Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 142

24/10/2018 à 22:00 - Vous avez créé le groupe “👸PRINCESSE👸”

27/02/2019 à 17:29 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI💑

_Samira Harouna_

*Wannan labari ne da na yishi a farkon fara rubutu na, amma abisa wasu kura kurai
da ke cikin waccen rubutu sabida rashin sanin miye rubutu a waccen lokacin, hakan
yasa zan sabinta maku shi ta hanyar canza Salan rubutun da ingantashi fiye da na
baya tare da canza wasu abubuwa daga ciki dan jin dad'in ku*

💗💗💗💗💗💗
Bismillahi Rahaman Rahim
💗💗💗💗💗💗

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da_ _amana insha Allah)_ 🤜🤛

*Page*

1⃣5⃣
1⃣-5⃣

Duk girman gidan bai hana shi cika ba sabida hidimar bikin da ake, kowa cikin
farin ciki ya ke babu bakin ciki a nata hayaniya, shagalin biki kenan na auren da
za'a d'aura nan da Minti Ashirin, Amare ne guda hud'u da angayen su.

ban an kara ba naji an bige ni har saida alkalamina ya fad'i k'asa, daga kai nayi
naga ko wace shedaniyar ce, wata kosansan Budurwa na gani sai gudu take tana
waiwayen bayanta kafin na kula naga wani 'Kakk'arfan Saurayi da gudu yana biyar ta
da belt a hannu, bin bayan su nayi har cikin katon falon da ta shiga in da taci
k'aro da wata kyakyawar tsohuwa ta b'oye bayanta tana fad'in,

"Dan Allah hajia ki taimake ni kice karya dake ni" tsaye yayi yana huci, cikin
zafin ray ya kai mata duka da belt kin hannunshi yanda ya sauka a bayanta ne yasa
ta saki k'ara tana Ihu, tsohuwar ce da ranta ya b'ace tace" kai SALMAN ashe ba kada
hankali wai miyasa kuke hakane kamar wasu Kananan yara?" juyawa tayi ga yarinyar ta
jawo ta tace" mi kika mashi nasan dai haka kawai baya biyo ki ba tunda ba mahaukaci
bane shi?" cikin kuka ta fara mata bayani" wallahi hajia kawai muguntar sace ta
tashi, daga naje karb'ar charger ta wajen yaya MUBARAK shine fa kawai yake kallo na
daga nace ya kama bakin shine wai ya biyo ni" tana rufe baki ya kama kunnanta cikin
masifa yace" kinji ko hajia dan ta raina ni ni zata ce wai na kama baki na, ina
abin kallo a jikin ta yake, wallahi sai na karyaki in kika k'ara shiga harkata
shedaniya kawai" fizge kunnen''ta tayi cikin zafin nama ta mike tsaye zatayi magana
kuma sai ta ruga a guje sabida d'aga belt kin yayi zai buga mata, juyawa yayi shi
ma yabar wajen.

Saïda tabi kowannen su da kallo kafin tace" na samu hanyar da zanyi Maganin ku
tak'adaran yara kawai, kuna yan uwa amma kun zama kamar b'era da mage, Insha Allah
Komai ya zo k'arshe daga yaou, idan kuka zama d'aya zaku daina duk, wannan shirmen"
wuce wa tayi d'akin kakan yaran inda bata gushe'ba har saida burin ta ya cika.

09:00 aka d'aura auren Amare guda hud'u gami da wadanda aka kara suka zama biyar.

*to yan uwa ya zata kasance idan aka d'aura auren wadanda babu su a cikin jadawalin
d'aurin auren yaou?*

Yan Uwa kuna san labarin in'ci gaba?

~Sai naji daga gare ku.~


27/02/2019 à 17:29 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI💑

_Samira Harouna_

*page*

0⃣6⃣1⃣0⃣
0⃣6⃣-1⃣0⃣

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da_ _amana insha Allah)_ 🤜🤛

Sank'ira ne ya fara fadin"(masha Allah, Allah ya nuna mana an d'aura wannan aure na
amare da angaye, aure na farko shine tsakanin,Mubarak Siraj Manu da Nadiya Yahaya
Manu, na biyu tsakanin Khamis Yahaya Manu da Jawahir Suleiman Manu, na uku shine
tsakanin Shamsudeen Suleiman Manu da Hafsat Siraj Manu,sai na hud'u tsakanin
Nouradeen Salihu Manu da Khairat Yunus Manu, sai na biyar tsakanin Salman Yunus
Manu da amaryar shi Zeinab Abdul-Hamid Manu wato (Ummi)."

Shiru ne ya ratsa illahirin mutanen da ke wurin dan jin aure na biyar,Kallan kallo
kawai a keyi saida kowa ya tabbatar sannan aka fara farin ciki, wasu da hukuncin
bai masu ba kamar zasu fashe dan bakin ciki Hajara uwar gidan baba yahaya taso ace
an had'a Salman da Rumana dan taci buri akan auren su, Ummi da ke d'aki ta nata
tsokanar su
Jawahir tana masu shegantaka, yayarta SA'ADATOU da RUKAYYA yayar Jawahir suka shigo
suna Bud'a suna murna a nanfa suka fad'a masu halin da ake ciki, Ummi da tak'i
yarda fitowa tayi tsakar gida tana tambayar Mahaifiyar ta wato HAWATAN(Hawaou)
kasancewar ta buzuwa yasa ake kiranta da Hawatan, tin'da tace" eh Ummi da gaske an
d'aura aurenki kema" cikin nuna rashin yarda tace" haba la mamma ta yaya za'a
d'aura aure na haka kwatsam ai ba haka ake ma kowa ba sai ni za'a fara kai na?"
hannunta ta d'ora a kafad'unta tace" kinga kiyi hak'uri kinji wannan hukuncin kakan
kune, kuma ai ba yaou zaki tare ba ke" jaye jikin ta tayi tana fad'in" a'a la mamma
hakan ba zaiyiwu ba miyasa sai yaya Salman za'a aura min"? da gudu ta koma d'akin
da amare suke ta kwanta ta fara ai kin kuka kamar ranta zai fita, k'awayenta kuma
yan uwanta sunyi ban hak'urin amma ina sun kasa dan haka suka rabu da ita.

tunda a kace Ummi na kuka hajia Babba tace a k'yaleta zata ji da ita, d'akin ta
shigo ta tayar da ita zaune saïda tasa ta daina kukan sannan ta fara magana cikin
nutsuwa da dubun hankali" Zeinab ki nutsu ki saurare ni kiji abinda zan fad'a maki
kinji shaleleta"Ummi shi aure da kuke gani darajar shi ce tasa Ubangiji ya hallata
shi a tsakanin bayin'sa, darajar aure da kuke gani tafi Karfin tinanin ki sabida
daraja da matsayin shine yasa hatta bishiya zakiga an mata aure kafin ta fara toho,
sannan aure sunna ce mai k'arfi daga sunnonin Manzo ( S A W ) kuma duk wanda ya
raya ta to ha'ki'ka zai samu babban rabo, sannan aure ya nada matuk'ar mahimmanci a
rayuwar mu wanda idan da babu shi da Ummi bana jin da yanzu akwai Duniya dan
bad'alar da za ayi ba kad'an bace a Sakamakon haka kuma Allah Zai iya kifar da
duniyar ma Baki d'aya"

" Ummi wani abun farin ciki anan shine duniyar nan munacin Albarkacin Annabi
Muhammad (S A W) ne sannan yara ma suna taka rawa a cikin rangwamen da Allah ya
keyi mana, to yanzu Ummi in har hakane mi zaisa ki k'i aure har ki tsaya kina bata
lokacin ki wajen kuka, ke da zaki samu wannan manyan mayan rabon, Bugu da k'ari
kuma Salman dan uwanki ne kinfi kowa sanin tsakaninki da shi, nice nan na haifi
iyayen'ku maza da ke da shi to miye matsala a ciki, nasan dai za kice sabida ba
bakwa shiri ne da shi, wannan kuma mai sauki ne In har ki kayi abinda zan fad'a
maki" share Hawaye tayi tace"hajia a gaskiya ba'amin Adalci ba, ta yaya za'a d'aura
min aure da mutumin da Kusan tsakani na da shi kunsan mugu ne shi ko kad'an ba yada
tausayi" kai ta girgiza tace" kash, Ummi ina baki kina rok'o, Salman fa ba kamar
yanda kika d'auka bane kece kawai kike masa Kallan mugu shi ma kuma ke kike ja ma
kan ki sabida kinsan abinda baya so amma se kika maida wannan abu kamar 'dabi'arki
duk lokacin da kika gan shi sai kinyi" amma hajia to miyasa za'a aura min shi ni
gaskiya bana san shi?" Ummi kiyi Hak'uri kamar yanda nafad'a maki, idan har kika yi
hak'uri kika bi Umarnin mu to basai na fad'a maki ba kisan za kifi kowa jin dad'in
Alhaji, amma in kika ki kika bijere tofa kinfi kowa sani wallahi zaki shiga
matsala" Ummi ke da Salman duka jikoki na ne naji dad'in wannan HAD'IN AUREN dan
ba'ataba irin Shi, ki kwantar da kanki ki zauna lafiya da dan uwanki kiyi masa
biyayya domin yanzu shine k'ofar shigar ki Aljanna, kiyi duk abinda yace in dai
kina so ki rabauta Duniya da Lahira, ki kyautata mashi idan kina so Allah ya yarda
da ke ya saki a cikin bayinsa mafifita, ki zama mace ta gari a wajan Mijinta ki
zama mace mai biyayyar aure ki zama yar Aljanna" bayanin da Hajia tayi gaba d'aya
amaren sun k'aru da shi kuma sun d'auka saidai a wajan Ummi ba haka abin yake ba.

Tunda Salman yaji sunan sa ya fito a cikin wannan résult wanda shi a wajan shi
kamar an kafe sunan yan wuta ne kuma sunan shi ya fito, rud'ewa da kid'imewa da
tashin hankali ya ma rasa wanne ne a ciki ya shiga, zai iyya zama da kowace irin
yarinya a duniya daga ciki har da karuwa amma banda Ummi dan kuwa yarinyar ta mugun
raina shi hakan yasa ya tsane ta duk da suna yan uwa kuma makotan juna yana wuni
gidan su tana wuni gidan su amma hakan bai sa suka jitu ba, Hakuri da rarrashin da
Abokan shi da sauran angayen ne suka fara bashi ganin ba zai'iya ba dan bâ abu bane
mai yi yuwa yasa ya shiga motar shi ya kama gaban shi ko ya ji Sauki a ran shi.

Yan Uwa dai bakin su suke sha babu kama hannun yaro, har lokacin da aka gama kintsa
amare izuwa gidan mazajen su, a lokacin ne Alhaji USMANE( Manu) ya tara su a
Babban falon su ya masu Nasiha mai ratsa jiki tare da gargad'in su anan Kowane ya
kula da Hakkin da Allah ya d'ora mashi akan shi na dab Abokin zaman shi, sannan ya
maida akalar akan Ummi da Salman, wanda ya kwadaitar da su akan in dai sun zauna
lafiya to za suji dad'in zama da shi in kuma aka samu akasin haka to akwai matsala.

Mahaifiyar Ummi ta nemi Alfarma wajen Alhaji akan ya amince Ummi ta zauna har nanda
sati biyu sai ta tare,amma yace sam baiga dalilin da zata zauna gida ba da aure a
kanta dan haka sati 'daya ya basu akan sun gama duk yan tsirfe tsirfen su kafin
nan.

*To Allah ya kai mu ranar Tariyar nan muga mi zai faru*


27/02/2019 à 17:29 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_ 🤜🤛

*Page*

1⃣1⃣1⃣5⃣
1⃣1⃣-1⃣5⃣

An nufi da amare gidan mazajensu inda Ummi kuma suka tafi gidan su tare da
Mahaifiyar ta, dama gidajen suna kusa ne, suna shiga d'akin ta ta shiga ta soma
wani sabon kuka har saida bacci ya d'auke ta duk da La mamma najinta amma ta
kyaleta dan yanda ta d'auki Salman bata d'auki Ummi haka ba shiyasa bataga abin
daga hankali a ciki ba.

Cikin dare Ummi ta farka ta fito falo ta bud'a frige ta d'auki madarar shanunta
wanda Mahaifin ta ya sabar mata shan ta tin tana karama yanzu haka in bata shaba
har kan ta ke ciwo, tana sha takoma d'aki tayo alwala tayi Sallah Isha'i da bata
yiba ta d'auki AlQur'ani tayi karatu sannan ta kwanta.
tana tashi da safe La mamma tasa aka fara mata gyaran jiki mai zafi dan ba suda
lokaci wanda aka basu kad'an ne.

kwana uku aka kwashe har yanzu Basu had'u da Salman ba, Abba ne kad'ai ke
rarrashinta da su hajia idan suka zo gidan sai kuma Mamar Salman kin wato Hajia
HALIMA, yaou kam Mahaifiyar Salman ta tiso shi gaba akan yazo yaga matar shi ba
karamin d'aci yake ji ba idan yaji sun kira Ummi da matar shi haka ya daure ya zo
gidan, tin'da tayi Sallah Magriba bata saké fitowa ba sabida kiran da JAMAL ya
mata, bud'e k'ofar da taji yasa ta saurin aje wayar tana muzurai duk alamun rashin
gaskiya ya bayyana a tare da ita, Kallan tuhuma Salman ya ke mata har ya k'araso in
da take cikin rashin yarda yace,

"mi ki keyi da wa kike waya?" wata harara ta dalla mashi tace" to ina ruwanka da ni
miye matsala ka?" hannunta ya fizgo da k'arfi ya karbi wayar ya duba number ce babu
suna dan haka yace" da wa kike waya?" cikin b'acin rai tace" a'ah Malam wai miye
haka ina ruwanka da ni to?" cikin hassala ya matse mata kumatu yana fad'in" bana
ciki da iskanci kar ki d'auke ni sakarai, ni yanzu mijinki ne dole nasan mi kike ai
katawa" duk da tayi 'kok'arin fizge hannunta amma ta kasa dole tace" aw kenan kai
ka d'auka da gaske ni matar kace, to wannan kishi ne ko mi?" sakinta yayi yace"
Allah ya tsareni nayi kishi a kan ki, wallahi ke kinsani in banda darajar aure ke
baki isa ba kira ki da matar aure na ba" nunata yayi da wayar yace" daga yaou babu
ke babu waya har lokacin da naga damar ki rik'e" wucewa yayi zai fita da sauri ta
sauko daga gadon ta tare gaban shi tace" kaga Malam dan Allah bani waya ta sai kace
wani kai ka siya min" nuna mata wayar yayi yace" ki k'wata mana idan kina da
k'arfi" shiru tayi tana k'are mashi kallo tasan bazai bata ba dan haka tana ganin
yasa ta cikin aljihun rigar shi sai ko tasa hannu, cabke hannun yayi ya murd'e mata
yan yatsu yana fad'in" marar kunyar banza, sai ki saka ma mutum hannu a cikin
aljihu wannan salan halin b'era kenan" duk da tana jin zafin murd'ar da yake ma
hannunta bai hana tace" b'eraye dai ai kai ne ma babban b'era gashi kamin gaba da
waya" tsaki yayi ya gitta ta ya wuce ya bar gidan.
su Abba ne zaune suna cin abinci kallan La mamma yayi yace" wai ina Ummi take ne?"
tab'e baki tayi tace" tana d'aki mana tunda ta d'ora ma kan ta larura" girgiza kai
yayi yace" ki dinga hakuri mana kema, kiyi la'akari da yanda nata auren ya kasance
ba kamar na kowa ba, itace ta farko a famille nan da aka mata aure babu saka rana
bare raba goro sai ki mata uziri ko" k'ara tab'e baki tayi tace" amma miye na
damuwa a ciki Salman fa dan uwanta ne tasan shi tunda tare suka tashi to miye saban
abu a ciki?" hakane amma kuma kinfi kowa sanin tsakanin ta da shi, ba shiri suke
ba" to ai auren da aka had'a su kaga sai su fara shirin watakila ma su so junansu
nan gaba kad'an" to Allah yasa haka, idan haka ta faru ai za mufi kowa jin dad'i"
gaskiya ne Allah ya tabbatar da Alkairi, ya basu zaman lafiya" Ameen Inji Abba.

haka aka k'ara wani kwana ukun ana gobe Ummi zata tare an gama kimtsata yanda ya
kamata kama daga kunshi kitso gyaran jiki har dama gyaran d'aki, gobe ake jira tayi
saidai duk abinda Allah ya tsara zai faru to babu makawa, Ummi ce da kewa da damuwa
ta mata yawa ta d'auki wayar La mamma ta kira Jamal sabida irin soyayyar da yake
mata tana jin dad'i dan shine na farko da ta fara soyayya da shi, hira sukayi sosai
har saida yace mata" kinsan wani abu a gaskiya ina so na saké ganinki?" gabanta
taji ya fad'i amma sai ta dake tace" um a gaskiya bazai yiwuba" da sauri yace"
miyasa Ummi baki san gani na ne?" cikin i'ina tace" ba haka bane kawai dai akwai
matsala ne" matsala kuma ta mi?" rasa abinda zata fad'a mashi tayi dan haka yace"
kinga Ummi zan zo gidan ku yanzu ruwan kine ki fito ko ki 'ki fitowa amma kisani
idan ma baki fitoba to ni har cikin gidan zan shiga in da na ajeki a ranar da muka
fara had'uwa da ke" kashe wayar yayi yabar Ummi baki bud'e gabanta ya tsananta
fad'uwa.

Minti talatin kenan Jamal ya kira Ummi yace gashi nan K'ofar gida ta fito ko ya
shigo tunda shi da aure yake santa, cewa tayi ya jira ta a bayan gidan su tana
zuwa, duk da tace mashi tana zuwa amma ta d'auki Kusan minti sha biyar kafin ta
fito ba tare da kowa yaga fitar taba, tana so ta fad'a mashi Komai akanta da auren
da aka d'aura mata dan taba shi hakuri suyi sallama.

*To Allah ya kauda b'acin rana*😞👏


27/02/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜🤛_

*page*

1⃣6⃣2⃣0⃣
1⃣6⃣-2⃣0⃣

zaune ta same shi cikin mota k'afafun shi a waje, yana ganin ta ya fito ya rufe
k'ofar bakin shi har kunne, gaissawa sukayi a gurguje Ummi tace" am Jamal na fito
ne dan na fad'a maka ko wacece ni, muna cikin halaka Jamal" cike da mamaki yace"
halaka kuma wace irin halaka Ummi?" kanta k'asa tace" Jamal ni fa ba yanda ka
d'auka b'ace, a yanzu haka ina da aure a kai na kuma na fito dan na fad'a maka
haka, Dan Allah muyi hakuri da juna kaje ka nemi wata wacce ta fini,watakila ita ce
mafi alkairi a gare ka" cikin wani irin yanayi yace" a'a Ummi dan Allah karki min
haka, wallahi ina sonki, kuma na fad'a maki Komai a game da ni kinsan koni waye
kinsan labaran soyayyata har guda hud'u, Dan Allah Ummi ki amince ki aure ni ko
zaki canza wannan labaran nawa marasa dad'in ji, idan kuma baki so na ne basai kin
b'ullo min ta wannan hanyar ba"
"A'a Jamal ba haka bane, wallahi an d'aura min aure yanzu haka gobe zan tare idan
Allah ya kai mu" haba Ummi kar ki raina min Wayo mana, ki fito ki fad'amin gaskiya
kawai" cikin kossawa tace" kaga Jamal na fad'ama gaskiya ina da aure dan Allah kar
ka saké kira na kuma ka manta da ni a rayuwarka, ka gafarce ni ban d'auka haka zata
faru ba" zata wuce ya rike hijabinta yayi dai-dai da karasowar Alhaji Manu wanda ya
tsinkaye su tun daga nesa amma yana tinanin ko su waye, yana ganin haka ya kunna
tocilar shi dake hannunshi, da sauri Ummi ta juya sai ko yaga fuskarta, Ummi ma ba
ganin Alhaji ta tsora ta sosai kubce hijabin''ta tayi ta ari na kare da gudu ta
shiga gida, yayi dai-dai da fitowar La mamma da Abba tare da Salman suna tambayar
k'annanta dake wasa a tsakar gidan.

yana ganin ta daka da gudu ya ciro wayar shi ya kira AUWAL Babban d'a ne ga baba
Yahaya, yana d'auka yace" kai kana ina?" cike da ladabi yace" yanzu na shigo gida
zan gaida su Mamma" to mu had'u da kai gidan baban ka Hamidu" bai ko amsa ba ya
kashe wayar, tunda Ummi ta shiga d'aki ta kasa zaune ta kasa tsaye dan tasan yaou
kam sai ta Allah babu abinda zai hana a dake ta a gidan nan, Addu'a ta ke koda za'a
dake ta to kowama ya dake ta amma banda yaya Auwal.

kai tsaye falo ya shiga ya zauna yana 'kare ma su La mamma kallo babu wanda ya iya
tambayar shi lafiya saïda Auwal ya shigo sannan ya kalli La mamma yace" Hawatan kin
bani kunya banyi tsammanin haka daga gare ki ba,na d'auka amanar da na baki zaki
kula da ita ashe ba haka bane" cikin rashin fahimta jiki na rawa La mamma tace" mi
kuma ya faru wallahi bansan Komai ba Alhaji" maida kallan shi yayi ga Salman yace"
kira min ita"wucewa yayi yana tinanin komi ta aikata hatsabibiyar oho.

yanda yaga tana ta safa da marwa yasa yace" wace tsiyar ki kayi?" hararan shi kawai
tayi taci gaba da kai da kawo warta," to wuce muje Alhaji na kiran ki kuma Allah
yasa ya bani bulalar da kai na na zane ki" yan cikinta ne suka kad'a da sauri tace"
bulala kuma?" gira ya daga yace" ai ke da kinga Auwal kinsan yana tare da bulalar
shi sabida ire irenku" Inna Lillahi Wa'inna Ilaihi Raju'un na shiga uku, Dan Allah
yaya Salman ka taimaka min wallahi babu abinda nayi, kace karya dake ni" ke wuce
mu tafi ni babu ruwa na nasan mi kika aikata, ina mijinki amma bansan fitar kiba
saidai naga kin dawo" wucewa yayi ya bar tanan kamar zatayi fitsari daga tsaye, jin
muryar Alhaji ne yana fad'in" kaga kace in ba zata fito ba ni sai naga shiga na
fiddo ta" a hankali ta bud'e K'ofar d'akin tana raba idanu ganin Auwal ya k'ara
kad'a mata yan hanjinta, kusa da La mamma ta durk'usa kamar zata shige jikinta,
cikin b'acin rai Alhaji yace" Ummi ni zaki zubarwa da mutunci, ni zaki tozarta a
unguwar nan da aurenki ki fita kije wajen wani dan Iska har yana rik'e hannunki" to
bari kiji wallahi baki isa ba ko ubanki bai isa in shinfid'a doka ba ya 'ketare
bare ke yar da ya Haïfa" carbin dake hannunshi ya tilla ma Auwal yace" zanemin ita
ta yanda bazata saké tinanin saba Umarni na ba nan gaba" tsabar rashin imani da
tausayi yasa Auwal jayo Hijabin Ummi ya fara tsula mata carbi kamar Allah ya
aikoshi, Ihu take tana ba Alhaji hakuri amma ina ga Abba zaune amma babu yanda
zaiyi koda Ummi taji duka yana ratsa har cikin ruhinta sai ta fara kiran sunan"
wayoo La mamma kice yayi hakuri wallahi bazan sake ba, Abba ka bashi hakuri wallahi
babu abinda nayi, wayoo yaya Salman dan Allah kace yayi hakuri" har saida hijabinta
ya fita ta zama daga ita sai doguwar riga, ganin yanda take ta k'o'karin shigewa
jikin Auwal tana so ta rike carbi yasa Salman jin ba dad'i, mikewa yayi ya rik'e
carbin ya kamo Oummi da hannu daya ya kalli Alhaji yace" Dan Allah ayi hakuri ba
zata saké ba Insha Allahu" mikewa Alhaji yayi tsaye yace" k'warai ba zata saké ba
kamar yanda ba zata k'ara koda Awa daya ba a gidan nan ba" kallan ta yayi ya daka
mata tsawa" wuce mu tafi" raba ido tayi dan bata san inda zata wuce ba duk ta
rud'e" zaki wuce ko sai'' na sa ya d'auko min ke?" da sauri ta d'auki hijabinta
jiki na rawa duk zugi ta keji a jikinta saïda ta kai bakin k'ofar d'akin ta juya ta
kalli su Abba cikin kuka tace" Abba ku yafemin dan Allah, La mamma kiyi hakuri" da
sauri ta bar wajen suna fita K'ofar gida Alhaji yace ma Salman " d'auko motar ka na
kai ta gidan ta" mamaki yasa Salman yin tsaye amma daya mashi tsawa saiya wuce babu
shiri ya d'auko mota, basu tsaya ko ina ba sai sabon gidan Salman da duka jiya ne
aka kammala gyaran shi.
Yana iza k'eyar ta yace Salman ya maida shi gida suna tafiya Ummi ta fad'i a tsakar
falon ta fashe da kuka tare da k'ara kamar ta kashe kanta take ji.
27/02/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_ 🤜🤛

*page*

2⃣1⃣2⃣2⃣
2⃣1⃣-2⃣2⃣

Koda Salman ya shigo ya sameta nan bai tankata ba ya wuce d'akin shi, Oummi kam
bata farka ba sai da aka gama sallah asuba tana tashi zaune tayi akan kujera tana
tinanin inda zatayi alwala tayi sallah, zazzab'i ne ruf ya rufe ta da k'yar ta fito
farfajiyar gidan ta samu panpo tayi alwala ta dawo falo tayi sallah ta koma ta
zauna.

Har saida gari ya waye sannan Salman ya shigo gidan daga massalaci lokacin har
bacci ya saké d'aukar ta saman kujera, kallanta yayi ya kalli agogon dake mak'ale a
bango dab da ita yazo ya kama kafar ta ya fizgo har saida ta fad'o k'asa, a tsora
ta bud'e ido ta sauke a kanshi, gyara zamanta tayi cikin muryar da tasha kuka tace"
miye haka dan Allah?" cikin fad'a yace" Dallah malama tashi kiyi sallah kin wani
saki baki kina bacci har safiya tayi" hararan shi ta murgud'a baki tace" amma ai
nayi sallah" tsayuwar sa ya gyara yace" to naji abin karyawa fa, ko shima harkin
gama?" tashi tayi tsaye tace" haba dan Allah wane irin abin karyawa kuma, ni ban
dafa ba kuma gaskiya ba zan'iya ba" tana rufe baki ya kama kunnenta ya murd'e yace"
karki saké bari saina maki magana akan abin karyawa, ki tashi kiyi abinda nasa ki
idan kin gama zan fada komai a kaina dan bana san shirme" ganin batada niyar tashi
yasa ya d'aga carbin shi zai tsula mata da gudu ta shiga cuisine kin ta fara had'a
abin kari.

Dak'yar ta kammala sabida zazzab'i gashi duk jikin ta ciwo yake sabida dukan da
tasha, falo ta same shi zaune cikin shiri a jiyewa tayi ta juya zata koma cuisine
tunda har yanzu bai bata d'aki ba," ke zo nan" a hankali ta dawo zaune tayi
hankalin ta a tv, cikin b'acin ray yace" miye wannan kika dafa?" wani banzan kallo
ta masa tace" aw kai bakasan ko miye wannan ba?" tassss ya kwashe ta da mari yana
fad'in" ke dan kin raina ni na zauna ina jiran abinci tsawon minti ashiri, amma a
k'arshe ki kawomin wannan abar a matsayin abinda zanci na fita, to bari kiji ni ba
haka nake kayana ba komai ina yinshi da tsari ki buda kunnuwanki kiji abinda zan
fad'a maki" ganin gaba d'aya hankalin ta na kan tv yasa ranshi ya k'ara b'acewa da
k'arfi ya fizgota ta fad'o k'asa kusa da shi yana kallan idanta yace" ki nutsu idan
bâ haka ba wallahi jikin ki zai dinga fad'a maki kinji na fad'a maki sakarya
kawai."

Kuka ta fara haka shi kuma ya fara zana mata sharad'an shi da k'a'idojin shi kamar
dai....,

" ki tabbatar kowace safiya ina samun abun Kari na da missalin k'arfe 08:00, 08:01
tofa bazan d'aga maki k'afa ba, sannan k'arfe 14:00 na rana ki tabbatar abinci ya
kammala kafin na shigo, haka zalika da k'arfe 20:30 na dare kiyi k'ok'arin gamawa
kafin minti d'aya ya hau sama"

"Sannan ya zama wajibi gareki da kin idar da sallah asuba kije har d'aki na ki
gaishe ni, sannan kowane dare kafin ki kwanta bacci sai kin tabbatar kin kaimin Tea
mai kayan kamshi a ciki sannan ki kwanta."

"Sannan ba komai nake ci ba, da safe inasan karyawa da abu mai nauhi,da rana kuma
inasan abu mai romo,da daddare kuma zaki iya kawomin komai naci amma banda
kifi,Kwaï,tuwo,wake, bana cin su da dare."

"Sannan kowane sati ina azumin litinin da alhamis, dan haka kowane bud'a baki ina
bukatar salade, lemon zob'o,kayan marmari, haka kuma duk juma'a zaki dinga dama min
fura da rana ina sha, sannan kowace juma'a ina yanka dabba sabida sadaka dan haka
zaki dinga sarrafashi ta hanyar data dace sai ayi sadakar, sannan kowace asabar ina
gayyatar abokaina suna zuwa muci abinci dan haka zaki dinga dafa abinci mai yawa."

"Sannan kowace juma'a zaki dinga wanke min kaya na kanana sannan ki gogemin
su,sannan kowace safiya idan nafita dole zaki gyaramin d'aki na kafin na dawo,
wannan shine tsari na kibi ki zauna lafiya, ki k'i bi kisha wahala dan nidai ba zan
gaji da dukan ki ba, sannan ki d'auke wannan abar dan bata daga cikin tsari na
wannan saike jaka."

Wani kallo ta watsa mashi tace" jaka kuma, ni d'in?" e ke d'in koba jakar bace?"
kauda da kai tayi gefe ba tare da yanda zai jita ba tace" jakuna dai" mikika ce?"
girgiza kai tayi ta mike tsaye tace" to Malam naji dokokin ka amma kasani ba
zan'iya ko d'aya ba, kaji mutum sai kace wani shiya haifeni ko ya hallice ni da
zaka zauna ka zana min dokoki" sa'ar cabko hijabinta yayi ya zaunar da ita ya rik'o
hannayenta duka biyu, saidai zafin da yaji a jikinta na zazzab'i yasa yace" kar
Allah yasa kiyi ko daya d'aya daga cikin abubuwan da na zayyana maki kigani saina
lahira yafiki jindadi shashasha kawai mai k'wak'walwar kifi." tsallaka ta yayi ya
wuce da sauri tace" to ina zan zauna ni kuma, ko d'akin naka zan dinga kwana?"
juyowa yayi yasa hannu aljihu ya ciro makullin ya jefa mata, tayi saurin cab'ewa
kamar masu jira a tare suka aikama juna harara Oummi harda tukwicin murgud'a baki,
wucewa yayi ya barta nan, d'akin ta ta shiga dak'yar tayi wanka sabida ciwon dake
jikinta ta shirya cikin riga da wando ta kwanta kuka ta dinga rerawa sabida
takaicin abinda aka mata gashi shi kuma ba imani ne da shi ba.

_Tofa wannan zama_


27/02/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

Samira Harouna

```Dedecated to My Meelat``` 😘

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

2⃣3⃣2⃣4⃣
2⃣3⃣-2⃣4⃣

Komawa tayi ta kwanta dan ko zai kasheta ba zata yi abinda yace ba, yana fita gidan
su ya nufa ya fad'awa Mahaifiyar shi duk abinda ya faru a daren jiya, ta tausaya ma
Ummi, ta kuma k'ara jaddada mashi ya rik'eta amana, d'akin shi ya shiga ya ida
harhad'a sauran kayan shi yace zai aiko azo a d'aukar masa.

Haka ma daya shiga gidan su Ummi ya gaishe da su La mamma ta had'a mata sauran
kayan ta yace zai aiko a d'auka anjima.

Tana bacci a d'aki taji bugun k'ofa, cikin magagin bacci ta taso ta bud'e, matashin
saurayi ne ya kawo kayan su, karb'a tayi ta koma d'akin nata tai masu wajen zama,
nashi kuma ta bar su nan kafin ya dawo, kwance tayi tana tunani shikenan ta rabu da
gida kenan har abada sai in taje da ziyara, tunda take bata taba jin labarin wacce
aka kai gidan miji kamar ita ba, kuka ne ya kwace mata ta nayi tana ajiyar zuciya
har bacci ya saké d'aukar ta.

Ummi na gama sallah azahar ta shiga cuisine ta dafa indomie, badan ita take so ta
ci ba saidan k'iwa, tana ci ta koma ta kwanta nan saman kujerar bacci ya saké
d'aukar ta, ruwa da taji an watsa mata yasa ta tashi a tsora ce tana piki piki da
ido, ganin Salman yasa ta fashe da kuka tana fad'in" ni dama nasani wallahi dan ka
dinga min mugunta ne yasa ka aure ni, haka kawai ina zaman zama na an wani had'a ni
da kai, gashi kana neman kashe ni" tsaki yayi kafin ya zauna idonshi a tv yace
"kawo min abinci na," wata harara ta galla masa tare da juya baki tace "ban dafa
ba, ai dama na fad'a maka ba bauta nazo yi ba."
Mik'ewar da tayi tsaye tana ta kakkabar riga, hakan yasa ya tashi tsaye cikin had'e
rai yace "durk'usa" wani kallo ta mashi, hakan yasa ya d'auke ta da mari yana k'ara
maimaitawa "ki durk'usa nace" zubewa tayi tana kuka ci gaba yayi da fad'in "ki
saurare ni da kyau kiji, karki saké bari na dawo gidan nan ban samu abinci shirye
ba, sannan daga yanzu karki sake tashi tsaye in har ina zaune, ko ina zaune ke ma
kina zaune, dole ki girmama ni a matsayi na na mijin ki kuma wanda yake gaba da ke,
kina jina.?"

Cikin turo baki ta d'aga kai, zaune yayi yana kallonta yace "ki tabbata Kin kawo
min ordevre nan da minti talatin, idan kuma ba haka ba to rai zai b'ace," ganin
babu alamar wasa a al'amarin yasa ta tashi dan gabatar da abinda yace d'in, awa
d'aya ya d'auke ta kafin ta kammala ta kawo masa ta koma ta d'auko ruwa ta aje
masa, tana turo baki ta koma d'akin ta tana gunaguni.
Yana ida wa ya mik'e tsaye yana k'walla mata kira "ke! ke!! ke!! ko ba kiji ne.?"

Cikin gadara ta fito tayi tsaye tana kallon k'ofa, bugu ya kai mata a kai yana
fad'in "me na gaya maki yanzu?" kamar zata fashe haka tana ji tana gani ta durk'usa
gaban shi yana fad'in "saura ki kwanta bacci tsiya ki k'iyin abinda na saki,
wallahi da kinga k'ask'anci a gidan nan dan sai na k'arya ki" kallan shi tayi tace
"wai yaya Salman me kake nufi dani ne, wannan fa ba daidai kake yi ba, haka kawai
kayi ta wani samin doka kamar kai ka halicce ni ko kuma siyo ni kayi. ?"
Waige waige da ya shiga yi ne na neman abun bugu yasa ta arta a guje ta shige d'aki
ta Kulle tana fad'in "wallahi saidai ka kashe ni amma ba zanyi ba, haka kawai daga
zuwa na zaka wani ce wai abokanan ka zasu zo dan bak'ar jaraba."
Jin abinda take fad'a ya santa farin sani ba zata yi bâ, dan haka ya fita ana idar
da sallah la'asar ya dawo gidan ya sata aikin dole hannun shi rik'e da tsumagiya,
harta gama aikin tana kuka shiko ko a jikin shi tunda ta mashi abinda ya ke so
wannan ba matsalar shi ba ce ko kukan jini zata yi.
Tana idar da sallah isha'i tayi wanka ta shirya cikin riga da wando na bacci tunda
babu wani abun daya rage mata daya wuce ta kwanta tayi kuka bacci ya d'auke ta,
Salman ne ya k'wank'wasa k'ofar d'akin a hankali ta bud'e tana kallan shi tace" ya
dai Malam?" tun daga sama har k'asa ya kalleta kafin yace "ki fito ku gaisa, amma
ki sanyo hijjab." Wuce wa yayi ya barta ita ma ta koma ciki ta d'auko hijjab tasa
sannan ta fito.

Oummi ta d'auka wasu bak'i ne ashe ma su Khamis ne da sauran y'an uwan nasu, cikin
farin ciki suka gaisa Oummi ta zuba masu abinci ta aje a gaban kowan ne, Salman ta
zuba ma tana dariyar mugunta da gangan ta zuba masa abincin a jiki, da sauri ya
mik'e yana fad'in "ke! ke!! wai ke wacce irin sakarya ce baki gani ne?" juya baki
tayi ta wuce tana rera waka ta barshi nan, hakuri Khamis ya bashi suka ci gaba da
cin abinci suna hira cikin nishad'i.

_Yan Uwa ance tuna baya shine rok'o, amma ance waiwaye Adon tafiya_
27/02/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _


( _Gidan zaman lafiya da_ _amana_ insha Allah)_ 🤜🤛

*Page*

2⃣5⃣2⃣6⃣
2⃣5⃣-2⃣6⃣

*Alhaji Usman mai Dala* Tshoho mai ran k'arfe haka jikokin shi suke kiran shi wani
lokacin, ya nada mata hud'u, *_Hajia Salamatou_ _Hajia_ Zeinab* *Hajia Hawa'ou
Hajia* *Mariya* , ya nada yaya ashirin da takwas jikoki da dama, mutum ne mai
kakkausan ra'ayi mai tilasta iyalen shi akan duk wani abu da yake so koda basu san
shi, ya d'auki turbar had'a tsakanin yayan shi da yayan yan uwa aure dan k'arfafa
zumunci, duka yaran sa babu wanda ko wacce ta kawo zabinta duka *AUREN HA'DI* ya
masu.

Zaman da matan shi suke sai san barka zama ne da kowace take girmama abokiyar
zamanta, sabida tsari da tarbiyar gidan yasa kowane yaro bai san ainahin wacece ta
haife shi ba, kowa mama ce kuma kowace tana d'aukar d'an yar uwar ta amatsayin
d'anta, da haka ne Alhaji Hamidu ya saka ma yar shi sunan Zeinab duk da bâ ita ta
haife shi ba.
Ba iya nan abin ya tsaya ba har jikoki haka yake tsitar su da dai daya yana had'a
su aure, sannan auren kaka manu kamar auren zobe ne babu saki saidai ya yarda duk
wanda aka ma ba daidai ba ya kawo kara, amma ko yaji kayi to take za'a d'ora maka
kayan ka aka ka koma inda ka fito.

Sabida rik'o da addini yasa babu d'à ko jika da ya kai shekara goma sha takwas ba
tare da ya aura da shi ba, sai Oummi tayi wannan sa'ar sabida k'wak'walwa da Allah
ya mata harta sauke Alkur'ani ta nada shekara goma sha hud'u sannan ta samu( BEPC)
ta nada shekara goma sha shida, hakan yasa ya barta ta ci gaba da karatun Alkur'ani
harta samu harda lokacin ta nada shekara goma sha takwas, Oummi dai ba wata
kyakyawar yarinya bace face abu biyu da Allah ya bata, jar fata da manyan ido masu
kyan gani sai dinple wanda ko d'umi take yake k'ara mata Kyaou.

Salman shi ne na farko a duka iyalen da kaka manu ya fi so, dan haka yake daga
mashi k'afa harya haura shekarun da ya ke ma mazan aure, amma ba dan yana so ba,
dama yana cewa idan lokaci yayi zai bashi mamaki to gashi ya mashi aure babu shiri.

_Kwana hud'u kafin d'aurin_


_auren___ *Salman da Oummi*

~Ku ja muje👌~
27/02/2019 à 17:31 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

_Cette page ce pour toi mon macho *Meelat AHK,* tu auras la bénédiction da Dieu
insha, que Dieu te bénisse. Bizou_ 😘

```dedecated to```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜🤛

*Page*

2⃣7⃣2⃣8⃣
2⃣7⃣-2⃣8⃣

Kamar yanda ya zama al'adar gidan yake idan ya rage saura sati d'aya a d'aura aure
to amare su kan dawo da zama gidan Alhaji har a d'aura auren.

Ummi ma ta dawo tare da amaren dan bâ zata iya zama babu su ba sune k'awayenta ita
ce k'awarsu kuma yan uwan juna, yaou tunda safe suke takura Ummi akan taje ta
karb'o sauran dinkin su daya rage amma sabida san jiki irin nata taki tafiya har
saida marece yayi ta fara shirin tafiya amma kuma hajia Babba tace ba zata ba tunda
babu wanda zai kaita kuma Alhaji ya hana su shiga adaidaita dan haka ta zauna jiran
Allah ya kawo wanda zai kaita.

Zaune take tana jiran taga wanda zai shigo, kwatsam Khamis da Salman suka shigo
cikin farin ciki suna hira,saida suka gaishe da su hajia suka fito zasu tafi
hajia Babba tace" yaran albarka ina zaku haka?" Khamis ne yace" hajia yadai ko ba
kisan mu fita ne?" tsaki tayi tace" kai tafi can ina ruwana da ku dan kun fita,
wace uwar zaku bani idan kuna gidan ma, ina so inji inda zaku ne dan ku biyamin da
wannan yarinyar" to ina zataje ita?" wajen tailleur kin su karb'o sauran dinkin su"
to ai ba damuwa dama wajen aski zamuje yanzu, taso muje Ummi" Salman ne yace" kaga
karfa ka d'auko mana yarinyar nan kasan yanzu raina zai b'ace" kafad'ar shi ya dafa
yace" haba karka damu wannan fa k'anwarka ce" maida kallanshi yayi ga Ummi yace"
taso muje".

Haka suka d'auki hanya Khamis da Ummi nata hirar su, Salman kuma ko tanke bai kula
su ba har suka isa wajen, ta samu ana cikin dinke na k'arshe dan haka ta zauna ta
jira Khamis kuma yace Salman ya kaishi wajen askin saiya dawo ya d'auketa, haka
kuwa akayi ya dawo d'aukar Ummi amma na second d'aya bai jira ba haka ya fara zuk'a
mata oder dole ta fito a hargitse tana saka kayan a leda ta shiga mota suka wuce,
suna bisa hanya hadari ya taso aka fara iska gari yayi jawur harda baki ga k'ura da
k'yar kake ganin gaban ka.

Salman ne yayi tsaki yana fad'in" wannan jaraba har yaoushe da irinta, gashi kinja
min na rasa aski sabida bakin halinki kod'an saurayi ma ba kida shi wanda zai maki
anfani idan irin haka ta taso, murgud'a baki tayi tace" e d'in banada ai kai naga
kanada budurwar, kuma duk bakin halin mutum ai baya rasa massoyi saidai in hali
baizo d'aya ba" da k'arfi yasa hannu ya bige bakin Yayana fad'in" yimun shiru kona
taka ki yanzun nan marar kunyar banza" rufe baki tayi tace" wallahi saidai mu taka
juna, haka kawai zaka takuramin" cikin d'aga murya yace" ke ni kike fad'awa haka,
Allah saina sauke ki a nan naga abinda zai faru" cike da tsiwa Ummi tace" yo ka
sauke ni mana saime inada wanda zai maida ni idan ma ka sauke ni" OK haka kika ce,
to sauka ya fad'a lokacin da yayi parking kamar wasa ya sauke Ummi a nan ba tare da
wani tinani ba, ganin yanda gari yake yasa har saida tayi kuka sannan ta matse
kayanta ta d'auki hanya a k'afa.

Tafe take tana share hawaye tana tinanin abinda zata ma Salman idan taje gida, oder
taji Daga bayanta wata tsaleliyar mota ce ke biyar ta amma bata tsaya ba har saida
ya tare gabanta sannan ta tsaya, wani santalelen saurayi ne ya fito daga ciki yana
fad'in" haba hajia inata oder amma kinki tsayawa" hararanshi tayi tace" to lafiya?"
kinga yanzu dai ba wannan ba ki shigo dan Allah na rage maki hanya inba damuwa"
sabida bacin rai yasa tace" da damuwa malam, dan Allah ka wuce ka barni" zata wuce
taji anyi tsawa mai k'arfi alamar ana ruwa a wani wajen, abar da tafi tsoro kenan
dan haka ta bud'e motar da sauri ta shiga tana k'ilu k'ilu da ido, dariya yayi ya
shiga saida sukayi nisa yace" yan mata ni suna na JAMAL, ke kuma fa?" bata fad'a
mashi ba sai kwatancen gidan su ta mashi dan ya sauke ta.

Dak'yar ya samu ta bashi number wayarta, tana fitowa yayi dai-dai da kawowar Salman
dan haka tabi bayanshi dan ta sauke ruwan bala'i, Jamal kam bin bayanta yayi da
kallo yana lasar leb'e yace" ina san faran mace amma fa badan na aureta ba, kema
zan latsaki kad'an duk da naga akwai tsiwa da jan aji a tare da ita, amma ba komai
naga wanda suka ninka ta so dubu dan haka zan fara shawo kanta kafin nan sai in
abka mata" kara lashe leb'en yayi yaja motar ya wuce.

K'ofar gidan ta tsayar da shi tace" to dan ciki bakin nazo gida lafiya babu abinda
ya sameni sai ka mutu tsabar takaici" tana fad'i ta wuce gidan su Alhaji a tinanin
su kuma Salman ne ya dawo da ita, tana shiga su Khairat suka karb'i kayan suka fara
dubawa, ba bata lokaci saiko aka keto da ruwa mai k'arfin gaske.

_To bari muji wai wannan Yar tsama yaoushe ta fara tsakanin Ummi da Salman ne?🤔_
27/02/2019 à 17:32 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```Mommyn Khadija``` ( ma Belle)


```Mommyn Sultan```
```Mommyn Labyb``` (Mamien mu)
```My Heenat``` (Raheenat)
```Choukoura``` (Chouk Beby)
```Halima```
```Maman samha```
( *Cette page ce pour vous)*

~Luv u😘~

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da_ _amana insha Allah)🤜_ 🤛

*Page*

2⃣9⃣3⃣0⃣
2⃣9⃣-3⃣0⃣

__A fahimtar Salman shine k'arshen rainin da mace zata ma namiji to ta harareshi
ko tsaki had'e da murgud'a baki, dan ko a film yaga haka to ya tsani wannan matar
kenan dan ko miji da matar shine ta_ _ma shi haka to ta gama raina shi dan haka ya
tsani abin sosai._

__Tunda Ummi ta tashi tana k'arama ya zama in dai Salman zai mata magana to sai
tayi abinda ya tsana harta girma, bayan ta mallaki_ _hankalin kanta sai ta gane
Salman baya so ita kuma sai ya zama d'abi'arta hakan, duk lokacin da yake mata
fad'a ko ya dake ta akan ta raina shi sai Mahaifiyar shi tace, kawai dai dan ya
sama ransa ne shiyasa ko d'umi tayi sai yaga kamar tayi abinda baya so, Mahaifiyar
Ummi kuma tana cewa, da gangan ta keyi dan tasan baya so, to haka_ _dai ya zama
kowa da bayan wanda ya ke bi, kasancewar su mak'otan juna dan Ummi bata wanka ta
bushe sai a gidan wajen k'awarta Khairat, haka ma Salman ya fi wuni gidan akan
gidan su sabida k'annan Ummi da Mahaifiyar su yana jin dad'in zama da su._
_
_Rayuwar Iyalin tana da ban sha'awa dan Ummi da su Jawahir duk lokacin da babu
école ko makaranta to suka_ _zab'i gidan da zasu je su kwana biyu a can, haka zasu
dinga farin ciki suna d'aukar photunan junan su sabida_ _tarihi shiyasa suka shak'u
sosai ba su tab'a samun sab'ani ba._

_In dai Ummi zata ma Salman_ _abinda baya so to ya kan dage ya tumurmushe ta san
ransa kuma hakan ya samu asali ne sabida la mamma tace duk sanda ta mashi to ya
daketa har sai ranar da ta daina dan kanta, burin Iyayen nasu bai wuce suga an
had'a auren su ba to amma yaran ma sunki jituwa tsakanin su duk da dama ana had'a_
__auren ne ba sai wanda ka ke so ba ko ku ke fahimtar juna._
_
```Wannan kenan``` 👈

_
Washe gari amare suka shirya zuwa wajen kitso,Salman da Khamis ne su ka kai su a
mota ma saida aka samu matsala tsakanin Ummi da Salman sakamakon..., sorry dear
wayar ta gaji😞.
27/02/2019 à 17:33 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

*(Yan uwa ku gafarceni a bisa kuskuren da nayi wajen saka num page, kamata yayi
wannan ta zama 27-28)* 👏

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜🤛

*Page*

3⃣1⃣3⃣2⃣
3⃣1⃣-3⃣2⃣
Salman da Khamis ne a gaba, yayin da su Jawahir ke su biyar ke baya Ummi kuma tana
bisa k'afafun Jawahir a bayan kujerar da Salman ke tuk'i, saboda rububin da yayi
yawa da ramuka dake wurin yasa Salman shiga wani rame da baisan da shi ba hakan
yasa kowa saida ya girgiza Ummi da ke k'afafun Jawahir saida tayi kamar zata fad'i
da sauri ta rik'e kafad'un Salman duka biyun tare da fad'in" Inna Lillahi Wa'inna
Ilaihi Raju'un, malam kashe mu kake so kayi ne?"da k'arfi Salman ya fizge
hannayenshi yana fad'in" ke wannan wani irin abu ne? muguwa kawai" mugu dai, kaji
mutum kamar makaho da ba zaka kalli inda zaka saka mu ba" ke rufa min wannan banzan
bakin naki kinji ko" idan kuma naki fa saime ya faru?" sai kisha dan banzan duka
kuwa mahaukaciya kawai" turo baki tayi ta harare shi kallanta yayi ta madubi dan
haka ya zuro hannu ya mazge kanta, haka suka kai suna fad'a.

Amare kitso aka masu Ummi kuma kunshi, bayan sun koma gida duk da dare yayi amma la
mamma ta mata nata kitson kanana mai kyawun gaske irin na buzaye.

Yau ta kama ranar Juma'a washe gari kuma d'aurin aure, Ummi da amare ne zaune a
d'aki suna hira hajia Babba ta kira Ummi tana fitowa tace" d'oki abincin nan ki
kaima su Khamis a d'akin baki" Kallan hajiar tayi tace" su yaya Khamis kuma,miya
kawo su nan da har za suci abinci?" to ina ruwanki?kiyi abinda na saki kawai" gwalo
ta mata tace" naji tsohuwa mai ran k'arfe"duka ta kai mata bata sameta ba tace" ke
tafi can in banda shegantaka babu abinda kika aje" d'auka tayi ta wuce tana dariya.

Saida tayi sallama suka bata izinin shiga sannan ta shiga, tana ganin Salman ta
murtuke fuska irin babu wasa dinnan, gaishe da Khamis tayi ta duk'a ta aje ta tashi
zata tafi Khamis yace" k'anwata ina kika baro min amarya ta?" murmuchi tayi tace"
yaya Khamis ko dai zance kazo? in kira maka ita" dariya yayi yace" a'a rufan asiri
karki sa tsohon nan ya balbaleni da masifa" dariya tayi ta juya zata tafi idonta
suka sauka akan Salman dake kallan kumatunta, harga Allah suna birgeshi idan sunan
lotsawar nan amma ba yarinyar ba, kamar daga sama Ummi tace" malam lafiyar kallo
na?" cikin d'aure fuska yace" ke ni sa'anki ne? wallahi ki kiyaye ni" juyawa tayi
ta fita saida ta kai kofar d'akin tasa takalminta sannan tace" kana kallan mutum
kamar maye" da gudu ta ida fita shi kuma ya bita da kallo ya, girgiza kai yayi
yace" Allah ya shirya ki" Khamis ne yace" da wannan Addu'ar ka ke mata ma tun tini
da yanzu ta shiryu" tsaki yayi yace"wannan din?ai ka barta inda ka ganta kawai"
abincin suka ci bayan sun kammala suka fito Khamis ya shiga wajen su hajia, Salman
kuma ya nufi b'angaren Alhaji.

Bayan sun gaisa Alhaji yace" Salman kaga dai yanzu gobe za'a d'aura auren yan
uwanka, na so ace da kai a ciki amma Allah bai nufa ba, nayi nayi da kai ka fiddo
da mata a cikin yan uwa, amma kayi wasa da damar da na baka wacce ban taba bawa
kowa ita ba, amma ba komai akwai lokacin da zan baka mamaki" kanshi k'asa yace"
kayi hakuri Alhaji, insha Allah zan samo nima nan ba dadewa ba" kafadu Alhaji ya
daga yace" kai ka sani, ni nasan da ka duba da ka samu, tunda ga sunan birjik muna
da su iri iri, in kuma wannan ka kake so abokiyar fad'anka sai ka fad'a babu yar da
zaka nema ka rasa a cikin dangin nan" wani kallo Salman ya masa kafin yace" ba
komai Alhaji zan nemo, amma ba wannan ba" haka su kayi sallama Alhaji yana mamakin
irin wannan rashin jituwa.
27/02/2019 à 17:33 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_ 🤜🤛

*Page*

3⃣3⃣3⃣4⃣
3⃣3⃣-3⃣4⃣
Washe gari da safe, Ummi ce keta bilinbituwar neman chargeur ta saboda wayar ta ta
kusan d'aukewa, cikin masifa tace"Khairat ke wai ina kika d'ora min chargeur ta
ne?" Khairat da ke dunkule cikin hijabi tace" to ni ina zan sani tunda ban d'auka
ba" ke wallahi ba zan yarda ba, duk in da kuka kaita sai kun fiddo ta" Nadia ce ta
lek'o da kanta daga cikin hijabi tace" ke jiya fa yaya Mubarak ya aiko yaro aka
karb'ar masa shi ma wai bai ga ta shi ba" hararanta tayi tace" oho kenan ke kika
bada dan yana mijinki? kuma kina ji ina tambaya kika min shiru, ta tashi ki karb'o
min kaya ta" ido Nadiya ta fiddo tace" wacece zata karb'o makin?ina ga ko da ba
kiyi abinda za kiyi da ita ba, kafin wannan ranar ma aka hana mu zuwa b'angarensu
bare kuma yau" tsaki tayi tace" to kenan nice zan karb'o da kaina, wai ku dan kunga
zaku aure ne shiyasa kuka raina ni?" a'a su Ummi manya ba haka bane, kije dai da
Kanki zaifi" amma kinsan yanzu suna tare da wannan dan rainin hankalin,ba zan juri
kallon banza ba ma daga gare shi bare bak'ar magana" dariya sukayi dan sun san wa
take nufi, juyawa tayi ta fita Jawahir kuma cewa tayi" kai Allah yasa a had'a yaya
Salman da Ummi aure muga cakwakiya" Hafsat ce tace" ke ai ko in Ummi bata kashe shi
da bakin ciki ba, to shi ya kashe ta da duka, ai had'a su bana jin zai haifar da
d'a mai ido".

Sallama tayi suka amsa Mubarak ne ya bata izinin shiga, saida ta shiga tayi da na
sanin shiga saboda yawan su su da abokansu ne sunfi su goma sai shiri ake, Mubarak
kawai ta kalla tace" yaya Mubarak chargeur kina nazo karb'a" cikin sakin fuska
yace" OK na kine dama? bari in d'auko maki" tsaye tayi tana jira Khamis ne yace"
k'anwata gaskiya kinyi kyau sosai, ina ma hada ke zamu angwance, gashi sai k'yalli
kike kema kamar amarya" murmuchi tayi in da Salman ya bita da wani kallo dan yasan
dama saita murmusa shi kuma yana so yaga dinple kinta, wani daga cikin abokanne
yace" abokina da in dai baku mata miji ba to ni kam ina so" kai na rabaka, kai bâ
kasan auren dangin mu ba?" to miye a ciki in haka ne ai sai na komo cikin dangin
naku" dariya suka saka, Salman kam cewa yayi" lalle kam da kayi asara ka dawo
danginmu saboda wannan abar" kallon mamaki suka mashi d'aya yace" to saboda me,
wannan zuk'ek'iyar budurwar, ko ni in har za'a bani ita ai da gudu zan dawo"
hararanshi Salman yayi yace" ka koji haushi wallahi ba kayi zab'en k'warai ba"
Khamis ne yace" ku fa baku fahimce shi ba yana so ya nuna maku ita d'in matar da
zai aura ce, amma kunk'i ganewa" da dariya ya k'arashe maganar, Salman kam kamar ya
kai mashi duka, kafin yayi magana Ummi ta murgud'a baki tace" haba yaya Khamis
kamar dai maza sun k'are a garin da zan auri wannan halintar" wani bakin ciki ne ya
taso ma Salman da yaji an kwashe da dariya, kallanta yayi yace" ke bar nan wajen"
tana karb'ar chargeur kin ta wuce saida ta kai k'ofar d'aki ta juyo tace" to kama
bakin ni ka daina kallona" wannan maganar ba k'aramin b'ata masa ray tayi ba,( *to
fa shine yan uwa ku kaga Salman ya biyo ta a guje har kuma suka zama miji da
mata* ).

```CiGaban Labari```

Su Khamis na tafiya Salman ya shiga d'akin Ummi dan ya san da gangan ta zuba masa
abinci a jiki, tsaye ya same ta tana gyaran shinfid'a ko riga babu a jikinta sai
bras da ta kamata sosai abunka ga mai yar k'iba hakan yasa duk bayanta ya kakkarya
gata jawur sai shatin bulaliyar da ta sha sai dogon wando a jikinta shi ma bak'i
kamar bras kin, shiru yayi ya ma rasa abinda ya zo fad'a Ummi kam ba tayi wani
k'ok'arin rufe jikinta ba duk da ta ganshi.

Hannunta rik'e da pillow ta kalleshi tace" malam ya dai lafiya ka shigo min wannan
lokacin haka?" da sauri ya d'auke kanshi daga kallanta bai ce k'ala ba dan haka
tace" ka shigo d'aki babu sallama, ba tapé ba excuse kawai ka shigo, yanzu idan
nayi ihu nace za kamin fyade kana ganin zaka fita?" ci gaba tayi da abinda take,
ganin ba yada abin fad'a yasa ya juya ya fita, d'akinshi ya shiga ya kwanta saman
gado yana kallon sama a hankali yake rufe idonshi yana bud'ewa wani sabon abu yake
ji a tare da shi, surarta ce take dawo mashi a k'wak'walwar shi a haka bacci yayi
gaba da shi duk da yaso ya fita.
27/02/2019 à 17:34 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜🤛

*Page*

3⃣5⃣3⃣6⃣
3⃣5⃣-3⃣6⃣

Misalin 23:30 ya farka, wanka ya farayi ya fito ya kalli agogo tsaki yayi yana
fad'in" mi yarinyar nan take nufi da ni ne da har yanzu bata kawo min Tea na
ba?"wani tsakin ya k'ara saki ya fito ya nufo k'ofarta, zai bud'e wata zuciyar ta
gargad'eshi karya saké ganinta a yanda ya ganta d'azun, ya dan jima a tsaye kafin
ya zira kai cikin d'akin, ga dukkan alama tayi nisa a cikin baccin ta har yanzu
babu riga a jikinta tayi rub da ciki, sai lokacin ya kalli shatikan carbin da ke
bayanta duk ya farfashe, ga kananan kitsonta daya kwanta a bayanta kamar ya taba
wata zuciyar ta gargad'e shi, k'afarta ya kama ya fizgo a tsorace ta mik'e zaune
tana murza ido tare da kallonshi kafin tace" wai dan Allah miye haka, haka ake tada
mutum daga bacci kamar a gidan mahaukata, kai idan aka maka haka sa kaji dad'i?" ke
rufe min baki ina abinda na saki?" kallaonshi tayi ido bud'e tace" wane abu kuma?"
dan 'kuwa ya mata yace" ban sani ba, Tea k'in fa, ko ni kike so naje na dafa?" kau
da kai tayi tace" nifa ba zan'iya ba, ace Tea ba za'a shashi da safe ko da rana ba
sai dare yayi kuma sai na kai har cikin d'aki haba gaskiya da saké" ganin ya fara
waige waige yana neman abun bugu yasa ta tashi da gudu ta bar d'akin ta shiga
cuisine ta fara had'awa.

Tana kammalawa ta kawo mashi har d'akinshi, kallo d'aya ya mata yaga bacci pal a
idonta dan haka ya mata tsaki yace" ba kida aiki sai bacci kamar kasa" lumshe ido
tayi ta saké mik'ama mashi faranti tace" ni ka karb'a dan Allah in tafiya ta" wata
harara ya watsa mata yace" ki aza a kaina mana tunda ba babu wurin ajewa" gefen
gadon ta d'ora harta juya zata fita yace" waye zai zuba kenan?" dawowa tayi ta
zuba mashi kallonshi tayi cikin muryar bacci tace" sugar nawa zan saka a ciki?"
d'aya" ya bata amsa idonshi na kallon hannayenta da suka sha jan lalle da bak'i
abin sha'awa,tana gamawa ta mik'a mashi wani kallo ya mata yace" ki aje ko dole sai
na karb'a" ajewa tayi ta juya cikin magagin bacci ta fita, har saida ta bace ma
ganinshi sannan ya kalli faranti yanda ta k'awatashi ma kad'ai da abin birgewa ne
ga kamshin da ke tashi mai dad'i, d'auka yayi ya kurb'a har saida ya lumshe ido dan
Khairat bata taba dafa mashi mai dad'in wannan ba kuma gashi duk abinda ake sakawa
a waccen nan ma an saka "to miye banbanci?" ya tanbayi kanshi.

Yau ma da zazzab'i ta tashi tana yin sallah asuba ta nufi cuisine dan ta tuna
abinda ya fad'a mata akan girkin, gashi kuma ta d'ora mai wuya abincin da Abbanta
yafi sone ya karya dashi ta d'ora tuwon shinkafa da miyar agushi, duk da ta d'ora
da wuri saida tayi late akan lokacin da ya bata sakamakon zazzab'in daya addabeta
ga kuka da tasha abunta ta k'oshi.

Tana fitowa zata aje kwanukan ta ganshi zaune ya hakimce rai a b'ace saida ta gama
jera duka kayan ta zuba mashi zata wuce d'aki yace" zonan" dawowa tayi ta tsaya
sannan yace" k'arfe nawa yanzu?" da k'yar ta gane lokacin dan jiri kawai take gani,
a hankali tace" 08:22" bien" ya fad'a yana kallonta yace" nawa mu kayi da ke na
dinga samun abinci a nan" kamar za tayi kuka tace" dan Allah kayi hakuri banji
dad'i ne shiyasa, kuma kaga tuwo ne nayi" cikin tsawa yace" to sai me, ina ruwana
da abinda kika dafa, kina nufin haka zan dinga zaunawa jiranki kullum kenan?" dafe
kanta tayi saboda sarawar da yake mata gashi shi kanshi Salman k'in guda uku uku
take ganinshi dan haka tace" kayi hakuri dan Allah ka taimaka ka siyo min madara
wallahi mutuwa zanyi" wani kallo ya mata yana magana akan wani abu ita kuma tana
magana akan wani abu daban, kafin ya ankara ya jita a k'asa ta dad'i hannunta kam
har yanzu a kanta ya ke cikin bacin rai yace" ke dan Allah tashi miye haka kamar
wacce tasha k'waya" ya jima yana mata magana amma kamar bada ita yake ba, dan haka
ya ka mata ta mike tsaye ya zaunar da ita akan kujera, da k'yar take bud'a baki
tana fad'in" madara yaya Salman dan Allah ka Siyo min in sha" hararanta yayi yace"
ke tafi can sai naci na k'oshi in yaso na siyo maki jarababba kawai kin d'ora ma
kanki shan madara kamar wacce saniya ta haifa" kanta a duk'e tace" kaima miyasa ba
zaka siyo min ba in yaso sai kaci tuwon, kenan duk jarabar gare mu, kuma wallahi
saina fad'ama la mamma nace ka ce mata saniya tunda ai kasan ita ta haifeni in ba
kana san cin zarafinta ba miye na had'a yar da ta haifa da saniya" maida
hankalinshi yayi ga cin abincin shi har saida ya koshi sannan ya fita ya barta a
wannan halin.

Tunda ya fita bai saké tuna wata Ummi ba harkokin gabanshi kawai yake hankali
kwance har saida lokacin dawowar shi yayi da rana, kai tsaye yazo gidan yana
shigowa baiga alamun girki ba dan haka ya d'auko belt a d'akinshi ya nufi d'akin
Ummi da ke kwance tun safe ga ciwon kai ga zazzab'i ga amai da take na duk wani
abinda ta ci.

Yanda ya ganta cikin bargo ya k'ara k'ona mashi rai matuk'a, bai ko tsaya Haye
bargon ba ya fara tsuga mata belt kin nan, ba tayi wata Kara ba sai kuka daya saké
kubce mata mai tsanani yana cikin dukanta amai ya taho mata haka ta fara kelayashi
dole ya tsaya yana kallon ikon Allah, duk ta b'ata gadon dan haka ta rairafa ta
dawo k'asa ta rakub'e tana kuka, tsaki ya mata ya fita daga d'akin dole ya fita
nemo madara da magani da abinda zai ci.
27/02/2019 à 17:34 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```dedecated```

```To```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da_ _amana insha Allah)🤜_ 🤛

*Page*

3⃣7⃣3⃣8⃣
3⃣7⃣-3⃣8⃣

Yana dawo ya sameta in da ya barta, da kanshi ya zubo mata madara a cup da abincin
ya kawo mata mik'a mata yayi kawai sai tak'i amsar ta cup d'in sai ta cikin gorar,
tana karb'a ta kafa kai saida ta sha fiye da rabi sannan ta aje tana maida nunfashi
a hankali, Salman zaune yayi yana kallonta baki bud'e ganin zata kwanta yace" ke
tashi dan Allah kici abinci" da k'yar ta koma ta zauna ta d'auki abinci saidai ba
taci sosai ba ta aje ya bata magani nan fa aka sha fama, yana mik'a mata ta ya
tsina fuska tace" a'a ban sha" kwance tayi ya fizgota yana fad'in" tashi Dallah
malama, wato magani ne ba zaki sha ba, amma abun dad'i kinci kinsha ko maza karb'i
kisha nan" ganin ba zata sha ba yasa ya d'auki cokalin da taci abinci da shi ya
k'wandara mata akai dole ta karb'a tasha tana kunkuni.

Baifi minti biyar ba bacci ya d'auketa, kujerar da ke fuskantar ta ya zauna ya fara


cin abinci yana tunani iri iri, inda wata zuciyar ke saka mashi ya horata ta hanyar
yi mata wasa da madara, wata zuciyar kuma na fada mashi kar yayi hakan tunda tana
shiga matsala in bata sha ba.

Ana sallah la'asar ta farka, wanka tayi sannan tayi alwala tayi sallah ta shiga
cuisine dan gabatar da abincin dare, tana d'orawa ta shiga d'akin shi ta fara gyara
masa duk da bâ wani datti yayi ba haka ta gyara shi tayi turare sannan ta rufe
d'akin taci gaba da sauran ayyukanta, sai bayan Magriba ta kammala komai tana shiga
d'akinta wanka tayi ta saka riga da wando na bacci ana kiran sallah isha'i ta saka
doguwar riga tayi sallah sannan ta kwanta saboda gajiyar da tayi, dan tunda take
bata taba aiki mai yawa kamar na yau ba.

Bacci mai dad'i ya d'auketa, amma shigowar Salman ya mata wani hargitsantsan tadi
da ruwan sanhi saboda ta fito ta zuba masa abinci, haka ta fito tana kuka tana zuba
abinci, tana idawa ta ajiye masa ta koma d'aki ta kwanta ta dinga shek'a kuka tana
fad'in" shikenan haka rayuwata zata k'are, an rabani da iyayena da yan uwana da
kowa nawa ba'a barni nayi ban kwana da su ba, gashi wannan mugun yana neman kashe
ni, wallahi ba zan zauna gidan nan ba dole na barshi in ba haka ba to zai kashe ni
ko ni na kashe shi" tunda ta fara kukan Salman ya tsaya k'ofar d'akin yana
sauraranta yana jin tace ko ta kashe shi ya bud'o k'ofar da k'arfi ya shigo dab da
ita ya tsaya ya kama kunnanta yace
"Wallahi karki bari zuciyar ki ta fara raya maki ki kashe ni, dan kafin ki kashe ni
ni zan kashe ki, kuma zama daram a gidan nan babu inda zaki je kuma dolenki kiyi
abinda na saki in kuma ba haka ba" k'wafa yayi alamar tasan mi zai biyo baya.

Iya k'arfinta ta sa ta tureshi da sauri ta mik'e daga kan gadon tana k'ok'arin
guduwa, yaji zafin turar data masa dan haka yayi saurin rik'ota duk da yayi nasarar
rik'o k'ugunta a tare suka fad'a saman gadon inda Salman ya fad'a samanta da gaba
d'aya nauyinshi, k'ara ta saki lokaci guda kuma ta soma kici kicin k'waceya,
d'agata yayi yana kallonta kafin ya juya ya fita daga d'akin.

Haka ta takure taci gaba da kukanta tsawon lokaci, duk da bata manta da Tea d'in
shi ba amma tayi niyar ba zata kai bâ saidai ya kasheta.

Tunda yaga 00:30 tayi ya tabbatar ba zata zo ba shi kuma yana so ya canzata dan
haka ya shigo d'akin hannunshi rik'e da belt, yana ganinta kwance duk da baccin bai
jima da d'aukarta ba haka ya ware iya k'arfinshi ya zabga mata belt d'in nan, a
gigice ta mike zaune tana dube dube tana ganinshi ta fashe da kuka lokaci guda kuma
ya soma tsula mata belt d'in, duk in da ta nufi saiya tarota ta shige cikin bargo
ya yaye shi da k'yar ta samu ta rik'e belt d'in tana fad'in" dan Allah kayi hakuri,
kayi hakuri wallahi ba zan saké ba na daina daga yau, zanyi duk abinda kace wallahi
ko, dan Allah kayi hakuri."

Wata harara ya wurga mata yace" nan da minti goma ki kawo min Tea d'akina" yana
fad'a ya wuce d'akinshi ya barta nan, ita ma tashi tayi jiki na rawa ta shiga
cuisine dan had'a mashi, hak'ik'a yau ta matuk'ar tsorata da al'amarin Salman, yana
dukanta ko a gida amma bai taba mata irin dukan daya mata yau ba, dan-danan ta gama
ta kai mashi d'aki, harta juyo zata fito yace" ke saurara kiji" cak ta tsaya tare
da juyawa tana kallonshi" daga gobe k'arfe 23:00 zaki dinga kawo min Tea, idan kika
wuce lokacin dana baki to jikinki zai fad'a maki" saida ta murgud'a baki sannan ta
juya da sauri yace" ke wa kike juyama baki?zo nan" tana zuwa yace" gwiwanki k'asa"
ba gardama tayi abinda yasata, ta d'auka zai fad'a mata wata magana ne amma wasa
wasa sai ga Ummi durkushe sama da awa d'aya, da tayi yin k'urin tashi zai dalla
mata harara dole ta koma, shi kuma yana ta latse latse a wayar shi yana dariya, shi
kam bai san Ummi raguwa bace daga nan ta d'ora kanta saman gadon sai bacci.

Tunda Salman yaga haka ya gyara kwanciyar shi yana fad'in" saidai ki kwana a haka
mahaukaciya kawai" Allah sarki kamar na daddab'ata ta tashi.

02:40 Ummi ta farka ta kalleshi tayi tsaki tace" mugu azzalumi wallahi kai ma sai
kaji abinda naji" cup d'in da yasha Tea ta d'auka ta zuba Tea d'in a ciki ta d'ora
saman gadon ta ja k'afafunta da sukayi nauyi ga ciwo ta fita ta bar d'akin.

Bata koma bacci ba har akayi sallah, tana idar da sallah ta fito ta shiga d'akin
Salman dan ta gaishe shi kamar yanda yace, tana shiga ta same shi akan sallaya kau
da kanta tayi daga tsaye tace" ina kwana" kallon banza ya bita da shi yace" bari na
tashi sai mu gwada tsawon" ta gane mi yake nufi dan haka ta durkusa ta saké fad'in"
ina kwana" a wahalce ya amsa mata da" lafiya" tashi tayi dan ta shiga cuisine yace"
zauna" zaunawa tayi yayin da ya mik'o mata Al-Qur'ani yace" fara daga Hizib biyar
har zuwa Al-Nass" karb'a tayi ta fara rera 'kira'a, masha Allah kamar ruwan sama ga
tattausan murya Salman sai yaji kamar ya samu kullum ta dinga karanta masa,
musamman Suratul Munafiqun kai kace gabanta akayi wahayinta ko wace kalma ko wane
harafi yana fita daki daki, tana karantawa yana jin tsantsar abinda surar take
magana akai, bai san lokacin da hawaye suka fara zubo masa ba har saida ta kai
Suratul K'alam ya d'aga mata hannu yana share hawaye tana d'ago ido su ka sarke
dana juna, ashe ita ma kuka ne take haka suka share hawayensu ta tashi ta fara
aikin gabanta.
27/02/2019 à 21:27 - Vous avez ajouté My Meelat
28/02/2019 à 17:02 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```dedecated to```

```Fans```

( __Luv you my mom tu est très chers pour moi, ce toi qui m'adonner une bonne
éducation pour devenir comme ca, je te remercie beaucoup bizou😘)_

*RABBIR HAM HUMA KAMA RABBAYANI SAGIRAN.*👏👏👏

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_ 🤜🤛

*Page*

3⃣9⃣4⃣0⃣
3⃣9⃣-4⃣0⃣

Tana cikin aiki taji yana k'walla mata kira, da k'asaita ta shigo d'akin tayi tsaye
tana kallonshi, dama ranshi a matuk'ar b'ace yake dan haka ya falleta da mari yace"
wani rainin wayo ne wannan? ina tsaye kina tsaye kina kallona da idon kinnan kamar
na aljanu" k'wallan da suka cika idonta ne ta matso su hannunta a kumatunta a
hankali ta zube k'asa, shi kuma ya d'ora da tambayar ta" ya akayi wannan Tea d'in
ya zuba akan gadon nan? dan ni dai nasan ban aje ba." kallon gadon tayi ta kalleshi
tace" ni kuma ta yaya zan san lokacin da kayi fitsarin kwancen ka" tana rufe baki
ya sake d'auketa da wani wawan marin da yafi na d'azu, zafi daya kai mata kawai sai
ta mik'e tsaye cikin zafin rai ta d'auki cup d'in da ta zuba Tea d'in ta jefa masa
a k'irji tana fad'in" karka saké dukana mugu kawai azzalumi macuci" dafe k'irji
yayi yace" Ummi ni kika jefa?lallai wuyanki yayi kauri, kuma idan banyi da gaske ba
to wata rana dukana za kiyi kema, amma bari yanzu nayi maganin wannan tantirancin
naki" wayar chargeur d'inshi ya d'auka a gefen gado sai ko ya fara zabga ma Ummi ba
'kakk'autawa, haka Ummi ta dinga ihu tana neman taimako da agaji, amma ina babu
haka Salman ya daketa san ranshi ya gaji ya bari, jefar da chargeur yayi ya shiga
douche ya barta nan rakub'e da gado tana ruzgar kuka jikinta sai rad'ad'i yake mata
kamar zai cire duk jikinta ya farfashe.

Haka ya fito ya shirya saida ya harareta ya nuna ta da yatsa yace" wallahi idan har
kika ce ba za ki girmani ba, to wallahi ranki idan yayi dubu zai dinga b'aci, ya
zama dole kisan abinda zai dinga fita daga bakin ki sakarya kawai" ficewa yayi ya
barta nan tana kuka.
Awa biyu ta d'auka kafin ta tashi ta fito daga d'akin, cuisine ta nufa dan tunawa
da tayi tana cikin d'ori ne ya kirata, tayi mamakin ganin gas a kashe tasan shi ya
kashe dan haka ta koma d'akinta ba tare da ta bud'a tukunyar taga abinda ke ciki
ba, ko wanka ba tayi ba ta kwanta saman gado taci gaba da kuka da k'unar zuci.

12:20 taga zaman ba zai gyarata ba ta fito ta shiga cuisine ta fara girkin rana,
tsananin yunwa da zafin jiki ga ciwon kai duk ya taru ya mata yawa, haka ta kammala
girkin da k'yar kamar zata mutu.

Tana idawa ta koma d'aki tayi sallah ko wanka ba tayi ba saboda raunikan dake
jikinta, tana kwance Salman ya shigo d'akin yace" wa kika aje da zai zuba maki
abincin" fita yayi bai jira amsarta ba tashi tayi tabi bayanshi, tsaf ta zuba masa
shinkafa da miyar kayan cikin ragon da tayi, bud'a ciki yayi ya ci abincin sosai,
yana kammalawa yayi wanka ya fita bâ tare da ya bi ta kan Ummi ba.

Abun ya k'ara tsananta ma Ummi kamar za tayi hauka ta keji, ga zafin ciwo da
rad'ad'i ga ciwon kai saboda kukan da take sha ga bakin ciki da kad'aici, tuna
dukan da Salman ya mata yasa ta shiga cuisine dan sarrafa abincin dare, macaronie
da miyar naman rago ta dafa d'an kad'an wanda zai ishe su.

Da k'yar ta watsa ruwa dan ciwon da ke jikinta ba zai bari ta cud'a ba, d'aure take
da towel tana ta kai da kawowa saboda wani sabon rad'ad'i da take ji, mai ta shafa
tasa turare gajeran wando tasa iya cinyoyinta sai bras da ta saka wanda taji kamar
ma karta saka, maganin da Salman ya siyo mata tasha sannan ta kwanta ba jimawa
bacci ya d'auketa.

Kusan awa biyu kenan da Salman ya shigo gidan amma babu ko motsin Ummi, abinci
kawai ya ke so yaci amma ya k'i zubawa yana jiran Ummi, a hankali ya bud'a k'ofar
d'akinta ya shigo, k'ura mata ido yayi yana k'are mata kallo tas, duk da shatin
bulalar da ya gani ya fito sosai a jikinta duk jini ya kwanta ga manyan birridda
duk a bayanta ya kwanta, tausayinta ya ji ya kama shi sai yaji baiji dad'i ba
lokaci d'aya kuma ya ji wani abu yana tsargar masa tun daga kwanyar kanshi har
babban dan yatsan k'afarshi, yana jin abun yana k'ara girmama yana fizgar shi
kamar zai aikata wani abu yasa ya daddab'a k'afarta, a hankali ta juyo da kanta
sannan ta tashi zaune tana murza fuskarta cikin tattausan murya yace,

"Wa kika aje da zai zuba min abincin?ko ni kike so in zuba da kaina?juyawa yayi har
ya kai k'ofar d'akin ya tsaya ya juyo yana kallanta, ganin bata taso ba yasa yace"
wai ba kiji ne ina maki magana?" a hankali tace" ina zuwa riga zan saka" kenan sai
na zaune ina jiranki harki gama, kinsan awata nawa a gidan nan ina jiranki,ko so
kike yinwa ta kashe ni?" yin k'urawa tayi ta tashi ta nufi drower, tsawa ya mata da
k'arfi" ke wai ba da ke nake ba da za kice sai kin gama abinda kike, ko wata tsiya
ce a jikin naki da zan kalla?dallah wuce mu tafi" ya mata alama da hannu wucewa
tayi sub'ur sub'ur k'ugunta na kad'awa harda kakkaryawa bayanta keyi, kamar
baturiya haka ta dinga kai da kawowa tana zuba masa, duk da hankalin sa na a waya
amma saida zuciyar shi ta fizgi idonshi izuwa shagalta da kallonta musamman ma
kunkuminta da k'irjinta sun matuk'ar tafiya da shi, tana zuba mashi ta kama hanya
zata koma d'aki ji yayi zata rage masa jin dad'i dan haka yace" zo ki zauna nan"
cikin shagwab'a ta kalleshi tace" yaya Salman kayi hak'uri na sako riga" zo nan
nace" dole ta zo taja kujera nesa da shi ta zauna tana ta b'oye k'irjinta, shiru
babu mai magana hakan yasa Ummi ta d'auki robar madara akan dinning ta fara sha
cikin d'ari d'ari, ana cikin haka hadari ya taso iska aka fara da k'arfi, Ummi duk
ta k'agu ta tashi Salman ko ko a jikinshi abincin shi yake ci hankali kwance, wutar
da aka d'auke tare da sako ruwa mai k'arfi yasa Ummi matso da kujerarta kusan
Salman, tunda ya lura a tsorace take kawai sai ya k'i kunna hasken wayar shi,
tsawar da akayi irin mai sa hanjin mutum kad'awa yasa Ummi mak'alewa a jikin Salman
ta lakayo da hannunta ta wuyanshi rik'e da robarta a hunnu tana fad'in" yaya
Salman tsoro nake ji, dan Allah muje d'aki" bai tankata ba saidai duk tasa jikinsa
yayi sanyi saboda yanda k'irjinsu ke had'e.
Ba tada niyar sakinshi dan haka ya kama hannunta ya kaita d'akinta, amma ina tace
ai ba zata zauna ita kad'ai ba, harya aje mata wayar shi kuma yaga shi ma baya gani
dan haka ya zauna gefen gadonta yana satar kallonta har bacci ya d'auketa,
lullub'eta yayi da zanin rufa yana kallonta yana girgiza kai fitowa yayi ya koma
d'akinshi yana fad'in" jaraba bacci da madara a hannu, kamar wata yar shekara biyu
a duniya, ai ko mai shan nono ba za tayi wannan jaraba ba."tsaki yayi ya kwanta
kafin bacci shima ya d'auke shi.
28/02/2019 à 17:02 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah_ )🤜🤛

*Page*

4⃣1⃣4⃣2⃣
4⃣1⃣-4⃣2⃣

Ummi tayi nisa a cikin baccin taji ana tsawa, zunbur ta tashi zaune tare da rik'e
robar madarar da tasha bacci ya d'auketa daga nan, ganin babu wuta a d'akin sai
duhu yasa ta fara k'ara tana fad'in" yaya Salman, dan Allah ka zo, wallahi tsoro
nake ji, dan Allah kayi hak'uri ka zo, Inna Lillahi Wa'inna Ilaihi Raju'un shikenan
mutuwa zanyi" shiru tayi dan tasan ba zai zo taimaka mata ba zanin rufa taja ta
k'ank'ame a ciki tana rawar jiki.

Cike da k'asaita ya shigo d'akin da wayar shi a hannunshi, gefen gado ya ajeta ya
zauna ya mik'e k'afafunshi saman gadon ya jingina bayanshi tare da rumgume
hannayenshi a k'irjinshi sannan ya kalleta yace" haka ya maki?nasan za kice tsoro
kike ji ba zaki iya bacci ke kad'ai bâ ana ruwa, to gani sai ki kwanta yanzu." ya
k'arashe maganar da hararenta turo baki tayi a hankali ta sulale ta kwanta tare da
gyara rufarta dan-danan bacci ya sake gaba da ita.

Makara yayi wajen tashi ko da Salman ya farka gari har yayi haske sai lokacin yaga
yanda ya kwana daga zaune, juyawa yayi ya kalli Ummi sai yaga ba tanan mamaki yayi
ta tashi amma ni ta k'yaleni, tashi yayi ya nufi d'akinshi ya nata matsar wuya
saboda ciwon da yaji yana yi masa, sallah yayi ya sako kayan sport ya fito dan ya
yaje bayan gidan a wani hankad'ed'en d'aki in da yasa aka gyara shi ya zuba kayan
motsa jiki, Ummi ya gani tana Aje kwanuka a dinning ba tare da ya tsaya ba yace" ki
biyo ni da jus mai sanyi" jiki na rawa Ummi ta bud'a fridge ta d'auko dan yanzu kam
harga Allah tsoron Salman ya kamata, saida ta kai farfajiyar gidan saboda sanyin da
taji na ruwan da aka sha jiya ta tuna doguwar riga ce a jikinta wacce ta d'ora a
kayan da ta kwana da su, juyawa tayi da nufi ta d'auko hijab Salman ya juyo yace"
zaki wuce ko sai rai ya b'ace" wucewa tayi da saurinta harya bud'a d'akin suka
shiga, kallo Ummi take sosai yanda aka k'awata wajen mik'a mashi jus d'in tayi dan
ta koma in da ta fito, hararan daya mata yasa ta sunkuya ta aje ta tashi zata fita
yace" zo nan, kinga waccen k'arfen shi nake so ki d'auko min" kallan k'arfen tayi
taga ko zai kasheta ba zata iya d'aukarshi ba,dan haka ta juya ta kalleshi tace"
yaya Salman ba zan iya d'aukar shi ba wallahi" wata kyakyawar waya ya d'auka yana
shirin zuk'a mata ta nufi wajen k'arfen a guje ta fara 'ko'karin d'aga shi, ganin
ta kasa yace ta d'auko na kusa da shi shima bata d'auko ba saida kanshi yazo ya
d'auka ya fara d'agawa k'wanji na fitowa da jijiyoyi haka ta saki baki tana
kallonshi, yana gamawa ya d'auki ball ya fito tsakar gidan ya fara bugawa, haka
kawai Ummi taji tana san ta yita kallonshi yanda yake ball d'in da kuzari da salo,
Salman na ganin ta saki baki ya jefo mata ball d'in da nufin koda ta sameta ta
sameta a in da bâ za taji ciwo ba, sai ko a fuskar Ummi ji kake Timm ball ta mare
ta, duk'ewa tayi tare da rufe fuskarta, jin ba tayi k'ara ba yasa Salman tunanin ba
taji zafi ba, d'aukar ball d'in yayi ya ci gaba da bugawa saida yaga Ummi ta jima
bata d'ago ba ya zo kusa da ita, sunkuyawa yayi ya d'ago da kanta take gabanshi
yayi wata mummunar fad'uwa saboda ganin idonta na dama ya kumbura ga jini ya
kwanta abin tausayi" oh mon Dieu, pardon Ummi kinji bansan haka zata faru ba dan
Allah kiyi ha'kuri" hawayenta ta goge ta mike tsaye tace" ba komai akwai Allah"
wucewa tayi d'akinta nan ta fara sabon kuka kamar da bakin k'warya.

Jikinshi ne duk yayi sanyi da yaji tace akwai Allah, Allah kuma ba azzalumin
bayinsa ba ne dole zai mata sakayya, aje ball d'in yayi ya koma ciki saida yayi
wanka ya shirya cikin k'ananan kaya wanda suka karb'e shi matuk'a sun masa kyau ga
k'amshin turarenshi mai sanyaya zuciya, haka ya shigo d'akin Ummi ya sameta tana ta
kuka a tsakiyar gado, sai ya ji baiji dad'in hakan ba tausayi ta bashi sosai
( k'aro na farko kenan a rayuwar Salman da ya ji tausayin Ummi har cikin zuciyar
shi) zaune yayi cikin muryar rarrashi yace" Ummi dan Allah kiyi ha'kuri ki
yafemin, wallahi banyi nufin ta sameki ba" d'ago da fuskar tayi yanzu kam gaba
d'aya fuskar ta d'an kumbura ido sun ida yin ja saboda kuka, kau da kanshi yayi kai
lokaci d'aya kuma ya kalleta yace" kin yafemin Ummi?" bata tanka saba haka yaci
gaba da rarrashinta har saida yace" dan Allah Ummi ki yafemin, wallahi ba zan iya
kwana dà alhakinki a kaina ba Ummi kin had'ani da Allah kinsan kuma dole zai maki
sakayya, kiwa Allah ki yafemin kinji, in kuma ba zaki iya ba to ki fad'i abinda
kike so nayi sannan ki yafemin?" sai lokacin kad'ai tayi magana tace

"In dai kana so na yafemaka to saidai in ka yarda zaka mayar da ni gidan mu"
kallonta yayi yace" kema kinsan hakan ba zai yiwuba, idan na kaiki gida ko da da
wuni d'aya ne to nima zan shiga cikin bak'in jadawalin Alhaji, ni kuma yanzu ban
shirya rabuwa da kowa nawa ba." kuka ta k'ara fashewa da shi tana fad'in" wallahi
ni sai na tafi gidan mu ba zan iya zama da kai a gidan nan ba ka kashe ni, ka duba
kaga yanda na koma kamar wata jaka kun same ni sai duka kuke, ta yaya zan iya zama
da Kai a gidan nan ni dama ba kyau ba jar fatar ce kawai gashi kuma yanzu kun mayar
da fatar ta koma kala biyu ja da bak'i, dan mugunta kuma yanzu fuskar tawa kake
hari ka nakasata" mik'ewa yayi yace" kiyi ha'kuri idan za kiyi, idan kuma ba zaki
yafe ba to ruwanki ne kuma." fita yayi ya zuba abinci yaci ya fita ya bar gidan.

Ganin fuskar tayi sauki yasa tayi girkin rana, bayan ya dawo yaga babu kumburi sai
dai har yanzu akwai ja a idon, dan haka yayi tunanin siyo mata magani idan ya fita,
abinci yaci yayi wanka zai fita Ummi tayi saurin tare gabanshi ta durkusa tace"
dan Allah yaya Salman ka taimaka min ka bani waya ta ina so in kira la mamma da
Abba" cikin dakewa yace" ki fidda rai da wannan wayar, dan bâ zan baki ba ki dinga
taramin maza cikin gida ba" kallonshi tayi tace" Salman me kake nufi?zargi na
kake?" kunnanta ya kama ya murd'e har saida ta saki k'ara yace" kar na saké jin
bakinki ya kira sunana daga yau, ko dai kice yallab'ai ko kuma ranka shi d'ad'e"
sabo yasa Ummi murgud'a baki tace" to sannu, kaji mun mutum wai ranka shi d'ad'e
kamar wani sarki" kwaf ya buge bakinta yace" to naji bakinki ya kira ni da sunana
kiga yanda zanyi da ke a gidan nan" wucewa yayi ya barta nan.

Da wuri Salman ya shigo saboda hadarin da ya taso, Saïda yayi wanka ya fito ya
zauna Ummi ta zuba mashi abinci, cewa yayi ta zauna tare suka ci abinci sannan ya
bata magani saïda yayi kamar ya bibbigeta sannan tasha.

23:59 Ummi ta kawo ma Salman Tea, ya ji dad'in ganin tsoronshi a idonta sannan tayi
abinda ya sata, tana zuba mashi ta zauna k'asa ta jingina da gado, kallonta yayi
yace" miye haka kuma?" kamar za tayi kuka tace" dan Allah kayi hak'uri karka
koreni, wallahi tsoro nake ji a can, amma idan aka d'auke ruwa zan koma" Tea d'in
shi yaci gaba da sha ya shareta har bacci ya d'auketa.

Bugun da taji a k'afa yasa ta bud'a ido tana kallon Salman da yasa jallabiya da
sallaya a hannunshi yana 'ko'karin shinfid'awa, tashi tayi ta koma d'akinta duk
jikinta ciwo saboda ta kwana daga zaune, sallah tayi tana idawa ta shigo d'akinshi
da sallama, durk'usawa tayi ta gaishe shi ya amsa yau ma kamar jiya Al-Qur'ani ya
bata ta d'ora a inda ta tsaya, ta jima sannan ya karb'a ta tashi ta nufi cuisine a
kasalance dan aikin ya fara gundurarta tunda ko a gida bata makamancin aikin da ta
keyi anan ko kad'an sai hutu.

Da k'yar ta samu ta had'a frite da omelette da Tea da yar matsakaiciyar sauce d'in
albasa da petit poids ta aje mashi, wanka ta shiga ta shirya cikin doguwar riga ta
atamfa mai da turare kawai ta shafa ta fito falo ta zauna.

Tana ganin ya fito ta tashi cikin ladabi ta sunkuya tace" ina kwana" sama da k'asa
ya kalleta ganin fuskarta tayi sauki yasa ya wuce bâ tare da ya amsa, bin
bayanshi tayi da harara, ganin ya nufi hanyar fita tace" yaya Salman abin karyawar
fa?" juyowa yayi ya kalleta yace" kin manta ko wace rana ce yau? ni ba kamar ki
bane mai bawa ciki wahala" shiru ta dan yi ta tuna yau alhamis yana azumi, amma
kuma ba taga yayi sahur ba, mik'ewa tayi ta tari gabanshi ta tsaya tace" yaya
Salman, dan Allah" katseta yayi da fad'in" me na fad'a maki jiya akan kiran
sunana?" rufe baki tayi sannan tace" kayi ha'kuri, dama ina so ne ka kiramin la
mamma ina so nayi magana da ita" mtssss, dogon tsaki yayi ya zauna saman kujera ya
fiddo waya, dad'i ne ya kama Ummi dan tasan zai kira mata mahaifiyarta ne.

Mik'a mata wayar yayi ta d'ora a kunne, tana jin an d'auka ta mik'e dan ta bar
wajen da hannu ya mata alama da ta koma ta zauna, jiki a sanyaye ta zauna tana
fad'in" wa'alaiki salam, la mamma ni ce, ina kwana" a dak'ile la mamma ta amsa da"
lafiya lau" cikin farin ciki Ummi tace" la mamma ina Abba da su Islam duk Suna
lafiya?" lafiya lau suke" jikin Ummi ne ya danyi sanhi jin amsar da Mahaifiyarta
take bata hakan yasa tace" la mamma ko dai fushi kike da ni?dan Allah kuyi ha'kuri
wallahi la mamma ba nida laifi, kawai Alhaji yayi kuskuren fahimta ne amma ban
aikata komai ba" hawaye ne suka fara biyo fuskarta Salman ko sai wani b'ata rai
yake yana hararanta, la mamma ce tace" kinga ni yanzu banda lokacin wannan maganar,
koma miye ai aikin gama ya riga da ya gama tunda kin ja mamu fad'a, ta kai har
gaisuwar mu yanzu Alhaji baya amsawa ni da Mahaifinki, kuma kinga ke ma kinci riba
tunda yanzu haka ya kafa ma kowa doka akan kar wanda ya kuskura yaje gidanki ko da
cikin yara ne, kuma ke ma yace kar mijinki ya yarda ya kawoki cikin iyalenshi dan
baya buk'atar ki yanzu." tana gama fad'a ta kashe wayar saboda kukan daya taho
mata, tana kashe wayar Ummi ta fashe da kuka kamar ranta zai fita, Salman karb'ar
wayar shi yayi ya fice ya bar mata gidan shi kam ko a jikinshi.

Haka ta wuni jiki babu k'wari ko girki bata yi ba tunda Salman ba zai dawo ba, haka
yamma tayi ta fara shirya mashi abin bud'a baki ba tare da ita taci komai ba, ta
kammala da wuri yana zuwa ta shirya komai haka ta kula da duk wani abunda zai ci
har ya fita bayan sallah isha'i sannan tayi wanka ta zauna tsakiyar gado ta nata
runguzar kuka kamar yarinya saboda takaicin abinda ya isheta.
28/02/2019 à 17:02 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```Luv you my fans```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


( _Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_ 🤜 🤛

*Page*

4⃣3⃣4⃣4⃣
4⃣3⃣-4⃣4⃣
Ko da ya shigo d'aki ya sameta tana ta faman kuka saï sharbar majina take alama
taci kukan ta koshi, zaune yayi yana fuskantar ta yace" wai har yanzu kuka kike? to
miye la mamma ta fad'a maki ne haka?" dama tana neman wanda zata fad'ama damuwarta
ko zata d'an rage zafi sai ko ta fara magana cikin kuka" yaya Salman wai miyasa
Alhaji yake mana haka ne, miyasa baya k'aunar mu, miyasa har yanzu shine mai
alhakin ruwa da tsak'i a al'amuran mu, miyasa baya fahimtar soyayyar dake tsakanin
Iyaye da yayansu shi kawai kansa ya sani.?"

"Ka duba kaga abinda ya min, ya min aure bada sani na ba ba tare da na shirya ba na
hak'ura, amma saïda ya kawo ni gidan miji kawowar da bana jin akwai wata ya mace a
tarihin duniya da aka tab'a mata ita sai ni shi ma na hak'ura, amma bai ishe shi ba
shine yanzu zai zareni daga cikin yan uwana ya hana ni zuwa inda suke, kuma suma ya
hana su zuwa inda nake, wannan wace irin uk'uba ce dan Allah, wallahi ni ba zan iya
zama a gidan nan ba yaya Salman, ni dole na tafi gidan mu dan in na zauna nan to
kasheni za kayi da duka" rigar baccin da ta saka ta tub'e da k'arfi tana nunawa
Salman jikinta da fuskarta tana fad'in" ka duba ka gani yaya Salman jikina duk
shatin bulala ne, dukan da Alhaji yasa aka min a gaban mahaifana da kuma wanda kai
kamin, wallahi ba zan iya zama a gidanka ba yaya Salman saboda bâ kada imani ko
kad'an k'eta kawai ka iya" fad'awa tayi jikinshi tana kuka da k'yar Salman yasa
hannu ya fara shafar bayanta amma da ya ji laushi sai ya fara mata wani salon shafa
har yana 'ko'karin kaiwa a k'irjinta dan haka ta d'agashi ta kwanta akan gado taci
gaba da kukanta, a kasalance Salman ya koma d'akinshi ya kwanta gaba d'aya ta
rikita mashi lissafi ko kad'an bai iya tuna abinda ta fad'a ba, shauk'in da ya ji
lokacin da ta rumgume shi kawai ya keji, da k'yar bacci ya d'aukeshi cikin wannan
mawuyacin halin da bai taba jin irin sa ba a rayuwar shi.

23:00 Ummi ta shigo d'akin cikin sallama da muryarta data dakushe wajen kuka, har
ta aje faranti ta zuba mashi duk yana bacci bai san ta shigo ba, saida ta daddab'a
pilow da yake kwance sannan ya tashi aje masa tayi ta ta koma d'akinta.

Tun 07:30 Ummi ta kammala had'a abun karyawa amma bata ji d'uriyar Salman ba haka
ta zauna tana jiran taga fitowar shi, 09:20 ya fito da dogon wando sai singlet fara
k'al kallonshi Ummi tayi ganin ba wani shiri bane yayi amma ya yi masifar had'uwa
a cikin zuciyarta tace(na tabbata yaya Salman bâ yada burin auren mace irina, shi
ma zaiso ace ya auri kyakyawa kamar shi amma Alhaji ya masa yankan k'auna).

Zaunawa yayi ya karya dan Ummi har tayi nata break d'in, yana idawa yace mata" ki
fito min da kujera waje" yana wucewa ta mik'e ta d'auki d'aya daga cikin na dinning
ta kai masa zata juya ta tafi yace" zauna nan" jujjuyawa tayi ganin babu wata
kujerar yasa tace" bara na d'auko kujera" kallon daya mata yasa ta cire takalminta
ta zauna in da ya nuna mata, k'afa ya d'ora mata a cinyarta tare da mik'a mata
abin yankar akaifu kallonshi tayi baki bud'e tace" wannan kuma fa, miye haka?" bai
tanka taba hakan yasa ganin babu wasa a al'amarin yasa ta fara masa gyaran akaifun,
kuma abin takaicin ma babu wani abinda za'a cire haka kawai tayi iya yinta ta cire
na cirewa tana idawa dana k'afa ya mik'o hannu, nan ma Kallon shi tayi tace" yaya
Salman wai miya samu hannayen naka?" Hararan ta yayi yace" wallahi zan zubar maki
da hak'ori" turo baki tayi ta rik'e hannun, Kallonta yayi ya kalli hannunta saboda
wani sanyi da ya ji tattausan hannun Ummi ma'abocin zufa a kowane yanayi zafi da
sanyi, haka hannunta yake cikin zufa kowane lokaci, sab'anin nashi mai cikakkar
tsoka da dogayan yatsu da santsi haka Ummi ta gama masa gyaran tsaf tana idawa
yace" to maza kije d'akina ki d'auki d'aya daga cikin jakunkuna da ke da kwai ki
shiryamin k'ananan kayana a ciki da duk wani abu da mutum zai buk'ata idan yayi
tafiya." kai ta dafe cike da nuna damuwa kafin tayi magana yace" ba zaki yi ba ko?"
kai ta girgiza sannan ta wuce jiki a sanyaye, Saïda ta b'ace ma ganinshi sannan ya
kau da kanshi.

Tsaf Ummi ta had'a mashi kayanshi tare da duk abinda zai buk'ata, kama daga turare
maclean brush mai zanin rufa kayan bacci ect...., tana idawa ta shiga cuisine dan
had'a abincin rana dan 12:50 tayi, tana cikin aiki ya lek'o yana fad'in" ina aikin
dana saki?" cikin sauri tace" na kammala suna d'aki" hararanta yayi yace" amma ba
kisan ki ce kin gama aiki ba idan an saki?" turo baki tayi tace" kayi
ha'kuri"wucewa yayi ya barta, d'akinshi ya shiga ya bud'a kayan sosai ya ji dad'in
ganin yanda ta had'a masa kayan ba tare da ya nuna mata ba harda ma abinda shi
kanshi bai taba tunanin d'aukaba duk lokacin da zaiyi tafiya wato maclean da brush,
duk lokacin da yayi tafiya saidai ya siyi sabbi idan zai taho kuma ya baro su dan
sun gama mashi aiki, wanka yayi ya shirya cikin dogayen kaya da hula yayi kyau
sosai yana fitowa ya k'walla kiran Ummi har tuntub'e take wajen sauri tana zuwa ta
zube k'asa tana fad'in

"Gani"d'auko min sallaya" mik'ewa tayi ta d'auko mik'a masa tayi, hararanta yayi
yace" bara na sunkuya saina karb'a ko?" turo baki tayi sannan ta sunkuya ta mik'a
masa, yana karb'a yace" wuce muje " binshi tayi tana guna-guni har saïda ya shiga
mota sannan yace" oya, kimin Addu'a zan fita" dalala ta kalleshi tace" yau dai da
alama bokan naka ce maka yayi saina maka addu'a sannan harkokin zasu tafi yanda ya
kamata ko?" cikin zafin rai ya bud'e k'ofar mota yana shirin fitowa, da sauri ta
maida k'ofar ta rufe tana fad'in" sai ka dawo to" juyawa tayi zata wuce yace" ke
wannan ce addu'a, haka ake a garin ku?" murgud'a baki tayi tace" in dai sai na maka
addu'a zaka tafi, to ka kwana anan" da gudu ta shige d'aki, shi kuma k'wafa yayi
yaja mota yana fad'in" lallai da sauranki har yanzu, amma zanyi maganinki nan ba da
d'ad'ewa ba."

Tana gama aikinta tayi sallah tana idawa ta shiga gyaran d'akinshi tana kammalawa
ya dawo gidan, saïda yaci abinci sannan ya shiga d'aki ya tattaro mata kayanshi
k'anana yace ta wanke, saida tasha mari sakamakon cewa da tayi" haba dan Allah
wannan wane irin rashin imani ne? wannan kayan ina zan iya wanke su, nifa ko a
gidan mu bana wanki bare kuma nan" bakinta ya murd'e yace" nan ai ba gidan ku bane
gidan mijinki ne, kuma daga yau karna saké jin kince min mara Imani, in kuma ba
haka ba wallahi saina sauke maki Kafad'a" tsaki tayi tace" wai miji, ina mijin yake
anan? saidai muna maza" ji kake Tasssss, ya kasheta da mari tare da fad'in" ke har
kin isa ki fad'amin haka, wallahi ko Sa'ada dake gaba dake bata isa ta fad'amin
haka ba, bare kuma ke da aka haïfa a gabanta" haka ta fara wanki tana kuka tana
fad'a, bata gama ba sai misalin 17:40,saboda ko a gida ita ma kayan da suka zama
wajibi ne a gareta ta wanke da kanta take wankewa, amma manyan kaya mai wanki ake
bawa ya wanke mata, amma yau gashi tana ma k'aton gardi wanki( inji Ummi fa).

Tana idawa ko wanka bata yiba ta d'ora girkin dare, a gajiye ta kammala aiki bayan
sallah isha'i, tana gamawa ta aje Kwanukan a dinning tayi alwala tayi sallah tana
sallamewa daga nan bacci ya d'auketa ko shafa'i da witri bata yiba, Salman na
lek'awa yaga tana bacci ya fito yana cewa" raguwar banza, ai dama da gangan nake
saka ki aikin dan babu tsiyar da kuke a gida ke da su Khairat da jawahir sai
iskanci da zuwa gidajen juna ana d'aukar photo" da kanshi ya zuba abincin yaci ya
koma d'akinshi yana latse latse a ordinateur d'in shi, jin an fara kad'a iska ga
walk'iya da ake ana cikin haka aka fara yayyafi har ruwa suka fara k'arfi, ganin an
d'auke wuta yasa ya kunna wutar wayar shi ya tashi ya nufi d'akin Ummi dan yasan
yanzu zata fara neman taimako, k'aro yayi da Ummi k'ofar d'akin tana shirin fitowa
daga ita sai towel d'in dake d'aure a k'ugunta tana shafa turare aka d'auke wutar,
kallon juna su kayi sum sum Ummi ta haye saman gadon ta kwanta, Salman ma zaune
yayi gefenta tsawon lokaci ya d'auka a zaune, ganin ba ada niyyar maido wutar ya
gyara kwancinshi shi ma bacci ya d'aukeshi.

Salman ne ya fara farkawa da k'yar ya bud'a idonshi saboda haske an maido wuta suna
bacci, addu'ar tashi daga bacci yayi( Alhamdu lillahi lazhi ahayana ba'ada ma
amatana wa ilaihin nushur).
Maida kallonshi yayi wajen da Ummi ke kwance, wani irin fad'uwar gaba ne ya ziyarce
shi ganin Ummi zigidir babu komai a jikinta komai ya fito waje, towel d'in da ta
kwanta da shi ya kama gabanshi saboda gigin bacci kuma ba tasan ma an yiba, wasu
irin yawune ya dinga had'iya da k'yar ga wata irin fitinanniyar sha'awa da ta taso
mashi lokaci d'aya ji yake kamar ya abka mata, saidai wata zuciyar na gargad'inshi
akan hakan, rufe fuskarshi yayi da hannayenshi yana fadin" a'a Salman ka zama
namiji mana, kar kayi haka karka zubar ma kanka mutunci mana" maida kallonshi
yayi amma ina saida zuciyar shi ce ta fizge shi ya kai hannushi a k'irjinta ya
shafa, lumshe ido yayi tare da sauke numfashi a hankali yace" ya salam, Allah ka
kare ni" zunbur Ummi ta mik'e tare da yayumo zanin rufa ta rufe jikinta tana
kallonshi tace" miye haka kuma, kai da kanka, ashe haka kake bansani ba "?" basarwa
yayi kamar ba shi ba ya tashi ya fita duk takaici ya ishe shi da kunya, sallah ya
fara yi sannan yayi wanka ya shirya, yana fitowa dai-dai da fitowar Ummi da
hijabinta ta idar da sallah, cike da raini tace" ina kwana" kallonta yayi yace"
bara na duk'a saina gaishe ki ni" durk'usawa tayi ta saké gaishe shi amma bai amsa
mata ba, mik'ewa tayi zata shiga cuisine yace

" ki had'a iya bakinki, ni yanzu zan tafi" cike da mamaki tace" ina kenan?" baiyi
tsammanin tambayar daga gareta ba shiyasa yace" balaguro zanyi" cikin ladabi tace"
balaguro zuwa ina kenan?" Cotonou " ya bata amsa baki bud'e ta kalleshi tace"
Cotonou fa yaya Salman,to idan ka tafi ni da wa zan zauna a gidan?" Kallo ta yayi
yace"kamar ya,mi zai cinye ki a gidan to?" kawai sai tasa kukan shagwab'a tace"
wallahi ni ba zan yarda ba, haka kawai ka tafi ka barni ni kadai cikin gida kamar
manya" abu kamar wasa Ummi ta dinga tsala kuka, amma rashin imani na Salman ya ki
damuwa saida ya wuce yace" idan kin zauna ke kad'ai mugun abu ya jima bai cinye ki
ba"sai kud'in daya fiddo ya jefa mata a k'irji ya wuce ya barta nan, da gudu ta
fito k'ofar d'akin ta tsaya tace" kaga kazo ka d'auki kud'inka, bana so tsiyar me
zanyi dasu, tunda dai kai bâ kada imani zalinci kawai ka iya mugu kawai"
takalmanshi ya ciro ya jefo mata, da sauri ta shige d'akin tare da rufewa da key,
d'aukar takalmanshi yayi yana fadin" zan dawo ai bacan zan zauna ba, sai kinsan kin
fad'amin haka, mai kama da mage kawai marar kunya"yana fita Khamis yana jiranshi
dama ya d'aukeshi suka wuce suna gaisawa, Ummi kam kuka kamar ranta zai fita.

```muje zuwa dai mutane na```


28/02/2019 à 17:02 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```wannan soyayya na yarda had'in allah ce, sai dai in ce allah ya bar k'auna😘```

```-My Meelat```
```-My Heenat```

```Ku na Musammam ne ku nada karamci sosai a gare ni.


```
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
( _Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜_ 🤛

*Page*

4⃣5⃣4⃣6⃣
4⃣5⃣-4⃣6⃣

Khamis ne yace" wai ni ban tambayeka ba da wa kabar mutuniyar ne a gida?"uhumm to


ita da wa kake so na barota to, ko kaima kana nufin na samo mata wanda zai taya ta
kwana kafin na dawo kamar yanda take fad'a?" gyad'a kai Khamis yayi yace" sosai
kam, kai da a tunaninka zaka barta ita kad'ai ne ba tare da kowa ba?ai kaima kasan
hakan ba zai yiwuba ka bar yarinyar mutane a gida ko sati ba tayi a gidanka ba kace
zaka k'yaleta ita kad'ai, dan ma kasamu ta barka ka tafi" wata irin dariya Salman
ya shek'e da ita kafin yace" lallai kam akwai mahaukata da dama a garin nan, kai
yanzu kana tunanin wannan yarinyar zata iya hanani yin abinda naga dama? to bâ ita
ba ko wacce ta fita ma bana jin ta isa bare kuma ita" haushi Khamis ya ji yace" kai
kaga wallahi da gaske nake fad'a maka, bai dace ba ace ka barta ita kad'ai a wannan
sabon gidan, kai kan kafa bak'one a gidan bare ita sannan babu wanda ta sani a
unguwar kaga hakk'inka ne kareta da kula da ita, idan wani abu ya sameta mi zaka
fad'ama iyayenmu?" shiru yayi yana tunani kafin yace" to malam Khamis yanzu
fad'amin ya kake so ayi?" to yanzu dai kaga wannan tsohon mai ran k'arfe ya hanata
zuwa wajensu bare ta koma can gida, haka kuma ya hana kowa zuwa wajenta bare a
d'auko ko yara akai mata can kasanta ko da wasa da yara, kenan ni ina ganin in har
zaka amince to yanzu idan na aje ka zanje sai na d'aukota na kaita can gidana sai
su zauna tare da Jawahir nasan za tayi farin ciki da hakan." kallonshi Salman yayi
yace" kana ganin hakan babu wata matsala?ni fa bana son abinda zai raba ni da
dangina" kai ya girgiza yace" insha Allah babu abinda zai faru da yardar Ubangiji
zan kula sosai" d'aga kafad'a yayi yace" OK ba damuwa ka d'aukotan kawai, amma
kafin ka d'aukota ka biya ka siya mata yar k'aramar waya wacce zata dinga kunna
tocila da dare idan an d'auke wuta, dan karta takura maku kuna tsaka da hutawa"
dariya Khamis yayi yace" saboda ta kunna tocila za'a siya mata wayar? badan ka
dinga kiranta kana jin halin da take ciki ba? kumafa karka manta kai ka amsar mata
waya kuma babbar waya ka amsa amma sai kace a siyo mata yar k'arama, wato ka siyar
da ta-ta kud'in kuma k'arfi ya cinye ko?" dariya kawai Salman ke yi tunda Khamis ya
fara magana kafin yace" e mana na cinye dan na nuna ma duniya da kai da kaya duk
mallakar wuya ne." gira Khamis ya had'e tare da d'agata sama yace" eyee,lallai
mutumin nan, ai banyi tunanin zaka fara irin wannan tunanin akan Ummi ba kaga kuma
idan kana jin irin haka a ranka to fa wata rana za muga yar k'anwar tamu da juna
biyu" yana k'arashe maganar ya fashe da dariya yana kallon Salman, shi kuma photon
Ummi ne ya dawo masa cikin 'kwa'kwalwa lokacin da ya ganta babu kaya a jikinta da
irin sanyin da ya ji lokacin da ya tab'a k'irjinta lumshe ido kawai yayi ya jingina
kansa a kujera yana murmushi, ina ma ace hakan zata sake faruwa ko da tab'awa ne
yayi, Khamis ne ya katse shi yana fad'in" to malam kawo kud'in ko?" hararanshi yayi
yace" kai gafara can dallah k'anwarka d'in dan zaka siya mata abu saina baka kud'i?
to bâ zan bayar ba." dariya Khamis ya ci gaba da yi yace" kaji mutum kai, baka ji
ance gwamnati ta hana aikin banza ba? ka kawo kud'i matarka ta samu waya ka dinga
kiranta kuna gaisawa, ka k'i bada kud'i kuma kaje ka dawo ba tare da kayi magana da
matarka ba." to sai me? na fad'a maka ina san jin muryarta ne, ni bata dameni ba"
wani Kallo Khamis ya watsa mashi yace" malam manu kenan har yanzu baka san mace ba
amma, daga ranar da zaka san wacece Ummi to fa a lokacin zaka fara damuwa da tunani
a kanta." tsaki Salman yaja yace" kar Allah ya kawo ranar da zan santa ko, yarinyar
da nake Addu'a naga tsorona a idonta sai gashi yanzu d'an zaman da mukayi na fara
ganin wannan tsoron, haka kawai lokaci d'aya saina b'arar dashi,Allah karya nufeni
da ganin ranar da zan tub'e kayana a gaban wannan k'azamar yarinyar harna
kusanceta."murmushi Khamis yayi yace" banda fariya manu, kai yaro ne baka san
tasirin mace a wajen namiji ba shiyasa, amma tunda Allah ya had'aku zama a inuwa
d'aya to ina tabbatar maka zaka sani lokacin zai zo, s'il plaît a Dieu."

Tsaki Salman yayi yace" insha Allah haka ba zata faru ba" shiru su kayi babu wanda
ya saké magana har ya aje shi gidan Bus Sonef su kayi ban kwana, kamar yanda tun
jiya yayi ban kwana dà iyayensu suka masa Addu'a sannan ya juya, saïda ya tsaya ya
siya mata waya tare da sabon puce( sim card) sannan ya wuce gidan.

Tunda Salman ya fita Ummi ta zauna saman kujera ta fara kuka, Sallamar Khamis ne da
taji ya sata saurin goge hawayenta tana amsa sallamar, tunda ya shigo ya fahimci
kuka take amma da yake mutum ne shi wanda bai san shiga rayuwar kowa dan haka koda
suka gaisa yace" k'anwata ko dai dan ya tafi ya barki kike kuka?" kai ta girgiza ba
tace komai ba dan haka shima yace" to kinga tashi ki had'o kayanki zan tafi da ke
can gidana ki zauna tare da yar uwarki har lokacin da zai dawo" kai Ummi ta girgiza
tace" a'a yaya Khamis ka barni anan idan yaji na tafi can bada izininshi ba zai min
fad'a ko ma ya daké ni, kawai ka barni zan zauna ni kad'ai Allah zai kareni"
tausayinta yaji ya kama shi sosai amma sai yace" haba hajia Zeinabou karki damu fa,
shi yace nazo na d'aukeki" da sauri ta d'aga kai tace" da gaske yaya Khamis ? "
k'warai Kuwa tashi ki had'o kayanki mu wuce" tashi tayi da gudu tana farin ciki
Khamis kuma a zuciyar shi cewa yayi,lallai duniya ta kusan tashi wai yau Ummi ce
take tsoron fad'an Salman ha'ki'ka yayi gaskiya da yace ya fara ganin tsoronshi
a idon Ummi kuma ga dukkan alama labarin Salman da Ummi ya kusa canzawa.

Tsaf ta had'o duk wani abun buk'atarta ta rufe gidan suka tafi bakinta har kunne.

Suna shiga gidan suka fashe da k'ara ita da Jawahir suna ta tsalle kamar yara
tsabar farin ciki, Khamis dai fita yayi ya barsu bayan ya had'a mata wayar ta ya
bud'a mata WhatsApp,haka suka wuni Ummi nata bawa Jawahir labari irin muguntar da
Salman ke yi mata ita dai Dariya kawai take, tare su kayi girkin dare suka kammala
suka shirya Suna zauna anan Jawahir ta bawa Ummi numbobin k'awayensu da nasu Nadia
nan fa aka hau charting k'arshe ma d'aki ta shige tare da maradarta tana kurb'a
tabar Jawahir tana jiran mijinta ya dawo.
28/02/2019 à 17:02 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜_ 🤛

*Page*

4⃣7⃣4⃣8⃣
4⃣7⃣-4⃣8⃣

Tunda Khamis ya dawo ya tambayi Jawahir ina Ummi, data fad'a masa tana d'aki wayar
shi ya ciro ya turawa Salman numberta sannan ya shiga harkokin gabanshi.

Ummi hira kawai take da k'awayenta a groupe d'insu musamman RAYUWAR MÛ A YAU, tana
jin dad'in hirar sosai dan duk ta k'aruwace a keyi, 23:30 ta wuce bak'uwar number
ta shigo wayarta, dubawa tayi dan taga ko waye sak'one a rubuce kamar haka,

_"waya baki izinin bud'a WhatsApp, sannan mi kike har yanzu da kike en ligne?"
take Ummi ta fahimci ko waye, amma tayi niyyar raina masa hankali dan haka ta
maida masa ita ma tace" wanda ya baka izinin bud'awa a lokacin da ka bud'a, sannan
abinda kake yi nima shi na keyi" bada jimawa ba ya maido mata yace" karki raina min
wayo, ina hira ne da budurwata mai deb'emin kewa" dakewa tayi ta maida masa ita ma"
kenan jirgi d'aya ya d'auko mu ni da kai, dan nima nayi kewar samari na ne shiyasa
nake rage dare da su" wani irin takaici ne ya kama Salman dan yasan ta aika, maida
mata yayi" ke bana san iskanci wallahi ki sauka ko kuma ranki ya b'ace" dariya Ummi
tayi ta maida masa da" 😏😏😏😏😏😏" take ya maido mata yana fad'in" wa kike juyama
bakin? wallahi ki kiyaye ni" dariya tayi tâ koshi sannan ta maida masa" kaga malam
dan Allah nifa matar aure ce ka kemin mad'e, idan mijina ya sanka to zai kashe ka,
dan haka sai anjima" harta koma cikin groupe ya aiko da wani sak'on dubawa tayi
taga yace" har haka mijin naki ke sonki dama?" maida mashi tayi da" sosai kam, yana
sona fiye da ransa, nice mahad'in rayuwarshi" dariya yayi yace" to ko zan iya ganin
photonki da na mijin naki?"cewa tayi" mi zai hana, amma karka ce mijin yafi matar
kyau idan ka gani" kafin ya aiko ta dunk'ule photo kusan talatin ta aika masa wanda
Jawahir ta tura mata d'azu, bud'a photunan yayi ya fara kallo, sak'onta ne ya saké
shigowa tace" idan ka fiddo ni a ciki zan maka kyauta" sai lokacin ya saké duba
photunan da kyau, babu inda take ita kad'ai duk ita da su Jawahir ne sai kuma
k'annanta su Islam da Mubbashir, inda ya ganta tare da su Jawahir da Khairat Kwance
akan gado tana tsakiyar su tayi dariya sosai hak'oranta sun bayyana ga kumatunta
sun lotsa kamar ka saka k'wandala kuma ta zauna daram, babu ko d'igon Kwalli a
fuskarta amma tayi kyau, shi ya aika mata yace" wacce tafi zama bak'a a ciki to ke
ce ita, kuma banga mijin naki ba?" dariya ta aika masa tace" ka canka dai-dai, dan
haka ka zo da kumatunka ka karb'i cadeaux d'inka, banda photon mijina" _tambayarta
yayi" ban gane kumatuna ba? miyasa baki da photon mijinki?" maida mashi tayi" kaga
nifa ina da abinyi , dole ne saina samu photonshi?nida nake ganinshi kullum a cikin
zuciyata, dan haka sai anjima_ " _tana aika masa ta sauka ta kwanta sai bacci_ .

Tunda Ummi tayi sallah ta koma ta kwanta sabon bacci, dan rabon da tayi baccin safe
harta manta, lokacin da Khamis zai fita yana break ya tambayi Jawahir Ummi, data
fad'a masa tana bacci dariya yayi yace" to wannan baccin haka take yin shi ko gidan
malam manu?inko hakane akwai dangwarma dan shi nasan ba yada da'bi'ar siyan abincin
waje, kuma yana fita da wuri to kenan ya yake oho"Jawahir ce tace" ai in fad'a maka
yaya Salman yanzu ya fara gyara mata zama, dan jiya zuwanta nasha labari , nidai
har cikina ma ya fara ciwo tsabar dariya" da gaske kike?" ya tambayeta, " e mana,
amma gaskiya yaya Salman baya kyautawa dan inda kaga jikinta duk duka ne,wallahi
sai taban tausayi kuma da naga jikinta a farfashe" wani iska ya hurar yace" ni
nasan dama sai haka ta faru, dan Ummi ba taji, Salman kuma ba yada hak'uri ga
zuciya" to mijina me zai hana ka masa magana akan dukanta, kaga fa hakan babu kyau
tunda yanzu tana yin abinda ya sata" ajiyar zuciya ya sauke yace" zan masa, amma
sai ya dawo daga tafiya, dan kinsan halin shi murd'add'an mutum ne" haka su kaci
gaba da tattaunawa harya gama break ya fita.

Jawahir ce zaune a falo tana charting, Salman ta gani en ligne dan haka ta gaishe
shi ya amsa, tambayar ta yayi ina Ummi tace tana bacci, cewa yayi taje ta tasheta,
haka taje tasa Ummi gaba tana tadi amma tak'i tashi, dole ta fad'a masa tak'i
tashi, kiranta yayi appel vidéo yace ta bata wayar, da k'yar Ummi ta bud'a idonta
ta kalli wayar sai magagin bacci take da hamma,

"ke dallah tashi malama, wato an samu dama ko?" juya baki tayi tace" dole kam na
dama, tunda nazo gidan yanci, ba kamar wancen kurkukunba" tsaki yayi yace" yanzu ai
kin fad'i komai, tunda kinga bana kusa dake" d'an karamin tsani tayi tace" wai ni
malam miye na sawa a tasheni ina bacci na dan Allah? kuma kai bâ wani abu mai
anfani zaka fad'amin ba, ko dai harka fara kewata ne tun yanzu?"cike da takaici
yace" waye zaiyi kewar ki? ni? Allah ya kiyaye" a cikin muryar baccinta tace" in
dai hakane to kashe wayar" tana gama fad'a yako kashe wayar, tsaki tayi ta koma ta
kwanta.

k'arfe 10:15 tana ta baccinta saiko Ihu da kwaramniya anata jinjigarta ana fadin"
ki tashi ki tashi ke" cikin Farin ciki ta bud'a ido dan ta d'auki muryar yan uwan
nata, Kallonsu tayi tace" Khairat daga ina kuke yanzu?" kinga kedai taso muje falo"
hannunata taja suka wuce da kayan bacci a jikinta riga da wando k'anana,falo suka
fito, tana fad'in" wai ku kuma miya kawoku nan ne ku dukan ku?" Nadia ce da duk
yayi wani yaushi tace" dama mun san yaya Salman zaiyi tafiya, shine yaya Khamis
yace kina nan , shiyasa muka zo dan munyi kewarki" gyara zamanta yayi tace" amma
kuma su yaya suka kawo ku?" cikin zumud'i Khairat tace" e mana, kuma sunce ma zasu
dunga kawo mu har lokacin da zaki koma" aifa nan hira ta b'arke Ummi ko wanka ta
kasa yi saboda dad'in hirar da suke, haka lokacin ya tafi har azahar kafin Ummi ta
kalli Jawahir tace"uwar gidan Khamis ba kishan furarki saida nono" dariya tayi
tace" kai yar uwa duk wannan kirari haka, ai saiki fasamin kaina" ita ma dariya
tayi tace" to ai girman ki ne, kinga nifa yunwa nake ji, me kika dafa mana ne?"
hararan ta tayi tace" saidai kije ki dafa, dan wanda na dafa munci ni da Mijina"
baki bud'e Ummi tace" lallai ma yarinya, kina nufin ina bak'uwarki amma zanje na
dafa abinci da kaina, kamar a gidan wancen mugun, ai kam ba zata sab'u ba"dariya
Jawahir tayi ta mik'e tsaye tace" to uwar gidan yaya manu mi kike so in dafa maki?"
k'ara shigewa tayi cikin Kujera tace" ki kawo min Tea da bred,sai ki soya kwai yaji
albassa sosai,amma karki samun arom ( d'and'ano),gishiri kawai ya isa." wucewa tayi
tana murmushi ta shiga cuisine, Khairat kuma cewa tayi" yayi dai hajia Abu, kenan
haka kike bawa Yayana umarni ko a gidan?" tab'e baki tayi tace" ke wannan yayan
naki? wanda ko murmushi ba yayi bare dariya ai shi kibar shi inda kika ganshi
kawai"

Tana gamawa ta kawo mata, k'asa ta zauna tana ci suna hira harta kammala, haka suka
wuni a gidan cikin farin ciki, tare sukayi girkin rana dana dare, suna idawa
Jawahir ta shiga wanka ta cab'a kwalliya wa mijinta, tana fitowa ta d'auko blander
tasa jik'akk'en dabino data jik'a da ranke da kanunfari a ciki ta markad'a, ta koma
tasa kankana ta markad'a ta tace ruwan, sannan tasa maltina a ciki da madara peak
da k'ank'ara (glasse).

Ummi data saki baki tana Kallonta tace" Jawahir kema harkin fara wannan tsirfa
tsirfen na bawa kai wahala ko?"dariya tayi tace" wannan aiba na bawa kai wahala
bane, wannan har lafiya zai k'ara maki, ko ba kiga da kanana a ciki ba? ga madara
sannan ga dabino da kanunfari"mik'a mata tayi tace" sha kiji kema" waro ido tayi
waje tace" ni, rufamin asiri kinji, wannan ai saiku masu maza" hararanta Khairat
tayi tace" bana san iskanci, ke kuma fa ina kika kai mijin naki, nasan Yayana fa
wallahi namiji ne na gaske, kisha dan Allah kiji akwai dad'i fa" ke wannan mutumin
babu abinda zai shiga tsakaninmu, dan na tsaneshi babu ta yanda zan bashi kaina
wallahi" Hafsat ce ta tab'e baki tayi tace" kinga karb'i in kinsha, in kuma ba zaki
sha ba ta bamu musha" Kallon mamaki ta bita dashi tace" oo Hafsat kema wai har
kinsan anfanin wannan, keda mijin naki nawa kuke?" dariya suka saka mata kafin
Nadia tace" ke namiji fa namiji wallahi baya kad'an" kau da kai Ummi tayi tace" ni
dai kam na rainashi gaskiya" Hafsat ce tace" lallai baki san shi bane shiyasa, amma
wallahi ina jin abinda yake ko mijinki baya yinshi" Jawahir ce tace" ku baku san
dalilinta na fad'ar haka ba, yaya Salman dai duk ya girme ma mazajen mû, a shekaru
dama girman jiki, kinga kenan ita kad'ai tasan azabar da take ji, amma in za'a
fad'i gaskiya Hafsat kinsan babu ta yanda za'a had'a yaya manu da yaya Deen" ido
ta fiddo tace" ke rufamin asiri, ina ni ina wannan ai sai ya kasheni" dariya suka
saka mata, Jawahir kuma ta saké mik'o mata, sannan ta karb'a ta kifa kai, bata
sauke ba saida Jawahir tace" ke bani nan malama, sai kin shanye?" dago kai tayi
tace"kai gaskiya da dad'i" dariya su kayi Jawahir tace" dad'i a baka, dad'i a k'asa
ba" tab'e baki Ummi tayi tace "humm, kina nufin wannan dad'in a baki haka yake ko
a wajan mai gida?" shigowar Khamis ne yasa su shiru, da sauri Jawahir ta mik'e ta
tare shi,nan ya fad'a masu su tashi mazajen su na jiransu, haka kowace ta kama
gabanta su naji kamar kar su rabu.

Ummi na ganin hankalin Jawahir ya koma wajen mijinta ta d'aga kai ta shanye sauran,
cikin sand'a ta mik'e ta shige d'akinta dan tasan akwai tashin hankali inta fahimci
ta shanye.

~Kuja muje~
05/03/2019 à 17:28 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

4⃣9⃣5⃣0⃣
4⃣9⃣-5⃣0⃣

Da safe Ummi da Jawahir suna zaune tana since mata kai suna hira, Abba ta kira
bayan sun gaisa take fad'awa Abba tana neman gafara akan abinda ya faru, budar
bakin Abba yace,

"Haba Mamana babu komai fa ni nasan ba laifinki bane, dan haka ki kwantar da
hankalinki kinji."

"Abba na gode amma ku nema min gafarar La Mama itama tana fushi dani?"

Cewar Abba "a'a ko kad'an mahaifiyarki ma bata fushi dake"

"To Abba na gode sosai ku gaishe min da kowa da kowa"

"Zasu ji insha Allah, nasan mijinki ya tafi yanzu to ke kad'ai ke zama a gidan?"

Dariya tayi tace "a'a Abba ina gidan yaya Khamis, amma fa Abba karku bari Alhaji
yaji."

Dariya Abba ma yayi yace "karki damu ba zai ji ba"

Haka su kayi sallama, Ummi da Jawahir haka suka wuni suna shan hirarsu suna aiki
har dare Khamis ya shigo yace masu Nadia bata da lafiya.

Bud'ar bakin Ummi cewa tayi "haba ni nasan sai anyi haka dama, dan tunda naga Nadia
jiya nasan akwai wani abu a cikin cikin nan nata data aje."

Jawahir ce tace "ke kuma ina ruwanki da cikinta to?"

"Haba wane ina ruwana dan Allah kina ganin yarinya ta d'auki ciki duka ko sati uku
ba ayi da aurenta ba."

"To sai me in ta d'auka ai albarkar auren kenan "

"Gaskiya tayi sauri kawai daga ta b'ata sai ciki kamar dama jira take, ai wannan
tayi saurin bada kai nasan ma yaron kama zaiyi da ita idan ta haiho shi."

Khamis daya saki baki tunda ta fara magana yana kallonta ne yace "lallai Ummi ashe
kin wuce in da nake tunaninki."

Tashi tayi cikin jin kunya tace "kayi hak'uri yaya Khamis na manta kana nan"

Jawahir kam dariya tayi ta haye k'afafun Khamis tare da shafar cikinta tace "nima
fa ina ganin kamar na d'auka"

Shafa cikin nata yayi yace "ashe dai ni bana wasa bane"

"To ba zan iya ganewa ba"

"Oho haka kika ce? to bari yau d'in nan saina saka mashi dan haka ki shirya da kyau
kuma babu raki babu wannan kukan."

Haka su kaci gaba da hirarsu irin ta ma'aurata cike da nishad'i.

*Da safe*Ummi na kallo bayan sun kammala cin abinci Jawahir ta shirya suna shirin
fita ita da Khamis, cike da mamaki Ummi tace "Jawa yau kuma tare zaku fita kenan?"

"E tare zamu fita amma ni gidan Nadia zai aje ni."

Zama Ummi ta gyara tace "kinji 'yar banza, yanzu zaku fita tare amma shine kika
k'yaleni?to tare zamu tafi yarinya."

Khamis ne yace "a'a kar ma ki fara dan babu in da zaki je sai kin fad'awa mijinki
sannan ki fita."

Cikin shagwab'a tace "haba yaya Khamis dan Allah ka bari naje idan na dawo saina
fad'a masa."

Cikin tsawa Khamis yace "ke ashe ba kida hankali, to wallahi babu in da zaki a
gidan nan, in kuma kina so kije ki kira ki fad'a masa"

"Haba wallahi dana kira na fad'a masa k'wara na zauna banje ba, wannan d'an rainin
hankalin idan na kirashi zai cikani da surutun banza kuma k'arshe ba zai bari naje
ba."

Cikin jin haushi Khamis yace "ke Ummi ashe ba kida hankali ina kallonki kamar mai
hankali, mijin naki kike fad'a ma haka, to bari kiji in dai kina so mu shirya dake
to dole ki girmama mijinki in dai muna tare dake dan ba zan d'auki wannan rainin
ba, kuma wallahi na sake ji saina nuna maki d'anyan kai fiye dana Salman."

"Shashasha kawai kina nan kina shirme kin kasa tsayawa ki kula da mijinki har kinsa
shi tunanin k'ara aure ko wata d'aya baki cika ba a gidanshi, za kiyi kuka in kika
bari ya auro Nuseiba k'anwarki a matsayin abokiyar zamanki." yana fad'a ya fice
daga gidan.

Ummi kam tv ta k'ura ma ido ta kasa d'aukewa har saida taji hawaye nabin fuskarta.
05/03/2019 à 17:28 - Mamar Latif💃: 💑 AUEEN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

*Choukoura (maman deeja)*

_Ina jin dad'in comment d'inki sosai, nima ina yinki💯_

_yan uwanmu, kuma ma'kotanmu *NIGERIA* muna muku fatan alkairi, muna tayaku addu'a
Allah ya zab'a maku shugaba na gari mai adalci da taussayinku, Allah yasa baba
*BUHARI* yaci gaba da mulki dama ire irensu masu adalci da 'kaunar talakawansu._

_My Heenat ( *RAHEENAT)* ina tayaki murnar kammala wannan daddad'an littafin naki
mai suna *RAYUWAR SAUDAT* tabbas ya fad'akar kuma ya ilimantar tare da
wa'azantarwa, ina maki fatan alkairi tare da kaifin bassira da zak'in hannu, Allah
kuma ya yafe maki kura-kuran da kikayi a ciki, dai-dai kuma Ubangiji ya baki lada
ya kuma sa sanadiyar shigarki aljanna kenan_

```Daga Samirar ki 😍ina sonki 'yar hannun dama na.```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*
5⃣1⃣5⃣2⃣
5⃣1⃣-5⃣2⃣

Abu kamar wasa sai Ummi ta d'aga murya sosai tana kuka, kusan minti biyar tayi a
haka, daga bisani wata zuciyar ce ta tambayeta" wai mi kike ma kuka ne, auren da
akace zai 'kara, ko kuwa dan an hanaki fitar?"

Da sauri ta goge hawayenta tana fad'in" haba ni d'ince zan tsaya ina kuka saboda
zaya aure, to ina ruwana da aurenshi, idan yana so yayi mata hud'u lokaci guda ma,
ni ina ruwana."

Maida kallonta tayi ga tv, amma sai taji wasu hawayen sun zubo mata, kawai saita
saduda, danta fahimci ciwon daga k'ark'ashin zuciyarta ne yake tasowa, dan haka ta
fad'a saman kujera ta 'kara fashewa da kuka, d'aci kawai ta keji a cikin zuciyarta
to amma meyasa.

Tunda Salman ya dawo daga dubo kayan da suka kawoshi garin, ya kwanta akan dan
madaidaicin gadonshi a k'aramin gidan daya kama haya.

Sosai ya shagalta da kallon pic d'in da tun jiya yake kallonshi, wanda jawahir ta
tura masa, ya burgeshi sosai jeans ne a jikinta bleue dark iya gwiwarta, sai
bak'ar riga mai kama da singlet d'in maza, tasha kitso k'anana sosai wanda ya zubo
har kafad'unta, pink colour d'in jan-baki ne a bakinta sosai pic d'in ya burgeshi.

Ya rasa me yake damunshi amma tun jiya yake jin babu dad'i, har yanzu bai saké
ganin Ummi en ligne ba amma har k'asan zuciyarshi yana ji yana so ya saké hira da
ita, watak'ila kodan bai tab'a hira da mace bane irin haka, amma yana so ya saké
hira da ita ko zata deb'e mashi kewar dake damunshi.

Wayarshi ya d'auka ya danna, pic d'in Ummi na gani a écran d'in tasha abaya bak'a
ta yane
kanta da k'aramin dan kwali, sai jan-baki ja da tasa, yana bud'e code d'in wayar
nan ma pic d'in tane ya fito inda take sanye da wandon nan, saida ya kalli pic d'in
da kyau sannan ya shiga WhatsApp saidai Ummi bata en ligne, ba yada zab'i daya wuce
kiran numberta.

Ummi na ganin kiran Salman taji ranta ya b'ace gaba d'aya haushinshi ya kamata,
d'aukar wayar tayi ta kashe gaba d'aya dan karya sake damunta.

Takaici ne ya rufe Salman ganin ya kirata amma ta kashe masa waya, k'arshe tama
kashe wayar gaba d'aya, tana tunanin ko ya fara damuwa da al'amuranta ne shiyasa
zata masa wannan wulakanci, k'wafa yayi yace" ba laifinki bane, laifina ne dana
damu sai nayi magana dake, dama wannan nake gudu shiyasa nake nesanta kaina dake,
amma ba komai, wallahi ba zan saké kiranki ba harna dawo." jefar da wayar yayi ya
saké mirginawa akan gadon.

Baifi minti talatin ba jawahir ta dawo gidan, ta samu Ummi kwance akan kujera tana
ta kuka, kusa da ita ta zauna ta cire hijab d'inta ta d'ago da ita k'yar ta fara
tambayarta" sister lafiya, miya faru ne haka kike kuka?"

Share hawayenta tayi tace" babu komai, ba kuka nake ba" hararanta tayi tace" karki
rainamin wayo mana, ko yaro ya ganki a haka ai yasan kuka kike, ki fad'amin abinda
ke damunki kawai"

Kai ta girgiza tace" nace maki babu komai, karki damu kanki" tashi tayi ta shige
d'akinta, binta tayi da kallo tana tunanin abinda ke damunta, dan a iya saninta
bata tab'a ganin Ummi na kuka ba tunda take.

Sallah kad'ai ke fiddo Ummi waje, amma ko abinci ta kasa ci duk bata jin dad'in
komai, madararta kad'ai take kurb'awa kad'an kad'an, jawahir duk ta shiga damuwa
da hakan, shiyasa ma ta kira khamis ta tambayeshi ko akwai abinda yama Ummi ne,
amma yace babu komai sannan yace ta rabu da ita.

Har khamis ya dawo gidan baiga Ummi ba, jawahir ta rok'eshi yaje yaji abinda ke
damunta har yasa ta kuka amma yak'i, saima fad'a mata da yayi auren da Salman ke
son k'arawa da zaran ya dawo tare da nuseiba.

Cikin rashin Fahimtar jawahir tace" aure kuma, da nuseiba, nuseiba dai k'anwarka,
amma yaushe yaya Salman yayi aure har yake tunanin saké wani auren, kuma yaushe
suka fara ma soyayyar bâ tare da kowa ya sani ba.?" kallonta yayi yace" e ita, ni
bama wannan ne a gaba na ba, kinsan mamarmu tana so ta had'a rumana da Salman, shi
kuma nuseiba ce tafi kwanta masa a rai, dukansu 'yan uwana ne amma fa rumana ciki
d'aya muka fito, duk inda na goyi baya sai na shiga matsala, shiyasa nake so ya
nemi k'uri'arshi da kanshi bana so na shiga cikin maganar."

Bata sake cewa komai ba, dan a ganinta hakan bai dace ba kuma yaya Salman zaiyi
hakane dan ya nuna ma duniya baya son Ummi.

*Bayan kwana uku*

Salman ne a d'akinshi keta birgima a k'asa, duk yayi kaca-kaca da d'akin da kaya ya
barbaza komai, hatta zanin gadon ya jayoshi izuwa k'asa ya rufe jikinshi dashi.

Abu guda kawai yake fad'i a bakinshi" Allah Allah Allah na wayyo Allah" kamar
mazari haka jikinshi ke rawa, duk jijiyoyinshi sun tashi idonshi jawur kamar
garwashin wuta, hak'oranshi had'e sai hard'ewa suke.

Cikin wannan yanayin ya d'auki wayarshi ya dannan, pic d'in Ummi ne ya bayyana,
kallo yake kamar zai had'iyeta, sai gani nayi ya buga wayar da bango yana wani irin
gunji kamar kuka kamar kuwa, saidai ya kasa furta ko kalma d'aya.

Da k'yar ya iya rairafawa ya kai ga jakarshi ya d'auki magani har kala biyu ya
b'alli guda bibbiyu ya had'a.

A hankali ya fara dawowa normal kamar yanda yake, nunfashinshi ya daidaita saidai
har yanzu akwai zafi a jikinshi, hawayene ke bin fuskanshi a hankali yake fad'in"
bazan yafe maki ba har abada, shekara d'aya kenan rabon da naji irin haka, amma
gashi yau na kusa mutuwa saboda kin shigo rayuwata, kin kusa tarwatsani."

" Dole na koma gida kafin na aikata ba daidai ba, dole naje gida na samu alhaji na
rok'eshi ya auramin nuseiba kafin na mutu, wallahi ke kuma sai kinyi kuka da idonki
muguwa marar imani, ba zan saké kallonki ba daga yau harna mutu."

_Salman kuma haka abin ya zama🤔_

*Ummi* na zaune d'aki, number naga tana danna kira tana kashewa, tun tuni haka
takeyi kamar wasan yara, d'aga kanta tayi sama tana fadin" miyake damuna, miyasa na
damu da tunaninsa, miyasa na kasa mantawa da maganar aurenshi, miyasa nake jin
haushinshi dan zai k'ara aure?"
Siraran hawayene suka biyo kuncinta, a hankali ta saké fad'in" ni dai nasan bana
son yaya Salman domin kuwa da muguntarshi ya raine ni, haka kuma ba ban tab'a jin
koda k'aunarsa ba a zuciyata ba, to miyasa?" kukan da tafe dashi ya jawo hankalin
jawahir dake zaune ita da khamis suna hira, tashi tayi ta shiga d'akin ta zauna
kusa da ita ta fara magana.

"Ummi sai yanzu ne nagane wani abu, ban tab'a tunanin zaki iya b'oyemin wani abu
daya shafeki ba, na d'auka ni da ke d'aya ne zaki fad'amin komai dake damunki,
kamar yanda nake fad'a maki abinda ke damuna kuma na nemi shawarar ki, ashe ke ba
haka bane a wajenki"

" Ki duba ki gani mana, yaya Salman ya amince da kizo gida na ki zauna, bayan kuma
ga k'anwarshi nan khairat, ga hafsat da nadia duka suma yan uwanshi ne amma baice
kije can ba,sai yace kizo nan, miyasa yace haka?"

Ci gaba tayi da fad'in" saboda yana ganin munfi kusa da juna shiyasa, yasan kuma
babu abinda zai dameki anan inhar muna tare, amma gashi yanzu kina cikin damuwa
tsawon kwana uku, ba kicin abinci sosai sai kuka kike amma kin 'ki fad'amin damuwar
ki saboda kina ganin ban kai nasani ba."

Kai ta girgiza mata tace" a'a jawahir ba wai baki kai bane, saidai bansan ta yanda
zaki fahimce niba, ni kaina bansan miye yake damuna ba, bansan akan mi nake damuwa,
saidai nasan za kimin dariya kuma ki fahimceni ba daidai ba idan na fad'a"
05/03/2019 à 17:28 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

_My 🅱K *BILKISU Z. YA'U* murnar kammala wannan littafi naki mai sunan *SO MAHA'DIN
RAYUWA* ha'ki'ka ya fad'akar ya nishad'antar, musammam ma a wajen mu 'yan soyayya,
ina maki fatan alkairi ina rok'on maki Ubangiji da ya yafe maki kurakuran dake
cikin wannan littafi, inda ki kayi dai-dai kuma Allah ya baki ladar fad'akarwa_👏👏👏

_Sai mun jiki a novel na gaba mutuniyata 'yar hannu dama na, ina mugun sonki BK ta_

``` daga samirar ki rabin ran bloodynki```😜

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

5⃣3⃣5⃣4⃣
5⃣3⃣-5⃣4⃣

Jawahir tace" haba Ummi, ta yaya zan fahimceki ba daidai ba, ki fad'amin insha
Allah zanyi k'ok'ari na fahimta yanda kike nufi" cikin kuka ta fara mata bayanin
abinda take tunani.

"Jawahir bansan miyasa nake jin haushin yaya Salman ba tunda yaya Khamis ya
fad'amin zai k'ara aure, na rasa dalilin tsanarsa nidai nasan ba kishinsa nake ba
domin kuwa bana sonshi kuma bana k'aunarshi, to amma miyasa nake damuwa bansani ba"
saida ta goge hawayen da suka zubo mata taci gaba da cewa.

" Jawahir wata'kila wannan itace 'kaddarar rayuwata, har abada bazan samu abinda
nake so ba, da farko an min AUREN HA'DI da wanda bana so ba tare dana shirya ba, a
bisa d'an k'ank'anin kuskure akamin dukan tsiya aka kawo ni gidan miji babu shiri,
to yana iya dole na hak'ura tunda banda yanda zanyi, Jawahir dama bana tsammanin
cin amarci ko farin ciki a tare da yaya Salman, saidai ina buk'atar na samu 'yanci
kamar kowace mace mai ji da kanta, amma ina na kasa samu azabtar dani kawai yake a
gidansa, ya tafi ya barni ko sati banyi a gidansa ba, shine yanzu zai k'ara aure
dan yaci mutunci na, shin Jawahir kinsan mai zai faru idan ya k'ara auren nan?"

Kai ta girgiza, ci gaba tayi da cewa" zai kawo min Nuseiba a matsayin amaryarsa,
yarinyar da bana jin ta cika shekara shabiyar a duniya, zata fini matsayi da 'yanci
a gidanshi saboda ita yana sonta, cikin k'ank'anin lokaci zata fahimci zaman da
muke da shi, daga nan saita fara jin ta fini sannan itace mowa a wajen mai gida
hakan zaisa ta fara min gani-gani."

"Bayan wani d'an lokaci kuma zata samu ciki, kinga daga nan komai zai k'are, domin
kuwa zata fara min gori akan hakan shi kuma zai dinga biye mata, d'awainiyarta
hidimarta rainon cikinta zai zama duk nice, idan kuma na'ki nasha duka haka harta
haihu daga nan zata fara min gorin haihuwa lokacin shi kuma ya d'auki soyayyar
duniyar ya d'ora akan d'anta da ita kanta, zai dinga fita da su duk inda zaije koda
barin garine, ni kuma zan zama 'yar gadin gida har lokacin da tawa zata zo
k'arshe." kallabinta ta kama ta rufe bakinta da shi taci gaba da rera kuka.

Da k'yar Jawahir ta rarrasheta tayi shiru, kafin ta fara magana" 'yer uwata kiyi
hak'uri, insha Allah duk abinda kika fad'a ba zai faru ba, ke da yaya Salman da
Nuseiba duka 'yan uwane ku, babu wanda zai cutar da wani, kuma ni bana tunanin
auren zaiyiwu, saboda yaya Khamis bayasan maganar gaba d'aya."

Kallonta Ummi tayi tace" dan yaya Khamis baya so, ba shi ke nufin zai fasa abinda
yayi niyya ba." kafad'arta ta dafa tace" to naji ma ace ya aureta, miye Nuseiba
keda shi da har zaki tashi hankalinki? ni kaina k'anwa take gareni, bare kuma ke da
kika ban shekara d'aya, kinga kenan k'anwarki ce kema." wani murmushin kan labb'a
tayi tace"Jawahir bakisan kishiya bane shiyasa, bata kad'an kuma bata k'arama"

Dariya jawahir tayi tace" yanzu ke harkin fara kallon nuseiba a kishiyarki? ai 'yer
uwarki ce" hararanta tayi tace" lokacin da zata shiga tsakanina da mijina ba baki
sani ba"kallon mamaki ta bita dashi tace" Ummi kece kike kiran yaya Salman mijinki,
to inaga fa kamar anjima da kashe boss" da gudu tabar d'akin saboda dukan da Ummi
takai mata.

Kwance ta koma tare da d'aukar pillow dake gefenta ta rumgume, a hankali take
tariyar rayuwarta a gidan Salman da tayi.

_Tambayoyi ne ta jero ma kanta" miyasa nake damuwa, miyasa nake jin haushin shi
dana Nuseiba, miyasa nake jin zafi a zuciyata, miyasa nake so naji muryarsa, kuma
miyasa na kasa kiranshi?"_

😜😜😜 ```in bata amsa, koko cikin ku akwai wanda zata bata?```

_Ma chérie ta Hakima fito mucashe, lokaci ya kusa yan bak'in cikin Salman saidai a
mutu😉😜_
05/03/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

_My seeya fatan alkairi da godiya tare da addu'ar ya fiyar Ubangiji a bisa
kurakuran da ki kayi, daidai kuma Allah ya baki ladar fad'akarwa da ki kayi, *BAMU
DACE DA JUNA BA,* darasi nishad'antarwa tare da ilimi da fad'akarwa ne a cikin
shi._
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)🤜_ 🤛

*Page*

5⃣5⃣5⃣6⃣
5⃣5⃣-5⃣6⃣

Tunda safe haka Ummi ta tashi sukuku jiki babu k'wari, Jawahir ce ta fad'ama Khamis
halin da take ciki, kiranta yayi tana zuwa da kanshi ya zuba mata abinci a plate ya
aje mata tare da fad'in" maza cinye ki bani plate d'in"

Kallonshi tayi tace" yaya Khamis ko zanci ba zan iya cinye wannan ba" yanda ya
had'e rai yace" Ummi ina wasa dake?" kai ta girgiza tace" kayi hak'uri yaya Khamis
wallahi yamin yawa"

"Ke, ina wasa dake ne, za kici ko saina takaki?" tsawar daya mata ce tasa tayi
saurin jan plate d'in a gabanta ta fara kai loma baki, Jawahir ma 'yan cikinta ne
suka kad'a, haka nima saida na saki alk'alamin.

Tana ci tana kuka tana rok'onshi ya isa haka, amma ya tsareta saida ta cinyeshi
duka ta bashi plate d'in, tunda uwar Ummi ta haifeta bata tab'a cin abinci mai
yawan haka, shiyasa Khamis na fita Ummi ta fara tsula amai, abin ya d'aga hankalin
Jawahir dan da farko tayi tunanin idan ta amaye abinci zata daina, amma sai taci
gaba da shek'ashi.

Cikin tashin hankali ta fara kiran Khamis ta fad'a mashi halin da ake ciki, cikin
tashin hankali yace da ita "gani nan zuwa saimu kaita asibiti"

suna jiranshi Salman ya kiran Jawahir dan tunda ya tashi bai fita ba, gab'a d'aya
hankalinshi ya koma gida, hakan yasa ya kira iyaye maza da mata da kakannin amma
saiya ji baibar kewa da damuwa na gidan ba, dole ya kira Jawahir ya tambayeta Ummi.

Tana d'auka cikin damuwa tace "assalama alaikum, ina kwana yaya Salman?" gabanshi
yaji ya fad'i, da k'yar ya daure yace "lafiya lau, kun tashi lafiya?"

Kamar zata fashe da kuka murya na rawa tace "yaya Salman da sauk'i dai, kaga Ummi
nan tana ta amai wallahi, nifa na fara jin tsoro" cikin d'aga sauti yace "amai
kuma, miyasa meta to?"

Cikin kuka tace "yaya Salman daga taci abinci fa shine take amai "innalillahi
wa'inna illaihir raju'un, kinga bata wayar" ya fad'a tare da nuna tsantsar
damuwarshi a fili.

Mik'a mata wayar tayi, wata harara ta wurga mata tare da kau da kai, maida wayar
tayi a kunne cikin sanyin murya tace "yaya tak'i karbar wayar" abun mamaki na
d'auka Salman zaiji haushine, amma sai naji yace "Jawahir karki min k'arya, ki
fad'amin abinda ke damunta?"

"Yaya Salman nima bansan miyake damunta ba, amma dai jiya ta fad'amin wani abu
wanda nake tunanin kaine silar shigarta wannan halin" cikin rashin fahimta yace
"bangane ni nasa taba?"

"E yaya Salman amma kayi hak'uri nima zato ne nake, amma banda tabbaci" cikin jin
haushi Salman yace "naji ni fad'amin me ta fad'a maki?"

Duk da tana d'ard'ar dashi haka ta daure ta fad'a masa duk abinda Ummi ta fad'a
mata jiya, dariya yayi yace "Jawahir lallai yarinya ce ke, waya fad'a maki ana
kishin wanda ba'a so?"

Saida ta sauke ajiyar zuciya tace "yaya Salman ai macen kenan, tsamar dake
tsakaninku ba zata hana zuciyoyinku fallasa sirrin dake cikin taba, ko bata sonka
zata iya kishinka saboda akwai aure tsakaninku, kamar yanda da zaka ganta da wani
namiji za kaji zafi a zuciyarka, amma idan aka fahimci hakan zaka iya wayancewa ta
hanyar cewa kana san kare martabar aurenka ne dake kanta, kaga kenan dan tayi
kishinka ba abun mamaki bane."

Shiru yayi yana tunanin abinda ta fad'a, murmushi yayi kamar yana gabanta yace
"Jawahir ban tab'a jin alamun haka a raina ba, ko zanyi soyayya zanyine da wata
daban amma ba Ummi ba, yarinyar da idan naganta sai gabana ya fad'i saboda tunanin
abinda zata min musammam idan ina cikin mutane"

Dariya tayi cike da jin k'arfin gwiwa tace "Yaya Salman ai fad'uwar gaba alamune na
so" dariya yayi yace " ke Jawahir banasan sharri, ke har kinsan alamomin so?"

Dariya tace "na san wasu yaya Salman wanda nake ji a duk lokacin da naga yaya
Khamis" cewa yayi "to fad'amin uku daga ciki, kuma idan ki kayi ba daidai ba to
idan nadawo dole kisha rank'wasa a kai"

Hannu ta d'ora a kanta dan bâ zata manta rank'wasan daya tab'a mata ba har saida
tayi ciwon kai, cewa tayi " yaya Salman duk lokacin da kaji gabanka ya yanke ya
fad'i a lokacin da gaka wata 'ya mace, to alamune na zuk'atanku suna shirin k'ulla
wata alak'a koda ku baku shirya hakan ba.

"Sannan lokacin da kaji komai na wata 'ya mace yana burgeka, komai yana nufin
dariyarta, murmushinta, fara'arta, kai dama kukanta to shima akwai yiwuwar ka kamu
da sonta ko kana shirin kamuwa."

"Yaya Salman akwai jin tausayinta duk lokacin da wani abu ya sameta na rashin jin
dad'i, haka kuma akwai son ganinta a cikin farin ciki tare da mata fatan farin ciki
mai d'orewa, son jin sautin muryarta a koda yaushe, son ganinta a kusa da kai a
kullum."

"Yaya Salman duk lokacin da kayi nesa da ita tunaninta zai iya hanaka sukuni, zaka
kasa komai burinka bai wuce ka dawo ka ganta ba, zaka ji kewarta na yawan damunka
kana buk'atar kasancewa da ita, sannan yaya Salman duk wacce kake so za kaga
murmushin da kake mata ma na dabanne, haka kallon da kukewa junanku ma zuk'atanku
ne kad'ai zasu iya fassarashi, don ko mai kallonku ba zai iya fassara maku shi ba."

"Ke" ya daka mata tsawa yana fad'in" nawa na tambayeki ni uku fa nace, waike
sarauniyar soyayya ko?" kai ta girgiza alamar a'a, tace " yaya nadai fad'a maka
abinda na sani ne kawai, amma ina so ka sani kai da Ummi koda baku son junanku, to
ku sani akwai jinin 'yan uwantaka da yake yawo a sassan jikinku wanda baku isa ku
cireshi ba, ko babu so a tsakaninku akwai k'auna, yaya Salman abune mai sauk'i
samun masoyi, amma samun wanda yake k'aunarka da gaskiya shine mai wahala,
mafiyawancin soyayya tana farawane daga k'iyayya sannan ta koma so wannan shine."

Kashe wayar yayi ba tare da sunyi sallama ba, maida kallonta tayi ga Ummi dake
kwance tana bacci, Khamis na zuwa Ummi tace taji sauk'i, dan babu abinda ta tsana
kamar shan magani da allura, dole suka k'yaleta da sukaga jikin yayi sauk'i ta
daina aman.

_Wato dai 'yarta bakin Salman baki son shan magani sai abun dad'i_😂
05/03/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑
_Samira Harouna_

*MEELAT*_(my meelat)_
*HEENAT*_(my heenat)_
*CHOUKRA*_(habibaty)_
*FATIMA*_(mom dady)_
*HALIMA*_(kakale ta)_
*SAFIYA*_(ma chérie)_
*AZEEMA*_(k'awata)_
*RAMATOU*_(rammess)_
*MAMAN LABYB*_(momy na)_
*MOMYN SULTAN*_(aunty)_
*MOMYN DEEJA*_(ma belle)_
*HAWA JAMIL*_(aunty na)_
*HAKEEMA*_(ma chérie)_

```WANNAN PAGE SADAUKARWA CE GAREKU, DAN HAKA KUYI YANDA KUKE SO DA ITA TAKU CE
KYAUTACE DAGA GARENI```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

5⃣7⃣5⃣8⃣
5⃣7⃣-5⃣8⃣

Yanda Salman yaga rana haka yaga dare ba tare daya rintsa ba, kalaman Jawahir sun
gigita tunaninshi sosai ya kasa fayyace gaskiya da k'arya, indai har fad'uwar gaba
yana d'aya daga cikin alamun so, to kenan tun Ummi na matashiya yake sonta, domin
ko duk lokacin daya ganta sai gabanshi ya fad'i sannan baya jurar kallon idanunta,
suna sashi yaji wani yanayi a tare dashi, hakan ma yasa yake kiranta da mai idon
aljanu kona mage wani lokacin.

Ya yanke shawarar komawa gida jibi, dan haka ya ciro ticket haka ya k'agu safiya ta
waye ko ya kama hanyar gida,yayi niyyar bankad'o gaskiyar abinda Jawahir ta fad'a
masa zaiyi k'ok'arin gano gaskiya ta hanyar lalubo kishin Ummi sannan yasan dalilin
kishin nata.

08:00 na safe suka kamo hanyar zuwa niamey, banda kallon pic d'in Ummi babu abinda
yake, ko abinci baisa a bakinshi har suka sauka, duk da gobe zai wuce amma yayi
niyyar bazai fad'ama kowa ba yana so ya masu bazata, sannan yaga yanda Ummi zatayi.

Bayan ya huta sosai abu d'aya yake da buk'ata yayi wato bacci, amma ina ya kasa
samuwa duk da cewar baiyi bacci daren jiya ba, wayarshi ya d'auka yana so ya kira
Ummi amma yana tuna ya fad'i bazai k'ara kiranta ba, haka ya daure ya kirata amma
abun haushin wayar kashe, haka ya k'urama pic d'inta ido yana kallo har bacci
b'arawo ya d'aukeshi.

*Washe gari* da safe Ummi ce ta fito farfajiyar gidan dan tasha iska, sanye take da
doguwar riga mai colour ja da bak'i da fari, sama a matse sai k'asa daya bud'e ba
tada dan kwalli dan haka ta d'ora na abaya ba'ka, zaune tayi akan 'yar gajerar
katangar da aka kewaye rabin harabar gidan da ita, jingina bayanta tayi ta rumgume
hannayenta a k'irji tayi shiru tana kallon 'yar k'aramar bishiyar mangaro, a
hankali ta tuna ranar da suka fito tare da Salman ta rakoshi zai fita, da kuma
ranar da ta fad'i saboda jiri ya d'auketa sannan ya kawo mata madara tasha.

Rayuwarsu take tunani tana murmushi ajiyar zuciya ta sauke tana mai k'ara fad'ad'a
murmushinta tace "ina ma kadawo yau, da zan zauna da kai ko dukana ne kaci gaba
dayi da wannan tattausan hannun naka"

Jawahir dake zaune gefe ita da Khamis ta kalleshi tace "mijina dubi mutuniyar
murmushi take ita kad'ai, ina ga fa tunanin yaya Mane take"

Dariya suka saka gaba d'ayansu hakan ya janyo hankalinta, mamakine ya bayyana a
fuskarta dan batayi tunanin suna nanba suma, saidai kallonsu kawai take saboda
ganin k'afar Khamis a cinyar Jawahir tana masa wankin k'afa, take ta tuna da ranar
da tama Salman yankan akaifu, wani murmushin ta koma saki tare da jin wani sanyi na
lullub'eta, gaba d'aya taji kawai tana son ganin Salman ko fad'ane ma su dinga yi
zata ji dad'i.

Jawahir ce data lura ba tada niyyar magana tace "Hajia Abu tunanin me ake ne haka?"
kallonta Ummi tayi tace "ba komai"

Tab'e baki tayi tace "to naji ba komai, amma ya kamata ki shirya gobe muje muyi
kitso" cikin farin ciki tace "yawwa dama nima ina so nayi kitso"

Cewa tayi "amma ai da kin bari har yaya Salman zai dawo sai kiyi" hararanta kawai
tayi ba tace komai ba, Khamis kam cewa yayi "to nidai kamar kullum ne, indai har
kina so kije to ki tabbatar kin kira mijinki kin fad'a masa."

Ba tada zab'in daya wuce ta kira ta fad'a masa dan haka tace "to yaya Khamis zan
kira, na lura kaidai kana jin tsoron mutuminan sosai"

Hararan ta yayi yace "ke kuma baki tsoronsa ko jaruma?" dariya kawai tayi ba tace
komai ba.

Ummi bata kira Salman ba saida safe sannan ta d'auki wayar ta kuna, ta danna
numbershi tana fara k'ara taji gabanta ya fara dukan uku-uku, da k'yar ta iya
daurewa tana sauraran ya d'aga.

Tana jin ya d'aga taji cikinta ya d'uri ruwa take taji tana buk'atar kewayawa, amma
haka ta dake ba tare da tace komai ba, Salman dake saman hanyar dawowa yana ganin
kiranta yaji farin ciki ya mamayeshi, ba tare daya kula ba ya samu kansa yana mai
kasaitancen murmushi amma daya tuna wacece Ummi da kuma kashe wayar da tayi, kawai
sai ya b'ata rai sannan ya d'aga.

"Oui je t'ecoute" ( na'am ina jinki) ya fad'a a tak'aice, cikin sanyanyen murya
tace "haba ba ko sallama?"

Cikin dakakkiyar murya yace "ki fad'i abinda yasa kika kirani da gaggawa inada
abinyi?" tab'e baki tayi tace "dama na kira ne dan na fad'a maka za muje wajen
kitso nida Jawahir yanzu, kuma yaya khamis yace dole saina fad'ama zanje shiyasa
na kiraka."

Wani buhun haushi ne ya kama shi, wato badan Allah ta kirani bama kuma saida akace
ta kira sannan ta kira, ba damuwa zanyi magananinki ya fad'a a ransa.

Bud'ar bakinshi yace "baza kiba to indai nine zan bada izinin, ni dama nasan kinfi
k'arfin ki kira ni ki gasheni bare ki tambayeni ya nake saboda bakisan mi ake nufi
da miji ba, amma yanzu buk'atarki tasa kin kirani bayan kashe waya da kika yi."
Haushi taji itama cike da tsiwa tace "kaga nifa na kirane badan kamin masifa ba,
sannan da kake cewa na kashe waya, e na kashe saboda banga anfanin kirana da zaka
yiba tunda kana da wacce zaka dinga hira da ita, kuma ni ba izininka nake jira ba
ina so naje kitso kuma zanje."

Cikin tattausan murya yace "to kenan kin fad'amin ne dan nasan zaki tafi, ko ko kin
fad'amin ne dan nasan kin isa da kanki, ko kuma umarni ne kike bani akan na baki
izinin fitar?"

K'irjinta k'ara tsananta bugawa yake amma haka ta daure tace "ka d'auki d'aya da
kaga yafi da cewa dani saika sani a mahalin" cikin jin haushi yace "Ummi ince dai
nine mijinki ko?"

Kamar tana gabanshi saida ta murgud'a baki tace "to saime mijin da baisan hakk'in
matarshi ba, zaka k'ara aure amma saidai naji a gari amma ba komai akwai Allah, dan
haka ni yanzu ko ka bani izini ko ka k'i bani izini, fitata zanyi in yaso in
kamatsu ka fara bada umarni to sai ka bari harka kawo k'waillar matar taka saika
fara mulkarta, amma ba Ummi ba."

Salman daya saki baki yana sauraranta izuwa yanzu ya fara fahimtar inda zancen,
wato tana jin haushi dan zan k'ara aure, murmushi yayi yace "babu ruwanki da
amayarta yarinya mai nutsuwa da hankali, sannan na fad'a maki karki je ko ina har
saina dawo"

Abinda ya fad'a shiya k'ara harzuk'ata, cikin fitina tare da k'ok'arin b'oye
hawayenta tace "saina je d'in, idan ka dawo ka kasheni." cike da izza yace "aiko
idan kika fita bada izinina bâ, to zaki rasa k'afa ko ido"

Cikin kuka mai tsanani tace "e na rasa k'afar tunda kaine ubana da zaka min baki Ya
kama ni." tana fad'a ta kashe wayar, toilet ta shiga ta wanke fuskar'ta sannan ta
fito ta samu Jawahir da Khamis suna jiranta fitowarta.

Khamis ne yace "kin kirashi?" kai ta fara girgizawa sannan tace "na kira kuma yace
naje, amma wai karna dad'e" hakan data fad'a yasa Khamis ya tabbatar data kirashi
d'in.

Cikin farin ciki Khamis ya aje su gidan mai kitson, amma yace idan an ida su hau
adaidaita sahu su koma gida tunda suce sai sun biya 'yar kasuwa sunyi siyayya.

_Ummi kam akwai marar jin magana, ko baki ji maganarsa a matsayinshi na mijinki ba,
ai kin ji ko a matsayinshi na yayanki._
05/03/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```OH ALLAH KABAWA 🅱K LAFIYA ALFARMAR ANNABI MUHAMMAD S.W.A, ALLAH YASA KAFFARA
NE```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

5⃣9⃣6⃣0⃣
5⃣9⃣-6⃣0⃣

Saida su kayi sallah azahar a gidan mai kitson sannan suka fito, a k'afa suka
k'araso 'yar kasuwa saboda duk bisa hanyane babu nisa sosai, sayayya su kayi sosai
musammam Ummi, duk kud'in da Salman ya bata kaf ta kashesu ga k'ananan kaya da
kayan bacci da kuma kayan kwalliya.

Ana kiran sallah la'asar suka tsaya bakin titi suka shiga adaidaita.

_Tsotsayi kenan wanda ba'a sa mashi rana, idan ya wuni tofa baya kwana_

Sun d'auki babbar hanyar da zata sadasu da gidan saiko wani mai mota daya fito daga
cikin kwana da iya k'arfinsa cikin ganganci, saiko yayi gaba da adaidaitar dasu
Ummi ke ciki.

B'angaren da Ummi take nan adaidaitar ta fad'a, mai adaidaitar na fad'owa k'asa
kuma wani mai babur ya taka kanshi take ko shurawa baiyi ba yace ga garinku nan,
tuni aka kewaye su ana k'ok'arin basu agaji, wasu samari ne suka kama Jawahir ta
taka adaidaitar ta fito ta sama, sannan aka d'aga adaidaitar dan a janye Ummi.

Ana d'aukewa Ummi ta tashi zaune idonta ne suka sauka kan mai adaidaita, tana
ganinshi ta dafe kanta tare da zankad'a uwar k'ara take kuma ta saké zubewa k'asa
somammiya, Jawahir da jiki keta mata rawa ta kasa tsayawa daidai wani dattijo ne ya
janyeta daga wajen, kafin aka d'aukesu aka nufi babbar asibiti da su.

Jawahir gurjewa kawai tayi a goshi, dan haka ana gama dubata aka amshi wayarta aka
kira Khamis, Khamis bawon Allah tashin hankali ne ya shiga wanda bai tab'a shiga
irinsa ba, haka ya garzayo yazo asibitin.

Saida aka bashi tabbacin jikinsu da sauki sannan ya tafi gida ya fad'ama manyansu
halin da ake ciki.

Babu wanda yayi yink'urin zuwa ba tare daya fad'ama Alhaji ba, amma sam ya rufe ido
yace a barta can ita da halinta, ran kowa ya sosu musammam ma iyayenta sunfi kowa
shiga damuwa sai kuma Hajia Zeinabou wacce babu wanda ya kaita d'aga hankalinta.

Ganin ba zai barsu ba yasa Hajia Zeinabou ta fara rera mashi kuka tana
lallab'arshi, ba zai juri kukanta ba shiyasa ya amince duk mai so yaje ya ganta
amma hakan ba yana nufin ya yafe mata bane.

Dan-danan sai asibiti ta cika da yan uwa, an masu barka ta wani b'angaren kuma an
jajanta masu, Khamis duk ya rud'e ya rasa ta yanda zaiyi ya kira Salman ya fad'a
masa, dan a ganinshi babu dad'i ace an baka amana amma amanar ta salwanta a
hannunka.

Missalin 17:20 Salman ya doko ma Khamis kira wanda yasa gabanshi tsinkewa, da k'yar
ya d'aga basu ko gaisaba Salman yace "kazo ka d'auke ni dan Allah na gaji da
kiranka" kashe wayar yayi ba tare daya jira me zaice ba.

Haka Khamis yaje gidan bus d'in ya d'aukoshi, kallo d'aya Salman yama Khamis yasan
akwai matsala amma baya cikin yanayin farin ciki shiyasa bai tanka saba, ganin sun
d'auki hanya daban yasa yace "ina kuma zaka kaini malam? ka kaini gida dan Allah
yunwa nake ji" baice masa komai ba sai cigaba da tuk'insa yake har suka kai babbar
asibitin.

Tunda suka shiga gabanshi keta dukan uku-uku, yana da 'yan uwa dayawa dan haka ya
rasa wa zaiyi tunani ke asibiti, zuciyarshi na raya mashi wani ko wata mai
mahimmanci sosai ne a gareshi ke kwance anan d'in.
Ummi na zaune an gama mata dressing d'in ciwon, sai yanzu ne take jin zafin ciwon
sai kukan shagwab'a take masu Hajia dasu Mama (mahaifiyar Salman) su kuma sai
rarrashi suke cike da taussayinta, kwatsam Salman ya fad'o d'akin yana zare ido
yana kallon ikon Allah.

Fad'uwar gabanshi ya k'ara tsananta duk jikinshi yayi sanyi ga wani jiri daya keji
yana 'dibarshi, kukan da Ummi keyi yasa yaji takaici ya rufeshi, wato rainawa
mutane hankali zatayi ma bayan bata ji maganarsa ba.

Sannu da zuwa su mama suka masa cike da mamakin yanda yazo bai sanar da kowa ba,
tsaye yayi kusan k'afafunta data ji ciwo k'afar dama an nad'eta da bandeji tun daga
wajen ijiyar sau har zuwa cikin tafin k'afar saboda k'arfen daya karceta har farar
coka ta fito, sai k'afar hagu kuma gurjewa ne a gwiwa amma saboda buguwa da k'afar
tayi kuma adaidaitar ta tausheta hakan yasa tayi kumburi sutum da ita, sai kuma
hannun dama data fad'a samanshi ba daidai ba ta goce.

_Hum dama 'yan magana sunce, in haka ji bari ba kaji hoho_

Da k'yar ya tambayi abinda ya faru, ana fad'a masa ya kalli Jawahir dake gefe da
'yar gurjewarta a hannu yace

"Kingani ko Jawahir da yake ke kina jin maganar mijinki, kinga baki ji ciwo sosai
ba Allah ya k'ara kiyayewa"

Take La mama ta maida kallonta ga Ummi, Ummi kam da hannu ta mashi alamar yayi
shiru, dan inhar La mama taji to abinda zata mata sai yafi ciwon dake jikinta yi
mata zafi.

Zagayowa yayi ya zauna kusa da ita, saida ta sauké ajiyar zuciya saboda shak'ar
kamshin turarenshi har cikin zuciyarta taji dad'in zaman da yayi kusa da ita, ji
tayi kamar ta fad'a jikinshi ya rumgumeta, kallonta yake sosai dan har yanzu yana
mamakin abinda ta aikata, baiyi tsammanin zata tafi ba daya hanata ashe da gaske
take zata tafi.

Cikin shagwab'a tace "yaushe ka dawo?" kafin ya bata amsa La mama tace "abinda ya
kamata ki tambayeshi kenan?" k'ara kwab'e fuska tayi tace" kazo lafiya, ya hanya?"

Tsawa La mama ta mata tace "Ummi mijinki kike kira da kai, babu girmamawa a ciki ba
zaki iya cewa kunzo ba, saidai kazo?" kamar zatayi kuka amma ba tace komai ba,
Hajia Zeinabou ba zata juri ganin b'acin ranta ba dan haka tace,

"Kai kuma ka amsa mana, yarinyar dake cikin halinnan ai tayi 'ko'kari ma data iya
gaishe shi." kallon Hajia yayi yace "ba zan amsa ba Hajia saboda bakisan méta
aikata ba"

Yana fad'a ya mik'e ya fita harabar asibitin, La mama tashi tayi tabi bayanshi,
tsaye tayi tana Kallonshi kafin tace,

"D'ana ka fad'amin meta maka dan Allah?" kallon La mama yayi cike da kunya sannan
yace "La mama babu komai wasa nake mata"

Murmushi La mama tayi tace "Salman yaushe ka fara b'oyema mahaifiyarka farin
cikinka da damuwarka dama sirrinka?" baya b'oyema La mama komai, idan har bai fad'a
mata abinda zata nutsu ba to ya san zata iya huce haushinta akan Ummi dan zata
titsiyeta saita fad'a mata.

"A'a La mama bawai na b'oye maku bane, kawai jiya munyi wayane da ita kuma munyi
akan ba zata saké kashe waya ba, amma nayita kira tun safe bata d'auka ba sai yanzu
nazo na tarar da abinda ya faru."
Ko kad'an La mama bata yarda ba, amma bata so ta takurashi dan haka tace "shikenan
ba damuwa" ciki La mama ta dawo amma badan mutanen dake d'akin ba da sai ta
tambayeta abinda ya faru.

Salman ya jima yana jin babu dad'i yana tunani akan abinda Ummi tayi "me yasa tayi
haka, me yasa da nace ta zauna tak'i zaunawa, shin abinda ya fad'ane da wasa dan
ya hanata fitar shine ya faru da gaske, shin dama haka bakin miji keda ta siri akan
matarsa, inko hakane dole nasan me zan dinga fad'a mata tunda dai ita ba zata ji
maganarshi."

"Yanzu gashi abinda ya faru da ita, yanzu da ita ce fa abinda ya faru da mai
adaidaita sahun ya faru da ita fa saime ya faru da ni?" ya tambayi kanshi.

Zunbur ya mik'e tsaye daga kan tabarmar da yayi sallah la'asar, cikin sauri ya nufi
d'akin da suke yana fad'in "ina babu abinda zai sameta insha Allah, tana nan tare
da ni ba zata mutu ba muna nan tare."

Tsaye yayi k'ofar d'akin saboda mutanen dake ciki, idonshi akan Ummi wace idonta
sukayi jawur alamar har yanzu tana kuka, juyawa yayi ya fita daga d'akin gida yasa
Khamis ya kaishi.

Wanka yayi ya shirya sannan suka fito tare restaurant (maqui) ya ajeshi dan yaci
abinci amma saiya kasa, tunaninshi ya koma kan Ummi da ciwonta dan gani yake kamar
shine silar hatsarinta, haka suka dawo asibiti suna zuwa lokacin magrib yayi dan
haka suka tsaya masallaci sukayi sallah sannan suka wuce d'akin da Ummi take.

Sun samesu sun shirya suna jiransu zasu tafi gida, Hajia ce ta kalli Salman tace
"kaga tunda ba zata iya takawa ba, ka d'auketa ko"

Ido ya fiddo ya kalli kowa dake d'akin yace "haba Hajia ai k'wara na d'aukeki na
goya akan wannan b'ulleliyar, dan zata iya karyani gashi dama ina jin yunwa, kinga
saimu fad'i daga ni har ita."

"Kaga banasan rainin wayo, in zaka d'auketa ka wuce muje ka d'auketa, in kuma ba
zaka d'auka ba nasa Khamis ya d'aukarmin 'yar leleta." ta fad'a tana kashe ma
Khamis ido.
05/03/2019 à 17:30 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```DEDECATED TO```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

_Kunada karamci a gareni matsayinku da girmanku ya mafi haka, domin daga cikinku ne
na samu makusanta masu nunamin k'auna a kowane lokaci *Yan ZAMAN AMANA* ina
k'aunaku dukanku._

'KUNGIYATA ABAR ALFAHARI MAI NUNA DAMUWA GA WANDA YAKE CIKINTA

*Page*

6⃣1⃣6⃣2⃣
6⃣1⃣-6⃣2⃣
Matsowa Khamis yayi kamar zai d'auki Ummi, saiko Salman ya hankad'eshi yana fad'in"
dallah malam gafara daga nan" bushewa sukayi da dariya, shi kuma sunkuyawa yayi ya
zura hannunshi ta bayanta ya tallabota, d'aya hannun kuma ta k'asanta nanma ya
ciccib'ota gaba d'aya.

Kamar zuciyarta zata fasa k'irjinta ta fito haka yake jiyo bugun zuciyarta, yana
sama da ita Ummi ta rufe ido ta kau da kanta gefe, Salman kam wucewa yayi su Hajia
na gaba suna baya, tafiya kawai yake fuskarnan a had'e kamar hadarin gabas gashi
babu wani alamu daya nuna yana jin nauyin abinda ya d'auka.

Dan kuwa a tsaye yake k'yam, dan shi anashi b'angaren kawai bai d'auketa mai nauyi
ba duk da k'ibarta, dan k'arafan da yake d'auka ma sunfita nauyi, suna haka ne
wayarshi ta fara ruri, ba tare daya kalleta ba yace,

"Malama fiddomin wayata".

Sai lokacin ta juyo da kanta, a hankali tasa hannu a cikin aljihun rigarshi na
gaba ta ciro wayar kamar ta d'auko maciji, tana ganin sunan daya fito a écran d'in
wai *REINE*(sarauniya).

Hawaye taji sun zubo mata haka kawai saiko ta jefar da wayar k'asa, Salman na
ganin haka ya tsaya cak tare da kallonta yace "miye haka Ummi kina lafiya kuwa,
kodai had'arin harda kanki ya tab'a?"

Kawai saita k'ara fashewa da kuka tana fad'in "azzalumi kawai dama kasan wacce zata
kiraka wato sarauniyarka shiyasa kace na d'auka dan dai naji haushi ko, to wallahi
sai Allah ya sakamin mugu kawai."

Sai lokaci yasan ko wacece ta kirashi, tabbas Nuseiba ce dan ita ya sama sunan
sarauniya, (kenan abinda Jawahir ta fad'a gaskiya ne, Ummi tana kishin shi, to amma
miyasa?),.

K'ara matseta yayi a jikinshi ya sunkuya ya d'auki wayar data fashe yasa aljihu,
sannan suka wuce.

Jiniyar kukan da take ne yasa yace "kenan wannan kukan na kishi ne ?"

Share hawayenta tayi tana kallonshi tace "Allah ya sawak'e nayi kishinka"

Ba tare daya kalleta ba yace "kenan najin dad'ine kike saboda na d'aukeki?"

Mitsiniya ta fara tana cewa "kaga ni saukeni dan Allah zanje da k'afata, abinda
hannun ma sai tauri kamar katako"

Tana fad'in haka hannunshi dake kusa da k'irjinta ya ida zurawa ya matse mata mama,
yar k'aramar k'ara ta saki saboda yanda taji zafi, kallonta yayi ya d'aga mata gira
yace "mi kika ji 'yan mata?"

Cike da shagwab'a tace "Allah saiya sakamin kuma ban yafe ba mugu"

Rufe idonshi yayi lokaci d'aya kuma ya bud'e, harga Allah baya so yaji tana fad'a
mashi irin haka, amma ya zaiyi bakinta ya riga ya saba ba zata iya dainawa ba.

Suna kaiwa Jawahir ta bud'é masu k'ofa ya ajeta sannan kowa ya shiga suka wuce,
gaba d'aya gidansu suka wuce, Hajia saida ta d'ora ruwan zafi ta barma Salman
sallahun ya gasa mata k'afa ya kuma tabbatar tasha magani sannan ta kwanta, haka ma
mahaifiyarshi saida ta saké jaddada masa kula da ita sannan suka bar gidan Khamis
ya mayar dasu gida.
Ruwan nayin zafi ya d'auko tare da d'an k'aramin towel, kusa da ita ya zauna inda
ta mik'e k'afafunta, towel d'in ya tsoma cikin ruwa ya fiddo ya matse sannan ya aza
mata a k'afar, k'ara ta saki tare da janye k'afar da sauri, saidai ina ta manta
ciwon da take mata, runtse ido tayi saboda azaba ta fara matso k'walla.

Salman kam in banda d'aci babu abinda zuciyar shi keyi masa, ji yake kamar ciwon ya
dawo jikinshi zaifi mashi sauk'i, rik'e k'afar yayi yace "sannu ko, bari na maki
hankali"

Mamaki ne ya lullub'e Ummi dan haka ta saki baki tana kallonshi, a hankali ya dinga
gasa mata k'afar Ummi kam tun tana jin zafi harta fara jin dad'i, kallonshi kawai
take zuciyar ta na k'ara narkewa akan son wani abu da bata so taji tana jinshi akan
Salman d'in.

Idonshi na kan k'afarta yace "mina fad'a maki a lokacin da mukayi waya?"

Gabanta taji ya fad'i, amma ganin ko kallonta baya yi yasa cikin tattausan murya
tace "kace karna fita"

"Sai kuma nace mi a gaba?"

Murya na rawa tace "kace idan na fita zan rasa k'afa ko ido" har yanzu yak'i
d'agowa ya kalleta yaci gaba da cewa,

"Sai ke kuma ki kayi mi?"

"Saina fita"

"Bayan kin fita kuma miya faru?"

"Nayi accident a hanya"

"Sai mi ya faru bayan had'arin ya faru?"

"Ciwo naji"

"A me kenan?"

Kamar zatayi kuka tace "a k'afafuna da kuma hannu"

"Me kika fahimta daga abinda ya faru?"

Cikin muryar kuka tace "na dinga jin maganarka, idan kace nayi to nayi, idan kace
na bari na bari."

Jinjina kai yayi yace "da kuma mi?"

"Tasirin bakin miji akan matarsa"

"To yanzu idan na hanaki zaki hanu?"

Kai ta girgiza ta k'ara fashewa da kuka tana fad'in" kayi hak'uri yaya Salman
wallahi ba zan saké ba daga yau, duk abinda kace nayi zanyi"

Sai lokacin ya d'ago kai ya kalleta yace "kin tabbata?"

Saida ta sharb'i majina tace "wallahi zanyi na maka alk'awari, amma dan Allah karka
fad'ama La mama"

Kafeta yayi da ido yace "kenan yanzu zaki dinga jin maganata idan na maki?"

"Wallahi zan ji yaya Salman"

Ajiyar zuciya ya sauké yace "shi kenan na yafe maki tunda kince ba zaki saké ba,
nima kuma ki yafemin dan bai kamata na fad'a maki haka ba, kamata yayi na tsoratar
dake ta wata hanyar daban ba wannan ba."

Kallon shi kawai take baki bud'e, karo na farko kenan a tarihin rayuwarsu da taji
makamancin wad'annan kalaman daga bakin shi.

Yana gamawa ya bata magani tasha, amma ta dinga tsala kukan shagwab'a wai ita ba
zata shaba, saboda tausayi yasa Salman rarrashin Ummi , amma fafur tak'i tasha sai
baud'ewa take tana botsarewa, dole dai tasa ya koma Salman d'insa na ainihi, tsawa
d'aya ya mata ta karb'a tasha jiki na rawa, dan Salman ba daga nan ba wajen tsare
gida.

Tashi yayi ya maida robar cuisine ya aje ya dawo ya d'auketa ya kaita d'aki ya
kwantar da ita yaja zanin rufa ya rufeta sannan yace "kiyi bacci" yana fad'a ya bar
d'akin.

Ummi na bacci cikin farin ciki saiko tayi mafarkin mai adaidaitar nan da taga
ganshi a fashe, girgigit ta tashi tare da fad'in "innalillahi wa'inna ilaihir
raju'un, innalillahi wa'ina ilaihir raju'un, Hasbunallahu wani'imal wakil."

Dafe kanta tayi ta fara rera kuka, saboda abunne kawai ke dawo mata a kai yana mata
yawo a k'wak'walwa, a hankali take rera kukan hannayenta biyu a kanta.

Salman dake tsaye yana nafilfili yaji tashinta dan haka ya shigo cikin azama dan
yaga mike faruwa.

Zaune yayi kusanta yana fad'in "Ummi lafiya miya faru?"

Tana d'aga kai ta kalleshi kawai saita fad'a jikinshi ta k'ara fashewa da kuka,
rigar shi kawai take ta cukuikuyewa tana k'ara tusa kanta cikin k'irjinshi tana
fad'in "yaya Salman shi nake gani wallahi tsoro nake ji, zamu k'ara fad'uwa, dan
Allah karka tafi duk jini ne a jikinshi ga kanshi ma ya fashe"

Shiru yayi yana tunani (dole ne abun ya tsaya mata a rai, dan yanda aka fad'a masa
gawar mutumin dole ko namiji yaji abu bare kuma mace mai rauni), hannayenshi ya
dora a bayanta yana cewa "shikenan to ya isa haka kinji, insha Allah bazai saké
dawowa ba, calme toi"

Haka yaci gaba da shafa bayanta har bacci ya d'auketa, a hankali ya maida kanta
saman pillow yayi mata addu'a ya shafa mata, idonshi akan fuskarta, mik'ewa yayi
ya shinfid'a sallayarta yaci gaba da sallarshi.

Har aka kira sallah asuba Ummi na bacci, Salman ne ya taso ya tayar da ita dan tayi
sallah, saida ta tashi zaune tayi addu'ar tashi daga bacci sannan ta kalleshi.

"Malama ki tashi kiyi sallah" yana fad'a ya juya zai fita, yunk'urawa tayi ta tashi
amma ina k'afafu sunyi tsami.

_Wayyo Ummi wallahi irin ciwon da naji nima kenan lokacin da na fad'i da moto,
saida na zama gurguwa ta kwana uku_
Da sauri tace "yaya Salman dan Allah kaini toilet"

Dawowa yayi ya tsaya yana kallonta kafin yace "haka ake neman taimako cike da bada
umarni?"

Turo baki tayi tare da zabga uwar harara ta kau da kai gefe tana wani jijjiga,
k'ura mata ido yayi yana jiran yaji ko zata rarrasheshi amma shiru kake ji.

Ummi tunaninta shine ya zatayi ta rarrashi mutum, batasan yanda zatayi ba dan tunda
take bata tab'a rarrashi ba idan tana son abu, ita dai idan taga abu tana so koba
nata bane to kawai za tace ne abata, idan ba'a bata ba ta fashe da kuka su Hajia
Alhaji maman Salman mahaifinta suna kewaye da ita su zasu goyi bayan abata ko sun
san ita ce marar gskiyar wannan shine.

Jin fitsari na shirin kubce mata yasa ta saké kallonshi tace "dan Allah haba ka
kaini fitsari nake ji fa"

Kallonta kawai yake kamar gunki, kwab'e fuska tayi tace "ni dai inba zaka kaini ba
wallahi zanyi shi a nan"

Baisan sanda dariya ta sub'uce masa ba, amma saiya dake yace "to kiyi mana gadonki
ne fa ba nawa ba"

Hawaye ne suka fara taho mata tusa hannayenta tayi tsakankanin cinyoyinta tana ta
matsewa wai karya fito, saiko taji fitsarin ya fara zubowa, fashewa tayi da kuka
tana fad'in "dan Allah ka kaini wallahi zai taho"

Cak ya d'auketa yayi toilet da ita ya aje tsaye, ina yana ajeta fitsarin ya ida
tahowa, Salman kam mutuwar tsaye yayi yana kallonta kafin ya fara shek'a dariya har
yana rik'e ciki.

Ummi kam ko a jikinta dan inta nuna masa taji kunya to ta shiga uku kenan zai dinga
tsokanarta kullum, cikin shagwab'a tace "ni dan Allah ka fita to na gyara jikina"

Da k'yar ya dakata daga dariyar ya nunata da hannu yace "ke yanzu ko kunya bakya ji
kamar wata k'aramar yarinya fitsari daga tsaye"

Turo baki tayi tace "to miye a ciki ai laifinka ne, kuma ma da kake cewa bana jin
kunya, kunyarka zanji? kaifa yayana ne kuma mijina to miye a ciki dan nayi fitsari
gabanka."

Kallon rigarshi yayi yace "dubi kinsa na d'auka ke kin b'atamin riga, yanzu dole
saina canja wata." juyawa yayi ya fita yana dariya.

Yana sauyawa ya nufi masallaci zuciyarshi cike da farin ciki, haka kawai yake jin
nishad'i, tabbas Ummi ta birgeshi yau data nuna ba wani abu bane dan tayi fitsari
daga tsaye kuma a gabanshi, dariya ya saké b'allewa da ita harya isa masallacin.

Ta kasa tsaye da kyau dole ta zauna k'asa tunda dai dama kayanta sun riga sun
b'ace, gashi hannu na ciwo ta kasa cire su dole ta zauna zaman jiran Salman, tare
da tunanin cire kunya ta rok'eshi ya cire mata kayan, sannan ya mata wanka.

```Irkwai beri```

Yana dawowa ya shigo d'akin ya sameta zaune a toilet, tambayarta yayi "miye haka ke
kuma, kina zaune har naje na dawo ba kiyi komai ba?"

Turo baki tayi tace "to ni dan Allah ka ciremin bazan iya ba" ido ya fiddo waje
yace "ke d'an aikinki kika mayar dani ko me?"

Langab'e kai tayi tana shirin kuka tace "dan Allah ka ciremin" hararanta yayi yace
"ke in zaki tashi kiyi abinda ya dace ki tashi, in kuma ba zaki yiba to ki zauna
nan har sarkin zama ya sameki."

Juyawa yayi zai fita Ummi tace "dan Allah yaya Salman, *AGU TIZEDAT*(kayi hak'uri)
*WURTU ZILISA*(ba zan saké ba)."

Juyowa yayi yace "iyee, d'iyar Mama kenan wato harda buzanci yau, kin tuna yaren
mahaifiya kenan, amma karki manta ni ban iya buzanci ba dama fulatanci ne to da
sauk'i ina ji kad'an kad'an"

Yanda tayi kalar tausayi yasa ya shigo toilet d'in ya kama hannunta ya mik'ar da
ita tsaye, kallon juna sukayi Ummi kam kawar da kai tayi gefe , zuciyar ta na k'ara
tsananta bugawa.

Bayanta ya koma a hankali ya fara zuge zif d'in rigarta, da k'yar ya had'iye wasu
yawu da suka tarar masa k'irjinsa kamar zai fito, take hannayensa suka fara
kakkarwa kamar mazari, Ummi najin ya sab'ile mata rigar ta zube k'asa ya rage daga
ita sai bras da pants, da sauri ta juya tana fuskantarshi amma kanta na kallon
k'asa rufe jikinta tayi tace.

"Ya isa haka nagode" kamar jira yake dama saiko fit ya fice daga d'akin gaba d'aya,
yana shiga d'akin shi ya fad'a saman gado ruf da ciki idonshi rufe yana sauke
numfashi a hankali, tashi yayi ya bud'e drower ya d'auki maganinshi guda d'aya
yasha sannan ya shiga wanka.

Ummi kam da k'yar ta samu ta wanke jikinta duk inda ya b'ace, sannan ta fito ta
d'auki wata doguwar riga tasa ta zauna tayi sallah, tana idawa bata tashi ba saima
tunani data shiga yi.

"Na d'auka kamar yanda nayi fitsari gabanshi ba tare da na ji nauyi ba, na zata
haka zan iya jarumtar fiskantarshi ya ciremin kayana sannan yamin wanka ya saké min
kaya, ashe ba haka abin yake ba, yana da wuya ka iya jarumtar tsayawa wani ya kalli
tsiraicinka ba tare da baka ji wani abu ba."

Ganin safiya tayi yasa ta tashi da k'yar ta dinga d'ogala k'afafu haka ta kai kanta
falo amma fa anci wuya.

_ALLAH YA BADA LAFIYA_


05/03/2019 à 17:31 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

6⃣3⃣6⃣4⃣
6⃣3⃣-6⃣4⃣

Salman ne ya fito cikin k'ananan kaya farar riga mai dogayen hannu sai bak'in
wando, yayi kyau sosai tsaf Ummi ta k'are masa kallo cike da birgewa.

Ganin yanda yake kallonta shima yasa tace " *WAYIWAN NEDIS*(ina kwana)"

Kallonta yayi sosai kafin yace "amma ai na fad'a maki bana jin buzanci ko, gwara
kimin fulatanci ko indianci sunfi sauk'i"

Kallon rainin hankali ta masa kafin ta girgiza kai tace "Ok *EN VETII
JAMNA*(antashi lafiya)?"

Kallonta yayi saidai baiyi mamakin jin fulatanci daga bakinta ba, domin kuwa yasha
samun su ita da Mama tana koya mata, murmushi ya mata yace " *NOI CHOMRII*(ya
gajiya)?"

Shiru tayi dan kuwa ta manta sauran darusan da Mama ta koya mata, maida hankalinta
tayi ga tv tana kallo, ganin ba zata amsa ba yasa ya kalli tv ya kalleta yace " sai
son kallon india amma baki jin mai suke fad'a"

Harya wuce yaji tace " *KAISE HO TUM*(ya kake)?"

Dawowa yayi kusa da ita yace" *HUM THEEK HOON*(lafiya lau nake), *AUR TUM*(ke fa)?"

" *HUM BILKUL THEEK HOON*"

Dariya yayi yace "lallai ba laifi, inaga zanje dake india idan na tashi tafiya" da
sauri ta dafe mararta tare da cije leb'e tace "wayyo mara ta ciwo take"

Matsowa yayi kusa da ita yace "ya dai miyake damunki?" wani kallo ta masa tace "ba
komai" tab'e baki yayi ya ficewarsa daga gidan, haka ciwon ya fara takura ta amma
ta daure.

Salman na fita gida ya nufa dan Mama tace yaje ya karb'o masu abinci, yana shiga
Mama ce kad'ai zaune a falo, da sallama ya shigo ya zauna yana fad'in "Mama ku
kad'ai zaune?"

Saida tayi hamma sannan tace "wallahi ni kad'ai duk sun tafi makaranta"

"Ok ina kwana?"

"Lafiya lau, antashi lafiya?"

"Lafiya lau Mama, ya gida ya gajiya?"

"Ba gajiya, ya d'iyata da jikin kuma, ina fata dai da sauk'i?"

"Um da sauk'i Mama tana nan lafiya"

Kallonshi tayi da kyau tace "ina fatan dai kana kula da ita baka mata cutar nan
daka saba ko?" dariya yayi yace "Mama kenan aini bana dukanta idan bâ laifi tamin
ba, ku kuma baku ganin laifinta, shiyasa kullum kuke ganin nine mai laifi ba ita
ba."

"Hmm, kaidai ka saba da narkarta kawai ko babu laifin fari bana bak'i kana jin
dad'in dukanta."

Jingina yayi a kujeran kamar zai kwanta yace "to Mama yanzu ai na bari tunda ita ma
ta rage tunda babu k'afafu da hannu d'aya"

Waro ido Mama tayi tace "aw kenan ciwon data ji kad'ai yasa ka daina dukanta?
shiyasa taji dad'in zamanta gidan Khamis."

"A'a Mama ba haka nake nufi ba, nasan dai yanzu zata rage tsokana tunda ta samu
rauni, ba zata iya jan fad'a ta ruga a guje ba."
Tab'e baki Maman tayi lokacin data mik'e tsaye tana fad'in "kaidai kasani kaci gaba
da dukanta tana matarka, akwai ranar horo ko kuma idan ka mata bugun da zai b'aran
mata da ciki, ai kaga saika huta."

Da k'arfi ya d'ago daga zaman da yayi cikin d'aga murya yace "ciki Mama, tace maki
tana dashi?"

Juyowa Mama tayi tace "saita fad'amin tana da, bayan rashin lafiyar da Jawahir
tace tayi ta kwana biyu harda su amai."

Shigewa tayi danta d'auko mashi abinci, shi kam shiru yayi gaba d'aya tunaninshi ya
tafi akan abinda Mamar ta fad'a, harta fito ta aje masa kwanukan guda biyu bai
masan ta aje ba.

Zaune Mama tayi tana kallonshi, gyara zamansa yayi yana kallon Mama yace "Mama wai
da gaske yarinyar nan ciki ne da ita?"

Tsaki Mama tayi tace "kaji wani rainin wayo, tana matarka amma bakasan tana da ciki
ba duk da rashin lafiyar da tayi, kodan baka nan?"

Cikin mamaki yace "amma Mama aini na d'auka wannan rashin lafiyar saboda wata
matsala ce dake damunta, amai kuma saboda taci abincin da yafi k'arfinta ne shiyasa
ta aman.?"

Hararanshi tayi dan ita a ganinta yana so ya b'oyene saboda baya so a sani ko kuma
kunya, cewa tayi "wace irin damuwa ce zata ja mata rashin lafiya, kuma dan anci
abinci mai yawa sai ayi amai.?"

To ganin Mama tak'i yarda ta fahimceshi yasa yace "Mama wai kun duba kayan nan
kuwa?"

"E na duba naga sunyi sosai, saura kud'in d'inkin kayan ko?"

"To Mama nawa ya dace a saka kenan?"

"To ai basai na fad'a maka ba, babu wanda ya kaika samun mata a b'agas, tunda gashi
za'a kai mata Lefe tana d'auke da juna biyu, aiko kaga kai dan baiwa ne, dan haka
tuwon girma miyarsa nama kayi bajinta kawai."

Cike da damuwa ya kalli Mama yace "Mamaa, bana so kina cewa tana da cikin nan, ba
tada komai fa"

Tab'e baki tayi tace "kaidai kasa ni, ni dai ka hanzarta kawo kud'in dan a samu
akai kayan da wuri"

Mik'ewa yayi yasa hannu a cikin aljihu ya ciro kud'i masu yawa ya bawa Mama, karb'a
tayi tana kallon kud'in kafin tace "wannan kud'in haka har nawa ne?"

Dariya yayi yace "Mama kuda gasunan a hannunku, ku irga mana"

"Kai bazan iya ba, idan ma na fara ba'cewa zanyi ka fad'amin kawai"

" Mama kenan, to d'ari biyar ne (500.000F CFA)"

Baki Mama ta washe tace "kai amma naji dad'i, yanzu ka tabbatarmin da kai mai yaba
kyauta ne, gaskiya naji dad'i Allah ya maku albarka, Allah ya albarkaci aurenku,
Allah ya bata lafiya ya rabata da abinda yake cikinta lafiya."

Ganin Mama tak'i fahimtarshi yasa sukayi sallama a haka, ya d'auki abinci ya kama
hanyar gida zuciyarshi cike da wasi-wasi.

Yana zuwa da kanshi ya zuba mata abinci a plate ya mik'a mata tare da zaunawa kusa
ita yana k'are mata kallo, wai mai ciki "to cikin wa?" ya tambayi kanshi.

Ummi kam dan danan ta cije leb'e saboda ciwon da mararta keyi, saida ta malmalo
lomar fankasu daya sha jar miya zata kai bakinta, cak ta tsaya tare da kallon
Salman.

Tunawa tayi jiya yace yana jin yunwa da Hajia tace ya d'auketa, kuma a iya saninta
bata ga sanda yaci wani abu ba da idonta, dan haka ta mik'a masa plate d'in tace
"ci"

Cike da mamakin abinda tayi ya girgiza mata kai yace "kici kawai"

Shagwab'ewa tayi tace "dan Allah kaci nasan kana jin yunwa, tun jiya baka ci komai
ba."

Kallonta kawai yake kafin yace "ki fara ci, idan kin ida zanci"

Kai ta girgiza masa tace "bazan iya ciba yaya Salman"

Idonshi akan tv yace "parce que (saboda)?"

A ranta kam cewa tayi "saboda kana jin yunwa" amma a fili sai tace "saboda bazan
iya ci ba alhalin kai baka ci ba."

K'yar idon Salman a kanta kamar zai had'iyeta, mamakin furcinta yake sosai da k'yar
yace "Ummi miyasa kika damu da sai naci, bayan kema nasan kina buk'atarsa.?"

Shiru tayi tana tunani, ba zata iya fad'a masa haka kawai taji tana so ya fara cika
cikinsa kafin ita ba, a hankali ta d'ora hannunta akan mararta tana matse fuska,
karb'a yayi ya yanko loma mai kyau, a hankali ya nufi bakin Ummi da ita tare da
cewa "haa."

Bud'a baki tayi ya saka mata, kallon junansu kawai suke, Salman ya had'a ido da ita
ne saboda yana so ya gano wani abu a tare da ita, kallon ne yayi yawa yasa Ummi
k'asa da idonta, amma duk da haka bai bar bata abincin ba shima kuma yana sawa
nashi bakin, haka har suka gama.

Suna idawa ya maida kwanukan ya aje ya d'auko mata madara daga nan zaune tana
kurb'a, shi kuma ya fita ya bar gidan zuciyar shi nata tunanin juna biyun da Mama
ta fad'a masa wai Ummi tana da.

Gidan Ummi ko kad'an bai tsagaita ba saboda tururuwar da 'yan uwa suka dinga yi a
gidan kamar ana biki, Ummi tsabar farin ciki kamar ta k'urma ihu, bayan hana 'yan
uwanta da Alhaji yayi zuwa gidanta, yau gashi dangi sun cika gidanta saboda zuwa
ganinta.

Sai misalin 22:30 kad'ai gidan yayi shiru ya rage Ummi kad'ai a gidan, sai lokacin
ta fara jin ciwon mararta yana dad'a taso mata, haka tayi ta murk'ususu har bacci
ya d'auketa daga nan kan kujera.

23:40 Salman ya shigo gidan, saida ya k'are mata kallo daga sama har k'asa,
durk'usawa yayi yana kallon cikinta daya lafe a mararta, tsintar kansa yayi yana
murmushi kafin ya mik'e tsaye yana fad'in "ta yaya za ace akwai ajiyar yaro anan
wurin, bayan a shafe yake."

Tsaf ya d'auketa ya direta akan gado tare da ja mata zanin rufa, sannan ya tofeta
da addu'a ya shafa kanta yace "saida safe".kamar tana jinshi.

Ciwon mara ne ya tayar da Ummi daga bacci, yarfa hannu kawai take gashi ba lafiya
bare ta samu damar murk'usawa da kyau, haka ta dinga cizar leb'e har taji Salman na
k'ok'arin shigowa d'akin, da sauri ta kwanta ta rufe ido kamar mai bacci.

Kallo d'aya Salman ya mata ya gane idonta biyu, dan daga yanda take sauke
numfashinta da sauri sauri,tsaye yayi a kanta yace " tashi ko malama"

Da k'yar ta tashi ba tare data kalleshi ba, zaune yayi kusa da k'afafunta yace
"miyake damunki wai"

Ko kad'an ba zata iya fad'a masa tana ciwon marar jinin al'ada bane, dan haka tace
"ciwona ne kemin ciwo"

Kallonta yayi kamar mai son gano wani abu a tare da ita, ajiyar zuciya ya sauké
yace "kinsha maganinki?"

"Bansha na dare ba gaskiya"

Harara ya dalla mata yace "zan d'auko maki yanzu kisha, amma wallahi idan kika
k'isha to ranki zai mugun b'aci a daren nan." fita yayi falo ya d'auko ledar
magungunan tare da ruwa.

B'allowa yayi ya mik'a mata, karb'a tayi ta rik'e a hannu tana shirin kuka, zaro
ido yayi yace "wallahi zanci gidanku kinji na fad'a maki"

Turo baki tayi tana kunkuni haka ta jefa maganin a cikin baki ta kora da ruwa,
ganin tasha yasa ya mik'e zai fita daga d'akin, motsa k'afafunta tayi amma taji su
gam kamar ba'a jikinta suke ba, da sauri tace,

"Yallab'ai" cak ya tsaya ya juyo yana fad'i a ransa "wato akwai abinda kike so
shiyasa na samu wannan sunan."

Kar kace kai tayi tace "dan Allah taimako nake nema?"

Ba murmushi a fuskar nan yace "ina jinki"

Da hannu ta masa alama da drower tace "dan Allah ka mik'o min coton a ciki"

Saida ya gama hararanta sannan ya nufi drower ya bud'e, coton Vania ya gani dan
haka ya d'auko ya nuna mata tare da fad'in "wannan kike nufi?"

D'aga masa kai tayi alamar eh, k'arasowa yayi yace "yanzu kema kinfi so kiyi anfani
da wannan, a maimakon kiyi anfani da abinda zaki wanke da hannayenki bayan kin
kammala saboda k'iwa ko?"

"Shin ko kinsan darajar wannan jinin, Allah ne fa ya halinceku dashi saboda


dacewarku dashi d'in, yafi daraja da mutunci mace tasa hannayenta tâ wanke da
kanta, duk da yana k'azanta amma kuma ta wani b'angare cuta kuke fitarwa, sannan
shed'anun aljanu suna samun damar sauk'in shiga jikinki a lokacin da kuka jefar
dashi cikin shara dama duk wani mai son cutar daku ta hanyar samun jinin hailarku."

Girgiza kai tayi tace "a'a yaya Salman wallahi bana aiki dashi haka kawai, sai
inhar zan fita unguwa saboda gudun kar jikina ya b'ace ban sani ba da kuma canzawa
idan buk'atar hakan ta tashi,dan shi d'in yafi k'yale wani lokacin, amma tun
lokacin dana fara Mama ta fad'amin komai akanshi,harma da mahimmancin wankewa da
hannuna."
Ya gamsu da maganarta sosai dan haka ya bud'e ya ciro d'aya ya mik'a mata, tana
karb'a yace "yaushe bak'on naki yazo?"

Baki bud'e ta kalleshi kafin ta kawar da kanta gefe, jin tayi shiru yasa yace "dake
fa nake magana?"

Ba tare data kalleshi ba tace "yanzu"

Juyawa yayi danya mayar da coton d'in yace "yaushe zai tafi?"

Dam!taji gabanta ya fad'i, a ranta kuma cewa tayi "wannan jaraba har yaushe da irin
ta, ko ina ruwanshi kuma."

Kamar daga sama taji yace "ba jaraba bace, kawai dai inaso in sani ne dan nasan
kwana nawa kike bakya sallah"

Kallonshi tayi k'asa k'asa yanda ba zaiji ba tace "ashe yaji"

Nan ma ji tayi yace "a'a banji ba, nasan dai abinda zaki fad'a kenan"

Hanyar k'ofa ya nufa zai fita tace "to yallabai" juyowa yayi cike da jin haushi
yace "miye kuma yanzu? bacci fa nake so nayi"

Cike da shagwab'a tace "kayi hak'uri naga baka d'aukomin pants bane kuma zaka fita"

Rik'e k'ugu yayi "ke wai d'an aikinki kina mayar dani ko me?" jin tayi shiru yasa
ya nufi wadrob d'in ya bud'e, da hannu ta masa ishara inda take aje k'ananan kayan,
haushi yaji ya kama shi dan ganinsu gasunan masu yawan kuma duk sabbi, gashi ya
riga ya siyo mata masu yawo shima.

Wasu jajaye ya d'auko mata a had'e da bras d'in yake, jefo mata yayi tare da fad'in
"size nawa kike sakawa?"

Ta gefen ido ta harareshi tace "to waini wannan wace irin tambayar k'wak'wafi ce
haka?"

Bata rai yayi yace " ke in zaki fad'amin ki fad'a, dan naga kamar kina saka wanda
suka fi k'arfin ki"

Kallon raini ta masa cike da masifa tace "wacece, ni d'in, wallahi sai tayi, kaji
in fad'a maka number 40 nake sakawa na bras haka ma pants,ashe ma kallon tsoro kake
min bakasan babbar macece ni d'in ba."

Saida ya k'are mata kallo ya juya zai fita, cikin kunkuni tace "haba bakasan niba
ne, kai kullum tunaninka bai wuce an haifeni a gabanka ba, amma muna nan da kai
akwai lokacin da ni d'innan zan d'aukeka tsaf wallahi."

Cak Salman ya tsaya tare da juyowa saida yazo gabanta ya rusuna kamar zai sumbace
ta sannan yace "karki saké tunanin haka ko a mafarki, nafi k'arfinki ko kad'an ba
zaki iya dani ba, kafin abinda kike tunani ya faru sai an had'a kamar ki guda goma,
dan ke kad'ai kinmin kad'an, tamilon wofi."ya fad'a tare da dan gware mata kai.

Yana fita tayi wata doguwar k'wafa tare da cewa " aiko zaka san ka fad'amin haka,
dan wallahi sai nasa ka gane kurenka, kuma wallahi saika d'and'ani kud'arka dani
kake zancen, kai har yanzu bakasan Annabi ya faku ba, ba komai ne shekaru keyi ba
amma zaka fahimci haka ranar da ka zubar da hawayenka a kaina."

Daga zaune ta gyara ta saké pants d'in tasa coton, sannan ta gyara kwanciyarta sai
bacci.

_To Allah yaba mai Rabo sa'a_

```Muje zuwa```😍
05/03/2019 à 17:31 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

6⃣5⃣6⃣6⃣
6⃣5⃣-6⃣6⃣

Cikin dare Ummi ta farka bayan tayi fitsari tayi brush ta dawo ta kwanta taci gaba
da baccinta.

Haka ma Salman koda yayi alwala masallaci ya nufa tunda yasan Ummi bata sallah,
yana dawowa kuma shima kwance yayi yaci gaba da bacci.

*Safiya*nayi Salman ya shigo d'akin Ummi dake bacci har yanzu, pillonta ya girgiza
dan haka ta bud'a ido tare da tashi zaune tana addu'a, kallonshi tayi lokaci d'aya
kuma ta kawar da kanta gefe saboda fad'uwar da gabanta yayi, bak'ar singlet ce a
jikinshi ta kamashi sosai duk surarshi ta k'akk'arfa ta fito, sai dogon wando shima
bak'i murya k'asa k'asa tace "wannan ba k'aramin k'ato bane gaskiya a daren farko
zai kasheni, dan haka na hak'ura da d'aukar fansa ta"

Wani shu'umin murmushi yayi yace "aiba ma zan fara ba, dan kuwa kin min kad'an sai
an har had'a irinki guda goma sannan zaki isheni kallo."

Kalllonshi tayi tace "ni d'in, wallahi nasan na isa harna wuce, waya fad'a maka
mace nawa namiji kad'an , hasalima kune kukewa yaran mutane fyaa..." saurin kame
bakinta tayi, kallonta yayi yace,

"Ki fada mana, nasan za kice maza kewa yara fyade, amma ki sani ba irina bane su
dan ni bake ba wacce tafi kima tamin k'arama bare kuma ke, sannan ki sani mace
nawa namiji kad'an amma namiji bayawa mace kad'an."

"Ki fito falo ni zanje gida." ya fara ya dak'ile

Juyawa yayi zai fita ummi tace "to wa zai fidda ni?"

Tsaye yayi yana kallonta kafin ya matso yace "d'an aiki kika mayar dani ko me?"

Shirun da tayi yasa ya matso yana shirin d'aukarta, da k'arfi ta d'aga murya tace
"a'a ni bana san d'auka goyo nake so"

Cikin b'acin rai yayi k'wafa sannan ya juya ya sunkuya, Ummi kam tintsirewa tayi
da dariya kafin tace "to yaya Salman taya zan hau nan?ai sai an aza min tsani ko
kai bakasan dogo bane?"

Juyowa yayi yana nunata da yatsa yace "wallahi karki b'atamin rai da safiyar nan
kinji na fad'a maki."

Turo baki tayi tare da d'aga hannu cikin shagwab'a tace "pardon"

Tsaye tayi akan gadon tare da d'anewa bayanshi, amma ko kad'an tak'i yarda jikinsu
ya had'u ta mashi wani zok'ok'o kamar ya d'auko buhun k'aya, cikin masifa Salman
yace,

"Ke wannan wane irin iskanci ne, kinsan bakya son had'a jiki dani miyasa kika ce
saidai na goyaki, munafuka kawai."

Tunda ya fara magana take ta murgudar baki kamar ta cireshi, a hankali tace "to
haka kawai saina had'a jiki da kai"

Haushi ne yasa Salman finciko hannunta ya manna ta a bayanshi da k'arfi, wani


numfashi ta sauke jinta a bayanshi kwance, Salman kam mutuwar tsaye yayi jin gaba
d'aya albarkatun k'irjkinta sun sauka akan bayanshi da k'arfi.

_🤣🤣🤣🤣🤣 waya aike ka dama?_

Kunya ce tasa Ummi ida narkewa a jikinshi ta kasa d'agawa, da 'kyar Salman yayi
k'arfin d'aga k'afarshi ya doshi hanyar fita idonshi lumshe, tunda yake bai tab'a
jin abinda yake jiba a yanzu a haka suka kai falo ya direta kwance kamar yarinya,
juyawa yayi ya mata runfa da faffad'an kirjinshi kamshin turarenta ne ya fara
tafiya da imaninshi, duk da ba sosai ake jinshi ba sai kana gaf da ita.

Kallon fuskarta kawai yake wani abu na fizgarshi da k'arfi, ganin Ummi tak'i had'a
ido dashi yasa ya cusa kanshi tsakanin kafad'arta da fuskarta ma'ana a wuyanta yana
shak'ar kamshinta yana sauke shed'a sannu sannu.

Ummi duk bata jin dad'i saboda ganinta yau kwananta biyu ba tayi wanka ba saboda
ciwo, duk da dai tasan akwai turare a jikinta wanda ko zatayi sati tofa zai zauna a
jikinta.

D'ago ido yayi harsun canja kala cikin wata irin murya k'asa k'asa yace "sunan
turarenki ma? gaskiya yana da dad'i."

Murmushi Ummi tayi jin wata irin tambaya a jirkice kafin tace " *ARABIAN OUD*"

D'agowa ya sake ya kalleta saidai, baisan lokacin da ya had'a bakinshi dana taba ya
fara tsutsa kamar mai shan sweet, tun yana abun a hankali harya fara mata cikin
sauri da son aika sak'on cikin gaggawa.

Ummi najin hannun Salman na shirin shiga cikin rigarta tayi saurin rik'e hannun
tare da tureshi daga kanta, zaune ya fad'a akan kujerar har yana shirin danne mata
k'afa, kanshi kasa idonshi rufe yake sauke numfashi da sauri sauri ya kasa tuna
komai, haka ya tashi ya shiga d'akinshi ya saka rigarshi yayi tsaye yana k'are ma
kanshi kallo.

Yana fitowa ko kallonta baiyi ba ya wuce, yana shiga mota ya kifa kansa a stiyari
ya jima kafin d'ago kanshi yana fad'in "pourquoi, pourquoi je fais ça, pourquoi je
fais ça de cette idiot fille? "

"Pourquoi je envis de cette pagaille fille? oh mon Dieu aide moi."

Ya jima kafin ya tayar da motar ya nufi gida, tunda yaje gida babu walwala a tare
dashi haka ya karb'i abincin ya fito, saida ya aje abincin a mota sannan ya shiga
gidansu Ummi dan su gaisa dasu La Mama.
Yana shiga dole ya saki ransa saboda ganin su Inna Hajara (kakar Ummi) da Tanti
Fateema (k'anwar La Mama), gaisawa sukayi sosai kafin Inna ta shaida masa sunzo
ganin Ummi ne, cike da jimami yace "haba Inna aida ba kuyi wahalar zuwa bama
wallahi tunda da sauk'i"

Dariya Inna tayi tace "ai dama nasan da kunsan zanzo da ba zaku bari ba"

La Mama ma haka tace "nima saida na fada masu da sunyi zamansu tunda da sauk'i."

Koda Salman zai wuce yace su tashi ya tafi dasu, haka suka tafi tare saidai tun a
hanya Inna ta fahimci damuwa a tare da Salman, dan haka tace "d'ana shin da matsala
ne zaman naku kai da k'anwar taka?"

Cike da san basarwa yace "a'a Inna babu wata matsala ko kad'an"

Bata yarda dan haka ma taci alwashin gano matsalar idan taje gidan, dan tasan
kuruciyar Ummi dama Salman d'in, ta kuma san yanda aurensu ya kasance dan haka ita
a nata ganin babu wani dalilin da zaisa Ummi tabar mijinta cikin damuwa koda kuwa
ba itace silar shigarsa damuwar ba.

Suna zuwa kuwa Ummi ta taresu da murna tana masu sannu da zuwa, Salman ne ya aje
mata abincin a gabanta ya juya zai fita, cikin b'acin rai Inna tace "kaga d'ana zo
zauna nan"

Tun kafin ya zauna Inna tace "kace babu matsala amma gashi daga zuwana na hango
babbar matsala a tsakaninku"

Maida kallonta tayi ga Ummi dake kallon Salman, saiko saukar mari a fuskar Ummi a
kid'ime ta dafe kunci tana hawaye, Inna kuwa d'orawa tayi da fad'in " 'yar iska
marar mutunci, ashe baki canja halinki ba?"

"Ummi sai yaushe zakiyi hankali? mijinki na sunna kina kallo ya shigo daga fitar
da nasan kece sanadi amma ko kallon fuskarsa baki yiba bare yasa ran samun sannu da
zuwa daga wajenki, kuma abin haushi kina kallonshi da kaya amma kinfi k'arfin ki
amsa koda daga zaune."

"Sannan kuma kina kallo ya juya zai fita ba tare daya ci abincin ba,amma ke ko a
jikinki kuma kinsan baici komai ba, haka kika bishi da ido ba tare da addu'a wa
mijinki ba zai fita."

"Wannan wane irin zamane kuke mai kama dana dadiro ko kuma rik'akk'u 'yan bariki,
zaman da babu girmamawa a cikin shi bare mutunta juna?"tayi maganar tare da
kallonsu su dukansu.

Salman ne ya bud'e baki zaiyi magana Inna ta dakatar dashi da cewa "a'a laifin kane
daka kasa dorata a turban da kake so, kaine namiji kuma babba kaine zaka tsawatar
mata amma gashi ka kasa, ka zama wani lusari a gaban k'aramar yarinyar da aka haifa
a gabanka."

Ummi ta kalla tace "ke kuma kici gaba, amma ki sani akwai ranar da zakiyi kuka
ranar da nadamarki ba zata anfaneki da komai ba, maza irin mijinki ba'a masu haka,
duk wacce ta samu irinshi k'ok'arinta shine ta mallakeshi ta hanyar yi masa biyayya
ko kuma bin bokaye da malami, nasan kinsan yanda zaki kula da miji a wajen
mahaifiyarki amma kike so ki zubar mata da daraja, ba komai kici gaba."

Hannu Islam Inna ta fizga suka wuce cike da b'acin rai Fateema ko damar magana bata
samu ba, suna fita Salman yabi bayansu amma fafur suka k'i shiga mota ya kaisu sai
adaidaita suka hau.
Salman kam baima dawo gidan ba ya shiga gari, Inna kuma suna zuwa suka fara shiri
tace kawai da safe komawa zasuyi, La Mama tayi tambayar koda matsala amma dayake
Fateema tace karsu fad'a mata yasa sukayi shiru, Islam kuma ko gidan bata shiga ba
ta fad'a gidansu Salman d'in wajen k'awarta Zeinab (autar su Salman).

Duk da ana zuwa duba jikinta amma haka tayi wunin ranar babu walwala duk abin
duniya ya zund'umeta ta kasa farin ciki, haka har dare kowa ya watse amma Salman
bai shigo ba da kanta taje ta kwanta kafin ya dawo gidan shima ya kwanta.

_Miji fa yana da daraja sosai 'yan uwa mu kula_.


05/03/2019 à 17:31 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

``` Kai kai kai, gaskiya babu abinda yafi dad'i kamar kayi abu a yaba, labarin
Salman da Ummi kowa magana yake akai, wasu na dariya wasu na nishad'i, abin farin
ciki yanda na samu abokanan fad'a wato 'yan team d'in Ummi.```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

6⃣7⃣6⃣8⃣
6⃣7⃣-6⃣8⃣

*Da safe*koda Ummi ta tashi wanka tayi cikin dabara saboda kar ciwonta ya jik'e
sosai, haka ta fito ta shirya powder kawai ta shafa a fuskarta sai turarenta data
shafa a jiki, gajeran siket ta saka ko gwiwa bai kai mata ba, saboda ciwonta gaba
d'ayanshi a baje yake sai bak'ar riga data dace da zanen siket d'in mai siraran
hannaye.

A hankali ta fito falo harta zauna saman kujera ta mik'e k'afafunta, bata lura da
Salman ba dake zaune akan d'aya daga cikin kujerun dinning d'in da kayan sport a
jikinshi yana shan ruwa tare da sauke gajiya.

Saidai tun fitowar Ummi ya saki baki yana k'are mata kallo, in har yace bata
birgeshi ba to tabbas k'arya ya fad'a, dan haka ya ci gaba da kallonta har saida
takai kallonta in da yake, cikin sauri tace,

"Ina kwana"

Bud'a baki yayi amma kuma sai ya nemi kowace kalma ya rasa, in'ina ya fara da k'yar
ya samu yace mata "bonjour"

Ita kam ko kallonshi bata saké ba, tashi yayi ya shiga d'akinshi dan yayi wanka,
Ummi kam sunna tv ta kama tana kallon d'aya daga cikin malaman dake birgeta wato
(malam Lawan Shu'aib Aboubakar).

Salman na fitowa d'akin Ummi ya shiga ya d'auko magungunanta, ya juyo zai fita ya
koma kan madubi yana duba turarukanta, duk wanda ya shinshina baya jin mai wannan
k'amshin, gashi kuma ya manta sunan data fad'a masa saboda lokacin baya cikin
hankalinshi, harya juya zai fita ya kuma dawowa 'yar k'aramar kwalbar daya gani ya
d'auka tare da karanta sunanshi, cike da farin ciki yace,

"Yes shine, arabian oud"


Abin mamaki sai yasa cikin aljihu.

_Ni kam nace toh_🤔


_Wannan aro ne ko gani zaiyi, ko kuma dai dogon aro ne_

Yana fitowa ya bata maganin yace ta aje kafin ya dawo, fita yayi daga gidan yana
shiga mota ya ciro turaren ya bud'e tare da shinshinar shi, lumshe ido yayi a
hankali ya bud'e ido ya ya saké maida shi cikin aljihu sannan yaja mota.

Ummi kam tana ganin ya fita tace "to komi ya kaishi d'akin nawa, kodai ajiya yayi
dani bansani ba?"

Yana zuwa gida yaga canji daga wajen Mama, dan kuwa ko gaisuwarshi bata amsa ba
fad'a kawai ta balbaleshi dashi, wai jiya yasa an yiwa Ummi fad'a harda mari, bayan
kuma laifinshi ne tunda baya sakar mata jiki da itama ta saba dashi.

Yayi mamakin jin abinda ya faru a bakin Mama saboda shi bai fad'a ba, tashin
hankalin kuma shine tunda Mama ta sani, to La Mama ta sani kenan kuma abinda ita za
tayi tofa ko kad'an bazai masa dad'i ba, dan ko baya san abinda zai tab'a lafiyar
Ummi yanzu.

Cikin ladabi ya kalli Mama yace "Mama wai dan Allah waya fad'a maku wannan
maganar?"

Cikin b'acin rai Mama tace "dama ai kai bâ fad'a za kayi ba, to Islam ta fad'a min
tunda gabanta a kayi."

Cike da mamaki ya saké maimaita sunan "Islam" gira ya had'e kafin ya mik'e tsaye
zai fita, cikin fad'a Mama tace "ni tsaya na d'auko maka abincinta ka kai mata"

Cak ya tsaya ba tare daya juyo ba, Mama kuma wucewa tayi tana fad'in "aikin banza
kawai, kai d'in wani k'aramin yaro ne da za ace saita baka abinci, idan kana jin
yunwa aika sani ka kuma san inda zaka je ka nemi abinci, amma haka kawai a dinga
takura yarinya harda bata lafiyar ma."

Bin Mama yayi da kallo, ganin ta dage tana ta fad'a akan abinda ba laifinshi bane,
ajiyar zuciya ya sauke yana tunanin abinda zai yiwa Islam d'in, saidai kuma ba zaya
iya mata komai ba saboda mutuniyarshi ce sosai, wata dabara ce ta fad'o masa in har
baya so La Mama ta b'ata ma Ummi rai, to dole ya nemi alfarma wajen Maman.

Mama na zuwa ta mik'a mashi kwanan harda dan gwara masa, karb'a yayi yace "Mama dan
Allah wata alfarma nake so kimin , in ba damuwa?"

Jin tayi shiru ya bashi damar cewa "dan Allah Mama kuje kuba La Mama hak'uri,
kunsan halinta wallahi zata iya zuwa gida kawai dan taci mutuncinta, dan Allah kuce
tayi hak'uri, sannan ku nuna mata nine mai laifi kamar yanda kuke ganin nine da
laifin abinda ya faru."

Zaune tayi a kujerar dake bayanshi hakan yasa ya juya yana kallonta tare da
sunkuyawa yana sauraran abinda zata fad'a, ba tare data kalleshi ba tace,

"Bana jin ta sani, dan kuwa da dare na shiga gidan mu kayi ban kwana dasu Innar,
kuma nidai banga wani alamu ba, haka ma Islam nan gidan ta wuni har dare, saida
tayi bacci Abbanka ya kaita gidan, ni kad'ai ta fad'ama saidai ko safiyar yau ta
fad'a mata."

Tsaye ya mik'e yace "ok bari naje gidan na gani, Allah yasa bata fad'a ba."

Dogon tsaki Mama tayi tace "in ma ta fad'a saime? ai hankalinka ya kwanta kenan
saika zuba ruwa k'asa kasha, dama burinka bai wuce a jibgeta ba, kuma uwarta ta
mata fad'a shikenan sai kaji dad'i."

Ko kad'an baiji dad'in abinda ya fito daga bakin Mama ba, amma haka ya dake yabar
gidan, kuma dama hakane famillynsu, kana k'in naka ne sai 'yan uwa su soshi, yafi
matuk'ar jin dad'in zama a gidansu Ummi saboda soyayyar dasu La Mama suke nuna
masa, haka kuma Ummi wani lokacin ma saita kwana ta wuni gidansu Salman ba tare
data lek'a gidansu ba.

Yana shiga kamar yanda ta saba haka ta tarbeshi cike da fara'a, zaune yayi k'asa
kusa da Abba inda yake break ya mik'a masa hannu su kayi musabaha, da kanshi ya
zuba kunun gyad'ar da Maman tayi wanda yasha madara sosai ya fara sha suna hira.

Yanayin La Mama bai nuna masa tasan da abinda ya faru ba, dan haka suka dinga hira
har Islam ta fito daga d'aki cikin shirin riga da wando masu kyau, yana kallonta
sai yaga sak ta masa kama da Ummi saidai ita tafi ummi dogon hanci, Ummi kuma ta
fita jar fata da manyan ido, amma har girman jikin da yatsun k'afarsu masu kyau
duka d'ayane.

Da gudu ta k'araso wajenshi ta fad'a jikinshi tare da fad'in "yaya Salman bonjour?"
(ina kwana Yaya Salman)

Cike da sakin fuska yace "bonjour Islam, bien réveillé ." ( lafia lau Islam, kin
tashi lafia )

Hannu ta zura ta d'auki cup d'in da yake shan kunu ta kai bakinta, tana fad'in
"bien , où est-Elle ?" ( yayi, ina take?)

Kallon idonta yayi yace " qui?" ( wa?)

Hararan wasa ta masa tace "aunty Ummi"

"Oho, elle est a la maison, elle va parfaitement bien ( tana gida, tana nan lafia
k'alau)

Abba ne yace "Salman kana so ka mayar min da yarinya banasariya fa, ka dinga mata
hausa mana tunda shine yaren mu."

Dariya yayi yace "Abba 'yar école ce fa, dole sai ana sirka mata danta dinga
fahimtar abinda ake koya mata da wuri."

La Mama ce tace "ai kuma gashi nan tana iya yin frensh da kai, amma yanzu ko zan
kasheta ba zata fad'amin ina kwana da yarena ba"

Gyara ma Islam zama yayi a cinyarshi yana kallon fuskar ta yace "lah bakya jin
buzanci ashe?"

Turo baki tayi inda shi kuma yabi bakin da kallo, La mama ce tace "ai dama duk
cikin su Ummi ce mai k'ok'arin son yare na da kuma yinshi amma fa idan tayi niyya,
kuma abin mamaki idan taso zata iya yin hira mai tsawo da harshen, kuma kaga ko
Inna babu abinda zata fad'a Ummi bata fahimce ta bâ."

Shiru yayi idonshi na kallon k'asa, sai ya ji ta k'ara birgeshi, dan haka ya mik'e
tare da Islam yace "to La Mama ni zan wuce, Abba sai anjima"

Islam ce ta k'ara rik'e hannunshi kamar mai shirin kuka ta kalli La mama tace "La
mama zan bishi ya kaini wajen aunty Ummi ?"

Salman ta kalla tace "yaya Salman je vien avec toi, s'il te plais?"(zan tafi tare
da kai),ta fad'a tare da zubo hawaye, durk'usawa yayi akan gwiwoyinshi ya share
mata k'walla yace " kema saurin kuka kamar auntynki ko?"

La Mama ce tace "ina Islam aiko rabin kukan Ummi ba tayi ba, Ummi fa tana k'arama
ko hararanta kayi sai hawaye, yanzu haka kuma da za tayi hamma sai ruwa sun zubo a
idonta, ai ita saurin kukanta ma babu kamarta duk gidan nan, sai kuma d'an banzan
rashin ji."

Murmushi kawai Salman yayi, dan kuwa saidai Ummi ba tayi niyyar kuka ba, yanzu ne
hawaye zasu cika kuncinta.

Haka Salman suka lallab'i La Mama ta barshi ya tafi da Islam d'in, amma da
alk'awarin zai dawo da ita gobe.

Ummi na zaune tana kallo Islam ta shigo da gudu tana kiran "aunty Ummi naaa"

Ummi na ganin Islam ta bud'e mata hannayenta ta rumgume ta suna murna, zaune tayi
kusanta tace "Islam waya kawo ki?"

Kafin tayi magana Salman ya shigo, nan fa suka fara zuba ba k'akk'autawa, Islam na
bawa Ummi labarin abokanan wasar data sake tunda tayi aure suka daina wasa tare.

Kular abinci dake hannunshi ya aje gaban Ummi sannan ya wuce ya d'auko plate da
cuillère da madara, tunda tafi sonta akan ruwa da jus, yana zuwa ya zuba abincin
mai yawa ya aje.

Hannayen Ummi ya kama ya sauko da ita k'asa sannan yace ma Islam "to sauko muci
abinci"

Haka suka keyawa suna cin abincin Islam na hira suna dariya tare da kallon juna
jefi jefi, Islam ce tace "aunty wai yanzu kina jin dad'in zama anan keda yaya
Salman?"

Ummi kallon Salman tayi shima ita yake kallo, murmushi tayi tace "sosai kam ina ji,
amma miyasa kika tambaya?"

Kallon Salman tayi tace "to ai naga yaya Salman bai iya irin wasar da muke ba nida
ke a gida"

Salman kam da yayi mamakin amsar data bawa Islam yace "wace irin wasa kuke a
gidan?"

Nan fa ta fara zayyana masa suna dariya, harda cewa "kuma yaya Salman muna wasan
goyo goyo, muna da d'iyan wasa muna masu kwalliya mu masu d'aki, kuma muna wasan
ruwan amma La Mama fad'a take mana bata barin mu."

Salman kam Mamaki ne ya cika shi dan haka yace "to amma tun yaushe kuke wannan
wasar haka?"

Cikin nuna rashin damuwa Islam tace "ai da Alhaji ya mata aure ne shikenan sai muka
daina, yanzu gashi bana da abokin wasa, kuma fa yaya Salman har rawa mukeyi"

Salman kam sauraran ikon Allah kawai yake, haka har suka gama cin abinci ya shiga
d'akinshi, turaren ya fiddo daga aljihunshi ya aje akan madubinshi yana k'are masa
kallo, a hankali ya tambayi kanshi "wai miyasa na d'auko wannan turaren, me zanyi
dashi?"

Tab'e baki yayi yace "ko ma dai miye ina son k'amshin, kuma zanci gaba da ajiyarshi
anan."

Yana fitowa Sa'adat ya samu zaune suna gaisawa da Ummi cikin farin ciki, k'arasowa
yayi suka gaisa da ita, Islam yaga nata faman hararan Sa'adat dan haka yace,

"Islam miye haka wannan ba yayarki bace?" turo baki tayi tace "to ni ina ruwana da
ita, ai bata sona."

Cikin tsawatarwa yace "ke Islam bana san haka fa, ki kiyaye ni" Sa'adat ce tayi
dariya tace "ai yaya Salman daka daina b'ata yawun bakinka, in dai nida Islam ce
mun saba, dan ita dama duk wanda baya wasa da ita to mak'iyinta ne, bana saké mata
kuma idan suna shirme ita da abokiyar shirmen ina magana, shiyasa take cewa bana
sonta."

Kallon Islam d'in yayi saiya ganta mak'ale a k'irjin Ummi kamar d'iyarta, ko kuma
zata bata nono harda daddab'ata take tana fad'in "ke rabu da ita dama tazo ne dan
ta b'ata mana rai"

Murmushi kawai Salman yayi ya fita,yana shiga mota tuk'i kawai yake kamar baya so,
ga favorite music d'inshi na tashi a hankali tana ratsa sassan jikinshi yana kuma
biyar wak'ar kamar shi yayi ta .

Ko kad'an Ummi bata da matsala, kawai dai tana da taurin kaine da raini ga wanda ta
raina.

Wani abu yaji yana k'ara narkuwa a cikin zuciyarshi, farin ciki yake ji har k'asan
ranshi.

Sa'adat ce ta kalli Ummi tace ".


05/03/2019 à 17:32 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

6⃣9⃣7⃣0⃣
6⃣9⃣-7⃣0⃣

"Ummi nifa wani abu ya ban mamaki, mijinki naga ya fita amma ko kalllonshi ba kiyi
ba, bare ki masa addu'ar Allah ya tsare ko sai ka dawo.?"

Turo baki tayi ba tare data kula taba, cikin b'acin rai Sa'adat tace "Ummi anya
kuwa kinyi hankali? ga dukkan alama har yanzu baki gyara halinki ba, amma ba komai
wallahi za kiyi nadama in har kika ci gaba a haka."

Kallonta Ummi tayi a shek'e tace "nadama, akan me fa?"

"Hmmm, lallai Ummi ba kisan ciwon kanki, shin ko kinsan irin tururuwar da 'yan uwa
keyi akan mijinki?"

"Ko kinsan yanda iyayenmu suke 'ko'karin had'a 'yayansu da mijinki saboda
dacewarshi da wuyar samun namiji kamarshi.?"

"Ummi ki nutsu kisan abinda ya dace dake tun kafin lokaci ya k'ure maki, namiji
kamar yaya Salman ba irin mazan da ake samu bane arha, amma ke gashi kin samu duk
da cewa kinsan yaya Salman yafi k'arfinki ta wani b'angaren, musamman idan ana
maganar kyau."

"K'anwata ki nutsu ki kama mijinki da kyau ta hanyar kyautata masa dayi masa
biyayya, zamanin nan abin tsoro ne 'yan mata suna nan bila adadi a gari, wasu ido
bud'e suke neman mazan aure sannan idan sun samesu su kyautata masu kota wace irin
hanya.

"Kama daga hanyar data dace dama wacce bata dace ba,Ummi kin tashi a gaban
mahaifiyar mu kinfi kowa sanin yanda ya kamata mace tama mijinta, dan tun muna
k'anana muke gani a wajen mahaifiyar mu, na tabbata kina da sani sosai akan yanda
zaki kula da yaya Salman amma shashanci ya hanaki tsayawa ki kula dashi."

"Ummi ko kinsan cewa aunty Hawa (mamar Khamis) tana k'ok'arin cusa ma yaya Salman
Rumana dan ya aure ta, haka ma aunty Rabi (kishiyar Hawa) tana so ta mak'ala masa
Nuseiba tazo a matarshi ta biyu."

"Kuma fa duk suna hakane saboda tabbacin da suke dashi a kanki na sanin ba zaku
tab'a zaman lafiya, saboda sanin yar tsamar dake tsakaninku dashi, to in hakane
miyasa ba zaki bawa mutane kunya ba ki rik'e mijinki hannu bibbiyu ta yanda zaki
bawa kowa mamaki."

"Ummi kisan fa duk abinda kika yi to zai iya shafar mutuncin Mamar mu, kuma Allah
ma shaida ne akan cewar mahaifiyar mu tayi iya abinda zata iya yi akan mu, kuma
kema kin sani irin maganganun da ake akan mahaifiyar mu cewa wai ta mallake
mahaifinmu har yanzu ita kad'ai ce a gidan."

"Bafa komai bane yasa ake fada mata haka sai dan iya kula da miji dayi masa
biyayya, dan haka 'yar uwata ki maida hankalinki kiyi abinda ya dace dake kafin
ranar da zata zo kiyi nadama ko kuma kiyi kuka da hawayenki, dan ko kad'an su aunty
ba suda nufin alkairi a kanki idan d'aya daga cikin 'yayan nan ta shigo gidan nan."

Tana fad'a ta gyara zamanta ta maida hankalinta ga tv tana kallo, Ummi kam duk
jikinta yayi sanyi tunani take in har akace za'a rabata da yaya Salman a yanda take
jinshi a yanzu, ba lallai bane ta iya daurewa.

Babu wanda ya k'ara magana a cikin su har su Mama da aunty Hawa suka shigo gidan
cikin sallama, tarbansu su kayi saida suka zauna sannan samarin da suka zo da su
suka fara shigowa da akwatinan lefen Ummi.

_😔😔😔 lefe kenen bayan tariyar amarya_

Akwati guda takwas haka aka shigo dasu kowace taf take da kaya na alfarma, Sa'adat
ce tace "amma Mama ku kad'ai kuka zo? gashi nan ma babu kowa"

Dariya Mama tayi tace "a'a karki damu, Alhaji dama yace mu dake manya muzo kawai ba
sai an tara jama'a."

Sai lokacin Ummi ta fahimci irin kallon da Mama Hawa take mata tare ma da kayan,
sosai ta k'ara shiga hankalinta tare da cin burin kyautatawa yaya Salman sannan ya
zama nata ita kad'ai.

Haka su Mama suka koma bayan tafiyar su Sa'adat ta duba kayan, matuk'a kayan sun
birge sosai sunyi kyau, haka suka wuni gidan Ummi da Islam nata shirmen su sai
yamma Sa'adat ta kammala girki da sauran gyaran gidan bayan takai akwatinan d'aki
sannan ta shirya dan tafiya gida.

Tana saka hijab d'inta tace "to Ummi ni zan wuce sai kuma na sake dawo wa, dan
Allah k'anwata kiyi tunani akan abinda na fad'a maki."

"Karki damu zanyi insha Allah" Ummi ta fad'a tana kallonta.

"Yawwa ko kefa, ni na wuce saida safe"

Kallon Islam tayi dake ta cakular kan Ummi wai tana mata kitso duk kitson dake
kanta , cewa tayi "to autar La Mama sai anjima ko"

Saida ta turo baki gaba tace "ni dai ki gaishe min da d'iyana"

Dariya Ummi tayi tace "k'awar yau kenan kin yarda d'iyanki ne?"

Dariya su kayi gaba d'ayansu ita dai ta wuce abinta, su kuma suka ci gaba da
harkokin su cikin nishad'i.

D'aki Ummi taje ta d'an gyara jikinta ta canja kaya hannu takai ta d'auki turarenta
sai taga wayam, tayi mamaki amma saita bud'a jakarta ta d'auko wani irinshi ta
shafa sannan ta fito falo ta zauna, Islam kam kallonta kawai take tana so tayi
magana kuma ta kasa.

Wayar Ummi Islam ta d'auka ta sambad'a masu wak'a, nan fa suka fara casu ba kama
hannun yaro, tun Ummi na rausaya daga zaune harta mik'e duk da k'afafunta amma haka
ta dage suna rawa.

Salman kam daya shigo gidan tsaye yayi yana kallon ikon Allah, wai Ummi mai ciwo
a k'afa amma gashi tana ta tik'ar rawa da k'afafun, ya shagala sosai wajen
kallonta ganin yanda take biyar kid'in da kyau.

Yana lab'e yana kallonsu har aka kai k'arshen wak'ar *DACE* wajen wani baiti da ake
fad'an,

_"Lokaci muke jira sai ka zo_"

_"In da rai rabon mu dole sai yazo_"

_"Babu kai kad'ai nake kira gwarzo_"

_"In da kake ba kira kawai nazo_"

_"Zuciya na saki, ba batun cire ki_"

_"Sa hannunka doki, banyi maka tsaki_"

_"Babu shi babu duka a tsarin soyayya_"

_"Na sani babu duka a tsarin soyayya_"

Take Salman yaji kamar dashi Ummi take, hannayenshi ya kalla duka biyu murmushi
yayi tare da fad'in "wannan shine dalilin da yasa yanzu bana san dukanki"

Maida kallonshi yayi garesu har sun shiga wata wakar ita ma ta Umar m sharif mai
taken *BABBAR RANA*
Kallonsu yake duk yanda tayi haka Islam keyi sai dariya suke suna farin ciki, kamar
ba ita ke rawar ba saboda gwanancewa har aka kai wani baiti daya saka shi darawa,

_"Mu tuk'a mota mata tukunya_"

_"Mota ba taje ba in babu taya_"

_Gida babu gida in babu mata_"

_"Mutum babu mutum in baida mata_"

Dariya yayi tare da kutsa kai cikin d'akin, da sauri Ummi ta zube k'asa tana fad'in
"wayo Mamana k'afata zata cire, wayo Allah na"

Murmushi kawai Salman keyi harya sunkuya wajenta ya rik'e k'afar yana kallon
k'wayar idonta yace "to yaya da sauk'i yanzu?"

Kunya ce ta rufe Ummi dan haka tace "da sauk'i, sannu da zuwa"

Cike da mamaki yace "Ummi yau ni ake wa sannu da zuwa?"

Kallonshi tayi cike da jin kunya tace "kayi hak'uri, muje kaci abinci"

Tana fad'a ta mik'e ta nufi dinning ta fara zuba abinci, kamar wawa haka ya bita ya
zauna yana kallonta cike da birgewa, Islam kam ba zata iya hak'ura ba dan haka ta
kalli yaya Salman cikin rad'a tace,

"Yaya Salman wai aunty Ummi bata jin kunya ne?"

Kanshi ya sunkuyo wajenta tare da rufe baki yace "me yasa kika ce haka?"

Cikin rad'a tace "to ni naga duk ta zama wata 'yar iska, bata jin kunyar saka
wannan kayan gabanka."

Bud'a baki yayi yana kallonta kafin yace "to ai ba komai bane, ni mijinta ne ke
kuma k'anwar ta."

A tare suka kalli Ummi dake tahowa hannunta d'auke da ruwa da jus, d'an k'aramin
siket d'inta sai wutsilniya yake, shi kam Salman yana jin dad'in ganinta a haka
kamar su zauna haka har abada.

Salman na kai loma bakinshi yace "ashe haka kika iya rawa?"

Ko kai Ummi bata d'aga ba bare ta kalleshi, dan haka yace "waya dafa abincin nan?"

"Ni" ta bashi amsa tana kallonshi, shi kam cewa yayi "um um ba ke bace, saidai ko
Sa'adat."

Jim Ummi tayi kafin tace "kasan ita tayi kuma kake tambaya?"

Ba tare daya kalleta ba yace "um um ba wai nasan ita tayi ba, saidai nasan
d'and'anon abincin ki"

Kallonshi Ummi tayi tace "ashe kayi manquén (missing) abinci na?"

Kallonta yayi ita kuma tayi k'asa da kanta, suna kammalawa suka koma falo suna
kallo, Islam da Salman na hira Ummi kam na jinsu har bacci ya d'auketa.
Islam ma bacci tayi saida Salman ya kallesu yace "dole kuyi bacci tun yanzu, tunda
kun gaji."

Islam ya d'auka ya kaita d'akin Ummi ya dawo ya d'auki Ummi ya kaita d'akin shi,
dan baya so ya bar wata k'ofa da zata falassa zaman da suke.

Yana direta akan gadon ta tashi a tsora ce tana fad'in "miye haka, ya zaka kawo ni
nan bayan ga d'aki na can?"

Mik'ewa yayi ya nufi wadrob ya bud'a ya d'auko kayan bacci zai shiga toilet ya juyo
yace "karki fita daga d'akin nan."

``` Salman kenan Ummin ce zaka bawa umarni haka```😏


05/03/2019 à 17:32 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

*SADAUKARWA GA DUKKAN MASOYAN WANNAN LITTAFI, INA YINKU KUMA INA SONKU SOSAI*

_MY HEENAT TACE WAI MAI TAURIN KAI *SALMAN BA*NA UMMI* NI MA SUNA SANI DARIYA_😍

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

7⃣1⃣7⃣2⃣
7⃣1⃣_7⃣2⃣

Ummi na ganin ya shiga toilet ta bishi da harara tana fad'in "kaji min mutum dan
Allah kawai sai na kwana a d'akinka, na san meka shirya min."

Fita tayi daga d'akin ko rufe k'ofar ba tayi ba dan kar yaji fitarta ma, kai tsaye
fridge ta nufa ta bud'a ta d'auki madara tasha ta mayar ta d'auki ruwa ta kora
dasu, zata rufe robar ruwan ta fad'i ruwan suka zuba, ajewa tayi ta nufi cuisine
dan d'auko abinda zata goge a rashin tsammani ta taka ruwan da suka fallatsa in da
ba tayi zato ba, sai ko sulb'i ya kwasheta tsaf ya ajeta k'asa ji kake timm.

K'ara tayi lokaci d'aya kuma ta kama bakinta tayi shiru, dafa fridge d'in tayi ta
tashi tana kallon ruwan, Salman ne ya fito d'aure da towel a k'ugunshi gabanta ya
fad'i saboda ganin ai niyin surarshi duk a mummurd'e, fizgota yayi da k'arfi bai
tsaya da ita ko ina ba sai d'akinshi, wurgata yayi akan gado ya koma ya rufe d'akin
da key ya kashe wutar d'akin.

_💃💃💃💃💃 FIRST NIGHT_

_MY HEENAT CE TA KWAB'E NI TACE "HABA MY MEERA ME YASA KIKA FIYA AZARB'AB'I NE WAI?
KI BARI MU GANI MANA"_

Ummi na ganin haka ta tashi da guda ta mak'ale a jikin bango ta manta da raunin
dake jikinta, Salman kam kallonta yayi yace "nace karki fita daga d'akin nan amma
sai gashi kin fita, na d'auka kwanan baya kince zaki dinga jin magana ta"

"Ni na rasa miye Alhaji ya gani a jikinki da har yayi tunanin kin isa aure, bayan
ke kuma har yanzu ba kida hankali."

Jin bata amsa masa ba yasa ya d'auko kayan baccin shi daga toilet, ganin yana
shirin zare towel d'in daga jikinshi yasa Ummi juyawa tana kallon bango ta d'aga
masa hannu ta baya tana fad'in,

"Miye haka malam? dan Allah ka rufa min asiri kar kasa naga ciji ina zaman lafiya
na."

Kallonta Salman yayi cikin takon izza ya k'araso wajenta tare da juyota da k'arfi
ya had'ata da bango yana kallon fuskarta yace "miye kuma ciji?"

Sai lokacin ta d'aga idonta ta kalleshi sai dai yayi kusa da ita sosai, dan haka ta
fara in ina " a...amm....amm...e...bbb ba komai"

Gaf da ita ya matso ya had'a hancinta da nashi numfashin su na gauraya dana juna
tare sark'a hannunshi ta bayanta ya rike kunkuminta ya had'a k'ugunsu waje d'aya,
hannayenshi yasa a jikin bango ya dafe gaba d'aya ya rufeta ko ganinta ba ayi.

Cikin wani irin yanayi ya mata magana "zaki fad'a min miye ciji, ko sai na nuna
maki ciji ganin idonki?"

Tana d'aga idonta k'wallan da suka taru suka zubo, gaba d'aya ta rasa iskan
shak'awa ga takura da matsatsi ga bak'on abinda taji kusa da k'ugunta yana tab'a
ta, ga kuma tambayar daya mata tare da cewa zai nuna mata ciji, da kyar ta fara
fad'in,

"A..ddd....dan" kawai sai Ummi tayi luuu tana shirin zubewa k'asa, cikin sauri
Salman ya tallabe ta yana kallon fuskarta cike da mamaki, kallona yayi yace
"yarinyar nan fa suma tayi."

D'aukarta yayi ya shinfid'e akan gado sannan ya fara saka kayanshi yana ci gaba da
kallon fuskarta yana matuk'ar mamakin suman da tayi, tab'e baki yayi yace "matsalar
had'a hanya da k'ananan yara kenan, wacce ta suma saboda kusancin da muka samu ni
da ita, to ina ga na kusanceta kenan sai mutuwa kamar yanda na fad'a."

Gefenta ya zauna tare da shafa mata ruwan daya d'auko a falo, a hankali Ummi ta
bud'a idonta kamar mai jin bacci, tana had'a ido da Salman ta zabura ta mik'e zaune
tana fad'in "wayyo Allah dan Allah ka rabu dani wallahi ni ba 'yar iska bace."

Rumgumeta yayi a jikinshi sosai tare da d'ora bakinshi a kunnenta ya fara fad'in
"ya isa haka Ummi ki nutsu babu abinda zan maki, na kawo ki nan ne saboda Islam
bana so taje ta fad'a cewa ni da ke kowa a d'akin shi yake kwana, kin santa da
surutu shiyasa na kawo ki nan."

Gaskiya kam ta gamsu da abinda ya fad'a dan haka tayi shiru tana shak'ar k'amshin
jikinshi tana sauke numfashi a hankali, bata sake motsawa ba har bacci ya d'auketa
a k'irjinshi.

Gyara mata kwanciya yayi ya mata addu'a yana kallonta na d'an wani lokaci, kafin ya
mik'e dan ya gabatar da nafilfili dan kusancin da suka samu da ita yanzu yasa
service d'in shi ya fara sauka, kuma idan ya ci gaba da zama haka to wani abu zai
iya faruwa amma duk da haka saida naga ya b'alli maganin nan yasha kafin ya fara
sallah.

```ALLAH SARKIN DAD'I IN JI B'ARAWON TAKAND'A```.

Har asuba Salman bai idar da sallah ba, saida yayi sallah asuba sannan ya kwanta
akan dardumar bacci ya d'auke shi.

K'wank'wasa k'ofa ne ya farkar dasu a tare suka tashi zaune suna kallon juna,
Salman ne ya mik'e cikin sauri dan jin muryar Islam na kiran sunan aunty Ummi, yana
bud'ewa ya kalli Islam yace "Islam kin tashi?"
Cikin shagwab'a tace "na tashi ina aunty Ummi take?"

Gefe ya matsa tare da nuna mata ita yace "wuce ciki"

Tana shigowa ta haye saman gadon tare da jan zanin da Ummi ke rufe a ciki ta
kwanta, Ummi ce tace "ke tashi kiyi sallah"

Bud'a idonta tayi tace "aunty nayi sallah fa"

Kallon tuhuma Ummi ta mata tace "kai Islam yaushe kika tashi?"

"Allah ko aunty nayi lokacin dana tashi fitsari sai naji ana sallah, kawai nima sai
nayi."

"To naji kwanta muyi bacci" Ummi ta fad'a tana sake kwantawa, Salman na tsaye yana
kallonsu ganin sun sake kwantawa yasa shi kuma ya fita daga d'akin ya koma falo ya
kwanta kan doguwar kujera tare da rufe ido.

A hankali yake jin abin kamar daga sama ya kuma rasa ta ina yake fitowa, zaune yayi
yana k'are ma d'akin kallo saidai baiga komai ba, sake kwantawa yayi amma har yanzu
yana jin abun ruf da ciki yayi yana k'ara tusa kanshi cikin kujerar yana shak'ar
k'amshin, sai lokaci ya tuna da kujerar da take zama ce tunda ta ji ciwo.

Idonshi a rufe yace "wannan wane irin turare ne mai rikita mutum idan yaji k'amshin
sa?"

Haka ya dinga birgima akan kujerar tsikar jikinshi na tashi yana dad'a k'ank'amewa
har bacci ya d'aukeshi marar dad'i.

_AH TO FANS DAI SUKA CE WAI ANAYI SUNA JIN DAD'I_

Bai jima ba ya tashi saboda shi kad'ai ya san me yake ji, daki ya shiga har yanzu
bacci suke abinsu, toilet ya shiga yayi wanka ya fito ya shirya cikin k'ananan kaya
bleue riga da bak'in wando da takalma sau ciki colour rigar, tsaf ya fito
had'add'en guy shi ya d'auki tabarau irin na 'yan zamani bak'i ya kifa, turaren
Ummi ya dauka yasa aljihu sannan ya k'araso wajenta ya sunkuya cikin kunne ya rad'a
mata,

"Hajia Abu tashi rana fa tayi sosai"

Ummi na tashi taga kamar a mafarki ne take yanda taga Salman ya had'e, shirun da
tayi tana kallonsa ne yasa yace "ki shiga toilet d'ina kiyi wanka zan d'auko maki
kaya d'akinki."

Fita yayi ta bishi da ido, haka ta shiga toilet d'in tana mai k'ara jin haushin
Nuseiba dan tana kallonshi taji ta tuna da ita, ji take yanzu ace duk wannan gayun
da kyawu na yaya Salman ba zata mallakeshi ita kad'ai ba.

```A YAU GA BANZA SUNAN WANI UNGUWAR MU```🤣


05/03/2019 à 17:33 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

*SADAUKARWA*
*Ga*
_Aunty Hawa_
_Aunty Hawa Jamil_
_Huseina_
_Fiddausi_
_Hussylurv_
_Hakeema ta_
_Fateema mom dady_
_Sister Ruky_
_Choukra_
_Salma Abdrur-rahman_
_Maman Samha_
_Kakata Haleema_
_My Lissa_
_My Heenat_

```ALLAH YA BAR MIN KU MASOYA NA INA K'AUNAR KU```😍😍 *JE VOUS AIME*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

7⃣3⃣7⃣4⃣
7⃣3⃣-7⃣4⃣

Haka Ummi ta fito daga wanka sanye da rigar wankan Salman, amma babu kaya babu
Salman d'an k'aramin tsaki tayi tace "kaji wai har yanzu d'auko kaya gashi ko brush
banyi ba."

D'akinta ta nufa rik'e da kayan data cire tana fad'in "yanzu haka ma ya manta da
alamarina ya shiga sabgar gabanshi."

Tana shiga ta watsa kayanta saman gado ta bud'a wadrob ta d'auko wata doguwar riga
fara mai siraran hannaye tare da bras da pants black, drower ta bud'a ta d'auki
coton sannan ta saka tana sawa ta cire rigar wankan ta jefa saman gado tana shirin
d'aukar bras taji motsi a bayanta, da k'arfi ta juyo take tsoro ya bayyana a
fuskarta ganin Salman ya fito daga toilet rik'e da brush da maclean da kayan
jikinta a hannu.

Kasa magana tayi sai hannu da tasa ta rufe k'irjinta wanda Salman ke kan kallo,
bud'a baki yayi yana so yayi magana amma ya kasa "aaaaaaaaa" kawai yake fad'a haka
ya fara takawa yazo ya aje kayan akan gado hanyar fita ya nufa amma sai ya juyo
yana kallon ma zaunan Ummi, da sauri ta juya tana kallonshi cikin tsiwa tace,

"Wai dan Allah miye haka? ka fita mana"

Gaf da ita ya matso yana kallon idonta duk da ta sauke nata k'asa, cikin taussasan
murya yace "Ummi zaki iya...?" kuma sai yayi shiru a hankali ta d'ago kanta ta
kalleshi.

Rintse ido Salman yayi dan ba zai iya hakura ba yana bud'a ido yasa hannayenshi ya
tallabo fuskarta sannu sannu yakai bakinshi a nata bakin ya sumbata, ya d'auka zai
iya tsayawa daga nan amma ina saiya k'ara had'a bakinshi da nata ya fara tsutsa
cikin salo, daga a hankali sai ya fara gaggawa da sauri, k'afafunshi ne yaji sunyi
nauyi jikinshi b'ari kawai yake idonshi rufe a yanda yake ji babu wanda ya isa ya
dakatar dashi yau d'in nan.

A hankali ya lula da ita akan gado hannayenshi kam akan k'irjinta kamar zai cirasu,
Ummi ta fara jin zafi dan haka tayi shirin k'watar kanta, abu fa ya ta'azzara ni
dai jiri ma ya fara d'ibata sai My Lissa na mik'ewa biro danta ci gaba da rubutun,
ma chérie Hakeema kuma ta b'allo paracétamol ta ban na had'iya.

Ummi kam kamar gunki dan har yanzu bata yarda da gaske ne hakan ke faruwa ba, dan
ta san yaya Salman ba zai aikata haka ba, jin abun ya fara girma yana shirin kai
hannunshi ga mararta yasa Ummi ture Salman daga jikinta tare da tashi cikin sauri.

Durk'ushewa yayi gabanta amma kanshi k'asa ya kasa d'agowa, saida tayi nesa da shi
ta tsaya tare da rufe jikinta da rigar wankan nan ta fara magana cikin shed'a sama
sama,

"Dama haka kake ban sani ba, ashe duk cika bakin nan na banza ne, tirr" ta fad'a
tare da kau da kanta, ci gaba tayi da cewa,

"In dai haka kake to baka dace da girman kai ba, banyi tunanin haka daga gareka ba,
kuma ka sani wallahi koda ina cikin tsarki ba zan tab'a baka kaina ba, domin kuwa
kana min kallon k'ask'anci, na san zaman mu ba zai d'ore ba dan haka zan ci gaba da
ajiyar budurci na dan na kaishi in da ya dace."

Tana fad'a ta shiga toilet ta barshi nan, yanda kanshi ke sarawa ga jikinshi rawa
kawai yake a daddafe ya kai d'akinshi ya d'auki maganinshi saida ya had'iyi maganin
sannan ya shiga toilet ya kifa kanshi a pampo ya sha ruwa.

Fitowa yayi daga d'akin saboda har yanzu Islam bacci take, kai tsaye motar shi ya
shiga ya kifa kansa a stiyari ido rufe, kalaman Ummi ne kawai ke dawo masa wai "
wallahi koda ina cikin tsarki ba zan tab'a baka kaina ba."

Kuma wai "zan kai budurci na a in da ya dace"

"Waye ya dace kenan daya wuce ni mijinta?" babu amsar tambaya.

Ya jima sosai a haka kafin ya bud'a idonshi cikin muryar tausayi yace "Allah ka
kare ni daga aikata ba daidai ba"

Wasu zafafan hawaye ne suka zubo a kumatunshi, gogewa yayi tare da tayar da mota
ya fita.

Yana saman hanya ya kira Khamis ya tambaye shi yana ina, cewa yayi "ina gida amma
yanzu zan fita, zanje gida wajen su Mama"

Cikin dakusashiyar muryarshi yace "ok jira ni ina zuwa yanzu."

"To sai ka zo" ya fad'a a takaice.

Yana zuwa Khamis ya fito suka wuce, a hanya ne Salman ne ya kalli Khamis yace
"Khamis dan Allah ka taimaka min, ka sanar dasu Abba ina neman auren Nuseiba
wallahi bada wasa nake ba."

Cike da kosawa Khamis yace "Salman na fad'a maka ka daina sani cikin maganar nan,
idan fa ka fad'a babu wanda zai hana ka auren Nuseiba amma ka tsaya ni kana takura
min."

Cikin damuwa Salman yace "me yasa ba zaka gane ba Khamis? ina cikin wani hali kuma
ina buk'atar taimako wallahi bana so na ci gaba da zama da yarinyar nan a gidan nan
mu kad'ai, in ba haka ba ban san mi zai biyo baya ba."

"Khamis yau saura kad'an na aikata abun kunya, saura kad'an na jawa kaina raini,
saura kad'an na aikata abinda zai dameni a gaba, saura k'iris na kusance ta."

Cikin raini Khamis yace "wai raini, kai a ganinka wannan ne raini?"

"To bari kaji, wallahi ko yanzu in kayi wasa to ina baka tabbacin cewa abinda ya
faru a baya shine zai sake faruwa a yanzu, dan tabbas sai kaga likita."

"Cousin, kayi abinda ya dace da kai kafin ka jefa rayuwarka cikin matsala, kana da
mata dan haka banga dalilin da zaisa ka bari ciwo ya illata ka ba."

"Malam ka sauke girman kai da izza ka kwashi albarkatun dake tattare da mace, Ummi
yarinya ce sosai idan aka had'ata da kai, zaka iya tafiyar da ita yanda ranka yake
so domin kuwa k'wace goriba a hannun kuturu abune mai sauk'i."

Girgiza kai yayi yana kallon gabanshi yace "baka san wacece wannan yarinyar ba
shiyasa, ka san ma mi tace min?"

"A'a" kallonshi yayi yace "tace ba zata bani kanta ba saboda ban dace ba"

"Hahahaha, to ai gaskiya ta fad'a saboda yanda kake cin magani haka wacece zata
yarda ta baka kanta? ai su mata saida rarrashi da lallami sannan idan kayi sa'a su
baka ka lasa."

Cike da mamaki yace "bayan rarrashin ma sai kayi sa'a?"

Dariya Khamis yayi yace "sosai kuwa, tunda kayan marmarin suna gurin su."

Kai ya girgiza yace "wannan k'ask'anci ai yayi yawa, bayan ma jikina da zata gani
saina tsaya ina lallab'ata bayan matata ce sadaki na biya, kuma a haka ace wai sai
nayi sa'a haba."

Kallonshi Khamis yayi yace "kai ma ai jikinta zaka gani, ko kuwa?"

Tabe baki yayi bai sake magana ba har suka kai gidan, da sallama suka shiga sun
samu su Mama duka a tsakar gida suna 'yan aikace aikace, gaisawa su kayi kafin suka
zauna.

Mama ce ta fara kiran "Rumana, Rumana" daga cikin d'aki ta amsa da "iye"

"Ke ki kawo ruwa"

"To" ta fad'a a takaice, Salman kam takaici kawai yake wai ace mahaifiyar ki ta
kira ki kice mata iye babu ladabi babu girmamawa, wannan shine dalilin da yasa baya
san shiga harkarta ma.

Haka ta fito gantsar gantsar ta aje masu ruwa da wata doguwar rigarta ko d'an kwali
babu a kanta, ko kallon ruwan Salman baiyi ba dan yanda yaga kanta a cunkushe yaji
zuciyarshi ma na tashi, "ina kwana".

Ta fad'a tare da juyawa zata koma d'aki, cikin fad'a Salman yace "ke ina d'an
kwalinki kike yawo haka?"

Cikin jin kunya tace "yana d'aki"

"Oho shine kike yawo haka? to in kika sake bari mu kayi ido biyu dake haka wallahi
saina k'ona gashin nan"

Rumana kam dad'i ne ya kasheta dan wannan tsananin na yaya Salman shine yasa take
sonshi, dan a tunaninta idan ta aureshi zata rik'eshi gam tsananin shi kuma zaisa
ya d'auke kanshi daga wasu matan.

Tana shiga d'aki ya kalli Maman Nuseiba yace "Mama ina Nuseiba ne ko bata nan?"

Cewar Mama "tana d'aki kam kuma na san tana jinka, shiru dai tayi"

Shiru yayi har Khamis ya gama abinda ya kawoshi suka tashi zasu wuce, saida suka
kai k'ofar gida Nuseiba ta fito tana fad'in "ina kwana yaya Salman?"

Juyowa yayi yana kallonta yace "ashe kina ciki kika yi banza dani?"

Wani fari tayi da ido mai kashe zuciya tace "lah yaya Salman ba haka bane, kawai
dai ina so mu gaisa ne ba'a cikin mutane ba"

Shagala yayi da kallon bakinta daya sha pink d'in ja leb'e (in ji uncle d'i na),
hira suka fara tab'awa suna dariya Khamis kam ya gama k'ulewa ganin yanda take wani
fari da ido na kissa, haushi ne ya kamashi yace "kaga malam dan Allah wuce mu tafi,
ke kuma wuce gida"

Saida ta harare shi ta k'asan ido tare da ji a ranta cewa yana mata bak'in ciki ne,
ciki ta shiga su kuma suka wuce.

Tunawa da Salman yayi yaune ranar komawar Ummi asibiti yasa ya dawo gida suka
shirya tare da Islam suka kama hanyar asibiti, suna zuwa suka nufi d'akin da zai
sada su da wajen likitar data duba Ummi ranar.

Layin da suka gani yasa su tsayawa suna k'ara kallon mutanen dake wurin, Salman
mota ya koma kafin layin ya rage, mutane na shiga kuma suna fitowa dan danan haka
yasa layin ya ragu sosai, mutane uku suka rage su Ummi su shiga Salman na ganin an
kusa kawowa garesu ya fito daga mota ya zo.

Suna haka wani kyakyawa kuma matashin likita ya fito daga wani d'aki kusa dasu,
yana ganin Ummi ya washe baki tare da fad'in "lah mutuniyar kece kika dawo? a to
bari na kai sak'on nan na dawo na rik'e ki dan na san yauma ba zaki tsaya ba."

Murmushi kawai ta masa shi kuma ya wuce d'aya d'akin, Salman kam kamar a tab'a shi
ya fashe saboda cika, an d'an d'auki lokaci kafin Ummi ta mik'e zata shiga, cikin
fushi Salman ya fizgo hijabinta yana fad'in "waye waccen?"

Saida ta kalleshi sama da k'asa tace "ban gane waye waccen ba?kai baga ko waye ba
ko baka iya fahimtar kayan aikin mutane?"

"Kamar zai bigeta kuma dai ya tsaya tare da fad'in "ina tambayar ki kina tambayata,
ki fad'a min miye tsakanin ki dashi?"

Ummi kam tuna Nuseiba tayi da irin haushi da k'uncin data shiga saboda su, dan haka
tace masa "ayya ai ya taimaka min ne ranar da muka zo nan shi ya rik'e ni aka min
d'inki da allura."

"Ya rik'e ki" wucewa tayi ta barshi nan, bin bayanta yayi Islam kam na zaune daga
waje da k'yar Ummi ta mik'a k'afarta dan a cire mata zaren da aka mata d'inki,
saida Salman ya matse ta ya tutsa kanta a cikin k'irjinshi sannan aka fara d'ebe
mata.

Ana gamawa Ummi ta d'ago kanta fuskarta duk ta jik'e da hawaye da majina, Salman
kam duk rigarshi ta jik'e sai kuma ta bashi tausayi haka aka gama masu suka kama
hanyar gida.
Daidai *Maradi Store* yayi parking, Islam ya kalla dake baya yace "Islam muje ko."

Fita tayi shi kuma ya kalli Ummi yace "ki jira anan muna zuwa yanzu" har zai fita
Ummi tace "ni kad'ai zan zauna, me yasa ba zamu je tare ba?"

A dak'ile yace "banga anfanin zuwanki ba, idan kuma kina da sak'o ki kawo na siyo
maki?"

Ba tare data kalleshi ba tace "ina da amma dole sai in ni naje da kaina."

Bud'a murfin motar yayi yace "sai kiyi ta zama anan to"

Ta jima zaune kafin suka fito daga ciki, ledar hannunshi ya mik'a mata tana karb'a
ta bud'e farin ciki ne ya bayyana a fuskarta ganinta kayan k'walam da mak'ulashe,
bata tsaya b'ata lokaci ba ta d'auki wata chocolat ta fara sha, jefi jefi Salman ya
kan kalleta yana mamakin yanda ta kasa masa godiya, amma Islam ma dake k'arama ta
masa tun kafin su fito, ya san ba daga tarbiya bace kawai dai tsarinta ne haka,
haka har suka isa gida.

Ko abincin rana Ummi bata ci ba saboda ciye ciye da tayi, da yamma ma kam suna
zaune farfajiyar gida ita da Islam Jawahir ta shigo a hargitse, Ummi ce tace "ke
kuma lafiya haka, daga ina kike kamar an koro ki?"

Saida ta zauna ta cire nik'ab da hijab tace "kedai bari wallahi, hadari ne a gari
shiyasa nayi saurin k'arasowa karya riske ni a hanya"

Sai lokacin Ummi ta kalli sama tace "hadari fa, kinga muna nan sai a tashi duniya
bamu sani ba."

Dariya Jawahir tayi tace "idan aka kawo gareku ai zaku sani" kafin Ummi tayi magana
iska ya taso da k'arfi, dan haka suka koma ciki nan fa aka fara ruwa kamar da bakin
k'warya dan dama an kwana biyu ba ayi ba.

21:00 aka d'auke ruwa ba jimawa kuma Salman da Khamis suka shigo gidan, Ummi ko
kallon Salman ba tayi amma ta gaishe da Khamis, haka ta shirya Islam suka tafi tare
da Jawahir, tunda Salman ya fita ya matsu ya dawo gidan dan sosai yaji haushin
banzan da tayi da shi gaban mutane.

Yana dawo har cikin d'akinta ya shiga amma abun mamaki kwance take tana hawaye,
tunani yayi ko dan Islam ta tafi ne, matsowa yayi cikin muryar fad'a yace "Ummi
naga har yanzu ba kya neman zaman lafiya da ni, ke kinfi k'arfin ki gaishe ni ko?"

Zuciyarta a wuya take dama dan haka ta harareshi sama da k'asa tare da tsaki ta kau
da kanta gefe, mamaki ne ya bayyana a fuskarshi cikin b'acin rai da zafin nama ya
cabko hannunta yana fad'in,

"Wa kike harara, ni kike wa tsaki?"

Cikin muryar kuka da fitar hayyaci Ummi tace "ka sake ni mugu kawai azzalumi,
wallahi sai Allah ya saka min kuma wallahi ka auri Nuseiba sai zaman gidan nan ya
gagareta dan babu abinda zai hana ni ci mata uwa, mugu kawai kana fad'a wai ni nama
k'aramta amma kuma shine zaka auri yarinyar dana bata shekara hud'u, dama ita kake
so shi yasa zaka aure ta."
Sakinta Salman yayi dan yanzu kam ya fahimci abinda ke cikin zuciyarta ne ya fito
fili, lallai har yanzu tana kishi da shi to amma me yasa.?

D'akinshi ya koma yana tunani akan abinda ta fad'a har bacci ya d'aukeshi, ita ma
bacci ne yayi gaba da ita.

💃💃💃💃😍😍😍😍
05/03/2019 à 17:33 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

7⃣5⃣7⃣6⃣
7⃣5⃣-7⃣6⃣

Tunda safe Ummi ta tashi ta had'a abin karyawa iya bakinta ta ci, tana kammalawa
tayi wanka ta komo falo ta zauna tana kallo, Salman ne ya fito daga d'akinshi
singlet da dogon wando da alama sport zai je.

Ko kallonshi Ummi ba tayi ba haka ta zauna har ya dawo saidai baiyi gumi ba saboda
ansha ruwa jiya, d'aki ya shiga kai tsaye ya shiga toilet dan yin wanka, yana
fitowa ya shirya cikin k'ananan kaya sannan ya fito falon.

Ba tare daya kalleta ba yace "tunda har yanzu ba kiyi wayon gaida mutane ba, to ki
kawo min abinci na."

Bata kalleshi itama tace "iya bakina kawai na dafa kuma na cinye."

Wani kallo ya watso mata kafin yace "Ummi karki saka ni abinda banyi niyya ba, ki
kawo min abinci na kafin ranki ya b'ace."

Saida ta watsa masa harara ta murgud'a baki sannan tace "kaji min mutum dan Allah,
to wallahi ba zai yiwu ba haka kawai ni da ciyar da kai kuma wata da morarka,
kaje mana amaryarka ta baka abincin."

Dariya ce ta sub'uce masa bai shirya ba, sosai yake dariya har da rik'e ciki yake,
Ummi kam ta gama cika dan haushi kawai sai taja dogon tsaki, shiru Salman yayi yana
kallonta kafin ya mik'e tsaye yasa hannuwa aljihu yace,

"Ok zan tafi naci a waje, amma fa karki manta Salman d'an dangi ne, iya gidansu
Khamis ma kad'ai zan iya cika ciki na har saina ture."

Yana shirin ficewa Ummi tayi karaf ta rik'e hannunshi tana fad'in "a'a dan Allah
kayi hak'uri to zan dafa maka abinda kake so."

Kallonta yayi ya kalli hannun data rik'e yace "sake min hannu malama"

"Dan Allah kayi hak'uri wallahi zan yi." ta fad'a kamar mai shirin fashewa da kuka,
dawowa yayi ya zauna bisa kujera har yanzu tana rik'e da hannunshi, kallonta yayi
sosai kamar yana so ya fahimci wani abu a tare da ita kafin yace,

"Mi amarya ta ta miki ne haka? tun jiya kike masifa a kanta."

Dama kamar jira take sai kawai ta fara kuka kamar an k'wak'wale mata ido, Salman
kam shiru yayi yana sauraranta har ta gama, kusan minti shabiyar tayi tana kuka
kafin ta bawa kanta hak'uri ta share hawaye ta kalleshi tace,

"Yaya Salman wai da gaske aure zaka k'ara?"

Cike da gamsarwa yace "e aure zanyi, miya faru?"

Shan majina ta fara tare da saukowa daga kan kujera ta zube akan gwiwoyinta biyu
ta had'e hannayenta biyu alamar rok'o tace "yaya Salman dan Allah kayi hak'uri
karka k'ara aure, wallahi ni kuma nayi maka alk'warin zan canja zan zama yanda
kake so kuma zanyi duk abinda kake so."

Hannayenshi ya d'ora akan gwiwoyinshi yana kallonta cikin mamaki yace "Ummi me yasa
ba kya so, miye matsalarki idan na k'ara aure?"

Kuka take sosai tace "ban sani ba nima yaya Salman, kawai dai bana jin dad'i idan
kace zaka k'ara aure zafi nake ji a cikin nan da k'unci." ta fad'a tare da d'ora
hannu a k'irjinta b'angaren zuciyarta.

Wani irin murmushi Salman yayi najin dad'i yayin da yake fad'a a zuciyarsa "lallai
wannan so ne kuma Ummi tayi nisa, kawai dai ta kasa fad'a kamar yanda nima na kasa
fad'an komai."

Da hannu ya mata alama ta zauna kusa dashi, tana zaunawa ya kalleta yace "Ummi da
gaske kike fad'an maganar nan?"

Cikin kuka tace "wallahi da gaske nake yaya Salman, ba zan sake maka rashin kunya
ba."

Shi kam kamar yayi dariya amma ya rik'e, cewa yayi "ok tunda kince haka na yarda,
amma a bisa wani sharad'i."

"Na yarda koma wane iri ne in dai zai hana ka k'ara aure."

"Ok ba zan k'ara aure ba in dai zaki dinga jin magana ta, amma ki sani duk sanda
kika min ba daidai ba to tabbas a satin nan k'anwarki zata shigo gidan nan a
matsayin amaryarki."

Saida ta harareshi ta gefen ido tace "na yarda, kuma wallahi idan nayi abinda kake
so kuma kace zaka k'ara aure to wallahi...." mik'ewa tayi danta had'a mashi abin
karin, da sauri ya rik'e hannunta yace,

"Wallahi me?"

Saida ta nuna shi da yatsa tace "saina kashe ka, dan ba zan had'u ni da wata a
kanka ba." Fak'at 😳

Wucewa tayi Salman ya bita da ido "anya yarinyar nan ba zata kashe ni ba kuwa in
ina maganar auren nan?"

_Ah to koma dai miye ni dai ina daga nan_

Haka ta wuni ita d'aya a gidan jikinta yayi sauk'i sosai shi yasa ma babu wanda
yazo gidan dubata saidai kiranta a waya kawai, har dare haka ta kammala 'yan aikace
aikacenta kafin Salman ya shigo gidan, kai tsaye d'akinshi ya shiga yayi wanka yana
fitowa ya shafa mai, tsaye yayi yana kallon kayan da zaisa kafin daga bisani ya
yanke wata shawara.
"Abule, Abule, wai Abu bata jine?" Salman ne fa ke kiran Ummi haka, Ummi dake
zaune falo tun kiran farko taji tasowa tayi tana fad'in "haba wallahi saina maka
rashin mutunci in kana kirana da wannan sunan."

"Gani" ta fad'a a tsaye, kallonta yayi dan bai san da shigowarta ba hankalinshi na
kan sak'on daya shigo wayarshi yanzu, ba tare daya kalleta ba yace "fiddo min kayan
da zansa."

Kallon ba kada hankali ta bishi dashi har ta bud'a wadrob d'in ta d'auko wasu bleue
noir rigar kamar singlet saidai hannuwan suna da fad'i sai dogon wando.

Aje masa tayi tana kallon wayar dake hannunshi, tashi yayi ya aje wayar dan yasa
kaya, sai kawai idonta ya sauka kan chart d'in da suke da mai wannan sunan *Reine*,
da sauri ta d'auki wayar tana kar'ema photon Nuseiba kallo wanda ga dukan alama
yanzu ta aiko shi, a k'asa kuma ta rubuta,

__kana da girma a wajena yaya Salman, ba zan iya had'a ido da kai ba koda a photona
ne._"

Jin hawaye sun taho mata ne yasa ta aje wayar tana kallonshi, kallonta yake shima
kafin yace "ya dai lafiya?"

"Allah zai saka min in har kaci amana ta, kuma wallahi zanje na samu Nuseiba har
gida sai naji dalilin da yasa take kula ka, azzalumai macuta kawai."

Zata fita ya rik'o hannunta tare da fad'in "ke kina hauka ne, wai mi yake damunki
ne?"

Cikin b'acin rai ta fizge hannunta tace "lâche moi (sake ni)"

Tana fita d'akinta ta shiga ta fad'a saman gado ta fashe da wani kuka mai cin rai
da ban tausayi.

*Kishi kenan, zama da kishiya sai dole amma idan a kayi hak'uri to komai ya kan zo
ya wuce kamar bai faru ba, mu dinga saka hak'uri tare da tausar zuciyar mu da kuma
addu'a, dan ba kowace mace bace zata iya hak'urin ganin ta had'a miji da wata.*
_Allah kasa muyi kishi mai tsabta irin na matan Annabi (S A W)_

Yana saka kaya ya d'auki wayar yana kallon Nuseiba kafin yace "kiyi hak'uri ba zan
iya juran ganin hawayenta ba, in dai har a kanki ne take shiga k'unci to daga yau
ba zata sake b'ata ranta ba, ina son aurenki ne saboda kashe wata matsalata, amma
idan maganar so ake to Ummi ce a cikin zuciyata dama birnin raina, bana jin wata ko
wani abu kamar yanda nake jinta a cikin zuciyata dan haka daga yau komai ya k'are,
ba wai zumuncin mu ba saidai daga yanzu ba zan sake maki kallon wacce nake so na
aura ba, daga yanzu kin koma k'anwata kamar yanda kike a da, Ummi kuma zan ci gaba
da k'ok'arin sakata farin ciki da yardar Allah."

"Dole na guji b'acin ranta in dai har a kaina take kishi haka, ban san me take ji
ba amma da zan iya kwatantashi da abinda naji jiya lokacin da tace min wannan
likitan ya rik'eta, to tabbas ba k'aramin b'acin rai da tashin hankali take ciki
ba."

Yana fad'a ya canja sunan Nuseiba daga Reine zuwa Cousine Nuseiba kamar yanda yake
a sauran numbobin 'yan uwa, d'akin Ummi ya shiga sosai ta bashi tausayi ganin ta
dage tana kuka dan taji sauk'in abinda ke damunta.

Zaune yayi tare da d'agota ya d'ora kanta a k'irjinshi yana fad'in "haba Ummi duk
wannan kuka dan kinga photon Nuseiba ne? amma ai ni na maki alk'awarin na fasa ko?"
D'agawa tayi daga jikinshi cikin kuka tace "yaya Salman me yasa, me yasa nake jin
haka? wallahi ji nake na tsani 'yar uwata? "

Kai ya girgiza mata ya k'ara janyota ya rumgume yana cewa "shhhh, kiyi shiru kinji
ya wuce ba zan sake ba"

Cewa tayi "yaya Salman ba wai na hana ka k'ara aure bane, ni kawai bana so ne ka
auri kowace mace, ina ji da ina da iko a kanka to dana hana ka auren kowace mace a
duniya, yafi muyi zaman mu haka koda ma za kayi ta duka na wallahi ba zan gaji ba."

Ji yayi duk ya k'ara jin haushin kanshi in dai har tana jin haka a kanshi, to miye
zaisa ba zai zauna da ita ba ya kuma k'ara sonta fiye da yanda ita take sonshi.

Rarrashinta yayi tayi har tayi shiru kafin suka komo falo ta bashi abinci yaci,
dare nayi kowa ya kama hanyar d'akinshi, suna kaiwa k'ofar d'akunan suka kalli
juna Salman ne yayi murmushi yace,

"Kiyi bacci ba sai kin kawo min tea ba."

Shiru tayi tana kallonshi dan haka yace " kina buk'atar wani abu ne?"

Nan ma babu amsa dan haka ya matso kusa da ita yace "ko zaki kwana d'akina ne?"

Tana jin haka ta bud'a d'akinta ta shige, dariya yayi ya shiga d'akinshi shima
yana fad'in "tsoro kamar farar kura, ko taya zata fuskanci daren farkonta.?"

```Wannan aiki kuma ai ya rage naka ```😍


05/03/2019 à 19:30 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

_'YAN K'UNGIYATA INA JI DAKU_

```MY HEENAT, MY BK, MY SEEYA, K'AWALLIYA CEYMER, HAPSY, QUEEN BK, MY LISSA```😍❤😉

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

7⃣7⃣7⃣8⃣
7⃣7⃣_7⃣8⃣

Yau Ummi ita d'aya tayi break dan yau alhamis Salman na azumi, tana kammalawa ta
fara sharar falo da goge goge tana cikin goge dinning Salman ya fito cikin bleue
shadda, d'inki ya masa kyau sosai gashi sun dace da k'irar shi, tsaye yayi yana
k'arewa Ummi kallo data sha dogon wando da k'aramar riga, sun kamata sosai kayan
gashi kuwa Ummi dama dai bata da kyau na nunawa amma k'ira kam ko a mujjala za'a
iya bugata, tsaf rigar ta tsaya a k'ugunta daram wata hula ce a kanta irin mai
maganin sanyi sai dai tsakiyar kanta ta tsaya sai gashinta daya kwanta a bayanta.

Daf da ita ya matso yana ci gaba da kallonta, k'amshin turarenshi da Ummi taji ne
yasa tayi saurin juyowa karaf idonsu suka had'u, k'asa tayi da kanta tace "ina
kwana"

Yanda rabin k'irjinta ke waje wuyanta hannayenta gaba d'aya sun d'auki hankalinshi,
hannunshi yasa a hankali ya shafi wuyanta har damtsenta, jin yanda yake wani latsa
fatarta yasa tayi saurin janye jikinta tana kallonshi, kallon idonta yayi da suka
fara tona asirin abinda ke zuciyarshi cikin wata irin murya yace,

"Ummi bana so ki sake saka irin wannan kayan a gidan nan."

Kallonshi tayi cikin mamaki tace "saboda me, me yasa zan daina? naga ko a gidan mu
ina saka kayan da raina ke so bare kuma gidana."

Cikin mamaki shima ya kalleta yace "gidanki fa ki kace? inama laifin kice gidan
mijinki."

"E mana gidana, domin kuwa in da babu ni ba za'ace danan gida ba, haka da baka da
ni da ba za'a kiraka mai gida ba."

Gaf da ita ya matso yana mata wani shu'umin kallo yace "amma ai a zahiri ne mutane
ke ganin haka, amma a bad'ini har yanzu ke k'aramar yarinya ce baki cika cikakkiyar
mace ba."

Ummi kam kallon jikinta ta fara tun daga sama har k'asa sai dai bata fahimci komai
ba, kallonshi tayi tace "a hakan ne ban cika cikakkiyar mace ba? ina haka dani?"

"Murmushin gefen labb'a yayi yace "cikakkiyar mace bawai tana nufin mai k'iba ko
kyau ko ilimi ko iya gayunta da sauransu ba."

Rik'e k'ugu tayi tace "to kenan me yake nufi?"

Gashinta ya janyo yana wasa dashi kafin yace "zan fad'a maki ranar da kika cika
babbar mace, amma ba yanzu ba dan ba zaki fahimce ni ba."

"Ka fad'a zan gane ina da fahimta sosai."

Sakin gashinta yayi ya nufi hanyar fita, da sauri Ummi tace "in dai ban cika
cikakkiyar mace ba, to kaima baka cika ba..." shiru tayi saboda yanda ya juyo yana
kallonta, saida ya matso kusanta yace "ban cika namiji ba kike so kice?"

Shiru tayi tana kallonshi dan haka yace "ok muje na nuna maki ni namiji ne kuma na
gaske."

Hannunta ya kama zuwa cikin d'akinta, tana ganin sun doshi d'akin ta fara k'ok'arin
kwace hannunta, rik'eta yayi sosai yace "muje saina nuna maki"

Zubewa tayi k'asa tana bille bille tana kuka tana fad'in "a'a wallahi bana so dan
Allah kayi hak'uri wallahi kai namiji k'arya nake dama."

Ganin zata b'ata masa lokaci yasa ya kimkimeta sai d'akinta ya zubdata akan gado,
ganin yanda take kuka tana bashi hak'uri yasa ya rik'e dariyarshi wutar d'akin ya
kashe tare da dawowa wajenta yana kallonta yana cire ma b'allan rigarshi yana
fad'in "to wai miye na kukan? naga ke zaki zama babbar mace ni kuma zan zama babban
yaro."

Cikin kuka Ummi tace "ni d'in banza wallahi bana son na zama dan Allah ka k'yaleni
wallahi cikina ke ciwo ga baya na ma rik'ewa yake, ko kana so olcerta ta tashi ne?

Baya ya bata dan ya samu damar dariya tare da cire rigarshi har da singlet d'in
duka ya aje a gefen gado sannan ya mik'a mata hannu yana fad'in "zo nan"

Da gudu ta nufi toilet dan neman tsira, da hanzarinshi shima ya bita tare da
rik'ota, baiyi wata wata ba wajen wurgata saman gado yayo kanta gadan gadan, runfa
ya mata da k'irjinshi yana k'ok'arin had'a bakinsu waje d'aya, ganin idon Ummi duk
sun canja bakinta bud'e tana k'ok'arin maida numfashi amma ta kasa dan ji take
kamar ya danne mata ma shak'ar iska ne.

D'agata yayi ya koma gefe ya kwanta yana dariya yana fad'in "matsoraciyar kawai,
ashe bakinki na rufuwa, ashe akwai lokacin da kike rasa abin fad'a.?"

Ummi na tashi k'ofa ta nufa ta kunna wutar d'akin, juyowa tayi tana kallonshi tsaki
ta masa tana shirin fita yace "zo nan."

Daga jin amon muryarsa babu wasa dan haka ta dawo tayi tsaye tana kallonshi har
yanzu kuma kwance yake, "wa kike wa tsaki?"

Shiru tayi ta kasa magana dan haka yace "ok kimin tsaki san ranki kafin amaryata ta
shigo gidan."

Tana jin haka ta zube k'asa tace "dan Allah kayi hak'uri wallahi ba zan sake ba
daga yau."

Ba tare daya kalleta ba yace "to naji, tashi ki fita ki barni zan kwanta a nan."

Tab'e baki tayi ta yunk'ura zata tashi idonta suka sauka akan wani abu, gabanta ne
ya fad'i sosai mik'ewa tayi tare da nuna wajen tace "yaya Salman miye wannan, meya
ji maka ciwo anan wurin?"

Da sauri ya dafe wurin tare da tashi zaune amma bai tanka taba, a hankali Ummi tace
"yaya Salman dan Allah miya ji maka ciwo a wurin nan mai hatsari, ko kaima kayi
k'in ji irin na yara?"

"Ke bana san wannan tambayar kinji ko,wuce kije in da zaki"

Wucewa tayi jiki a sanyaye tana tunanin wannan wane irin ganganci ne ciwo a kusa da
mara ko tsoro ma baya ji, to wai mima yaji masa ciwon ne?"

Tashi yayi yaje gaban madubi yana k'ara kallon ciwon dake k'asan cibiyarshi wanda
shekara d'aya kenan daya same shi, kayanshi yasa ya fito daga d'akin tana zaune
yace "saina dawo."

"A dawo lafiya" ta fad'a a takaice shi kuma ya fice daga gidan.

Tana zaune rana ta fito sosai taji ana bubbuga k'ofar gida, cike da mamaki ta saka
hijab ta fito ta bud'e tana kallon mai buga k'ofar mamaki k'arara a fuskarta,
MANNIR ne tare da Alhaji gefe ta matsa tana fad'in "ku shigo ciki".

Ciki suka shiga Ummi har yanzu jikinta a sanyaye yake dan bata san da wacce Alhaji
ya zo ba, wuri suka samu suka zauna saida suka gaisa da Mannir sannan ta kalli
Alhaji a tsorace tace "ina kwana"

"Lafiya lau, kun tashi lafiya?"

"Lafiya lau muke, yasu Hajia suna lafiya?"

"Lafiya lau suke, amma basu san zan zo nan ba"

Shiru Ummi tayi tana sauraran abinda zai fad'a, shiru ne ya ratsa wajen na
dak'ik'u shabiyar kafin Alhaji yayi gyaran murya yace "Ummi na san kinyi mamakin
ganina a gidan nan ko?"

Cike da ladabi ta jinjina kai dan haka yace "ba abun mamaki bane, nazo ne dan naga
jikinki nima, sannan na shaida maki na daina fushi dake yanzu."

Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tana fad'in "na gode sosai Kakana"

Da hannu ya mata alama ta matso kusa dashi tana zuwa kanta ta d'ora akan gwiwarshi
tana hawaye tace "Alhaji ka yafe min, wallahi ranar ma babu abinda ya faru kawai
dai...." bai bari ta k'arasa ba yace "ya isa haka Ummi, nima nayi kuskure matakin
dana d'auka akan ki bai kamata ba ko kad'an, domin kuwa na sanki farin sani dan
rayuwar da ki kayi a gidana, tafi wacce ki kayi a gidanku yawa kiyi hak'uri kinji
ko."

Haka suka jima suna hira kafin suka tashi tafiya Alhaji ya k'ara mata nasiha akan
ta kula da mijinta sannan ta zama mai ladabi da biyayya ga mijinta.

Ummi taji dad'in yinin nan fiye da sauran yinin da 'yan uwa ke zuwa mata, haka ta
wuni cikin farin ciki da annashuwa.

*A GURGUJE*
11/03/2019 à 17:51 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

7⃣9⃣8⃣0⃣
7⃣9⃣-8⃣0⃣

Haka zaman nasu yake tafiya ba yabo ba fallasa, har yanzu babu abinda ya canja
daga zaman nasu sai dai abu d'aya shine yanzu Ummi tana yin duk abinda Salman ya
sakata, har yanzu Ummi ba tada sarau dan kuwa ko yanzu Salman yace mata kule to
kai tsaye za tace masa cas.

Amma tana mayar masa da yace zaiyi amarya kuma zata fara bashi hak'uri, haka Salman
ya samu yana wasa da Ummi son ransa ta hanyar k'ara aure, kullum soyayyar junansu
ce ke k'ara k'aruwa a tsakaninku sai dai har yanzu kowa baya yarda d'an uwansa ya
fahimta, haka suke zaune sai dai wani lokaci daga kallon da suke aikawa junansu ya
kan tona sirrin zuciyoyinsu.

Salman yayi niyyar ba zai fara fad'awa Ummi kalmar so ba,saboda sanin Ummi da yayi
zata iya watsa masa k'asa a ido idan ya fad'a mata, shi kuma a yanda yake jinta a
zuciyarshi dama sauran sassan jikinshi baya tunanin zai iya jurar rasata ko jin
rashin amincewarta daga bakinta.

Ummi ma haka ta zab'i ta b'oye ta barwa kanta ita kad'ai ba tare data fad'a masa
ba, tunda ta fahimci bata gabansa ko kad'an shi yasa ma zata ci gaba da b'oyewa har
lokacin da shima zai fara jin irin abinda take ji sannan ya fad'a mata.

A haka kuma warin auren su Ummi suke ci gaba da kula da cikinsu, Khairat, Nadiya
suna fama da laulayi mai tsanani su Jawahir kuma alhamdulillah za'a ce.
Har yau har gobe idan Ummi ta kira La Mama dan su gaisa, sai La Mama ta k'ara
jaddada mata akan ta kula da mijinta sannan saita fad'a mata wani abu da zata k'aru
da shi ko dan rayuwar gaba.

*WATA BIYU*

A lokacin ne su Jawahir suka fara shirye shiryen komawa makaranta, in da Ummi ita
ma ta nemi izinin Salman akan ya barta ta koma makaranta, sam Salman yak'i amincewa
yace sai tayi hankali sannan zata fara fita ma daga gidan.

Ummi tayi kuka tayi magiya tayi rarrashi amma sam yak'i yarda, dole Ummi ta hak'ura
ta shafa ma kanta lafiya, yayin da su Jawahir suka fara karatu sai dai suma suna
kewar Ummi sosai duk da tana gaba dasu a ajin, amma dai koba komai zasu dinga
had'uwa.

Tun lokacin sai Ummi ta sauya gaba d'aya ta daina walwala ba kamar da ba, yanzu duk
abinda Salman zai mata bata kula shi sai dai ta bishi da ido kawai, hakan ba
k'aramin tab'a Salman yayi ba dan kuwa farin cikinta shine nashi, amma yanzu gashi
ta daina gaba d'aya, dole Salman ya nemi mafita daga matsalar dan a ganinshi koda
ace ba abinda yake da iko a kanshi bane ai zaiyi k'ok'arin ganin ya sata farin
ciki, bare kuma yana da iko.

Ummi na zaune a falo tana kallo tare da uban tagumin data rabka Salman ya shigo da
sallama, kallo d'aya ta masa ta kau da kanta tana amsa sallamar, zaune yayi
kusanta yana kallonta, ledar dake hannunsa ya mik'a mata ta karb'a tana kallonsa ta
aje ledar dan a tunaninta irin kayan k'walam d'in da yake siyo mata ne.

Kallonta yayi yace "miye haka kuma? ya za'a baki abu amma ba zaki duba ba ki gani,
kawai saiki aje."

Ko kallonshi ba tayi ba ta d'auki ledar ta fara dubawa, take farin ciki ya


lullub'eta saboda ganin d'inkakken tenue (uniform) da sauran kayan makaranta da
duk abun da d'an makaranta zai buk'ata.

Fiddo kayan tayi ta mik'e tsaye tana gwadasu a jikinta bak'ak'e (tenue 'yan lycée
ne na moufida), riga iya gwiwa wacce ta bud'e sosai da gajerun hannuwa sai dogon
wando mai forme d'in slim da kuma hijab daya wuce rigar, sannan da nik'ab, cikin
mamaki tace,

"Wannan fa yaya Salman na miye?"

Murmushi yayi yana kallon tsantsar farin cikin dake kan fuskarta yace "naki ne"

Bud'a baki tayi cike da farin ciki tace "wow, yaya Salman amma naji dad'i sosai,
hakan kenan na nufin zan koma makaranta nima?"

Da ido kawai ya mata alamar Eh, cike da farin ciki ta k'araso wajenshi ta zube
k'asa tana fad'in,

"Kai amma yaya Salman naji dad'i sosai, Allah ya saka maka da alkairi, Allah ya
k'ara bud'i na alkairi, Allah bar min kai, Allah ya saka maka son...."shiru tayi ta
kasa k'arasawa.

Mamaki ne ya bayyana a fuskarshi tare da fad'in "ya saka min son mi?" kai kawai ta
girgiza alamar ba komai, mik'ewa yayi ya nufi d'akinshi ita ma haka, suna kaiwa
k'ofar d'akin Ummi tace,
"Yaya Salman yaushe zan fara tafiya?"

"Gobe mana"ya fad'a yana bud'a d'akinshi, murmushi tayi wanda ya bayyana hak'oranta
tare da dinple d'inta sosai, Salman dake k'ok'arin shiga d'akinshi ne tsaya tare da
dawowa yana kallonta, a hankali yasa d'an yatsarshi akan dinple d'inta ya latsa,
ita kam k'ura mashi ido tayi tana kallo yayin da shi kuma kasa had'a ido da ita
saboda tartsatsin da yake ji idan yana kallon idonta ma abota girma da fari.

Bai bar latsa kumatunta ba yace "Ummi na barki ki koma makaranta ne saboda tabbacin
da nake da akan ki, na san zaki kula da kanki sannan zaki karemin mutunci na dama
mutuncinki."

Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon cikin idonshi tace "insha Allah yayana, ba zan
tab'a baka kunya ba, sannan ba zanyi abinda zai shafi mutuncin ku ba, zanyi iya
bakin k'ok'arina wajen ganin na kare maku hakk'inku da yake kaina musamman ma kai."

Murmushin jin dad'i yayi yace "me yasa musamman ma ni?"

K'asa tayi da idonta cikin jin kunya tace "saboda kai mijina ne." tana fad'a ta
k'arasa shigewa d'aki tana dariya, Salman ma haka d'aki ya shiga yana jin wani
sanyi na ratsashi yana ji ina ma ace Ummi ta fad'a mashi kalmar so a matsayin
godiyar abinda ya mata.

Tun asuba Ummi da tayi sallah bata kwanta ba, tana gama had'a abinda kari ta d'an
gyara abinda zata gyara a d'akinta da falo dama cuisine, tana kammalawa ta shiga
wanka tana fitowa tsaf ta shirya cikin tenue d'inta.

Jakarta ta d'auko da hijab da nik'ab ta fito falo ta ajesu saman kujera sannan ta
nufi d'akin Salman dan ta tashe shi, da sallama ta shiga amma shiru bai amsa ba
alamar bacci yake, saida ta k'arasa har gabanshi ta k'ura mashi ido tana kallo
yana baccinshi cikin kwanciyar hankali.

Rumgume hannayenta tayi a bayanta a hankali tace "ina sonka yaya Salman, sai dai ba
zan iya fad'a maka ba, dan na san kai baka sona kuma ba zaka soni ba, amma zan ci
gaba da jiran lokaci na san zai zo."

Lek'a fuskarshi tayi taga sosai yake baccinshi dan haka ta sunkuya daf da k'eyarshi
ta sumbata, mik'ewa tayi tare da zura hannunta ta rufe hancinshi, da sauri ya juyo
da kanshi yana bud'a idonshi yana ganin Ummi ya tashi zaune yana ci gaba da
kallonta, murmushi kawai take masa kafin yace,

"Wannnan kuma wane irin tayar da mutum daga bacci ne?"

D'aga kafad'u tayi tare da d'aga gira sama alamar ba magana, saukowa yayi daga kan
gadon yana fad'in "saina ji kamar an sumbace ni a kaina ko?"

Bud'e baki tayi cike da mamaki, lokaci d'aya kuma tayi k'asa da kanta tana wuru
wuru da ido, gaf da ita ya matso yace "kece ko, ko dai akwai abinda kike b'oyewa ne
ban sani ba?"

D'ago ido tayi suka kalli juna, ja tayi da baya tana fad'in "haba dai sumbata fa?
sai kace wani jariri."

Toilet ya nufa yana fad'in "banyi mamaki ba dan kince haka, amma ki sani wani
lokacin ma miji yafi jariri buk'atar kulawa."

Kallonshi tayi tace "to, ni dai na san ana cewa namiji kamar k'aramin yaro ne, duk
in da kayi dashi can zaiyi."
Tsaye yayi yana kallonta kafin yace "kuma ke kin yarda da abinda aka fad'a d'in?"

Murmushi tayi tace "me zai hana ko, tunda mune ke jan ragamar."

Ganin ya tun karota yasa tayi saurin ja da baya tana fad'in "dan Allah ni dai kaje
ka shirya kar nayi late a zuwan farko."

Sai lokacin ya lura da kayan dake jikinta dan haka yace "oh, hakane fa, ok ki bani
5 minute ina zuwa."

Kallon agogon dake gefe gadon tayi tace "ah bon, 5 minute? Ok je t'atend."

Ciki ya shige ita kuma ta dawo falo ta zauna jiranshi, kallon agogo take lokaci na
tafiya amma Salman shiru bai fito ba, ido Ummi ta fiddo tare da mik'ewa tsaye tana
dafe da k'irjinta ganin 07:45, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in,

"Shikenan zuwan farko zan fara da late."

Hijabinta ta saka ta goya jakarta ta d'aura nik'ab, d'akin Salman ta nufa sai kuma
suka ci karo da juna, ido ya fiddo waje yana k'are mata kallo sama da k'asa kafin
ya nunata da hannu yace "ke kuma wannan shiga haka bak'a k'irin kamar wata 'yar
wuta."

Turo baki tayi duk da baya gani sannan tace "yaya Salman ka dubi lokaci fa ya wuce,
wallahi nayi retard."

Lokaci ya duba ya k'ara zaro ido yana fad'in "kai kai kai, lallai kam, to wuce muje
ina fatan dai kin karya?"

"Ni ban karya ba, kawai idan naje naci wani abu."

Wucewa sukayi bayan ta rufe d'akin, tunda suka kama hanya tayi shiru tana kallon
gari, Salman ne ya kalleta yace "ina fatan dai ba zaki cire nik'ab d'innan ba idan
kinje can?"

"Haba yaya Salman dole zan cire mana dan nasha iska, lokacin zafi ne gashi yanzu
ba'a ruwa sosai."

Hararanta yayi yace "bana so, karki bud'e fuskarki kowa ya gani."

"Amma yaya Salman akwai takura fa, kai baka san nik'ab ba wallahi tana hana mutum
kyakyawan shed'a."

Kallonta yayi irin ba wasanan yace "wallahi idan naji labarin kin cireta, to daga
ranar bake ba k'ara komawa makaranta."

Cikin shagwab'a tace "to yayana idan zan ci abinci kuma fa?"

"To na yarda ki d'aga idan zaki ci abinci, amma da kin ida ki mayar."

Hararan gefen ido ta watsa masa a ranta tace "sai kace wani sona yake da yake
takura min haka"

Kallonshi tayi tace "wai yaya Salman ta yaya ka sama min gurbin karatu anan ne
cikin sauri haka?"

Ba tare daya kalleta ba yace "to miye na wahala a ciki, dama anan kike karatu kuma
sun baki gurbi in da zaki ci gaba, kawai baki zo da wuri bane har anyi karatun wata
biyu babu ke."

Cikin tsoro Ummi tace "to yanzu idan suka tambayeni ya zance masu?"

"Na gama da wannan ma, dan na fad'a masu kinyi aure kuma yanzu ba kida lafiya."

Wani kallo ta masa tace "to me kace masu yake damuna?"

Wani kallon raini ya mata yace "na fad'a masu kina fama da laulayi ne."

A firgice ta kalleshi tace "laulayi, na ciki ko na me?"

"Ke wanne kika sani?"

Kallon gabanta tayi tace "na san na ciki."

Shima ba tare daya kalleta ba yace "to shi nake nufi."

Wani lallausan murmushi tayi tare da dafe cikin tace "wai ciki, Ummi da ciki,
babbar magana."

Kallonta yayi yace "kina sonshi kenan?"

"Ina so sosai, Allah ya nuna min na samu nima."

Kallon ba kida hankali ya mata yace "keda ko hanyar daya bi baki bi ba, kuma a
hakan kike neman shi."

Bata kalleshi ba tace "to miye a ciki? ai abun rabone kura ta haifi akuya."

Kallonta yayi yace "lallai kam, amma ki sani wanna kura za tasha dukan tsiya idan
ta haifi akuya."

"Lallai kam, watak'ila kuma ba zata sha ba." fad'ar haka yayi daidai da zuwansu
ecole d'in, bud'a k'ofar tayi zata fita tace "sai anjima."

"Idan kun tashi ki kira ni." ya fad'a yana kallonta, har zata fita ta tsaya tare da
tara masa hannu tace "kud'in abinci na."

Hannu yasa aljihu ya fito da kud'i yana tambayar ta "nawa zan baki?kin san ni ba
d'a gareni ba bare na san nawa ake bayarwa, kuma ma ke har wani kud'i za'a baki da
girmanki."

"To ina girman yake? har yanzu fa ban wuce jaririya ba."

Kallonta yayi sosai yace "a hakan, uwar wasu kakar wasu?"

Cikin shagwab'a tace "nifa yarinya ce, har yanzu a wanke nake babu datti."

"Allah ya shirya min ke 'yan matana, ni fad'a min nawa zan baki."

Dariya tayi tace "ameen yaya Salman, kawai ka kimanta sai ka bani."

Kafin su ankara suka ji k'arar k'araurawa (sonner) lokacin shiga aji yayi.

Cikin hanzari tace "kawai ka lissafa nawa ake baka da kana kamar ni."

"Ni ai ina kamar ki kud'in makaranta ma ni na biyawa kaina."


Cike da k'aguwa Ummi tace "to kawai ka ban 1000f ta isheni."

Dubawa yayi sai dai babu wacce ta buk'ata, dan haka ya bata 5000f tana karb'a ta
fita tana fad'in "zan aje maka canjinka, sai kazo."

Kallonta yayi sai gudu take har ta shige ciki, kai girgiza yaja motar yana fad'in
"kaji gudun da take kamar yarinya, ba zata yi hankali ba wannan har saina saita
ta."

Yaji dad'i sosai ganin yanda kayan suka mata d'as da ita, gashi duk sun rufe
jikinta sai idanunta kawai da hannayenta ne a waje, dan takalman data saka ma k'afa
ciki ne maras tudu(valerine) bak'ak'e.

```SAM```😍
11/03/2019 à 17:51 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

7⃣9⃣8⃣0⃣
7⃣9⃣-8⃣0⃣

Haka zaman nasu yake tafiya ba yabo ba fallasa, har yanzu babu abinda ya canja
daga zaman nasu sai dai abu d'aya shine yanzu Ummi tana yin duk abinda Salman ya
sakata, har yanzu Ummi ba tada sarau dan kuwa ko yanzu Salman yace mata kule to
kai tsaye za tace masa cas.

Amma tana mayar masa da yace zaiyi amarya kuma zata fara bashi hak'uri, haka Salman
ya samu yana wasa da Ummi son ransa ta hanyar k'ara aure, kullum soyayyar junansu
ce ke k'ara k'aruwa a tsakaninku sai dai har yanzu kowa baya yarda d'an uwansa ya
fahimta, haka suke zaune sai dai wani lokaci daga kallon da suke aikawa junansu ya
kan tona sirrin zuciyoyinsu.

Salman yayi niyyar ba zai fara fad'awa Ummi kalmar so ba,saboda sanin Ummi da yayi
zata iya watsa masa k'asa a ido idan ya fad'a mata, shi kuma a yanda yake jinta a
zuciyarshi dama sauran sassan jikinshi baya tunanin zai iya jurar rasata ko jin
rashin amincewarta daga bakinta.

Ummi ma haka ta zab'i ta b'oye ta barwa kanta ita kad'ai ba tare data fad'a masa
ba, tunda ta fahimci bata gabansa ko kad'an shi yasa ma zata ci gaba da b'oyewa har
lokacin da shima zai fara jin irin abinda take ji sannan ya fad'a mata.

A haka kuma warin auren su Ummi suke ci gaba da kula da cikinsu, Khairat, Nadiya
suna fama da laulayi mai tsanani su Jawahir kuma alhamdulillah za'a ce.

Har yau har gobe idan Ummi ta kira La Mama dan su gaisa, sai La Mama ta k'ara
jaddada mata akan ta kula da mijinta sannan saita fad'a mata wani abu da zata k'aru
da shi ko dan rayuwar gaba.
*WATA BIYU*

A lokacin ne su Jawahir suka fara shirye shiryen komawa makaranta, in da Ummi ita
ma ta nemi izinin Salman akan ya barta ta koma makaranta, sam Salman yak'i amincewa
yace sai tayi hankali sannan zata fara fita ma daga gidan.

Ummi tayi kuka tayi magiya tayi rarrashi amma sam yak'i yarda, dole Ummi ta hak'ura
ta shafa ma kanta lafiya, yayin da su Jawahir suka fara karatu sai dai suma suna
kewar Ummi sosai duk da tana gaba dasu a ajin, amma dai koba komai zasu dinga
had'uwa.

Tun lokacin sai Ummi ta sauya gaba d'aya ta daina walwala ba kamar da ba, yanzu duk
abinda Salman zai mata bata kula shi sai dai ta bishi da ido kawai, hakan ba
k'aramin tab'a Salman yayi ba dan kuwa farin cikinta shine nashi, amma yanzu gashi
ta daina gaba d'aya, dole Salman ya nemi mafita daga matsalar dan a ganinshi koda
ace ba abinda yake da iko a kanshi bane ai zaiyi k'ok'arin ganin ya sata farin
ciki, bare kuma yana da iko.

Ummi na zaune a falo tana kallo tare da uban tagumin data rabka Salman ya shigo da
sallama, kallo d'aya ta masa ta kau da kanta tana amsa sallamar, zaune yayi
kusanta yana kallonta, ledar dake hannunsa ya mik'a mata ta karb'a tana kallonsa ta
aje ledar dan a tunaninta irin kayan k'walam d'in da yake siyo mata ne.

Kallonta yayi yace "miye haka kuma? ya za'a baki abu amma ba zaki duba ba ki gani,
kawai saiki aje."

Ko kallonshi ba tayi ba ta d'auki ledar ta fara dubawa, take farin ciki ya


lullub'eta saboda ganin d'inkakken tenue (uniform) da sauran kayan makaranta da
duk abun da d'an makaranta zai buk'ata.

Fiddo kayan tayi ta mik'e tsaye tana gwadasu a jikinta bak'ak'e (tenue 'yan lycée
ne na moufida), riga iya gwiwa wacce ta bud'e sosai da gajerun hannuwa sai dogon
wando mai forme d'in slim da kuma hijab daya wuce rigar, sannan da nik'ab, cikin
mamaki tace,

"Wannan fa yaya Salman na miye?"

Murmushi yayi yana kallon tsantsar farin cikin dake kan fuskarta yace "naki ne"

Bud'a baki tayi cike da farin ciki tace "wow, yaya Salman amma naji dad'i sosai,
hakan kenan na nufin zan koma makaranta nima?"

Da ido kawai ya mata alamar Eh, cike da farin ciki ta k'araso wajenshi ta zube
k'asa tana fad'in,

"Kai amma yaya Salman naji dad'i sosai, Allah ya saka maka da alkairi, Allah ya
k'ara bud'i na alkairi, Allah bar min kai, Allah ya saka maka son...."shiru tayi ta
kasa k'arasawa.

Mamaki ne ya bayyana a fuskarshi tare da fad'in "ya saka min son mi?" kai kawai ta
girgiza alamar ba komai, mik'ewa yayi ya nufi d'akinshi ita ma haka, suna kaiwa
k'ofar d'akin Ummi tace,

"Yaya Salman yaushe zan fara tafiya?"

"Gobe mana"ya fad'a yana bud'a d'akinshi, murmushi tayi wanda ya bayyana hak'oranta
tare da dinple d'inta sosai, Salman dake k'ok'arin shiga d'akinshi ne tsaya tare da
dawowa yana kallonta, a hankali yasa d'an yatsarshi akan dinple d'inta ya latsa,
ita kam k'ura mashi ido tayi tana kallo yayin da shi kuma kasa had'a ido da ita
saboda tartsatsin da yake ji idan yana kallon idonta ma abota girma da fari.

Bai bar latsa kumatunta ba yace "Ummi na barki ki koma makaranta ne saboda tabbacin
da nake da akan ki, na san zaki kula da kanki sannan zaki karemin mutunci na dama
mutuncinki."

Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon cikin idonshi tace "insha Allah yayana, ba zan
tab'a baka kunya ba, sannan ba zanyi abinda zai shafi mutuncin ku ba, zanyi iya
bakin k'ok'arina wajen ganin na kare maku hakk'inku da yake kaina musamman ma kai."

Murmushin jin dad'i yayi yace "me yasa musamman ma ni?"

K'asa tayi da idonta cikin jin kunya tace "saboda kai mijina ne." tana fad'a ta
k'arasa shigewa d'aki tana dariya, Salman ma haka d'aki ya shiga yana jin wani
sanyi na ratsashi yana ji ina ma ace Ummi ta fad'a mashi kalmar so a matsayin
godiyar abinda ya mata.

Tun asuba Ummi da tayi sallah bata kwanta ba, tana gama had'a abinda kari ta d'an
gyara abinda zata gyara a d'akinta da falo dama cuisine, tana kammalawa ta shiga
wanka tana fitowa tsaf ta shirya cikin tenue d'inta.

Jakarta ta d'auko da hijab da nik'ab ta fito falo ta ajesu saman kujera sannan ta
nufi d'akin Salman dan ta tashe shi, da sallama ta shiga amma shiru bai amsa ba
alamar bacci yake, saida ta k'arasa har gabanshi ta k'ura mashi ido tana kallo
yana baccinshi cikin kwanciyar hankali.

Rumgume hannayenta tayi a bayanta a hankali tace "ina sonka yaya Salman, sai dai ba
zan iya fad'a maka ba, dan na san kai baka sona kuma ba zaka soni ba, amma zan ci
gaba da jiran lokaci na san zai zo."

Lek'a fuskarshi tayi taga sosai yake baccinshi dan haka ta sunkuya daf da k'eyarshi
ta sumbata, mik'ewa tayi tare da zura hannunta ta rufe hancinshi, da sauri ya juyo
da kanshi yana bud'a idonshi yana ganin Ummi ya tashi zaune yana ci gaba da
kallonta, murmushi kawai take masa kafin yace,

"Wannnan kuma wane irin tayar da mutum daga bacci ne?"

D'aga kafad'u tayi tare da d'aga gira sama alamar ba magana, saukowa yayi daga kan
gadon yana fad'in "saina ji kamar an sumbace ni a kaina ko?"

Bud'e baki tayi cike da mamaki, lokaci d'aya kuma tayi k'asa da kanta tana wuru
wuru da ido, gaf da ita ya matso yace "kece ko, ko dai akwai abinda kike b'oyewa ne
ban sani ba?"

D'ago ido tayi suka kalli juna, ja tayi da baya tana fad'in "haba dai sumbata fa?
sai kace wani jariri."

Toilet ya nufa yana fad'in "banyi mamaki ba dan kince haka, amma ki sani wani
lokacin ma miji yafi jariri buk'atar kulawa."

Kallonshi tayi tace "to, ni dai na san ana cewa namiji kamar k'aramin yaro ne, duk
in da kayi dashi can zaiyi."

Tsaye yayi yana kallonta kafin yace "kuma ke kin yarda da abinda aka fad'a d'in?"

Murmushi tayi tace "me zai hana ko, tunda mune ke jan ragamar."
Ganin ya tun karota yasa tayi saurin ja da baya tana fad'in "dan Allah ni dai kaje
ka shirya kar nayi late a zuwan farko."

Sai lokacin ya lura da kayan dake jikinta dan haka yace "oh, hakane fa, ok ki bani
5 minute ina zuwa."

Kallon agogon dake gefe gadon tayi tace "ah bon, 5 minute? Ok je t'atend."

Ciki ya shige ita kuma ta dawo falo ta zauna jiranshi, kallon agogo take lokaci na
tafiya amma Salman shiru bai fito ba, ido Ummi ta fiddo tare da mik'ewa tsaye tana
dafe da k'irjinta ganin 07:45, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in,

"Shikenan zuwan farko zan fara da late."

Hijabinta ta saka ta goya jakarta ta d'aura nik'ab, d'akin Salman ta nufa sai kuma
suka ci karo da juna, ido ya fiddo waje yana k'are mata kallo sama da k'asa kafin
ya nunata da hannu yace "ke kuma wannan shiga haka bak'a k'irin kamar wata 'yar
wuta."

Turo baki tayi duk da baya gani sannan tace "yaya Salman ka dubi lokaci fa ya wuce,
wallahi nayi retard."

Lokaci ya duba ya k'ara zaro ido yana fad'in "kai kai kai, lallai kam, to wuce muje
ina fatan dai kin karya?"

"Ni ban karya ba, kawai idan naje naci wani abu."

Wucewa sukayi bayan ta rufe d'akin, tunda suka kama hanya tayi shiru tana kallon
gari, Salman ne ya kalleta yace "ina fatan dai ba zaki cire nik'ab d'innan ba idan
kinje can?"

"Haba yaya Salman dole zan cire mana dan nasha iska, lokacin zafi ne gashi yanzu
ba'a ruwa sosai."

Hararanta yayi yace "bana so, karki bud'e fuskarki kowa ya gani."

"Amma yaya Salman akwai takura fa, kai baka san nik'ab ba wallahi tana hana mutum
kyakyawan shed'a."

Kallonta yayi irin ba wasanan yace "wallahi idan naji labarin kin cireta, to daga
ranar bake ba k'ara komawa makaranta."

Cikin shagwab'a tace "to yayana idan zan ci abinci kuma fa?"

"To na yarda ki d'aga idan zaki ci abinci, amma da kin ida ki mayar."

Hararan gefen ido ta watsa masa a ranta tace "sai kace wani sona yake da yake
takura min haka"

Kallonshi tayi tace "wai yaya Salman ta yaya ka sama min gurbin karatu anan ne
cikin sauri haka?"

Ba tare daya kalleta ba yace "to miye na wahala a ciki, dama anan kike karatu kuma
sun baki gurbi in da zaki ci gaba, kawai baki zo da wuri bane har anyi karatun wata
biyu babu ke."

Cikin tsoro Ummi tace "to yanzu idan suka tambayeni ya zance masu?"
"Na gama da wannan ma, dan na fad'a masu kinyi aure kuma yanzu ba kida lafiya."

Wani kallo ta masa tace "to me kace masu yake damuna?"

Wani kallon raini ya mata yace "na fad'a masu kina fama da laulayi ne."

A firgice ta kalleshi tace "laulayi, na ciki ko na me?"

"Ke wanne kika sani?"

Kallon gabanta tayi tace "na san na ciki."

Shima ba tare daya kalleta ba yace "to shi nake nufi."

Wani lallausan murmushi tayi tare da dafe cikin tace "wai ciki, Ummi da ciki,
babbar magana."

Kallonta yayi yace "kina sonshi kenan?"

"Ina so sosai, Allah ya nuna min na samu nima."

Kallon ba kida hankali ya mata yace "keda ko hanyar daya bi baki bi ba, kuma a
hakan kike neman shi."

Bata kalleshi ba tace "to miye a ciki? ai abun rabone kura ta haifi akuya."

Kallonta yayi yace "lallai kam, amma ki sani wanna kura za tasha dukan tsiya idan
ta haifi akuya."

"Lallai kam, watak'ila kuma ba zata sha ba." fad'ar haka yayi daidai da zuwansu
ecole d'in, bud'a k'ofar tayi zata fita tace "sai anjima."

"Idan kun tashi ki kira ni." ya fad'a yana kallonta, har zata fita ta tsaya tare da
tara masa hannu tace "kud'in abinci na."

Hannu yasa aljihu ya fito da kud'i yana tambayar ta "nawa zan baki?kin san ni ba
d'a gareni ba bare na san nawa ake bayarwa, kuma ma ke har wani kud'i za'a baki da
girmanki."

"To ina girman yake? har yanzu fa ban wuce jaririya ba."

Kallonta yayi sosai yace "a hakan, uwar wasu kakar wasu?"

Cikin shagwab'a tace "nifa yarinya ce, har yanzu a wanke nake babu datti."

"Allah ya shirya min ke 'yan matana, ni fad'a min nawa zan baki."

Dariya tayi tace "ameen yaya Salman, kawai ka kimanta sai ka bani."

Kafin su ankara suka ji k'arar k'araurawa (sonner) lokacin shiga aji yayi.

Cikin hanzari tace "kawai ka lissafa nawa ake baka da kana kamar ni."

"Ni ai ina kamar ki kud'in makaranta ma ni na biyawa kaina."

Cike da k'aguwa Ummi tace "to kawai ka ban 1000f ta isheni."

Dubawa yayi sai dai babu wacce ta buk'ata, dan haka ya bata 5000f tana karb'a ta
fita tana fad'in "zan aje maka canjinka, sai kazo."
Kallonta yayi sai gudu take har ta shige ciki, kai ya girgiza yaja motar yana
fad'in "kaji gudun da take kamar yarinya, ba zata yi hankali ba wannan har saina
saita ta."

Yaji dad'i sosai ganin yanda kayan suka mata d'as da ita, gashi duk sun rufe
jikinta sai idanunta kawai da hannayenta ne a waje, dan takalman data saka ma k'afa
ciki ne maras tudu(valerine) bak'ak'e.

```SAM```😍
11/03/2019 à 17:51 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

*HASBUNALLAH WANI'IMAL WAKIL*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

8⃣1⃣8⃣2⃣
8⃣1⃣_8⃣2⃣

Su Jawahir sunyi farin ciki sosai ganin Ummi a makaranta ba zato ba tsammani, haka
suka kasance tare har lokacin tashi yayi Ummi ta kira Salman yazo ya d'auketa.

Sosai su Jawahir suka birge Ummi ganinsu da tayi kowace da d'an k'aramin cikinta
tana turawa, babban abinda yafi shiga ranta shine, ganin yanda suka canja lokaci
d'aya duk sun canja abincin cinsu, abinda waccen take ci yanzu bata ko san
k'amshinsa, haka abinda wata bata ci a da yanzu kuma tana cinshi sosai, wannan
canjin ya birge Ummi sosai.

```ALLAH YA KAWO MAI ALBARKA```

Suna shiga gida ta cire nik'ab da hijab da jakarta ta yab'a akan kujerar falo ita
kuma tayi ciki, Salman kam ruwa ya d'auko a fridge ya zauna yana sha, ya jima zauna
yana jiran ta fito ta fad'a mashi abinda zata ci dan ya siyo mata amma shiru,
mik'ewa yayi ya nufi d'akin, k'ofar kawai ya bud'a ba tare daya shiga ba.

Da k'yar ya had'e wasu yawu da suka tarar masa sannan ya kau da kansa gefe yana
satar kallonta yana tambayarta "amm, dama na zone naji abinda zaki ci na siyo
maki?"

Ummi dake ci gaba da shafa manta d'aure da d'an k'aramin towel d'in da ko cinya bai
k'arasa rufe mata ba, sannan duk ta barbaza manyan kitsonta a bayanta ya kwanta,
cike da karsashi tace masa,

"A'a yaya Salman ina zuwa yanzu saina dafa mana abinda zamu ci, saurin da nake
kenan dama."

Cikin satar kallonta yace "kefa yanzu kika dawo kina buk'atar hutu, kawai ki
fad'amin me zaki ci."
Juyowa tayi ta nufi wadrob ta bud'a tana duba kayan da zata d'auka tana fad'in "a'a
yaya Salman zan dafa da kaina, a cikin kwana shida na karatu, kwana hud'u duk zan
dinga tasowa k'arfe 13:30 , kaga idan nace zaka dinga siyomin abinci ai ban kyauta
ba, dan haka ka barshi yanzu zan fito na d'ora mana yafi ace munyi latin cin abinci
amma ba siyowa ba, kuma ma naga ai daga ni sai kaine a gidan."

Murmushi yayi tare da kallonta yace "sai kin fito."

Sai lokacin ta kalleshi taga yanata wani sunkuye kai, a hankali ta tako tazo
gabanshi ta tsaya, hannunshi ta kama kamar yaro ta d'ora a gefen fuskarta tace
"kace Allah ya min albarka, kamar yanda Abba yake min."

Duburburcewa yayi ya rasa me zai fad'a, gaba d'aya ya rasa network d'inshi take
idonshi suka sauya suka fara canja launi, Ummi kam tsoro ne ya rufeta dan haka taja
da baya tana fad'in "ina zuwa yanzu."

Kamar zai tashi sama haka ya fita daga d'akin ya shiga nashi, gado ya fad'a ruf da
ciki yana taro abinda k'wak'walwarshi ta gane mashi hakan yasa kuma ciwonshi ya
k'ara tunzura yana dad'a gaba.

Maganinshi ya d'auko ya b'alla yasha tare da mai sa bacci yasha, lokaci k'alilan
bacci yayi gaba dashi ba dan ciwon ya bari ba.

Ummi na fitowa cuisine ta shiga ta fara had'a abincin rana mai sauk'in sarafawa,
14:40 ta kammala d'akin Salman ta shiga ta tashe shi daga bacci, yana fitowa tare
suka ci abinci suna idawa ta d'auke kwanukan ta mayar cuisine ta wanke ta goge duk
inda ta b'ata.

Tana fitowa Salman ta gani da jakar makarantar ta ya fiddo litattafanta yana


dubawa, k'arasowa tayi tana kallonshi ta zauna, kallonta yayi yace "kin gane
darasin da aka maki yau?"

Gyara zama tayi tace " taya zan gane da zuwa d'aya, dole ina buk'atar na samu mai
koyamin idan na dawo gida."

Cike da raha Salman yace "to in hakane ki dinga biyana duk


wata saina dinga koya maki."

Matsowa tayi kusa dashi tace "da gaske yaya Salman? to ka fad'i nawa kake so na
baka?"

Cike da fara'a yace " ki fad'a da kanki me zaki iya bayarwa duk wata."

"Duk wata?" ta tambayeshi, kai ya d'aga mata alamar Eh, dan haka tace "ok, to ka
koyamin, ni kuma duk wata zan biyaka ta hanyar haifa maka kyakyawan yaro ko yarinya
masu kama da kai."

Salman bai san lokacin daya fashe da dariya ba yana fad'in "yara dai, duk wata? ba
kida dama Abu."

Turo baki tayi gaba cike da shagwab'a tace "Eh mana, miye a ciki?"

Da k'yar ya tsagaita da dariyar yana kallonta yace "to amma me yasa sai masu kama
dani, me yasa ba kya san ki haifi masu kama dake?"

K'asa tayi da kanta tace "to ai ka fini kyau ne shi yasa."

Ya mutsa fuska yayi yace "Ummi waya fad'a maki ba kya da kyau?"
Kallon idonshi tayi tace "kasha fad'amin haka sau da dama, har wani lokaci ma ka
kan kwatantani da mage ko aljana."

K'asa yayi da kanshi dan bai tab'a tunanin abin yana cikin ranta ba har yanzu,
kallonta yayi yace "Abu karki damu da wannan, kawai ina fad'a ne amma ba wai yana
nufin ke mummuna bace, kina da abinda ba kowa keda shi ba."

Hararan wasa ta masa tace "hmm, kamar me kenan?"

Kallonta yayi sosai kafin yace "kamar idonki masu abin al'ajabi, wanda basa kalluwa
ga ragon namiji bare kuma mace, sannan kina da dinple wanda yake k'ara maki kyau
idan kina dariya ko murmushi ke har ma da kuka idan kina yi."

Wai dad'i kashe Ummi, yau Salman d'inta ne ke yabanta haka, farin ciki ne ya
k'umeta yasa tayi fari da ido cikin kissa tace "hmm, to ni dai naji muyi karatun."

*A kwana a tashi* lokaci na tafiya al'amura na faruwa da dama daga rayuwar Salman
da Ummi, tun lokacin Salman kema Ummi lesson ba dare ba rana in dai har yana gida,
shak'uwa sosai ta k'ara shiga tsakaninsu a wani b'angaren kuma suna k'ara zurfafa
soyayyar da sukewa junansu.

*Sati uku* da fara karatunta Salman ya sake tafiya Cotonou, da k'yar ya iya kwana
goma a cikin sati biyun daya d'iba zaiyi, dan kuwa babu abinda yake daya wuce
tunanin Ummi da kewarta.

Haka ma a wajen Ummi, dan kuwa ko abinci ta daina ci sosai dan yanzu ta saba da cin
abinci tare da Salman, kafin ya tafi saida ya d'auko Islam tare da Momy (autar su
Salman) ya kawosu dan su tayata bacci, hakanne yake rage mata damuwa da tunani da
kuma k'arfafa gwiwar da Salman yake mata akan karatu duk lokacin da sukayi waya.

Tunda safe Salman ya kan kirata yaji ya suka tashi, kasancewar yana da jadawalin
lokacin karatunta (emploi du temps) yasa tana fitowa daga aji kiran Salman zai
shigo wayarta, da dare haka zasu sha hira abinsu har dama karatu yana k'ara
kwatanta mata a waya.

*Ranar* da Salman ya dawo, ya dawo da k'udirin sauke hakk'in dake kanshi, yayi
niyyar kusantar Ummi ta hanyar data dace bawai ko ta halin yaya ba.

Rashin sa'a a ranar daya zo, a ranar bak'on Ummi yazo (period), bayan wannan kuma
gashi suna shirin shiga satin jarabawa, hakan yasa Ummi ta zama busy sosai bata da
lokacin komai har lokacin kanta, hak'uri kawai Salman yayi amma ba dan haka yaso
ba.

*Litinin* Ummi suka shiga zana jarabawa, kwana uku sukayi kuma a kwana ukun nan
Ummi ko abinci bata san ci sai Salman ya matsa mata lamba sannan, hasali ma ba ita
ke dafa abincin ba siyowa Salman keyi, ririta ta kawai yake dan shirin shi shine
suna gama jarabawa tofa shima dole ya shiga hq dan tashi jarabawar.

*A kullum d'an Adam na nashi ne, Allah ma yana nashi, mutum baya da ikon tsarawa
kansa rayuwa sai yanda Allah ya tsara masa* su Ummi na fitowa daga aji aka fara
ruwa kamar da bakin k'warya, zuwan Salman dan ya d'auketa yasa Ummi fitowa daga
mafakarta ta k'arasa in da yake, ruwa sun jik'ata sosai hakan yasa tana shiga mota
ta cire hijab d'inta da jakarta, suna zuwa gida ma haka suka tsaya suna kallon juna
ganin yanda ruwan ke sauka da k'arfi.

Cike da shagwab'a Ummi tace "to yaya Salman kaine namiji kuma mai hakk'in kula
dani, dan haka ka rufeni saimu shige ciki."

Hararanta Salman yayi yace "ahan, kenan yau kin tuna haka ko?"

Turo baki tayi gaba tace "to ni dai wallahi idan na shiga ruwan nan zan iya mura,
dama gashi na riga dana jik'e."

"To shikenan, ki shirya zan fita yanzu kema saiki fito."

Fita yayi ya zagaya ma zauninta ya kamo hannayenta ta fito, rumgumota yayi a


jikinshi ya matseta a hankali ya d'agata ya d'ora k'afafunta akan nashi sannan ya
d'auko hijab d'inta ya masu runfa dashi, a hankali ya fara takawa saboda tana bisa
k'afafunshi ne kamar ya d'auketa ne, idon Ummi na kan k'irjin Salman data d'ora
hannayenta ta kasa had'a ido da shi, shi kam fuskarta kawai yake kallo tare da
k'ara matse kunkuminta da duka hannayenshi biyu.

Suna shiga falo ta zame jikinta daga nashi, sai dai duk da haka saida suka jik'e da
ruwa take jikin Ummi ya fara rawar d'ari, kallonta Salman yayi lokacin da yake cire
takalmanshi k'afa ciki, saida ya gama cirewa ya d'ago yana b'alle ma b'allan
rigarshi yace,

"Ya dai malama?"

Bud'ar baki tayi zatayi magana ji kake "hatshimmm." ta b'arzo wata atshiwa, ja baya
Salman yayi yana fad'in "kai, haba ke kuwa atshiwa ba sanarwa kawai saiki fyace
ni."

Wata maganar taje tayi amma ina sai wata atshiwar tare da fitowar majina a
hancinta, ajiyar zuciya Salman ya sauke cike da tausayawa ya matso kusa da ita yana
kallon fuskarta, kallabinta ya cire ya jefar a kujera haka ma ribom (chouchou)
d'inta take gashinta marar kitso ya zube a bayanta wanda ya jik'e da ruwa sai
k'amshin man kai yake *(BLACK QUEEN {COCONUT OIL} )*.

A hankali ya had'ata da k'irjinshi ya zura hannayenshi a bayanta ya zuge zif d'in


rigarta, tana kallonshi har ya rabata da rigarta yayi saura bras d'inta fara,
sunkuyawa yayi yana shirin zame wandonta daga jikinta tayi saurin ja da baya tana
fad'in "a'a ya isa haka....atshimm." ta k'arasa maganar tana k'ara atshaweshi.

Tissue ya ciro a aljihunshi ya matso kusanta yasa ya goge mata majina har da cewa
"fyato" kallonshi tayi sai dai ba tayi magana saboda ya rufe mata hanci da tissue,
bud'e mata ido yayi ya sake cewa "fyato"

Tsaf Ummi ta fyato ya goge mata, juyawa tayi ta bud'e d'akinta ta shige tana ci
gaba da atshiwar, shi kam binta yayi da kallo kafin shi ma ya nufi nashi d'akin.

Zuwa dare Ummi ta galabaita sosai dan mura bata mata da dad'i dama in dai ta
damk'eta abinka ga jar fata duk ta fita hayyacinta ta sukurkurce, tun doguwar rigar
data saka dawowarta har yanzu ita ce a jikinta, kanta duk ya yamutse saboda kwanci
da take hancinta har yayi ja saboda goge majina, idonta banda ruwa ba abinda sukeyi
ko magana bata ji sosai dan kunnuwanta sun d'ume, haka gaba d'aya mak'oshinta ciwo
yake ga bala'in ciwon kai, duk ta rikita Salman da kukan shagwab'ar da take bata
tab'a tunanin zai damu haka ba, amma data ga ya nuna damuwa a fili saita k'ara
narkewa tana zuba shagwab'arta.
Zaune suke a falo duk Ummi ta dunk'ule a cikin k'aton bargon da Salman ya d'auko
mata a d'akinshi wai ita zazzab'i, Salman ne ya fito daga cuisine hannunshi rik'e
da cup na tea, yana zuwa ya zauna kusa da ita yana fad'in " yawwa Abun Alhaji to
karb'i kisha wannan, Insha Allah zaki ji sauk'i kinji."

Ganin bata amsa ba yasa ya kalleta, idonsu ne suka had'e dana juna ganin idonta
suna neman kawo ruwa yasa hannunshi ya shafe mata idon yana fad'in "miye kuma?"

Leb'en k'asa ta turo gaba kamar mai shirin fashewa da kuka tana fad'in "tsoro nake
ji yaya Salman."

Kallon mamaki ya mata yace "tsoron me kuma? keda kina tare da ni miye zai baki
tsoro a duniyar nan."

Wani shu'umin kallo ta masa tace "da gaske yaya Salman? to amma ai bana da
tabbacin zaka zauna tare dani har k'arshen rayuwata."

Wani kallo ya mata da yasa tayi k'asa da kanta kafin yace "Ummi, me yasa kike
tunanin haka?"

Kai ta girgiza tana fad'in "ba komai."

"To in dai hakane karki sake wannan tunanin, ni ina tare dake kuma zan zauna dake
har abada, sannan babu abinda zan bari ya cutar dake matuk'ar ina raye, saboda ni
yayanki ne mai alhakin kula dake."

Dad'i ne ya kama Ummi yasa ta fad'a a k'irjinshi tana murmushi tare da fad'in "oh,
mon ice cream."

Lek'a fuskarta yayi yana fad'in "aw, da ice cream zaki had'a yayanki?"

Dariya tayi tare da tusa kanta cikin k'irjinshi tace "to ai saboda irin son da nake
masa ne yasa."

"Kenan son da kike min ma baya dayawa?"

Da sauri ta d'ago daga k'irjinshi za tayi magana, suna had'a ido ya mata kwarjini
dan haka tayi shiru ta koma k'irjinshi tana fad'in "kawai ka ban tea nasha."

Daga kan k'irjinshi ya dinga bata tana shan tea d'in dashi ya had'a mata yaji cinta
sosai da lemon tsami, tana sha Salman yace "yanzu kenan ke kika koma mai tea d'in
dare?"

Ba tare data d'ago ba tace "to ai nice kesha da dalili, dama kai kana shane saboda
ra'ayi da kuma karka barni na huta."

Tana fad'a ta rufe bakinta dan ta gane tayi sub'ul da baka, cewa tayi "kayi hak'uri
yaya Salman sub'utar baki ce."

Cike da nuna rashin damuwa yace "ba komai, ai kin riga da kin fad'a, amma zan tuna
maki kin fad'i haka ranar da amaryata ta shigo gidan, tunda ke iya fahimtarki
kenan."

Tashi tayi daga jikinshi tana kuka tana fad'in "wallahi tallahi ni bada kai nake
ba, kuma ai sub'utar baki ce kuma na baka hak'uri, wallahi idan yarinyar nan tazo
gidan nan ko kwana d'aya ba zatayi ba."

Rik'e dariyarshi yayi ya kalleta yace "ni kuma naga idan kece kika kawota gidan,
aure kuma ba fashi." yana fad'a ya mik'e ya shiga d'akinshi.
Tashi tayi da bargon a jikinta ta bishi, toilet ya shiga amma tayi tsaye tana
masifa har ya fito d'aure da towel alamar yayi wanka, tsaye yayi yana shafa mai
haka tayi ta bali'i wai ita wallahi ba zaiyi aure ba dan yaci mutuncinta.

Wadrob ya bud'a ya d'auki kayan baccinshi saida ya saka wando sannan ya cire towel
d'in zai saka riga, muryar Ummi yaji tana fad'in "gashi ma wannan ciwon naka har
tambayarka nayi me yaji maka amma kak'i fad'amin, wallahi saina fad'a ma Mama
watak'ila ita ta fad'amin."

Tsayawa yayi daga saka rigar ya jawota har kan gado ya kwantar da ita shima ya
kwanta ya rumgumeta a jikinshi yace "in har kika fad'awa Mama to tabbas ranar zan
nuna maki ciji."

Cikin sigar rarrashi tace "dan Allah kayi hak'uri wallahi ba zan fad'a mata ba."

"Ah to, da yafi maki."

"To amma yaya Salman me yasa ba zaka fad'amin ba? nifa matarka ce."

Ajiyar zuciya ya sauke akan fuskarta tare da k'ara matseta yace "hakane, zan fad'a
maki amma sai ranar da kika zama cikakkiyar macen aure na."

Ido ta d'aga ta kalleshi tace "dama ni ban cika matarka ba har yanzu?"

Kuka ta fara shi kuma ya fara rarrashin yana fad'in "ba haka nake nufi ba Ummi,
shifa aure da kika gani ana gina shine a bisa wasu sharadd'ai, idan har babu d'aya
a ciki tofa ana iya raba aure akan wannan d'ayan a cewar wasu malamai."

"Ummi hakk'in saduwa ba k'aramin hakk'i bane akan ma'aurata, ni ba yaro bane haka
kema kuma mu 'yan adam ne masu matuk'ar sha'awa dole muna buk'atar junanmu kafin mu
rayu musammam ma ni, to amma ya zanyi ke kina nuna tsoro ni kuma ba zan iya maki ta
k'arfi ba Ummi."

"Yaya Salman dan Allah kar kayi fushi dani, wallahi ina jin tsoro sosai ban san
taya zan fuskanci wannan k'alubalen ba, amma dan Allah ka yafe min in har baka so
Ubangijina yayi fushi dani."

Haushin maganarta Salman yaji, dan ya d'auka zata bada kaine kawai amma ta kasa,
sassauta rik'on da yayi mata yayi yana fad'in "shikenan kiyi bacci."

K'ara lafewa tayi a jikinshi tace "mu zauna haka yayana, zamu iya rayuwa ko babu
wannan abun haka ma ai muna cikin farin ciki."

Gaban Salman ne ya fad'i wata zufa yaji ta tsatsafo masa, a sanyaye yace "ba zai
yiwuba Ummi na fad'a maki mu 'yan adam ne, muna buk'atar wannan d'in domin mu rayu,
a k'alla na fara cinye k'uruciyata ba tare da anfanar ni'imar da Allah yayi min
ba."

Yana fad'a ya juya mata baya yana sak'e sak'e, yanzu kam in dai har ba zata canja
ba to dole yayi aure, dan shi kam ba zai iya mata ta k'arfi ba dan yafi kowa sanin
wanene shi, in har ya mata ta k'arfi to ko bata mutu ba za tayi k'anwar mutuwa in
kuma ba haka ba to za tasha jinya ba kad'an ba.

```My Lovely Heenat ya kika ce ne akan wannan lamarin?```


11/03/2019 à 17:51 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_
*Wallahi fans ina matuk'ar jin dad'in comment d'inku, bayan _KAUSSAR_, _AUREN
HA'DI_ shine na biyu da nafi so*

_Komai wayon amarya sai ansha manta._

```ALLAH KASA MU CIKA DA DUNIYA LAFIYA```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

8⃣3⃣8⃣4⃣
8⃣3⃣-8⃣4⃣

Kwana uku kenan Ummi na fama da matsananciyar mura ga zazzab'i da ciwon kai, sosai
Ummi ta fita hayyacinta duk ta susuce kamar ba ita ba, sosai Salman ya tausaya mata
halin da take ciki dan yanda yaga duk ta koma ko abinci baya mata dad'i sai abu mai
yaji ko tsami.

Yau ta tashi kuma jiki da sauk'i sosai, haka ta wuni har dare ba tare data ji
zazzab'i ba, kamar yanda Salman ke kula da ita kullum haka yau ma saida ya bata tea
ta tasha mai cinta da lemon tsami sannan ya bata magungunanta tasha yace taje ta
kwanta.

Tana shiga d'aki ta kwanta tare da dunk'ulewa cikin bargo tana san tayi bacci, daga
k'asan gado ta fara jin motsin abu hakan yasa ta tashi zaune tana zare ido taga
daga abun ina zai fito, shiru shiru babu komai amma kuma har yanzu tana jin
motsin, a hankali ta sauka daga kan gadon da gudu ta fita daga d'akin ta nufi
d'akin Salman.

Salman dake zaune bakin gado da waya a hannu da kuma towel a jikinshi ya nuna wanka
zai shiga, kallonta yayi cike da mamaki kafin yace "miye kuma haka zaki shigo wuri
babu sallama? yanzu da babu komai a jikina fa kuma sai kice kinga ciji."

Kamar zatayi dariya kuma dai tayi shiru tare da turo baki tana fad'in "to miye a
ciki? ai kai mijina ne duk abinda na gani halak d'ina ne."

Wani kallo ya mata tare da jinjina kai yace "uhumm, aiko zan gani."

Mik'ewa yayi zai shiga toilet da sauri ta tareshi tana fad'in "yaya Salman dan
Allah bari na fara wanka, idan na fito saika shiga." Ummi ta fad'i hakane saboda a
d'akinshi take so ta kwana, bata so yaji wani abu a jikinta da ba kamshi ba koda
komai ba zai faru ba.

Zaune Salman yayi yana fad'in "to shiga, amma kiyi sauri."

Tana shiga ta cire kayan jikinta ta fara sakarma kanta ruwa cike da farin ciki,
Salman dake zaune k'ofar ya k'urawa ido yayin da zuciyarshi keta sak'a mashi tana
kwance mashi, zuciyarshi ce tace "SALMAN kaga wata kyakyawar dama?"

"Hakane, amma ba yanzu ba."


"To sai yaushe kenan?"

"Sai lokacin daya dace."

"Wane lokaci kenan?"

"Akwai abubuwan da nake so na fara gabatarwa kafin wannan."

"Amma ai wannan ba zai hana wannan ba, zaka iya gabatar da wannan kafin waccen."

Salman bai gushe ba har saida zuciyarshi ta gamsu da wannan shawara, tsam ya mik'e
ya nufi k'ofa key naga yasa ya rufe tare da kashe fitilar d'akin.

Ido rufe Ummi ke wanka ruwa na sauka har kanta tana jin dad'in ruwan, kamar tafiyar
maciji taji a bayanta dan haka ta juyo da iya k'arfinta, Salman ta gani shima dai
kamar ita babu komai a jikinshi, da k'arfi taja da baya tare rangad'a k'ara mai
k'arfi.

A sukwane Salman ya k'arasa wajenta har saida ya dan ganata da bango sannan ya
matse mata baki da hannu yana fad'in "karki sake kimin ihu."

Yanda sukayi kusa sosai ne yasa Ummi jin numfashinta ya fara rauni, kallo d'aya
zaka mata kasan a tsorace take jikinta b'ari kawai yake duk idonta sun fito waje,
ta k'ame waje d'aya ta kasa motsi numfashinta ne ya fara tafiya da sauri dan haka
Salman yace,

"Idan kuwa kika saki kika suma wallahi sai dai na k'arasa ki."

Da sauri tasa hannu ta rufe bakinta hawaye na zarya a kumatunta kallonshi kawai
take da ido, jawota yayi tsakiyar panpo ruwa suka fara sauka a jikinsu a haka kuma
ya dinga wasa da ita kamar 'yar tsana, ita kam ta daskare waje d'aya.

Saida suka jima a haka kafin ya fito da ita daga toilet d'in ya shimfid'eta akan
gado, yanzu kam Ummi ta fahimci da gaske Salman yake dan haka ta yunk'ura danta
tashi, da k'arfi Salman yasa hannunshi a k'irjinta ya maida ita kwance tare da mata
runfa ya kai bakinshi a kunnenta yace "ki nutsu kefa ba yarinya bace."

Lokacin kam abu d'aya ne ya rage da Ummi zatayi, iya k'arfinta tasa ta fara tureshi
daga jikinta tana k'ara had'e da kuka, cizo yakushi duka aika mashi take amma
Salman ko motsi.

Ganin abin yayi yawa yasa Salman rad'a mata a kunne "dan Allah Ummi kiyi shiru,
karki saka naji maki ciwo wallahi ba zan iya dakatar da kaina ba, idan na tsaya zan
iya rasa rayuwata nasan kuma ba zaki bari haka ta faru ba, Ummi ina cikin wani hali
mai wuyar fassarawa idan kika barni nayi ni kuma na maki alk'awarin zan fad'a maki
komai a game da ciwona da kike san kiji."

Kamar hanjinta zasu fad'o k'asa haka k'irjinta kamar zai fito waje, cikin kuka tace
"a'a nidai ka k'yaleni wallahi bana so, tsoro nake ji dan Allah ka rabu dani."

Salman da baya hayyacinshi ko kulata bai sake yi ba har ya fara k'ok'arin shiga
hq.

_To daga nan nima nayi waje dan kam yau na deb'o ruwan dafa kaina, falo na dawo na
zauna ina jin kukan Ummi amma ba yanda zanyi, karo na farko da naji tausayinta to
amma ya za'ayi hakk'ine dole a sauke shi._
Rabin tsawon daren nan Salman akan Ummi yayi shi, ba tare da sarara mata ba ko
d'aga mata k'afa, dan Salman yunwarshi ta tsawon shekara hud'u yau saida ya kusan
darjeta akan baiwar Allah Ummi.

Tsaye yake a toilet ruwa na sauka tun daga kwanyar kanshi har kan k'afafunshi,
Salman yau ji yake kamar ya bud'a k'irjinshi ya fito da zuciyarshi ya rage tsabar
farin cikin dake cikinta ko yaji sauk'in farin cikin da yake ciki.

A sannu sannu ya dinga magana da zuciyarshi,

"Ashe wannan itace ni'imar da Khamis yake fad'amin a tattare da mata?"

"Lallai Khamis yayi gaskiya da yace su keda kayan marmari, amma ai nihin gaskiyar
maganar shine, mata sune mafi kayan dad'i kuma ni'imar da Allah ya bamu a duniya. "

"Dolenmu mu girmama mata, dole ne garemu mu rarrashe su ko dan samun nutsuwarmu,


yanzu na fahimci Khamis da yace ana rarrashinsu."

"Hak'ik'a na zama mafi girman sakarai a duniya, da nake tunanin Ummi ba zata iya
dani ba kuma tamin k'aramta, ashe abun ba daga nan take ba, yau gashi Ummi ta canja
salon labarin rayuwata."

Lumshe idonshi yayi lokaci d'aya kuma ya bud'e yana tunanin ta yanda zai fuskanci
Ummi, haka ya tsarkake kanshi kafin ya fito ya bud'a drower ya d'auko doguwar riga
fara tas wacce ta dace da daren ya saka kafin ya kunna fitilar d'akin dan ya
taimakawa Ummi.

Da sauri ya rufe bakinshi da hannu lokaci d'aya gabanshi ya fad'i, "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un." saida ya maimaita haka har sau uku, da azama ya k'araso
wajen Ummi inda fuskarta ke kallo, zubewa yayi akan gwiwoyinshi yana kallon Ummi da
idonta ke rufe kai kace gawace in banda numfashin da take a hankali ba zaka tab'a
cewa tana raye ba.

A kid'ime ya fara tattab'ata yana fad'in "Ummi na, Ummi dan Allah ki tashi karki
min haka, ki tashi dan Allah Ummi karki mutu akan wannan shashashan mahaukacin
kuskuren nawa."

Ummi kam azabar da take ji har zaifi ace mutuwa tayi, a hankali ta bud'a idonta da
suka kumbura sukayi jawur saboda kuka ta kalli Salman, hannunta ta fara k'ok'arin
d'agawa tana so ta mik'awa Salman, Salman na ganin haka yayi saurin rik'o hannunta
yana fad'in "Ummi ki tashi ki min magana dan Allah."

Magana ta fara amma ko d'aya babu wanda Salman keji saboda shak'ewar da muryarta
tayi, k'ara matsawa yayi ya kara kunnenshi a bakinta yace "kiyi magana Ummi ina
jinki."

A shak'e duminta ya fita tace


"ina, ina, ina sonka yaya Salman, ba bana so na mutu ban fad'a maka ba."

Wasu hawaye ne suka fito a idonshi bai san lokacin daya fashe da kuka ba ya k'ara
matse hannunta ya had'a da goshinshi yana fad'in "a'a Ummi ba zaki mutu ba insha
Allah, zamu rayu tare kuma mu mutu tare, Ummi nima ina sonki so mai tsanani so
marar misaltuwa, Ummi ba zan iya rayuwa babu ke ba dan Allah ki taimaka min ki
tashi kinji."

Wani tattausan numfashi Ummi ta sauke lokaci d'aya farin ciki ya rufeta, ko a
mafarki ba tayi tunanin Salman zai fad'a mata haka ba, amma gashi a zahiri Salman
na fad'a mata yana sonta kuma ba zai iya rayuwa babu ita ba.
Murmushi tayi mai kama da kuka har saida hawaye suka zubo a fuskarta, tashi yayi ya
had'a mata ruwa ya dawo ya d'auketa yakai cikin bahon wanka ya nasa, da sauri ta
rik'e hannunshi tare da fad'in "washsh,zafi"

Zaune yayi bakin bahon yana rike da hannayenta lokacin idonshi suka sauka akan
rigarshi data b'ace saboda d'aukar daya mata, dubara yayi ya rufe wajen da
hannunshi yana fad'in "kiyi hak'uri kinji Ummi na, insha Allah zaki ji sauk'i, ki
yafe min a bisa waoutata."

Sun jima a cikin toilet kafin ya barota ya fito, bakin gadon ya dawo ya sake zubewa
akan gwiwoyinshi yana kallon jinin dake kwance akan zanin gadon, ba lallai kaga
haka ba a daren farko amma ya dangata da yanda kajewa macen, kai ya girgiza yace
"kiyi hak'uri, ba haka na so ba banyi haka da gangan ba."

Wani zanen ya shinfid'a shi ma ya sake wata farar rigar sannan ya koma toilet
d'in, ya samu ta gama dan haka ya d'aukota sai kan gado ya direta, rigar bacci ya
d'auko mata da kanshi yasa mata sannan ya gyara mata kwanciyarta durk'ushe yayi a
gabanta yana shafar fuskarta had'i da kanta har baccin wahala da gajiya ya
d'auketa, addu'a ya mata kafin ya mik'e.

Alwala yayi ya dawo raka'a biyu yayi dan ba zai iya yin nisa da Ummi ba, yana
sallamewa ya d'auko Alqur'ani ya zauna gefen Ummi saman gadon ya mik'e k'afafu ya
fara karanta suratul AN'AM.

dan danan ya kalli Ummi dake saurin sauke ajiyar zuciya saboda kukan da tasha, duk
lokacin daya kalleta wani basaraken murmushi ne ke bayyana kan fuskarshi, haka har
aka kira sallar asuba, sallah yayi yana kan sallaya ya kalli Ummi yace,

"Na yau kad'ai za kiyi jinkirin sallah, ba zan iya tashinki ba a wannan halin da
kike ciki, ki gafarce ni."

Daga nan zaune ya d'ora kanshi akan gadon har bacci ya d'aukeshi, basu farka ba
har saida kiran Khamis ya tayar da Salman....
12/03/2019 à 13:53 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

```FARIN CIKIN MARAR MISALTUWA, INA JIN DAD'I MUTANE NA SAI DAI FATAN ALLAH YA
BARMU TARE DA MASOYANMU.```😘💋😘

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

8⃣5⃣8⃣6⃣
8⃣5⃣-8⃣6⃣

Yana d'aukar wayar Khamis ya fara masifa "yanzu kai dan Allah miye haka? ka wani
shige gida ka zauna bayan kasan akwai masu jiranka a waje."

Muryar da yayi magana da ita ne yasa Khamis yasan akwai wani abu, cikin tattausan
murya yace "kaga dan Allah karka takura min, kaji da harkokin na yau ba zan samu
damar fitowa ba."

"Iye, ba zaka fito ba fa kace, to me yasa?"


"Wannan ba matsalarka bane, kayi abinda nace kawai."

"To naji zanyi, dan naga alama kamar Ummi ta fara juyaka yanda take so."

Maida kallonshi yayi ga Ummi data gyara kwanciyar ta a hankali tare da yamutsa
fuska duk da a cikin bacci take, ajiyar zuciya ya sauke kafin yace "zata iya yin
duk yanda take so dani, ni Salman nata ne halak d'inta ne ni."

"Ahan, ni kam me Ummi ta baka ne kasha?"

"Kaga kayi abinda ke gabanka, sai an jima."

Yana fad'a ya kashe wayar ya aje gefen gado ya zauna yana ci gaba da kallon Ummi, a
hankali ya fara magana da kanshi "ban sani ba ko haka duka mata suke, ko kuma kece
kad'ai haka."

"In har haka kuke, to tabbas dole mu godewa Allah daya halitta mana ku, in kuma
Ummi nace haka, to hak'ik'a nafi kowane namiji sa'ar mata a duniya, Ummi kin had'u
tako ina sai dai na biki da addu'a kawai."

_Hey Salman , stop this nonsence, what do you mean Ummi, 🙊(kaga har kasa na fara
sambad'o turanci), mu ma haka jariranmu ke fad'a mana._

Ci gaba yayi da maganarshi bayan hararar daya watsa min,

"Ummi na Allah ya albarkace ki, Allah ya saka maki da alkairinsa, Allah ya baki
juriya da hak'urin zama dani, ni kuma Allah ya bani ikon kyautata maki, Allah ya
bani ikon saka ki farin ciki har k'arshen rayuwata, hakane kawai zaisa na saka maki
da alkairin da kika min."

Ya kasa tashi daga wurin dan gani yake kamar wani abu zai sameta idan ya gusa, a
hankali Ummi ta fara motsawa tana san tashi, b'angaren da take ya dawo tare da
k'ura mata ido yana jiran ta bud'e nata idon, ido ta bud'e ta sauke su akan Salman
hakan yasa taji kunya taja zanin rufar ta rufe fuskarta.

Zaune yayi tare da fad'in " ki bud'a fuskar mana, na jima ina jiran naga tashinki,
dan naga yanda jikin naki yake fa."

Hannu yasa ya janye bargon yana sakar mata murmushi, tana ganin haka ta yunk'ura
danta tashi, wani irin bala'i ne taji da gaba d'aya jikinta k'asanta kam kamar ta
kama ruwa da yaji haka take ji.

Cike da rad'ad'i ta rik'e hannunshi sosai tare da matse fuska take wasu k'walla
suka zubo mata, hannayenshi ya kai da nufin ya gyara mata zama zafi yaji a jikinta
mai matuk'ar zafi sosai, gyara mata zaman yayi ya koma ya zauna yana kallon
fuskarta, k'asa tayi da kanta yayin da take addu'a ya tashi ya fita dan ta koma ta
kwanta dan zaman ba dad'i, hannayenta ya kamo duka biyu yace,

" *ZEINAB* kiyi hak'uri ki yafe..."da sauri Ummi ta rufe masa baki da hannunta, kai
kawai ta girgiza dan ba zata iya magana ba ko tayi ma ba zai ji ba, kallon idonta
yayi ya d'oke hannunta yace,

"A'a Ummi, ki barni na saka maki albarka tare da nuna maki tsantsan farin cikina
idan ba zaki bari na nemi yafiyarki ba."

Ci gaba yayi da fad'in "ZEINAB, INA SONKI SO MAI TSANANI, SON DA BA ZAN IYA RAYUWA
BABU KE BA."
"Ummi kin zama silar sauyawar rayuwata, kin sabinta min ita ta hanyar da banyi
tunani ba, ko kad'an ban tab'a tunanin kece wacce zata kawo wannan sauyin a
rayuwata ba, Ummi na san ni mugu ne a idonki kuma azzalumi, amma duk da haka baki
hanani kanki ba a gaskiya na gode maki sosai."

Ganin hawaye na zarya a fuskarta yasa Salman rud'ewa ya fara goge mata da hannunshi
yana fad'in "kiyi hak'uri idan na fad'i wani abu da bai maki dad'i ba, Ummi bana
san ganin hawayenki ko kad'an saboda suna tab'amin zuciya sosai."

Tashi yayi tare da fad'in "bari na kawo maki tea kisha kafin na samo maki abinda
zaki ci kisha magani, dan naji jikinki da zafi."

Yana fad'a ya fita ya barta, yana fita Ummi ta fara k'ok'arin saukowa daga gadon
dan tayi fitsari ta dawo ta kwanta, ansha daga kafin ta iya sauko da k'afafunta
tana sauke numfashin wahala, Salman ne ya sake shigowa d'akin dan ya tambayeta ko
zata iya cin indomie ya dafa mata.

Tsaye yayi yana kallonta ganin ta kasa tashi yasa ya k'araso yana fad'in "bari na
taimaka maki tunda naga kin kasa."

Hannu ta d'aga masa alamar ya barshi, kallonta yayi yace "bari na taimaka maki
mana, ko zaki iya ne?"

Kai ta d'aga masa alamar Eh, d'aga kafad'a yayi yace "ok, zaki ci indomie na d'ora
maki."

Dariya ce ta sub'uce mata har tana nunashi da hannu, cikin dakusashiyar muryarta
tace "wai kaine zaka dafa indomie naci?"

Kallon mamaki ya bita dashi kafin yace "me kike nufi to, ban iya ba? to ni tun
kafin a haifeki nake dafa abinci."

Kai kawai ta girgiza masa dan ita kad'ai ta san me take ji, juyawa yayi zai fita
tace "yaya dan Allah ka kawo min madara."

Tsaye yayi yana kallonta kafin yace "kenan ba zaki daina shan madarar nan ba ko?"

Bud'a baki tayi tace "rayuwata ce fa, me yasa zan daina lokaci d'aya haka?"

"Saboda kin zama babbar mace."yana fad'a ya bar d'akin, binshi tayi da kallo kafin
ta tab'e baki dan bata gane komai ba.

Cije leb'en k'asa tayi ta rufe ido haka ta dogara ta tashi da k'arfi har takai
kanta toilet d'in, saida ta k'ara saka wasu ruwan zafin sannan ta kama ruwa dasu
tare da yin wanka tayo alwala sannan ta fito, sallaya ta shinfid'a ta d'auko
doguwar rigar Salman ruwan k'asa ta saka.

Zaune tayi bakin gado tana sauke numfashi dan kwance kawai take so tayi, Salman ne
ya shigo da plate d'in indomie da robar madara da ruwa a hannunshi, ajewa yayi gefe
ya kalleta yace " da alama kin fara cin gadona tun yanzu, ina fatan dai kinyi
sallah?"

Cike da shagwab'a ta turo baki tace "kai nake jira ka d'auko min hijab, tunda kai
ma ka ci gadon k'afafuna."

Dariya ya tin tsire da ita har ya fita daga d'akin yana dariya, yana kawo mata ta
saka ta kabbara sallah a daddafe, tana sallamewa tabi lafiyar sallaya ta kwanta dan
ko kad'an zaman babu dad'i, Salman daya fito daga wanka ne ya kalleta yace "malama
tashi kici abincin mana, idan kin ida kya fad'amin me kika ji."

Da sauri ta d'ago kai ta kalleshi tana fad'in "na fad'a maka me?"

Juyowa yayi ya kalleta yace "karki damu, ina nufin ki fad'amin ya kika ji abincin."

Ajiyar zuciya ta sauke tare da sake komawa ta kwanta, har saida ya shirya cikin
wata dalleliyar shadda (couleur préféré) d'inshi bleue sai walk'iya take kai dagani
ka san ansha kud'i wajen, ga hula da takalma da agogo ta fata duka kalar d'inkin
rigar bak'ak'e, wani irin shek'i ne fuskarshi keyi kamar sabon wata dan sha hud'u,
bayan k'yali da fuskarshi keyi ga tsantsar kyanshi daya k'ara fitowa fili, k'amshi
kawai yake zubawa na had'add'en turarenshi DOLBY, sak ya fito angonshi.

Da kanshi ya zo ya bata abincin sannan taci tasha madara ya bata magani tasha,
saida yasha rarrashi kafin ta yarda tasha maganin.

Kwance ta sake komawa yana kallonta yace "anya kuwa Ummi zaki kai yamma, ko dai na
d'auko wuka na k'arasa ki kafin ki min musai."

Sai dai ba tayi magana sai ko amai ya sub'uce mata, sosai tayi amai dan saida ta
maido duk abinda taci, hankalin Salman ya tashi sosai duk ya rud'e ya rasa ya
zaiyi, yana gyara mata jikinta d'auke sallaya ya wanke ya shanya ya dawo wajenta ya
zauna yana kallonta.

"Ummi bari na d'auko maki kaya ki canja sai muje asibiti a duba min ke, dan
watak'ila har na samu k'aruwar yaro ko yarinya."

Kunya ce ta rufeta ta fad'a jikinshi tana dukan k'irjinshi, zameta yayi daga
jikinshi yace "ina zuwa."

Riga da zane ya d'auko mata simple d'inki ba kwalliya sosai, saida ya canja mata
kaya kawai ta dage ita babu in da zata je kawai taje a mata tonon asiri sai kowa ya
san me ya faru.

Dole ya sake bata paracétamol tasha bayan tasha madara dan cikinta babu komai,
komawa tayi ta kwanta ya rufeta da bargo ba jimawa bacci ya sake d'aukarta, ya
jima yana kallon fuskarta gaba d'aya sai yaga yau tafi masa kyau akan kullum, wani
shek'in amarci take ita kanta, falo ya dawo ya zauna dan dama ita yama kwalliyar
kallo ya fara cike da farin ciki murmushi ya kasa barin fuskarshi dan har yanzu
yana taro daren jiya, daren daya fi kowane dare a wurinshi daren da ba zai tab'a
mantawa dashi ba, ajiyar zuciya ya sauke fuskarshi d'auke da k'asaitaccen murshi
yace,

"Ummi ba dai zafi ba."

_Hum wai zafi._😏😏😏


25/03/2019 à 16:14 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

~ALLAH YA BARMU DA MASU SON MU~

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*
8⃣7⃣8⃣8⃣
8⃣7⃣-8⃣8⃣

Har sallah azahar Ummi na bacci saida Salman ya dawo daga masallaci ya tasheta tayi
sallah, tana kammalawa ta fito falo da tafiya kamar mai koyo tana zuwa ta zauna
k'asa kusan k'afafun Salman, saukowa yayi ya zauna kusa da ita yana fad'in
"aljannata ya jikin naki?"

Kallonshi tayi da mamaki tace "aljannarka kuma, yanzu kenan na tashi daga aljana na
koma aljannarka?"

Gira ya d'aga mata yace "in dai har Ubangiji yana bamu aljanna a duniyar nan, to ni
kece aljannata."

Had'a kanta tayi da gwiwa tana murmushi, yana ganin haka ya fara mata cakulkuli
yana fad'in "tunda ba zaki fad'a ba sai mu sake komawa ciki."

Ummi kam dariya take tana bille bille duk ta hayeshi, saida yaga hawaye sun fara
fitowa a idonta tsabar dariya sannan ya daina, ba tare data tashi daga jikinshi ba
ta gyara kwanciyarta ta yanda suke kallon juna tace "nifa yunwa nake ji."

Wani kallon so ya mata yace "na sani dama dole zaki ji yunwa, amma kiyi hak'uri na
kira Mama na fad'a mata kuma yanzu zata aiko maki da abinci."

Cikin yaushi ta kalleshi tace "yanzu fad'awa Mama kayi?"

"A'a, na dai fad'a mata ba kiyi d'ori ba tasa dake a nasu."

Kallonshi tayi tace "yaya Salman na d'auka fita kayi duk kasa hankalina ya kasa
kwanciya."

Cike da mamaki yace "me yasa?"

"To ai naga kayi kwalliya ne dayawa, kuma naga ko a aurenmu ba kayi irinta ba."

Dariya yayi yana kallon fuskarta yace "kwalliya fa,to kenan kwalliyarce ta d'aga
maki hankali?"

"Yaya Salman ina jin baka duba madubi ba bane shi yasa, kai kyakyawane kuma yau
naga kafi kullum kyau, kaga dole hankalina ya tashi dan ban san da suwa zaka had'u
ba."

"Wai mata kike nufi?"

Turo baki tayi tace "Eh mana."

Gashinta ya fara shafawa yana fad'in "da a jiya kika fad'i haka kafin dare, to da
saina yarda, amma yanzu ni Salman na Ummi ne ita kad'ai babu k'ari."

Murmushi tayi sosai hakan yasa ya saka d'an yatsarshi a kurmin kumatunta yana
kallonta cewa tayi "amma fa yaya Salman kai kace zaka k'ara aure."

"Eh, a dah kenan, amma banda yanzu da Ummi ta zama ta Salman suka had'u suka zama
manyan yara."

Dariya tayi tace "ni dama babbar yarinya ce."

"Da gaske, to shikenan zamu gani."


Cikin shagwab'a tace "yaya Salman da gaske ba zaka k'ara aure ba?"

Murmushi yayi yace "ba zan k"ara in dai kina tare dani."

Tashi tayi zaune ta tara mashi tafin hannunta tace "ka rantse ba zaka k'ara ba."

Fashewa yayi da dariya ya janyota jikinshi ya had'e kanta da k'irjinshi yace


"Allah ya shirya min ke."

Tashi tayi daga jikinshi tace "yaya Salman wallahi da gaske nake, in san samuna ne
na zauna da kai ni kad'ai, wallahi ba zan juri ganinka da wata mace ba."

Tsaida dariyar sa yayi ya sauke ajiyar zuciya, tabbas ya fahimci da gaske take kuma
ga dukkan alama Ummi zata iya yin komai dan taga ta sameshi ita kad'ai.

Ganin baiyi magana yasa Ummi tace "yaya Salman dan Allah kamin alk'awarin zama dani
ni kad'ai, idan kamin haka ni kuma zan zama kamar baiwa a gareka, ba zan tab'a
gajiyawa da hidimarka ba insha Allah."

Fashewa tayi da kuka, dan yanzu kam yanda take jin Salman a cikin zuciyarta ba
kamar kullum ba, zuciyarta ta gama tunbatsa da soyayyarshi, sake kwantar da ita
yayi a k'irjinshi yana fad'in,

"Kiyi hak'uri Ummi, ki daina kuka bana san ganin hawayenki, kuma in dai akan
maganar k'arin aurena ne yasa kike kuka, to ki kwantar da hankalinki dama wasa nake
maki babu wani auren da zanyi yanzu, ke kad'ai kin isheni rayuwa."

Cikin kuka tace "da gaske?"

"Da gaske nake Ummi, kece kika sabinta min rayuwata, burina yanzu shine na samar da
farin ciki a rayuwarki kamar yanda kika sani farin ciki nima."

"In ko hakane yaya Salman, to kasa a ranka cewa daga yanzu farin ciki shine abokin
rayuwarka, bak'in ciki kuma sai dai kaji a wani wuri, in dai ina raye babu kai babu
shiga kunci da yardar Allah."

D'agata yayi daga jikinshi ya d'ora hannayenshi a kumatunta suna kallon juna,
murmushi ya sakar mata yace "zanyi iya bakin k'ok'arina wajen ganin na samar da
farin ciki a tare dake, Ummi ki zauna tare dani, nima zan zauna tare dake tare da
killaceki anan har k'arshen rayuwata." ya fad'a tare da d'ora hannunshi a
k'irjinshi b'angaren da zuciyarshi take.

K'ayataccen murmushi ta sakar masa tare da had'e hannayensu waje d'aya tace "insha
Allah, zan zauna da kai har abada, zamu rayu tare cikin so da k'aunar juna, tunda
har kamin alk'awarin zama dani ni kad'ai."

Kallon mamaki ya mata kafin yace "aljannata, nifa ban maki alk'awarin zama dake ke
kad'ai ba, amma fatana da burina shine na zauna dake ke kad'ai, alk'awari wani
muhimmin abune wanda idan kayishi yana buk'atar ka cikashi ko dan kiyaye imaninka,
Ummi ban san rayuwar da Allah ya tsaramin ba anan gaba."

"Ummi mun tashi a babban family, wanda ya had'a mutane iri iri muna ganin masu mata
sama da d'aya, mafi wayancinsu basa cikin farin ciki sai tashin hankali, amma ana
b'oyewa saboda gudun b'acin ran Alhaji."

"Ummi bana fata nayi rayuwa irin ta iyayena, ban san ko kin tab'a fahimtar zamansu
ba?amma basa farin ciki da junansu, tunda na fara mallakar hankalin kaina na
fahimci haka duk da suna b'oyewa kar a fahimta, Ummi duk tsawon lokacin nan da suka
d'auka wallahi har yanzu basa k'aunar junansu musamman ma Mama, na tabbata rabone
ya kawomu duniya amma kamar yanda Mama bata son mahaifinmu haka ma bata k'aunarmu
kamar yanda kowace uwa ke k'aunar nata 'ya'yan, na san dole akwai soyayya ta
tsakanin uwa da 'ya'ya amma dai nuna mana ita ko kad'an ba tayi, wannan ne yasa na
fahimci matsalar dake cikin *AUREN HA'DI*.

"Zan godewa Allah da yasa abinda nake tunanin ba zai yiwuba ya yiwu, ko a mafarki
ban tab'a tunanin zamu so junanmu ba, amma gashi iko na ubangiji yasa mun zama
d'aya kuma masu k'aunar junansu, Ummi a kullum ina ji ina ma ace La Mama ita ce
mahaifiya saboda uwace da kowane d'a zaiyi burin mallakarta a matsayin uwa saboda
jajircewarta akan tarbiyar yaranta."

"Soyayyar da take nuna min tana sani farin ciki, kamar yanda kema kinfi jin dad'in
zama da mahaifiyata da haka nake mana fatan farin ciki mai d'orewa tare da
iyayenmu, Allah kuma ya bamu jikan da zasu soshi fiye damu, akan k'ara aurena kuma
ki kwantar da hankalinki bani ba wata."

Rumgume juna sukayi sosai kamar zasu had'e waje d'aya, Ummi ce tace "hakane yaya
Salman, ina jin dadin zaman gidanku saboda a waccen lokacin tunanina shine
mahaifiyata bata sona, a gidanku kad'ai nake samun hutu amma a gidanmu, kamar baiwa
La Mama take mai dani bana baccin safe saboda dafa abincin kari, bana baccin rana
saboda sarrafa na rana idan kuma na gama ba zan kwanta ba tace yana saka ragwanci,
saina tabbatar na aje komai a in da ya dace kafin na kwanta baccin dare, bayan
kankanin lokaci zata tashemu sallah dare duk wannan lokacin gani nake tana takura
mana ne, kullum hirar mu da ita bai wuce yanda za muyi ba idan munyi aure kullum
maganarta dai miji miji, gani nake kawai tana so mu zama kamar bayin mazane ashe ba
haka bane gatane take nuna mana wadda uwace kad'ai take nunawa yaranta shi."

Kallonta yayi yana shafar fuskarta yace "La Mama akwai tsanani, amma kuma tana
yinshi ne dan saboda taga kun zama mutane na gari, ni kaina baki ga yanda take min
fad'a ba idan nayi ba daidai ba?"

K'ara matseshi tayi tace "gaskiya ne, nima yanzu na gane komai soyayyace tasa take
mana haka."

K'aran bubbuga k'ofa suka ji, dan haka Salman ya kalleta yace "gimbiyata, ko zaki
iya yimin izini naje naga ko waye?"

Cikin shagwab'a tace "to waye yazo da yake neman rage min jin dad'i?"

"Umm, ina jin mai kawo abincin ne yazo, amma kiyi hak'uri ai yanzu zan dawo ba
dad'ewa zanyi ba, idan na dawo kinga ko goyaki sai nayi."

Cikin kasala ta tashi shi kuma ya fita, har ta zauna ta koma ta kwanta dan har
yanzu tana jin zafi a k'asanta sosai, bai jima ba ya dawo d'auke da kulolin abinci
guda biyu, yana zuwa ya aje ya nufi cuisine ya d'auko plate da cuillère tare da
ruwa da jus da kuma madara domin Ummi.

Zuba masu yayi shinkafa da miyar naman rago, sosai Ummi taji dad'in abincin haka
suka ci suka k'oshi, haka suka ci gaba da hira abinsu kai kace Ummi da Salman sun
jima suna soyayya, shagwab'a kawai take zubawa san ranta yayin da Salman keta biye
mata yana rarrashi koma kamar k'aramin yaro, haka ya wuni gida masallaci kad'ai ke
fitar dashi waje yana idawa zai dawo gida su ci gaba daga in da suka tsaya.

Haka suka kwana mak'ale da juna kamar za'a rabasu duk da Ummi tana jin kunyarshi
har yanzu bata iya had'a ido dashi, Ummi ta yarda su kwanta tare ne saboda yace
mata babu abinda zai faru, dan har yanzu tana jin ciwo zata so ya barta har taji
sauk'i sosai in yaso aci gaba, shi kam yayi ta mazane ya daure amma ko yanzu aka ce
dashi ya k'ara k'arawa zaiyi da gudu, dan har yanzu yana tuna daren jiya.

*DAREN JIYA* manya sunan wani film ne.🤣


25/03/2019 à 16:14 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

8⃣9⃣9⃣0⃣
8⃣9⃣-9⃣0⃣

A hankali Salman ya bud'a idonshi ya sauke a b'angaren da Ummi ke kwance, ganin


bata nan yasa ya tashi zaune saida ya wartsake kafin ya sauko daga kan gadon yana
jinshi kamar wani sarki, toilet ya fad'a dan yin wanka dan yasan Ummi watak'ila
tana aiki ne.

Tsaf ya shirya cikin wata had'ad'iyar shadda maroon, sosai kayan suka masa kyau sai
dai bai d'ora hula ba wannan karin, fitowa yayi daga d'akin sai dai babu Ummi a
falo amma kuma yasha gyara sai k'amshin turaren wuta yake had'e da airfreshner,
saida ya k'are kallon falon kafin ya shiga d'akin Ummi nan ma bata nan sai gyaran
d'akin da tayi, fitowa yayi da nufin ya shiga cuisine, turus ya tsaya yana kallon
Ummi dake aje wasu manya plate a dinning.

Ba wannan ne ya tafi dashi ba illa kayan dake jikinta, kayan da akafi sanin buzaye
ne dasu colour ja daya k'ona sosai kamar jinin kare masu kwalliya sosai rigar iya
gwiwa da zaninta bak'i, duk da kayan manya ne bai hana su fito mata da surarta ba,
d'aurin d'an kwali simple tayi ta maida jelarshi saman wuyanta b'angaren dama,
sakin gashinta tayi ya bazu a bayanta sai mak-eup da tasha sosai dan dama gwana ce
wajen iya kwalliya kawai dai bata son yine, sai dogayan takalmin data saka
bak'ak'e.

Haka ya k'araso in da take baki bud'e yana kallonta, rumgumeta yayi ta baya tare da
tusa kanshi tsakiyar wuyanta yana sumbatar ta, murmushi ta saki ta langab'ar da
kanta ta d'ora a nashi kan suka had'e waje d'aya tana fad'in "ina kwana *MON
ANGE*."

Cikin murya k'asa k'asa ya amsa da "lafiya lau aljannata, kin tashi lafiya?"

"Lafiya lau na tashi nima."

Juyowa yayi da ita saida ya k'are mata kallo ya rik'o hannayenta biyu yana murmushi
yace " *MA REINE* kinga kuwa yanda kika had'u? ashe dama b'oye mana kyawun kike kar
mu gani.?

Wani shu'umin murmushi tayi ta fara shafar k'irjinshi cikin salo tana kallon
idonshi tana fad'in "lokaci ne yayi na in bayyana, dama ina b'oyewa ne saboda
banga wanda ya dace daya gani ba, amma yanzu dana samu sahibin raina shi yasa zan
fara nunawa."

Cikin sigar zolaya yace "ashe dai kin jima kina sona shi yasa ma kika guji tayar da
kishi na, dan kinsan ina da kishi sosai."

Fari tayi da ido kamar wata 'yar duniya tace "kusan hakane, dan tunda na lura kana
da kishi na daina kwalliya gaba d'aya."
Murmushin da tayi tare da ci gaba da gyara dinning d'in yasa Salman fahimtar magana
ce ta fad'a masa, cabko k'ugunta yayi yana fad'in "me kike nufi kenan, kina so kice
nima ina sonki tun waccen lokacin?"

Cikin dariya tace "ban sani ba, amma dai nasan gabanka na fad'uwa idan ka ganni
saboda tsoro."

Hancinta ya kama yaja tare da fad'in "ke ko, wallahi baki da dama, to waya fad'a
maki haka?"

Cike da dariyar mugunta tace "da kaina na gane hakan."

Hararanta yayi yace "ta yaya kenan?"

Tana kallon idonshi tace "daga yanda kake had'a gumi idan muka had'u, sannan baka
cika san kallona ba."

Wata irin dariya yayi tare da janyota jikinshi suka rumgume juna suna dariya, Ummi
ce tace "kaga zauna ka ci abinci."

Sakinta yayi yaja d'aya daga cikin kujerun yana fad'in "me kika dafa min?"

Bud'a plate d'in tayi wanda tayi had'add'en ordevre d'ayan kuma salade, sai bred da
aka yanka aka tsomashi cikin ruwan kwai da kuma lemon orange da aka matse ruwanshi
(natural).

Saida ta had'a komai sannan ta zauna suka fara cin abincin cikin nishad'i, Salman
ne ya kalli Ummi yace "amma fa kinyi k'ok'ari, duk wannan aiki ace da safe kika
yishi."

Murmushi tayi tace "to miye a ciki, bauta ce kuma ko ba komai wa mijina nayi."

Cike da gamsuwa yace "hakane, Allah ya miki albarka."

Cike da jin dad'i tace "ameen *MON ROI*."

" *ZEINAB*." ya kira sunanta cikin wata murya mai nuna tsantsar abinda yake so ya
fad'a daga zuciyarshi yake.

D'ago manyan idonta tayi ta sauke a kanshi, tana jin wani abu a cikin ranta duk
lokacin daya kira sunanta, cikin sanyin murya ta amsa mashi da "na'am."

"Ina sonki, ina sonki son da ba zan iya misalta shi ba, Dan Allah Zeinab karki
barni ki zauna tare dani har abada, idan kika barni ban san wane irin garari zan
fad'a ba, amma nasan zan shiga bala'in daya fi na baya, dan kece kika sabinta
rayuwata ta hanyar jiyar dani abinda ban tab'a ji ba tunda nake a duniyar nan."

Aje cokalinta tayi ta kalleshi tana fad'in "haba yaya man, me yasa kake tunanin zan
iya rabuwa da kai? karfa ka manta a baya ma mun zauna tare lokacin da bama jituwa,
to sai yanzu ne zamu rabu bayan ni da kai duka muna da tabbacin rayukanmu zasu
shiga had'ari idan har muka nisanta da juna, ai kaga wannan ba abu bane mai sauk'i,
ni Ummi ina tare da kai har izuwa numfashina na k'arshe da yardar Allah."

Kamo hannunta yayi ya janyota zuwa kujerarshi ya zaunar da ita akan cinyoyinshi
yana shafar fuskarta yace "nagode sosai Ummi, in haka ta kasance ni kuma Insha
Allah zan kula da ke ta yanda kowace mace zatayi fatan ina ma ita ce ke."

Cokali ya d'auka ya soma bata abincin a baki ita ma tana bashi har suka kammala,
Salman ne yace zai fita Ummi har da kuka wai ba zai tafi ya barta ita kad'ai ba, da
k'yar ya lallab'ata tare da mata alk'awarin ba zai dad'e ba zai dawo.

Bayan fitarshi Jawahir ta kira Ummi bayan sun gaisa Jawahir ta fara tsokanarta wai
"Hajia Abu naji ance yanzu kin fara mulki a gidan yaya Salman, dan ance jiya ko
fita baki bari yayi ba."

Dariya Ummi tayi sosai kafin ta tsaya tace "oh Allah, yanzu wai ace gulma ta bar
kan mata ta koma kan maza, wannan ai shine sa ido kana rayuwarka amma mutane idonsu
yana kanka, bamu damu da kowa ba amma kinji har an fara barbard'amu, ai na d'auka
sai mara aikin yi ke sa ido ashe kice har yaya Khamis ma ya fara tab'awa."

Gimtse fuska Jawahir tayi kamar suna gaban juna tace "ke bana san iskanci, mijin
nawa ne d'an sa ido?"

Tsaida dariyarta tayi tace "Eh mana, shi d'in, nasan shine ya fad'a maki dan shi
kad'ai ya san da haka."

Dariya Jawahir tayi tace "ashe dai gaskiya ya fad'a kin fara mulkin, kin san wani
abu? nifa ina so naga yaya Salman yana maki k'aramar murya."

"Eh, na fara d'in sai me? kinga fad'a min abinda yasa kika kirani, dan bana da
lokacin ki tashi zanyi na sake sabon shiri kafin mijina ya dawo."

Cikin d'aga murya Jawahir tace "Iye, yarinyar nan fa ba kida dama, da alama wannan
hutun na makaranta ya maku dad'i ko?"

"Sosai kam, nifa watak'ila ma ba zaku sake ganina ba koda an koma makaranta, dan na
riga dana gano abinda yafi min karatun wato kula da mai gidana."

Dariya sosai Jawahir tayi har saida Ummi ta fara k'ulewa sannan tace "haka ya maki
kyau, ba kuma zan hanaki ba dan ban san zumar da yaya Salman yake d'ubga maki ba
kina sha."

D'orawa tayi da "dama cewa nayi bari in kira in fad'a maki gobe réunion na famille
na k'arshen wata, dan Allah Ummi wannan karan ki takura yaya Salman ya barki ki zo
kema cikin 'yan uwa kiga mutane mutane su ganki."

Cikin sanyin jiki tace "zan k'ok'arta amma fa banda takura masa, dan abune da ba
zanso wani ya masa ba bare kuma ni, idan ya barni zaki ganmu tare, idan kuma bai
bari ba, to zaki ganshi shi kad'ai."

"Amma dai ya kamata kiyi k'ok'ari ko dan ki had'u da 'yan uwanki, karfa ki manta
tunda ki kayi aure ko sau d'aya baki ziyarci gida ba sai kace wata matar kulle."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "to ya zanyi, kullum cewa yake wai saina zama
cikakkiyar mace, ban sani ba ko yanzu zai fara barina tunda na zama yanda yake so."

Cike da zolaya Jawahir tace "ke dan Allah 'yer uwa, kenan dai kice an kashe boss
mai film na likita."

Tsaki Ummi tayi tace "kinga matar Khamis sai an jima, idan zanje na kiraki."

Tana fad'a ta kashe wayar ta fad'a kogin tunanin yanda rayuwarsu ta canja cikin
k'ank'anin lokaci, dan bata tab'a tunanin ko nan da shekara d'aya ba zasu fara
fahimtar junansu bare kuma maganar soyayya.
***************

Kamar yanda ya mata alk'awari, bai jima ba ya dawo gidan dan tare sukayi girkin
rana dama na dare, sosai suka shiga nishad'i su kansu take suka fahimci tsantsar
farin cikin da suke ciki, suna jimawa kafin su kammala girkin saboda duk rabin
aikin soyayyarsu suke bugawa tare da wasanni.

Saida sukayi shirin kwanciya sannan Ummi ta fad'ama Salman tana so taje réunion
gobe ita ma, ak'alla saida yayi minti d'aya kafin ya kalleta yace "Ummi kiyi
hak'uri, ba zan barki ki fita gobe ba tunda har yanzu jikinki babu kyau."

Shiru tayi na 'yan dak'ik'u tare da tuna abinda mahaifiyarta ta fad'a mata a irin
wannan gab'ar, ajiyar zuciya ta sauke cikin tattausan murya tace "shikenan *GORKO*,
ba komai Allah yasa haka shi yafi alkairi."

Wani hamshak'in murmushi yayi ya shafi fuskarta yace "da kyau haka ake so, amma
waya fad'a maki sunan miji da fulatanci."

Kafin tayi magana yace "au, na manta fa, ashe ke d'in 'yar Mama ce dole ki iya
yarenta."

Cike da shagwab'a tace " Eh mana, kuma nasan ko kai dake ba fulatanin baka kaini
jin yaren ba."

Dariya yayi yace "a'a nanfa d'aya, karki ma had'a kanki dani, dan ni kullum cikin
yaren nake dan wani lokacin Mama bata min hausa sai fulatanci."

Tab'e baki tayi ta fara magana tare da nunashi da yatsa tana kalkad'ashi tace "amma
ka sani tunda ba zani ba, to kaima ba zaka da wuri ba, dan haka sai kayi sallah
azahar a gidan sannan ka tafi."

Dariya yayi yace "na yarda ma reine."

Daga haka suka lula duniyar ma'aurata, duk da dai Ummi sabon shiga ce babu abinda
ta iya yi daya wuce sauraren Salman na juyata son ranshi.

Ko kad'an abin ba sauk'i, dan kuwa yau tafi shan wahala fiye da shekaran jiya sai
dai kawai waccen shine farko, dan haka rad'ad'in ya banbanta, Salman kam a ganinshi
kuma a tunaninshi ai Ummi yanzu ba sabuwar shiga bace dan haka ya zage damtse ya
d'irki abarshi son ranshi, ganin abin bana k'arau bane yasa Ummi ta fara kuka tana
rok'on ya barta, da k'yar ya barta ko motsi ba tayi ba bacci ya d'auketa tana
numfashin wahala, Salman kam tsayuwar dare yayi yana saka ma Ummi albarka har
sallah asuba sannan ya tasheta ya had'a mata ruwa tayi wanka sannan ya nufi
masallaci.
25/03/2019 à 16:14 - Mamar Latif💃: 💑 AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

``` 'YAN UWA GASKIYA INA GODIYA DA IRIN K'AUNAR DA KUKE NUNA MIN```😍

*AUREN HA'DI, DUK DA CEWA NAYI LABARIN SHEKARA BIYU DATA WUCE, AMMA YANZU SAI NAKE
JINSHI KAMAR YANZU NE FARKO SABODA IRIN MASOYAN DAYA SAMU, DUK DA NA SAKE WASU
ABUBUWA A CIKI DAN WANDA SUKA SAN LABARIN A BAYA ZASU FAHIMCI HAKAN, AMMA KUMA
SUNCE WANNAN D'IN YAFI MASU DAD'I SOSAI.*👏🤝🤜🤛

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

9⃣1⃣9⃣2⃣
9⃣1⃣-9⃣2⃣

Tunda Salman ya lura da Ummi duk tayi sukuku da ita jikinta babu k'wari, hakan yasa
yace mata "nifa tea nake buk'atar nasha mai kauri da kuma bred, dan duk jikina babu
k'wari duk na k'arar da kazar kazar d'ina jiya."

Hararanshi Ummi tayi tare da fad'awa jikinshi tace "bana so fa ka daina."

Dariya yayi yace "to shikenan na daina, yanzu zaki iya had'amin abin karin, ko na
had'a da kaina kema saina had'a maki?"

Kwance tayi akan doguwar kujera tare da fad'in "ka had'a kawai nima saika kawo min,
tunda ka gama gajiyar dani."

Cuisine ya nufa yana fad'in "an gama ranki shi dad'e, yanzu zan wadata gabanki da
abin kari."

Haka ya had'a abin karin har da soyayyen k'wai, haka suka ci suka gama kafin suka
shiga wanka tare suka fito, sun d'auki kusan awa d'aya kafin su gama shiryawa su
fito falo saboda soyayya da wasa cikin raha.

Misalin k'arfe 09:40 Salman ya kalli Ummi yace "kinga tashi ki canja kayanki kizo
mu wuce ko."

Da mamaki ta kalleshi tace "zuwa ina kenan?"

Kallonta yayi yace "Ummi burin kowane namiji shine ya samu macen da zai bata umarni
kuma tabi kai tsaye ba tare da jinjina al'amarin ko tambayar dalili ba, kin
faranta raina jiya a lokacin da nace ba zaki ba kuma kika amince ba tare da kin
b'ata ranki ba, to in dai har kinyi hakane dan ki faranta min ko dan biyayya a
gareni, to ni me zai hana nayi haka dan na kyautata maki, dan haka jeki ki shirya
nasan baki manta colour d'in kayan da ake sakawa ba."

Cike da farin ciki Ummi ta mik'e tsaye tace "kai mijina gaskiya naji dad'i sosai
wallahi, Allah ya saka da alkairi, to tashi muje mu sake kayan tunda kaima ba sune
a jikinka ba."

Tashi yayi tsaye tare da rumgumota yace "to amma sai in ke zaki saka min kayan,
kin yarda?"

Cike da tabbatarwa tace "oui j'accepte."

Tare suka shirya suka fito, masha Allah sunyi kyau sosai kasancewar shadda bata
cika birge Ummi ba hakan yasa ta shirya cikin wani rantsantsan boyel fari tas mai
duwatsu farare, riga da siket ne sosai kayan suka kama jikinta cif suka fito da
surarta, farin hijab da sac da takalmi ta saka sai dai ba tayi kwalliya ba sai jan
jan-baki data saka.

Haka ma Salman farar shadda yasa dogon d'inki ne aka mashi kalar zaren da aka
mashi kwalliyar dashi, kalar takalma da hular da agogon da yasa bak'ak'e, saida
suka d'auki kansu photuna kafin suka fita suka bar gidan.
Ummi bakinta yak'i rufuwa saboda farin ciki, haka har suka kai gidan Alhaji gaba
d'aya Ummi gani tayi unguwar ta sauya mata kamar ba in da ta tashi ba, Ummi na
fitowa daga mota yara dake wasa k'ofar gidan kowa da fararen kayanshi suka tarbeta
da murnarsu tsalle kawai suke wasu na fad'in "aunty Ummi, wasu na fad'in aunty,
wasu na fad'in Ummi sak, wasu na fad'in tanti."

Masha Allah gidan ya cika tamk'am da 'yan uwa 'ya'ya jikoki da 'yayan jikokin,
nan Ummi ta dinga kwasar gaisuwa ga manyanta dama na k'asa da ita, kowa dake wajen
yayi mamaki da kuma farin cikin ganin Ummi da Salman a tare, ko ba'a tambaya ba
kasan suna farin ciki dan dukansu jikinsu ya nuna hakan, fatarsu tayi fresh kamar
k'wai ga k'iba da Ummi ta k'ara, hakan ba k'aramin dad'i yama mutanen dake wajen
ba.

Mamar Nuseiba da Mama Hawa basu ji dad'in hakan ba, dan kuwa a tunaninsu shirin
Ummi da Salman kamar barazana ne ga 'ya'yansu wajen hanasu shiga gidan Salman a
matsayin mata, Ummi ma haka ta gaishe dasu sama sama ba kamar yanda tama kowa ba,
dan a ganinta suna so su rabata da farin cikinta ne, su Jawahir murna har tayi
masu yawa saboda ganin Ummi, saida ta gama gaisawa da kowa ta shiga babban falo nan
ma ta jima sosai suna gaisawa da kakanin nasu suna tsakonarta ita da Salman wai sai
yau ya barta ta fita har yasa ta kod'e fatarta ta fice tayi haske.

Alhaji kamar ya d'aukesu ya goya ganin yanda suka zama abin sha'awa, gashi alamu ya
nuna suna zaune lafiya da junansu, Mamar Salman kam tunda ta zauna kusa da Ummi ta
d'ora kanta a saman cinyarta tana ta shafar kanta fira kawai suke gashi ta hanata
ta tashi suyi hira dasu Jawahir da suke fama da 'yan cikunnansu da basu wuce wata
hud'u ba, duk da basu girma ba amma kallo d'aya zaka masu ka gane dan ya d'an turo
rigunansu gaba.

Mama duk tunaninta shine Ummi ma ciki gareta shi yasa take ta nan-nan da ita kamar
jaririya, haka Ummi ta kwanta saman k'afafun sarakuwar tata hira kawai ake sha cike
da farin ciki wanda kuma dama wannan ne musababbin yin taron a kowane k'arshen
wata.

Salman kam kallon mahaifiyar tashi kawai yake tare da matar tashi da suke hira
abinsu kamar ba surukai ba, farin ciki da soyayyar Ummi na k'ara nunkuwa a cikin
zuciyarshi tare da girmanta, ya kuma yarda Mama zata iya yi masa komai akan Ummi
d'in.

La Mama ma kallonsu kawai take ita har kunya ma take ji, yayin da Mamar Nuseiba
ranta ke k'ara b'acewa tana ganin Mama ma zata iya basu matsala akan burin nasu,
haka aka dinga hira ana raha har sallah azahar sannan maza suka nufi masallaci mata
kuma suka fara aika tasu sallah a cikin gida.

Ummi na kammala sallah a d'akin Hajia Zeinabou ta mik'e ta cire hijabinta zata fito
falo, Hajiar ce ta kalleta cike da mamaki tace "takwara halan wasa kike da cin
abinci?"

Cikin rashin fahimta Ummi tace "me kika gani Hajia?"

Ci gaba tayi da d'aura d'an kwalinta tace "naga 'yan uwanki kowace cikinta ya fito,
amma banda ke, na sanki fa da tsinannen tamne tamne, kinga damar ki maida kayan
mak'ulashe abincinki."

Gyara tsayuwarta tayi tace "to Hajia su ba ciki garesu dole cikinsu zai taso mana,
ni kuma me na aje a cikin?"
Hajia tasan Ummi da barkwanci, dan haka tace "shikenan to."

Tab'e baki tayi ta bud'a labulen d'akin dan ta fito, tsaye tayi ganin Nuseiba da
Rumana zaune cikin 'yan uwa ana hira, kallonsu take sosai dan kamar ta shak'e wuyan
ko wacce a cikinsu take ji.

Salman ma idonshi na kan Ummi data fito babu hijab, ranshi ya b'ace duk da dai
kusan kowa dake nan haka suke, amma ai ya kamata ace ita ta rufe jikinta ko dan
yanda kayan suka ma jikinta d'araf, cikin sanyin jiki ta k'arasa fitowa ta zauna
wajen da La Mama ke zaune tare da Mama suna hira yayin da Mama ke gyaran zogale
saboda Ummi.

Nuseiba sarkin tsoro tuni cikinta ya d'uri ruwa dan tasan Ummi farin sani, tsaf
zata cinyeta ko ruwa ba zata sha ba, tunda tayi k'asa da kanta bata sake d'agowa ba
sai gabanta dake fad'uwa, har yanzu kuma tana nan akan bakanta akan son auren yaya
Salman duk da dai tana ganin canji yanzu daga wajenshi, kusan wata biyu kenan baya
kiranta babu text, idan ita ta masa baya maido mata to amma kuma duk da haka bata
sare ba, gashi yanzu ma da suka zo gaisuwarsu kawai ya amsa bai sake ko kallonta ba
bare kuma Rumana da dama ba ra'ayinta yake ba.

Ummi kam har yanzu bata daina kallonsu ba, juyawa tayi in da Salman d'in yake,
karaf idonsu suka had'e dana juna dan dama kallonta yake, kunya ce ta rufeta dan ta
d'auka za taga yana kallon d'aya daga cikinsu ne, k'asan da tayi da kanta tare da
d'an murmushi yasa Mama ta kalleta tace,

"Ya dai Ummi na?"

Cike da shagwab'a ta girgiza kai tana fad'in "ba komai Mama."

D'ora kanta tayi a kafad'ar Mama, La Mama kam take ta jefeta da wata harara wanda
tasa Ummi d'aga kanta daga kafad'ar Mama, duk a idon Mama hakan ta faru shi yasa
Mama ta sake maida kan Ummi a cinyarta tace "kwanta ke rabu da ita kinji."

Kallon La Mama tayi tace "dan Allah Hawatan ki rabu da yarinyar nan, haba kamar ta
tsare maki wani abu."

Hararan Ummi ta sake yi tana fad'in "kenan baki fahimci abinda nake nufi ba ko,ke
marar kunyar ina ce, wannan ba sarakuwarki bace da zaki maida ita kamar abokiyar
ki?"

Ummi na shirin d'aga kanta Mama ta sake kwantar da ita tace "bana san haka fa
Hawatan, akan me zaki takura mata, ke ko tausayinta ma ba kya yi? kuma mu babu
ruwanmu da wata surukanta ka ni a matsayin 'ya na d'auketa kuma ita ma uwa ta
d'auke ni, dan haka ki shafa mana lafiya muyi harkar mu."

Duk abinda suke Salman na kallonsu dan haka ya taso ya zauna k'asa ya lank'washe
k'afafunshi, Ummi ya kalla yace "ina kika baro hijabinki?"

Kafin tayi magana Mama ta bishi da harara tace "bata sani ba, dama dan ka mata
wannan tambayar ne ka zo nan?"

Sosa k'eya yayi yace "a'a, naga dai baya jikinta ne shi yasa."

"Mu da babu a jikinmu me yasa baka tambayemu ba?"

Baiyi magana ba La Mama ta kalli Ummi tace "wai ba dake ake magana kina ji kinyi
shiru, ki tashi ki d'auko hijabinki."
Tashi tayi tana shirin yunk'urawa, take siket d'inta tayi hakan yasa ta koma ta
fad'i zaune, da sauri ta rik'e k'ugunta ba dan taji wani abu dan gane da hakan ba,
da sauri Mama ta janyota ta rumgumata a jikinta tana kallon Salman tace "kai tashi
ka bani waje dan Allah, daga zuwanka kana nema kaja mana matsala."

La Mama cewa tayi "dan Allah ki barshi, ina kike so ya tafi daya wuce wajen
iyalenshi, ko yana da wanda suka fi mashi mune a duniya."

Da hannu Mama ta nuna shi tace "to ki fad'a masa kar ya sake shiga harkar 'yata."

Haka suka dinga sama da k'asa yaran na jinsu dan dama wannan ba sabon abu bane a
wajensu, Mama na gama gyaran zogalen ta tashi Ummi tare dasu Hafsat da Nadia da
Khairat suka ci Jawahir kuma tace bata ci.

Suna cikin cin zogalen su Sa'ada da sukayi girki suka fara rarrabawa kamar dai a
gidan biki, Ummi kam bata ci ba saboda zogalen data ci ta isheta, Mama kam saida ta
kalli Salman tace "yarinyar nan nasan bata damu da cin abinci ba, kuma kai da yake
sakarai ne baka damu da lallab'ata ba har ta samu ta ci, kanka kawai ka sani shi
yasa kake mulluk'a uwar k'iba kana barinta."

Kusan kowa dake d'akin saida ya dara, Hajia Abu ce tace "to ai zaifi idan kika mata
fad'a da kanki watak'ila taji maganarki, dan nima na lura da hakan kamar bata san
cin abinci."

Shagwab'e fuska Ummi tayi dan har yanzu bata fahimci in da zancen yayi ba, haka kam
kowa dinga sa baki yana fad'in ta dinga cin abinci kar tayi wasa da lafiyarta,
Salman ta kalla dake nesa da ita suna cin abinci tare dasu Khamis, ido ta masa
alama akan ita fa bata fahimta ba, shi ma da hannu ya mata alama ta hanyar d'ora
hannunshi a cikinshi sannan ya nunata da yatsa alamar ita, da sauri ta bud'a baki
ta dafe k'irji tana fad'in "ni d'in?"

Kallonta kowa yayi dan maganarta ta fito fili, haka aka kammala cin abincin daga
nan kuma Alhaji ya nemi da kowa ya bashi hankalinshi akwai muhimmiyar magana,
kusan yan mata biyar dake wajen babu wacce gabanta bai fad'i ba, dan sun san sun
isa aure kuma in dai har maganar aure ce Alhaji zaiyi to zaiyi wuya su tsallake,
daga ciki har da Nuseiba da Rumana.

Shiru kowa yayi yayin da Alhaji yayi gyaran murya ya fara da godiya ga Allah sannan
d'ora da "to, kamar yanda kuka sani ne a kowane k'arshen wata akan had'u ba dan
komai ba sai dan a sada zumunci tare da magance wata matsala data tun karomu ko
take shirin tun karowa."

"A wannan karin ma babu wata matsala sai dai akwai ranar auren dana tsayar a
k'arshen watan da zamu shiga, kenan nan da wata d'aya."

"Wannan karan AUREN HA'DI ne tsakanin, Nuseiba da ABDUL WAID, Rumana da KABIR,
Zaliha da BASHIR, Rafi'a da ISHAQ, sai kuma Fatima da JUNAID."

Cikin fitar hayyaci Nuseiba ta dafe kanta da hannu tana fad'in "na shiga uku, Abdul
waid kuma? ni dake burin ganin na zama matar rik'akk'en namiji kamar yaya Salman,
kawai saina b'ige da auren Abdul waid."

Da sauri Mamarta ta dafe mata baki tana fad'in "ke rufa mana asiri."

Kowa dake wurin saida ya kallesu anan kowa ya san manufarsu, Ummi wayyo dad'i
kasheta haba Ummi ai bata iya b'oye farin cikinta ba saida ta rangad'a bud'a irin
tasu ta buzaye tace "kakana Allah ya k'ara maka lafiya da nisan kwana, gaskiya
tunda nake ban tab'a jin dad'in AUREN HA'DIN da kayi ba kamar wannan."
Mama Hawa da bak'in cikin ya kawo mata wuya saboda bak'in cikin irin mijin da aka
had'a 'yarta dashi, cike da takaici tace "ke Ummi, haka kika ji kowa yace? wa kika
tab'a ganin yayi farin ciki da irin wannan ranar? ba kamata yayi ace kin taya 'yan
uwanki jimami ba."

Kallonta Ummi tayi tace "tanti jimamin me kuma?aure fa za'a masu, kuma sun isa bare
ace za'a masu aure shekarunsu basu kai ba, kuma naga ai sun iya soyayya."

Cikin b'acin rai Mama Hawa tace "ke uban wa ya maki haka lokacin aurenki?"

Cike da rashin tsoro Ummi tace "amma ai ni ban samu gatan da kowa ya samu ba,
k'wara su ansa masu rana sun kuma san lokacin jiranshi kawai za suyi, ni kuma fa
saida naji ance an shafa min fatiha."

"Amma dai Ummi ba kida mutunci, yaushe kika zama fitsararriya?"

"Ki gafarce ni tanti, banyi haka dan na b'ata maki rai ba, kawai na fad'a maki
gaskiyar abinda yake cikin zuciyata ne, kuma har ga Allah ba zan b'oye ba kan cewa
naji dad'in wannan had'in saboda an nesanta ni da k'udan dake bibiyar farin ciki."

Cike da tuk'uk'in bak'in ciki Mama Hawa tace "su wanene k'udan, ba dai 'ya'yanmu
kike nufi ba ko?"

"Ni dai ban....." marin daya sauka a fuskarta har guda biyu yasa tayi shiru, kumci
d'aya ta samu damar dafewa hawaye na zarya a kumatunta, Salman dake zaune wani gumi
yaji ya fara tsatsafo masa, ta d'auki kusan sakan talatin kafin taga La Mama a
gabanta ta kuma tabbatar ita ce kad'ai keda zarrar da zata iya dukanta, cikin
tsantsan b'acin rai La Mama ke magana da rufewar ido da takaici dan abinda Ummi
tayi ya k'ona mata rai fiye da kima.

"Ummi wannan ita ce tarbiyar dana baki, wannan ita ce tarbiyar dana koya maki raina
na gaba dake, Ummi me yasa kike so ke kad'ai ki zamar min k'arfen kafa, me yasa
kike so ki zamar min zakka a cikin 'ya'yana?"

"Ke kad'ai ce da ban a cikin yarana, masifarki ta fara hawan min kai, da farko kin
raina Salman rainin da ko matarka ta maka shi, to ta gama raina ka, yanzu kuma
shine kika zo mana da wani sabon iskanci rainin ya bar kan 'ya'yunku ya kuma kan
iyaye."

"To bari kiji wallahi na gaji da wannan iskancin naki, daga yanzu ba zan sake yarda
kina zubar min da mutunci a idon jama'a, Allah ya sani na baku tarbiyar data dace
da kulawa a matsayina na uwa, amma ke kullum k'ok'arinki ki watsar da abinda na
koya maku dan ki zubar min da mutunci."

Juyawa La Mama tayi cikin fushi ta bar gidan ta fad'a nasu gidan dan dama suna
kallon juna ne, Alhaji ne ya kalli Ummi yace "Zeinabou tashi kiba tantinki hak'uri
kinji."

Share hawayenta tayi ta mik'e har saida taje gaban Mama Hawa ta durk'usa tace "dan
Allah tanti kiyi hak'uri ki yafe min, wallahi ba zan sake ba."

Dafa kafad'arta tayi dan kar a gane b'acin ranta tace "ba komai ya wuce, ki share
hawayen kinji ko."

Kusan kowa dake wajen baiga laifin Ummi ba ,dan k'aramar magana ce tayi amma Mama
Hawa ta mayar da ita ciwon kai, wasu kuma da suka san nufinsu akan mijin Ummi dad'i
suka ji da abinda ya faru daga ciki har da jawahir da take sarakuwarta, Khamis ma
dake d'anta baiji wani abu ba dan babu wata bak'ar magana da Ummi ta fad'a face
gaskiya.
Gaba d'aya haka alhaji ya had'a kan iyalin nashi ya masu nasiha da gargad'i da
rok'on su zauna lafiya tare da masu addu'ar samun farin ciki mai d'orewa, ana
sallah la'asar kowa yayi sallah ya tattara nashi ya nashi ya tusa k'eyar yaranshi
gaba suka koma in da suka fito, Ummi duk jikinta yayi sanyi hankalinta ya koma kan
mahaifiyarta da ranta ke b'ace da ita, ta kama murfin mota zata bud'e Salman ya
kalleta cike da kulawa yace,

"Kinga, kije gida wajen La Mama ki zauna, zuwa bayan sallah isha zan dawo na d'auke
ki."

Duk da taji dad'i amma gabanta ya fad'i, kai kawai ta d'aga masa alamar to ta wuce
cikin gidan, hirar da Salman ya tsaya da Khamis yasa suka d'an d'auki lokaci a
tsaye, Ummi na shiga La Mama ta gani zaune tsakar gida tana yankan d'anyar kub'ewa.

Tana d'agowa taga Ummi ta tashi tsaye cikin b'acin rai ta d'auki muciyar da take
d'ora miyar akai tana yankawa ta jefo mata, kare kanta tayi tare da sakin yar
siririyar k'ara, cikin zafin nama La Mama tayo kanta tana fad'in...

😍😍😍 luv u guys.


25/03/2019 à 16:14 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

~Luv you guys~ 💋😍

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

9⃣3⃣9⃣4⃣
9⃣3⃣-9⃣4⃣

"Fita ki barmin gidan dan ubanki tun kafin na sabattaki."

Ummi kam fashewa tayi da kuku ta zube k'asa tana fad'in "dan Allah La Mama kiyi
hak'uri wallahi na daina ba zan sake ba daga yau, kuma ma na nemi gafarar tanti
gaban kowa, kuma ta yafe min."

Hararan sama da k'asa ta mata tace "ke d'in, ke dai dana sani ce zaki bada hak'uri
cikin sauk'i haka?"

"Wallahi La Mama da gaske nake, ki tambaya ma kiji idan k'arya na maki ki


hukuntani."

Zaune tayi akan kujerar data tashi ta ci gaba da yankan miyarta ba tare data
kalleta ba tace "ban san me yasa kike haka ba Ummi, ita fa kamar mahaifiyarki ce
amma ki rufe ido ki mata rashin kunya, alhalin duk ga yaranta a wajen, me kike so
suji a ransu kenan?ai haka bai dace ba ki daure ki gyara halinki ko dan rayuwarki
ta gaba, ki zama mai kau da kai ga abubuwan da ba zasu rageki da komai ba kinji
ko."

Tashi tayi ta matso kusa da La Mama ta duk'a tace "insha Allah zan gyara, kuma na
maku alk'awarin canjawa da yardar Allah."
Sai lokacin La Mama ta kalleta tace "Allah yasa zaki iya, yanzu ki tashi ki wuce
gidanki yamma nayi."

Murmushi tayi tace "La Mama ai yaya Salman ne yace nazo nan...." bata k'arasa ba ta
rufe bakinta saboda dukan da La Mama ta kai mata a bakin tana fad'in "mena fad'a
maki akan kiran sunan mijinki?"

K'wallan da suka taho mata ne ta matsosu suka fito tace "kiyi hak'uri, dama su
sukace nazo an jima zai zo ya d'auke ni."

Hararanta tayi tace "koda wasa kar na sake jin bakinki ya kira sunan mijinki haka
kawai, ko naji kin kirashi da kai ko shi."

*GARGADI*

```'YAN UWANA MATA MU KULA WAJEN KIRAN MAZAJENMU DA SUNAN, (KAI KO SHI) WALLAHI
BASU JIN DAD'IN HAKA, KOWANE NAMIJI YANA SO YAGA YA KUMA JI GIRMANSHI DAGA WAJEN
IYALINSHI, BASU HAD'A MATAN DAKE KIRANSU DA KU DA WACCE ZA TACE KAI, ALLAH YA BAMU
IKON KIYAYEWA.```

Turo baki tayi tace "naji ba zan sake ba."

Ba tare data kalleta ba tace "tashi ki wuce ciki to, kuma ina fata bake kika
tilasta masa barinki ki zo ba?"

Tsaye ta mik'e tace "wallahi La Mama bani bace, shi..."tayi shiru sannan ta sake
fad'in "su sukace nazo."

Juyawa tayi ta shiga d'akin da gudu, cikin d'aga murya La Mama tace "ke ke, zo
nan."

Kamar zata fashe da kuka haka ta juyo ta dawo ta tsaya, kallonta tayi tace "wai
yaushe za kiyi hankali? duk da abinda kike d'auke dashi sai kinyi wannan tsalle
tsalle kamar ba matar aure ba."

Da farko Ummi taso ta harbo jirgin, amma da tace kamar ba matar aure ba sai tayi
wani tunani na daban, dan haka tace "na daina."

Juyawa tayi ta shiga d'akin a hankali, babu kowa dan haka ta zauna ta kunna tv tana
kallo, zaman ne ya isheta dan haka ta sanyo hijab d'inta ta fito, La Mama na
ganinta tace "to azagwaigwai sai ina kuma?"

Saida ta had'iyi yawu tare da addu'ar Allah yasa kar ta hanata sannan tace "wajen
Mama zanje."

A hankali La Mama ta kalleta tace "kin fad'awa mijinki?"

Rarraba ido ta shiga yi dan haka La Mama tace "to koma ki zauna kamar yanda mijinki
ya umarceki har sai ya dawo."

Juyawa tayi tana kukan shagwab'a har ta shige ciki, dole ta hak'ura ta zauna har
saida su Islam da Momy dasu Mubasheer suka shigo sannan ta fara deb'e kewa.

Ganin La Mama nata fama a cuisine yasa Ummi ta tashi ta gyara falo da tsakar gida
dama wasu wajajen, tana kammalawa tayi alwala saboda kiran sallah da aka fara,
sallah tayi a tsohon d'akinta tana idawa bata tashi daga wajen ba ta maida
hankalinta ga Salman da kuma mu'amular data fara shiga tsakaninsu, gabanta ne ya
fara fad'uwa take tsoro taji ya rufeta gaba d'aya zulumi ta shiga, dan a ganinta
wahalar nan zata ci gaba da fama da ita kullum, gaba d'aya duk jikinta yayi sanyi
ta rasa meke mata dad'i har La Mama ta aiko Islam ta kirata.

Tana fitowa ta samu La Mama zaune akan sallaya tana lazimi, sunkuyawa tayi da nufin
ta zauna La Mama ta tsaida ita ta hanyar fad'in "zaman me za kiyi kuma? ki wuce
kije ki deb'o abinci kici, kinsan yanzu mijinki zai zo d'aukarki."

Cikin sanyin jiki ta wuce in da La Mama ta bita sa ido tana zancen zuci "Allah yasa
ba wannan dalanb'ayar kike masa a gidan ba."

Tana fitowa ta zauna gefen La Mama ta aje plate d'in dake hannunta, hannu tasa ta
fara cin tuwon, kallonta La Mama tayi tace "Ummi wannan abincin ne kika deb'o ki
ci?"

Kamar zatayi kuka tace " ya isheni haka La Mama."

Cike da tausasawa La Mama tace "kinga Ummi, kefa yanzu bake kad'ai bace dole kina
buk'atar cin abinci ko dan lafiyar d'anki, koke baki so ki haifi yaro d'an dumul
dumul?"

Cike da mamaki Ummi tace "La Mama, wai waya fad'a maku ina da ciki? nifa bana da
komai har yanzu."

Haka ma La Mama cike da mamaki tace "ban gane ba, kina nufin ba kyada ciki, to
kenan miye kike da da har yasa ki rashin lafiya har da amai?"

Ajiyar zuciya ta sauke tace "wancen lokacin ma fa kawai saboda naci abinci mai yawa
ne, amma ni bana da komai."

Kallonta sosai La Mama tayi kafin tayi k'asa da muryarta tace "Ummi, kin tabbata
kina bawa mijinki duk wani hakk'inshi?"

Shiru Ummi tayi na yan dak'ik'u kafin tace " La Mama ba zan iya tabbatar maku ba
saboda ban san zuciyar yaya, amma ina tunanin ina k'ok'ari a kanshi yanda ya
kamata."

"Kash Ummi, kinga ni kuma ba haka naso ba, Ummi naso ace kin yarda da kanki ta
hanyar bawa kanki tabbacin cewa kina kula da mijinki yanda ya dace, bai zama lallai
ace kin mashi yanda yake so ba d'ari bisa d'ari, amma koba komai ya dace ace ke
kiji a ranki cewa kin kai duk in da wata mace maiji da kanta ta kai wurin."

"Ummi ina so ki k'ara k'ok'ari ta yanda ko wuk'a aka d'ora maki a wuya zaki iya
cewa ke kinyi abinda ya dace, amma ba kice kina tunanin haka ba, gaskiya ki dad'a
zage damtse kinji ko."

Cikin ladabi Ummi tace "nagode La Mama, kuma insha Allah zan k'ara k'ok'ari wajen
ganin ban baki kunya ba, haka ma wajen ganin na kula da yaya yanda ya dace."

"Yawwa 'yar albarka nasan zaki iya in dai kinsa kanki, Allah ya maki albarka." tana
fad'a ta mik'e ta shiga d'aki, Ummi kuma ta ci gaba da cin abincinta.

Duk tayi wani shiru da ita jikinta babu k'wari, haka su Islam suka shirya suka tafi
wajen lessons yayi saura ita kad'ai zaune a falon, har saida tayi sallah isha
sannan La Mama ta fito cikin kwalliya mai birgewa wanda ta dace da dattijuwa mai
kamala, Ummi ba tayi mamaki dan ta san mahaifiyarta dama ko kad'an bata yarda
Abbansu yaga wani abu marar kyau daga jikinta ba, kamar yanda bata gamsu mijinta ya
shak'i wani abu da ba k'amshi ba daga jikinta ko gidanta.

Abba na shigowa Ummi da La Mama kusan a tare suka mike suna nufeshi da fara'ar su
suna mashi sannu da zuwa, kan Ummi ya dafa yana fad'in "Mamana dama baki tafi
gidanki ba?"

Kanta k'asa cike da kunya tace "Eh, Abba ban tafi ba amma yanzu zasu zo mu tafi."

Cike da jin dad'in yanda yaji Ummi ta girmama mijinta yace "ah to yayi kyau ma
hakan."

Har suka zauna saman kujera Abba yana fad'in "Mamana banji dad'in abinda ki kayi ba
dazu, amma kuma da kika bada hak'uri sai naji dad'i, kuma kinga Abbanki (Abban
Salman) ma cewa yayi yaji dad'i dan baiga laifinki ba."

K'ara sunkuyar da kanta tayi tace "kuyi hak'uri Abba, ba zan sake ba daga yau."

"Yawwa yarinyar kirki, Allah ya maki albarka ya k'ara maki hak'urin zama da mutane
a duk in da kika samu kanki."

Cike da jin dad'in addu'ar mahaifin nata tace "ameen ameen Abba nagode."

Sai lokacin ya kalli La Mama suna had'a ido ta galla masa wata harara ta kau da
kanta gefe, murmushi Abba yayi dan yasa akwai rikici, cike da zolaya Abba yace
"Mamana kinga ganinki yasa ban ko kula mamata ta ba ko, gashi yanzu kinsa ta fara
hushi."

Dariya Ummi tayi ta kalli La Mama data rumgume hannayenta a k'irji wai ita a dole
hushi take, kallon Abba tayi tace "Abba ai nasan yanzu zaku shirya in dai kune."

Tana fad'a ta tashi ta koma d'akinta, matsowa Abba yayi ya dafa kafad'ar La Mama
yace "haba uwar gidana meya faru ne haka ake min wannan kumburin? kofa murmushin
yau ban gani ba."

Ture hannunshi La Mama tayi ta kalleshi tace "au, ko murmushin kenan ma baku gani
ba? duk wanda na maku tun shigowarku, dama ai na sani in dai kuna tare da Ummi to
baku ganin kowa."

Murmushi yayi yace "haba wane ni na kasa ganinki dan tana tare dani, kawai dai
shak'uwace ta d'a da uwa."

Ajiyar zuciya ta sauke tana kallonshi, jin ba tayi magana yasa yace "dan Allah to
kimin murmushin nan na gani mai sanyaya min zuciya ko naji k'arfin jikina."

Wani hamshak'in murmushi La Mama ta saki tare da cewa "in dai wannan ne zaisa kaji
k'arfin jikinka, to ka d'auka kullum zaka kasance cikin k'uruciya."

Hannunta ya kama yana kallon fuskarta yace "ko rantsuwa nayi nasan ba zanyi kaffara
ba kan cewa nafi kowa sa'ar mata a duniyar nan, a wajen wasu AUREN HA'DI masifa ne
kuma bala'i, amma a wajena wallahi yafi komai dad'i, da ace zab'in zuciyata nabi
ban san ya zata zama a gareni ba, watak'ila ta zama ita ce tension d'inta da wannan
nake k'ara godewa Allah daya had'ani dake."

Murmushi tayi tace "nima haka ina godiya ga ubangiji daya bani ku a matsayin abokin
rayuwa kuma uban 'ya'yana, dan haka yanzu ku tashi muje kuyi wanka kuzo kuci
abinci."

Sun mik'e da nufin shiga d'aki Salman ya shigo da sallama, tsaye sukayi har ya
k'araso suka gaisa kafin Abba yace "to inaga abar wankan nan har muci abinci koko?"

La Mama cewa tayi "ko baku fad'a ba nasan ba zaku rabu ba in har ba dare ku kaga
yayi ba."
Dariya sukayi tare suka d'unguma izuwa dinning, Salman da kanshi ya zuba ma Abba
abincin shima ya zuba suka fara ci suna hira ta kasuwanci La Mama na jinsu ita dai,
dan dama tana zaune ne saboda ya zamar mata jiki ta zaune kusa da mijinta musamman
lokacin da yake cin abinci.

A hankali La Mama ta kalli Salman da hankalinshi ya tafi kan hirar da suke tace
"d'ana"

Cike da kulawa ya kalli La Mama yace "na'am"

"Dama ina so naji komai lafiya a gidan naku babu wata matsala?"

Murmushi yayi yace "lafiya k'alau La Mama babu komai wallahi, muna zaune lafiya."

Cikin rashin yarda La Mama ta kalleshi tace "nasan ba zaka fad'amin ba dama saboda
baka so na d'auki mataki."

"Wallahi gaskiya na fad'a La Mama, ai yanzu Ummi ta kimtsu kamar ba ita ba idan
tayi wani abu."

Mik'ewa tayi tsaye tace "bari na kirata ku wuce, dan dare nayi."

Tana shiga Ummi ta gani kwance akan gado ta lak'ume kamar mai bacci, daddab'ata
tayi tana fad'in "tashi ke ku tafi mijinki ya zo."

Idonta ta bud'e lokacin da gabanta ya shiga fad'uwa saboda firgici, ganin bata
tashi ba yasa La Mama d'aga murya tace "dan Allah ki tashi ki wuce mijinki na
jiranki ko."

Tashi tayi zaune tana kallon La Mama data ci gaba da cewa "nifa bana san wannan
sanyin jikin, komai ki dinga saka kasala a ciki ta yaya zaki birge miji a haka."

Wani irin d'aci ne Ummi take ji dan haka kawai ta rik'e hannun La Mama ta fashe da
kuka, jikin La Mama ne yayi sanyi dan haka ta zauna kusanta ta dafata tana
tambayarta "Ummi lafiya me yasa kike kuka?"

Bata bata amsa ba shi yasa ta sake fad'in "ki fad'a min mana Ummi, ko wani abu
Salman d'in ke maki a gidan?"

Nan ma shiru "haba Ummi ya zaki d'aga min hankali, ko ba kya san zuwan gidan naki
ne?"

Kai ta d'aga alamar Eh, dan haka La Mama tace "to me yasa, wani abu mijin naki yake
maki ne a gidan?"

Bata ce komai ba dan haka La Mama tace "kinga kiyi hak'uri ki tashi ki koma
gidanki, can d'in yafi maki nan daraja a can zaki fi samun sukuni da farin ciki
fiye da nan, abu d'aya zan fad'a maki shine, ki zama jaruma kuma gwarzuwa sannan
ki zama mai jajircewa akan duk wani abu daya danganci mijinki, sannan ki d'ora da
hak'uri dan sai dashi zama keyin dad'i."

"Ummi ki dage sosai wajen farantawa mijinki rai, wallahi in ki kayi haka zaki ci
riba a duniya sannan kici riba a lahira, Ummi ki zama mai biyayya ga mijinki sannan
ki kiyaye ganinshi da jinshi da ma iskar shak'arshi, ma'ana karki bari mijinki yaga
k'azanta a jikinki ko gidanki, sannan karki bari mijinki yaji gurb'atanciyar kalma
ko magana marar dad'i daga bakinki, sannan ki kula sosai karki kuskura ki bari
mijinki ya shak'i k'amshi a jikinki ko a cikin d'akinki ko ban d'akinki ke dama duk
wani sassa na gidanki wanda ba kamshi mai dad'i ba."

Kai ta d'aga tace "nagode La Mama, Allah ya bar mana ke."

Suna fitowa zaune suka samesu kai kace abokaine, hira suke sosai har da tab'a hannu
suke idan tayi dad'i, cikin ladabi Ummi tace ma Salman "sannu da zuwa yaya."

Cikin dariya yace "yawwa sannu, ya gidan?"

Cikin shagwab'a tace "ni gidan ma nake so na kwana."

Kallonta yayi yace "to ki kwanta mana idan kina so, nima saina koma gidanmu na
kwana."

Take murmushi ya bayyana a fuskarta tana fad'in "da gaske yaya ka yarda na kwana a
nan?"

Tsakin da La Mama tayi tare da jefarta da wata harara yasa tace "muje kawai na
fasa."

Haka suka baro gidan dukansu suna ji kamar karsu rabu da iyayen nasu, saida Salman
ya tsaya a hanya ya siya masu fruits da chocolat wa Ummi da kuma madararta sannan
suka wuce gida.

Suna zuwa suka tub'e suka shiga wanka tare duk da Ummi a d'an tsorace take, amma
tayi niyyar zama jajirtanciya kuma jaruma dan gane da duk wani abu daya shafi
mijinta domin ta birgeshi.

Cikin wata kyakyawar rigar bacci Ummi ta shirya sabuwa colour ruwan powder ta matse
k'irjinta amma gaba d'aya daga k'irjinta har zuwa in da rigar ta tsaya bakin gwiwa
duk a bud'e take, mulke jikinta tayi da turare tare da shek'a kwalliya mai ban
sha'awa, d'akin Salman ta shigo in da ta sameshi tsaye gaban madubi yana duba
wayarshi.

Bai kula da zuwanta ba saida yaji ta sakaya hannayenta ta tsakiyar nasa hannayen ta
rumgumeshi ta baya, lumshe ido yayi tare da shak'ar k'amshinta mai dad'i, sumbatar
bayansa tayi har saida jan-bakinta ya fito hakan yasa tayi dariya tace "ga shaidar
bakina nan a bayanku karku gogeshi ko wurin wanka."

Janyota yayi ta gabanshi ya rumgumeta sosai yana fad'in "Ummi ina sonki, ina son
kasancewa tare da ke har abada, ina mamakin yanda nake k'ara jin k'aunarki a
zuciyata."

D'agowa tayi daga jikinshi ta fara shafar bud'add'an k'irjinshi dako riga babu har
ta kai kan cibiyarshi, a firgice ta kalleshi tace "kun manta baku fad'a min komai
game da ciwon nan ba?"

Ajiyar zuciya ya sauke tare da kamo hannunta ya zauna kan gado ita kuma ya d'orata
akan cinyoyinshi yana shafar duk wata gab'a ta jikinta ya fara mata bayani kamar
haka.

"Ummi shekara d'aya data wuce baya, wani abu ya faru dani wanda ko a mafarki banyi
tunanin faruwarshi ba, Ummi nasan kina da ilimi kin kuma san yanda Allah yake
halittar bayinshi yanda yaso, dan haka babu buk'atar saina fad'a maki raba raben
'yan adam."

"Abun ya faru ne a lokacin da muka tafi cotonou ni da Khamis, to a wannan lokacin


ne wani ciwon mara da nake fama dashi tsawon lokaci ya takura min sosai wanda takai
ta kawo idan ya taso min ko kaina bana iya ganewa saboda azabar ciwon, lokacin ne
Khamis ya addabeni akan dole muje asibiti dan a gane meke damuna."

"Bayan munje ne aka fad'a min abinda naji kunyar d'an uwana sannan naji kamar
k'asa ta stage na shiga, Ummi kinsan me docteur d'in yace?"

Kai ta girgiza dan gabanta fad'uwa kawai yake yi, ci gaba yayi da fad'a mata "Ummi
cewa yayi dole amin opération (thearther) wai saboda sperm (maniyi) ya tarar min
a mara dole a cireshi, sannan na hanzarta yin aure da wuri kafin na illata kaina
tare da bani shawara akan na daina cin kayan marmari duk saboda lafiya ta."

"Khamis yasha fama sosai dani kafin na amince na yarda amin aikin amma a can garin,
dan ba zan iya kallon dangina alhalin ina da wannan matsalar ina jin kunya sosai,
haka aka min aikin cikin nasara aka kammala, bamu samu wata matsala da gida ba
saboda a kullum muna waya dasu muna fad'a masu muna cikin k'oshin lafiya hakan yasa
basu d'aga hankalinsu ba har muka kwashe wata d'aya a can kafin muka dawo gida,
amma duk da haka babu wanda muka fad'a ma munja bakinmu munyi shiru."

"A lokacin kuma nayi niyyar yin aure, sai dai a ganina babu wata yarinyar da zata
iya d'aukata a lokacin dan ni nasan kaina nasan zanyi takura da jaraba ga iyalina,
duk a cikin yaran dake akwai a lokacin babu wacce take da shekara shabiyar a
duniya, ke kad'ai ce keda sha shida a lokacin amma kuma saboda abinda ke tsakaninmu
yasa a waccen lokacin nake ji gwara na auri mai zaman kanta dana aureki."

"Dole na k'ara hak'uri na ci gaba da shan maganin da aka bani har lokacin da wata
tafiyar ta kamani, bayan tafiyata kuma aka saka auren su Khamis wanda banji dad'i
ba da babu ni a ciki, ya rage yan kwanaki kuma na dawo a lokacin naga Nuseiba sai
naji nutsuwarta ta birgeni sai nayi tunanin neman aurenta idan an gama bikinsu
Khamis duk da dai bai zama lallai a bani aurenta ba dole sai wanda Alhaji ya zab'a
min."

Ajiyar zuciya yayi tare da sumbatar kumatunta yace "ashe kana naka Allah yana nasa,
ashe ni Salman nine zan zama mijin Ummi, a ranar da aka d'aura aurena dake naji
kamar na sake ki a lokacin, amma saina hak'ura saboda bana so na zama na farko da
zai kafa tarihi na saki a familyn Alhaji, bayan tarewarki kuma naso na mayar dake
gida sannan na fad'a masu ba zamu iya zama a matsayin ma'aurata ba, amma kuma sai
tunanin La Mama da Abba ya hanani, bayan kuma wani lokaci saina fara jin wani abu a
tare dake da ban tab'a jinshi a game da wata 'ya mace ba."

"Yau, yau gani gaki mun zama kamar wad'anda aka haifa suna son junansu, Ummi Allah
ya bar min ke, ina kuma fatan zaki iya hak'uri da juriya dani."

Cikin kukan shagwab'a ta rumgumeshi tana fad'in "Allah sarki mijina na kaina, ashe
kasha wahala."

Murmushi yayi yace "sosai kam, dan idan ciwon nan ya taso min wallahi kamar zan
mutu."

Kallonshi tayi tace "yayana insha Allah na maka alk'awarin hak'uri da kuma juriya a
duk yanda na sameka, kuma zan zama mai amsa kiranka a duk lokacin daka kirani ba
zan tab'a gajiyawa ba bare kuma k'orafi, zan d'auke hankalinka daga wajen matan
banza dan na taya ka kare mutuncin addininka dama naka da nawa da namu baki d'aya,
sannan na godewa Allah da yasa har tsawon wannan lokacin baka tab'a neman sauk'i ko
biyan buk'atarka ta hanyar haram ba."

Cike da jin dad'in kalamanta ya rumgumeta suka fad'a kan gadon, nanfa suka fara
bayyana wa junansu tsantsar k'auna da soyayya kamar ba gobe, Ummi ta darje ta cire
kunya ta farantawa mai gidanta ta hanyoyi da dama wanda ta sani a matsayinta na
'yar zamani, Salman yayi ihu yayi kuka yayi dariya yayi....kai sauran ma basu
fad'uwa.🤣

_Daga wannan lokaci komai ya sauya zama sai farin ciki kawai a gidan ma'auranta._💋
😍😍
25/03/2019 à 16:14 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

_WANNAN PAGE *SADAUKARWA* CE GA *RAHEENAT* MY HEENAT DA KUMA AUNTYN MU *AISHA UMMA*


TAKU CE KUYI YANDA KUKE SO DA ITA. INA SONKU 😍_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

9⃣5⃣9⃣6⃣
9⃣5⃣-9⃣6⃣

Haka rayuwa ta dinga tafiya ma Salman da Ummi cikin farin ciki da k'aunar juna, sun
dunk'ule sun zama d'aya yayin da suka zama abokan juna suna hira da kuma shawartar
junansu akan duk wani abinda ya shafesu.

Lokaci gudu yake yayin da kowace awa ke wucewa cikin gaggawa, kwana kuma tamkar
k'yabta idone a lokacin kuma kwanaki ke taruwa suna zama shakara, a haka kuma har
aka fara k'idaya shekaru.

*BAYAN SHEKARA HUD'U*

Abubuwa sun faru da dama a cikin shekarun nan, Ummi ta kammala karatunta cikin
nutsuwa da kwanciyar hankali tare da taimakon mijinta d'aya tilo kuma gwarzonta,
wato Salman.

Tun kafin Ummi ta kammala karatunta Salman ya mayar da ita 'yar kasuwa ta hanyar
siyo mata takalma da jakunkunan mata tana siyarwa, duk abinda Allah yasa ma albarka
to tabbas akwai nasara da ci gaba a ciki, tun ana kawo mata guda hamsin har aka
fara kawo mata guda d'ari har d'ari da hamsin daga nan kuma sai ya fara kawo mata
less, atamfofi, material, da boyel, da mayafai, had'e da takalma da jakunkuna.

Kasuwanci na tafiya yanda ya kamata saboda jajircewar Ummi akan harkarta, ko kad'an
babu wanda ya isa yama Ummi wasa da al'amarin kud'inta, tofa za kaga tijara tana da
sauk'in kai wajen mu'amula amma idan ka fara mata wasa da hankali wajen biyan kud'i
to ba zaka ji da dad'i ba, lokuta da dama Salman yakan sha dariya idan yaji tana
waya tana fad'a akan k'in biyan kud'i, wani lokaci kuma yakan sa ta d'aga ma wata
k'afa musamman idan yaga mai shirin biya ce, duk lokacin da zata tafi karb'ar kud'i
da kanta to Salman ne ke kaita in dai har yana gari, in kuma basuyi tafiya tare ba
saboda karatu to dama ya bata izinin zuwa ko ina in dai akan maganar data shafi
kasuwancinta ne akan babur d'inta daya siya mata.

Yanzu dai haka Ummi ta zama gwaska a kasuwancinta, tana yinshi yana kuma tafiyar
mata yanda take so, yanzu haka burinta d'aya take so ta cimma wanda ta shawarci
Salman ya kuma girmama tunaninta.

Salman kanshi yanzu duk wani abu da zaiyi mai mahimmanci to saiya shawarci Ummi
akai, akwai lokacin da wani mutum ya bashi fili a maimakon kud'in da yake biyarsa,
suna zaune da Ummi ya kira Khamis yana fad'a mashi cewa bai san yanda zaiyi da
filin ba, dan haka kawai ya samo masa mai siya ya sayar dashi, Ummi na jin haka
tayi shiru saida suka kammala hira ya kashe waya sannan ta gyara zama tana
kallonshi cikin nutsuwa tace,

"Mon sweet, saina ji kamar kuna magana akan zaku siyar da filin ko?"

"Eh, ina so in siyar dashi, dama na karb'a ne saboda in ban karb'a ba to bai zama
lallai kud'in su fito ba."

"Amma da ba zaku damu ba da nace wani abu?"

Murmushi yayi yace "damuwa kuma, tame kenan? fad'i kawai ina jinki."

"Sai nake ganin fili kadarace bai kamata ku siyar ba, wanda ya baku shi ya baku ne
saboda rashin sanin mahimmancinshi da kuma rasa yanda zaiyi, shi yasa nake ganin me
zai hana ku tayar da gini a wajen tunda kunce filin yana cikin mutane ne akan titi,
kunga kenan zai iya yin amfani."

"To ke yanzu me kike ganin ya kamata ayi a wajen idan an gineshi?"

"Zaku iya tayar da shago a wajen, ko dai ku dinga zuba kayan da kuke kawowa, ko
kuma ku mayar dashi wata babbar super market in har kuna ganin aljihunku yana da
nauyi zaku iya yi, amma fa wannan tunanina ne."

Wani kallo ya bita dashi ya jima yana kallonta, hakan yasa ta tsargu dan bata san
me kallon yake nufi ba, fad'awa tayi jikinshi tana fad'in "kuyi hak'uri dan Allah
idan na fad'i wani abu ba daidai ba, shawara ce kawai."

Rumgumeta yayi sosai a jikinshi yace "Ummi na kin had'u sosai gashi kin bani
shawara akan abinda banyi tunaninshi ba, nagode sosai kuma insha Allah zanyi yanda
kika ce."

Daga wannan lokaci Salman ya zama komai zaiyi ya kan shawarceta, idan shawarar ta
masa ya d'auka, idan akasin hakane kuma zaiyi tunani akai, wasu lokuta ma idan ta
baya shawara akan wani abu ya kan fad'awa Abbanshi ko Abban Ummi, amma sai ayi
katari sun bashi shawarar data bashi, wannan ne ya k'ara karfafa masa gwiwa akan
shawartar ta, gashi kuma duk abinda suka tattauna babu mai ji koda mahaifiyarta ce.

Bayan wani d'an lokaci ya gine filin kamar yanda tace, yayin da ya mayar dashi
had'add'iya kuma matsakaiciyar mall, ya bawa Ummi zab'in sunan daza a saka a wajen,
bud'ar bakinta cewa tayi "asa US super market."

Dariya yayi yace "US kuma kamar wata turai?"

Cikin salon yarinta tayi maganar "Eh mana, U yana nufin Ummi, S yana nufin Salman."

Sai lokacin ya fahimceta dan haka aka lak'abawa wajen US super market, _to dai
zanje na siyowa fans d'ina chocolat acan😉_

Salman bai gushe ba saida ya sake tambayarta yaran da za'a saka a wajen dan tsaro,
shawarar da Ummi ta bashi baiyi tsammaninta ba, bai kuma tsinke da al'amarin ba har
saida ya bincika ya samo matasa daga cikin 'yan uwa wanda ba suda abinyi ya d'orasu
a wajen, irin farin ciki da godiya tare da sa albarkar da iyayensu suka dinga saka
masa yaji dad'i sosai, hakan yasa ya k'ara girmama duk wani tunani na Ummi, yanzu
haka duk wani lissafi da zaiyi a gida to tare sukeyi, wani lokaci da gangan yake
yin kuskure a take Ummi zata fad'a masa ba haka bane.

_MATA SUNA DA ABIN MAMAKI, WALLAHI WATA SHAWARAR IDAN MACE TA BAKA ITA ZA KAYI
MAMAKI, AMMA MAZANMU BASU SON SHAWARTARMU AKAN KOMAI SABODA SUNA MANA D'AUKAR MASU
K'ARAMAR K'WAK'WALWA._😏 Hum.

Duk shekarun nan da aka d'auka ko sau d'aya Ummi bata tab'a koda b'atan wata ba,
saboda yanda Salman ke kula da ita da kuma farin cikin da suke ciki yasa ko kad'an
Ummi bata damu da rashin samun cikinta ba, da farko ta fara damuwa a duk lokacin da
suka had'u wajen wata sabga ko réunion d'in gidan Alhaji idan suka had'u da sauran
'yan uwanta kuma abokan aurenta su Jawahir, to tabbas ta kanji babu dad'i tana ji
ina ma itama ta samu nata, hakan yasa duk ranar da akayi wata sagba Salman yana
fahimtar damuwa a tare da ita, daga wannan lokaci ya k'ara zage damtse wajen ganin
ya sakata farin ciki, yanzu kam koda tana damuwa to ba kullum ba, dan harkokinta ma
sun isheta suna kau da hankalinta daga duk wani abu da zai sata tunani marar kyau.

Duk da abin na cikin ranta amma bata yarda ta nuna damuwarta a fili ba, musamman a
gaban Salman dan kowane lokaci suna tare, dan tunda ta kammala karatunta to ya
daina tafiya shi kad'ai sai dai su tafi tare, dan ko lokacin tana makaranta ko hutu
akayi to tare suke tafiya baya yarda ya barta saboda sabo da sukayi da junansu.

A wannan lokacin kuma Jawahir da Khairat suna da 'ya'ya bibbiyu da kuma tsohon ciki
wato na uku, Hafsat tana da d'iya uku sai Nadiya dake da biyu, cikin hakane kuma
mijin Khairat yaya Noura da mijin Jawahir yaya Khamis suka k'ara aure na biyu,
mijin Hafsat ma haka wato yaya Shamsu yana nan yana shirin k'ara aure.

A lokacin auren ansha badak'ala sosai, amma dama duk abinda Allah ya hukunta babu
wani mahaluki daya isa ya dakatar face Ubangiji, duk da dai Khamis ba zab'inshi
bace domin kuwa Mamarshi ce ta zab'a mashi yarinyar d'iyar k'anwarta ce, hak'uri
kawai Jawahir tayi tare da kau da kanta daga duk wani abu da zai sata bak'in ciki,
lokacin kuma Khairat ta kasa hak'uri da b'oye kishinta har saida ta baro gidan
mijinta tayi yaji, amma tana zuwa ta samu Salman a gidan hakan yasa ya fafarota da
kanshi ya mayar da ita gidan mijinta tare da mata kashedi akan kar ta sake maimaita
wannan kuskuren.

Lokacin hankalin Ummi ya tashi sosai saboda a tunaninta ai Salman da Khamis kullum
suna tare, dan haka in dai har Khamis zai k'ara aure to Salman ma dole zai k'ara
wataran, musamman ma ita da bata haihuwa, hakan da Salman ya fahimta ne yasa ya
fara kwantar mata da hankali ta hanyar sake kusanci da ita, kuma hakan yayi amfani
saboda ta shiga farin ciki sosai.

Daf da bikin Khamis Ummi da La Mama da Sa'ada da Islam suka tafi AGADEZ wajen
bikin d'iyar aunty Fateema k'anwar La Mama, sun tafi da niyyar yin sati biyu dan
suga 'yan uwa saboda jimawa da sukayi basu je ba, a ranar da suka je Inna ta kalli
Ummi tace,

"Ummi kenan, gashi yanzu an girma hankali kuma yazo maki?"

Dariya tayi tace "Inna dama ai ina da hankali, girman daine ya k'ara zuwa yanzu."

Murmushi Inna tayi tace "humm, haka kika ce dai, ya mai gidan naki babu wata
matsala dai ko?"

"A'a Inna babu matsalar komai, lafiya k'alau muke."


"Ai koda matsalar ma ba fad'a zakuyi ba daga ke har shi d'in, dan shima abinda yake
fad'a kenan duk lokacin da mukayi waya."

Cikin mamaki Ummi tace "Inna dama suna kuranku?"

Hararanta tayi tace "kin d'auka shima mara kula ne kamar ke, ai duk safiya ta Allah
saiya kirani ya gaishe ni."

Dariya Ummi tayi tace "to amma ai nima ina kiranki ko?"

"Eh, kina kira sati ko kwana biyar ba."

Dariya sukayi gaba d'ayansu, Inna kuma ta d'ora da "gaskiya yaron nan yana da kirki
sosai, wallahi ko 'ya'yan dana haifa basa min abinda yake min, kinga duk wata saiya
aiko min da kayan abinci da kuma kud'i, kuma abinda yake min dad'i kullum godiya
yake min da nuna jin dad'in zama da jikanyata."

Murmushi Ummi tayi tace "to yanzu kin tabbatar muna zaune lafiya ko?"

"Eh mana, dama tsokanarki nake."

Haka akayi biki aka gama cikin farin ciki, yayin da a gida kuma ake bikin Khamis
cikin rikici da tashin hankali, domin kuwa amaryar akwai rawar kai dan ko fad'a da
akayi amaryar ce gaba, Ummi data samu labari ta waya ji tayi kamar tayi hira tazo
wajen bikin.

Kwana d'aya da gama bikin nan Inna tace su tattara su koma in da suka fito, nan
suka fara mata magiya da ban hak'uri akan ta barsu su kara koda kwana uku, amma ina
tace sai dai su kuma su kula da mazajensu, jin haka yasa La Mama tace to su sutafi
su barta ta k'ara kwanaki, bud'ar bakin Inna cewa tayi,

"Au, kenan ke zaki zauna su sutafi ko?"

"Eh, tunda su yara ne su tafi kawai, ni saina zauna daga baya naje."

"Ke hin ki kiyaye ni wallahi, ki tashi ku tattara kayanku gobe ku koma kinji na
fad'a maki, in banda hauka waya fad'a maki ana tsufa da kula da miji da za kice wai
su yarane."

Haka suka shirya suka dawo badan ransu ya so ba, a daren ranar kam Salman yayi
farin ciki sosai, dan kwana hud'u da Ummi tayi bata nan ya jikkata sosai.

Tunda Salman ya d'aukosu daga gidan bus ya kawosu gida, yana aje Ummi kayanta
kad'ai ya shigo mata dasu ya fita, ita kuma tana ganin haka ta shiga 'yan gyare
gyare tana idawa ta fad'a toilet tayi wanka tana fitowa ta shirya cikin k'ananan
kaya, riga mai sirara hannu sai wando jeans bak'i iya cinyoyinta, sakin kitsonta
tayi k'anana ya bazu a bayanta mai kawai ta shafa da turare sannan ta fito falo,
mamaki had'e da murmushi ne ya bayyana kan fuskarta har ta k'araso in da Salman ke
zaune yana kallo.

Duk da ta jima a d'aki amma tayi mamakin ganinshi cikin wata sabuwar shiga, babban
rigace da yar ciki da wandonsu sak dai ango, ga hula da agogo da takalmi komai fari
sosai yayi kyau sai k'amshi da yake bugawa, tana zaunawa ya mik'e ya nufi cuisine
yana fitowa ya fito hannunshi d'auke da plate mai fad'i, gabanta ya aje tare da
kamo hannayenta ya zaunar da ita k'asa sannan ya zauna.

Mamaki yak'i barin fuskarta har yanzu, plate d'in kawai take kallo wanda ke d'auke
da gasassar kaza wacce akayi mechuix d'inta sai kuma tsire a gefe ga kuma kayan
marmari an yankasu, sai jus da ruwa da madarar Ummi, cike da mamaki tace "wai
wannan duk na miye haka?"

Wani tattausan murmushi ya sakar mata kafin yace "na amarcinki mana, ko kin manta
baki ci kazar amarci ba."

Wata irin dariya Ummi ta fara shek'awa har saida cikinta ya fara k'ullewa kafin ta
tsagaita tana nuna kayan da hannunta tace "wannan duk na amarcina ne, to wane irin
amarci kenan?"

"Amarci dai da kika sani, shi nake nufi."

Dariya tayi tace "gyaran amarya bayan d'aurin, kawo amarya ba shiri ba tare da
rakkiyar 'yan uwa ba, lefe kuma bayan tariya, yau kuma ga kazar amarya bayan an
riga da an kashe arna, kai gaskiya ni 'yar baiwace komai nawa daban dana saura,
haka k'addara rayuwata take watak'ila zanyi nak'uda ne bayan na haihu." ta k'arasa
fad'a tana dariya.

Dariya yayi shima yace "hakane kam, amma dan Allah kar kice ba zaki ci ba."

"Ni na isa nace ba zan ci ba, amma fa karku manta da Allah yasa rabonmu na kusa,
to da yanzu nima ina da 'ya'ya biyu watak'ila ma dana uku a jikina, dan haka ni
banga amfanin wannan kazar ba yau tunda kusan kullum ina cinta."

Langab'ar da kai yayi yace "ai shi yasa nace maki wannan ta amarci ce kinga kenan
ta dabance."

Murmushi tayi tare da fad'in "to Allah ya k'ara mana kwanciyar hankali, ya kuma
bamu hak'urin zama da juna sannan ya barmu tare har k'arshen rayuwarmu."

Da "ameen ameen my chocolat." ya amsa mata, da haka suka fara ciyar da junansu
cikin nishad'i da annashuwa, haka kuma suka raya daren kamar daren farkonsu kamar
sababin amaren da suka tare a ranar.

*Washe gari* da yamma Ummi ce tsaye Salman na zaune akan kujera wai a dole aski
zata masa ta kuwa d'auko tondeuse d'in ta jona da waya ta rik'e taja daga, shi ma
kuma ya dage akan ba zata b'ata masa kai ba, da k'yar ya nuna mata yanda yake so
haka ta fara deb'e masa gashin sama sama kamar yanda yace saboda lokuta da dama
tana ganin yanda yake yi, hannunshi rik'e da madubi yana dubawa yana nuna mata har
Khamis ya shigo ya samesu a haka.

Ko gaisawa basuyi ba Khamis yace "kai kuma miye haka, yanzu askin ma sai a gida za
kayi saboda karka je in da zaka biya a maka?"

Dariya sukayi dukansu Salman ya d'ora da cewa "kaji mun mutum dan Allah wa yak'i
banza, kowa ai yana san sauk'i a rayuwa, ko kuwa ya ki kace madam?"

Hannu ya d'ago mata ta baya suka bige biyar tana fad'in "ah to, nima dai shi na
gani."

Tsaki Khamis yayi yace "ku dai kuka sani, kullum iskancinku k'ara gaba yake."

Wata dariyar suka sake sakawa tare da sake kashewa da hannu, Salman ne yace "kaga
kayi abinda ya kawoka dan Allah ka barni da jaririyata, yau amarci muke shi yasa ko
fita banyi ba."

Tab'e baki yayi tare da fad'in "kaga karbi nan sak'on da kace na karb'o maka ne."ya
fad'a yana mik'a masa enveloppe d'in dake hannunsa.

Karb'a yayi tare da cewa "yawwa d'an k'anena ka kyauta."

"Ba wani na kyauta, ni dai dan Allah karka sake takura min ina tsaka da wata
hark'alla dazu ma ka kira ni, wallahi dan kana yayana ne yasa naje aiken nan."

Ummi dai rik'e dariyarta tayi Salman kuma yace "lallai ango kana shak'atawa fa,
mata biyu sun saka tsaka sai kwantar ma da hankali suke, gaskiya naso naji yanda
ake jin dad'in nan na mata biyu, ni gashi k'waya d'aya ma duk ta baibaiyeni da
farin ciki har na fara jin tsoron kar sai an kaini asibiti ace jin dad'i yamin yawa
sai an rage min."

Khamis kam cewa yayi "kai, wallahi na rabaka ai zaifi maka dad'i ka ci gaba da
zama da k'waya d'ayanka yafi kwanciyar hankali, dan ni yarinyar nan wallahi in tayi
wasa ta kusa komawa gidansu, kaini gaba d'aya wallahi tsantsaninta ma nake tayar
min da zuciya kawai take idan na ganta."

Jin irin dariyar da suka saka masa ne yasa ranshi ya b'ace ya fice ya bar masu
gidan yana fad'in "ai ku dama shed'anu ne in dai kun had'u waje d'aya, saiku kashe
mai rai."

*BAYAN KWANA UKU*

Ummi ce ta fito daga d'aki da gudu ta taka d'aya daga cikin kujera dinning ta d'are
kan dinning d'in tana dariya daga ita sai d'armin k'irji da key motonta a hannu,
Salman ne ya fito cikin k'ananan kaya yana tara mata hannu yana fad'in "haba
jaririyata ki bani mana yanzu zan dawo fa."

Cikin dariya tace "um um , gaskiya ba zan baku ba, nasan yanzu da kun tafi saina
koma ina kiranku, ni kuma gashi nayi wanka kaya kawai zan saka ba sai muje na kaiku
ba."

Dafe k'ugu yayi yace "kin yarda zaki kaini da kanki?"

Cike da tabbatar masa tace "Allah kuwa da gaske nake."

"To kije kiyi sauri kisa kayan dan Allah karki jima."

"To" ta fad'a tare da d'aga masa hannuwa tace "to sauko dani na kasa."

Kallonta yayi yace "da nine na d'oraki?"

Turo baki tayi tace "dan Allah ku saukeni, koso kuke wajen saukowa da kaina na
bud'e k'afafuna iska ya shiga?"ta k'arashe maganar tana fashewa da dariya.

Ido ya zaro tare da zura hannayenshi ya sauko da ita yana fad'in "kai, ai ba zanso
haka ba, bana so ko shi iskan ya shiga."

Haka ya zauna yana jiranta, bata jima ba ta fito cikin doguwar rigar atamfa sai
hijab da nik'ab data saka, fita sukayi ta kulle ko ina kafin ta goyashi akan babur
d'inta suka wuce izuwa in da yake zama, ya yarda da tuk'inta shi yasa ya dinga mata
hira suna dariya wani lokacin har tsakulkuli yake mata, haka har suka kai in da
yake zama kaf abokananshi idansu ne ya dawo kansu, yayin da mafi yawansu suka k'ara
ji har zuciyarsu sun birgesu tare da fatan ina ma sune, 'yan bad'anul aswad kuma
suka ji ransu ya b'aci tare da takaici.
Gaishe dasu tayi cikin girmamawa kowa ya amsa da fara'arsa,Khamis ne ya taso suka
gaisa da Salman sannan yace ma Ummi "yau kuma ke kika kawoshi da kanki?"

"Eh, yaya Khamis yau rigima suke ji wai dole da motona zasu fito, ni kuma kaga zan
fita shi yasa na biyo dasu."

"To ina zaki yanzu?"

Saida ta tayar da moton tace "gida zanje, amma saina biya naga Jawahir da kuma
amaryarka."

"To Allah ya kiyaye hanya, ki gaishemin da Jawata nima."

Dariya tayi tace "to amaryar fa?"

"Kiyi abinda na saki kawai."ya fad'a yana jan Salman izuwa wajen zamansu.

Hannu Salman ya d'aga mata yace "ki kular min da kanki, sannan ki kula da hanya
sosai kinji ko."

Itama hannu ta d'aga masa tace "ku kular min da kanku, saina dawo."

Saida ta b'ace ma ganinshi sannan ya zauna suka fara gaisawa da abokan nasu, anan
kuma hira ta b'arke irin tasu ta maza.

Bata jima gidansu Jawahir ta wuce gida zuciyarta d'auke da tunanin yanda taga matar
Khamis kamar ba amarya ba, dan kayan dake jikinta ma daban daban ne, haka har takai
gida, gidan su Salman ta fara zuwa taga tarba wajen Mama dan da k'yar ta samu ta
fito ta lek'a gidan Alhaji da kuma nasu gidan, ko kad'an Mama bata nuna mata damuwa
ko wani abu dangane da rashin haihuwarta, wannan kuma na k'ara kwantar mata da
hankali tana kuma jin dad'i sosai.

Sai bayan sallah isha ta kama hanya, saida ta biya ta d'auki Salman sannan suka
wuce gida cikin farin ciki da nishad'i abinsu.

```Fans```😍
26/03/2019 à 11:20 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

9⃣7⃣9⃣8⃣
9⃣7⃣-9⃣8⃣

*SHEKARA BIYU BAYA*

Ummi ce zaune a tsakiyar gado tana ta ruzgar kuka iya k'arfinta, Salman ne gefenta
ya k'ura mata ido yana kallo dan ya gaji da rarrashinta, ganin kukan bana k'arewa
bane yasa sake gyara zama yace "Ummi na baki hak'uri yafi cikin carbi amma kink'i
hak'ura, ban san ya kike so dani ba."
K'ara fashewa tayi da wani kuka yayin da ya d'ora da cewa "dan Allah kiyi hak'uri
ki daina kukan nan, kinfi kowa sanin bana k'aunar ganin kukanki, amma shine ki keyi
dan ki d'aga min hankali."

Bata kulashi ba hakan yasa ranshi ya b'ace ya daka mata tsawa "ke, wai ba dake nake
magana ba kina jina kinyi banza dani, miye haka raina nine ki kayi ko me? wallahi
idan baki daina kukan nan ba to ranki zai b'ace fiye da tunaninki."

Tunda ya mata tsawa ko shed'a ba tayi ba saboda tsorota da tayi, cikin shashek'ar
kuka tace "dan Allah kuyi hak'uri, wallahi ba laifina bane zuciyata ce ta kasa
hak'uri, ban san yanda zanyi ba."

Cikin fad'a yace "to me yasa ba zaki taushi zauciyar taki ba, haka zamu zauna
kullum in dai kinji anyi haihuwa sai kin tayar da hankalinki kisa kanki damuwa,
haka kawai ki dinga kuka kina d'aga min hankali saboda baki haihuwa, shekara shida
ce fa, kinsan wasu lokacin da suka d'auka basu haihu ba."

"To wai in tambayeki, shin haihuwar nan waye ke bayar da ita?"

Cikin kuka tace "Allah."

Ajiyar zuciya ya sauke tare da janyota jikinshi yace "to kuma kinsan da haka amma
shine kike bawa kanki wahala, kuka ba naki bane addu'a ce taki, mu dage da addu'a
insha Allah muma wata rana za muga jininmu a duniyar nan, har yanzu ban cire rai da
samun haihuwa ba kuma koda Allah bai ban ba, toni zan zauna dake ba tare da
tsangwama ba ko na had'aki da wata saboda rashin haihuwa, ki daina damun kanki
hakan babu kyau dan kamar kin kasa hak'uri da k'addarar Ubangiji ne, koda Allah bai
bamu haihuwa ba idan mukayi duba da rayuwar mu za kiga akwai abinda Allah ya bamu
wanda bai bawa kowa ba, shin ko zaki iya fad'a min miye wannan abun?"

Saida ta k'ara lafewa a k'irjinshi cikin muryar kuka tace "farin ciki da kwanciyar
hankali had'e k'aunar junanmu."

"Ahan, to in dai har hakane meye zaisa mu tada hankalinmu saboda wani abu da Allah
bai bamu ba, wanda ko dashi in har babu wad'ancen abubuwan na baya to akwai
matsala, da wannan nake cewa ki k'ara hak'uri, kuma tunda naga abin hakane to
gaskiya ba zaki bikin Nadiya ba gobe idan Allah ya kaimu."

D'aga kanta tayi ta kalleshi tace "a'a dan Allah kuyi hak'uri karku hanani, wallahi
ba zan sake ba daga yau nayi alk'awari."

Tunda tace tayi alk'awari yasan zata daina, ko bata daina ba to zata kiyaye dan
haka yace "shikenan to tunda kinyi alk'awari, Allah ya kaimu gobe."

A haka bacci ya d'aukesu, cikin dare Ummi ta farka jikinta lullub'e da zazzab'i da
ciwon kai, gudun karta tayar da Salman daga bacci yasa ta lallab'a ta tashi drower
ta bud'a ta d'auki magani tasha, tana komawa ta kwanta sai ko taji abu ya taho mata
da sauri ta tashi zaune tana shirin tashi da nufin ta shiga toilet, tuni aman ya
taho mata bata ankara ba, a firgice Salman ya tashi cikin bacci ya fara tambayar ta
lafiya, maganin da tasha gaba d'aya ta maidoshi hakan yasa tayi tunanin maganin da
tashane kawai ta maido.

Dafe kanta tayi a lokacin da aman ya tsagaita mata tana sauke numfashi, saida taga
Salman a gabanta yana gyara wurin data b'ata, kallonshi tayi tare da mik'ewa tsaye
tana fad'in "na tasheku ko? wallahi zazz..."bata k'arasa ba ta shiga toilet da gudu
wani aman.

Toilet d'in ya shiga ya sameta tsaye tana kurkure bakinta, saida ta juyo da nufin
fitowa yace "me yake damunki ne haka, ko wani abu kika ci?"

"Wallahi zazzab'i ne kawai naji ya rufe ni, shine nasha magani kuma gashi ina
amayarwa."

Abu kamar wasa sai Ummi ta dinga tsula amai ba k'akk'autawa, kafin gari ya waye ta
galabaita sosai Salman kuma ya jikkata saboda tausayinta, ga amai ga ciwon kai ga
zazzab'i mai zafi safiya nayi Salman yace su tafi asibiti, amma Ummi tace kawai ba
zata je ba haka ya dinga lallab'ata amma tak'i yarda sutafi dan allura kawai ta
tsana.

Ganin ta dage akan ba zata je asibitin ba yasa ya kira Kareema (yayar Nadiya) dan
tazo gida ta dubata, yana fad'a mata tace masa tana kasuwa siyan kayan cefanai na
abincin biki, amma sai tace masa idan zai yiyu ya kawo Ummi gidan bikin saita duba
nan, Ummi najin haka tace Eh ta yarda ya kaita dan dama zuwan take so, ba dan yaso
ba haka suka shirya suka tafi gidan bikin da sunan ya kaita biki ne.

K'ofar gida ya zauna tare dasu Khamis ita kuma ta shiga ciki, Mama da La Mama da
Mama Hawa ta fara karo dasu suna hira zaune, durk'ushe tayi akan tabarmar da suke
suka gaisa kafin La Mama tace "Ummi sai yanzu kika taho har an fara kiran sallah
azahar?"

Saida ta had'iye wani d'aci da take ji a bakinta cikin sanyin murya tace "wallahi
La Mama da bama zanzo ba, bana jin dad'i yanzu ma aunty Kareema nake jira tazo ta
duba ni."

Cikin tashin hankali Mama tayi karaf tace "subhanallah, Ummi ba kida lafiya amma
kuma kika zo nan!"

La Mama cewa tayi "to meya sameki?naga jiya lafiyarki k'alau da kika biya can kuma
ki kace nan zaki zo."

Fuskar nan a yamutse tace "wallahi La Mama zazzab'i ne ga ciwon kai ya takura min
sosai, sai amai da nake fama dashi tun jiya da dare."

Abun mamaki kallon juna sukayi tare da murmusawa kafin Mama tace "to Allah ubangiji
yasa rashin lafiyar alkairi ce, yanzu kije ciki ki samu wuri ki kwanta kafin ta
shigo."

Da k'yar ta tashi tana shiga falo tayi karo da wasu 'yan uwan sunata hira, ciki
ciki ta gaishesu da "sannunku da hira."

Wucewa taje tayi d'akin mai bikin sai muryar Sumayya taji ta bayanta tana fad'in
"aikin banza aikin wofi, wai har mu za'a ma d'aukar kai, da bamu san asalin balbela
ba da sai tace mana daga misra take, wai dan iyayi da ganin kinfi kowa ace sai
yanzu kika zo bikin 'yar uwarki, mtssss."ta k'arashe da jan dogon tsaki.

Cikin yanayi marar dad'i Ummi ta jiyo tana kallonta tace "aunty Soumayya lafiyarki
k'alau, meya faru?"

Wani tsaki ta kuma ja kafin tace "asibiti ce a kaina iyakar rashin lafiya, ko nima
ci mun mutumci za kiyi ne?"

Cikin dakakkiyar murya Ummi tace "bari har narar da ki kayi shi, in yaso saina ci."

Ciki da hassala tace "ranar da nayi me?"

"Wai dan Allah miye haka, shigowata fa kenan me yake damunki ne haka?"
Cikin gadara Soumayya tace "bikin 'yar uwarki ake fa, amma ace sai yanzu ana kiran
sallah azahar zaki zo, saboda ke kina tunanin yanzu kin zama wata tsiya mijinki ma
haka shi yasa kike yanda ki kaga dama."

Saida Ummi ta gyara tsayuwarta cikin rashin jin dad'i tace "uhum, to kinji dai
maganar nan yanzu ta fito fili, amma ba saboda na jima bane kike wannan abun, naga
akwai dayawa wanda har yanzu suma basu zo ba, sannan tsawon sati d'aya nayi ina
zarya gidan nan, sannan kina ina daren jiya dana kusan raba dare a gidan nan.?

Cikin b'acin rai tace "miye ke raina to?gaskiya ce na fad'a danni ban iya b'oye
b'oye ba, danni bana jin tsoronki kamar yanda sauran 'yan uwa da sarakuwarki da
kuma shi mijin tacen suke tsoronki."

Cikin zafin nama Ummi taci kwalar rigarta tana fad'in "Mamana kike fad'a ma haka da
mijina?"

Itama cikin zafin rai ta fincike rigarta tana fad'in "dallah sakeni malama, kinji
wani d'aurin duniya wai Mamana da mijina, to an fad'a d'in ko k'arya nayi basa
tsoronki, kije ki tambayesu kiji shin basa damuwa da rashin haihuwarki ne, amma
saboda an riga an gama dasu yasa ko idon tuhuma babu wanda ya tab'a kallonki dasu
duk sunja bakinsu sunyi shiru."

D'orawa tayi da fad'in "duk kunbi kun mallake mutane ke da 'yar uwarki da kuma uwar
taku sai yanda ku kaga damar yi dasu, shi yasa tun yanzu nake ma d'an uwana
(Abdul) kallon k'arshe dan tunda akace za'a hadashi da tsatsonku Islam da namu
tsatson nasan nan da d'an lokaci kad'an zamu daina ganinshi."

Ummi da tuni hawaye suka wanke mata fuska bata iya cewa k'ala ba sai kallonta da
take, da k'yar tace "tun yaushe kika fara jin haushina, tun yaushe kika fara
hassada damu, tun yaushe kika fara bak'in ciki dani?"

D'orawa tayi da "koda yake babu amfanin sanin wannan d'in, dan nasan ba zai rasa
nasaba da d'aya daga cikin biyun nan ba, kodai rashin auren da Allah bai nufa ba
tsakanin mijina da 'yar uwarki, ko kuma rufin asirin da yayi mana, hakane ko?" ta
tambayeta.

"Haushin me zanji, Allah ya kiyaye wallahi nafi k'arfin sama dukiyarki ido, domin
ni Allah ya bani abinda ke kuma ba kida shi, wato haihuwa."

Wani murmushin takaici Ummi tayi tace "ai kinji aikin jahilci, gashi kuma ki kace
abinda Allah ya baki wato haihuwa, hakan na nufin kenan kinsan da shine ke bayarwa,
sannan kince abinda ni kuma banda shi amma sai ba kice abinda Allah bai min ba, dan
Allah da tsayawa kina sawa rayuwar wasu ido da makaranta kika koma ki sake karatun
tauhidinki dan akwai gyara a ciki."

Cike da jin zafin abinda ta fad'a mata tace "an fad'a maki bamu san komai bane, ai
mata irinku 'yan neman duniya ido rufe kuna sadaukar da mahaifarku ne wa bokayenku
da aljanu, kinga kuwa rashin haihuwarki ba zamu dan gantashi da All...."bata
k'arasa ba taji wawan mari har guda uku a kumatunta.

Wa zamu gani in ba Salman ba da Islam ta kirashi a k'ofar gida saboda gani da tayi
abin yak'i k'arewa, idonshi ne suka kad'a sukayi ja sai huci yake, cikin tsananin
b'acin rai ya fara magana "dan ubanki waya aikeki fad'a mata haka, an fad'a maki
kowa kece shi yasa har kike tunanin ta sadaukar da mahaifarta, to naji ta sadaukar
saime ai buk'atarta ta kuma biya tunda ta samu abinda take so."

D'an yatsa ya nuna mata yace "wallahi daga yau sai yau kar na sake ji ko ganin ki
tareta da makamanciyar wannan maganar, in dai har bake ke bayar da haihuwar nan ba
ba kuma uban wani yake bayarwa ba to ku rabu da ita kinji na fad'a maki."
Juyawa yayi ya kalli Ummi data dafe kanta yace "kije ki samu wuri ki kwanta, karki
sake kula duk wani da zai d'aga maki hankali."

Kallonshi tayi sai dai gani tayi ya rabu kusan gida hud'u sai gaba d'aya d'akin
taga yana juya mata saboda jiri, hannunta ta mik'a mashi kamar makauniya dan ba ida
yake ta mik'a hannun ba, kamo hannun yayi yace "lafiyarki k'alau kuwa?"

Ba tare da maganarta ta fito ba tace "kaini gida, ba zan iya...." luuuu tayi baya
zata fad'i Salman yayi saurin tallabota, Kareema ce ta shigo dan haka Salman ya
d'auketa suka kaita d'akin yaran Nadiya suka kwantar da ita anan ta fara dubata.

Gaba d'aya iyaye da kakanni fad'a sosai suka ma Soumayya, hakan yasa ta bar gidan
cikin b'acin rai ta koma gidanta, su Jawahir ma haka ransu ya b'ace sosai kuma
sunyi mamakin yanda Ummi bata kaima Soumayya bugu ba, dan ita bata juriyar magana
har k'wara kaji hannu a maimakon bakinta.

Tunda Kareema ta tambayeta yaushe rabonta da ganin aladarta tace wata biyu, tun nan
ta fara jiyo k'amshin alkairi amma saida tasa aka siyo jeux test ta gwada
fitsarinta sannan ta tabbatar, wai da gudu ta fito daga d'akin tana k'walla kiran
"yaya Salman, yaya Salman."

Su Jawahir dasu Mama ne a k'ofar d'akin dan haka suka tambayeta lafiya, bud'ar
bakinta cewa tayi "Mama, La Mama ba zan fad'a ba sai kun ban goron albishir?"

Cikin rashin fahimta suka ce "goron me kuma, meya faru da Ummi ne?"

Cike da tsantsar farin ciki ta rumgume La Mama tana fad'in "wallahi juna biyu ne da
ita har wata biyu."

_Tab', farin ciki fassara irin wanda akayi ma b'ata lokaci ne da kuma b'annan ruwan
birona 😎 ah to._

Sujuda Salman bai san adadin da yayi ba ta godiya ga ubangiji, Ummi ta zubar da
hawaye na farin ciki tare da godiya ga Allah, anan aka tayar da abinda ya faru
tsakaninta da Soumayya ana mai k'ara girmama al'amuran ubangiji, shi yasa babu kyau
shishigi ga al'amarin Allah, gashi dai ta bud'e baki tana fad'a akan wai ta jima
har take goranta mata akan rashin haihuwa, ashe ma rashin lafiyar d'aukan cikin ne
ya tsayar da ita.

Daga wannan rana daga wannan lokaci Ummi ta fara rainon cikinta tare da taimakon
duk wani d'an uwa makusancinta mai k'aunarta, haka kuma daga wannan lokaci sai Ummi
ta dinga taka tsantsan da kowa in ba 'yan uwanta kuma aminanta ba, sosai take samun
kulawa daga wajen danginta da kuma oga Salman dan yanzu ko goyonta ya daina yi haka
kuma duk wani abu da yasan idan yayi zaisa tayi gudu, to ya daina duk dan kula da
lafiyar abinda yake cikinta, Ummi kam yanzu in banda hutu da motsa jiki babu abinda
take, dama dai mutuniyar mutane ce kama daga mak'ota 'yan uwa abokan arziki kowa na
baibaye da ita, hakan ne yasa idan Salman ma ya fita baya da damuwa yasan akwai
masu kula mashi da ita.

Idan kuma sukayi tafiya tare, to tana wajen mak'otansu in zai fita dan sun saba
dasu an zama kamar 'yan uwa na jini, gasu da kulawa da kirki mutanen shi yasa Ummi
ke jin dad'in zama dasu.

Cikinta na wata biyar lokacin kuma suna Cotonou, gashi lokacin ana sanyi sosai
kullum cikin kayan sanyi take duk abin ya isheta, ranar tana zaune a gidansu Sara
sunata hira abinsu tana kallonsu sunata kai da kawo, Salman ne ya kirata a waya
tazo gashi ya dawo gida da gudu ta tashi ta shiga gidan.

Tun kafin ta shiga d'akin Salman ya taso da gudu ya rik'eta yana fad'in "miye haka
kuma Ummi? gudu fa kike sai kin fad'i ki jamin bala'i."

Cikin shagwab'a tace "kuyi hak'uri, na daina."

Bai tankata ba sai zif d'in rigarta daya cire mata tare da aje rigar gefe, ta
d'auka buk'atar tane yake amma sai taga ya cire mata kayan sanyin ya saka mata
wanda suka fisu girma da nauyi, hular sanyi ya saka mata da cash coux tare da
siririn glass fari sannan ya duk'a ya saka mata takalma k'afa ciki sannan ya mik'e
tsaye ya kalleta daga k'asa har sama sannan yace "yah, haka yayi ba?"

Turo baki tayi tace "to wannan so kuke na mutu ko, ni gaskiya ku mayar dani gida
wallahi na gaji da saka kayan nan kullum."

Dariya yayi yace "to muje dama ciren ticket d'in zamu je ki raka ni."

Cike da farin ciki ta nufeshi da k'arfi da nufin ta rumgemeshi, hannun ya d'aga


mata tare da fad'in "tsaya tsaya, dan Allah ki dinga yi a hankali kinji saboda
abinda ke cikinki."

Kukan shagwab'a tasa tana fad'in "ni wallahi ku mayar dani gidanmu wajen Mamana
tunda yanzu kun bar sona tunda na samu ciki sai shi kuke so."

Janyota yayi ya rumgume yace "haba Mamar 'yan biyuna, ni na isa na daina sonki ai
sai dai in babu numfashi na."

Kafin tayi magana yayi sama da ita suka fita daga d'akin sannan ya ajeta ya rufe
d'akin suka wuce, sosai Ummi taji dad'in fitar dan yawo sukayi sosai har bakin ruwa
saida ya kaita, sunyi farin ciki sosai saida yamma sannan suka hau taxi suka ciro
ticket sannan suka dawo gidan hannun Ummi d'auke da ice cream da bonbon mai tsike,
dan kuka ta saka mashi da yak'i ya siya mata ice cream d'in, amma gashi har yanzu
bata ko lasa ba bare tasha.

Tunda ciki ya shiga wata na shida sai laulayi ya dawo mata sabo pil a leda, cikin
wata shida kamar na wata takwas sosai yayi girma, haka ta dinga fama kullum da
abinda zata ji sabo ga nauyin jiki kasala duk ta hargitse kamar ba ita ba, duk wani
abu na jikinta bata san tab'ashi hakan yasa kanta ta daina kitso yankan farata kuma
Salman ne ke mata dan bata iyawa, wanka kawai take da k'ok'arin yin saboda bata so
mijinta yaji wani odeur daba k'amshi ba a jikinta, shima babu sabulu sai dai tayi
tsaye ta kunna panpo ruwa na zuba in ta gaji ta kashe ta fito ta shafa turare,
Salman ne ke mata da sabulu in zaiyi, kaya kam ko kad'an yanzu ko atamfa ta daina
sawa bare less ko shadda kullum cikin dogayen riguna take na kantie marasa nauyi.

```CIKI SAYIN MATA```

Kwana tashi a wajen Allah babu wuya, haka har cikin Ummi ya shiga wata na *TARA*
daga lokacin kuma Mama ta hana tafiya tare da suke tunda lokacin haihuwarta ya
kusa, shi ma kuma tunda ta shiga watan haihuwarta ya tsaida duk wasu harkoki da
zasu sa saiya bar gari ya maida hankalinshi akan jaririyarshi.

Masha Allah cikin Ummi shine rigani kwana, dan yanzu kam idan ta zauna to sai an
had'a da addu'a take tashi tsaye, sosai sosai cikinta yayi girma ga tsini k'afafu
kam sukace ja bani wuri saboda kumburi kai kace iska ne aka busa mata, amma duk da
haka sai cikin yasa tayi kyau a fuska ga haske kamar wacce bata da jini a jiki,
Mama da Salman tausayinta suke kullum haka suka duk'ufa wajen rok'on Allah ya
sauketa lafiya, kuma har yau Salman Mamar 'yan biyu yake kiranta dashi.

Koda taje likita aka fad'a mata nan da sati biyu zata iya tsammanin jiran haihuwa,
koda tazo gida ta tada hankalin Salman saiya kaita gida ta haihu acan, bai mata
gardama ba ya kaita gida wajen La Mama, daga ranar suka tare can da zama har Salman
d'in, yau ta kama asabar d'in k'arshen wata ana reunion gidan Alhaji, amma La Mama
ta hanata tafiya saboda ganin yanda tayi wata iri da ita kamar dai ace mata ta
haihu kuma ta haihun.

Haka akayi réunion Ummi kuma bata damu ba dan ita tasan abinda take ji, ana sallah
la'asar su Jawahir Nadiya Khairat Hafsat suka zo wajen Ummi anan suke fad'a mata
wani sabon tsari da taji dad'inshi sosai, wai Alhaji ya dakatar da auren Islam da
Abdul dan yaji abinda Soumayya ta fad'a watak'ila kuma maganar daga manyanta taji
shi yasa ta fad'a ita ma, Abdul kam yana son Islam sosai hakan yasa baiji dad'i ba
yaji kuma Soumayya ta bashi haushi, abin mamakin ma shine cewa da Alhaji yayi idan
Islam d'in tana da wanda take so ta fito dashi tunda babu wani matashin saurayi
daya isa aure, hakan ba k'aramin k'ara b'atama wasu rai yayi ba dan a ganinsu yanzu
ma shige da ficen ne akayi shi yasa haka ta faru.

Sun jima suna tattaunawa kafin suka tafi La Mama kuma ta shigo, tunda taga Ummi
tasan lokaci ya kusa tunda dama kwana goma sha d'aya kenan a cikin sati biyun da
aka bata, kallonta kawai take tana yamutsar fuska tare da cije leb'e amma ba tace
mata komai ba, har bayan sallah isha Salman ya shigo gidan ya zauna kusanta ya
mik'e k'afafu yana kallonta cike da tausayawa, ganin yanda zufa keta keto mata har
ta kai fitowa take, ko uffam ta kasa cewa sai jujjuya kai take yi haka har La Mama
ta kawo masu dafaffen naman kai data dafa.

Gashi dai Ummi tana so ta ci amma ina ta kasa, a hankali Salman ya dinga dib'a yana
sa mata baki, amma koda ta karb'a sau uku bata k'ara na hud'u ba, cikin rarrashi
yace "haba Mamar 'yan biyuna ki k'ara mana ko kad'an ne."

Kamar za tayi kuka tace "La Mama ki fad'a masu su daina cemin Mamar 'yan biyu."

Bud'ar bakin La Mama cewa tayi "haba Ummi wannan girman ciki naki masha Allah in
baki haifi 'yan uku ba ko yan hud'u, ai dai kya haifi 'yan biyu."

Salman bushewa yayi da dariya yace "ahan, kinga ashe La Mama ma kallon Maman 'yan
uku da hud'u take maki."

Ba tayi magana ba Islam ta shigo hannunta rik'e da Ihsan autar Sa'ada, wajen Ummi
ta zauna tana mata magana amma ko jinta ba tayi, Salman ne yace "Ihsan ki rabu da
auntynki bata lafiya nak'udar 'yan biyu take." ya fad'a yana shek'ewa da dariya.

Cikin d'umin yara Ihsan tace "eh tonton, ai kasan aunty 'yan biyu zata haifa ko?"

Cike da fara'a yace "ashe kema kin sani, to waya fad'a maki?"

"Wallahi ko tonton 'yan biyu ne ni da kaina na gani."

Dariya La Mama tayi tace "shi kenan ya tabbata 'yan biyu zaki haifa insha Allah,
sai dai fatan Allah ya sauke ki lafiya sannan muga mi zaki haifa."

Tun Salman na hira da Abba ya lura da Ummi bata jin dad'i sosai, haka ma Abba yana
kallonta duk saiya ji tausayinta ganin yanda ta canja k'afafu a mik'e ko motsin
kirki bata iya yi, ai kam sai nak'uda tace salamu alaiki Ummi gadan gadan ta taso
mata, tuni suka d'auketa sai asibiti yayin da Mama dasu Hajiyoyin Alhaji suka biyo
bayansu, 22:30 suka je asibiti amma cikin ikon Allah da addu'o'in iyaye sai ga
santalen santalen kyawawan yara maza guda biyu an fito ma dangi dasu waje su gani
da misalin k'arfe 23:40.

💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃

```FARIN CIKI KENAN```

'Yan biyun farko kenan a cikin famillyn Alhaji Manu mai dala (tsoho mai ran karfe),
irin farin ciki da walima tare da kyaututtukan da 'yan biyu suka samu basa
misaltuwa, mahaifin yara bakinshi ya kasa rufuwa komai siyowa yake wa yara da mai
jego, ya bawa Ummi kyautar yaran dukansu saboda bai san me zai bata ba, amma
matsayinshi na uba yayi alk'awarin kula dasu, haka aka gudanar da suna aka kashe
kud'i sosai Ummi ma tayi bajinta dan ba komai take cewa Salman yayi ba ita ma nata
kawai take yi da guminta.

Yara sun samu suna ```MOHAMED TAUFIK' da ```MOHAMED RAFIK', Allah ya rayaku akan
sunna.

Kwana biyu da biki Inna da aunty Fateema suna shirin tafiya, Salman ya shigo d'auke
da ledoji biyu d'ayar ya bawa su Inna d'ayar kuma ya mik'awa Ummi wai na 'yan biyu
ne, tana bud'awa kayan yara ta kuma gani kuma abin dariyar kowane iri hud'u hud'u,
cikin jin haushi Mama tace,

"Wai kai miye haka, abu kamar hauka ina ma laifin ka siyo kala biyu, amma saika
siyo kowane har hud'u hud'u, duk me za ayi dasu ka duba kaga gudan tarin tilin
kayan da yaran nan suka samu fa."

"Ayi hak'uri Mama, ai sai a aje ko wasu an bawa idan anyi haihuwa." cewar Ummi da
taji babu dad'i kalaman da Mama ke fad'ama jarumin nata.

Haka suka dinga tafiyar da sabuwar rayuwarsu tare da yaransu masu kama da mhaifinsu
sai dai kumatunsu suna lotsawa ko murmushi sukayi kamar dai mahaifiyarsu haka kuma
jikin mahaifiyarsu dan 'yan lukutayene yaran, Islam da Momy ne suka zauna gidan
bayan tafiyar mai tsaronta suke tayata kula da yaran, gashi har yanzu bata iya masu
wanka ba sai Salman keyi masu, nono kad'ai ke had'ata dasu da sunsha su Momy zasu
karb'e su suyita jagula sai in sunyi bacci kawai, idan kuma babansu ya dawo to suna
hannunshi dan ko bacci sai dai ya d'orasu akan k'irjinshi yana shafasu har suyi
bacci.

```Muje zuwa```😍😍😍💋
29/03/2019 à 20:22 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑

_Samira Harouna_

*FIN*
```{k'arshe}```

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*


_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

*Page*

9⃣9⃣1⃣0⃣0⃣
9⃣9⃣-1⃣0⃣0⃣

💃💃💃💃💃💃💃💃

Salman ne zaune k'asa ya mik'e k'afafu yasa robar wankan yara tsakiyar k'afafunshi
da Taufik' a hannunshi yana masa wanka sai lumshe ido yake alamar bacci yake ji,
Ummi kuma na gefensa da Rafik' tana shiryasa cikin k'ananan fararen kaya masu kyau,
masha Allah yaran sun girma dan har sun iya zama suna k'ok'arin fara rarrafe, wasa
take masa shi kuma yanata dariya yayin da kumatunshi keta lotsawa ciki kamar na
Ummin, doguwar hammar da Salman yayi ce yasa ta kalleshi amma ba tace dashi komai
ba, saida ya k'arashe sannan tace "haba 'yallab'ai irin wannan doguwar hamma haka,
duk ta kwanan ce?"

Cikin muryar bacci yace "Eh mana, ya kike so nayi to? tunda kin kasa barina nayi
baccin."

Tab'e baki tayi tace "hum, to nidai ku kula karku sakawa yarona kunfa a hanci, dan
in haka ta faru ba yarda zanyi ba." ta k'arashe tana murguda baki.

Kallonta yayi yace "ke yanzu ko kunya ba kiji ba da ki kace d'anki, to d'anki dawa
ya baki?"

Cikin kuri tace "Allah ne ya bani."

Ci gaba yayi dayi masa wankan yana fad'in "hum, amma kuma har yanzu baki san yanda
zakiyi kiyi masu wanka ba, watansu biyar a duniya amma bana jin kin tab'a masu
wanka ko sau d'aya."

Turo baki tayi gaba tana fad'in "to ai dai zan iya nima, kuma kune ku kace kun
d'auki alhakin yi masu wanka , dan haka ni kuma bana masu."

Kallonta yayi yace "shi yasa kenan kike tayar dani daga bacci yanzu dan nayi masu
wanka?"

"Eh mana." ta fad'a tana sumbatar kumatun Rafik' data gama masa shirinsa.

Yana gama d'auraye ma Taufik' jikinshi ya sakashi cikin towel ya mik'a mata ta
karb'a dan ta shiryashi, mik'ewa yayi tsaye yana fad'in "dan Allah kiyi zuciya ki
iya yi masu wanka da kanki, sannan zanje na kwanta kiwa Allah karki tasheni ki bari
na k'arasa hantsewa."

Hararan sama da k'asa tayi masa kafin tace "sannu, na barku kuyi bacci?ai bazai
yiyu ba tunda baku gama dani ba."

Dafe k'ugu yayi da duka hannayenshi biyu yace "duk ni kad'ai keda wannan hararan?to
na gode, amma dan Allah ki barni na huta, kefa kinfi kowa sanin gajiyar dana deb'o
kuma ban shigo garin nan ba sai cikin dare har kunyi bacci, amma shine duk da haka
kin kasa barin mijinki ya huta."

Dariya tayi tace "shikenan kuje ku kwanta, ba zan tayar daku ba, amma zan shigo
kumin wanka ku shiryani saboda lokaci yayi na tafiya gidan Alhaji, ko kun manta yau
k'arshen wata ne?"

Wucewa yayi yana fad'in "to ni dai zan kwanta ba yanzu zanje ba saina huta gajiya."

Tana gama shirya Rafik' cikin shiga irinta Taufik' ta ajiyeshi kusa da Taufik', ita
kuma ta d'auke robar da akayi masu wankan ta gyara wurin sannan ta aje masu kayan
wasa a gabansu ta sunkuya tace masu "zanje wajen papanku yamin wanka, kuyi wasa
kafin na dawo."

Tana fad'a ta shiga ciki, kwance ta sameshi cikin blanket, yaye blanket d'in tayi
ta haura kan gadon ta hayeshi ta fara mashi magana cikin kunne "ku tashi kafin na
tayar daku."
Saida ya k'ara dunk'ulewa yace "um um, ba zan tashi ba, dan Allah ni ki d'agani kin
wani zo ki sakar min nauyinki."

K'ara mak'alewa tayi a jikinshi tace "wallahi ku tashi kafin na tayar daku, kunsan
dai zan iya ko?"

"Nak'i d'in, kiyi abinda za kiyi." ya fad'a yana tutsa kanshi tsakiyar pillow.

Dagewa tayi iya k'arfinta ta fara k'urma mashi ihu cikin kunnen b'arin dama,
k'ok'arin rufe kunne ya fara dan haka ta rik'e hannayenshi duka biyu, haka suka
dinga turmushe turmeshe akan gadon saida yayi sarander ya d'aga hannayenshi yana
fad'in "shikenan nayi sarander."

Kafin tayi magana ya juyo ta yanda yake fuskantarta hakan yasa tayi zaune akan
k'ugunshi suna kallon juna, hannayenta ya kama yace "naga ke har yanzu baki san kin
girma ba, kullum k'ara yarinta kike yi alhalin kin aje yara har biyu a gabanki."

Saida ta masa fari da ido tace "girma fa? to ina abin yake, ni d'in ta nawa ce da
har zan maida kaina tsohuwa? ai ko ku da kuka girmeni ba za kuce kun girma ba bare
kuma ni."

Wani shu'umin kallo ya mata yace "ni kam na tsufa yanzu na bar maki duk wani
girman, ni dake da yara a gabana an kusa kawo min surukai."

Itama wani kallon ta masa tare da sunkuyowa kusan kunnenshi ta dinga mashi wani
irin salo mai d'aukar hankali, hannunta tasa ta fara shafar duk wata gab'a da
tasan tana tayar masa da sha'awarsa, yayin da kuma ta dinga motsa mazaunanta akan
k'ugunshi da take zaune akan, cikin wata irin murya tace "fad'a min, me kuke ji a
halin yanzu?"

Kasa magana yayi sai mik'ewa da yake yana rufe ido tare da cije leb'en k'asa, hakan
yasa ta kalli fuskarshi ganin halin da yake ciki yasa ta kama leb'enshi na k'asa
tad'an ciza a hankali lokaci d'aya kuma ta saki ta kama kunnenshi tana lasawa,
saida ta gama rikita mashi lissafi yakai mak'ura wajen san abinda take masa, kawai
tayi saurin direwa daga kan gadon da sauri ya murgino ya rik'o hannunta, tana had'a
ido dashi ya mata alama da ido akan ta dawo, kai ta girgiza masa tace "wanka zanyi
lokaci na tafiya."

Da idon shinnan kamar na mayu ya sake mata alama da tazo, Ummi kam sai taji ya bata
tausayi saboda yanda duk taga yayi wani iri yakai k'uloluwa wajen tashi, murmushi
tayi tace "kufa ku kace kun tsufa, amma ya haka daga d'an abinda bai taka kara ya
karya ba sai duk ku fita hayyacinku."

Janyo hannunta yayi da k'arfi ta fad'o kan k'irjinshi, cikin zafin nama ya juye da
ita ya mata runfa yana fad'in "yaushe nayi tsufan da har zan kasa azabtuwa da
salonki mai rikita duk wani namiji mai cikakkiyar lafiya?"

"To amma ai kun tsufa shekara arba'in fa ba wasa bace."

Kallonta yayi da ido waje yace "ke, waye yayi arba'in d'in, duka duka fa talatin da
shida ne gareni, ai ni yanzu ma nake jin wata sabuwar k'uruciya, dan duk lokacin da
kika kusantoni to na kan ji wata sabuwar wuta na ruruwa a gaba d'aya illahirin
gabb'an jikina."

Yana gama fad'a ya fara aika mata da nashi sak'onnin cikin salo da k'warewa, haka
suka lula wata duniyar suka manta da yaransu dake falo har saida suka samu kansu
sukayi wanka suka fito sannan suka fito wajen yaran cikin shirinsu ta shigar farin
kaya.

Kasancewar yaran ba suda rigima yasa suka tarar dasu kowa ya kama gabansa duk suna
k'ok'arin d'auko abinda yayi masu nisa alamar rarrafe suke san yi, Taufik' ta
d'auka shi kuma ya d'auki Rafik' sannan suka fita daga gidan, haka Salman ya d'ora
Rafik' a k'afafunshi kuma yana tuk'i har suka kai gidan Alhaji.

Suna shiga gidan yara sukayo masu cah kowa na k'ok'arin karb'ar yaran, haka aka
rabasu dasu sukayi cikin gidan dasu suna murna, su Ummi kuma gaisawa suka dingayi
da iyaye da sauran 'yan uwa yayin da kowa ke tambayarsu ya yara, suna shiga babban
falo suka tarar dasu Jawahir dasu Nuseiba Rumana dama Soumayya, kallonsu sukayi da
gani ba magana kasan ma'auratan suna cikin farin ciki , bugu da k'ari ga wata k'iba
mai birgewa da dukansu sukayi fatarsu ta kwanta sosai, musammam Salman da kyawunshi
ya sake bayyana hakan yasa Ummi fargaba, dan tasan dole wasu matan zasu dinga kawo
masa farmaki, kuma ta sani tunda ba kyawun fuska gareta ba za'a iya samun wata data
fita zata iya shiga tsakaninta da farin cikinta, wannan ne yasa ta dage sosai wajen
ganin ta kyautata masa ta kuma cika zuciyarshi da soyayyarta da farin ciki tare da
kewarta a lokacin da yayi nesa da ita.

Da gani kasan arzik'i ya kwanta fiye da baya, kallo d'aya za kama less d'in dake
jikin Ummi kasan cewa tsadaddene haka ma gyalenta da takalmanta da jakarta duk
jajaye kalar duwatsun da aka mata ado dasu a rigarta, har saida Salman ya zauna
Nuseiba bata daina kallonshin ba cike da birgewa dan har yanzu bata daina jin ina
ma ace Salman ne mijinta, yaranta uku amma har yanzu tana son yaya Salman, su Momy
da Islam ne suka shigo d'auke dasu Taufik' Hajia takwarar Ummi ce ta karb'i Taufik'
mahaifiyar mahaifin Ummi da Salman ne wato (Hajia babba) ta karb'i Rafik'.

Hira suka fara yayin da Soumayya zuciyarta keta tafasa saboda bak'in ciki, ko
kallon Ummi da yaranta bata san yi Rumana kam rayuwarta take bata damu ba dan dama
bata sa a kai ba, Jawahir ce ta kalli Salman ta kalli Ummi tayi murmushi tana
fad'in,

"Duniya kenan, yau ga Ummi da Salman a inuwa d'aya a matsayin ma'aurata masu
k'aunar junansu."

Dukanta Ummi tayi a kafad'a tace "ke kuma da tashin tashina, miye na tado abinda ya
wuce?"

Khamis ne ya harareta yace "karki sake dukar min mata, an tuna bayan."

Salman ne ya doki kafad'arshi yana fad'in "an doka d'in me zaka yi?"

Jawahir ce tace "wannan fa zalinci ne, kawai dan kuna gaba damu sai ku dinga
d'irkanmu."

Hajia babba ce tace "to ai dole ne Ummi, dan idan aka had'a rayuwarku ta dah data
yanzu dole kowa zaiyi mamaki, kullum idan muka ganku sai mun tuna da shiriritarku
ta baya."

Kallon juna sukayi da Salman lokaci d'aya suka k'yabtawa juna ido tare da siririn
kiss, dariya tayi tace "to Hajia ai dai aikin gama ya gama sai a daina tuna baya."

Hajia Abu ce tace "ank'i a daina tuna bayan, rayuwa in ba'a d'an tab'o abinda ya
faru baya ai babu armashi."

La Mama ce tace "to ai bata da gaskiya ne shi yasa take so abar maganar."
Mama ce tace "ai shine mai laifi tunda shine mai dukanta ko ba tayi laifin komai
ba."

Daga gefe Salman yace "haba Mama ta yaya za'a doki mutum baiyi laifi ba, ai da
kunga na daketa to wani abu tamin."

Hararanshi Mama tayi tace "dubeshi dan Allah har wani dad'in fad'a kake ji."

Sa'ada ce tace "kuma su La Mama ai kun zama kamar b'era da mage idan su Ummi suna
tare kuma saiku koma mafad'ata."

Dariya akayi Abba ne da Rafik' ke hannunsa yace "to ai kowa akwai team d'in da
yake, kowa baya so aga laifin nashi."

Alhaji dake zaune a kujerarshi yana kallon kowa yace "to waini abinda ma ban gane
ba, bansan miye ya haddasa wannan rikici ba a tsakaninsu? ni dai naga kawai suna
fad'ansu."

Kallon juna sukayi ita da Salman sukayi dariya, Ummi ce tace "to nima dai ban sani
ba, amma ku tambayi papan 'yan biyu kuji."

Wata harara Soumayya ta jefi Ummi da ita ta gefen ido jin abinda ta fad'a, Salman
kam cewa yayi "a'a nima ban sani ba, ke zaki iya tunawa."

Hajia babba ce tace "uhum, kun gani ko, a k'arshe ma basu san akan me suke wannan
shirmen ba kawai rashin hak'uri ne da k'uruciya dake damunsu."

Ummi ce tace "a'a Hajia, ni dai nasan cewa a waccen lokacin yaya baya san ana
murgud'a masa baki da harara, uwa uba kuma ka masa tsaki, to ni kuma kawai saina ji
inayi idan muna tare dashi amma bawai dagangan nake ba."

Wani kallo Salman ya mata yace "ai ko yanzu bana so, kawai dai na daina dukane
yanzun saboda na samu hanyar da tafi ta dah."

Wani kallo Ummi ta masa tare da wurga mashi ido alamar akwai mutane fa, Alhaji ne
yace "to koma dai miye yanzu ai gashi nan suna zaune lafiya kamar ba sune lokacin
da aka d'aura auren suketa kururuwa ba suna fad'in basa so, amma yanzu na tabbata
da za'a ce a rabasu to sai dai ku jisu a asibiti."

Abin mamaki bakin Salman dana Ummi ne suka had'u wajen fad'in "sai dai k'abari."

Tin tsirewa akayi da dariya Hajia ta d'ora da "ja'iran yara kawai, ku kun d'auka
*AUREN HA'DI* da ake maku ana maku dan ba'a sonku ne, amma idan har zakuyi hak'uri
kuyi biyayya to ku zaku fi kowa jin dad'inshi da moriyarshi."

Saida akayi sallah azahar aka ci abinci sannan Alhaji ya tara iyalin nashi ya masu
nasiha tare da gargad'i da mahimmancin had'a kansu, ya kuma nuna masu da lokacinshi
ya kusa dan haka yace "yanzu ya rage naku ku ci gaba da had'a 'ya'yanku aure, ko
kuma ku barsu su auri zab'insu, amma ni dai Allah ya sani nayi yina wajen ganin na
had'a kan iyalina na k'ulla zumunci a tsakaninsu ko bayan ba raina, wasu tunaninsu
kawai ina masu *AUREN HA'DI* ne saboda ina gaba dasu da iyayensu, amma ba haka bane
babban dalilina shine naga kun tashi kanku a had'e kuna son junanku sannan ranar
lahira fiyayyen halitta (S A W) yayi alfahari da zuri'ata, da wannan nake bawa duk
wani wanda nama ba daidai ba hak'uri nake kuma neman yafiyarku."

"Sannan ku zama tsintsiya mad'aurinki d'aya, ku had'a kawunanku ta yanda babu wani
mahaluki da zai iya ganin bayanku, kar wanda ya ware kanshi daga cikin 'yan uwanshi
dan duk lokacin da wani bala'i ya taho, to zai fara tunkarar wanda ya ware kanshi
shi kad'ai, dan Allah ku zama masu k"aunar junanku kuso junanku ku zauna lafiya,
dan da hakane zan samu kwanciyar k'abarina cikin lumana, sannan ina rok'on duk
wanda yaji dad'in abokin zaman dana had'ashi dashi, to ya aikamin da sak"on addu'a
a k'abarina a lokacin da nabar duniya, dan shine kad'ai tukuicin da zaku iya
yimin."

"Sannan daga yanzu na daina saka hannuna a al'amuran da suka shafi rayuwarku, kowa
zai iya cin gashin kanshi amma kuma kowane mahaifi ko mahaifiya zata iya yanke
hukunci akan d'an da koda ba daga cikinka ya fito ba, haka kuma duk wani daya
girmema wani koda da kwana d'aya ne to yana da damar da zai iya tsawatarwa dana
k'asa dashi, da wannan nake cewa Allah ya maku albarka, Allah ya albarkaci
rayuwarku, Allah ya had'a kawunanku, Allah ya sakama zuriarku albarka, Allah ya
kareku daga sharrin masharranta, Allah ya kawar da idon mak'iya daga kan wannan
zuria tawa mai tarin albarka, duk wani mai son ganin bayanku Allah shiryashi idan
mai neman shiriyane, idan kuma ba haka ba to Allah ya mana maganinshi."

Kamar yanda suka dinga amsa masa da ameen, haka a k'arshen addu'ar ma suka amsa da
"ameen."

Ana gama sallah la'asar kowa ya koma gida, Mama da k'yar ta basu 'yan biyu suka
tafi dan ji take kamar su bar mata su su kwana anan, suna zuwa gida Ummi ta cire
masu kayan ta saka masu marasa nauyi itama ta canja sannan ta shiga girki.

Salman na kwance akan gado yana kallon tv da bai jima da yasa aka mak'ala mashi ita
ba, remonte ce a hannunshi ko riga babu a jikinshi sai dogon wango, Ummi ce ta
shigo d'akin cikin wata had'add'iyar kwalliya mai d'aukar hankali, doguwar rigar
bacci ce a jikinta kad'an ya rage ta sauka k'asa sai dai shara shara ce da siraren
hannuwa, best colour d'in da Salman yafi sone wato bleue sai fari da bak'i sosai
rigar ta mata kyau, ga wasu dogayen takalmi data saka suma bleue sai gashinta data
saki ya sauka a bayanta, tafiyar da take yi ce ta d'auki hankalinshi sosai bai
d'auke ido daga kanta ba har saida ta cire takalminta tabi ta kanshi ta kwanta
gefenshi suna kallon juna.

Wani hamshak'in murmushi yayi mata tare da fad'in "wannan kyau haka, kinga yanda
kika had'u, ai da farko ban ganeki ba na d'auka wata sabuwar amaryarce Alhaji ya
auramin ban sani ba."

Wata yar k"aramar dariya tayi hakan yasa ya lotsa hannunshi a dinple d'inta, cewa
tayi "ai ko a mafarki idan kaga wata mace ta shigo d'akin nan, to ka tabbata ZEINAB
ce, wato Umminka."

Janyota yayi jikinshi ya rumgumeta suna kallon juna yace "tabbas wannan haka yake,
ke kad'ai ce keda ni kuma zan ci gaba da zama naki da yardar Allah, kamar yanda zan
ci gaba da yiwa Alhaji addu'a da wannan *AUREN HA'DIN* da yayi mana."

Murmushi tayi tace "gaskiya kam, nima zan ci gaba dayi masa addu'a har k'arshen
rayuwata."

Remonte d'in hannunshi ya juya ya kashe tv sannan yaja musu blanket suka shige ciki
yana tambayarta " kin yiwa yarana addu'ar bacci?"

Gira ta d'aga masa tare da cewa "na masu mana."

Sumbatarta yayi yace "kin kyauta my zuma."

Dariya tayi tace "gishirina kenan ba kada dama."


D'ago da kansa yayi daya tutsashi tsakiyar mamanta yana lasa yace "gishiri kuma,
yau haka na samu? nan gaba kuma bansan me zaki cemin ba."

Dariya tayi tace "to ai kune kuka cemin zuma."

Saida ya had'a goshinshi da nata hancinshi da nata hancin sannan yace "to ai zumar
ce ko? nifa dama ina so in fad'a maki wani abu."

"Ina jinku."

"Tunda nake tare dake kullum gamsuwa da farin ciki ne kike cika zuciyata dashi, da
wannan nake cewa dan Allah ki rage amfani da abinda kike amfani dashi wanda kullum
kike rikita min lissafi dashi, wallahi ina tsoron wata rana dad'i yamin yawa na
mutu, wallahi sai dai kiji ni shiru babu numfashi."

Wata shu'umar dariya tayi tace "wasa kuke dani, kuna nufin kenan na daina gamsar
daku ta yanda zaku samu damar d'auko min wata a matsayin k'anwa ko?"

Cikin dakusashiyar murya yace "wallahi da gaske nake fad'a maki, dad'in ya fara min
yawa dan har yanzu banji wani d'and'anon abu a duniyar nan ba daya kai min ke
d'and'ano mai dad'i."

Tana shafar bayanshi tace "to ku rok"i Allah yasa ya rage, amma bani ba."

_Ni kam dake tsaye ina kallon ikon Allah, tab'e baki nayi nace "kaji wani kicihi
kuma wai wani zak'i da galmi, to ko me hakan yake nufi?"🤔

Da sauri Salman ya yaye blanket d'in yana kallona da mamaki, Ummi ce tayi dariya
tace "aunty Sam bafa gishiri da zak'i muka ce ba, zuma ne da gishiri."

Cewa nayi "ayyah, yanzu na gane, to kenan me sunan yake nufi?"

Cikin tsawa Salman yace "keh, waike wace irin 'yar sa ido ce?dallah malama b'ace
min da gani."

Ummi ce tace "haba sweet cocomber, wannan fa aunty Sam ce, ko baka ganeta ba?"

Kallonta yayi yace "ke dallah wace aunty Sam, ke ba kiga hark'allar da nake bane?"

Kallona Ummi tayi tace "auntyna kiyi hak'uri dan Allah ki jiramu a waje ina zuwa
yanzu."

Hararan Salman nayi nace "su hark'alla manya, sai kace wanda yake filin daga yana
fama da arna irinsu ABU JAHAL, ABU SUFYAN, DA MUSAILAMATUL KAZZAB."

Ban an kara ba naji Salman ya jefomin pillow yana k'ok'arin tasowa daga kan Ummi
yana fad'in "ke, zan ci gidanku wallahi, kinsan irin arnan da nake kashewa anan
d'in?sunfi FIR'AUNA kafirci."

Da gudu na bar d'akin, har na fita kuma na tuna da sak'on MY HEENAT hakan yasa dole
na kuma bud'e k'ofar d'akin a hankali na lek'o kaina ina fad'in "dan Allah yaya
Salman minti biyu?"

Cike da k'osawa Salman ya kalleni yace "oh my gosh, na rasa yanda zanyi da yarinyar
nan, to miye kuma yanzun?"

Saida na tattare siket d'ina sannan na fara masa bayani cikin sauri "dama my
heenat ce tace wai na fad'a maka akwai k'annenta, idan kana son d'aya daga ciki
zaka iya yin magana saita had'aka da d'aya daga cikinsu."
Remonte d'in dake aje gefe naga ya d'auka tun kafin ya jefo min na bar d'akin @360,
gudu nayi sosai har saida na bar unguwar na tsaya ina sauke numfashi cikin zuciyata
kuma ina fad'in "my heenat da nasan haka sak'onki zai zama, da ban fad'i ba."

Sai lokacin na lura ban d'auko takalmana ba, amma dai nace ma chérie da Maman dady
suzo su d"auko min, danni da gidan Salman sai kuma haihuwa ta biyu idan Ummi tayi.

Ashe ina fitowa Ummi ta kalli Salman tace "haba babban mutum, aunty Sam d'in kama
haka, kasan itama fa tana da masoya wallahi zamu ji ba dad'i fa idan ta fad'a
masu."

Cikin wani yanayi yace "gobe zanje na bata hak'uri, shikenan hakan ya maki?"

"Idan ma baku jeba ni zanje na bata hak'uri."

Hancinta ya kama yace "amma bada izini na zaki jeba."

Hararanshi tayi sama da k'asa cikin dariya tace "to waya fad'a maku dama ina neman
izininku idan ina san fita."

Dariya yayi dan ya fahimci ta tuna dah ne, a lokacin da ta nemi izinin fita ya
hanata har tayi hatsari, cewa yayi "in ko ki kaje to zaki rasa ido ko k'afa."

Cikin dariya tace "idan ma na rasa ai kune za kuyi jinyata."

Kafad'a ya d'aga yace "um um, ba zanyi ba wannan karin, za kiji da kanki ne"

Dariya tayi tace "dole zakuyi kodan gudun kar na maku fitsari akan kago."

Fashewa yayi da dariya yace "ai a gadonki zakiyi jinyar ba a nawa ba."

Cikin kunne ta rad'a masa "amma ai kunfi jin dad'in bacci akan gadona."

Kallonta yayi yace "kuma fa hakane yarinyata."

Hararan wasa ta masa tace "wacece yarinyar?"

Hannu ya d'aga mata yace "afuwan, to 'yan matana."

Duka ta kai mashi a k'irji lokaci d'aya kuma ta rumgumeshi tare da fad'in
"shashasha na kenan, ina sonku sosai."

Shima rumgumeta yayi yace "nima ina sonki sosai rabin raina."

Haka suka lula duniyarsu mai wuyar fassarawa da kuma dad'i da annashuwa a wajensu.

*ALHAMDULILLAH, ALHAMDULILLAH, ALHAMDULILLAH KASIRAN.*

_ALLAH NA GODE MAKA DAKA BANI IKON KAMMALA WANNAN NOVEL LAFIYA KAMAR YANDA NA
FARASHI LAFIYA, 'YAN UWA KUMA MASOYANA INA SONKU INA ALFAHARI DAKU._

*BANDA NOVEL D'IN DAYA FI _KAUSSAR_ AMMA KUMA _AUREN HA'DI_ MA YA ZAMA ZAKARAN
GWAJIN DAFI, DAN DAGA IRIN MASOYAN DAYA SAMU NASAN CEWA SAK'ON DA NAKE SAN ISARWA
YAJE IN DA NAKE SO YAJE.*

```AUREN HA'DI BAWAI NAYI SHI BANE KAWAI DAN NISHAD'I KO SAK'ON SOYAYYA, DUK IN DA
AKACE AUREN HA'DI, TO CIKIN BIYU DOLE D'AYA ZAI FARU,```
_1-IN MA ZUMUNCI YA D'ORE KO KUMA YA WARGAJE,_

_2-TSAYAWA TSAYIN DAKA AKAN KOWACE UWA AKAN 'YA"YANTA, MUSAMMAN MATA DOMIN GIDAN
AURE ZASU JE, KAMAR DAI YANDA LA MAMA TAYI._

_3-SANIN GIRMAN MIJI DOLE AKAN KOWACE MACE MAI NEMAN ALJANNA._

_4-SOYAYYA KAN IYA SA MACE TA MANCE DA KOMAI, KAMAR DAI YANDA UMMI TAYI DUK DA BATA
SAMU HAIHUWA DA WURI BA, DAMA MU MATA 'YAN SOYAYYA NE HAKA ALLAH YA HALLINCE MU._

_5-GIRMAMA MIJI TA HANYAR YI MASA BIYAYYA DA LADABI DA KUMA JIN MAGANARSA._

_WANNAN SUNE GINSHIK'IN DA YASA NA SAKE RUBUTA WANNAN NOVEL, SANNAN 'YAN UWA BANCE
MAKU HAR ABADA BA, AMMA DAI BANA TUNANIN SAKE RUBUTU MUSAMMAM MA NAN KUSA, AMMA
WATAK'ILA KU JIMU A CI GABAN *AURENMU A YAU* WANDA MUKE NI DA 'YAN HANUNA._

*ALLAH KA YAFE MIN KURA KURAINA DAKE CIKIN WANNAN RUBUTU, A IN DA NAYI DAIDAI KUMA
KA BANI LADAR TARE DA LADAR FAD'AKARWA, DUK WANDA YA KARANTA KUMA YA K'ARU ALLAH
KAYI MASA ALBARKA, ALLAH KA SHIRYA MIN YARANA KA K'ARA MAMU DANK'ON SOYAYYA DA
MIJINA D'AYA TAMKAR DA DUBU, INA ALFAHARI DAKU, DOMIN KUNA BANI 'YANCINA A
MATSAYINA NA MACE, KUNATAUSAYA MIN A MATSAYINA NA MAI RAUNI, KUNA WASA DANI DA HIRA
DANI A MATSAYINA NA ABOKIYAR ZAMANKU. LUV YOU MON ANGE💋*👏👏💃

*SEE YOU GUY'S*

_SAMEERA CE_🤜🤛

You might also like