SOJANA by Tnovels.com.ng

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 29

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.

ng ku ziyarci
shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama
daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku

This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to
download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography
including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490
its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng


to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[29/05 à 17:06] MRS SADAUKI 💫: *SOJANA...*💞

☀️ *FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*☀️

Chamsiya Laouali Rabo✍🏻

*MARUBUCIYAR :*
SO KO ƘAUNA
JININA NE KAI
HASKEN SOYAYYA
CIWON SO
SADAM
ƘAWAR MOMYNA
ABBANA NE
MAHAUKACIN SO
ILLAR LUWAƊI
ABOKIN MAGAJINA NE
ƳAN UKU
ƁOYAYYEN SIRRI
DA CIWO A ZUCIYATA
DJINN
ƘADDARA

Page 1-2

Tafe suke suna hira ita da ƙawar ta, sun zo daidai bakin titi suka tsaya jiran har
ababen hawa su tsaigaita wucewa.
Kamar walƙiya haka gungun motocin sojawan ke wucewa shuuu har wata ƙura ke tashi
tsabar yadda suke gudun.
Tsuki Munat tayi tana mai cewa ƙawarta Maryam "wlh na tsani soja a rayuwata, dubi
dan Allah yadda duk suka ɓatawa mutane da lokaci saboda kawai su wuce an wani
tsayar da mu kan titi mtsw..."ta ja wani dogon tsaki, murmurshi Maryam kawai tayi
ta na mai cigaba da kallon motocin cike da burgewa dan ita a rayuwarta babu abinda
ke burge ta irin soja.
Motocin ne suka fara ragewa a sannu har aka zo da motar ƙarshe wacce ke gudu a
slow,hannu Maryam ta ɗagawa sojawan ciki da ya ke motar irin wannan ce mai baya a
buɗe suma maido mata su ka yi.Cike da jin haushi Munat ta tsallake ta bar Maryam
tsaye tana hangen motar da ta wuce,da ɗan gudu ta tsallaka ta cimma Munat wacce ta
cika tayi fam tamkar za ta fashe.
"Kiyi haƙuri ƙawata wlh na sha'afa ne sam ban lura da lokacin da kika tsallaka ba
sorry"cewar Maryam ta na mai kamo hannun Munat ,fizge hannunta tayi tace "ta ya
dama zaki lura ki na kallon dangin Iya"dariya Maryam tayi tace "yanzu ni kike zagi
ki na cewa ina kallon dangin uwata ?"hararar ta kawai Munat tayi ta na mai shigewa
cikin gidan su dama gidan su ne farko sannan na su Maryam.

A yadda ranta ya ke ɓace shi ya hanata yin sallama,ta na sanya ƙafarta cikin falo
ta wani tsaya turus ta na mai fiddo ido waje tare da dafe ƙirji kamar ta ga wani
mugun abu.
Sanye ya ke da kayan sojoji masu dogayen hannu idon shi manne da baƙin gilashi
wanda ya zauna ɗaf bisa doguwar fuskar shi mai yalwatacen saje baƙi ƙirin,ja hular
shi na bisa dogon gashin kan shi wanda ya ke baƙi siɗik irin na buzayen usuli.
Yadda ta ƙame ƙyam kamar mai cutar sanƙaro shi ya so bashi dariya amman ya cije
tare da haɗe fuska tamkar bai taɓa dariya ba,"ƙaraso mana kin ga ɗan uwan ki ne
Mohammed ya kawo mana ziyara"cewar Mami ta na murmurshi.
Duk da akwai gilashi a idon shi bai hanata gane kallon tsaf ɗin da ya ke mata ba
hakan ya sa ta turo baki gaba "shine zai wani tsare ni ya na kallo kamar maye"a
tunaninta a zuci tayi maganar sai jin dakakiyar murya shi tayi yace "mi za'a kalla
a nan?ko maye ne ni na rasa wacce zan lashe sai ƴar Baƙa"dariya Mami tayi ta na jin
daɗi a ranta ganin duk da ba su san juna ba sun fara wasar cousinage irin ta Ɗan
mace da Ɗan namiji.
Wani haushi ne taji ya kamata dan duk duniya in akwai abinda ta tsana shine a
shammace ta da baƙin ta wato baƙar fatar ta,baki ta sake turowa ta fara magana
cikin sangarta na autanni "Ni dai ba baƙa ba sai dai..."sai kuma ta ƙyale ta na
kallon farar fatar shi wacce dan tsananin farin shi kace Balarabe ne,miƙewa yayi
tsaye ya fara takowa inda take da sauri ta fara marche arrière saboda yanayin
tsawon shi da faɗin ƙwanjin shi ba ƙaramin cika mata ido yayi ba.
Ido ta rumtse jin ya zo daf da ita,riƙe ƙugu yayi kamar wata mace yace "wai Mami
wannan autar ta ki har yanzu ba ta bar tsiwa ba ko mi?wai ni take kallo da ƴan
ƙananan idonta tana turo min baki da ki bar su a buɗe ki gani da na cire maki su na
baki abun ki a hannu gobe sai na ga da wane zaki harare na"wani fitsari Munat taji
ya cika mata mara a take tsabar tsoro dan a yadda ake faɗin sojawa ba su da imani
to wannan ba ƙaramin aikin shi ba,a fili ta furta "shikenan da na zama kamar Laila
ta cikin LE DESTIN wayyo Allah da na shiga uku"ta faɗa tana shirin rugawa sai kuma
taci karo da shi.
Hannunta ya riƙe yace "ai kam kin kawo idée hakan zan yi maki"ƙara Munata ta saka
tana kiran sunan Abba,a can bayan shi yaji Mami na cewa "a'a Mohammed kar fah a
takura min auta dan in baya na ƙyale yanzu ba zan yi haƙuri ba"cikin dariyar da ta
bayyana fararen haƙoran shi masu ɗauke da hauren Makka biyu yace "bar ni na tuna
mata baya Mami da alamu ta manta ni ne"ya faɗa ya na mai lanƙwasa mata yatsun
hannunta suna bada sautin ƙwas ƙwas ƙwas.

Sakin ta yayi tare da dungure mata kai yace "ƙazama mai kukan kitso"ba ta kula shi
ba ta ruga part ɗin ta, toilet ta shiga ta fara yin fitsarin da ke shirin kubce
mata sannan ta sakarwa kanta shower tana mai lumshe ido.
Tana fitowa doguwar riga ƴar kanti ta saka tare da fesa turare ta dawo falo wayam
ba shi ne,samun kanta tayi rashin jin daɗin haka ta so ta ƙara kallon kyakkyawar
fuskar shi mai kama da ta larabawa.
Abinci ta zuba ta fara ci kawai sai taji sallamar shi,dammm ƙirjinta ya buga amman
sai ta danne tsoron shi da ya tsargar mata tana mai ɗagowa ido ta waro ganin ya
cire hular kan shi ya baje baƙin gashin shi wanda ya zo har kusan wuyan
shi."Astagfirullah"ta furta da ƙarfi ba tare da ta janye idonta daga kallon shi
ba,fuska ya turniƙe ya zauna kujerar da ke facing nata ya na mai kakaɓe gashin shi
da yayi ƴar lema.
Baki ta turo ganin ya tsare ta da fararen idon shi masu kamar madara tare da sunne
kai tana yawo da cokali sam ta kasa cigaba da cin abincin,"maras kunya ai na zata
ba zaki janye idon na ki ba masu kama da na wara🦗"cewar Mohammed ita dai ƙin tanka
shi tayi dan har ga Allah tsoron shi ma take.
Mami ce ta fito daga wanka har ta canza kaya tace "Auta ke ɗaya ke cin abincin baki
bari na fito?"ɗagowa tayi ta kalli Mami sannan ta juyo inda Mohammed ke zaune ya na
aikin kallonta tace "shi wannan yaushe zai tafi?"waro ido yayi yace "zuwa ina?tab
yarinya ina nan kuma in zan koma da ke zan tafi can dajin sambisa wajen ƴan boko
haram dan su koya maki hankali"da sauri Munat ta miƙe tana shirin guduwa dan duk
tsiwarta tsoron tsiya ne da ita.
Saurin fizgota yayi ta faɗo jikin shi,dariya yayi mata sannan ya jawo abincin yace
"ci abincin ki wasa ni ke maki Mimina"da mamaki ta kalle shi jin ya kirata da wani
suna a zuci tace "wai Mimi ko miye ma'anar haka?"ba zato kawai taji ya buɗe bakin
tare da tura mata loma,ba ta da zaɓi ta fara taunawa ta na mai mashi kallon cikin
ido.
Har sai da Munat ta cinye abincin ba ta san da ta cinye ba,nan Mohammed ya shiga
tsokanar ta rufe fuska tayi tana dariya shi kuma ya fara ɗaukarta video kafin yayi
mata hotuna.
Jin an fara tada haramar sallah yayi saurin miƙewa ya na mai miƙa mata wayar ta
shiga duba hotunan da yayi mata gabanin ta cigaba da ɗaukar kanta.

Ko da Mohammed ya dawo daga sallah ya tarar da hotunan Munat sun fi ɗari har da
canza kaya tayi wasu kuma da hijab ta yi su, murmurshi kawai ke fita daga fuskar
shi.Muryata yaji tana cewa "yauwa Moha buɗe min code ɗin na gani"ta faɗi hakan tana
cire hijabin da tayi sallah .
Kafaɗa ya maƙe mata yace "ina sauri yanzu za mu wuce Zinder ki bari zan turowa
Mustapha ta WhatsApp"narai-narai tayi da ido tace "shikenan yanzu tafiya za
kayi ?"yace "eh!ko ki na zuwa ne?"kai ta girgiza tace "a'a amman yaushe za ka
dawo?"
"Nan da 3mois (3month) in shaa Allah kin ga ba jimawa zan yi ba kamar gobe ne"tace
"haka ne"kallon ta Mohammed yayi da kyau yace "ko baki so naje ne?in baki so sai
nayi zamana"da sauri tace "dagaske?"yace "eh mana " "to kawai kayi zamanin ka
"cewar Munat dariya yayi yace "so kike a kore ni daga aiki ko?"gira ta ɗaga tace
"eh ɗin dama na tsani soja"har zuciyar shi yaji rashin jin daɗin haka a sanyaye
yace "kin tsani soja koko aikin soja?"shiru tayi can tace "duka biyun"ba tare da ya
kuma cewa komi ba ya shiga danna wayar shi da alamu text ne ya ke rubutawa.
Tsure shi tayi da ido ta ga sam babu alamun fara'a a fuskar sai taji kuma ba ta
kyauta ba dan ta gano ɓaranɓaramar da tayi,to amman ya za tayi?nature ɗin ta ne
Allah ya sa mata tsanar soja a zuciya.

Miƙewa yayi ya na mai zuwa bakin ƙofar Mami yace "Mami ni zan tafi sai kuma in
Allah yayi mamu dawowa ƙila mu biyo ta Maradi"fitowa Mami tayi ta raka shi da
addu'a tare da bashi wata tsanwar leda,yayi godiya ya karɓa har ya kai bakin ƙofa
ya juyo ya kalli inda Munat ke tsaye tsamo-tsamo yace "Mimi babu rakiya?"hararar ta
Mami tayi tace "je ki raka shi mana har samu adaidaita"ledar hannun shi ta amsa
suka fita waje suna jiran ɗan sahu.
Ita dai kanta a duƙe ya ke ba ta ɗago ba duk da taji a jikinta ita ya ke
kallo,nisawa yayi yace "Mimi zan tafi mission ban sani ba ko na dawo ko akasin haka
abinda ni ke so da ke ki kula da kanki banda biye ma ƙawaye da shirme na yin
samari,ki tsaya waje guda in dai na dawo da raina to na san dan mu rayu ne"ya
ƙarashe maganar ya na mai cire wani abun wuya nashi mai ɗauke da wani dutse mai
shatin love a tsakiya.Cikin hannunta ya damƙa mata ya na mai karɓar ledar daidai
nan mai adaidaita ya tsaya ya shiga,hannu ya ɗaga mata lokacin da ɗan sahun ya fara
tafiya.Jijiyoyin ƙafafunta ne taji sun ƙulle sam ta kasa tafiya kamar wacce aka
yiwa dabaibayi,lafuzan shi take son warwarewa dan sanin ma'anar su amman kwanyarta
ta tsaya cak daga aiki abu guda ke yi mata yawo ```na tafi mission ban sani ba ko
na dawo ko kuma ba zan dawo ba``` tambaya tayi ma zuciyarta "to ina zai tafi in bai
dawo ba?"nan take kuma ta bata amsa da "in ya mutu"wata irin kariyar zuciya ta samu
lokaci guda kuma idonta ya fara zubar da ƙwala a hanya mutane sai kallon ta suke
har ta shige gida.
"Auta lafiya kike kuka ko sakarcin ne ya motsa?"cewar Mami tana kallonta,baki ta
turo ta shige ɗakinta.

A ɓangaren Mohammed kuwa tun bisa hanya ya sauke App ɗin da ake ɓoye hotuna,nan ya
ɓoye duka hotunan Munat dan ko kaɗan bai ji zai iya bari wani ya ga hoton ta ba sam
zuciyar shi ba ta aminta da haka ba saboda tsabagen kishi irin nashi ga kuma abokan
shi maras kan gado sun ga dama in sun amshi wayar shi su kalle mashi ita.
Ko da ɗan sahun ya kai shi Company ba'a ɗau lokaci ba suka kama hanyar Zinder,suna
fita daga Maradi sai yaji tamkar an raba shi da wani jigo na rayuwar shi duk sai ya
koma sukuku duk da ya kasance mai yawan magana.
Baƙin daji ne baƙi ƙirin suka sauka inda anan ne za su yi patri na wani lokaci
kafin su yi gaba,wayar shi ya ɗauka ya danna lambar Mustapha Yayan Munat har sai da
ta kusa yankewa ya ɗauka.
Cikin girmamawa suke gaisawa kafin yace "BABBAN YAYA dan Allah ina neman wata
alfarma ka baiwa Mimi wayar ina son yin magana da ita kar ka bari Mami ta
gani"cewar Mohammed ya na mai marairaice fuska,tsuki Mustapha yayi yace "banza na
zata wani abun ne za ka nema ashe wannan ficikar kake son na kaiwa waya,to uwar
miye za ka gaya mata kuma yanzu?"cikin jin haushi Mohammed yace "kamar ya?"yace "eh
ba naji Mami tace yau ka zo nan ba?shine kuma dan tsabar kirkin ka ko ka kira ni a
waya ka shaida min za ka zo"murmurshi mai sauti Mohammed yayi yace "sorry nima ban
yi zaton za mu tsaya Maradi ba shiyasa kuma ina cikin sauri ne, Please ni dai tafi
ka kai mata"tsuki Mustapha ya sake ja yace "girma dai ya faɗi"Mohammed dai bai ce
komi ba ya na jin yadda Mustapha ke tafiya da ɗan sauri har lokacin da ya buɗe ɗaki
ya na yi Munat tsawa wacce ke zaune bakin gado tayi tagumi "uwar mi kike tunani da
har ina maki magana baki ji ba?"ya faɗi hakan ya na mai miƙa mata wayar murya na
ɗan rawa tace "wanene?"Mustapha yace "ban sani ba in kun gama ki kai min wayata
ɗaki".
Shiru tayi tana sauraren saukar numfashin shi da ke fita da sauri-da sauri,can ta
nisa tace "hello"ƙyaleta yayi sai da ta sake maimaitawa sannan yace "Mimi naaa"baki
ta turo dan ta gane mai maganar tace "Ni ba Mimi sunana ba"murmurshin gefen baki
yayi yace "to ya kike son nace tunda sunan Mamyna gare ki?" "Sai ka faɗa kamar
yadda kowa ke ce min Munat"ta bashi amsa "na ƙi ɗin,yanzu dai gaya min mi kike
yi?"tace "Komi" "kuma Musto yace ki na tunani?"sai da ta cire wayar a kunne ta
harare shi tace "eh mi?"sai da rumtse ido jin yadda ta bashi amsa gatsal babu
respect amman ya danne zuciyar shi yace "ah babu komi ai na san bai wuce tunanin
sojan ki kike yi ba"shiru tayi kamar ba za tace komi ba sai ta tambaye shi kuma da
"ina hotuna na?ka turo mashi ne?"
"A'a ban turo mashi ba bari na kunna data yanzu na turo"ya faɗa tare da kashe
kiran.Munat da ta iya taro rigima ta hauda connexion ɗin wayar Musto,ba'a ɗau
lokaci ba messages suka fara shigowa nan ta ga hoton Mohammed inda ya ke da kayan
sojoji shiga tayi ta fara buɗe hotunan.
Tana tsaka da kallo appel video ya shigo,ganin Mohammed ne yasa ta ɗauka ta mai
waro ido ganin ba'a ganin komi sai duhu shi kuwa ƙureta yayi da ido ya na kallon
wuyanta wanda ya ke a cike gami da murɗiya har zuwa cikaken ƙirjinta wanda suke dam
kamar za su faso rigar,shatin nipples ɗin ta sun fito sosai kasancewa rigar mai
santsi ce.Turo baki tayi tace "Ni fah ban ganinka ka shiga haske mana ka wani tsaya
cikin duhu kamar mugu ko wani munafuki"dariya yayi a zuci kuwa ƙara jinjina girman
tsiwa irin ta Munat ya ke yace "yanzu Mimi Ni ne munafuki?"murguɗa baki tayi tace
"Ni fah ban ce ba cewa nayi kamar in kuma shine tom..."
"Tom mi?"cewar Mohammed ya na kallonta sarai kasancewar ampoule ɗin ɗakin ba dai
haske ba,cikin tsiwar da ta zame mata jiki tace "ah sai ka faɗi mu ji saboda mu
kiyaye zuwa gaba ko kuma ka miƙa kan ka da hukuma"ta na faɗin hakan ne tana wani
jujuya kai ita duk a tunaninta shi ma bai ganin ta.
Lumshe ido yayi ya jingina da ƙaton dutsen da ya ke bisa a kai yace "Please saka
hijabin ki kar ki ɓallo min ruwa ina zaman zamana sai wani rangaji kike kamar
bishiya"Waro ido tayi tace "wai ka na nufin ka na gani na?"yace "eh mana"ai kuwa ta
shiga bubuga ƙafafu da ƙasa tana kukan shagwaɓa.....

*PAID BOOK NE 500₦/500f ga mai buƙata ya tuntuɓi wannan number* +22795045822


[29/05 à 17:07] MRS SADAUKI 💫: *SOJANA...*💞

*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*

*Matan Sojawa da ƴan matan Sojawa ina kawo gaisuwa*👍🏻

✍🏻
Chamsiya Laouali Rabo

🆓 Page 3-4

Musto ne ya shigo ɗakin ganin shiru-shiru ba ta kawo mashi wayar shi ba,tsayawa
yayi ya na kallonta shi a tunanin shi ko aljanun ta ne suka tashi sai jin murya
Mohammed yayi ya na cewa "Please Mimi ki daina ban so,ki tsaya wuri guda ki nutsu
za mu yi magana"turo baki tayi tace "ba kai ne ba"warce wayar shi yayi yace "shine
yayi uwar mi mahaukaciya kawai dubi yadda kika hargitsa gashin kan ki wajen shirme
sannan wannan rigar maza kije ki cire ta, tunda ba jin magana kike ba ina ga sai na
fara nausar ki"cewar Mustapha ya na mai kashe appel ɗin ya fice ya bar Munat da
haushin katse mata nishaɗi da yayi.
Cike da baƙin cikin ganin Mimin shi da Mustapha yayi ya turo mashi text " miye na
shiga ɗakinta ba tare da neman izini ba ?kuma shine ka amshe wayar ba tare da mun
gama ba mtsw"wani haushi Mustapha yaji ya maida mashi da "uwar mi ta aje cikin
ɗakin da har sai na nemi izini ko ka manta Munata ƙanwa ce gare ni?kuma waya ina ce
dai tawa ce shiyasa na karɓo"Mohammed na karanta text ɗin ya dannawa Mustapha kira
ɗagawa yayi ya na cewa "yane ko ta shafe ka ne mai zuciyar ƙarfe?to in kaji haushi
ka saya mata wayar can kuje kuyi sakarcin ku amman ni ba da wayata ba"a zafafe
Mohammed yace "look Musto bari ganin ina kyaleka ka san ba wani girme min ba ne
kayi sosai balle dan nayi maka rashin mutunci a ga laifina,daga yau dan Allah kar
ka ƙara shiga ɗakin Mimi sai da izini"dariya Mustapha ya sheƙe yace "kaji wani
rainin hankali ni da ƙanwata shine za'a min shamaki to yaro tun wuri ka aje wannan
banzan kishin na ka dan ba zai kai ka ko ina ba"Mohammed yace "na ƙi na aje ɗin
kuma wlh in ba kayi sannu ba sai na zane ka tunda ni ne Chef ɗin ka"murmurshin
gefen baki Mustapha yayi yace "ai sai na rama da ƴar ƙwailar ka na sa ta tsalon
kwaɗo🐸 ka ga kuwa yadda take ƴar lukutar nan za taji jiki"tsuki Mohammed yayi yace
"Allah shirya ka yanzu ƙanwar taka ma sai kayi mata shegantaka?hum ni dai duk ba
wannan ba gobe ka cire kuɗi cikin account ɗina ka saya mata waya wacce ta dace
Please kar kace a'a wannan karon ba zan yi toléré ɗin ka ba dan Mimi ba yarinya ba
ce da za ka hanata riƙe waya"fuska Mustapha ya tamke yace "elle a juste 18ans fah
kuma kake maganar waya haba kafi kowa sanin haɗarin da ke cikin portable gaskiya
ba..."da sauri Mohammed ya katse shi yace "Please ko ƴar ƙarama ce mai touche wadda
zan rinƙa samun labarin ta dai" "naji Sarkin naci mtsw sai da safe ma babyta na
kira na" Mohammed yace "Allah shirya ka mai kwashe-kwashe"bai jira cewar shi ba ya
kashe wayar.

Direwa yayi daga kan dutsen da ya hau dan samun network ya nufi inda suka hahaƙa
rumfunan su na tanti,ɗan gadon ya kakaɓe tare da yin Bismillah ya kwanta.Allah ya
sani shi ya kasance cikaken namiji wanda ƙaramin abu zai tayar mashi da hankali
shiyasa ya ke kiyaye duk abinda zai motsa mashi sha'awa,a wajen aikin su ko magana
bai yiwa mata duk da wasun su suna mugun son shige mashi amman kasantuwar shi mai
ɗaure fuska suke shakkar shi.
Gudun bugun zuciyar banda ƙara hauhawa babu abinda ya ke yayinda duk tsikar jikin
shi ta tashi har wayam ya ke ji a jikin shi nayi,ko kaɗan bai so ya ga Mimi a haka
ba ya san kafin hoton ya ɓace a idon shi sai an kwan biyu.
"Hasbunallahu wani'imal wakil"kawai ya ke maimaitawa ƙasan zuciyar tare da roƙon
Allah ya rage mashi wannan masifar🤭.

A ɓangaren Munat kuwa bayan fitar Musto hararen ƙofa tayi tana cewa "ko ina ruwan
shi da riga ta kawai haka nan sai in yi ta sa manyan riguna kamar wata uwar mata"ta
faɗa tare da cire rigar mai siraren hanunuwa ta saka wata sai gunguni take.
Kwantawa tayi tana mai jin zuciyarta tayi nauyi kamar ta na buƙatar wani abu ko
kuma wani abun ta yayi nisa da ita, numfashi ta ja sosai ta sauke ajiyar zuciya wai
ko ta samu dama amman shiru sai ma tunanin Mohammed da ya faɗo mata a bayyane tace
"mugu shi ma har da wani kallona kamar ƴar gidan su"Mami da shigowar ta kenan kuma
taji abinda Munat ta faɗa tace "wa kenan ?ke yanzu a haka ne zaki kwanta da haske
kamar dangin sheɗan ni na zata ma kin yi barci"ta faɗa tana mai kashe ampoule ɗin
ɗakin.Da sauri Munat ta diro tana ƴar ƙara tace "Wlh Mami tsoro ni ke ji Ni dai ki
bar min ƙwain fitilata"kunna hutar Mami tayi ta girgiza ta fita tana mai cewa "ki
tabbatar kin yi addu'a kafin ki kwanta"da "toh"ta amsa tana mai komawa kan bed ta
ja zanen gado ta rufe har kanta,ji tayi kamar wulgawar wani abu da sauri ta miƙe
zaune tana waige-waige ba ta ga komi ba hakan yasa ta koma ta kwanta, ampoule ɗin
ɗakin ne ya fara ɗokewa ya na dawowa sai yayi fatsee kamar yayi masse.
Addu'a Munat ta fara kafin ta danna suratul Baƙara da ɗan ƙaramin MP3 ɗin da ke
bisa kan gado nan barci yayi awon gaba da ita.

Washegari a gurguje ta shirya ko breakfast ba ta tsaya yi ba ta biya gidan su


Maryam wacce ita ma tuni ta shirya,a bisa hanyar su ne ta zuwa school Munat tace
"ƙawata wai baki san jiya ina zuwa na tarar da mun yi baƙo soja ba?"da sauri Maryam
tace "ke haba?dagaske?in ji dai baki nuna mashi ƙiyayar da kike masu ba a
fili"dariya Munat tayi tace "a'a wlh ya na da kirki da takura har wayar shi ya bar
min da zai tafi sallah kuma da dadare ya kira ni da wayar Musto mu ka sha
hira"Maryam tace "halan son ki ya ke da har zai kiran ki?"hararar ta tayi tace "ke
banza wannan fah COUSIN ɗina ne da baban shi da Mami uwar su ɗaya uban su ɗaya to
miye dan ya kira ni?"Maryam tace"ah na zata abokin Mustapha shiyasa,am ya kamanin
fuskar shi suke ya na da kyau ko kuwa ?fari ne ko baƙi"shiru tayi mata can kuma
tace "uwar shi buzuwa to miye gamin shi da baƙi kuma?Ko ni ai dan na biyo baƙin
Abba ne amma ai kin ga yadda Mami take fara sol ko?"kai Maryam ta gyaɗa mata "to
Moha yafi Mami fari dan in ba gaya maki aka yi ba cewa za kiyi Balarabe ne tsabar
kyau da farin fatar shi uwa uba dogon gashin kan shi wanda ko wata maccen
albarka"wani irin abu ne Maryam taji ya caki zuciyar ta yayinda tsikar jikinta ta
tashi,sak kusan irin mijin da ta ke so cikin rawar murya tace "am ƙawa nace ya na
da saje da geme kuwa?"tsuki Munat ta ja tace "ke kam akwai banza ina soja ina gemu?
sajen dai shi ma ba sosai can ba in da kin gani gwanin kyau"ta ƙarashe maganar tana
sakin murmurshi daidai nan kuma suka shiga layin da zai kai su CSP HIKIMA inda a
nan ne school ɗin su.
Suna shiga direct bakin 3A suka wuce inda mutane ƙwarara ne kawai suka zo,har za su
zauna Maryam tace "am ina zuwa bari na je na dawo"ta faɗa tare da fita ta nufi
direction ba jima ta dawo hannunta riƙe da fararen takardu irin uwanda ake zane da
su.
"Please yi min dessiné ɗin sojan nan na gani,kuma da kayan sojojin nike son ganin
shi"cewar Maryam tana aza takardar bisa table ɗin da Munat ke zaune.
Dariya tayi tana mai fiddo crayon tace "alƙur'an sai kin biya ni na gaji da yi maki
zane"Maryam dai ba tace komi ba sai zaunawa tayi cike da murna.
Kasancewar Munat gwanar zane ce cikin ƙanƙanan lokaci ta zana shi raɗam nan ta
shiga saka mashi couleur irin na tenue soja,sai da ta gama ta miƙawa Maryam tana
murmurshi.
A tsaye ta zana shi hannun shi duka biyun cikin aljihun wandon shi,fafaɗen ƙirjin
shi kuwa galoli ne kusan biyar kan shi sanye da béret rouge wato ja hulla,fuskar
nan a murtuƙe kamar wanda ya ke filin daga yayinda sajen shi ya ƙawata fuskar.
Taɓin da ƴan ajin suke suna cewa "waooo!yayi kyau"shi ya maido Maryam daga duniyar
tunanin da ta lula wai ga ta ita da Mohammed a cikin gidan su na aure har da ƴan
yaran su😱.....

Please in kin karanta kiyi share domin Allah🙏🏻


[29/05 à 17:07] MRS SADAUKI 💫: *SOJANA...*💞

*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*

✍🏻
Chamsiya Laouali Rabo

Page 5-6

Amshe dessin ɗin Munat tayi tace "to bani kaya na cikin ɗaki zan laƙa shi na ga
kamar ya fi ko wane zane da ni ke yi kyawu"marairaice fuska Maryam tayi tace "dan
Allah ƙawata ki bar min kin ga dama tun farko ni soja ke burgewa ke kuma haushi
sojawa ke baki"taɓe baki Munat tayi tace "yanzu duk saboda dessin ne kike wani
kwantar da murya kamar ki na neman gafara ?to na ƙi ɗin yaga shi ma zan yi"da sauri
Maryam ta fara girgiza kai tace "dan Allah kar ki yaga bari na saye in ma ba zaki
bani kyauta ba"ta faɗi hakan tana mai fiddo 1000f cikin sac ɗinta ta miƙawa Munat
karɓar kuɗin tayi tana mai bata zanen.
"Nasara ai ya hana aikin banza ba zan zauna na zana hoton ƙaton banza ba a
kyauta"cewar Munat tana saka kuɗin cikin jakka,hararar ta Maryam tayi tace "wlh ni
*SOJANA* ba ƙaton banza ba ne iyeee sai dai can in Buhari mai shayi ne "dariya
Munat ta gagaɓe da ita tace "yo ni ina ruwana da wani Buhari mtsw can ta matse maku
ke da shi,tunda ni ko abun hannun shi ban taɓa ci ba asali ma saboda shi na tsani
shayi gaba ɗaya"shiru na ɗan lokaci Maryam tayi kafin tace "amman kin san ya na son
ki sosai ko?kuma ban ga abinda ya ke da ba ɗan saurayi kyakkyawa da shi"dundu Munat
ta kai mata ga baya tace "eh yau na san ba ki ƙaunata ace wa na aura?in ce Buhari
mai shayi na bakin school ɗin mu?"ta tufar da yawu ta cigaba da cewa "Allah kiyaye
min"
"Ai sana'a ba ta da kaɗan kuma da ka auri marar aikin yi gwara ka auri mai shayin
ko ba komi ya na da zuciyar nema bai tsaya jiran a bashi ba"cewar Maryam cikin
fushi dan halin ƙawarta ta ya fara bata haushi duk wanda yace ya na sonta sai ta
nemo aibun shi,"ta baya ga wasa kenan wai ihu bayan hari,ke mi zai hana ki aure shi
?ai ina ce ke ma mace ce"cewar Munat tana mai tashi ta barwa Maryam wajen ta sake
wani table tuni kuma malamin da zai fara yi masu cours ya shigo aji.
Karatu ake masu amma sam hankalinta bai gare shi,tunaninta da ruhinta sun tafi gun
mutumen da ke can cikin dokar daji wato Mohammed.Ba ta san ko miyasa ba kawai ji
take zuciyata na yi mata zafi na zanen shi da tayi kuma ta sayar ma ƙawata
Maryam,sam ji tayi ba za ta haƙura ba amshe kayanta za tayi ta mayar mata da kuɗin
ta.
Murmurshi tayi tuno maganar shi ta jiya ```bari Mimi kar ki ɓallo min ruwa```
zuciyarta ta tambaya ko mi ya ke nufi da haka? oho.
Mr Arman wanda tun ɗazu ya ke lura da ita yayi interrogé ɗin ta ya na mai kiran
sunan ta,firgigit tayi tana mai zuba mashi manyan idonta masu kamar madara uwanda
kuma su ne suka fi jan hankalin Mr Arman a tare da ita.
"Quel est la différence entre aimer et plaisir?"rau-rau tayi da ido kafin tace
"banbanci SO da BURGEWA kamar yaya kenan?"ƙureta yayi da ido ta yadda zai isar da
saƙon zuciyar shi cikin sauƙi Allah ya sani saboda ita ne yau ya zaɓi wannan cours
ɗin,cikin cool voice yace "eh shi mu ke son sani"shiru tayi ta ɗaga idonta na wani
lokaci alamar tunani kafin ta saki murmurshi tace "shi SO abota ce in ka na son
mutum har abada son ba zai canzawa ba bima'ana in wani ya son wata zai so ta ne a
duk yadda ta ke ko da kuwa ta canza halaye ko kuma ta samu wata nakasa a jikinta
yayinda shi kuma BURGEWA na ɗan lokaci ne ta yiyu wani na burge ni saboda wani abu
na shi kamar dai ace wata aikin soja na burge ta shiyasa ta ƙulla alaƙa da wani
soja to ka ga duk ranar da abokin nan nata ya bar aikin soja shikenan ya bar
burgeta dama ba shi ne ke burgeta ba aikin sojan ne"tsit ajin yayi kowa na
saurarenta da kallonta ba ma kamar Maryam,Mrs Arman kuwa murmurshi yayi yace "to
wane za ka fi ji a ranka wanda yace ya na sonka koko wanda yace kana burge shi"wani
ɗaga ido tayi🙄 tace "to ai na ma sai an tambaya ba duk wanda yace ya na sonka ai ya
gama maka komi,miye amfanin burgewa tunda ita ta ɗan lokaci ce?"murmurshi yayi mai
kamar dariya dan har sai da fararen haƙoran shi suka bayyana kafin ya bata umarni
ta zauna.
Nan yace kowa ya ɗauki takarda zai masu text akan haka, kasancewar ko wane ɗalibi
ya san Mr Arman na da sauƙin kai ne yasa ba su wani tada hankalin su ba sosai.
Ya na fita Mr ɗin Mathématiques ya shigo shi ma yayi na shi cours ɗin ya fita.
Lokacin cin abinci na yi Maryam da Munat suka fita,Buhari na ganin su ya shiga haɗa
masu indomie da ƙwai sai kallon Munat ya ke wacce ta sha kunu sai wani kaɗa ƙafa ta
ke.
A gabanta ya aje mata plate ɗin yace "Mrs B da fatan an tashi lafiya?ya karatun?"a
taƙaice ta amsa mashi da "alhamdullah"ta jawo plate ɗin ta fara juya cokali
ciki,Buhari bawon Allah kallon ta yayi ya kalli Maryam ya na yi mata signe da hannu
Maryam tace "Mijin bari har mu gama za muyi magana"da fara'ar shi yace "toh bon
appétit"taɓe baki Munat tayi bayan ya fita daga cikin ƴar rumfar da students ke
shiga su ci abinci tace "kin ji kinibibi har da wani turancin ƙarya dan nace yayi
école,wai wace uwar ce ma za ku hiranta naji kina cewa har mu gama?"shareta Maryam
ta fara yi ta far kurɓar tea zuwa can tace "wannan kuma ba matsalar ki ba ce,naji
yau dan rainin hankali a kaina kika bada exemple to miye dan nace ina son
soja?"dariya Munat tayi ta aje cokalin hannunta tace "wlh Allah ne ya so ni ina
fara tunani kika faɗo min a rai sai kuma na tuna zancen Mami na jiya da naji ta na
gayawa Mustapha wai tun ina ƴar ficiciyata Mohammed ke sona ni kuma wlh ban ma san
shi ba lokacin da ya tafi aikin soja ko wando ban fara sawa ba"ido Maryam ta fiddo
tace "wai dagaske ne?to a yaushen ne kika ji Mami na gaya mashi ɗin ke da kika ce
Musto bai zauna gida ba duk wuni jiya?"annurin fuskar Munat ne ya ɗauke tace "wlh
ƙawata jiya ma tsoro aka ta bani sam ban yi barci ba to sama-sama na jiyo hirar ta
su"cikin jimame biyu Maryam tace "kin gayawa Mami kuwa?"kai ta girgiza tace "a'a
kin san fah da zarar na gaya mata wajen granny za'a kai ni kuma ni wlh har yanzu
zuwa tsoron zuwa gidanta ni ke da ita karan kanta saboda tsafi da borin da
take"Waro ido Maryam tayi cike da mamaki tace "wai ki na nufin har yanzu granny ba
ta bar bori ba?"baki Munat ta taɓe tace "hum bari ma za tayi kenan?ai mutuwa ce
kawai za ta rabata da harakar tsafi kin san jajayen buzaye da kafiya babu irin
yadda Uncle Harun bai yi ba dan ta bari amman ta ƙi ya wai neman kuɗi ne ta ke kuma
ba za ta bar gadon gidan su ba"suna tsaka da hira ko abincin ba su gama ci ba aka
buga sonné na komawa aji.

Munat na dawowa daga school agajiye ta shigo gida,wanka ta fara yi sannan ta fito
zuwa falo inda Mami ke zauna tana kallo."Washhh Allah na gaji wlh mi aka dafa
Mami?"cewar Munat tana mai zaunawa bisa capet kafin Mami tayi magana Mustapha da ke
kwance bisa salon yace "to acici kazar gidan gona kullum ci ko gajiya ba kiyi dubi
yadda kika zama wata ƙatuwa kamar wace za ta tafi kokowa"turo baki tayi gaba tace
"to haka nan zan zauna babu cin abinci?"hararar ta yayi tare da cillo mata kwalin
waya ƙirar itel yace "je ki ta ci in abun ƙwarai ne in kika kasa tashi ai sai a
rinƙa tura ki cikin baro"ita dai bata kula shi ba sai murna ma da take ganin ya
bata sabuwar waya.
Kunna wayar tayi dan tuni an saka Batur da sim "na gode Babban yaya"baki ya ja yace
"in kuma na ga kin cika sakarci amshe ta zan yi can ya rinƙa kiran ki da wayar
Mami"ba tare da tace mashi komi ba ta fara latsa wayar video da waƙoƙin da ke cikin
memoryn ta fara kallo har sai da ta gaji sannan ta dakata caji.
Da dadare misalin ƙarfe tara kira ya shigo wayar,ba tare da yin tunani ba ta ɗauka
tana mai cewa "hello?"kai ya girgiza yace "Mimi sallama ya kamata kiyi ba ɗabi'ar
turawa ba"in ba dan taji ya kirata da sunan da shi kaɗai ta san ya na kiranta ba da
sam ba za ta gane ko wanene ba saboda yadda Muryar shi ta ɗan shaƙe "mi ya same ka
ne naji muryar wata kala?"abinda tace kenan "wata kala kamar ya?"Mohammed ya faɗa a
ɗayan ɓangaren tace "eh babu sugar kamar ta wani ɗan daba ta zama ƙatuwa kuma a
shaƙe kamar munafiki"ido ya lumshe ya na saurarenta wai shi Mohammed shine ake ma
tsiwa ana gaya mashi magana?kuma ƴar ƙaramar yarinya wacce ba ta wuce ya murjeta ba
kamar kiyashi amman so hana ganin laifi, murmurshi kawai yayi yace "banda lafiya ne
mura ta kama ni"taɓe baki tayi tace "ashe abu na gida makaɗi da ya yaje gidan
mabushi,to ai mura ita da buzaye kamar Ɗan juma da Ɗan jummai suke"cikin kasalar da
ta saukar mashi sakamakon jin muryar ta kaɗai da yayi yace "Mimi ba ki tausayina?
kece fah silar ciwona dan da ba ki sani yin wankan asubahi ba da mura ba ta kama ni
ba"a mamakance tace "Ni kuma?na kira ka koko tada ka nayi nace Moha tashi kayi
wanka?"dafe goshi yayi dan ya ga har yanzu da sauran ƙurciya ga Munat yace "to
mafarkin ki nayi"waro ido tayi tare da rufe fuska wannan karon kuwa ta gane mi ya
ke nufi.
"Kin yi shiru" "to mi zan ce?"ta bashi amsa yace "Mimi na wlh ina cikin wani hali
na buƙatuwa ya kamata ki tausaya ki karɓi tayin soyayyata ina zuwa a yi mamu aure a
wuce wurin,dan ina jin a jikina ba zan iya haƙurin rashin ki kusa da ni ba"wani abu
ne Munat taji ya tsarga mata tun daga tsakar kai har cikin tafin ƙafa,murya na ɗan
rawa tace "Moha kayi haƙuri ni na tsani soja ba zan iya auren ka ba"ido ya rumtse
da ƙarfi ka azabar da ya ke ji a mara ga wata kuma tana sukar shi da kalaman ta.
A wahalce yace "wlh Mimi ke ce rayuwata in babu ke babu ni in dai zaki aure ni na
yarda zan aje aikin soja"Waro ido tayi ta shiga girgiza kafin ta kai da cewa wani
abu network ɗin wajen su Moha ya yanke......

*PAID BOOK NE*


[29/05 à 17:08] MRS SADAUKI 💫: *SOJANA...*💞

*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*

✍🏻
Chamsiya Laouali Rabo

🆓 7-8

Wani irin baƙin ciki ne ya ziyarci zuciyar Mohammed bayan ya gwada kiran Munat yafi
a ƙirga ana maido mashi kiran alamun babu réseau,a ƙarshe ma duka Sim ɗin suka
sauka.
Ba dan ya so ba ya sauka daga kan dutsen ya nufi makwancin shi,kwantawa yayi ya na
mai dafe zuciyar shi wacce ke barazanar faso ƙirjin shi ta fito tsabar son da ya ke
yiwa Munat da kuma muradin kasancewa da ita wanda ya ke ji kusan kullum a ko da
yaushe kuma.
Ajiyar zuciya ya sauke yace "ita ce ƘADDARA ta tabbas son Munat JARABTA ne(Haj
Maryam Sakatare)in ba haka ba tabbas ba zan susuce har haka ba a kan ƙanƙanuwar
yarinya"Omar da ke kusa da shi yace "wai akan wa kake magana koko baby Angel ɗin
ka?"shiru Mohammed yayi sam bai san a fili yayi maganar ba da "um"kawai ya amsa
mashi, Omar ya cigaba da cewa "to ba cousine ɗin ka ba ce kawai ka shaidawa iyaye a
san nayi ba wai ka zauna dakon son yarinya ba tun ta na cikin tsumman goyo amman ta
zo ta na haɗa maka café ba(tension😂)"cikin fushi Moha yace "wai ina ruwan ka ne?ba
café ba in ta na so ta haɗa min har da Lipton ai ni zan sha ba kai ba,ya fah ka
mata ka shafawa Mimita lafiya kusan kullum sai kayi zancen ta wanda ban san dalili
ba kawai ka sata faɗuwar gaba babu gaira babu dalili"dariya Omar yayi yace "to ai
doli na sa ma ido saboda ni kuke cutarwa a kullum ku na maida min aiki baya,sai ka
kusan ka warke kuma sai kace min marar ka na ciwo har da bay..."dundu Mohammed ya
kai mashi ga baya yace "Allah shirya ka wlh ai ba yin kaina ba ne kuma wannan shine
cikar mazantakar wasu a shekara ma ba su sanin wane matsayi suke namiji koko mata
maza"Omar yace "ai ba lalle sai ka sani ba kai ma abinda ya sa ni ke sani dan babu
yadda ka iya ne na zamo likitan ka sannan jaraba ka tayi yawa ko hoton wannan
mitsitsiyar yarinyar ka kalla shikenan har ka shiga shauƙi"harar shi yayi duk da ya
san ba zai gani ba kasancewar dajin da suke babu haske sai duhun itace "kai tafi
can ɗan iska ni ban iya maka bar ni ma da abinda ya sha min kai"cewar Mohammed ya
na komawa luf kan gado ya kwanta Omar kuwa cewa yayi "ka sa minjaye dan wani wa kai
kuma gatanar gizo ai ba ta wuce ta ƙoƙi dama na san an runa wai an saci zanen
mahaukaciya ko da na ga ka tafi neman network na san kai ma sai ta haudo ma naka"da
ƙafa Mohammed ya ɗan shure shi yace "arrr!to ni can na nufa ba kawai haushi ni ke
ji réseau ya yanke a daidai wurin da ni ke buƙatar jin amsa"taɓe baki Omar yayi
yace "Allah ya ƙara mayen appel"Mohammed bai tanka shi ba sai ma tunanin da ba zai
fishe shi ba ya shiga yi wato na Munat.

A ɓangaren Munat kuwa cilli tayi da wayar tana zumɓuro baki ita a tunaninta haushi
ya ji dan tace ba ta son shi,a fili tace "A'i ta gaida A'ishah ni gaba ta kai ni
gobarar Titi, Allah na tuba na rasa wanda zan aura sai buzu buzun ma fari kuma soja
tab ba da ni ba.In haka ta kasance ai naji kunya kuma zan sha iskanci gun Maryam
dan haka ban so aka kas..."motsin da taji mai haɗe da ƴar buɗa yasa sauran maganar
laƙewa cike da tsoro ta fara waige-waige amman ba ta ga komi ba.
Toilet ta ke so ta shiga ta ɗauro alwala ta kwanta amman ta kasa shiga tsabar
tsoro,cikin ƙarfin hali ta buɗe ƙofar toilet ɗin tana shirin shiga taji ta taka
wani abu mai taushi da kuma shegen sanyi wani uban ihu tayi wanda yasa Mami da ke
shirin zuwa ɗakinta yin saurin shigowa.
Wani tsalle Munat tayi da zumar ta dira bisa gado aka samu akasi ƙafar ta gaubce ta
faɗi ƙasa,ɗaga ƙafar da tayi ya ba ƙaton kwaɗon🐸 damar tsallawa ya shige toilet.
Ta miƙar da ita tana cewa "subahanallah Auta ba ki ji ciwo ba?"kuka ta fashe da shi
ta faɗa jikin Mami daidai nan Mustapha ya shigo ya na tambayar lafiya?da hannu
Munat ta nuna mashi ƙofar toilet.
Shiga yayi can ya tsinkayi kwaɗon sai tsalle ya ke ya na hawon gini,tsuki yayi ya
fita ya ɗauko abun kwasar shara ya ɗauke kwaɗon.Ihu Munat ta sake yi ganin kwadon
ya ƙuro mata ido ya na kallo daga cikin pelle,bubuga bayanta Mami tayi tace
"shikenan dai yanzu an fitar da shi,ko daga ina ma ya shigo?"cikin kuka tace "Mami
ki tafi da ni ba zan iya kwana a nan ba tsoro ni ke ji"Mustapha da ya dawo yace
"uwar mi za kiyi a can part ɗin Mamin?ina ce dai wajen ƙiriniyar ki kika kwaso shi
a waje in ba haka ba mi zai kawo kwaɗo har ƙurya ɗaki?"Mami tace "nima abinda nace
kenan ƙila cikin babouche ɗin ta da suka kwana waje ya shige ita kuma ta kwaso su
ba tare da ta duba ba"banda shasheka babu abinda Munat ke yi.
Wayar hannun Mustapha ce ta ɗau ruri ya ɗaga ya na gaishe shi can kuma yace "lafiya
lau Daddy ga ta ma kusa da ni kwaɗo ne ya shigo ɗakinta shine fah take wannan
kukan"a can ɓangaren Daddy yace "haba shiyasa naji duk hankalina ya ƙi kwantawa
ashe autata ke kuka bani ita naji gaskiya kwaɗon nan bai gyara min ba har zubar da
hawayen Auta"cikin jin haushin banbancin da Daddyn nasu keyi tsakanin su yace "ai
ta na jin ka ba sai na bata da hannun ta ba a yadda ta firgice ai sai ta sakar min
waya ƙasa"hawaye ta goge tace "Daddy nima ai nayi sabuwar waya ka kira bisa layina"
hararar ta Mustapha yayi ya na mai kashe kiran ya turawa Daddy number ta kamar
yadda ya buƙata.

*ASALIN LABARIN...*

Attahir da Fadimatu sun kasance jajayen buzaye na usuli ,auren haɗi (na gida)aka yi
masu.
Allah ya azurta su da ƴaƴa biyu mace da namiji,Alzuma shine babba sai ƙanwar shi
Agaisha.Sun taso cikin so da ƙaunar junan su sai sun tsani abinda suka tashi suka
ga iyayen su na yi wato harakar tsafi da bori,babu yadda Alzuma bai yi ba ganin ya
rusa wannan baƙin gado da iyayen shi suke ikirarin gada su ka yi amman abu ya
cuttura tun abun na damun shi har ya kai ya raba kan shi ya bar zancen.
Lokaci guda aka yi bikin su na aure shi da ƙanwar shi,inda Alzuma ya auri farar
buzuwa mai suna Maimuna yayinda Agaisha ta auri bafulatnin Zinder mai suna Illiyas.
A shekarar farin Allah ya azurta su da samun ƴaƴa maza Agaisha ita ta fara haihuwar
Ɗanta Mustapha sannan Maimuna ta haifi Mohammed wanda bai wuci wata biyu ba ne a
tsakanin su kuma tun daga wannan lokacin haihuwa ta ɗauke masu su duka biyun.

Kasancewar Alzuma mai mugun son yara ne yasa shi ganin likita an tabbatar mashi da
lafiyar su lau ƙwan haihuwar shi ne sam ba zai iya fécondé ba,sosai hankalin shi ya
tashi wanda har ya taɓa lafiyar shi kusan kullum cikin tunani ya ke ko barci bai
iyawa.
Tsakar dare kamar wanda aka dadaɓa haka ya tashi daga barcin da ya ke ya fito
waje,suratai ya fara ji a cikin ƴar buƙar da Attahir ke tsafin shi kamar zai wuce
sai kuma yaji ya na ambaton sunan shi ```Ta yaya za ku lalata ƙwan haihuwar Alzuma
duka bayan ba haka mu kayi da ku ba?``` cikin wata murya marar daɗin amo aka bashi
amsa ```dama ƘWAI ƊAYA (Haj Maryam Sakatare ku nemi na ku kar a baku labari)kawai
mu kayi alƙawarin za mu bar mashi shi ma ɗin saboda a samu magaji ne kuma ga shi
nan an samu``` cikin ɓacin rai Attahir wato mahaifin Alzuma yace ```kar ku yi min
haka kar ku cutar da jinina ku daina...``` kutso kan da Alzuma yayi cikin bukar ne
ya hana shi ƙarasawa a take kuma hayaƙin da ya cika wata ƴar ƙwarya ya shiga
ɓacewa,wata irin maƙura Alzuma ya yiwa mahaifin shi ya kamo maƙogwaron shi ya riƙe
nan idon Attahir suka firfito tare da kafewa .
Alzuma bai sake shi ba sai da yaji zuciyar shi ta daina bugawa lumfashin mahaifin
shi ya tsaya cak,nan ya faɗi ƙasa babu rai.
Ko da gari ya waye Maa (mata gun Attahir uwa ga su Alzuma da Agaisha)ta fito ta
nufi bukar tsafin mijinta dan tun a daren jiya aljanun da ta ke biya na bori sun
gwada mata mutuwar Attahir,kuka ta fasa tana kiran sunan Alzuma.
Maimuna ce ta fito da gudu jin kururuwar Maa tare da maganganu maras daɗin ji,tsaye
tayi turus gaban gawar sirikin nata wadda Maa ta jawo zuwa waje.
Kawar da ido Maimuna tayi saboda gawar babu kyawun gani kafin ta fashe da kuka tana
kiran sunan Alzuma amman shiru ya ƙi fitowa.
Alkaba'in da Maa ke yi inda ta ke cewa "yadda aka tarwatsa farin cikina nima sai na
tarwatsa farin cikin duk wanda ya kashe ka mutum ko aljan,ga shaida nan ina gani
cikin idonka ba mutuwa Allah da Annabi ba ce kayi"wannan zantuka karaf suka shige
cikin kunnen Alzuma da fitowar shi kenan idon shi duk sun kaɗa sun jajur kamar
barkono tsabar baƙin ciki da takaici da kuma raɗaɗin da zuciyar shi ke yi.
Ɗagowa Maa tayi daga jikin gawar ta dubi Alzuma tace "sun kashe shi ni kuma na
ɗauki aniyar *ƊAUKAR FANSAR RUHI*(My next novel in shaa Allah)yadda ya bar duniya a
tozarce sai na aika duk uwanda suka kashe shi lahira kuma daga yau na ɗauki kambun
sarautar tsafin koko ka na so na baka ?na san kai ma ruhinka ya cika da muradin
kashe mahaifin ka"Waro jajayen idon shi yayi ya na kallon Maa ya nuna kan shi yace
"Ni?tsafi?a'a har abada ke ma kar ki fara har borin barin shi za ki yi tunda ba
aikin Allah ba ne".......
[29/05 à 17:09] MRS SADAUKI 💫: *SOJANA...*💞

*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*

✍🏻
Chamsiya Laouali Rabo

🆓 9-10

Kafin Maa ta kai da cewa wani abu tuni Alzuma ya fice daga gidan,duniyar ya ke jin
ta na wani juya mashi ga wani irin tsanar garin Agadez da yayi.
Agaisha kuwa Mohammed aka aika gidan ta ya shaida mata rasuwar mahaifinta,cikin
kuka ta shigo gidan wanda alokacin ƴan uwa da maƙwabta har sun cika shi.Har aka
kaudo Attahir Alzuma bai dawo gida ba,da yawan mutane sun zata shock ɗin mutuwar ne
ya sa shi barin gidan babu kamar labarin da Maa ke ta faman gayi tsabar shock da
yadda mutuwar ta shigi Alzuma ya kasa kuka sai idon shi da suka yi ja kamar
garwashin huta.
Ta na tafe tana tuntuɓe saboda rashin ganin da ta ke yi da kyau har ta zo bayan
gari,a zaune ta tarar da Alzuma ya curawa waje guda ido.Kallo guda za ka yi mashi
ka gane zuciyar shi cike ta ke da ƙunci, cikin yaren buzanci Agaisha tace "ya kai
Yayana ka sani mutuwa rigar kowa ce,duk mai rai sai ya ɗanɗana ta.Miye ribar ka da
za ka ƙaurace kai ɗaya ko sallatar gawar mahaifin ka ba ka zo an yi da kai ba?ka
san irin tashin hankalin da Maa take ciki kuwa?miyasa kake son ƙara mata
wani?"tunda Agaisha ta fara magana bai ɗago ba sai da yaji ta tsaya sannan ya ɗago
kan shi ya watsa mata jajayen idon shi wanda dan firgicin ganin su sai da yasa
Agaisha yin baya za ta faɗi tare da dafe ƙirji.Miƙewa yayi tsaye ya wani jawota ya
na jijigata yace "azzalumin kike so na sallaci gawar shi?mashiriki munafiki wanda
bai san darajar kan shi ba,wanda ya bayar da ƙwan halitta ta ga dodon tsafinshi shi
kike son na sallata?"ido Agaisha ta fiddo cike da tsoro maganar Yayan nata ya kusan
sa zuciyarta ta buga,baki na ɗan rawa tace "ka na nufin kai ma shine sila?"sakinta
yayi ya juya mata baya yana mai dafe kai da yarfe hannu, muryar Agaisha yaji ta na
cewa "nima ban taɓa tunanin Baa (Attahir mahaifinta)zai iya cutar da ni ba sai
gashi lokacin da mu ka tafi Zinder wani malami ya tabbatar min duk avortement
(zubewar ciki,ɓari)ɗin da ni ke to da sawar hannun wani mafi kusanci da ni,na je
nayi tunani cikin dangin mu wa ke haraka da aljannu"ta na kawowa nan ta fashe da
kuka,Alzuma da ya juyo ya na kallonta yace "to ya aka yi kika san da Baa
ne?"tsagaita kukan tayi tace "mafarki nayi wani aljanni zai zaƙulo ɗan cikina Baa
na girgiza mashi kai amman bai fasa ba sai da ya jawo cikin jikina ina farkawa kuma
na ga jini duk ya ɓata bed"tun daren jiya zuwa yau bai ji zuciyar shi ta karye ba
sai yanzu da yaji hawaye na bin kuncin shi.
Cikin murya ta mai kuka yace "wane irin uba Allah ya bamu?miye amfanin shirka cikin
rayuwa ?duk mai bin doguwa tabbas ya san doli ta buƙaci jini,yanzu ya kike gani wa
za mu tai mu gayawa wannan mugun abun ?"kai Agaisha ta girgiza tace "a'a Yaya
wannan ai SIRRIN MU(Nimcyluv ku je ku nemi na ku kar a baku labari)ne babu wanda ya
cancanci jin haka sai Maa ita kuma a yanzu idonta ya rufe da ɗaukar fansa ko mun
gaya mata ba za ta dubi lamarin ba sai ta cika alƙawarin ta na kashe wanda ya kashe
Baa"shiru Alzuma yayi ya na neman mafita can dai ya ce Agaisha ta koma gida.
Sai bayan sallah magrib Alzuma ya koma gida,ɗan Ɗan shi guda tilo Mohammed ya zauna
ya na kallo kamar wani tv wanda shi kuma sam bai san ya na yi ba karatun alƙur'anin
shi kawai ya ke,shekarun shi goma sha ɗaya a duniya amman ya hardace alƙur'ani mai
girma wannan shi ne ɗaya daga cikin baiwa Mohammed.
Bayan shekara guda
Tuni Maa ta zama ƙasurgumar matsafiya harakar bori kuwa babu abinda ya rage sai ma
gaba da tayi an naɗa ta Iya ta garin Agadez wanda hakan ya sa ta koma gidan sarki
da zama,dama da biyu ya naɗa ta Iyar dan ta rinƙa yi mashi aiki ne yadda ya kamata.
Lokacin da Agaisha ta gano tana da shigar ciki ta shaidawa mijinta nan ya tashi
tsaye wajen addu'o'i da rabawa malumai kuɗi,sosai aka yi yinƙurin zubda cikin kamar
kullum sai dai babu hali saboda matakan tsaron da aka sawa cikin.
Watan haihuwarta na tsayawa ta samu ƴarta mace,saboda ƙaunar da Mohammed yayi ta
nunawa jinjirai yasa aka bashi zaɓen suna.
Maimunatu ya bada wato sunan mahaifiyar shi sai dai su suna kiranta da Munat
yayinda Mohammed ke ce mata Mimi.
Mustapha da Mohammed sun kasance aminnan juna tun yarintar su,komi na su a tare
suke kasancewar ra'ayin su kusan iri ɗaya ne da na juna.
Mohammed na da 17ans ya tafi aikin soja a lokacin kuma Munat na da biyar a duniya.
Tun da ya tafi bai dawo ba sai da yayi 5ans a lokacin har ya zama ɗan saurayi,zuwan
shi da tenue ya sa Mustapha ma yaji ra'ayin tafiya soja bai wani ɓata lokaci ba ya
haɗa takardun shi cikin ikon Allah kuma ya dace.
Munat kuwa tunda ta ƙyallara ido ta ga Mohammed cikin kayan sojawa taji ta tsani
kaki ba ma kamar yadda Mohammed ke takurata ya na punir ɗin ta in tayi laifi
mafarin ƙiyayar Soja kenan a cikin zuciyar Munat.
Shi ya na sonta ita kuma ta tsane shi ko kaɗan ba su shiri,a duk lokacin da yace
zai ɗaukar ta hoto kuwa ta aniya kuka kenan.
Ana haka Daddy ya samu canjin wurin aiki Maradi,sosai Munat taji daɗin haka za ta
rabuwa da ƙaya😅.
Tunda Mohammed ya koma gun aikin shi bai da aikin yi sai kallon hotunan Munat,a nan
soyayyar ta tayi gini tare da toho cikin zuciyar shi.Sau tari Omar ya kan tambaye
shi mi ya ke yiwa dariya a duk sadda ya ga ya na manipuler portable sai dai yace
mashi ba komi,yawan tambayar shi da Omar ke yi yasa ya nuna mashi hoton Munat cikin
mamaki Omar ya tambaye shi "to mi kake yiwa dariya a nan?"yace "rigimamar Black
Baby uwata buzuwa amman ta wani biyo babanta salesalen ta haifo min yara masu kama
da ita"Omar yace "dan ba ka san sirrin da ke ga Baƙar mace ba ne shiyasa,amman mu
likitoci mun fi son baƙa dan fararen nan ragwayi sun fi yawa"shiru yayi ya na
nazarta maganar shi kafin yace "kai ya aka yi ka sani?"harar shi Omar yayi kawai.
Tun daga wannan rana Mohammed ya kan yi zaune yayi ta tunanin yadda rayuwar su za
ta kasance shi da Mimin shi in ta girma,wannan tunanin shi yayi mashi babba illa ya
haifar mashi da mahaukacin sonta da muguwar sha'awar ta, kasancewar Omar likita ne
yayi saurin gano matsalar sosai ya ke bashi shawara ya rage tunaninta tunda ya san
hankalin shi na tashi shi kuwa Mohammed yayi nisa ba ya jin kira.
Tun komawar su Maradi ta mance da wani Mohammed dama ba kasau ta ke riƙe abu ga
kwanya ba,haɗuwar ta da Maryam ne wanibi ta kan ji kamar ta san wani soja saboda
yadda Maryam ke yawan ambaton soja na burgeta shi ya ke ƙarawa zuciyarta tsanar duk
mai aikin shiyasa ko Yayanta Mustapha ba wani shiri su ke ba sosai.
Lokacin da ta tarda Mohammed gidan su sosai tayi ƙoƙarin tuna inda ta san shi amman
ta kasa saboda ko Vacance ta tafi Agadez har ta dawo bai taɓa zuwa ba.

*Cigaban labarin...*

A shagwaɓe ta ke yiwa Daddy bayanin yadda ta taka kwaɗon sai wani goga ƙafar take a
drap tana jin kamar yanzu ne ta taka shi,"Auta ki rinƙa kula da addinin ki kin ji
ko?ki yawaita addu'o'i sannan MP3 da na baki ya zamana kullum a kunne ki bar kashe
shi ko da kuwa za ki fita ne"a shagwaɓe tace "Daddy ni fah mantawa ni ke shiyasa
sai in zan barci kawai ni ke kunnawa"Daddy yace "to daga yau kar ki sake mantawa je
ki kwanta bn8".
Mami da ke zaune ta na sauraren su ta sauke ajiyar zuciya tace "Auta ki yi yadda
baban ki yace,sai da safe bari ba tafi naji wayata na ringing"da sauri Munat ta
sauka daga gadon da zumar bin ta sai dai ƙafa tace ban san wannan ba,ƙara ta saki
tace "Mami ƙafa ta "duba ƙawa Mami ta fara da ta taɓa sai Munat ta saki ƙara.
"Innalillahi ina ga gudun gocewa ce kika yi Auta bari na kirawo Mustapha"cewar Mami
ta na mai ƙwala kiran shi.
"Mami a bari har gobe yanzu ina zan samo mai ɗori cikin wannan daren?"kuka Munat ta
fashe da shi hakan yasa Mami ta fatattaki Mustapha ala doli ya fita ya nemo maɗori.
Sai da Mustapha ya riƙe ta sosai sannan aka samu aka ɗora ta ashe cirar nama ce
tayi.
Washegari shiru-shiru Maryam na ta jiran ta har 7h30mn amman babu alamar ta.
Da sallama ta shigo gidan,bayan ta gaishe da Mami ne tace "ina Munat ko har ta tafi
ne?"daga can daƙin tace "ƙawa wuceke ga ni nan zaune babu ƙafa ɗaya"Mami tace "to
kin ma ji ta can ashe ta farka".
Cike da jimame Maryam tayi mata sallama ta wuce école, direction ta fara shiga ta
shaida masu Munat ba ta da lafiya.Ta na fitowa ta ji Mr Arman ya kirata daga bayan
ta,dawowa tayi tace "bonjour Mr"ba tare da ya amsa gaisuwar da tayi mashi ba yace
"Mi ya sameta?"cikin rashin fahimta tace "wa fah?"fuska ya tamke yace "Muna"a zuci
tace "ka ji wani sabon kiciyi Maimuna ce ta koma Muna?"a zahiri kuma cewa tayi
"gocewa tayi a ƙafa jiya da dadare"
"Ok zuwa 10h ki zo nan administration"bai jira cewar ta ba ya koma taɓe baki tayi
ta wuce a classe nan ma sai da aka yi ta tambayar ta.

Kamar yadda Mr Arman ya buƙata haka ta nufi direction,tun kafin ta ƙaraso ta


tsinkaye shi daga nesa sai karkaɗa key ɗin mota ya ke.Fuskar nan tamau ya amsa
gaisuwar da ta sake yi mashi kafin ya nuna mata motar shi yace "gidan su za ki kai
ni"ba tare dace komi ba ta nufi motar har za ta buɗe baya taji muryar shi ya na
cewa "gaba za ki shiga"ba ta musa ba ta shiga zuciyarta na ɗan bugawa ganin duk
students ɗin da ke waje sun zuba mata na mujiya.
Sai da suka hau kan titi sannan ya tambaye ta wani waje zai,da ta faɗa mashi sai
yace "ashe nan kusa ne"tace "eh babu nisa a ƙafa ma ana iya zuwa"babu jimawa suka
zo ƙofar gidan su Munat,Maryam ta fara shiga ta shaida zuwan malamin nasu kafin
tayi mashi iso.
Zaro ido Munat tayi a zuci ta ke cewa "ashe dagaske Mr Arman ne na zata wasa Maryam
ke yi min"sunne kai tayi ta na amsa tambayar ya jikinta da ya ke,Mami ce ta kawo
mashi ruwa Maryam ta karɓa ta tsiyaya mashi.Ya na shan ruwan ya na kallonta ta
ƙasan ido,kallon tsaf ya ke yi mata ya na ƙarewa ƙirar jikinta kallo a take ya ji
sonta ya ƙara shiga zuciyar dan can da hijab ne ya ke ganinta yanzu kuma ko ɗan
kwali babu kanta gashin ta wanda ya sha gyara sai ƙyalli ya ke ga wata farar riga
da ta sa marar hannu wacce ta fidda duk shap ɗin jikinta.Ko kaɗan zama da ƙananun
kaya bai damun Munat ita babu ruwan ta da wani ɓoye kanta muddin dai cikin gida
shiyasa ba ta wani damu ba dan Mr Arman ya ganta a haka.
Ƙwarewa yayi nan ya shiga tari sakamakon jikin Munat da ya motsa wajen ta zuɗa dan
gyara zaman ta,saurin kallon shi tayi suka haɗa ido gabanta ya faɗi ganin wasu
abubuwa na yawo cikin idon Mr Arman ga wani abu da taji ya na janta daga idon
nashi.Sauke kanta tayi ƙasa ta na wasa da yatsun hannunta yayinda Maryam kuma ta
fice daga ɗakin dan tuni ta karbo jirgin Mr Arman.
"Munaaa?"ya faɗa lokacin da tarin ya lafa,wani irin yammm taji yanayin yadda ya
kirata ɗin tace "uhum"ba tare da ta ɗagon ba dan zuciyarta banda bugawa babu abinda
da take.
"I love You"da sauri ta ɗago ba tare ta shirya ba kai ya jinjina yace "Yes je
t'aime Muna"bai jira cewar ta ba ya fita waje.
Mami tace "an fito ko?to Allah saka da alkhairi"murmurshi yayi yace "ba komi"signe
ya yiwa Maryam hakan yasa tayi saurin bin bayan shi.
Mota ya buɗe ya miƙa mata wasu ledodi tare da 10.000f yace ta kaiwa Munat kuma tayi
sauri ya na jiranta.
Wasu hawaye ne suka fara zarya kan fuskar ta wanda ta rasa na minene na murna
abinda ta daɗe tana jira daga gare shi?koko na tausayin Mohammed da ba ta so kuma
lokacin barin shi yayi?.
A haka Maryam ta shigo ta sameta,baki ta taɓe tace "shagwaɓar ce ta tashi to Allah
kyauta,ga shi dai in ji Mr"tana ajiye mata ta fito da ɗan sauri.

Mami kuwa sai albarka ta ke sawa Mr Arman ta na ganin yin haka da yayi alamu ne na
rashin girman kai ne Malami ya zo ganin ɗalibar shi kuma har da kawo baƙar leda
😹.Mami ta tambayi Munat "kukan mi kike Auta?"tace "ƙafar ce naji kamar ta ɗan riƙe
amman da dama barci zan yi"ta faɗa tana rufe ido Mami kuma ta nufi kitchen dan
cigaba da girki.Number Mohammed ta shiga gwada kira amman shiru appel ɗin bai zuwa
haka ma text,cike da jin haushi tayi cilli da wayar ta shiga tunani Mr Arman wanda
tun ranar da ta ƙyallara ido ta ganshi taji tana son shi amman irin kunya ta ɗiya
mace yasa ta bar sirrin a zuciyata ba tare ta bari kowa ya gano hakan ba......
[29/05 à 17:09] MRS SADAUKI 💫: *SOJANA...*💞

*FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS*

✍🏻
Chamsiya Laouali Rabo

🆓 11-12

Cike da nishaɗi ya ke ciyar da ita da lafiyayun kayan marmari,a shagwaɓe cike da


yanga Munat ke guntsirar pomme🍏 ɗin da Mr Arman ke bata a baki ya wani zuba mata
tsumamin idon shi masu kama da na mashayin giya.
Kawar da kai gefe tayi alamun ta ƙoshi,cikin cool voice yace "Please Muna ki ƙarasa
wannan daga shi shikenan"kai ta girgiza tace "haƙora na sun yi ciwo wajen tauna shi
bari ni na huta"jin haka yasa Mr Arman guntsirar pomme ɗin ya fara tauna shi a
bakin shi kafin ya nufi na ta bakin.
Lumshe ido tayi ganin ya zuro halshen shi zai kai cikin bakinta zumar ya bata aple
ɗin da ya tauna,bakin shi bai ƙarasa kaiwa ba taji saukar murya Mohammed ya na
aikawa Mr Arman ashar tare da ture shi ya faɗi ita kuma ya finciko ta ba tare da
yayi la'akari da ciwon da ta ke da a ƙafa ba ya miƙar da ita tsaye ya na mai
sharara mata wani kurman mari.
Ihu Munat ta saki a zabure kuma ta farga daga mafarkin da ta ke,baki ta turo tace
"maƙetaci har da wani mari na"sai kuma tayi murmurshi tuna yadda suke shan love ita
da Mr Arman.Ledar da Maryam ta kawo ta buɗe nan tayi arba da fruits, pomme ta ɗauka
ta wanke ta fara ci sai lumshe ido ta ke irin ala doli imagine take Mr Arman ne ke
bata a baki😏.

Ɓangaren Mohammed kuwa zuciyar shi ke ta bugawa tun jiya da dadare ya kasa tsaye ya
kasa zaune, training duk sauran sojawan su ke saboda nan da wani ɗan lokaci za su
ƙara gaba amman shi sam nutsuwar shi ba ta gare shi.Omar ya nufo shi ya na cewa
"har yanzu wayar ba ta shiga ba Sarkin naci?na san muddin ba ka kira ta ba haka za
ka cigaba da zama kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki"Mohammed yace "ban sameta
ba kuma ji ni ke kamar wani mumunan abu na faruwa"ya ƙarashe maganar kamar zai yi
kuka,jinjina kai Omar yayi yace "yanzu akan mace ne ka dawo haka kamar ba namiji
ba? Mohammed ka na cikin hankalin ka kuwa?ka ga wajen da zamu wuri ne mai matuƙar
hatsari gwara ka aje hankalin kayi aiki mai kyau daga baya kayi tunanin nata"kallon
ba ka da hankali ya ke bin shi da shi yace "ita ɗin rayuwata ce babu yadda zan samu
nutsuwar ruhi muddin ban ji halin da ta ke ciki ba"ya na gama faɗin haka yayi gaba
ya bar Omar sake da baki bai taɓa tunanin Mohammed ya zauce har haka ba.Mutumen da
in ya ji maganar yaƙi musamman irin mai haɗarin nan har jikin shi ke mazari tsabar
jarumta da son aikin shi amman akan mace ya wani share sai tunani ya ke alhalin ya
san za su fita aiki?gwabran numfashi ya sauke ya na yiwa abokin shi addu'ar samun
sassauci.
Yau ta kama sati guda kenan da katsewar network wanda yayi daidai da wa'adin barin
su daga wajen,har ƙasan ran shi ya ke jin daɗin tafiyar tare da addu'ar Allah ya sa
suna gusawa ya samu réseau.
Bayan sun isa ƙauyen da ƴan tsirarun mutane ne kawai ke ciki irin Bugajen nan
matafiya, Chef ɗin su ya bada umarnin duk mai waya ya kashe ta saboda haɗarin wajen
hasken salula ma kawai zai iya jawo hankalin magauta gare su.
Wani irin kallo Mohammed ya ke bin Chef ɗin da shi wanda ya mutuƙe fuska ya tara
wata leda sai wayoyi ake cillawa,miƙewa Mohammed yayi kafin a kawo gare shi ya nufi
wata bishiya bedi.Kamar wani ƙadangare haka yayi laƙaƙam ya haye dakyal,wayar shi
ya zaro daga aljihu ya fara jaraba kiran Munat kiran ya shiga sai dai da alamu tana
cikin waya ne ƴar baturiya sai ce mashi take ```Wanda kuke kira ya na cikin magana
ku sake kira zuwa gaba``` kiran da yayi mata ya fi goma da ya katse ya maida,tuni
zuciyar ƴan maza ta fara hawa kafin ya ankare sai gani Chef ɗin nasu yayi tsaye
bakin bishiyar ya na daka mashi tsawar da yasa sauran sojawan sunne kawunen su in
ka fidda Omar da waro ido kafin kuma ya kai ga yin magana Mohammed ya saki ƴar ƙara
tare da dafe cinyar shi ta hagun,macijin na shirin ƙara mashi wani cizo ya dirike
daga kan bishiyar bai shirya ba.
Wayar da ta faɗi Chef ɗin ya ɗauka wacce tuni ta bugi dutse screen ɗin ta duk ya
tartse,da sauri Omar ya ƙaraso ya na zare rawanin da ke kan shi ya raba shi biyu ya
ƙulle ƙafar Mohammed Farko da kuma can kusan ƙarshen cinya sai ya zamana gubar
macijin ta tsaya ne a tsakiya.
Cike da ƙwarewa Omar ya shiga bashi taimako ya samu ya fitar da gubar yayinda wani
soja ya halbe macijin da bindiga.
Da tambaya mutanen ƙauyen Omar ya samu mai bada maganin macizai na gargajiya na sha
da kuma barbaɗe,duk wannan aikin da ake yiwa Mohammed hankalin shi bai kan ciwon
Chef kawai ya ke kallo kafin maganin da aka bashi na barci ya fara aiki ga jikin
shi.

Cikin kwanakin da ba su wuce biyar ba soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanin Munat da
Mr Arman abun ka da dama kowanensu ya na son ɗan uwan shi tun tuni an ɓoye dai ne a
zuci.
A kullum Mr Arman cikin zarya zuwa ganin Munat ya ke in bai zo ba suna manne a
waya,yanzu ma waya su ke wacce sun fi awa ɗaya da somata tana jin ƙara tiii..tiii
alamun wani kiran ya shigo wayarta amman taƙi dubawa ma balle ta san mai kiran love
ɗin ta kawai ta ke sha.
Sai Mr Arman ya kashe kiran sannan ta duba appel en absence,zaro ido tayi tana jin
bugun zuciyar ta na harbawa da sauri-da sauri.Rappeler ɗin shi tayi amman wayar a
kashe,tagumi tayi ta zura ma ƙafarta ido wacce kumburin ta ya sace sai walƙiyar man
ƙashin da aka shafa mata ta ke.Wasu hawaye da ba ta shirya zuwan su ba suka ziraro
mata a kumci,gogewa tayi da bayan hannu tace "mi yasa na kasa dubawa dan ganin mai
kiran?oh Moha Sarkin zuciya shine ya kashe phone ɗin dan Allah ka kunna wlh ban san
kai ne ba na zata Maryam ce"ta faɗa tana sake gwada wani kiran amman shiru.
Ta na cikin JUYAYI(Nimcyluv) Maryam ta shigo ɗakin tana kallon wayar hannun Munat
tayi niyya ne yau ko da wayo da dabara ko kuma da tsiya sai ta ɗauki lambar
Mohammed.
"Ke lafiya kike wani matsar ido kamar tsohuwar kuturwa?"cewar Maryam tana zaunawa
kusa da ita,wasu hawayen ta shaye tace "wlh Moha ne ya kira ni to muna tsaka da
waya da Mr ne shiyasa na ƙi ɗauka kuma yanzu na kira indisponible ina gudun zuciya
ce yayi kin san sojoji ba hankali ne da su ba abu ƙanƙane sai zuciyar su ta
hau"Maryam tace "a'a ba zai kashe waya ba dai ko problème ɗin réseau balle kin san
ƴan Moov da ƙarya amshi wayata ki kira kiji tunda ni airtel ne da ni"ba tare da
wani tunani ba Munat ta saka lambar Mohammed a wayar Maryam nan ma dai
indisponible.
Ta ƙarɓe wayar tana cewa "bari in yi redémarrer portable ɗin sai a sake gwadawa".
Abincin da Mami ta kawo masu ne ya sa suka bar zancen wani appel suka shiga ci nan
Maryam ta fara yi mata hirar Mr Arman,ita kuwa da ya ke nan ya ke yi mata ƙaiƙayi
ta saki baki sai zuba uban surutu ta ke.

Hôtel Horizon shaharara Hôtel ce wadda tayi fice tun daga kyawun zubunta har izuwa
abincin da ake sarrafawa,a duk faɗin Maradi babu hotel ɗin da ta fi ta.
Wata farar mace ƙatuwa irin rainon madara rairafen capet😹 ke zauna bisa cinyar
Mustapha sai wani fari ta ke yi mashi da idanu yayinda ta ke wasa da gashin dokin
kanta wanda ya zubo har izuwa ƙirjinta.
Cikin murya irin ta shagwaɓaɓin yara tace "haba my Hony ka saki jikin ka mana ka
wani takure waje guda kamar ba wayaye ba,dube ka fah ka gani handsom da kai "tana
maganar ne ta na shafa farar fuskar shi mai zagaye da baƙin saje,lumshe ido
Mustapha yayi ya na jin tsikar jikin shi na tashi a zuci kuwa faɗi ya ke "ashe
dagaske dai mace ma za ta iya yiwa namiji FYAƊE(Haj Maryam Sakatare)? dube min ita
yadda ta wani kanekane a jikina kamar ta samu mijinta"a zahiri kuma kasa cewa yayi
komi dan kuwa duk abinda ya same shi da son shi dan da bai amince ya amsa gayyatar
ta ba da ko mai kama da shi ba za ta gani ba.
Zuciyar shi ta tsinke lokacin da yaji kyawawan laɓanta kan bakin shi,cikin fizgewar
numfashi ya tureta ta faɗi ƙasa timmm.Ya miƙe tsaye ya na cewa "Fi'a miye haka?dama
ba dan muyi magana ba ne kika ce na zo nan?"cikin marairaice fuska tace "magana za
mu yi bb juste ina son isar ma ka da saƙon da ke cikin zuciya ta,am ina sonka ne
shiyasa ka yarda da Ni"ta ƙarashe maganar tana mai kamo hannuwan shi ganin irin
kallon da ya ke watsa mata."Shine kuma kika rasa ta hanyar da zaki faɗa min sai ta
haramtacciyar hanya?wai ma da mi kike so aure koko soyayyar shan minti"cewar
Mustapha ya na kafeta da ido dan ya lura tana shakkar hakan,kai ta sunkuyar tace
"auren ne ba zai samu ba yanzu saboda ban gama karatuna ba,ka ga za mu iya fara
soyayyar shan minti ɗin kafin lokacin auren mu"cikin ƙaraji yace "ja ki ban waje na
wuce na ga alama ƙusoshin kan ki sun kwance in kin sake tunani kya kira ni"ya faɗa
ya na mai fita daga cikin room ɗin dama ita ta kama shi ba shi ba.
Ya haye babur ɗin shi sai gida,ya na shigowa idon shi suka sauka kan Maryam wacce
ta ɗaga rigarta tana gwadawa Munat ƙarin da ya fito mata kusan breast🤭.Saurin sakin
rigar tayi a tare zuciyoyinsu suka buga,Maryam kuma sai zare ido ta ke tana kallon
Mustapha da ke yi mata kallon cikin ido......
[29/05 à 17:11] MRS SADAUKI 💫: 🆓 13-14

Munat sam ba ta lura da Mustapha da yayi mutuwar tsaye ba,ta kai hannunta za ta
ɗaga rigar Maryam tana cewa "mu ga ƙululun kuma shine ba ki tafi asibiti ba ko
tsoro kike ji ace Cancer ne?"ta buge hannunta ta na mai cigaba da kallon Mustapha
wanda shi ma sam ya kasa motsawa ba tare da ya san dalilin tsayuwar ta shi ba.
Ganin ta kafe wuri guda da ido ya sa Munat kallon gun, turo baki tayi tace "kawai
sai a shigo ma mutane ɗaki ba sallama"yadda tayi maganar ciki-ciki ko Maryam da ke
kusanta ba ta ji ba balle wanda aka yi dan shi.
Cikin ta ya yo ya na cewa "dan uban ki ni kike yiwa gunguni ?uwar mi za ki duba
cikin rigar ta ko likita ce ke?"a sangarce tace "to ba ita tace na duba na ga ko
minene ba😩"harara ya banka mata yace "ke uwarta ko?to na sake gani ku na ɗage-ɗagen
rigar ku ga ikon Allah,wlh sai nayi maki ɗan banza duka shashashu da baku san ciwon
kan ku ba kuma ki tashi ki cire wannan ƴar banzar rigai mai kama da ta karuwan
daji"Mami da shigowar ta kenan tace "miye haka Mustapha?ina ruwan ka da rigar ta
wai miyasa ka cika sa ido ne han?"Mustapha yace "haba Mami sabida Allah wannan
shigar ƴar musulmai ce?dubi yadda rigar ta ɗame jikinta kuma rigar ko hannuwan
kirki ba ta da su" "to ai ba waje ta fita da ita ba cikin gida ne ta ke"cewar Mami
ta na son kare autar ta.
Cike da jin haushi yace "sai kuma aka ce ya halitta ayi yawo tsirara cikin gida?
yanzu in fah wani ya shigo ya ganta a haka?"Mami tayi shiru ta na nazarta kalaman
shi sai ta ga kamar ya na da gaskiya duba da irin tsarin halittar Munat ko ina a
cike ya ke,cikin fushi ya nufi ɗakin shi Mami tace "abincin fah?"ba tare da ya juyo
ba yace "a kawo min"gaban Maryam ya faɗi dan kuwa ta san ƙarshen ta ita za'a
aika,kallonta Mami tayi tace "ɗoki abincin shi ki kai mashi ga ya can kan table ki
"ba dan ta so ba ta miƙe a sanyaye ta ɗauka tare da nufar ɗakin shi.Ƙofa ta bubuga
ya na jinta yayi banza da ita can da ta gaji ta tura ƙofar tare da yin sallama ta
tsaya bayan labule sai da ya amsa mata sannan ta ida shiga.Bisa ɗan ƙaramin table
na katako ta aje abincin tana shirin juyawa taji yace "dawo ki zauna "a dake.Da
sauri ta waigo ta na kallon shi alamun tsoro ƙarara bisa fuskar ta,zaunawa tayi
ƙasan Capet ta sunne kai zuciyarta na lugude.
Har ta fidda tsammani sai kuma taji muryar shi ya na cewa"Maryam miyasa kuke da
ƙiriniya?Na zata ke mai hankali ce saɓanin Munat ashe taron kofi da farenti ne?
miyasa kuke yin abu kamar wasu yara ko ba ku san kun girma ba ne?Yanzu da kike son
ki gwada mata ciwon da ya same ki magani za ta baki?"kai Maryam ta girgiza ya
cigaba da cewa "miyasa ba za ki gayawa mahaifiyar ki ba sai wannan wacce kwanyarta
ita da ta ɗan yaro duk ɗaya?"kuka Maryam ta fashe da shi tace "Ni kunya Mama ni ke
ji"sororo Mustapha yayi yace "ka ji wani sakarci kunya Mamar ki kike ji amman ba ki
jin ta ƙawar ku?hummm wlh mata ƙaramar ƙwaƙwalwa gare ku in ku na da wata damuwa
maimakon ku faɗe ta inda za'a ayi maku magani kun fi son faɗar ta inda za'a baku
shawara.Gayamin tun yaushe kike jin abun?"tana matsar ƙwalla tace "2week"kai ya
jinjina yace "ok tun da gobe weekend ne ki isko ni Clinic Agaji da misalin ƙarfe
goma na safe lokacin na hau aiki"da "toh"ta amsa yace "tashi ki tafi dan Allah kuma
ki rinƙa yiwa ƙawar ki faɗa ta bar saka ƙananun kaya"kai kawai ta ɗaga ta na fitowa
taji wani irin sanyi har sai da ta sauke ajiyar zuciya.

Munat ta kalleta tace "mi kika tsaya ko dukan ki yayi?"kai ta girgiza tace "a'a
yayi min dai nasiha kuma wlh da gaskiyar shi sam ba mu da nutsuwa daga ni har ke
sannan ya kamata ki bar saka irin wannan kaya dubi fah shatin nipples ɗin ki fah
ana gani"taɓe baki tayi tace "toh Mami wacce ta kawo ni duniya,kawai sai nayi ta
fama da manyan kaya daɗa zafi ya kashe ni hum"tayi ƙyaci tana mai kwantawa tare da
cigaba text ɗin da suke ita Mr Arman.

Maryam na zuwa gida ta shige ɗaki number Mohammed tayi ta training amman bai shiga
hakan ya sa ta shiga aika masa text mai ɗauke da kalaman soyayya wanda ita kanta ba
ta san ta iya su ba sai yanzu.Ta rungume wayar a ƙirji tana sakin murmurshi ta
matsu ta ga réel visage ɗin shi ko da kuwa a hoto ne,zumbur ta miƙe jin ƙululun na
yi mata yawo ita har tsoro ta ke ji a zuci tace "kar dai Cancer du sein ne ya same
ni kamar yadda Munat ta ce"a take wani tsoro ya kama ta tuna har yanke breast ake
in yayi tsanani a fili tace "shikenan na rasa *SOJANA* ta yaya zai so ni da sein
guda "nan ta fara matsar ƙwalla bisanin kuma ta shige toilet dan duba ƙululun 😹.

A can ƙauyen Zinder kuwa sosai Mohammed ke samun kulawa ta likitan shi Omar tare da
ta mai maganin macizai.Su na fita aiki a duk ko wane dare sai dai a bar Mohammed
shi ɗaya kamar maye, wannan abun ya na mugun ɓata mashi da rai babban baƙin shi
kuma shine babu waya a hannun shi dan ya matsu yaji da wa Mimi ke waya.
Ya na kwance kishingiɗe da misalin ƙarfe sha ɗayan rana,babu kowa sai shi ɗaya
kamar an ce ya buɗe idon shi haka ya tsinkayi wata farar mace doguwa siririya sanye
da fararen kaya ta na tunkaro.Lumshe ido yayi ya buɗe sai kawai ya ganta har ta
kawo kusa da shi cikin second da bai wuce ɗaya zuwa uku ba, murmurshi yayi ya fara
karatu sai ji yayi tace "ba cutar da kai zan yi ba nima mutum ce kamar ka"bai
kulata ba ya cigaba da karatu ba shiri ta ɓace ɓat.
A fili ya furta "Ni za ki yiwa baiguwa?to kurwata tafi ƙarfin ki tun kafin na san
ko wanene ni aka wanke ni da ayar Allah dan haka ki ƙarata can gaba"abun mamaki
kuma sai ta ɓullo ta wani ɓangare ta na magana da asalin muryata na latizuwar mace
"yayi jikan Sarkin borin ƴan Agadez masu"bai dai kulata ba yayi banza da ita irin
wannan kan ki dai ake ji.
Ba jimawa group 1 nasojawan suka dawo wanda Omar ya na cikin ƴan group ɗin,labari
Mohammed ya bashi irin baiguwar da wata mayya tayi mashi.Omar ya zaro ido yace
"shine kake zaune? wai in ma tambaye ka daga ina ta fito?mutanen dajin nan fah sai
ka ƙirga su kuma duk Fulani ne"Mohammed na shirin yin magana sai ga Chef ya tsaya a
gaban su tamkar wani zaki,taɓe baki Moha yayi dan shi sam bai ƙaunar Chef haka kuma
bai jin tsoron shi ko ɗaya a zuciya ya na yi mashi biyayya ne saboda shi ke gaba da
shi.
"Na ce ka tashi ka taka ƙafar na gani ina son ka fita aiki gobe"cewar Chef ko
kallon arziki bai samu ba balle ya sa ran yi mashi magana.Zungurar shi Omar yayi ya
waigo ya harare shi kafin yace "ta yaya zan taka ƙafar alhalin ban ji sauƙi ba ko
dan ciwon ba'a jikin ka ya ke ba?"ya na maganar ne ya na kallon Omar tamkar shi ya
tambaye shi.Wani ƙuluƙulun baƙin ciki ne ya turniƙe Chef "to doli ka tafi aiki
tunda sai da kayi rantsuwa kafin a ɗauke ka"cewar Chef a hasale murmurshin gefen
baki Mohammed yayi yace "in kuma na aje aikin sai ya kenan?za'a bar ni nayi jinyar
kaina ne koko tilasta ni za'a yi sai na je?"shiru Chef yayi a zuci yace "wannan an
yi shegen yaro kin ji a tambaye shi dalilin ajen aikin na shi yace ni,ɗan banza ba
za ka ɓallo min ruwa ba garin neman gyaran gira a rasa ido"cike da borin kunya ya
bar wajen ya na mai baiwa Omar ya biyo bayan shi,harara Mohammed ya bi shi da ita
yace "munafuki".

****AGADEZ

Maa ce zaune gaban wani madubin tsafi gefe da gefen ta kuwa wasu baƙaƙen tasa ce
sai tururi ke fita,madubin ta shafa ta na karanto ɗalasiman tsafi amman shiru
madubin ya ƙi buɗo komi sai wani gurzajen image wanda ta kasa tantance namiji ne ko
mace.
Cike da baƙin ciki ta rufe madubin da baƙin ƙyalle ta tashi tsaye ta na zagayen
ɗakin,"doli ne nayi hijira zuwa Japon tsafina yayi ƙasa ƙwarai ga shi kuma har
yanzu ya kasa gwada min wanda ya kashe min Attahiru na,wlh nayi rantsuwa da jinin
Kanana Zaffar sai na ɗanɗanawa makashin Attahiru azaba irin wacce sai ya gwammaci
mutuwa kan rayuwa tabbas sai na ɗau FANSAR RUHIN ka mijina muddin ban yi haka ba
ban cika Iya ƴar bori ba"ta na maganar ne tana dunƙule hannu.
Tana cikin zagaye Jakadiya ta shigo ta kawo mata saƙon SARKI(Miss flower)na son
ganin ta.Maa a gaban Sarki zaune kamar yadda ya buƙata ta dubi fuskar shi wacce ta
a tunuƙe cikin rawani tace "Ya shugabana ina sauraran ka faɗi buƙatar ka na aiwatar
kar ka ji shakka gayamin ko ma miye ya gusar da annurin da ke bisa wannan
kyakkyawar fuskar ta ka"murmurshi yayi dan har ga Allah ya na son zama da Maa ko
dan dadaɗan kalaman ta,yanzu ma wannan lafuza nata sun sanyaya mashi zuciya.
Miƙewa yayi tsaye ya bata baya ka nan yace "Sarkin Zinder ne ke nuna min ɗagawa ya
na jinshi shi wani ne har ya fito a gaban bainar jama'a ya na cewa a soke al'adu
sam ba su dace a musulunci ba,wai shirka ta fiya yawa a tsarin sarauta shiyasa har
ake samun jefe-jefe a tsakanin sarakuna..."Maa ta miƙe tsaye ta na cewa "shi ɗin
banza shi ɗin wofi,har shi ya isa ya dakatar da abinda mu ka tarar kakani da iyaye
su na yi?yanzu mi kake so ayi?ɓatar da shi za'a yi koko cutar da ba ta da magani
za'a tura mashi?"zuciya wasai ya juyo yace "ki yi abinda kika ga ya dace"Maa tace
"an gama"cike da murna ta koma part ɗin ta domin ita a duniya in akwai abinda ta fi
so to ƙeta ce ko cutar da wani.
Surkulenta ta shiga haɗawa uwanda sun fi ɗari sannan ta kirawo sarki dan tafi son
ta aiwatar da aikin a gaban shi.
Babu tsoron Allah a zukatan su ko kaɗan,madubi ta shafa sai ga hoton Sarkin Zinder
ya bayya a zaune bisa karagar mulki fadawan shi na ƙasa yayinda s'wasu dogarai su
ke mashi fifita.
"Wannan fitsarin jinjirin aljani ne amfanin shi shine ƙarawa sihiri ƙarfin tasiri,
wannan kuma sawun ƙafar Giwa ne amfanin shi shi kuma zai ta ƙarawa gangar jiki
girma ne"cewar Maa tana mai zuba duk abinda ta ambata cikin ƙwayar da ta yanka
baƙaƙen zakaru biyu,Sarki kuwa sai jinjina kai ya ke zuciyar shi fal farin ciki so
ya ke ayiwa Sarkin Zinder sihirin da zai sa ya nemi taimakon ƴan bori dan kan
shi,wani na hannun damar sarki ne ya shigo hannun shi riƙe da wata kwalba mai ɗauke
da jinin raƙumin da Maa tace a yankawa doguwa.
Babu ɓata lokaci Maa ta shiga aikin ta tana amta sunan sarkin Zinder wanda kuma a
zahiri suna kallon shi ta madubi,fatar jikin shi ce ta fara réagir inda ya ke jin
wani irin raɗaɗi sunan Allah ya fara ambata cikin ƙaraji Maa tace "kar ka kira ma
mu Allah kar ka ɓata min aiki "Sarkin Zinder da ya ji azabar na cigaba yayiwa
jama'ar shi sallama ya shige ciki tare da kwantawa zuwa wannan lokacin ko hannun
shi bai iya motsawa domin kuwa asiri gaskiya ne ya na kuma tasiri inda Allah ya so
to hakan ce ta kasance da shi.......
[29/05 à 17:11] MRS SADAUKI 💫: 🆓 15-16

Wasa farin girki ciwon Sultan Hashim ne ya tsananta inda aka fancama neman magani
kan na asibiti kan na gargajiya.Ana haka kwatsam kuma sai aka kawo mashi attaque
ana son kashe shi wanda ko tantama babu aikin magauta ne,cike da tsumaye Sultan ya
nemi a bashi matakan tsaro ba'a ɗau lokaci ba président ɗin Niger ya baza sojoji a
gidan Sultan na Zinder tun farkon shigowa layin za ka ganin canji sannan a ƙofar
gida ma an saka soji fiye da ashirin.
Kallo guda za ka yiwa Sultan ka san da ya na jin jiki kawai dai ta maza ce ya ke ya
na ɓoyewa,Balkis uwar gida kuma mata ɗaya ƙwal ga Mai martaba ita ke jinyar mijinta
domin Allah bai azurta su da samu haihuwa ba balle ƴaƴan su jinyace shi.
Wanka ta ke yi mashi ta na kallon ikon Allah da ya bi duk fatar jikin shi ya
kankare kamar mai cutar kuturta,cike da tausayi irin na mata da miji ta tsane mashi
jiki ta murza mai ta shafe shi sannan ta saka mashi kaya maras nauyi.
Kallonta yayi cike da so da ƙauna yace "Allah yi maki albarka Mar'atu saliha,da ina
da iko da na zauna da ke dan kar na mutu hawayen ki su zuba sai dai wannan ciwon ba
mai barina ba ne"kai ta girgiza tace "ya kai shugabana ka sani babu cutar da ba ta
da magani,kuma duk tsanani ya na tare da sauƙi.Ka ɗauka wannan jarabta ce daga
Allah dan saboda ita rayuwar ga duk wanda yace yayi imani da Allah da Manzonsa to
tabbas zai dinga ganin ƙalubale na rayuwa kenan kala-kala,in ka rabu da wannan yau
to ka shirya zuwan wata jarabawar gobe"duk da ciwon da ke cin shi bai hana kalaman
ta samun gurbi a zuciyar shi tare da tasiri.
Yace "Tabbas haka ne sai dai ni abun ya fara bani tsoro likitoci sun ce ba su ga
komi ba sai tension wadda dama na san ina da ita,masu bada maganin gargiya sun ce
sihiri ne kuma sai magani ake amman shiru babu sauƙi"wani murmurshi Balkis tayi
wanda yayi matuƙar ba Sultan mamaki amman sanin matar ta shi ta na da baiwar ɓoye
ya sa shi yin shiru,tashi tayi ta nufi ƙofa tace "ka sani tun kafin wannan ciwon ya
same ka tun tuni aka nuna min shi a mafarki kuma an tabbatar min da za ka warke
ne"ba tare da ta jira cewar shi ba ta fice.Numfashi ya sauke dan kuwa ya san rabin
mafarkan Balkis sukan zama gaskiya ne hatta attaque ɗin da aka kawo mashi tayi
mafarkinta kuma ta gaya mashi tun kafin a kawo harin,ita tace ya cewa président ya
na son a bashi matakan tsaro kuma sojoji.A zuci yace "Allah sa ma wannan karon ya
zama gaskiya dan tabbas ina son na rayu a duniya ko da na ɗan lokaci ne"sallama
Waziri yayi tare da shigowa,ya gaishe da Sultan kafin ya baiwa sauran mutanen da ke
son ganin shi damar shigowa.

A firgice ya farka daga mumunan mafarkin da ya ke ya dafe zuciya,kamar wanda yayi


gudun fanfalaƙe haka ya ke fitar da numfashi.Ruwan sanyi ya ke son sha amman babu
hali tsuki yayi yace "kai rayuwa soja ba tayi ba da ranka amman kamar matacce"ƴar
aci balbal ɗin ya ƙara ɗagawa nan hasken ta ya ƙaru,ƙafarshi ya kalla wacce ya ji
wani irin raɗaɗi na ƙara shigar shi,lumshe ido yayi ya na ambaton Allah sai yaji
raɗaɗin na ragewa.Maganar Abba ce ta faɗo mashi a rai «ka zamana mai yawan azkar da
sallolin dare,ka riƙe imaninka ka sa yarda ka wajen Allah babu wani mahaluki da ya
isa ya cutar da kai in ba Allah ya so hakan ba.Sannan ka sani ban koya maka wannan
aikin ba dan ka cutar da wani a'a na koya maka shi ne dan tare halbin maƙiya
Mohammed kar ka zamo raggo wajen yiwa kan ka aikin tsare kai daga magauta»gwabron
numfashi ya sauke da ya gama tunanin ɗaya daga cikin zantukan da Abban ki ke yawan
yi mashi a lokacin da ya ke koyar da shi ilimin tsibo😱.
Tashi yayi ya buɗe sac au dos ɗin shi ta sojawa,wata ƴar ƙarama jakka mai kama da
ta fata ya fiddo wacce ke cike da wasu takardu da ƙullin magani barkatai.
Alwala yayi tare da yin Sallah raka'a biyu ya karanta addu'ar Istakara
‫ الَّلُهَّم‬،‫ َو َأْنَت َع َّالُم اْلُغ ُيوِب‬، ‫ َو َتْع َلُم َو اَل َأْعَلُم‬،‫ َفِإَّنَك َتْقِد ُر َو اَل َأْقِد ُر‬، ‫ َو َأْس َأُلَك ِم ْن َفْض ِلَك اْلَعِظ يِم‬، ‫ َو أْسَتْقِد ُرَك ِبُقْد َرِتَك‬، ‫الَّلُهَّم ِإِّني َأْسَتِخ يـُرَك ِبِع ْلَم َك‬
‫ِإْن ُكْنَت َتْع َلُم َأَّن َهَذ ا اأَل ْمَر (َو ُيَسِّم ي َح اَج َته) َخْيٌر‬
‫ َو ِإْن ُكْنَت َتْع َلُم َأَّن َهَذ ا اَألْمَر َشٌّر ِلي ِفي ِد يِني َوَم َع اِش ي‬،‫ َفاْقُدْر ُه ِلي َوَيِّسْر ُه ِلي ُثَّم َباِرْك ِلي ِفيِه‬،‫ِلي ِفي ِد يِني َو َم َع اِش ي َو َعاِقَبِة َأْم ِر ي‬
‫ َفاْص ِر ْفُه َع ِّني َو اْص ِر ْفِني َع ْنُه َو اْقُدْر ِلَي اْلَخْيَر َح ْيُث َك اَن ُثَّم َأْر ِضِني ِبِه‬،‫َو َعاِقَبِة َأْم ِري‬
Ya na gamawa ya sha maganin da ya kaɗa cikin nono sannan ya kwanta.
A cikin mafarkin shi aka nuna mashi yadda karnuka ke bin shi a baya shi kuma ya na
gudu har ya kusa shigewa ɗaki dan ya ɓuya wani kare ya samu nasara cizon shi,sai
kuma mafarkin wata tsohuwa na tura shi cikin wasu irin ruwa masu mugun zafi yayinda
gefe guda kuma ga ruwan sanyin da ya ke muradin shiga amman ta hana shi,mafarki na
uku kuwa ganin shi yayi cikin wani ƙaton gida tangameme wanda bayi ne barjit suna
kai da komowa yayinda shi kuma ya ke zaune bisa wata kujera ta haske gefen shi hagu
da dama wasu Twins ne mace da namiji sun sa shi tsakiya.
Washegari bayan Mohammed ya gama sallah asubah ya tsaya ya na nazarta mafarkan
shi,ya sani mafarkin karnuƙa maƙiya ne biyun ne ya kasa gane su.Nisawa yayi a fili
yace "mi zai kai ni gidan sarauta kuma har na zama sarki bayan ni soja ne kaiii ba
zai yiyu ba ni sam sarauta ba ta burge ni kawai dai wata fassara ce daban amman ba
wannan ba"ɗan dattijon da ke kula da shi ne ya shigo bayan sun gaisa ya kwance ɗan
ƙyalen da ya ƙule cinyar Mohammed ya na haskawa da fitilar hannu.
"Ƴan samari ciwon na ka da saura ga shi kuma shugan ku yace yau za ku bar gun nan
zuwa Dourkou,ka kula sosai sannan ka yawaita yin addu'a domin kyakkyawar zuciyar ka
ya sa magauta na san ganin bayan ka"murmurshi Mohammed yayi yace "na gode Baba
Allah shi yi albarka da kyakkyawan ƙarshe"farin dattijon yayi saurin kallon
Mohammed jin ya kira shi da baba hawaye suka zubo kan fuskar shi bai san lokacin da
ya rungume Mohammed ba yace "na gode sosai matuƙa karon farko a rayuwata wani ya
kira ni da Uba ba a yau ɗin nan sai ni ke ji na tamkar wani sarki,tsaya ina zuwa"ya
faɗa tare da fita bai jima ba ya dawo hannun shi riƙe da wata baƙar leda.
Wata sarƙa mai boule ƙato ya fara saka mashi sannan zoben azurfa yace "ka ga wannan
(zobe da sarƙa)a gun mahaifina na gaje su tun da ran shi ya ban su ban san amfanin
su ba sai da na shiga tarko am...kar ka tambaye komi da sannu za ka fahimta kai dai
duk runtsi kar su bar jikin ka"ya faɗi hakan ne saboda ƙur ɗin da Mohammed yayi
mashi ko ƙyaftawa babu.
Murya Chef suka ji a bakin ƙofa hakan yasa yayi saurin bashi baƙar ledar yace "yi
sauri ka tafi Allah ya tsare"da "amen"ya amsa sannan ya saka wandon tenue dama
rigar already tana jikin shi.
Da Mohammed ya fito ko kallon inda Chef ya ke a tsaye bai yi ba, direct inda
collègues ɗin shi ke tsaye cikin shiri ya nufa.
Duk taron su Omar ne kaɗai ya tambayi jikin shi,"da sauƙi"ya faɗa tare da nufar
mota ya shige.
Chef na tsaye ya na kallon su ɗan nesa da su a zuci yace "Allah Sarki bawan dubi
yadda ya ke ɗangasawa Allah dai ya baka lafiya ya sa kuma za ka iya draving"ya faɗi
hakan ne lokacin da Mohammed ya shiga mota kuma mazaunin drever.Fuska a tamke ya
ƙaraso gun ya bada umarnin kowa ya shiga motar da ya san ya na shiga,kusan a tare
motocin da suka haura goma suka tashi tare nutsawa cikin ƙasungumin daji.

Tun safe Maryam ta shirya domin zuwa asibiti,kallo guda za ka yi mata ka san ta na
cikin fargaba.Ganin tsayuwar bai yi mata ta fito waje tare da cewa Mama "na tafi
gidan su Munat"a dawo lafiya Mama tayi mata.
Ta tsayar da abun hawa ya kaita Clinic Agaji,tana shiga gabanta ya faɗi réception
ta nufa murya na ƴar rawa tace "dan Allah Mustapha ya na nan?"ɗagowa Hajiya tayi
dubeta murmurshi kan fuskarta ta nuna mata wani bureau "ki shiga ya na nan ciki"
"toh na gode"cewar Maryam tana mai nufar inda aka nuna mata,ƙwanƙwasawa tayi daga
ciki ya bata izini ta shiga.
Har ta zauna bai ɗago ya dube ta ba rubutu kawai ya ke a farar takarda,sai da ya
kusa ciketa sannan ya ɗago ya dubeta idon shi masu kama da na mashayi,saurin sunne
kai tayi dan sosai ta ji kunya kamata da yayi tana kallon shi.Murmushi yayi yace
"Barka da zuwa soeurette bari na kira abokin aikin nawa ya duba ki mu gani,in bai
wani tsanani sai a baki magani in kuma yayi tsanani sai an fasa gun"idon Maryam ta
fiddo tace "wani?wani kuma Musto?"yadda tayi maganar sai da ya so bashi dariya yace
"eh mana "baki ta turo tace "Allah kiyaye ni na zata kai za ka duba ni"yace "dan mi
ba wani ba?"cikin shagwaɓa tace "haba kai ma dan Allah haka kawai wani ƙato ya duba
ni"fuska ya ɗan tamke yace "to ni mi ye in ba ƙaton ba?"kallon shi tayi tace "ai
kai magajina ne"murmurshi yayi ya na nuna mata gado,ta kalli gadon ta kalle shi
yace "eh je ki hau ki tabbatar kin cire rigar sai ki gwada min inda ya ke ciwon"bai
jira cewar ta ba ya fita ko da ya dawo hannun shi riƙe da allurai.
Ya kalleta yace "ko baki shirya ba?"ya faɗi haka ganin ta haye gado ta zauna daram
sai hijab da ta cire,sunne kai tayi ta shiga kiciniyar fidda Zip ɗin rigai tsawon
minti ɗaya,ƙarasowa yayi tare da maida hannuwan shi bayanta da zumar taimaka mata
hakan sai ya ba fatar jikin su haɗuwa ta yadda su kayi kusanci har bugun
zuciyoyinsu suna ji.
Saurin jan Zip ɗin yayi ƙasa tare da cire rigar ya bar mata bra kawai, kwantawa
tayi tare da rumtse idonta ta ɗan jan gefen bra ɗin da breast ɗin ta ke ciwo.Hannun
shi ya kai daidai inda ta janye nata nan kuwa yaji ƙululun,massaging wurin ya fara
yi sannu-sannu saurin riƙe hannun shi Maryam tayi tare da fashe mashi da kuka ta na
yarfa hannu....
[29/05 à 17:12] MRS SADAUKI 💫: 🆓 17-18

Ta yi saurin riƙe hannun shi tana jin wani kala biyu,tun da take ko hannunta namiji
bai taɓa riƙewa ba balle breast.
Cikin murya shagwaɓa-shagwaɓa tace "please ka bari ban so"kallonta Mustapha yayi
kawai ya maida hannun shi kan breast ɗin ya ɗan matsa inda ya ke jin sauran ƙululun
da har yanzu bai baje ba,ƴar ƙara ta saki tace "Washhh zafi"bai kula ta ba har sai
ya tabbatar ya naguje ƙululun ya na yi ya na saka wani crème har ya gama ya ja mata
bra ɗin ta.Allura ya ɗauko yayi mata a hannu sannan yace "ragguwa tashi to"turo
baki tayi tace "eh tunda ba non..."sai kuma ta ƙyale murmurshi yayi yace "ida mana
tunda ba minene nawa ba?"sunne kai tayi hakan ya baiwa Mustapha ƙare mata kallo
tsaf musamman cikakkun ƙirjinta uwanda suka cika bra ɗin ta har wuri bai ishe su
ba.
Tayi saurin jan rigarta ta maida saboda jikinta ya bata ya na kallon ta,wani
gwabron numfashi ya sauke ya na jin wata kasala na rufe shi wacce bai san dalili ba
hakan ya sa doli ya samu wuri ya zauna tare da lumshe ido.Ƙuri Maryam tayi tana
kallon kyakkyawar doguwar fuskar shi mai zagaye da saje,a zuci tace "masha Allah
nan Allah yayi halitta ba dai kyawu ba"buɗe idon shi guda yayi ya kalleta ta
ƙasa,kafin ya nuna mata ledar magani da hannu.
Ɗauka tayi tana jiran bayani sai kuma ta kama hanyar fita dan kuwa ba ta ga alamar
Mustapha zai yi mata magana ba.
Cak ta tsaya tana kallon ƙadangaren da ya ƙureta da ido ya na kallo kuma ko alamun
motsawa bai yi ba,da baya -da baya ta fara yi tana yarfa hannu, Mustapha da ke
zaune lumshe da ido ya na jiran yaji ƙarar buɗe ƙofa shirun da yaji ya sa ya buɗe
ido,ganin yadda take marche arrière ya sa shi miƙewa tare da nufota ya na cewa
"minene?"ba ta zaci jin muryar shi ba hakan yasa ta ƙwalla ƙarar da ta firgita
ƙadangaren ai ko ya yo cikinta,ihu tayi tare da tsalle ta laƙanƙame Mustapha.
"Ya Allah!"ya furta jin ya ƙara shiga wani shauƙi fiye da na farko,ledar maganin ta
saki ta ƙara damƙe muscule ɗin shi ta na kuka.Tafiya ya fara yi da ita a haka har
ya kawo kusan gado ya sauketa sannan ya nufi ƙadangaren yayi mashi wata damƙa ya
fitar da shi waje ya dawo ya na mamakin yadda aka yi ya shigo.
Jingina yayi da ƙofa ya na kallon yadda ta ke faman goge hawaye wasu kuma na
zubowa, yace "toh sauko ki tafi gida na fidda shi"kafaɗa ta maƙe tana waro ido tare
da dube-dube.A zuci yace "tab wannan mijinta na dai aiki"ya ƙarasa bakin gadon da
zumar sauketa kawai sai ya tsaya cak ganin ta zuba mashi ido tana kallon yadda ya
ke tafiya cike da jarumta,a zuciyar Maryam kuwa faɗi ta ke "da ace Mustapha soja ne
da babu abinda zai hanata liƙe mashi har sai ya aure ta"yatsar shi ya kai ya shafi
gashin idonta da suke kamar na ɗiyar poupée tsabar tsayi,lumshe ido tayi tana
sauran bugun zuciyarta da ya canza gudu.Mustapha bai taɓa sanin in shauƙi ya ɗibi
mutum ya na sa shi abinda bai yi niyya ba sai yanzu da ya sauke idon shi kan lips
ɗin Maryam,ba zato ba tsammani ya sauke nashi kan nata.Ido tayi saurin buɗewa cike
da tsoro sai kuma tayi saurin rufe su ruf tana jin yadda ya ke kissing nata,ba tare
da ya shirya hakan ba ya kwantar da ita ya na bin duk jikinta da sumba.Maryam kuwa
tamkar wacce sheɗan ya busawa sarewa sam ta manta a inda ta ke,da wanda ta ke tare
da shi da kuma abinda suke aikatawar nan bai da kyau.Yadda ta biye mashi tana maida
mashi martani shi ya ke ƙara hura hutar sha'awar Mustapha har suka kawo gaɓar da ba
su isa su dakatar da junansu abinda zuciyarsu ke muradin yi ba.Idon shi na zubar da
ƙwalla ya fara shiga jikinta😭 kasancewar ta Virgin sam ya kasa shiga duka,duk
masifar zafin da ya ziyarci Maryam bai sa ta yi yunƙurin hana shi ba dan kuwa tuni
zuciyarta ta yanke da lamarin Mustapha aikin da ƙwaƙwalwar ta ke yi ya tsaya cak.
Cikin ƙunar rai ya fidda jikin daga cikinta ya na jin zuciyar shi na bugawa ga wani
irin ƙunci wanda bai taɓa riskar shi ba,sai a lokacin Maryam ta fashe da wani irin
kuka mai ɗaci tana jin wata irin tsanar Mustapha da duk wani mai irin sunnan shi.
Bai da wani zaɓi da ya wuce ya bata taimako hakan ya tara ruwa mai zafi a cikin
toilet ɗin da ke office ɗin shi ya rinƙa tsomata ciki tamkar wata kaza🙄 ta na ihu
ta na ƙari amman bai saurareta ba har sai da ya gaji dan kan shi,bisa gado ya mayar
da ita ya dubata dan ganin ko ya ji mata ciwo sannan ya mayar mata kayan ta tare da
fita ya dawo da wasu magani da allura ya yi mata .
Shiru ne ya biyo baya kowanensu da abinda ya ke rayawa a zuci,Maryam ta sunne kai
haka ma Mustapha dan wata irin kunyar ta ya ke ji.
Cikin ƙarfin hali ya dubeta yace "Ita ƘADDARA in za ta zowa mutum ba ta neman
shawarar shi ban ida yarda ba sai a yau,wlh Maryam tun da ni ke ban taɓa riƙe ko
yatsar mace ba duk da ƙarfin sha'awar da ni ke da ina danneta ta ƙoƙarin nisanta
kaina da duk abinda zai tado ta,ke kan ki shaida ce ta yadda ni ke yiwa Munat
kullum faɗan saka kayan da ba su dace ba.Maryam da ace ɗan Adam ya na da ikon duk
abinda ya ga dama da tabbas ko minti guda ba zan sake bari nayi a duniya ba da tuni
na yankewa kaina numfashi,za ki iya kirana da duk sunan da kika ga dama munafiki,
mayaudari,maha'inci duk daidai ne na cancanci haka dan kuwa ya tabbata zan iya yiwa
Munat FYAƊE ( Haj Maryam Sakatare)tun da har na kasa contrôler kaina na abka
maki..."kukan da ya ƙwace mashi ne ya sa shi yin shiru ita ma kukan ta ke ta kasa
cewa komi sai ƙoƙarin tashi da tayi ta ɗauki ledar maganin ta dan ta na buƙatar
su,bai yi ƙoƙarin hanata ba sai tafiyarta da ya bi da kallo.
Phone ɗin shi ya ɗauka ya turawa Chef ɗin su na sojoji text na demande ya na son
zuwa mission dan Allah,cike da murna kuwa Chef ɗin yace ya shirya zuwa gobe ya je
Madama.

Maryam kuwa ta na fita ta samu abun hawa,ya na sauketa ta shige gida ta na addu'ar
Allah sa Mama ba ta waje.
Har sai da sauke ajiyar zuciya saboda har ta shiga ɗaki Mama ba ta gan ta ba,
kwanciya tayi ta fara tunanin makomar rayuwarta hawaye ta goge ta na ji a ranta ta
ci amanar Mama irin tarbiyyar da ta bata ba ko wace uwa ba ce za ta zauna ta rinƙa
gayawa ƴar ta abubuwa game da rayuwa ba.

A ɓangaren Munat kuwa ba laifi ta samu sauƙi tsabar son jikinta da shagwaɓa da
sakuwa sune suka hanata nuna haka,ba ma kamar yadda Mr Arman ke riritata,tun da
Mami ta gane son Munat ya ke ta kasa samun sukuni dan kuwa ta san Ɗan Yayanta na
son Munat sai dai babu yadda ta iya farin cikin Autar ta ya fiye mata komi a
duniya.Ayaba ya ke bata a baki sai langwaɓe kai ta ke irin ƴan gatan nan "baby ya
kamata fah ki koma school tunda ki na iya taka ƙafar ban so ki rasa point
(maki)dayawa in ni na baki na banza sauran mushani ba za su ba ki ba"cewar Mr Arman
ya na kallon inda ya fi tsone mashi ido a duk jikin Munat Allah yayi shi da son
manyan breast sai kuma aka yi katari Munat na da su kuma ta na sakar mai su a banza
ta yadda kullum ta ke sanya ƙaramar riga.Baki ta ɗan turo tace "naji"lips ɗin ta ya
shafa da bayan hannu tayi saurin kallon tare da watsa mashi harara tace "miye kuma
haka?"yace "haba baby juste fah shafawa ne nayi "cikin ƴar masifa tace "toh ban so
ka bari ni ba ƴar iska ba ce"ta na gama faɗin haka ta miƙe ta na ɗan tsangala
ƙafarta ta bar shi a falo zaune da ya gaji ya miƙe dan kan shi ya bar gidan.
A hargitse ya shigo gidan Mami na tambayar shi lafiya bai saurareta ba ya shiga
haɗa kayan shi cikin sac, tenue guda biyu kawai ya zuba dan shi har ga Allah bai
son sakata shiyasa mutane dayawa ba su san soji ba ne sun yi tunanin Dr ne kawai
hatta Munat da ke ƙanwar shi ba ta daɗe da sani ba.
Har ƙasa ya duƙa ya kwashi albarkar Mami tare da shaida mata za su tafi mission
ne,sai da Mami tayi kuka Allah ya sani ba son wannan aikin ta ke ba cikin kuka Mami
tace "saboda wannan baƙar mission ɗin ya sa tun farko ban so ka tafi ba amman
Daddyn ku ya ɗaure ma gindi har da cewa ai aikin likitar ka ne za ka cigaba da
yi""ki yi baƙuri Mami ke dai ki yi min addu'a na tafi"ba jira cewarta ba yayi
tafiyar shi.

***MADAMA

Ƙasungurmin daji ne da ke can gabacin Niger kusan frontière Mali,daji ne da duk


wani mugu ya ke fargabar shigo shi saboda matakan tsaro na sojoji uwanda suka san
aikin su da aka sa.
Wannan dajin babu hutar lantarki in ka ga haske to énergie ne,ruwan garin kuwa sai
dai ace an godewa Allah domin marabar su da laka ɗan kaɗan ne a jawur suke.
Duk sojin da ka gani garin to na musamman ne ya iya aiki shiyasa ba kowa ake kawowa
ba duk da cewa sojawan ba su jin daɗin garin sai dai babu yadda suka iya.
A zaune suke gungun-gungun sojawa sai miter suke an kawo su wannan baƙin dajin da
alamu su yau ne farkon zuwan su, Mustapha da ke kwance ya na sauraren su sam shi
bai wani damu ba asali ma daɗi ya ji ko ba komi zai samu damar yin tunanin kuskuren
shi.
Ido ya rufe ya fara tuna moment ɗin su,wani irin yar ya ke ji bugun zuciyar na
ƙaruwa wanda zai iya cewa na tsaninin sonta ne da ya kama shi wata irin kasala ta
saukar mashi yayinda duk wata gaɓa ta jikin shi ta motsa jin kamar mode ɗin shi zai
canza ya bar tunanin ba dan ran shi ya so ba......
[29/05 à 17:13] MRS SADAUKI 💫: 🆓 19-20

Kiran sallah zuhur ya tasheta daga barcin gajiyar da ta ke,miƙa tayi tana mai
ambaton sunan Allah duk gaɓoɓin jikinta sun yi yami ga wani yaji-yaji da ta ke ji a
ƙasanta tsabar zafi da zugin da ya ke yi mata.
Dakyal ta ƙoƙarta ta miƙe ta fito sai gwale ƙafa ta ke ta na yamutsa fuska,madafa
ta nufa ta tarar da Mama ta gama girki sai garwashin da ta bari dan shinkafar ta
ida tsanewa.Wata tasa ta samu ta zuba ruwa ba'a ɗau lokaci ba suka yi zafi ta juya
a buta tare da shigewa banɗaki,sai da ta gasa jikin ta sannan ta fito tayi
alwala.Ta na tsaka da yin Sallah Mama ta shigo ɗakin,yadda ta ke kallonta ya sa
Maryam daburcewa babu shiri ta sallame sallar ta dubi mahaifiyarta."Ina kika tafi
Maryam na je gidan su Munat tace ita sam duk yau ba ta gan ki ba?"gabanta ne ya
faɗi cikin rawar murya tace "eh ta na barci shiyasa na wuce school da wata Friend
ɗin mu tace mu haɗu mu yi exercice"Mama tace "shine kika ƙi dawowa ki faɗa min
kafin ki tafi saboda kin girma kin isa yanka ko?"yadda Mama tayi maganar a hasale
yasa hajin cikinta murɗawa ba ta tantance ba sai ji tayi ta kai mata dundu a baya
"nace ki faɗa min gidan ubanda kika je "cikin kuka tace"Allah Mama school na tafi
to miyasa zan yi maki ƙarya?" "School shine sai kin shiga adaidaita nan da can?"
"Yi haƙuri ba zan sake ba"cewar Maryam tana sharɓar kuka,fita Mama tayi zuwa can ta
ƙwala kiran sunan Maryam jiki na ɓari ta nufi madafa abincinta ta miƙa mata ta juyo
ta koma ɗaki sai ƙoƙarin daidaita tafiyar ta ta ke amman kash tuni Mama ta gane.
Ta na shirin zama Mama ta shigo "mi ya same ki da ƙafa kike gwaleta?"plate ɗin
hannunta ta saki ba tare da ta shirya hakan ba ta shiga girgiza kai Mama kuwa sai
sake maimaita tambayarta ta ke,kwantar da Maryam tayi ta dubata duk da tirjewar da
ta ke.Zaman ƴan bori Mama tayi tare da fashewa da kuka kafin ta miƙe ta shiga
labtar Maryam kamar wacce Allah ya aiko kafin wani lokaci ta sauya mata kamanni
juyin duniya Maryam ta ƙi faɗin wanda yayi mata fyaɗe.
Sai da numfashin ta ya kusa barin gangar jikinta sannan Mama ta ƙyaleta ta bar
Maryam a kwance cikin halin buguwa.
Tashi tayi cikin ɗan ƙarfin da yayi mata saura ta ɗora ruwan zafi tayi wanka tare
da gasa jikinta musamman fuskar ta wacce tayi suntum kamar ta ɗan dambe😰,babu yadda
ta iya haka ta tutura abincin sannan ta sha maganin da Mustapha ya bata.

Washegari tun da safe sai ga Munat ta biyo mata zuwa school,Mama tace "ta na ɗaki
ta na barci ba ta jin daɗin jikinta ne" "ayya Allah bata lafiya"cewar Munat ta na
mai fitowa ta samu mai adaidaita ya kaita school.Bayan sun tashi Mr Arman ya ɗauke
ta a mota maimakon ya nufi gida da ita sai ya zarce da ita Plaza,abinci mai rai da
lafiya yayi masu oder suka ci suka ƙoshi sannan ya wuce da ita shopping.
Duk tarin kayan da ke cikin Mall ɗin Munat kasa ɗaukar komi tayi sai can ta hangi
portables kala-kala cikin madubi,da hanzarinta ta ƙarasa Mr Arman ya buɗe mata ta
shiga dubawa wata Galaxi ta nuna ya ɗauko ya riƙe sannan ya shiga zaɓar mata
dogayen riguna da riga da wando sai kayan barci ita dai Munat sai kallon shi ta ke
yadda ya ke kashe mata kuɗi ko zafin su bai ji nan matsayin shi ya ƙaru a zuciyarta
har ta ke jin duk wanda yace zai rabata da Arman ko kashe shi za ta iya yi kuma iya
wuya ta na tare da abun ta.
"Babu abinda kike buƙata ?"cewar Mr Arman lokacin da aka kai kayan wajen da za'a
biya kuɗin,kai ta girgiza dan ba za ta iya ce mashi chocolat ba,kamar ya shiga
zuciyarta haka ya sa aka haɗa mata kayan maƙulashe wanda hakan ya sa Munat kasa
ɓoye murnarta har sai da tayi kamar za ta rungume shi.
Tun a bisa hanya Munat ke cin biscuit shi kuma Mr Arman sai mayen kallo ya ke binta
da shi dan ba ƙaramin daɗin sakewar da Munat ke yi a gaban shi ba dan ya san da
gaban wani ne da ba za ta iya cin komi ba saboda kunya.Parking yayi a ƙofar
gida,kamo hannunta yayi ya shiga murzawa cikin nashi ya na jin hutar sha'awar ta na
sake hauhawa.Gyaran murya tayi ya ɗago ya kalleta da idon shi da suka canza
launi,baki ta turo tace "ka buɗe min na tafi gida na gaji"ta faɗi hakan ne dan ya
sakar mata hannu sanin hakan kuma ya sa shi murmusawa ya na mamakin yadda Munat ta
tsani ya riƙe ko da yatsanta ne da zarar kuma yayi haka sai sun yi faɗa.Cikin
kasala yace "wlh baby banda lafiya sosai kullum sai na sha wuya kafin barci ya
ɗauke ni"cike da tausayi ta dube shi tace "mi ke damun ka?miyasa ba za ka tafi
asibiti ba?"lumfashi ya sauke jin yadda marar shi ke ɗan sacewa riƙe hannunta kawai
da yayi ya na samun nutsuwa fuskar shi ya fara matsawa da zumar sumbatarta ta kawar
da kai tana jin wani irin baƙin ciki.
Sakinta yayi yace "tafi ki ɗauki kayan ki na bayan mota "ya faɗi hakan ya na kifar
da kanshi ga volant,ficewa tayi ba tare da ta ɗauki ko da tsinke ba ta shige
gida.Babu yadda ya iya haka ya ja mota ya tafi dan a halin da ya ke ba zai iya fita
ba ya tonawa kan shi asiri.

Munat na shiga ɗaki ta fashe da kuka ta ɗauki waya ta rubuta mashi text ```Kenan
dama ba dan Allah ka yi min shopping ba sai dan na rama maka abinda ka yi min?dama
ashe ba Sona kake ba sha'awata kake?to ka sani ni ba ƴar iska ba ce da kuɗi za su
ja ni in aikata abinda duk duniya na fi tsana,wlh Arman ka bani kunya a yadda kake
shiru-shiru ɗin nan na zata mutumen kirki ne to ka tai can ka ƙarasa ka nemi ƴan
iskan ƴan matan ka da ka saba iskanci da su Munat tayi maka nisa wawa sakarai da
bai san ciwon kan shi ba``` Mr Arman na gida kwance ya ji saƙo ya shigo wayar shi
da ya karanta ƙarara tashin hankali ya bayyana fuskar shi hannu na rawa ya mayar
mata ```Muna ni kike zagi?baby yanzu ke ki na iya rabuwa da ni ?``` cikin ƙuna rai
Munat ta mashi reply ```eh kai ɗin ƙarya nayi ba ɗan iskan ba ne?yo tare aka haife
mu balle na kasa rabuwa da kai?``` Mr Arman kasa maida mata yayi sai Safa da Marwa
ya fara dan nemo mafita.

Misalin ƙarfe takwas na dare sai ga Mr Arman shi da wata mata wacce kallo guda za
ka yi mata ka hango tsantsar kamar su da ita,a falo Mami ta sauke su cike da
karramawa.
Bayan ya gabatar da mahaifiyar shi gun Mami ya nemi son ganin Munat,ba tare da wani
tunani ba Mami ta nuna mashi ɗakinta tace "ta na ciki tun dawowar ta daga école ba
ta fito ba abinci ma ƙin ci tayi ƙila kai in ta gan ka ta ci"Mami ta faɗa tana miƙa
mashi abincin Munat na dare.
A kwance ya sameta tayi rub da ciki ta rungume pilow,tsayawa yayi ya na ƙarewa
halittar ta kallo yadda manyan mazaunanta suka cika ɗan ƙaramin towel ɗin da ta
ɗaura iya ƙugu sai hijab ɗin da ta saka kuma ta tattare shi zuwa gaba bai rufe baya
ba da alamu sallah tayi a haka,ƙarasowa yayi ya aje abincin kan coiffeuse ya zauna
a bakin bed ɗin,bayanta ya fara shafawa kasancewar barcinta bai yi nisa ba tayi
firgigit ta tashi zaune wanda yin haka yasa illahin jikinta motsawa.
Suman zaune Mr Arman yayi ganin yadda hijab ɗin ya lafe a dukiyar Fulanin ta masu
barazanar fashewa tsabar cikowar su,waro ido tayi cike da tsoro da mamakin ganin
shi.Jarumta ya aro tare da maida maitar shi ciki cikin son gamsar da ita sonta ya
ke ba sha'awata ba yace "ki tashi ki kimtsa Momina na falo tare mu ka zo dan nema
min auren ki tunda ke ba ki san banbanci so da sha'awa ba"ya na gama faɗa ya fice
dan ba zai juri zama kusa da ita a yadda ta ke haka ba.
Sororo tayi kafin ta zura doguwar riga ta fito,tsayawa tayi tana kallon matar da ke
sakar mata murmurshi wata kunya ce ta rufe Munat sai ta sunne kai ta na wasa da
zoben hannunta.
"Ƙaraso mana ƴata"cewar Momi ta na murmurshi kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki
haka Munat ta ƙaraso tare da gaida Momi ta na mai zaunawa ƙasawa.
"Masha Allah surukuta kyakkyawa ce to ka dai kula kar ka sake ɓata mata rai dan
babu ruwana da sakarci in tayi fushi can ka lalaɓata kai ɗaya ba zan sake rakiya ba
gun bada haƙuri"dariya Mami tayi tace "kaji shirme kenan fushi tayi da shi kaiii
Auta Allah shirya min ke"Momi tace "ke dai bari ɗazu ina zaune ya ke gayamin baby
tayi fushi da shi wai na zo na nema mashi auren ta"dariya kawai Mami tayi nan dai
suka yi masu sallama suka wuce bayan Mr Arman ya bata phone da sauran kayan da ya
sawo mata ɗazu.
Cike da murna ta kunna wayar sai ta ga ashe har ya caza mata ita ta ɗau caji,gidan
su Maryam ta nufa a daren nan ba ta zame ko ina ba sai room ɗin ta.A kwance ta
sameta ta lumshe ido hawaye na zuba kan fuskarta yayinda kuma bakinta ke motsi
alamun tana tasbihi ne ta na jan tazbaha.Taɓe baki Munat tayi tace "Tom yau kuma da
wani sabon kiciyi aka tashi?koko ciwon ne yasa tsoron Allah ya dirar maki a
zuciya?"duk da ta na cikin halin ƙunci bai hanata murmusawa ba dan sau tari ko
fushi ta ke Munat kan saukota.
Buɗe idonta tayi uwanda har yanzu ba su ida sacewa ba ta kai dubanta ga Munat wacce
ke tsaye tana shafa screen ta na dariya,wayar da ta gani a hannunta yasa Maryam
saurin tashi zaune tace "yaushe kika shigo cikin haske?ashe kin yi idanu?"hararar
ta tayi tace "da can makauniya ce ko?a'a daga ƙauye na ke ba cikin duhu ba.Wai ma
miye ke damun ki ɗazu Mama tace ba ki lafiya?"ta faɗa tana mai zaunawa bakin bed
sai kuma ta zaro ido tare da yin dariya tace "kan uban can wai kin ga yadda idon ki
suka yi luhuluhu kamar alala🤣"dundu Maryam ta kai mata ta na mai amsar wayar ba
tare da ta tanka ta ba ta shiga dubawa can kuma ta saya mata méga ɗin Moov ta buɗe
mata WhatsApp ita dai Munat kallonta kawai ta ke har sai da ta daidaita komi sannan
ta shiga statut ta rubuta sallama.
Munat tace "wlh ƙawata da ace yadda kika iya manipuler portable haka kika iya
Mathématiques da mun caɓa"hararta Maryam tayi tace "ai dai duk da haka na fi ki
iyawa"dariya ta kece da ita tace "dan Allah bari harare na Allah sai idon ki suka
yi kamar ƙosai irin bai soyi ɗin nan ba,am mu gani ko Moha ya na en ligne"rasss
gaban Maryam ya faɗi ta miƙa mata kasancewar ba wasu contact gare ta dayawa ba tayi
saurin kawowa ga compte ɗin shi.Hoton shi na kan profil (dp) ta jawo amman ya ƙi
buɗewa zuciyar Maryam banda das.das babu abinda ta ke ta matsu hoton ya buɗe sai
dai babu connexion😝 balle ta ga fuskar da ta ke mararin ganin duk dare da rana na
Allah.Kiran Mr Arman ne ya shigo hakan yasa Munat tayi mata sallama tana mai barin
gidan da sauri,ta na fitowa ta hangi motar Mr Arman ƙofar gidan su cike da mamakin
abinda ya maido shi ta ƙarasa ba tare da ta ɗauki kiran ba.
Seat ɗin gaba ya buɗe mata ta na zaunawa ya ja motar da gudun bala'i ba tare da ya
jira cewar ta ba,cikin tsiwa Munat tace "gidan uban wa za ka kai ni ?wlh ka mayar
da ni gida in ba tashin hankali kake son sayarwa kan ka ba da kuɗin ka"Mr Arman ko
kallonta bai yi ba ya cigaba da draving burin shi bai wuce ya gan su a gidan cikin
yanayi ba ya matsu ya ji ta ajikin shi.
Horne yayi mai gadi ya buɗe ya cinna hancin motar cikin madaidaicin gidan,"fita mu
je ciki ki ga abinda ni ke son gwada maki amman kike ta min"cewar Mr Arman cikin
ƙarfin hali kafaɗa ta maƙe cikin nuna alamar ba tajin tsoro ko fargaba tace "Ni za
ka yiwa wayo to babu inda zan je"ganin za ta ɓata mashi lokaci ya zagayo ya
sungumeta sai zillewa ta ke amman yayi mata riƙon da ba za ta iya ƙwatar kanta
ba.Sai da ya shiga falo sannan ya dire ta tare da sawa ƙofar key da gudu Munat tayi
ƙurya ɗaki tana shirin rufe ƙofar ya bangaje ta,hannu ta fara yarfawa tana girgiza
kai.Cikin son kwantar mata da hankali ya fara nufota ya na cewa "juste romance baby
wlh ba abinda zan yi maki kawai massage za ki min"ya faɗa ya na mai fizgota zuwa
jikin shi.....

*ƘARSHEN FREE PAGE MAI SON CIGABA YA TUNTUƁI* +22795045822 500 ne kacal😤

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin


na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga
kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku

This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there


Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to
download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography
including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490
its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng


to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

You might also like