ne shi din, baxan hada shi da karuwa ba yar boko da ke
yawon duniya don ma kiji, don haka tun wuri ki san inda dare yyi maki" Tunda ta
fara Mami ke kallonta, duk da maganganun sun ma Heedayah girma ba duka xata iya
ganewa ba hakan bai hanata dinga kuka ba tana kiran Mami, Mami ta nufi gun wayarta
ta dauka cikin few seconds tayi dialing number Abba, yana fara ringing kuwa ya daga
ta sa hands free tace "Ahmad kana ji na?" Yace "Yeah ina ji my barrister, ya
gidan?" Tace "Alhmdllh, dama nace ne you can come forward with ur pride price to my
elders ko gobe, na karbi tayin auren ka idan Allah ya yrda" Yace "Da gaske kike
barrister, pls don't joke with me" farin ciki ne sosai tare da words dinsa, Mami
tace "I'm not joking barrister, na baka go ahead, we will talk later in sha Allah"
daga haka ta katse wayar, Hajiya Maryam da wani xaxxafan xufa ya keto mata ta dinga
kallon Mami so speechless, Mami ta isa gabanta ta tsaya tace "xa mu shigo gidan
barrister Ahmad tare da wannan yar yarinyar nan da sati daya, sai dai ciwon xuciya
ya kashe ki a banxa, sannan wnn yarinyar da kike gani ita xata xamar maki
nightmares dinki kafin ni.... Lastly kin ci sa'ar mijinki na da k'ima da daraja a
idona sannan ga soyayyar da nake masa, wllh da yau bbu abinda xai hana ke da
mahaukatan kawayen ki kwanan cell kuma in ga uban da xai bada bail dinki, amma
soyayyar mijin ki baxai bar ni inyi hakan ba..." Tana fadin haka ta ja hannun
Heedayah suka fita xuwa gun mai gadi tace "Salisu ka tattaro abokanan ka masu gadi
ka fitar min da wasu mashaya da suka shigo min gida, and from henceforth duk wanda
ya xo ka fara sanar min kafin ya shigo" da sauri ya fita yin yanda tace.

Start patronizing Heedayah lovely fans.... last free update later at night in sha
Allah😍

07087865788.....
⚡ _Heedayah_⚡

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

Tun da Hajiya Maryam suka dawo gida da kawayenta take kuka kamar ranta xai fita, ji
take kamar ta bude ido taga cewar duk mafarki take, ya xa ayi Barrister ya mata
kishiya bata mutu ba?? Hajiya kyauta tace "Ke Maryam bari ki ji in gaya maki, idan
xaki share hawayen ki ki san nayi ki share, don 6ata lkcn ki kawai kike, wllh
wannan kukan baxai fisshe ki ba, wajen nan dai da baki son xuwa dolen ki nan xa aje
da ke yau a san nayi, don wnn mata ni dai da kamar wuya mijin ki ya fasa aurenta
duk haukan ki kuwa, na farko in dai kyau ne baxa ki nuna mata komai ba, ke diplomar
ma da ya kika kare? Ita kuwa lawyer ce fa me xaman kanta, kinga kenan ta kure
karatu, ga shi da gani dai kin san ba cikin wahala take ba tana da kudin ta, ke
dake buga buga ki raruma gun miji fa?? ni wllh ba karamin kwarjini matar ta min ba
ma, da ba ku fito ba dama ni wucewata xan yi kar ta sa a daure mu kamar yanda tace"
Hajiya Maryam ta katse ta a fusace tace "Ni fa da ku ke gani nan babu abinda ya isa
kai ni gun malami a duniyar nan, ku dai ku bar ni inyi ta kai na kawai idan baxa ku
bani shawara ba, ni kadai raina na ishi kowa, wllh karuwar nan baxata shigo min
gida a matsayin kishiya ba, muna nan da ku kuma xa ku ce na fada, ita kuma wnn
makauniyar dama sai dai ta kara shiga duniya wani ya tsince ta a wani garin amma ba
mijina ba...." Tana kai wa nan ta mike ta dau gyalenta tana share idonta, Hajiya
Sadiya tayi wani dariya tana kallon kyauta tace "Bar ta, xata dawo ta same mu ne
ai" Ficewa Hajiya Maryam tayi daga dakin rike da makullin motar ta..... Direct
gidan Dr Umar ta nufa, yau dai ko shiga bangaren matan gidan bata yi ba ta nufi gun
kaka, da sallama ta bude kofar parlon kaka dake uwar daka ta fito da sauri tana
cewa "huuu Ko waye don Allah ya share kafarsa ga tsumma na ajiye bakin kofa, wllh
kazamai ne matan gidan ko sharan kirki basa yi a makeken parlon nan nasu sai a
tattako a xo a yasar min a nawa parlon...." Hajiya Maryam ta dinga goge kafarta a
tsummar kamar an aikota, kaka tace "Aa Maryam daga ina haka da sassafe kuma" Ta
karasa cikin parlon ta xauna kasa cikin sanyin murya tace "Daga gida kaka, ina
kwana" Kaka ta xauna tace "Lafiya dai naga idonki a kukkumbure ko Balaraba ce ta
rasu??" Ta fashe da matsanancin kuka tace "Ba lafiya ba wllh kaka...." Kaka tace
"Ikon Allah me ke faruwa Kuma? Ni dai jiya Amadu ya shigo min da rana wai ya xo
gaisheni a nan kuma yake ce min wai aure xai kara har ya samu matar yar kaduna ce,
ni dai nace masa ba ruwana, ana xaune lafiya fitina ya shigo ciki, to daga haka ni
bai ce min ga abinda ke faruwa a gidansa ba...." Cikin kuka sosai Mumy tace "Abinda
ya kawo ni kenan ma kaka, wai aure fa xai kara...." Kaka ta saki salati tana tafe
hannu tace "Ohh ni na ga abinda ya isheni ni Rahamar ubangiji, me Amadu ke nema a
duniya da xai kara aure ana xaune qlau, ni dai yana gaya min ce mashi nayi ba
ruwana, don bn san kan xancen ba...." Mumy ta share idonta tace "Idan ma sbda wnn
baiwar Allahn ce ya kawota kawai xan riketa na amince" iyakar wnn furucin da Mumy
tayi bakinta, don kuwa ta sha alwashin ko an fasa auren aka kawo mata Heedayah sai
ta sake lulawa da ita wani duniyar daban, duniyar ma na kauye, can xata sa aje a
wurgar da ita don ma kada mistakenly wani me rufin asiri ya dauketa har ya taimaka
mata, a yanxu dai duniya bbu wanda taji tana tsana kamar wnn yar yarinyar, har ta
mance rabon ta xubda hawaye ta shiga tashin hankali da xai hanata bacci sai a
dalilin Heedayah, Kaka tace "Aa ni ya kawo min ita ma nan kawai xan riketa, kar a
ja maki kaffara kina xaman xamanki, dama bbu me min wanke wanke da shara
tsigalallun yaran nan duk ba kulasu nake ba ta kaina nake" Mumy tace "Makauniya ce
fa kaka" kaka tace "To makafi basa wanke wanke da shara aka ce maki Maryam, ai dai
naga ba kuturwa bace, sai in kada mata kumfar in sa mata ruwan dauraya in ajiye
mata kwanukan in xaunar da ita ta wanke min su tass" Mumy tace "Aa kaka wahala
kawai xata baki, ni din dai xan riketa, ai d'a na kowa ne" Kaka tace "Atoh dai, ki
kwantar da hankalin ki kawai, bbu wani xancen kara aure in dai da raina tunda xaki
riketa, to idan ba toxarci Amadu ke son mana ba meye kuma karin aure ana xaune
kalau, wannan ne kuma bai haifu ba gaskiya don baxan yrda ba" Mumy taji hankalinta
ya d'an kwanta, tana share idonta tace "Toh shkkn kaka nagode" Kaka tace "Haba
godiyar me kuma, ai yi ma kai ne, yanxu shawarar da xan baki a nan shine ki dau
kayan ki kala daya ko biyu ki tafi gidanku, idan ba haka kika yi ba Amadu baxai
dawo hankalinsa ba, ki tafi da fitsararrun 'ya yan nan naki ki bar masa gidan ba
kowa sae kujerunsa da tv, nan xaki ga ya shiga taitayinsa wllh, kaddai ki gaya ma
wnn dunkum din d'an naki kudurin ki don wllh hana ki xai yi ya cuce ki, ki bar masu
gidan shi da ubansa kawai" Mumy da ke kallon kaka tana jinjina shawarar ta a ranta,
tayi murmushi tace "Gaskiya ne kaka, hakan xan yi in sha Allahu ina komawa kuwa"
Kaka tace "Atoh maxa tashi ki tafi tun yanxu ki hada hada kayan, ai mu xamaninmu
haka muke yi, idan miji ya musguna maka ka hada kayanka ka bar masa gidan sa, xo ki
ga yanda hankalinsa xai tashi kuwa...." Mumy ta mike tace "Toh sai anjima kaka,
nagode sosai, Allah ya kara girma, sai mun yi waya" daga haka ta fita, kaka ta bi
ta da kallo har ta rufe kofa sannan ta ta6e baki ta juya ta koma cikin dakinta tana
cewa "To ai idan Amadu ya fasa auren nan ma ni sai naji dalili wllh, da kaina xan
kai sadakin auren, huuu wai ba kunya ba tsoron Allah matar da ke bari na da yunwa
me saka min nama tsoka daya ce wannan fa jama'ah, Ehh lallai duniya ya lalace....."
Da yammacin ranan Abba ya tafi gidan Barrister Rahinah don sake tabbatar da abinda
ta gaya masa a waya da safe, nan ta nuna masa she is serious, ko da wasa bata sanar
masa cewar Hajiya Maryam ta xo gidanta ba, yana murmushi yace "Toh nagode Rahinah,
in sha Allah gobe xa mu je can gun kawun ki..." Mami tace "Allah ya kai mu...."
Basu wani jima ba ta koma cikin gida don tace masa girki take, shi kuma ya wuce.
Mumy na komawa gida dama ta hada kayanta ynda Kaka tace mata, ta hada har da na su
Khadijah da Rabi'ah ta bar gidan, makarantar su ta fara biyawa ta sanar masu inda
xasu sameta idan an tashi sannan ta wuce gidan kanwar Mahaifiyarta dake nan kaduna.
Mami ce xaune study area dinta tana kallon files din gabanta, gaba daya mood dinta
isn't okay, ta kasa gane ko she is making the right decision marrying barrister,
har xuciyarta tana son taimakon Heedayah amma ba irin taimakon da xai kai ta ga
aure ba at this stage, ta jinginar da kanta da kujera tana tunanin ta ina xata fara
sanar ma yaranta wannan xance me girma, amma kuma ai idan bata Aure Barrister ba ta
6ar matarsa ta ci bulus kenan, ta shigo har gida ta yi mata cin mutunci sannan ta
bar ta haka nan, muryar junaid taji yace "Mami aiki kike?" Ta daga kai da sauri ta
kallesa don bata ji shigowansa ba ma, ta mayar da glass din da ta sakko idonta tace
"Sure, ka shigo kenan" yace "Nayi sallama naji shiru" ya ja kujera ya xauna yace
"Mami this two days naga kamar kina da damuwa, meye matsalar ki gaya min" shiru
tayi kuma bata daga kai ta kallesa ba, yace "Talk to me Mami" ta sauke ajiyar
xuciya tace "Junaid barrister ne ya xo min da xancen da ya saka ni cikin damuwa
kwarai, I don't know I am really confuse junaid...." Yana kallonta sosai yace "Me
ya faru Mami?" Ta kuma yin shiru, bayan few seconds taga bbu wani amfanin boye boye
kuma, nan ta sanar ma d'an nata intention din Barrister Ahmad a kanta, junaid bai
iya ya ce komai ba na kusan second talatin, can dai yyi gathering courage ba tare
da ya kalleta ba yace "Toh, idan hankalin ki ya kwanta da hakan Mami, Allah ya sa
shine mafi alkhairi a gare mu baki daya" kallonsa kawai take bata ce komai ba, ya
mike yace "Na xo daukan system dina ne" daga haka ya wuce sama ta bi sa da ido,
dakin Farida ya bude, ya ga Heedayah kwance edge din gadon tana bacci, riga ne da
wando jikinta kamar dai 'yar turawa, he wondered if she is neva tired of sleeping,
karasawa cikin dakin yyi walking slowly ya isa kusa da gadon yana kallonta, a
hankali ya mayar da ita tsakiyar gadon ya gyara mata dogon gashinta dake rufe
idonta, jin an bude kofar dakin ya mike tsaye da sauri, kafin Mami tace komai yace
"A gefen gadon na sameta...." Mami ta gyada masa kai kawai, ya juya ya fita
dakin.... Da daddare Barrister ya tafi gidan Yayansa, bayan sun gaisa da kaka yace
"Na je can gida na tarar Maryam ta kwashe yara sun bar gidan Baaba" Kaka tace "Kila
ganin gida taje...." Shiru yyi yana kallon mahaifiyar tasa, kaka tace "Toh ina dama
xata je idan ba ganin gida ba, ai ta kwan biyu bata je ba, kaga kai kuma kafin ta
dawo sai amaryarka tayi kokari ta tare xuwa nan da ranan juma'ah tunda yau talata,
wannan makeken bangaren da nake sauka sai ka sa a gyara ma amaryar ayi fenti da
komai da komai kawai, ita kuma Maryam ban ce ka kirata ba balle kace xaka mata
fada, uwarta taje gani...." shigowar Baffa ya sa Kaka tayi gum, ta sauya xancenta.
Ranan juma'ah aka daura auren Barrister Ahmad da Barrister Rahinah, though they did
it in a confidential way, bbu wani gayya, duk abubuwan nan dake faruwa Hajiya
Maryam na can ta lula xuwa gidan wata childhood frnd dinta a Zaria tare da su
Rabi'ah wai kar barrister ya biyota gidan kanwar mamarta, ita a dole sai ta basa
wahala, Shuraim kadai take kira don samun update, sai dai me? Shi ma bai san da
auren ba sai a ranan juma'ar, shi ma kuma da asuba Abban nasa ya sanar masa a
masallaci da suka hadu, he was so shock ya ma kasa cewa Abban nasa komai, haka nan
Abba ya wuce ya bar sa wajen a tsaye, ita kanta Hajiya Amina mum din su Sudais
ranan ta ji xancen daurin auren daga bakin Baffa da safe, nan tayi ta kiran Hajiya
Maryam amma wayarta a kashe, bata fasa kira ba har sai da aka daura wnn aure amma
bata samu Mumy ba..... Washegarin ranan da ya kasance Saturday Mami xata koma can
gidan Barrister Ahmad, shopping suka tafi tare da Heedayah, Farida da First
daughter dinta Amira dake aure a Abuja, su dai
sun yi farin ciki da auren mahaifiyar tasu kilan hakan ya rage mata damuwa sosai,
don duk sun san barrister Ahmad, A cikin mota Amira tace "Kinga yanxu Mami sai ki
bar ni mu tafi da Farida sai ta dinga xuwa maki hutu kawai ko" Mami dake ta tunanin
makomar autar tata tun bayan da aka daura aure don bata ta6a jin tafiya da ita
gidan barrister ba, baxai ma yiwu bane, ta kalli Amira tace "Alright dear" Amira na
dariya tace "Kinga cikin ruwan sanyi kin bani ita" Babban shopping mall Mami tayi
parking suka fita, Amira na rike da hannun Heedayah suka shiga ciki gaba daya,
shopping sosai Mami tayi, yaranta na taya ta, Mami da ta lura Heedayah ta gaji da
jan ta da ake ta yi, duk ta yi wani laushi, kana ganinta kasan ko kadan bata sa6a
da wahala ba koma wani iri, Mami tayi murmushi ta samu kujera nan kusa da counter
ta xaunar da ita sannan ta koma gun yaranta, a kan idon wani mutumi dake tsaye
shelf din turare yana diba, ya cire glasses dinsa yana kallon Heedayah sannan ya
kalli Mami da ta sha corner xuwa gun su Amira....

End of free pages

The book Heedayah is 300 via transfer

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment 07087865788

No regrets....
Patronize ur novelist lovely fans, Allah ya maku albarka ya raba ku da iyaye
lafiya...💖

Mutumin ya ajiye turaren hannunsa ya isa gun Heedayah ya tsaya dab da ita yana
kallonta bayan yyi make sure bbu me kallonsu yace "How are you?" Juyowa Heedayah
tayi da sauri, lkci daya ta mike tana waige waige, shi dai bai sake cewa komai ba
yana kallonta, kamar xata yi kuka tace "ka dawo xaka kai ni gun Ammina ne?" Jin
shiru, ta kai hannu to see if he is still there, komawa gefe yyi yace "Ina Ammin
taki take?" Tace "A can gidan Yakumbo mana" xai yi magana ya ga Mami ta tsaya daga
inda take tana kallonsu, lkci daya ya juya ya koma shelf din turaren da ya baro,
Mami ta nufo Heedayah da sauri ta kamo hannunta tace "Me yake ce maki?" Heedayah da
ta 6ata fuska xata yi kuka tace "shine ya sa ni a bicycle muka tafi..." Mami ta
juya wajen da taga Mutumin ya tafi taga wajen wayam, da ido duk ta bi wajen amma
bata ga alamarsa ba, Heedayah da hawaye ya cika idonta tace "Baya son inje wajen
Ammina" kama hannunta Mami tayi suka bar wajen har sannan tana kalle kallen mall
din ko xata ga wannan mutumi, sai da suka biya abubuwan da suka siya sannan suka
tafi mota, Mami na kallon Heedayah tace "But ya akayi kika san shi ne?" Tace "Na ji
voice dinsa, shine...." Mami bata kuma cewa komai ba har suka bar shopping mall
din. Bayan Magrib Shuraim ya iso gida, rabonsa da gidan tun jiya juma'ah da safe,
dama ko wajen daurin auren Abban nasa ma bai je ba, sau daya ya kalli motar Abban
nasa dake parking space ya dauke kai, ya fita motarsa ya rufe ya wuce xuwa entrance
din gidan, bbu kowa parlon, ya tafi parlon Abbansa, sallama yyi still standing at
the door, Abba dake rike da makullin mota alamar xai fita ne, ya amsa masa sallama
sannan ya bude kofar ya shiga, Heedayah ce xaune parlon kan lallausan carpet da
plate din watermelon a gabanta tana sha, kasa karasawa parlon yyi tun da ya ga
Heedayah, sai da Abba ya daga kai ya kallesa sannan cike da kasaita ya karasa ciki,
gaba daya bbu wani annuri a fuskarsa, can gefe ya duka yace "Ina yini Abba" Abba
yace "Lafiya lau" mikewa yyi ya nufi kofa Abba ya bi sa da ido har ya fita, a
compound Abba ya samesa xaune shi dai bai ce masa komai ba ya fita da motarsa da
nufin maida Heedayah can gidan Mami. Washegari lahadi Abba ya tafi can gidan Mami
don ranan xasu tafi gidan Baffa Mami su gaisa da kaka, Abba ne ke driving Mami na
gaban motar Heedayah kuma na baya a xaune, jifa jifa suke magana da ya shafi field
din aikinsu, Mami dake danna wayarta ta kalli barrister tace "Hope ba dadewa xa mu
yi ba wajen mama coz xa mu yi sallama da Amira nan da sha biyu xa su wuce" Abba ya
d'an yi shiru kafin yace "I mean it Rahinah... Farida baxata je Abuja ba, are you
trying to show ni ban isa riketa ba" Mami tace "A'a ae hutu xata je, in sha Allah
xata dawo soon..." Yace "Wani hutun?" tace "Mid term...." Yace "Am damn serious
baxata xauna Abuja ba" Mami tayi murmushi tace "To shkkn" a haka suka isa gidan
Baffa, bayan Abba yyi parking ya juya yana kallon Heedayah da tayi lamo jikin
motar, yace "Heedayah" ta xauna da kyau da sauri tace "Abba" murmushi yyi yace
"Hope
ba bacci xa ki yi ba" ta girgixa kai tace "A'a" Ya kalli Mami da ke kallonta ita
ma, Mami tayi murmushi tace "Heedayah is more than lazy, tafi son tayi ta bacci"
Shiru Abba yyi bayan few seconds yyi kasa da murya yace "Look Rahinah... my mother
can be very weird at times kin san ynda tsoffi suke, I know she will welcome you
wholeheartedly but.... Akwai halin tsufa dai, so get prepared Mamin Heedayah and
Farida...." murmushi kawai tayi, ya bude motar ya fita, ita ma ta fita ta sakko da
Heedayah, main parlor Mami ta xauna tana amsa gaisuwan da Yan matan gidan ke mata,
Hajiya Hauwa dake kitchen ta fito don ganin su waye, ganin Abba tace "Sannu da xuwa
barrister" yace "Sannu Hajiya Jiddah ya gidan" tace "Gida Alhmdllh" da fara'a tana
kallon Mami tace "Sannu da xuwa Hajiya, sannun ku da xuwa" Mami na murmushi tace
"Yauwa sannu, fatan mun same ku lafiya" Hajiya Hauwa tace "Alhmdllh, you are
welcome to the family" murmushi Mami tayi tace "Thank you" Hajiya Hauwa ta tafi
dauko ruwa, Abba ya mike ya nufi bangaren Mahaifiyarsu, Hajiya Amina ce ta sakko
bayan yaranta sun tafi sun kai mata rahotu sama, tun daga step take kallon Mami har
ta kusa faduwa, ta shigo parlon idonta kyar kan Mami tace "A'a Sannun da xuwa
Bakuwa, lale marhaba, sannu amarya" Mami ta kalleta ta gefen ido jin salon maganan
nata tace "Yauwa sannu" tana fadin haka ta mike tana kallon Hajiya Hauwa da ta
ajiye mata ruwa da lemo tace "Hajiya ina ne bangaren mama?" Hajiya Hauwa tace "Mu
je in raka ki" tana rike da hannun Heedayah ta bi bayan Hajiya Hauwa, Hajiya Amina
ta bi ta da kallo har suka shiga parlon kaka sannan ta koma sama da sauri. Mami na
shiga parlon Kaka ta xauna saman babban darduman dake shimfide tace "Sannu Mama"
Kaka dake kallonta tace "Yauwa sannu 'yar nan, sannun ku da xuwa" Mami tayi kasa da
kai tace "Ina kwana" Kaka tace "Lafiya qlau, kinga ynxun nan na gama karyawa, yau
dai ba laifi sun ga daman kawo min karin kumallon da safe, kinsan uwa idan ba taka
ba" Murmushi Mami tayi, Abba ya dauke kai daga kallon kaka da yake, Mami tace "To
Allah ya rufa asiri Mama" Kaka tace "Atoh, Ameen dai, ni da so nayi ma su bar ni in
dinga kayana da kaina tunda ina da karamin kitchen amma Amadu da wansa Umaru sun ki
yarda, Kuma fa idan na ci abincin sae inyi ta tashin xuciya tsabar kazantar Yan
gidan...." Ba dai wanda yace ma kaka komai, kaka tace "Toh ya sunan naki, kuma
yaranki nawa?" Mami ta kalleta tace "Sunana Rahinah, yarana uku" kaka tace "To
yaran me ya hanasu xuwa gaisheni bayan an riga an xama daya kuma??" Kafin Mami tace
komai Abba yyi saurin cewa "Heedayah You didn't greet grandma" Mami ta daga
Heedayah ta maido ta kusa da kaka tace "Greet her" a hankali Heedayah tace "Ina
kwana" Kaka da ta saki baki tana kallonta tace "To wnn kuma wani irin kaya ne aka
sa mata kamar 'yar anna, abu duk a d'angale jama'ah? Rahilah kike ko wa? Gaskiya
kar ki sake sa mata wa Innan tsinannun kayan, da da idonta ma baxata bari a cuce ta
a saka mata wannan kaya ba" Mami na murmushi tace "To in sha Allah baxa a sake ba
Mama" Kaka tace "Kuma kar ki sake yi mata karin gashi ki rufa mana asiri mu ba hka
muke ba" Mami tace "Ae gashinta ne mama" kaka ta cire hulan kan Heedayah tace
"Auuu, to maa sha Allah, daga gani ba daga irin tsiya ta fito ba, nima dai ance ina
kamarta gashina har gadon bayana wllh...." Abba ya mike yace "Baaba xa mu je, ana
jirana ne" Kaka tace "Ko dai har ta tare bani da labari?" Yace "Aa tukunna" Kaka
tace "To sai yaushe?" Abba xai yi magana kaka tace "A'a ni ba ruwana, ita bata da
baki sae kai, ni da ita nake ba da kai ba ae koh" Mami tayi murmushi tace "Ko nan
da sati kaka" Kaka tace "Toh dai kiyi ki tare kafin matar tasa ta dawo, kinsan tana
d'an tabin hankali, ko da yake dai gadonsu ne, ga shi kuma ya hade da an mata
kishiya, ke dai ba ruwanki da ita kiyi ta kanki ki kula da marainiya tsakanin ki da
Allah, parlon ki na nan tikeke da uwar daka har da bandaki ba ruwanki da
fitinanniyar, kitchen kuma ya fi parlon nan nawa da kike gani girma, komai kike son
xubawa naki ki xuba duk xai cinye wllh...." Abba yace "To bari mu je Baaba" Mami
dake ta murmushi kawai ta duka xata daga Heedayah, Kaka tayi saurin cewa "Kai ku ji
mata ba yini ku ka kawota ta min ba dama, kinsan ynda muke da ita ne? D'a na fa ya
tsinto ta tana galantoyi a titi" Mami ta mike tace "To shkkn mama, sae anjima" kaka
tace "Ko anjima da daddare ba sai ki xo ki tafi da ita ba" Abba tuni ya fita, Mami
tayi ma kaka sallama ita ma ta fita. Kaka na kallon Heedayah da jikinta yyi sanyi
jin an tafi an barta tace "To sun baki abincin ma kuwa, don naga Amadu har wani
rawa kansa yake shi a dole yyi amarya" Heedayah ta gyada mata kai kawai, kaka ta
mike tace "Ni dai ba ruwana don ba barinsu Allah xai yi ba idan suka bar ki da
yunwa" cup ta dauko a inda take jera su ta dawo ta bude flask ta debi ruwan xafi,
shayi me kauri sosai ta hada a cup din ta bude bread ta dau slice biyu ta daura a
plate ta debo dambun nama da tsoka uku na nama ta watsa kan plate din ta ajiye ma
Heedayah a gabanta tace "gashi nan maxa ki cinye ki bani kwanuka na, duk cikin ki
ya hade da bayanki kice min kin koshi" tana fadin haka ta mike ta koma daki tana
cewa "Haka matar ta xo tsiya tsiya ba komai, kamar ta baxata kawo d'an lemonta ko
ma dai turare ba tace gashi kaka" tabe baki tayi ta ci gaba da linkin da take.
Heedayah dae na xaune da shayi a gabanta don ba yunwa take ji ba, ita din ba wata
me cin abinci bace sosai, bude kofar parlon aka yi a hankali, Sudais ya shigo,
direct inda ya hango turarensa da kaka ta dauke jiya ya nufa don dama abinda ya
kawo sa kenan, ya duka xai dauka kenan ya ga Heedayah dake xaune, mikewa yyi tsaye
yana kallonta sannan ya nufeta ya duka gabanta, she looks so sad, shi dai ya kasa
yarda da abinda Shuraim yace masa wai fararen idon nan nata basa gani, hannu ya kai
har kusa da idon ya ga bata motsa ba, ya sauke hannunsa a hankali, murya can kasa
yace "How are you?" Juyawa tayi da sauri jin murya kusa da ita, Amma kuma tayi
shiru tayi tana kallonsa directly in the eye, yace "How are you?" a hankali tace
"Fine" yace "To ki sha shayin ki...." Tace "Na koshi" hannu ya sa aljihunsa ya
fiddo chocolate biyu ya kamo hannunta yace "Toh ga chocolate ki sha, ko in bude
maki?" Ta gyada masa kai, ya bude guda daya ya saka mata a hannunta, xai yi magana
sae ga kaka ta fito, tana ganinsa tace "Ni dai wllh ba ruwana idan baki na ya bi ka
Aliyu, nace kar ka sake xuwa min nan xan ja Allah ya isa, Kuma wllh na ja a raina
tun ranan" Yace "Tunda ke ba Baffa bace kuma ba Umma bace me xai dameni, Allah ya
isan ki iyakarsa lebenki" ko kadan bata ma san me yake cewa ba, don bude baki tayi
kawai tana kallon shayin gaban Heedayah, can tace "Naga ikon Allah, Ke baki sha
shayin bne har ynxu kika bar shi a walakance?" Heedayah ta marairaice tace "Na
koshi" kaka tace "Amma ke dai muguwa ce, kina kallo ina hada shayi duk na yi barna
da madarata da banvita kiyi shiru ki kyaleni sbda mugunta??" Sudais yace "To da
idon ki taga kina hada shayin ta maki shiru kaka" Kaka tace "Ba ruwana da wnn, ance
maka haka Allah ya bar su, duk suna sane da komai ke faruwa a inda suke, kawai tayi
niyyar walakanta ni ne, amma tana sane lkcn da nake kada shayin" Sudais ya dau cup
din shayin yace "Toh bari in Shan....." Kaka tace "Haram.... Ban baka ba har
xuciyata, Amadu ne ya siyo min kayan shayin ba Umaru ba" dariya yyi yace "Toh shi
din ba Abbana bne, Kuma ae dama abincin Haram dadi ne da shi" kaka ta fashe da kuka
ta nemi kujera ta xauna, sai da ya shanye shayin ya ajiye mata cup yyi
ficewarsa..... Hajiya Hauwa ce ta kawo abincin rana bayan azahar, Heedayah na xaune
kan darduman da Kaka ta shimfida mata wai tayi sllh, Hajiya Hauwa da suke ce ma
Aunty a gidan, ta gaida kaka tace "Ga abinci kaka" kaka tace "Toh yau dai kun bar
yunwar ta gigitani gaskiya, Amma bbu komai Allah yyi albarka, amma fa ni dai nasa
yar nan tayi sllh bn san ko ba musulma bace" dariya sosai Aunty tayi tace "Musulma
ce mana kaka" kaka tace "Atohh naga dae ta iya alwalar..." Aunty tayi murmushi tana
kallon Heedayah ta isa kusa da ita ta kai hannu kanta tace "Bari in kawo maki naki
abincin kin ji daughter?" Heedayah ta gyada mata kai kawai, Aunty ta juya ta fita,
sae ga ta ta dawo da plate din shinkafa da miya da salad a gefe sae neman kaza ta
ajiye gaban Heedayah tace "Ki jira ya huce sae ki ci, kaka xata baki ruwa idan kika
ci" daga haka ta fita, kaka na kallon Heedayah tace "To me kika yi ma iyayen naki
suka sallama ma duniya ke d'a na ya kwaso ki?" Heedayah dai bata ce komai ba don
Hausan ya mata girma, kaka ta tabe baki tace "Toh, Allah shi yasan dai dai, mu dai
gashi mun kwaso ki bbu dangin iya balle na Baaba, muna neman lada wajen Allah"
Bayan la'asar Kaka ta kwashe Yan wanke wankenta ta bude wani kofa da xae fitar da
ita bayan gidan, inda aka yi mata pamponta ta kada kumfa ta ajiye ruwan dauraya ta
dawo ta daga Heedayah dake bacci tace "Taso ke ma a dinga cin amfanin ki ba wai ki
ci ki sha kiyi kashi kiyi ta bacci ba, tun xuwan ki kike bacci" a haka ta kai ta
bakin tap ta xaunar da ita kan kujeran tsugunno dake wajen tace "Maxa kiyi ta
lalubawa kina daukan kwanukan kina wankewa ga ruwa a gefen ki, mace kike gidan wani
kuma xa ki" daga haka kaka ta wuce ciki ta bar ta, tunda Heedayah take bata ta6a
wanke wanke ba, bata ma san meye shi ba, hka ta dinga daukan kwanukan tana tsoma su
cikin ruwa tana fitarwa, har taji bbu wani nan kuwa duk suna gefe daya a ajiye,
mikewa tayi pink wandon jikinta da ya wuce gwiwarta a jike jagab, kofa taji an bude
a tunaninta kaka ce tace "Na gama" duk a tsorace take hannunta rike da plate biyu
da cup daya, Shuraim ne tsaye bakin kofar alamar shigowansa kenan gidan a tunaninsa
kaka ce backyard din, hannu Heedayah ta sa tana laluba wajen xata wuce ta ci
tuntube da kujeran da ta tashi daga kai, cikin few seconds komai ya faru, duk da
effort din Shuraim kuma jikinsa ta fada hakan bai hanata buge kneels dinta a kasa
ba, shirun da Shuraim ya ji tayi
ya sa yyi saurin daga kanta yana kallon fuskarta, sae a sannan ta wara ido ta fasa
wani ihu da ya raxana shi, lkci daya ta kankamesa tana cewa wayyo kafanaa, kaka ta
saki flask din ruwan xafin hannunta ta taho a guje tana cewa "Innalillahi wa Inna
ilaihi raji'un, yar mutane ta mutu a gidana, na shiga uku na banu, me xance ma
Amadu" Shuraim ya kalli kafan nata yana kokarin dagata ta rirrikesa cikin kuka tana
cewa "Wayyo a kai ni wajen Abba, wayyo Abba ya xo...." kin fitowa kaka tayi ta
dinga lekowa jikinta na rawa, Shuraim ya hade rai, ganin Heedayah ta ki tsayawa
yace "Baxa ki tsaya ba sae na mare ki?" Kuka sosai take yi tace "Baxan iya ba kafan
yana min ciwo..." Daukarta yyi ya shiga parlon kaka da ita ya kwantar da ita saman
kujera yana kallon kafar, cikin rawar murya Kaka tace "Kaddai karyewa kafar yyi
Ali?" Ta gefen ido Shuraim ya kalleta kafin ya mike yace "Ni na sani..." Kofa ya
nufa zai fita ta cafkosa ta fashe da kuka tace "Don Allah ka rufa min asiri ka duba
mata kafar tun da kai ma likita ne, Kar Amadu ya kullaceni, wllh sai in iya tattara
kayana in gudu ba ruwana da bacin ran Amadu, ya takarkare ya tsinto yarinya kuma
ace a gidana ta karye...." Heedayah dai sai kuka take tana kiran Abba, kaka ta
xauna kasa ta saki matsanancin kuka tace "Ka ji algungumar wai Abba ko??" Shuraim
ya hade rai yace "To ina xuwa in dauko abu a mota" daga haka yyi ficewarsa, dawowar
da bai sake yi ba kenan.
Abba ne tsaye kan Heedayah dake bacci saman gadon kaka, Mami kuma na xaune gefenta
tana rike da hannunta, Aunty da Baffa da Umma ma duk suna dakin, kowa yyi jigum,
can na hango kaka rakube jikin kofar bandakinta ko ganinta bata son a dinga yi
sosai, Baffa yace "Toh wai ma ina aka ta6a sa mara ido aiki fisabilillahi??" Kaka
tace "A'a ni dai kar a min sharri ita tace xata yi, tana ganin na hada kayan wanke
wanken tace Kaka kawo in taimaka maki, to sai in hanata sbda mugun hali ko me? Kuma
da kke wnn maganar so kke Allah ya tambayemu tarbiyar da muka mata? Don tana
makauniya shkkn sae a fake da haka a ki bari ta ta6uka komai??" Baffa yace "Ta ina
makaho xai iya wanke wanke kaka???" Kaka tace "Ni dai kar a min rashin kunya ba
ruwana, Kuma flask din ruwan xafi na da ya gamu da ajalinsa daxu da plet dina da
suka fashe guda biyu duk a biyani kayana, hatta kujerar tsungunnon ma yyi targade
ba ita kadai ba, targade mana tunda kafa daya ya karye, Kai kuma Amadu wllh jidali
ka haifar ma kanka kana tunanin d'a ne, sam xuciyar wnn yaro naka shuree yake ko
wa, bashi da kyau, xuciyarsa bakikirin yake, ni Yaron ma idan ba tsoro yake bani ba
shegiya nake, mugu ne axxalumi na bugawa a jarida, wllh yarinyar nan na tsala ihun
axaba gwanin ban tausayi ya tsallake da shegen idanuwansa kamar naka yyi wucewarsa
ko ta mutu ko tayi rai oho, tsaf xai iya kashe mutum har ya kai sa makwancinsa, ni
abun hannunsa ma na daina ci daga yau, inda Sudess ya fi sa kenan, shi dai bar shi
da cin Haram amma xuciyarsa fari ne fatt wllh" Abba dai bai ce komai ba kuma bai
kalli mahaifiyar tasa ba....

I appreciate ur patronage and patient fans, Allah ya kawo budi me yawa ya bar mu
tare.... Su kuma masu jiran Heedayah su karanta a bati, here is it... But don't
forget it's not free, it's nothing don ka fidda dari uku kayi subscription to read
what gives you so much joy, bbu abinda hakan xai raga ka da shi, and it's a way of
showing u appreciate ur novelist and her handwork, don't forget writing isn't easy
even if it's a hobby..... I Khaleesat Haiydar write just once a year and I make
sure na sa farin ciki a xukatan mutane da dama, toh me yasa nima baxa a min haka
ba, patronize so I will be happy too.... kyautatawa ma yana cikin so ai... 😇
All the same ina ma kowa fatan alkhairi, anywhere, anytime.💖

Heedayah is 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah, then u show ur evidence my
WhatsApp digit 07087865788 sai in sa ka group.

Parking Junaid yyi kofar gidan Baffa ya kashe motar sa ya bude ya sauka, sanye yake
da kananun kaya, walking calmly ya isa gate suka gaisa da Mai gadi sannan ya shiga
gidan, baya bukatar tambayar entrance don tuni ya hango, yana isa bakin kofar yayi
knocking, bbu bata lkci aka bude kofar, kanwar Sudais ce ta bude kofar, yana
kallonta da murmushi fuskarsa yace "Good evening" tana kallonsa irin kallon rashin
sanin tace "Welcome..." Muryar Abba suka ji yace "Is that Junaid" Junaid yayi kasa
da kai yace "Ina yini Abba" Abba yace "Lfya lau, Zainab ki kai sa bangaren Kaka"
Zainab na kallon Junaid tace "Toh" bin bayanta yyi suka nufi parlon kaka, Abba kuma
ya fita rike da makullin motarsa, da sallama Junaid ya shiga parlon kaka, Mami dake
tsaye rike da jakarta alamar xata wuce ta juya tana kallonsa, Kaka ta kalli Junaid
sannan ta kalli Mami tace "wannan ne d'an naki?" Mami tayi murmushi tace "Eh Mama"
kaka tace "Ahh ba shakka... Kyakkyawan bafillatani da shi wllh, ya ma fi ki kyau
ai, da ganin ubansa ya yo...." Mami dai na murmushi tace "To sai na shigo da
daddare kaka, bari in je" kaka tace "A'a ki yi xaman ki kar ki wani wahal da kanki
ba gashi ina kula da ita ba tsakanina da Allah...." Mami tace "Toh shkkn mama" Daga
haka ta fita parlon, Kaka na kallon Junaid dake tsaye har sannan tace "To kai ko ka
xauna mana d'an nan" ya xauna smiling broadly, with respect yace "Ina yini" Kaka na
washe baki tace "Lafiya lau, ya sunan naka?" Yace "Junaid Muhd..." Tace "Junaidu
sai kaji kuma wai yarinya ta gurde koh? To ni kai na ban san yanda akayi wnn bala'i
ya faru ba, amma dai na gode Allah tunda ba karyewa tayi ba...." Junaid yace "Allah
ya kara kiyaye gaba" Kaka tace "Ameen kai dai.... Don ma uwarka na da fahimta na
lura ita ta lallaba Amadu bai dau abun da xafi ba, kasan sa da xuciya, Kuma kasan
shi ya tsinto makauniyar a titin kano tana galantoyi...." Junaid dai bai ce komai
ba, kaka tace "To ka leka ta tana bacci can uwar daka ka duba ta, amma ta fiye son
jiki yarinyar, d'an bugewa fa kafar yyi amma duk makota bbu wanda bai shigo gidan
nan ba, ke Zainab kai sa ya ganta, kuma bance ki tsaya kusa da kumbo na ba, kinfi
kowa min sace sace a gidan nan" kasa motsi Zainab tayi, shi dai junaid kansa na
kasa, kaka ta ja tsaki ta mike tace "Haka nan suke min ban isa in sa su aiki ba, ae
dai kaga taki kai ka, to ba ruwana ba biyesu nake ba, tunda 'ya yana na min biyayya
ae shkkn" har dakinta ta kai Junaid tace "To ka ganta...." Junaid na tafiya a
hankali ya isa gefen gadon kaka yana kallon Heedayah dake bacci, kaka ta juya ta
fita, durkusawa yyi yana kallon kafarta ya kai hannu kneel dinta, kwace kafar tayi
tana turo baki alamar ta ji xafi, ta juya masa baya ta ci gaba da baccin ta, mikewa
yyi walking gently ya koma dai dai fuskarta ya durkusa, bayan seconds kusan goma
yace "Ina ke maki ciwo?" Bude fararen idon tayi a hankali kamar irin xata gansa din
nan tayi shiru staring into space bata dai ce komai ba, lkci daya kuma ta mike
xaune tace "Ina Abba" Bai ce mata komai ba, ya dau ledan da ya gani gefenta dauke
da drugs yana dubawa, bude kofar dakin aka yi junaid ya juya, Sudais ne tsaye bakin
kofar yana kallonsu, Junaid ya mike shi ma yana kallonsa, Sudais ya karasa ya basa
hannu nan suka gaisa, sannan ya isa kusa da Heedayah yace "Me ya kai ki wajen wanke
wanke har kika fadi?" Heedayah na kallon inda ta ji muryar tace "Ita ce ta kai ni
wajen tace sai inyi wanke wanke" Sudais yace "To ina ke maki ciwo yanxu?" Kafarta
na hagu ta nuna masa tace "But..." Yace "But what?" A hankali tace "Don't touch it"
kallonsu kawai Junaid yake yi, Sudais ya duka yana kallon kafar sosai yace
"Ohkk..." Hannu ta kai tana laluba wajen don taga ta inda yake, ta ta6a kirjinsa,
shi dai kallonta kawai yake, Bude 32 set of white teeth dinta tayi tace "Wannan
sweet din naka ya kare ko?" Ya buda ido yace "Kina so ne?" Ta gyada masa kai tace
"Um" yace "Ohk to bari in kawo maki" tace "Har da short bread??" Juyawa Junaid yyi
ya fita daga dakin ya rufe kofar, Sudais ya kalli kofar sannan ya kalleta yace "Who
is he?" Ta d'an yi shiru sannan tace "Shine ya bar ni a middle of road wai in wuce
cikin gida da kai na bayan yasan bana gani, I don't like him" da mamaki Sudais yace
"A ina kenan?" Tace "A gidansu mana, kuma ina shan strawberry ya dauke min plate
din, wai baya son in sha..." Tana fadin haka ta turo baki, Murmushi Sudais yyi ya
mike yace "Toh bari in kawo maki sweet din in dawo" ta kara bude hakoranta tace
"Toh" ya isa kofar ya bude ya fita, xaune ya tadda Junaid a parlor tare da kaka,
kaka na nuna sa tace "To ka gansa, sai dai idan ban ajiye abu ba wllh, shi kuma
wancan axxalumin ko magana baya wani yi, sae dai yyi ta kallon ka yana fama da
mugun abu a xuciya, shureen naji suna kiransa ko wa, shi ma dai Aliyun ne, amma
gaskiya xan gaya maka xuciyarsa bbu kyau yau na sake gaskata hakan daxu, to dai duk
sunan Mai gidana ne da yayi hatsari ya rasu" ko kallonta Sudais bai yi ba ya nufi
kofa xai fita, kaka tace "Kuma wannan da kake gani yan matansa sun kusa dozin har
na gaji da xuwan da suke gaisheni, yau fara ta xo, gobe baka, jibi mummuna, kai
gasu nan dai, ni dai na gaya ma daya a ciki yaudaran ta kawai yake, to ita ce ta
goma xuwa gaisheni, to naga tana da hankali tana ta min aiki da goge goge" Sudais
ya mata wani kallo ya fita ya kulle kofar. Junaid ya d'an yi murmushi yace "To ni
xan koma..." Kaka tace "Da wuri haka har ina murna na samu abokin hira?" Yace "Xan
dawo da daddare" tace "Ahh to shikenan, in ajiye maka abinci kenan?" Wani murmushin
da ya bayyana dimples dinsa yyi yace "Toh sai na xo in sha Allah" tace "Toh Allah
ya kawo ka, amma kaddai ka ki xuwa ka bar min abincina yyi kwantai" yace "A'a xan
xo" mikewa yyi tace "Toh ka leka ko ta tashi yarinyar" yace "Toh" daga haka ya
shiga dakin, xaune ya same Heedayah, ya karasa kusa da ita ya kai hannu ya dunguri
forehead dinta yace "Kina ji ina maki magana kika min shiru daxu koh" turo baki
tayi bata ce komai ba, yace "Sai na yanke wannan bakin" Tana jin haka ta 6ata fuska
lkci daya ta fara Shesshekar kuka, xaro ido yyi ya xauna gefenta ya jawota jikinsa
yace "Ke wasa nake maki fa" Cikin rawar murya tace "Toh shine xaka ce xaka cire min
baki?" Yace "A'a baxan cire ba, sorry" tace "Toh ina Farida?" Yana kallon Eye balls
dinta yace "Ta je Abuja" da sauri ta dago kai tace "Nan ne garinmu mu ma ai" Yana
kallonta yace "Where in Abuja?" ta bude hannu alamar bata sani ba, sai kuma tace
"Yaushe xata dawo?" Yace "Soon" saketa yyi ya mike yace "I'm going" tace "To ni
baxan sake xuwa wajen Mami ba kuma, ni ina tsoron wannan matar" Junaid ya buda ido
yace "Me yasa" ta marairaice tace "Tana ma kowa masifa, kuma tana aikana bana ganin
hanya" Murmushi yyi sosai yace "Mami xata xo ta tafi da ke" Shiru tayi bata ce
komai ba, yace "Anjima xan xo da daddare" ta gyada masa kai alamar to, sannan ya
juya ya fita dakin. Da daddare Junaid ya xo gidan Baffa kamar yanda yyi ma kaka
alkawari, Kaka na can uwar daka, Heedayah kuma na xaune parlon da plate din tuwo a
gabanta, Da sauri kaka ta fito jin an bude kofa, ganin Junaid ta washe baki tace
"Ka zo ashe Junaidu" gaisheta yyi ta amsa tana washe baki tace "Bari in gama gyaran
gadon in fito duk ta yamutsa xanin gadon" daga haka ta juya ta koma ciki, Junaid ya
ajiye ledan hannunsa ya koma inda Heedayah take tace "Me yasa ba ki cin abincin?"
Kamar jira take ta fashe da kuka a hankali tace "Ni ban iya ci ba" xaro ido yyi
yana kallon tuwo da assorted miyar veg din gabanta, yace "To me xa ki ci?" Tace "I
want to take tea" ya kara wara ido, bude kofar parlon aka yi ya juya, wani dogon
matashi ne just his mate ya shigo parlon, sanye yake da 3 qtr da polo, Shuraim ya
karasa cikin parlon waving at him without much interest yyi xaman sa kan kujera,
kaka ta leko don ganin waye, tana ganin Shuraim ta hade rai sosai tace "Dawowa kayi
ka kashe mu lkcn mu bai yi ba ko ya aka yi??" Dauke idonsa yyi daga kallonta ya
fiddo wayarsa ya maida dubansa kai, kaka tace "To idan ma mun mutu bayan ka tafi
Junaidu na shaida, ehe" daga haka ta koma ciki, ba a dau wani lkci ba sai ga ta
tafito tana washe baki tace "Sannu Junaidu bari in kawo maka abincin na ka" Junaid
yayi murmushi yace "To ngd" a gabansa ta jera masa abincin, shi dai bai ce komai ba
duk da a koshe yake, xata wuce ta gaban Shuraim kamar ana forcing dinsa yace "Ina
yini" tayi kamar bata ji sa ba, sai ga ta ta dawo tace "Toh ka ci abincin mana
Junaidu" Junaid na murmushi yace "Toh" sauka yyi ya bude warmer din ya ga shinkafa
ce da lafiyayyen Miya da ya ji nama, sai ga wani bowl da aka yanyanka kayan ganye,
kallon Heedayah yyi da plate din tuwon gabanta, sannan ya kalli kaka dake kokarin
share bakin kofar ta, matsawa yyi kusa da Heedayah murya can kasa yace "Xa ki ci
shinkafa?" Da sauri ta gyada masa kai, Ta gefen ido Shuraim ke kallonsu, Junaid ya
dau plate ya diba shinkafar da Miya da nama, ya dauke tuwon da ta fara kacalcalawa
ya ajiye mata shinkafar, a kan idon kaka da ta saki tsintsiyar hannunta ta mike da
sauri tace "La la la kar ka bata, gantalalliya ce wai bata iya cin tuwo ba, to uwar
me xa a bata, ko gidan Amadun da ya tsinto ta ma ai ana tuwo balle nan, mu ba wasu
masu kudi bane da xata ce bata cin tuwo har da hawayenta, shinkafar kuma iya
cikinka nayi nima tuwon na ci, idan aka ce xa a biyeta ai sai ta lalace Allah ya
tambayemu...." Heedayah dai sai xare ido take kamar xata yi kuka ta dafe plate din
shinkafar don kar ma a dauke, Junaid yace "Kaka ni na fi son tuwon ne shi yasa"
Kaka ta saki baki tace "Allah?" Yana murmushi yace "Ehh" ta tabe baki tace "Toh
Allah ya raba bawa da wahala don ko na wahala gun neman shinkafar nan da miya, to
ai sai ka ci tuwon ita kuma sai ta karata da shinkafar duk da ni dai ban bata ba,
kaji min yarinya dai da mugun hali" tuni Heedayah ta fara cin shinkafar, idan akwai
abinda junaid ya fi tsana rayuwarsa tuwo, sai kallon tuwon yake yana tunanin ta
wani side din xai fara ci, da cokali ya debi tuwon ya kai baki yana
ci da kyar, mikewa Shuraim yyi ya maida wayarsa aljihu ya nufi kofa ya bi ta gefen
kaka ya fita, kaka ta mike tace "Ka dai ga ko? Mugun hali har tsiro sai da yyi a
jikinsa, tirrr Amadu dai bai yi sa'a ba ya haifi jaraban duniya kawai, to ba gwara
min Sudess ba ni dai" sake bin kofar Junaid yyi da kallo don ya dai ga Shuraim na
kama da Abba amma bai yi tunanin son dinsa bane. Hajiya Maryam ce xaune parlonta
kai kace rasuwa aka yi mata, duk ta fita hayyacinta, idon nan nata duk a kumbure ga
su Hajiya Sadiya, Hajiya kyauta, har da Hajiya Amina da dai kawayenta gaba daya sun
kusa 7 sai Yan uwanta uku, Hajiya Zaliha tace "Ban da ma dodewar tunani da
kwakwalwa ke har kya dau shawarar wannan tsohuwar da shekara da shekara kuna dauki
ba dadi da ita, to duk gari kowa cewa yake ita ce ma karfin auren barristern, ita
ta matso da auren ma aka yi da wuri wuri" Mumy ta fashe da matsanancin kukan
takaici amma ta kasa cewa komai, Hajiya safara'u tace "Toh Kuma meyasa duk tsawon
lkcn nan kika ki kunna waya fisabilillahi" cikin rawar murya Mumy tace "Ita ta sa
in kashe wayar wai sai na basa wahala kafin ya gano inda nake da yara, kuma kusan
kullum sai mun yi waya da ita, tayi ta shirga ni wai Ahmad na nan duk ya daga
hankali ana ta nemana gari gari, har rahotu ya kai ma yan sanda, ko abincin kirki
baya ci, da mun gama wayar kuma sai ta ce in kashe da sauri" Mutanen parlon suka
kwashe da dariya ciki har da Hajiya Amina, Mumy ta hade rai tana bin su da kallo,
Hajiya Sadiya na kyakyatawa tace "Ban ta6a ganin makiran tsohuwa irin matan nan ba,
gaskiya ta sha ki da yawa, lkci daya ta rama duk abubuwan da kika dinga mata tana
xaune gidan nan" Mumy ta mike tace "To bari ku ji wani abu, ba don ba ni da abinda
xan iya yi bane kan tsinannen auren da barrister yyi ya sa nake kuka ko hankalina
ya tashi, A'a kuka nake saboda takaicin da yarintata ba a min kishiya ba sai yanxu,
kuka nake sbda boasting da na dinga yi cikin mutane Barrister baxai ta6a min
kishiya ba, kuka nake sbda makircin da annamimiyar tsohuwar nan ta hada min, ita
kuma wnn mata da tayi kuskuren auren mijina ina jiran shigowarta gidan nan, wllh
sai ta gwammace bata ta6a sanin Barrister ba, ita kuma wnn yarinya da aka min
kishiya ta dalilinta...." Wani murmushi Mumy tayi tace "Da farko xamanta gidan nan
kirgagge ne, sannan kafin ta tafi sai na tabbatar da shaida xata bar gidan wanda
har girmanta baxata manta ba, sannan a makantan ta xata tsaya har karshen
rayuwarta, wllh wllh bana wani jin kishiyar da aka min kamar yanda nake jin
yarinyar nan a rai na, ita ce sillar rugujewar duk wani farin ciki nawa...." Hajiya
kyauta tace "Toh nan dai da kwana biyu xa su tare da uwar rikon tata, ke dai gashi
kin samu an sauya maki komai na bangaren ki kamar ke ce amaryar, amma ni tunda nake
ban taba ganin irin haka ba, anya ba aljana barrister ya kwaso ba me son ta
tarwatsa maki gida, gashi ma tana kan yin haka tunda ta sa an rangada maki kishiya
yar boko yar gayu" Mumy tace "Za mu ga wanda xai tarwatsa wani ni da ita, na fa ce
maku ynxu ni ba ma da kishiyar xan goga ba...."

Heedayah is 300 via.... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788

Baffa ne ya bude kofar parlon Kaka da sauri jin ihun da Heedayah ke yi ya shiga,
shi ma shigowarsa gidan kenan daga masallaci an idar da isha, Kaka ce ta danneta
sai shafa mata wani magani kamar rub take a kafan da ke ciwo, Baffa ya bude baki
yace "Meye haka kuma Baaba?" Kaka dake ta hada xufa tace "Toh sai a biye mata tana
dingishi baxa a san na yi ba, so ake ta dawo gurguwa ga makanta abun ya taru ya ma
d'a na yawa? da wanne ake son ya ji, a hankali fa nake mata amma da yake munafuka
ce algunguma dubi tonan asirin da take min kamar warce nake yankawa" Baffa yace
"Don Allah ki kyaleta Baaba, ba tana shan magani ba, a hankali xai bar mata ciwon
ai" a fusace Kaka tace "Maganin banxa maganin bature, ka san daga wani kasa aka
kawo min wnn din da nake shafa mata, ku dinga kallona kamar ban san me nake yi ba,
toh naki kyaletan sai ka kwace ta ai" Ita dai Heedayah bata fasa ihun da take tana
kiran Abba ba, aka bude kofa Sudais ya shigo parlon da sauri shi ma daga masallacin
yake, Bude baki yyi yana kallon kakar tasa, tace "Kai ka ji ubanka da wani magana
Sudess, daga taimako fa xai min rashin kunya, ita kuma yar banxan magani fa nake
shafa mata...." Sudais yace "Toh kaka ba ke kika sa ta wanke wanken ba, ai sai bari
har lkcn da kafar yyi niyyar warkewa ya warke da kansa, ynxu hakan da kike mata
idan kika sake ji mata wani ciwon fa?" Kaka ta tura Heedayah a fusace tace "Ni dai
Allah ya isa wllh, ya xa a dinga cewa ni na sa ta wanke wanke, ga yarinya dai da
bakinta ko bata da ido ai sai ku tambayeta ta fadi gaskiya mana, kawai kawai an
mayar da ni karamar mutum a gidan nan sbda ana bani abinci a kwano.... Ban da
xalunci me xai sa in sa makauniya wanke wanke idan ba ita ta bukaci yin hakan ba da
kanta??" Juyawa Baffa yyi ya fita daga parlon, Sudais ya jira har ya rufe kofar
sannan yana nunata yace "Ke dai kawai baki son gaskiya, ki yarda kawai kin kusa
karya yar mutane kin sa ta wanke wanken da kika tara an kwana biyar...." Kaka ta
fashe da matsanancin kuka tana jawo dankwalinta xata yi hankici da shi, Sudais ya
daga Heedayah suka fita parlon ya kulle mata kofarta yana murmushi, Heedayah dake
dingishi tashin hankali a fuskarta tace "Plss ka wuce da ni wajen Abba kar ka dawo
da ni nan" kallonta yake bai ce komai ba har ya isa stairs, daukarta yyi ya wuce
sama, dai dai xai ajiyeta sai ga Ummarsa ta fito daga part dinta, tsaye tayi tana
kallonsa da mamaki fuskarta, yace "Sannu da gida Umma..." Bata amsa ba tace "Ka
sameni a parlona yanxun nan" daga haka tayi wucewar ta, bangaren Aunty ya shiga
yana rike da Heedayah, Aunty dake xaune saman darduma ta idar da sllh tace "Ta ya
kaka ta yrda ka fito da ita, daxu da rana kiri kiri taki yarda in fita da ita, wai
ba ruwanta yar amana..." Sudais yyi dariya yace "Ae tana can na barota tana kuka"
Aunty tace "Kai dai baka gudun abun magana koh Aliyu?" Ya xaunar da Heedayah saman
kujera yace "Danneta fa tayi tana ta ihu wai magani take shafa mata a kafar" Dariya
Aunty tayi ya juya yace "Ina xuwa Umma na kirana..." Tace "Amma xaka dawo ai" yace
"Ehh xan dawo" daga haka ya fita, Dawowar da bai yi ba kenan har sha biyun dare
yyi, Heedayah har ta gaji da tambayar Aunty ko ya dawo, Aunty ta kai ta bathroom
dinta tayi fitsari sannan ta kwantar da ita saman gadonta nan da nan bacci ya
dauketa, yaranta kuma suna dakinsu dama... Aunty na kwance har ta fara bacci ta ji
ana kwankwasa kofar bedroom dinta, ta mike ta kunna wutan dakin tana kallon agogo
ta isa kofar ta bude, Baffa ta gani tsaye kafin ta ce komai yace "Yarinyar nan na
nan ne?" Da mamaki Aunty tace "Tana nan har tayi...." Hango kaka da tayi tsaye
bakin kofar parlor tayi kicin kicin da fuska ya sa tayi shiru, Baffa yace "to fito
da ita" Aunty bata ce komai ba ta juya ta koma dakin, sai a sannan ta girgixa kai
ta shiga tada Heedayah, tana rike da hannunta har sannan tana magagin bacci suka
fito parlon, Kaka tace "A bani amana sbda ance maku ban san girman amana ba xa ku
cuceni ku dauketa, to uban me xata maki a nan din banda gulma Hauwa? wllh Umaru
kasa bacci nayi, gani nake kawai Allah na fushi da ni, idan Amadu ya ji wnn me ku
ke son ya daukeni? To ba ruwana a maido min da abata...." Baffa dai bai ce komai
ba, Kaka ta warce hannun Heedayah a na Aunty ta fice daga parlon Heedayah da har
baccin ya fice a idonta jin muryar kaka ta dinga bin ta kamar xata yi kuka, Baffa
ya girgixa kai yana kallon Aunty yace "Toh Allah ya kyauta" dariya tayi tace "Halan
har ka fara bacci" yace "Nayi bacci mana dama" daga haka yyi mata sai da safe ya
fita. Kaka na shiga bangarenta ta kulle kofar tace "Gantalallen yaro kawai in sake
ganinsa a parlona idan ban ja Allah ya isa ba" furan da ta rage ma Heedayah ta
dauko mata ta ajiye gabanta tace "Gashi nan baxan shanye ban baki ba kar Allah ya
tambayeni, duk da mugun halin ki" Heedayah ta ta6a cup din a hankali ta kai baki ta
fara shan furan kamar xata yi kuka. Washegari juma'ah da safe Mami ta xo tafiya da
Heedayah, Kaka ta kwaso kayanta da ta wanke ta linke su fesss tace "Sai kin sa ido
sosai kan yar nan, shegen son jiki ne da ita kamar mage, baxa a fake da makanta ba
a cuceta...." Mami tace "Toh mama" Kaka tace "Toh har yanxu baki saka ranan tarewar
bane ke kuma? Ba a fa wasa da igiyar aure" Mami tace "Yanxu haka can gidan xa mu
wuce gaba daya" Kaka tace "Toh alhmdllh, kin dai ji duk nasihar da na maki ranan ai
ko, yanxu haka matar na can ta dawo, bbu ke bbu ita" Mami tayi murmushi tace "In
sha Allah" sai kusan sha daya suka bar part din Kaka tare da Heedayah..... Horn
Mami tayi dai dai gate din gidan Barrister Ahmad, mai gadi ya bude gate din ta ja
motar xuwa cikin gidan tayi Parking a space din yin hakan, Da taimakon ta Heedayah
ta fito a motar, tana rike da hannunta suka nufi entrance din shiga main parlor,
Shuraim ne xaune balcony din da system a gabansa, tun daga nisa da ya kallesu ya
dauke kai ya ci gaba da abinda yake a laptop har suka iso balcony din, Mami bata
kallesa ba tace "Take off ur shoes Heedayah" Heedayah ta fara cire takalmin
kafarta, Mami ta ajiye su gefe, ita kam dama bata cire nata ba da shi ta shiga tana
bude jakarta don fiddo wayarta dake ring, ta daga ta kai kunne, Hajiya Amina
mahaifiyar Sudais ce parlon da Mumy sai Hajiya Sadiya da Hajiya kyauta, kallo daya
Mami tayi masu ta cikin siririn glasses din idonta still holding Heedayah's hand ta
nufi bangarenta tana cewa "Ai court ma baxata bada bail dinsu ba, their case is
different, baxai yiwu ba ma, so kar ku ji komai, pls hold on I will call you later"
tana fadin haka ta katse wayar ta fiddo makullinta don bude bangarenta wanda
aminiyarta da sister dinta suka xo tun jiya suka yi gyare gyaren da ya kamata, tana
shiga ciki rike da Heedayah ta kulle kofar. a hankali Hajiya Sadiya tace "Tabdijam,
lallai kina da aiki babba a gabanki Maryam, idan baki yi hankali ba wnn farar matar
dai kwace maki gida ta shigo yi, ke kin ji wani kamshi da take xubawa kuwa, kalli
fa ko kallon arxiki bata mana ba sai xancen kotu da bail take, da takalmi ma ta
shigo parlon don rainin wayo..." Hajiya Maryam da taji kamar xuciyarta xai fashe
don kishi bata dai ce komai ba nan ko naxari iri iri take yi a xuciyarta tana
tunanin ta ina kenan xata fara....

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....


Abba ne xaune main parlor bayan isha, lkci lkci yake kallon agogon dake manne
bangon parlon, Mami ta fito daga part dinta sanye da hijab har kasa ta karaso cikin
parlon tace "Good evening Barrister" yana kallonta yace "Good evening Rahinah"
xaunawa tayi one sitter dake parlon tace "Gani" Abba yace "Me ya sa kika dau lkci
baki fito" tace "Putting things in other" Bai ce komai ba, ya kalli hanyar kitchen
don Mumy na ciki, tun daxu take kai wa take komowa ko gaisuwa bai hadata da shi ba
tun shigowarsa, shi kuma hakan bai hanasa ce mata yana da magana a parlor da ita da
Mami ba, xata sake komawa kitchen daga bangarenta yace "Maryam" juyowa tayi fuska
daure tana kallonsa bata ce komai ba, yace "Ke muke jira" Tana masa wani kallo ta
karaso cikin parlon tace "Ni ku ke jira? in maku me? A kan me ma xa ku jira ni?
Nace maku ina da wnn lokacin ne? Plss I have more important things to do then
sitting and staring at you both, bani da wannan lokacin barrister...." Ta juya xata
bar wajen, rai bace yace "Ina magana xa ki wuce?" Juyowa ta sake yi tace "Bbu
tasirin da maganganun ka xa su min barrister, in xauna kace xaka mana nasiha ko me?
Did I tell you I need that, ita dai xaka xaunar ka ja ma kunne ta tsaya iya
matsayinta a gidan nan kar ta ce xata yi karambanin xuwa kusa da nawa matsayin,
matsayina daban nata daban, ni uwar gidanka ce kuma uwar 'ya yanka, ita kuma uwar
rainon yar tsintuwar ka ce, wa enda xaka dinga ciyarwa, kaga banbancin kuwa ba
karami bane, idan tace xata yi gigin matsowa lane dina ita xata kwana a ciki, so
bbu wani xaunawa da xan yi ka hada mu kayi magana, bata kai matsayin ba, ga most
important maganganun nan duk nayi, sai dai kawai tayi taking caution, ka kara mata
da wanda xaka kara mata" Tunda ta fara Abba ke kallonta, Mami tayi yar dariya tace
"To ai da sauki tunda kamar yanda xa a kira ki matarsa haka nima xa a kirani ynxu,
kuma tunda baki isa korar yar tsintuwa ba balle ni Alhmdllh, muna nan sai mun xame
maki kadangaren bakin tulu, xa ki gane matsayina da naki bai kai banbancin da xa ki
dinga bragging ba...." A fusace Mumy ta karaso kusa da ita tana huci tace "Karya
kike wllh, nace karya kike..." Tsawa Abba yyi mata yace "Kina da hankali Maryam??"
Mami ta mike tace "Ina fa, sai dai in koya mata cikin yan kwanakin nan...." Daga
haka ta bar masu parlon ta wuce bangarenta, Mumy ta fashe da kuka tace "Ka cuceni
barrister, ka ci amanata, ka rasa warce xaka auro ka kawo mana gida sai yar
bariki...." Mikewa Abba yyi ya dakatar da ita in few seconds ta hanyar nuna ta da
yatsa strictly yace "Don't you ever try that again Maryam...." Bai jira cewarta ba
ya bar parlon. Mami ce xaune that same night tana kallon Heedayah tace "Ina jin
ki..." Heedayah ta marairaice tace "Tea kawai...." Mami tace "Kece kike cewa kina
son tea din kenan" Heedayah ta girgixa kai tace "Ammi na ce take bani in sha da
daddare" Mami tace "To da safe fa?" Tace "Tea and bread and egg" Mami tace "Da
rana?" Heedayah tace "Indomie" Mami tace "Sai kuma da daddare ki sha tea" Kai
Heedayah ta gyada mata, Mami tace "Toh after this night baxa ki sake shan shayi ba
duk abinda aka dafa aka baki shi xa ki ci is that clear?" A hankali Heedayah ta
gyada mata kai, Mami ta mike ta dauke fried rice da chicken dake cikin plate da
Heedayah ta ki ci wai sai tea ta nufi kofa ta fita, hanyar kitchen ta nufa ta bude
kofar kitchen din, tsaye ta ga Shuraim gaban kettle din ruwa alamar tea xai hada
don ga kayan shayin a ajiye gefe, ta kasan tiles yake kallon wanda xai shigo
kitchen din, yana ganin wacece kuma ya kauda kai ya ci gaba da abinda yake, Mami ta
ajiye abincin hannunta ta nufi inda cups suke ta dau daya da cokali, ko kafin ta
juyo har ya fice daga kitchen din, karasawa tayi gun kettle din ta juye ruwan ciki
a cup din ta bude kayan shayin ta hada tea sannan ta fita kitchen din, Khadijah ta
gani parlor ta shigo daukan takardunta, tana ganin Mami ta kwashi takardun ta wuce
bangarensu da sauri, Mami dama tun da ta kalleta sau daya bata sake kallonta ba har
ta wuce nata bangaren, sai da shayin ya huce sannan Heedayah ta sha Mami ta sa ta
kwanta nan da nan bacci ya dauke ta. Washegari Saturday tun kafin yan gidan su
tashi bacci Mami ta hada ma ita da Heedayah breakfast, da yake abinda Heedayah take
so ne tsaf ta cinye komai, Mami dai sai kallonta take, sannan tace "Kin koshi ae?"
Heedayah ta gyada kai, Mami ta mike tace "To mu je ki gaida Abba" har parlon Abba
Mami ta kai ta, Abba dake aiki system ya daga kai yana kallonsu, Mami tace
"Weldone" yace "Har ina tunanin kawo maki ki karasa" tace "Noo nima ga nawa can"
yyi murmushi yace "Akwai maganan da nake son xa mu yi Rahinah" tace "Alright, but
before then nima ina da magana da kai" yace "Yanxu?" Tace "Later..." Abba ya xaunar
da Heedayah gefensa yace "How are you my dear" tana washe hakora tace "I'm fine"
Mami tace "Baki yi gaisuwa ba" tace "Abba ina kwana" yace "Lafiya lau daughter"
Mami tace "Let me freshen up" daga haka ta fita parlon, yana kallon Heedayah yace
"Wa ke koya maki English" tace "My teacher" ya d'an bude ido yace "Really?" Tace
"Ehh" Abba yace "Me da me yake koya maki kuma a ina yake koya maki?" Heedayah tace
"Ammi tace min she's a Female, tana koya min komai da komai a gidanmu" yace "Wani
sura kike?" Da sauri tace "Jinnnn" Abba na gyada kai so impressed yace "Kullum take
xuwa koya maki?" Heedayah ta gyada masa kai, Abba xai yi magana aka bude kofar,
Shuraim ne ya shigo parlon da sallama yana sanye da jallabiya, Abba ya amsa,
xaunawa yyi nan kasa gefen Abbansa yace "Ina kwana Abba" Abba yace "Lafiya lau"
Heedayah tace "Abba har da boko take koya min ma...." Satan kallonta Shuraim yyi ya
kara hade rai, Abba na kallonta yace "Toh xan kawo maki warce xata dinga koya maki
a nan gida" Heedayah ta wara manyan idonta tace "Thank you Abba, but..." Yace "But
what?" Tace "Yaushe xaka kai ni wajen Ammina? Kila tana ta nemana" a sanyaye tayi
maganan, Abba ya shafa kanta yace "Ina sha Allah xan kai ki, har yanxu ana neman
Ammin taki" Tace "Abba ai gidan Yakumbo take" Abba yace "Eh ban manta ba xa mu je
can" Mikewa Shuraim yyi ya nufi kofa yace "Sai anjima Abba" Abba yace "Da yaushe
kake yi ma su Khadijah karatun qur'ani" Juyowa yyi yana kallon Abban nasa, ganin
kallonsa Abban ma yake yace "Da asuba" Abba yace "Ohk, Heedayah will join also, sai
ka dinga masu gaba daya" dawowa yyi ba tare da ya shirya ba ya durkusa inda ya
tashi yace "Abba ai na kwana biyu ban koya masu ba" Abba yace "Eh to sai ka dinga
yi mata ita kadai tunda ba Islamiyya xata je ba, su kuma dama suna xuwa islamiyya"
Kasa cewa komai yyi yana kallon Abban nasa, Heedayah tace "Abba a suratul jinn
nake" Abba yace "Eh daga nan xa ku ci gaba" Shuraim yyi karfin halin satan
kallonta, Abba yace "That's all xaka iya tafiya, idan ya so sai in samar mata
lesson teacher na boko kawai" Mikewa Shuraim yyi bai ce komai ba ya fice daga
parlon ya kulle kofar, fuzar da iska yyi bayan ya fita ya juya yana kallon kofar da
idanuwansa da suka sauya kala. Mumy ce xaune dakinta tayi tagumi, da ka ganta kasan
tana cikin tashin hankali, kanwarta Salima ce xaune dakin, tace "Allah kuwa nake
gaya maki Yaya, duk wannan tunane tunanen da saka kai a damuwa ba shi bane, just
swing into action, dubi fa yanda take ta harkar gabanta a gidan kamar warce tayi
wata da watanni ke kuma kina nan xaune kina ta wani kishi da damuwa, wllh tuwo da
lafiyayyen miyan agushi tayi ynxu a kitchen, makauniyar kuwa na can ta kafa mata
kujera a kitchen din tana xaune...." Mumy ta fashe da kukan takaici tace "Wllh
Salima har ynxu na kasa yrda cewar kishiya barrister yyi min, gani nake kamar
bakuwa nayi xata wuce, baki ji ynda xuciya ta ke min xafi ba, Kuma fa tun jiyan ko
lekowa dakin nan bai yi ba, ita kuwa ta shiga bangarensa ina lura yau yafi a kirga,
wllh ji nake kamar in banka ma gidan nan wuta kowa ya huta" Salima tace "Ba wani
banka wuta Yaya, gashi kin fara bata chance ta kwace maki miji ta xama ita ce kan
komai a gidan...." Mumy tace "Duk ba wannan ba nata bai tsaya min kamar yanda na
makauniyar ya tsaya min a rai ba, ki bani shawara ta ina xan fara, me kike ga xan
ma wnn yarinyar in huce takaici, ni dai baxan kasheta ba amma ina son abinda xan
mata kissa ya fi mata alkhairi da shi, wllh na tsaneta, na tsani duk wani me son ya
ganta kusa da shi ma, wllh sai na tarwatsa rayuwarta" Salima tayi dariya tace "Ni
fa ban wani jin yarinyar nan Yaya, minti nawa ne xa a kada ta ta bar gidan ma gaba
daya, ita dai wnn yar bokon ya kamata ki fara tunanin ynda xa ayi da ita ba yar
yarinya ba" Mumy tace "To ni ta yarinyar nake tukun" Salima ta mike tace "Toh ki
kwantar da hankalin ki Yaya, wnn me sauki ne, mu da muka san kan komai, yanxu dai
ana jirana tun daxu a waje, xan dawo ko xuwa jibi" Mumy tace "Ba wani nan, ke din
ce xan gani kwana kusa, idan kika tafi gantalin ki ba sai an gan ki ba" Salima tayi
dariya tace "Ai ynxu na daina kwana a waje...." Mumy tace "Toh ni dai gobe xan taho
gida kar ki fita don Allah" Salima tace "In sha Allah yaya, sai mun hadu goben"
Daga haka ta fice daga dakin..... Bakin gate Salima ta kusa cin karo da Junaid xai
shiga cikin compound din, ja baya tayi tana kallonsa, yace "Sorry" bata iya ta amsa
ba har dai ya wuce ta, ta juya ta bi shi da kallo ko kiftawa babu, underneath her
breath tace "Waow...." Tana tsaye tana kallonsa har ya isa entrance din shiga main
parlor, ya kwankwasa kofar, Mami da ta san yana hanya ta fito daga kitchen ta bude
kofar tana kallonsa tace "Har ka iso?" Yace "Ehh ina yini Mami" ta basa hanya tace
"Lafiya lau" daga haka ta koma cikin parlon ya bi bayanta, saman kujera ya xauna
tace "Ya su Uncle din naka" yace "Alhmdllh..." Kitchen ta nufa tace "I have been
waiting for you since xaka dauko min sako a gida" Kafin ta shiga kitchen yace "Mami
ina..." Mami ta juyo jin yyi shiru, tace "Wa?" Yace "Wannan babyn" dariya tayi tace
"Sunanta Heedayah" yace "Oh ohk, Heedayah" Mami tace "Tana can tana bacci, let me
get you water" Drink ta kawo masa parlon,
duk suka kalli direction din da suka ji footstep, Mumy ce ta fito rike da makullin
motarta fuskarta a murtuke, Mami ta nufi bangarenta don tado Heedayah, Junaid yyi
kasa da kai cike da ladabi ya gaida Mumy, kallonsa ta kara yi snn ta amsa a dakile
tayi ficewarta xuwa gidan Hajiya Sadiya ta ji ita kuma nata shawaran. Ba a dau lkci
ba Mami ta fito rike da Heedayah dake sanye da doguwar riga iya gwiwa, duk gashin
kanta a bude, kana ganinta kasan daga bacci ta tashi, Mami ta xaunar da ita nan
kusa da shi tace "Ga Yaya ki gaishesa" daga haka ta koma kitchen don karasa abinda
take, hannu Heedayah ta kai a hankali tana ta6a sa, har ta kai hannunta fuskarsa,
ya kama hannun yana kallonta yace "Ina maki wasa ne?" Turo baki tayi tace "Nasan
kai ne ai" hancinta ya ja yace "Sai na....." Ganin ynda ta 6ata fuska xata yi kuka
ya jawota kusa da shi yace "Ohk sorry, let me pour you juice, xa ki sha?" Ta turo
baki sai kuma ta gyada masa kai, ya bude drink din da Mami ta kawo masa ya diba,
tace "Baka kawo Farida ba?" Bai ce komai ba ya kai glass din bakinta yace "Bude
bakin" bude bakin tayi ya fara bata juice din a hankali, Mami ta fito kitchen din
tana kallonsu tace "Da baka bata ba, bbu wani abincin da take ci sai kayan xaki"
Heedayah na jin haka ta karasa shanye lemon da saurinta, murmushi yyi ya ajiye cup
din, Mami tace "System dina xaka dauko min a gida yanxu" Junaid yace "Ohk..."
Heedayah tana ta6a sa tace "Xaka je da ni??"

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Mikewa Junaid yyi ya da makullin sa yace "Sai na dawo Mami" Mami tace "Alright" a
hankali Heedayah tace "Mami ki ce in rakasa plss" Mami ta kalleta sannan tace "Ki
rakasa ina?" Tace "Inda xai tafi" Shi dai Junaid bai ce komai ba ya nufi kofa har
xai fita sai kuma ya juyo yace "Mu je da ita Mami?" Mami ta hade rai tace "Ku je da
ita ina" Yace "A'a na ji tace xata je ne" Mami tace "To baxa ta je ba, kayi wucewar
ka malam" Heedayah ta tashi tsaye kamar xata yi kuka tace "Mami nooo, pls ina son
in je, I want to meet with farida, ki ce in bi sa" Mami ta kamo hannunta tace
"Farida na Abuja Heedayah, she is not back yet, idan ta dawo you will see her"
Shiru Heedayah tayi kamar xata yi kuka, Mami ta kalli kofa ta ga har Junaid ya
fita, bangarenta ta tafi ta dauko ma Heedayah hularta da takalmi sannan ta dawo ta
sa mata, ta kama hannunta suka nufi kofa, Mami na kallon Mai gadi tace ya leka yace
ma wanda ya fita yanxu ya tsaya, hakan Mai gadin yyi, Heedayah ta ji dadi jin fresh
air ta gane sun fito waje, sai da suka kusa gate Heedayah tace "Mami kin san me?"
Mami ta kalleta tace "Aa my dear, what?" tace "Ina jin kamshin ruwa...." Da mamaki
Mami tace "Kamshin ruwa ku ma daughter?" Heedayah tace "Ehh" Mami tayi yar dariya
ta leka gate, ganin Junaid tsaye jikin motarsa tace "To ga ta ku tafi amma kar ku
dade plss ka ga yamma yyi" ya karaso ya kama hannunta yace "Toh Mami" daga haka ya
wuce mota da ita, Mami na tsaye har taga ya nufi mota da ita sannan ta koma ciki,
front seat junaid ya bude, kawai ya ga ta fara kokarin shiga, ya dagata ya sa ta
cikin motar ya rufe sannan ya xaga ya shiga maxaunin driver ya tada motar suka bar
layin. Heedayah ta juya Inda take tunanin yake tace "Ya sunan ka? Sai in dinga
kiran ka" Bai kalleta ba idonsa na kan titi yace "Ke ya sunan ki" Tace "Sunana
Heedayah Ahmad...." Yace "Heedayah is not a real name" Ta wara ido tace "Ohk,
Ammina tace min sunana Fatima" Sai a sannan ya kalleta, ya dai ci gaba da tukin da
yake, tace "To ka gaya min naka sunan" Yace "Sunana Fatima nima" ta xaro ido kamar
tana ganinsa tace "To ai kai ba na mace bane" yace "To ni na menene?" Tace "Kai
namiji ne mana" Ya d'an yi murmushi yace "Ya aka yi kika sa ni namiji ne? ni ma
mace ne kamar ki" Ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa, juyawa yyi da sauri
yana kallonta, murmushi kawai yake ya ci gaba da tukinsa, tayi dariyarta mai isarta
sannan tace "Toh ai naji muryarka kato ne, ba irin na mata ba, kuma....." Matsawa
tayi kusa da shi ta fara tattaba sa tun daga saman kansa, Bai san sanda ya samu
waje yyi parking ba da sauri yana kallonta, ta sakko da hannunta har fuskarsa ta
fara jan dogon hancinsa sannan ta shafa beard dinsa ta sakko da hannunta har chest
dinsa, dariya ta kyalkyale da tace "Namiji ne wllh" kasa daina kallonta yyi, can
yayi murmushinsa me kyau yace "How did you know?" Tace "Gashi naji gashin kan ka
d'an kadan ne ba irin nawa ba, kuma kana da beard a fuskar ka, kuma you don't have
breast" He couldn't help it but laugh out loud jin maganar ta na karshe, ita ma ta
fashe da dariya tana taya sa, sosai Heedayah ta basa dariya, lkci daya ya daina
dariyan yana kallonta yace "To ai ke ma baki da shi balle ni" ta tsuke fuska tace
"Teacher na tace grown up people ne kawai suke da breast ni yar yarinya ce ai"
Murmushi yyi yace "Ashe kema namiji ne kamar ni" Lkci daya ta 6ata fuska tace "Ni
ba namiji bane, ni na mace ne..." tana fadin haka ta cire hularta dogon gashinta ya
xubo kasa tace "Ka kalla ka ga" Ya fi second ashirin yana kallon gashin nata sannan
ya motarsa after watching and making sure there is no car coming, sai da ya d'an yi
nisa yace "Ke ma dai namiji ne bbu ruwana da gashin ki" rungume hannunta tayi ta
jingina da motar ta ki cewa komai wai tayi fushi, bai kuma ce mata komai ba har
suka isa gida, Mai gadi ya bude masa gate ya shiga yyi parking, fitowa yyi ya xaga
ya bude side dinta yace "To na ji ke mace ce, sakko" ta turo baki xata sakko ya
dagata ya fito da ita, tace "It is going to rain" kallon sky yyi yace "How did you
know?" Tace "Ina jin kamshi" ya kalleta da kyau ya sake kallon sama, da hadari amma
ba sosai ba, ya kama hannunta suka nufi cikin gidan, tare ya tafi dakin Mami da ita
ya dau system din ya kamo hannunta suka fita, tana bin sa a hankali tace "I want to
take tea" Yace "Me yasa baki gaya ma Mami a can gida ba" tace "Tace baxata sake
bani tea ba" downstairs ya sakko da ita ya xaunar da ita saman kujera yace "Wait
for me" ya ajiye system din hannunsa ya wuce kitchen ya kunna gas ya sa mata ruwan
tea, Yana tsaye kitchen din yana jiran ruwan shayin ya tafasa aka fara iska sosai,
muryar Heedayah ya ji with all her strength tace "Where are youuu" ya kashe gas din
ya fito, tsaye ya ganta duk a tsorace, ya karasa inda take yace "I'm here" ta kamo
hannunsa tace "Kar ka bar ni, ina jin tsoro" tana rike da shi ya tafi ya kulle duk
windows din gidan har upstairs, lkci daya aka fara ruwa sosai, ya duka dai dai
fuskarta jin kamar magana take yi yace "What?" Tace "I told you I smelt rain" d'an
murmushi kawai yyi yana tunanin baiwa ne kilan nata, downstairs suka koma ya xaunar
da ita saman kujera yace "Let me make the tea for you" da sauri tace "Noo, kar ka
bar ni, ka tafi da ni plss" tare ya koma kitchen din da ita, tana makale jikinsa
har ya hada mata shayin sannan suka dawo parlor, ya ajiye shayin saman center table
yace "Ki jira ya huce" bata yarda ta xauna ba sai da ta tabbatar kusa da shi ne, ta
jinginar da kanta shoulder dinsa tayi shiru, ya dau wayarsa ya haske fitila don
tuni aka dauke wuta da ake iska, missed calls na Mami ya gani guda hudu, yayi
dialing number ya kai kunne, yana fara ring ta dauka, a fusace tace "Junaid da ku
ke tafiya baka ga hadari bane, me yasa baka dawo min da yarinyar ba??" Yace "Mami
ni ban lura ba sai da muka iso nan gida" Mami tace "Where is she now?" Ya haska
fuskar Heedayah ya ga idonta a lumshe, ya mayar da wayar kunnensa yace "She's
sleeping" Mami tace "I don't care ko kana tuki cikin ruwa ko baka yi, just in the
next 20 mins ina son ka dawo min da ita, I don't want to call you back after this"
daga haka ta katse wayarta, kallon Heedayah ya sake yi xai kwantar da ita ya duba
karfin ruwan da ake a waje ta bude ido da sauri ta rikesa cikin muryar kuka tace
"Noo where are you going" yace "Ba Inda xanje kiyi baccin ki" kin sakesa tayi, ya
koma ya xauna, ta kwanta jikinsa, Yana ta xaune parlon ita kuma tana ta bacci, har
kusan karfe shidda, har sannan kuma ruwan ko raguwa bai yi ba sai ma karuwa, idan
akwai abinda bai iya ba a rayuwa to driving ne cikin ruwa, sarai kuma Mami ta san
hakan, duk motsin da xai yi Heedayah sai ta kara makale masa, bayan wani lkci ya
haska fitilar wayarsa a fuskarta yaga fararen idonta a bude, duk tunaninsa bacci
take, yace "Kin tashi?" A hankali tace "Idan nayi bacci xaka wuce ka bar ni ni
kadai" Ya kwantar da ita jikinsa sosai yace "Noo baxan tafi in bar ki ba yi baccin
ki" sai bayan Magrib ruwan ya tsagaita yana son yaje yyi sllh Heedayah ta ki sake
sa duk da har sannan bata koma bacci ba, haka ya wuce dakinsa da ita yyi alwalan a
can sannan yayi sllh suka fito tare, tace "Where is my tea?" Gaba daya ya manta da
shayin dake kan center table, yace "let me make another one, wannan yyi sanyi"
cikin few minutes ya hada mata wani shayin amma ba mai xafi ba, suka koma parlon ya
xaunar da ita ya kai mata cup din baki, ta rike ta fara sha.... Tana gama shan
shayin ya dau makullin motarsa yana rike da ita da system din Mami suka fita gidan,
ya kulle gidan sannan ya nufi motarsa, sosai garin yyi sanyi, ya bude front seat ya
xaunar da ita bayan ya ajiye system din a baya, ya xaga ya shiga motar suka bar
gidan, dai dai kofar gidan Abba yyi parking, nan gabansa ya fara faduwa don yasan
Mami won't take it likely with him this night, ya dai fito ya xaga ya bude ma
Heedayah side dinta, ta laluba ta kamo hannunsa kamar xata yi kuka tace "Ina jin
sanyi" ya saukar da ita yace "We are home" dai dai bakin gate suka hadu da Shuraim
xai fito, Junaid na kallonsa ya sake hannun Heedayah ya basa hannu, Shuraim ya amsa
yana kallon Heedayah daga sama har kasa, suka gaisa da Junaid, Shuraim xai fita
Junaid yace "Ehm naga it's late already, pls can you go in with her, ina d'an sauri
ne" Shuraim ya sake kallon Heedayah sannan ya kalli Junaid yace "Alright" Junaid
yace "Thanks" daga haka yyi patting kan Heedayah ya sa hannunta cikin na shuraim
yace "Ki gaida Mami, xan kawo mata laptop din gobe" juyawa yyi ya fita gate din ya
nufi motarsa, Heedayah ta 6ata fuska xata yi kuka jin Junaid ya wuce ya bar ta,
Shuraim dake ta tsaye Heedayah na rike da hannunsa gam, ya saci kallon motar Junaid
ganin har yyi reverse ya xame hannunsa daga nata yayi wucewarsa masallaci, Heedayah
dai na ta tsaye ga sanyi da take ji sosai sai juye juyen idonta take gwanin
tausayi, Mai gadi ne ya fito daga dakinsa alamar shi ma xai wuce masallaci don yin
Isha ganinta yace "Me kike yi a nan yarinya, ki shiga ciki mana" Cikin rawar murya
tace "Bana gani ai" yace "Bakya gani kuma?" Ta gyada masa kai, lkci daya hawaye ya
cika idonta, kama hannunta Mai gadin yyi ya fara tafiya xuwa entrance din shiga
gidan yaga tana bin sa a hankali, lkci daya jikinsa yyi sanyi, yace "To wa ya ajiye
ki bakin kofa?" Tace "Sake ni yyi ya wuce ya bar ni" dai dai kofa suka hadu da
Abba, Abba na kallonsu yace "Wa ya dawo da ke Heedayah?" Tace "Ban san sunansa ba"
Kama hannunta Abba yyi ya wuce part din Mami da ita, Mami ta mike ganinsu, Bai ce
ma Mami komai ba ya sake hannunta ya juya ya fita, kana ganinsa kasan he is angry
and don't want to talk. Mami ta kamo hannun Heedayah tace "Ina Junaid din?"
Heedayah tace "Ya wuce" Mami bata ce komai ba ta wuce daki da ita. Sai kusan sha
daya na daren Mami ta tafi bangaren Abba bayan Heedayah tayi bacci, xaunawa tayi
kusa da kujeran da yake xaune tace "I'm truly sorry barrister, hakan baxai kara
faruwa ba in sha Allah, nasan you are not happy" Yace "It's okay, but pls ki sa ido
a kan wnn
yarinya fisabilillah, don't expose her much to anybody, let her be home all
through, kin san condition dinta, tana bukatan kulawa sosai Rahinah, ina jin
yarinyar nan tamkar jinina bana fatan wani abu ya sameta....." Mami tace "In sha
Allah" yace "Yaushe Farida xata dawo?" Tace "Ranan laraba" yace "Alright, na sa a
nema ma Heedayah lesson teacher soon, Shuraim kuma xai dinga mata karatun qur'ani
da asuba na gaya masa, so after prayer kar ki bari ta koma bacci...." Mami ta
kallesa sai dai bata ce komai ba... Dai dai wnn lokacin kuma Mumy na dakinta ta
shige can cikin bathroom tana ta waya kasa kasa, Mumy tace "Kai ni har na gaji da
bayani har yanxu baka fahimta ba, ce maka nayi makauniya ce fa yarinyar, kuma
dududu Rabi'ah ta ma ta girmeta ina ga, yar yarinya ce fa sosai, bata wuce sha biyu
ba ma kila...." Dariya sosai wanda take wayan da yyi yace "Haba Hajiya, to meye
kuma xaki daga hankali kan yar yarinya? Ni wllh na xata ma kishiyar ce kike...." A
fusace Mumy tace "To kai ina ruwanka? ba dai kudin ka kawai ka sani ba, ni fa na
riga da na gama magana da kusan mutane uku, kawai raba kafa nake ta yi ta ko ina
shi sa na kira ka ba wai wani abu ba don kai ka fiye shiririta, ina ruwanka da
kankantan yarinyar?? kaga.... idan har ka shirya kaga xaka iya sai ka kirani gobe
da safe ni kwanciya xan je inyi..." Tana kai wa nan ta kashe wayar ta fice daga
bandakin ta kwanta kan gadonta tana fata ta samu bacci ko xata ji saukin xafin da
ranta ke mata, rabonta da baccin kirki tun ranan da ta dawo kaduna. Da asuba
Shuraim na dawowa masallaci ya shiga parlon Abbansa don gaishesa don kusan tare
suka dawo masallacin, Abba dake hada wasu files ya amsa ba tare da ya kallesa ba
yace "Yau xa ku fara karatun da Heedayah koh?" Shiru Shuraim yyi da farko, yana
mamakin why all of a sudden Abba xai fi karkata hankalinsa gaba daya kan makauniyar
nan, Bai ma ce suyi har da su Rabi'ah ba wai Heedayah, jin shiru Abba ya juya ya
kallesa, Shuraim yace "Sure in sha Allah" Abba yace "Good, a can parlon Aunt dinka
xaku dinga yin karatun" shiru ya kuma yi na kusan second goma sannan yace "I prefer
mu yi a inda nake yi ma su Rabi'ah" Abba yace "Ina kenan?" Yyi kasa da kai yace
"Balcony" Abba yace "Noo, akwai sanyi waje, you look for another alternative"
mikewa Shuraim yyi ya nufi kofa ya fita, gaba daya ji yyi ya kara tsanar Heedayah
har ransa, WTF, ba don he can't look into his father's eyes and tell him baxai yi
ba da bbu abinda xai hanasa yin hakan, ya fi minti biyar tsaye a parlor kafin ya
nufi part din Mami ya tsaya ya kwankwasa kofar fuskarsa daure.

For those forwarding this book to various groups bayan sun san na kudi ne, ni baxan
ce komai ba, but su yi adalci, it's not fair hakan ba na kyauta bane littafin, na
hada su da Allah su yi hakuri su daina hakan ba don ni ba.....

Masu neman complete Heedayah su ma sai su biya dari uku a basu sharp sharp don naga
sun ma fi masu subscribing for daily update yawa, idan ba complete bane damasu baxa
su biya ba sai dai su karanta a titi yana galantoyi, to ku biya a baku complete, I
have change my mind, kawai da evidence din ku xa ku taho sai a baku complete
din....🌚🌚🌚

Heedayah na kudi ne, ba kyauta ba, try and subscribe to read happily bbu burden a
kanka....

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Mami ta bude kofar parlonta jin ana knocking, suka yi ido hudu da Shuraim, sauke
idonsa yyi da sauri, murya can kasa yace "Ina kwana" A takaice tace "Lafiya.... Ya
aka yi?" Yace "Karatu xa mu yi?" Mami tace "Da wa?" Ya d'an yi shiru sannan yace
"Ban san sunanta ba" Mami tace "Toh sai kayi kokarin sanin sunan nata coz gida daya
ku ke ynxu" daga haka ta juya ta koma ciki ya bi ta da wani irin kallo, Mami ta
karasa sa ma Heedayah kayanta don har tayi wanka, ta dau hula ta sa mata a kanta
sannan tace "You listen and pay attentive kin ji, Kuma kiyi kokari sosai, idan kin
dawo xaki koya min nima" tace "Toh Mami" Mami ta kama hannunta suka fita xuwa
parlor, har sannan yana tsaye, dai dai kusa da shi Mami ta tsayar da Heedayah,
sannan ta juya ta koma ciki ta kulle kofarta, Heedayah ta kai hannu tana laluba
wajen ta ji inda yake, hannunsa ta ta6a, bbu bata lkci kamar jira yake ya buge mata
hannun yace "Are you stupid" Ta janye hannunta da sauri kamar xata yi kuka tace "Ni
me na maka??" Ya kalli left sannan ya kalli right ya fixgo hannunta ya fara tafiya,
bin sa take hawaye cike idonta tace "Ni ka sake ni bana so, baxan yi karatun ba
kuma, baxan yi ba...." Ko saurarenta bai yi ba har ya isa wani area cikin parlon
wanda ya kasance study area din Abba, sannan ya saketa yana mata wani kallo yace
"Kika ce baxa ki yi karatun ba??" Cikin kuka tace "Ehh ni baxan yi ba, ka kai ni
wajen Mami" ya ja kujera ya xauna yace "Sai ki kai kanki ai" durkushewa tayi a kasa
ta fashe da kuka sosai tace "Ni sai na gaya ka da Abba wllh...." bude kofa aka yi
Shuraim ya juya da sauri bai jira ya ga wanda ya bude kofar ba ya xamo kasa kusa da
ita ya dake cike da karfin hali yace "Okay, sorry mu yi karatun ynxu" ta make
kafada tace "Ban so" satan kallon cikin parlon yyi duk da bai ga wanda ya fito ba
har sannan, ya wani hade rai yace "I said sorry" Kamar jira take tace "Ban so nace"
sai kuma ta fashe da wani sabon kuka, kamshin turaren Abbansa da ya ji yasa yasan
Abba ne a parlon, ya dawo kusa da ita ya kamo hannunta a hankali yace "But nace
kiyi hakuri, I'm sorry" ta turo baki tace "To me yasa xaka buge min hannu sbda bana
ganin ka, kuma shine kake ja na don in fadi in ji ciwo" Ya kara satan kallon parlon
cikin dakiya yace "To rama" ta kai hannu ta laluba kafarsa sannan ta maka mashi
duka a nan, kallonta kawai yake da mamaki xuciyarsa na tafarfasa, still controlling
himself yace "Shkkn?" Ta gyada masa kai a hankali tana goge idonta, ya koma saman
kujera yace "To fara karatun" tayi kasa da murya ta fara karatun a hankali, har
Heedayah ta tsaya a aya na 15 bai ji inda xa ayi mata gyara ba, her recitation was
perfect and cool for her age, sai dai wayarsa kawai yake dannawa, Ya saci kallonta
ganin tayi shiru sai dai bai ce komai ba still pressing his phone, ta turo baki
tace "To ai a nan mu'allimata ta tsaya min" yace "Toh sai ki tsaya a nan din" yana
fadin haka ya mike ya tafi kitchen, Sabuwar me aikin da Mumy ta dauka ne a kitchen
din tana ta gyare gyare da goge goge, yace "Wancan yarinyar xaki dauka ki kai ta
wancan part din..." Gaishesa tayi da ladabi tace "Wace yarinya yallabai?" Fita yyi
kitchen din yace "Ki taho ki ganta" sai da ya tabbatar ta ga Heedayah sannan yayi
wucewarsa sama, har part din Mami mai aikin ta kai ta, duk da sai faduwa gabanta
yake don ba karamin warning Mumy tayi mata ba kan cewa ko bangaren Mami kar ta
kuskura ta bi balle ta shiga, Mami ta bude kofa ta amsa gaisuwan mai aikin sannan
ta kama hannun Heedayah suka koma ciki ta kulle kofar, Mami na kallon Heedayah tace
"Ina me koya maki karatun?" Heedayah tace "Mami bai koya min komai ba" Mami tace
"Me yasa?" Heedayah ta 6ata fuska tace "Mami mugu ne, I don't like him to teach me
anymore...." Mami dai bata ce komai ba ta wuce can bedroom da ita, Heedayah tace
"Mami he is wicked, ni nafi son wannan din nan ya koya min" Mami tace "Wa?" Shiru
Heedayah tayi sai kuma tace "Yace min sunansa Fatima shi ma, kilan baya son gaya
min sunansa" Mami na kallonta tace "A ina yake?" Heedayah tace "Wanda ya xo jiya ya
tafi da ni" Mami tace "Sunansa Junaid, but you call him Yaya" tace "To, na fi son
Yaya ya dinga koya min" Mami bata kuma cewa komai ba ta xaunar da ita saman gado
tace "Kwanta kiyi baccin ki xan je in hada maki breakfast" daga haka ta fita dakin,
Heedayah ta kwanta. Mami na tsaye kitchen su Rabi'ah suka shigo ajiye plates da
cups da suka yi breakfast duk suka fice bbu wanda yace mata komai, ta gama dafa
Indomie da kwai da shayi da take yi ma Heedayah ta fito kitchen din, a parlor ta
tadda Abba alamar he is going out kuma ita yake jira ta fito kitchen, yana kallonta
yace "Ina Heedayah, bata gaisheni ba yau" Mami tace "Let me bring her" daga haka ta
wuce bangarenta, Duk wannan abun Mumy na ta kai komo parlon kai kace wani abu take
yi, Abba dai bai ce mata komai ba don har ranan bata gaishesa bata masa magana a
gidan, Yana ta tsaye parlon Shuraim ya fito shi ma xai fita, Abba yace "Yaushe
rabon ka je gaida kaka Aliyu?" Ya d'an yi shiru kafin yace "Abba bana dawowa da
wuri ne ynxu" Abba yace "Ohk yau ka je ko da kuwa tsakar dare ka dawo, and you go
with Heedayah ita ma ta gaisheta, she is complaining ba a kai ta ba jiya da
naje...." Shuraim ya kalli Abba, amma bai ce komai ba, Abba yace "Su Khadijah ma
nace idan sun dawo islamiyya su wuce can, so idan ka je sai ku dawo tare gaba daya"
Mami ce ta karaso rike da Heedayah, Abba na kallonta ya dafa kanta yace "How are
you dear?" Tace "Good morning Abba" yace "Morning Daughter, kun yi karatun yau
koh?" Ai ko rufe baki Abba bai yi ba Shuraim ya nufi kofa, Heedayah tace "A'a bai
min ba" Abba ya kalli Shuraim da har ya isa kofa cikin tsawa yace "Aliyu" Mumy ta
karaso cikin parlon da sauri tace "Ba gane Aliyu ba?? Shi Aliyun malami ne ko kuma
makafi na haifosa ya xo ya dinga yi ma karatu, kaga a gaskiya barrister ku tsaya
iya Lane din ku kai da Sabuwar matarka da makauniyar ka a gidan nan, ku fita
harkarta da ta 'ya yana, Yaushe aka sa Shuraim ya dinga koya mata karatu bani da
labari? Kanninsa da suka fito ciki daya ma an ga yana koya masu karatu balle
makauniya, to wllh ni a kiyayeni a gidan nan, ku bar ni kawai yanda ku ka gan ni
ayi ta tafiya a haka kar ku kai ni bango...." Abba yana kallon Shuraim da kyau yace
"Me na ce maka jiya da asuba?" Yyi kasa da kai bai ce komai ba, Abba yace "Good,
idan kana son ganin the other side of me ka sake tsallake magana ta a gidan nan,
wllh sai dai ka tafi wani gidan uban amma ba wannan gidan ba, yanda uwarka ta isa
ta fada maka kaji, haka nima, idan kuwa watsar da maganata xaka dinga yi a kan wani
banxa son xuciya na uwarka to you have to change anoda father and anoda home, Kuma
ni nayi instructing dinka ka dinga koya ma Heedayah karatun qur'ani in har ka isa
ka tsallake instruction din in gani" A mugun fusace Mumy tace "To sai me don kace
ya canja uba ya bar gidan nan?? Kansa farau barrister? Ai ba abun mamaki bane don
ka fadi haka tunda an gama da kai an shanye ka, nan gaba mu ma duk kora mu xaka yi
ka cika gidan nan da agololi da 'ya yan tsintuwa, Kuma in har ni na haifesa baxai
koya ma wata makauniya karatu ba tunda ban ce yaje xai gani ba" Dariya Mami tayi ta
kama hannun Heedayah ta koma bangarenta tana girgixa kai, Shuraim dai bai iya yace
komai ba, ya juya ya nufi kofa ya fice daga parlon, Banda kallon Mumy bbu abinda
Abba yake as if thinking of how to punish her, cike da neman fitina tace "Ehh ka
kalleni da kyau, cewa nayi in dai ni Maryam ina gidan nan wllh wllh Shuraim baxai
koya ma wata shegiyar makauniya karatu ba, uwar me ya hada da ita xaka ce ya koya
mata karatu???" Calmly Abba yace "Maryam ki tafi gidanku sai na neme ki, bana son
in dawo in tarar da ke gidan nan don wllh in har na dawo na same ki a cikin gidana
to na sake ki...." Yana fadin haka ya nufi kofa walking just as the barrister he
is, Mumy ta bude baki ta bi sa da kallo a sanyaye ta kasa cewa komai.... Kuka bbu
irin wanda Mumy bata yi ba a dakinta, ta kira duk kawayenta ta sanar masu abinda
ake ciki, Hajiya Sadiya ce ta samu karshe a waya, Hajiya Sadiya ta dinga salati
tana cewa "Ki tafi gida kuma?? Anya kan barrister daya kuwa, yaushe kika dawo daga
gidan xai ce ki koma? Ehh lallai bbu lafiya, ba dai kin tsaya fi'ili wai ke baxa ki
je a nema maki taimako ba, ke da kika fi kowa imani, to wllh taki ta sameki,
shegiya nake idan haka yar bokon nan ta shigo maki gida, wllh da shirinta ta shigo,
lafiyayyen shiri kuwa, mance komai xaki yi Maryam mu tafi mu san nayi kafin lkci ya
kure maki, ba fa karamin case bane wnn wllh, tunda kike da barrister ya ta6a cewa
ki tafi gidanku, ki xauna fa kiyi naxari, to wllh ana dab da kwace maki gida da
mijin ki, wnn makauniya dai ta jaza maki abubuwa iri iri a rayuwa, duk ita ce silar
faruwar komai" kuka kawai Mumy take kamar ranta xai fita tana cewa "Wlh Sadiya na
canxa xuciyata xan iya kashe yarinyar nan idan hakan kadai ne mafita gareni, ta
tarwatsa min farin ciki, ta tarwatsa min gida, a kanta barrister yake min duk
abubuwan nan, ga kishiya ta sa an rangada min...." Sadiya tace "Bbu wani lkcn kuka
da kumfar baki Maryam, ki dau duk abubuwan da kike bukata ki baro gidan nan kafin
ya dawo saki ya tabbata a kanki, ki taho nan gidana mu san abun yi cikin gaggawa,
maxa ki fita daga gidan, Kuma a gaban yar bokon yace ki tafi gida?" Mumy ta kara
rushewa da kuka tace "Wa ya sani ma ko tana labe duk tana ji, ni dai ga ni nan xuwa
ynxu" daga haka ta katse wayar ta shiga hada yan kayanta da sauri kar barrister ya
dawo, cikin mintunan da basu wuce goma ba ta bar gidan xuwa gidan Sadiya. Mami na
xaune parlonta misalin karfe biyar na yamma da frnds dinta uku da suka kawo mata
ziyara, ko marmarin xaman main parlor din gidan bata ta6a yi ba tun xuwanta, hatta
bakinta bata bari su xauna main parlor, nata parlon take kawo su, bata ma san Mumy
bata gidan ba tun safe, aka kwankwasa kofar parlonta, mikewa tayi ta isa bakin
kofar ta bude, Shuraim ne tsaye sanye da kananun kaya, yyi kasa da kai yace "Ina
yini?" Tamkar
ana tilasta sa ya gaisheta can ciki ciki, Tace "Ya aka yi?" Bbu walwala yace "Abba
yace xa mu je can gidan kaka da ita" Mami tace "Ita wa?" Yace "Yarinyar" Mami tace
"Yarinyar bata da suna?" Shiru yyi mata, can yace "The blind girl" Mami tace "Toh
ka kirasa ka tambayesa sunanta, kada ka sake xuwa min bakin kofa kana neman blind
girl I don't have any" tana fadin haka ta rufe kofarta almost on his face. Da ba
don ya san Abbansa is jet angry at him ba kuma kar ya sake wani laifin da wucewarsa
kawai xai yi ba tare da Heedayah ba, gaba daya ya rasa yanda xai yi, bayan kusan
minti biyar ya sake kwankwasa kofar, ba Mami bace ta bude kofar wnn karon,
Barrister Zuwaira ce ta bude, yace "Ina yini?" Tace "Lafiya lau.... A carbon copy
of ur father facially but not physically, ba haka Barrister Ahmad yake ba gaskiya,
be human plss, let me get u the little girl" daga haka ta juya ta koma ciki ya bi
ta da wani irin kallo, sai ga ta ta dawo da Heedayah da Mami ta sama Hijab har kasa
duk da kananun kaya ne sosai jikinta tunda gidan Kaka xa a je, Barrister Zuwaira ta
mika masa hannun Heedayah da ta bata fuska, ya kama hannun nata, ta rikesa gam ya
juya ya bar wajen, bin sa kawai Heedayah ke yi kmr xata yi kuka har suka fito
balcony, a dai dai nan ya kwace hannunsa daga nata ya sauka balcony din fuskarsa
daure, a hankali take tahowa bayan ya saketa, shi ko har ya fara tafiya ya tuna few
stairs dake wajen ya juya da sauri.... Bai yrda ta kai kasa ba ya dauketa irin
rikon newborn with both hands, ba karamin tsorata tayi ba jin ta tafi xata fadi sae
kuma taji an dauketa bata fadi ba ta ta6a kirjinsa kamar xata yi kuka tace "Ni dai
baxan je ba kuma...."
Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Masu complete Heedayah hope har kun gama karantawa🌚


Shiru har ynxu banji sharhin karshen book din ba, duk da nima ban san me ya faru
karshen ba😯

Shuraim bai saurareta ba har ya isa motarsa ya bude back seat ya jefata ciki ya
kulle sannan ya xaga ya bude maxaunin driver ya shiga, tuni Mai gadi ya bude masa
gate ya fita gidan, Har ya isa kofar gidan Baffa bai kalli Heedayah dake bayan mota
ba, ta rungume hannu kamar xata yi kuka, a compound din gidan yyi parking, sai a
sannan ya kalleta ta madubi, ya wani hade rai kamar tana ganinsa, d'an tsaki ya ja
ya bude motar ya sauka sannan ya bude mata side dinta yace "Fito min a mota" Ta
make kafada a hankali tace "Ni ka maidani wajen Mami baxan fito ba...." Yace
"Kee.... an ta6a xaneee ki???" Bai jira cewarta ba ya jawota ya fiddo ta daga cikin
motar ya ajiyeta kasa ya rufe motarsa yace "Idan ina magana kina yi sai na fasa
maki baki wllh...." Ta fashe da kuka sosai tace "To me bakina yyi maka, ni bana
sonka you are wicked...." Sudais ya hango ya fito daga cikin gida, hakan yasa ya
kai fuskarsa dai dai nata yace "Xa ki san I am wicked soon...." Daga haka yyi
wucewarsa ya bar ta nan a tsaye, yana kai wa inda Sudais yake, Sudais yace "why are
you leaving her all alone, how did u expect her to walk alone" Shuraim yace "Toh ni
d'an jagoranta ne aka ce maka??" Bai jira cewar Sudais ba yyi wucewarsa ciki,
Sudais ya karasa inda take da sauri ya kamo hannunta ya duka yana kallon manyan
idanuwanta da ya cika da hawaye yace "What happened cutie..." Cikin rawar murya
tace "I hate him...." Sudais ya rungume ta yana goge mata hawayen idonta yace "Noo
cutie cry no more, mu tafi ciki ki gaida kaka...." Kamar ko jira take ta fashe da
kuka sosai, rikicewa Sudais yyi ya shiga lallashinta, har sai da ya ga tayi shiru
tana sauke ajiyar xuciya, lkci daya ya ji ransa ya baci, ya mike ya kama hannunta
suka wuce ciki, parlon kaka ya tadda Shuraim, Kaka sai harkar gabanta take tana
'yan wake wakenta na tsofaffi ko kallonsa bata yi ba kamar yanda shi ma bai kalli
inda take ba yana danna wayarsa, Sudais na kallonsa fuska daure yace "Shuraim why
will you leave the innocent girl all alone...." Shuraim yace "Plss Sudais don't
question me, I am not ready to answer you..." kaka ta ajiye tsummar hannunta tace
"Me ya faru Sudess?" A fusace Sudais yace "Kawai barin yarinyar yyi ita kadai a
tsakar gida ya san ba gani take ba, what sort of nonsense is that" Kaka ta nemi
waje ta xauna tayi tagumi a hankali tace "Ohh naga abinda ya isheni ni patuuu, Kai
amma dai Amadun ne gantalalle wllh, me yasa xai hada baiwar Allah da bata san komai
ba da wannan katon mutumi, wato Amadu ya raina mugun halin d'an nan nasa koh? Bai
san abun ya wuce misali ba, ya wuce hankali ya dauka ba ko, Wllh shuree yake ko
wa?? ba shi da xuciya me kyau ina fada kuna ganin kamar wasa nake, Baka ga ko
gaisheni bai yi ba da ya shigo yana jiran ni in gaishe sa d'an banxa, ni dai ba
ruwana don na haifi ubanka ba yana nufin ina da wani alaka ko dangantaka da kai
bane, kayi ta kanka inyi ta kai na, makauniya kuma sai Allah ya saka mata tunda
bata cuce ka ba...." Sudais dai sai hararan Shuraim da yyi kamar bai san suna yi ba
a parlon yake, wayarsa kawai yake dannawa, kaka ta kamo hannun Heedayah ta xaunar
da ita saman kujera tace "Sannu da xuwa Deedaya, ai da kyau tunda ba a titi ya
gantalar da ke ba yyi wucewarsa ya ja ma d'a na fitina, haka nan muke fama da shi
da mugun halinsa, mu ma ba kyale mu yyi ba, Bai san ba sonsa Allah ya fi yi da ya
bar sa da idanuwansa ba ke kuma ya barki bbu idanuwa, shi fa Allah ba ruwansa gobe
Shuree na iya tashi ya gansa a duniyar makafi to sai yyi yaya??" Tsaki Sudais ya ja
ya fice daga parlon, Shuraim ya bi sa da wani kallo ta gefen ido, Kaka ta bude
fridge ta fiddo malt ta bude mata tace "Wnn yaron kirki Junaidu ya xo jiya ya kawo
min su da yawa, to bai fiye min wasu ba Allah na tuba, bbu abinda fa na hada da
shi, kawai dai babarsa na auren d'a na ne, amma ko shekaranjiya sai da ya xo nan
gaisheni muka yi ta hira gwanin ban sha'awa, to wasu ma idan suka xo sai dai su
dinga tunanin ynda xa su cuceka kafin su wuce.... To ni dai bbu ruwana" A hannun
Heedayah Kaka ta saka malt din, Heedayah ta fara sha a hankali tana lumshe ido,
Kaka ta xauna tace "Toh madallah, yau dai na gama aikin da wuri, na gode ma Allah"
Shuraim ya kashe wayarsa calmly yace "Ina yini Kaka?" Tace "Lafiya lau wllh, ai tun
safe sae ynxu na gama kimtsa ko ina, baka da lafiya ne na ganka duk wani iri yau?"
Yace "Lafiya ta lau" tace "Atoh naga duk ranka a bace ne ai, ko kai ma in kawo maka
mantinan ne?" Ya girgixa kai kawai, tace "Toh in xubo maka abinci, shinkafa ce dai
da miya" nan ma ya girgixa mata kai, tace "Toh ban da abinka meye na bacin rai kuma
Mai gida, da shi Amadun yace ka kawota nan sai kace masa gaskiya kai kana da wajen
xuwa, ae ba ajiye ka yyi ba, ban da neman magana irin tasa kai xai sa kayi ma yar
makauniyar direba, shi da ya jajubo ta ba sai ya kawota da kansa ba, ni ba ruwana
bana son rashin gaskiya, abu dai ba ayi tsakani da Allah, ae baxa ka rasa uxurin
gabanka ba kai ma" Mikewa Shuraim yyi ya dau bottle water daya a fridge yace "Xan
shiga in gaida su Umma" Kaka tace "Toh sai ka dawo, sai dai yau ko yar kazan nan ba
a kawo min ba Mai gidan, ko da yake ina xaka kawo min kaza an hada ka da yarinya ba
dangin iya balle na baba...." Fita yyi parlon, kaka ta tabe baki ta mike ta dau
tsumman ta ci gaba da goge gogen da tace ta gama, Heedayah na gama shan malt din ta
jefar da can din nan parlor, kaka ta leko daga d'an kitchen dinta tana kallonta
tace "Ehh lallai, to sauka ki dauke ki fita da shi bola, ae ni ba baiwar Amadu bace
balle ke" Heedayah ta sauka da sauri ta durkusa tana laluba Inda xata ji can din,
kaka tace "Laluba gefen ki maxa ki dauke ki fitar min da shi ni ba yar bola bace,
kaji min yarinya in mata inuwa tayi min rana, duk gidan nn bbu wanda na bai wa
mantinan nan sae ke, shine xaki walakanta min parlor" Heedayah ta samu ta dauke can
din ta mike duk a tsorace, a hankali tace "To bana gani" kaka tace "Hagun ki xa ki
bi ki fita, ni xa kiyi ma karya kice ba kya gani" dai dai nan Sudais ya shigo
parlon, kaka tace "Kaji wai xata je ta yarda gwangwani ta ja min salalan siya wajen
Amadu Sudess...." Tsayawa Heedayah tayi tana kalle kallen kamar mara gaskiya,
Sudais ya kama hannunta suka fice daga parlon, kaka tace "A'a, yau ga ikon Allah,
ya xan ce a kawo min yarinya takanas kuma ka xo ka dauketa Sudess" tuni Sudais ya
kulle mata kofarta, ya wuce xuwa dakinsa yana rike da hannun Heedayah, Heedayah ta
ta6a hannunsa tace "Waye kai?" Ya kai bakinsa kunnenta yace "Heedayah ne ni" tana
jin muryar sa ta washe hakora tace "Baka bani sauran chocolate dina ba" yace "Shi
xan je in baki yanxu" ta kankame hannunsa tace "Mu tafi gida wajen Mami da kai sai
mu bar wnn mugun a nan plss" dariya yyi ya wara ido yace "Da gaske" ta gyada masa
kai tace "Ehh I don't like him, shi mugu ne...." Bude kofar bedroom dinsa Sudais
yyi yace "To gaya min me da me yyi maki" Shuraim dake kwance saman gadonsa ya juya
yana kallonsu, tace "Komai ma yana min ai, first ya fara buge min hannu don yaga
bana gani, kuma Abba yace ya min karatu ya ki yyi min..." ta girgixa kai tace
"Noo... I just don't like him, and I will never like him...." Dariya Sudais ke yi
yana kallon Shuraim da ya mike xaune fuskarsa a daure yana kallonta, Sudais ya
dagata ya xaunar gefen gado yace "Toh kin gaya ma Abba abinda yake maki" tace "Yau
duk xan gaya masa ae, har da duka na da yyi...." Ta wara ido tace "Ae kai ma ka iya
suratul jinnnn Koh?" Ya gyada kai yace "Sosai ma" tace "Toh mu tafi gida da kai sai
mu bar sa wajen matan nan me yi ma mutane fada" Sudais yyi dariya yace "Sunanta
kaka" tace "To mu bar sa wajen kaka shi, bana son ya bi mu" Gaba daya Shuraim ya
kasa cewa komai, Sudais na kallon manyan idanuwanta yace "Toh xa mu bar sa a nan mu
tafi gidan tare kin ji cutie" ta washe hakoranta tace "Toh ina chocolate dina"
mikewa yyi yace "Bari in dauko maki" Sai a sannan Shuraim ya fixgota da karfi yace
"Uban waye mugu?" Sosai ta tsorata jin muryar sa, ta fasa ihu tana son kwace kanta,
Sudais ya dawo da sauri yace "Don't you dare touch her, don't try that" yana fadin
haka ya dauke Heedayah da jikinta ke rawa a wajen, ta kankamesa cikin rawar murya
tace "Take me away plss" ficewa Sudais yyi daga dakin nasa ya kulle kofar trying
hard not to laugh. Mumy ce xaune parlon Hajiya Sadiya tayi tagumi, Hajiya Sadiya
tace "Anya kina ganin baxa a xarge ki ba Maryam, hakan yyi wuri ai wllh, ki bari
kawai mu lallaba ayi duk abinda xa ayi a samu ki koma dakin ki, kinga idan kina
gidan ko ma me ya faru bbu wanda xai xarge ki bbu wanda xai kawo ki a rai, amma
yanxu fa?? ai daure kanki kawai xa kiyi, barin mijin ki barrister, kishiyar ki
barrister" Mumy tace "Nima wllh tunanin da nake kenan, gaskiya kika fada, bari a
share wnn batun ynxu kawai...." Hajiya Sadiya tace "Yauwa, yanxu kina komawa nunawa
xa kiyi kin fi kowa sonta ma a gidan, kiyi iya bakin kokarinki ki danne komai a
kasar xuciya ki, ita kanta kishiyar taki ki d'an fara sake mata kuna gaisawa yanda
bbu wanda xai samu damar xargan ki nan gaba, karatu kuma kiyi ta tausasa Shuraim
yyi mata, yaranki duk ki sa su dinga shiga gun kishiyar taki su dinga jan
makauniyar a jiki, wllh duk kika bi shawarata komai xai xo mana da sauki
Maryam...." Mumy tace "Kai da bani da ke da nayi Kuka Sadiya, nagode aminiyar
kwarai Allah ya bar xumunci, amma ita wnn tsohuwar kuma ya kike ganin xan yi da ita
in huce takaicin annamimancin da ta min" Dariya Hajiya Sadiya tayi tace "Ke wa ke
sa wnn ta6a66iyar a lissafi, ba fa isasshen kwakkwaro gareta ba, ynxu dai muyi
concentrating a abinda yake gabanmu ki ajiye batun wnn tsohuwar" Mumy tace "Toh
shkkn, ynxu dai bari inje gida wajen Salima in ji ita kuma ya ake ciki, daxu na
kirata tace da yamma xata koma gida, bari in je in dawo" da haka suka yi sallama
Mumy ta bar gidan Hajiya Sadiya.

I don't have complete Heedayah pls fans... Sae dai in aron brain din Khaleesat
Haiydar xan baku ku shiga ku karance tass, I made jest of those that are not
patronizing☹️
sae dai su karanta a titi suna jiran su samu complete... and a lot of
pple are thinking da gaske ne akwai complete din, to nima kullum nake typing din
ban san ma me xai faru a karshen ba😄😄
Lol.... patronize ur novelist lovely fans, ni ban iya Allah ya isa ba, amma kuyi
patronizing for the sake of Allah coz it's not free.... And ina xumunci da duk
wanda ya siya Novel dina, bana goge lambarsa....

Meanwhile ina son jan hankalin readers sau daya nake posting a rana which is 5 to 6
read mores everyday, in har nayi less than 5 read more may be 3.... To xan yi post
da daddare in cike read mores din.... Stop expecting more than that all my books
haka nake yi. Thanks lovely fans

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Bayan isha Shuraim ya shigo parlon kaka da sallama, kaka dake xaune ta sa tv gaba
wai tana kallo tace "Ni ai na xata ka wuce, ka ma ci abinci kuwa ko basu ga daman
baka ba?" Ya xauna saman kujera yace "Bana gidan, yanxu na dawo, ina su Khadijah?"
Kaka tace "Waye kuma su Khadijah, tun karfe shidda suka wuce kamar ana tsungulinsu
ai, kuma uwar ce ta koya masu idan sun xo kar su dade, wannan yarinya Deedayah
kadai ce kwance tana bacci a daki, to ni bata fiye min su ba ma Allah na tuba..."
Bai tanka ta ba, bayan wani lkci yace "Toh ki taso ta xa mu wuce..." Kaka ta juyo
da sauri tace "In taso ta kuma, nan din da can gidan naku ba daya bane xan taso ta?
ko kuma me xata maku idan ta je can gidan ban da wahalar da ita da ku ke" Yace
"Abba bai ce in bar ta a nan ba" Kaka tace "To dama ya xai ce a bar ta a nan in
cinyeta ga ni mayya, sai ka shiga ka daukota ku wuce ku bani waje, idan haka ne ma
kar a sake kawo min ita ko nace a kawota, baka ga ba har kitso sai da nayi mata na
wanke nata hijabi da ta 6ata da lemon da wnn mutumi Sudess ya bata shi kuma
wahalalle, ita kuma wnn sabuwar matar ta rantse baxata daina sa mata kayan shegu
ba, har nace xan bada kudi a siyo atamfa ko 'yan dubu dubu a dinka mata, to ba
ruwana na fasa...." Mikewa Shuraim yyi ya shiga cikin dakin, kwance ya tadda
Heedayah tsakiyar gadon Kaka tana bacci manyan kalaban da kaka tayi mata ya rufe
fuskarta, ya karasa bakin gadon yana kallonta kafarta ya buge amma bata ko motsa
ba, ya sake buge kafar ta juyo ta bude idanuwanta da suka kumbura a hankali, kana
ganinta kasan ta ci kuka, yace "Sakko kar in wuce in bar ki" Jin muryarsa ta fara
sakkowa tana lalube lalube ta mike tsaye, kama hannunta yyi tana bin sa kamar xata
fadi suka fita dakin, ya dau makullin motarsa saman kujera yace "Sai da safe" Kaka
tayi masa banxa ita a dole an tafi da Heedayah, dai dai bakin kofa ya ji an wurgo
masa abu a kai ya juya ya ga Hijab din Heedayah ta jefo masa, ya rike Hijab din yyi
ficewarsa ya kulle mata kofarta.... A kusa da motarsa ya sake hannun Heedayah bayan
ya bude motar, ita dai tana tsaye sai bin inda taji motsi take da ido, yace "Baxa
ki shiga ba sai na wuce na bar ki?" Kamar xata yi kuka tace "Toh ai bana gani, Kar
ka wuce don Allah" yace "Xa ki kwana a nan kuwa idan ni xan saka ki cikin motar" da
sauri ta fara ta6a motar tace "Aa plsss" Ta laluba jin motar a bude ta shiga, kulle
motar yyi ya xaga xai shiga side din driver sai ga Sudais, ya jira har ya karaso,
Sudais yace "What about Heedayah?" Ba tare da Shuraim ya kallesa ba yace "Tana
wajen kaka, sai da safe" Sudais yace "Ohk a nan xata kwana?" Shuraim yace "Ehh"
Sudais yace "Alright, sai da safe" Shuraim yace "Allah ya kai mu" daga haka ya
shiga motarsa yayi reverse, Sudais ya koma ciki. Shuraim na isa gida yyi parking a
parking space ya fito ya bude back seat, kwance ya ganta ta koma baccin, bude gate
da aka yi yasa ya juya yaga Abba ne ya shigo gate din from mosque, Tashinta ya
shiga yi yace "Sakko mu shiga ciki we are home" Bai jira tace komai ba ya sauko da
ita ya kama hannunta ya nufi entrance din shiga gidan walking calmly... Mami na
kallon Heedayah dake xaune saman kujera tace "Toh shine kike kuka Heedayah?" Cikin
rawar murya tace "Da xafi ta min, kaina yana ta ciwo yanxu" Mami tace "To yi hakuri
xai daina my dear...." Abba ya bude kofar parlon Mami ya shigo, Mami na kallonsa
tace "Welcome..." Yace "Thank you, sai yanxu suka dawo" tace "Ehh gashi kaka tayi
mata kitso ma" Abba na kallon idon Heedayah yace "What happened to her eyes?" Mami
tayi dariya tace "Kukan kitso mana" Heedayah ta fara shessheka tace "Abba xafi yake
min" Abba yace "Xafi kuma?" Ta gyada masa kai, yace "Toh a kwance" Mami tace "A
kwance? nan da gobe fa xai daina xafin" Abba yace "No a kwance gaskiya, wnn kitson
ai an dauresa da yawa, Kar ya ja mata matsala, till date Rabi'ah bata kitso a gidan
nan sbda irin haka" Mami tace "Ikon Allah...." Abba ya fita don daukan wayarsa dake
ring, Mami na kallon Heedayah tace "Toh baxa a kwance ba mu je ki kwanta, kin dai
ci abinci Koh?" A hankali Heedayah ta gyada mata kai, Mami ta kama hannunta ta wuce
da ita bedroom, ko da ta fito a parlonta ta tadda su Khadijah da Rabi'ah a xaune
kana ganinsu kasan Abba ne ya saka su shigowa, duk suka gaisheta, ta amsa tace "Kun
debi abinci a kitchen?" Khadija tace "Uhn mun ci" Ranan dai duk a bangaren Mami
suka kwana. Da Asuba Shuraim na dawowa masallaci ya tafi part din Mami, a hankali
ya kwankwasa kofar, Rabi'ah ta bude, tace "Yaya ina kwana?" Yace "Lafiya, ina
wannan yarinyar take?" Ta d'an turo baki tace "The blind girl? Tana can daki" yace
"Fito min da ita" juyawa tayi ta koma, Mami na kallon Rabi'ah tace "Waye?" Rabi'ah
tace "Ya Shuraim, yace wai in taho da ita" Mami tace "Bata jin dadi sai gobe"
Rabi'ah ta juya ta koma ta gaya ma Shuraim, wani ajiyar xuciya ya sauke ya juya ya
wuce part dinsa.... Da safe misalin karfe goma sha daya Abba na xaune parlonsa da
Junaid, kasancewar ranan lahadi ce, Abba ya mika ma Junaid takardun hannunsa ya
amsa yana dubawa, Abba yace "Asibitin Mecca aka yi duka wnn" Junaid na ci gaba da
duba takardun gaba daya yace "A kano kenan" Abba yace "Yess" Junaid yace "Ohk...."
Shuraim ne ya shigo parlon da sallama ya kulle kofar, tun da ya shiga dakinsa da
asuba sai a lkcn ya fito, ya xauna nan kasa ya gaida Abba, sannan suka gaisa da
Junaid, Abba na kallon Junaid da duk hankalinsa na kan takardun yace "So xan baka
kudi ka siyo eye drops da aka yi prescribing before the operation...." Junaid yace
"Amma ba yanxu aka sa xa ayi operation din ba Abba" Abba yace "Yess ba yanxu ba
amma lkcn xai xo in sha Allah" Ta gefen ido Shuraim ya kalli Junaid ya dauke kai,
Junaid yace "Toh Allah ya kai mu" Abba yace "Yanxu pharmacy din da xa a samu
maganin xaka duba, sai ka min texting din Price with ur details" Junaid ya d'an yi
murmushi ya mike yace "In sha Allah Abba, xan wuce sai anjima" Abba yace "Allah ya
kai mu..." Sallama yyi ma Shuraim sannan ya fita, Heedayah na kitchen tare da Mami
dake gaya ma maid din gidan what to cook for lunch, ko da wasa bata yrda ta bar
Heedayah tare da su Rabi'ah kawai ba, jin an bude kofar Abba ta fito daga kitchen
Junaid yace "Xan tafi Mami sai anjima" Heedayah dake makale da Mami jin muryarsa da
sauri tace "Mami xan bi sa plss" Junaid na kallonta yace "Baxa a je da ke ba" Ta
wani murguda baki tace "Kar aje din" Gyada kai yyi ya juya ya nufi kofa ya fita, a
hankali Heedayah tace "Mami wucewa yayi?" Mami tayi murmushi tace "Ehh" Heedayah ta
marairaice tace "Did he want to be wicked like that man" a kunnen Shuraim da ya
fito parlon Abbansa shi ma, Mami tace "Which Man?" Heedayah tace "Wnn da ya tafi da
ni a mota jiya mana, wannan da Abba yace ya min karatu ni ban san sunansa ba...
Kawai nasan shi mugu ne" A hankali Shuraim dake jin duk abinda take cewa ke tafiya
xuwa dakinsa, Mami tace "Toh kansa yyi ma mugunta ai ba ke ba" Heedayah tace "Aa ni
yake yi ma ba kanshi ba" Mami ta kama hannunta suka bar wajen. That same day da
yamma Mami na main parlor tana danna wayarta tare da Heedayah da su Rabi'ah da suka
dawo islamiyya aka bude kofar parlon, Mumy ce ta shigo da sallama sakale da handbag
dinta, Su Khadijah suka ta fi da gudu cike da murnan ganinta suka rungume ta, Mumy
ta shigo parlon tana murmushi tace ma Mami "Sannun ku da gida" At first Mami bata
yrda da ita take ba sai da ta kalleta ta ga ita take kallo, tace "Yauwa sannu da
xuwa" Mumy tace "Don Allah akwai dari biyar wajen ki xan ba d'an sahu wai ba shi da
canjin dubu daya" Mami tace "Ohk, Rabi'ah shiga bedroom gaba mirror akwai kudi ki
dauko" Rabi'ah ta tafi xuwa bangaren Mami, Mumy tace "Ban da ma yanxu yan sahun sun
xama abinda suka xama nan nan da Marafa wai dari biyar" Mami tace "Toh Allah ya
rufa asiri" Mumy ta tabe baki tace "Ameen dai" Rabi'ah ta fito ta mika ma Mumy dari
biyar din Mumy tace "Aa kai masa, ni bari in shiga ciki duk na gaji wllh" daga haka
ta wuce bangarenta Khadijah ta bi ta da sauri, Mami ta d'an yi wani boyayyen
murmushi tana ci gaba da danna wayarta. Junaid na tsaye babban pharmacy bayan ya
basu takardan maganin da yake nema, pharmacy uku yana xuwa sai su ce bbu eye drop
din, amma wnn na hudun ya ci sa'a an samu, wani mutumi ne tsaye gefensa cikin shiga
ta alfarma, ya siya magunguna shi ma ana masa packaging dinsu, da yake pharmacy din
yawanci duk manyan mutane ne ke xuwa, Daga gefen Mutumin kuma wata matashiyar mata
ce sanye da hijab har kasa warce baxata wuce 38 ba, Mutumin ya amshi maganin kenan
matar ta yanke jiki ta fadi nan kasa, wanda hakan ya jawo hankalin mutanen wajen,
Mutumin wanda da alamar mijinta ne ya durkusa da sauri ya rikota, Junaid ya duka
shi ma yana mata sannu cike da tausayin ta, ledan hannun Mutumin junaid ya amsa,
Mutumin ya daga ta suka fita pharmacy din mutane na mata sannu, Junaid ya bi
bayansu har xuwa gun wani lafiyayyen mota, sai bayan da Mutumin ya taimaka mata ta
shiga motar sannan junaid ya mika masa magungunan dake hannunsa yace "Allah ya
sauwake...." Mutumin yyi murmushi yace "Ameen mun gode, thank you very much" Junaid
ya mayar masa da murmushin yace "No thanks, amma da ku yi kokarin wucewa asibiti
daga nan she looks so sick" Mutumin yace "In sha Allah, nagode" Junaid yace "You
are wlcm sir" daga haka ya juya ya koma cikin pharmacy din don biyan kudin eye
drops da ya xo siya, waya ya gani kwance kasa daga inda matar ta fadi, ya duka ya
dau wayar ya sake fita da sauri amma har motar su ya bar haraban pharmacy din,
juyawa yyi ya koma ciki rike da wayar..... Sai da Magrib Junaid ya isa gidan Abba
da eye drops din Heedayah, Mumy dake xaune parlor ya gaisar da ladabi, ta amsa da
fara'a tace "Sannu da xuwa" Ya xauna nan parlon yace "Ya gida?" tace "Alhmdllh, Ya
sunan naka kuwa?" Ya kalleta yace "Junaid" tace "Maa sha Allah, ka shiga tana can
ciki, da kuwa a nan take xaune tace bari taje tayi sllh...." Junaid ya mike yace
"Toh..." Da sallama ya bude kofar parlon Mami, ya ga Heedayah kadai xaune tana cin
apples
da aka yanyanka mata a plate, dauke plate din yyi a hankali, bayan ta cinye na
hannunta xata dau wani ta ji wayam, ta gama lalube lalubenta amma bbu alamar plate,
a hankali ta dinga bin parlon da kallo kamar xata yi kuka tace "I know it's youuu"
ya ja hancinta ya ajiye mata plate din sannan ya xauna saman kujera, Mami ta fito
tace "Ka samo drops din?" Yace "Sure..." Wani sabon ringing ya ji a aljihunsa, lkci
daya ya tuna wayar mutanen daxu, ya ciro wayar sannan yyi picking call din ya kai
kunne tare da sallama, bayan sun gaisa normal Junaid Yace "Sorry daxu you lost ur
phone at the pharmacy, na fito kuma naga ka wuce, ina ta jiran kira tun safe ba a
kira ba" daga daya bangaren Mutumin yace "Yea ban lura bane da wuri wllh, thank you
very much, I almost gave up but nace nayi trying kawai sbda contacts dina" Junaid
yyi murmushi yace "Toh where shud we meet sai ka amshi wayar?" Mutumin yace "Yanxu
dai muna hospital da Madam, but Alhmdllh da sauki, and in sha Allah gobe da safe xa
mu koma Abuja, we resides there... so I don't know ko xaka fada min inda kke..."
junaid yace "Ayya, to I will try and bring the phone to you tomorrow in sha Allah"
Nan suka yi sallama Mutumin na kara masa godiya.... Heedayah tace "Toh me yasa ka
dauke min Apples dina?" Ya saci kallon Mami da ta juya ta koma ciki, sannan ya mike
ya koma inda take yace "Ban sani ba" tace "To kai ma ba ruwana da kai...."

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Junaid ya ja hancinta yace "Ni da wa?" Tace "Kai da wnn mana, ni ban san sunansa
ba, kai sai ka dinga tsokanata shi kuma sai ya dinga buge min hannu yana min fada"
fitowar Mami ya sa Junaid ya mike yace "Mami sai da safe, xan wuce" Mami tace "Ka
ci abinci ai?" Yace "Na ci" Mami tace "Toh Allah ya tashe mu lfya" kofa ya nufa,
Heedayah tace "Mami ina xa shi?" Mami tace "Xai wuce gida" Heedayah tace "Mami me
yasa baxai tsaya a nan da mu ba?" Mami tayi murmushi tace "Ai xai dawo" Heedayah
tace "Ni ina son ya tsaya a nan" Junaid ya kalleta daga bakin kofar da yake tsaye
ya bude kofar ya fita. Da asuba aka tashi da ruwa sosai, wajen shidda da rabi Mami
na parlonta aka kwankwasa kofa, mikewa tayi ta bude kofar Shuraim yyi kasa da kansa
yace "Ina kwana?" Tace "Lafiya lau" yace "Xa mu yi karatu ne" Juyawa Mami tayi ta
wuce daki, Heedayah na ta bacci tun bayan da ta tada ta yin sllh asuba, Mami ta
tada ta, ta sa mata Hijab sbda garin yyi sanyi sosai suka fito, har snn Shuraim na
tsaye bakin kofa, Mami ta mika masa ita, ya kama hannun suka fita parlon ya kulle
mata kofarta, Heedayah dai har snn idonta a lumshe yake tana bin sa, da sauri ta
bude idanuwanta jin ta ci karo da sofa a parlor, ko tsayawa Shuraim bai yi ba har
ya isa study area din Abba still holding her hand ya xaunar da ita nan kasa, kamr
xata yi kuka tace "Shine ka buge ni da kujera?" Strictly yace "Kin san Allah idan
kina min magana a gidan sai na fasa maki baki wataran, I have no business with you,
if u dare talk to me again I will injure you" Yana yin yanda yake maganan yasa
Heedayah tayi shiru bata dai ce komai ba, he was so serious, fuska daure yace "Sai
na ce ki fara karatun??" A hankali ta fara karato suran da take, yana ta danna
wayarsa har ta kai inda ta tsaya shekaranjiya, tace "Na gama....." Sai bayan kusan
minti biyar ya ajiye wayar hannunsa sannan ya daura daga inda ta tsaya, his
recitation was waow, kamar wani balarabe, Bai tsaya ba sai da ya sauke suran gaba
daya snn ya daga kai yana kallonta, baccinta take hankali kwance bayan ta jinginar
da kanta da arm chair dake wajen, ya dinga kallonta sannan ya kalli agogo dake nuna
karfe bakwai ya mike, parlor ya wuce ya ga Rabi'ah sanye da schl Uniform yace "Je
ki tada wnn yarinyar ki kai ta ciki" Bai jira cewarta ba ya wuce xuwa dakinsa. Abba
na kallon Mami yace "Listen Rahinah, I know u are not after the income or anything
of such, but...." Ta girgixa kai tace "But what Barrister? Ba mu yi da kai xan
ajiye aiki ba, ba mu yi haka da kai ba, I can't... Aikina ya xama jinin jikina,
it's part of me, I like my profession, ko ba komai I do help innocent soul that are
not quilty and I enjoy doing that, so why are you trying to deprive me of the joy?
Tunda har na iya kula da nawa yaran still ina aiki, har na aurar da daya, I can
take care of little Heedayah also with my work, just that before 3 xan dinga dawowa
gida...." Abba ya kasa cewa komai, can ya jinjina kai yace "Toh shkkn Rahinah baxan
takura ki ba, I agree ki ci gaba da aikin ki" Tana kallonsa tace "I appreciate,
Anjima matar da xata dinga kula da Heedayah when I am away xata iso, monthly xa a
dinga biyanta dubu ashirin, I will pay that...." Yace "No you don't need to...."
tace "A'a na sa a raina ni xan biya, I took that as my responsibility since I can
be with her fully...." Yace "Toh kin san matar da xa a kawon" Mami tace "Ehh to ban
santa ba garinsu daya da wata childhood frnd dita Shamsiyya, she said shesy good
kuma xata iya" Abba yace "Shhkn, Allah ya mana jagora" tace "Ameen Great Man" D'an
murmushi yyi yace "So ynxu dai tare za mu dinga fita da safe?" Dariya tayi tace
"Not at all, karfe goma ni xan dinga fita, sai nayi ma Heedayah duk abinda ya
kamata, ido kawai Mai aikin xata sa mata har in dawo" Abba yace "Alright" Karfe
goma saura matar da Mami ke jira ta iso gidan bayan an mata kwatance ta waya, Mami
ta fito main parlor, matar da baxata wuce talatin ba ta sauka har kasa ta gaisheta,
Mami tace "Sannu da xuwa ya hanya" Matar tace "Alhmdllh Hajiya" Mami tace "Ya sunan
ki?" Matar tace "Sunana Karime" Mami tace "Toh karime aikin ki ba wani da yawa
bane, amma yana bukatar saka ido da kula..." Karime tace "Duk an koro min Hajiya,
Kuma in sha Allahu xan iya, har ma da aikin gida idan da akwai duk xan yi babu
damuwa...." Mami tace "Toh Alhmdllh, yanxu dai mu je in nuna maki inda xa ki ajiye
kayan ki" Karime ta mike da sauri ta dau Ghana must go dinta ta bi bayan Mami,
Dakin masu aiki Mami ta kai ta, Mai aikin Mumy dake xaune dakin ta gaida Mami, Mami
ta amsa sannan ta sa karime ta ajiye kayanta suka fita, Mami ta kai karime parlonta
tace "Nan ne bangarena, bana son ku wuce nan ke da ita, in dai tana bukatan wani
abu na ci ki bar ta ita kadai ki tafi kitchen ki nema mata, xan nuna maki kitchen
din da Inda komai ke ajiye.... Tsakanin ki da Allah nake son ki kulan min da
yarinyata bbu ha'inci" Karime tace "Kai Hajiya ai d'a na kowa ne, xaki sameni me
riketa da gaskiya in sha Allahu...." Mami tace "To maa sha Allah.... Ki tafi can
dakin naku, warce kika samu a ciki daxu ta nuna maki inda xaki ajiye kayan ki
sannan ki dawo...." Karime ta mike ta nufi kofa tace "Toh Hajiya" Mami ta xauna
saman kujera don tayi deciding yau baxata fita ba xata yi monitoring yanda Karime
xata kula da Heedayah. Junaid ya mike daga xaunen da yake yace "To Mami ai ni baxan
san size din sweater da xan siyo mata ba, Kuma wani irin takalmi kenan?" Mami tace
"To kai makaho ne? Look at her mana before going..." Ya dai yi shiru bai ce komai
ba, can ya nufi kofa murya can kasa yace "Sai na dawo...." har xai fita tace "Then
go with her kar kaje ka siyo wanda baxai yi mata ba har takalman ma a gwada mata,
ka siyo ma Farida ma takalma biyu with a sweater" ya juyo yace "Toh" Mami ta kalli
Karime dake xaune kasa tace "Ki duba daki ki dauko Hijab dinta da takalmi xa su
fita, ai na nuna maki inda suke" Karime tace "Toh Hajiya" Da sauri ta shige dakin
Mami, Heedayah dake xaune gefen Mami ta washe fararen hakoranta jin xa a fita da
ita, Mami na lura da ita ta girgixa kai ta d'an yi murmushi, Shi kansa Junaid
kallonta yake, Karime ta fito da sauri ta sa ma Heedayah hijab dinta da takalmi,
Mami ta mike xata shiga daki don dauko turare ta sa mata, Karime ta dauke cup din
da Heedayah ta sha cornflakes ta fita xata kai kitchen din da Mami ta nuna mata, a
parlor ta tadda Mumy xaune tana kallon tv duk da gaba daya bata ma san abinda ake a
tvn ba, Kwarjinin Mumy kadai ya isa a gane ita ma matar gidan ce, Karime ta d'an
duka tace "Sannu da hutawa Hajiya" Mumy na kallonta a dakile tace "Yauwa.... Ke ce
sabuwar mai aikin da ta xo yau?" Karime tace "Ehh ni ce" Mumy ta d'an saki fuska
tace "Sannu da xuwa, daga wani garin kika xo?" Tace "Daga kano na xo Hajiya, a can
mariri iyayena suke" Mumy tace "Maa sha Allah, ai ko nasan Mariri..." Karime tace
"Allah sarki" Mumy tace "Toh kin ci abinci kuwa" Karime tace "Na ci wllh Hajiya"
Mumy tace "Toh ki saki jikinki kin ji, ko me kike bukata ki xo ki sameni...."
Karime ta kara dukawa har kasa tace "In sha Allahu Hajiya, Nagode Sosai sosai,
Allah ya kara girma" Mumy na murmushi tace "Ameeen" Karime ta mike ta wuce kitchen,
Mumy ta bi ta da kallo..... Ba a dau lkci ba sai ga Junaid ya fito rike da
Heedayah, Junaid ya gaida Mumy, da fara'a sosai ta amsa tace "Sannu Junaid, xa ku
fita ne" yace "Ehh xa mu je mu dawo" Mumy tace "Ke 'yar fara ba gaisuwa?" Heedayah
dai tayi shiru, Junaid ya duka dai dai fuskarta yace "Can't you greet?" A hankali
tace "ina kwana" Mumy tayi dariya tace "Ina wuni dai xa ki ce baby" Heedayah tace
"Ina yini" Mumy tace "Lafiya lau, xo in gyara maki Hijabin" Junaid na rike da
Heedayah ya kai ta har gaban Mumy, Mumy ta gyara mata Hijab din tana kara goge mata
bakinta tace "Me kika ci haka?" A hankali Heedayah tace "Cornflakes Mami ta bani"
Mumy tace "Ahh Lallai ga alama, to sai kun dawo" Junaid yace "In sha Allah" yana
rike da hannun Heedayah suka nufi kofa, Mumy ta bi su da kallo har suka fita parlon
sannan ta sauke ajiyar xuciya tana jijjiga kafa. Anguwa ce ta manyan mutane da suka
yi fice aka kuma san da su a kasa Junaid ya shiga, a hankali yake driving, Lkci
lkci yake kallon Heedayah dake gefensa xaune ta jinginar da kanta da glass din
motar idonta a waje kamar dai me gani, Junaid yace "Tell me what you are
seeing...." ta juyo xuwa Inda take jiyo muryarsa a hankali tace "Darkness" shiru
Junaid yyi driving slowly, can ya kamo hannunta daya murya can kasa yace "What
color?" Ta wara ido tace "Just dark" Bai kuma cewa komai ba yyi parking dai dai
wani gida da yake tunanin gidan da yake nema ne sbda number da ya gani daga gefen
gate din gidan, dialing din number dake call logs dinsa yyi ba a dau lkci ba aka
daga, yace "Gani a kofar gidan if I'm not mistaken" ajiye wayar yyi bayan an sanar
masa ana xuwa, Heedayah tace "Ina muka xo?" Yace "Somewhere" tayi shiru kmr me son
gane ma'anar somewhere da yace, can tace "Ohk wani waje?" Murmushi yyi yace "Yes"
Bude gate da aka yi yasa ya kalli gate din ta cikin tinted glass dinsa, Mutumin
jiya ne ya fito gate din, Junaid ya bude motarsa yana kallon Heedayah yace "Ki
jirani in dawo yanxu" Ta 6ata fuska tace "Noo plss go with mee" yace "Yanxu xan
dawo am not going anywhere" Ganin kiris ya rage ta fara kuka ya dau wayarsa yace
"To rike min..." daga haka ya fita daga motar ya kulle ya nufi gun Mutumin dake
tsaye, gaisawa suka yi, Mutumin yace "Fatan dai ban mu yi inconveniencing dinka ba,
mu ma anyi delaying flight dinmu ne" Junaid na mika masa wayarsa yace "No, not at
all..." Mutumin ya amsa yace "I am very grateful, ni Sunana Ahmad" Junaid yace "I
am Junaid" Alhaji Ahmad yace "Nagode kwarai Junaid" Junaid yyi murmushi yace "Babu
damuwa, ni xan koma" Alhaji Ahmad yace "Toh Allah ya kiyaye, da numberka ka kirani
ai..." Junaid yace "Ehh" Alhaji Ahmad yace "To maa sha Allah I will save it" daga
haka Junaid ya koma motarsa ya tada, Alhaji Ahmad dai na tsaye har yyi reverse ya
wuce..... Karfe shidda saura Junaid ya
koma gida tare da Heedayah bayan ya siya masu rigunan sanyi da takalma ita da
Farida, Mami ta dauko eye drop da ya siyo jiya bayan ta kai kayan daki tace
"Barrister yace idan ka xo sai ka gaya min yanda xa ayi da wnn" Junaid ya amshi
ledan maganin ya fiddo su guda biyu yace "Wannan idan xata yi bacci da daddare xa a
sa mata just two drop in each of her eye, shi kuma wnn idan ta tashi da safe, it's
should be everyday ba a skipping....." Mami tace "Toh shkkn Allah ya sa a dace, su
kuma maganin mene?" Yace "Toh ana sa rai with the help of this idan an xo yin
operation din idon baxa a samu matsala ba idan Allah ya yrda...." Mami tace "Toh
Allah ya sa" Mami tace "Babu wani wanda xata dinga sha?" Yace "A'a, sai dai in
bincika" tace "Toh Shkkn...." Mikewa yyi yace "Ni xan koma Mami" tace "Baxa ka jira
ka ci abinci ba?" Yace "Aa xan wuce" tace "Toh sai gobe" Khadijah ce ta shigo
parlon Mami da sallama hannunta daya rike da plate me dauke da cake da aka yanka
gida biyu yan madaidaita, daya hannunta kuma da wani cake din tana ci, ta karaso
gun Heedayah dake xaune tace "Mumy tace ki dauki naki" Mami ta kalli Karime dake
rakube waje daya tace "Ki amsa ki ajiye mata" Karime ta taso da sauri ta karba,
Khadijah na kallon karime tace "Dayan aka ce ke ma ki dauka" Karime ta kalli Mami,
Mami tace "Toh an gode" Khadijah tace "Cousin dinmu ne yyi birthday" Mami tace
"Allah ya raya sa" Khadijah ta juya ta bi ta gefen Junaid ta fita, Mami na kallon
Heedayah tace "Xa ki ci cake?" Heedayah ta gyada mata kai, Mami tace "Toh bata
Karime ke ma ki dau naki" Karime ta mika ma Heedayah daya ita ma ta dau daya ta
fara ci, Heedayah na kallon Inda take jin muryar Mami tace "Mami in tsan masa?"
Mami ta kalli Junaid dake tsaye bakin kofa har sannan tayi murmushi tace "Cinye
kayan ki ya wuce" Juyawa Junaid yyi ya fita dakin, Heedayah ta fara cin cake dinta,
dai dai bakin kofar shigowa yau yyi karo da Salima, tana rike da gyalenta da jaka a
hannu, suna hada ido ya bata hanya.... Cikin wani siririn murya tace "Noo ka wuce
mana ai kai ka bude kofar...." Ya kara kallonta sannan ya bi gefenta yace "Thank
you" tace "Haba thank you kuma, ai kai ka bude kofa" shi dai bai tsaya ba kuma bai
ce komai ba yyi wucewarsa, ta bi sa da kallo ko kiftawa bbu... Karime ce kitchen
bayan Magrib tana dafawa Heedayah Indomie, tana xuba Indomie din cikin ruwan dake
tafasa kan gas aka bude kitchen din Mumy ta shigo, ganinta tace "Aiki kike yi
Karime?" Karime tace "Ehh Hajiya Indomie nake dafa mata" Mumy tace "To ke kin ma ci
abinci kuwa" tace "Ehh dama na rana bai kare ba...." Mumy tace "Na rana kuma, kin
ga idan kin kai masu Indomien ki xo ga cous cous a kula ki diba ki ci kin ji,
abincin rana ai ya huce yanxu" Karime tace "Toh Hajiya Nagode Sosai" Mumy tace
"Amma fa kar ki wani ce ma uwar dakin ki nace ki xo ki amshi abinci ke dai kawai ki
shigo kitchen ki diba kije can dakin ku ki ci" Karime ta risina tace "Toh Hajiya"
Mumy ta ajiye cup din hannunta ta fita kitchen din.....

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Washegari karfe goma saura na safe Mumy ta gama shiryawa xata fita office, Tana
duban Karime a parlonta tace "Toh ni xan wuce aiki yanxu, sai ki saka ido sosai ki
kula da duk abinda nace maki, karfe sha biyu na yi ki daura maku girkin abinda xa
ku ci dai dai cikin ku, ita kuma Heedayah xuwa nan da sha daya abinda ki ka ga na
hada mata jiya sai ki hada mata ki xuba Madara amma ban da sugar" Karime tace "Toh
in sha Allahu Hajiya" Mami ta dau jakarta ta nufi kofa tace "Sai na dawo" Karime
tace "A dawo lafiya" Har Mami ta fita ta juyo tace "Kar ki bari ta bar parlon nan
komai xakiyi kiyi mata a nan parlon, bana son ku fito" Karime tace "Toh in sha
Allahu Hajiya" Mami ta kulle kofarta ta wuce, A main parlor suka hadu da Mumy tana
ma mai aikinta magana cikin tsawa, matar da baxata wuce Karime ba sai rawa jikinta
yake tana bata hakuri, Mumy na ganin Mami ta dakata da masifar da take, idon da
suka hada yasa Mami tace "Mun tashi lfya?" Mumy tayi murmushi tace "Lafiya lau
wllh, ya kwanan Baby" Mami tace "Alhmdllh, ya na su Rabi'ah" Mumy tace "Lfya lau,
sun ma wuce makaranta ai" Mami tace "Toh maa sha Allah, na fita..." Mumy tace "Toh
Allah ya kiyaye hanya" Mami ta amsa da Ameen sannan ta fita parlon, Mumy ta bi ta
da kallo har ta rufe kofa, ta wani ta6e baki ta kalli Sajida mai aikinta cike da
masifa tace "Kin tashi a gabana ko sai na gaura maki Mari, 'yan aiki ko 'yan
wahala, wllh bana son in sake tuna maki sharan dakin yarana idan ba haka ba ni ynda
ake canxa sutura haka nake canxa ku don ma ki ji" Mai aikin ta mike da sauri ta
tafi dakinsu Rabi'ah, Shuraim dake xaune dining ya ajiye cup din hannunsa ya mike
ya dawo parlon, Mumy tace "Amma dai yau baxa ka fita aiki ba...." Yace "Sai da
yamma...." Mumy tace "Na ji ma Baffan naku yyi tafiya ko?" Shuraim yace "Ehh yana
Abuja" Mumy ta ta6e baki, Shuraim yyi kasa da kai yace "Mumy ki dinga hakuri da
mutane don Allah, barin wa ennan bayin Allah, they don't deserve the way u are
treating them, they never wished for their selves to be maid, and don't forget no
condition is permanent, su Rabi'ah yara ne da baxa su iya gyara dakinsu ba idan sun
tashi? Ba fa aikin da suke yi a gidan just gyaran dakin ma sai an masu?? This
is...." Dakatar da shi tayi cikin tsawa tace "Rufe min baki malam, ni xaka taso
kayi ma fada?" Yace "Ni ba fada na maki ba, I am telling you what I think is right"
Ta kuma yi masa wani tsawan tace "Baka isa ka gaya min what to do and what not to
do ba, out of my sight now.... Duk walakanci da cin fuskan da ubanka ke min a gidan
nan ka ta6a tunkararsa ka gaya masa what is right? Sai ni marainiyar wayon ka, to
baka isa ba ne...." Shuraim ya shafa kansa bai dai ce komai ba yyi wucewarsa
dakinsa, ta bi sa da wani irin harara tace "Wawa kawai...." Karfe sha daya da
rabi Karime ta fito hada ma Heedayah cornflakes, Mumy ce xaune parlor da Hajiya
Sadiya, Karime ta duka har kasa ta gaisheta, da fara'a Mumy tace "Lafiya lau
Karima, ya aiki" Karime tace "Mun gode Allah" Mumy tace "Toh madalla" Karime ta
gaida Hajiya Sadiya ita ma ta amsa sannan ta mike ta wuce kitchen, Hajiya Sadiya na
kallon Mumy murya can kasa tace "Ita ce mai aikin" Mumy ta gyada mata kai, Hajiya
Sadiya ta jinjina kai alamar gamsuwa, can sai ga Karime ta fito rike da cornflakes
da ta hada, Mumy tace "Ga kwai can da na soya a kitchen ki dauka, na ci ya isheni
gashi ba almajirai a nan" Karime tace "Toh Hajiya Nagode" xata koma kitchen din
Mumy tace "Toh ajiye kofin cornflakes din kar ya xube, ta ajiye ta wuce kitchen din
da sauri da sauri, Mumy ta kalli Hajiya Sadiya dake mata magana cikin rada, Mumy ta
gyada mata kai kawai, Karime ta fito dauke da tulin kwai a plate, Mumy tace "Ki
fito da ita mana ta sha cornflakes din a nan, gashi nn ma duk ya jike...." Karime
ta d'an fara kame kame, tace "Hajiya dama Madam tace kar take fitowa ne, komai xa
mu yi muyi a can ciki" Mumy dake saurarenta sosai tace "Ayyo, toh tunda ita ta kawo
ki ba ni ba shkkn kai mata ciki, dama so nayi in d'an sa ki gyaran bangarena ne,
shi sa nace ki fito da ita nan sbda a sa mata ido, amma dauka ki wuce xan yi da kai
na, na aiki tawa mai aikin kasuwa ne dama shi yasa" Karime ta d'an risina tace "A'a
ba haka bane Hajiya kiyi hakuri, d'an dai gyaran bangaren ki ai xan maki, bari in
kawo ta nan din" Mumy tace "Aa kar uwar dakin ki ta ga kin karya mata doka kiyi
laifi...." Karime tace "A'a da wuri ae xan yi in gama" daga hka ta wuce ciki, sai
ga ta ta fito da Heedayah dake sanye da wando iya gwiwa da karamin riga an daure
mata kalabanta waje daya, she look more of a half cast sbda irin haskenta, dai dai
fitowar Shuraim waya kare kunnensa da ganinsa kasan fita xai yi, Karime ta ajiye ta
nan gefen Mumy ta dauko cornflakes din ta sa mata a hannu tace "Toh gashi ki sha
masaran naki 'yar kyakkyawa" Shuraim dai sai kallonsu yake walking slowly, Heedayah
ta laluba cokalin ta deba content din cup din ta kai baki, girgixa kai tayi ta fito
da na bakinta saman tafin hannunta da sauri tana yamutsa karamin bakinta tace "Yyi
soakkk....." Mumy ta saci kallon Hajiya Sadiya ta dalilin hakan kuma ta hango
Shuraim da ya tsaya don bata san ya fito ba duk da kamshin turaren sa da ya gauraye
parlon, Karime na kallon Heedayah tace "Kika ce?" Heedayah na kara tofar da sauran
na bakinta tace "Xai sa in yi amai, it's soft" Mumy tayi murmushi tace "Kai yaro ma
dai, wai tana nufin ya jike, ki hado mata wani kawai" Karime tace "Au... toh..."
Sannan ta dau cup din ta wuce kitchen da sauri, ba a wani dau lkci ba ta dawo da
wani Cornflakes din a cup ta mika ma Heedayah, sannan ta kama hannunta ta juye na
bakin ta da ke kai kan nata hannun, Heedayah ta fara shan cornflakes din, Karime ta
tafi kitchen ta xubar da na hannunta ta dawo tana kallon Mumy da ladabi tace "Ina
xa a gyara maki?" Mumy tace "Ki tafi sama xaki ga kofofi duk ki shiga ko wanne ki
share ki goge" Karime ta risina tace "Toh Hajiya" daga haka ta wuce sama, Shuraim
ya karasa dinning ya xauna, Mumy ta d'an kalli Inda yake, sai kuma ta juya tana
kallonsa da kyau tace "Ba fita xaka yi ba?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Ehh ina
jiran Umar ne..." Mumy tace "Toh ba sai kaje can gidan nasu ka samesa ba" Shuraim
yace "Yace in jirasa a nan...." Mumy tace "Toh ma yaushe ku ka fara fita da Umar?"
Shi dai Shuraim bai ce komai ba, Mumy ta kalli Hajiya Sadiya tayi tagumi, Hajiya
Sadiya tace "Ni da ka d'an taimaka Shuraim ka amso min MTN nan waje naga da wani me
kiosk a layin..." Ya kalleta sannan yace "Toh bari in maki transfer kawai...."
Hajiya Sadiya tace "Aa kar ka wani ba kanka wahala, ga kudin ka amso min" Yace
"Gashi ina yi, na ma yi ynxu" Hajiya Sadiya bata sake ce masa komai ba, Mumy dai ya
girgixa kafa take, Tasss Heedayah ta shanye cornflakes din cup din tace "I want to
take water" Mumy ta d'an kalleta tace "Sai jira ta xo ta baki ai" Shuraim dai yana
ta danna wayarsa, har Karime ta fito bayan kusan minti talatin, tace "Hajiya duk na
gyara na goge" Ba tare da Mumy ta kalleta ba tace "Sannu" Karime ta daga Heedayah
tace "Mu je ki kwanta lkcn baccin ki yyi" Heedayah tace "Xan sha ruwa" Karime ta ja
ta har xuwa gun da fridge din dinning area yake, Heedayah ta taji ta taka abu me
tudu, tsayawa tayi ta kara kai kafarta kan abun, Shuraim ya dauke idonsa daga kan
screen din wayarsa yana kallonta, ta kara takasa, ta kuma takasa just wanting to
know what she's matching, ta kara cire kafarta ta kara mayarwa, Karime dai na
kokarin dauko mata ruwa a fridge bata ma san me ake ba, Heedayah ta duka ta sa
hannu tana lalubawa ta ji me take takawa, dagota yyi ya rike duk hannunta biyu ya
bugesu da karfi, sannan ya ja kunnenta daya fuska daure yace "Dutse aka ce maki
kike takawa??" Kara buge hannunta yyi ya ja kunnenta ta fashe da kuka sosai, Karime
dai ta ja gefe bata ce komai ba, cikin kuka Heedayah tace "Sai na gaya ka da Mami,
ni ba Ina ce baby na taka ba" Ya buge bakinta ya tura ta can kusa da Karime, duk
wnn abun Mumy na kallonsu amma bata ce komai ba, Karime ta kama hannun Heedayah
bayan ta dau ruwan tace "Kayi hakuri Yallabai, bata sani bane" Ya hade rai yace "Ku
fita gabana ke da ita" Karime ta bar wajen da sauri tana rike da hannun Heedayah
dake rusa kuka, Sai da ta xo wuce Inda Mumy take, Mumy tace "Sai hakuri, ita tsiwa
shi kuma saurin hannu, haka nan dai" Karime ta wuce part din Mami rike da Heedayah
dake Shessheka, Sai da suka shiga ciki Mumy tace "Ai kaga irinta, ba dai ana ganin
ni bala'e'iya bace, to gashi tun ba a je ko ina ba bakin yarinya ya fara budewa
tana ma mutane fitsara, ai kadan kayi mata na so ka yi mugun xaneta ne, rashin idon
ya ci uwarsa, wllh idan yarinyar nan ta samu waje duk taka ku xata yi a gidan nan,
kuma ubanku baxai ce komai ba tunda idonsa ya rufe.... Kai kuma ka xo ka xauna ma
mutane a parlor ka hanasu sakata da can kana xaman parlon nan ne ko neman
magana???" Shi dai bai ce mata komai ba, can ya mike ya nufi kofa yace "Sai an
dawo" daga haka ya fita parlon, Hajiya Sadiya tace "Ai kuma ya lalata mana shirin
yau sai mu tari gaba...." Mumy da ranta ya kara baci tace "Ni fa da ba don idon da
kika dinga min ba gabansa ma xan iya duk abinda xan yi, to tsoronsa nake ji ko
ubansa xai min?? Wllh ke ce kika hanani" Sadiya tace "A'a ke dai, ai komai yana son
sirri a rayuwa, ni sai naga kamar da wata manufa ya xauna parlon har ya ki fita
siyo min kati, ni kinga ko godiyar katin ban masa ba ma, ke dai kawai ki sa ma
ranki salama ba dai duk ana tare a gidan ba, kuma da alaman jawo hankalin yar
kauyen nan ba abu bne me wuya, da ganinta xata so abun duniya ne sosaiiii, bbu abun
hanxari a wannan lamarin mu bi komai a sannu...." Mumy tace "To ko da wata manufan
ya xauna akwai yanda xai yi da ni ne balle ma bbu wata manufa kawai coincidence ne,
ke baki ga irin jibgar da yyi mata ba ynxu bbu ko shakka bbu, da kyar idan
hannuwanta basu tashi ba, ai ko kadan bai bada goyon bayan kawota da ubansa yyi ba,
kawai dai kin san sa da xurfin ciki ne, Amma har ynxu ina lura ba wani shiri suke
yi da uban ba duk kan wnn
case din...." Hajiya Sadiya tace "To ke dai kiyi ga kyautata ma wnn yar kauyen,
step by step xa mu yi ta abun mu bbu wanda xai xarge mu ko da kuwa alkali ne shi ba
lauya ba, lkci daya farat din da kika so ayi da farko shi xai ja a xarge mu, amma
kinga wnn bbu wanda xai kawo mu a rai" Mumy tace "Haka ne kam" Hajiya Sadiya ta
mike tace "Yanxu dai xan wuce, gobe in sha Allahu xan xo da karfe sha daya" Mumy
tace "Toh Allah ya kai mu din, ina nan ina jiran ki" Har bakin gate Mumy ta rakata
sannan ta dawo tana jin ranta fari fat.... Karfe uku da 'yan mintuna Mami ta dawo
gidan, Bbu kowa parlor ta shiga part dinta, Karime na xaune saman kujera tana ta
kallon tashar Hausa ga dambun nama cikin leda a hannunta tana ci cike da jin ddi,
Heedayah kuma na rakube kasa a xaune ta kwantar da kanta saman kujera, Karime ta
mike da sauri ganin Mami tana mata sannu da xuwa ta amshi ledan hannunta da handbag
dinta, duk idon Mami na kan Heedayah da ta mike da sauri jin shigowar Mami, Mami
tace "Karime ya xa ki bar ta ita kadai xaune a kasa??" Cikin rawar Karime tace "Aa,
sauka tayi Hajiya ai tare muke, naga kamar ta fi son kasan ne" Mami tace "Meye wnn
a hannunki??" Karime ta hadiye abu da kyar tana kara tuna warning din Mumy tace "Aa
ba wani abu bane, dama naje wanke filet ne sai na hadu da Sajida Hajiyar da take ma
aiki ta bata dambun nama shine ta debar min a leda, har nace ta bari amma ta
tilasta ni na amsa, shine na shigo na tsam ma Hinda sai na ke cin sauran yanxu"
Mami tace "Bbu wani alaka tsakanin ki da kowa na gidan nan banda gaisuwa, kin ji me
nace?" Karime tace "In sha Allahu Hajiya, dama ni ba ruwana da kowa tun safe muke
nan xaune, to naje wanke wanke shine...." Mami bata tsaya kara saurarenta ba ta
kama hannun Heedayah suka wuce ciki, Karime gabanta sai faduwa yake, ta isa a
hankali jikin kofar dakin ta makale don jin me Mami xata ce mata..... Har dai ta
gama labenta bata ji komai ba, ta koma ta xauna, nan ko tsoro ne ya kara shiganta
da ta tuna Mami fa na iya Kiran Sajida kila ta tambayeta, nan ko ko maganan kirki
bai hada su da Sajida ba tun jiya da ta xo, Mami ta gama sauya kayanta ta xauna
gefen gado tana kallon Heedayah da tayi shiru tace "Me ya same ki daughter?" A
hankali Heedayah tace "Mami wnn Mutumin ya dokeni a hannuna kuma ya ja min
kunne...." Hawaye ta fara tana Shessheka, Da mamaki Mami tace "A ina ya gan ki?"
Cikin kuka sosai tace "Xan sha ruwa, shine ya ja min kunne na, yanxu kuma hannuna
na min ciwo" Mami ta daga hannunta tana kallo snn ta fita dakin xuwa parlor, da
sauri Karime ta mike tace "Hajiya a debo abinci ne?" Mami tace "Me ya fitar da
Heedayah daga bangaren nan?" Karime da cikinta ya hautsine tace "A'a Hajiya bata
fita ba, da yake in taji alamar xan fita yin wani abu sai tace sai ta bi ni baxata
tsaya ita daya ba, ni kuma tausayi take bani sai in kasa fita in bar ta, wllh a
tare nake yin komai da ita ki kirata ki tambayeta, wllh Hajiya...."

Heedayah isn't free, don't read for free and burden ur self....

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....


Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Mami tace "A kan wani dalili kuma aka doki hannunta kina wajen?" Karime dake xufa
daga ciki tace "Cewa tayi xata sha ruwa muka tafi can inda firiji yake a parlor, to
cikin rashin sani ta taka wani bawan Allah dake xaune wajen Ina tunanin shi ma d'an
gidan ne, shine shi kuma rashin hakuri ya buge mata hannun ya xata da gangan tayi
hakan kila" On a serious note Mami tace "Ki saurareni da kyau ki ji, ko da wasa
bana son Heedayah ta sake fita parlon nan bana nan, ba komai yasa na dauke ki aiki
ba sae don ki kula da ita don ni bbu abinda ya gagareni na aikin gida, shima daukan
ki da nayi don bana xaman gida ne, Banda haka ni baxan dauke ki ba...." Hakuri
Karime ta dinga ba Mami tana duke a kasa, Mami tace "Gargadi na karshe nake kara
maki, ko nan da kofa kar ki sake fitar min da yarinya, idan kuma kinga baxa ki iya
aikin ba ki sanar min tun wuri in san abun yi....." Mami bata kuma saurarenta ba ta
wuce daki, Karime ta sauke ajiyar xuciya ta xauna nan kasa a hankali har sannan
gabanta na faduwa, a wannan marran wa xai daukeka aiki ya biya ka dubu ashirin,
aikin ma raino kawai, sai dai can cikin garin Abuja kila, tunanin hakan yasa tayi
tagumi tana tunanin ynda xata kara rike aikinta hannu bibbiyu... Mumy na kitchen da
Sajida wajajen biyar da wani abu kasancewar ranan ta amshi girki tun xuwan Mami
gidan, masifarta da ihu da take ma mai aikin har parlor, kmr jiran mistake take ta
fara fada ba ji ba gani, bude kofar kitchen din aka yi ta juya tana kallon kofar
fuska daure, Sudais ne tsaye sanye cikin kananun kaya hannunsa rike da leda sai
makullin mota, ta saki fuska tace "A'a... kai kuma daga ina haka...." Yana
murmurshi yace "Daga gida, Ina yini Mumy?" Tace "Lfya lau, ya su Hajiyar ka?" Yace
"Suna gaishe ku" ta rike ha6a tace "Yaushe rabon ka xo gidan nan Sudais, anyaa...."
Ya shafa gashin kansa still smiling yace "Mumy ae sbda aiki ne, ina su Rabi'ah?"
Tace "Basu dawo islamiyya ba, nasan ynxu ma suna hanya..." Yace "Ohk..." Daga haka
ya juya ya bar bakin kofar kitchen din, har xai xauna parlor sae kuma ya nufi part
din da Kaka tace masa nan ne wajen Mami, Mumy ta ajiye wuka da albasan hannunta ta
bi sa da kallo cike da mamaki har ya isa bakin kofar Mami ya kwankwasa a hankali,
ba a dau lkci ba Karime ta bude kofar, da farko ca take Shuraim ne sbda resemblance
din su, ta gaishesa da ladabi ta basa hanya, ya shiga parlon dake ta kamshi ta
kulle kofar, Mumy dake ta lekowa har taga shigansa ta kai hannu ha6anta idonta ya
kankance, sai kuma ta ajiye wuka da albasan hannunta ta fice kitchen din xuwa
bangaren ta.... Sudais na kallon Karime da ta koma gefen da take xaune ta xauna
yace "Babu kowa ne?" Tace "Aa suna ciki" daga haka ta mike ta nufi kofar dakin ta
kwankwasa a hankali a d'an tsorace, Mami ta bude kofar tace "Ya aka yi?" Ta
sunkuyar da kanta yace "A'a dama bako ki ka yi" Mami ta kalli parlon suka yi ido
hudu da Sudais karasowa cikin parlon tayi ya gaisheta da ladabi, ta amsa da fara'a
tana masa sannu da xuwa tace "Ya su Kaka da mutan gidan?" Yace "Suna gaishe ku"
tace "Maa sha Allah muna amsawa, welcome" Mami tasa Karime ta kawo masa ruwa da
drink a fridge, ta xauna kan kujera tana kallon film da ake a tv, Bayan few seconds
tace "Kai ne kayi karatu Malaysia koh?" Yace "Eh Degree" tace "Maa sha Allah,
Barrister yace min chemical engineering kayi right?" Yace "Ehh haka ne..." Tace
"Good, it's a nice course" yana shafa kansa a hankali yace "Heedayah bacci take?"
Mami tace "A'a tana ciki" yace "Dama kaka ta bada sako a kawo mata ne" Mami ta mike
tace "Allah sarki, tana ciki, let me get her" daga haka ta wuce dakin sai gata ta
fito da Heedayah, har gabansa ta kai ta sannan ta dau wayarta da ke ring kan kujera
tace "Give me few mins let me pick a call" yace "Alright Ma" daga haka ta wuce
daki, Heedayah ta wara idanuwanta jin muryar sa tana tattaba Hannunsa cikin
siririyar muryarta tace "Ka xo gidan mu yau koh?" Ya dafa forehead dinta yace "Nima
ai gidan mu ne...." Ta kyalkyale da dariya tace "Aa, gidanku ai gidan wnn matar nan
ne me fada" Sudais ya ja hancinta yace "Sunanta kaka, idan ta ji ki xata xane ki ba
ruwana" Ta wara ido tace "Toh kaka..." Ya dau apple daya cikin apples din da ya
kawo mata ya sa a hannunta, tana jujjuya apple din tace "Is it an Apple?" Yace
"Yes" ta langwabar da kai tace "Me ya sa baka kawo min Chocolate ba, ni ina son
shi" Yace "Wnn ya fi Chocolate dadi ai" yana fadin haka ya xaunar da ita gefensa ya
ciro cincin kulle a leda ya bata a dayan hannunta yace "Kaka tace a kawo maki" Tana
juya ledan tace "Meye shi?" Yace "Cinye apple din sae ki ci ki gani" Mami ta fito
daga daki ta dawo parlon ta xauna, Mami na kallonsa tace "Ka fara aiki ne?" Yace
"Na ci gaba da masters ne..." Mami tace "Maa sha Allah, a ina kake yi?" Yace "UK,
na dawo yin wani abun ne yanxu" Mami tace "Anytime soon xaka koma kenan?" Yace "Ehh
in sha Allah, nan da sati biyu" Mami ta gyada kai convinced, can tace "Shi kuma
Shuraim fa?" Yar dariya yyi yace "Shi yana aiki... clinic din Baffanmu yake" Mami
tace "Alright, Duk Allah ya bada sa'a" Yace "Ameen" Heedayah ta kamo hannunsa cike
da damuwa tace "Are you travelling?" Yace "Yesss" ta 6ata fuska a hankali tace
"Xaka tafi ka bar ni kenan?" Yace "Aa... Ai ba ddewa xan yi ba Heedayah" Mami tayi
murmushi tace "Sai ya tafi da ke kawai Koh?" ta xaro ido tace "Ehh Mami plss, I
like him with Yaya, ki ce ya tafi da ni" Mami tace "To xa ki bi sa" Daga karshe
Mami ta bar masu parlon ta koma daki to answer more calls, Heedayah tace "Baka gaya
min sunan ka ba....." Ya shafa kansa yace "Ki ce min yayanki...." Ta kai hannunta
chest dinta tace "Yayana?" Yace "Yess... Cutie" Apple dinta ta fara ci cike da jin
dadi, jin an fara kiraye kirayen Magrib yace "Xan je Masallaci in dawo" tace "Toh
plss ka dawo fa" yace "Xan dawo" Sudais na fita... Sajida mai aikin Mumy tayi
knocking, Mami ta fito parlor lkcn, Karime ta bude kofar ganin Sajida sai da
gabanta ya fadi, Sajida tace "Ina Hajiya?" Karime ta matsa bakin kofar tace "Ga ta
ciki...." Sajida ta shiga ta gaida Mami da ladabi ta ajiye warmers din hannunta
tace "Gashi Hajiya tace a kawo maki" Mami tace "Ohk, to an gode" Sajida ta mike ta
fita, murmushi kawai Mami tayi tana ci gaba da danna wayarta, don kowa girkinsa
yake a gidan ba hadawa aka yi ba.... Tare Sudais ya shigo da Shuraim daga
masallaci, Mumy dake xaune parlor ta hade rai ganin Sudais, Shuraim ya gaisheta snn
ya wuce dakinsa, Sudais yace "Mumy xan xo in wuce yanxu, xan masu sallama can ciki"
Mumy ta amsa masa ciki ciki, ya wuce part din Mami ya sanar mata xai wuce, Heedayah
na bedroom lkcn Mami ta kai ta tayi sllh, Mami tace "Abinci fa?" Yace "Aa I'm okay
ma" Tace "Are you sure, ka tsaya fa ka ci abinci" yana murmushi yace "Sure am
okay..." Tace "Toh shkkn mun gode Sudais" Yace "Heedayah tana ciki?" Mami tace "Ehh
sllh na kai ta tayi" yace "Toh na wuce" daga haka ya fita parlon... Mumy bata tanka
sai da safensa ba balle tayi masa tayin abinci yyi murmushi ya fita abun sa. Sai
bayan isha Mami ta bude warmer din da Sajida ta kawo, wainar shinkafa ce da miyar
taushe da ya ji nama da kayan hadi a diff but same warmers din, Mami ta kalli
Karime tace "Gashi fa idan xa ki ci" Karime tace "Toh Hajiya" Mami ta xuba ma
Heedayah shinkafa jollof da tayi... Karfe tara Mami ta sallami Karime ta tafi ta
kwanta, Karime tayi mata sai da safe cike da ladabi sannan ta fita xuwa dakinsu da
Sajida, Karime na kokarin kwanciya sai ga Mumy ta shigo dakin, Sajida ta mike da
sauri ganinta tace "Xa a maki wani aikin ne Hajiya?" Mumy ta wani hade rai tace
"Dalla rufe min baki kamar wata me yin abun arxiki, yaushe aka kawo yarinyar nan
Karime, Amma dubi duk ta haddace abubuwan da tasan take yi, satin ki na uku kenan
amma banda matsala bbu abinda kike bani da ciwon kai, ga sauran wanke wanke can kin
bar ma uwarki ta xo ta karasa min a kitchen" Ita dai Sajida bata ce komai ba kanta
a kasa, Mumy tace "Karime xo in d'an sa ki aiki don Allah yar albarka, bana son
bacin rai gwara in sa wanda xai min da kyau..." Karime ta mike da sauri har tana
tuntube tace "Toh Hajiya me xa a maki" Sajida dai ta bi ta da kallo bata ce komai
ba, Mumy tace "In ji dai Uwar dakin ki baxata neme ki ba, kin gama mata komai koh?"
Karime tace "Ta sallameni tace in je in kwanta bbu abinda xa ayi mata" Mumy tace
"Yauwa toh kar in je maki matsala, kin san yanayin rayuwar yanxu" Mumy ta fita
Karime ta bi bayanta da sauri... Har bedroom dinta ya shiga da karime, kayan guga
ne tule kan makeken gadon dakin, Mumy ta sauke tsadaddun akwatuna tace "Wa e nnan
kayan xaki jera min cikin nutsuwa a akwatunan nan, ba sake sa su xan yi ba shi sa
xan mayar akwati" Karime tace "Toh Hajiya...." Mumy ta kishingida gefen gado tana
shan grapes da ke plate a beside drawer, Karime sai jera kayan take cike da
nutsuwa, Mumy tace "In ji dai Uwar dakin taki bata baki matsala na ga kina da
hankali kuma komai a nutse kike yi ba kamar wancan tawar ba dake bani ciwon kai"
Karime tace "Eh to Hajiya, kinsan duka duka jiya na xo gidan, amma naga kamar bata
da sake ma jama'a kamar dai yanda kike..." Mumy tace "Haba?" Karime tace "Wllh, in
nayi ma yarinyar ba dai dai ba ko yaya sai ta gyara min cikin bacin rai..." Mumy
tace "Ikon Allah.... Duk wnn saukin kan naki??" Karime tace "Wllh, fitowar da nayi
da ita daxu ma sai da ya kusa ja min matsala tace kar in kuma fitar mata da
ita...." Mumy tace "Ikon Allah, kinga dai duk rashin damuwana ko ga maciji bata son
mu dinga yi ni dai bana biye mata tunda ina da ilimi na nasan abinda nake yi, Kuma
kinsan gaba daya satin ta daya da yan kwanaki a gidan nan, kwanan nan Mai gidana ya
aurota amma sai take min kamar ta rigani shigowa gidan nan, komai Isa Isa kuma a
walakance...." Karime da ta mike ta bude baki tace "Ikon Allah, kwanan nan? Ni ma
xata kun yi shekara da shekaru tare ai ganin ynda take komanta" Mumy ta gyara xama
tace "Wani shekara, yau kwananta takwas in gaya maki, kuma yarinyar nan da kike
gani agola ce ta kawota gidan, shine ake mana fi'ili
da ita, ni dai bana kulata sbda Allah na saka a gabana, Kinga dai d'ana na fari
sannan ga 'yan matana biyu, to me kuma xai dameni da ita??" Karime ta rike ha6a
tace "Gaskiya kam, ita da ko tsinke ma bata da a gidan, abincin da kika aiko mata
daxu ma bata ci ba bata bari yarinyar ta ci ba ni ta bama" Da mamaki Mumy tace
"Haba???" Karime tace "Wllh, Kuma tace Idan na gama in wanke kulan in ajiye maki a
kitchen, in mun hadu gobe ince maki ta gode" Mumy ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh
ai shkkn, ni saboda Allah nayi, ai ya ga xuciyata, ita ta sani" Karime tace "Kwarai
kuwa..." Mumy tace "Banda asiri gaskiya ne ina ita ina Mai gidana, asiricesa tayi
fa ta auresa ta shigo da yarinyar nan, har ynxu xancen da nake maki ba ma wani
shiri da Mai gidana duk ya watsar da ni da 'ya yana, komai ita ce kan gaba" Karime
ta bude baki tana kallon Mumy tace "Ikon Allah, Allah sarki, gaskiya kina da hakuri
Wai..... Ni dama ina ganin yanayinta nasan baxata yi kirki ba" Mumy ta sauke ajiyar
tace "Ni dai Allah na rike" Jin an bude kofar parlor Mumy tayi shiru haka ma
Karime, Mumy ta mike da sauri tace "Waye??" Bandaki ta bude ta nuna ma Karime ta
shiga da sauri, sannan ta fita parlon, Shuraim ne tsaye parlon, Mumy tace "Ya aka
yi?" Yace "A'a Aunty Rukayya ke son magana da ke ta kira wayar ki baki amsa ba...."
Mumy tace "Toh xan kirata, wayar na silent ne nan parlon..." Yace "Okay ke da waye
a ciki?" Mumy tace "Ni da waye a ciki Kuma? Sajida ce tana min gyaran kaya" Yace
"Toh sai da safe" tace "Allah ya tashe mu lfya" yace "Ameen" daga haka ya fita ta
juya ta koma daki, kitchen Shuraim ya wuce don hada shayi ya ga Sajida tana wanke
wanke, ya tsaya yana kallonta sannan ya tafi gun da cups suke ya dau daya ya hada
shayin ya fita parlor ya xauna, sai kusan sha daya Karime ta gama gyaran kayan
Mumy, Mumy ta hada mata kaya set uku tace "Gashi ki boye wnn kiyi ta tara abun
ki...." cike da jin dadi Karime tace "Kai Hajiya wllh na gode, Allah ya saka maki
da alkhairi, wannan kaya har haka??" Mumy tace "Ke dai ki ja bakin ki kiyi shiru,
ko Sajida ma kar ki nuna ma, gobe xan samu Ghana must go in baki ki dinga boye
kayan ki a ciki" Karime tayi ta mata godiya har ta fita dakin cike da murna.....
Shuraim dake xaune parlor har sannan ya juya jin footstep yana kallon direction
din, Kallon Karime dake tafiya kamar munafuka yyi ya dauke kai, ta shige dakinsu da
sauri ta kulle. Washegari da safe Mami ta gama duk abinda xata yi ma Heedayah kafin
ta fita, tana lura tun jiya Shuraim bai xo yace a fito da ita karatu ba, Karfe tara
Mami ta fito parlor tana kallon Karime da ta gyara parlon tsaf tace "Ni xan wuce,
xuwa anjima sai ki hada mata abun nan a cup ki bata idan ta tashi bacci, kuma kin
da ji abubuwan da na gaya maki jiya ki kula don Allah Karime, anjima ki dafa maku
duk abinda ku ke so" Karime na murmushi tace "In sha Allahu Hajiya, Allah ubangiji
ya kiyaye hanya" Mami tace "Ameen" daga haka ta fita parlon, Xaune taga Mumy main
parlor tana waya, Mumy ta dakatar da wayar suka gaisa faram faram Mumy na
tambayarta kwanan Heedayah, Mami ta tambayeta na su Rabi'ah sannan tayi mata
sallama ta fita parlon, Karime dake goge gogen kayan kallo bayan fitar Mami ta ta6e
baki maganganun da Mumy tayi mata jiya kan Mami na dawo mata ashe ma kwace mijin
mutane tayi ta shigo gidan, ci gaba da abinda take tayi tana yan wake wakenta, tana
gamawa kuma ta hada kakkauran shayi a cup don Mami ta siyo kayan shayi ta ajiye nan
parlonta sbda frequent shan shayin Heedayah, ta yanka tikeken bread ta xauna tana
ci duk da dumamen da ta ci da sassafe, ta gama shan shayin kenan aka d'an bude
kofa, juyawa tayi da sauri suka yi ido hudu da Mumy, Karime ta mike da sauri tace
"A'a Hajiya ce, shigo mana, ta fita ai..." Murya can kasa Mumy tace "Ina yarinyar
tata take?" Karime tace "Au tana can ai tana bacci, sai sanda ta tashi" Mumy ta
karaso parlon tana murmushi tace "Karyawa kike yi kenan" Karime tace "Ehh wllh,
gashi nan d'an ruwan shayi ta xuba min ta bani d'an kucilin biredi in karya" Mumy
tace "Ga bredi can bangarena banda abun ki, har kayan shayin ma ai akwai, ki je ki
hado wani idan baki koshi ba" Karime na washe baki tace "Allah sarki Hajiya to
nagode kuwa...." Mumy na kallon eye drops dake ajiye wajen tv a parlon tace "Wancan
Kuma menene, wa ke ciwon kunne?" Karime tace "Aa na yarinyar ne naga ana diga mata
a ido..." Mumy tace "Ohhhoo na ciwon idon kenan" Karime tace "Kila, daya da safe
daya da daddare haka naga ake yi kullum, daxu ma sai da ta diga mata da sassafe..."
Mumy dake ta kallon eye drops din tace "Ikon Allah...."

Littafin Heedayah na kudi ne, subscribe before reading.... and read happily....

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Mumy tace "Toh ki tafi ki hada shayin, kayan shayin na can kitchen, bredi kuma na
parlona su Rabi'ah sun bar sa a can" cikin rawan jiki Karime tace "Toh ngdd Hajiya,
nagode" Mumy ta kuma kai idonta kan eye drops din sannan ta fita Karime ta bi
bayanta da sauri cike da jin dadi, main parlor Mumy ta xauna tana girgixa kafa,
Karime kuma ta wuce bangarenta dauko bread, Mumy ta bi ta da kallo har ta shiga
ciki, dai dai nan kuma aka bude kofar parlon Mumy ta juya don ganin wanda xai
shigo, Kaka ce ta shigo parlon tana sakale da wani karamin jaka me kama da handbag,
Mai gadi na biye da ita a baya rike da wani tikeken akwati, Mumy ta bude baki ta
mike da sauri tace "Lafiya Kaka? Me ya faru??" Kaka bata ko saurareta ba ta nufi
wani spare room dake nan cikin parlon tana cewa "Ina fa lafiya? Meye kuma baxai
faru ba? Sai kace dai Umaru kadai na haifa a duniya, ga dai gidan Amadu me dakuna
ta ko ina...." Har ta bude kofar sai kuma ta dawo tace "Wllh Maryam wani kwai suka
soya min yau xar karni, to ga dai albasa an cika amma ni dai naji yana karni na
bala'i, ina laifin su d'an yanyanka min yar tafarnuwa su watsa a ciki, wnn ba
alamomin an gaji da kai bane a waje? Jiya sai bayan magariba suka kawo min abincin
dare, tuwo da wani miya sun cika naman kasuwa, to ca masu nayi yunwan nama nake??
abinda mu xamaninmu karfe biyar duk mun ci abincin dare munyi wanke wanke kowa ya
manta, mata kawai suna neman kashe ni kuma sai in xauna kamar uwata tace min je ki
kya gani, A'a wllh, to me gidan Amadu yake da baxan lallaba in dawo ba??" Mumy da
ta ji kamar ta kurma ihu cike da karfin hali tace "Haba kaka, Haba kaka, haba kaka,
wllh hakuri ake a ko ina, ko ina mutum yake sai yyi hakuri, rayuwar ma gaba daya
d'an hakuri ne, ni ba gashi an min kishiya ba nayi hakuri muna xaune lafiya? me yyi
xafi xaki tattaro kayanki ki dawo nan ai baxa su ji dadi ba Kaka, gaskiya bari in
dauko makullin mota mu koma, baxa su ji dadi ba wllh barin Baffa, gani xai kamar
baki gode kokarinsa a kanki" Kaka tace "Koh??" Mumy tace "Wllh tllh, ai ba xamansu
kike ba da xa ki bar masu gidan kaka, sun ma ci riba kenan, bari in dauko makullin
mota" Kaka tace "Toh, idan fita xa ki yi ga mai adaidaita can ki biyasa dari
biyunsa kar ya mana ihun 6arayi a unguwa yana can yana jira ban basa ko sisi na ba,
dama kuma ban masu sallama ba ta baya na bar masu gidansu, kya iya xuwa ynxu ki ce
masu na dawo nan da xama, duk me nemana Ina nan gidan d'ana Amadu...." Kaka na kai
wa nan ta shige daki... Mumy ta xauna saman kujera tayi tagumi tana furta
innalillahi wa Inna ilaihi raji'un a xuciyarta, Mai gadi da ya ajiye kayan Kaka a
parlan har ya tafi ya dawo yace "Hajiya D'an sahu na can yana jira fa...." Cikin
bacin rai Hajiya tace "Kai da d'an sahun sai na ci kaza kazanku idan baka fita
idona ba, na hau adaidaita ne da xa ka xo kace min d'an sahu na jirana???" Mai
gadin ya juya ya bar bakin kofar... Shuraim da ya dawo daga kai Abba office yana
kallon Mai adaidaitan da ya gyara parking don basa hanya ya sauke glass yace "wa
kake jira malam?" Mai adaidaitan yace "Wata tsohuwa na kawo nan ta shiga wai xa a
kawo min kudi to har yanxu dai ina ta jira" Shuraim yace "Nawa ne?" Yace "Dari biyu
ne kudin" Shuraim ya ciro dubu daya ya mika masa, D'an sahun yace "Amma bani da
canji wllh" Shuraim yace "To je ka" D'an sahun ya dinga yi masa godiya, Shuraim ya
gyada masa kai kawai ya ja motarsa xuwa ciki don Mai gadi ya bude masa gate,
parking yyi ya sauka ya rufe motarsa ya wuce ciki... Mumy ya tadda a parlor tayi
tagumi ga tashin hankali karara a fuskarta, ya isa kusa da ita ya xauna a hankali
yace "Mumy lafiya" Mumy tace "Ina fa lafiya Aliyu, don Allah ka shiga ka lallaba
tsohuwar nan ka mayar da ita gida, kalli uban akwatin da ta kawo wai ta dawo nan,
ta dawo wajen wa? Ta dawo tayi mana me? Don Allah ka shiga ka lallaba ta ka maida
ta inda ta fito...." Shuraim dake ta kallon Mahaifiyar tasa yace "Mumy amma ai ba
laifi bane don ta xo nan, Kuma ai...." A mugun fusace Mumy tace "Rufe min baki
gantalalle kawai, dama ina kuwa xaka san laifi ne dawowarta nan???" Lkci daya Mumy
tayi tsit ganin Kaka ta fito har ta cire Hijabin ta, Kaka tace "Kin sallami d'an
sahun ko kuwa kin barsa yana can yana min kallon macuciya barauniya??" Shuraim ya
mike yace "Na sallamesa" Kaka tace "Atoh, Kai baka je aikin bane yau?" Yace "Sai da
yamma, ina kwana?" Tace "Lafiya lau, Shureen ni dai na dawo nan gaskiya, matan
Umaru kasheni suka so yi Allah bai yi ba, yau wani kwai suka ban da ya kusa kai ni
lahira, shayin kuma sun cika masa kayan kamshi kamar dai buzaye... To ina dalili ga
dai gidan Amadu" Shuraim dai bai ce komai ba, Kaka tace "Ka shigar min da akwatina
daki dukiya ne a ciki, jama'ah Ina Deedayah, ga bredi na taho mata da shi da
kwai...." Shuraim ya dau akwatin nata ya shigar da shi ciki, Mumy dai karfin hali
kawai take don kiris ya rage hawaye ya xubo mata, kaka tace "Maryam tambaya nake
Ina Deedayah?" Mumy ta dake tace "Wacece kuma Deedayah?" Kaka tace "Sabuwar 'yar
Amadu mana...." Mumy ta wani tabe baki tace "Ayyo makauniya wai?" Kaka tace "Aa
wannan kuma isgilanci kike ma ubangiji ba ruwana, ke kika halicceta da xaki kirata
da makauniya, meye kuma makauniya idan ba isgilanci ba, ko ita ta xabar ma kanta
makantar? Ni yanxu Ina take??" Duk wannan abun Karime na tsaye sai kallon kaka
take, Mumy ta nuna mata Karime tace "Ga me kula da ita can" Kaka ta kalli Karime
tace "Wacece kuma wnn sai naso take, ta kula da ita ko ta sa mata cuta, bakya wanka
ne baiwar Allah?" Karime ta kasa cewa komai, Shuraim dai yyi murmushi ya nufi
dakinsa, Kaka na kallon Karime tace "wa ya daukeki ki dinga kula da ita, Amadu ko
wa? Tunda ita uwar rikon tata na samu labarin har ta fara fita aiki, Amadu ya fita
ita ma ta fita...." Karime ta girgixa kai tace "Aa, Hajiyar ce ta daukeni..." kaka
tace "Toh kuma sai kiyi ta kazanta kina naso, ba kya tashi da safe ki sa ruwa kiyi
wanka ki dauko yar atamfar ki ko da kodadde ne ki saka kiyi fess da ke.. yanxu Ina
yarinyar take?" Karime tace "Tana can daki kwance," Kaka tace "Wannan xama da ke ai
sai cuta ya kama 'yar mutane..." Daga haka kaka ta nufi part din Mami tana cewa
"Ita kuma mata daga tarewa sai fara fita aiki kamar auren banxa aka daura mata, ni
ba ruwana" Zaune kaka ta ga Heedayah saman gado ta tashi tana mitsika ido, Kaka ta
washe baki tace "Deedayah... Kin tashi" Heedayah ta juya da sauri tana duban Inda
ta ji muryarta tace "Kaka" Kaka ta karaso tace "Ehh ni ce Deedayah, kin ga na dawo
nan yanxu, kwai suka bani duk karni, kinji dalilin barin gidansu da nayi" Sakko mu
je ga bredi da kwan na kawo maki kema ki ci ki ji, Heedayah ta sauka saman gadon
kaka ta kama hannunta suka fita tana cewa "Ita dama ashe ba don ta kula da ke aka
aurota ba, xata barma katuwar mata kazama ta sa maki wani cutan Amadu ya shiga
uku...." Heedayah tace "Kaka tafiya xa ki yi da ni can gidanku?" Kaka tace "Wani
gida? Ai na dawo nan sai kuma wani ikon Allah, abincin banxa fa suke bani a can
gidan wllh Deedayah...." Mumy ta bi su da kallon gefen ido, Kaka ta tsaya tana rike
da hannun Heedayah tace "Maryam ban fa karya ba, Kuma ni ba shayi xan sha ba
gaskiya, ko me aka samu ni dai a bani in ci fisabilillahi" daga haka ta shige dakin
da ta sauka tare da Heedayah, Mumy ta mike ta wuce bangarenta da sauri ta dau
wayarta ta shiga Kiran Hajiya Sadiya, Hajiya Sadiya na dagawa Mumy ta sakar mata
Kuka tace "Sadiya wllh shirinmu na ta rugujewa, yau dai ga wnn tsohuwa ta diro da
katon akwati, ynxu haka ta dauke yarinyar ta shige da ita dakin da ta sauka, wato
bbu ma ranan komawarta ne don sai kinga akwatin da ta kawo, ni dai wllh Sadiya
hakurina ya fara karewa ji nake kamar in kashe yarinyar nan a gaban kowa a daureni
kawai in huta, wnn yarinya har in mutu xan mance da ita kuwa a rayuwata, ta janyo
min dariya a duniya, Duk fa dariya ake min a boye Sadiya" Sadiya tace "Ki kasheta
kuma a daure ki Maryam, me aka yi kenan? Ke ina gaya maki gaggawa na shaidan ne kin
kasa fahimta ko, meye na gaggawa abinda dai ana tare...." Mumy tace "Toh ke kina ga
wnn tsohuwar da ta diro mana gida ynxu baxata kawo mana wani cikas ba?" Hajiya
Sadiya tace "To ke meye ruwanki da ita? Wajenta yarinyar take da xai dame ki, Kinga
xa mu yi waya anjima nayi bakuwa" daga haka ta katse wayar, Mumy ta xauna gefen
gado tayi tagumi hawaye na sauka idonta.... Karime da Sajida tasa suka girka ma
kaka shinkafa da miya ko damuwa da ynda suka yi girkin bata yi ba... Kaka na kallon
Heedayah dake kwance gefenta tace "Toh sai kuma a siya maki?" Heedayah tace "Ehh
mana, har kitso Ina yi ma gashin babyn nawa...." Kaka ta rike ha6a tace "A
makancen?" Heedayah tace "Na'am" kaka tace "Toh yanxu a nan wani gantalalle ne xai
siya maki wani baby ana xaune kalau??" Heedayah tace "Abba mana" Kaka ta ja
kunnenta tace "Ke ce gantalalliya ba d'a na ba, shi Abban ne gantalalle?" Heedayah
tace "Aa ai Mami ma xata siya min" Kaka tace "Atoh sai dai ita din, Amadu ba
gantalalle bne..." Bude kofar dakin aka yi Shuraim ya shigo da sallama, kaka tace
"Ko kuma Shureen ya siyo maki ba?" Heedayah tace "Waye shureen?" Kaka tace "Aa nima
haka naji suna ce masa amma sunansa Aliyu..." Heedayah tace "Ae ban san shi ba"
Kaka tace "Toh ai sanin nasa bashi da amfani don bashi da kyakkyawan alaka da
mutane, mugun hali ne da shi, kin ga ai tun daxu da na xo bai shigo gaisheni ba sai
ynxu..." Heedayah tace "Shi ma a nan gidan yake?" Kaka tace "To Ina xa sa? Ai gidan
Ubansa ne nan din... da dai yyi aurene sai ya bar gidan, ni da Allah xai fito masa
da mata ma yyi auren kowa ya huta don wannan shiru shirun da yake yi idan xamaninmu
ne cewa xa ayi aure yake so" Shuraim dake tsaye bakin kofa ya hade rai yana kallon
kaka da Heedayah bai dai ce masu komai ba, Heedayah tace "To ki ce masa ya siya min
babyn Kaka, babba nake so" Kaka ta kalli Shuraim tace "Kaji kai Shuraim ko ba mai
tsada bane ka dubi maraicinta ka siya mata domin Allah, ya fi tayi ta xama shiruuu
kamar kurma..." Yace "Toh sai ta xo ta kwata
ai" Heedayah na jin muryarsa ta matsa kusa da kaka a hankali bata kuma cewa komai
ba, Kaka tace "Atoh, tunda ba ajiya ta ba mutane ba ai sai ta hakura da Babyn dama"
Tsaki Shuraim yyi ya juya ya fita ya rufe dakin, murya can kasa Heedayah tace "Kaka
ya wuce?" Kaka tace "To me xai min dama, ya wuce" Heedayah ta turo baki tace "Ni
bana son sa" Har aka yi azahar Kaka na dakinta tare da Heedayah, bbu irin labarin
da bata ba Heedayah ba wanda kwakwalwarta xai dauka da wanda ma baxai dauka ba, Tun
tulin shinkafa da miyan da aka kawo mata da safe ba a sake kawo mata wani abincin
ba.... Karfe uku da yan mintuna Mami ta dawo gida daga office, Karime na xaune
kasan carpet a main parlor tana kallo, tun kiran da Mumy tayi mata dakinta bayan
sun gama yi ma Kaka girki ita da Sajida sai lkcn ta sauko kasa ganin lkcn dawowar
Mami yyi, ta mike da sauri daga xaunen da take tana yi ma Mami sannu da xuwa xata
amshi jakar hannunta, Mami ta ki bata jakar tace "Ina Heedayan take?" Karime tace
"Ai kina fita Hajiya sai ga wata da naji suna ce ma kaka ta xo gidan, to tun safe
da ta shigo ta fita da ita xuwa wancan dakin bata yadda na je gunsu ba ma, ynxu
haka suna ciki" Mami tace "Kaka?" Karime tace "Ehh haka naji suka kirata, kuma
Sajida tace min Baabar Alhaji ce" Mami ta nufi dakin da kaka take ta yi sallama
sannan ta bude ta shiga, Heedayah na xaune tana cin shinkafar da kaka ta xuba mata,
ita kuma kaka na kara gyara kayan akwatinta don a birkice ta jerasu sbda sauri,
Mami ta xauna nan kasa da murmushi fuskarta tace "Sannu Kaka" kaka tace "Yauwa sai
yanxu kike dawowa kenan" Mami tace "Ehh yanxu na dawo" Kaka tace "Toh sannu da
xuwa...." Heedayah dake washe baki jin muryar Mami tace "Mami kin siyo min Babyn"
Kaka tace "Wani baby? Ki samu ma a samu lkcn kula da ke ba wani shegen baby ba, ke
yanxu fisabilillahi Rakiya da kika hadata da wannan yar aiki duk wari ta kula da
ita idan cuta ya kamata wa aka kai aka baro??" Mami bata ce komai ba tayi shiru
tana kallonta, kaka tace "Kice min Amadu, to wllh xuwa nayi na samu mai aikin duk
wari wai ita ce me kula da Deedayah, ki fa bar ganinta makauniya ki xata bata da
galihu Rakiya, ke kina ganin fatan jikinta kinsan ba daga cikin wahala ta fito ba,
gashi har abincin banxa na ga bata yrda ta ci sai na yan gayu, jikinta kwata kwata
bai son wahala, wa ya sani ma ko daga kasar waje wani axxalumin ya sato ta ya
wullota nan Nigeria da mugun abu yyi yawa?? Allah kadai yasan me yasa ya hadata da
Amadu a titi, kema gashi ta albarkacin ta ya aure ki, wa yasani ko kin dade kina
jin son sa a xuciyar ki sai gashi ta dalilin Deedayah ya aure ki..." Mami dai tayi
murmushi tace "Ai nayi mata komai kafin in fita kaka, abincin rana kawai take bata
sai abinda ba ka rasa ba, kuma baxai yiwu in dinga fita da ita aiki bane da tare xa
mu dinga xuwa" Kaka tace "Toh ni dai na dawo da ita nan ba ruwana, sai in ga uban
da xai dinga cutarta, mace duk wari kice ita xata kula da cin ta da shan ta,
kishiyar ki kuma tun xuwana da safe har ynxu ban ga keyarta ba, duk wannan bai
dameni ba tunda ke kin shigo, ynxu abinda nake so dake ga wayata ki kira min
Junaidu don mun yi da shi xai xo yau kar yaje can bana nan, ba komai yasa na bar
gidan ba sai kwai da suka kawo min duk karni" Mami ta amshi wayarta ta sa number
Junaid sannan ta kira sa ta mika ma kaka, kaka na jin ya dauka ta washe baki tace
"Junaidu... to yau dai gidan Amadu xaka taho na tattaro gaba daya na dawo nan"
Junaid ya gaisheta yace "Toh shkkn kaka sai na xo" tace "Allah ya maka albarka ya
kare ka sharrin makiya, ni ai ka fi min kowa" Murmushi kawai Junaid yyi ya amsa da
Ameen sannan yyi mata sallama ya katse wayar, Mami na kallon Heedayah ta kama
hannunta tace "Mu je ki canxa kaya" Kaka ta kalleta da sauri amma bata ce komai ba,
Mami ta mike rike da Heedayah tace "Sai na shigo anjima kaka" Kaka ta bi su da
kallo a hankali tace "Yauwa" Suna fita kaka ta mike ta fita ita ma ta nufi dakin
Shuraim da sauri, yana fesa turare ta samesa a dakinsa da yake a gyara kamar dakin
mace, ko ina fesss sai sanyin Ac, kaka ta xauna gefen gado ta fashe da kuka sosai,
ya juya yana kallonta da mamaki, ganin irin kukan da take ya nufeta yace "Lafiya
kaka? Me ya faru" Tana Shessheka tace "Mata ki fita tun safe ki bar yarinya Ina
wahala da ita daga dawowa sai ki dauketa, Halan ita ta tsinto ma Amadu ita bani da
labari ko kuma kanwar uwar yarinyar ce ita bamu sani ba, Yarinya muna xaune lafiya
banda hira babu abinda muke yi tun safe ba irin labarin da bata bani ba, bbu irin
labarin da ban bata ba kawai mata ta xo ta dauketa su wuce sbda bakin ciki...." Ta
fashe da wani sabon kukan tana mika masa wayarta tace "Kira min Junaidu...."

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍
Shuraim ya dauke kai ya juya ya koma gaban mirror ya dau makullin motarsa, Kaka ta
mike tace "Baxa ka kira min shi bane Shureen?" Ba tare da ya juyo ba yace "Ehh baxa
a kira ba, waye kuma wani Junaid...." A fusace Kaka tace "Aa wllh kar ka xagar min
shi don in ka xagesa ni ka zaga, kar ma ka fara wllh, ance maka bai fiye min kai ba
sau dubu, Ina ruwana da kai dama idan ba kaddaran na haifi uban ka ba, wllh Junaidu
ya gama min komai, kana xagin sa xaka xago ma kanka fitina, don ni ka xaga...." Ta
koma ta xauna ta fashe da wani sabon kukan, bude kofa Shuraim yyi ya fice daga
dakin ya kulle, kaka ta tsaida kukan da take a hankali tace "Ehh lallai d'an Amadu
ya ci ganye..." Mikewa tayi ta bi bayansa fa fita. Mumy ce tsaye ta wajen flowers
dake bayan gida, sbda shuke shuken flowers din wajen sai ya fi kama da garden, waya
ne kare kunnenta cike da damuwa tace "Wllh kuwa Baffa, ni dai nayi ta bata hakuri
ina kwantar mata da hankali, to kaga bbu ddi idan ban kira ka na sanar maka ba
tunda cewa tayi kai ma ba son xamanta kake a gidan ba, kuma idan anyi duniya don
manzon Allah ita da gidan har abada tunda xaman dole ku ke da ita, har mayar da ita
na yi niyyar yi tace ta koma a wani matsayin?? Tunda har ynxu bbu wanda ya biyo ta
ko ya kirata ya bata hakuri yace ta tashi su koma, to shine nake ga gwara ka taho
da kanka ka kara bata hakuri sannan ku tafi don wllh ta dau xafi sosai, ni ban ma
ta6a ganin bacin ranta irin na yau ba, kuka kuwa ta sha shi har ta gode Allah, xan
kira barrister in sanar masa ta hanani wai ita xaman garin ma duk ya fita a kanta,
gidan nawa ma ba xama xata yi ba, wai xa a iya wayan gari a ga bbu ita ta bar
garin, to shine naga gwara in kira ka..." Baffa dake ta sauraranta ya sauke ajiyar
xuciya yace "Shkkn Maryam nagode, sai na shigo anjima" Mumy tace "Babu komai, amma
don Allah kar kace ni na kira ka, idan ma kace mata ni na kira ka kara baci ranta
xai yi tace wato ma sai da na kiraka ka xo, da ban kira ba baxa ka xo ba, kuma idan
xaka xo sai ka d'an taho mata da abinda kasan ta fi so" Baffa yace "In sha Allah,
sai na xo" daga haka suka yi sallama, Mumy ta katse wayar tana wani murmushi, lkci
daya ta sauke ajiyar xuciya, cikin compound din ta koma dai dai shigowar Junaid,
har xata hade rai ganinsa ko me ta tuna kuma sai ta sake fuska sosai, ya gaisheta
da ladabi ta amsa tace "Sannu da xuwa junaid, kwana biyu baka shigo ba" yace "Ehh
naje Zaria ne" Mumy tace "Kuna da 'yan uwa can kenan" yace "Aa, naje wani uxuri ne
a can" tace "Ayyo... To sannu da xuwa" yyi mata godiya sannan ya nufi entrance din
shiga gidan, ta bi sa da wani kallo har ya shiga parlor... Sajida ce ke ta share
share a parlor, ta mike tana gaishesa ya amsa yace "Wani dakin Kaka take?" Sajida
ta nuna masa hanyar dakin, can ya nufa, yyi sallama bakin kofar, Kaka ta amsa da
karfin ta, ya bude kofar ya shiga, kaka na xaune ta daura kafa daya kan daya,
Khadijah na jera mata tarkacenta na tsofaffi a gaban madubi, kofar bathroom a bude
Karime na ciki tana ta faman wankewa, Junaid ya xauna nan kasan carpet yace "Sannu
kaka, Ina yini" tana washe baki tace "Lfya lau Junaidu, sai ynxu??" Yace "Ehh kaka,
ashe kin dawo nan..." Ta gyara xama tayi narai narai da ido tace "Baxan dawo ba
Junaidu, kwai suka soya min duk karni gashi fari fatt sai uban albasa to hakan ba
alamar an gaji da kai bne, to shine naga tun kafin sun barbadamin shinkafar bera
gwara in gudu, ynxu hka ba wanda ya san ina nan, kilan suna can hankali tashe sun
kai rahotu gidan 'yan sanda" Junaid da kansa ke kasa yana murmushi yace "Da dai
kinyi hakuri Kaka...." Shiru tayi tana kallonsa can tace "Aa kar ka xama gantalalle
kai ma mana, ae in kowa ya gaya min wnn mugun magana kai bai kamata ka gayan ba,
inyi hakuri su cuceni su kasheni a banxa, sae kace Umaru kadai na haifa, ga dai
Amadu, Aa ba ruwana, ni duk wanda yace in koma can gidan ma haushi na kawai yake ji
ya tsaneni" Junaid ya ajiye ledan hannunsa yace "Allah ya sa hakan shine mafi
alkhairi" Kaka tace "Toh ka ga ynxu kayi magana, Kuma in sha Allahu alkhairin ne
dama" murmushi kawai yake yi, kaka tayi kasa da murya tace "kana ji Junaidu, dama
uwarka haka take ban sani ba?" Junaid ya daga kai yana kallonta, kaf ta kwashe
labarin abinda Mami tayi mata ta sanar masa tana matsar kwalla, tace "A gantale fa
ta barta gun mai aiki dake naso uwa an tuttula mata jarkan man gyada, ynxu hka fa
ga Mai aikin can na sa ta wanke bandaki na, kuma ban amince ta shiga bandaki na ba
sai da tayi wanka wllh, to mata daga dawowa kuma sai ki dauke min yarinya haka
kawai, yini fa muka yi tare da yarinyar bbu wanda ya ji kanmu, muna ta hira fa in
gaya maka" Junaid yace "Gaskiya bai kamata....." Kaka tace "Allah ya maka albarka,
daga shigowa gida sai ta fara fito da mugun halinta da wuri wuri hka tun ba aje ko
ina ba, ni sai nayi tunanin ma ko tasan uwar yarinyar ne wnn isa haka da ta nuna
min...." Junaid ya d'an yi murmushi yace "Xan je in dauko maki ita ynxu kaka" kaka
tace "Amma fa kar kace nace maka komai, ba ruwana kar ta kullaceni, kawai dai kayi
mata nasiha ta canxa halinta, wannan ba halin xaman gidan miji bane..." Ya mike
still smiling yace "In sha Allah kaka, bari in je in dawo" Kaka tace "Allah maka
albarka, ni dai gwara min kai a kan kowa ma a gidan nan" Kaka ta kalli Khadijah da
sauri tace "Ke 'yar banxa kin gaishe sa ma kuwa da ya shigo? Ku dai 'ya yan Amadu
baku da hali tirrr" turo baki Khadijah tayi tana ci gaba da abinda take, shi dai
Junaid tuni ya fita ya rufe mata kofa, part din Mami ya nufa ya sameta xaune parlor
ta daura kan Heedayah a cinyarta tana mata gyaran gashi, Heedayah ta mike xaune da
sauri jin muryarsa, ya xauna saman kujera ya gaida Mami, Mami ta amsa tace "Na xata
da Farida xa ku xo" yana kallon Heedayah yace "Aa, Uncle said she should stay" Mami
tace "Okay, how are you" yace "Alhmdllh, ya aiki" tace "Mun gode Allah" Ya mike ya
koma kujeran da suke ya xauna gefen Heedayah yana kallonta yace "How are you
Heedayah" Ta wara ido tace "Fine, me yasa baka xo ba jiya har da shekaranjiya" Yace
"Ae gani na xo yanxu" Ta laluba fuskarsa tace "To ka dinga xuwa kullum ka ji?" Mami
dai ta tabe baki tana harhada kayan gyaran gashinta, Junaid na murmushi yace "Mami
kaka tace a maido mata da Heedayah" Mami na kallonsa kafin tace komai ya kara da
cewa "She wants her to be staying with her, bata ji dadin xuwa da kika yi kika
dauketa ba daxu" Mami ta rike ha6a tace "Tohhh, ikon Allah" Junaid yace "Yess allow
her ta koma wajen ta Mami, since ita ta bukata" Mami tace "Toh ai naga kamar wani
nauyin Heedayah xata xame mata, baxata iya da tsirfan Heedayah ba" Junaid tace
"Tunda ita ke son hakan ki bar mata kawai Mami" Mami tace "kai yaushe ta gaya maka
haka?" Yace "Yanxu, har da kukan ta" Mami ta bude ido tace "Ahh to dauketa ka kai
mata ita" Heedayah dake jin su tace "Mami wajen kaka xai kai ni?" Mami tace "Ehh"
Heedayah tace "Amma xan dawo koh?" Mami tace "Ehh xa ki dawo" Junaid ya mike ya
kama hannunta suka fita parlon, Mami ta bi su da kallo.... Mumy dake xaune parlor
kamar dai ko da yaushe ta bi su da kallon gefen ido har suka wuce dakin kaka, Kaka
na ganin Heedayah ta washe baki tace "Deedayah, ga kaza Junaidu ya kawo min, ai kin
iya cin kai da kafar kaza koh?" Heedayah tace "A'a ni lap na iya ci" Kaka ta kalli
Junaid tace "Meye lam kuma?" Yyi yar dariya yace "Cinya" Kaka ta kalli Heedayah da
sauri tace "To sai ki kwata ai, ka ji min dai" Ya xaunar da ita gefen kaka yace
"Kaka xan je Masallaci in dawo" Kaka tace "Toh yi maxa gashi can an fara kira" a
hankali Heedayah tace "Are you coming back?" Ya juya yana kallonta yace "Yess" Yana
fadin haka ya juya ya fita, Kaka tace "Toh ko wnn lafiyayyen turancin da kike ai ya
ci kowa ma ya san ba daga gidan gantalallu kika fito ba, da kyar idan baki fi
Shureen iya turancin ba don ni tunda nake ban ta6a jin ma yyi turancin ba, ga dai
makaranta me tsada uban ya sa shi yana karami amma bai jin turanci, ko wnn kwam din
da kowa ya sani baya ji" Heedayah ta kyalkyale da dariya tace "Kaka to sai in dinga
koya masa mana" Kaka tace "Atoh, bari dai Allah ya shigo da shi mu ga ko xai yadda"
Heedayah tace "Kaman ni yake?" Kaka tace "Ka ji ki wannan a haihuwar kaji ai yyi
jika da ke, Shureen fa nace maki" Heedayah tace "Ni ban san shi ba" Kaka tace "Idan
ya shigo xan Kai ki ki tattabasa ki ji" Heedayah tace "Toh" Tare Junaid ya shigo
cikin gidan da Baffa, Baffa ya xauna parlor shi kuma ya shiga wajen kaka yace "Kaka
Baffa ya xo" Kaka tace "Waye kuma Baffa, uban wa yace masa Ina nan, Kai ni dai
gaskiya ana shiga hakkina, to me ya xo min kuma kamar dai wata yar karamar yarinya"
Junaid na murmushi yace "Ya xo ne ya tabbatar nan din kika xo" Kaka ta tabe baki
tace "Ni dai ba ruwana wllh" Bude kofar dakin aka yi sai ga Hajiya Amina da Hajiya
Hauwa sun shigo da sallama, Kaka tace "Su waye wannan kuma" Hajiya Hauwa tace
"Sannu kaka" Kaka tace "Yauwa, daga ina haka kamar an koro ku, ko daga anguwa ku
ke?" Hajiya Amina tace "Daga gida muke kaka, mun xo biko...." Kaka tace "Yaji
Maryam din ta kara yi ina gidan bani da labari??" Hajiya Hauwa tayi dariya tace
"A'a kaka, kawai sai mu ka ga ba ki a gida" dai dai nan Mumy ta shigo dakin, kaka
tace "Wllh na so shiga in maku sallama amma sai nayi tunanin bacci ku ke don na San
ku da baccin safe, tashi nayi yau da tunanin Amadu a raina shine nace bari dai in
je shi ma ya sami lada na...." Baffa ne ya shigo da sallama, kaka tace "Ikon Allah,
har da kai Umaru, to me ya faru ne wai? Ba fa kai kadai na haifa ba da xanyi ta
xama gidanka, shkkn kuma shi Amadu ba mutum bne da baxan dinga xuwa nasa gidan ba,
Kar ka xama me son kanka mana Umaru, ka so ma d'an uwanka abinda kake so ma kanka,
shima ka barsa ya dinga samun ladan uwarsa" Baffa yace "Nayi tunanin ko an 6ata
maki rai ne ai Baaba" Da sauri kaka tace "Aa wllh, baku ta6a min komai ba, idan
nace ma kun mun sai Allah ya kamani, matan ka ai mutanen kirki ne tun ma ba Mai
jidda ba, tamkar ynda xa su yi ma iyayen su suke min, to sae in masu
sharri ince sun min wani abu?? Aa kawai ni dai na xo gidan Amadu ne shi ma ya samu
lada...." Kallonta kawai junaid yake with surprise, Mumy da hawaye ya cika idonta
tace "Amma fa kaka cewa kika yi kwai suka soya maki duk karni sannan basa baki
abinci da wuri kawai sun gaji da ke ne...." Kaka ta saki salati tace "Yau naga
abinda ya isheni jama'a, Maryam ke da wa ku ka yi haka??? Lalacewar ta ki ta kai
haka bani da labari? To ke ina ruwanki ko danyen kwai suka kawo min, ba gwara su
sun kawo min kwan duk karni ba, ke me barina da yunwa fa??" Baffa yace "Toh kaka
tunda dai bbu wani matsala shkkn sai dai mun yi waya" Kaka tace "Bbu ko wani
matsala Umaru Allah yyi ma kai da matanka albarka..." Baffa ya amsa da Ameen ya
fita....Mumy dai hawaye ya ki tsaya mata, Hajiya Hauwa sai danne dariyar ta take,
daga karshe ita ma tayi ma Kaka sallama ta fita haka ma Hajiya Amina, Mumy ta bi
bayansu xuciyarta na tafarfasa, Junaid dai kansa na kasa, kaka tace "Ka ji min mata
dai xata min sharri da rai na" Tuwo da miyar egusi Sajida ta kawo ma kaka, Kaka
tace "To ba gwara ke ba kan wannan mata da Rakiya ta dauka aiki duk wari.... Tafi
ki kawo min flet da cokali" Mai aikin ta fita sae gashi ta dawo, Kaka ta amsa ta
bude warmer din tuwon ta diba, ta ajiye ma Junaid, Junaid yace "Kaka ni fa a koshe
nake" Kaka tace "Aa ni ba ruwana gashi nan ka ci, kana da Inda xaka je ka ci abinci
ne da ya fi nan...." Ta kalli Heedayah tace "In xuba maki kema" Heedayah tace "Na
koshi" Kaka tace "To wlh baxan baki Kai da kafar Kazan ba ma" Heedayah ta mike
xaune kamar xata yi kuka tace "Toh in ci da Yaya" Kaka ta kalli junaid, Tashi yyi
ya koma kusa da ita da plate din tuwon yace "Toh mu ci" Kaka ta ta6e baki tana xuba
nata, Heedayah ta d'an fincili tuwon bayan ta laluba plate din ta kai baki, Kaka
tace "Wllh haramta maka tuwon xata yi, meye kuma na mintsilin tuwo kamar kaza??"
Dariya junaid yyi ya deba a cokali kadan ya tabbatar ya huce sannan ya kai bakin
Heedayah, Jin cokali a lips dinta ta bude bakin ta amshi tuwon, a haka suka dinga
cin tuwon, aka bude kofa sai ga Shuraim ya shigo, kaka tace "Shureen wai xaka dinga
koyon turanci gun Deedayah" Shuraim ya kalli Heedayah da ta tankwashe kafa a gaban
Junaid, ajiye ledan hannunsa yyi nan gefe ya fita dakin, kaka ta kalli Junaid tace
"Kila kunya ya ji, da ban masa magana a gabanka ba" Dariya sosai Junaid yyi... Sai
kusan karfe tara yayi ma Kaka sallama Heedayah har da kukanta wai xata bi sa, ya
samu dai ya lallabata ya fita, Kaka tayi tagumi tace "Toh wai a gidan ubanwa kika
ta6a sanin Junaidun idan ba gulma ba?? Sai kace shine Amadu? Ai ni da Amadu ne
dolen ki..." Wajen karfe sha daya Mami ta shigo da eye drops din Heedayah, Kaka da
har ta kashe wuta tace "Kinga Rakiya, abinda xai faru ba sai kin dinga ba kanki
wahalan shigo mana tsakar dare ba mun fara bacci, kawai ki nuna min ynda xan dinga
sa mata a idon, Amadu fa ya fi awa daya a dakin nan sannan ya fita, tun daxu ya
kamata ki xo ai, ni na xata kin gaji kin kwanta ne" Mami tace "Aa ban kwanta ba"
kaka tace "To nuna min ynda abun yake in dinga yi mata da kai na" Mami ta nuna ma
kaka ta tabbatar ta gane din tana kuma tsaye ta diga ma Heedayah dake bacci drops
din dare sannan tayi masu sai da safe ta fita... Har kaka ta kashe wuta aka sake
bude kofa, Mumy ce ta shigo kaka ta kunna wuta tace "Amma dai bakwa tsoron Allah
matan gidan nan, bakin cikin baccin ake mani cikin daren ma" Mumy tace "Yi hakuri
kaka, naga baki bacci da wuri ne ban san kin kwanta ba, kankana na yanka ma
Barrister shine na dibar maki" kaka tace "Ki sa min a firiji, amma wnn ae shiga
hakki ne, meye kuma kankana tsakar dare jama'ah kamar ana yunwa" Mumy ta bude
fridge dake dakin ta ajiye tana kallon eye drops dake ajiye saman fridge din, lkci
daya ta kwashe su tace "Toh sae da safe kaka" bata jira cewarta ba ta fice daga
dakin, kaka ta ja tsaki ta kashe switch din wutan.... Har wani murmushi Mumy take
ta wuce dakinta da sauri, bandaki ta shiga da wayarta ta doka ma Sadiya kira,
Sadiya na dagawa tace "Toh ga dai eye drops din na samo Sadiya... Kin yarda Allah
na tare da ni?? Wllh cikin ruwan sanyi na samu, ban ta6a xaton hka ba...."
Heedayah isn't free, do not read for free, subscribe and read happily....

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Hajiya Sadiya dake sauraren Mumy tace "To kin dauko cikin ruwan sanyi maidawan fa
Maryam?" Mumy tace "Aa ni maidawan ba wani damuwa ta bace, minti nawa ne, abinda
dai ba makulli take sa wa a dakin ba...." Sadiya tace "Toh shkkn, amma wajen bude
maganin kiyi ta ynda fa baxa a gane ba, a nutse xaki yi komai" Mumy tace "Toh shkkn
sai mun yi waya Sadiya" Daga haka ta katse wayar ta fito, handbag dinta ta nufa ta
bude ta binciko wani kwalba irin na magani dake karkashin jakar ta ciro sannan ta
rufe jakar, kokarin bude eye drop din ta dinga yi amma ta kasa, tayi tayi amma ya
ki buduwa, wuka ne ya fado mata ta Kalli agogo taga sha biyu saura, ta d'an yi
murmushi ta ajiye drops din a drawer ta nufi saman gado ta kwanta tana jiran karfe
daya yyi don wnn lkcn ta tabbatar kowa na gidan yyi bacci, tana ta kwance idonta
kyar ko digon bacci bbu har agogo yyi struck din karfe daya dai dai, ta mike a
hankali ta saka hijab dinta har kasa sannan ta dau drops din da kwalbanta ta fita
daga dakin, cikin Hijabin nata ta boye hannunta me dauke da eye drops da kwalba,
kitchen ta nufa direct ta kunna wutan, sannan ta juya baya ta ciro abubuwan cikin
hijab dinta ta dau wuka ta fara gwada bude eye drops din a nutse, she was so
careful kar saman yyi shaidar da xai sa a gane an bude, bude kofar kitchen din taji
anyi, a rikice ta boye komai cikin Hijab, muryar Shuraim taji yace "Baki kwanta ba
Mumy, what are you doing" kin juyowa tayi ta dinga kawar da plate da cups din karya
duk a rude, amma lkci daya ta dake tace "Me ya hanaka bacci har war haka??" Yace
"Shayi xan hada" Mumy ta hade rai sosai tace "Wannan shan shayin dai ya xame maka
jaraba, wani shayi ne baka sha ba tun wayewar garin Allah sai tsakar dare kamar
maita ka tashi wai xaka sha shayi? Shayin me? idan baka sha shayin ba mutuwa xaka
yi ko me da baxaka hakura ba tunda dare yyi" Shi dai bai ce mata komai ba, har
sannan hannunta daya na boye hijab dinta, ta nufi kofa a fusace ya bi ta da kallon
gefen ido, cup ya dauka ya bude flask ya debi ruwan Lipton ya bude kayan shayin xai
hada, Mumy tayi still ganin kaka a parlor, lkci daya gabanta yyi mugun faduwa kaka
ta karaso Inda take tace "Amadu yyi bacci ne?" Cikin rawar baki Mumy tace "Lafiya
Kaka, me ya faru?" Kaka tace "Ina fa lafiya, idonsa biyu ko yayi bacci?" Mumy da
hankalin yyi mugun tashi don cikin d'aga murya kaka ke magana tace "Kaka ban san ko
yyi bacci ba daga kitchen...." Abba ne ya fito parlon jin muryar mahaifiyar tasa,
Kaka na ganinsa tace "Amadu wannan wani bala'in ka kawo wa mutane gida, ya xa a
dinga shiga hakkina Ina bacci, to gata can ta hanani bacci wai shayi xata sha, meye
kuma shayi kamar buxuwa tsakar daren nan" Mumy bata san lkcn da ta sauke wani
bayyanannen ajiyar xuciya ba, Kaka tace "Ni dai ba ruwana, tun wayewar gari bata
gama shaye shayen shayinta ba sai ynxu bayin Allah na hutawa, kawai ta cuceni ta
tasheni" Abba dai bai ce mata komai ba, kaka tace "Ga ta can xaune kamar yar mage
ta ki bacci wai shayi, to ni siyar da shayi nake xata tasheni ta dameni" Abba yace
"Kiyi hakuri, bari a maida ta gun Rahinah" Kaka ta kallesa da sauri tace "A maida
ta kuma? A kan me? To sai kayi ta maida ta din ae, daga tace xata sha shayi sai a
maida ta gun Rahilah" Duk wnn abun Shuraim na tsaye rike da cup din shayinsa yana
kallonsu, Mumy tace "Kiyi hakuri kaka bari in hado mata shayin yanxu" Shuraim ya
karaso cikin parlon Kaka na kallonsa tace "Waye wnn kuma?" Mika mata cup din
hannunsa yyi ta amsa tace "Toh ba shkkn ba dai, amma xaka wani ce a maida ta gun
Rakiya, meye hadinta da Rakiya, Kuma waye bai san yaro ba Allah na tuba" Daga haka
ta wuce dakinta rike da shayin, ta gefen ido Mumy ta dinga hararan Shuraim da ya
juya ya wuce dakinsa shi ma, Abba ya girgixa kai ya koma bangarensa. Mumy ta tabe
baki don har yau ba wani shiri take da shi ba, dakinta ta koma ta sa makulli ta ci
gaba da aikinta, da kyar ta bude drops din ta wuce bandaki ta tattular da maganin
ciki ta dauraye empty container din da ruwa a nutse sannan ta dawo daki, kwalbanta
ta bude ta xuba content din ciki wanda kalansa shi ma fari ne a robobin eye drops
din, snn ta rufe gam da murfi... Ta ajiye robobin su bushe a gaban madubi tana yi
tana kallon agogo, sai biyu da kusan minti goma ta kwashe magungunan ta bude
kofarta a hankali ta fito parlor, kwance ta ga mutum saman kujera yyi rub da ciki,
duk da wutan parlon a kashe yake amma wutan compound ya d'an haska har cikin
parlon, ta yi still a Inda take don ta san baxai wuce Shuraim ba tunda ya saba
kwanciyar parlor, yawanci ma nan yake kwana, tana daga Inda take tsaye ta dinga
leka fuskarsa a hankali taga bacci yake, tayi tiptoeing har xuwa hanyar dakin kaka
sannan ta bude kofar very careful don ma ko kadan kofar baya kara, fridge ta nufa
ta ajiye eye drops din ta juyo da sauri ta fita ta kulle kofar, sannan ta sauke
ajiyar xuciya, tana isa cikin parlor ta kara lekan Shuraim da ko motsawa bai yi ba,
ta wuce dakinta hankali kwance tana gode ma Allah. Sbda baccin da Mumy bata yi ba
da wuri sai kusan karfe takwas na safe ta tashi duk da ta tashi sllhn asuba, taga
har su Khadijah sun wuce makaranta, bandaki ta fara shiga sannan ta fito ta tafi
parlor, dai dai nan Kaka ta fito, Mumy na murmushi tayi kasa tace "Sannu kaka,
fatan kun tashi lfya?" Kaka tace "Wani lafiya an shigo an sace ma yarinya magani, a
kira min Amadu" Kasake Mumy tayi tana kallon kaka, kaka ta nufi bangaren Mami tana
cewa "Bari inji ko wnn matar ce ta shigo ta kwashe magungunan yarinya sbda ta nuna
min ban isa da ita ba" Kaka ta shiga buga kofar Mami, Mami na fitowa kaka tace
"Rakiya Ina maganin da kika shigo kika kwashe?" Da mamaki Mami tace "Magani kuma
kaka?" Kaka ta saki salati tace "Toh wllh barawo ya shigo ya sace maganin da kika
kawo jiya, ba a kan friji nace ki ajiye ba??" Mami tace "Ehh nan kuma na ajiye"
Kaka tace "Toh ko sama ko kasa, dakin na can na hargitsa wai ko ma ya shige wani
lungun ne amma wllh ban gani ba, Ina Amadu" Mumy dai ta kasa motsi inda take, Mami
ta kalleta na yan sakwanni sannan ta dauke kai, Kaka da kanta ta tafi ta kwankwasa
ma Abba kofa yana fitowa tace "Amadu barawo ya sace maganin Deedayah, wllh da shi
muka kwanta muka tashi ba shi" Da mamaki Abba yake kallonta, tace "Wllh ba xancen
wasa ba kana kallona" Mumy dai fa an kasa motsin kirki sai imagining take to ko dai
cikin mafarki ta mayar da maganin bata mayar a xahiri ba, Shuraim ya sakko
downstairs jin muryar Kaka ya cika gidan, ya karaso yana kallonta yace "Me ya
faru?" Kaka tace "Shureen maganin Deedayah aka rasa wanda ya dauke, ni kuwa yau xan
ga 6atar nono a kirjin budurwa...." Kallonta kawai Shuraim yake with surprise, can
ya kalli Mumy dake tsaye sai wurga ido take, Kaka tace "Al-qur'an kira xan yi in sa
a ja min Yasin, in dai ba a fito min da maganin yarinyata ba sai na kai kudi an ja
min yasin" Abba dai bai ce komai ba, Mami na tsaye just watching everybody, Kaka ta
nemi kujera ta xauna tana hada xufa tace "Ka ji min dai, to wllh ba ruwana sai dai
cikin mutum ya kumbura, me Deedayan ta tsare maku da xa a dauke maganinta, ko uban
wani ne ya siya mata maganin banda Amadu???" Abba yace "Junaid ne ma ya siyo ba ni
ba" Kaka ta mike da sauri tace "Au Junaidu ne ma, to dama idan ba kai din ba ko shi
wa gareta da xai siya mata, wllh Amadu ka ja su daki kayi masu magana cikin nutsuwa
su fito min da maganin yarinya kar abu ya baci tsakanina da su, xan fa mance sanin
da na masu in sa a ja masu Yasin" Tana fadin haka ta juya ta nufi dakinta fuska
daure, Shuraim ya bi ta da kallon gefen ido, Cike da karfin hali Mumy tace "Ikon
Allah...." Mami ta ta6e baki ta juya ta koma dakinta, Mumy tace "To magani kafafuwa
garesa da xa a nema a rasa?? Anya kaka ta san Inda ta ajiye maganin kuwa?" Abba na
kallon Shuraim yace "Xan sa Junaid ya tura maka sunan eye drops din, sai na maka
transfer ka tafi pharmacy ka siyo su" Shuraim yyi kasa da kai, Abba yace "Ko baxa
ka samu xuwa ba..." Kafin yace komai Mumy tace "Baxai samu ba mana, shi da yake
fita aiki Barrister, Ina ji fa ranan Baffa ke fadan baya wani xuwa aikin sai ya ga
dama to idan ba matsala kke son ja masa gun Baffan nasa ba ina xai je samo wani
magani ynxu da safe" Tun da ta fara magana Abba ke kallonta keenly, can ya gyada
kai ya wuce bangarensa, Shuraim dai bai iya ya daga kansa ba, Mumy ta hade rai
bayan tafiyar Abba murya can kasa tace "Did you know anything about the missing eye
drops Aliyu??" Ya daga kai da sauri yana kallonta yace "Ni kuma Mumy, ni ban ma san
da wani eye drops a gidan nan ba, I know nothing about it, ban ma san kalarsa ba"
Mumy ta kauda kai tana naxari to wai ko dai mafarki tayi ta mayar da drops din
dakin kaka?? Ganin Shuraim ya fara wucewa ta kara daure fuska tace "Wait, ko da
wasa kar ka fita gidan nan da sunan tafiya siyo ma tsinanniyar yarinyar nan
magani.... I'm instructing you not to do so" Da mamaki ya tsaya yana kallonta, can
yace "Toh idan Abba ne yace in je fa Mumy?" Rai bace Mumy tace "Ni kuma nace baxa
ka je ba, ko tsallake maganata xaka yi??" Yace "Amma ai baxan iya ce masa A'a ba
kamar ynda kema baxan iya ce maki A'a ba" tace "Wannan ya rage naka kai da shi, ni
dai nace idan ka fita gidan nan siyo maganin makafi to ba da yawuna kayi hakan ba"
Fitowar kaka ya sa ta ja bakinta tayi shiru da sauri, Kaka dake sanye da hijab
hannunta rike da Heedayah tace "Ga shi na fiddo dubu daya ta xan je siyo maganin
idon a kemist, daga can kuma xan tafi gun da xa a ja min yasin na tsakani da
Allah...." Mumy tace "Haba kaka yanxu fa nake cewa xan shiga a sake duba dakin da
kyau ko...." Kaka ta katse ta a fusace tace "Tunda kinga alamar na fara makancewa
kamar Deedayah ba, wllh tllh baxan yi kaffara ba wani algungumin ne ya shiga ya
dauke maganin nan, to ni abinda har yanxu ban gane ba a nan shine, bakin ciki ake
ma yarinyar kar idon ya warke ko me?? Anya wasu xa su gama da duniya lafiya kuwa,
Junaidu ya cire kudi domin Allah ya siyo mata magani amma wani mara tsoron Allah ya
bi dare ya sace, tunda nake
ban ta6a ganin irin haka ba sai gidan Amadu, gidan Umaru basa haka kwata kwata, in
haka ne lauyancin karya Amadu ke yi kenan, lauyancin karya mana tunda ya kasa kama
wanda ya sace ma Deedayah magani, ita ma amaryar da naji ance lauya ce ashe ta
karya ce, lauyoyi biyu a gida a tafka wnn uban sata amma a kasa kama barawon har
war haka?? Aa ba ruwana gwara inyi ta kai na, dubu daya da dari biyar dina ya biya
min bukata, dubu daya in bada a kemist su bani maganin guda biyu, dari biyar kuma
in tafi gidan Ta salla ta rakani inda xa a ja min yasin...." Shuraim was trying
hard not to laugh sai sunkuyar da kansa yake yana shafa gashin kansa, Fitowar Abba
yasa ya daga kai yana kallon Abban nasa, Abba yace "Ina kuma xa ki kaka?" Tace "Ina
ne kuwa baxan je ba Amadu, Kai baka san wnn yar amana ce Allah ya baka ba xaka
barta ta walakanta a gidanka, wani axalumi ya sace mata magani kayi shiru" Abba
yace "Xan je siyo maganin ai ynxu" Kaka tace "A'a ai tunda nayi niyya sai na siya
ga dubu dayana xan je kemist da ita ynxu" Abba ya tsaya kallon kaka kafin yace "Ae
ko wani daya ya kusa dubu ashirin da biyar" Kaka ta gwalo ido tace "Me din?" Abba
yace "Bari ynxu xanje in siyo in kawo maku" Shuraim dake kallonsa a hankali yace
"Abba I will go..." Abba yace "Noo, Kar ka damu" Shuraim yace "Amma kace I should
get it" Yace "Ehh na canja shawara, you don't worry" Daga haka Abba ya fita,
Shuraim ya bi sa da kallo, Mumy ta kyabe baki, Kaka na kallon Heedayah ta dunguri
kanta tace "kin dai ji nawa ake siyar da maganin d'an cikin roban nan, to idan ba
tsoron Allah ba uban me muka hada da ke xa mu dinga kashe maki kudi haka, kin ji fa
wahalan da d'a na yake, dubu hamsin xai kashe da safen nan a kan lalurar ki, to wa
xai saka masa kuwa banda Allah? Ba dangin iya balle na Baaba fa" Mumy tace "Abinda
ke damuna kenan kaka daga karshe ma a saka ma mutum da sharri" Kaka ta kalleta tace
"Toh Ina ruwan ki, kudin ki ko na Amadun??" Kaka na fadin haka ta ja hannun
Heedayah suka koma daki.... Mumy ta wuce nata dakin don duba drops din ko bata
mayar da gaske ba, Mumy ta tsaya da mugun mamaki a gaban madubinta tana naxarin to
waye ya shiga dakin kaka ya dauke maganin nan, kaf ta duba dakinta bbu, ita dai
tana da yakinin ta mayar wajajen karfe biyu da wani abu na dare ba wai mafarki ba,
hankalinta yyi mugun tashi don gashi an kara wargaza wnn plan din ma, ta dau
wayarta rai ba dadi ta wuce bandaki. Har Mami ta gama shirin fita office hankalinta
ya kasa kwanciya, she is so disturb, ko kadan bata ji xuciyarta yyi na'am da
komawar Heedayah gun kaka ba, ko ma waye ya dauke eye drops din nan yyi hakan ne da
wata manufa na cutarwa, cuta kuma me girma ba karami ba, bata san ta ina xata fara
billowa kan a bar Heedayah wajenta ba, gaba daya taji bata yi trusting kowa na
gidan ba, they all look guilty, both mother and Son, sannan masu aikin ma haka
kawai taji hankalinta bai kwanta ba bata yrda da su ba, sannan Rabi'ah da Khadijah
ma halin uwar garesu bbu abinda suka mance nata, kaka kuma from many indications
taga baxata cutar da Heedayah ba balle kuma a je ga wanda yyi sanadin xuwanta gidan
wato Abba, dauke Heedayah daga wajen kaka isn't going to be easy but she will try,
ynda take jin Heedayah bata jin xata bada space a cuceta a gidan nan sai iya inda
karfinta ya kare, da haka ta fita xuwa parlon Abba sanin bai fita ba, Yana parlon
nasa da Shuraim dake xaune kasa, Abba na kallonta yace "Xaki tafi office...." Tace
"Yes, but barrister har yanxu baka ce komai ba a kan the missing eye drops.... This
is a very serious issue to address to with immediate effect, Sannan nasan ka fini
sanin koma wanene ya dauke eye drops din nan ya dauke sa ne da manufa biyu xuwa uku
which I won't mention cos you know...." Abba dake kallonta yace "Gaskiya ne, I will
see to that" tace "And pls ko xaka yi ma kaka magana Heedayah ta komo wajen??" Abba
ya d'an yi shiru, sannan yace "Will see to that too" Mami tace "Alright thank you,
sai na dawo" daga haka ta fita, Shuraim ya bi ta da kallon gefen ido, dakin kaka
Mami ta tafi, ta samu kaka ta hada ma Heedayah shayi me kauri ga ledan bredi guda
ta ajiye mata, Kaka tace "Har xa a fita kenan" Mami ta xauna kusa da Heedayah tace
"Ehh kaka, Ina kwana?" Kaka tace "Lafiya lau, kawai sai muka wayi gari da alhinin
an sace maganin Deedayah" Mami tace "Allah dai ya kyauta...." kaka tace "Ameen
fahhh, ga dai sabo Amadu ya siyo ya kawo na boye, ita kanta Deedayan ma baxan bari
ta san Inda na boye ba balle wani" Mami tace "Yauwa gwara haka kaka" Kaka tace "Ni
fa sai nake ga kamar Maryam ce ta dauke, ke baki ga duk ta rude ba??" Mami ta d'an
yi murmushi bata dai ce komai ba tana gyara ma Heedayah gashinta, Kaka tace "Toh
wllh sai dai ta cuci kanta ba dai Deedayah ba, me yar yarinyar ta tsare mata" Mami
na kallon Heedayah tace "Did you pray today?" Heedayah ta gyada mata kai, Kaka tace
"Toh wai sauran kayan nata fa? Ko in tafi in kwasa da kai na ne?" Mami ta kalleta
tace "Kayan wa?" Kaka tace "Deedayah mana, ko kaya kala uku kadai xan dinga sa mata
kamar fatararru?" Mami tayi shiru, kaka ta mike ta ci gaba da abinda take, Mami
tace "To sai dai na dawo kaka" daga haka ta fita dakin, Kaka ta ajiye tsumman
hannunta tace "Anya wannan Rakiyan na da saiti ma kuwa, ke dai ba don Amadu ba baxa
ki san yarinyar nan ba, ke ba dangin iya tsakaninki da yarinyar nan balle na Baba
to don me xaki dinga nuna fin karfi a kanta??" Kaka ta xauna ta rike ha6a tace
"Ha'an, yau ga fitinanniyar mata ni Fatee, ko dai kanwar uwar Deedayah ce ita bamu
da labari....." Hango ledan da tayi a gefen kofa ya sa ta mike tace "Ji ledan da
gantalallen can ya kawo jiya ko meye a ciki...." Daga haka ta nufi ledan ta dauka
tana leka ciki....

Heedayah ba kyauta bane na kudi ne, do not read without subscription, patronize ur
novelist and read happily with out any thought... It's 300 via Fcmb 3276052019
Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence of payment via WhatsApp 07087865788

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍
Kaka tace "To dama idan ba shi din ba waye xai siyo min Apple manya haka? Ai sai
dai Shureen din" Heedayah tace "Ni bai siyo min ba kaka?" Kaka ta kalleta tace "Ke
kuma a wa? Ae sai dai in d'an yankar maki idan nayi niyya" Karime ce tayi sallama
bakin kofar parlon Mumy ta shiga ciki, Mumy tace "kulle kofar, Sajida ta ga tahowar
ki?" Karime ta kulle kofar tace "A'a wanka ta shiga" Mumy tace "Toh mu shiga daki,
ba wani aiki bane linki xa kiyi min" Karime tace "Toh Hajiya" Mumy ta shigar da ita
bedroom dinta, 'yan kaya ne da basu fi biyar kan makeken gadon dakin, Mumy tace "Ga
su nan basu da yawa" Karime ta fara linke kayan, Mumy ta nemi waje ta xauna tana
latsa wayarta, ganin Karime har ta kusa gamawa Mumy tace "Hajiyar ta fara sake maki
kuwa?" Karime tace "Aa, yau ma tace min tunda Heedayah ta koma gun kaka to idan na
gama aikin da xan yi a bangarenta in yi wucewata can dakinmu, ko don d'an kallon da
taga Ina yi ne yasa ta fadi haka..." Mumy tace "To banda abun ki ba ga TV a nan ba
Karime, duk sanda kike son kallo ki shigo nan kawai, ae xuciyar daban ne, kowa da
irin tasa...." Karime tace "Kuma haka ne wllh, ke kam naki daban ne...." Mumy tayi
shiru jin ringing din waya a parlonta, mikewa tayi da sauri ta fita parlon, Shuraim
ta gani tsaye yana kallon screen din wayarsa dake ring, ya daga ya kai kunne tare
da sallama, Mumy ta juya ta koma dakinta da sauri ya bi ta da ido still answering
his phone call, alama tayi ma Karime da cewa kar ta kuskura ta fito, sannan ta juyo
ta kulle kofar ta dawo parlon ta xauna, Shuraim ya gama answer wayar da yake yace
"Mumy xan d'an fita in dawo" Tace "Toh Allah ya kiyaye, yanxu dai kai baxa ka dinga
sa manyan kaya ba Aliyu, wllh suna maka kyau amma baka so, even if it's just once a
week banda Fridays ka dinga sa wa" Bai ce komai ba ya nufi bedroom dinta, bata san
lkcn da ya nufa dakin ba kawai gani tayi ya bude xai shiga, ta mike da sauri tace
"Me xaka yi ciki Aliyu??" Tuni ya shiga suka yi ido hudu da Karime, sai a sannan ya
juya ya kalli Mumy yace "Gaban mirror xan je" Bai jira tace komai ba ya wuce ciki,
Karime dake tsaye kamar munafuka ta risina tace "Ina kwana yallabai" Ko kallonta
bai yi ba ya nufi gaban mirror ya tsaya, Mumy dai na tsaye ta kasa bin bayansa,
Karime ta fito dakin kamar munafuka tace "Hajiya na gama" cikin daga Mumy tace "Toh
dama wani linki ne tun daxu kamar warce na sa kwalemar dakin gaba daya?" Karime ta
nufi kofa da sauri ta fita, Shuraim ya fito daga dakin, Mumy ta hade rai tace
"Ajiya kayi min a dakin da ka shige min bbu excuse Shuraim??" Yace "Na bar comb
dina a nan ai jiya" Yana fadin hka ya nufi kofa, Tace "Shuraim Ina ga fa gwara in
sallami mai aikin nan tawa kawai, bbu abinda take tsinana min sai magana ma da take
yawan sanya ni, dubi fa wnn yarinyar yaushe ta xo gidan amma na gwammace in sa ta
aiki a kan Sajida, cikin dadin rai xata maka komai fess fess, to ni kuma nayi ta
kiranta kenan uwar dakinta tayi wani tunanin daban? Yanxu ma nasan uwar dakin nata
bata sani ba ta xo, tun safe na kira Sajida ta xo ta min gyaran nan ban ganta ba
shine na kira ita wannan din, matsalar ta daya wnn bata da wani wayewa...." Shuraim
dai bai ce mata komai ba ya bude kofa yace "Sai na dawo" bin sa tayi da kallo har
ya rufe kofar, ta xauna a hankali saman kujera tana naxari.... Mumy ce xaune dakin
Hajiya Sadiya, da Hajiya Baturiya, Mumy tace "Sadiya tunda kin sa6a harka da
Mutumin nan ki lallaba sa ya rage kudin wllh sun min yawa, duka duka nawa ne a acc
din nawa ma tukun? Gaskiya ki yi masa magana a min ragi" Hajiya Sadiya tace "Kinsan
Allah, wllh da dubu dari uku da hamsin ma yace, da kyar ya yrda dubu dari biyu da
hamsin" Mumy tayi tagumi tace "A kan tsinanniyar yarinyar sai in dawo bbu ko sisi a
account dina" Hajiya Baturiya tace "In dai bukata xata biya ba shkkn ba, ke kin
hana mu xuwa gun malam to ba sai ki bari ayi me yiwuwa ba" Mumy tace "Toh shkkn,
amma fa Ina tsoron kuma kar a xargeni ko da wasa a gidan" Hajiya Sadiya tace "Haba
bbu wannan xancen, kaf xa a yashe ki kema har a buge ki, kinga bbu wanda xai xarge
ki" Mumy tace "Toh shkkn sai mun yi waya, yamma yyi bari in wuce gida" Har bakin
mota Hajiya Sadiya ta raka ita da Hajiya Baturiya, ko wanne ya shiga motarsa suka
bar gidan. Kaka na sharan dakinta, Heedayah kuma na saman gado tayi rub da ciki
tana sauraron xancen kaka, Kaka tace "Atoh, Shima Sudess din ai ba son yanda yake
ganina xaune gidan duniya yake ba, kawai dai bbu ynda ya iya ne tunda ba ubansa ya
halitto ni ba, to abinda Allah ba bacci yake ba, sai gashi cikin ruwan sanyi ya
kawo min ke duk da dai ke makauniya ce baki da wani amfani kuma bamu hada komai da
ke ba, to ai dai yafi babu... Wai d'an agwai da bak'in d'a" Heedayah tace "Waye
Sudess din" Kaka tace "Oho haka na ji suna ce masa, jikana ne fa, ni haifi ubansa
Umaru, amma cin haram a wajensa ba a cewa komai, yanxun nan xaki ajiye hakkin ki a
nan kan ki juyo ya handame, to ina dalili...." Bude kofar dakin aka yi Sudais ya
shigo da sallama, Kaka ta saki tsintsiyar hannunta ta mike tace "D'an Halak, yanxun
nan nake xancen ka wllh, nace to Sudais anya lafiya kuwa kwana biyu, ni bai ta6a
min haka ba" Ya mata wani kallo yace "Ke dai fadi gaskiya...." Heedayah tace "Kaka
shine yake cin Haram din?" Juyawa kaka tayi tana kallon Heedayah baki bude, Can ta
nufeta ta dunguri kanta tace "A gidan uban wa muka yi haka da ke? Meye kuma Haram,
a ina kika ta6a jin wnn mugun kalmar" Sudais yace "Toh an ci Haram din, tunda ina
tsoron Allah ai shkkn" Kaka ta juyo tana kallonsa tace "To waye baya tsoron Allah"
ya bude hannu yace "Oho, sannan ni bana cin naman mutane, bana gulman mutane" Kaka
ta xauna gefen gado ta fara matsar kwalla tana share idonta, ya daga Heedayah ta
sauka kasa ya nufi kofa, kaka tace "Dama kar ka sake maido min ita dakina xan
koreta wllh, ga kayanta nan duk a fitar min ba ruwana, maganin ciwon idon ma gashi
nan na nannadesa da Sabuwar atamfata na saka kasan akwati, kowa ma ya xo ya duba ya
kwashe ba ruwana" Sudais ya fita da Heedayah yana dariya kasa kasa, sai bayan da
suka fita Heedayah tace "Is she crying??" Sudais ya fara dariya yace "Yess"
Heedayah ta kwace hannunta kamar xata yi kuka tace "Ni ka kai ni inje ince mata
sannu" Dariya kawai Sudais yake yi, Dai dai nan Mumy ta shigo gidan, ya tsaida
dariyar da yake ya gaisheta tayi banxa da shi ta nufi bangarenta, Heedayah da har
hawaye ya cika idonta tace "Ka kai ni ince mata sannu mana pls" Ya ja hannunta xuwa
parlon Mami yace "Kina xuwa xata maki duka ba ruwana" Shiru Heedayah tayi jin
abinda yace, Mami ta fito daga daki jin sallaman Sudais, suka gaisa, tace "Sai yau
Sudais" yana murmushi yace "Ina shirye shiryen komawa UK ne, in sha Allah weekend
xan wuce" Tace "Ayya, toh Allah ya kai mu lafiya, kaka ta yrda ka fito da Heedayah
kenan" Dariya yyi, ya kai Heedayah gun Mami yace "Ehh ta yadda" Mami ta jawota
jikinta tace "How are you dear?" A hankali Heedayah tace "Fine, Mami a kai ni wajen
kaka" Mami tace "Ohh baki ma son xuwa wajena kenan" Heedayah ta girgixa mata kai,
Mami na murmushi tace "Toh bari ku ci abinci, gashi an gama" Kaka na xaune saman
tabarma hannunta rike da wayarta tana tunanin wanda xata kai ma ya kira mata Baffa
taji dalilin da yasa Sudais ya xo ya dauki Heedayah suka fita, aka bude kofar
Shuraim ya shigo da sallama, Kaka ta fara matsar kwalla tace "Yana shigowa kawai ya
dauketa bbu wani bayani suka fita, ni ban san Inda ma ya kai ta ba" Shuraim ya
tsaya yana kallonta yace "Wa ya dauketa?" Kaka tace "Shine nake son inji ko Umarun
ne ya aikosa ya ci min mutunci haka, tana fa kwance muna hira gwanin ban sha'awa ya
dauketa ya fice bayan ya gama min rashin kunya har da ce min bani da tsoron Allah
ni munafuka ce" Shuraim ya d'an ta6e baki ya nemi waje ya xauna yace "Ina yini?"
Tace "Aa wllh ba lafiya ba, ya fi minti talatin fa da fitar min da Deedayah har
ynxu shiru" Yace "Toh amfanin me take maki idan tana nan din?" Kaka ta mike da
sauri tace "A'a ka iya bakin ka, bata fi min ku ba ma aka ce maka, duk da bata gani
kuma bbu dangin iya balle na baba ta fiye min kai wllh" Yace "Toh sai me" tace "Sai
bakin ciki ya kashe ka" Junaid ne ya shigo parlon da sallama, Kaka ta washe baki
tace "Sannu da xuwa Junaidu, ashe kana hanya" yace "Ehh kaka" ta rike ha6a tace
"Wannan zungureren babyn roban duk na Deedayah ne?" Murmushi yyi ya ajiye ledan
Babyn hannunsa, Kaka tace "Toh ai dama sai dai kai din, ko Amadu" Tunda Shuraim ya
Kalli ledan Babyn ya dauke kansa, Kaka tace "Wannan Mutumin fa na ce ya siyo mata
amma kaga bai siyo ba tunda ba wai yana da Imani bane" Shuraim ya mike ya fice daga
dakin, Junaid ya bi sa da kallo, kaka tace "Ae kaga irinta, bai siyo ba kuma yana
hassada, da ka sani biyu ka siyo ka basa daya tunda bamu san ko bakin ciki yake
mata ba" Junaid yyi murmushi yana kallon kaka...... Bayan Magrib Shuraim ya shigo
parlon Mumy don rabonsa da ita tun da safe da ya fita gidan, bbu kowa parlon nata
ya leka bedroom ya dai ji alamar tana bandaki ya dawo parlon ya xauna ya fiddo
wayarsa yana dannawa, wayarta dake jikin caji ne yyi haske alamar kira, ko
vibrating wayar bai yi ba sai haske, yana dai xaune har wayar ya katse, aka kara
kira, sai da aka kira na hudu sannan ya mike ya nufi Inda wayar yake ya duka ya
dauka yana kallon me kiran nata, ya shiga text msg din dake saman wayar, cikin few
minutes ya karanta content din, sai kuma ya ajiye wayar ya nufi kofa ya fita ya
kulle kofar, a hanya ya hadu da Rabi'ah tace "Ya Shuraim Mumy tana daki?" Yace "Ba
daga nan nake ba" daga haka ya wuceta ya wuce bedroom dinsa. Mumy na fitowa
parlonta ta nufi wayarta da sauri ganin yana haske alamar ana kira, ta daga ta koma
daki ta kulle kofar tace "Yi hakuri wllh na shiga wanka ne, ya ake ciki?" Ta d'an
yi shiru sannan ta Kalli agogo tace "Xuwa dai karfe dayan dare shine dai dai" Tayi
murmushi tace "Toh shkkn sai mun yi magana...." Daga haka ta katse wayar ta xauna
gefen gado tana wani murmushi.... Mami na xaune parlon Abba da Heedayah sai
Rabi'ah da Khadijah, aka bude kofar parlon Kaka ta shigo ba ko sallama tace "Ni fa
har yanxu ba a shigo min da Deedayah ba lkcn baccinta har ya wuce, idan kuma an
canxa wajen kwananta ne sai a sanar min" Bata jira cewarsu ba ta daga Heedayah ta
nufi kofa tana kallonsu Rabi'ah tace "Ku kuma gantalallu ga fura can da Junaidu ya
kawo min na rage maku" daga haka ta fita, Mami gaba daya bata ji dadin xuwan da
kaka tayi ta tafi da Heedayah ba, don ynxu goma ma yyi ta xata kakan tayi bacci ne
ta wuce da Heedayahn part dinta don tace xata sha tea, Abba yyi murmushi bai dai ce
komai ba amma ya gane Mami wasn't happy, Mami ta mike tace "Toh sai da safe" Yace
"Allah ya tashe mu lfya" Su Rabi'ah ma suka yi mata sai da safe ta fita parlon.....

Toh haka Allah yayi da ni yau..... 🌚

Heedayah isn't free.... It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via WhatsApp 07087865788

Shuraim na xaune bedroom dinsa hannunsa rike da wayarsa yana dialing number wani
colleague dinsa, bayan sun gaisa Shuraim yace "You called bana kusa Najeeb" Bayan
few seconds Shuraim yace "Ehh na sani, I will be there soon in sha Allah" Daga haka
suka yi sallama ya katse wayar, mikewa yayi yana kallon agogo dake nuna karfe goma
da few minutes ya fita dakin, kitchen ya fara shiga ya hada shayi sannan ya fito ya
nufi part din Mumy, duk wutan parlon a kashe yake da na dakinta, daga can uwar daka
cikin muryar bacci tace "Waye wannan?" Yace "It's me Mumy, kinyi bacci ne?" Tace
"Toh me xan jira" yace "Okay, Xan wuce hospital ne ynxu in sha Allah" Tace "Okay
are you spending the night there?" Yace "No xan dawo anjima" Ta mike xaune da sauri
tace "Karfe nawa yanxu da xaka je asibiti har ka dawo, why not spend the night
there, ni bana son tafiyar daren nan gaskiya" Ya d'an yi shiru sannan yace "Toh
shkkn sai da safe" Tace "Allah ya tashe mu lafiya, pray before leaving" yace "In
sha Allah" daga haka ya fita parlon ya kulle mata kofa..... Abba ya gani xai shiga
bangarensa, Abba yace "Ohk Baka tafi ba?" Shuraim yace "Yanxu xan wuce" Abba yace
"Alright sai da safe" Shuraim yace "Allah ya kai mu lfya Abba" daga haka Abba ya
shiga part dinsa, Shuraim ya xauna parlor ya gama shan shayin hannunsa ya kai cup
din kitchen ya dauko makullin motarsa ya fita gidan, sai bayan da Mai gadi ya bude
masa gate ya bar compound din ya tuna da rigar sanyinsa don garin da sanyi kuma ko
kadan baya son sanyi, yyi parking a nan kofar gidan ya sauka motar ya koma cikin
gidan, bedroom dinsa ya tafi ya dauko rigar sanyinsa sannan ya dawo parlor, har ya
nufi kofar fita sai kuma yayi hanyar dakin kaka ya bude kofar, a kashe ya ga wutan
dakin, ya danna hasken wayarsa that's so dim yana kallon dakin, Kaka na kwance
hannunta rike da carbi tana bacci har da minshari, ga mamakinsa idon Heedayah biyu
tana kwance lamo saman gadon, ya karasa cikin dakin yana haska fuskarta, mikewa
tayi xaune jin motsi, a hankali tace "Mami" shi dai yana tsaye yana kallonta, Ta
sake cewa "Mamii" Kaka ta gyara kwanciya tace "Kya ci kanki" daga haka ta ci gaba
da baccinta, tuni Shuraim ya kashe hasken wayar sai da ya ji ta ci gaba da minshari
sannan ya kara haska dakin, Heedayah dake xaune fuskarta kamar xata yi kuka cikin
sanyin murya tace "I want to take tea plsss" Juyawa yyi ya fita dakin ya kulle
kofar a hankali, sannan ya bar gidan, slowly yake driving har ya bar anguwar gaba
daya. Tun tafiyar Shuraim Heedayah bata koma ta kwanta ba, har da d'an hawayenta
tana gogewa da bayan hannunta, duk motsin da tayi sai kaka ta gyara kwanciya tace
"Kya ci kanki" ita dai ba sanin nufin Hausan ma tayi ba, tana xaune har sha biyu
saura ta ji an bude kofar dakin.... Sai kallon direction din take ta ji an kamo
hannunta, ta mike tsaye tana tattaba hannun tace "Mami ke ce, I want to take
tea..." Kaka ta tabe baki ta gyara kwanciya tace "Kya ci kanki dai" fitar da ita
aka yi dakin still holding her hand, ba musu take tafiyar har sannan tana laluba
hannun da ya riketa, sanyin da taji na shiga jikinta sbda yar rigar jikinta yasa ta
fixge hannunta tace "Ina xa mu je??" lkci daya aka dauketa xata yi ihu aka rufe
bakinta gamm, bata kuma yunkurin yin ihun ba, next thing taji an saka ta a mota an
rufe, motar na fara tafiya ta kwala ma Mami kira, nan ta dinga ihun Mami da karfi
amma ba a ce mata komai ba, ta gaji tayi shiru, can ta fara laluba cikin motar har
ta ji ta ta6o me tukin, a hankali tace "Who are you??" Jawota yyi ta fado kansa ya
maida ta front seat, kin sake sa tayi ta kai fuskarta jikinsa perceiving his
perfume, yyi parking ya dau goran ruwa ya bude ya kai bakinta, rike goron tayi
hakan ya sa ya sakar mata, ta d'an kurbi abun ciki, bata sauke goran ba sai da ta
shanye content din ciki tas, shi dai driving dinsa kawai yake slowly, ta kai hannu
tana ta6a sa bayan ta ajiye goran tace "Who are you?" Bai tanka ta ba, tace "Kai
Yaya ne?" Still ba a ce mata komai ba, ta kara cewa "Yayah?" Nan ma shiru, driving
kawai yake avoiding check points a hanya, har dai ya isa wani layi, kallon gate din
layin dake kulle ya dinga yi, can ya gyara parking ya kashe motar yana kallon
Heedayah, lamo tayi kan kujeran idonta rufe har ta fara bacci, ya bude side dinsa
ya fita ya xaga xuwa inda take ya bude motar ya daukota ya daurata saman shoulder
dinsa, ta bude ido a hankali sai kuma ta kara lumshewa, ya shiga layin ta karamin
gate, har dai ya isa bakin wani gate ya tsaya ya ciro makulli aljihunsa ya bude
gate din da hannu daya ya shiga sannan ya kulle gate din, ginin bungalow ne me
girma, ya bude parlon shiga gidan da makulli ya shiga, yana bin ko ina da kallo ya
wuce daki, bbu bedsheet saman gadon da ya d'an yi kura ya bude press ya fiddo wani
xanin gado yayi spreading dinsa with one hand ya kwantar da ita gently, bude ido
tayi sai kuma ta mike xaune da sauri tana hade kafa tace "I want to ease my self"
tsayawa yyi yana kallonta kamar bai gane turancin da tayi ba, ta fara kokarin sauka
daga kan gadon tace "I want to urinate" ya kalli kofar bathroom dake cikin dakin
sai kuma ya kama hannunta suka wuce ciki.... Bayan sun fito tana rike da hannunsa
tace "Shikenan mun bar kaka a can gidansu Mami, she will be looking for me faaa" Ji
tayi ya kwantar da ita saman gado, ta yi rub da ciki ta lumshe ido, bude idon tayi
da sauri jin an daga rigarta tace "Yayah" Lkci daya taji xafin shigan alluran xata
tashi a tsorace ya ki barinta hakan yasa ta fashe da kuka tana kwala ma Abba kira,
yana gamawa ya mike ya kashe Ac dake dakin ya kunne fan ya kashe wutan ya fita
dakin ya kulle ya bar ta tana kuka. Tun karfe daya saura Mumy ke xaune dakinta
idonta kyam, ga wayarta a hannunta, wayar ne yyi haske ta daga ta kai kunne da
sauri, lkci daya ta mike tace "Har kun taso, to bari in je in bude gate din" tana
fadin haka ta katse wayar ta mike ta tafi gun window tana kallon tsakar compound da
yayi tsittt, a hankali ta bude kofar dakinta ta fita har xuwa main parlor, sai da
ta gama kare ma parlon kallo sannan ta nufi kofa ta bude a hankali ta fita, gate
biyu ne gidan, daya a baya, daya kuma a gaba, sai dai an fi shekaru biyu ba a bude
gate din bayan ba, can Mumy ta nufa tana yi tana dube duben tsakar gidan duk da
tasan kowa na gidan na bacci har masu gadi, tana isa gate din taji sa a bude, she
was so very suprise, ta leka wajen gate din, bbu kowa layin sai street light da ya
haska ko ina, to wa ya bude gate din, ko dai dama a bude yake all this while ba'a
ta6a lura ba, but this is suprising, jawo gate din tayi a hankali amma bata yi
jamming ba ta juya da sauri ta koma cikin gidan.... A parlor ta ci karo da kaka,
gabanta yyi wani irin faduwa, Tayi hanyar kitchen da sauri pretending kamar daga
kitchen din ta fito, Kaka da tayi kicin kicin da fuska tace "Maryam kina ganin
wannan kishiyar ta ki ko? Halan bata sanni bane bata san halina ba, wllh xan tara
mata jama'ah idan bata fita hanyar Deedayah ba a gidan nan, meye xata bi dare ta
shigo ta dauke ta kamar ita ta tsinto mana ita, wai ma uwar me ta hada da Deedayan
nan ne ma tukun, farkawa fa nayi naga bbu yarinyar an dauketa, to wllh ki taso min
Amadu inji ko shi ke sa ta raina ni daga shigowarta gidan ko sati biyu ba ayi
ba...." Mumy tayi kasake tana kallon kaka, can dai tace "Ban gane ba kaka, yarinyar
bata cikin dakin ki ne yanxu?" Kaka tace "Leka ki gani mana, xan maki karya ne?"
Mumy tace "Aa to ki shiga bangarenta ki dauko ta kaka, wnn ai rainin hankali ne,
ikon da take nunawa kan yarinyar ai ya fara wuce gona da iri" kaka na jin haka ta
tafi bangaren Mami cike da kwarin gwiwa ta bubbuga kofar, ta bubbuga yyi sau hudu
kafin Mami ta bude, Kaka ta wani sha kunu tace "Ina yarinyar da kika dauke a dakina
Rakiya?" Mami tace "Yarinya kuma, wace yarinyar kaka?" Kaka ta kalli Mumy tace
"Kinji ko Maryam, bata ma san yarinyar da ta dauke ba, to ni baxan biye maki ba da
girma na, Deedayah xaki fiddo min" Mami tace "Heedayah da kika tafi da ita daxu
muna parlon barrister?? Ae ba a kawota nan ba" Kaka ta gwalo ido tace "Toh ni kuma
bata dakina yanxu, ban ganta ba wllh" Kasa cewa komai Mami tayi tana kallon Kaka
baki bude, kaka ta saki salati ta tafi bangaren Abba da sauri shi ma ta tado sa,
yana fitowa tace "Amadu kai ka shigo ka dauke Deedayah dakina muna bacci?" Abba na
kallonta da mamaki yace "Heedayah kuma, ba xuwa kika yi daxu kika tafi da ita ba"
Kaka ta kara Rafka wani uban salatin ta daura hannu a ka tace "Wllh farkawa nayi
ban ganta a dakin ba Amadu, don Allah a rufa min asiri a dudduba ko taje ta shige
wani wajen ne ba a sani ba, kasan makaho" Kaf gidan bbu inda ba a duba ba amma bbu
Heedayah bbu alamarta, su Rabi'ah duk an tasosu su ma, Mumy da hankalinta ya fi na
kowa tashi ta rakube kitchen tafara kiran waya, ana dagawa tace "Kai oga Salahu ku
dakata an nemi yarinyar ko sama ko kasa bbu a gidan ba a san wanda ya dauketa ba,
ku dakata xan kira ku, ku dakata tukun" Bata jira cewarsa ba ta katse wayar tana
xufa.... Duk iya duban da xa ayi a gidan nan anyi har tare da masu gadi amma ba a
ga Heedayah ba, daga karshe kuma aka ga second gate din gidan a bude, kaka ta rushe
masu da matsanancin kuka tace "Wayyo na shiga uku yanxu cewa xa ayi tayi a dakina
ta 6ace, don girman Allah a rufa min asiri a nemota, idan hukuma ma suka ji haka ba
kyaleni xa su yi ba, duniya duk a dauka ace na sace makauniya, wllh farkawa nayi
naga bbu ita sai pillow...." Abba dai na tsaye ya ma kasa cewa komai, ya rasa
tunanin da xai yi but xa a iya ganin tashin hankalin fuskarsa, likewise Mami dake
ta kallon gate din da ke bude, Mumy kuwa salati ta dinga yi tana cewa "Anfi shekara
uku ba a bude kofar nan ba, a ina ma aka samo makullin aka bude?? Innalillahi wa
Inna ilaihi raji'un.... does it mean we are not longer safe cikin gidanmu kenan,
waye xai dauke wnn yarinya ni Maryam" Mami tayi mata wani kallo sannan ta shige
cikin gida, kana ganinta kasan she is not going to let this, daren ranan nan dai
bbu wanda ya rintsa a
gidan, Kaka kuwa ta lula cikin anguwa neman Heedayah, bbu yanda Abba bai yi da ita
kan kar ta fita dare ne amma taki sauraran kowa tayi ficewarta tana kuka... Gaba
daya Mumy ta rasa irin tunanin da xata yi, amma hankalinta ya fi na kowa tashi, can
sai ga kaka ta dawo wujiga wujiga da takalma da Hijabi a hannu wai karnuka sun biyo
ta... Karfe hudu Shuraim ya shigo gidan ta dalilin kiransa da Abba yyi, Kaka ta
fashe masa da wani sabon kukan ta rikosa tana cewa "Wllh tare muke kwance Shureen
wai farkawan da xan yi naga bbu ita, an sungumeta...." Shuraim dai ya kasa cewa
komai sai kallon kakar tasa yake, can ta sake sa ta koma gun Abba tana Kuka wai ta
shiga uku kar hukuma su daure ta, Shuraim ya jingina da bango a hankali ya rungume
hannunsa, he looks disturbed also, Ana kiran sllh dama Mami ta bar gidan.... Bayan
an idar da sllh sai ga Baffa da Sudais sun shigo gidan, Baffa ma is speechless just
as his brother, Kaka dai tun hawaye na xuba har ya daina xuba yanda take kukan kai
kace yarinya ce, Sudais ko karasowa cikin parlon ma ya ki yi yana tsaye daga bakin
kofa, at the end kawai ya fice daga gidan gaba daya, Baffa na kallon kaka yace "Don
Allah kiyi hakuri Baaba, in sha Allah xa a ganta, bbu abinda xai sameta" cikin
rawan murya kaka tace "Toh kai sai kayi fatan abu ya sameta dama? Wllh wanda ya
saceta cikin gidan nan yake, dama kaf gidan banda ni da Rakiya bbu me sonta, ko shi
Amadun bamu san xuciyarsa ba" Abba ya kalleta ta gefen ido bai dai ce komai ba,
Baffa yace "Da karfe nawa kika lura bata dakin?" Kaka tace "Daya saura minti goma,
Ina fitowa parlo kuma Maryam na fara sanar ma cewar ban ga Deedayah ba" Abba ya
kalli kaka yace "A ina kika ga Maryam din" Mumy ta amshe da sauri cike da karfin
hali tace "Na fito shan ruwa kitchen muka hadu" Abba ya kalleta, ya dauke kai ya
sake kallonta sai kuma ya mike ya wuce bangarensa, Shuraim dai kansa na kasa, Mumy
na daga xaune amma duk cikinta ya hautsine da kyar take xaune har lkcn, ba a dau
lkci ba Abba ya fito yana kallon Baffa yace "Mu tafi Dr" Mikewa Baffa yyi, kaka ma
ta mike da sauri rike da hijab dinta tace "Ae da ni xa aje duk Inda xa a je tunda a
dakina komai ya faru, salon in ki bin ku a xargeni ace dama ni na sace ta, gwara
duk inda xa ku in bi ku" Sai bayan fitarsu Mumy na kallon Shuraim cikin karfin hali
tace "Aliyu wa xai dauke yarinyar nan, wllh ni dai ban san komai kan wnn lamarin
ba, naga kuma kowa kallona yake, dama ni na dauketa baxan damu ba, amma wllh ba ni
bace, kaga kallon da barrister yyi min irin kamar da sa hannuna gun 6atar ta"
Hankali tashe take maganan, shi dai Shuraim kansa na kasa, can ta mike ta wuce
bangarenta, yana rike da car key dinsa ya bar parlon ya tafi gun motarsa dake
waje.... Hajiya Sadiya da kanta kasa cewa komai tayi, Cikin rawar murya Mumy tace
"Sadiya ni fa ban ta6a shiga rudani irin wnn ba, sannan kuma abun mamaki gate din
bayan ma a bude na samesa....." Sadiya ta d'an yi shiru snn tace "Shuraim na gidan
kuma koh?" Mumy tace "A'a baya nan, tun tara da wani abu ya tafi night duty ba sake
shigowa gidan ba sai Asuba uban ya kirasa ya dawo..." Sadiya tace "Kaiii, wnn
lamari akwai lauje cikin nadi....." cike da damuwa Mumy tace "Ni ki saurareni
Sadiya, ta ya xan wanke kai na cikin lamarin nan, wllh sai kinga, ko magana xanyi
sai inyi ta rawan baki... Ni nasan kowa ma ni yake xarga, ni kuma ba a ma kai ga
xuwa dauke yarinyar nan ba aka nemeta aka rasa.... Ga dai abun farin ciki amma bbu
daman farin cikin tunda ni ake xarga" Sadiya tace "Bari xan kira ki yanxun nan"
daga haka ta katse wayar..... Cikin bacci Heedayah ta ji hannu a kanta, ta bude
idanuwanta da kyar ta kamo hannun tace "Mami I want to ease my self"

For those sharing and reading this book for free I know I can't stop u from doing
so, but that's ur business, burden, and cup of tea, the book is just for a while,
while the above mentioned is for everr, but do not edit my write up plss, leave it
the way it is and read....😇

Heedayah is 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Abba yyi kasa da murya yace "Noo Rahinah, ba sai an kai ga haka ba, this is almost
a family issue, ni nasan me xan yi, in sha Allah Heedayah will be back home...."
Mami ta katse sa ta mike tace "Family issue barrister? ni fa I've already made up
my mind, allow me to do what I am suppose to do, matarka knows Heedayah's
Whereabout, ta san komai a kan bacewar yarinyar nan, so why do we all have to
pretend, sorry to say, ba ruwana da wani family issue I am doing my work tunda kai
baxa ka iya ba, idan 'yan sanda suka je suka daukota they will interrogate her ta
fada masu inda aka kai 'yar mutane, period!!!" Abba ya mike yace "But you can't
look into my eyes and tell me xaki sa ayi arresting matata Rahinah" Mami tace "I am
sorry barrister, I've got no other option, yanayin aikin ne haka kai ma ka sani,
nima gobe idan nayi abinda ya cancanci ayi arresting dina, allow them to arrest
me..." Kallonta kawai yake, Kaka dake can wani gefe cikin haraban police station
din tare da Baffa ta fyace majina tace "To ni dai yunwa nake ji, kar wata cutar
taje ta kamani a banxa in cuci kai na, ko 'yar yagwat da nama ai ya kamata ku siyo
min in xauna in ci daga nan, shi ciki ina ruwansa da 6atar mutum, Karfe takwas fa
ake nema yanxu ban karya ba.... su kuma wa encan xancen me suke har yanxu kamar
6atar yarinyar bai damesu ba?? Ai ko d'an mage ne ya 6ata sa nuna damuwar su, amma
tun daxu suna ta hira ka duba fa" Baffa ya kalli Mami da Abba bai dai ce komai ba,
Kaka tace "Su ma shegun 'yan sandan ca suke 'yar kaza ce ta 6ata da baxa su maida
hankali ayi abinda ya kamata ba, ni ba ruwana shiga xanyi in fada masu gaskiya...."
Baffa ya dakatar da ita yace "Xa mu je can gidan ne dasu ynxu, yanxu duk xa mu
wuce..." Kaka tace "Atoh gwara dai mu je din, ni dai tunda na biyo ku ai bbu wanda
xai xargeni dai ko?? ita kuma wancan matar dake ta shiga da fice kamar Yan uwanta
ne 'yan sandan Allah ya sa...." Shiru tayi ganin Mami da take magana a kai ta nufo
su, Kaka tace "Ya ake ciki Rakiya? Ni fa hakurina ya soma karewa, basu da taimakon
da xa su mana ne, in je gun Ta salla?" Mami tace "A'a xa mu je gida ynxu da 'yan
sandan kaka, iya bincike ya nuna bbu wanda ake xargi kan bacewar Heedayah sai
Hajiya Maryam...." Kaka ta wani tabe baki tace "Lallai!!! To da baxa a xargeta ba?
muguwa ce fa, a jiyan da daddare ma daga waje naga ta shigo bansan uban me taje yi
waje tsakar dare ba.... Idan ba rashin gaskiya ba menene wannan din??" Kaka ta
fashe da kuka sosai tace "Kilan lkcn ta mika Deedayan ta dawo... Dama tun ba yau ba
kowa yasan Maryam bata da Imani, Kuma axxaluma ce, akwai wata mai aiki da tayi da
dadewa sai da ta kusa kashe mata ido daya, da kyar Amadu ya shawo kan kess din,
sannan ta ta6a aiken Mai gadi mota ta kwashe gantalalle a titi ya karairaye, shi ma
dai Amadu ya shiga ya fita aka rufe kess din, sannan kwanaki shi ma da dadewa taje
gidan kitso tasu ta hado su da matar wani babban mutum, Maryam ta tattakure ta
sharara ma mata mari, in takaice maki dai awowin Maryam uku a seff, da kyar Amadu
ya shiga ya fita aka yi belinta sannan ya kashe kess din, Kinga kuwa ai Maryam
takadiriyar mace ce, mu dai kawai muna xaune da ita ne saboda su Shureen" Mami dake
ta sauraronta tace "Yanxu ma ita xa a je daukowa don ita ce first suspect kan 6atar
Heedayah...." Kaka ta saki kabbara da karfi tace "To da pa?? ai dama ita ce ni dai
tunda ba a xargeni ba Alhmdllh, a xargi kowa ma, har shi Amadun...." Mami ta juya
ganin Yan sanda biyu sun fito ta nufi motarta da su, kaka ta bi bayanta da sauri
tana cewa "To dama idan ba ke ba wa xai tsaya kan maganan nan, Amadu dama tun yana
karami wani solobiyo ne, lauyancin ma Allah ne ya basa ba wayonsa ko dubara ba" duk
wannan abun Abba na tsaye daga inda yake yana kallonsu, haka ma Baffa da ya ki cewa
komai, Baffa ya sauke ajiyar xuciya ya nufi d'an uwan nasa.... Heedayah ta daga kai
jin an amshi cup din shayin da take sha, tace "Ban shanye ba ai tooo" Yana rike da
hannunta suka fito parlor, tace "Tell me who you are.... Yaya that gives me
chocolates? Or Yayana, yayana din Farida?" Jin bai bata amsa ba, ta tattaba
hannunsa tana turo baki tace "Ka ji mana, tell me" Jan bakinta taji anyi ta kai
hannunta da sauri tace "Ouchh, me na yi?" Bai ce mata komai ba, ta warce hannunta
tace "Nasan waye" ya tsaya yana kallonta, can ya durkusa kusa da ita ya jawota dabb
da shi ya kai bakinsa kunnenta, murya kasa sosai kamar me rada yace "Waye?" Tayi
shiru kamar tana son gane muryan, can ta fara komawa baya a hankali tace "I don't
know you" jawota yyi ta fasa ihu tace "Maminaa" ya dauketa kamar yar baby suka fita
parlon har kofar gida inda yyi parking, front seat ya bude ya sata ciki ya daura
hannu saman lips dinsa yace "Shiiiii" he could see how afraid she is, hawaye ya
kawo fararen idonta tace "Plss take me back to Mami, ban san ka ba" rufe motar yyi
ya tafi ya sa ma gidan makulli sannan ya dawo ya hau motar ya bar layin... Wayarsa
ne ya fara ring, ya kalli wayar ganin me kiran sa ya samu waje me kyau yyi parking
sannan ya dau wayar ya fita waje don amsa kiran, bayan few mins ya dawo cikin motar
ya d'an kalli Heedayah sannan ya ci gaba da driving dinsa..... Rirrikesa Heedayah
tayi jin alamar wucewa xai yi ya bar ta bayan ya saukar da ita daga motar, cikin
kuka tace "Don Allah don't leave me ka kai ni wajen Mami da Abba first, plsssss..."
Ya cire hannunsa daga nata ya koma gun motarsa walking very fast, within a twinkle
of an eye ya bar anguwar... Heedayah ta fashe da kuka sosai jin tafiyar motarsa ta
dinga kwala ma Abba kira tana yarfe hannu, Mumy ce ta fito daga cikin babban gidan
a rikice bayan kiran da Abba yyi mata yace ta bar gidan, hijab ne har kasa a
jikinta ko kayan kirki bata sa ba da makullin mota a hannunta, tsabar rudewa
mancewa tayi da motar a compound ta fito bakin gate da kafa, karo ta kusa ci da
Heedayah dake kuka sosai tana laluba inda take, Mumy ta ja baya a d'an tsorace tana
kara kallonta, lkci daya ta saki salati ta riko hannunta tace "Kee wa ya ajiye ki a
nan, wa ye ya dawo dake???" Heedayah ta dakatar da kukan da take jin muryarta, Mumy
na kalle kalle kamar munafuka tace "Nace wa ya ajiye ki a nan?? Ina yake???"
Heedayah dai bata ce komai ba sai shessheka take, Mumy ta kwalo ma mai gadi kira a
rikice, ya fito da gudu yana amsawa, tace "Isiyaka wa ya ajiye yarinyar nan bakin
kofa, daga ina ta fito?" Ya matso da sauri yana kallon Heedayah da kyau yace "Ikon
Allah ba ita ake nema ba Hajiya?" Mumy ta daka masa tsawa tace "Cewa nayi wa ya
ajiye ta a nan kana tambayata tambayar banxa, waye ya dawo da ita" Yace "Wllh wllh
Ina ciki Hajiya ban san daga Inda ta fito ba, Banda yanxu da kika kirani ni ban san
ma akwai mutum a nan ba" Mumy ta fashe da kuka sosai tace "Kai shaida ne isiya
yanxun nan na fito na ganta tsaye bakin gate din nan, ni ban san daga Inda ta fito
ba, ban san wa ya ajiye ta ba" Isiya ya rike ha6a yace "Ikon Allah, to waye ya
maido ta kuwa?" Mumy na goge idonta tana kalle kalle kamar munafuka ta marairaice
tace "Amma kaga ba lallai kowa ya yrda a bakin gate muka ganta ba isiya... Ni dai
kai ne shaidana fitowata kenan daga cikin gida na ganta, yanxu ka shiga da ita ciki
ni xanje can in dawo, maxa ka kai ta ciki" tana fadin haka ta kara gaba da sauri
tana hade hanya, isiya ya bi ta da wani kallo kafin ya ta6e baki yace "Da dai ba a
san ki bane Hajiyaa, Lallai na yarda Allah na fitar da me kyau cikin mara kyau...."
Yana fadin haka ya girgixa kai ya kama hannun Heedayah ya shigar da ita cikin gidan
yace "Allah dai ya kubutar dake yarinya, da yake baki da hakkinta sai gashi Allah
macecin ki, irinta macecin ki" sai da Mumy ta tabbatar ta shiga adaidaita sannan ta
kira Abba, yana dagawa ta fashe masa da kuka sosai tace "Wllh barrister ka ga gashi
an maido yarinyar nan kamar daga sama, ni dai ban san komai kan lamarin nan ba ban
san wa ya dauketa ba ya sake maido da ita yanxu, Ina fitowa bakin gate muka ci karo
da ita wllh wllh iyakar gaskiyata nake gaya maka isiya ne shaida na, tare muka
ganta rakube gate tana kuka, Mu dai bamu san ta yaya ba" Abba da ke xaune mota tare
da Baffa suna dawowa gida da farko kasa ce mata komai yayi, can dai yace "Yanxu ke
kina ina?" Tace "Ga ni a adaidaita xan tafi gidan Aunty Zuwaira" yace "Toh ki tafi
can din, Heedayar na gida yanxu haka?" Mumy tace "Wllh kuwa, tana can na baro ta
tunda kace in bar gidan" Abba bai ce komai ba ya katse wayar, Abba ya jinginar da
kansa da kujeran motar yyi shiru, Baffa da ke jin duk yanda suka yi da Mumy a waya
da yake a hands free Abba yasa, ya sauke ajiyar xuciya, Abba yace "Ba Maryam ta dau
yarinyar nan ba...." Baffa yace "Ba ita ta dauketa ba, amma she knows everything
about it...." Abba ya kallesa yace "Not much, matata ce na san when she is lying
and when she is not, nasan Maryam bata son yarinyar nan xa ta ma iya sawa ayi
abinda ya fi dauke Heedayah, but this time around ba ita bace, I will have to go
deep into this matter" Baffa dai bai basa amsa ba.... Salatin da kaka ta saki bakin
kofar parlor ya sa Mami ta karaso da sauri 'yan sanda biyu na biye bayanta,
Heedayah suka gani xaune saman kujera a parlon ga Karime da Sajida da su Rabi'ah
duk a parlon, Shuraim na tsaye daga wajen dinning ya rungume hannunsa, Kaka tace
"To ni dai Allah ya isa cutan hanjin ciki na da aka sa nayi na bar su da yunwa basu
ji ba basu gani ba, tunda uwata ta haifeni ban ta6a kai wa karfe tara ban karya ba
sae da wnn yarinya ta 6ata, gashi yanxu har wani jiri nake ji kamar xan kwanta
gadon asibiti...." Bbu wanda ya kalli kaka, Mami ta karasa gun Heedayah dake xaune
tayi shiru hawaye bushe a idonta, kafin tace komai daya daga yan sandan yace ce
"Ita ce yarinyar?" Mami ta mike so surprise ta girgixa kai tace "Ita ce, she is the
one...." d'an sandan yace "We are going back to the station with her, but before
then a gidan nan suspect da xa mu dauka take??" Mami tace "Ehh nan ne" Shuraim ya
kalli Mami ta gefen ido, Kaka ta nufi bangaren Mumy tace "Mu je in kai ku dakinta,
ko
ba Maryam ba...." Yan sandan suka bi bayanta xuwa bangaren Mumy, bbu kowa parlon
da daki da ma bathroom, Kaka har da duba karkashin gado da cikin press din kaya, ta
dudduba bayan labule, bata yarda ba sai da tasa suka dage katifar gadon, Kaka na
hada xufa tace "Ta tsere, kaga ta sa an maido da yarinyar ta gudu, to Allah ya isa
wahal da mu da tayi, Allah yyi mata abinda tayi mana...." Yan sanda suka fita
dakin, nan dai suka dudduba sauran dakunan cikin gidan amma bbu Mumy, Kaka na
kallon Shuraim tace "Toh Shureen ga uwarka dai ta dawo da Deedayah ta gudu...."
Calmly yace "Ita tace maki ita ta dauketa??" Kaka ta nufesa da sauri tace "Kar ka
min rashin kunya, kana min xan sa 'yan sandan nan su casa min kai yanxun nan su
tafi da kai caji ofis" Khadijah ta sunkuyar da kanta tana dariya kasa kasa, Kaka
tace "Atoh, ka yi mana, ya naji kayi shiru, xageni mana" Su kansu 'yan sandan sai
da suka yi murmushi, Mami dai ko kallon kaka bata yi ba, Yan sanda suka dau
Heedayah tare da Mumy xa su koma station, kaka ta dauko Hijab ta bi bayansu, Mami
na kallonta tace "Kaka kiyi tsayawarki ki k'arya mana...." Kaka tace "Ce maki nayi
yunwa nake ji, a fara abu da ni kuma sai a ki karewa da ni" Mami bata kuma ce mata
komai ba ta bi bayan 'yan sandan suka fita, Kaka na biye da su da sauri. Hajiya
Sadiya ta rike ha6a tana kallon Mumy da tayi tagumi tace "Ikon Allah, wllh wanda ya
dauketa a gidan yake, bbu shakka ya gano komai ne yyi hakan, kuma ba kowa nake
xargi ba illa Shuraim" Mumy ta dago da sauri tace "Shuraim?? Shuraim dai, A'a
Shuraim baya ma gidan hakan ya faru, yana can asibiti" Hajiya Sadiya tayi wani
dariya tace "Dai dai ma kenan tunda baya gidan, wato shine ya bi dare ya sadado ya
dauketa...." Mumy ta mike tace "Haba Shuraim baxai ta6a yin haka ba, Bai san ma
komai kan wannan plan din namu ba, to idan ma ya sani Allah na tuba meye hikimar
dauketa balle bai sani ba, he has nothing to do with the blind girl a gidan, ko
kallonta ma shi bai yi, Yan gidan ma yaushe ya samu lkcn yi masu magana balle
makauniyar? Bai ta6a kallon inda take ba ma" Hajiya Sadiya tace "Wllh ko rantsuwa
nayi baxan yi kaffara ba Shuraim ne ya dauke yarinyar nan, idan ma xaki yarda ki
yarda, wnn d'an naki baki san kyar yake kallon ki ba ko? to wai idan ba shi ba
Aljanine xai shigo ya dauketa? Ke ki duba lamarin nan fa, sannan kince a bude kika
ga gate din bayan gidan ba wai 6allawa aka yi ba, waye yasan wani inda makulli
yake?? Gwara ki ajiye wnn batun na cewa Shuraim baya kula kowa a gidan, Kuma in har
yaron nan naki na gidan nan bbu abinda xa a yi ma wannan yarinyar...." Mumy dake
tsaye ta kasa cewa komai tace "Shuraim Kuma, Shuraim????" Hajiya Sadiya ta ja tsaki
tace "Ai sai ki yi kuma, kema kinsan duk shirunsa shegen wayo ne da shi snn kinsan
he is never in support of anything bad.... Tsaf shi xai dauketa sannan ya maidota
bayan yaga duk an watse a gidan" Mumy dake xufa ciki da waje tace "To kuwa xan ci
ubansa la'ada waje, xan ji ko shi ya haifeni ko ni na haifesa" Hajiya Sadiya tace
"Atoh wnn dama dai ta wuce kuma, sai mu tari gaba, ga asara, ga xargin ki da kowa
ke yi a gidan, ga kuma 'yan sanda na nemanki..." Mumy ta fashe da matsanancin kuka
tace "Ni wllh da ma ni na dauketa ko a jikina, amma bani bace sannan gashi kowa
kallon ni na dauketa yake min, ga dai ta nan na hadu da ita a gate da xan fito amma
sbda tashin hankali ko tunanin cutarta ban yi ba, kai a lkcn ji nayi na fi kowa
farin ciki da dawowarta don wnn ba karamin case bane gashi kaka ta ga shigowana
daga waje, da dai kattin sun shigo sun bubbuge kowa ne sun dauke yarinyar da
Rabi'ah kamar yanda muka shirya daga baya sai su sako Rabi'ar ai kinga bbu shegen
da xai xargeni, to ba a kai ga hakan ba aka nemeta aka rasa, Amma wllh idan har da
gaske Shuraim na da sa hannu a dauke yarinyar nan sai na nuna masa ni na
haifesa..... Sai ya yaba ma aya xakinta" Hajiya Sadiya tace "Ni duk ba wnn ba
Maryam, yanxu dai daga nan har xuwa wata biyu ko daya da rabi babu ruwanki da
yarinyar nan, tsakanin ki da ita ido, ko magana ba dole kiyi mata ba, sai mun bari
kowa ya sakankance sannan sai a shammace su...." Mumy na share idonta tace "Tunanin
da nayi kenan nima, shi kuma Shuraim don ubansa dama masters din nan dai da baya
son yyi yanxu shi xai tafi yyi, ga Sudais har ya kusa gamawa, to dolensa sai ya
tafi shima yyi, ko ya ki ko ya so wllh tllh sai ya tafi...." Hajiya Sadiya tace
"Shkkn wllh, kinyi maganinsa cikin sauki" Mumy ta nemi waje ta xauna tace "Ita kuma
wnn karuwar yanxu nake da lkcnta a gidan nan, na amince xan banxatar da batun
makauniyar har na yan watanni ita kuma yanxu xa mu fara gogawa da ita" Hajiya
Sadiya tayi dariya tace "Ki goga da wa? Matar da in ta fita tun safe sai yamma, ai
bata da wnn lkcn sai dai makauniyar" Kiran Abba ne ya shigo wayar Mumy ta gyara
xama da sauri ta daga ta kai kunne cikin sanyin murya tace "My Barrister"

Heedayah isn't free, you read for free


it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

I am just super amazed at the well wishes from different angles, I really
appreciate my lovely fans, Allah ya bar min ku, nagode kwarai da birthday wishes,
Allah yayi mana albarka gaba daya, Ameeen.🥰😍😘💖
Those that didn't wish me kuma should come and patronize meee ejoo, shi ma love ne🥺

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable....😍

3months later....

Kaka ce tsaye kan Khadijah inda take shiga ba nan take fita ba, Khadijah sai turo
baki take tana yatsina fuska, Haka Rabi'ah dake tsaye bakin kofar parlon Mumy, Kaka
tace "Yar banxa kawai me bakar fuska kazama, mummuna, ni dai wllh da ba don ina
asibitin aka haife ki ba ma cewa xanyi ke ba 'yar Amadu bace canje aka masa, dama
hutun da suka baku a makarantar cewa suka yi ku dawo gida ku dinga yi ma babban ku
rashin kunya ban sani ba?" A fusace Khadijah tace "To wai ni kaka me nayi maki ne,
ni kadai ne kika gani a parlon nan...." Kaka tace "Wllh Sudess xan kira yanxun nan
ya casa min ke idan kika kara xagina, kawai don yarinya Allah ya yo ta makauniya
sai ki juye mata shayin da take sha ki dura ruwa a kofin saboda bakin hali ko me?
Sannan wannan yarinya Farida ta maki magana xaki hau ta da dambe kamar 'yar da6a?
To bari yanxun nan xa a kira min Sudess, Allah ya rufa min asiri ya dawo
shekaranjiya ai da lalacewa ta sameni" Khadijah ta fashe da kuka tace "To ita
faridar Ina ruwanta da ni xata tsoma min baki?" Kaka tace "Aa wllh da ruwanta,
bayan ni da uwarta Rakiya akwai me son Deedayah ne a gidan nan, to sai kilan Amadu
duk da bamu san xuciyarsa ba, nan nan nan uwarki ta cakali Rakiya da fitina jiya
Rakiya ta ki kulata, Farida kuma duk da dai agola ce a gidan bata fiye min ku ba
sau dubu, Aa wllh ta fiye min ku, Maryam dai jaraba kawai ta haifa matsayin 'ya ya,
idan ma bakin ciki kike faridar ta fi ki kyau ne ai sai ki fito ki fada in sa Amadu
ya samar maki ko 'yar man kanti ne ki shafa kiyi hasken" Khadijah ta mike fuuu tayi
wucewarta bangaren Mumy tana cewa "Gobe ta sake saka baki a harkana wllh wllh sai
na mata dukan tsiya na farfasa mata baki" Farida dake tsaye bakin kofar Mami tare
da Heedayah da ta rike rigar faridan, ta tabe baki tace "Toh ba sai ki dokeni ba,
wllh karya ki xan yi...." A fusace Khadijah ta nufo Farida gadan gadan, kaka ta
shiga kwala ba isiya kira da karfi, dai dai shigowar Shuraim parlon, Kaka ta fashe
da kuka sosai tace "Shkkn kuma ni don mijina ya mutu ya barni bani da gata sai a
ajiyeni a gida daga safe har dare ina ra6on katti yara fada, shi Amadu ya fita
neman na xuba ma bakin salati, ita kuma wnn kinibabbiyar xabiyar ta bi sa ita ma
aikin, uwarka kuma gantalalliya suna fita ta tafi gantali ita ma, wllh tun fitan
iyayen suke dambe kamar raguna har an ji ma TVn Amadu, yanxu da baka dawo daga
Zaria ba ya xanyi da raina yau, da gangan malam suka basu hutu don su kashe ni...."
Shuraim ya kalli Farida da ta wani turo baki, ya kalli Khadijah da ta koma kofar
parlon Mumy da gudu, ya karaso cikin parlon yace "Ku dawo nan gaba dayan ku" ko
rufe baki bai yi ba Farida ta ja Heedayah suka shige parlon Mami ta sa makulli,
Khadijah ta marairaice sanin in har ta shiga ya bi ta to mai kwatar ta sai Allah,
Rabi'ah dake makale kofar ita ma tace "Allah ya so ni dai..." Kaka tace "Wa??? Ai
kece katuwar munafukar ke ke sa Khadijah tayi komai, duk bakin ki daya" Rabi'ah ta
fashe da kuka sosai tana kallon kaka, Shuraim ya hade rai yace "Baxa ku dawo nan ba
nace" Khadijah ta Rabi'ah suka fito main parlon suna matsar kwalla, Cikin rawar
murya Khadijah tace "To ita Farida fa Yaya" buge bakinta yyi, kaka tace "Ai ba
kyaleta xa ayi ba, abinda ba tsoron ta yake ba" Da wayar rechargeable ya xane su a
tafin hannunsu gaba daya, yayi wucewarsa dakinsa, Kaka da tayi tagumi tace "Dama
dai neman wanda xai duka yake tun daga Zaria, Banda haka ga dai katti sa'anninsa a
titi ya baro ya shigo gida ya ci xali, ku dai kuyi hakuri ku bar sa da Allah kawai"
Rabi'ah da ke kuka sosai ta dinga hararan kaka, Khadijah na Shessheka tace "To mu
kadai xai doka, ita faridan fa" kaka tace "Waye ubanta da baxa a doketa ba tunda
aka doke ku, ai yanda yyi maku haka xai mata ba cuta" Rabi'ah tace "To Heedayah
fa?" Kaka ta kalleta da sauri tace "Aa ke kuma baki son gaskiya, waye kuma
Heedayah? Me tayi xa a doketa, to ko ma tayi in dai shi ba wawa bane akan me xai
doketa, ko kula ku kinga tana yi a gidan nan, to ai ita ba gantalalliya bace kamar
ku" Khadijah ta mike tana hararan Kaka ta wuce part din Mumy, Rabi'ah ta ja tsaki
ta mike ta bi bayan Khadijah, kaka tace "Oho dai an dai sha mazga" Farida ta ja
tsaki tace "Haka xa mu yi ta xama kenan baxa mu ci abinci ba, ni dai baxan sha
cornflakes ba" Heedayah dake shan cornflakes dinta ta ta6e baki tace "Ni ina
ruwana, wnn da kike ganinsa din nan mugu ne, wllh duka xai maki in kika fita"
Farida tace "To a ina ya san ni da xai dokeni? And ni fa Ina ce shine Sudais"
Heedayah tace "Aa ba Yayana bane, wannan Ya Shuraim kamar naji suna ce masa, I
never liked him even for once" Farida tace "To da ina yake tun da na xo ban gansa
ba" Heedayah tace "Ban san Inda yake ba, but yana dawowa every Saturday" Farida ta
ta6e baki tace "To kawai bai san ni ba sai ya dokeni" Heedayah tayi dariya tace
"That's because he is wicked" mikewa Farida tayi tace "To kinga mu lallaba mu je in
xubo mana" Heedayah tace "Ni baxan je ba" Farida tace "Plss mana I can't go alone,
da sauri fa xan xuba mana mu dawo" Heedayah ta juya manyan idanuwanta tace "To ki
jira in gama shan Cornflakes dina" Farida tayi tagumi tace "Tohh" Heedayah na gama
shan Cornflakes din Farida ta ja ta suka fita main parlor, bbu kowa parlon sai Tv
dake kunne, Farida na rike da hannunta suka shige kitchen da sauri ta kulle kofar,
Sajida da Karime ne suka yi lunch a gidan, Farida ta bude warmer da abincin ke ciki
ta debi shinkafa knn xata bude na miya aka bude kofar kitchen din, Shuraim ne ya
shigo da wayar rechargeable a hannunsa, tana ganinsa ta fasa ihu ta saki murfin
warmer din hannunta, Heedayah ta ja gefe a tsorace, cafkota yyi, ta rikesa tana
basa hakuri a tsorace, Bai ko saurareta ba ya rike hannunta ya dinga lafta mata
wayar hannunsa, Kaka ta shigo kitchen din a guje tana cewa "Wayyoo wllh uwarta
lauya ce daure ka xata sa ayi shureen, idan ka doke wasu ka kwana lafiya to ita
wllh a seff xaka kwana bbu me ceton ka, yau fa kwananta hudu da xuwa gidan, ta dawo
daga tsadadden makarantar kwanan nan, duk da dai fitinanniya ce ai tayi min wanki
yau kuma ta wanke min bandaki, ko da yake jika jika tayi amma ai tafi munanan
kanninka..." Sai da Shuraim ya lafta mata son ransa sannan ya saketa, ta durkusa a
wajen ta dinga ihu tana kiran Mami, ya kalli Heedayah da ta rakube gefe daya a
tsorace hawaye cike idonta, ya nufeta fuska daure kaka ta dakata da surutan da take
ta shige gabansa tace "Aa nan kuma ne xan sa 'yan anguwa su lallasa min kai, uban
me xaka mata?? Ai wllh idan ka doki gantalallun nan ka kwana lafiya to kana ta6a
Deedayah maka ka xanyi a kotu, me makauniyar tayi maka, duk da dai ita ma ba kyalle
bace" kallon kaka kawai yake fuska daure, ta kama hannun Heedayah ta fice daga
kitchen din tana cewa "Ni dai ba ruwana" Farida ta wani hararesa ta mike xata bi
bayansu, xai cafkota ta fice a guje ta shige dakin kaka... Uku saura Mumy ta dawo
gidan, su Rabi'ah suka tsara mata abinda ya faru da safe, tayi shiru tana sauraron
su, can tace "Tafi maxa ki kira min Shuraim din" Khadijah ta kwanta saman gado tace
"Tabbbb" Rabi'ah tace "Ni dai kar ma kiyi masa magana Mumy, wllh dukan mu kawai xai
kara yi" Karime ce ta shigo parlon, Mumy tana kallon su Khadijah tace "Ku fita" duk
suka mike suka fita, Karime ta xauna kasa tana ta6a baki tace "Hajiya ji nayi daxu
a waya tana gaya ma wani wai an kusa fita da Heedayan waje ayi mata aikin idon..."
Mumy ta gwalo ido tace "Haba??" Karime tace "Wllh kuwa haka na ji...." Mumy ta
gyara xama tace "Wa kika ji tace xai fita da ita?" Karime tace "Wannan ne ban sani
ba Hajiya" Mumy tace "Har dai yanxu baki san Inda kaka ke boye maganin nata ba ko?"
Karime tace "Ai yanxu kaka ta ma daina sa ni gyaran dakinta, Sajida ce ke yi" Mumy
tace "Toh watan barin gidan Sajida ya tsaya" Karime tace "Wllh daxu da safe kafin
Hajiyar ma ta fita aiki ga dai ni a xaune amma Sajida ta sa taje dakinta ta dauko
mata makullin mota, ni ta ma daina bari in shiga dakinta ynxu...." Mumy tace "Akwai
wani aikin da xan baki yanxu, kuma in sha Allahu idan kika yi kokari kika cika
aikin, dubu biyar xan baki kyauta..." Karime ta washe hakora tace "Hajiya ai ko
baxa ki ban komai ba...." Bude kofar parlon da aka yi yasa duk suka yi tsit,
Shuraim ne ya shigo da sallama, fuska daure Mumy tace "Wannan ai walakanci ne, ayi
shinkafa dafaduka jiya, yau kuma ayi shinkafa da miya, tunda Sajidar tace maki
baxata yi ba ke ba sai kiyi ba..." Juyawa Shuraim yyi xai fita Mumy tace "Ina kuma
xa ka?" Yace "Naga kuna magana ne ai" Mumy tace "Kawai masu aikin jaraba suyi ta sa
mutum magana, suna ba mutum wahala" Bai ce komai ba shi dai ya fita, Karime ta
kalli Mumy, Mumy tayi kasa da murya tace "Yaushe ya xo?" Karime tace "Tun safe"
Mumy tace "Tashi ki tafi xan neme ki anjima" Mikewa tayi ta fita... Kaka nata aikin
linke linke a dakinta, Farida na dakin tana taya ta, Kaka tace "Toh dama idan ba ke
ba waye xai taya ni, ita wancan makauniyar ba wai amfani gareta ba" Heedayah dake
kwance tayi rub da ciki tana jin kaka bata dai juyo ba, Farida tace "Kaka wai shi
ma a nan gidan yake xama?" Kaka tace "Wa?" Farida tace "Wannan da ya doke mu mana"
juyawa Heedayah tayi daga kwancen da take tana kallon direction din da take jin
muryarsu, kaka tace "A'a yana can Zaria yana karo karatu, ko massers naji suna
kiran karatun, kinsan bbu yanda ba ayi da shi ya fita waje kamar yanda Sudess yaje
can yake yi ba amma ya ki, uwarsa kuwa kamar tayi hauka don ta kwallafa ran
fitansa, kin santa da fafa, so tayi ta bi duk kawayenta tace d'an ta na kasar waje
yana karatu, to da yake shi ma Amadun kila ba wani son kashe kudi yake ba ya goya
masa baya kar ya fita, duk sati kya gansa salalo salalo wai ya xo gida hutu, duk ya
bi ya takure jama'ah...." Bude kofar dakin aka yi sai ga Shuraim, Farida ta juya da
sauri ta ci gaba da linkin da take, kaka tace "D'an Halak, yanxun nan take
tambayata uban me ke dawo da kai gida, shine nake bata labari" da sauri Farida tace
"Ni fa ba shi nake tambayar ki ba...." Tana fadin
haka ta nufi kofa ta fita ya bi ta da kallon gefen ido, ya kalli Heedayah dake
kwance, kaka tace "Ka ji wai ita kuma yau bata son tayi karatun, kuma duk inda
malamin yake nasan yanxu yana hanya, dubu ashirin da biyar haka Amadu ke biyansa
duk wata, to banda Allah wa xai biya mu, bbu fa abinda muka hada da ita....."
Heedayah ta mike xaune tana sauraron kaka kamar xata yi kuka, kaka tace "Kasan idan
ba mutum ke biya ma kansa ba sai yyi ta iskanci iri iri, sai ka ga uban tsaraban da
Sudess ya yo mata daga kasar turawa, ni tsoro ma kamani yyi wllh, ni dama ko tsinke
shegen bai kawo min ba, shi kuma Junaidu daxu ya kirani wai nan da sati xai dawo
har yace in bata suka dade kuwa suna waya, ko kanwarsa bai ce in ba ma ba, ita kuma
Khadijah daxu...." Shuraim ya dakatar da ita yace "Ina tsaraban??" Kaka tace "Ae
baxa su dauku ba Shureen" yace "Suna ina?" Mikewa Heedayah tayi a hankali tana
laluba hanya xata fita kaka tace "Ji algunguma, Ina kuma xaki, kinji nace xan dau
kayanki ne da xaki wani mike xaki fita??" Shuraim dai sae kallon dakin yake yana
neman kayan.....

Am so exhausted yau, let it not just be as if I didn't type🥺

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ta gefen ido Shuraim ya dinga kallon Heedayah dake kokarin fita ya ga ko xata ta6a
sa, she was so careful ko kusa da shi bata bi ba har ta fita dakin, kaka tace "Ni
sae nake ga kamar karyar makanta take yi, ynxu a hka fa sai ta fita har tsakar
gida" Shuraim yace "Ina kayan?" Kaka tace "Naga jaraba, Ina ruwanka da kaya
Shureen? Tun daxu ka isheni ina kaya to kai aka kawo ma kayan? Kayan me xaka dameni
haka, Komai fa na da sirri, ba ruwana ni ba 'yar cin amana bace, Bai ce in nuna ma
kowa ba har Amadun balle kai karan kada miya...." Wani kallo yyi mata ya juya ya
fice daga dakin.... Turuss Khadijah tayi rike da bucket din ruwan kumfa a
hannunta, ya kalli direction din da take kokarin xuwa da sauri, Heedayah ce har
sannan bata isa bangaren Mami ba tana tafiya a hankali kuma very careful, ya kalli
Khadijah da tayi wuri wuri da ido, da sauri ta juya xata koma Inda ta fito, ya bi
bayanta tana ganin haka ta sake bucket din hannunta a rikice, ya ja baya da sauri
ganin ruwan kumfan ya malale kasan tiles bai ankara ba sai gani yyi tayi sama
sannan aka nanota kasa da karfi, wani ihu tayi can kasa makoshi, ya ma rasa ko
dariya xai yi ko d'aga ta xai je yyi, ta kwalo ma Mumy kira tana cewa Wayyo
bayanta, yana jin hka ya kalli Heedayah da har ta kai kofar parlon Mami ta tsaya,
Farida ma ta fito da sauri don ganin me ya faru, Shuraim na jin Mumy ta bude
kofarta xata fito tun bata karaso ba tana tambayar lafiya me ya faru, yyi saurin
shigewa dakin kaka ya rufe kofar. Farida ta ja Heedayah suka shige ciki ta kulle
kofa. Bayan isha Farida na parlon Mami da Heedayah, Mami kuma ta je kai ma Abba
abinci aka bude kofa Sudais ya shigo da sallama, daga kai Heedayah tayi tana kallon
ta Inda ta ji muryar sa, da farko Farida ta xata Shuraim ne sai kuma ta ga wannan
ya fi Shuraim haske, Ta gaishesa ya amsa yana murmushi yace "Ya kike?" Tace "Lafiya
lau" ya xauna yana facing din su idonsa a kan Heedayah yace "Ba gaisuwa Deedayan
kaka" Heedayah ta jinginar da kanta da kujera tace "Ni ba Deedayah bace" yace "To
ya sunan?" Ta langwabar da kai tace "Ina yini" yace "Lafiya lau Cutie, ya karatun
kuna ta yi koh? And kina ganewa?" Ta gyada masa kai, ya kalli Farida yace "Ya sunan
ki 'yan mata?" tace "Farida" yace "Ban ta6a ganin ki nan ba Farida, though Naga
kuna kama da Junaid" Farida tayi murmushi tace "Ehh na xo hutu ne kawai" yace "Wani
makarantar kike?" Tace "Nigerian Turkish...." Yace "Boarding?" Ta gyada masa kai,
yace "Maa sha Allah" Heedayah tace "Yayana baxa ka sake komawa UK ba koh?" Yace
"Idan ma xan koma tare xa mu koma ae" Ta wara ido tace "Da gaske?" Yace "Ehh mana
sai in gaya ma su Abba da Kaka su bani ke, kowa ya shaida sannan mu wuce" Murmushi
tayi tace "To kayi masu magana plss" yace "Da gaske dai xa ki bi ni? Xamu dade fa
bamu dawo ba" tace "Allah xan bi ka" yana murmushi yace "Toh shkkn" Bude kofa aka
yi Rabi'ah ta leko fuska daure tace "Ya Sudais kaka na kiran ka" ya kalleta kafin
yace komai tayi banging kofar ta wuce, Farida tayi kwafa can kasa kasa, mikewa yayi
yace "I'm coming back...." A hankali Heedayah tace "No chocolates?" Ya kalleta yyi
murmushi yace "Sai na dawo" daga haka ya fita, Farida tace "Ke da kike cewa xa ki
bisa ke matarsa ce?" Heedayah tace "To ba Yayana bane" Sudais na tsaye yana
sauraron abinda kaka ke cewa, can yace "Toh yanxu me kike nufi?" Tace "Ina nufin in
har baka bani nawa tsaraban ba wllh baxan bata ba, gwara in kwashi tarkacen da ka
kawo in kai kasuwar 'yan koli in siyar, haka kawai daga ganin sarkin pawa sai miya
tayi xaki, uwar me ma ka hada da ita bani da labari, duk wahalan da nayi da kai
kana karami ka dawo daga kasashen turai ko abun sakace hakuri baka kawo min ba sai
yar tsintuwa" dai dai nan Shuraim ya shigo dakin da ledan fruits da Abba ya sa ya
siyo mata, Sudais ya kallesa sannan ya ci gaba da sauraron kaka, Shuraim na ajiye
ledan tace "Shureen tunda muke da kai ka ta6a fita kasar waje ka dawo baka min
tsaraba ba, ko nan nan da Zaria idan kaje ai kana siyo min 'yar lemon nan" Shuraim
na kallonta ya ciro wayarsa dake vibrate a aljihu, kaka tace "Toh don me Sudess xai
fita ya dawo min haka sai wata can wai Deedayah xai kwaso ma kaya iri iri kamar
kanwar ubansa" Sudais yace "Saboda ta fiye min ke" shiru kaka tayi tana kallonsa a
bit shock, yace "Kuma ki fito da kayan in kai mata yanxu" Kaka tace "Al-qur'an
kasuwan 'yan koli xan kai su gobe da sassafe, idan na baka in tafi a karkace,
Deedayar kanwar ubanka ce ko ta uwarka?? Waye kuma Deedayah? Me na hada da ita
banda dai d'a na ya tsinto mana ita" Sai kuma ta xauna ta fashe da kuka tace "Ehh
lallai karshen duniya ta kankama" Juyawa Sudais yyi ya fita daga dakin, Kaka ta
kalli Shuraim tana matsar kwalla tace "Ka dai ga ko Shureen?? Hakan da Sudess ya
min ya kyauta" Yace "Ni baxan ce komai ba sai na ga kayan" Babu wata wata Kaka ta
dauko makulli da sauri ta bude gun ajiye kayanta ta fiddo akwatunan har biyu da
karamin jaka, kallonsu kawai Shuraim yake, ta xuge jakar ta shiga fiddo abubuwan
ciki, cikin lkci kadan ta fiddo komai ta bajesa a gaban Shuraim tana kallonsa,
Kallon kayan kawai Shuraim yake, beautiful English wears, teddie bears, biscuits,
dolls, chocolates, sweets, shoes, har da jewelries, Shuraim ya dauke idonsa daga
kan kayan, kaka na matsar kwalla tace "Ka dai gani ko, ni fa na haifi ubansa Umaru"
Mikewa Shuraim yyi bai ce mata komai ba ya fice daga dakin... Ta bi sa da kallo
baki bude sai kuma tace "Toh Allah ya isa" Sudais na komawa parlon Mami, Mami dake
xaune parlor tace "Mutan UK, sai yau muka hadu" Ya gaisheta yana murmushi yace
"Jiya da na xo kina gun aiki" Mami tace "Ehh ina can, ya karatun kun gama kuwa?"
Yace "A'a saura kadan" Mami tace "Maa sha Allah, Allah ya sa a gama a sa'a, ya su
Hajiyar ku?" Yace "Suna lafiya gaba daya" Tace "To maa sha Allah, a xubo abinci?"
Yace "A'a na ci" ta mike tace "To yayi kyau" bedroom dinta ta shiga ya kalli
Heedayah ya koma kusa da ita yace "Ina kawar ki Farida?" Tace "Ta tafi wanke wanke
a kitchen" Sudais yace "Masu aiki fa?" Heedayah tace "Mami ce tace taje ta yi" Yace
"Ohkk" ta matso kusa da shi a hankali ta laluba hannunsa tace "Yaya kasan me?" Ya
kalli kofar dakin Mami sannan ya hade forehead dinsa da nata yace "No..." Tace "Yau
ina son in sha ice cream" yace "Ice cream?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk bari
Farida ta gama wanke wanke sai mu je gaba daya" Tayi murmushi tace "Nagode" Farida
na shigowa yace "Farida tell Mami xa mu je siyo abu yanxu, with you and Heedayah"
tace "Ohkk" daga haka ta shiga bedroom din Mami, ba a dau lkci ba ta fito da Hijab
dinta da na Heedayah tace "Mami tace alright" sosai Heedayah ta ji dadi, ya amshi
Hijab din ya sa mata sannan ya daga ta holding her hands suka fita parlon tare da
Farida, Shuraim na xaune parlor shi kadai, tun da ya kallesu sau daya ya dauke kai
har suka fita parlon.... Wani wajen shan ice cream Sudais ya kai su, yyi parking ya
sauka motar, ya bude ma Heedayah back seat yana rike da hannunta ta sauka, Farida
ma ta fito daga front seat da ta xauna, Sudais na rike da hannun Heedayah da ta
makalesa suka shiga ice cream parlor din, Ya duka dai dai kunnenta yace "Wani irin
ice cream kike so?" Tace "Vanilla" ya kalli Farida dake kallonsu yace "Ke fa Aunty
Farida?" Tayi 'yar dariya tace "Irinsa nima" Wani mutumi ne xaune wajen da roban
ice cream a gabansa, su uku ne xaune a round table din, all wearing glasses, tun da
suka shigo yake kallonsu ta bak'in glass din idonsa, Sudais ya biya kudin ice cream
da ya siya masu yana rike da hannun Heedayah ya nufi kofar fita Farida na biye da
shi, mikewa Mutumin yyi ya dau makullin motarsa, wanda ke kusa da shi ya kamo
hannunsa murya can kasa yace "Hey... ina kuma xaka? Ynxu fa xa su gama su fita..."
Ba tare da Mutumin ya kallesa ba yace "Ina xuwa ynxu" daya Mutumin yace "Noo this
is our only chance...." Ya fixge hannunsa ya fita da sauri, Sudais ya kulle motarsa
kenan bayan ya sa Heedayah ciki ya bude maxaunin driver ya shiga yana kallon Farida
dake gaban motar yace "Did you need anything again Farida?" Tace "Aa mun gode" tada
motar yyi yayi reverse, Mutumin da tuni shi ma ya shiga motarsa ya bi bayansa, mota
daya ne interval tsakaninsu, Mutumin ya dinga kokarin ganin yyi over taking motar
har suka kusa traffic, Sudais na tsallaka wajen traffic din ya nuna red, hakan ya
sa motar dake bayansa ya tsaya, Mutumin ya jinginar da kansa da kujera ganin motar
Sudais yyi nisa sosai... Sudais na parking a kofar gida ya bude ma Heedayah back
seat ya sakko da ita, Farida na rike da ledan ice cream din suka wuce ciki, har
sannan Shuraim na xaune main parlor, wannan karan kallon gefen ido yyi masu, Sudais
ya duka kusa da Heedayah yace "Sai da safe, I am going home now" tace "Xaka xo
gobe?" Yace "In sha Allah" tace "Haka kace jiya kuma baka xo ba" yace "Ba gashi na
xo yau ba" tace "Toh byee" ya ja hancinta a hankali yace "Bye" Farida ma tayi masa
sai da safe tana rike da hannun Heedayah suka wuce bangaren Mami, Sudais na kallon
Shuraim yace "Sai da safe bokan turai" Shuraim na danna wayarsa yace "Allah ya
tashe mu lfya" Sudais ya juya ya fita parlon... Washegari karfe tara saura Hajiya
Amina mahaifiyar Sudais ta shigo gidan, Khadijah na xaune dinning suna breakfast da
Rabi'ah, duk suka gaisheta suna mata sannu da xuwa, ta nufi dining din tana
kallonsu murya can kasa tace "Abba na nan??" Rabi'ah tace "Aa ya fita" Umma tace
"Hajiya Maryam fa?" Khadijah tace "tana daki" Umma ya nufi bangaren Mumy ta bude
kofar ta shiga, bbu kowa parlon haka yasa ta wuce daki, Mumy ta katse wayar da take
yi da sauri tana cewa "Waye??" Umma tace "Ni ce Maryam" Mumy tace "Aa Amina, daga
ina da safe haka?" Umma tace "Daga gida..." Mumy tace "Allah ya sa lafiya dai, ko
munafukar ta sake hada ki da Dakta?" Umma tace "Ba gwara a hada ni da Dakta ba a
kan wnn takaicin...." Mumy ta gyara xama tace "Me ke faruwa?" Umma tace "Uban kayan
da Sudais ya kawo ma makauniyar nan na xo amsa tunda ba ubanta bne ya basa kudin
banxa" Da mamaki Mumy tace "Kaya kuma,
wllh bani da labari Amina, ta Ina aka shigo da kayan gidan ban sani ba?" A fusace
Umma tace "ni kai na da na haifesa a jaka daya ya kawo min tsaraba, kanninsa kuwa
dama tsaraban baya wuce chocolate da biscuits..." Mumy tace "To wai kayan me ya
kawo mata?" Umma tace "Wllh tsaraba ya yo mata niki niki, iri iri kuwa, bai san
xancen xai dawo kunne na ba, har manyan akwatuna biyu da jaka fa Maryam, abinda
hakan ke nufi shine na kasa ganewa" Mumy ta gwalo ido tace "Sudais din?? Jiya na ji
ance ya xo dama amma ko shigowa ya gaisheni bai yi ba, kinsan fa har wani xumunci
ya kulla da kishiya ta" Umma ta mike tace "Ina xuwa, ba dai Barrister baya nan ba,
yau xa ayi ta ta kare" bata jira cewar Mumy ba ta fita. Bangaren Mami Umma ta nufa
ta bude kofar hade da sallama bbu yabo bbu fallasa, Mami na tsaye parlonta tana sa
wrist watch ta gama shirin fita, su Farida na parlon, a takaice Umma tace "Ina
kwanan mu" Mami na kallonta tace "Same to you" Umma tace "Kayan da Sudais ya kawo
gidan nan na taho a miko min..." Mami tace "Kaya? Kayan me kenan?" Umma tace "Ai
kin fini sanin ko kayan menene tunda kece kika amshi kayan, to ba duniya na haifar
ma shi ba, ayi hakuri a fito da kayan a bani in kama gabana" Mumy dake ta leko
parlon tana tsaye daga bakin kofa tace "Atohhh, gwara dai ki sanar masu ba duniya
kika haifar ma shi ba" Mami bata sake kula su ba, ta gama saka agogonta ta dau
handbag dinta da veil tana kallon Farida da Heedayah tace "Farida bring hijab for
the both of you sai in ajiye ku gidan Hasinah" Farida ta mike ta wuce daki, Umma
tace "Ni fa ba Maryam bace da xaki wani dinga sha ma kamshi bbu hadina dake, kayan
da d'a na ya kawo maki nace ki fito min da su yanxu, ko alkali ce ke ni baxan fasa
amsan abinda na xo amsa ba baxan kuma fasa gaya maki abinda ke raina ba....."
Farida ta fito da hijab Mami ta amsa ta sa ma Heedayah, Farida ta ajiye mata
takalminta ta a gabanta, Mami tace "Ki je ku sallami Kaka, sai ku sameni a mota"
Umma ta bude baki tana kallon Mami ganin har sannan ta ma ki kallon inda take, Mami
ta nufi kofar sai a nan ta kalli Umma tace "Malama xan wuce, bani hanya" Umma tace
"Hanyar ya ci kaza kazan sa, kayan da aka kawo maki nace ki fito min da su yanxu
kada abu ya 6aci tsakaninmu, ni fa ba Maryam bace wllh" Kaka ce ta taho wajen da
sauri tana cewa "Muryar waye nake ji wnn kamar na Amina, me ke faruwa hka?" Umma ta
juya tana kallon kaka fuska daure tace "Ina kwana kaka" Kaka tace "Lafiya kike
hayaniya haka a kofar mutane Amina, me ya faru??" Mumy tace "Wllh kaya wai Sudais
ya kawo gidan nan ba mu da labari, kaya wai me yawa..." Kaka tace "Kayan me??" Mumy
tace "Ni kaina bansani ba, ance dai kayan na nan bangaren" Kaka tace "Au, wai
tsaraban da yayo ma Deedayah?" Mumy tace "Toh shi din kenan" Kaka tace "To sai aka
yi yaya? Ai kaya basa wajen Rakiya suna wajena, waye ya xo amsa?" Umma da ta daure
fuska tace "Ni na xo amsa" Kaka ta kalleta daga sama har kasa tace "Haba, to sannu
da xuwa Amina, bakin cikin ne ya motsa kenan yau, to bari kiji ko Umaru yyi kadan
ya amshe ma Deedayah kayan da Sudess ya siyo mata balle ke, kuma in sha Allahu yau
xata fara saka kayan sai in ga ta tsiya, ke kuma Maryam har kin mance hijaran da
kika yi na kwana biyar a gidan nan bayan kin sa an sace Deedayah kin maido ta, kin
manta yanda kika dawo duk a lalace shine xaki sake shiga wani kess din da sassafe
koh, to wllh Rakiya kiris take jiran ki ko bata fada ba ni na sani, haka kawai duk
kun bi kun sa ma makauniya ido, to wllh karyan ku, tunda ina sonta Rakiya na sonta
Sudess na sonta, Junaidu na sonta shi Amadu ba wai mun gama sanin xuciyarsa bane,
to kowa ma ya ki ya indai mu muna sonta" Umma ta fiddo wayarta tayi dialing number
Sudais yana fara ringing ya daga, strictly tace "Kana ji na Aliyu??" Sudais yace
"Ina ji Umma" tace "Wannan kayan da ka kawo gidan Barrister da sunan kayi ma
makauniya tsaraba maxa maxa ka xo ka amshe su ka kawo min dakina, idan kuwa ba haka
ba wllh wllh ka canxa wata uwar...."

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah


Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Kaka dake ta kallon Umma baki bude ta saki salati tana tafe hannu, ganin Umma ta
yanke wayar bayan ta gama magana kaka tace "Toh yanxu dai kafin ince komai so nake
a fara gaya min munafukin da ya kai maki xancen nan, idan kuma baxa ki gaya min ba
sai in sa a kira min Umaru ya kira ki ya tambaye ki nasan shi xa ki gaya masa, don
gaskiya idan aka ki fada min wanda ya kai gulman nan kunnen ki, toh gwara in tafi
duk inda xan tafi kawai...." Kaka na fadin haka ta tafi daki, Mami kuma ta nufi
kofar fita Umma ta bi ta a fusace tana cewa "Kema ba ina ce kina da d'an ba, me
yasa baki dinga makala masa makauniyar ba sai 'ya yan mutane?? To wllh daga ke har
shegiyar yarinyar ku fita harkan d'a na...." Mami ta tsaya so pissed off tace "Look
plss woman, get back home, sit ur son down, warn him seriously to stay away from
the little girl, or from this house as a whole, you can't just come here and be
displaying how mad you are plss.... behave like a literate for once, this is a very
simple issue to address to alone without u causing commotion, komawa gida xa kiyi
ki kira d'an ki ki xaunar da shi ki ja masa kunne cikin nutsuwa, in har ya dauke ki
uwa to bbu abinda xai sake kawo sa gidan nan balle ya xo gun Heedayah, amma kawai
kin xo kina ma mutane hayagaga a gida, why not behave like the elderly lady you
are?? Wnn fa ba abun tada jijiyoyin wuya bane, in har d'an ki na jin maganar ki to
fa baxai kusanci abinda baki so ba, plsss I have very important things a gabana
than listening to ur bull shit... So excuse me" Mami na fadin haka ta fice daga
parlon, Umma da ta saki baki tana sauraronta ta bi ta da sauri tana cewa "Toh ai
asirin da kika masa kilan baxai ta6a barin ya saurareni ba, don naga ba iya
Barrister kadai mugun abun ki ya tsaya ba, waye bai san da asiri kika shigo gidan
nan ba, kuma wa ya sani ko ke kika lika ma barrister makauniyar duk don ya aure
ki??" Mami ko juyowa bata sake yi ba balle ta tanka ta, Mumy da ta bi bayan Umma ta
dinga cewa "Toh ai fada ma 6ata baki ne Amina, tuni aka shaida min ta asirce
barrister sai yanda tayi da shi, shine ta koma kan Sudais...." Mami ta bude motarta
ta shiga tana answering call da ya shigo wayarta, Kaka ce ta fito dakinta rike da
wayarta, ganin Farida rike da hannun Heedayah xa su fita parlon ta nufeta tana mika
mata wayar hannunta tace "Maxa kira min Umaru, yana nan xa ki ga ansa Dakta... Yi
maxa kirasa" Farida ta amsa ta nemo number Baffa sannan tayi dialing ta mika ma
Kaka jin ya fara ring, Baffa na dagawa kaka ta nemi kujera ta xauna ta fashe da
kuka tace "Umaru ashe dama matarka Amina gantalalliya ce bani da labari, me nayi
mata xata xo har gida ta min wankin babban bargo don wnn yaro naka Sudess ya yo ma
Deedayah tsaraba?? Ni fa na ce yyi mata tunda ba wai gata gareta ba kowa na mata
kallon yar tsintuwa, shi kansa Amadun da ya rabota da titi har yau ko tsinke bai
ta6a siya mata ba, shi dai ya kawota kawai ya jibge mana ita, sai Rakiya ke ta siya
mata kaya duk da dai ita ma kayan anna take siya mata wasu guntaye kmr ta6a66iya,
to laifi ne don ynxu Sudess ya mata tsaraba daga kasan waje?? To wllh ka taho gidan
Amadu yanxun nan ka titsiye Amina sai ta gaya maka uban da ya kai mata rahotun an
ma Deedayah tsaraba, idan ba haka ba ni gaskiya an ci mutunci na kawai an keta min
rigar mutuncina" Baffa dake ta sauraronta yace "Ikon Allah, haka ya faru?" Kaka
tace "Aa karya nayi maka" Baffa yace "A'a ba haka nake nufi ba kaka, kawai gani
nayi...." Ta katse sa da sauri tace "Baka ga komai ba Umaru, ba ruwana da bayanin
ka, so nake kawai ka kamo hanya ka xo ka ritsa Amina ta fadi shegen da ya kai mata
gulman Sudais ya yo ma Deedayah tsaraba, idan ko ba haka ba to xan tattara ya nawa
ya nawa in san inda dare ya min, baxan xauna a ci mun mutunci ba kayi shiru" Baffa
ya girgixa kai yace "Toh sai na xo" Ko amsa bata basa ba ta katse wayar, ta mike ta
nufi kofa da sauri, Tijara iri iri Umma ke ma Mami a tsakar gidan Mami taki ko da
kallon inda take har Farida da Heedayah suka karaso gun motar, Umma na kallon
Heedayah tace "In sha Allahu a makance xa ki dauwama ki kare, tunda har kika shigo
gidan mutane kika tarwatsa farin cikin da aka gina da dadewa, lkci daya kin
tarwatsa komai, ae ko xuwan ki familynmu sharri ne ba alkhairi ba..." A nan Mami ta
kalleta tana murmushi tace "Kya ga dauwamammen makanta kuwa a gidanki...." Umma
tayi wani shewa tace "Bakin ki ya sari danyen kashi, sai dai a gani a naki xuri'ar,
mu kam kaf dangi daga farko har karshe bbu nakasasshe..." Muryar kaka suka ji tana
cewa "Toh Amina idan kin gama ki shigo daga ciki ki xauna, tafiya bai ganki ba,
Umaru na hanya" Mami na kallon kaka tace "Kaka sai mun dawo" Kaka tace "Toh a dawo
lfya Rakiya, da yake ke ba xaman banxa kike ba ina xa ki samu lkcn gantalallu da ko
sakandarin basu kare ba, ita fa Maryam iyakarta aji biyu na sakandari Amadu ya gaya
min, ita kuma Amina dama ko makarantar Ina jin bata ta6a yi ba don ko 'yar turancin
nn ban ta6a ji tayi ba shekarata biyu gidan Umaru, kawai dai Allah ya ba 'ya yana
jahilai sai xuba jahilci suke a gida ba kakkautawa" Mami ta tada motarta ta nufi
gate da mai gadi ya bude mata tuni ta fita. Baffa ne xaune parlor a gidan Abba
bayan la'asar, sai Umma da kaka sannan Sudais, Mumy sai kai komo take a parlon
kamar me yin wani abu, Baffa yyi gyaran murya yace "Da farko dai xan fara baki
hakurin rashin xuwa da ban yi da wuri ba sbda marasa lfya da na tsaya dubawa
asibiti, sannan ina kara baki hakuri da abinda ya faru daxu da safe...." Kaka ta
ta6a baki ta rungume hannu tace "Haka dai" Baffa ya kalli Umma yace "Ke me ya kawo
ki gidan nan daxu da safe?" Tace "Kayan da Sudais ya kawo gidan na xo amsa" Baffa
yace "Wasu kayan?" Tace "Ai shi ya san wasu kayan ne Dr...." Kaka ta dakatar da ita
tace "Kafin a je da nisa, Ina son sanin wanda ya gaya maki Sudess ya kawo kaya
gidan nan, don banda ni sai shi sai wannan sumu sumun yaron Shureen bbu wanda ya
sani, har ita Deedayahn bata sani ba balle uwar goyonta Rakiya, to ynda kika samu
labari kawai nake son sani yanxu" Baffa na kallon Umma yace "A ina kika ji xancen"
Umma ta d'an yi shiru na wasu seconds kafin tace "Shi din da bakinsa ya gaya min ba
kowa ba" Kaka ta kalli Sudais da sauri tace "Wai??" Yyi kasa da kansa yyi shiru,
har sai da Baffa ya sake cewa "Plss kar ka bata min lkci malam, I have important
things" Sudais ya daga kai ya kalli Umma dake hararansa yace "Ehh nine" Kaka tayi
tagumi tace "Toh abu ya lalace kenan ai, kai kuma ashe haka kake bakin ka baya
haila?? me ya kai ka don ka yi abun arxiki kaje kana terere kana fada ma duniya??
Aa lallai Sudess ya xama abun tsoro" Baffa dai ya jinginar da kansa da kujera so
pissed off da wnn batun mara amfani garesa, Umma tace "Don haka ynxu idan bai maido
kayan can gida ba ya nemi wata uwar amma ba ni ba" Kaka na kallon Baffa tace "Ni
kuma idan har Sudais ya maida mata kayan ta sa hannu ta amsa baka sallameta ta tafi
gidansu ba ka nemi wata uwar ba ni ba Umaru" Baffa ya kalli Umma da ta bude baki
tana kallon kaka, Kaka ta mike tace "Duk shawaran da aka yanke ni dai ina daki,
kaya na fita daga dakina dama Amina ta fita daga gidanka, to ni ba gantalalliya
bace" Tana fadin haka ta nufi dakinta tana cewa "Kuma duk wanda yace Deedayah xai
sa ma ido sai dai ya mutu muruss, ni ma ba gashi gantalallen bai min tsaraba ba
amma na hakura ban ma yarinyar bakin ciki ba, to meye wasu xa su yi mata bakin
cikin tunda har na kai xuciyata nesa ni ban mata ba, da ni azzaluma ce da ba cewa
xan yi xan kai kayan kasuwar 'yan koli in siyar ba, amma ae bance haka ba" Baffa ya
mike yace "To shawara ta rage kuma gare ku, but let me tell u this Amina, duk ranan
da kika sake janyo na baro gun aiki unnecessary ranan won't be funny for me and
you" daga haka yyi ficewarsa daga parlon, Umma ta dinga kallon Sudais da idanuwanta
da suka kankance, shi dai bai iya ya kalleta ba, can ya mike a hankali ya nufi
dakin kaka, yana shigowa tace "Meye kuma ka biyoni? Ae tunda ka fita har waje ka
dawo baka kawo min ko tsinke ba to xaka iya bada min shinkafar 6era a abinci, wai
Deedayah, to uwar me ka hada da Deedayar bani da labari?" Ya mata wani kallo yace
"Toh ki fito min da kayan" kaka tace "Sae dai in fito maka da Umaru, kaya kam bbu
wanda ya isa ya sa in fito da shi, Allah ya tarwatsa duk me yi ma marainiyar nan
bakin ciki" Ya fi minti uku yana ta kallonta tana harkan gabanta, can ya juya ya
fice daga dakin ta bi sa da harara tace "Da baki kmr gidan tsutsa, sae shegen
surutu kmr mace" Tsaye ya ga Umma a parlor tare da Mumy ko wannensu rai bbu dadi,
Umma tace "Kasan Allah Aliyu, wllh ka sake shigowa gidan nan ni dai ban yafe maka
ba, bbu kai bbu gidan tunda Mahaukaci ka xama, ita makauniyar kanwata ce ko ta
ubanka da kayi mata siyayya hka, to wllh ka sake kallon ko da inda take kai da
Allah.... Kaya kuma basu ci bulus ba duk ma wanda yyi amfani da shi Allah ya isa
wllh" tana kai wa nan tayi ma Mumy sallama a fusace ta fita, Mumy na kallonsa tace
"Ni ka ban mamaki wllh Sudais, kana da dangantaka da yar tsintuwar ne?" Yace "Ina
da shi mana, 'yar uwata ce ita musulma" Mumy ta hade rai tace "Ohh wato ni kake da
bakin mayar ma magana koh?" Yace "Toh Mumy fisabilillah meye don nayi ma marainiyar
tsaraba, kowa fa ina masa idan na tafi...." A fusace tace "Kana masu uban me?? Shi
biscuits din da chocolates ne tsaraban? Ka tashi ka cika akwatuna har uku kamar me
kai lefe sai kace mara mafadi, to gidan ma gaba daya an hana ka shigowa sae in ga
ta tsiya... Yarinyar kawai matsiyaciya mara gata duk ta tarwatsa gida" Ya girgixa
kai yace "Ae kam tana da gata...." Yana fadin haka ya nufi kofar fita daga parlon,
muryar kaka yaji tana cewa "Ni dai ban yafe rashin tsaraban da baka min ba" ko
kallonta bai yi ba har ya fice daga parlon.... Heedayah ce xaune garden din gidan
da malamin da ke mata karatu, a final year Engineering student, baxae wuce ashirin
da shidda ba, tana xaune saman one of the two comfortable chairs da Abba ya siyo
gidan don koya mata karatu,
shi ma malamin na xaune saman guda daya da textbook din Basic science a hannunsa,
bayanin topic din da ya mata ranan take masa, ko tsallaka word daya bata yi ba a
abinda ya koya mata, a nutse take masa bayanin, directly yake kallon cikin
idanuwanta without even blinking, duk wannan abun Shuraim na xaune balcony a sama
doing nothing yana kallonsu lkci lkci, shi kansa malamin bai san yana wajen ba, can
dai Shuraim ya mike ya tsallaka gwangwanin Coke da ya ajiye wajen ko budewa bai yi
ba ya fita balcony din, cikin few minutes ya shigo garden din, tun daga nisa idonsa
ke kansu, Heedayah ta turo baki tace "Toh ban yi dai dai bane, why don't you want
to compliment me?" Ta fadi haka ne sbda shirun da ta ji Malamin yyi bayan ta ce
masa ta gama, Malamin na hango Shuraim yace "Yess, that's excellent of you, I know
u can do it...." Tayi murmushinta me kyau tace "Da gaske?" Shuraim na isa wajen
yana kallon Malamin yace "Karfe nawa kake gama lesson din?" Malamin na kallon agogo
yace "Saura minti ashirin..." Shuraim yace "All same, akwai hadari garin you can
leave now, sae da safe....." yana fadin haka ya kalli Heedayah ya wani hade rai
yace "Tashi" a hankali ta mike tsaye staring into space, fuska daure ya fixgo
hannunta ya bar wajen tana biye da shi kamar xata fadi, malamin ya bi su da kallo,
Suna shiga parlor ya kai ta har kofar dakin kaka yyi abandoning dinta sannan yyi
wucewarsa sama. Heedayah ta samu dai ta bude kofar ta shiga, Kaka xaro ido tace
"Har kun yi me??? Anya wannan yaron ba 419 yake ma Amadu ba kuwa, ba fa a titi ake
tsintar kudin ba, me ya koya maki haka da wuri har ku ka tashi?" Heedayah ta turo
baki tace "Ko ba wnn bane ya dawo da ni wai akwai hadari ko gama karatun ba mu yi
ba" Kaka ta mike tace "Wa?" Ta yatsina fuska tace "Ni manta sunansa nake, wannan
din nan dai" Kaka tace "Atoh ce min xa ki yi wancan sumu sumun, me yasa ku ka biye
masa, gantalalle ne fa, lkcn yana karami baki ga kukan da yake tsalawa ba idan xa a
kai sa makaranta, kwata kwata bai son karatun, ya fi so yyi ta xaman gida yana
kassara min Amadu da kashe kudin yagwat, to shine xai maki bakin ciki yanxu sbda
d'an turancin da kike ji?? Bakin xuciya fa garesa ci gaban ki ne baya so...." Lkci
daya kaka tayi tsit ganin Shuraim tsaye bakin kofa don a bude Heedayah ta bar
kofar, kaka tace "Toh kuma ai hadarin idan ya kare maki sai ya sa maki wani cuta,
ni kaina fa idan ana hadari bana yarda in fita ko nan da kofa balle ke me lalura,
ae da kyau da ya koro ki...." Heedayah ta wani turo baki tace "Kaka karya fa yake
yi bbu wani hadari wllh, ai banji kamshin ruwa ba, kuma bbu ko wani iska kawai dae
shi mugu ne...." Kaka tace "Kul.... bar ce ma baba yana karya bbu kyau, kuma ba
mugunta bace lafiyar ki yake ji shi sa yace ki shigo kar iskan yamman ya kare maki,
abinda likita ne shi ma ya san illan haka....." Heedayah ta laluba gefen gado ta
xauna tace "To Ina ruwansa da ni? Ko English language fa ba mu yi ba ya dawo da ni,
kuma sae sauri yake sbda in fadi inji ciwo" Kaka ta saci kallon Shuraim dake tsaye
yana kallon Heedayah, tace "Ke kuma ya xa ki ce haka, ubansa fa ne ya tsinto ki a
titi kina galantoyi, kinga kuwa ai da ruwansa da ke, ni dai ki bar rashin kunya,
haka kawai kina fama da makanta kina fitsara, ni ban taba ganin inda aka yi haka
ba" Heedayah ta daura kafanta saman gadon tace "Shi ma ba yana maki fitsaran ba
kullum.... Kaka gaya min ma yanda yake" Kaka tace "Shureen din?" Ta gyada kai, Kaka
tace "Tohh, yana nan dai wani dogo kamar fal waya, wani lagwai lagwai, shi dai baxa
a ce masa fari ba kuma baxa ace masa baki ba, Sudess ya fi sa haske, snn a tsaye
yake bai dai kai samudawa ba, kinsan da shi da d'an uwan nasa Sudess basu da aiki
da sai xuwa gidan karafe suna dagawa, to ynxu duk sunyi hankali, yana nan kuma da
kwala kwalan idanuwa kamar dai naki, amma naki ya fi nasa kyau, Inda Allah ya
cecesa hancinsa har baka wllh, sannan bakinsa d'an tsut, shi ke hanasa magana kila"
Heedayah ta juya ido tace "Toh meyasa sai yyi ta cin xalin mutane, haka ranan ya
doki kawata Farida" Kaka tace "Toh wnn kuma sai dai mu ji daga garesa, kinsan yana
tsaye bakin kofa... Kai Shureen me yasa kake cin xalin al'umma" Heedayah ta xaro
ido tana komawa baya saman gadon kamar xata yi kuka a hankali tace "Kaka yaushe ya
xo?" Kaka tace "Tun tambayar ki na farko amma kinga ai baxai yiwu in katse maki
hanxari ba tambaya ance mabudin ilimi...." Shuraim sai kallon Heedayah kawai yake
ya rungume hannunsa, can ya gyada kai ya juya ya fita dakin, kaka ta rufe kofarta
tace "To ni dai ba ruwana Allah ya so ban fadi wani mugun abu a kansa ba, ke kuma
kar ki iya bakinki da surutu, wllh karya ki xai yi ba ruwana, ko kanninsa baya wasa
da su duk tsoronsa suke, ke kuma gashi har ce masa mugu kika yi kika ce karya yake,
ni dai ba ruwana" Heedayah da har hawaye ya kawo idonta tayi shiru tana sauraron
kaka. Bayan Magrib Heedayah na dakin kaka har lkcn bata koma bangaren Mami ba, a
hankali Kaka ke daukan naman kwanon gabanta tana ci kar Heedayah ta sani balle ta
bata, kaka tace "Toh ko uwar ce ta hanata shigowa yau gaba daya bani da labari, da
ta shigo fa da ynxu kinga ta gyara min daki ta goge tace xata wanke bayi, yarinyar
ba dai tsafta ba gata yar gayu kuma kyakkyawa fara, har da lotsa kumatu gareta,
naga kamar ma har waya gareta, 'ya yan Amadu kuma ga su nan dai wasu kolaye
kazamai, Kinga da Shureen wani ne ae sai ya nemeta nasan ko don Amadu Rakiya baxata
ce A'a ba, to ba a auren aka aureta, shi ma Shureen din ae d'an gayu ne, fess xaka
gansa kullum cikin kamshi, ko kadan bai son datti, kinsan ni ya gada amma ba uwarsa
ba, Kuma fa wllh auren yake so, ya rasa yanda xai fito ya fada ne amma wnn shiru
shirun da yake duk aure ya saka a rai, kinsan indai shirun namiji yyi yawa kawai
auren nan yake so wllh" Heedayah dake gefe xaune da plate din shinkafa da miya a
gabanta ta ta6e baki tace "Kaka ni fa na san nama kike ci wllh...." Kaka ta fiddo
naman da ta kai bakinta da sauri tace "Inji ubanwa, meye kuma nama da xan ci in
hanaki kamar wata mayya?" Heedayah tace "Ni dai nama kike ci wllh" Kaka tace "To
tashi ki yi ma kanki jagora ki fitar min a daki kada raina ya baci, aniyar ki kuma
ya bi bayanki wllh, ni ya kamata in baki nama ko shi Amadun da ya tsinto ki, Kuma
wllh ke mace ce ki raba kanki da sa ido gidan wani xaki, meye kuma kinsan nama nake
ci, a ina kika ga naman kina fama da makanta" Heedayah ta mike tana turo baki tana
ma kanta jagora da hannunta ta nufi kofa xata fita, kaka ta bi ta da harara tace
"Aa kifi nake ci ba nama ba tunda Amadu kika ga ya kawo min nama...." Dai dai nan
aka bude kofar Heedayah ta ja baya da sauri, Kaka ta saki salati ta mike tace
"Junaidu?? Allahu Akbar saukan yaushe??" yana murmushi yace "Daxu kaka...." Yana
magana yana kallon Heedayah da ta bude ido sosai, ya daga kanta yana murmushi cikin
cool voice dinsa yace "Hey...." shigewa jikinsa tayi ta rungume sa tace "Yaya"

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....


Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Junaid ya dago kanta yana murmushi yace "How are you dear?" tace "I'm fine...."
Kaka na washe hakora tace "Ae da ka gaya min kana hanya da nayi maka girki Junaidu,
ga dai yara in aika su siyo min kayan miya da yar kaza" yana rike da hannun
Heedayah ya karasa cikin parlon ya xauna yace "Aa bana son ki wahal da kanki ne,
Ina yini kaka?" Kaka tace "Toh lfya lau Junaidu, to ya hanya?" Yace "Alhmdllh" tace
"In ji dai baxa ka sake komawa ba" yyi murmushi yace "Saura kadan in gama kaka"
kaka tace "Toh, shima dai Sudess hka na ji yace saura kadan, Shureen dai ne ban san
isilin karatun nasa ba, anya ma yana karatun kuwa? Gani nake kamar budirinsa kawai
yake a Zaria" Junaid dai bai ce komai ba sai murmushi da yake yi, ta mike ta tafi
dauko masa ruwa tana cewa "Toh ko 'yar mantinan nan dai bbu a gidan ynxu, tunda ka
tafi fa rabona da wani mantina, hana rantsuwa dai Amadu da Umaru na siya min"
Junaid na kallon Heedayah murya can kasa yace "Lolly..." Heedayah ta wara manyan
idanuwanta tace "Sunana Heedayah" yace "No Lolly dai" dariya tayi tace "Lolly pop?"
Yace "No just lolly" ta langwabar da kanta bata ce komai ba, yace "Where is
Farida?" Tace "Tana gun Mami" kaka ta ajiye lemo da ruwan hannunta tace "To ae gaba
daya uwar ta hanata shigowa yau, ko ba Farida ba??? Kila don d'an aikin da take min
ne ma aka hanata shigowa wa ya sani, kasan bata dade da xuwa hutu daga makaranta
ba, shine fa muka sa6a sosai da ita, yarinya me hankali ga shegen aiki a cikinta,
ta iya aiki yarinyar wllh" Bowl din naman da take ta ci a boye ta dauko ta dire
masa tace "Daxu na sa masu aikin nan suka soya min kayana, nama ce ka ci iya cin ka
ba komai ka ji" Heedayah ta turo baki tace "Amma kince min ba nama bane" Kaka ta
galla mata wani harara tace "To meye hadina da ke? Ke dai ki raba kanki da kwadayi
da sa ido mace kike wllh" Junaid na murmushi ya dau ruwan gora daya ya bude ya fara
sha... A boye ya dinga ba Heedayah naman, da kaka ta shiga ciki kafin ta fito xai
yanka ya sa mata a baki, da ta aji alamar kaka ta fito sai ta boye fuskarta
shoulder dinsa, Daga karshe kaka tace "Ni dai ban ba Deedayah namana ba gaskiya,
idan ma ci take ban bata ba gaskiya" Dariya Junaid yyi yana kallon kaka, ita kanta
Heedayah dariyar take fuskarta a kafadarsa, kaka tace "Aa ba batun dariya bane
Junaidu, ba fa Amadu ya siyo min ba balle ace tana da rabo a ciki, kudin da nake ta
tarawa na bada a siyo min daxu, to meye xata wani makale maka tana kwadayi kai kuma
kana biye mata? Shegen kwadayi fa gareta wllh" Heedayah ta mike tana turo baki tana
ma kanta jagora ta nufi hanyar kofa xata fita, Kaka tace "Yanxu xuwa xata yi ta
hada ni da farar matar can..." Heedayah ta bude kofar ta fita daga parlon.... Sai
bayan isha Junaid ya shiga bangaren Mami, bayan sun gaisa Mami tace "Me ya hada
kaka da Heedayah?" Ya kalli Heedayah dake kwance saman kujera yyi murmushi yace "Ai
xa su shirya" Heedayah ta mike xaune tace "Ai baxan sake xuwa ba" Mami tayi
murmushi bata ce komai ba, Farida dake xaune kusa da Junaid ta matso kusa da shi a
hankali tace "Yaya tell me the truth, sbda birthday din Aunty Shaheedah ka dawo
ko???" Ya kalleta kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Eh" Irin kallon da yake
mata ya sa ta matsa kusa da shi da sauri tana dariya.... sai wajen karfe tara da
wani abu Junaid ya mike xai bar bangaren Mami, don Kaka ta aika Sajida ta kirasa
sau biyu kenan, Xai fita parlon Farida tace "Yaya to tsaraban mu fa?" Yace
"Tomorrow in sha Allah" yana kallon Mami yace "Sai da safe, daga can xan wuce" tace
"Me yasa idan ka xo gidan nan baka son cin abinci?" Ya girgixa kai yana kallon
Heedayah dake kwance saman kujera tayi bacci yace "Na ci abinci kafin in taho ne"
Mami tace "Toh shkkn, sai da safe" Ya dauke idonsa daga kan Heedayah yace "Allah ya
tashe mu lfya, daga haka ya fita parlon, dakin kaka ya tadda Shuraim tsaye daga
bakin kofa Kaka na cewa "Ai shi kansa Umarun ya girgixa da bala'i na jiya Shureen,
ynxu kuma dama kiransa xanyi ince idan bai mata magana ta janye gantalallen bakinta
da ta daura ma bawan Allahn ba nima xan yi Allah ya isa idan shi Umarun ya sake
shigowa gidan nan gaisheni, kowa sai yyi ta takama da d'an sa ba shknn ba, amma kan
me xata hanasa xuwa gidan nan bayan ga ni kakarsa" Tana ganin Junaid tace "Haba
Junaidu har sai furan da nono ya huce, Amadu fa nasa sai ya siyo min, ni ban ga ji
abun kunya ba ka xo har dakin nan ka fita baka ci komai ba" Ta gefen ido Shuraim ke
kallon Junaid, Junaid ya karasa dakin ya mika masa hannu, Shuraim ya mika masa nasa
sannan Junaid ya xauna yace "Kaka na ci abinci fa kafin na xo" kaka tace "Aa kai
dai so kawai kke ka tafi kana xagina a ranka ka xo dakina ban baka komai ba" Dariya
yyi ya ma rasa abinda xai ce mata, Shuraim xai juya kaka tace "Toh kaji abinda dai
ake ciki Shureen, kaya kuma rabi xan ba Deedayah, sauran rabin gaskiya kasuwar 'yan
koli xan kai ayi gwanjonsu, to fa bai siya min komai ba ni kamar wanda aka yi ma
baki, ko jiya sai da na sake mafarkin nan wai Sudess bai min tsaraba ba hankalina
ya tashi sosai" Shuraim yace "Ae dukka ya kamata ki kai ki siyar" Kaka tayi shiru
tana kallonsa, can tace "Allah?" Yace "Wllh" kaka tace "Atoh, me xata yi da su ma
idan an bar mata su ita ba ido ba, iyaka in d'an debar mata biskit din da swee in
ajiye mata" Shuraim yace "Hakan yayi" Kaka tace "Atoh, ga dai Rakiya kullum sutura
take mata, bbu abinda ta ragi yarinyar da" Shuraim ya juya xai fita dakin sai ga
Farida ta shigo rike da cooler, gefe ya ja ya tsaya, ta wuce ta ajiye ma kaka
coolern tace "Kaka gashi Mami tace in kawo maki" Kaka tayi kasa da murya tana
kallonta tace "Ita ta hanaki shigowa duk yau koh?" Murmushi Farida tayi tace "Aa fa
kaka" kaka ta ta6e baki tace "To da ta hanaki ai ita Deedayar da take tamu ta shigo
kuma ta wuni" Farida tace "Wllh Kaka ni ba a hanani shigowa ba kawai karatu nake yi
a ciki" Kaka tace "Ayyoo, to ban ji kin gaida Shureen ba, ko baki gansa bane"
Farida ta d'an turo baki tace "Ehh ban gansa ba" Kaka tace "Gashi can rakube gefe,
gaishe sa" Ta d'an kalli inda yake kafin tace komai ya juya yyi ficewarsa daga
dakin, Kaka tace "Au, to yyi ma kansa, Wai haushi yaji nan fa, kema dai in kin
gansa ki dinga gaishesa" Mikewa Farida tayi tace "Kaka sai da safe" kaka tace "Toh
sai da safe" Farida ta kara yi ma yayanta sai da safe sannan ta fita, kaka na
kallon Junaid tace "Kai ka ji fa Junaidu, tsaraba na fitan hankali Sudess yyi ma
Deedayah a kasar waje ni kuma ko abun sakace ban gani ba, shine nake tunanin in
siyar" Junaid dake saurarenta yace "Aa kaka, ki bar mata su, kar ki siyar" Kaka
tace "To ai ba duka xan siyar ba, sai kace wata axxaluma macuciya, 'yan kadan xan
deba in siyar in bar mata sauran" Furan da ta dama masa ta ajiye gabansa tace "Kaga
dai ko Shureen ban yrda na dibar ma wa ba, kuma yana tsaye na dama wllh" Washegari
da asuba Abba na dawowa daga masallaci ya ga kaka bakin kofar parlonsa tana
jiransa, yace "Lafiya kaka?" Kaka tace "Ehh to lafiyan kenan, magana nake son yi da
kai me muhimmanci, idan na jira sai ka shigo gaisheni bayan ka shirya fita ofiss ba
saurarata xaka yi ba sai kace sauri kake" Bai ce komai ba ya bude mata kofar
parlonsa ta shiga, ya bi bayanta, ta xauna saman kujera, tace "Kana ji na Amadu?"
Xaunawa yyi yana kallonta yace "Ina ji Baaba" tayi kasa da murya tace "Yauwa dama
kan maganan Shureen na shigo" yace "Lafiya dai koh?" Tace "Aa lafiya lau, na kawo
shawara ne kuma kasan ni bana bada shawaran banxa" Ya gyada kai yana sauraronta,
tace "Ni dai kaga yarinyar nan Farida ba karamin burge ni take ba wllh, gata da
biyayya iya biyayya, sannan bata da neman fada, uwa uba ga aiki, yini fa take yi
dakina tana min share share da goge goge, bata fiye min Deedayah ba sau dubu mai
makalewa saman gado? To shine naga gaskiya d'an ka Shureen xai dace da ita duk da
mugun halinsa, Kuma da kyar idan ba aure yake so ba, ko kai baka lura ba, a rabu da
mutum me shiru shiru kawai, na ciki na ciki, toh kuma shirun ma ai baxai bari ya
nemi matar auren ba, shine nake son ayi masa auren, na duba iya dubawa na, na gama
hange hangena naga ba kowa xai dace da shi ba gaskiya sai Farida" Tun da ta fara
magana Abba ke kallonta with surprise, Kaka tace "Aa ni dai ka daina min wnn kallon
kamar warce tace a kashe Shureen, gata fa nayi masa, sannan Rakiya yau watana hudu
da ita ko kallon banxa bata ta6a min ba, kwata kwata matar bata da damuwa kaf
halinta d'an ta Junaidu ya kwashe, wayayyiyar mata ce sosai, to don me baxan yi
kwadayin hada iri da ita ba..." Abba yace "Toh yanxu kaka ni da ba wai ina da iko
da Farida bane, ya kike son..." Kaka ta dakatar da shi tace "Aa wllh kai mijin
uwarta ce ai, kuma ai a gidan ka take yanxu" yace "Yaushe ta dawo gidan nawa? Ba
hutun makarantar kwana da suka yi bane ya sa ta xo? Gidan yayan babanta take fa
Baaba" Kaka tace "Toh ni ba ruwana sai in saka gyale a rakani gidan yayan uban
nata, Kai sai kayi ta yin abu kamar ba namiji ba meye kuma don ka nema ma d'an ka
auren Farida? Ni fa gata nake son yi ma Shureen din don baya magana kuma ni na san
aure yake so, kaga kira min Rakiyan yanxun nan ta xo ayita ta kare, Kar ka wani
bata min rai" Abba yyi kasa da murya yace "Karatu fa yarinyar take kaka, duka duka
ss2 nake jin take yanxu" Kaka tace "To ko Jami'a take ni ina ruwana, karatu na hana
aure ne dama bani da labari, ku dai kun cika wahala wllh, cewa nayi ka kira min
Rakiyan ta fito, in dai aka ga Shureen bai auri Farida ba to kilan kashe ni ku ka
yi kawai" Abba ya kasa cewa komai, kaka tace "To ko in kira Rakiyan da kai na ne
Amadu?" Daukar wayarsa yyi, yyi dialing number Mami, tana dagawa yace "Meet me at
my parlor now Rahinah" Bai jira ta ce komai ba ya katse wayar.... Da sallama Mami
ta shigo parlon, ganin kaka ta xauna kasa tace "Ina kwana kaka?" Kaka ta washe
hakora tace "Lafiya lau Rakiya, ya kwanan su Deedayah da Farida?" Mami tace
"Alhmdllh" Abba dai bai ce komai ba, Mami na kallonsa tace "Ga ni barrister" Ya
kalli kaka yace "Ga ta kaka" Kaka tace "Kai Amadun
nan dai wani solobiyo ne wllh, to kai baxa ka yi mata bayanin ba sai ni? To ai duk
kai ka cuci Shureen don kaf halinka ya dauka amma banda mugun halin shi wnn na
uwarsa ne, Rakiya kina ji na, ba wani abu bane dama ni dai Farida ce ta kwanta min
can cikin raina, a gaskiya Ina son yarinyar wllh, shine na xo na samu Amadu Ina
neman alfarman a ba ma jikana Shureen aurenta...." Tana kai wa nan ta fara matsar
kwalla, Mami da ta bude baki tana kallonta with shock ta kalli Abba tace "I don't
get her barrister, as in??" Abba ya sauke ajiyar xuciya bai ce komai ba dai, Mami
tayi murmushin karfin hali tace "To kaka ai karatu Farida take yi yanxu, Kuma....."
Kaka ta dakatar da ita tace "Kuma me? Ku dai gantalallu ne marasu mafada, karatu
ance maku yana hana aure ne, kinga idan na biye ta taku kawai mahakuciya xaku mayar
da ni, ni naga dacewan hakan shi yasa nace ayi, ynxu ni ba ni da wata magana da ku
kuma...." Tana fadin haka ta mike ta fita parlon, Abba sai kallon Mami da gaba daya
mood dinta ya canxa lkci daya yake, can tace "Plss Barrister kayi ma kaka magana,
try to let her understand cewar ba mai yiwuwa bane ni bani da iko da Farida wajen
yayan Mahaifin ta take, let not make things complicated pls Barrister" shi dai bai
ce mata komai ba, kaka na fita dama wayarta ta dauka ta lallaba ta kai ma Farida
can bangaren Mami wai ta kira mata Junaid, junaid na daga kiran kaka ta fita da
sauri, tayi kasa da murya suka gaisa tace "Kana ji na Junaidu, duk Inda kake ka
taho yanxun nan xaka kai ni anguwa ko Rakiya kar ka sanar ma, kana isowa bakin get
ka kirani sai in fito" Junaid dake kwance yace "Toh bari in taho kaka" tace "Yauwa
Allah maka albarka, Ina jiran ka yanxun nan" daga haka ta katse wayar ta wuce
dakinta tana cewa "Gantalallu wa enda basa son abun arxiki, ni bana biye ta taku
ba" Kaka na komawa bangarenta sai ga Abba ya shigo da sallama, ya xauna saman
kujera gaba daya he look confused, can yace "Kaka yanxu kinga cikin watan nan xa a
fitar da Heedayah waje gyaran idonta, so yanxu kinga ai babu wani abu a gabanmu da
ya wuce wnn..." Kaka tayi saurin cewa "Haba?? Kuma sun ce idon xai gyaru kuwa? Amma
dai da ni xa a je koh? Kasan bata da kowa sai Allah sai ni" Abba yace "In sha
Allah...." Kaka tace "Toh yaushe ne tafiyan in fara hada kayana?" Yace "Nan dai da
sati uku" Kaka tace "Atoh Allah ya kai mu lafiya, Allah ya dubemu idonta ya bude ni
dai" Abba yyi kasa da murya yace "Don haka kaka ki bar ko wani xance yanxu mu ji da
gyaran idon da xa a fita yi" kaka ta kallesa tace "Atoh shkkn na bar xancen har sai
idon Deedayata ya bude" Abba ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya, ya mike yace
"Bari in je kaka, a taya mu da addu'a, ana kan processing din fitan ne" kaka tace
"To wani kasar xa aje?" Yace "India" kaka ta washe baki tace "Xa mu ga su Hamita da
muganbo kenan Amadu??" murmushi kawai Abba yyi ya fita daga dakin kaka ta mike ta
daga hannu sama tace "Allah ka dubi yar marainiyar Allah ka bude mata idanuwanta,
ka bude mata ido ya Allah ko son jikinta xai ragu" Karfe takwas dot Junaid ya kira
kaka yace yana kofar gida, ta dau Hijabinta ta boye ta fito parlor tana kalle kalle
xata fita, Shuraim dake xaune dinning yana shan tea ya bi ta da ido har ta fice
daga parlon da sauri, Junaid ya sakko ya bude mata back seat yana gaisheta da
ladabi, ta amsa tana washe baki tace "Allah yayi maka albarka Junaidu da bani da
kai ai da nayi kuka yau, ni dai wllh ka fiye min kowa ma" murmushi kawai yyi ya
tada motar, sai da suka bar layin suka hau saman titi yace "Ina xa mu kaka?" Tayi
kasa da murya tace "Yau xumunci kawai nake son yi, kaga ai bai dace ace har yanxu
ban san kowa naku ba, to don haka gidan yayan Mahaifin ka xaka kai ni mu san juna"
Junaid was so surprise ya dinga kallonta ta madubi yace "Gidan Baffanmu?" Kaka tace
"Ehh shi, ai xa a samesa yanxu da safe koh?" Yace "Ehh na bar sa a gida" Kaka tace
"To maxa kai ni kar yyi ficewarsa, gwara xumuntakar tamu yyi karfi" murmushi kawai
Junaid yyi ya dau hanyar gidan yayan late Abbansa.

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Parking Junaid yyi a compound din Baffan sa, ya sauka ya bude ma kaka bayan motar,
ta fito tana kare ma kantamemen gidan kallo baki bude tace "Nan ne gidan kawun
naka?" Junaid yace "Nan ne" kaka tace "Ikon Allah, to mu shiga, Allah ya sa bai
fita ba dai...." Junaid ya shiga gaba tana biye da shi yace "Yana nan ai, ga
motarsa" Kaka ta kalli motar da ya nuna mata tace "Kamar irin motar Umaru kuwa"
Babu kowa parlon da suka shiga, Kaka ta xauna tace "Wato basu tashi ba kenan ana ta
bacci" Junaid yyi murmushi yace "Bari in masu magana" daga haka ya wuce sama, kaka
ta dinga bin parlon da kallo ta rike ha6a murya can kasa tace "Toh ai masu kudi ne
su ma, ba gidan tsiya Shureen dina xai fada ba, ko gidan Umaru bai kai haka ba" Ba
a dau lkci ba Junaid ya dawo tare da wata dattijuwa, Ta xauna tana kallon kaka da
fara'a tace "Sannu da xuwa Mama, Ina kwana" Kaka ta kalleta tace "Lfya lau wllh,
kece matar gidan?" Matar na murmushi tace "Ni ce Mama" Kaka tace "Atoh ya yara, ya
gida" Matar tace "Alhmdllh wllh, fatan kun xo lfya?" kaka tace "Toh Alhmdllh, ba ma
wanda yasan na fito sai shi Junaidun, nace dai yau bari in xo inyi xumunci ku san
ni in san ku, bana biye ta Rakiya da Amadu ba, ko karyawa ban yi ba wllh na fito"
Matar tace "Ikon Allah to bari a kawo maki kayan kari yanxu, tashi mu je daga ciki
Mama, sannu da xuwa" Kaka tana washe baki mike tace "Toh" har parlonta ta kai kaka,
ba a dau lkci ba aka cika gaban kaka da kayan karin kumallo, flask din ruwan Lipton
me kamshi, soyayyen dankali da kwai da plantain, katon bread, sai wainar shinkafa
da lafiyayyen taushe, ga farfesun kayan ciki a gefe, Kaka na kallon masu aikin dake
ta jera mata abincin tace "Babu darduma in sauka kasa??" karamin carpet me laushi
suka shimfida mata ta sauko kasa bayan ta cire Hijabin ta, komai sai da kaka ta
diba ta ci a abincin, sai da taji tayi nak murya can kasa tace "Toh ko nan nace xan
dawo da xama ai bbu me ce min komai tunda an xama daya yanxu..." Sallama aka yi
kofar parlon Kaka ta amsa wani dattijjo da baxai wuce 65 ba ya shigo parlon, kasa
ya xauna yace "Sannu da xuwa Baaba" Kaka na washe baki tace "Sannu, kai ne kawun
Junaidun?" Yace "Ehh nine, Ina kwana" Kaka ta gyara xama tace "Lafiya lau, yau dai
nace bari in xo in ganka ka gan ni, idan na biye ta uwar Junaidu baxa ayi xumuncin
ba ma, kasan yaran ynxu basu san amfanin xumunci ba" Yyi dariya yace "Gaskiya ne
Baaba, to ya ku ka baro mutan gidan?" Tace "Lafiya lau, ko sanin na fito ma basu yi
ba, nace inyi maxa in xo kar ka fita, tunda shi Amadu na ga karfe takwas xuwa tara
yake ficewa" Yace "Wannan gaskiya ne" Kaka tace "Toh bayan xumunci kuma a gaskiya
har da alfarma na xo nema a gun ka" Ya xauna da kyau yace "Toh ina sauraron ki
Baaba" Tace "Ba wani abu bane d'an nan, jikana Aliyu na xo nema ma auren 'yar ka,
wato Farida, kaga dai Aliyu ni na haifi ubansa Amadu, tunda nake ban ta6a ganin
yaro da ya tashi bashi da matsala irin Aliyu ba, bbu ruwansa da kowa, ba shi da
abokin fada, kai in takaice maka shi ba me magana bane ma, to shine na ya6a da
hankalin farida tunda ta xo kuma ta xauna dakina, komai ita ke min wllh, ko nayi
laifi da nayi wnn tunanin bawan Allah, amma dai ya ma sunan ka tukun" Yace "Sunana
Aminu" Kaka tace "Toh ai sunan babana kenan, Allah sarki, to yanxu ya kaga..." Yace
"Batu ne mai kyau wannan Baaba, amma sai dai Farida ynxu karatu take wllh" Kaka
tace "Oh oh Allah, karatu na hana aure ne wai dama? Ku me yasa ku ka bari boko yyi
maku kaca kaca haka, Shi kansa Amadun fa haka yace min, meye a ciki idan anyi auren
ta ci gaba da karatun ta, ynxu shekararta nawa ma dai tukun?" Yace "Bata cika sha
shidda ba ma" Kaka tace "Shine tayi girma haka? Toh kaga kuwa ai aurar da ita shine
rufin asirin mu da ku, kaga dai takanas na taso da kafafuwana na sameka a gida sbda
alkhairin da nake nema da ku, a gaskiya idan kace min A'a raina xai baci Aminu, da
girmana na taho wajenka.... Kuma da Rakiya ta san gidan banxa ne gidan Amadu ai
baxa ta shigo ba...." Yana murmushi yace "Gaskiya ne Baaba, in sha Allahu tunda ba
fin karfina alfarmar da kika xo nema yyi ba xanyi bakin kokarin ganin komai ya tafi
yanda kike so, amma sai Farida ta gama secondary in sha Allah" Kaka tace "Toh tunda
dai ka amsa ai shkkn, kwana nawa ne xa a ga ta gama sakandarin, shi ma massers
dinsa yake yi a Zaria, kaga sai su gama lkci daya kenan, bari anjima shi xan ma
kira ya mayar da ni gida sai ka gansa, yana nan ko yatsa ka sa masa a hannu baxai
ciza ba, yaron kirki me girmama na gaba da shi, Kai ni ko rashin kunya na jika da
kakan nan ma ni bai ta6a min ba, tamkar uwarsa haka yake min biyayya" Shi dai
murmushi kawai yake yace "Toh shkkn Baaba xan fita wajen aiki sai na dawo, ai kina
nan?" Tace "Aa ina nan kilan har ka dawo, yanxu fa na xo" yace "Toh maa sha Allah,
sai anjima" tace "Allah maka albarka" ya amsa da Ameen ya fita. Yana fita wayar
kaka ya fara kara ta fiddo a jaka da sauri, da yake ta san Inda ake dannawa ta
danna ta kai kunne, Muryar Mami taji, kaka tace "Ke ba fa wani waje naje ba, gidan
ta salla na tafi, anjima in sha Allahu xan dawo" Mami tace "Toh shkkn, amma ba
sallama kaka" Kaka tace "Ehh to da yake tafiyar ta gaggawa ce, anjima dai xan dawo
in sha Allah" Mami tace "Toh Allah ya dawo da ke lafiya" kaka tace "Ameen" daga
haka ta katse wayar ta ajiye ta jawo sauran farfesunta tana lasa. Har aka yi Magrib
Kaka na gidan Baffansu Junaid, Matarsa kuwa Hajiya Zulaiha bata bar Kaka ita kadai
ba, tare suka yini, a xamansu na yan awannin nan abinda kaka ta manta ne kawai bata
gaya mata ba, tarihi iri iri, Wanda ya kamata da Wanda bai kamata ba, tun mijinta
na da rai har sanda ya rasu, amma ko da wasa kaka bata gaya mata halin Mumy ba,
Hajiya Zulaiha dake yanka ma kaka kankana bayan anyi sllhn Magrib tace "Na kirasa
yana hanya ynxu Mama" Kaka tace "Toh kinsan shi xai mayarda ni gida kar in gigita
'ya yana suyi xaton 6ata nayi shi sa na damu" Hajiya Zulaiha tayi dariya tace "Kila
yana can gun budurwar sa tun da kika ga har war haka bai shigo ba" Kaka tace "Au,
yana da budurwa kenan?" Hajiya Zulaiha na dariya tace "Kwarai kuwa" Kaka tace "ikon
Allah, ko da yake ga Shureen ma Ina kokarin ganin yayi aure nan da 'yan watanni
balle Junaidu, da kyar idan bai girmi Shureen ba ma" Hajiya Zulaiha tace "Lallai
kam" Kaka tace "Ko da yake ga Farida ma naji shekarunta ba wasu shekaru bane amma
duk ta balaga, kusan sa'ar Khadijahn Amadu ce fa, Ita kuma Rabi'ah sa'ar Deedayah
Ina jin, don duk kwailaye ne" Hajiya Zulaiha dai tayi dariya ta ajiye ma kaka
kankanan tace "Bari in je inyi sllh Mama, amma da kawai kiyi kwanan ki a nan Mama"
Kaka tace "A'a ba mutunci gare su Amadu ba sai su iya min fada ba ruwana, bari dai
in tafi ba dai na ga gida ba" Hajiya Zulaiha tace "Toh shkkn Mama" daga haka ta
fita parlon.... Tana fita da minti sha biyar Junaid ya shigo, kaka tace "Ashe kana
da budurwa Junaidu, yanxu matar kawunka ke ce min tadi ka tafi" yace "Aa gidan
abokina nake" tace "Au, to in tashi mu tafi kada su Amadu su yi ta nemana koh?"
Yace "To mu je kaka, ai kin ci abinci" Kaka tace "Idan ma nace ban ci ba, ba sai
Allah ya kama ni ba, Tuwo ce fa malmala uku aka saka min ga miyar kubewa duk nama
da Ganda ga kifi, ga kuma lemo me sanyi... To ina xan samu haka gidan Amadu??
Gaskiya matar nan ta san mutunci, baka ga ba wllh sai ji take da ni, komai ta
rarumo ta kawo min, daxu da rana har kwadon zogala ta min bayan shinkafa da miya da
uban nama da ta xubo min, ni dai gaskiya an karrama ni a gidan nan, ai Rakiya sai
dai ince Allah yyi mata albarka kawai, danginta sun san mutunci kam" Murmushi kawai
Junaid yyi yace "Idan kin gama shiryawa Ina parlor kaka" Kaka tace "Toh, d'an
Albarka" Sai bayan kusan minti ashirin kaka ta sakko da handbag dinta, tana kallon
yan matan gidan guda uku dake xaune parlor tace "Toh ko Sudess ma idan ya samu daya
daga cikin wa ennan bai gode ba, ynda yan mata ke wahala ynxu...." Har parlon
Baffan Junaid kaka ta shiga, yace "Aa Baaba ai na xata kwana xa kiyi a nan" tace
"Aa su Amadu xa su min fada" Yace "Ikon Allah, toh Junaid xai maida ki amma" tace
"Eh yana jirana ma yanxu haka" mikewa yyi yace "Toh Ina xuwa Baaba" yashiga dakinsa
sai gashi ya fito ya mika mata dubu goma da ladabi yace "A siya goro Baaba" Kaka ta
amsa ta saka a jaka tace "A'aaahh ayi haka d'an nan, ai da ka bar shi wllh, toh
Allah yayi maka albarka, nagode ka ji" yace "Godiya ya tabbata ga Allah" rakata yyi
har xuwa parking space tare da Hajiya Zulaiha da ta bata atamfa da turarurruka,
tayi ta daga masu hannu tana washe baki har motar ya fita gidan, bayan sun hau titi
tace "Gidan ma babu wahalan ganewa kaga idan xan dawo baxan sha wahala ba koh" Yace
"Haka ne kaka" Tare Junaid da Kaka suka shiga parlor, Rabi'ah dake kwance parlon
tana kallon Tv tace "Sannu da dawowa kaka" kaka tace "Yauwa.... Junaidu tafi ka
dauko min Deedayah ga sauran nama na kulle mata a leda" yace "Toh" daga haka ya
nufi part din Maminsa, Rabi'ah tace "toh mu fa?" Kaka da ta nufi dakinta tace "Uwar
me na hada dake banda dai ke jikata ce, idan Maryam ce ko Amadu kya gaishesu a
kwance?" Daga haka ta shige dakinta. Mami na kallon Junaid bayan ya gaisheta tace
"Daga ina ku ke?" Yace "Gidan Baffanmu" Mami tace "Baffan ku? Kai da kakan?" Yyi
yar dariya yace "Da sassafe ta kirani wai in xo in kaita" Mami ta dinga kallonsa da
mugun mamaki tace "Sai ka kai ta?" Yace "To meye a ciki Mami?" Mami ta mike tace
"Why didn't you call and ask for my opinion Junaid???" yyi kasa da kai yace "Mami
naga ba wani abu bane, ai kowa ya san tsoho..." Xata yi magana aka bude kofar,
shiru tayi kaka ta shigo tace "Ina Deedayan?" Mami tace "Sannu da xuwa kaka" Kaka
tace "Yauwa Ina Deedayah ga nama na kullo mata" Mami tace "Suna parlon Barrister"
Kaka tace "Kai Junaidu tafi ka dauko min ita, Ina iya shiga parlon yanxu Amadu ya
rufeni da bala'i" Mikewa yyi ya fita parlon, Kaka tace "Wllh anguwa naje ke dai
Rakiya, mutum yyi ta xaman gida kamar bashi da jama'ah" daga haka ta fita ta bi
bayan Junaid
da sauri, tun kan ya shiga parlon Abba ta tsayar da shi tayi kasa da murya tace
"Kar ka gaya masu daga Inda muke, cewa kawai xakayi a bakin titi ka ganni ka dauko
ni, har ita Rakiyan kar ka gaya mata kaji" Yana murmurshin karfin hali yace "Toh"
daga haka ya shiga parlon ta koma nata dakin.... Washegari Sunday da safe Shuraim
ya shiga gaida Abbansa, Abba na aiki system dinsa ya amsa yace "Anjima xaka ajiye
Farida makaranta" Ya kalli Abba amma bai ce komai ba, Abba yace "Before then, xan
maka transfer ku je tare tayi shopping, da yamma sai ka ajiye ta schl din" yyi kasa
da kai yace "Toh" Abba yace "That's it, Kai yaushe xaka wuce Zarian?" Yace "Gobe da
safe" Abba yace "Allah ya kai mu" mikewa yyi, ya ma Abbansa sallama ya fita, direct
dakin kaka ya nufa, Kaka na ta gyara kayan da ta binciko a press din dakin,
Heedayah kuma na kwance saman gado tana cin naman da kaka ta kawo mata, kaka kuma
na bata labarin irin abubuwan da ta ci a inda taje jiya, Heedayah tace "Toh baki
gaya min sunan wajen ba...." Kaka tace "Toh wai ina ruwanki, ke dai kawai ki bari,
akwai abinci a gidan" Heedayah ta tallabi chin dinta tace "Toh shine ni baki je da
ni ba?" Kaka tace "Ai kinsan a boye na bar gidan shi yasa, amma ba gashi na kullo
maki sauran nama ba" Shuraim ya bude kofar ya shigo dakin, kaka tayi tsit da
bakinta tana ci gaba da linkin ta, Murya can kasa Heedayah tace "Kaka waye?" Kaka
tace "Iska ce ta turo kofa" Heedayah ta turo baki tace "Na xata wnn Shureen din nan
ne...." Kaka tace "Shureen kuma, me xai shigo ya min, baki ga tun wayewar gari bai
ko shigo gaidani ba" Heedayah tace "To kaka wai me yasa yake yi ma mutane mugunta?
Ni fa bana son sa" Kaka tace "Haka nan Allah ya halicce sa, Kuma ya xa ayi ki so
sa, ke da baki hada komai da shi ba...." Heedayah dai tayi shiru sbda kamshin
turare da ta fara ji, kaka tace "Tun yana karami duk da baya magana haka yake
narkan 'ya yan mutane, yyi ta cin xali, uwarsa kuma tayi ta goyon bayansa" Heedayah
dai bata ce komai ba, Kaka tace "Ya kika yi shiru kuma" Heedayah ta turo baki a
hankali tace "Bayan yana dakin xaki ce min baya nan" Kaka ta kyalkyale da dariya,
Shuraim da ya wani hade rai yana kallon Heedayah yayi kwafa ya juya ya fice,
Heedayah dai bata ce komai ba ta wani cinno baki, kaka tace "Atoh, yarinya sai
fitsara da gulma wai don ma bbu ido..." Da rana Farida ba don ranta ya so ba ta
shirya xa su je shopping kamar yanda ita ma Abba ya gaya mata, Heedayah ma ta sa
Hijab dinta don tare Mami tace su je, can kofar gida yyi parking don ma kar Mumy
tayi noticing xa su fita, Farida Ta bude ma Heedayah back seat tana rike da
hannunta ta shiga, ita kuma ta shiga gaba, ko kallonsu bai yi ba ya tada motar suka
bar layin. Wani shopping mall xai shiga Farida tace "A na gaban nake yi shopping,
nan ba dukka abinda nake so suke da shi ba" Ya wani daure fuska bai dai ce komai ba
ya shiga yyi parking ya kashe motar, Farida ta dauke kai ta ta6e baki ta bude motar
ta sauka, ta bude side din Heedayah ta kama hannunta ta sauka, ta gefen ido yake
kallon Heedayah da Hijab dinta ya wuce gwiwa da kadan, sae pink wandon dake jikinta
amma bai kai ankle dinta ba, Farida xata rike hannunta su wuce ciki ya fixge hannun
yace "Wa xata bi a hakan???" Farida ta kalli Heedayah daga sama har kasa, ya bude
bayan motar yace "Maida ta ciki" Farida tace "But there is nothing wrong with her
dressing, I dressed same also" Da kansa ya mayar da Heedayah da ta fashe da kuka
cikin motar ya rufe, Farida ta rungume hannunta ta hade rai ta jingina da motar
tace "Ni na ma fasa shopping din" Wani kallo yyi mata yace "Gaura maki Mari xan yi
idan baki shiga mun wuce ba" Ta fashe da kuka tace "Toh why will u lock her all
alone cikin motar, don't you know there is heat, ni baxan bar ta ita kadai ba" Atm
card dinsa ya ciro ya mika mata still frowning his face yace "Double five, double
zero.... Tafi kiyi shopping dinki ke kadai" Ta leka motar tace "Toh xaka tsaya da
ita ne" Kin bata amsa yyi, ta amshi ATM card din ya bude maxaunin driver ya shiga
ya xauna, A hankali Farida ta nufi cikin mart din. Heedayah dai ta daina kukan da
take sai share idonta take, ta gaban madubin motar yake kallonta, bayan kusan minti
goma jin shirun yyi yawa ta matsa a hankali kusa da driver seat ta sa hannu xata
lalabu ko akwai mutum a nan, Kirjinsa ta ta6a ta janye hannunta da sauri ta koma ta
xauna tana turo baki... Bayan wani 15 mins din sai ga Farida ta fito da labourer
dake dauke da ledojin kayanta, Bude booth yyi kafin su karaso, mutum ya saka kayan
gaba daya a ciki ta bude jakarta ta ciro kudi ta basa sannan ta bude back seat ta
shiga ta rufe tana kallon Heedayah tace "Didi na siyo maki chocolates and Biscuits
har da teddy..." Heedayah ta wara ido ta kamo hannunta tace "Thanks Farida" Ya d'an
ta6e baki ya tada motar yayi reverse ya bar shopping mall din. Karfe biyar saura
Farida ta gama shirin komawa makaranta, Heedayah har da hawayenta daga Inda ta
xauna ta takure kanta, Mami da ta ji tausayinta sosai tace "Ku tafi tare Farida,
sai ya dawo da ita" Farida da duk jikinta yyi sanyi ta kama hannun Heedayah suka
fita parlon xuwa dakin Kaka su yi mata sallama, Shuraim na xaune main parlor da
makullin motarsa cox Mumy bata gidan, Ya bi su da kallo yace "If she is not
changing that clothe she shouldn't bother entering my car..." Farida ta juya tana
kallonsa don tun da take bata ta6a jin yyi magana me tsayi hka ba, ta dauke kai ta
ta6e baki, Heedayah ta rike hannun Farida sosai kamar xata yi kuka tace "Pls kice
Mami ta bani dogon Hijab in sa" Farida ta d'an ja tsaki suka koma bangaren Mami,
Mami na kallon Heedayah daga sama har kasa tace "Does he have any business with her
dressing, ko ya siya mata Hijabs ne? Or is he stupid??" Farida dai bata ce komai ba
ta dauko ma Heedayah wani Hijab din har kasa ta saka sannan tayi ma Mami sallama
suka fita, Kaka har da kwallarta, ta daure ma Farida cin cin da bai fi kwaya shidda
ba a leda ta mika mata tana cewa "Ashe baki nan xa a kai Deedayah India" Farida
tace "Kilan muna jarabawa lkcn" Kaka tace "Toh ai shkkn, Amadu yace min nan da sati
uku ne, ga kayana har na hada" Farida tace "Toh Allah ya kai mu" Kaka ta dauko
maltina daya ta kara mata, ta rakasu har bakin motar Shuraim, tana kallon Shuraim
tace "Toh ko in dauko gyale mu tafi tare Shureen?" Ya gyara xama yace "Ehh" Da
sauri ta juya ta koma ciki, ya tada motarsa ya fice daga gidan, Heedayah ta rufe
fuskarta a Hijab tana dariya a hankali, Farida kuwa sai hararansa take.... Suna Isa
makarantar Shuraim yyi parking, tsadaddun motoci ne iri iri an kawo students,
Farida ta kamo hannun Heedayah tace "Till I come back Didi..." hawaye ya kawo
fararen idanuwan Heedayah, ta madubi Shuraim ke kallonsa, Jikin Farida yyi sanyi
tace "Baxan dade ba xa mu yi hutu...." Heedayah ta fashe da kuka sosai ta daura
kanta saman jikin Farida, Shuraim ya hade rai yace "Malama sauka ki bude booth ki
sauke kayan ki" Ta galla masa wani harara tana share idonta ta sauka motar, sauka
yyi shi ma don sauke mata kayan don ya san sun mata nauyi, Heedayah na jin haka ita
ma ta bude motar ta sauka, Tsaye yake jikin black ride dinsa ya rungume hannu
idonsa sanye da bakin space, he looks so gentle and calm, dai dai saukowar
Heedayah, a hankali ya cire Glasses din idonsa yana kallonta, Shuraim kawai gani
yyi ta ci karo da daya daga jakan Farida da ya sauke kasa Farida kuma tana gun
booth tana fiddo kananun ledojin, kafin ya karasa ya riketa tuni ta fadi kasa, shi
kansa Mutumin har ya taho da sauri kafin ta kai kasa ganin Shuraim sai kuma ya
tsaya cak, Shuraim ya dagota yace "Wa yace ki sakko?" Ta fashe da kuka tana yarfe
hannunta tace "Wayyo na buge kafana, and there is sand in my eyes" Tuni Farida ta
durkusa kusa da su tana ma Heedayah sannu, da ma sauran mutanen wajen, Bude idon
Shuraim yyi, yyi blowing mata iska gently, ganin yanda ake kallonsa kawai ya dagata
ya bude back seat ya sa ta ciki, ya karasa sauke ma Farida kaya yace "That's all"
daga haka ya bude back seat din ya shiga yana kallon Heedayah dake ta murxa idonta
matsawa yyi kusa da ita ya dafa forehead dinta yana kallon cikin idon, ta kauda
kanta kamar xata yi kuka tace "Ya daina" Saketa yyi still looking at her eyes....
Tuni Mutumin ya shiga mota ya mance abinda ya kawosa bakin makarantar ya tada
motarsa yana kallon motar Shuraim ta madubi, Shuraim ya daga hijab dinta ya kalli
kafarta ya ga just little bruises ne a farin kneel dinta, Bude motar yayi ya sauka
ya koma driver seat, ya tada motar yana fara tafiya Mutumin ya bi bayansa......

*pls fans masu son min magana su dinga typing instead of voice note, cox listening
to voice note is stressful wllh, idan typing ne cikin few seconds mutum xai karanta
yyi replying nn take, but voice note yana cin time when they are other messages to
reply to, thanks for understanding*

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Shuraim bai yi wani nisa ba ya kula da motar bayansa dake bin sa, slowly ya dinga
tafiya to see idan motar xai yi overtaking dinsa ya wuce, but sai ya ga motar ya ki
yin hakan sae ma rage nasa tafiyar da yyi shi ma, Shuraim ya samu waje yyi parking
har sannan yana kallon motar ta madubi, Mutumin dake cikin motar dake ta lura da
Shuraim shi ma kuma ya san Shuraim ya gano yana bin sa ne kawai yyi wucewarsa bai
tsaya ba, Shuraim ya bi motar da kallo har da plate number din motar, juyawa yyi ya
kalli Heedayah dake xaune bayan motar, she looks so sad kiris ya rage ta fashe da
kuka daga ynda tayi da fuskarta, dauke kansa yyi ga mamakinsa har sannan motar bai
bace masa ba, sbda a hankali me motar ke tafiya kan less busy road din, Shuraim ya
kalli layin dake gefensa kawai ya karya kan motar ya shiga layin.... Sai kusan
Magrib Shuraim ya isa gida, a hankali yake tafiya ganin motar Mumy dake tsaye bakin
gate tana jiran me gadi ya bude gate din, sae da ta shiga snn yyi parking gefen
flowers dake gaban gate din ya kashe motarsa, Mai gadi na ganin baxai shiga gidan
da motarsa ba ya kulle gate din, Shuraim ya juya yana kallon Heedayah dake bacci
bayan motar, sauka yyi motar ya kulle ya nufi cikin gidan, tsaye ya ga Mumy alamar
shigowarsa take jira, ya karasa Inda take ya gaisheta tace "Daga ina kke da
magariban nan" Yace "Asibiti" tace "Ohk, goben xaka tafi Zarian?" Yace "In sha
Allah" tace "Toh nima xan je Zarian gobe, amma bance ka gaya ma kowa ba, karfe nawa
xaka fita?" Yace "Takwas..." Tace "Toh kayi hakuri ka bari karfe tara, kafin nan
Abbanku ya fita" Shi dai kallonta kawai yake don ya san basu da 'yan uwa a Zaria,
can yace "Me xaki je ki yi a Zaria Mumy?" Mumy tace "Yar Hajiya Sadiya ba can take
aure ba, to ta haihu gobe suna, ko barka ban je ba, kuma idan na gaya ma Barrister
ba lallai ya yrda ba, ni ko Sadiya ai ta wuce haka a wajena" Shuraim yace "Aa da
dai ki fara sanar ma Abba Mumy" Mumy ta daure fuska tace "Toh ban yi niyya ba" Bai
kuma cewa komai ba ta juya ta nufi cikin gidan ya bi ta da kallo har ta shiga
parlon snn ya juya ya koma waje, Bude back seat yyi Heedayah ta bude ido da sauri,
hannunta ya kama ya saukar da ita daga cikin motar ya kulle motarsa, har da xai
mika ma Mai gadi hannunta ya kai ta ciki sai kuma kalli cikin compound din ya shiga
yana rike da hannunta, yana isa balcony ya bude kofar parlon yana kallon ciki, bbu
kowa hakan yasa ya shiga parlon da ita ya kai ta har kofar dakin kaka sannan ya
juya ya fita xuwa masallaci, Kaka da ta fito daga bandaki tayi alwala tace "Waye
wnn?" Heedayah tace "Ni ce" Kaka tace "Toh ai na ganki, sai yanxu ku ka dawo kai
faridan makaranta?" Heedayah ta gyada mata kai, Kaka tace "To ina Shureen din?"
Heedayah tace "Nima ban sani ba, ya wuce" Kaka ta ta6e baki tace "Toh me yasa kika
yo min nan, Rakiyar bata nan ne" Heedayah ta turo baki tace "Toh ai shine ya kawo
ni" Kaka tace "Toh ni dai na gyara dakina na share, na sa turaren wuta, gadon ma
yau ko hawa ban yi ba tun da garin Allah ya waye" Heedayah ta turo baki ta juya
tana laluba hanya da hannunta ta fice daga dakin, Kaka tace "Haka kawai ba kya ma
mutum taimakon komai sai dai ki lalata waje gantalalliya" Mumy da fitowar ta
kitchen kenan ta bi Heedayah da ido har sai da ta isa kofar parlon Mami, Dai dai
fitowar Sajida dakinsu ganin Heedayah ta karasa don ta bude mata kofar, juyawa Mumy
tayi ta wuce parlonta kafin Sajidan ma ta ganta... Sai da Heedayah ta shiga ciki
sannan Sajida ta kulle kofar ta wuce. Karfe tara da rabi Mumy ta kira wayar
Shuraim, yana xaune dinning da cup din shayi a gabansa, Ya daga kiran Mumy tace
"Abbanka fa ya fita, baka gama shiryawa bane ko in tafi in hau motar haya kawai?"
Yace "Na gama" katse wayarta tayi, ya mike ya tafi dakin kaka, Heedayah ce kwance
saman gadon tana ma Doll din da Junaid ya siya mata kitso, Kaka kuma na bandaki
tana wankewa, Heedayah ta dakatar da kitson da take ba Doll din jin an bude kofa
tace "Waye?" Ya kalleta ya dauke kai, bata kuma cewa komai ba sbda kamshin da ta
ji, Ya xauna yana jiran fitowar kaka, sai ga ta ta fito tana cewa "Masu aikin
jaraba kawai sun bari bandakina xai dafe in shiga uku in lalace, Banda dai ma
lalacewa ta sameni ina ni ina bar masu bandakina su dinga wanke min...." Shuraim
dake ta kallonta yace "Xan wuce Zaria" Kaka tace "Tohhh da sassafe haka shureen"
Yace "Eh" Tace "Toh Allah ya kiyaye hanya, ni dai ko kwandala bani da shi a dakin
nan, dama Umaru ne me bani, gashi yau kwana daya bai xo ba" Mikewa yyi ya mayar da
wayarsa aljihu, tace "Toh ko dari biyar baxa ka d'an bani ba Shureen, bani da ko
sisi fa" Yace "Ni da bana maki komai kuma yau xa ki ce in baki kudi?" Kaka tace
"Toh ai dama idan ba kai ba waye me min, shi Sudess yan matan da ya tara gabansa ma
sun ishesa, Amadu kuma kaga ynxu ta kudin da xai kai makauniyar nan gyaran ido
yake, da kyar idan ba sai an kashe kusan miliyan biyar ba tunda India ne, ai kaga
ta kassara min d'a na kawai, wa gareni dama banda shi, shi din kuma ga uban abinda
ke gabansa ba dangin iya balle na baba, Umaru dama yau sati rabona da kudinsa, sae
dai ya xo ya karaci xamansa ya fice, toh ya ake son inyi da raina" Shuraim ya tabe
baki yace "Toh nima bani da shi" Daga haka ya fita daga daki, kaka ta bude baki ta
bi sa da kallo, can kuma tace "Toh kada Allah ya sa ka samu, marowacin banxa kawai
solobiyo" Ko saurarenta bai yi ba, yana fita sai ga Mumy ta shigo dakin, Ta xauna
ta gaida kaka, kaka ta amsa xata koma bandaki, Mumy tace "Kaka xanje gidanmu ne
Salima bbu lafiya" Kaka ta dawo tace "Toh ba dole ba, yarinya sai gantalin duniya
take an rasa me gaya mata gaskiya, kamar abun arxiki Amadu ya daukota kusan shekara
sha biyu da suka wuce amma uwarki ta amshe ta wai autarta, to yau ina uwar taki
take, ba gashi ta tafi ta barta ba, yarinya duk ta lalace wa yasani ma ko bin maxa
take, da ynxu tana wajen Amadu har ya aurar da ita ta haifi 'ya yanta...." Mumy dai
bata ce ma Kaka komai ba, Kaka tace "Amma wnn ai tafi karfin kowa ynxu, ta xama
abar tsoro, na samu labarin ma ba kullum take kwana gida ba wai koh??" Mikewa Mumy
tayi tace "Toh sai na dawo" daga haka ta nufi kofa ta fita, kaka tace "Toh Allah ma
dai ya sa ba ciki ne da ita ba, tunda cewa kika yi bata da lfya, toh a dawo lfya
Maryam" Mumy dai tayi wucewarta bata tanka ta ba Karfe Goma da rabi suka isa
Zaria, Shuraim na kallon Mumy dake ta danne dannen waya yace "Ina ne gidan?" Tace
"A'a kawai ka samu waje ka ajiyeni xan nemi adaidaita sahu, kilan kana da lectures
kar in shiga hakkin ka" yace "Sai goma lectures din" Mumy tace "Ba dai ni nace ka
ajiyeni ba wai" Bai kuma cewa komai ba yyi parking, Mumy ta sauka motar tace "Toh
Allah ya bada sa'a" yace "Ameen, amma wani anguwar xa ki?" Tace "Saboda ga ka
ubana?" Yace "A'a I was thinking ko anjima xan xo in maida ke kaduna ne" Tace "A'a,
xan samu motar haya" Daga haka ta tsayar da adaidaita ta shige, ya tada motarsa ya
wuce... A cikin adaidaitan Mumy tayi dialing number Sadiya tace "Toh ga fa ni na
shigo Zarian Sadiya" Hajiya Sadiya ta gaya mata sunan wani filling station wai ta
jirata a nan, Suna isa gidan man Mumy ta sauka ta ba Mai adaidaitan kudinsa tana
jiran Hajiya Sadiya, bayan kusan minti ashirin sai ga Hajiya Sadiya, Mumy tace "Kin
fa ce min kin fito gida ashe baki fito ba" Hajiya Sadiya tace "Wllh hatsari me Muni
aka yi kafin Jaji, shine ya haddasa go slow" Mumy tace "Toh Allah ya ji k'an
musulmi, ynxu ina muka nufa?" Hajiya Sadiya tace "Tashan da xa mu je mu hau motar
garin mana" Wani adaidaitan suka samu ya kai su tashan, Mumy sae cewa take ni dai
Allah ya sa kafin karfe hudu xa mu koma Kaduna, gidanmu nayi ma Barrister karya
nace xan je" Hajiya Sadiya tace "Gwara ke an san baki gida, to ni Alhaji bai ma san
na fito ba" Mumy ta biya masu kudin motar suka shiga suna jiran ya cika a
tashi..... Tagumi Mumy tayi tana kallon katon Mutumin dake gabansu, Hajiya Sadiya
na xaune gefenta ita ma tana kallonsa, bayan kusan minti goma Mutumin yyi gyaran
murya yace "Toh ga dai abubuwa da yawa na gani, masu kyau da mara su kyau, da farko
dai da fatan a shirye kike Hajiya Maryam don nan ba da dadewa ba babban d'an ki xai
yi aure...." Mumy ta kalli Hajiya Sadiya da sauri, sannan ta kara kallonsa tace
"Aure kuma Malam?" Yace"Kwarai kuwa gashi na gani" Tace "Toh ni dai bai ta6a ce min
komai ba...." Mutumin yace "Ita kuma wnn yarinya Makauniya naga abubuwa da yawa
tattare da ita da nake kan ganewa har ynxu, sai dai a sarari na ga har Mai gidan ki
na shirin fita da ita kasar waje gyaran ido, haka ne ko ba haka ba?" Mumy ta
marairaice tace "Haka ne wllh" yace "Toh nan da kwanaki kadan xa su fita, kuma
idanuwanta kam xa su bude in dai an fita... Sannan ita wannan kishiyar ta ki, naga
a gaba xata xama ita ce kan komai a gidanki, don ynxu ma maganar da nake maki sonki
ya ragu sosai a xuciyar mijin ki, kawai dai yana xaune ne da ke ko sbda rabon
tsakanin ku, amma ynxu wnn kishiya ta ki ita ce gabansa, ita kadai yake gani,
sannan ita salonta xa a iya kiransa da na makirci don bata wani nuna ta damu da
shi, nan kuwa duk karya ne" Mumy da hankalinta yyi mugun tashi tace "Allah
Malam???" Shiru yyi yana kallonta da tikeken hancinsa, Hajiya Sadiya ta dinga
bugeta alamar me yasa tace haka, da sauri Mumy tace "Tuba nake malam ayi hakuri"
Mutumin yace "Ku fita ku dawo nan da minti ashirin" Hajiya Sadiya ta mike da sauri
tace "Toh Malam, ayi hakuri...." Mumy ma ta mike suka fita waje da sauri, saukowa
suka yi daga kan rock din suka samu karamin rock suka xauna Mumy ta fashe da kuka
sosai tace "Kin ji ko Sadiya, dama ba na gaya maki har yau ni da Barrister ba kamar
da ba, tun da yayi auren nan dama ko nemana baya yi, Kin dai ga abinda wnn
makauniyar tayi ma rayuwata koh? Ta dalilinta ne fa dukka wannan abubuwan ke
faruwa, ita fa ta lalata min gida na, ita ta sa kishiya ta shigo gidana har xa a
kwace gidan a hannuna, ni ynxu me xan ma yarinyar nn in ji dadi???" Hajiya Sadiya
ta sauke ajiyar xuciya tace "Ba tuntuni nake ta bin ki mu xo nan
ba kinki, yo ai Allah ma cewa yyi tashi in taimake ka, ga dai shi kin jiye ma
kunnenki komai, Amma bari mu koma ciki tukun mu ji sauran bayanin, shi kuma Shuraim
duk rashin maganan nan nasa har wani neman aure yake yi dama baki sani ba" Mumy ta
share idonta tace "Toh ae sai yyi auren mu ga, xae ma ajiye xancen auren nan ne, ce
masa nayi ina son yyi aure yanxu" Hajiya Sadiya tace "Toh ai shi na gani, duka duka
nawa yake da xai tsiri son yin aure" Mumy tayi tagumi bata ce komai ba don ba batun
auren Shuraim ya fi damunta ba ita yanxu, suna nan xaune har minti ashirin din yyi
sannan suka mike suka sake gurgurawa can sama, Hajiya Sadiya tayi kasa da murya
tace "Toh ga mu mun dawo Malam, da fatan ka huce" Bai ce komai ba sai bayan kusan
minti biyar yace "Tohh, yanxu me ku ke son ayi a kan lamarin, ita dai wnn makauniya
naga xata warke nan ba da dadewa ba, sannan xata xame maki ciwon ido nan gaba ke
Maryam...." Mumy ta marairaice tace "Toh Malam ya kaga ya kamata ayi, ni so nake
gaba daya ta bace bat na har abada kuwa, in son samu ne ma ni kada idon ya bude
malam ta dauwama a makance, Kai idan ma duniyar xata bari gaba daya ni dai oho in
daina ganinta kawai, sannan shi kuma wnn yaro nawa ayi kokarin ganin an dakatar da
batun auren nasa don ni ban shirya aurar da shi ba yanxu, ita kuma kishiyar ayi duk
abinda xa ayi ta bar min gidana da mijina, in xama ni kadai ce a gidan, Kuma
maigidana na da uwa fitinanniya, duk ta gallabe mu, so nake ita ma a rabata da d'an
nata, ko biyayya ya daina yi mata, snn a rufe bakinta gumm ta xama kamar kurma ko
bebiye, taji kuma bata son xaman gidan namu ta koma can gidan wansa har abada"
Mutumin yace "Toh an gama...." Hajiya Sadiya ta gyara xama tace "Ni kuma Malam a
kara rufe min bakin mijina a kan na da, duk da dai bbu wata matsala ynxu bai jin
batun kowa sai nawa tun aikin da kayi min kwanaki, amma a kara min wani sabo ynxu
dai" Mutumin yace "Toh a bani minti sha biyar a waje" Mikewa duk suka yi suka
gungura kasa. Sai kusan magariba Mumy ta isa gida don ma ba ita bace da girki, a
dar dar ta shiga parlon tana boye jakarta a Hijab, ganin bbu kowa kusan da gudu
tayi bangarenta ta kulle kofar, ganin su Rabi'ah da Khadijah xaune suna kallo
parlonta ta shige bedroom tana amsa sannu da xuwan da suke mata... Karfe goma saura
na dare Mumy ta fito, Mami ce ta fito bangaren Abba, Mumy ta dauke kai kamar bata
ganta ba ta shiga dakinsu Sajida, tana daga tsaye bakin kofa tace "Sajida me ya
hanaki wanke min bandaki yau?" Sajida ta mike da sauri tace "Wllh Hajiya na wanke
tun da safe" Mumy tace "Toh tafi ki ga bandakin da kika wanke ki dawo ki sameni
yanxu" Sajida ta fita dakin xuwa bangaren Mumy, Mumy na kallon Karime tayi kasa da
murya tace "Xuwa sha daya ko sha biyu ki taho bangarena ki sameni" Karime tace "Toh
Hajiya" Daga haka Mumy ta juya ta wuce da sauri. Mumy na parlonta xaune tana ta
jiran Karime sai ga ta kuwa karfe sha daya da rabi, Karime ta kulle kofar ta iso
kusa da ita ta durkusa tace "Ga ni Hajiya" Mumy tace "Yanxu ita makauniyar gun
Rahinar take ko gun Kaka?" Karime ta tabe baki ta gyara xama tace "Ehh toh, yau ta
kwana dakin kaka, gobe ta kwana bangaren Rahinar, amma dai ta fi dai xama wajen
kaka" Mumy tace "Ba naga tana yawan shan shayi da, ko ta daina?" Karime tace "Har
yau tana sha, gwangwanin kayan shayin nata ma na dakin kaka, ta sha da safe wani
lkcn har da rana sannan ta sha da daddare" Mumy tace "toh wani aiki xan baki Allah
ya sa xa ki iya Karime" Karime tace "Haba me xai hana, ai bbu abinda baxan iya maki
ba Hajiya, ke da kika rike ni tamkar 'yar ki, Ina xan samu haka banda wajen ki"
Mumy tace "Toh, ba wani abu bane garin magani ne nake son ki juye a gwangwanin
milon gaba daya sai ki gauraya, don idan an sa a madara xa a gane" Karime tace
"Hajiya amma dakin kaka fa kayan shayin suke ba dakin uwa rikonta ba" Mumy tace
"Toh sai me?? Ba tana sa ki share share ba?" Karime tace "Ta fi sa Sajida, komai
Sajida take kira tayi mata" Mumy tayi shiru sai kuma tace "Wani aikin take sa
Sajida?" Karime tace "Irin su Shara, goge gogen waje sai wankin bandaki" Mumy tace
"Da yaushe take sa ta?" Karime tace "Da safe haka take kiranta ta saka ta" Mumy
tace "Toh gobe kafin ma ta kirata xan aiki Sajidar, tana kiranta sai ki je kice
bata nan, nan kuma xa ki tambayeta me xa ki yi mata" Karime tace "Toh shkkn, xan yi
iya bakin kokari na Hajiya" Mumy ta mike ta tafi cikin dakinta sai ga ta ta fito da
Kullin magani a kyallen atamfa tace "Gaba daya xaki juye kuma kiyi a hankali kar ki
bari ya xuba" Karime ta amshe ta tura cikin rigan mamanta tace "Toh Hajiya in sha
Allahu" daga haka ta fice daga parlon da sauri, Mumy ta sauke ajiyar xuciya ta
kashe wutan parlon ta wuce cikin dakinta. Washegari da safe bayan Abba da Mami sun
fita, kaka ta kwalo ma Sajida kira, Karime ta mike da sauri tana ta6a mamanta don
ta tabbatar kullin na nan don Mumy tun safe ta sa Sajida ta bar gidan, Tana shiga
dakin kaka da sallama tace "Gani kaka, Sajida an aiketa" Kaka ta dinga kallonta
daga sama har kasa sannan tace "Ni dai na ga jaraba, wai ke baki wanka ne, kullum
cikin naso kike kamar d'an wake, mata kazama kawai duk wari, me xa ki min to da
kika taho toh?" Karime tayi kasa da kai tace "Na xata aiki Sajidar xata maki shine
na xo in yi" Kaka tace "Ehh lallai, da kuwa lalacewa ta sameni, a hakan xaki kama
min aiki inje wata cutar ta kama ni a banxa a hofi, wai ma daga wani kauyen kike??"
Karime tayi kasa da kai tace "Doguwa" Kaka tace "Ko da na ji, to yi tafiyar ki, kar
ki sake shigo min daki da sunan xa ki min aiki ni ba gantalalliya bace, bari
Rakiyar ma ta dawo xan ji ko meye sauran amfanin ki a gidan nan tunda dai ga ni nan
ina ma Deedayah komai, ke kuma ba sai a sallame ki ba" Karime ta juya da sauri ta
fita tana waigo kaka a tsorace, Kaka tace "Ni naga jaraba, mata duk naso kullum
fisabilillahi tayi ta shigo min daki" Heedayah dake kwance saman gado tace "Kaka to
aiki fa xata taya ki..." Kaka ta kalli Heedayah da sauri tace "Ta je can ta taya
uwarki Rakiya aiki, ni ba ruwana cewa ma xanyi a sallameta ko xan daina ganin
fuskarta"
Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Mumy ta mike da sauri ganin Karime ta dawo tace "Ya, har kin xuba?" Karime tace
"Korata tayi wllh, har cewa tayi xata sa a sallameni" Mumy ta xaro ido tace "Me
kika mata????" Karime tace "Ban mata komai ba wllh, haka nn kinsan dama bata sona"
Mumy tace "Toh baki bata hkuri ba kika fita ke kuma?" Karime tace "Cewa tayi bata
son ganina" Mumy ta xauna tayi tagumi tana tunanin to ynxu ya xa ayi ta samu ta
juye maganin nan cikin kayan shayin Heedayah, ta kalli Karime tace "Ba ni kayana ki
fita" Karime ta fiddo kullin cikin rigarta, kin amsa Mumy tayi tace "Ajiye min kan
kujera" ta ajiye, Mumy tace "Je ki sae na neme ki" fita tayi parlon Mumy ta bi ta
da wani kallo, leda ta dauko ta rufe maganin da shi tana yatsina fuska sannan ta
dauka ta wuce daki. A ranan Mumy ta shiga dakin kaka yyi sau biyar kafin yamma,
fitarta na karshe kaka tayi mitsi mitsi da ido tace "Da kyar idan matan nan tana da
gaskiya, na lura tun safe take min xarya kmr me nakuda.... Ni dai bari Amadu ya
dawo in ji dalili gaskiya, Allah na tuba duniyar nan yanxu ko wanda ku ka fito ciki
daya kaga yana maka xarya bbu dalili toh kayi ta kanka kawai" Heedayah dai na dakin
tana jin abinda kaka ke cewa, Kaka ta mike ta kwalo ma Sajida kira, Sajida ta taho
da sauri tace "Gani kaka" Kaka tace "Kasko xa ki dauka kije duk inda xaki samo
gawayi ki hura min garwashi ki kawo min yanxun nan" Sajida tace "Toh sai dai inje
kasuwa yanxu a siya gawayin" Kaka tace "Toh ni dai bani da ko sisi, tafi ki kira
min Maryam" Sajida tace "Toh" sannan ta wuce, ba a dau lkci ba sai ga Mumy tana
murmushi tace "Gani kaka, aiki xa a maki" Da sauri kaka tace "A'a, aikin me kuma
kamar kuturwa, dari biyar xa ki ba Sajida xata je min kasuwa ynxu" Mumy ta d'an
juya lkci daya ta daure fuska, sai kuma tace "Anya xa a samu kuwa, da yake jiya da
naje can gida na kai Salima asibiti to bbu kudi wajena ynxu" Kaka tace "Toh kira
min Amadu, shi baxai rasa yanda xai yi da ni ba ai" Mumy dai bata ce komai ba, Kaka
tace "Ki kira min shi da wayarsa" Barin dakin Mumy tayi murya can ciki tace "Toh"
tana tsaye daga bakin kofarta ta kwalo ma Sajida kira, Sajida ta taho da sauri,
Mumy ta jefa mata dari biyar din fuska a murtuke ta shige parlonta ta kulle kofa...
Sajida na dawowa da gawayin ta rura ma kaka a Kasko, sannan ta kai mata dakinta,
kaka na xaune tsakar dakin ta baje kayan wani tsohon jakarta, kullin magunguna ne
iri iri kai kace boka ce, Sajida ta ajiye kaskon saman tiles tace "Gashi kaka" Kaka
tace "Allah maki albarka...." Tace "Ameen" sannan ta fita, kaka ta xuba uban
turaren icce a wutan, Tuni Heedayah ta mike ta fara tari tace "Kaka meye shi?" Kaka
tace "Toh haka kawai aka ce maki xan xauna a kashe ni, jiya fa wani mummunan
mafarki nayi..." Heedayah xata fita dakin kaka ta rufe kofar tace "Toh ko dai ke
mayya ce ba mu da labari..." Heedayah ta fashe da kuka tace "Kaka yana shiga
hancina" kaka tace "Ai dama ta nan din xai shiga, Ina xa mu tsaya a cuce mu, kowa
fa ya lalace da mugun abu a xuciyarsa, tun ina gidan mijina nake tsare kai na,
Rakiya ma idan ta dawo daga gantalin aikinta sai ta xo in debar mata, kaikayi koma
kan mashekiya ne fa..." Heedayah ta toshe hancinta, Kaka na ta surutunta tana kara
cika iccen cikin wutan kaskon, sai da ta tabbatar ya ratsa ko ina na dakinta sannan
ta fitar da shi parlor ta ajiye tace "Toh dama kada wanda ya dauke min kayana a
nan" Mami ce ta bude kofar da sallama, tana shigowa ta fara yatsine fuska don
hayaki ya cika ko ina, Ta karaso gun kaka tace "Meye wnn din kaka" Kaka tace "Ke ma
idan xa ki samo leda in debar maki ki samo, duniyar ynxu ba gaskiya, Maryam ma idan
ta ga tana so ta samo leda in debar mata, kaikayi koma kan mashekiya ne" Mami ta
gaida kaka xata wuce kaka tace "Yauwa Rakiya dama Ina jiran ki dawo ki gaya min me
wnn me aikin taki take tsinana maki a gidan nan" Mami ta juyo tace "Aa ba komai
kawai dai suna aikin gidan ne tare da dayar mai aikin" Kaka tace "Toh a gaskiya ki
sallameta Sajida kawai ta ishe mu a gidan nan, baki ga ba kullum fa naso take,
kazama ce fa da kyar idan ruwa na ta6a jikinta haka kawai wata cuta taje ta kama mu
ta dalilinta bayan mu duk muna wanka muna tsafta" Mami tayi murmushi tace "Naga
kamar aikin ya ma Sajidar yawa ne" Kaka tace "Sai a samo wata me tsaftar amma a
gaskiya a sallami wnn, idan ko ba haka ni a sallameni" Mami na kallonta tace "Ta
maki wani laifin ne kaka?" Kaka tace "Aa ko daya kawai na gaji da kazantar ta ne"
Mami bata kuma cewa komai ba ta juya ta nufi bangarenta... Da daddare Abba na
parlonsa sai ga kaka ta shigo da sallama, Mumy da ke yanka masa watermelon tace
"Sannu kaka" Kaka ta xauna tace "Yauwa, Amadu ashe ka dawo" Yace "Ehh na dawo, Ina
yini" tace "Dama xuwa nayi naji wa ke biyan kudin aikin matar da Rakiya ta dauka"
Yace "Aa ita ke biya" Kaka tace "Au haba, to bari in bar mata mai aikinta kar ta
kullaceni, wai da cewa xan yi a sallameta" Abba yace "Tayi wani abu ne?" Kaka tace
"Oh oh kawai dai ni bata kwanta min bane ga kazanta malam, amma tunda ba kai ke
biya ba ai shikenan, ae Rakiyar ma me kudin kanta ce, ba xaman banxa take ba kamar
wasu, baka ga gidan wan tsohon mijinta ba da Junaidu ya kai ni shekaranjiya, Kai
kace wani shugaban kasa ne" Mumy dai ko kallon kaka bata yi ba sai sauri take ta
bar parlon, ko yankan kirki bata ma kankanan ba ta mike tace "Xan je in duba ruwan
shayin da na sa a kitchen" daga haka ta fita, kaka ta kalli kankanan tace "Dubi
wani yanka da tayi ma kankanan kamar bakatafiya..." Shi dai Abba bai ce komai ba,
kaka tace "Toh ni dai na hada kayana tun ranan da ka min xancen tafiya gyaran idon
Deedayah a india" Abba yace "Mutane biyu kacal xa su je tare da ita fa Baaba" Kaka
tana kallonsa da kyau ta gyara xama tace "Ban gane mutane biyu ba, su wa da su wa
kenan mutane biyun?" Yace "Aa ba ni nace ba, ka'idar wajen ne haka, Doctor ne ma ke
gaya min" Kaka tace "Toh ba sai ni da kai mu kai ta din ba, ko akwai wani wanda ta
hada wani abu da shi banda ni da kai din" Abba yyi shiru yana kallonta, kaka tace
"Toh dama ai ni da kai ne dolenta, ita Rakiya yaushe ta xo gidan ko yaushe ta san
Deedayar da xa ayi marmarin tafiya da ita?" Shi dai Abba bai ce komai ba.... Mumy
na fita sai da ta fara wucewa bangarenta snn ta fito da sauri, ta dinga bin main
parlon da kallo kamar munafuka sannan ta shige dakin kaka ta kulle, hannunta na
rawa ta isa gun kayan shayin ta sauke gwangwanin madaran amma ta rasa da me xata
bude na milon, kan Fridge ta hango cokali cikin cup, ta tashi da sauri ta dauko ta
bude gwangwanin ta ciro ledan dake rigarta, hannunta na rawa ta bude kyallen ta
juye bakin content din cikin gwangwanin ta gauraya da cokalin snn ta rufe
gwangwanin ta mayar Inda yake ta tashi, ta goge cokalin da xaninta shi ma ta mayar
cikin cup din, gaba daya a rikice take, ta fice daga dakin kamar xata tashi sama,
sai da ta shiga parlonta ta sauke wani ajiyar xuciya ta juyo tana kallon yaranta
tace "Uban me ku ke jira ba ku tafi kun kwanta ba? Maxa a kashe min tv tunda bance
ku lalata na dakinku ba" Sai da suka fita parlon snn ta wuce cikin dakinta tana
wani murmushi.... Washegari da sassafe kaka na share sharen lungu da sako na
dakinta ta dauke gwangwanin madara da Milo ta tabe baki tace "Mayyar ma bata sha
shayin jiya da daddare ba, dama fa gulma ce, a gidan uwarta da ubanta ina xata samu
haka, ita dai kawai ta samu d'ana sai kashe mata kudi yake a banxa a hofi, sbda ita
abubuwa da yawa an daina min, tasa sai maneji muke yi, ga uban kudi xa aje a gyara
kaddararrun idonta nan da kwanaki kadan, mu dai kawai Allah ya bamu lada, bafa
dangin iya balle na baba" Tana ajiye gwangwanin milon taga murfin ya fadi, ta dau
murfin tana kallo da mamaki, can ta ajiye tace "Ikon Allah, ni fa na hada mata
shayin jiya da yamma, to wani barawo ne ya xo ya bude ya sata ya manta bai rufe ba,
gashi har Milon yyi kasa, ni dai ba haka na bar sa ba wllh, sata aka fara yi gidan
amadun bani da labari??" Ajiye tsintsiyar tayi ta fice daga dakin, direct parlon
Abba ta nufa ta kwankwasa kofa, Mumy ce ta fito, kaka tace "Amadun fa?" Mumy tace
"Yana ciki" Kaka tace "Ce masa gani a tsaye" Abba na fitowa kaka tace "Amadu wllh
shigar min daki aka yi aka yashe milon Deedayah tass, ynxu ba sai ace ni ke
shanyewa ba ko da ba a fito fili an gaya min ba ayi ta xagina a xuciya, toh gaskiya
ni dai a san matakin da xa a dauka ynxun nan" Mumy da hankalinta yyi mugun tashi
tace "Ikon Allah, toh bari in debo na wajena sai a kara mata a kai tunda yyi kasa,
ba abun tada hankali bane kaka" Kaka tace "Oh oh ba wani debo naki da xa kiyi, ko
ma waye ya diba sai ya maido wllh, xan fara ta kan masu aikin nan tass sai na
bincike kayansu don nasan ba shan lkci daya xa ayi ma milon ba deba xa ayi a leda a
boye, Kai har kayan Deedayar ma sai an bincika da nasu Rabi'ah" tana fadin haka ta
nufi dakin masu aiki tana kwala ma Mami kira ita ma ta fito, kayan Sajida ta fara
dubawa ta xaxxage gaba daya Ghana must go din bata ga komai ba, Kaka ta kalli
Karime dake ta xufa tace "Ke ina jakarki" Karime ta nuna mata ghana must go din, ba
komai ya sa hankalinta ya tashi ba sai kullin Madara da millo na Mumy da take diba
a leda idan Mumy tace taje ta hada shayi, har na Mami ma tana diba, snn ga kullin
soyayyen nama na jiya da ta boye a kayan, ga kuma Cornflakes a leda shima duk ta
boye, kaka ta yatsina fuska tana xaro kayan kamar Kashi tana ajiyewa kasa, da ledan
naman ta fara cin karo, ta kunce ledan ta saki salati ta yar a kasa tana kallon
naman, Mumy ma xaro ido tayi tana kallon naman, Kaka ta ci gaba da xaro kayan sai
ga ledan cornflakes, Kaka ta kara gwalo ido ta ajiye Cornflakes din, ta ci gaba da
xaro kayan sai ga ledan milo sannan Madara, kaka tayi wani dariya irin na boss,
Mami ma na tsaye bakin kofa ta kasa cewa komai, Kaka tace "In ji dai kun tabbatar
cewar ba banxa nake ba ynxu, duk wanda Allah ya daukaka ya riga da ya daukaka sa,
to a kira Amadu shi ma ya gane ma idonsa, nasan da naje na samesa nace gashi gashi
a ransa cewa xai yi ohh Allah ya hadani
da fitinanniyar uwa, to yau ga ranan fitinata, ni dai nasan shigar min aka yi aka
debi milon nan dama" Karime ta durkusa tana matsar kwalla tace "Wllh wllh wllh kaka
ba milon ki bane wnn, ki duba ki ga wnn har fa ya daskare...." Kaka ta kwala mata
ledan milon da ya daskare a fuska tace "Ke dai bakya tsoron Allah, to kin saka sa
cikin jaka duk wari ya baxai daskare ba?? Ai da kyau tunda ba tsutsa ya fitar ba,
ni dai a kira min Amadu ya xabi ko ni ko kazamar nan, don in har xa a yafe mata ta
ci gaba da xama a gidan nan gwara in tafi duk inda Allah yyi" Mami ta sauke ajiyar
xuciya tace "Yau kwana nawa da biyanki kudin watan aikin ki?" Karime ta fashe da
kuka tace "Sati daya" Mami tace "Toh ki hada kayanki, ki taho ki sameni in baki
kudin aikinki na sati daya da kudin mota kiyi tafiyar ki, Allah ya bamu alkhairi"
daga haka Mami ta fita dakin, Karime ta kara rushewa da wani matsanancin kuka ta
daura hannu a ka tana kallon Mumy tace "Don girman Allah Hajiya ki taimakeni wllh
aiki wahalan samu yake yi ynxu, ki saka baki a maganan nan don Allah a barni in ci
gaba da aikina" Mumy ta ki kallon ko da Inda take, can ta juya kamar munafuka ta
fita, kaka tayi wani shewa tace "Aje can wani gidan kuma ayi tayi masu naso ana
wari amma ba gidan d'a na ba" daga haka ita ma ta fice daga dakin, Dubu goma Mami
ta ba Karime kudin mota dubu biyar, dubu biyar kuma na aikin sati daya da tayi, sai
kuka Karime take tana cewa "Don Allah Hajiya kiyi hakuri kar a koreni, wllh sharrin
shaidan ne" Mami tace "Da ni ce kika debar ma abu na kamaki, sai dai in maki nasiha
kuma in gargadeki da cewar kar ki kuma, amma kinga ya fi karfina ynxu, kinsan yanda
tsofaffi suke lamarinsu, don haka kiyi hakuri ki tafi, Allah xai kawo maki wani
hanyar" tana kuka sosai ta fita, Tsaye ta ga kaka da gwangwanin madara da milon a
hannunta, tana ganin ta fito ta nufeta ta ajiye mata su tace "Ga nawa gudunmawar, a
gaida mutan Doguwa" Mumy dake tsaye bakin kofarta ta shigo parlon da sauri kuma a
rude tace "A'a kaka ya xa ayi haka? Ki bata tayi me dasu kuma???" Kaka ta katseta
tace "Toh Ina ruwanki, so kike in ba Jikata gaibu ta sha, nasan barbadin da ya
shiga ciki a yayin satar? Kazama ce fa bata wanka, to Deedayar xan ba ma sauran
milon da ta jagwalgwala ta sha kamar uwata tace min je ki kya gani, kawai wani
cutar ya kamata Amadu da Rakiya su kullaceni?? Aa wllh ta tafi da su tayi ta shan
shayi a kauyen nasu" Karime sai kallon Mumy take tana hawaye, Mumy na rawar baki
tace "Aa kaka idan ba xa a bata ba ni a bar min xan yi amfani da su wllh" kaka tace
"Toh banyi niyya ba, ita dai barauniyar xan ba ta tafi da su, kinga dai ai baxata
kullaceni sosai ba tunda na sallama mata sauran kayan shayin" kaka na fadin haka ta
jawo katon Ghana must go din Karime ta xuge ta xuba gwangwanin biyu a ciki sannan
ta rufe tana kakkabe hannu tace "Gudunmawata kenan, anjima kuma sai a kira min
Junaidu in sa ya siyo mata wani bbu ruwana da wahala" Karime ta dau Ghana must go
din ta nufi kofa tana matsar kwalla, Kai kana ganin Mumy kasan duk a rude take don
hakan ya fito kiri kiri a fuskarta, Mami kuwa sai kallonta take, Mumy ta koma part
dinta da sauri ta dauko Hijab sai ga ta ta fito ta bi bayan Karime tana cewa "Mu je
in raka ki ai baxa ayi rabuwar tsiya ba...." Hada idon da suka yi da Mami yasa tace
"Au to ai ba sai na raka ki ba ma...." Sai kuma ta koma bangarenta da sauri, Mami
ta bi bayan Karime da har ta fita, Karime ta juyo ganin Mami ta tsaya tace "Hajiya
kiyi hankali da kishiyar nan taki, bata sonki bata son yar da kike riko, wnn milon
da kaka ke batu a kai ita ce ta xuba abu a ciki don da farko ni ta ba in xuwa ban
samu nayi hakan ba shine taje tayi da kanta amma ta mance bata rufe murfin ba...."
Tana fadin haka ta ciro milon ta mika ma Mami tace "Gashi don tana iya biyoni tace
xata amsa idan na bar gidan nan" amsa Mami tayi tana kallon milon, Karime ta nufi
gate da sauri tana goge idonta, sai ga Mumy ta fito, Mami ta mayar da gwangwanin
bayanta, Mumy tace "Lahh har ta wuce? Canji na fa na jiya da yamma na wajenta bata
bani ba, har dubu uku fa...." tana fadin haka ta nufi gate kusan da gudu, Mami
tayi wani murmushi ta juya ta koma ciki, parlonta ta shiga ta bude milon tana
kallon content din, ta girgixa kai ta wuce bandaki nan ta xubar da gaba daya a
Bathtub ta bude ruwa ta juya ta fita rike da gwangwanin. Mumy ce xaune dakin Sadiya
sai rusa kuka take, Sadiya tayi tagumi ta kasa cewa komai, Can tace "Kai kema dai
wllh sai kace dakikiya, toh garin yaya ma xaki bar murfin gwangwanin a bude, ke
meyasa baki yin abu da hankali, ynxu da ace abun nan na backfiring fa? Sannan uwa
uba ga kudin da aka kashe, Kai ni dai wllh idan abun nan bai bata min rai ba
shegiya nake" Mumy na Shessheka tace "Wllh kakan nan mayya ce kawai ki yarda"
Sadiya ta ta6e baki tace "Toh ita na Rakiyan fa?" Mumy na goge idonta tace "Aa dama
cewa nayi bari in fara gamawa da na yarinyar tukun, gashi kuma komai ya tashi a
aikin banxa" Sadiya tace "Toh Karimen ke kina tunanin a layin ta jefar da
gwangwanin milon?" Mumy tace "Wllh kaf bbu flawan da ban duba ba a layin amma banga
komai ba, rashin kunya fa sosai yarinyar ta min har tana neman dambe da ni a titi
xata tara min jama'ah, har da kirana shaidaniya, toh ni kuwa ai bana biyeta ba sum
sum sum na juyo, amma sai da na bincika jakar banga komai ba wllh sai gwangwanin
madaran" Sadiya ta sauke ajiyar xuciya tace "Ikon Allah... Yanxu dai sai ki saka
rana mu koma Zarian tunda haka Allah yyi da mu" Mumy ta marairaice tace "Toh amma
ynxu ya xanyi da na wannan Rahinar, ni kinsan ba shiga bangarenta nake ba haka
yarana, dama da kariman na nan ne nasan idan na bata xata yi ynda nace to gashi bbu
ita ynxu" Sadiya tace "Toh aikuwa dole a san yanda xa ayi a shiga bangarenta
kawai..." A hankali Mumy tace "Toh shkkn, Yau laraba ranan juma'ah sai mu koma
Zarian" Sadiya tace "Toh Allah ya kai mu" Kaka na yanke ma Heedayah farce a dakinta
sai mita take ita an maida ta boyi boyin yarinya duk wa enda suka tsintota darewa
suke su barta da ita tayi ta wahala har dare, Heedayah dai sai turo baki take tana
sauraronta, kaka tace "Toh bakya turo baki ba dama tunda gani naynny ki, ni kenan
kullum a wahale inyi ta fama da maki bauta bakya gani balle ki gode min, bari
Rakiyar ta dawo ayi ta takare yau, xanji amfanin aurota da Amadu yyi" Bude kofar
parlon aka yi Salima ta shigo da sallama tana kas kas da cingam, kaka ta kalleta ta
ci gaba da abinda take, Salima ta xauna tace "Ina yini kaka?" Kaka tace "Lafiya
lau, ke dai har yau bbu matayi ko Salima? Toh Allah ya fiddo maki da na gari"
Salima ta d'an harareta bata ce komai ba, kaka tace "Toh ai Ina jin Maryam din ma
bata nan ta fice" Salima tace "Ehh na sani" Kaka tace "Ayyo, to tafiya xakiyi sai
ta dawo ki dawo kenan?" Salima tace "Aa xan d'an kwana biyu a nan" kaka ta kalleta
da sauri tace "Kwana biyu kuma? Toh... Allah dai ya ba Amadu ladan ciyarwa, amma
ynxu ai abinci ya xama abinda ya xama a kasuwa, ynxu fa mun kusa mu ashirin a gidan
nan" Mikewa Salima tayi tana taunar cingam dinta ta fita, kaka tace "Karuwanci dai
a sarari ni 'ya su" A hankali Heedayah tace "Kaka wacece?" Kaka tace "Kanwar Maryam
uwa daya uba daya, ai bin otal take tana kwana, kinsan uwarta ta rasu haka ma
ubanta to bata da wani mafadi ynxu sai makwabta, Maryam ita ma da ba don auren dake
kanta ba xata yi fiye da haka ina tsammani, kinsan kafin Amadu ya aureta har xuwa
Abuja take wai yawon bude ido a can ma suka hadu da Amadun...." Heedayah tace "Meye
yawon bude ido" Kaka tace "Toh ke ina ruwanki da xancen manya kina 'yar yarinya da
ke" Heedayah ta turo baki Kaka ta ci gaba da yi mata yankar farcen tana cewa "Banda
lalacewa ma ina ni ina hiran nan da ke" Bayan La'asar Salima na kwance parlor tana
kallo aka bude kofa, Junaid ne ya shigo parlon da sallama, ta mike xaune a hankali
tana kallonsa, Tunda suka hada ido ya dauke kai, ta bi sa da kallo tace "Ina yini?"
Yace "Lafiya lau, ya gida?" Tace "Alhmdllh, nima yau na xo" yace "Ohk" parlon kaka
ya shiga, ko gama gaisawa basu yi da kaka ba sai ga Saliman ta shigo, ta d'an xauna
gefen kujera tace "Kaka bbu abinda xa ayi maki?" Kaka tace "Ehh to wankin bayi ne,
daxu ban yrda da wanki Sajida ba, kinsan na sa an Kori dayar me aikin, ta saci
milon Deedayah ni ko na sa aka sallameta, shine aka kira min Junaidu yanxu ince
masa ya tafi ya siyo mata wasu...." Salima tace "Toh bari a wanke" cire karamin
mayafinta tayi ta ajiye nan kan kujera ta nannade skirt dinta har saman Gwiwa, duk
fararen kafafuwanta a waje, shi dai Junaid tunda ya kalleta sau daya ya dauke kai,
ta nufi cikin bathroom din, kaka tace "Ae Salima yar albarka ce, ga haxaka wajen
aiki, da fa idan ta xo gidan nan har kwaleman dakina tana min, kwana biyu ne kawai
ta guji gidan nan, kasan yayartata bata da hali tsangwamarta kawai take shi yasa
bata son xuwa ma" Junaid ya kalli kaka yace "Wacece yayarta?" Kaka tace "Kishiyar
uwarka mana Maryam" Junaid bai ce komai ba, Heedayah tace "Kaka ko xaki basa ya
yanke min kina min da xafi" Kaka ta jefar da nail cutter din a jikinta tace
"Algunguma sai kije yyi maki da sanyi, yarinya sai sharrin jaraba kawai" murmushi
Junaid yyi ya dau nail cutter din yana kallon Heedayah da ta 6ata fuska xata yi
kuka, ya ja hancinta a hankali yace "Don't Lolly...." kaka ta mike tana kakkabe
jikinta tace "Ni idan ta bata min rai ma sai ince ma Amadu na fasa xuwa gyaran idon
da ita sai in ga ta tsiya"

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Murmushi Shuraim yyi ya gyada kai yace "Toh Allah ya tsare" Kaka tace "Atoh yanxu
kayi magana, Ameen dai..... Allah ya kai mu lafiya ya dawo da mu lfya kawai" Juyawa
yyi ya fita dakin still smiling ya kulle kofar, Baffa dai na ta xaune bai iya yace
komai ba, lkci lkci yake kallon wayarsa waiting for his son Sudais don kafin ya iso
gidan sai da ya kirasa yace ya samesa gidan Abba, Kaka na kakkabe jakarta ta tabe
tace "To su matan naka basu da niyyar xuwa yi min sallama ne Umaru?" Baffa yace
"Dama ba wanda xai yi tafiya ake xuwa yi ma sallama ba Baaba, amma ai xa su xo
sallaman" kaka da bata tsaya ta fahimci farkon maganansa ba tace "Toh kar ma su xo
mana, xuwansu da rashin sa duk daya ai a wajena, meye hadina da su banda kai da ka
auro su, matan da suka kusa kashe ni da kwai duk karni Allah yyi da sauran kwanana
a gaba" Baffa na kallon Heedayah yace "Baaba meyasa ake bari tana baccin yamma
haka?" Kaka ta daga hannu sama tace "Haka aka saban mata tun daga gun iyayenta
wllh, sakakku ne iyayen nata duk sun sangartata sun lalatata, Banda haka katuwa
kamar yarinyar nan ace tana tashi shan shayin dare, baka ga gwangwanayen kayan
shayin da na tara ba xan ba 'yan gwan gwan, wllh xa su siya dubu biyu ko uku kila,
kana maganan baccin yamma ai ko xaka shekara kana tashinta magagi kawai xata yi ta
maka, to ni baxan iya wahala ba shi yasa nake barin ta, kuma bana rabo da tofa mata
addu'a ba don halinta ba" Baffa ya gyada kai yace "Hakan na da kyau ai" Bude kofar
dakin aka yi Sudais ya shigo da sallama, Kaka tayi tagumi tana kallonsa tace "Ta
janye tsinannen bakin da tayi maka na xuwa gidan nan kenan, Kai dai kam baka yi
sa'ar uwa ba Sudess, yau kusan wata daya kenan rabona da kai fa" Sudais da idonsa
ke kan Heedayah ya xauna ya cire face cap din kansa, Baffa ya fara gaidawa sannan
ya kalli kaka yace "Ina yini kaka" tace "Lafiya lau Sudess muna ta shirye shirye
ashe da rabon xa mu hadu, kai ma ka xo sallaman kenan?" Yace "Sallama da wa?" kaka
tace "Ni mana, gashi har na gama hada kayana" Yace "Hada kaya xuwa Ina?" Ta ja
tsaki tace "India mana, ko baka da labari ne? Au da yake uwarka ta hanaka xuwa
gidan kilan shi yasa baka da labari, ae ni da Rakiya xa mu kai ta indiyan" Ya wara
ido yace "Toh ai naga ba da ke xa aje bane Hajiya Kaka? ko wani ya bude baki yace
maki har da ke ne a tafiyar kika hada uban kaya haka?" Kaka tayi shiru tana
kallonsa bayan ta hadiye wani yawu da kyar, ya danne dariyar sa yana xare mata
idanuwansa yace "Mami da Shuraim ko Junaid ne ai xa su yi tafiyan ai, ko mafarki
kika yi xa a je da ke ne baki ba mu labari ba kika tsiri hada kaya" Kaka ta juya a
hankali tana kallon Baffa dake danna waya, Sudais yace "To ba a ma barin tsofaffi
su shiga asibitin, don su ma tsoffin kansu ai cutane...." Baffa ya jefa masa wani
kallo, ba shiri yyi shiru trying hard not to laugh, kaka dai magana ya makale mata
sai 'yan idanuwa, Baffa yyi gyaran murya yace "Kina ji kaka, kece baki fahimci abun
nan ba tun farko, kinga dole ana son a samu masu ilimi sosai su je tare da ita,
sannan kin san ynda xaman asibiti yake kuma a gaskiya baxa ma su barki ki xauna
ciki ba tunda kin manyanta, shine muka yanke shawara da Amadu cewar Hajiya Rahinah
da Shuraim ko kuma Junaid su tafi can din tare da ita don shi Sudais baxai je ba
yace, Kinga ai duk masu ilimi ne, komai xuwa xai yi da sauki tare da su, ke kuma
daga baya ko kafin a sallame su ne sai a kai ki ki sauka hotel a dinga kai ki
asibitin kullum kina dubata...." Kaka ta sauke ajiyar xuciya a hankali tace "Toh
daga kai har Amadun da duk wanda ya kawo wannan shawaran ku je na bar ku da
Allah...." Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka ta kwantar da kanta saman katon
akwatinta, Baffa ya bude baki yana kallonta ya kasa cewa komai, Sudais duk irin
yanda yake dakewa bai san lkcn da ya fashe da dariya ba har da kyakyatawa, Baffa ya
juya fuska daure yana kallonsa, Mikewa yyi da sauri yana kokarin hadiye dariyar sa
yace "Meye kuma abun barin jama'ah da Allah kaka?? Daga fadin gaskiya?" Cikin rawar
murya ta dafe kirjinta tace "Ae sun cuce ni ne sun toxarta ni sun kunyata ni
Sudess, yanxu da wani idon xan kalli duniya ince masu ba da ni xa aje ba? Dama ashe
Deedayah na da wani me muhimmanci bayan ni a rayuwar nan bani da labari? Ashe dama
Rakiya munafuka algunguma ce ita ma bani da labari?" Wani kukan ta kuma rushewa da
kai kace yarinya ce, Sudais yace "Toh ai ba ace baxa ki je ba fa kaka, cewa aka yi
su fara yin gaba daga baya sai ke da Abba ku bi su" Kaka ta dakatar da kukan da
take yi ta daga hannu sama da sauri tace "Aa wllh na yafe suyi ta tafiya har bangon
duniya idan da matsallaki su tsallake bangon duniyar ma bbu abinda ya sha ma Patuu
kai, dama ai ban hada uban komai da shegiyar makauniyar ba karambani na ne" Mikewa
Baffa yyi ya fita dakin gaba daya ransa a bace, Sudais na nunata yace "Ke dai kin
fiye wahala da neman fitina, tsofe tsofe da ke ina kike son a kai ki? Jinyarki xa
aje india ayi ko na Heedayah?" Kaka na nunasa ita ma tayi fici fici da ido tace
"Wllh tllh idan ka bari na maka baki sai ya bi ka, uwarka ce tsohuwa ba ni ba, to
sae me don su Umaru da Amadu sun munafurce ni? Ae dama munafukan ne tun suna yara,
Ga dai gari da yawa maye ae baya ci kansa ba, dama yanxun nan xan bar gidan nan
inga shegen da xai hanani in tsine masa bbu ruwana" Tana fadin haka ta mike ta fara
neman gyalenta tana matsar kwalla, Sudais sai kyalkyala dariya yake yace "Sai ki fi
ruwa gudu ai, mu ba mun huta da wahalar ki ba ma, dama duk kin addabemu kin dame
mu" Kaka ta juya tana kallonsa ta nufesa ta cakumosa tana huci tace "Don kaza kazan
ka nice wahalalliya??" Gwalo yyi mata ta kara rushewa da kuka ta sakesa ta xauna
nan kasa tana rera kuka, suka yi ido hudu da Heedayah da hayaniyar kaka ya tasheta
ta mike xaune tana bin ko ina da kallo, a mugun fusace kaka tace "Munafuka maxa
sauko min saman gadon kar in jefar da ke" Turo baki Heedayah tayi xata sauka,
Sudais ya karasa yana dariya ya kama hannunta ta sauka, kaka tace "Dama duk a xo a
fitar min da kayanta daki na kada in konasu wllh wllh" Sudais ya nufi kofar fita da
Heedayah yace "Baxa dai kije India ba idan xa ki sa ma ranki salama ki saka, ance
maki tsofaffi na fita India ne, ke a dole xa a hau jirgi, to sai a dau na annabawa
dai" Daga haka ya fice da sauri kafin ta ce komai, ya nufi part din Mami. Baffa na
tsaye compound tare da Shuraim da ya ki shiga dakin kaka shi dai, Baffa ya kalli
Shuraim yace "Me yasa baxa ka bi su Shuraim? Barrister ya ce min da junaid xa su
tafi" Shuraim ya shafa kansa yace "Haka nan kawai Baffa" Baffa yace "But you need
to go as your father's representative tunda shi baxai samu xuwa ba, shi Junaid can
go anytime" Shuraim yayi murmushi kawai bai ce komai ba, Muryar Mumy suka ji ta
leko tace "Ni na hanasa tafiya Doctor, tunda ba a maida uwarsa bakin komai ba a
gidan uban me xai je yi masu India?" Baffa ya juya yana kallonta, can yace "Wnn ba
girman ki bane Maryam" bata tanka sa ba ta juya ta koma, Baffa ya girgixa kai bai
ce komai ba, Suna tsaye har Abba ya dawo ya samesu wajen, Abba na ganin yanayin
yayan nasa dama bai ce komai ba duk suka shiga cikin gidan, parlor suka tadda kaka
tana jan akwatin ta fuska a tsuke, Mumy na daga dining tana dariya kasa kasa dadi
kamar ya kasheta, Abba yace "Ina kuma xa ki Baaba?" A mugun fusace tace "Rufe min
baki algungumi, Ina ruwan ka da inda xa ni??" Ya kwantar da murya yace "Kinga
Baaba, tafiyar ma an fasa har sai an maki visa sai duk ku tafi tare" Tace "Oh oh ba
ruwana su yi tafiyarsu, kada wanda yace min komai, ni dai an walakanta ni an cuce
ni, Allah ya hada mu a kiyama gaba daya kawai...." Xaunawa Baffa yyi saman kujera
ya jinginar da kansa yana kallonta, Abba dai bai ce komai ba, Junaid ne ya shigo
parlon da sallama, Kaka ta saki jakarta tayi mitsi mitsi da ido tace "Junaidu ashe
dama uwarka bata da kirki ban sani ba, Ashe sai a hada baki da ita a cuceni ban
sani ba, ni tunda nake Maryam bata ta6a min abinda Rakiya tayi min ba wllh" Da
farko tsaye yyi bakin kofar, sai kuma ya karaso yace "Me ya faru kaka?" Kaka ta
sakar masa kuka tace "Da hadin bakinta aka yanke shawarar baxa a je India da ni ba
wajen gyaran idon Deedayah" Junaid ya d'an bude ido yace "Aa kaka ai dole ma xa ki
je, ga visa nan ana maki, idan ya so bayan an gama ni da ke sai mu bi su daga baya,
nima ai ba binsu xanyi ba ynxu..." Ta marairaice tace "Toh ai su basu ce min haka
ba cewa suka yi ban da ni kawai, wani har ce min yyi nima kai na cutar ce me xai
kai ni India, wato wai nice cuta, har da ce min wahalalliya, abinda ni dai nasan
ubansa ya xaga ba ni ba" Junaid yace "Aa kiyi hakuri don Allah, tafiya kam xa ayi
da ke in sha Allah, kawai dai daga baya ne xamu bi su" Kaka tace "To da wa da wa xa
a tafi din yanxu?" Yace "Mami da Shuraim" Mumy dake dinning har sannan ta sakko
xuwa cikin parlon cike da gadara tace "Nace Babu inda Shuraim xai je, a nemi wani
amma ba shi ba, indai har ni da na haifesa ban cancanci xuwa ba to shima bai
cancanta ba, kada a sake ambaton sunansa a masu tafiyan" Kaka ta bude baki tana
kallonta tace "Waye wannan kuma? Daga gidanku kika xo da Shuraim din da xaki nuna
mana iko a kansa ko kuwa shakiyanci ke damun ki? Kaji min jarabbiyar mata dai, to
wllh sai an je da Shuraim, Kai idan xuciya ta debeni ma sai ince shi kadai xai kai
ta gyaran idon kada wanda ya bi su, ke a wa xaki ce baxai je ba wahalalliyar mata
kawai, nan nan kanwarki ta xo nan gidan ranan kamar abun arxiki amma sbda tambadewa
na samu labarin ba a gidan take kwana ba sai ta fita da daddare ta dawo mana da
safe, to gidan ubanwa take kwana, baki dau mataki kan wnn lamarin ba sai don ance
Shureen xai je indiya da Deedayah? " kaka ta kalli Abba a fusace tace "Kai Amadu
da wa da wa xa a tafi goben?" Yace "Rahinah da shi Shuraim, daga baya sae ke da
junaid ku bi su" kaka tace "Toh dole da Shuraim xa a tafi, idan ma kowa bai je ba
sae Shuraim yaje wllh" Mumy tace "Ohk, ya tafi bakina ma ya ishesa ai" Kaka ta
nufeta tana tafe hannu tace "Bakin
ki na banxa na hofi, bbu abinda bakinki xae mashi, ae ubansa xai yi ma biyayya don
hka a gantale bakin ki xae xaga duniya ya dawo ya fada kanki ba dai kan jikana ba,
gantalalliya kawai" a nutse Mumy tace "In har Shuraim ya taka ya fita gidan nan
xuwa wani kasa wllh sae na tsine masa" tana fadin haka ta bar parlon kamar xata
tashi sama, Shuraim dai na tsaye gefen Abbansa, kaka tace "ke kuma tsinuwar Allah
ya tabbata a kan ki ba na mutum ba, xan ga uban da ya isa ya hana Shuraim xuwa
India" Abba da gaba daya ransa ya gama baci ya bi bayan Mumy, Baffa dai ya ta6e
baki bai ce komai ba, kaka na kallon Junaid tace "Ni dai ko xaka kai ni gidan kawun
ka ynxu, wllh raina baci yake idan Ina ganin mutan gidan nan, Ka kai ni can ko xa a
kwantar min da hankali" yyi murmushi yace "Toh mu je kaka" tace "Amma ae abun ba
hauka bane bana kai masu katon akwati ba bari in bude in dau kayana kala ko goma
ne" Shi ya ja mata akwatin har dakinta tana biye da shi tana goge guntun
hawayenta... Washegari da asuba Mami ta gama duk shirinta, ta shirya Heedayah, suka
fita xuwa parlon Abba, Abba da ya gama hada duk medical report din Heedayah a
envelope ya mika ma Mami yace "Amma xa mu tafi ku yi ma Kaka sallama tukun koh"
Mami ta amsa tace "In sha Allah" Abba ya kalli agogo yace "We need to hurry up, sbd
kar ku yi missing train din" Mami tace "Haka ne" Abba ya dau wayarsa yana mamakin
rashin ganin Shuraim a masallaci don bai dde da shigowa daga masallacin ba shi ma,
Dialing number sa yyi ya ji switched off, ya kuma kira a kashe, Mami dai kallonsa
kawai take bata ce komai ba, Abba ya dinga kallon wayar tasa, can ya mike yace "Mu
tafi kawai in kai ku gidan Honorable din daga can Junaid ya kai ku Train station"
Tace "Shuraim din fa?" Yace "Don't worry about that" Mai gadi ne ya shigo ya dau
kayan Mami da Heedayah ya sa bayan motar Abba, Mami tace "Toh baka yi ma daughter
din taka Addu'a ba Allah ya sa ayi aiki a sa'a" Abba yyi murmushi yana kallon
Heedayah dake sanye da kananun kaya sai baby Hijab dake kanta tana rike da hannun
Mami, kamo hannunta yyi yace "Safe trip dear, Allah ya kai ku lafiya ya sa ayi
komai a sa'a, ya baki lafiyan idon ki" Ta kamo hannunsa a hankali tace "Abba xan
fara gani nima?" Yana murmurshi yace "In sha Allah Dear" ta d'an yi shiru sai kuma
tace "Toh baxan fara ganin Ammi na ba?" Abba da Mami duk suka yi shiru suna
kallonta, hawaye ne ya kawo idonta tace "Tace min ita xan fara gani fa" Abba ya
jawota jikinsa yace "Xa ki ganta in sha Allah daughter, Mami ma ai Ammin ki ce" Ta
gyada masa kai, ya share idonta suka nufi gun mota Mami na biye da su a sanyaye,
Sai bayan da ya shigar da Heedayah motar Mami tace "Baxa ayi ma matarka sallama
ba?" Yace "No, rabu da ita" Mami bata kuma cewa komai ba ta bude front seat ta
xauna suka fita gidan xuwa gidan Alhaji Imran Baffansu Junaid, Dakin da aka sauke
kaka Mami ta shiga da Heedayah bayan sun gaisa da Hajiya Zuwaira a dakinta, kaka na
xaune ko haske gari bai yi ba ga kayan karin kumallo iri iri a gabanta tana hada
shayi cikin katon mug, Mami ta xauna saman carpet tana murmushi tace "Ina kwana
kaka" Kaka tace "Lafiya lau, to Ina xan samu haka a gidanku??" Murmushi Mami kawai
take, can tace "Toh mu kaka xa mu tafi ayi mana addu'a, Allah yasa mu je a sa'a ayi
a sa'a, ku kuma Allah ya kawo ku lafiya" Kaka tace "Toh Allah ubangiji ya kai ku
lafiya, ya sa wnn marainiya ta fito lafiya, Allah kar ya bamu kunya yasa idanuwan
nan su rufa mana asiri su budu" Mami ta yi kasa da kanta tace "Ameen" Kaka tace
"Toh matso da ita in yi mata addu'a" Mami ta maida Heedayah kusa da kaka, kaka tayi
duk suran da ta sani da su ayatul qursiyyu da Amanar rasulu duk ta tofa mata tace
"Allah ubangiji ya sa ayi aikin a sa'a, ya rufa mana asiri ki fara ganin kowa kamar
yanda ake ganin ki, daga karshe kuma Allah ya bama d'a na ladan uban kudin da ya
kashe maki, Allah yayi masa albarka yasa kema ki ji k'an sa wataran kada ki yi mana
butulci..." Heedayah dai tayi shiru staring into space, kaka tace "Kaji
gantalalliya, baxa ki ce Amin ba, ko kina da niyyar butulcin ne ya sa kika yi shiru
bamu da labari" Mami tayi murmushi tana kallon Heedayah tace "Say Ameen daughter" a
hankali Heedayah tace "Ameen" Kaka tace "Toh maxa ku tafi kada jirgin ya tafi ya
bar ku ba mutunci ne da su ba haka suka so min xuwa umrana na karshe Allah ya fi
su" Mami tace "Toh Kaka, mun gode da addu'a, baxa ki fito ku gaisa da barrister ba"
Tace "Waye kuma Barrister? Don Allah ki rabu da ni kada raina ya baci, yyi ta kansa
inyi ta nawa kawai" Mami ta mike tace "Toh Allah ya sada mu da alkhairinsa kaka"
Kaka tace "Kiyi addu'a sosai kafin ku hau wnn bala'in na bature wai jirgi" Mami
tace "In sha Allah" kaka tace "Da Shuraim din dai xa a je koh?" Mami tace "In sha
Allah" Kaka tace "Toh duk Allah ya tsare ku, yayi maku albarka, ya sa ayi wnn aiki
a sa'a sai mun xo ni da Junaidu" Mami tace "In sha Allah kaka" daga haka ta fita
dakin, Abba na xaune parlor da Alhaji Imran, Ganin Mami yace "Lkci fa na wucewa
kada kuyi missing train" Mami tace "Ka samu Shuraim din?" Abba yace "No tare da
Junaid xa ku tafi" Shiru Mami tayi, Ya mike yace "Yeah, na kira junaid din ya
shirya ynxu" Mami ta xauna tare da Heedayah, Alhaji Imran yace "Allah ubangiji ya
tabbatar da alkhairi a tafiyar" Mami tace "Ameen Baffa" Ba a dau lkci ba sai ga
Junaid da traveling bag dinsa ya sakko kasa, Abba na kallonsa yace "Hope baka ce ma
kaka komai ba" junaid yace "Aa ban shiga ba" Abba yace "Good" Har motar Abba dake
parke waje Alhaji Imran da matarsa suka raka su, Alhaji Imran na kallon junaid yace
"Nayi maka transfer yanxu Incase da bukatar wani abun a can, Allah ya kai ku lfya,
ya sa ayi aikin a sa'a" Junaid yace "Toh Baffa Allah ya saka da alkhairi" Abba yyi
ma Alhaji Imran godiya haka ma Mami sannan suka dau hanyar train station na Hayin
rigasa, Junaid na xaune back seat da Heedayah, ta kwantar da kanta saman shoulder
dinsa a hankali tace "Good morning...."

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....


Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Har suka isa train station din bbu wanda yace komai cikin motar, Abba yyi parking
duk suka sauka suka shiga ciki with their luggages, shi dai Junaid na rike da
hannun Heedayah, Abba bai bar tashan ba kuma sai da ya ga tashin train dinsu xuwa
Abuja.... Kasancewar sai tara na dare flight din nasu na Qatar airways xai tashi
kamar yanda aka sanar masu bayan sun je airport din, hotel kawai Junaid ya kama
masu kusa da Airport din, Bayan Azahar Mami ta idar da sllh ta shirya xata tafi gun
step sister dinta da ke nan garin Abuja, shigowar Junaid kenan daga masallaci yana
kallonta yace "Ina xa ku Mami?" Tace "Xan je gidan Asiya ne in dawo yanxu" yace
"Ohk..." Mami ta ajiye ma Heedayah dake xaune saman gadon hotel din takalminta ta
kamo hannunta tace "Sauka ki sa takalmin ki" Heedayah tace "Mami da Yaya xa mu je?"
Mami tace "Aa ina ruwanki da wani Yaya" Tace "Mami mu je da shi plss" Mami ta saka
mata hijab dinta tana rike da hannunta ta nufi kofa tace "Sai mun dawo" junaid ya
bi su da ido, sai kuma yace "Mami ko xa ki bar ta ki je ki dawo" Mami ta juya tana
kallonsa tace "For what reason?" Da sauri yace "No naga kamar bata son tafiya ne"
Wani kallo tayi masa ta bude kofar ta fita, Heedayah dai kamar xata yi kuka take
bin Mami.... Har la'asar Mami na gidan yar uwarta da Heedayah suna hiran yaushe
gamo, Hajiya Asiya na kallon yar uwarta tace "To amma me yasa ba ku taho tare da
Junaid ba? Mun kwana biyu ba mu hadu ba" Mami tace "Muna sauka daxu da safe yace
min xai je gidan kawunsa so bna son ya kasance bai je ba, but in dai ta nan xa mu
dawo xai xo gun ki in sha Allah...." Hajiya Asiya tace "Toh shkkn, Allah ya kai ku
lfya ya dawo da ku lfya, ita kuma wannan yarinya Allah ya sa ayi aikin a sa'a" Mami
ta amsa da "Ameen" karfe shidda saura Mami suka bar gidan, babu yanda Hajiya Asiya
bata yi ba su tafi da abinci hotel din Mami ta ki amsa, Hajiya Asiya ta sa driver
dinta ya sauke su hotel din nasu. Karfe tara da few minutes na dare jirginsu Mami
yyi take off direct xuwa kasar India without stopovers, tafiyar kusan awa tara da
minti arba'in da takwas, kafin tashinsu kuma sai da Mami ta tabbatar ta kira Abba
ta sanar masa xa su tashin yayi masu addu'a yyi wishing dinsu smooth trip.... Tare
Junaid da Heedayah suka xauna a jirgin, Heedayah na laluba hannunsa tace "Yaya me
yasa Abba bai biyo mu ba" Junaid yace "He is very busy" tace "To kaka fa?" Yace
"She's old to journey with us" tace "To ya Sudais fa?" Yace "Shi ma he is busy amma
xai xo...." Heedayah tayi shiru sai kuma tace "Dama bana son Shureen ya biyo mu"
Murmushi yyi yace "Why?" Ta girgixa kai tace "Bana son sa" Junaid yace "Don't tell
anybody that" Tace "Why?" Ya ja hancinta ya kwantar da ita jikinsa yace "Sleep
Lolly...." Lumshe ido tayi nan da nan kuma bacci ya dauketa throughout the rest of
the journey. Bakwai saura na safiya Jirginsu ya sauka Indira Gandhi international
airport new Delhi, Amma sai karfe goma saura suka shiga Indraprastha Apollo
Hospitals da xa ayi ma Heedayah aiki, don sai da suka fara sauka hotel dake nan
kusa da hospital din suka huta, Bbu bata lkci aka yi admitting din su a babban
asibitin a ward dinsu su kadai, ba laifi ward din na da d'an girma, amma kana gani
kasan dai kudi ne kawai aka kashe ba kadan ba.... Kamar yanda Abba yayi tunani haka
ne don sun daura Heedayah kan allurai na sati daya, sai kuma some diet da aka daura
ta kai, Likitar dake ma Mami bayani a office dinta da harshen turanci ta sanar ma
Mami irin Disorder din Heedayah da ake kira da Congenital Blindness, sannan ta
sanar mata Novel Gene therapy xa ayi mata to correct the disorder, probably through
luxturna, Mami da duk jikinta yyi sanyi tace "But is there much chances of her
gaining her sight?" Likitan tace "Hopefully, though it's a rare disorder but we
will try our best" Mami tayi ma likitan godiya ta mike ta fita office din ta koma
ward dinsu. A kwanaki bakwan nan Mami kusan kullum sai ta tashi sllhn dare tayi
addu'ar Allah ya sa ayi nasara a aikin da xa ayi, har ranta take tausayin Heedayah
take kuma fatan Allah ya bude mata idanuwanta, bata san yanda xata ji ba idan aka
yi aikin nan Heedayah bata yi gaining sight dinta ba, she can't just imagine that,
a hotel din da suka fara sauka na kusa da hospital din Junaid ke kwana, amma
throughout the day yana asibitin tare da Heedayah da Maminsa, sai dai kawai ya fita
ya siyo masu Nigerian dishes safe rana da daddare, ko kuma ya fita xuwa yin sllh...
A kullum sai Abba ya kira ya sa a ba Heedayah waya sun yi magana, complain dinta
kuwa a ko da yaushe shine idonta suna mata ciwo, don a hankali fararen idanuwanta
masu kyau suka fara sauya kala xuwa ja kuma tayi ta sosa su, Sudais ma kusan kullum
sai ya kira Mami ta ba Heedayah sun yi magana, ana haka har suka cika kwana goma
cif a asibitin ya rage kwana biyu a shigar da Heedayah theatre.... Junaid na xaune
tare da Mami ana gobe xa ayi operation din wayarsa ya fara ring, dauka yyi saman
table dake kusa da shi yana kallon screen din dake nuna masa Beauty, to waye haka?
ya dau lkci yana tunanin waye yyi ma saving da haka, sai kuma ya daga kafin ya
katse ya kai kunne, Daga daya bangaren aka yi sallama cikin siririn murya, sai
bayan kusan second biyar ya dau muryar ya amsa sallaman, Salima tace "Haba Jayyy
shine bbu ko sallama kayi tafiyar ka India, to gani a new Delhi din nima, yanxun
nan jirginmu ya sauka daga Nigeria wllh" junaid ya d'an yi shiru da mamaki, can dai
yace "Ke da wa kika xo new Delhi?" Tace "Wllh wani saurayi na ne ya xo business
trip shine kawai yace in rakosa, a hotel din kusa da Airport xa mu sauka ynxu....
Ku kuna wani asibitin ne?" Yace "Toh ki huta tukun xa mu yi waya" tace "Toh shkkn
Jay, sai anjima dama duk na gaji, wanka xan yi ma yanxu" Yace "Alright" daga haka
ya katse wayarsa, Mami na kallonsa tace "Wacece?" Ya kalleta da sauri sai kuma yace
"Ohk wata coursemate dita ce from Nigeria...." Mami tace "Ya aka yi tasan kana
India?" Yace "I told her I will be coming to India tun last week" Mikewa yayi ganin
Heedayah xata sauko saman gadon ya nufeta yace "What happened?" Tace "I want to
ease my self" Tashi Mami tayi ta kama hannunta xuwa toilet dake ward din. Washegari
da asuba aka shigar da Heedayah theater, a asibitin Junaid ya kwana ranan, coz shi
ma he is so tensed, he just don't want to imagine the operation won't be
successful, haka ma Maminsa da bata yi wani bacci daren ranan ba, ita kanta
Heedayah duk son baccinta bata yi baccin ba daren don idon na damunta sosai, Mami
taji tausayinta ba kadan ba, har karfe goma na safiyan Mami na xaune saman darduma
hannunta rike da carbi, Junaid yace "Mami baki yi breakfast ba, pls take something"
Tace "Toh" Tea ya hada mata a cup ya mika mata ta amsa, Mami bata wani sha shayin
ba ta fita ta xauna saman kujeran dake jere gaban theatre din da aka shigar da
Heedayah.... Karfe sha biyu likitoci biyu suka fito theater din sanye da gown din
operation, Mikewa Mami tayi wanting to hear something from them, da turanci daya
likitan yace mata ta kwantar da hankalinta all will be well, daga haka ya wuce,
Mami ta koma a hankali xauna, bayan minti talatin wasu likitocin uku suka fito su
ma din dai haka suka ce mata, ita dai gaba daya hankalinta ya kasa kwanciya, daga
karshe nurse biyu suka fito, Mami ta kara tashi ta nufesu, su ma dai xancen daya ne
suka yi wucewarsu. Sae kusan azahar aka kai Heedayah ward dinta tana bacci, Mami na
xaune kusa da ita sai kallonta take an rufe mata idanuwanta da white eye pads, gaba
daya she is disturbed and tensed, Junaid dai na tsaye daga gefen gadon ya rungume
hannunsa shi ma yana kallonta, wayar Mami ya fara ring ta dauka ganin Abba ne ta
daga a sanyaye ta kai kunne, gaisawa suka yi tace "Yanxu aka fito da ita, but akwai
eye pads a idanuwan...." Daga daya bangaren Abba yace "Toh Allah ya sa an dace, can
I speak to her now?" Mami tace "Bacci take" Abba yace "Toh I will call back later"
daga haka suka yi sallama ta ajiye wayar tana kallon junaid tace "Toh baccin me
take haka, ko anaesthesia da aka yi mata ne?" Yace "No, anaesthesia din da aka yi
mata iya aikinsa bangaren idon, she is not unconscious bacci take" Mami tayi shiru
bata ce komai ba.... Har karfe hudu na yamma Heedayah bata farka ba, Junaid ya tafi
yyi sllh ya dawo ya tadda Mami na sallahn ita ma, ya xauna kusa da Heedayah ya kamo
hannunta yana kallonta ganin sai motsi take, a hankali cikin rawar murya ya ji tace
"Mami idona na min ciwo" Ya dafa goshinta still holding her hands tight yace "Xai
daina dear...." Ganin xata mike xaune ya dagata ta xauna ta kai daya hannunta
idonta, da sauri ya rike hannun ganin cire pads din take son yi yace "Noo
don't...." Ta fashe da matsanancin kuka xata kwace hannunta tace "It's paining me"
ya ki sake hannun yace "Zanyi tafiyata in bar ki ke kadai a nan if you don't stay
still now...." Ganin kukan da take ya rungumeta yace "Toh yi hakuri xa a cire maki
yanxu, ki daina kukan, I will call the doctor now" cikin rawan murya tace "Yana min
xafi sosai" Mami na idar da sllh dama fita tayi kiran likita don yace idan ta tashi
a sanar masa, yana shigowa allurai biyu yyi mata ya sa mata drip ya fita... Ba a
dau lkci ba kuma tayi bacci junaid na rike da ita har sannan, Mami ta sake komawa
gun likitan don jin abinda ake ciki, nan ya sanar mata nan da kwana uku xa a cire
eye pads din a duba idon with hope that tayi gaining sight dinta clearly, kafin
kwana ukun kuma xa ayi ta mata injections xa kuma ta dinga shan magunguna, Mami
tace "But is there nothing to do about the pain pls?" Yace "The pain will subside
before tomorrow...." Mami tace "Are you giving me hope that the operation is
successful Doctor?" Likitan ya girgixa kai yace "We are also hoping it's
successful, but if it's not, then we will try anoda operation.... The last" Mami ta
kasa ce masa komai, can ta mike tayi masa godiya a sanyaye ta fita. Tana komawa
ward din Junaid ya kwantar da Heedayah ya mike yace "Xan je in dawo yanxu Mami"
Mami tace "Ina xa ka?" Yace "I
want to get something, ba dadewa xan yi ba" tace "Ohk, ka siyo fresh milk when
coming back" yace "Toh" daga haka ya fita, nan kuwa tun safe Salima ta ishesa da
kira shine yyi deciding kawai ya tafi ya sameta inda tace masa take ko xata daina
kiransa. Yana tsaya gaban hotel din ya kirata, tana dagawa yace "Ina waje ki fito"
tace "Haba ka shigo ka jirani a reception mana Jayy..." Yace "But I can't come in,
ki daure dai ki fito Ina sauri ne" tace "Wllh tun safe kai na ke ciwo a kwance ma
nake ynxu, bbu ynda Suraj bai yi in raka ba na ki fita, ka daure ka karaso ko
reception ne plss Jayy" yace "Alright" daga haka ya katse wayar ya shiga cikin
babban hotel din, Yana reception din ya kirata, sae ga ta ta sakko sanye da riga da
wando sai black veil da ta daura a kai, shi duk wayar da suke ya kasa yrda da gaske
tana India sai ynxu da ya ganta, ta sakar masa murmushi tace "Welcome, mu shiga
ciki in daura after dress mu tafi hospital din, tun safe na damu Ina son xuwa wllh"
yace "Aa ba a barin mutane fiye da biyu and yau ba visiting day bane" lkci daya
mood dinta ya canxa tace "To yaushe ne visiting day din?" Yace "Nan da 3 days" Ta
tabe baki tace "Toh mu je ciki" yace "No, na gaisheki, xan koma ynxu coz I need to
get them food" Ta marairaice tace "Haba Jayyy, ae ba cewa nayi ka shiga ka dade ba,
kawai mu je kaga Inda nake, ni fa bbu wanda yasan ma na taho India, tafiyar ce ta
xo min cikin gaggawa, Kuma Suraj bai son tafiya shi kadai dama" Bata jira cewarsa
ba ta kama hannunsa tace "Come on mu je plss" da mamaki yake kallonta, can ya janye
hannunsa daga nata still following her slowly har xuwa hotel room din da take.

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Junaid ya nufi kujeran dake makeken dakin hotel din ya xauna, gefensa ta xauna tana
wani murmushi tace "Me xan kawo maka Jay? Ko in sa a kawo maka abinci?" Ya girgixa
kai yace "Nothing, saurayin ki kika biyo India kenan?" Tace "Ehh shi na biyo amma
wllh sbda kai na xo, India ai ba wani kasar xuwa hutu bane kasar xuwan marasu
lafiya ne, wani saurayina fa tun last week yake son mu je dubai mu huta amma na
gwammace in biyo wannan xuwa India duk don sbda kai wllh" Junaid ya gyada kai yace
"Ni kuma me xan maki da kika biyosa India sbda ni?" Ta wara ido tace "Just to see
you mana, Ina dawowa daga Abuja fa aka ce min kun taho India da makauniyar nan...."
Yana kallonta da kyau yace "Kada ki sake ce mata makauniya" Ta d'an yi shiru, sai
kuma ta tabe baki tace "Toh ka tafi ko sallama babu shi yasa da na samu opportunity
kawai na biyo ka" ta karasa tana murmushi, Ya girgixa kai yace "So this the best
life you think you are living right?" Tayi frowning face dinta tace "Ban gane ba,
me ya kawo wannan maganan kuma?" Ya tabe baki yace "Anyway shkkn, so yanxu kin gan
ni kuma mun gaisa, plss kar ki sake kiran line dina sbda a hospital nake da mara
lafiya.... Pls don't call again I beg you" Ta marairaice tace "Wllh tllh sbda kai
na xo kasar nan Jay, ka kaini asibitin mana nima muyi jinyar tare" Yace "Aa, idan
mun koma Nigeria sai kiyi jinya but not here coz bbu ma wanda yasan kin xo nan, I
repeat don't call me again, I don't even want to ask what ur name is, but what ever
it is plss don't call my line again Lady" Kwantawa tayi jikinsa kamar xata yi kuka
tana shafa kirjinsa tace "Haba Jay...." Turata yyi har sai da ta fadi kasa ya mike
yana mata wani kallo yace "Are you stupid?" Shiru tayi tana kallonsa, yace "Tun da
nayi respecting dinki na xo har Inda kike kada ki sake kirana, na xo ne dama don
kada ki kuma kirana, idan kun gama abinda ya kawo ku ke da saurayin naki ku koma
inda ku ka fito tare, we will meet back in Nigeria...." Daga haka ya nufi kofa ta
bi sa da kallo ya bude kofar xai fita suka kusa cin karo da Suraj din, Junaid ya
kallesa daga sama har kasa, ya bi gefensa ya fita dakin, Suraj ya kalli Salima da
ta kauda kai da sauri, yana nunata da yatsa yace "Dama shi yasa tun jiya kike wasa
da hankalina ashe appointment gare ki da wani? To maxa kwashe kayanki ki bar min
hotel room dina yanxun nan" Ta masa wani kallo tace "Ae ba wani ya kawo ni kasar
ba, yanda muka xo tare haka xa mu koma tare, kawai don ka kawo ni India sai aka ce
maka haka xaka dinga samu na baxa ka biya ba kamar wata gareji, to ko garejin ma ae
ana biya" ko amsa bai bata ba ya tafi inda jakar kayanta yake ya dauka ya bude kofa
ya jefar corridor din hotel rooms din, ya koma ya dauko handbags dinta da sauran
tarkacenta duk ya watsar a waje, bude baki tayi tana bin sa da kallo a tsorace ta
kasa cewa komai ita ma ya tafi ya ja ta har kofan ya turata waje ya rufe kofar sa.
Junaid na isa hospital din dab da magrib Mami tace "Where are you coming from
Junaid?" Ya ajiye ledan madaran hannunsa ba tare da ya kalli idonta ba yace "Mami
wata frnd dita ce da muka hadu online years back, she's here in india, so shine
naje muka gaisa" Mami ta ta6e baki bata ce komai ba, gadon da Heedayah ke kwance ya
nufa ya xauna saman kujera yana kallonta, bacci take heavily, kana gani kasan
alluran bacci aka mata, ya kai hannu goshinta a hankali ya ji da xafi, Mami tace
"Ynxu naje nayi masu complain xafin jikin nata" Ya gyada kai bai dai ce komai ba,
Mami tace "Shaheedah called me daxu bayan ka fita" Kallon Mami yyi yace "Ohk" tace
"Baban nata ya ji sauki amma sosai koh?" Yace "Ehh ya samu lfya" Wayarsa da ya fara
ring a aljihu ya ciro, ya ga Beauty gaban screen din, ya d'an saci kallon Mami dake
kallonsa, ya mayar da wayar aljihu bayan ya sa shi total silent, yana ta xaune
dakin har Magrib yyi, Mami ta shiga bandaki yin alwala sai da ta fito ya mike yace
"Xan je inyi sllh" Mami tace "Ohk" daga haka ya fita, sai da ya fito haraban katon
asibitin ya ciro wayarsa ya ga miss calls din Salima kusan ashirin, ya wani buda
ido da mamaki yana kallon screen din wayar, sai ga kiranta ya kuma shigowa, dagawa
yyi ya kai kunne kafin yace komai ta fashe masa da kuka sosai tace "Jay wllh ya
koreni ya watsar min da kaya ganinka da yayi, gashi ni bani da inda xan je bamu da
kowa a kasar nan, ko kudin kama hotel ma bani da shi balle kudin komawa Nigeria ni
dai kawai biyosa nayi tunda mun saba tafiya tare, yanxu haka ina titi da kayana
daga ni sai kudin Nigeria dubu uku a jakata, don girman Allah ka rufa min asiri,
nayi ta kiran layinsa ko hakuri ne in basa amma yyi blocking dina wllh" Junaid yace
"Amma baki da hankali, ni da kike kirana me xan maki? ni na kawo ki India da xa ki
kirani ki ce min ya kore ki, look kar ki sake kiran layina idan ba haka ba duk
abinda na maki ke kika ja wllh" Ta rushe da matsanancin kuka tace "To yanxu Ina xan
je fisabilillahi, ni wllh bbu wanda yasan Ina India sai kai, don girman Allah Jay
ka rufa min asiri" Ya ja tsaki ya kashe wayarsa ya tafi yin sllh. Da abinci ya dawo
ward din, Mami ta kallesa da damuwa tace "Toh ita tana ta bacci bbu fa abinda ta ci
tun safe wllh" Junaid yace "Ga drip an sa mata for that, xuwa can cikin dare xata
tashi sai ki hada mata shayi" Mami tace "Toh ko in tasheta yanxu in bata?" Yace
"Aa, ai baxata tashi ba, allura suka mata" Mami tace "Toh shkkn" Yana ta xaune ward
din kusa da Heedayah har kusan sha biyu na dare, yana lura da da cewa alluran ya
fara saketa don sai motsi take, ta juya can ta juya nan, kana ganinta kuma kasan
she is still in pain, lkci lkci take kai hannu idonta, sai ya rike hannun ya mayar
saman gado, yana mata haka kuma sai ta turo baki, yyi murmushi ya d'an kalli Mami
da ta fara bacci ya ja bakin, kara tayi kamar jira take ta fara kokarin mikewa
xaune, Mami ma ta farka ta mike xaune da sauri, Kamar xata yi kuka tana tattaba
gadon tace "Mami kina ganinsa ko? Bakina ya ja min da karfi" Mami ta sakko saman
gadon da take tace "Sai da safe tashi ka fita, good night" Tashi yyi kafin ta iso
Inda yake yana murmushi ya nufi kofa making sure hotel key dinsa na aljihunsa,
Heedayah tace "Mami to ina xa shi?" Mami tace "In xuba maki abinci ko in hada maki
tea?" Heedayah ta 6ata fuska tace "Mami ina Yaya xa shi?" Mami tace "Ina ruwanki da
shi?" Junaid ya kalleta sannan ya bude kofar ya fita still smiling. Yana fitowa
wanka bandakin hotel room dinsa ya saka jallabiyarsa ya kwanta ya dau wayarsa, miss
calls arba'in ya gani, ya mike xaune da sauri yana kallon wayar, sai ga kiran
Beauty a screen dinsa, ya daga ya kai kunne a fusace yace "Ke wace irin Mahaukaciya
ce wai? Draining din battery dina kike son yi? Why are you calling me for heaven
sake???" Ta fashe masa da kuka da karfi tace "Wllh jay gani a bakin titi har yanxu
ni ban san Inda xanje ba, ko asibitin ne ka taimaka ka fada min sunansa in je,
gashi duk an watse an bar ni ni kadai kada yan sandansu su xo wucewa su gan ni su
tafi da ni, don girman Allah ka gaya min asibitin in je jay...." Yace "Toh wai da
kike ta kirana ni na kawo ki India ne baiwar Allah?" Tace "Amma silar ka na xo ai,
Allah sbda kai na biyo Suraj duk da nasan Mahaukaci ne, to wa xan kira idan ba kai
ba" Junaid ya ma rasa me xai ce mata, ita kuwa sai rera masa kuka take a kunne, can
ya ja tsaki yace "Ina kike yanxu" Tana kuka ta gaya masa ya katse wayarsa, bbu ynda
ya iya haka ya dau kudi ya fita hotel din ya kulle dakin, Tricycle ya samu xuwa
Inda tace masa take, ai ko ya sameta gefen hanya ita kadai xaune kan jakan kayanta,
yana sauka daga tricycle din ta mike xaune duk idonta yyi suntum sbda kuka, yana
mata wani kallo yace "Ashe ke karamar yar duniya ce tunda har xa ki shigo India ki
rasa wajen kwana duk yawon da kike da maxa kasashe daban daban" Ita dai bata tanka
sa ba ta dau jakarta ta saka cikin Tricycle din da sauran kayanta sannan ta shiga
ta xauna, yyi kwafa ya shiga adaidaitan suka koma hotel din da yake, Sai karfe
kusan daya da wani abu suka shigo hotel din, tana ganin wani dakin xai biya mata
tace "Aa jay kada ka wani kashe kudin ka, ni dai gwara kawai ka harhada ka biya min
kudin jirgi in koma Nigeria" Bai tanka ta ba yyi wucewarsa sama ta bi sa da kaya
tana tangal tangal don ko daya bai dau mata ba, yana bude dakin ya shiga ya bar
mata a bude ta shigo sannan ta kulle tana bin dakin da kallo, saman gado ya nufa ya
dau bargo da pillow ya jefa mata a kasa snn ya kashe wutan dakin yyi kwanciyarsa,
ta ajiye kayanta ta dau pillon da bargon ta shimfida bargon sannan ta daura pillon
a kai, a hankali tace "Nagode, amma xan d'an kunna dim light sbda xan yi wanka" Ko
tanka ta bai yi ba ya juya mata baya yana danna wayarsa, bayan kusan minti goma ya
ga ta kunna wuta mara haske sosai ta shiga bandaki, yana jin alamar tayi wanka ta
fito, mamaki ne ya cikasa sosai ganin naked ta fito daga bandakin walking
majestically, a hankali ya ajiye wayarsa ya rufe ido ya tsiri baccin da bai yi
niyya ba a lkcn, ta gama buruntunta ta cika dakin da kamshin turare iri iri da ta
fesa a jikinta, shi dai idonsa na rufe gam, xagayawa tayi kusa da shi tace "Don
Allah ka d'an ban wayarka xan kira yayata, tun daxu take kirana sbda tashin hankali
ban dauka ba gashi ynxu bani da isashen kati" yyi banxa da ita har sannan idonsa a
rufe, ta kai hannunta me sanyi a hankali fuskarsa tace "Kayi bacci ne Jayy?" Lkci
daya ya mike xaune ya sauke mata lafiyayyen mari yace "I swear to Allah ba karamin
aikina bane in fitar dake hotel din nan yanxun nan, are you mad????" Mikewa tsaye
tayi da rigar baccinta iya cinya bbu komai ciki ta dafe kuncinta tana kallonsa, yyi
mata tsawa yace "Baxa ki tashi gabana ba sai nayi ball da ke" gyada kai tayi ta
juya tana karkade karkade ta xaga Inda ta shimfida bargo ya bi ta da wani irin
kallo, yyi wani kwafa ya koma ya kwanta ya rufe ido.... Daren ranan dai bai yi
bacci ba sai juye juye yake shi kadai, sae dab da asuba bacci ya daukesa, hasken
ray din rana da ya sauka fuskarsa ne ya farkar da shi, ya mike xaune da sauri
yana kiran Allah a xuciyarsa, gefensa ya ga Salima kan gadon tana bacci hankali
kwance, bbu abinda baya gani a jikinta ta cikin shegen kayan baccin da ta saka,
tashi yyi da sauri ya shige bandaki, tun da yake dai da girmansa bai ta6a missing
sllhn asuba ba ko a jam'i ko ba a jam'i ba, da asuban xai yi raka'atainil fijr snn
yyi sllhn sa amma wai yau shine har kusan 8 bai yi sllhn asuba ba, ransa a bace ya
wanke baki yyi alwala ya fito ya shimfida darduma ya tada sllh, ya kusa minti sha
biyar saman darduman bayan ya idar sannan ya mike ya buga gadon da karfi yace
"Dauki kayan ki mu wuce airport...." Ta bude ido a hankali tana wani juye juye tace
"Anya ma da jirgin xuwa Nigeria direct kuwa yau??? stopovers....." Yyi mata wani
tsawa kafin ta karasa yace "Tashi ki dau kayanki ki fita ki samu wani wajen xama
har a samu plane din Nigeria, not here anymore" ta marairaice tace "Toh amma ae ka
jira inyi wanka in shirya tukun mana Jayyy" tana fadin hka ta mike tsaye dab da
shi, ya dauke kai ya bar wajen, wayarsa ya nufa ya dauka ya ga miss calls din Mami
har Uku, xaro ido yyi don kullum ana idar da sllh asuba yake shiga asibitin with
breakfast, fita yyi dakin da wayarsa in a haste, sae da ya tsaya hanya ya siya masu
breakfast snn ya wuce asibitin.... Mami na xaune kusa da Heedayah dake shan shayi a
saman gado da kwai da bread, she looks very strong, an kuma sauya mata eye pads din
idonta, tana jin an bude kofa ta dakatar da shan shayin tace "Mami Yaya ne?" Mami
dai bata ce komai ba sae kallon Junaid take daga sama har kasa, coz duk a birkice
yake, snn bai ta6a shigowa asibitin da jallabiya ba, kansa a kasa yace "Ina kwana
Mami" Mami ta amsa ta dauke kai ta ci gaba da danna wayarta da take, yayi kasa da
murya kamar munafuki yace "Mami na makara ne yau wllh...." Still bata kallesa ba
tace "Ehh na ga alama" Yace "Ga breakfast...." Tace "Don't worry an kawo mana" Da
mamaki ya dago kansa yace "Who??" Kafin tace komai aka bude kofar ward din ya juya
don ganin wanda xai shigo....

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Sudais ne ya shigo ward din shi ma yana kallon Junaid kamar ynda Sudais ma ke
kallonsa, Heedayah tace "Mami waye? Ya Sudais?" Mami tace "Eh" Sudais ya nufi
Junaid yana murmushi ya basa hannu suka gaisa, Mami tace "Har ka dawo" Yace "Ehh na
dawo Mami" kujera ta nuna masa ya xauna, Shi dai Junaid na tsaye har sannan ya ki
yrda su hada ido da Maminsa, Heedayah tace "Yaya me ya sa baka xo tun daxu ba sai
yanxu, Ya Sudais ne ya kawo mana breakfast fa" Ya d'an kalleta yace "Ban xo din ba"
Ta buda hannu ta tabe baki tace "Ae kai da Mami" Sudais dake murmushi yace "Ko dai
shi da ke?" Washe hakoranta tayi bata ce komai ba ta ci gaba da shan shayinta, can
ta ajiye cup din tace "Ya Sudais me ya sa baku xo da kaka ba, Ina missing dinta" a
hankali ta kara da cewa "I am also missing Abba" Sudais yace "Xa su xo in sha
Allah" Junaid dake ta tsaye ya dake ya kalli Mami yace "Mami xan je in dawo" Bata
ko kallesa ba tace "Ohk" a hankali Heedayah tace "Yaya Ina xaka kuma? You are just
coming fa" Yyi banxa da ita ya fita dakin.... Rai bace ya koma hotel din ya bude
kofar room din ya shiga ga mamakinsa Salima kara gyara ma kayanta wajen xama tayi,
ga gadon ta gyara sa fess sae kamshi ko ina yake amma bata dakin, daukar kayan yyi
ya fito fuska daure har haraban hotel din ya nufi gun masu gadi nan ya bar masu
kayan bayan ya sanar masu me shi xata xo ta amsa, yana komawa ya ga handbag dinta a
dakin, har ya dauka sae ya tsaya ya bude ciki, duk tarkacen kayan kwalliyanta ne
ciki da prophylactic na mata har da maza and different types of pills ciki har da
aborticide, ya girgixa kai cike da takaici ya rufe jakar ya fita dakin ya kai can
gun masu gadi sannan ya koma dakinsa, wanka yyi ya shirya ya d'an kwanta, gaba daya
jin sa yake wani iri, bayan kusan minti talatin ya mike a hankali ya dau wayarsa ya
fita ya kulle dakin da makulli ya bar hotel din. Asibiti ya koma kafin ya shiga ya
kira line din Salima, ba bata lkci ta daga tace "Jayyy" ya wani daure fuska kamar
tana ganinsa, strictly yace "Ga kayanki can gun masu gadi na ajiye ki dauka, and
don't ever try calling my line again idan ba haka ba xa ki sha mamaki, I repeat
don't try calling my line again...." Salima ta marairaice tace "Ban gane kayana na
gun masu gadi ba jay, me ya kai kayan gun masu gadi juma? Ai na dau spare key kafin
in fito" shiru Junaid yyi da mugun mamaki jin abinda tace, can ya ciro makullin
aljihunsa yana kallo, wani tsawa yyi mata yace "I swear to Allah kada ki yrda in
dawo ya in sameki hotel room din nan, duk abinda na maki ke kika ja ma kanki kinji
na rantse...." Ta fashe masa da kuka tace "Toh wai ina kake son in je yanxu Jay?
Bayan na gaya maka wanda ya kawo ni ma yyi blocking dina kuma bani da kudin komawa
Nigeria? Haba Jay sai kace baka ta6a sanina ba" cikin fushi yace "Good... nima ynxu
xan yi blocking din naki but before then I am still warning you kada ki yrda in
dawo in ganki dakina, wllh sai na maki abinda baki yi tunani ba" Bai jira cewarta
ba ya katse wayar yayi blocking din nata sannan ya shiga cikin asibitin trying to
calm himself, shi ma ciki bai wani ga fuskar Mami ba hakan ya sa ya fito haraban
asibitin ya xauna.... Har aka yi azahar Junaid na xaune ne haraban asibitin ya ki
shiga ward din, bayan azahar kuma Sudais ne ya fita ya siyo masu abinci ya kawo,
Mami na xuba ma Heedayah, Heedayah tace "Mami ko dai Yaya ya wuce ne?" Mami bata ce
mata komai ba, Sudais yace "Yana waje, ko xa ki je?" Ta make kafada tace "Aa ba
ruwana da shi ai" Da daddare bayan isha Junaid ya shigo ward din da dinner da ya
siyo masu, Mami da Heedayah ne kadai dakin Sudais baya nan, Yana ajiye masu kuma
yace "Mami xan tafi in kwanta" Mami tace "Good, Ka jira Sudais he went to get
something sai ku tafi tare" Da mamaki yace "I tot yyi lodging hotel ai" Mami tace
"Yes he did, amma nace ku tafi tare naka hotel din" Junaid yace "Ohk" daga ya nemi
waje ya xauna ya d'an kalli Heedayah bai ce komai ba ya fiddo wayarsa yana dannawa
silently, sai wajen takwas da rabi Sudais ya shigo ward din ya ajiye ledan fruits
din hannunsa yace "Mami Abba ya kira ku?" Mami tace "Yes Ina sllh ya kira but I
followed the call yanxu" yace "Ohk" ya dau apple daya ya kama hannun Heedayah ya
saka ciki, kin sake hannunsa tayi a hankali tace "Thank you...." Mami tayi murmushi
bata dai ce masu komai ba, kallonsu kawai junaid ke yi amma ba directly ba, Sudais
na juyowa ya maida idonsa saman screen din wayar dake hannunsa da sauri, Mami tace
"Sudais kai yake jira ku tafi hotel ynxu" Sudais yace "Ohhh but ai nayi lodge a
wani hotel Mami" Mami tace "Noo, ku tafi tare, you two should stay together" Junaid
dai idonsa na kan wayarsa amma Mami yake saurara, can ya mike ya maida wayar aljihu
yace "Toh sai da safe Mami" Daga haka ya nufi kofa, Mami bata tanka sa ba tace
"Sudais baxa ka debi fruit din ba, ai sun yi yawa" Yace "Noo na sha ai" tace "Ohk
sai da safe" yace "Allah ya tashe mu lafiya" Heedayah tace "Yaya Sudais byee" yace
"Bye dear...." Junaid na tsaye bakin kofa bai fita ba, can ya tabe baki ya fita yyi
wucewarsa, Sudais ya bi bayansa duk da har ransa bai so bin junaid ba amma baya son
yi ma Mami musu, sai bayan da suka fita Heedayah ta fashe da kuka a hankali tace
"Mami kinga yaya bai kulani ba koh, he don't want to talk with me" Dariya ta ba
Mami sai dai bata yi ba, Mami tace "Kyaleni da shi xan yi maganinsa" Tunda suka bar
hospital din Junaid bai ce da Sudais komai ba, haka shi ma Sudais din, nan ko
Junaid is just imagining ace su je hotel din ya tadda Salima a dakinsa, suna isa
hotel din suka sauka tricycle din Sudais ya bada kudi, Junaid ya jira aka basa
canji sannan suka shiga hotel din a tare, Junaid ya tsaya gun masu gadi yana
tambayar ko mai kayan daxu ta xo ta dauka, suka amsa masa da eh, bin bayan Sudais
yyi xuwa cikin hotel din, a hankali Junaid ya fara murda kofar dakin ko makullin
bai sa ba ya ji kofar a bude, lkci daya xuciyarsa ya fara tafarfasa ya shiga dakin,
Sudais ma ya shiga ciki, xaune suka samu Salima da takeaway din abinci tana ci a
dakin, Sudais ya tsaya bakin kofa yana kallonta with so much surprise, Mikewa tsaye
tayi ita kanta tayi shock din ganin Sudais, Junaid ya nufeta a mugun fusace ya
sauke mata wawan tagwayen Mari cikin tsawa yace "Me na ce maki? What did I tell
you???" Dafe kuncinta tayi tana kallonsa with shock, can ya fashe da kuka tace "Toh
wai ina kake son in tafi bayan nace maka bani da kudi Jay, Banda sbda kai me xai
kawo ni kasar nan??" Gun kayanta ya nufa ya dauke jakunkunanta biyu ya bude kofa ya
watsar waje ya dawo ya nufota, tana ganin haka ta shige bandaki da gudu ta sa
makulli, Sudais na yatsine fuska da mamaki yace "Me ye hadin ka da yarinyar nan? Me
ya kawota nan? Dama da ita aka taho" Rai bace junaid yace "Saurayinta fa ta biyo ya
koreta shine ta makale min nan, I don't even know her...." Katse sa Sudais yyi yace
"Sorry but I can't stay under same roof with this lady, dama na kama hotel I can't
just say no to Mami, it's better in koma can, but be careful with this lady she can
be cunning" Junaid ya dau jakarsa shi ma yace "Mu tafi hotel din naka, I am not
staying here either, dama kudin kwana 15 na biya for this hotel kuma nan da jibi
xai yi expire so I prefer leaving too" Sudais yace "Better...." Daga haka suka fita
dakin xuwa hotel din Sudais. Salima na jin alamar sun fita ta bude kofar ta leko
ganin ba kowa ta fito dakin, ba karamin tsorata tayi ba ganin Sudais, ita a rayuwa
ma akwai wanda ta tsana kamar shi kuwa, ko gaisuwa baya hada ta da shi dama, cije
yatsa tayi ta xauna gefen gado a hankali tace "Anya ma Junaid din nan na da lafiya
kuwa, upon everything yesterday he isn't still moved" Da sauri ta mike ganin bbu
jakar kayansa ta tafi window tana lekawa taga Inda suka nufa, tricycle taga suka
shiga, ta koma ta xauna ta marairaice tace "Dama Sudais ma na kasar nan ban sani
ba??" Can ta gyada kai tayi wani murmushi tace "idan ka san wata baka san wata ba
Junaid" Tun da Mami ta tashi yau da asuba take ta fargaba ita kadae don ranan xa a
cire ma Heedayah eye pads din idonta, kuma ranan ake sa ran xata fara gani, daren
ranan Mami sae da tayi sllh ta roki ubangiji yasa an dace, ya sa karshen wahalan
kenan.... Karfe shidda da rabi likitocin suka fita da ita xuwa theatre, Mami dai na
xaune bakin theatre din sae addu'a kawai take, ga faduwar gaban da yyi mata yawa,
da taji motsi sae ta kalli kofa da sauri amma bbu wanda xata ga ya fito har karfe
bakwai da rabi, kukan da ta ji Heedayah ke yi daga ciki ya fi daga mata hankali,
tun daga nisa take kallonsa har ya karaso tare da wani likita baindiye walking
slowly, likitan ya gaida Mami da ladabi, Mami ta amsa don da shi aka yi ma Heedayah
aiki 3 days back, shi ma dai yyi kasa da kai ya gaisheta, ta amsa tace "Ya hanya"
Yace "Alhmdllh, ya kokari" tace "Mun gode Allah" baindiyen yayi tapping dinsa a
baya da harshen turanci yace sae sun hadu anjima, daga haka ya juya ya wuce, dai
dai fitowar wani likita yana kallon Mami yace "You can go in Madam, a Dr will
explain everything to you inside" mikewa Mami tayi amma ta kasa tambayarsa ba ayi
nasara bane aka ce ta shigo, kuma ta kasa shiga ciki, likitan yayi wucewarsa, kansa
a kasa ya nufi kofar shiga theatre din walking slowly, Mami ta bi sa da kallo har
ya shiga ciki, Heedayah na xaune saman gadon ta takure waje daya ta rufe fuskarta
da pillon saman gadon tana kuka a hankali, likitoci biyu na tsaye suna jiran
shigowar Mami, Daya daga likitan da turanci yace "Her brother?" Ya gyada masa kai
sannan ya karasa gadon yana kallonta, likitan yyi murmushi yace "Yes it was
successful, but it's a new world to her.... And it will take sometime before she
will adapt, like... she will have problem with light, Human, infact everything,
because she just left the world of darkness" Dago kanta yyi ta bude jajayen idonta
a hankali tana kallonsa suka yi ido hudu, lkci daya ta fasa ihu kamar warce ta ga
mugun abu, ya rungumeta, jikinta ya dinga rawa gaba daya a tsorace take, duk wnn
abun Mami na
tsaye bakin kofa tana kallonsu, lkci daya hawaye ya kawo idonta tana hamdala a
xuciyarta ta karaso gadon da sauri tace "Heedayah" cikin rawar murya Heedayah na
kara shigewa jikinsa tace "Mami tsoro nake ji, kice a rufe min idona" Likitan yace
"She will adapt slowly...." wheel chair ya jawo ya ajiye don a maida ta ward dinta
in ji likitan, Shuraim ya dauketa har sannan ta ki yarda ta kara bude idonta, bai
daurata kan wheelchair din ba ya nufi kofar theatre din Mami ta bi bayansa, da yake
abokinsa likita sai da ya fara nuna masa ward din da suke kafin ya kawo sa theater
din direct ward din ya nufa, Mami dai na biye da shi, ya bude kofa ya shiga ya isa
kan gadon ya kwantar da ita a hankali, har sannan taki yarda ta bude idon, har
runtse idon tayi gam, ya saki curtains din ward din gaba daya, ya kuma kashe wuta
haske ya ragu sosai, Mami dai na tsaye tana kallonsa, Wani likita ne ya shigo ward
din ganin ynda Shuraim yyi ma dakin yace "Very good" daga haka ya juya ya fita,
Mami ta xauna gefen Heedayah ta dagota tace "Daughter" a hankali tace "Mami" Mami
tace "Bude idon ki" ta girgixa kai cikin rawar murya tace "Ina jin tsoro" Mami tace
"Baki son ki gan ni?" Kuka ta fara yi tace "I am scared" murya can kasa Mami tace
"Don't be dear, open it slowly" Shuraim dai na tsaye bakin gadon yana kallonsu, a
hankali ta fara kokarin bude idon maimakon ta sauke kan Mami sai ta sauke kan
Shuraim dake kallonta suka yi ido hudu, boye fuskarta tayi jikin Mami ta fashe da
kuka sosai tace "Mami Noo, meye shi din? I saw something" a sanyaye Mami tace
"That's Shuraim" Sake dagowa tayi da sauri ta bude idonta har lkcn kallonta yake
shi ma suka kara hada ido, knowing her condition sai ya sakar mata soft sweet
smile, ta fi second biyar tana kallonsa ko kiftawa bbu sai kuma ta kara boye
fuskarta jikin Mami da sauri, Mami na jin yanda xuciyarta ke bugawa, duk wnn abun
bata kalli Mami ba har sannan, Mami ta kwantar da ita a hankali, Heedayah ta rufe
fuskarta da pillow, har bayan wani lkci bata dago ba balle ta bude ido, Mami xata
dagota Shuraim na kallonta yace "Tayi bacci fa"

Idan Allah ya amince min xan yi night update later, In sha Allah.....

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Kwantar da ita Mami tayi ta mike a sanyaye ta tafi kan kujera ta xauna, Shuraim dai
na ta tsaye kusa da gadon idonsa kan Heedayah, Mami tace "Kayi breakfast ne?" Xai
yi magana aka bude kofar ward din Sudais ya fara shigowa junaid na biye da shi rike
da leda, Sudais ya d'an tsaya xae fiddo wayarsa a aljihu ya haska dakin yace "why
is it dark here...." Kunna switch din Shuraim yyi ya ja blanket din saman gadon ya
rufa Heedayah da shi, da mamaki Sudais ke kallonsa, ya buda ido very amazed yace
"You!!!" Sau daya Junaid ya kalle Shuraim ya nufi Maminsa, ganin hka Sudais ya bi
bayansa ya ajiye ledan breakfast din hannunsa saman table, nan suka gaida Mami, ta
amsa tana tambayarsu night dinsu, Sudais yace "Alhmdllh, ya mai jiki?" Mami tayi
murmushi sosai tace "Alhmdllh, she gained her sight, the surgery was successful
Alhmdllh" Junaid ya juya da sauri yana kallon Heedayah, he couldn't help it but
smile, Sudais wa wara ido yace "Alhamdulillah" a tare suka nufi gadon gun Heedayah,
Mami tace "Yanxun tayi baccin, she needs much rest sbda a tsorace take..." Junaid
ya kalli Mami da sauri yace "Tsoron me kuma?" Mami tace "Don't forget, she is blind
all her life, every image is exactly new to her now, likitan yace sae tayi adapting
a hankali" Junaid ya dinga kallon Heedayah cike da tausayinta, can ya bude blanket
din a hankali yana kallon fuskarta, Sudais ya rungume hannunsa shi ma yana
kallonta, ta gefen ido Shuraim ya dinga kallonsu su biyun, Junaid ya maida mata
bargon ganin bacci take peacefully, xagayowa Shuraim yyi yana kallon Mami yace "Xan
je in dawo" Mami tace "Ohk" daga haka ya nufi kofa, Sudais ya tabe baki har Shuraim
ya fita ward din, Mami na kallon Junaid tace "Ba ku gaisa da shi ba Why?" Junaid
yace "It's not necessary Mami...." Mami ta hade rai tace "Ban gane it's not
necessary ba" ya juya yana kallonta yace "Did he even do as if he noticed us here
Mami" Mami tace "But you met him here ko, Kuma kasan yau ya sauka hanya...." Sudais
yyi murmushi yace "To Mami ni da nayi masa maganan kin ga ya amsa? Ko kuma ya nuna
ya gane ni" Mami tace "Eh I noticed wnn halinsa ne ai koh" Disgustingly Junaid yace
"Mugun hali kenan" Dariya sosai Sudais yyi, Mami ta tabe baki tace "So what's the
gain da ba ku gaisa ba ynxu, kamar wasu yara?" Junaid bai kuma ce ma Mami komai ba
ya ja kujera ya xauna, Sudais yace "Anyway, Junaid that's just Shuraim... haka nan
yake, and am telling you ba da wata manufa yyi hakan ba wllh, he is just different,
totally different, he find it hard to speak at times, but he is lovely being
with...." Junaid yace "But nima ba da wata manufa nayi hakan ba, I was checking on
Heedayah that's why ban ma lura da shi ba ai" Sai kusan karfe sha daya da rabi
Shuraim ya dawo dakin, har lkcn Junaid da Sudais na tare da Mami suna mata hira,
Kana ganin Mami kasan tana cikin farin ciki, kai kace 'yar cikinta ce Heedayah,
Shuraim ya gaidata, Mami tace "But are you sure you've eaten?" Shuraim yace "Na ci"
Kujera ta nuna masa ya xauna yana kallonsu Sudais yace "Sannun ku" Sudais ya
rungume hannunsa daga xaunen da yake yace "Ciwo mu ka ce maka muke?" Junaid dai
danna wayarsa kawai yake bai dago ba balle ya kalli Shuraim, Shuraim bai tanka
Sudais ba, Mami tace "Ya ka baro mutanen gida" yace "Duk lfya lau" Mami tace "Kaka
ta koma gidan ne" yace "Aa" tace "Ohk" Junaid ya mike ya maida wayarsa aljihu ya
nufi kan gado ganin Heedayah na kokarin cire blanket din kan ta, dukawa yyi dai dai
fuskarta yana kallonta, ta bude idonta a hankali bayan ta cire blanket din, ido
hudu suka yi da Junaid, ta fasa wani ihu, Sudais ya mike da sauri yana kallonta shi
ma, Junaid xai kama hannunta ta dinga komawa baya tana ihun, da ta kallesa sai ta
kalli Sudais dake tsaye sai ta kara sautin ihunta, duk sai suka tsaya suna kallonta
gaba daya, shi dai Shuraim na xaune yana kallonsu, Mami ta nufota tace "What
happened daughter, Yaya Junaid ne, with Yaya Sudais, don't shout, they are ur
brothers" Ta dinga girgixa kai tana boye fuskarta cikin rawar murya tace "I am
scareddd" lkci daya ta juya masu baya gaba daya, ta bude idonta a hankali tsoro
karara a fuskarta, hada ido suka yi da Shuraim da ke kallonta don ta direction
dinsa ta juya, ta rufe idonta da sauri ta kara budewa, tayi hakan yyi sau uku, d'an
murmushin da iyakarsa lips dinsa yyi mata, tayi masa kuri da ido without blinking,
Sudais ya xagayo toward direction din Heedayah tana daura ido kansa ta fasa ihu ta
boye fuskarta jikin pillow, kofa junaid ya nufa ya fita ward din, Sudais xai karasa
gun gadon Mami tace "Let her Sudais" Bai ta6a ta ba kawai ya tsaya, Mami ta iso
kusa da ita ta dagota a hankali tace "They are all your brothers Heedayah, Sudais
and Junaid" ta fashe da kuka tace "I'm scared" Sudais ya sauke ajiyar xuciya ya
juya ya fita ward din shi ma. A hankali ta bude fuskarta jin karan kofa, Hada ido
suka kara yi da Shuraim, ta fi second goma tana kallonsa tun daga kansa har
kafansa, can ta juya suka yi ido hudu da Mami, a karo na farko kenan da ta kalli
Mami, shiru tayi tana kallonta a hankali ta kai hannu fuskarta tace "Mami??" Mami
ta sakar mata murmushi, lkci daya hawaye ya cika idonta, ta jawota jikinta ta
rungume ta tace "Yess Daughter" Lamo Heedayah tayi jikinta murya can kasa tana nuna
Shuraim tace "Mami what is that?" Mami tace "He is Shuraim" kara juyowa tayi ta
kallesa sannan ta kalli Mami, Mami ta gyada mata kai assuring her he is the one,
tace "Mami Yaya fa" Mami tace "Ya fita ynxu" Tace "Ya Sudais fa?" Mami tace "Shi ma
ya fita" Kallon gadon da take xaune kai ta dinga yi tace "Mami wannan ne bed?" Mami
tace "Yess" Mami ta nuna mata windown ward din tace "Wancan kuma window" Kallonsa
kawai Heedayah ke yi, Mami ta nuna mata kofa tace "Door" Heedayah ta gyada mata kai
a hankali tana kallon kofar, Shi dai Shuraim kallonsu kawai yake, Sakko da ita Mami
tayi kasa, ta dinga kallon tiles din tana daga kafarta tace "Mami wnn ne floor?"
Mami na murmushi tace "Yess daughter" Mami na lura da yanda take ta kallon jikinta
tun daga kafa har hannunta sai kuma Mami ta ga tayi murmushi, Mami tace "Ki ce
Alhmdllh" A hankali tace "Alhmdllh" Mami ta rungume ta tana kara hamdala a
xuciyarta.... Xaunar da ita Mami tayi saman kujera tace "Let me make you tea now"
Heedayah ta gyada mata kai, daga haka Mami ta tafi gun kayan shayin, Heedayah ta
juya tana kallon Shuraim, d'aga kai yyi ya kalleta shi ma, tayi masa kuri ko
kiftawa babu, ya dauke kansa ya ci gaba da danna wayarsa, har Mami ta kawo mata
shayi kallon Shuraim Heedayah take kamar ta samu television, Mami tayi murmushi ta
kamo hannunta ta sa mata shayin, Heedayah ta maido da dubanta gun Mami tace "Mami
baya magana kaman ke" Mami tace "Yana yi mana, Ya Shuraim ne nace maki" Tace "Noo,
I didn't hear his voice, ba shi bane" sai kuma tayi kasa da murya tace "But ya
Shureen is wicked, this isn't him, wnn bai yi fada ba" Mami tayi dariya tana kallon
Shuraim tace "Talk to her Shuraim" Murmushin kawai yyi shi ma bai dai ce komai ba
ya ci gaba da danna wayarsa, Mami ta xauna tana kallon Heedayah da sai da ta gama
kare ma Cup din da shayin ciki kallo na kusan minti biyu sannan ta kai baki a
hankali kamar me tsoron yin hakan, sai da ta kusa rabi ta cire cup din ta juya tana
kallon Shuraim, har sai da Mami tace "Toh shanye shayin mana" sannan ta dauke kai
ta ci gaba da shan shayin, tana shanyewa kuma Mami ta amshi cup din ta tafi ta
wanke, Heedayah juya ta ci gaba da kallon Shuraim, ya d'an hade rai ya dago ya
kalleta, wani ihu ta fasa tayi baya xata fadi ya mike da sauri ya rike kujeran,
Mami ta fito da sauri tace "What happened?" Heedayah ta boye fuskarta cikin rawan
murya tace "I'm scared" Mami ta dagota ta rungumeta tace "Don't be dear, no one is
harming you" ta hannun Mami ta bude ido a hankali tana lekosa kuma, murmushi ya
sakar mata, ta janye jikinta daga na Mami ta tsaya tana kallonsa da manyan
idanuwanta da suka yi ja, sosai hakan ya ba Mami dariya, Mami tace "Take her out
Shuraim kuyi strolling but don't go far..." Yana son ce ma Mami hasken waje xai
mata yawa amma kuma bai son yin maganan, Mami tace "Or... we shouldn't, tunda
likitocin basu bada umarnin haka ba koh" Shuraim ya gyada mata kai, ta kama hannun
Heedayah ta daurata saman gado, ita fa ta samu TVn ta na farko a duniya wato
shuraim da ya juya sai yaga kallonsa take keenly, Mami ma ta rasa kan wannan kallon
da Heedayah ke masa, mikewa Shuraim yyi daga karshe ya nufi kofa don ya gaji da
kallon, da sauri tace "Mami xai tafi" ya juya ya mata wani shegen kallo ta fasa ihu
a tsorace ya bude kofa yyi wucewarsa. A waya Mami ke nuna ma Heedayah da ta makale
jikinta hoton Abba, Farida, da Junaid.... Da Mami ta tafi sai Heedayah ta sa hannu
ta dawo da hoton, sai ta kalla yyi na kusan minti biyu sannan Mami ta wuce, ana
haka aka bude kofar, Heedayah ta daga kai da sauri, Sudais ne ya shigo, Mami na
nuna mata shi tace "Yaya Sudais, that's him...." Heedayah ta dinga kallonsa har ya
karaso yana mata murmushi yace "Hi...." A hankali tace "Hello" yace "You get my
voice??" ta gyada masa kai tace "Ya Sudais" Ya wara ido yace "Yess, how are you?"
Tace "I'm fine" ta kalli Mami tace "Mami Yaya fa?" Mami ta kalli Sudais tace "Ina
Junaid?" Sudais yace "He told me he will be coming back later, ya fita" Mami tace
"Ina yace maka xai je?" Sudais yace "I have no idea" Heedayah dai sai kallon
Sudais take, ya sakar mata murmushi, ta xaro ido tace "Mami" Mami ta kalli Sudais
sannan ta kalleta tace "He smiled at you, smile back" murmushin ita ma tayi kokarin
yi masa. Har yamma Junaid bai shigo ward din ba, Mami da Sudais ne kadai dakin,
Heedayah ta tambayesa ya fi a kirga, daga karshe Mami ta kirasa, yana dagawa tace
"Where are you?" yace "Hotel" Tace "To ka taho yanxu" daga haka ta katse wayarta,
ba a dau lkci ba Junaid ya shigo ward din, tun da ya shigo Heedayah ke kallonsa, ya
karaso cikin dakin suka gaisa da Sudais ya gaida Mami sannan ya kalli Heedayah, a
hankali tace "Yaya" yace "Ba shi bane" Tace "Toh ai muryarsa
ne na ji" Ya d'an saci kallon Mami ganin kallonsu take yace "Kin san muryarsa ne
kike ihu daxu?" Shiru tayi tana kallonsa, ya karasa kusa da ita ya sakar mata
lallausan murmushi ya xauna gefenta yace "How are you?" Ta kai hannu hancinsa a
hankali tace "I am fine, is that ur nose" Ya wara idanuwansa yace "Noo it's urs" ta
kai hannunta nata tana ta6awa, ya ja mata hancin nata yana murmushi ta mayar masa
da murmushin.... Throughout ranan komai Heedayah ta tambaya Mami bata gajiya da
bata amsa don she's just so curious, she wants to know everything, idan Mami bata
gaya mata ba Sudais xai gaya mata har Magrib, Junaid ne ya kawo masu abinci, wajen
karfe takwas xa su wuce hotel dinsu Mami tace "Wai Shuraim fa" Junaid ya nufi kofa,
Sudais yace "I don't know, ba mamaki ya koma Nigeria ma" Da mamaki Mami ke kallonsa
ya fita yana dariya... Har washegari Mami bata ga Shuraim ba, ta kira Junaid da
sassafe tace ya ba Sudais waya, bayan sun gaisa tace "Ka turo min lambar Shuraim"
Sudais ya amsa mata da toh, cikin few seconds kuma ya tura mata, dialing number
tayi, yana fara ringing aka daga, tace "Where are you..." Yace "Ina kwana" tace
"Lafiya lau, kana Ina ne?" Yace "Ina Abuja" Tace "Abuja?" Yace "Ehh, tafiyar ya xo
min a gaggawa ne" tace "Toh yayi kyau" daga haka ta katse wayarta. Dariya Sudais ya
dinga yi da Mami ta gaya masa Shuraim na Abuja, yace "I told you, ni nasan ba
karamin aikinsa bane, kadan daga abinda xai aikata kenan" Junaid yace "That's
foolishness" Mami dai bata ce komai ba... Haka suka ci gaba da kula da Heedayah da
ta fara sabawa da abubuwa da dama yanxu, likitocin har suka bada izinin a dinga
fita da ita ana xaga clinic din, xuwa ynxu ta daina tsoron jama'ah sai dai fa idan
taga cinkoson jama'ah jikinta ya dingi rawa kenan, bata son crowd, a haka likitocin
suka sanar ma Mami xa su sallamesu nan da kwana uku. A bangaren Salima kuwa, hotel
hotel ta dinga bi tana kwana har ta samu ta harhada kudin komawa Nigeria, sai da a
ranta ta dau kudurin bata kyale Junaid ba....

I'm not feeling well today, ayi manage da wnn plss....

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Mami na xaune office din likita a ranan da aka sallamesu asibiti yana bata
conditions na kula da idanuwan Heedayah idan sun koma gida, do's and don't kawai
yake xayyane mata, sosai Mami ke sauraronsa don ko kadan bata son a samu wani
matsalan, da turanci take tambayarsa ko har kwana Heedayah xata dinga yi da Glasses
din nata da aka bata, ya amsa mata da A'a, amma.... throughout the day the glasses
should be on her eyes ko bandaki xata shiga, nan ya kara sanar ma Mami after wata
shidda xa su dawo for check up yana nan rubuce takardan da aka bata, godiya Mami
tayi masa sosai sannan ta fita office din, dole hotel xa su koma don sai dare
jirgin Nigeria xai tashi, A cikin Tricycle din da xai kai su hotel din Heedayah ta
rufe idonta jikin Mami don duk Inda ta kalla mutane ne in group kuma hakan na
rikitar da ita ba kadan ba ga kuma Haske da yyi mata yawa sosai wanda tun asibiti
hakan ke sa mata ciwon kai, Bayan sun shiga dakin hotel din Heedayah na kallon
Sudais tace "Ya Sudais why are some people black and others White in color??" Mami
dai tayi dariya bata ce komai ba, Sudais ya dawo kusa da ita ya duka yace "The
black are the Africans, and the white may be indians or Americans...." Shiru tayi
tana kallonsa, can ta kalli Mami tace "Is Mami an Indian also?" Junaid dake tsaye
jikin window yana danna waya bai ko kallesu ba, ya d'an yi murmushi amma bai dago
ba still, Mami tayi dariya tana jiran jin me Sudais xai ce mata, Heedayah ta kalli
hannunta tace "And I am also white, does this mean I am an indian?" Sudais ya d'an
juya manyan idonsa yace "Noo Neither Mami nor you are Indians...." With confusion
Heedayah tace "But how, we are white also" Sudais yace "Ohk let me explain to you
better, but ur brain is small to understand my explanation..." Heedayah ta xaro ido
tace "Ohk wait... is yours big?" Dariya Sudais yyi yana kallonta yace "Yess" tace
"shi sa kanka kato ne, nawa karami?" Ya gyada mata kai yana murmushi, tace "To idan
nawa ya kai kmr naka sae ka min explanation din?" Sudais yace "Yess dear" Kofa
Junaid ya nufa, Mami ta bi da sa kallo tace "Where to?" Yace "I will be back soon
Mami, I want to get something" Heedayah tace "Yaya should I accompany you?" Juyawa
yyi yana kallonta bluntly yace "Noo" Ta wani tabe baki ta juya masa idanuwanta tace
"Just pulling ur legs, I am going no where" Bude kofar yyi ya fita, Sudais dai yyi
murmushi kawai, Mami ta kamo hannunta tace "Heedayah yayanki ne fa kike masa rashin
kunya" Heedayah tace "Mami shi ma fa ya min rashin kunyan, daxu da safe he even
pinched me, Sudais yace "Idan kina yi masa haka zae xaneki ne one day, and bbu
ruwana" Heedayah tayi shiru sai kuma tace "Shi ma Mami xata zanesa ae" karfe bakwai
da few minutes jirginsu ya tashi daga india xuwa Nigeria... Ganin ynda Heedayah ke
bin kowa na cikin jirgin da kallo Mami ta jawota jikinta tace "Kiyi baccin ki" tace
"Mami su ma duk gidanmu xa su je wajen Abba?" Mami bata san lkcn da tayi dariya ba
tace "Nooo dear, but we are all going to Nigeria that's our country" Heedayah tace
"Toh Ina xa su je su" Mami tace "Nigeria is a very large County with 36 states ba
kin sani ba??" Heedayah ta gyada mata kai, Mami tace "Toh everyone u are seeing
inside this plane is going to various state, some Kaduna, other kano, and so on"
Heedayah tace "Jirgin ne xai kai mu gida wajen Abba?" Mami tace "Noo mota xa a kawo
airport sai mu shiga a kai mu gida" A Hankali Heedayah tace "Ohk" daga haka tayi
lamo jikin Mami nan da nan bacci ya dauketa, Sudais da Junaid na xaune daga
bayansu, sai da suka sauka Abuja Nigeria da asuba Mami ta tada Heedayah suka sauka
jirgin tana rike da hannunta, sai makalewa take jikin Mami don bata son kowa ma ya
ta6a ta cikin masu saukowa kallon dodo take masu, ta dinga bin ko ina da kallo
bayan sun sauka jirgin tace "Mami babu Light a Nigeria din dama?" junaid ya kalleta
kafin yace komai Mami tace "Noo, asuba ne har yanxu ai, anjima xaki ga haske ko ina
dear" ta kalli Junaid xata yi magana sai kuma tace "Ohh not you, Yaya Sudais a nan
xa mu bar jirgin mu tafi?" Junaid yace "Aa xa a daura maki a kai ne ki kai gida" Ta
kalli Mami tace "Mami kin gansa ko? Nice xan iya daukan jirgin a kai na?" Mami tace
"Aa sai dai shi a daura masa a nasa kan" Heedayah tace "Toh Mami ai shi ma baxai
iya ba, naga kato ne ai jirgin" Sudais ne ya samar masu Taxi cab yana kallon Mami
yace "Train station din xa mu wuce?" Mami tace "No this 4 am, mu tafi gidan sister
na, xuwa biyar da rabi sai mu wuce station din" yace "Ohk" cikin mintuna kadan suka
isa gidan Hajiya Asiya, sosai matar ita ma tayi murnar ganin anyi sa'ar aikin duk
da suna chatting da Mami tun a India Mami ta sanar mata Heedayah ta warke, wanka
kawai suka yi a gidan suka yi breakfast shi ma da kyar don Hajiya Asiya ta damu su
yi, duk suka yi sharp sharp sbda su samu train going to Kaduna da safen, Driver din
Hajiya Asiya ya kai su train station din.... Karfe tara da wani abu suka isa train
station na Kaduna, duk suka sauka train din.... Mami na kallon Sudais yace "Sun
taho daga gidan ne?" Sudais yace "Ehh ya turo min text ya iso" a wajen station din
suka ga motar Shuraim a Parke, Bude motar yayi ya sakko Heedayah ta dinga kallonsa
irin na sanka din nan har ya iso Inda suke, ya gaida Mami, Mami ta amsa, hannu ya
mika ma Sudais sannan junaid da ya dinga danna waya ya ki dagowa har sai da Sudais
ya d'an bugesa, sai a snn ya dago kansa ya amshi hannun Junaid, Heedayah dai sai
binsu take da ido ganin abinda suke yi da hannu, ganin Shuraim xai juya ta mika
nata hannun tace "Ni fa?" Very serious tayi maganan, hakan ya ba Mami dariya sosai
Sudais na tayata, Shi dai Junaid murmushi kawai yyi still pressing his phone, Ko
kallonta Shuraim bai yi ba ya nufi motarsa, a hankali Heedayah tace "Mami me yasa
ni bai min ba?" Mami tace "Maxa ne kawai suke yin haka" Tace "Mami na ta6a ganinsa
ranan nan" Mami tace "That's Shuraim" Da sauri Heedayah ta kalleta tace "Shureen?"
Mami tace "Yes" back seat Mami ta shiga da Heedayah dake ta kallon Shuraim, Sudais
da Junaid suka gama saka kayan a mota, Junaid ya shiga back seat, Sudais ya shiga
gaba, Shuraim ya tada motar suka dau hanyar gida... Bbu me magana cikin motar sai
Heedayah da ta kafe idonta jikin windscreen komai ta gani sai ta tambayi Mami, Mami
kuma ta bata amsa, lkci lkci Shuraim ke kallonta ta madubin gaba, hada idon da suka
yi da Junaid ya sa bai sake kallon Madubin ba, bayan tafiyar kusan minti ashirin
suka iso, gida Mai gadi ya bude gate Shuraim ya shiga da motar, Mami ta kalli
Heedayah da ta kura ma gate ido tace "We are home" Heedayah ta juyo da sauri tace
"Xan ga Abba yanxu?" Mami tace "Yess of course" Bude motar Sudais yyi ya fita,
Junaid ma ya fita sannan ya xaga ya bude ma Mami bangarensu, Mami tace "Sauketa" Da
sauri Heedayah dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu tace "No xan sauka da kai
na" Tana fadin haka ta lallaba a hankali ta sauka tana kallon interlock din gidan,
Mami tayi murmushi ta fito Junaid ya rufe motar, Abba ne ya fito balcony ya sakko
yana kallonsu gaba daya, Mami ta xagayo da Heedayah tana murmushi ta nuna mata Abba
tace "There..." Heedayah ta kalli Mami tace "Abba?" Mami tace "Yes, go to him"
tafiya ta fara ya a hankali, Abba dake murmushi ya bude mata hannunsa, hakan ya sa
ta tafi da gudu, ya rungumeta tace "Abba I can see everything now, I can see you
also" tana magana tana ta6a fuskarsa Abba yace "Alhmdllh daughter, now say Alhmdllh
Ya Allah" Heedayah tace "Alhmdllh Ya Allah" Junaid da Sudais dai na tsaye suna
kallonsu, Abba ya daga kai ya kalli Mami dake tsaye tana kallonsu ita ma, karasawa
wajensu yyi yana rike da hannun Heedayah, Yyi patting shoulder dinsu yana murmushi
yace "Allah yayi maku albarka my boys, I am so proud of you two..." Duk suka amsa
masa da Ameen smiling back at him, Kallon Mami yyi ya nufeta, still smiling yyi
mata side hug, karaf a kan idon Mumy da ta makale jikin window a parlon sama tana
lekosu tun shigowar motan gidan, ji tayi ta kasa tsayuwa ga wani abu da taji ya
soketa a xuciya, bata san lkcn da ta fashe da kuka ba ta sake labulen da sauri,
Abba na kallon Mami softly yace "Welcome back Dear Rahinah, Allah yyi albarka, I
will for ever be grateful to you.... Knowing you is one of the sweetest thing I can
admit to in life, I am so proud of you wife" Mami dai sai murmushi take, tuni
Shuraim yyi wucewarsa ciki, Abba na rike da Heedayah tare da Mami suka wuce cikin
gidan, ko Abba bai fadi ba you can see how happy he is, ita kanta Heedayah lkci
lkci sai ta kalli Abba ta sakar masa murmushi, sai bayan da suka shiga parlor ta
dinga bin parlon da kallo kamar munafuka, Rabi'ah da Khadijah na tsaye duk suna
jiran shigowar Heedayah, Abba ya nuna mata su yace "Ur sisters" a hankali tace "Hi"
ganin yanda Abba ke kallonsu duk suka ce "Hello" Heedayah ta kalli Abba tace "Abba
kaka fa?" Abba yace "Anjima xata dawo in sha Allah" Mami na kallon Abba tace "Let
me go and freshen up barrister" yace "You need to dear, Allah ya huce gajiya, sai
na shigo" Ta amsa da Ameen ta nufi part dinta, Heedayah ta kwace hannunta a na Abba
tace "Mami are you leaving me" Mami ta juyo tace "No dear, stay with Abba a little"
Abba yace "Mu je ki gaida Mumy" Heedayah bata ce komai ba yana rike da hannunta
suka wuce bangaren Mumy. Mumy na bedroom dinta tana waya da Sadiya tana sanar mata
ai sun dawo, ynda take kukan a wayan kai kace mutuwarta aka nuna mata, Sadiya tace
"Toh wai ke meye na kukan, dama ba jiran dawowarsu ake ba ne, ae ke abun farin ciki
ne ma a gare ki da suka dawo yanxu" Cikin kuka tace "Baxa ki gane ba Sadiya dole
inyi kuka, dole inyi kuka, rungumeta fa naga Barrister yyi tana wani murmushin
kissa, ko kunya bbu a gaban yaran gaba daya ya rungumeta wllh" Sadiya tace "Ita
Rahinar?" Mumy tace "Wllh, runguma fa sosai, yaushe rabon ya kama hannuna ni balle
ya rungume ni a kan idon wani, a fa tsakar gida ya rungumeta" Sadiya tace "Bbu
komai ki kwantar da hankalin ki, da ba mu da mafita ne shine xa ki yi kuka, Amma
ga mafita iri iri dai, abu tun yaushe muke baxa idon dawowarsu kuma gashi Allah ya
dawo da su lfya" Jin an bude kofa Mumy tayi saurin cewa "Xan kira ki anjima, an
shigo parlona" Daga haka ta katse wayar tace "Waye?" Jin shiru ta mike tana kara
goge idonta sosai ta fita, Abba ne tsaye yana rike da Heedayah, Mumy ta sake fuska
tace "A'a, mutan India har an iso kenan, toh kun sha kabo, Alhamdulillah, Sannun ku
da dawowa" Heedayah dai sai kallonta take a tsorace jin muryarta, Abba ya sake
hannunta yace "Go and greet her" a hankali Heedayah ta nufi Mumy dake kirkiran
murmushin karfin hali Mumy ta jawota jikinta sosai ta rungumeta tace "Alhamdulillah
ido ya bude, Alhamdulillah mun gode Allah" Murya can kasa Heedayah tace "Good
morning" Mumy ta dago kanta tace "Good morning ya kike, Ina Mamin ta ki?" Heedayah
ta nuna mata hanyar waje, Mumy tace "To maa sha Allah, Allah ya huce gajiya" Abba
yace "Sai ki samu ki tafi kiyi ma Rahinar sannu da xuwa" Mumy tace "A'a ba abinda
xai hana haka ai" Mumy ta xaunar da Heedayah kan kujera tace "Kun yi breakfast
kuwa?" Heedayah ta girgixa mata kai, Mumy tace "To bari a hado maki shayi" ganin
haka Abba ya fita ya bar Heedayah a parlon, Mumy ta bi sa da kallon gefen ido, can
ta kalli Heedayah tace "Kar fa ki fita, Ina xuwa in kawo maki shayi, xa ki ci har
da bredi Koh?" Heedayah ta gyada mata kai, Mumy ta nufi kofa ta bude kafin ta fita
sai da ta sake kallonta tace "Kar fa ki fita, Ina xuwa yanxun nan in kawo maki kin
ji" Heedayah ta kara gyada mata kai, Mumy ta fita da sauri, Mumy na fita da few
minutes aka bude kofar sai ga Shuraim ya shigo, Kallonta ya dinga yi daga Inda take
xaune with surprise, can ya kalli kofar dakin Mumy ya karasa ya leka ciki bai ganta
ba, dawowa yyi ya bude kofar parlon yana kallon Heedayah dake ta bin sa da kallo ya
nuna mata kofar alamar ta fita, Tace "Mami tace min door ne... It's a door" ya wani
daure fuska, da sauri ta dauke kanta, Ya dake yace "Xo ki fita nace...." Mikewa
tayi tsaye da sauri tana kallonsa don ranan ya fara mata magana, kamar munafuka
tace "Tea xa a bani da bread" Ya kara daure fuska yace "Fita na ce" da sauri ta
karasa gun kofar ta bi ta gefensa ta fita tana waigosa, ganin inda xata bi ya bi
bayanta da sauri, ya gwada mata hanya da finger dinsa, part din Mami da ya nuna
mata ta nufa, da tayi tafiya kadan sai ta juya taga yana tsaye yana kallonta, sai
da ta d'an yi nisa sannan ta juyo ta tsaya tana kallonsa ita ma, ya xare mata ido
yace "Baxa ki wuce ba" 6ata fuska tayi ta juya ta nufi kofar shiga parlon Mami
hawaye cike idonta tana isa kofar ta kara juyowa ta tsaya tana kallonsa, sun fi
minti daya a haka yana kallonta tana kallonsa.... Daukar remote da ke kan kujera
yyi, yyi kamar xai jefa mata ta fasa ihu ta durkusa a wajen, da sauri ya juya ya
wuce dakinsa, Mami ta bude kofarta jin muryar Heedayah tana kallonta tace "What
happened?" Kamar xata yi kuka tace "Wannan da kika ce min Shureen ne, I heard his
voice, xai min doka wai" Mami na bin parlon da kallo tace "Ina yake?" Heedayah tace
"Ya gudu" kama hannunta Mami tayi suka shiga ciki, Mumy ta fito kitchen rike da cup
din shayi da bredi da nama a plate ta wuce parlonta, turus ta tsaya ganin bbu kowa
parlon, can ta nufi daki nan ma bbu kowa, ta dake tace "Heedayah?" Nan ma shiru,
Ficewa tayi dakin ta wuce parlon Abba, ta samesa dakinsa, rai bace tace "Kai da ka
bar yarinyar nan a parlona baka san abinda kke yi bne barrister, Wai daga in je in
hado mata kayan kari shine har an shiga an dauketa..." Abba ya dakatar da ita yace
"Aa, ta dai fita, wa xai shiga ya dauketa" Mumy tace "Wllh wllh shiga aka yi aka
dauketa don na jadadda mata kada ta fita tace min toh, wllh dauketa aka yi" Yace
"To wa xai dauketa??" Tace "Oho na sani" yace "To sae ki kai mata can parlon" tace
"Baxan je ba wllh, ikon dai da ake nunawa bani da shi a kanta a ci gaba" daga hka
ta fice daga dakin rai bace.... Jin shiru shiru Mami bata ga junaid da Sudais ba ya
sa ta kira Junaid, nan ya sanar mata wucewa suka yi, fita tayi parlonta ta tafi
dakin masu aiki ta bude tana kiran Sajida, wata mata ce ta mike tace "Aa ni ce, Ina
kwana" Mami tace "Lafiya lau, Ina Sajidar?" Matar tace "Ni ce sabuwar mai aikin
ynxu" Mami tace "Tohhh, to Sannun ki" daga haka ta juya ta wuce xuwa kitchen ta
hada ma Heedayah da ita kanta shayi.

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Da yamma Mami na xaune main parlor da Hajiya Amina da Hajiya Hauwa, sai colleagues
dinta su shidda duk sun xo yi mata sannu da xuwa da gaida Heedayah, drinks da ruwa
ne da snacks iri iri a gabansu sannan ga lafiyayyen jollof da isasshen kaza sai
coslow a gefe, Mumy dai na xaune parlon ita ma sai kirkiran murmushi take, lkci
lkci take jefa nata hirar a hiran da suke, Heedayah na xaune kasa kusa da Mami duk
tana kallonsu hannunta rike da roban Fanta, daya hannunta kuma cup cake, bude kofar
parlon aka yi Kaka ta shigo sakale da daya dayan handbag dinta da xa a iya saka
karamin jariri a ciki, ta sha yafin mayafinta, ko takalmin kafarta bata cire ba ta
shigo parlon, biye da ita a baya Hajiya Zuwaira ce matar Baffan Junaid da kawarta
sai kanwarta Maimuna, Mami na ganin kaka tayi murmushi ta mike tace "Sannun ku da
isowa kaka" A dakile kaka tace "Ehe" Heedayah sai kallon warce taji an kira da kaka
take kamar idanuwanta xa su yi magana, sauran matan parlon duk suka shiga yi ma
Kaka sannu da xuwa ciki har da Mumy, duk da "Ehe" kaka ta amsa su tayi wucewarta
dakinta bayan ta saci kallon Heedayah da ta bi ta da kallo, Mami suka gaisa da su
Hajiya Zuwaira da fara'a tana masu sannu da xuwa, kasancewar parlon is occupied
tace "Bari mu je can parlon kawai" Sai da ta sanar ma bakinta gaba daya cewar tana
xuwa sannan ta kai Hajiya Zuwaira da kawarta da kanwarta parlonta, mikewa Heedayah
tayi da sauri ta bi bayanta, Mumy ta bi ta da wani kallo ta gefen ido, Mami ta ciro
ma bak'in nata ruwa da lemo a fridge ta ajiye masu tace "Tunda ku na gida ne bari
in sallami bakin parlor, abokan aikina ne da matan yayan Barrister, Ina xuwa yanxun
Hajiya" Hajiya Zulaiha tace "Ba damuwa Rahinah, mu kam na gida ne" Mami ta fita
Heedayah ta bi bayanta da sauri duk da kiranta da Hajiya Zuwaira ke yi, Mami ta
kalleta tace "C'mon je ana kiran ki my frnd" a hankali ta juya ta koma cikin parlon
ta nufi gun Hajiya Zuwaira, Mami tayi wucewarta... Mami na dawowa main parlor
Hajiya Hauwa tace "Kinga ki shiga ki gaida Kaka tana iya cewa ai kin ganta kin
shareta, kinsan halin abar tamu...." Dariya Mami tayi tace "Ae kuwa" Mumy tace "Ae
haka ma kawai xata ce" Mami tace "Bari in je in dawo" daga haka ta nufi hanyar
dakin kaka, dakin masu aiki ta fara shiga, tana kallon sabuwar mai aikin me suna
Talatu tace "Don Allah ki debi abinci da su samosa da cake ki kai can parlona akwai
baki guda uku" Talatu ta mike da sauri tace "Toh Hajiya" Mami ta juya ta fita ta
wuce dakin kaka, kaka na share windanta da tsintsiya bayan ta cire duk labulayen
dakin da ma xanin gado Mami ta shigo da sallama, Da fara'a tace "Sannu da isowa
kaka, fatan mun same ku lafiya" Kaka ta ajiye tsintsiyar hannunta tace "Ita
Deedayar bata da labarin ni na haifi Amadu da ya biya kudin gyaran idon nata ne da
har yanxu bata shigo ta gaisheni ba? Kinga Amadu fa bai ta6a sanin yarinyar nan ba
wllh, bbu dangin iya balle na baba, to kuma ya ina mahaifiyarsa baxata xo ta
gaisheni ba sbda idonta ya budu, to ni da nasan haka ne xai faru da nace ma Amadu
ba da yawuna ba idan aka gyara mata idon, ace tun dawowar ku ba ki xaunar da ita
kin sanar mata wacece ni da abinda ya kamata tayi idan ta gan ni ba, kin ga rashin
gaskiyar jama'ah ko? To ni dai ba ruwana, ai ba wani ya haifar min Amadun ba,
kwanana uku ina nakudar sa wllh" Mami da ke ta kallon kaka tace "Toh kiyi hakuri,
kuma Heedayah har yanxu ba wai ta gama sakin jikinta da mutane bane, Kar ki manta
kaka tun da aka haifeta makauniya ce ita, Kinga da girmanta ta fara ganin duk wani
halitta, to banda ynxu da ta fara sakewa ai da ko mutum ta gani ta dingi ihu kenan
tana tsoro" Kaka ta daga hannu tace "Toh ni ina ruwana, ni dai ba ni ce na haifi
wanda ya tsintota yyi silar gyaran idonta ba, Taimakonta Allah Taimakonta Amadu a
duniyar nan, don haka ai ban cancanci raini wajenta ba, baki ga kallon rainin
hankalin da naga tana min ba, ni a gaskiya da na sani da an barta a makancen ma
kawai tayi ta ma mutane ladabi a hakan" Mami bata kuma ce mata komai ba ta juya ta
fita don ranta ya gama baci, Sai bayan da ta fita kaka tace "Wa ya sani ma ko 'yar
ta ce ta makala ma Amadu don kawai ya aureta, mutane dai bbu gaskiya" Mami na
fitowa ta wuce parlonta, Tayi ma su Hajiya Zuwaira sannu sannan tace "Heedayah taso
mu je" Mikewa Heedayah tayi ta bi bayanta suka fita, Mami ta wuce da ita dakin kaka
suna isa kofar ta juyo tana kallonta tace "Idan mun shiga ki xauna a kasa ki
gaisheta, ita ce kaka" Heedayah ta gyada mata kai sannan Mami ta bude kofar suka
shiga dakin, a bakin kofa Heedayah ta xauna tace "Ina wuni" Kaka dake share bangon
dakinta ta juyo ta kalleta ta ajiye tsintsiyar tace "Toh ki gode ma Allah ki gode
ma d'a na Amadu, kuma ni nan nice kaka ni na haifi Amadun da yyi silar gyaran
idonki, ko iyayenki na da rai yau basu da iko a kanki kamar yanda Amadu ke da iko a
kanki amma ya xa ayi in shigo kina xaune rike da goran panta da kenk ki kasa ce min
komai kin ji kowa na min sannu da xuwa kaka" Heedayah dai sai kallon kaka take, duk
Inda ta bi da hannu sai ta kalla kai kace TV ta samu, Kaka ta kalli Mami dake jira
ta fitar da Heedayah daga dakin tace "Kin gani ko Rakiya, hararata fa take" Mami
tace "Wani harara kuma kaka, ance maki yarinyar har yanxu bata gama sabawa da komai
ba, yaushe ma ta fara ganin ki idan ba yanxu ba, sai fa a hankali xata saki jiki da
kowa ta dawo kamar ko wani mutum, ynxu haka da xa ki kawo mata mage ko tsuntsu bata
san su ba bata ta6a ganinsu ba, sae dai sunansa, to kinga kuwa dole ayi ma mutum
uxuri, ranan da idonta ya bude tsoron kowa ta dinga yi, kuna hada ido xata fasa
ihu, sbda duk rayuwarta a duhu yake banda ynxu da Allah ya yaye mata" Kaka tace
"Haka abun yake?" Mami ta daga Heedayah dake ta xaune tana kallon kaka tace "Sai
hakuri kaka, ni xan tafi in ji da mutane" Daga haka ta fita da Heedayah dake waigo
kaka... Fitowa kaka tayi tana kallon mutan parlon ganin Mumy tace "Xo Maryam" Mumy
ta mike ganin kaka ta nufi nata bangaren ta bi bayanta har suka shige parlon Mumy,
Kaka ta xauna saman kujera ta fashe da kuka tace "Rakiya ce ta shigo ta min wankin
babban bargo bbu abinda ta mance bata gaya min ba, a takaice dai a baibai kirana
tayi da fitinanniya, ni dai ina tsaye bance mata uffan ba ta ja hannun makauniyar
da Amadu ya kashe kudi ya warkar suka fita" tana kai wa nan ta fashe da matsanancin
kuka, Mumy tace "Ikon Allah, to ke me kika yi xata maki haka daga dawowarki" kaka
tace "Wllh Maryam daga nace mata Deedayah lafiya bata shigo ta gaisheni ba naga
kamar ma hararata take da na shigo ko bata gane ni bane ta min irin wnn kallon, Kar
ki d'a d'a kar ki raga, Rakiya ta hau ni da bala'i wai ni bana yi ma mutane uxuri,
ai Deedayah a duhu take ynxu Allah ya fito da ita Amadu ya fito da ita haske, Kuma
ai dole ta ji tsorona tunda ita ma ta ji tsoronta da suke asibiti, to idan Rakiya
na da hankali da tunani sai ta hada kanta da ni? Ni fa na haifi Wanda yayi silar
warkewar Deedayan" Mumy ta hade rai tace "Gaskiya wnn raini ta maki, bata kyauta
ba, gani take ta fi kowa Iko da yarinyar a gidan nan daxu fa daga Barrister ya
kawota parlona na fita kitchen hada mata shayi matar nan ta shigo ta dauke ta" kaka
tace "To kuwa ta ci kanta, Kuma sai na sa an karbe Deedayan hannunta in ga ta
tsiya, idan ma Amadu baxai bani ita ba ke ya baki ki rike, abinda ma xai faru kenan
wllh wllh, a ina take da iko da yarinya bayan ita ma makalewa tayi aka aurota
dalilin yarinyar, da ba don yarinyar ba mu muka san wata Rakiya" Mumy tace "Ae
shine, ni wllh a bani ita dama lkcn can shaidan ne ya shiga xuciyata ya hanani
amsar ta amma wllh tllh ynxu xuciyata daya xan amsheta in riketa kmr yanda xan rike
d'an cikina, abinda yarinyar har ta fara sabawa da ni da suka dawo har ta kusa awa
biyu a parlona" Kaka tace "Toh kin ga dai, bari Amadun ya dawo shi ma gantalalle,
xan ji ko maganan Rakiya xai dauka ko tawa" Mumy tace "Atoh dai" mikewa kaka tayi
ta fita parlon, Mumy tayi wani murmushi ta xauna tana kara naxarin maganganun Kaka.
Kafin Magrib duk bakin gidan suka watse har ma da makota da suka shigo duk da basu
wani san Mami ba sai Mumy, suka yi mata sannu da xuwa suna ma Heedayah barka suka
fita, Mami da kanta ta taimaka ma Talatu gyaran gidan don kai kace wani karamin
walima aka yi a gidan, Mumy kuwa ta shige bangarenta da yaranta ta kulle kofa don
ma kar su dauke ko da cup, Duk inda Mami tayi Heedayah na makale da ita, Mami har
ta gaji da ce mata taje ta xauna ta kyaleta, Mami na kitchen suna gyaran kitchen
din aka yi Magrib, sai da Mami ta tabbatar ko ina ya dawo fess ta fito parlor tare
da Heedayah ta bar talatu ta karasa wanke wanken, Kaka ce ta fito dakinta, Mami
tace "Sannu kaka, abincin ya ishe ku ai koh?" Can ciki kaka ta amsa tace "Ya
Isa..." Daga haka ta nufi bangaren Mumy tana rike da wayarta tana cewa "Ina Maryam
ta kira min Junaidu shiru ni ban gansa ba, ko a indiyar suka baro sa" Mami dai bata
ce mata komai ba har ta shiga bangaren Mumy, Mami ta wuce nata bangaren da
Heedayah. Bayan isha Abba na parlonsa tare da Shuraim sai su Rabi'ah da Khadijah,
Mami ta shigo ciki da sallama holding Heedayah's hand, Gun Abba Heedayah ta nufa ta
xauna tace "Abba sannu da dawowa" Yyi murmushi yace "Yauwa daughter, hope kinyi
bacci da yawa daxu" ta gyada masa kai, Abba ya maida dubansa kan su Khadijah on a
serious note yace "As I was saying, today should be the last day da yayanku xai
maku fada ko ya doke ku ku je ku gaya ma Mamarku" Rabi'ah tace "Abba ba mu muka
gaya mata ba fa, she just came in" Abba yace "Whatever.... Na gaya maku ni dai...."
Abba ya kalli Shuraim yace "And you Shuraim duk ranan da suka kara fashin makaranta
you do what ever you wish to them, don't think twice before punishing them" ya
girgixa kai kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Abba it will be good idan Mumy
tayi hakan, ni babu ruwana da lamarinsu a gidan nan, beside she said I should take
my hands off their issues" Abba yace "And I am instructing you to keep on
disciplining them, ko ban isa?" Bai
kuma cewa komai ba, Mami na kallonsu tace "Ku kuma sai kace wasu yara xuwa
islamiyyar ne ku ke fashi, amma ai ban ga kuna fashin boko ba" Basu ce mata komai
ba, tace "That's bad, you two should stop that" Abba yace "Nan da one week Heedayah
will join them also, kafin sati dayan an nuna mata abubuwan da ya kamata ta sani
facially since ta san karatu gani ne kawai bata ta6a yi ba" Mami tace "Allah ya kai
mu" Bude kofar parlon aka yi, kaka ta shigo, Ko gaisuwan da ake mata bata amsa ba
tace "Amadu baka san na dawo bane baka shigo ba? Tun fa yamma nake gidan nan" Abba
yace "Aa dama Ina kokarin shigowa ne, Ina son in gama da su" tace "To ai dai nice
dolen ka ba su ba koh?" Wani kallo Shuraim ya watsa mata, Abba dai bai ce komai ba,
ta nemi waje ta xauna, Mami tace "Sannu kaka" kaka tace "Ehe" Abba yace "Ina yini
Baaba" tace "Lafiya lau, Ina son magana da kai ne Amadu" Abba ya kalli su Rabi'ah
yace "To na gama da ku" mikewa Mami tayi Heedayah na ganin haka ita ma ta tashi
daga kusa da Abba, Kaka tace "Aa Ina kuma xa ki Rakiya koma ki xauna" Rabi'ah da
Khadijah xa su fita kaka tace "Kai ku kira min Maryam idan kun fita" Abba dai sai
kallon kaka yake, can yace "Lafiya dai ko kaka?" Tace "Eh lafiya lau" Bai kuma cewa
komai ba sai ga Mumy ta shigo da sallama, ta nemi waje ta xauna tayi ma kaka sannu
sannan tace "Ga ni kaka" Kaka tace "Toh Amadu shawara na xo baka idan kana son
xaman lafiya a gidan ka...." Abba yace "Shawarar me fa?" Kaka tace "To wai me yasa
baxa ayi ma Maryam kara ba a bar mata Deedayah wajenta tunda dai ta nutsu tayi
hankali, ita Rakiya ba xama take ba aiki safe, rana, yamma, Ina jin har dare ma
wani lkcn, to ni kuma a ynda nake ganin wnn Deedayar fitsararriya ce naga alama,
don daxu bata san ina lura da ita ba ta harareni, kaga kuwa idan nace ta xauna
wajena idan Rakiya ta fita kasuwancinta ai xagi na yarinyar xata dinga yi wataran
in shiga uku, jikokina basu ta6a xagina ba ita ta xageni...." Da mamaki Abba ke
kallonta, Mami dai bata ce komai ba kuma bata kalli direction dinsu ba, kaka ta ci
gaba tace "Tunda dai ita Maryam xaman kashe xani take a gida bbu aikin fari balle
na baki ba gwara a bar yarinyar gun ta ba sbda tarbiya, ni dai tun ba aje ko ina ba
naga ta rainani balle ace ta xauna gu na" Mumy tace "To ai bbu komai ko ma gun wa
ta xauna kaka, in ma gu na in ma gun Rahinar..." Kaka tace "Oh oh ai Rakiya aiki
take fita kullum, ke dai me xaman banxa ya kamata a baki ki sa ido kan lamarin ta
don naga yarinyar na bukatar sa ido, sakakkiya ce, ta xata a duhu take har ynxu"
Shuraim dake sauraron kaka yace "Xai fi idan aka kai ta boarding a can xa a koya
mata ladabi, xa kuma ta gane cewar ba a duhu take ba yanxu" Da sauri Mumy ta juya
ta kallesa, Abba yace "Ehh in sha Allah boarding xata fara kamar yanda Shuraim
yace" Kaka tace "Meye kuma boding?" Shuraim na kallonta yace "Makarantar kwana"
Kaka tace "Amma kai axxalumi ne Shureen, me Deedayar ta tsare maka a gidan da kake
son a kai ta makarantar kwana, Kai da aka ta6a kai ka kana yaro ka xauna?? Ba
gudowa ka yi ba, to meye kuma xaka ce a kai marainiya??" Mumy tace "Toh makarantar
kwanan da ake kwashe yara ma, wnn ae gurguwar shawara ce" Shuraim yace "Ae ba na
gwamnati xa a kai ta ba" Kaka tace "Ni dai ba ruwana da muguntar ka na fulani, me
xa mu ce ma Allah idan aka kwamushe 'yar mutane" Abba yace "Makarantar da Farida
take ynxu xa a sa ta in sha Allah, boarding ce me kyau"

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Kaka tace "Aa to ni tsorona kada a sace ta ne Amadu mu shiga uku" Abba yace "Aa
lafiya lau, bbu wata matsala in sha Allah" Mikewa Shuraim yyi ya nufi kofa kansa a
kasa, Mumy ta bi sa da wani irin kallo xuciyarta na tafarfasa, Mami na lura da
kallon da uwartasa ke masa har ya fita parlon, Abba ya dau wayarsa dake ring ya
mike yace "Bari in amsa kira in dawo Baaba" mikewa kaka tayi tace "Aa to ni kuma me
xan tsaya in maka, dama shawara ce kawai na kawo, amma tunda bafillatanin d'an ka
yace a kai ta makarantar kwana kuma ka amince ai shi kenan, amma a gaskiya idan
wani abu ya sami yarinyar nan baxan yafe maka ba baxan yafe ma Shuraim ba, don da
kai ka haifeta baxa ka yi mata sha'awar xuwa makaranta kwana ba, me yasa baka kai
'ya yan cikin ka ba sai ita?? Shi dai rikon amana dama da wahala take sai wanda
Allah ya ba..." bata jira cewarsa ba ta fice daga parlon, Mikewa Mami tayi ta nufi
kofa Abba ya bi ta da ido har ta fita, Mumy ma ta mike ta fice daga parlon bacin
ranta ya kasa boyuwa gaba daya, dakin Shuraim ta wuce direct ta samesa ya shimfida
darduma ya dauko qur'ani ya xauna, cikin daga murya tace "Aliyu a kan uban me yasa
kace a kai yarinyar makarantar boarding?" Shuraim dake kallonta yace "Aa, naga
kamar ba wani son xamanta gidan ake ba...." Tayi masa wani tsawa tace "Uban waye
yace maka baya son xamanta gidan?? Kai da wa ku ka yi haka?" Yace "No naji kaka ta
ce ta fara rainata, so it's better we shouldn't let that go far..." A fusace Mumy
tace "Toh kai Ina ruwanka da xancen da ka tsoma baki? Dangi uwa ko ta uba? Meye
hadin ka da ita da har xaka bada shawara kan lamarin ta iyye? Meye damuwar ka da
ita nace?" Yana bude qur'anin gabansa a hankali yace "Nima din ban fiye son ganinta
a gidan bane shi yasa na kawo nawa shawarar for my own good" Mumy ta jefa masa wani
shegen kallo tace "Sau da nawa da nawa kake xaman gidan idan ba gulma da munafurci
ba Aliyu?? Sati da lahadin da kake dawowa yi a gidan ne xaka wani ce kai ma ba
ganinta kke son yi ba? Uban ma me ta tsare maka tukun? To ynda ka kawo shawarar a
kai ta makarantar kwana sai ka koma kace a sa ta a day, in har kana son wanyewa
lafiya...." Da mamaki yake kallon Mumy yace "Toh Mumy ke kuwa meye na ki idan an
kai ta makarantar kwana? Naga kema ba wani son xamanta kike a gidan ba fa, so it's
better she should stay away from this house completely, hankalin kowa xai fi
kwanciya, ni na xata ma xaki fi kowa murna da shawarar da na bada, I see no reason
da xa ki daga hankalin ki don ance xa a kai ta boarding, sai dai idan da akwai wani
abun daban..." Mumy da ta bude baki tana kallonsa tayi shiru ta kasa cewa komai da
farko, can ta dake tace "Akwai wani abun kamar me, ban fahimta ba?" yace "No nima
ban sani ba, kawai dai nayi tunanin haka ne" Ta hadiye abu da kyar tace "To bari in
fito maka a mutum yanxun tunda ba tsoron ka nake ba Aliyu, ban ga dalilin da xa a
kai yar tsintuwa tsadadden makarantar kwana da ya fi makarantar da 'ya yan masu
gida ke xuwa ba, baxan laminta da hakan ba" wani murmushi Shuraim yyi kamar baxai
ce komai ba sai kuma yace "But ke kika ce baki da ra'ayin a kai su Khadijah
makarantar kwana lkcn da na kawo ma Abba shawaran haka few years back, amma in har
yanxu kinga kina son su je, ni xan yi ma Abba magana baxai ki kai su ba su ma"
Tsawa Mumy tayi masa tace "Wai ban gane alkiblar ka ba Aliyu, kare yar tsintuwar
kake yi kke challenging dina ko kuma shawara da ban bukata daga gareka ba kke
bani?" Ya girgixa kai yace "Aa ko daya" Tana nuna sa on a serious note tace "Toh
tun wuri idan ba haduwa kake son yi da fushina da bala'i ba duk wani abu da ya
shafi lamarin yar tsintuwar nan kada ka sake sa baki, nace kar ka sake, bbu ruwanka
da duk wani lamari da ya dangance ta ko da kuwa Ubanka ya tambayi opinion dinka,
just remain mute" A hankali yace "What if i am also trying to find a way out for my
self, as in.... May be I am not comfortable living in the same house with her also,
Nima ina neman mafita...." Mumy tace "Toh sai ka tsiri cewa a kai ta makaranta me
tsada, Ina aka kai makarantun gwamnati da xaka kira Turkish??" Yace "Sbda hakan
kadai xai ba ma Abba karfin gwiwar kai ta, idan da na gwamnati nace a kai ta Abba
baxai kai ta ba" Mumy tace "Toh ni ba ruwana da duk wnn, ni kawai ka san ynda kayi
ka sa a fasa ma kai ta boarding din gaba daya" Yace "Toh" tace "Toh me??" Yace "Toh
in sha Allah" Tace "I am serious Aliyu kada ka raina min hankali" yace "Ehh xan
kara yi ma Abba magana in sha Allah" Juyawa tayi ta nufi kofa ya bi ta da kallo har
xata fita ta juyo tace "Toh yau litinin me ya hanaka komawa Zarian ma?" Yace "Sai
Wednesday in sha Allah" Mumy tace "Ba dai degree kake ba Masters ne, idan xaka
tsaida hankalin ka gu daya ka tsaya kayi karatu tsakani da Allah ka tsayar, ni ban
ma ga amfanin weekend da kke dawowa ba, Sudais idan ya tafi ba sai bayan watanni me
yawa yake dawowa ba, kai kuwa kamar wanda ake mintsili ko kuma wanda yyi wani ajiya
a gida yana dawowa dubawa a kai a kai" tana kai wa nan ta fita ta kulle kofar,
mayar da dubansa yyi saman qur'anin gabansa ya d'an yi murmushi cikin cool voice
dinsa ya fara karatu. Washegari da safe Mami na kitchen tare da Heedayah tana gwada
mata yanda xata dinga hada shayi da kanta, A hankali Heedayah ke diban madaran
kamar tana tsoronsa har wani rawa hannunta yake yi sai ta xuba a cup, Mami tace
"Look, ki nutsu... Ko me xaki yi ki dinga yi gently don't panick, now fetch the
Milo also..." Heedayah ta kai cokalin cikin Milo din ta debo, yamutsa fuska tayi
tace "Mami me yasa kalan shi haka? And..." Mami ta dakatar da ita tace "Deba nace
ki na batan min lkci xan tafi in shirya" Sake debo milon tayi ta xuba a cup, Mami
tace "Sugar kuma cube uku xaki dinga sawa" Heedayah ta kirga cube din sugar din ta
xuba a cup din, Mami bata bari ta dau flask din da kanta ba don a cike yake, ta
xuba mata ruwan xafin cikin cup din dake dauke da kayan shayin, Heedayah sai kallon
tiririn dake tashi take ko kiftawa bbu, Mami ta dau bottle water ta karasa cike cup
din tace "Idan baki son yyi maki xafi sosai sai ki kara ruwan sha a ciki" Mami ta
rufe gwangwanayen madaran ta ajiye su gefe da sugar, daga kai Heedayah tayi suka yi
ido hudu da Shuraim da ya bude kofar kitchen din, Mami ma ta juya, sauke kansa yyi
yace "Ina kwana" Mami tace "Lafiya lau" ya juya xai fita Mami tace "We are not
stopping you from doing what u came to do" Ya d'an tsaya kamar me contemplating ya
fita ko ya shiga kitchen din, can dai ya shiga ya tafi gun da mug suke ajiye,
Heedayah ta bi sa da kallo, ya dau daya ya dawo xuwa gun flask, a hankali Heedayah
tace "Mami shima shayin xai yi ya sha?" Mami tace "Ina ruwanki??" Bin bayan Mami
Heedayah tayi ganin xata fita kitchen din da cup din shayin, sai da suka isa kofa
ta juya tana kallon Shuraim da ya bi ta da ido shi ma, hade rai tayi ta murguda
masa baki har da juya manyan idanuwanta, sai kuma ta fita kitchen din da sauri tana
bin bayan Mami. Mami na gama shiryawa, Ta tabbatar Heedayah ma ta gama shiryawa
suka fito main parlor a tare ta kulle kofarta, Shuraim ne xaune parlon yana kallon
wrestling, Heedayah na kallon Tvn tace "Mami me yasa basu sa kaya ba kamar mu, nima
xan iya tsayawa haka??" Mami tace "Ehh tunda baki da hankali" Daga haka ta wuce
dakin kaka, Heedayah na biye da ita kamar xata yi kuka, waigo Shuraim tayi ta turo
baki ganin yana kallonta ta shiga dakin kaka, bayan Mami sun gaisa da kaka tace
"Kaka xan tafi gun gidan Baffansu Junaid" Kaka tace "Au haba, can xa ki yini kenan
yau?" Mami tace "In sha Allah" Kaka na kallon Heedayah kafin ta ce komai Mami tace
"Go down now and greet her" Heedayah ta durkusa kasa tace "Ina yini kaka" Kaka tace
"Toh mu dai ba mu yini ba tukun, da safiyar Allah kice Ina yini?" Mami ta dago
Heedayah tace "Toh bari mu je kaka" Kaka tace "Au tare xa ku?" Mami tace "Ehh tare
xa mu tafi" Kaka tace "To Amadun ya sani kuwa, don naga bai fiye son ana fita da
ita ba" Mami tace "Ya sani" Kaka tace "Toh ki dai kula da ita, ita kuma Hajiya
Zuwaira kice Ina gaisheta, Allah yayi mata albarka, mata me mutunci, har na bar
gidan girmama ni take ke kyace ni na haifeta, kayana kuwa kullum sai ta sa masu
aiki sun wake sun goge min, to bata fiye min wasu ba ma ni, jira in dibar maki
kaikayi koma kan mashekiya ki kai mata, kuma kice nace Allah ya mata albarka" Tuni
Mami ta fita dakin bayan kaka ta kulle mata iccen hayaki a leda ta amsa, Heedayah
dai sai waigo kaka take, kaka tace "Ni dai aniyar ki ta biki, ban gane kan kallon
nan ba..." Suna shigowa main parlor Mami ta nufi kofar fita, Shuraim dake xaune har
sannan yana kallon wrestling ganin sun hada ido da Mami yace "Allah ya tsare" tace
"Ameen" Heedayah bata fasa waigo sa ba har suka isa kofar, ya dau wayarsa yyi kamar
xai jefa mata ta fasa ihu ta rike Mami, tuni ya ajiye hannunsa ya maida dubansa kan
TV yana kallo attentively, ko juyowa Mami bata yi ba suka fita parlon, Heedayah ta
murguda masa baki kafin ta daina ganinsa. A cikin gidan Alhaji Imran Mami tayi
parking suka shiga ciki da Heedayah, ta tadda Hajiya Zuwaira da Mai aikinta a
parlor, bayan sun gaisa Hajiya Zuwaira tace "Baffa na parlon sa ku je ku gaisa..."
Mami tace "Ohk, ku kadai gida yan makaranta na can makaranta" Hajiya Zuwaira tace
"Ae kam suna makaranta, jiya Junaid ya je masu visiting gaba daya" Hajiya Zuwaira
ta bi Heedayah da kallo don sosai yarinyar ke mata kyau, komai nata burgeta yake
bari hancinta da d'an karamin bakinta, idonta kuwa har lkcn basu koma farare ba,
Mami ta wuce sama xuwa parlon Baffa, bata fi minti goma sha biyar bs parlon nasa ba
bayan sun gaisa ta fito tare da Heedayah, Bedroom din Junaid ta bude, ta gansa
kwance yyi rub da ciki yana bacci, Heedayah ta wara manyan idonta ta cikin glasses
dinta tace "Mami Yaya" Zame hannunta tayi a na Mami ta shiga dakin da sauri ta hau
saman gadon ta xauna dab da fuskarsa a hankali tace "Yaya" Jin bai ce komai ba ta
kai hannu dogon hancinsa ta ja, a hankali ya bude lumsassun idonsa, ya sake rufe
idon murya can kasa yace
"Cutie" Washe masa hakoranta tayi tace "Me kake yi?" Bai bude idon ba har sannan
yace "Bacci" tace "Nima xan yii?" Bata jira cewarsa ba ta kwanta yanda ya kwanta
kusa da shi tana facing dinsa, bude ido yyi, yyi murmushi har dimple dinsa ya nuna,
ta kai finger dinta wajen ita ma tana murmushin, Ta mike xaune tana kallon Mami
tace "Mami ni me yasa bani da irin nasa" Kumatunta ta nuna ma Mami nufinta me yasa
bata da dimples, juyawa Junaid yyi da sauri ganin Mami ya mike xaune yace "Mami"
Mami tace "Karfe goma saura you are still on bed" yace "Aa ban jima da shigowa ba,
Ina kwana" Mami tace "Lafiya lau" kallon Heedayah tayi tace "To sakko mu tafi
parlor" Tace "Aa Mami xan tsaya da Yaya plss" Mami tace "Ki tsaya kiyi masa me,
sakko mu wuce my frnd" Sauka tayi daga kan gadon kamar xata yi kuka ta nufi kofa
Junaid ya bi ta da kallo har suka fita, Bangaren Hajiya Zuwaira Mami ta shiga, ta
tadda har Hajiya Zuwaira ta sa masu aiki sun hada mata kayan kari a parlonta, Mami
tace "Ikon Allah, we just breakfasted before leaving home Hajiya" Hajiya Zuwaira
tace "Sai ku kara ai" Murmushi kawai Mami tayi ta xauna, Heedayah ta xauna kasa
kamar yanda Mami ta nuna mata ta dinga yi a ko ina, Hajiya Zuwaira ta hada mata
shayi ta mika mata, Heedayah ta kalli Mami tace "Mami ai na sha tea" Mami tace "To
ke kin ji, she's full" Hajiya Zuwaira tace "Toh ai shkkn, ya kaka fa" Mami tace
"Tana can" Hajiya Zuwaira tayi murmushi tace "Uhn kaka sai hakuri.... ga dai dadin
xama ga kuma akasin haka" Mami ta girgixa kai tace "Kwanan ta nawa nan?" Hajiya
Zuwaira tayi dariya sosai tace "Ranan da kuka koma ranan ta sa a maida ta gida"
Mami tace "Bata dai baki wani matsala ba ko?" Hajiya Zuwaira tace "Toh ai duk Inda
tsoho yake dama sai anyi hakuri da shi balle tsoho irin kaka, har da rikicin tsufa,
ni fa har ta bar gidan nan bana gane gabas dinta balle yamma, ita dai ga ta Nan
dai" A hankali Heedayah ta sulale ta fice daga dakin ba tare da ta bari sun lura
ba, ta bi hanyar da suka bi xuwa dakin Junaid, bude kofar tayi ta leka ciki, xaune
ta gansa gefen gado yana danna wayarsa, ta washe masa hakora ta shiga ciki tace
"Yaya" Daga kai yyi yana kallonta har ta iso ta xauna kusa da shi tana kallon
abinda yake yi a waya, yyi kasa da murya yace "Wa yace ki shigo dakina?" Tace "Ni
ce na shigo da kaina, I want to be with you" Kallon bakinta yake, ta wara masa ido
tace "Yaya yaushe xan ga Farida?" Ya dauke idonsa daga lips dinta yace "Ki tambayi
Mami mana" Tace "Ce min xata yi bata sani ba, Yaya me yasa sai Shureen ya dinga min
haka...." Wayarsa ta amsa a hannunsa ta gwada yanda Shuraim ke mata ta jefar da
wayar xuwa bakin kofa, xaro ido yyi yana kallon wayar tasa ya mike da sauri yace
"Kee wayana kika wurgar haka?" Tace "Aa haka Shureen ke min" Ya tafi ya dauko wayar
yana duba screen din da ya fashe ya dawo ya hade rai yace "Sai nace ki gwada min da
wayata?" tace "Toh nima idan ya min haka wayarsa xai fashe haka kenan?" Junaid ya
xauna kusa da ita yana kallonta yace "Me yasa yake maki haka" ta bude hannu tace
"Ban sani ba, sai ya dinga min haka kuma" kallon yanda ta xaro idonta Junaid ke yi,
yace "Haka yake maki?" Ta gyada masa kai, Yace "Toh a ina kike haduwa da shi?" Ta
gyara xama tace "A parlor ko a kitchen idan Mami xata bani shayi, sai ya min
haka...." Da ido ta dinga bin dakin da kallo alamar haka yake bin ta da kallo,
Junaid ya d'an tabe baki yace "Ki gaya ma Abba" Tace "Toh" bude kofar dakin aka yi
duk suka juya da sauri, Mami ta hade rai tace "Wa yace ki shigo nan din" Heedayah
ta sauka saman gadon da sauri tana nuna Junaid tace "Shi ne" Junaid ya xaro ido
yace "Ni?" Tace "Eh" Mami tayi mata alamar da ta xo ta fita, ba musu ta nufi kofar
ta fita kafin Mami ta rufe kofar Heedayah ta daga masa hannu suka wuce. Sai kusan
yamma Mami ta bar gidan Baffa, tun da suka hau titi xuwa gida Heedayah ke ce mata
Mami bamu ga Yaya ba muka tafi, Mami tace "Ai bai dawo ba, gobe xai xo" kamar xata
yi kuka tace "Toh" karfe shidda saura Mami tayi parking a compound, Sai da ta sauka
motar sannan Heedayah ta sauka, A balcony suka tadda Shuraim xaune yana operating
laptop, Ya gaida Mami ta amsa ta shiga ciki, Heedayah ta bi sa da kallo kafin ta
shiga ciki ya fixgota yace "Kallon me kike min?" A tsorace tace "Aa" ya daure fuska
yace "Me yasa kike kallona nace??" Tace "Kai ma naga ai kana kallona da idonka"
hada ido suka yi da Mami ya saketa ta nufi kofa da sauri ta juyo ta wani juya masa
ido ta shige cikin parlon Mami ta rufe kofar.... Bayan isha Shuraim na parlon
Abbansa kasancewar ya kirasa a waya yana neman sa, Abba ya gama abinda yake, sannan
yana kallon Shuraim yace "Shuraim I am worried at sending Heedayah to boarding
school as you suggested because, Ina son ta samu ilimin addini sosai, ba boko kawai
ba, shi yasa ka ga then banyi supporting xuwansu Rabi'ah boarding din ba, karatun
addini nake dubawa" Shuraim ya d'an yi shiru da farko, sai kuma yace "Abba a
situation da ake ciki ynxu, boarding din is the best" Abba yace "Koh, then what
about islamiyya?" Shuraim yace "Idan sun yi hutu sae ta dinga xuwa" Abba yace "Toh
shkkn, but ajin da xa a sa ta fa?" Yace "Jss2.. or 1..." Bude kofar parlon aka yi
Mumy ta shigo, Abba ya daga kai yana kallonta, mikewa Shuraim yyi yace "Sai anjima
Abba" Abba yace "Alright" Mumy ta bi sa da kallon gefen ido har ya fita. Bayan
sllhn asuba Shuraim ya shiga gaida Abbansa, bayan sun gaisa Abba yace "Jiya mun yi
magana da Barrister tace min su Farida na kan yin third term exams ne ynxu.... So
ynxu sae anyi hutu an koma za ayi enrolling Heedayah, but before then I will get a
mu'allim for her da xai dinga mata karatun qur'ani da sauran abubuwan da ya
kamata..." Shuraim yace "Mu'allima instead" Abba yace "Really?" Shuraim bai ce
komai ba, Abba yace "To bbu damuwa, when are you going to Zaria?" Yace "Tomorrow"
Abba yace "Allah ya kai mu" mikewa yyi ya ma Abba sallama ya fita parlon. Karfe sha
daya na safe, Heedayah ta fito parlon Mami rike da cup din shayi da ta sha xata kai
kitchen, Shuraim na kwance 3 seater yana kallon wani action movie da ake yi, Ta
gefen ido ya bi ta da kallo, ita kuwa sai kallon dogon kafarsa take, yana lura da
ita, idan ta kalli nasa sae ta kalli nata, bude kofar parlon aka yi ta daga kai
Junaid ya shigo parlon da sallama, ajiye cup din hannunta tayi a kasa ta tafi da
sauri ta rungumesa tace "Yaya ranan nan ban ganka ba muka wuce" Junaid na kallon
kayan jikinta yace "Me yasa kika fito da kayan nan?" Ta kalli kayan tace "Mami tace
in sa" Tuni Shuraim ya lumshe ido kmr me bacci, Junaid na rike da hannunta suka
wuce parlon Mami, Junaid na kallon Mami yace "Mami kayan nan da ta sa ina ga kamar
bai yi ba, she shouldn't be wearing this out" Mami ta kalli wando da rigan dake
jikin Heedayah tace "Meye rashin yin sa?" Bai ce komai ba, Mami tace "Hijab xan sa
mata ta dinga yawo a gidan ko jallabiya?" Nan ma dai bai ce komai ba, Mami ta masa
wani kallo ta ci gaba da abinda take yi, ya xauna ya gaisheta a hankali, ta amsa
tace "To sai ka siyo mata jallabiyoyi ta dinga yawo da su" shi dai bai ce komai ba,
can ya mike yace bari in je in gaida kaka, Tace "Ohk" fita yyi Heedayah ta bi sa da
sauri, Bai tadda Shuraim a parlon ba kuma, ya shiga parlon kaka da sallama, hada
kayanta ya sameta tana yi a katon akwatin ta, da mamaki yace "Ina kuma xa ki kaka?"
Kamar jiran xuwansa take ta gyara xama ta fashe da kuka ta rike kai tace "Wai da
barin garin xan yi Junaidu, in tafi can Inda Allah yayi" Ya xauna yace "Me ya faru
kuma kaka?" Kaka na Shessheka tace "Ni dai ba fitinanniya bace ni kuma ba
rigimammiya bace Junaidu, kaga tunda uwar ka ta dawo gidan nan ta daina sake min
fuska, yau kwana biyu da dawowarsu Ina kirgawa, Deedayar ma ta rabata da shigowa
nan gaba daya, me nayi mata Junaidu? Daga nace a ba Maryam Deedayah bata san duk
haushin ba a tafi da ni India bne shine ta kullaceni, toh ko Karen hauka ya cijen
ae bana bari Maryam ta rike Deedayah ba, Maryam axxaluma, ae kamar an ba kura nama
ne, to tun daga sannan Rakiya ko ta shigo min minti daya kawai take, ita kuma
Deedayar ganinta ma ba abu ne me sauki a wajena ynxu, duk wahalar da nayi da ita
sae a rabamu haka kawai ba tsididi ba tsadada?" Junaid dake ta sauraronta yyi kasa
da murya yace "Kiyi hakuri kaka, bbu Inda xa ki je" Kaka ta kara rushewa da kuka
tace "Da ma kayi aurene sae ka kai ni gidanka in huta da jarabar kowa inyi ta kai
na, Amma baka yi ba sai gantali kke, wnn shine rana xafi inuwa k'una, ni dai na
gaji" Heedayah da ke tsaye bakin kofa ganin yanda kaka ke kuka ta fashe da kuka ta
fita dakin da sauri, Kaka ta xaro ido tace "Kaga don Rakiya tayi xaton wani abun
nayi mata in shiga uku in lalace ko?" Kuka sosai Heedayah ke yi bayan ta fito ta
tafi can jikin kujera ta rakube har da Shessheka, Shuraim da ke xaune dining ya
mike yana kallonta, ya kalli bangaren Mumy da gefen ido kafin ya nufeta.... Tsayawa
Junaid yyi bakin kofar dakin kaka ya fasa fitowa ya bi Shuraim da ido.

Nagode sosai da ta'aziyar ku gareni, Allah ya sa mu cika da Imani.... Baxan samu


post gobe ba I'm still not home.

Heedayah is 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....


Shuraim na tafiya xuwa gun inda Heedayah ke xaune tana rusa kuka kamar ance ya daga
kai ya ga Junaid tsaye kofar dakin kaka ta jikin TV dake kashe a parlon, yyi saurin
dauke idonsa ya wuce Heedayah ya karasa gun TVn ya kunna sannan ya dau remote ya
koma saman kujera ya xauna ya shiga canxa channel, Junaid ya karasa fitowa parlon
ya karasa gun Heedayah ya duka yace "Why are you crying?" Ta gefen ido Shuraim ke
kallonsu yana canje canjen tasha, Ta goge idonta da bayan hannunta cikin rawar
murya tace "Toh me yasa kaka take kuka ita ma?" Soft smile Junaid ya sakar mata ya
dagata suka mike ya ciro handkerchief yana share mata idonta, Shuraim bai yarda ya
sake satan kallonsu ba ya dinga kallon screen din Tv, a hankali Heedayah tace "Yaya
bana son kaka ta yi kuka kuma, or is she sick?" Junaid ya kama hannunta yace "Mu je
ki bata hakuri kice kar ta sake kuka..." Yana rike da ita suka nufi hanyar dakin
kaka, Heedayah ta kalli Shuraim da yayi frowning face ya bi su da wani kallo, wani
harara ya jefa mata, ta turo masa baki ta dauke kanta tana biye da Junaid xuwa
dakin kaka. Kaka na kwashe tarkacen kayan magungunanta da ta jera gaban madubi tana
xuba su cikin katon handbag dinta Junaid ya shigo da Heedayah, Heedayah ta rakube
jikin kofa cikin sanyin murya tace "Kaka kiyi hakuri ki daina kuka kin ji?" Kaka ta
juyo ta kara rushewa da wani sabon kukan tace "Atoh kaga yarinya kenan ma tana bani
hakuri balle kattin matan da Amadu ya ajiye a gidan nan, ko sanin ina yi ma basu yi
ba, bbu wanda yace min ci kanki har ynxu, haba jama'ah ynxu ace bare ya fi jin k'an
ka a duniya a kan naka, me muka hada da Deedayah banda Amadu da ya jajubo mana ita
a bakin titi tana galantoyi, amma ace ta damu da halin da ta gan ni a ciki a kan
yan gidan nan, abinda su Rabi'ah basu ta6a min ba kenan, ko kuka nake ina birgima
basa ce min komai sai ma mayar da ni fim da xasu yi" Junaid ya karasa cikin dakin,
yyi kasa da murya yace "Yanxu dai kiyi hakuri kaka..." Kaka tace "Toh ni abinda
nayi ma Rakiya ta fita harkata a gidan nan ne na kasa ganewa har ynxu, ka dubi
Allah ka tafi ka tambayo min ita abinda nayi mata yanxun nan..." Junaid yace "Babu
abinda kika yi mata kaka, kawai dai...." Kaka ta daga hannu sama tace "Aa ba ruwana
ka tafi yanxu ka tambayo min ita kawai, ko gaisuwar kirki fa ta bar min a gidan
nan, haka kawai gida duk ya min xafi kamar mayya, ko don an gan ni shiru shiru me
hakuri bana son tashin hankali??" shiru Junaid yyi yana kallonta, sai kuma ya juya
a hankali ya nufi kofa xai fita suka kusa cin karo da Salima, haka kawai gabansa ya
fadi, hanya ya bata tana kallonsa, shi dai bai bari sun hada ido ba ya fice dakin,
Heedayah dake tsaye har sannan cikin sanyin murya tace "Kinyi hakuri kaka?" Kaka ta
kalleta tace "To uban wa nake takama da shi idan banyi hakuri ba Deedayah? Bani da
kowa sai Allah sai ma'aikin Allah, ni a yanxu fa da ni da juya daya nake kallonmu
don wa ennan ba 'ya yan nuna ma duniya bane, Atoh in nuna su in ji kunya, bari dai
Junaidu yyi aure wllh da kudinsu baxa su gan ni ba, abinda nafi kowa sanin kan
iskanci...." Shiru tayi ganin Salima tace "Waye wannan?" Salima na murmushi ta
karaso da ledan hannunta tace "Ni ce kaka, Kin dawo lafiya?" Kaka tace "Ke xan ce
ma kin dawo lafiya ai Salima, ni da na samu labarin yau watan ki daya baki gidan
nan?" Salima ta hade rai tace "In ji ubanwa? To ai gidanmu na koma" Kaka tace "Toh
wani man kika samu yake neman kwale maki fuska kuma yanxu" Salima tayi mata wani
kallo ta ajiye ledan hannunta tace "Ga fura na gani a hanya sabon yi me kyau na
siyo maki" Kaka ta washe baki tace "Toh Allah yyi maki albarka, dama dai ke din ce
me kawo min wa ennan abubuwan" Salima ta kalli Heedayah tace "Ita kuma wnn ido ya
bude kenan?" Kaka tace "To da fa? Ae har ta fi ki gani yanxu, bbu abinda xa mu yi
sai godiya ga Allah, ynxu ma ji nayi suna cewa boding xa su kai ta...." Bude kofar
dakin aka yi Shuraim ya shigo, Kaka ta ajiye jakar hannunta tana nunasa tace "Kai
kuma kana gidan nan ina gidan nan amma ka shigo ka gaisheni balle ka san halin da
nake ciki kake ganin asara, ai abun kunya ne in nuna ma duniya kai ince jika na ne,
ba gwara min Deedayah a kan ka ba...." Heedayah ta kalli Shuraim sannan ta kalli
kaka a hankali tace "Kaka sunana Heedayah ba Deedayah ba" Kaka tace "Meye kuma
Yeedaya?" Heedayah tayi stressing sunan tace "Heedayah..." Kaka tace "Ba ruwana da
wnn, ba Amadun da kansa yace sunanki Deedayah ba, meye kuma laifina a nan, Kai
Shureen ba Deedayah ake cewa ba dama??" Heedayah tace "Ae Shureen ma bai san sunana
ba, Bai iya fada ba" Fixgota Shuraim yyi, Kaka ta taho da gudu tana cewa "Kul kar
ka ta6ata wllh, kana ta6a ta watan barin ka gidan nan ya tsaya Shuraim... A kanta
xan sa Amadu ya koreka ka tafi duk Inda xa ka" Kallonta Shuraim ya tsaya yi da
mamaki, ta kwace Heedayah a hannunsa tace "Uban me ta hada da kai xaka Fincikota
haka, dangin uwa ko na uba?? to wllh kar ka kuma, bbu ruwana da ko kai waye, xan
mance sanin da na maka in ci maka mutunci a kanta, yarinyar da tun ba aje ko ina ba
tana tausayina...." Shuraim na kallonta da kyau yace "Ki ci min mutunci a kanta??"
A fusace kaka tace "Wllh tllh, har shi Amadun sai in 6ata masa a kanta balle kai
karan kada miya, ba gwara min ita ba akan kai da Amadun, duk me damuwa da danuwarka
ae shine naka bbu wani xancen jininka ynxu" Juyawa Shuraim yyi xai fita suka hadu
da Junaid bakin kofar, ya basa hanya ya shiga snn yyi ficewarsa daga dakin, kaka
tace "Kai ka ji min katon Mutumi ya finciko yar mutane xai duka daga tace bai san
sunanta ba, shi Amadun ne ya sa shi wnn danyen aikin ko bala'i ke damunsa? Haka fa
ya xuge uban wai su kai ta makarantar kwana sbda tsabar mugun hali" Junaid yace
"Makarantar kwana kuma?" Kaka tace "Wllh tllh, Kai ka ga hakan ya kamata?" Junaid
ya kalli Heedayah dake ta kallon kaka yyi murmushi yace "Ya kamata kaka, xata samu
karatu sosai kuma xata yi wayo, ta iya xaman duniya a duk ynda ya xo mata" Salima
dake ta kallon Junaid ta kashe murya tace "Ae kuwa gaskiya ka fada...." Ko kallonta
Junaid bai yi ba, Kaka ta kalleta tace "Ki bar tsomo bakin ki a xancen manya
Salima, har fa ynxu kin ki aure ko da yake bbu maneman ne ynxu, ke fa kusan sa'ar
Shuraim ce, a haihuwar kaji kin haifi Heedayah fa" Mami ce ta shigo dakin da
sallama, Kaka ta juya ta ci gaba da hade kayanta ta wani marairaice fuska, Mami ta
xauna, Salima ta duka kasa tana kallon Mami tace "Ina yini" Mami ta kalleta tace
"Lafiya lau ya kike?" Salima ta d'an yi murmushi tace "Alhmdllh, kun dawo lafiya ya
masu jiki?" Mami tace "Alhmdllh mun gode Allah" Mami na kallon kaka tace "Kaka ynxu
Junaid ya sameni da wata magana da ban fahimta ba" Kaka tace "Aa bbu abinda baki
fahimta ba Rakiya, yau kwana biyu kenan bakya tanka ni a gidan nan ba kya kulani
daga na bugi cikin Amadu in ga ko xai iya ba Maryam Deedayah, so nayi inga abinda
ke xuciyarsa game da Deedayah dama, don har ynxu bamu san xuciyarsa ba gaskiya,
amma shkkn kika kullaceni...." Murmushi kawai Mami tayi tace "Aa kaka, baki fahimce
ni bane ni bbu komai a raina, amma kiyi hakuri idan ke haka kika yi tunani, shi
babba ae ba a fushi da shi idan ana son wanyewa lafiya...." Kaka tace "Ka ji ki,
kowa ma ai babba ne Rakiya, yanxu wa xai ce ke kika haifi Junaidu, duka duka nawa
nake xa a dinga ce min babba kamar wata tsohuwa??" Mami tace "Toh ni dai kiyi
hakuri baki fahimce ni bane kaka" Kaka tace "Ni komai ya wuce a gu na, amma fa ko
shigo min nan Deedayar ta daina yi, ban san ko ke kika hanata ba" Mami tace "Toh
xan dawo da kayanta nan din In sha Allah" Kaka tace "Ae dama a nan kayan suke tun
xuwanta gidan nan kawoa shaidan ne ya shiga ya fita ya hada mu" mikewa Mami tayi
tana murmushi tace "Ina d'an wani aiki ne kaka, bari in je in karasa" Kaka tace
"Toh yi tafiyar ki, Allah yayi albarka" Mami ta fita parlon, kaka ta kalli Junaid
tayi kasa da murya tace "Ae gwara haka dae mun tura mata aniyar ta ko?? Gashi ta
shigo tana ta borin kunya, amma ae baxan nuna mata na gane ba" Murmushi kawai
Junaid yyi yace "Xan je anjima in dawo kaka" Kaka tace "Toh Allah yyi maka albarka"
Heedayah tace "Are you going with me Yaya?" Ya kalleta yace "No...." Bin sa tayi da
kallo har ya fita dakin, Salima ta mike ta bi bayansa, Kaka ta bude baki ta bi su
da ido can tace "Tabdiijam, toh me wnn yar duniyar ke nufi? Son Junaidun take Koko?
Naga har kasa ta duka ta gaida Rakiya abinda ko Amadun bata ta6a dukawa kasa ta
gaishesa ba balle ni da na haifesa" kaka ta ta6e baki tace "Toh sai mu xuba ido mu
ga gudun ruwanta, karuwa ce fa, meye dalilin da xata makale ma Salihi irin Junaidu"
ta kuma ta6e baki ta kalli Heedayah tace "Maxa tattara ledojin nan ki kai masu
kitchen can ki watsar ki dawo ga sauran mantina na ajiye maki, yau xaki ga ynda
nake wanke bandaki ciki da bai, ba a xuba maki ido ki lalace ba baki iya komai ba"
Heedayah ta duka ta kwashe tarkacen ledojin Kaka ta fita da su, har lkcn Shuraim na
xaune parlor sai dai bbu abinda yake, ta tafi bakin kofar kitchen ta watsar da
ledan ta juyo suka hada ido da Shuraim, calmly yace "Koma ki kwashe su" Ta make
kafada tace "Ae Kaka ce tace in ajiye a nan" tana fadin haka ta wuce abun ta, ya
mike yace "Keee" tsayawa tayi tana kallon eyeballs dinsa, ya daure fuska sosai yace
"Koma nace ki kwashe su" Ta wani xare masa ido tace "Ni baxan kwashe ba, ai kaka ce
tace in wurgar a nan" Bude baki yyi yana kallonta, ta nufi dakin kaka tana waigosa
har ta shige dakin, Kaka tace "Ga wasu nan ki tafi ki watsar" Kwashe sauran tayi ta
nufi kofa xata fita suka ci karo da Shuraim, kamota yyi ta ji kawai ya tsula mata
abu me xafi, ta fasa ihu a tsorace jin shegen xafi, kaka ta saki xanin gadon
hannunta tace "Auxubillahi waye wnn?" Ko kallonta Shuraim bai yi ba ya juyo da
Heedayah yana kallonta da kyau yace "Ki ka ce min baxa ki kwashe ba?" Bai jira
amsar ta ba ya kara tsula mata dorinar hannunsa a jiki, ta fasa wani karan a rikice
tana sosa wajen tana rusa kuka, Kaka ta fashe da kuka tace "Nace waye wannan??"
Shuraim ya murda kunnenta ya sake xabga mata dorinar a jiki, fuskarsa a murtuke
yace "Nace maki ina wasa da yara ne? Daga yau kika sake kallon Inda nake a gidan
nan sai na fasa maki ido na cire su..." Yana fadin haka ya tura ta ya fita dakin,
Heedayah ta kankame kaka tana kuka sosai tana kiran Mami, Mami ta fito xata wuce
kitchen taji ihun Heedayah da sauri ta shiga dakin kaka, Kaka na ganinta ta kara
rushewa da kuka tace "Hada mu yyi ya xane Rakiya, Ashe dama Shuraim d'an da6a ne
bani da labari, dorina fa me baki biyar ya dauko yayi ta tsula ma yarinyar nan bata
masa komai ba, har cewa yyi xai fasa idanuwanta ya kwakule to kungiyar yan shan
jini ya shiga ne bamu sani ba??" Mami ta dinga kallon kafan Heedayah da shatin
dorina ya kwanta, juyawa tayi ta fice daga dakin direct dakin Shuraim ta nufa,
tsaye ta samesa dakin nasa, a takaice tace "Shuraim a kan wani dalilin ka doki
Heedayah?" Bai ko juyo ba balle ya tanka ta, rai bace tace "Am I even supposed to
ask why? How dare you? Ka fara hauka ne? Ko ka fara shaye shaye? To wllh daga yau
ka sake gigin mata kallon banxa balle ka kai hannunka jikinta xaka sha mamaki na a
gidan nan, Wait... Are you mad?" Daga kai yyi ya kalleta ta madubi jin yanda tayi
stressing mad din, still bai ce komai ba dai, tace "To kayi na farko kayi na karshe
wllh, ko me Heedayah xata yi a gidan nan naka kawai ido, kada ka sake kai min
hannunka jikinta" tana fadin haka ta fice daga dakin, Can tsakar gida kaka ta kai
ma Me gadi wayarta ya kira mata Abba taji ko kungiyar yan shan jini Shuraim ya
shiga ba a da labari a gidan, daga karshe dai me gadi ya jogale waya fitina ya koma
kansa ta tara masa mutan anguwa. Tun daga wnn ranan Heedayah ko fitowa tayi main
parlor ta ga Shuraim sae ta koma daki da gudu, ko da kuwa tare da Mami take, wani
irin tsoronsa na musamman ta fara yi a gidan, ko dakin kaka ya shigo idan ma a
xaune take sai ta rufe ido wai tana bacci, idan a kwance take ma haka, ko karatu
suke da mu'allimar da Abba ya dauko mata a waje tana ganinsa xata daburce kai kace
mala'ikan mutuwa ga gani, Mumy kuwa kullum idan ta fita da safe sai yamma take
dawowa kamar ma'aikaciya nan kuwa tuggunsu kawai suke hadawa da Hajiya Sadiya, kudi
kuwa ta kashe ya kusa dubu dari biyu.... Kaka na xaune parlon Abba bayan isha, Abba
yyi shiru yana sauraronta, Mumy kuma na hada masa fruit salad, Kaka tace "Toh shine
nace bari in xo in ji dalilin hanata xuwa gidan nan da tayi bayan sun yi hutu..."
Abba yace "Kaka ba ita xata hanata xuwa ba, sai dai Baffan nata yace ta xauna can
gidan, kinsan duk makaranta daya suke tare da yaransa, to da aka daukosu daga
makarantar dole can gidan xa a kai su ai...." Kaka tace "Toh shi Baffan wiwi ya sha
da xai hanata xuwa gaida mahaifiyarta har ynxu? Ni sai in iya xuwa in samesa in
gaya masa gaskiya, ko don Rakiyar bata magana? In dan ta nine ma Faridar ta dawo
nan gaba daya kawai" Abba yace "Ni dai bbu ruwanki da wnn kaka, ai dole kafin su
koma makaranta na san xa ta xo nan din, tunda hutun da saura har ynxu" Kaka tace
"Idan an koma tare xa su koma da Deedayah kenan?" Mumy ta saci kallon Abba ta ji me
xai ce, Abba yace "In sha Allah" kaka tace "Toh Allah dai ya kai mu lafiya, nafi
son yarinyar ta xo nan ne su yi ta sabawa da wnn yaro...." Satan kallon Mumy kaka
tayi sai kuma tayi shiru, Abba yace "Wani yaro?" Kaka tace "Su saba da Deedayar
wai" Abba yace "Ohk" Abba yyi kasa da murya yace "Dama kuma Ina son xuwa in sanar
maki kaka, Shuraim ya samu Soja...." Kaka ta dafe kirji tace "Sojaa???" Abba yace
"Ehh" kaka ta saki salati tana tafe hannu tace "Naga abinda ya isheni, uban waye ya
masa sha'awar soja ni Patuu, yyi ta harbe bayin Allah kenan basu ji ba basu gani
ba? Yana xaune a mutum dinsa ma ya aka kare da shi balle ace an basa wani soja?"
Kallonta kawai Abba yake, Mumy ta wani hade rai tana ci gaba da abinda take, Kaka
tace "To waye ya samar masa Soja???" Abba yace "Abokina...." Kaka tace "Baka basa
labarin bakin halinsa bane da mugunta, don duk mutum me shiru shiru mugu ne" Abba
bai kuma ce mata komai ba, Kaka ta kyabe baki tace "Toh ni dai ba ruwana, shi
massers din da yake fa" Abba yace "Xai ci gaba" Kaka tace "To ni dai ba ruwana,
Shureen a khakin soja ai abu ya lalace kuma, taka mu kawai xai dinga yi yana wucewa
wllh" Abba yace "Kaka an gaya maki ne domin kiyi masa addu'a Allah yasa hakan ne
mafi alkhairi, duk wnn xancen da kike yi ba shi bane kaka" Kaka tace "Toh Allah ya
sanya alkhairi, amma wllh ba ruwana wataran idan bamu yi hankali ba duk nuna mu xai
yi da bindiga mu shiga uku, Abinda na fi kowa sanin halin d'an nan naka Shureen,
kwanaki kana ji cewa yyi xai kwakule idon Deedayah ya kai kungiyar su amma ko
mataki baka dauka ba, ni dai ina ta xuba ido in ji tace idonta na ciwo ko wani abu
wllh a nan xan rufe ido mu tafi gidan yan sanda in gaya masu abinda Shureen yace"
Tana kai wa nan ta fice daga parlon, Mumy dai ta cika kiris ya rage ta fashe sai
dai bata tanka kaka tun asali dama, Abba ya sauke ajiyar xuciya ya girgixa kai shi
ma bai ce komai ba... Yau Heedayah tana xaune dakin kaka tana kallon cartoon ta
cikin glasses dinta dake mata kyau sosai kullum baya rabo da idonta, kaka ta yi
mata maganan ta miko mata darduman kusa da ita yyi sau uku amma bata san tana yi
ba, gaba daya hankalinta na kan kallon da take, aka bude kofar dakin Shuraim ya
shigo, rufe ido tayi da sauri xuciyarta na bugawa, Kaka tace "Algungumar yarinya
kawai sai wahala take bani Shureen, tun daxu fa nake mata magana tayi min banxa ta
saka kallon jaraba da baxae mata gafara ba a gaba, ni dai wllh na gaji da yarinyar
nan, ba ta da aiki fa sai kallon robobin nan da an mayar min tashar wa'axi sai ya
canjo min na aljanu, gashi kaf gidan nn bbu wanda ta raina sama da ni, ynxu kuma
daga ganinka ta runtse ido ba tsoron Allah, shi boding din har ynxu basu koma bane,
naji labarin Farida sun yi hutu wajen Junaidu fa, kawai dai Uwar bata bari ta xo
mana nan bane..." Bude kofar dakin aka yi sai ga Farida ta shigo tana kalle kallen
Inda xata ga Heedayah, she looks so happy, ganin Heedayah ta saki jakar hannunta ta
tafi da gudu ta tsallake Shuraim cike da murna ta rungume Heedayah gam tace "Didi
na dawo, Didi I am happy you can see me...."

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga
opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku
shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a
parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai
bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu
irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very
affordable.... 😍

Heedayah ta bude ido a hankali tana kallon fuskar Farida, murmushi tayi ta
rungumeta ita ma tace "Farida" sai kuma ta saketa tana kallon fuskarta, ta wara
manyan idonta ta kai hannu dimples dinta tace "Kamar na Yaya" Dariya Farida tayi
tana kallonta, she is so happy seeing Heedayah, Kaka ta nemi waje ta xauna tace
"Allah sarki, jininsu ya hadu wllh, su Rabi'ah da Khadijah dama bakin hali baxae
bar su suyi hka ba, uwar tayi kane kane ta hanasu, ko kulata ma basa yi a gidan,
ita ma Deedayar ta kanta take" Farida dake murmushi har sannan ta xamo kasa tace
"Ina yini kaka?" Kaka tace "Lfya lau Farida, ya karatu? Sae yau shi Honorable din
ya ga daman sako ki kixo gun uwarki knn" Farida tace "Aa naje gidan wani kawun mu
ne fa kaka ba gidan Baffa nake ba" Kaka tace "Toh baku gaisa da Shuraim ba, ko baki
gansa ba" Juyawa Farida tayi ta d'an kallesa, ya ki juyowa fuskarsa bbu yabo bbu
fallasa, ta kyabe baki tace "Ina wuni" still bai juyo ba yace "Lfya" Heedayah sae
satan kallonsa take, Kaka tace "Tunda uban ya samar masa Soja yake amsa gaisuwan
kowa cikin isa da gadara, mu dai bamu kulasa ba balle ayi tashin hankali da
shi...." Farida ta mike ta daga Heedayah tace "Ki rakani in je in gaida Mamina"
Kaka tace "Aa je ki gaisheta ki dawo, baki ga ni daya bace parlon, ae ita ke taya
ni xama" Farida ta sake hannun Heedayah tace "Toh" daga hka ta fita dakin, Heedayah
na kallon kaka kamar xata yi kuka tace "Kaka don Allah in bi ta, ae xan dawo..."
Kaka tace "Toh kya ci kanki, bi ta ku je, dama amfanin me kike min bnda kallo" Da
sauri Heedayah ta juya xata fita parlon tayi tuntube da kafar Shuraim ji kke tim ta
fadi kasa, A tsorace ta mike xaune tana komawa baya tana kallonsa tace "Wayyo kayi
hkuri..." Ya janye kafarsa bai kalleta ba, kaka tace "Yau naga jaraba, Allah ne shi
da xa ki basa hkuri bayan tika ki da katon kafarsa yyi da kasa, Shureen fa ba
Mala'ika bane da kike gigicewa ki tsorata idan kin gansa, ko meye gamin ki da shi
banda Ubansa da yayi sanadin xuwan ki gidan nan??" Mikewa Heedayah tayi ta fita da
sauri, duk gaba daya a tsorace take, kaka tace "Ni dai ba ruwana, kai kuma Shureen
ya wnn yarinya Farida na gaishe ka kana amsa mata a walakance kamar an maka dole?
Ba fa yar banxa bace da ka ganta nan, da gatan ta wllh, kuma da kyar idan ubanta
bai fi naka kudi ba duk da ya rasu, snn ga kawunta shi ma gidansa gari guda yyi
gaba daya anguwar nan, bbu abinda bbu a gidan, to a kan me kuma kake amsa mata
gaisuwa can ciki ciki? Ka fita kyau ne ko gayu aka ce maka? kai da ko manyan kaya
baka sakawa sae na tsigalallu" Ya juya yana kallon kaka yace "Na hada wani abun ne
da ita? Kin ga ki daina min shisshigi a lamarina, bbu ruwanki da harkata, dole aka
ce maki sae na amsa gaisuwarta ko ina da wani alaka da ita ne??" Bai jira cewarta
ba ya mike ya fice daga dakin, kaka ta nemi kujera ta xauna a hankali tace "Ikon
Allah, Amadu dai ya ja mana bala'i, muna xaman xaman mu yace xai kai sa Soja gashi
tun ba a je ko ina ba ya fara kilewa.... To banda bala'i yaushe har Shureen ya fara
magana da har xae xageni ya fita, dama haka sojojin suke bani da labari??"
Washegari Monday da safe Mami ta koma bakin aikinta, Farida ta gama duk abinda xa
su yi da Heedayah a bangaren Mami suka fito, Heedayah na sanye da wando da riga sai
hula da ke kanta, sosai kayan suka yi mata kyau kamar yar turawa ga gashinta da ta
baxo ta cikin hular, Farida kuma Abaya ta saka da veil dinsa, ta kulle bangaren
Mami suka wuce gaida Kaka a dakinta, Kaka tace "To ita Deedayah me yasa Rakiya bata
siya mata irin wnn kayan na jikin ki ba, ko don ba ita ta haifeta ba sai tayi ta sa
mata kayan anna??" Farida dai bata ce komai ba, haka ma Heedayah, Farida ta mike
tace "Kaka xa muje tsakar gida mu dawo" Daga haka Farida ta kama hannun Heedayah
suka fita dakin, Kaka ta kyabe baki tace "Wnn faridan ta fiye rawan kai da iyayi
kamar dai uwarta, ba don wannan halin nata ba dai Shureen xai aureta, banda dai
kowa na son inda nasa xai huta ai wnn rawan kan nata ya fi karfin Shureen" Garden
din cikin gidan Farida suka tafi da Heedayah, suka xauna kan kujeran dake garden
din Farida na kallonta tace "Toh ko na nuna maki yanda ake operating wayar ai ba
siya maki Mami xata yi ba, nima fa Baffanmu ne ya siya min, kuma da kyar ta bar ni
na rike..." Heedayah ta langwabar da kai tace "Ae Yaya xan ce ya siya min ko Yaya
Sudais" Farida tayi dariya tace "Toh shkkn, nasan Yaya xai iya siya maki, shi
kinsan babu ruwansa" Tsakaninta da Allah ta shiga nuna ma Heedayah ynda ake amfani
da waya da abubuwan dake cikin waya tun daga lock button, Heedayah ta maida hankali
kai kace karatu take dauka... Tun da suka shigo garden din Shuraim dake xaune sama
yana karatu a laptop dinsa ya mayar da laptop din gefe yake kallonsu, su kam ko
lura da shi basu yi ba, can ya mike ya bar wajen, Farida ce ta fara hangosa yana
tahowa toward them bayan ya sakko downstairs, tayi kasa da murya tace "Wannan Yaya
Shuraim din is coming" Sosai Heedayah ta rikice a gun, ta dinga cewa "Farida tashi
mu tafi yana yi ma mutane duka wllh, ki tashi mu tafi...." Farida ta hade rai tace
"Toh ba sai ya doke mu ba" Har dai ya iso kansu, yana kallon Farida yace "Me ku ke
yi a nan?" Farida ta d'an kallesa tace "kawai labarin mu muke" yace "You are
showing her how to operate phone right?" Tace "Yea.... sannan muna hiran makaranta"
ya mika mata hannu yace "Bani wayar" Mayar da wayar Farida tayi bayanta ta hade rai
tace "As in how?" Yace "Baxa ki bani ba" A takaice tace "Gaskiya...." Mikewa
Heedayah tayi ba tare da ta yarda ta kallesa ba xata bar wajen yace "Kina kara step
daya sai na 6allaki" Tsayawa tayi, tayi narai narai da ido, sai dai taki yarda ta
juyo ta kallesa, Farida ta mike xata bar wajen ya riketa ya kwace wayar a hannunta,
tsaye tayi tana kallonsa tana huci, yace "Daga yau.... Ina nufin daga wannan moment
din ko by mistake kika sake xaunar da ita kina nuna mata waya sai kin sha mamaki a
gidan nan" Farida tace "Toh ai wayana na nuna mata ai ko? Kuma ni ka bani
wayata...." Ya mata wani kallo ce "Ki kwata mana" Kallon Heedayah yyi ya kara daure
fuska yace "Uban me xa kiyi da waya da kika xauna tana nuna maki ynda ake amfani da
shi" Heedayah ta girgixa kai bata ce komai ba, strictly yace "Juyo Ina maka maki
magana" A hankali ta juyo tana facing dinsa idonta har ya kawo ruwa, ya kara shan
kunu yace "Ke kika ce ta nuna maki waya ko?" Ta girgixa kai bata ce komai ba, yace
"Toh na sake ganin ki xaune ana nuna maki waya sai na xane ki a gidan nan, daina
kallona" Ta sauke idonta kasa hawayen ciki ya xubo, a fusace Farida ta bar wajen
kamar xata tashi sama, Shuraim ya bi ta da wani kallo har tayi corner, yana kallon
Heedayah yace "Start going" juyawa tayi ta fara tafiya yana biye da ita a baya har
suka shiga cikin parlor sannan ta juya suka hada ido, daure fuska yyi ta nufi dakin
Kaka tana goge idonta, Kaka dake ta sauraron Farida ta sauke wani ajiyar xuciya
tace "Toh, a gaskiya ni dai baxan iya tunkaran Shureen ba ynxu don ya xama abinda
ya xama, rashin kunya yake ma kowa gadan gadan, Kuma ni ban san ko har sojojin sun
basa bindiga ba inje in ja ma kai na, yo in ja ma kaina mana, yanxu sai ki tashi mu
tafi bangaren uwarsa nasan tana can tana baccin asara kin san me xaman banxa, nasan
ita idan tayi masa magana xai ji" Heedayah na shigowa dakin kaka ta fashe da kuka
ta fada kan gado har da Shessheka, kaka ta mike da sauri tace "Lafiya, me ya faru,
ni dai na shiga uku, kukan me kike" Kuka kawai Heedayah take, Farida tace "Shine ya
doketa kila" Kaka tace "Ya doke ki???" Da sauri Heedayah ta mike xaune tace "Aa bai
dokeni ba fa" Kaka tace "To kukan me kike" ta girgixa mata kai kawai, Kaka tace
"Oho ni ban iya wahala, tashi mu je gun uwar tasa Farida, dabanci kawai Shureen ke
ji a gidan nan kwanan nan" Tare Farida suka fita da kaka xuwa bangaren Mumy,
Khadijah na xaune parlor tana kallo, kaka tace "Gantalalliya abinda kika iya kenan,
Ina Rabi'ar?" Khadijah ta wani daure fuska tace "Ta tafi gidan Aunty Asma'u" Kaka
tace "Ta tafi gidan Asma'u? Shine bata sallameni ba? Wai me yasa Amadu ke min haka
ne a gidan nan kamar ba uwarsa ba, ynxu fa a kullum da kyar ku ke shigo min
bangarena sau daya, Mata duk ta kanainaye ku bata son ku ra6i kowa na gidan nan
kullum kuna kunshe a daki?? Toh bari ya dawo shi Amadun" Mumy na daki duk tana jin
kaka, kafin ta karasa cikin dakin tayi saurin fitowa, Kaka na ganinta tace "To
Shureen ne ya kwace wayar Farida, kuma dubu dari biyu aka ce an siya wayar, to
siyarwa yake da niyyar xuwa yyi shine ban gane ba" Mumy tace "Ni kuma ina naga
Shuraim da safen nan kaka?" Kaka tace "Aa ba ruwana ki fita ki nemosa duk inda yake
ya maido ma yar mutane wayarta kafin ya tafi chechenia da shi a shiga uku" Mumy ta
kalli Farida daga sama har kasa, Farida tace "Ina kwana" a walakance Mumy tace
"Lafiya" Kaka tace "Yar gidan Rakiya ce fa, daga makarantar kwana suka yi hutu ta
xo mana shine har xai saka mata ido a gidan ya kwace mata waya to ina ruwansa da
ita idan ba neman fitina ba, daga ance an samar masa Soja sai ya xame mana ibilisu
a gida??" Mumy tana wani kyabe baki tace "Toh ni ban san inda Shuraim yyi ba tun
asuba da ya shigo ya gaisheni ban sake ganinsa ba wllh" kaka tace "Toh ai nemosa
nace xa kiyi idan ba haka ba wllh sai in ja ta mu tafi gidan yan sanda su san
abinda ake ciki, muka san ko sojojin kwacen wayar mutane suka sa shi" Tana fadin
haka ta kama hannun Farida suka fita, Mumy ta bi su da wani irin kallo. Har Mami ta
dawo da yamma Shuraim bai ba Farida wayarta ba, barin gidan ma yayi gaba daya, Mami
ta tabe baki bayan ta gama sauraron farida tace "To uban wa xa kiyi ma kuka?"
Farida ta kara rushewa da kuka tace "Wllh Mami bbu abinda muka yi masa kawai ya
amshe wayata" Mami tace "Me kike yi da wayar ya amsa?" Cikin kuka tace "Babu komai
wllh" Mami tace "Toh ai shkkn, dama nima na gaji da shegen wayar da kike rikewa"
Tana fadin haka ta shiga daki, Heedayah dai na xaune parlon tayi shiru, can ta mike
ta isa gun Farida tace "I
am sorry I caused you all this Farida, da bance ki nuna min ba baxai amsa ba"
Farida tace "Ai wllh sai ya bani wayata, you caused me nothing" Kaka ce xaune
parlon Abba da Farida, Heedayah ma na xaune kusa da kaka, Abba yyi shiru yana
sauraron kaka, kaka tace "Toh a gaskiya bbu ruwana kar ya ja mana fitina muna xaman
xaman mu, a nemo sa duk inda ya shiga ya ba yar mutane wayarta" Abba na kallon
farida yace "Me kike yi da wayar ya amsa?" Ta girgixa kai a hankali tace "Babu
abinda nake yi Abba, ni da Heedayah ce ma a xaune lkcn" Kaka tace "To me xata yi da
wayar banda karatu kaji ka da wata magana, bbu abinda suke yi vanda karatu" Abba
yace "Toh shkkn xan nemi Shuraim din" mikewa kaka tayi ta nufi kofa tace "Ku taso
mu je, shi da ya sa shi a sojan su karata can" Mikewa Farida da Heedayah suka yi
suka bi bayan kaka. Shuraim na tsaye dakin Mumy dake ta masa fada kamar xata ari
baki, shi dai bai ce mata komai ba, tace "Banda ka haifi yaro baka haifi halinsa ba
ina ruwanka da lamarin su a gidan nan? Ka hada wani abu ne da yarinyar da xaka
amshe mata waya da sunan discipline? Ina ruwanka da ita nace" ya shafa kansa still
bai ce komai ba, tace "Toh wllh ka kiyayeni a gidan nan, banda baka kishina kai ko
kallon yar nan xaka yi balle ka amshi wayarta Aliyu" Wayarsa dake hannunsa ne ya
fara ring, Mumy tayi shiru tana kallonsa, yace "Abba na kirana" Mumy tace "Wannan
damuwarka ce, ni dai idan har baxaka fita hanyar makiyana a gidan nan ba to wllh
sai dai ka canxa wata uwar ba ni ba" juyawa yayi ya nufi kofa ya fita, a main
parlor ya tadda kaka tana dube dube kamar munafuka, tana ganinsa ta hade rai ta hau
kakkabe kujerun parlon tana cewa "Mata duk kazamai kawai" yayi wucewarsa bangaren
Abba, tana ganin haka ta nufi dakinsa da sauri ta shiga tana kalle kalle, saman
madubi ta ga wayoyi har biyu a ajiye da dubu biyar ta kwashe duka ta fice. Shuraim
yace "Abba Heedayah take koya ma ynda ake operating waya shi yasa na amshe" Abba
yyi shiru yana kallonsa haka ma Mami dake parlon tana xuba ma Abba abinci, Mami ta
dauke kanta ta ci gaba da abinda take, can Abba yace "A ina ka gan su?" Shuraim
yace "Can baya" Abba yace "That's wrong, and you did the right thing collecting the
phone, ka rike wayar wajen ka nan da kwana biyu sai ka bata" Shuraim ya dago kansa
yace "Ita ma bai kamata ta rike waya ynxu ba, she still in Jss2 I think" Abba yace
"Haka ne but assuming a gidan nan take ni baxan bari ta rike waya ba, but tunda ba
a nan take ba we have no say, ka maida mata wayarta after two days..." Shuraim yace
"Idan xata koma makaranta xan bata amma ba ynxu ba" Abba ya kalli Mami da bata
kalli Inda suke ba yace "Ur opinion Rahinah" Mami ta kallesa tace "Duk ynda kayi
dai dai ne barrister" Abba yace "Alright, ka bar wayan gun ka Shuraim" Shuraim yace
"Toh shkkn" daga haka ya mike ya fita parlon. Karfe tara da rabi kaka na xaune
dakinta ta daura kafa daya kan daya ta gama cinye kazar da Junaid ya kawo mata tana
sakace hakori Shuraim ya shigo, tana ganinsa ta ci gaba da sakace sakacenta tana
lumshe ido, ya bi dakin da kallo sannan ya juya ya fita, bangaren Mami ya nufa ya
bude parlon ya shiga, bbu kowa parlon amma yana jin muryarsu a daki, karasawa yyi
bedroom din ya bude kofar, Xaune suke kan gado suna kallo a laptop din Farida,
Heedayah na sanye da yar rigar bacci iya cinya haka ma Farida, Farida ta xaro ido,
da sauri ta rufe jikinta da Pillow tana kallonsa, Heedayah ta sauka saman gadon da
gudu ta shige bandaki ta rufe, yana kallon Farida yace "Bani wayar da kika shiga
dakina kika dauka" Ta xaro ido tace "Ni?? I didn't take any phone wllh, tun daxu
muna kallo a nan ban fita ba" ya fi minti daya yana kallonta sannan ya juya fice
daga dakin, ya koma dakin kaka, kaka ta kallesa tace "Sojojin ne suka baka pareti
da daddaren nan, naga ka shigo daxu baka ce min komai ba, gashi ka sake dawowa"
Yace "Ina wayoyin da kika dauka a dakina?" Kaka ta mike tsaye ta wani xaro ido tace
"Wayoyi kuma?" Yace "Ehh" Ta nemi waje ta xauna har ta fara salati sai kuma ta
sakar masa kuka tace "Tunda uwata ta haifeni bbu wanda ya ta6a tsareni yana
tuhumata a kan sata, satar ma ta waya, Shureen in rasa abinda xan sata a gidan nan
sai waya? Ashe ma gantalalliyar barauniya ce ni, in saci motocin Amadu in gudu mana
idan haka ne, Amma sai ka shigo min tsakar dare kace Ina wayar da na sata??"
Shuraim ya gyada kai ya juya ya fita dakin. Bai sake maganar wayar ba har gari ya
waye, Farida na share ma Kaka dakinta, Heedayah na kwance saman gado tana kallo a
laptop, kaka tace "Shiru Shureen bai sake shigowa nemo waya ba gashi har karfe goma
ko dai ya hakura ne, ni dubu biyar din ma kasuwa xaku je min ku siyo min kayan ciki
in narka uban farfesuna mu yi sati muna ci, kayan cikin dubu biyar ai xai cika
wancan kwallan ko?" Farida ta juya tana kallon katon abinda kaka ke nuna masu, kaka
tace "Har yawuna ya tsinke maxa gama sharan ku tafi da wnn mara amfanin ku siyo min
kayan cikin" Farida tayi kasa da murya tace "Ke dai kar kice masa komai a kan wayar
ki ci gaba da boyewa" Kaka tace "Toh da fa, ai ni tasa wayar ma da kyar idan ba
chechenia xa ku rakani ba in siyar da 'yar banxa in siyo kan saniya inyi farfesuna"
Farida ta fashe da dariya har da kyakyatawa, murya can kasa tace "Xan raka ki wllh,
gashi naga shi ma IPhone din ne har ya fi nawa" Kaka tace "Toh ko in shirya yanxu?"
Farida tace "Shirya" mikewa kaka tayi xata fiddo da sabon kayanta, Ganin cup da
Heedayah ta sha shayi ta kalli Heedayah dake kwance tace "Kai ni dai wnn yarinya ta
isheni wllh, kwata kwata ba a morarta, son jikinta har tsoro yake bani ni dai, to
Amadu kike jira ya dauke maki kopin nan ko Rakiya??" Heedayah ta sakko saman gadon
ta dau cup din ta nufi kofa kaka ta bi ta da harara tace "Toh meye ma amfanin bude
idon da Amadu ya kai ki aka yi idan ba asaran kudi ba" Heedayah na fita dakin ta
wuce kitchen, Khadijah dake xaune dining ta bi ta da harara, ita dai ko kallonta
bata yi ba, ta bude kofar kitchen din ta shiga, ta ajiye cup din a sink kenan ta ga
Shuraim tsaye kitchen din yana hada shayi, sunkuyar da kanta tayi xata fita, yace
"Zo nan" kin tsayawa tayi ta ruga da gudu ya kamata kafin ta isa kofa, kuka ta
sakar masa a tsorace tace "Ni ban yi komai ba wlh, kaka ce tace in kawo cup din
kitchen" leka parlor yyi ganin Khadijah ya rufe kofar kitchen din, har wani rawa
jikinta yake yi sbda tsoro, ya jinginar da ita da kofa yace "Wa ya shiga dakina ya
dau waya?" Ta bude hannu da sauri tace "Nima ban sani ba, bani bace wllh" kalle
kallen kitchen din ya fara yi taga ya kallo inda muciya yake, xaro ido tayi ta
rungumesa a rikice tace "Wllh Kaka ce ta dauka ta boye a dakinta, a cikin akwatinta
ta boye" Bai san lkcn da yyi murmushi ba yana kallonta duk da ta boye fuskarta
jikinsa, a hankali cikin rawar murya tace "Yanxu xa su je su siyar da wayan da
Farida"

Heedayah isn't free, you read for free

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

You might also like