BABBAN GIDA (seemaluv)

You might also like

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 124

[5/23, 2:49 PM] Jameesha: .....

馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

馃尮 GODIYA 馃尮
Dukkan Godiya Da Yabo Sun Tabbata Ga Ubangiji Mallakin Sammai Da Kassai, Wanda Ya
Tsaida Ita Ya Kuma Shinfidata Ba Tare da Wani Majingi Ko Taimakon Wani Abin Halitta
Ba. Tsira da Amincinsa Su Tabbata Ga Annabin Karshen Zamani Cikamakin Annabawa,
Wanda Haskensa Da Kamshinsa Basa Gushe wa Daga Zuciyar Wanda Yafi Kowa Yi Masa
Salati.

馃尮 SADAUKARWA 馃尮
Na Sadaukar Da Wannan Littafin Ga Marigayi Muhammad Abdulmumin Suraj Da Marigayi
Lawal(Na Goggo )Allah Yaji Kansu Da Rahmarsa Ya Haskaka Makwancin su, Allah Ya Bamu
Guzurin Ishesu Cikin Ni'imarsa Amin-Amin.

馃尮 IYA YENA 馃尮
Iyayena Alhaji Idris Musa Alhasan Da Hajiya Amina Ango Abdullahi, Allah Ubangiji Ya
Biya Muku Dukkan Buka tunku Ya Kuma Yi Muku Sakayya Da Gidan Aljanna Kan Irin
Tarbiyyar Da Kuka Bani Na Gode Kwarai, Allah Ya Kara Lafiya Da Tsawon Rai Amin Ya
Allah.

馃尮 KANNAI NA 馃尮
-Hafsat Idris
-Alhassan Idris
-Fatima Idris
-Sa'adatu Idris

馃尮 Allah ya bar Zumunci Yan Uwana.馃尮


-Aunty Bara'atu
-Aunty Mahadiyya
-Aunty Hafsat (Ummi)
-Aunty Khadija (Yarinya)
-Aunty Fatima (Gaje )

馃尮 KAWAYEN ASALI 馃尮
-Asiya Muhammad (Reality )
-Rabeeat Idris Baba (Slexy )
-Fatima Ango Abdullahi (Queenart )
-Zainab Abubukar (Sparkle)
-Zainab Ibrahim.

馃尮 BAN MANTA DAKU BA 馃尮


-MISS XOXO
-MELODY
-CUTE ZARAH
-ZAHRA BUKAR
-ILILEE
-MR SMILE
-RAHEEM
-ASY KHALEEL
-MAMAN USY
-SADNAF
-ANKA
-.........AND THE REST....

1-2page 馃尮

Da Gudu Fadwa ta biyo Ta tana Fad'in,


"Allah ilham ki bani Waya ta bana so.
Fitowar Umma Keda wuya ilham taje bayan Umma ta Boye ' Umma ta ce,
"Ilham? Fadwa kika tsokana koh?
"Eh Umma duba fa Chatting takeyi da Wani Saurayin ta.
Ilham Zata Nunawa Umma Wayar kenan ' Fadwa tayi Sauri ta Fizge Wayar daga Hannun
ta.
"Aunty Karya Ilham takeyi miki, ni banda Wani Saurayi.
Umma zatayi magana kenan Yaya Farook ya shigo parlon cikin bacin Rai ' Fadwa Da
Ilham suna ganin shi suka sunkuyar da kai cike da Nutsuwa.
"Wannan wane irin iskancin banza ne ' bance maku idan ina bacci banason
surutu ba?
A tare suka Amsa mashi da cewa,
"Ka ce!!!
Yaya Farook kallon wayar da ke hannun Fadwa yayi,
"Ke kuma ban wayar Nan ' nayi seezing dinta,
Nan Hawaye suka cika idon Fadwa jikin ta na rawa Ta mika mashi Wayar,
"Yaya Farook please am....
Tun Kafin ta Karasa fada ya daka mata tsawa da cewa,
"Yimin Shuru.
Yaya Farook Ansan Wayar yayi sannan ya juya ya Wuce Dakin Shi.
Umma Koma wa tayi ta Zauna ba tare da ta saka masu baki a Maganar su ba,
"To ai saiku dawo ku zauna tunda ya wuce.
Cikin Sauri suka dawo suka zauna ' Fadwa kuwa idanu cike Da Hawaye.
"Umma Don Allah kitayani bawa Yaya Farook Hakuri ' ya dawomin da Waya ta.
"A'a babu ruwa na a maganar ku, Aikune dun bakwajin Magana.
Fadwa maida kallon ta tayi ga Ilham wacce itama jikin ta dar dar yake saboda tsoro.
"Ai duk Ke kikaja gashi nan ya Anshemun waya.
Harara Ilham ta watsawa Fadwa,
"Ke inda kinsan tsoron da ke jikina da bakimin wannan Maganar Banxan ba.
Shuru sukayi nad'an lokaci sannan Fadwa tayi Zanbur ta mike tsaye tare da dafe
kanta,
"Nashiga uku ilham ' na manta ban sanyawa wayata security ba, gashi Yaya
Farook zai iya shiga wani wajen dabam.
Umma tashi tayi tare da cewa, "Ni yaran nan kuna neman kusamin ciwon kai
wallahi ' bakin bazai ta'bayin shuru ba.
Ta na gama fad'in haka ta wuce sashen ta.
"Nifa Fadwa duk fa laifinki ne ' ke ce da kike yawon fito da wayar ki parlor
gashi nan tsautsayi ya Afka mata.
Cewar ilham.
Fadwa koma wa tayi ta zauna tare da zuba tagumi,
"Don dai Abba yayi tafiya ne Amma dashi zai kwatarmin wayata.
Ilham najin haka tayi saurin toshewa Fadwa baki,
"Ke wai bakisan duk Abinda muke fada Anaji ba? To nidai karki jamun duka '
kinsan halin Yaya Farook sarai don ya jibge mu bawani abu bane Awajen shi.
"To yaji din mana ni ina ruwa na?
Cewar Fadwa.
Ilham mikewa tayi tsaye tare da yiwa Fadwa kallon Naman kaza.
"Lallai kuwa jiki zaiyi tsami ' ni kinga tafiyata... 馃毝
Ilham juyawa tayi a guje ta wuce dakinsu ' nan wajen Tabar Fadwa rai abace.
Wacece Fadwa, 'yace Ga Alhaji Aminu Muktar ' kuma yace Ga hajiya Amina Shehu,
Allah yayi masu rasuwa ne sakamakon Goborar da suka ' gaba daya suka kone. Fadwa ce
kadai ta tsira, A lokacin Fadwa Tana da shekara Goma sha tara 19 ' Hakan yasa
Alhaji Sulaiman wato Aminin Mahaifin Fadwa, Ya amince shi zai rike ta da Amana
kuma zai saka ta cikin Y'ay'an shi ' tamkar shine Ya haifeta.
Alhaji Sulaiman Mahaifine awajen Yaya Farook da Yaya Khaleel da kuma Ilham,
haka zalika 'ya'yane Awajen Hajia Maimuna, wacce suke kira da Umma.

馃憚馃憚馃憚馃槣
Dedicated To My Fan's.
漏 ONLINE HAUSA WRITERS.
[5/23, 2:49 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

3-4page 馃尮

Fadwa na Zaune ' sai ga Yaya Farook ya shigo parlon, Ta na ganin shi ta mike
tsaye.
"Yaya Farook kayi hakuri don Allah.
Ko kallon ta biyi ba ' ya Wuce. Ta na ganin ya fita ta nufi Dakin shi kai tsaye,
"Yanxu zan sami damar Daukar wayata ' kuma inyi mirsisi .
Tana gama Fadin haka ' ta hau yimashi bincike A dakin, gaba daya ta birkice dakin
' Fadwa ta du'ka zata bude Drower kenan taji magana kamar daga sama.
"Kinyi ajiya a wajen ne dazaki dauka?
Da sauri Fadwa ta dago kanta har tana Bige goshin ta ' Fargaba da tsoro ya hanata
juyowa,
"zaki juyo ki kalle ni, ko sai kinji saukan duka? Cewar Yaya Farook.
馃槰 Nan Fadwa ta hauyin adduoi kala kala ' saboda tsabar tsoro, A hankali ta juyo
ta kalle shi.
"Me kike nema a dakin?
"Yaya Farook ' Don Allah kayi hakur....
Tun kafin ta gama rufe baki ' ya dauke ta da mari tasss.... Nan take Fadwa ta Dafe
kumatun ta tare da Dukawa kasa, cikin kuka. Cen bata ankara ba taji saukar Hauri a
jikinta,
"Ahhhhgg!
Nan take ta fara Aman Wahala ' a galabaice,
"Zaki sake shigowa daki na ba tareda iznina ba? Zaki sake? Fadwa inbanda
girgiza kai babu abinda takeyi Alaman A'a.
"Good! Tashi ki fice mun a daki kuma ki dauko Mopper ki goge aman da kikayi!!
A guje ta tashi ta fita ' cikin hanzari ta dauko Mopped ta goge Aman, Yaya
Farook na kwance saman gadon shi yana kallon ta '
"idan kuma kingama ki dauko Perfume ki sa awajen ' don banason Karni yadame
ni.
To kawai Fadwa ta ce sannan ta je ta dauko turare ta sanya ma wajen. Da sauri ta
fice donma kada ya tsaida ita, kai tsaye ta wuce dakinsu ' Ta iske Ilham akwance ta
nata sharar baccin ta, Fadwa zuwa tayi ta zauna a gefen gadon ta kafa wani sabon
Kuka tamkar yanxu ne Yaya Farook ya mareta.
Kukan ta ne ya dami Ilham ' yasa ilham farkawa daga baccin da takeyi, Ganin Fadwa
a cikin wani hali ne yasa tayi hanzarin gangarowa kusa da ita.
"Fadwa? Me yafaru?
Da sauri Fadwa ta share hawayenta '
"Babu komai Ilham ' kawai na tuna da Iyayena ne...
Ilham rungume Fadwa tayi cike da tausayi,
"ayya kiyi hakuri Fadwa ' kedai kirinka masu addua kawai, kuma duk abinda
kikeso a Abbanmu na nan ko?
Kai Fadwa ta daga mata alaman Eh, Sannan Ilham ta lura da shedan yatsu a fuskar ta,
Alamun mari.
"Subhanallah! Fadwa Waye ya mareki haka?
Cewar ilham.
Fadwa shuru tayi bata Ce mata komai ba, sannan Ilham ta ce.
"Hmm Kinje daukan wayar ki dakin Yaya Farook ko?
"Ilham na dauka yayi nisa ne sabida naga fitarshi, Amma ina shiga ya ritsani
aciki.
"Aikin gani Allah yakara ' yanzu ai jikinki ya gaya maki, Kina abu kamar
bakisan wanene Yaya Farook ba.
"ilham Yaufa tsawon Shekara Biyu kenan ' da zuwa na gidan nan Saidai inji
Kuna labarin Wani Yaya Khaleel, wai waye shi.
Ajiyar zuciya Ilham tayi gami da Zuba ta gumi,
"Meyafaru naga kinyi ta gumi?
cewar Fadwa.
"hmm, Dole inyi Ta gumi domin kuwa Inhar Yaya Khaleel ya dawo ' to zaman
parlor ma sai ya gagaremu.
馃槰 Zaro ido Fadwa tayi cike da mamakin wannan Alamari,
"To wai wanne yafi zafi cikin su?
Cewar Fadwa.
Nan Ilham ta gyara zama tare da kama Hannun Fadwa,
"hmm Fadwa ai inhar Yaya Khaleel ya dawo to Yaya Farook dan kallo zai zama.
Wani ihu Fadwa ta Saki ' cike Da Zulumi,
"Ahhh 馃檰 to yaushe zai zawo?
Cewar Fadwa.
Dariya Ilham ta yi cike da buga kafa,
"What are you eating nabaka is falling dawn?' abba ya ce mun Next month Yaya
khaleel zai dawo, Kuma zai gama School din shi gaba daya.
馃槰馃槰馃槰馃槰
Ilham nagama fadin haka , Fadwa ta ruga da gudu ta fada Toilet...
Sai da Tayi 5 minutes sannan ta fito ' tana fitowa suka hada ido Da ilham, Babu
abinda ilham keyi inba dariya ba.
"Ke ni bazan biye maki ba ' duk kinbi kin gama tsorata mun ciki, Ni yanzu ma
bacci xan.
Fadwa na gama fadan haka ' ta haye gado ta fara bacci, ita kuwa Ilham ta Dauki
wayae ta ta hau chat.

*AROUND* *7pm*

Ilham Da Umma suka fito parlor Domin suyi Dinner dinsu, Shima Yaya Farook
Fitowa yayi daga dakin shi yaje Yayi joining dinsu a Dinning table ' bayan Sunfara
cin Abinci ne Umma ta ankara bata ga Fadwa a wajen ba,
"ilham? Ina Fadwa take ne?
"Umma tana daki a kwance ' wai zazzabi take ji,
Yaya Farook ajiye spoon dinda ke hannun shi ' tare da cewa,
"Zazzabi? And she is too big tazo ta fada abata magani ko? Umma bara inje
induba ta,
Kai Umma ta daga mashi alaman Tor, sannan Yaya Farook ya tashi ya nufi dakinsu
Ilham.
Koda ya shiga a Dukunkune ya iske ta acikin Blanket ' Ta na kuka, Yaya Farook
karasawa yayi ciki ya zauna a gefen gadon tare da yaye Blanket din. Ganin yadda
take rawan sanyine tausayin ta yakamashi,
"Bakida Lafiya meyasa Bazaki fada ba?
Fadwa shuru tayi bata ce komai ba,
"Ki tashi ki shirya inkaiki Hospital yanzun nan.
Har Yaya Farook ya mike tsaye da niyyar bata waje, yaji ta riko hannun shi.
"Yaya Farook don Allah idan Munje kace Masu ' karsumin Allura please!!!
Tausayin ta yasa ke shiganshi ' yayi sauri ya cire hannun ta daga Jikin shi,
"Is Ok! Ki dai tashi ki shirya ' kafin kuma Raina ya baci yanzun nan.
Ya na Gama Fadin haka ya juya ya fita cikin Sauri, Ya wuce dakin shin domin ya
dauko key din mota.

馃憚馃憚馃憚馃槣
*Dedicated* *To* *My* *Fan's*
[5/23, 2:49 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

5-6page 馃尮

Har saida Yaya Farook Yaje ya dauko key din ya dawo parlor, ya zauna zaman
jiran Fadwa.
sai da ta Bata Minti 30,sanan Ta fito Parlon.
"Yaya Farook gani!
Cewar Fadwa.
Tashi tsaye yayi tare da saka hannun shi cikin aljihu ' gami da yimata Wani mugun
kallo,
"Na dauka ko ' kinji sauki ne ai.
"Don Allah nidai Farook ka kaimin yarinya aduba ta.
Cewar Umma dake zaune a dinning table ta na kallon shi.
Yaya Farook fitane yayi Fadwa na biye dashi a baya har suka isa wajen motan, Ya
fara shiga sannan itama tashiga cikin hanzari mai gadi ya bude gate din ' tukunna
Yaya Farook Yaja motar.
Ba tare Da wani bata lokaci ba suka isa cikin Hospital yayi packing A gefe
sannan suka fito, ganin Fadwa ba ta sauri yasa ya kama hannun ta ' Haka ya dunga
janta har suka kai Office din Doctor din. Sannan likitan ya duba ta Ya rubuta mata
magun gunan da za'a siya, Cikin jin Dadin Fadwa ta Ansa takaddar magungu nan don
ganin babu allura ko daya aciki.
Har ta mike tsaye Likitan ya tsaida ita da cewa,
"Ki tsaya Akwai Allurar da za'ayi yanzu guda biyu, Data amai da kuma Wanda
zata rage maki zafin jiki.
Ta najin haka ta juyo ta kalli Yaya Farook, Suka hada ido ' Ganin Ya hade rai ne
yasa ta sunkuyar da kanta ba tare da tace komai.
"Idan kin shirya sai ki juyo.
Cewar doctor,
Jin haka Yasa ta juya ta mika mashi baya kamar da gaske ' Daya matso sai ta
matsa haka suka dungayi da Dr din, Abin ne yabawa Yaya Farook haushi ' A fusace ya
mike tare da finciko Fadwa ' ya rungumeta sosai ta yadda bazata iya motsi ba,
"Doctor yi mata Allurar ' don sauri nakeyi.
Cewar Yaya Farook,
Fadwa bata ankara ba taji shigar karfe ajikin ta ' jin haka yasa tasaki ihu cike
da kankame Yaya Farook,
"Wayyo Allah Yaya Farook!!!
"Shhhh, kiyi hakuri saura guda daya kinji ko?
Cewar Yaya Farook.
Fadwa ta naji tana gani aka sake tsira mata wani allurar, Sai da aka gama
sannan Yaya Farook ya zaunar da ita.
"Yanzu Zaku iya tafiya ' but saika dan rike ta saboda akwai Allurar da akayi
mai sanya jiri.
Ok kawai Yaya Farook ya ce ' sannan Ya rike hannun Fadwa suka fita daga wajen '
daker Fadwa Take jan kafar ta Yaya Farook ya lura da haka,
"Zaki daga kafa kimin sauri Ko saina dauke ki tukunna?
Dago kai tayi ta kalleshi a gala baice ,
"Yaya Farook bazan iya bane!
Bata gama rufe baki ba ' taji ya dauketa cakk tamkar wata jaririya, Fadwa Kara
lafewa tayi a jikin shi don kuwa batada wani karfi a jikinta.
Haka ya ratsa cikin Hospital din da Fadwa a hannun shi ' mutane kuwa sai
kallon shi sukeyi, kai tsaye ya nufi wajen Motar shi yasa key ya bude sannan ya
zagaya ya saka Fadwa A seat din baya,
"Saura kuma ki 'ki kwanciya.
Abinda ya fada kenan sannan ya shiga mota yaja suka koma gida A cikin *30*
*Minutes* .
Horn Yaya Farook ya yiwa Maigadi yazo ya bude ' tukunna ya karasa ciki. Packing
yayi cikin hanzari ya fito gami da Jan hannun Fadwa,
"kokarta ki fito don Yanzu dai ' nima nagaji bazan iya Daukanki ba don nauyine
dake!.
Jin haka yasa Fadwa taja jikin ta fito daga motar cikin sanyin jiki, har suka shiga
cikin parlor ' A zaune suka Iske *Ilham* tana Danna waya, Ganin su Yaya Farook ne
yasa tayi saurin sake wayar a riga.
"Ina Umma?
Cewar Yaya Farook.
"Tana Sashen ta,
"Tor ki kawowa Fadwa Dinner dinta yanzu taci a gaba na.
Cikin hanzari Ilham ta tashi ta nufi Kitchen,
"Ke kuma bazaki sami waje ki zauna bane kokuwa?
Cikin sanyin jiki ta zauna ' Gami da kallon kasa, don batamaso su hada Ido dashi.
Cikin dan kan kanin lokaci Ilham ta dawo da plate a hannun ta, Jellof rice ce a
ciki sai naman kaza cinYa daya.
Fadwa ansan abincin tayi tare da toshe hanci '
"Aiko zaki amayar da Hanjin cikin kine ' saikin cinye abincin nan tass,
bakina wani toshe hanci ba.
cewar Yaya Farook,
Tun da ta ansa abincin ' sai kollon shi takeyi, takasa sawa abaki. Ganin haka ne
Yaya Farook Ya Ansa abincin daga Hannun ta tareda diban spoon daya,
"Oya Ansa ' dakaina zanba ki ' kinayin Amai kuma kiji saukan duka.
Ba musu Fadwa ta bude bakin ta Yasa ka mata Abincin ' daker ta iya haddiyewa.
Ilham na tsaye a wajen Ta na kallon su ' Dukka dukka Spoon uku kawai Ta ci, ta fara
Kakarin Amai ' Bata Ankara ba Taji saukan dundu tiim Abayan ta haka yayi Dai dai da
Shigowar Umma Parlon,
"Subhanallah ' Wai kai Farook mekakeso ka maida kanka? Mugu ko mene?
Umma zuwa tayi taja hannun Fadwa, ta zauna a kusa da ita.
"Ya jikin naki?
Cewar Umma.
"Umma da sauki ' Amma Umma na koshi da abincin haka bacci zanyi.
Kai Umma ta daga mata tare da cewa,
"Shikenan, *Ilham* rike ta ku tafi daki.
Hannu *ilham* ta kamama *Fadwa* sannan suka tafi daki. Yaya Farook kallon
wristwatch din hannun shi yayi yaga ' 9:20pm dare yayi sosai, sannan ya maida
kallon shi wajen Umma.
"Umma sai da safe , ni zan kwanta.
"To Allah ya tashemu lafiya!
A tare suka tashi kowannen su ya wuce sashen shi. yaya Farook na shiga daki ya
cenja kayan jikin shi zuwa na bacci, sannan ya Haye gado tare da ciro Wayar Fadwa a
drower gado ' ya shiga Gallery ya fara kallon pictures dinta inbanda smilling babu
abinda yakeyi, Cen sai ya cikaro da wani hoton da tayi itada wani namiji A School
ta dafa shi. Nan fa Zuciyar shi tafara mai radadi da zafi,.
"Allah ya kaimu gobe saikin Fadamin Uban waye wannan.
Ya na gama fadin haka jefar da wayar a kasa, Daker ya iyayin bacci a wannan
lokacin.

*Washe* *Gari* *Around* 4:00am


Yaya Farook Ya tashi ya wuce masallaci, Bayan ya dawo ne ya koma bacci.
Wajen 6:30 *Ilham* ta shi ' tashiga bathroom tayo Alwala sannan ta tada *Fadwa*
daga bacci,
"Fadwa tashi muyi Sallah ' kada lokaci ya kure.
Cikin Magagin bacci ta tashi tafada Bathroom ita tayi Alwalan tukunna ta fito suka
yi sallah, Bayan sun sallame ne Fadwa taga Ilham ta haye gado tare da Lullube wa.
"Ilham bazaki je School bane yau?
"Eh ' saboda bakida lafiya konaje school din bazaimun dadi ba.
Murmushi kawai tayi sannan ta mike tsaye tare da cire hijjab dinta,
"Allah yasa Yaya Farook ya gane cewa bazakije School ba.
Nan take ilham taji cikin ta ya murda,
"insha Allah haka bazata faruba.
Fadwa hayewa gado tayi ' bacci yayi awon gaba da ita. Basu suka tashi ba sai
wajen 7:30, koda suka tashi Ilham kitchen ta shiga domin hada Breakfast. Yaya
Farook ' farkawa yayi daga Bacci yashiga bathroom yayi wanka ya fito sannan ya
shirya ' ya fita siyowa Fadwa Magungunan ta, Ba shiya dawo ba saida aka gama hada
breakfast sannan ' Yana shigowa parlor ya iske su Umma a dinning suna shan tea.
Karasawa wajen yayi yasami waje ya zauna ' sannan ya gaida Umma cike da ladabi,
Bayan ta amsa ne ya maida kallon shi akan Fadwa.
"Idan kingama breakfast din ' kizo Ki sameni a daki Kisha magana.
To kawai tace ' sannan Ya dauki tea dinshi ya sha, Yana gama wa ya mike tsaye
gami da cewa.
"kiyi ki gama Kizo ina jiranki ' don akwai inda zanje,
"To wai Shi maganin dole saikai ne zaka bata?
Cewar Umma.
"Eh Umma ' Saboda Batason magani.
Yana fadin haka ya juya ya wuce dakin shi, Ita kuwa Fadwa Hankalin ta atashe yake
' Cikin Zulumi ta ajiye cup din da ke hannun Ta tashi ta bishi Dakin.
*Dedicated* *To* *My* *Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:49 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

7-8pages 馃尮

Tana zuwa abaki kofa ta tsaya, Tayi Knocking gami da yin Sallama sannan ta
shiga. A zaune ta ganshi ' yana dannan wayar shi,
"Yaya Farook gani!
dago kanshi yayi ya kalle ta ' tundaga sama har kasa sannan ya ce,
"Ni zan biyoki Nan wajen inbaki maganin ko?馃槧
cikin hanzari ta karasa cikin dakin, kusa dashi ta tsaya ' Yaya Farook ya aje wayar
shi a gefe sannan ya duk'a inda ya jefar da Wayar Fadwa ya dauko, Gami da Tashi
tsaye. Damko kunnen ta yayi Tare da murdabawa,
"Idan kika sake kikayi ihu ' Umma taji to abinda zanmiki sai yafi haka.
Kai Fadwa ta daga mashi alaman To, sannan Yaya Farook ya kunna wayar tare da Nuna
mata Hoton da yagani.
"Uban waye wannan?
Ya fada yana sake murda kunnen,
"Yaya Farook Don Allah kayi hakuri ' Akwai zafi....
Cikin launi na kuka ta karashe maganar, Kunnen ta duk yayi jaaa duk da Kasan cewar
Chocolate colour ce sai da yanuna.
"Oh akwai zafi kike cemun? Akwai zafi kike cemun?
Jikake timmm ' saukar duka a bayan ta, Cikin kuka tace.
"Yaya Farook, kayi hakuri ' wallahi zan fada maka.
Sakin kunnen yayi ' sannan ya sami waje ya zauna,
"daman wannan School friend dina ne ' Kuma ni banmasan shi na dafa ba .
Ta na fadin haka ya watso mata wata harara ' Cikin sauri ta,
"Wallahi Yaya Farook ' ka tambayi Ilham, babu wani abu tsakanina dashi.
Ta Na gama rufe baki ' Ya hada Wayar da bango, Ta fashe. 馃槺
"Idanma Akwai wani abu tsaka ninku, to na fasa Wayar ' Kuma bazaki sake yin
Waya ba tunda abun naku iskanci zai koma, har itama Ilham din saina karba nata.
Fadwa babu abinda takeyi inba kuka ba ' Yaya Farook mikewa yayi ya dauko mata
magun gunan, ya cire mata wanda zatasha yanxu Ya bata tare da bata cup din ruwa ta
rike a hannu.
"In kinga dama kiyimin Amai a daki ' Jikin ki kuma yagaya maki.
Daker ta iya shanye Maganin ' Aje mashi Cup din tayi sannan ta juya da niyyar
tafiya,
"ke!!! Na sallame kine?
Tsayawa tayi gami da Juyowa ta kalleshi ' Lemon sweet ya dauko daga cikin drower
din shi, Ya bata.
"Bude kisa abaki yanzu, Saboda maganin da kikasha Akwaisu daci.
Babu musu tayi yadda yace '
"Oya Share hawayen ki '
Fadwa Share hawayen fuskarta tayi ' sannan ta kalleshi.
"And Yanzu kinsan me nakeso kiyi?
Ta girgiza mashi alaman A'a.
"Murmushi nakeso kiyi yanzu ' saiki wuce.
Don dole Fadwa ta matso murmushin karfin hali ' tayi mashi, Shima Murmushi yayi
mata gami da cewa.
"Good gurl, kokefa ' yanxu kina fita ki wuce daki ki kwanta, ki huta.
Juyawa tayi ta wuce ba tare da tace mashi komai ba, Ta na fita taja tsaki.
"Mtsweee!!! Wai adaki mutum ahana shi kuka, Nidai Wallahi sai Allah yasaka
min.
Dakin su ta shige ta kwanta kamar yadda ya Umarce ta'.
Yaya Farook Fitowa yayi ' ya nufi Parlor ya iske Ilham,
"Ke! Babu School ne yau?
Cewar Yaya Farook.
Nan take ta mike tsaye Ta tako har inda yake cikin Dingishin kafa,
"Yaya Farook, targade nayi dazun ' shiyasa.
Tayi maganar gami da nuna mashi kafar, Harara ya watsa mata sannan Ya fice. Ta
ganin fitar shi ' takoma wajen Umma ta zauna,
"*Umma* don Allah cewa Yaya Farook ' ya rika shan Ruwan Buta, Seriously Umma
ya cika fushi da yawa matar shi zatasha wuya.
"allah ko? to bari yazo sai infada mashi ' abinda kikace game dashi.
馃槰"No Umma kada ki fada babu ruwa na walkahi, Ban shirya shan duka ba.
Tashi ilham tayi zata wuce sai kuma ta dawo ta zauna tare da cewa,
"Yawwa *Umma* please ki bamu izni nida Fadwa mu fita.
"Ina kuma zaku je? Kinsan dai Fadwa batada lafiya koh?
"Haba Umma Shopping mu keso muje ' kibarmu kawai , ai ta sami lafiya.
Cewar Ilham,
Umma dogon Numfashi taja sannan ta ce,
"A'a Ilham kidai bari Yayanku ya dawo sai kuje,.
To kawai Ta ce sannan ta tashi ta wuce dakinsu ' Jikin sanyin jiki. A kwance
Ilham ta iske Fadwa ' tukunna ta sami gefen gado ta zauna,
"Fadwa? Ki tashi kishirya muje ' Shopping.
Cewar Ilham,
Zanbur Fadwa ' tayi ta tashi zaune cike da fara'a.
"Wow! Aikam yanzu zan tashi inyi makeup, but yanaga jikinki a sanyaye?
"Umma ce tace wai saimun jira Yaya Farook,.
Ajiyar zuciya Fadwa tayi ' gami da mikewa tsaye,
"Shine duk zaki wani damu? Ki dai tashi ki shirya.
Ilham itama mikewa tayi ta shirya ' suka caba ado sannan suka nufi Parlor suka
zauna zaman jiran Yaya Farook.

*Around* *2:30pm*

Yaya Farook Ya shigo gida ' Cikin sallama sanan suka amsa tare da Mikewa tsaye,
"Lafiya? Kuka mimmike tsaye kamar soldiers?
sunkuyar Da kansu sukayi ' sannan Umma dake gefe ta ce,
"Cewa sukayi ' wai zasuje Shopping shine nace subari kadawo, tukunna.
Watsa masu harara yayi ' ya wuce gami da cewa,
"Babu inda zakuje.
Kallon junan su sukayi ' sannan suka koma daki cikin kunkunai. zama sukayi gami
dayin shuru nadan lokaci,
"Nidai gaskiya, xanje inroke shi ' don seriously inada abinda zan saya, Idan
ba haka ba kuwa Gobe daga school zanje.
Harara Ilham ta watsawa Fadwa,
"I think you're very stubborn right? Fadwa kinfiso Kici dukan banza ko?
Alright Allah yabaki Sa'a.
Ameen Ta ce tare da mikewa ' ta wuce Dakin Yaya Farook, Knocking tayi sannan ta
shiga ciki ' A tsaye ta iske shi ya na kokarin cire rigar jikin shi, hakan yasa
Tayi saurin juya mashi baya.
Hakan yasa Yaya Farook yin Murmushi cike da cije leben shi, ya daure fuska.
"Ke!!! Lafiya kika juyamin baYa? Dalla juyo ki fuskan ceni.
Cikin tsawa yayi maganar ' Haka yasa tayin hanzarin Juyowa ta Fuskance shi.
"Yaya Farook ' daman nazo ne Innemi izni awajenka.
"For What?
"Yaya Farook ' Please kadan barmu Mu tafi shopping nida Ilham i really want to
buy something.
"No!!!,
Ya fada cikin tsawa!
Nan take Idon ta ya ciko da Kwalla,
"Yaya Farook, don Allah....
"banace A'a ba? Ko so kike sai nayi kwallo dake?
Juyawa tayi ta fita daga dakin cikin bacin rai' a zuciyar ta tace,
"Lallai kuwa gobe After School zanje'...
Ta na gama Ayyana hakan a ranta ' ta wuce parlor ta yi zamanta wajen Umma.
*Dedicated* *To* *My* *Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:49 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

*9-10* page 馃尮

*Some* *minutes* *later*


Yaya Farook ' ya shigo cikin Parlor Ya iske Umma da Fadwa suna kallo,
"Fadwa Kiramin Ilham.
Jin maganar tayi kamar daga sama' don batasa da shigowar shi parlon. Cikin hanzari
ta tashi ta kira Ilham na dan wani lokaci, sannan suka dawo parlon tare.
"Yaya Farook gani!
"Indomie zaki dafamin ' yanzun nan, kuma *30Minutes* na baki.
Babu musu ko wani alaman damuwa a fuskar ta ' ta fada kitchen, A cikin wannan
*30minutes* ta gama ' ta zuba a plate sannan ta kai mashi Parlor.
"Yaya, Gashi nan.
Ansa yayi ya fara ci ' cikin sauri, Tukunna Ilham ta koma Ta zauna.
Yana gamawa yayi Hamdala ' gami dayin gyaran murya,
"Mhnm, Ilham da Fadwa ' tashi zakuyi Yanzu Ku shiga kitchen, Ayi lunch da wuri
domin akwai Abokina da zaiyi joining dinmu.
Cikin hanzari suka tashi suka bar Parlon zuwa kitchen ' Jellof rice with
chicken sukayi preparing yi. cikin *1* *hour* Suka kammala komai sannan suka jera
Abincin Saman Dinning Table.
Yaya Farook kira ne ya shigo cikin wayar shi ' yayi recieving dinshi,
"Hello Taj? Harka iso ne? To shikenan ganinan zuwa.
Abunda sukaji ya ce kenan sannan ya tashi ya fita ' cikin *5* *minutes* suka shigo
tare da Abokin nasa.
Bayan Isowar su parlon ne ' Abokin nashi ya duk'a ya gaida Umma ta amsa cikin
kamala, sannan Ta tashi tare da cewa.
"Fadwa biyoni da Abinci na Daki.
Cike da ladabi ta zubawa Umma abincin ta a plate ' Ta bita da shi, ita kuwa Ilham
zama tayi A dinning sannan Yaya Farook ya Umarci Abokin sa da suje su zauna domin
suci abinci. Bayan zaman sune Ilham ta yiwa Abokin nashi sannan da zuwa sannan tayi
serving dinsu Abinci '
"Wannan ce kanwar ka?
Yayi tambayar ya na kallon fuskar Yaya Farook,
"Eh ita ce Kanwa ta.
maida kallon shi yayi kan Ilham wacce take cin abinci,
"Well, sunana Tajuddeen ' amma zaki iya kirana da Taj.
Ko kallon shi Ilham ba tayi ba ' tace,
"Am Ilham by name.
Ta na gama fadin haka ne ' Fadwa ta shigo parlon tunda ta shigo Taj ya ke kallon ta
' kai tsaye ta wuce inda Ilham take, bayan ta zauna ne ' ta Zuba abinci ta faraci,
still idon shi na kanta.
"Farook? Wannan kuma wacece? Kuma mene sunan ta. Cewar Taj,
"Ai gaka gata ' ka tambaye ta mana.
Fadwa Kallon Taj tayi ' tare da yimashi Murmushi,
"Sunana Fadwa ' kuma nima kanwar shi ce, Kaima meye sunan ka?
Tajuddeen yaji dadin yadda Fadwa ta saki jikinta,
"Sunana Tajuddeen ' Fadwa you have a nice name.
Jin Haka yasa Yaya Farook ya kalle shi, cikin bacin rai.
"Meye haka kakeyi Taj?
Cewar Yaya Farook,
"Me nayi kuma yanzu?
yaya Farook kallon Fadwa yayi ' haka yasa ta sunkuyar da kanta kasa,
"Ku tashi ku dauki abincin ku , ku shiga daga ciki.
turo baki sukayi ' sannan suka mike tsaye, suka bar wajen cikin kunkuni.
"Farook naga Alaman Kana takura wa yaran nan ' meyasa?
Taj yayi tambayar gami da Ajiye spoon din hannun shi.
"look, idan ka koshine mutashi ' mukara gaba, don nalura kacika shirme!
"No Farook, ba shirme nakeyi ba ' wallahi tunda naga kanwar ka naji inason
ta.
馃槰, Gamm ' gaban Yaya Farook ya Fadi,
"Wace Kanwar ta wa?
*Taj* murmushi yayi gami da gyara zafi,
"Kanwar ka nakeso, Fadwa!!! And I hope bazaka hana niba?
Yaya Farook is totally speechless ' yama rasa abinda zaicewa Taj, haka yasa shi
mikewa tsaye tare da Sanya hannun shi a aljihu.
"Ya naga ka mike tsaye ' kuma kayi shuru?
Cewar Taj,
"Saboda kazo abu mafi wahala.
"Meyasa?
"Saboda bazan iya baka Fadwa ba ' Taj ka nemi wata kawai.
Ajiyar zuciya yayi ' sannan ya ce,
"hmm, Farook kodai inada wani mugun hali ne?
"Taj, Bakada wani mugun hali ' Kawai dai...
"Kawai dai me?
Yaya Farook shuru yayi ya kyaleshi ' don kuwa zuciyar kemashi zafi,.
"Hm shikenan Farook, Yanzu inaso ka bani Damar yiwa Fadwa magana ' na *30*
*minutes* kawai.
OK kawai Yaya Farook ya ce ' sannan ya kwalawa Fadwa kira, Cikin sauri ta iso
Parlon.
"Yaya Gani.
"Tajuddeen ne yakeso ku gaisa.
Kallon Taj tayi ' cike da fara'a, Taj Mika mata Card dinshi yayi.
"Ga card dina nan, Zaki iya nema na ta wannan Number din.
Murmushi tayi gami da Kala kanta alaman to ' sannan sukayi sallama ta koma daki.
Yaya Farook da Tajuddeen, fita sukayi Don suga gari.
Bayan Shigar Fadwa daki ne ' tayi tsalle ta fada saman gado cike da jin dadi,
"Wai ke lafiyan ki kuwa?
Cewar Ilham,
mika mata Card dinda yabata tayi ' tare da cewa,
"Kinga Card din da abokin Yaya Farook ya bani ' kuma yace In nemeshi.
"Ke kuma shine kiketa wani zumudi kinma kasa kama kanki gaba daYa.
Tashi Fadwa tayi ta zauna ' Tareda cewa,
"Ilham nidai guy din yaymun ne wallahi, Shiyasa gashi kyakkyawa .
Yatsine Ilham tayi ' sannan tace ,
"Kudai kuka sani ' daga ke harshi din.
Komawa ilham tayi ta kwanta abinta.

*AROUND* *6:00PM*

Da yamma Yaya Farook ya maida Taj gida, sannan ya tsaya yayi Sallah a masallaci
tukunna ya dawo gida. Bayan shigo warshi ne ya iske su Ilham suna cin abinci,
"Ilham ina Umma?
"Umma ta na dakin ta,
Waje ya samu ya zauna ' sannan yace,
"Amma taci abinci kuwa?
"Eh ta ci abinci.
"Tor yanzu ' Kinsan me nakeso dake?
Ta girgiza kai alaman A'a,
"Kije Ki dauko min wayar ki kikawomin yanzun nan,
馃槰, zaro ido tayi gami da cewa,
"Yaya Farook Menayi?
wata mugun harara ya watsa mata, batasan lokacin da ta ruga aguje taje ta dauko
wayar ta bashi ba ' itadai Fadwa ta na Gefe ta kallo. Ilham dawo wa tayi Parlon
tare da wayar ta ahannu ' ta mika mashi,
"Yawwa, kema Babu ke bayin Waya daga yau Ilham.
Cewar Yaya Farook,
"Yaya Farook don Allah kayi hakuri, wallahi....
Tun kafin Ta gama rufe baki ' Yaya Farook ya tashi ya wuce dakin shi tare da cewa,
"Ki biyoni ki karba.
*Dedicated* *To* *My* *Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槤
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

*11-12* pages 馃尮

Nan Wajen Ilham ta zauna ' kusa da Fadwa, Idanuwan ta cike da hawaye.
"Karki damu Ilham ' ninasan meyasa ya karbe maki waya, Saboda Taj Yace in neme
sane shiyasa.
Cewar Fadwa,
"To ni meyasa abun zai shafeni?
"Hm kada kidamu ' Bari Abba ya dawo mu fada mashi.
Da sauri ta kalle ta ' cikin fuskar mamaki,
"Lallaima Fadwa ' to nidai wallahi babu ruwa na, Idan kika fadawa Abba
kinsan dai ' Yaya Farook kanmu zai rama ko?
Ajiyar zuciya Fadwa tayi sannan ta ce,
"Tor Allah ya kyauta ' nidai xanje in kwanta don banajin yunwa, kuma inaso in
tashi da wuri gobe.
Tana gama fadin ta tashi ta wuce Dakin su ' itama Ilham tabi bayanta.

*Washe* *Gari*

Da sassafe Su Fadwa suka tashi ' cikin hanzari suka shirya sannan sukayi breakfast,
Suka wuce School.
Bayan shigan su cikin Class ne ' lecturer ya shigo Yagama lecture sannan ya
fito, Haka Yasa Fadwa ta sami wayar wata friend dinta ' Ta kira Tajuddeen ta hanyar
yin Amfani da Card dinda ya ba ta. Ringing Uku yayi ya dauka,
"Hello Who's this?
Cewar Taj,
"It's me Fadwa.
Jin haka yasa yayi murmushi ' tamkar yana ganin ta.
"Wow! Fadwa Yakike ' kina Ina ne haka? Naji surutu.
"ayya! Ina School ne yanzu.
"Zan iya zuwa School din domin mu gaisa?
Murmushi tayi har sai da yaji ' Sautin shi, sannan ta ce.
"Eh Zaka iya ' But kazo 2:00 lokacin munyi closing.
Ok kawai ya ce ' sannan ya kashe wayar, ita kuma ta maidawa mai wayar ' wayanta.
Ilham na zaune A seat dinta ' fadwa tazo ta zauna kusa da ita tare da cewa,
"guest What!!!
"Fadwa you know that am not good in that ' so kawai ki fadamun menene?
Cewar Ilham,
"Taj, ne yace min zaizo School din nan Anjima ' Domin mu gaisa.
"wanene Taj kuma?
"Tajuddeen mana ' Abokin Yaya Farook,
馃槰 a tsora ce Ilham ta mike tsaye tare da cewa,
"What!!? Fadwa? Keko? Amma shikenan Allah ya baku sa'a,
"Ke miye? Duk kika wani tsora ta? Aidama na fada maki ' zanje Shopping yau so
After closing Idanma driver ya zo bana nan, kawai ki wuce.
"Ok ' ai dayake ma ba jikina ne zaiyi tsami ba.
Harara Ta watsa mata sannan ta tashi ta bar wajen.

Bayan anyi closing ne ' suka fito daga school suka tsaya abakin gate, Don jiran
driver.
"Yanzu Fadwa ' bazaki hakura da wannan Shopping din ba?
Cewar Ilham,
"Nifa gaskiya Ilham banason haka ' ni idan kina fadim haka banajin dadi, Kawai
addua zakimin kada Yaya Farook ya gane cewa bana gida.
Suna cikin haka ne driver yazo ' Ilham ta shige mota ta bar Fadwa anan wajen. Bayan
wuce warsu ne ' nadan wani lokaci Tajuddeen yazo da motar sa yayi Packing daidai
inda take tsaye, sannan ya sauke glass din motar.
"Kiyi hakuri na bata maki lokaci ko?
Murmushi tayi ' Tare da Girgiza kai Alaman A'a.
"To yanzu dai ki shigo mota sai muyi magana,
Shiga motar tayi kamar yadda ya umarce ta, Bayan zaman ta ne ta ce.
"Nifa dama shopping nakeso inje ' Saboda sauri nakeyi banaso Yaya Farook ya
gane.
Shuru Taj yayi nadan lokaci ' sannan ya ce,
"Yayan ki yana takura maki ko?
Ta daga kai alaman Eh ' Sannan yasa hannu ya shafa kumatun ta,
"kiyi hakuri ' Ai muna tare ko?
tsoro taji ganin yadda ya shafa fuskar ta ' hakan yasa ta fara dar dar Dashi.
Shima lura yayi da yadda Fuskar ta ya sauya ' haka yasa ya ciji lips dinshi
gami da yin Murmushi,
"Nina fasa Zuwa shopping din ma ' Bara kawai in sami taxi ya kaini gida.
Cikin damuwa tayi maganar ' har saida Ya nuna a fuskar ta, bude Kofar motar tayi
xata fita ' yayi sauri ya rike Gelen ta cikin fargaba ta juyo ta kalleshi.
"Haba Fadwa, why are behaving like a kid? na lura tunda na taba fuskar ki '
yanayin ki duk ya cenja Why?
Nan take jikin ta ya fara rawa ' cikin rawar murya tace,
"Don Allah Taj ' ka sakemin gele na intafi, Please.
"Tor yanzu bazaki bari intaba abinda yafi fuskarki tsadaba?
馃槰, Da karfi ta fizge gelen ta ta fito daga motar ' cikin hanzari ta tare Napep,
bayan ta zauna ne ta kalli wristwatch din hannun ta taga 2:30pm ' nan gaban ta ya
sake Faduwa.
"Don Allah bawan Allah kayi sauri mana!
"To aibaki fadamun inda zan kaikiba hajia.
Cewar mai keke napep,
Nan ta fada mashi inda zaikai ta ' sannan suka dauki hanya. Ba ita takai gida ba
sai wajen 2:56pm, Tana sauka ta mika mashi kudin shi sannan ta shige gida ' Saida
ta tsaya a bakin kofa tayi Adduo tukunna ta bude ta shiga ciki.
Ta na shiga da Yaya Farook ' ta fara hada ido, Ya watso mata wata muguwar
harara gami da Karkada kai ' Gaban ta ya fadi dakerr ta iya hadiye miyau, sannan ta
waiga bata ga Umma a kusa ba haka zalika babu Ilham a kusa. Haka ta taka tare da
yin sallama ' ta wuce ciki,
"Hmm Ba yanzu zan kama kiba tukunna!
A zuciyar shi ya fadi haka, ' ita kuwa sai jin dadi takeyi ganin bai tsaida ita ba,
Cikin fara'a ta shige daki ' akwance ta iske Ilham ta na Assignment, Sannan Fadwa
ta ajiye handbag dinta a saman Drower ta koma ta zauna a gefen Ilham,
"Ke! Ilham Yaya Farook ' baimin komai ba wallahi.
Ilham dariyar mugunta tayi tare da jan tsaki,
"saida ya tambaye ni ' ina kika tsaya nikuma na fada mashi duk abinda
nasani,sannan ya ce yau jikin ki zai gaya maki kuwa.
"Na shiga ukku ' ni Fadwa banda ruwan wanke kai yau, inama ace Abba zai dawo
yau.
Cewar Fadwa,
Tabe baki Ilham tayi ' sannan ta cigaba da abunda takeyi, Ita kuma Fadwa ta
tashi ta cire kayan jikinta ta daura towel ' tukunna ta shige bathroom don Watsa
ruwa. Bayan Shigan ta Bathroom ne Yaya Farook ya shigo dakin,
"Ina Fadwa?
Cikin tsawa yayi maganar ' haka yasa Ilham firgita, Ta yi saurin cewa,
"Tashiga wanka!
"Ok Tana fito wa kice tazo ta sameni ' kada kuma ta batamun lokaci..
To kawai ta ce sannan ta maida kanta akan Assignmenta dinta.
Bayan *5* *Minutes* Fadwa ta fito daga wanka, Ta na fitowa Ilham ta ce.
"*Yaya* *Farook* yazo da kansa kuma yace kina fitowa kije kisame shi ' yanzu.
Raras gaban ta ya Fadi ' Gami da zaro ido.
"Ilham please kicemun wasa kike!
Shuru Ilham tayi ta kyaketa ' aibabu shiri Fadwa ta baza a guje taje dakin Yaya
Farook, saida tayi Knocking Sannan Ta shiga ' tama manta Towel ne a jikinta, Yana
ganinta ya mike tsaye .
"Yaya Gani!
Daf ita Ya matso ' sannan ya riko hannun ta yajata har cikin Dakin,
"meyasa Bakijin magana Ehe!!!!
SunkuYar da kai tayi ba tare da tace komai ba,
"Ba zaki fadamun inda kukaje ba saina mareki?
Hawaye ke zubo mata a fuska amma babu yadda ta iya,
"Yaya Farook, Tajuddeen ne yazo School dinmu Shineee....
Bata gama rufe baki ba ' taji saukan mari a fuskar ta Tasss....
"Ahhhgggg!!!!
Sauri Dafe wajen tayi ' cikin kuka,
"Fadamun Ubanwa ya gayyace shi wajen ' idanba ke ba!!!
Hannu biyu yasa ya dafa kafadunta gami da girgiza ta,
"Kinsan meyasa nadamu ke? Kuma kinsan meyasa nake miki haka? Hmm Saboda ina
sonki!! Ina sonki Fadwa!!!
Jikinta yayi sanyi ' tsayawa Tayi ta na kallon shi cike da mamaki,
"nan *BABBAN* *GIDA* * NE!!* Kuma cikin shi kike ' Fadwa kinsan waye Taj dahar
kika saki jiki dashi haka?
Ya fada gami da Girgiza ta ' da har sai da Towel din jikinta ya Kwance, Sauri
Fadwa tayi ta rike Towel din ' cikin kuka ta ce,
"Yaya Farook don Allah kayi hakuri ' bansan haka abun yake, please kayi
hakuri.
Harya daga hannun shi zai sake marin ta ' sai kuma ya fasa, ya sauke hannun tare
da juya mata baya.
"Fita ki bani waje ' before i did something that you will regret it.
Juyawa tayi ta bar dakin' da gudu cikin kuka ' ta shige dakinsu. Saman gado ta fada
' kuka kawai takeyi tamkar ranta zai fita.
*Dedicated* *To* *My* *Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

*15-16* pages 馃尮

Suna cikin Haka ne Umma ta shigo Parlon Ta sami Waje ta zauna Sannan Ta kalli
Fadwa ' Ganin yadda jikin ta duk yayi sanyi,
"Fadwa ya naga duk jikin ki yayi sanyi? Ko Halan Farook ya dake ki?
Cewar Umma,
Saida Ta kalli Yaya Farook sannan Ta girgizawa Umma kai alaman A'a, Suna cikin
Wannan ne Sukaji Sallama Abba ' Ilham ce tayi zambur ta mik'e tsaye tare dayin Ihu,
"ahhh!!! Yeee Abban mu ya dawo.
Gaba d'ayan su Mik'ewa sukayi tsaye cikin murna suka tunkare shi, Ilham ta karb'a
jakar hannun shi tare da cewa.
"Abba sannu da dawo wa!
Amsawa yayi Cike da fara'a sannan ya kalli Fadwa wacce ta rakub'e a bayan Umma ita
a dole ta na fushi,
"Haba Wa ya tab'amin Y'ata Fadwa?
Cewar Abba,
Nan ta saki Fuskarta Tayi murmushi sannan ta ce,
"Abba kaine Kaimin Laifi da baka dawo da Wuri ba ' amma Yanxu Tunda Kadawo
shikenan.
Gaba d'ayansu dariya sukayi sannan suka nufi Dinning Table domin cin abin, Ilham
kuma sashen Umma ta nufa Domin ta ajiye jakar Abba.
Bayan Sun zauna ne ' Fadwa ta fara Yimasu Sarving Abincin, Sai da tabbatar ta
zubawa kowa sannan Ta koma tazauna itama Ilham ta zo ta zauna suka fara cin Abinci
' Abba kallon Yaya Farook yayi sannan ya kuma kalli Ilham da Fadwa,
"Fadwa??
Abba ya kira sunan ta cikin kamala ta d'ago kai ta kalle shi tare da cewa,
"Na'am Abba.
"Naga kin rame mun ne, A kwai mai takura maki ne?
Abba na fad'in haka ta kalli Yaya Farook taga shima ita yake kallo ko zata ce wani
abu,
"A'a Abba babu mai takura mun, nayi rashin Lafiya ne.
Ta na gama rufe baki Umma tayi sauri ta ce,
"Karki wani boye mashi ' babu mai takura maku inbanda Farook.
"Haba Umma ki barta ta fad'a Da bakinta mana , ai ita tasan babu abinda nake
mata.
cewar Yaya Farook,
Shuru kawai Fadwa tayi ta sunkuyar da kanta.
"Hmm aini dama Nasan za'a rina Wannan zaman gidan naka wasane? Ainasan duk
wannan bak'in halin kansu zai kare.
Abba na gama fad'an haka Fadwa ta mik'e tsaye da niyyar wuce wa d'akin su.
"Ina kuma zakije?
Cewar Ilham,
"Wallahi bacci nakeji sosai ' shiyasa zanje in kwanta.
"Tohm nidai bacci ba yanzu ba,
Fadwa d'aukan plate d'inta tayi tare da yiwa Umma da Abba sallama , sannan ta
kad'a kanta ta wuce d'aki.
Bayan Wuce warta ne da y'an mintoci, Yaya Farook shima ya tashi gami da
yimasu sallama ' kai tsaye ya wuce d'akinsu Ilham, Ko sallama bai yiba yana shiga
ya iske Fadwa har tayi shirin bacci rigar bacci ne ma a jikin ta ' tana zaune a
kujerar Madubi.
Ganin mutum kawai tayi a tsaye a bayanta, hakan yayi matuk'ar bata tsoro ' a
firgice ta mik'e tsaye tana shirin yin ihu yayi saurin Toshe mata baki,
"Are you out of your sense? Akwai wanda zai shigo d'akin nan bayan nine?
Girgiza mashi kai tayi sannan ya sake mata baki ',
"Yaya Farook Lafiya?
Tayi tambayar ta na kallon idon shi,
"Fadwa meyasa bakiyi sallama dani ba kafin Kije ki kwanta?
Yayi maganar a sanyaye ' ita kanta saida tayi mamaki,
"Am sorry Yaya Farook.
"Ba kya tunanin halin da zan shiga?
Zaro idanu tayi cike da Mamaki a zuciyar ta tace,
"Oh ni Allah Yau kuma Yaya Farook ni yake fad'awa haka.
K'ara matsowa yayi dafff da ita suna shak'an numfashin junan su, sannan ya riko
habar ta.
"Am totally in love with you Fadwa ' am in love with your dress,
Abun ne ya bata tsoro ganin yadda ya sauya lokaci d'aya gashi kuma su biyu a d'akin
hakan yasa ta cewa,
"Yaya Farook please Kaje kada Ilham ta zo ta sameka a nan wajen kaji.
Saurin sakin ta yayi tare da cewa,
"Tor Promise me that we will Always be together.
Kai ta d'aga mashi Tare da cewa,
"I promise you that i will always be with you!!
Tana gama fad'in haka Ya juya Ya fita daga d'akin ya wuce d'akin shi.
Bayan fitan shine Ilham ta shigo d'akin a tsaye ta sami Fadwa,
"Kinyi wani tsaye kamar soldier ' ya akayi.
ta fad'a tana kokarin cire rigar jikinta don sanya ta bacci, Murmushi kawai Fadwa
tayi sannan ta ce.
"I think am in love with him.
ta fad'a tana k'ok'arin Hayewa saman gado, Cikin sauri Ilham ta sanya rigar bacci
itama ta d'are saman gadon Tare da zurawa Fadwa ido,
"In love with who ' Fadwa?
"No lokaci baiyi ba tukunna Ilham ' kibari sai lokaci yayi sai in fad'a
maki.
Ya tsine Fuska tayi gami da jan pillow,
"Kyadaiji dashi kuma idan tayi wari aizanji.
Cewar Ilham,
smilling Fadwa tayi sannan suka kwanta.

*** *** *** *** ***

*Washe* *Gari* ...

Da sassafe Fadwa ta farka daga bacci ' Jitayi tamkar an d'ora mata dutse a marar ta
saboda Azabar Ciwo,
"Ahhhghh Ilham don Allah ki tashi ki taimaka min,
Cikin Magagin bacci Ilham ta farka , Ganin yadda Fadwa keta hawaye ne yasa Baccin
idon ya washe.
"Meke damunki?
"Menstrual cramp, ke damuna Ilham please... ki bani pain reliever please.
Cikin hanzari Ilham ta diro daga gado taja side drower ' ta ciro Paracetamol ta
bata, sannan ta nufi Kitchen ta d'auko ruwa ta kawo mata. Bayan ta sha
maganin ne ta tashi cikin dabara Ta sanya Pad (Always) a jikin ta sannan ta koma ta
kwanta , bacci yayi awon gaba Da ita.
Ilham Bathroom ta shiga tayo wanka tukunna ta fito ta shirya ' Sannan ta wuce
Kitchen don ta had'a Breakfast, Cikin Sauri ta had'a tea tazuba cikin Plask takawo
parlor ta ajiye, Su Umma da Abba suka shigo cikin Parlon Suka zauna sannan Ilham ta
gaishe su.
"Ina Fadwa??
Cewar Umma,
"Umma Tana daki batajin dad'i Menstrual cramp ke damunta.
"Subhanallah to tasha magani daiko?
Cewar Abba,
Kai Ilham ta d'aga mashi Alaman Eh sannan ta zuba masu Tea din Ta basu, Itama ta
cigaba da shan nata tea din. Bayan ta gama breakfast d'inta ne ta wuce d'aki domin
tayi shirin wucewa School, Tana shiga ta d'auki Handbag d'inta sannan ta juya ta
fito daga d'akin.
Ta na fitowa suka had'e da Yaya Farook, ta gaishe shi sannan ta juya Zata wuce
Yayi saurin dakatar da Ita da cewa.
"Ita Fadwa bazata je School d'in bane yau?
"Eh Batada Lafiya ne!
Ok Kawai ya ce mata sannan tayi tafiyar ta.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

@ *_I_* *_Honestly_* *_Dedicated_* *_this_* *_page_* *_to_* *_All_*


*_Members_* *_of_* *_PWF_* *_Group_* ' *_you_* *_Gurls_* *_are_* *_simply_*
*_Amazing_* *_in_* *_Anyway_*!!!

*13-14* pages 馃尮

Kukan ne Ya dami Ilham yasa tayi saurin Rufe Littafin ta,


"Haba don Allah Fadwa, Sai ka ce wata karamar Yarinya? And beside ke fa kika
jawa kanki.
Cewar Ilham,
Fadwa tashi tayi ta d'auki Hijab ta sanya sannan Ta bar D'akin da gudu, bata tsaya
ko ina ba sai a harabar Lambu. Numfashi taja nadan wani lokaci ' sannan ta share
hawayen fuskar ta Gami da cewa,
"Tabbas Taj baida hali mai kyau, to Amma aishima Yaya Farook d'in mugune '
Ta Ya zaayi yace yana sona? Kilama dai Banji dai kyau bane.
Juyawa tayi cikin sauri ' ta nufi d'akin Yaya Farook, Bud'ewa tayi gami dayin
Sallama. Akwance ta ganshi saman gadon shi yana kallon Fanka,
Tsoron tambayanshi taji ' yasa ta juyawa zata koma inda ta fito,
"Fadwa???
Ji tayi ya kira sunan ta ta wata irin sigarda bazata iya Fayyace wa ba ' Haka yasa
ta juyo ta fuskance shi, sannan ya Sauko daga gadon ' ya tako har inda take ya riko
hannun ta gami da murza gannun,
"Is Everything Alright?
Yayi tambayar ya na kallon cikin kwayar idonta, hakan yasa ta kasa Cewa komai ' sai
dai ta tsinci kanta da cewa,
"Yaya Farook ' dama hakuri nazo in baka.
Nan ya saki hannun nata tare da juya baya ' Yayi Murmushi sannan ya ce,
"No Fadwa idan har akan maganar Taj ne ' to bazan hakura ba.... Har sai
kince min....
sai kuma yayi Shuru ' bai k'arasa maganar ba.
"Yaya Me kakeso in fad'a? I promise you duk abinda ka ce inyi to zanyi shi '
Inhar zaka yafemun.
Da sauri ya juyo ya kalle ta,
"Fadwa ki ce kina sona!
馃槰 zaro ido tayi cike da mamaki , ganin haka yasa Yaya Farook ya d'aure fuskar.
"Meye kika wani zaro ido ' ko na fad'a abunda bazaki iya bane?
Sunkuyar da kai tayi gami da girgiza kai,
"Yaya Farook Ina sonka.... .
Ta fad'a Tare da rufe Fuska ' k'o k'arin Juyawa tayi zata fita Yayi saurin fizgota,
Har sai da tad'an tokare shi.
"ina zakije? Mun gama magana ne dazaki wuce?
Yayi maganar cikin Fad'a, Mamaki ne ya cika ta ganin yadda ya sauya cikin
k'ank'anin lokaci.
"Ba Dake nake magana ba?!!
Cikin tsawa Yayi maganar ' nan take idanuwan ta suka ciko da hawaye,
"Yaya Farook kayi Hakuri, nakasa....
bata k'arasa maganar ba ya dakatar da ita da cewa,
"Come on, yimin shiru ' yar wannan maganar ce zaki cemun kinji kunya? Dama
tuncen kina Sona...
D'ago kai tayi ta kalleshi ' Cike da mamaki, harta bud'e baki zatayi magana yayi
saurin taron Numfashin ta da cewa.
"Karki fad'amun wata maganar Banza Anan wajen, Kuma zan gayawa Umma tayi
maki Aure tunda Shi kikeso.
"Yaya Farook Hakuri don Allah...
Dariya taso ta kwace mashi yayi saurin Juya mata baya ' ya ce,
"Oya fita kibani waje!!!
Jiki a sanyaye ta bar d'akin, Kitchen ta nufa ta bud'e fridge ta d'auko ruwan
sanya tasha, sannan ta wuce dakin su. Tana shiga ta iske Har Ilham tayi wanka ta
shirYa,
"Hm Harkin shirya nikuwa ko Mai banshafa ba!
Cewar Fadwa,
"Ke kuwa kina mene?
Ajiyar Zuciya tayi ' sannan ta sami waje ta zauna,
"Hm Babu komai ' Ai tunda kika koreni d'azun Daga d'aki nawuce Lambur.
OK kawai Ilham ta ce , sannan ta wuce Parlor ' cikin sauri Fadwa ta sanya kaya
Cikin shigar Tamfa tukunna tayi makeup, itama ta fito parlor ta zauna tana Kallo.

*AROUND* *4:32PM*

Umma ta fito daga sashen ta zuwa Parlor, Cikin hanzari tazo ta sami su Fadwa da
Ilham a zaune.
"Ku tashi maza, Ku shiga kitchen don Abban ku yacemin jirgin su ya kusa
sauka.
Jin haka yasa Fadwa tayi zambur ta mik'e tsaye cikin Fara'a ta ce,
"Wayyoo Allah na Abbana Zai dawo ' Umma naji dad'in wannan Good news d'in.
Nan suka fara gardama ita da Ilham akan Abunda zasu dafa, Hayaniyan sune yasa Yaya
Farook fitowa Daga D'akin shi, Kai tsaye ya tunkaro inda suke hayaniyar ya tsaya
yana kallon su. Ilham ce ta fara ganin shi ' tayi saurin Tab'a Fadwa, Amma inaa...
ta riga tayi nisa.
"Haha Tunda har kikayi Shuru ' to da magana ta za'a amfani.....
Cewar Fadwa,
Ta narufe baki taji anyi gyaran murya ' Haka yasa tayi saurin juyawa domin Ganin
waye, Ido hudu sukayi Da Yaya Farook ' nan take cikin ta ya murd'a saboda tsoro,
"Surutun Ubanme kukeyi?
Ilham ce tayi k'arfin hali ta ce,
"A'a dama Abba ne Umma tace zaidawo yau, shine nida Fadwa Muke Magana Akai.
Harara Ya watsa masu ' dukkansu suka sunkuyar dakai, sannan ya ce.
"Allah Ya dawo dashi lafiya ' inji wani ya bud'e baki ya kai k'arata wajen
shi kuga yadda zanyi daku.
Ya na gama fad'in haka ya Koma d'akin shi. Bayan ya wuce ne Ilham ta ce,
"Hm Kadaiji dashi, Kinji Fadwa Mutafi Kitchen domin musan Abunyi.
Jan hannun ta tayi suka nufi kitchen suka fara preparing girke girken Abinci kala
Uku, Cikin *2hours* da y'an mintoci suka kammala komai, sannan suka jera a dinning
table cike da Fara'a. Yaya Farook fitowa yayi daga d'aki cikin hanzari ya wuce
masallaci , Acen yayi Magrib sannan Ya dawo. Fadwa tsayawa tayi a bakin kofa Tana
jirar isowar Abba ' bud'e k'ofa taji anyi hakan yasa tayi saurin jan handle din
gami da cewa,
"Oyoyo Abb....
kasa k'arasa maganar tayi ganin Cewar ba Abba bane ya dawo Yaya Farook ne ya shigo,
Cikin tsoro da sanyin jiki tace.
"I thought Abba ne ya dawo shiyasa....
Harara ya balla mata tare da jan tsaki ' sannan ya je wajen dinning table yayi
zaman shi, Itama komawa tayi ta zauna Ilham kuwa babu abinda takeyi inbanda dariya.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

*17-18* pages 馃尮

Bayan wucewar ta yayi sauri ya shiga cikin d'akin nasu, A kwance ya iske Fadwa
rungume da pillow ta na bacci ' zuwa yayi ya zauna a gefen ta setin fuskar ta, a
hankali yasa hannu ya shafa saman goshin ta tare da kissing d'inta a goshi.
Sannan ya tashi ya wuce parlor, a zaune ya sami Umma da Abba suna hira ' zuwa
yayi ya tsugunna ya gaishe su sannan ya koma ya zauna.
"Ka karya kuwa Farook?
Cewar Umma,
"A'a Umma ban karya ba tukunna.
Yaya Farook maida kallon shi yayi akan Abba ' sannan ya ce,
"Ammm... Abba dama nazo ne natuna maka ' maganar Neman Aikin.
"Kaga Farook na manta aigwara daka tunamin ' kaje d'akina zakaga Wani
envelop ka d'auko min.
Cikin hanzari ya tashi ya nufi d'akin Abba ' cikin minti Uku ya dawo d'auke da
Envelop d'in rik'e a hannun shi, Sannan ya mik'awa Abba cike da ladabi.
"A'a rik'e a wajenka domin nakane, Wannan itace takardar samun Aikin naka
Farook.
Murmushi yayi Har sai da hak'oran shi suka bayyana saboda jin dad'i ' cikin
fara'a ya ce,
"Thank you so much Abba, nagode sosai Abba ' Allah ya bani ikon kyautata
maku.
Ameen suka amsa a tare ' sannan Abba ya ce.
"A Company din Abokina ka sami aikin ' gobe Insha Allah zan kaika.
Cikin Farin ciki Ya tashi ya wuce d'akin shi ' nan ya dinga kiran Friends
d'inshi suna Congratulating d'inshi. ya na gama wayar ya d'auki key d'in motar shi
ya fita.

*Around* *10am*...

Fadwa ta farka daga bacci ' ta nufi bathroom tayi wanka sannan ta fito, Simple
makeup tayi ta sanya doguwar rigar atamfa ' tukunna ta nufi parlor ta taradda Umma
da Abba ta gaishe su sannan ta juya zata koma ciki Umma ta tsaida ita da cewa,
"Fadwa yaya jikin naki?
"Da sauk'i Umma.
"To Allah ya k'ara sauk'i,
Ameen ta ce sannan ta juya ta wuce.
kai tsaye ta nufi Lambu ta zauna tare d'aga kanta sama tana kallon yadda
Tsuntsaye keta safa da marwa a wajen, abun Yayi matuk'ar burge ta yasa ta tashi ta
k'arasa cen cikin Lambun tana kallon tsuntsaye kala dabam dabam.
Cikin ta ne ya fara mata k'ara sakamakon Karya wanda batayi ba, hakan yasa ta
tsinki Tuffa(Apple) a wajen ta ci saida taji ta koshi sannan ta cigaba da kallon
Cikin Lambun.
Yaya Farook dawo wa gida yayi ' Ya shigo parlor babu kowa sannan ya wuce cikin
gidan, d'akin su Fadwa ya fara lek'awa ganin bata cikine yasa ya tafi Lambun shima
kai tsaye, A zaune Ya hangi Fadwa ita kad'ai Fuskar ta cike da Fara'a, Ya k'arasa
wajen ' jitayi anrufe mata Ido.
"Waye please? Ilham kece ko?
Shuru yayi ya kyaleta ba tare da yace mata komai,
"Mtsw Dalla malama ki sakemun ido na.
sake mata ido yayi sannan ta juyo ta kalle shi, ganin shine yasa ta tsorata ta
mik'e tsaye gami sakin k'ara,
"Ahhghh, Yaya Farook kayi hakuri bansan kai bane.
D'aure fuska yayi ya matso daff da ita,
"Na sami Aiki Fadwa.
"Wow! Alhamdulillah Yaya Farook naji dad'i kuma na tayaka Murna.
Murmushi yayi Tare da tallabo fuskar ta da hannu biyu,
"Fadwa ai kece yadace azo a tayaki Murna ' Domin Wannan samun aikin tamkar
ke ce kika sameshi.
Haka ya fad'a ya na k'ok'arin Kissing d'inta,
"Yaya Farook what are you trying to do?
Tayi tambayar gabanta na dukan uku uku, tana k'ok'arin Kub'uce wa ya k'ara
matseta.
"Yaya Farook please ka daina mana ' banajin dad'in hakan....
Cikin sauri ya saketa Tare da juya mata baya yana maida numfashi, itama ta juya
tayi gami da dafe k'irjin ta hannunta na rawa ta ce,
"Yaya Farook Am sorry but i just can't.
"Yes bazaki iya ba ai ' saboda bakya sona Fadwa.
Da sauri ta juyo ta kalle shi idanuwan ta sun kad'a sunyi jaaa.
"Yaya Farook na dad'e da fara Son ka a cikin Zuciya ta , kad......
Bata kaiga k'arasa maganar ba Ya dakatar da ita da cewa,
"Inhar kina sona dagaske ' to kije ki fad'awa Su Umma domin suyi mana Aure,
Fadwa baxan iya jure rashinki a kusa dani ba.
mamaki ne ya rufe ta ' yasa ta je Gaban shi ta tsaya,
"Yaya Farook kada ka d'auramun nauyin da banice Ya dace insauke shi ba.
Tana gama fad'in haka ta juya zata wuce yayi sauri ya rike hannun,
"Fadwa bazan iya fad'a ma Umma da Abba ina sonki ba.
Saurin fizge hannun ta tayi cikin bacin rai sannan ta juya ta wuce.
D'akin su ta wuce direct ' tana shiga ta fada saman gado, wasu zafafan hawaye ke
zubo mata a fuskar ta,
"Wannan wace irin soyayya ce? Wannan wane irin azabtar wa ce? Dama haka
Soyayyar take?....
Cikin kuka ta k'arashe maganar, tashi zaune tayi ta share hawayenta sannan ta
wuce Kitchen ta daura girki.

*** *** *** *** ***

*AROUND* *1:56PM*

Fadwa ta gama girkin ta zuba cikin Plask ' sannan ta kawo parlor ta ajiye, ta wuce
sashen Umma ta fad'a mata cewa ta gama Abinci, koda ta dawo iske Yaya Farook tayi a
dinning table a zaune ' yana kallon ta cike da murmushi, Kawar da fuskar ta tayi
sannan ta k'arasa wajen cikin sauri ta Zuba mashi abinci, fuskarta babu annuri a
cikin ta. Bayan tayi sarving d'inshi ne ta koma ta zauna Suna kallon kallo,
"Bazaki zuba abincin bane?
Shuru tayi ta kyaleshi sannan ta zuba ruwa a cup tasha,
"Fadwa am i not talking to you?
"Am not hungry!
Abunda ta ce kenan ' ta mike tsaye da niyyar barin wajen yayi saurin tsaida ita,
"Fadwa son da nake miki bashine zai hanani hukunta ki ba idan kikayi laifi.
Cikin fad'a yayi maganar hakan yasa ta jin tsoro ' gudun kar jikinta ya dimamu
ne yasa ta saki fuskarta tare da yin murmushi,
"Yaya Farook don Allah ka barni ' wallahi banajin Yunwa.
"Fadwa ban yarda ba ki dawo ki zauna,...
Yana gama fad'an haka Umma ta shigo parlon cikin hanzari Fadwa ta boye a bayan
ta,
"O'o lafiya?
"Umma, Yaya Farook ne wai dole sainaci abinci yanzu ' ni kuma banajin yunwa,
"Ha'a Farook banason zalunci, antaba yin abune dole ne wai?
sosa kai yayi Cikin fara'a Sannan ya ce,
"Umma ni ban mata dole ba ni kawai...
Tun kafin ya k'arasa Umma ta ce,
"Yi tafiyar ki kinji ki kyaleshi,
Saida tayi mashi gwalo sannan ta juya ta wuce.

*2:00pm*

Bayan sun gama cin abinci ' Umma ta dawo harabar parlor ta zauna' shi kuma Yaya
Farook ya d'auki key din motar shi ya fita, Ilham ce ta shigo cikin parlon a gajiye
' Ta gaida Umma sannan ta nufi d'akin su, ta na shiga ta Iske Fadwa a zaune ta na
duba handOut. Zuwa tayi ta jiye Handbag dinta sannan tace,
"Ke baiwar Allah ya jikin naki?
Ajiye handout din tayi a gefe ta d'ago kai ta kalle ta,
"naji sauki kad'an Ilham.
"To gwara da kika warke da wuri don gobe munada test din Anatomy.
Cewar Ilham,
"Tabb hmm Allah dai kawai ya taimake mu kawai.
Ameen Ilham ta ce sannan ta dauki towel ta daura ' ta fada bathroom donyin
wanka.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_P.W.F_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

@*JAMEESHA* *_wannan_* *_page_* *_d'in_* *_nakine_* *_i_* *_just_* *_feel_*


*_like_* *_dedicating_* *_this_* *_page_* *_to_* *_you_* *_because_* *_of_*
*_love_* *_and_* *_friendship_*

*19-20* pages 馃尮

Bayan wasu y'an lokuta k'alilan ne Umma ta ga kiran Yaya Khaleel ya shigo cikin
Wayarta, Murmushi tayi gami da girgiza kai tukunna ta d'auka,
"Sallamu Alaykum, "
"Hello Umma!? Umma yau zan dawo gida in sha Allah."
"Tor Khaleel Allah ubangiji ya tsare ' har jirgin naku ya tashi ne?"
"A'a Umma But yanzun nan zai tashi ' shiyasa nakira!"
Addua Umma tayi mashi sannan sukayi Sallama ta kashe wayar. Umma tashi tayi ta
wuce d'akin su Ilham ' koda ta shiga Fadwa ce kawai tagani,
"Fadwa Ina Ilham? "
Cewar Umma,
"Umma Ta shiga wanka ne,"
"To idan ta fito Kice mata ' kushiga kitchen ku shiryawa Khaleel Abinci, don
yau zai dawo."
馃槺 To kawai Fadwa tace sannan Umma ta juya ta koma parlor ' nan wajen ta tsaya
tana kokwanto akan Maganar Umma,
"Kai Kardai Yaya Khaleel dinda Ilham ta bani labari? Wayyo ' shikenan
mumbanu "
Cikin hanzari ta mike tsaye ' Ba tare da tasan abinda zatayi ba , kai da komowa
kawai takeyi ' tana cikin hakan ne Ilham ta fito daga bathroom dauke da karamin
towel a hannun ta tana goge gashin kanta, ganin yadda Fadwa keta yawo a dakin ne
yasa ta tsaya cak ta na kallon ta.
"I hope ba wani laifin kika kara Daukowa kanki ba?"
Cewar Ilham,
Tsayawa tayi ta kalleta with sad face ' sannan tace,
"Kin fito kina wani Goge gashi ' verysoon zaki manta da wannan ai!!"
"Me kike nufi?"
"Eh Umma tace Mu shiga kitchen Mu shiryawa Yaya Khaleel abinci ' don ya kusa
dawo wa,
"What!!?"
Cikin tsawa da muryar tsoro tayi magana ' Hakan yasa ta samu waje ta zauna a
sanyaye tare da cewa,
"Shikenan, ya dawo Lafiya ' basai na shiga harkar shiba sannan zansha
wuya?"
Shuru sukayi nadan lokaci sannan Ilham ta ce,
"Please Fadwa kije kifara Kafin Ingama shiryawa ' koma mene ne sai indaura
daga baya."
Ok kawai Ta ce mata sannan ta fita daga Dakin Zuwa kitchen.

*Around* *3:00pm*
Bayan Fadwa da Ilham sun kammala Komai sun jera a dinning table ne ' Abba ya dawo
Gida,
"Anata preparation din dawo war Khaleel ne?"
Yayi magana cikin sauri ya na k'ok'arin wuce wa sashen shi, Ilham ta d'ago kai ta
kalle shi cikin sanyin jiki.
"Eh Abba wai haka aka ce."
Komawa sukayi suka zauna a harabar Parlor suna kallon, Yaya Farook ya shigo d'auke
da leda Guda biyu a hannun shi ' Wurgama ko wannen su yayi Fuska a daure ya sami
waje ya zauna.
Cikin sauri Fadwa ta bude ledarta da kwalin waya ta fara hada ido ' xambur ta
mike tsaye cike da murna,
"Wayyoo Yaya Farook..."
Juyowa tayi ta kalleshi cike da Fara'a, ganin ya daure fuska ne yasa Ta koma a
zaune jiki a sanyaye. Itama Ilham bude nata tayi taga wayace ' sannan tayi mashi
godiya, kai kawai ya daga Mata alaman Yaji ' sannan yace,
"Yau Khaleel zai dawo Hope ' kun kammala komai."
A tare suka amsa da cewa Eh, Sannan kowannen su ya mik'e tsaye d'auke da wayarshi a
hannu suka wuce d'aki. Shima Yaya Farook tashi yayi ya wuce d'akin shi, yana shiga
ya ciro wayar shi ' yayi dailing wata new Number.
Fadwa na zaune bayan sun kunna wayan ' cikin jin dadi Itada Ilham sai taga kira
ya shigo Wayar,
"Kai!! Ilham harda Sim a ciki."
Abunda ta ce kenan ' tayi saurin yin recieving call din, Sai jitayi ance.
"It's Me Farook, kizo d'akina Yanzun nan."
Yana gama fad'in haka ya kashe wayar, kallon Ilham tayi Cike da mamaki.
"Wane ne?"
Cewar Ilham,
Smilling tayi mata ba tare da tace mata komai ba ' ta tashi ta bar d'akin, kai
tsaye ta wuce dak'in Yaya Farook ' saida tayi knocking sannan ta shiga tare dayin
Sallama,
"Yaya Farook gani!
Juyowa yayi ya kalleta ' sannan ya jawo hannun ta ya zaunar da ita a saman gadon
shi,
"I hope kinji dad'in Gift d'inda na baki?"
Ya fad'a yana k'ok'arin zaunawa kusa daita,
"Eh Yaya Farook na gani ' kuma na gode sosai"
"Fadwa you completely changed my life ' koda nayi niyyar yin wani abun
saboda Soyayyar ki sai inji nakasa, because i love you so much."
Yana gama fad'in haka yayi kissing d'inta a goshi,
"Tashi ki wuce d'aki, bazan iya jore ganin ki a nan wajen ba ' komai zai iya
Faruwa Fadwa!!"
Cikin Sanyin Murya yayi Maganar ' hakan yasa taji wani Yarrrrr a jikinta, da sauri
ta mik'e sannan ta bar d'akin cikin hanzari. parlor ta wuce kai tsaye ' Suka had'e
da Umma zataje kitchen,
"Lafiya Fadwa? Naganki kamar Wacce aka biyo ne?"
Had'd'iye miyau tayi daker, tare da zurowa Umma idanu tana tunanin k'aryar da
zatayi mata.
"Fad'amin mana, Don Fuskarki ta kasa boye tsoron da take d'auke dashi, "
"Amm...well Umma babu komai ' and please don't worry about me, tsaka
nagani a kitchen shiyasa naji tsoro."
"To shikenan Allah ya kyauta."
Ameen Ta ce sannan ta k'arasa Parlor ta zauna ' zamanta keda wuya taji ana Knocking
K'ofa, tashi tayi taje ta bud'e. Cikin izza ya shigo Cikin parlon ' Fadwa baki ta
saki ganin yadda ya shigo kai tsaye,
"Malam lafiya? Kuma wa kake nema? "
Juyowa yayi ya kallet ta cikin b'acin rai da jin haushin tambayar da tayi mashi,
yasa ya dawo daff da ita ya tsaya tare da k'are mata kallo.
"Ke? .."
Kasa k'arasawa yayi saboda haushi, sannan ya juya zai k'arasa cikin gidan tayi
sauri ta rike mashi riga.
"Malam magana nakeyi ai...."
Ji kake Tasss ' tun kafin ta gama rufe baki ya sharara mata mari,
"ke!! Wace ce dazaki yimun irin wad'an nan tambayoyin, Koda yake dama haka
y'an aiki suke ' To nine Khaleel kuma idan kika cigaba da Yimun tambayoyi dukan
banza zakisha."
Zukunna wa Fadwa tayi rik'e da fuskarta hawaye na gangaro mata ' Lallai ta
tausayawa kanta jin Yadda sukayi Arba da Yaya Khaleel for the first time, Haka nan
Ta share hawayen ta tare da mik'ewa tsaye.
"kayi hak'uri Bansan kaine Yaya Khaleel ba...
Tsaki ya ja gami da zama a saman kujera,
"Naji kije ki kiramun mutanen gidan."
Juyawa tayi ta nufi d'akin su ta iske Ilham a zaune, Ilham d'ago kai tayi ta kalle
Ganin fuskarta babu annuri ne yasa tayi saurin mik'ewa tsaye,
"Fadwa? Ya dawo ko?"
"Hmm ya dawo mana ' tunda harya watsamin mari"
Zaro ido tayi sannan ta fita d'akin cikin sauri ta nufi kitchen ta fad'awa Umma,
sannan ta zarce d'aikin Yaya Farook shima ta sanar dashi ' ita dai Fadwa zama tayi
a bakin gado ' cike da jimamin marin da tasha.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

*21-22* pages 馃尮

Umma kai tsaye ta baro kitchen Ta nufi parlor Ilham da Yaya Farook suna biye da
ita ' Suna Isa cikin Parlon suka iske Yaya Khaleel a zaune ya d'aura k'afa d'aya
kan d'aya yana kallon TV, Jin Sallamar su ne yasa yayi saurin Juyowa ya kallesu
tare da mik'ewa tsaye cike da Farin ciki, Cikin sauri ya rungume Yaya Farook Cike
da jin dad'i,
"Yaya! Nayi kewar ku sosai wallahi"
Cewar Yaya Khaleel,
Murmushi yayi sannan suka sami waje suka zauna ' Yaya Farook yace,
"Khaleel kenan ai muma haka ' and Yanzu ai Kewa ya k'are tunda gaka a gida,"
"Hakane Yaya!"
Umma ce ta katse masu ' magana da cewa,
"O'!! Hanta da jini kenan, To ai saiku tashi Aje aci abinci ' don nasan
Khaleel da yunwa ka shigo."
Dukkan su Dariya sukayi sannan suka mik'e tsaye da niyyar Zuwa dinning table Yaya
Khaleel yaja kunnen Ilham gami da cewa,
"Ke haryanzu rashin kunyar ki tana nan ko? Bakisan kimun sannu da dawo wa ba
ko?"
Saida ya bari Umma tafarayin gaba tukunnan ya zungure ta ' har saida ta fad'a
saman kujera tukunna ya k'ara gaba. Cikin hanxari ta tashi kamar zatayi kuka sannan
ta nufi dinning d'in.
Bayan zauna wansu ne Ilham tayi Sarving d'insu , ta zubawa kowa sannan ta zuba
nata ' saida suka fara ci sannan Umma ta lura Fadwa bata wajen,
"Ilham me Fadwa takeyi ne ' da bazata zo taci abinci ba? "
"Bara inkira ta Umma."
Abin da Ilham ta ce kenan ta tashi ta bar wajen domin kiran Fadwa ' Yaya Khaleel
kuwa Mamaki ne ya cika shi,
"Fadwa kuma? To bakuwa mukayi a gidan?"
Abinda ya ce kenan A zuciyar sannan ya cigaba da cin abincin.
"Kaii!!.. Umma abincin nan yayi dad'i wallahi Kodon na dad'e banci abincin
ki bane? "
Cewar Yaya Khaleel,
Murmushi Umma tayi ' Cike da fara'a ta ce,
"Uhmm.. Khaleel kenan aibani nayi wannan abincin ba dakake ta zuba santi. "
"To Umma wane yayi? Kardai kice Ilham ce tayi abincin nan."
Tambayar ne ta bawa Yaya Farook dariya,
"To mai ka maida Ilham ' ina gidan nan ace bata iya abinci ba? Aiko da taci
najaki."
Cewar Yaya Farook,
"Ai Ilham da Fadwa sune sukayi maka wannan girkin."
Tana gama rufe baki Fadwa da Ilham suka k'araso parlon ' cikin sauri bayan sun
zauna ne Yaya Khaleel ya d'ago kai ya kalleta,
"Umma wannan ce Fadwa d'in? Ita kuma wacece? Na d'auka y'ar aiki ce ai."
Yayi maganar ya na kallon Umma, Nan Umma ta bashi labarin duk abinda ya faru ' da
yadda akai ta dawo gidan da zama. Nan take tausayin ta ya kamashi ' cike dayin dana
sanin Marin ta da yayi mata, Fuskewa yayi 馃槑 sannan yace.
"welcome to our house Fadwa,"
"Yaya Khaleel aini ba bak'uwa bace kai zan cewa haka ai,"
b'ata rai yayi ya maida kallon shi ga abinci, Shi kuwa Yaya Farook Ita kawai ya
ke kallo cike da shauk'i, Umma ta na gamawa ta tashi ta wuce sashen ta ' ganin haka
yasa Yaya Farook mik'ewa da niyar Wuce wa d'aki tare da cewa,
"Dare yayi 8:00 yanzu ' idan kin gama kizo ki gyaramun gado na, don inaso
inyi bacci ne. "
D'ago kai tayi ta kalle shi suka had'a ido tasan cewa da ita yakeyi, Sannan ya
juya ya wuce. Ilham cikin hanzari ta kammala cin abincin ta tashi da niyyar tafiya
' Fadwa tayi sauri ta rik'eta,
"Please Ilham ki tsaya kid'an jirani na kusa gamawa.
Yaya Khaleel d'ago kai yayi ya kalli Fadwa, "
"A'a tunda kina zaune da aljani ai dole kice ta tsaya ta jira. "
Maida kallon shi yayi akan Ilham wacce duk ta gama tsorata ' cikin tsawa Yace,
"Come on ke kuma ki wuce kije ki kwanta ' tun kafin inb'ata maki rai a
wajen nan. "
Da gudu ta k'arasa d'akin, Fadwa kuwa kasa cin Abincin tayi ta tsaya tana kallon
plate d'in.
"Look! Idan kin k'oshi ne to ki tashi ki kwashe plates d'in don nagaji da
ganin ki. "
Cikin sauri ta tashi ta hau hahhad'a plates d'in wajen, tana cikin haka ne ta
ture Cup da ruwa aciki ' sam batasan ma tayi ba, haka ruwan nan yadinga malalewa
har ya sauka a jikin Yaya Khaleel ' shigar ruwa yaji a jikin sa yasa yayi sauri
mik'ewa tsaye,
"Kutma!! "
Jin haka yasa ta juyo ta kalle shi a razane,
"Fadwa jik'ani kikayi? Lallai jikin ki zai gaya maki."
"Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri ' bada sani na nayi haka ba."
Matsowa yayi kusa da ita ya d'aga hannu zai sharara mata mari kenan Abba ya
dakatar dashi da cewa,
"Karka kuskura , Koda wasa kada kasake ka mareta ' Au ashe muguntar taka
tana nan ko? "
Abba ya fad'i haka yana k'arasowa wajen, Yaya Khaleel sauke hannun shi yayi Sannan
ya watsa mata harara ' tare da cewa ,
"zamu had'u ai. "
Bayan Abba ya sami waje ya zauna ne ' yace,
"Me kika masa? "
"Abba Ruwane ya zuba a jikin shi by mistake ' shine yace... "
Bata k'arasa ba ta sunkuyar da kai,
"Kyaleshi ' karki damu dashi, Yanzu dai zo ki zubamun abinci na ' don yau na
wuni ina aiki. "
To kawai ta ce sannan ta zuba abincin a plate ta aje mashi ' Tukunna tayi mashi
sallama don bacci takeji, har ta kama Hanya zata wuce Yaya Khaleel ya ce.
"Ki biyoni da trolley d'ina d'akina"
Babu musu taja trolley d'in nashi tabishi dashi ' tafiya yake ta na binshi
abaya, ganin sun wuce d'akin Yaya Farook ne yasata mamaki.
"Mun bani, i thought d'akin Yaya Farook zai kwana ' innalillahi kenan yanada
d'aki dabam wanda bamu gyara shi ba. "
Haka ta fad'a a zuciyarta jikin duk yayi sanyi, suna isa bakin k'ofar Yaya
Khaleel yasa hannu ya bud'e d'akin ya shiga kai tsaye sannan itama tashiga, tsayawa
yayi yana k'arewa d'akin kallo ranshi abace ' ganin haka tasan cewa lallai yau
zasuci ubansu hakan yasa ta fara zubda hawaye tunkafin ya yanke hukunci.
"Yanzu haka ake gyaran d'aki agarinku??"
shuru tayi ba tare da ta ce komai ba ' jin haka yasa shi juyowa a fusace,
"Fadwa ba dake nak....."
Kasa k'arasa maganar yayi ganin yadda hawaye kebin fuskarta, cikin hanzari ya matsa
kusa da ita tare da cewa.
"Fadwa are you Okey?"
"Yaya Khaleel don Allah kada kabigemu ' wallahi aikine yayi yawa shiyasa
muka manta da gyara d'akin, kuma ni nad'auka tare da Yaya Farook zaka rik'a
kwana....."
Tana gama rufe baki yayi saurin rungume ta ' tare da shafa bayanta,
"is Okay! Fadwa ki daina wannan kukan ' tunda banyi bugunba tukunna. "
Yadda take ta mutsu mutsune ' ya gane cewa batason Hugging d'inne, Raba jikin
shi yayi da nata gami da cewa,
"Yanzu dai kije ki d'auko min bed sheet, sai kizo ki samun a gadon
inkwanta kafin gobe sai ku gyara."
Ok ta ce sannan ta juya ta fice cikin hanzari ' bata wani b'ata lokaci ba ta
dawo d'auke da bed sheet a hannun ta ' ta mik'a mashi ya karb'a gami dayin kissing
d'inta a goshi hakan yasa ta zaro ido,
"is a normal thing ' so don't fall in love with me, don nasan halinku Y'an
nigeria ' saboda haka zaki iya tafiya."
Yana fad'in haka ta kama hanya ta wuce d'aki ta kwanta, Kwanciyar ta keda wuya
ta tuna maganar Yaya Farook ' da sauri ta tashi zaune, Ilham dake kwance ta na
chatting ne tace.
"Lafiya kuwa ?"
"Lafiya kalau kitchen zanje don k'ishi nakeji."
Ok kawai Ilham ta ce sannan Fadwa Ta tashi ta nufi d'akin Yaya Farook, Handle
d'in ta murd'a taji a k'ofar a bud'e yasa ta shige cikin sauri. Akwance ta hangi
Yaya Farook hakan yasa ta kiran sunan shi,
"Yaya Farook"
Jin yayi shuru ne yasa ta k'arasa cikin d'akin tare da cewa,
"To ko yayi bacci ne?"
Hayewa tayi har tsakiyar gadon shi ' sannan ta sunkuya tana kallon fuskar shi, bata
ankara ba taji ya jawo ta jikin shi, lips dinta daff da nashi ' haka yasa ya matse
ta sosai yadda bazata iya Kuccewa ba ' nan fa ido Ya raina fata,
"Yaya Farook na d'auka ko kayi bacci ne shiyasa."
Ta fad'a tana k'ok'arin janye jikinta,
"Yau anan nakeso ki kwanta ' Inaso ki d'ebemun kewa Fadwa,"
"Yaya Farook please ka bari intafi ' kasan banason irin wad'an nan
abubuwan."
Ta fad'a tare da yi mashi magiya,
"Ke ! Am serious fa ' Karma ki bari raina yab'aci."
Ya fad'i haka cike da d'aure fuskar.
Murmushi tayi mashi tare da kashe mashi ido d'aya (wink), Sannan ta sa hannu a
k'irjin shi ta fara yinmashi waiwayi a Wajen, Nan take ya farajin launin jikin shi
yafara sauyawa ' cikin wata murya yace,
"Fadwa stop it ' kidaina yimin wannan abun please,"
"A'a"
Ta fad'a saida ra bari ya sakan kance sannan tayi wufff ta sauko daga gadon ' cikin
Sauri har tana had'awa da gudu tabar d'akin, Yaya Farook Sai ninshi yakeyi yana
mutsu mutsu.
D'akin su tashige a guje ' har saida Ilham ta razana,
"ke kuwa ina kika shiga? Don na je kitchen ban ganki ba,"
Fadwa kwanciya tayi gami da jan blanket ' sannan tace,
"Well, Ilham lambu naje."
"lambu da daddaren nan Fadwa?"
"yes ' fruit naje nasha, A tsorace na dawo shiyasa Ma kika ganni a haka."
"ke kika sani dai."
Abunda tace kenan ta maida kanta akan waya ' nan bacci yayi awon gaba dasu.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

*23-24* pages 馃尮

*Washe* *gari*....
Da sassafe around 6:22Am ' Fadwa da Ilham suka tashi sukayi Sallah, Bayan sun
idar da sallah ne Ilham tayi wuff ta tashi tana k'ok'arin d'aura towel a jikin ta,
"Ilham kada kiyi wanka yanzu ' saboda gyaran d'aki yana jiran mu."
Cewar Fadwa,
Ilham tsayawa tayi tana kallon Fadwa d'auke da alaman tambaya a fuskar ta,
"Gyaran d'akin ina kuma? "
"Gyaran d'akin Yaya Khaleel kuwa, domin kuwa ya ce yau da safe zamu gyara
shi ' Ai auna arzik'i mukayi jiya don wallahi da jikinmu ya gaya mana."
Tsaki Ilham taja ' tare da jan kwafa,
"To wallahi ' babu wani gyaran d'akin da zamu tsayayi, don kuwa test
garemu yau ' shi ya gama nashi karatun mu zaizo ya takura mAna, "
"Tab!! To aini mantawa nayi banyi mashi bayani ba tun jiya d'in."
Ya tsine baki Ilham tayi gami da buga cinyar ta,
"ke kika sani, wallahi ki zauna nan harkisami Carryover ' shine na farko
wanda zai jibge ki, "
Fadwa mik'ewa tayi tsaye tare da yaye hijab d'in jikin ta,
"To yanzu yaza'ayi kenan mu fita ba tare da kowa ya sani ba? "
"Yanzu dai kibari inshiga wanka ' infito saike ma ki shirya. "
Ilham harta juya zata shige bathroom Fadwa tayi saurin dakatar da ita da cewa,
"Ilham Amma kinsan dai bazamu fita ba tare da ' mun shirya musu breakfast
ba ko?"
"Fadwa wai wane breakfast kuma? Bayan kinsan muddin muka tsaya tofa '
gyaran d'akin nan tamkar mun gama yin shine, kawai mubar musu Umma idan ta tashi
saita had'a kokuma d'aya daga cikin su."
Ta na gama fad'in haka ta shige bathroom ba tare da ta jira abunda Fadwa zata ce
ba. A bakin gado ta zauna Tayi jugum ' babu abinda take tunowa sai irin marin da
Tasha wajen Yaya Khaleel.
"Anya kuwa Ilham zan iya bin shawarar ki kuwa?
Haka ta fad'a idanuwan ta cike da tsoro. "

*Some* *Minutes* *Later*

Bayan Ilham ta fito daga bathroom ne Fadwa ta shige cikin sauri ' Tukunna Ilham ta
fara Shiryawa.
Yaya Farook saukowa yayi daga gado ' gami dayin mik'a sannan Ya fad'a bathroom
cikin Sauri yayi wanka tare da yin Alwala, sannan ya fito yayi sallah. Bayan ya
idar ne yaji cikin shi tamkar anyi mashi yasa aciki, Hakan yasa yayi saurin mik'ewa
tsaye.
"Ashhh wace irin yunwa ce da sanyin safiya haka? "
Fita d'akin yayi cikin sauri, ya nufi kichen ' lipton ya fara nema baigani ba,
ganin haka yasa Ya nufi d'akin su Ilham cikin sauri,
"Ke zo ki had'amun Tea insha yanzun nan Yunwa nakeji, "
Jitayi maganar ta daki zuciyar ta ' kallon shi ta juyo tayi, cikin k'unk'uni
tace.
"To, "
Yaya Farook juyawa yayi ya koma d'aki ya cigaba da shiryawa, Ilham bayan ta kammala
shirin tane ' ta je ta tsaya bakin Kofar bathroom,
"Fadwa dalla kiyi sauri, inba haka ba wallahi Tafiyata zanyi ' kinga har
Yaya Farook ya sani aiki ko? "
Cewar Ilham,
"Ke naji ' yanzun zan fito dalla, "
Tsaki taja sannan ta wuce kitchen ' cikin d'an k'ank'anin lokaci ta had'a mashi
ta kai mashi d'aki,
"Yaya Farook ga tea d'in nan, "
Nuni yayi mata da yatsa ' alaman ta aje saman side drower, Bayan ta ajene Ta juya
ta wuce ' tana komawa d'aki ta iske Fadwa a zaune ta na Shafa mai,
"Wai ke Fadwa kanki d'aya kuwa? amma kinsan dai sauri mukeyi ko?"
Cikin hanzari ta tashi tasa kayanta sannan Tasha powder sama sama ' tukunna ta
d'auki gelen ta yafa a kirji,
"Tow Am done. "
Ta fad'a rik'eda k'ugu ' sannan Ilham ta d'auki gelen ta itama ta yafa, suka fito
parlor cikin sand'o har suka fita cikin garage ' Fadwa ce ta kwankwasa wa driver
kofa,
"Ka fito mun shirya!
Cewar Fadwa, "
Ba tare da wani b'ata lokaci ba driver ya fito, ya bud'e motar sannan suka shiga
' tukunna yayi hone mai gadi ya bud'e gate d'in suka fice.
Bayan wuce warsu ne ' Yaya Farook ya fito rik'e da key d'in shi a hannu ya
wuce Office,. Yana fita Umma ta fito daga sashen ta ita da Abba ' kallon dinning
table tayi taga babu komai,
"ha'a inasu Fadwa ne? Ya haryanzu basu Had'a breakfast ba?"
Abba zama yayi a kujerar harabar parlor,
"Kila basu gama bane da wuri, "
Cewar Abba,
Umma d'akinsu ta nufa ganin basa cikine yasa ta wuce kitchen domin duba, nan ma
haka ' cikin hanzari ta Koma parlor,
"Wallahi basa gidan, kardai sun tafi School ne yaran nan."
"Kinga bara kawai in wuce wajen aiki ' zan karya acen, tunda kikaga haka
to sunda uzri ne a gabansu."
Yana gama fad'in haka ya tashi ya fita, Haka yai daidai da shigowar Yaya Khaleel
parlor , a tsaye ya iske Umma tayi folding hannayen ta ' sannan ya zukunna cike da
ladabi,
"Umma ina kwana! "
"Lafiya k'alau Khaleel ya gajiyan jiya? "
"Lafiya lau Umma ' Umma lafiya na ganki haka?
Yayi tambayar tare da mik'ewa tsaye,
"Hm Khaleel al'amarin yaran nan ne yabani mamaki, School suka wuce ba
tareda sun had'a breakfast ba."
Cikin yanayi na mamaki yace, "what!! Lallai ransu zai b'aci yau, nasan wannan
iskanci Wannan yarinyar ce Fadwa jikinta zai gaya mata. "
Umma zatayi magana yai saurin taren numfashin ta da cewa, "Umma karki damu nima
gwani ne a kitchen ' da lafiyata da komai bazaki shiga kitchen ba ina kallo. "
Murmushi yayi mata sannan ya juya ya nufi kitchen ' indomie ya dafa cikin d'an
k'ank'anin lokaci sannan ya kawo Ya aje a dinning table.
Umma na zaune a harabar parlor ' tana kallon kai da komo wanshi, saida ya gama
jera komai sannan ya dawo ya zukunna inda take zaune.
"Umma ga abun karya war nan na kammala, "
To Umma ta ce sannan ta tashi ta nufi dinning table ta zauna ' cikin hanzari
yayi sarving d'inta sannan shima ya zuba,
"Amm Umma Yaya ya tashi kuwa?"
"Gaskiya banji motsin shiba Khaleel,"
Tashi yayi ya nufi d'akin Yaya Farook, ya murd'a kofar yaji a kulle sannan ya
juya ya koma parlor.
"Farook d'in na nan kuwa?"
Cewar Umma,
"a'a Umma k'ofar shi a kulle. "
"Ohh Hakane yaune zai fara shiga Office,"
OK kawai yace sannan ya maida kallon shi a kan plate d'in indomie d'inshi ya
cigaba da ci.

*** *** *** *** ***

*Around* *11:30am*

Su Fadwa sun fito daga exam hall ' rik'e da handbag d'insu a hannu.
"Yanzu inda munsan zamu gama da wuri ' aida mun sanarwa Driver, "
Cewar Fadwa,
"ai bari kawai in kirashi ' don naga inada Number d'inshi. "
Ilham ciro wayarta tayi daga handbag d'inta tayi dailling number d'in Driver,
"Hello, kazo ka d'auke mu daga school ' don munyi closing. "
To kawai driver ya ce ' sannan ta kashe wayar, cikin hanzari driver yaje ya d'auko
su daga school ' ya kawosu gida haka yayi daidai da fitowar Yaya Khaleel cikin
Garage domin shan iska. Bayan su Ilham sun fito daga motor ne suna k'ok'arin
shigewa gida, Yaya Khaleel ya dakatar dasu da cewa.
"Where did you think you're going to????"
Yayi maganar cikin yanayi na fad'a , a tsorace suka tsaya tare da juyowa suka
kalleshi.
"Yaya Khaleel ciki zamu shiga,"
Cewar Fadwa.
"ciki ko? To kushiga!! Aike dama daga ganin kwayar idonki to baza kiyi
kunya ba!!!. "
Fadwa kallon Ilham tayi suka had'a ido sannan ta sunkuyar da kanta k'asa,
"Ubanwa kuka mayar y'an iska??? Umma? Kokuwa Abba?? Ko kuma nida Yaya
Farook?"
"Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri ' zanyi maka bayani,"
Cewar Fadwa.
"Zakimin shuru ko sai nazo na tattaka ki? To bari kuji infad'a maku, da
zarar kun shiga ciki kun aje wannan kima kiman handbags d'in naku ku zarce d'akina
ku jirani. "
Tsoro duk ya gama cika Ilham idanuwan ta kuwa ' gabb suke da zubar da hawaye,
d'ago kai tayi ta kalleshi gami dayin fuskar tausayi.
"Yaya Khaleeel please....
Bata kaiga k'arasawa ba ya daka musu tsawa,
"zaku b'ace mun da gani kokuwa?"
Da gudu suka shige cikin gida ' cike da tsoro.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

@ *_I_* *_proudly_* *_dedicated_* *_this_* *_page_* *_to_* *Jameesha* & *Husna*


*_Good_* *_Friends_* *_Are_* *_Hard_* *_to_* *_Find_* *_Difficult_* *_to_*
*_Leave_* *_Impossible_* *_to_* *_Forget_* *_Nikam_* *_babu_* *_abinda_* *_zance_*
*_sai_* *_godiya_*...*_dana_* *_sameku_* *_a_* *_matsayin_* *_Friends_*

*25-26* *pages*馃尮

Suna shiga cikin parlor suka iske Umma a zaune tana kallo ' basu san lokacin da
suka tsugunna a k'asanta idanuwan su ciccike da hawaye,
" Umma don Allah kicewa Yaya Khaleel karya dake mu!
Cewar Ilham,"
Umma rage k'arar TV d'in tayi da remote sannan ta kalli Ilham,
"Ai bansan bakida Kunya ba sai yanzu Ilham ' inbanda kun raina mutane
kwatafi ba tare da kun had'a mana abin karya waba? "
Sunkuyar da kai Ilham tayi Hawaye kawai ke zubo mata,
"Umma don Allah kiyi mana Hakuri ' wallahi Uzri mukeda shiyasa amma insha
Allah haka bazai maimaita kanshi ba, "
Cewar Fadwa,
"Au kema zaki nunamin taki rashin kunyar kenan ko? Ai Fadwa koma wane
irin Uzri ne daku ' ai kamata yayi Wani cikin ku yazo yaimun bayani, bawai ku kad'a
kanku ku fita ba."
Umma na gama rufe baki Ilham taji saukar dundu a bayan ta, a kid'ime suka
waiga domin suga waye ' Haba ido hudu sukayi da Yaya Khaleel, haka yasa suka tashi
a guje tare da cillar da handbags d'insu zuwa d'akin shi.
Suna shiga d'akin shi suka zube a k'asa Cike da tsoro, Yaya Khaleel kwafa yayi
gami da girgiza kai sannan ya biso.
"To banda mugun duka dai ' don nasan halinka. "
Cewar Umma,
Kai tsaye ya zarce d'akin shi ba tare da yacewa Umma komai, Cikin zafin nama ya
bud'e k'ofar ganin su yayi a zukunne kowan nen su da hawaye sharkaf a fuskarshi,
fuskar nan tashi a d'aure ya nufi wardrope dinshi ya zaro belt ' da Fadwa ya fara
had'a ido sannan ya nufo kanta, ganin haka yasa tayi zambur ta mik'e tsaye.
"Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri ' Karka dakemu please...."
Cikin kuka ta k'arashe maganar ta cike da shash shek'a,
"Ohhh Kokowa xamuyi koh? Aike dama nasan babu abinda bazaki iya ba.... "
Jikake zafff zafff ' saukar belt a bayan ta, Da gudu ta nufi wajen gadon shi ta
rakub'e cikin kuka tace.
"wayyo!!! Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri please forgive us....."
Komawa kan Ilham yayi wacce ko ina najikin ta rawa yakeyi,
"Ke dan ubanki ' da hankalin ki da komai, zaki biyewa wancen tsageran?
saboda kin manta wanene Yaya Khaleel ko? To jikinki zai fad'a maki kuwa."
Sai da ya sauke mata belt shida a jikin sannan ' ya k'ara mata da hauri a
jikin ta, saboda tsabar kuka Ilham ko hawaye ya daina fita daga idonta.
"Tashi ki fita ki bani waje ' idan ba haka ba saina kakkarya ki a wajen
nan. "
Da gudu Ilham ta bar d'akin jin haka yasa Fadwa mik'ewa tsaye Cikin sauri zata
fita, ya cafko ta A gigice ta juyo ta kalle shi.
"ina kike tunanin zaki? Ba tareda jikin ki ya gaya maki ba? Mara kunya!!!"
Jin saukar belt tayi a k'afa funta ' yasa tayin tsalle cikin rad'ad'i ta
k'ank'ame shi jikinta sai rawa yakeyi,
"Ya..Yay. Yaya please kaimin afuwa ' wallahi zan iya mutuwa...."
Wani zirrr yaji tundaga k'afar shi har saman kanshi, shuru yayi nad'an lokaci
sannan ya finciko ta da karfin tsiya har saida ta fad'a k'asa, a hankali yake
takowa inda take ' ganin ya nufo ta da belt d'in ne hankalin ta ya k'ara tashi ,
"Yaya wallahi wannan ba plan d'ina bane Ilham ce tace muyi haka, please
karka kasheni.
Jin haka yasa shi tsayawa cak ' tare da wullar da belt d'in a saman gado,
"Tashi ki fice mun da gani ' gobe idan Ilham tace ki shiga wuta sai ki
shiga...."
Da sauri ta mik'e tsaye gami da had'awa da gudu ta fice daga d'akin, ba ta tsaya
ko ina ba sai a saman gadon su.
Saida ta gama dawo wa normal sannan ta lura da Ilham rik'e da bucket d'in ruwan
d'umi a hannunta tare da K'aramin towel tana gasa jikinta,
"Ilham?"
A gajiye Ilham ta juyo ta kalli Fadwa,
"Ya akayi?"
Fadwa tashi tayi ta zauna cikin jin zafin jikin ta,
"Meyasa Yaya Khaleel ya tsane ni?"
"Mtsww wannan wace irin banzar tambaya ce ' ni dalla ki kyaleni naji da
d'aya mana aida kinsani kin tambaye shi kafin ki fito.!"
Ya tsine baki tayi sannan ta tashi ta fada bathroom don yin wanka da ruwan
d'umi, ko da ta fito bata iske Ilham a d'akin ba nan ta d'aga kai ta kalli a goge,
"Ok! Lokacin girka lunch yayi 2:00pm Ilham na kitchen yanzu.
Bayan ta zauna agaban mirror ne ta fara gyara jikinta ' wayar ta tayi k'ara,
cikin hanzari ta d'auka ganin Yaya Farook ne yasata yin picking cikin sauri.
"Hello Yaya.."
"Baby na yakike? Hope kina lafiya?"
A wahale ta ce, "lafiya kalau Yaya"
"Meyasa meki naji kamar bakida lafiya Fadwa!"
Jitayi kamar ta fad'a mashi abinda ya faru sai kuma ta fasa,
"Well, Yaya Farook babu komai ' is just that nad'an sami bacci ne
d'azun. .
Ok yace tare da yinmata sallama sannan ya kashe wayar ' a tsanake ta tashi ta
sanya kaya ajikin ta doguwar riga atamfa, sannan ta fito ta nufi parlor ganin Yaya
Khaleel tayi a zaune ' nan take cikin ta murd'a ta juya xata koma ya dakatar da ita
da cewa,
"Kije ki gyaramun d'aki na yanzun nan kuma ke kad'ai.
To tace sannan ta juya ta nufi d'akin shi, bayan y'an lokuta k'alilan ne ta dawo
parlon ta zauna tare da cewa,
"Yaya Khaleel na gama.
ok ya ce ba tare da ya d'ago kai ya kalleta ba.

*Around* *2:30pm*

Ilham ta gama jera abinci da duk wani abun buk'ata a saman dinning table , sannan
ta haura sama ta yiwa Umma magana ' hakan yayi daidai da dawo war Abba daga wajen
aiki, Fadwa da Ilham da sauri suka tunkari Abba tare da yi mashi sannu ' sannan
Fadwa ta karb'a bag d'in hannun shi ta kai sashen shi, Yaya Khaleel ya tare Abba
cikin ladabi ya zukunna a gaban sannan ya ce,
"Abba sannu da dawo,"
Yawwa Abba ya fad'a sannan ya nufa dinning ya zauna, tukunna Umma ta fito cike
da fara'a a fuskarta ta zauna gami da yiwa Abba sannu da dawowa, Ilham ce ta tashi
donyin sarving d'insu Fadwa tayi saurin karb'ar Spoon d'in tare da cewa,
"Ai Abba nane so kibari na zuba mashi,"
Nan Ilham ta koma ta zauna gamida balla mata harara ' Abin haushi ya bawa Yaya
Khaleel yasa yaje ya zauna awajen ,
"Ke kiyi ki zuba min yunwa nikeji!"
Ya fad'a a gadaran ce ' Abba ya kalle shi,
"banson takurawa fa Khaleel ' hannu biyu gareta ba takwas ba.
Saida Fadwa ta zubawa kowa tukunna ta nemi waje ta zauna ta fara bawa ciki
abinci , saida kowa ya kammala sannan Ilham ta tashi ta tattara plates d'in wajen
ta wuce kitchen dasu.
Umma da Abba tashi sukayi suka tafi sashen su ' Yaya Khaleel kuma ya fita
harabar gida don shan iska, fitar shi keda wuya Yaya Farook ya dawo ' shigowa yayi
tare da yin sallama, Fadwa da ke a zaune ta amsa mashi cike da fara'a.
"Baby na ke kad'aice a parlon?"
Yayi tambayar a gajiye gamida zaunawa,
"Eh ni kad'aice Yaya, In zubo maka abincin ne?"
Juyowa yayi ya sakar mata wani kallo ' tare da yin murmushi,
"Yes, but ki zubomin ki kawomin d'akina."
To tace mashi sannan ta yunk'ura ta nufi kitchen kasan cewar Ilham ta tattara
komai ta kai kitchen, koda ta je kitchen babu kowa har Ilham ta gama ta wuce d'aki.
Cikin hanzari ta zuba abincin d'an daidai a plate tare da d'aukar roban ruwan
sanyi ta nufi d'akin Yaya Farook ta aje masa a saman side drower sannan ta juya
zata fita ya turo k'ofar, a tsora ce taja dabaya ta tsaya Yaya Farook ya k'araso
daff da ita gami dayin mata kiss tare da rungume ta.
"i missed you so fucking much Fadwa!!"
Nan take ta saki wani k'ara cikin sauri ya saketa gamu da tallabo fuskarta nan
yaga idonta yayi jaaa Alaman daf take dayin kuka,
"Babyna lafiya? Ko dai bakida lafiya ne?"
Yayi tambayar yana kallon Cikin idonta,
"Yaya Farook ' ka famamin inda aka dakeni ne d'azun!"
Nan ya waro manyan idon shi ' cike da mamaki,
"What!!! Waye ya dakeki??"
Ranshi abace yayi tambayar ' sunkuyar da kai kawai tayi hawaye na d'iga a
hankali......

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚鉁�
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*27-28* *pages*馃尮
Sake tambayar ta yayi cikin tsawa,
"Nace waye ya dake ki!!!?
Ranta abace ta d'ago kai ta kalleshi, "
"Waye zai dake ni idanba Yaya Khaleel ba!! "
Jin haka yasa jikin shi yin sanyi ' Cikin d'an k'ank'anin lokaci ya ce,
"hm Fadwa ai bakwajin magana ne ' ni nasan Bro ba zai dake ki haka nan ba,
sai idan kinyi laifi."
Tsayawa tayi tana kallon cikin kwayar idon shi cike da mamaki,
"I know that Yaya Khaleel d'an uwanka ne and ni ban fad'i haka da wata
manufa ba and beside kai ne ka nemi kasani. "
fuuuu ta juya zata fita yayi saurin rik'e mata hannu,
"I know that you're hurt Fadwa ' but ki kiyi hak'uri bazan iya cewa Khaleel
komai ba. "
"Is OK, na fahimta. "
Fizge hannun ta tayi ta fice daga d'akin , har ta nufi d'akin su sai kuma ta juya
ta nufi d'akin Yaya Khaleel ' kasan cewar tasan cewar baya d'akin yasa ta bud'e
Kofar a hankali gami da yin sand'o, ta na shiga ta tura ta rufe. Ciki ta k'arasa
cikin izza ' ta hango Album a saman gadon shi tare da diarry d'insa a gefe.
Cikin sauri ta hau saman gadon ' gami da d'aukan Album d'in ta d'ora a
cinyarta, ( *Ohh* *Ni* *Seemaluv* *kodai* *Fadwa* *ta* *mance* *d'akin* *da*
*shiga* *ne*?)
Budewa takeyi a hankali ta na kallon hotunan shi da abokanan shi mata da maza,
haka taita kallon hotuna daga wanda zai bata dariya sai wanda zai bata haushi ' a
haka har ta bud'o wani hoto, ganin hotun yasa gabanta fad'uwa.
"Dama Yaya Khaleel haka kake? Daman abunda kake tsina nawa a American
kenan? Wannan kuma wacece to!!. "
Hoton cikakkiyar mace ce kyakkyawa ' haihuwar Uwarta, wacce babu kaya ajikinta
ta na zauna. Cike da tsoro Fadwa ta rufe Album d'in tare da jan dogon tsaki,
"Mtsww wannan wace irin rayuwa ce? Yanzu shi kuma Yaya Khaleel me yakeyi
da wannan picture d'in?"
Ta fad'a cike da takaici ' sannan ta jefar da Album d'in a gefe ta d'auki Dairy
d'in. Bayan ta bud'e ne taga An rubuta, (Dear Diary...) A America ; ranar Litini ce
na tafka babban kuskuren da ban tab'a tunanin zan tabka shiba a rayuwa ba, haka
yasa duk idan na tuna dashi nakan zubda Hawaye.....
Fadwa bata kaiga k'arasawa ba taji an bud'o k'ofa bamm , da k'arfin tsiya
hakan yasa ta razana ta mik'e tsaye cikin rawar jiki rik'e da Dairy d'in a hannun
ta, Yaya Khaleel tsayawa yayi cak yana kallon ta cikin mamaki cen ya hangi Dairy
d'in shi rik'e a hannun ta hakan yasa shi k'arasowa wajen ta cikin zafin nama da
b'acin rai,
"Uban me kike min a d'aki? Ke wane irin stubbornness ke damun ki?"
Ya fad'a tare da kama kunnen ta,
"Ahhhggh Yaya Khaleel please am sorry ' zaka ciremun kunne!!!"
Ta fad'a Idonta cike da hawaye, Yaya Khaleel ya fizge diary d'in nashi gami da
cewa,
"Bincike kike yimin dama? Da kikayi binciken ubanme kika binciko fad'amin,
Iyee fad'amin nace!!!!"
Ya k'arashe maganar cikin tsawa, hakan yasa ta fashewa da kuka ' don kuwa tasan
idan har tayi wasa to kuwa wani dukan zata sake sha,
"Yaya Khaleel don Allah ka tsaya kaji ' wallahi Allah ba bincike nake yi
maka ba Yaya Farook ne ya ce inje in nemo masa biro, shine nazo nan ina
dubawa....."
Ta na gama rufe baki ya d'auke ta da mari tasss, a gigice ta dafe wajen tare da
sakin k'ara,
"Ahahhgg..."
"Ke!! Ni zakiyiwa k'arya da rainin hankali? Kaff d'akin ku babu mai Biro
sai kin shigo nan? Iyeee ba tambayar ki nakeyi ba??"
Kwata kwata kasa magana tayi saboda kukan da yaci k'arfin ta, girgiza kai kawai
takeyi Alaman a'a.
"In banda ke kin gama raina mutane ' Diary na a hannun ki sannan ki dubi
tsabar idona kice Biro kikazo nema, Kakkarya kine kawai yau bazanyi ba Fadwa."
Sakin ta yayi ya nufa Wardrope d'inshi ganin haka ya bata damar fallawa a guje
ta bar d'akin , kai tsaye ta wuce d'akin su cikin tsoro ta tura k'ofar ta rufe da
key. Ilham wacce keta waya tun d'azu ne ganin halinda Fadwa ke ciki yasa ta yanke
wayar ta cillar da ita saman gado, tayo kanta cikin hanzari.
"Lafiya Fadwa? Meyasa meki?"
Tayi tambayar tare da d'ago fuskarta, nan ta ga shedar hannu Alamun mari.
"Subhanallah meya sameki? Waya mareki! Halan Yaya Khaleel?"
Nin shi kawai Fadwa keyi sama sama ' saboda azabar da takeji a fuskar, Ilham
rik'e hannun Fadwa tayi sannan tajata zuwa gado.
"Fadwa idan akwai wanda ya dace ki fadawa damuwar ki to ni'ce, "
d'ago kanta tayi ta kalleta da rinan nun idanun ta,
"Ilham d'akin Yaya Khaleel na shiga ni karan kaina bansan meya kaini ba,
Bayan na shigane ya iske ni aciki shine yayi mun wannan mugun marin ' Ilham wai
meyasa Yaya Khaleel ya tsane nine? Meyasa kokad'an baya d'aukata amatsayin k'anwar
sa?"
D'an k'aramin tsaki Ilham taja sannan ta rungume Fadwa tare da bubbuga mata
bayanta ,
"Amma dai Fadwa kinsan ko wajen Abba za'aje kece bakida gaskiya ko? Kuma
tunda kinsan cewa ya tsaneki ai sai guji fad'awa tarkon shi, kuma sanin kankine
gidan nan babu mai nuna miki banbanci ' yadda akemun haka kema ake miki.."
Saurin share hawayen ta tayi tare da cewa,
"Nagode Ilham ' lallai kin cika y'ar uwa, "
Ilham tashi tayi ta wuce parlor, Fadwa kuwa a zuciyar ta tace .
"Naji duk abinda kika ce Ilham ' amma ni gaskiya koda zai kakkarya nine
kamar yadda yace, to fa saina binciko abinda Yaya Khaleel ke b'oyewa a diary
d'innan. "
Nan ta tashi ta fad'a bathroom ta wanke fuskarta sannan ta wuce parlor, suka
ci gaba da kallo.

*** *** *** ***

*Around* *4:30pm* ...

Su Fadwa na zaune a parlor suna kallo Umma ta shigo parlon ' bayan ta zauna ne ta
ce,
"Aikin ku kenan kallo ' to kun d'aura girkin yamma ko?"
Fadwa cike da fara'a ta juyo ta ce,
"A'a Umma ai d'azu tare muka had'a mukayi,
"yawwa aiko kun kyauta, yanzu ku tashi kuje ku kira Farook da Khaleel '
Abban ku keson magana daku gaba d'aya. "
To sukace a tare, sannan suka tashi suka tafi ' ba tare da wani b'ata lokaci ba
suka iso parlon, Umma na ganin sun iso ta tashi ta haura sashen su don kiran Abba.
Yaya Farook da Yaya Khaleel a k'asa suka zauna cike da ladabi, su kuwa su
Ilham suna saman Kujera don ita Fadwa ma harda hard'e k'afafu d'aya kan d'aya Yaya
Farook ya d'ago kai ya kallesu,
"Wane irin iskancin banza ne? Ba ankira mun nan don su Abba zasuyi magana
damu bane? Shine kuke zaune d'are d'are a saman kujera?"
Jin haka yasa Yaya Khaleel juyowa ya watsa masu wani irin kallo ' ai tuni suka
sulale k'asa cike da nutsuwa.

*Dedicated* *To* *My* * Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*29-30* *pages*馃尮

Suna cikin haka ne Umma da Abba suka shigo parlon ' cikin kamala suka sami waje
suka zauna daga bisani Abba yayi gyaran murya,
"Ba komai ne yasa nace ku hallara anan ba ' illa maganar da zanyi wacce
bata wuce uku zuwa hudu ba, wacce kuma ta k'unshi had'in kanku baki d'aya."
Abba gyara zama yayi sannan yace,
"Zan fara da kai Farook! Well Alhamdulillah yanzu ka sami aiki ' to me kuma
ya dace kayi yanzu?"
Sai Umma tace,
"Aure!!"
Yaya Farook yana jin haka ya d'ago kai ya kalli Fadwa, ya ga itama shi take kallo
cike da fara'a sannan Abba ya cigaba da cewa,
"nayi tunanin in had'a ku kai da Fadwa aure amma sai Umman ku ta ce had'in
baiyiba ina ma laifin a had'a Khaleel da Fadwa? Dana duba sai naga Eh shawarar da
ta kawo tayi, Amma nan da Two weeks kai Farook mukeso ka kawo mana wacce zaka
aura!."
Jin haka gaban Yaya Farook ya fad'a, ita kuwa Fadwa idanuwanta cike suke da
hawaye ' Yaya Khaleel kuwa ai abun ba'a magana don kuwa zuciyar shi tuk'uk'i kawai
takeyi.
"Ke kuma Ilham yanzu kina iya bawa samarin naki damar zuwa domin ku fahimci
juna ' amma mind you ba kowane zaki kawo cikin gidan nan ba!"
Bayan ya gama ne Umma ta ce,
"Ko kunada abun cewa game da wannan zabin?"
Yaya Farook gyara zama yayi tare da kai zuciyar shi nesa ya ce,
"Umma & Abba, bamuda abin cewa illa mu gode maku domin kuwa farin cikin ku
shine farin cikin mu ' bak'in cikin ku kuwa! Shine namu, saboda haka wannan zab'in
yayi."
Abinda Yaya Farook ya fad'a yayi matuk'ar tab'a zuciyar Fadwa, hakan yasa ta
farajin jiri na d'ibarta. Abba da Umma sunji dad'in kalaman Yaya Farook sosai ba
kad'an,
"Allah yayi maku albarka ' Allah kuma yasa naku y'ay'an suyi maku
biyayya,"
Ameen suka ce sannan Umma tayi musu umarni da su tashi su tafi, bayan sun tashi
Fadwa taji jiri na d'ibarta harta kaiga babu abinda take gani a gabanta face duhu '
hakan yasa ta yanke ji zata fad'i Ilham tayi saurin rik'eta.
Cikin tashin hankali Umma da Abba suka yo kanta,
"Innalillahi lafiya Fadwa? Meke faruwa ne?"
Cewar Umma!,
Yaya Farook ne yayi saurin sanya yatsun sa guda biyu wajen hancin ta,
"Subhanallah bata numfashi, Khaleel yi maza kaje ka tada mota akaita
hospital. "
Cikin hanzari Yaya Khaleel ya fice ' Abba kuwa duk ya gama rud'ewa domin daka
ganshi zaka gane cewa yana cikin tashin hankali,
"Fadwa don Allah kada ki mutu ' banason rasaki amatsayin y'a kamar yadda
Allah ya d'auke min mahaifinki amatsayin amini!"
Cewar Abba,
"Don Allah mai gida ka kwantar da hankalin ka ' insha Allah Fadwa rayayya
ce in Allah ya yarda,"
Yaya Farook d'aukar Fadwa yayi cen caka kaff d'aukar jarirai, yaje ya sata a
mota sanna ya dawo ciki ya Umarci Ilham taje ta d'auko gelenta, bata tare da wani
b'ata lokaci ba tadawo rataye da gele a k'irjin ta sannan suka fice ita da Yaya
Farook , har Umma zata bisu Abba yayi saurin rik'ota,
"Bazakije a haka ba! Ki kintsa tukunna sai mufita tare . "
Ya fad'a tare da samun waje ya zauna sannan Umma ta haura sashen ta domin
kintsawa, cikin hanzari ta Umma sauko parlon sanye sa hijab d'inta a jiki,
"A'a ki dakata tukunna harsai sun dawo sannan mu tafi baki d'aya,"
To kawai tace masa sannan ta sami waje ta zauna gami dayin tagumi.
Bangaren su Yaya Farook kuwa tunda Khaleel ya tada mota suka wuce gudu kawai
yake zabga wa ' cike da tausaya wa Fadwa.
Cikin d'an k'ank'anin lokaci suka isa asibiti, bayan sunyi packing ne Yaya
Farook ya fito cikin zafin nam ya d'auki Fadwa sannan suka shiga ciki, suna shiga
ne sukayi kicib'us da Doctor zai shiga wani Ward d'in Yaya Khaleel ya tsaidashi,
"Doctor!!! Please wait you have client here!!."
A tsanake likita ya juyo ya kalle su sannan ya kwalawa Nurse kira ' cikin
hanzari tazo wajen,
"Yes Sir!
"Ki hanzarta ki basu Ward ' kafin inzo yanzu!
OK tace sannan tayi masu jagora zuwa d'akin, bayan Yaya Farook ya kwantar da ita
Nurse d'in ta fita zuwa kiran Doctor ' Ilham na zaune a gefen Fadwa,
"But Yaya baka tunanin Zab'in nan dasu Umma sukayi ne yajawo wa Fadwa
wannan abin?"
Cewar Yaya Khaleel,
"What!!!? Karda insake jin wannan maganar daga bakinki Khaleel!! Ai duk
abinda su Umma suka yanke shine daidai, "
"But nifa Yaya gaskiya bana son ta,"
Yana gama rufe baki ya d'auke shi da mari tasss,
"Ashe bakada hankali Khaleel?"
"Kayi hak'uri Yaya, nayi kuskure insha Allah bazan sake ba!"
Ya na fad'in haka ya tashi ya fice ya nufi wajen mota yayi zamansa, bayan fitar
shine likita ya shigo ward d'in kai tsaye ya zarce inda Fadwa ke kwance '
stethoscope yasanya a k'irjin ta domin sauraron Numfashin ta, sai da ya kammala
sannan ya cire ya juyo ya fuskanci Yaya Farook.
"wato tayi doguwar suma ne, Amma insha Allah nan bada dad'ewa ba zata
farfad'o." . "To likita thank you so much,"
"You are welcome ' yanzu zan turo Nurse tazo tayi mata settling IV fluid, "
OK kawai Yaya Farook yace sannan Likita ya fita, cikin d'an k'ank'anin lokaci
Nurse tazo tayi mata settling drip, sannan ta fita.

*Around* *6:42pm*

Yaya Khaleel ya shigo cikin ward ' ya sami Yaya Farook zaune a kujera,
"Yaya wai har yanzu bata farka ba?"
"Eh wallahi Khaleel,"
"Yaya yanzu kamata yayi mutashi ita Ilham a maida ita gida ' don taje ta
d'an shiryowa Fadwa abinda zataci , bayan Munyi sallah sai mu taho da su Abba gaba
d'aya ' nasan kafin nan ta farka."
"Hakane Khaleel muje!!
Yaya Farook mik'ewa yayi suka fita Ilham ta bi bayansu, fitarsu keda wuya Fadwa ta
bud'e ido cike da kasala haka yayi dai dai da shigowar likita.
"Alhamdulillah ina y'an uwan naki?"
Yayi tambayar tare da dafa k'arfen gadon nata, kai kawai ta girgiza mashi sannan
ya ce.
"Oh may be lokacin da kika farka basu nan ' bari inje sallah in dawo,
Abinda ya fad'a kenan ya juya zai wuce tayi saurin tsaida shi da cewa,
"Doctor!! Please meke damuna?
Juyowa yayi ya kalleta tare da sanya hannun shi a aljihu,
"A yadda na fahimta ' kamar kinsami wani bad news ne wannan ne kad'ai zai
iya samar da shock a jikin d'an adam harta kaishi ga suma,"
"haka ne doctor tabbas bad news ne nasamu ' but please doctor can you do me
a favor?"
Tayi tambayar tana kallon kwayar idon shi,
"For what?
"Doctor please ' idan y'an uwana sukazo kace masu na suma ne saka makon
ciwon kan da yasami cikin d'an k'ank'anin lokaci please."
"is Ok i can do that for you ' akwai wannan sirrin tsakanin Doctor da
patients d'insa, so you don't have to worry about that."
Murmushi tayi masa tare da cewa thanks ' sannan ya fice.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*31-32* *pages*馃尮

Bayan sun Isa gida ne ' Yaya Khaleel yayi packing motar Ilham ta fito sannan su
kuma suka wuce masallaci, Ilham tana shiga ciki ta iske Umma a zaune ' jin motsine
yasa Umma d'ago kai ta kalle ta a razane,
"Haba Ilham ki shigo haka babu Sallama? Yaya jikin Fadwa?"
Ilham samun waje tayi ta zauna ' sannan tace,
"Umma Fadwa insha Allah zata sami sauk'i, likita ya ce zata farka bada
dad'ewa amma mudai har muka baro ta bata farka ba 馃槩."
Umma hannu biyu tasa ta rufe bakinta, tare da yin salati.
"Umma karki damu Insha Allah zata farfad'o, bari in shiga wanka kafin su
Yaya su shigo. "
Kai kawai Umma ta d'aga mata sannan ta tashi zata wuce sai kuma ta tsaya,
"Umma ina Abba ne?"
"Abban ku yana masallaci,"
To tace sannan ta wuce d'akin su.

*Around* *7:00pm*

Abba da su Yaya Farook suka shigo gida cikin nutsuwa, bayan sun shiga ciki ne
Yaya Farook yace.
"Abba i think ' ni kawai zan koma hospital d'in yanzu, don jiki na yabani
Fadwa ta farfad'o kuma baza taji dad'i ba idan ta farka taga babu kowa."
A zuciyar Yaya Khaleel kuwa cewa yayi,
"Mtsww Don Allah ji Yaya kuma! To dama wane dad'i kuma akeso taji itada
take a gadon Hospital? "
"To shikenan Farook , maganarka haka take ' to amma ka ci abinci kuwa?"
Cewar Abba,
"A'a Abba wallahi banajin yunwa.
"Haba Yaya yaza ai kace bakajin yunwa? Don Allah ka tsaya kaci abinci and
beside likitocin nan suna iyakar yinsu ' am sure Fadwa zata sami sauk,"
Cewar Yaya Farook,
Yaya Farook kallon shi kawai yayi tare da cewa,
"Bani key d'in mota!"
sannan ya juya ya wuce ' ba tare da yace masa komai ba.
kai tsaye ya wuce hospital d'in, direct ya nufi d'akin da Fadwa take ' koda ya
shiga a zaune ya iske ta hawaye kawai ke zubo mata a fuska, da sauri ya k'arasa
kusa da ita tare da tallabo fuskarta gami da share mata hawaye.
"Ko kad'an bana son inga hawaye na fita daga idonki,
A fusace ta d'ago rinan nun idanun ta ' ta kalleshi cikin b'acin rai,
"Hawaye?!! Hawaye fa kace!"
Ya d'aga mata kai alaman Eh,
"Ko dayake a fatar bakin ka kawai ya tsaya ' saboda nasan duk duniya babu
wanda ya kaika son ganin hawaye na!!..."
Ta k'arashe maganar cikin matsanan cin kuka,
"Subhanallah Fadwa meyasa zaki jefeni da wad'an nan kalaman? Nasani wannan
hukuncin da su Abba suka yanke ' dole zai yi mana ciwo amma we just have to accept
the fact, dole zamu yarda da k'addara kumm..."
Tun kafin ya gama rufe baki ' ta d'aga mashi hannu alaman dakatar wa sannan ta
goge hawayen ta,
"K'addara? K'addara fa kace! Wannan ai ba ita ake kira da k'addara ba Yaya
Farook, Yaya Farook ko a yanzu zaka iya warware komai ' kafad'a masu cewa ni kakeso
' ka fad'a masu cewa akwai soyayya tsakanin mu ple...."
Ba ta kaiga k'arasa maganar ta ba ya daka mata tsawa da cewa,
"Me kike nufi!!? Kina nufin inkoma ince masu zab'inda sukayi baiyi ba ko
kuwa mene?
"Eh abinda nikeso kenan kayi ' idan kuma ba haka ba to Wallahi zan bijire ,
ba don komai ba sai saboda kwata kwata babu soyayya a tsakanin mu da Yaya Khaleel '
baka ganin yadda yake treating d'ina? Yaya Farook wallahi inasonka."
"Wai meyasa bazaki fahimci abinda nikeson fad'a miki bane? Fadwa inason ki
amma haka nan zan hak'ura dake, hakuri kawai ya dace muyi baki d'aya."
Ya na gama fad'in haka ya juya zai fita tayi saurin rik'e mishi hannu,
"Please Yaya Farook ' meyasa baka sona? Amma shikenan naji kuma na hak'ura
zan aure shi, amma Yaya Khaleel bazai tab'a jin dad'in aure ba wallahi. "
jin haka yasa shi juyowa ya kalleta cike da b'acin rai sannan ya fizge hannun
shi ya fice, ya na fita suka had'e da su Umma a bakin k'ofar Ward d'in.
"Ina kuma zaka je?
Cewar Umma,
Komawa ciki yayi sannan suka bi bayanshi, Umma na shiga taje ta zauna gefen
Fadwa cike da fara'a.
"Ina wuni Umma? "
"Lafiya kalau Fadwa yaya jikin naki?"
"Umma kada ku damu naji sauk'i ina Abba?
Murmushi Umma tayi ' zatayi magana Ilham ta tari numfashin ta da cewa,
"Haba wa ai Abba ya ce yayi fushi dake ' shiyasa ma baizo ba,"
"lalala Umma dagaske ne?"
Cewar Fadwa,
"A'a k'arya take miki Abban ku yana cen tare da Doctor suna magana."
To kawai Fadwa ta ce sannan ta ballawa Ilham harara, Yaya Khaleel kuwa yana gefe
a tsaye rik'e da waya a hannun.
Abba ya shigo tare da doctor ' ya cirewa Fadwa canulla d'in hannun ta sannan
aka sallame su sannan suka koma gida.
*** *** *** *** **

*Around* *8:00pm*
Suka koma gida ' basu wani zauna yin hira ba kowa ya tafi d'akin shi domin yin
bacci.

*_babu_* *_yawa_* *_kuyi_* *_hak'uri_* *_da_* *_wannan_*

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me
*33-34* *pages*馃尮

Bayan shigarsu Fadwa d'aki ne Ilham ta sanya key a d'akin ta kulle tare da
ajiyan zuciya sannan taje ta sami waje ta zauna a gefen gado, Fadwa kuwa tana tsaye
tana k'ok'arin sanya rigar bacci,
"Alhamdulillah Fadwa watan mu ya tsaya! "
Fadwa tsayawa tayi cak ita bata sanya rigar ba ' ita kuma ba cire ba,
"Wane irin wata ne kuma ya tsaya?
"Eh mana kinga yanzu ' ni anbani damar in tsaya da duk wanda nikeso, ke
kuma an zab'a miki Yaya Khaleel ' kuma wallahi Fadwa ba k'aramin dacewa kukayi ba."
Ya tsine baki tayi sannan ta sanya rigar baccin ta ' ba tare da tace mata komai
ba ta haye gado ta kwanta gami da jan bargo,
"Ha'a Fadwa meye haka? Magana fa ni keyi kika shareni! Wai ma tsaya ko dai
bakyason Yaya Khaleel ne? "
Nan take Fadwa ta matso murmushi a fuskarta ' tare da tashi zaune,
"Haba Ilham wace irin magana ce wannan? Aini su Umma sun gama min komai '
to donme zance banason Yaya Khaleel? "
Murmushi Ilham tayi har saida fararen hak'oran ta biyu suka bayya,
"Naji dad'in jin haka Fadwa,"
Kwanta wa sukayi a tare ' sukayi shuru nad'an lokaci sannan Fadwa tayi zambur
ta tashi zaune,
"Ilham?"
Ilham ta amsa da "Na'am,"
"Ilham amma sai nake ganin kamar zansha wuya a hannun Yaya Khaleel '
saboda baya sona kuma kinga bawani sabawa mukayi dashi ba."
Ilham dafata tayi tare da cewa,
"Hmm Fadwa kenan ' karki bani kunya mana kamar ba'a *BABBAN* *GIDA* kike
ba? Ai wannan lokacinki ne da zakiyi amfani da damarki ' ki tsigilgila mashi rashin
kunya dole yayi hak'uri saboda ke zai aura! Kuma dole ki rik'ayin abubuwan da zai
rik'a jawo hankalin shi gareki although dama ya riga yace ke bakida kunya ' so
saiki nuna mishi haka."
Sakin baki tayi ta na kallon yadda Ilham keta zuba zance,
"Niko Ilham wai ina kikasan wad'an nan abubuwan?"
Cewar Fadwa,
"To ki zauna nan ' don wallahi Yaya Khaleel yana da y'an mata da yawa
saikinyi dagaske am telling you this! "
Murmushi kawai Fadwa tayi mata sannan suka koma suka kwanta ' A zuciyar ta tace,
"Nifa Ilham ba son Yaya Khaleel nakeyi ba, amma da wannan shawarar taki
zanyi amfani in nunawa Yaya Farook kuskuren daya tafka."
Tana gama ayyana haka a zuciyar ta ne bacci yayi awon gaba da ita.

*** *** *** *** ***

*Around* *6:30am*
Alam d'in wayar Ilham ya fara k'ara haka yasa Fadwa tashi a firgice,
"Haba don Allah wane irin abu ne wannan? Kinsama mutane Alam kamar wasu
yara!"
Cikin magagin bacci Ilham ta tashi ' tare da yin mik'a,
"Ke dai kika sani!! "
Cewar Ilham,
Ilham shigewa Bathroom tayi tayi wankan ta tare dayin Alwala ' sannan ta fito ta
iske Fadwa sai sharar bacci takeyi,
"Oh Fadwa wato bacci kika koma ko? To tashi zakiyi wallahi yanzun nan!"
K'ara sawa wajen gadon tayi ta yaye blanket d'in sannan tahau bubbuga ta,
"Ke dalla ki tashi ' kinsan ko k'arfe nawa yanzu,"
Ba arzik'i Fadwa ta tashi cikin b'acin rai sannan ta shige bathroom itama. Ko da
ta gama wanka ta fito ' ta iske Ilham harta idar da Salla, sannan itama tayi Sallar
a gurguje suka shirya don ganin kada lokaci ya k'ure masu.

*Around* *7:00am*

Suka gama kammala had'a breakfast, Fadwa ta shirya komai a saman dinning table '
sannan suka zauna ita da Ilham, haka yayi daidai da isowar Yaya Farook da Yaya
Khaleel cikin parlon ' hakan yasa Ilham kashewa Fadwa ido d'aya (Wink 馃槈) alaman
tayi wani abu. Bayan sun zauna a wajen ne Fadwa tayi wuff ta mik'e tsaye gami da
cewa,
"Let me serve! "
Zubawa ko wanen su tea tayi a cikin cup ' suka fara sha, sannan ta dafa hannun Yaya
Khaleel tare da cewa,
"Dear? A k'wai wani abunda kake buk'ata ne bayan wannan?"
Yaya Khaleel zaro ido yayi ' cike da mamaki tare da sakin baki ' hakan yasa
Yaya Farook sark'ewa,
"A'a babu abinda nike buk'ata!"
"Oh i see ' ai kamar Yaya Farook ne ma ke buk'atar ruwa a kusa dashi!"
Cewar Fadwa,
Nan take ta zuba mashi ruwa a cup ta mik'a mashi tare da cewa,
"Sannu,"
Ko kallon ta beyi ba ya karb'a ruwan tare da balla mata harara, sannan ta koma ta
zauna. Bayan sun gama karya wane Umma da Abba suka shigo parlon ' tukunna su kuma
su Ilham suka tashi da niyya wuce wa School,
"Har kun gama karya wanne?"
Inji Umma,
zukunna wa sukayi ' dukkansu suka gaishe su sannan suka mik'e tsaye,
"Umma zamu tafi School yanzu."
Cewar Fadwa,
"To Allah ya kaiku lafiya ' ya kuma baku sa'a!"
Ameen suka ce sannan suka nufi d'aki domin d'aukar handbag d'in su. Bayan
shigarsu d'aki ne Ilham ta ce,
"Fadwa ki cewa Yaya Khaleel shi zai kaiki School yau!"
Zaro ido tayi ' ta tsaya tana k'arewa Ilham kallo cikin tsoro,
"kinsan me kike fad'i kuwa?"
Ta d'aga mata kai alaman Eh ' sannan Fadwa ta girgiza mata kai gami da cewa,
"A'a wallahi bakisan me kike fad'iba, so kike ranmu ya b'aci da sassafen
nan ko Ilham?"
"Ko kad'an kawai k'ok'ari nike inga ya fara sabawa dake, kafin Aure!"
Girgiza mata kai kawai tayi ' sannan ta jawo handbag d'inta zata fita ' Ilham
tayi saurin rik'eta,
"Please ki gwada don Allah, "
To kawai ta ce sannan ta fice itama ta bi bayanta, saida suka kai tsakiyar
parlor sannan Fadwa ta tsaya.
"Ammm... Mhm Yaya Khaleel please zaka d'an kaimu School yau?"
Cikin bacin rai ya juyo ya kalleta ' sannan ya kalli su Abba dake karyawa,
"What!!?"
Ya fad'a a tsawa ce ' hakan yasa k'afafun ta suka fara rawa, Ilham tayi saurin
tab'ota tare da cewa,
"dalla ki dake!"
Fadwa kallon Yaya Farook tayi ' ta ga idon shi nakan wayar shi, haka yasa ta saki
murmushi sannan ta maida kallon ta kan Yaya Khaleel ' wanda ya had'e rai kai kace
mutuwar shi ya gani,
"Yes! Cewa nayi kad'an zo ka kaini School, "
"Driver d'in aikin uban me yakeyi?"
Sunkuyar da kanta tayi ' cikin shagwab'a tace,
"Nidai kai nikeso ka kaimu yau ' please Swe..."
Yaya Farook ne yayi gyarar murya ' tukunna Yaya Khaleel ya ce ,
"To shikenan muje!"
Ya fad'a cikin sanyin jiki ' sannan suka fita ya bi bayansu.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*35-36* *pages*馃尮

Bayan fitarsu ne daidai bakin k'ofa ya finciko ta cikin zafin nama ' Ganin haka
yasa Ilham yin sand'o ta shige mota,
"Don't you think kin cika zak'ewa da yawa? Ko cemiki akai ina..."
Nan yayi shuru ba tare da ya k'arasa ba ' ita kuwa tsoro ya gama cika idon ta '
Nan tayi k'arfin hali ta fizge hannunta tare da cewa,
"Yes ainasan cewa baka so na ' haka zalika nima bana sonka don baka tab'a
shiga raina ba Yaya Khaleel..."
Ta na rufe baki ya d'auke ta da mari tasss ' nan ta dafe wajen wasu zafafan
hawaye ke zuba mata a fuska,
"Kamar kin manta wanene a gaban ki ko?! To bara in tuna miki ' kina
magana da Khaleel ne, bana d'aukar raini Fadwa harni zaki kalla kice bakya sona?"
Nan ya ja hannun ta zuwa gaban mota ' ya bude seat d'in gaba cikin b'acin rai ta
shiga sannan ya rufe bamm, ya shiga ya ja motar.
Fadwa kuwa tunda ta shiga babu abinda take in banda kuka ' kukan ne ya ishe shi
yasa shiyin packing a gefen titi tare da cewa,
"Zaki min shuru ko saina k'ara miki? Idan kuma bazaki yi shurun ba to ki
fitarmun a mota,"
Aiba arzik'i tayi shuru don tasan halin shi babu abinda ba zai iya ba. Bayan sun
kai School d'in ne yayi packing Ilham ta fita ' Fadwa bud'e mota tayi zata fita ya
tsaida ita, sai da yayi shuru nad'an lokaci sannan ya ce,
"idan kuma kika sake ' kika fad'awa Umma ko Abba cewa na dakeki ' to
wanda zan miki sai yafi haka!,"
Sunkuyar da kai tayi ta had'e rai ba tare da tace Uffan ba,
"And ' anjima ni zan dawo na d'auke ku,"
Yayi maganar cikin sanyin rai ' ya na kallon ta,
"A'a ka barshi zan kira driver sai yazo ya d'auke mu,
"What!! Ina magana kina magana? To idan na dawo d'aukar ku ' kice bazaki
shiga ba! Fita ki bani waje, "
Da sauri ta fita tare da rufe mashi k'ofa sannan ya ja motar shi ya koma
gida. Ko da ya koma gida ' Umma kawai ya iske a parlor, Abba da Yaya Farook duk sun
wuce Office ' samun waje yayi ya zauna,
"Ina kaje ne?"
Cewar Umma,
"Umma na kai su Ilham School ne,"
Umma murmushi tayi sannan ta cigaba da kallon ta ' suna cikin hakan ne wayar shi
tayi k'ara Alaman kira, cikin hanzari ya d'auka.
"Ok to gani nan zuwa ' just give me some minutes Ok?"
Abunda ya fad'a kenan sannan ya kashe wayar gami da mik'ewa tsaye,
"Umma zan fita ' amma bazan dad'e ba zan dawo!"
To kawai Umma ta ce sannan Yaya Khaleel fita , wajen motar shi yayi ' ya bud'e ya
shiga sannan mai gadi ya bud'e gate tukunna ya fita.
kai tsaye ya wuce wajen wani k'aya taccen restaurant, sannan ya d'aga wayar shi
yayi kira tukunna ya k'arasa ciki.
Wata kyakkyawar mace ce zaune a kujera ' daka ganta kasan cewa kud'i sun zauna
mata kuma ba y'ar k'ana nan mutane bace. Ganin shi yasa tayi saurin mik'ewa tsaye
ta tare shi cikin murna ta rungume shi,
"i missed you so much ' my Love, "
Ta fad'a tare da k'ank'ame shi sosai,
"I missed you more baby,"
Rabata yayi da jikin shi ' sannan suka koma suka zauna , "jiya na
sauka Nigeria ' na biyo kane akan wannan maganar,"
Nan ya had'e rai tare da cewa , "wace magana kenan?"
"Ha'a don't tell me cewa dawo warka Nigeria ' harka manta maganar dake
tsakanin mu !"
"To basai ki tuna min ba! Ko aibune don kin tunamin?"
Sunkuyar da kai tayi cikin takaici ' tukunna ta d'ago idanun ta ta kalle shi,
"Khaleel ' maganar Auren da ke tsakanin mu mana, ka fad'amun cewa dazarar
na gama school na dawo gida zaka turo!"
Shuru yayi nad'an lokaci sannan yayi gyaran murya,
"Lubna, ba zan Aure ki ba!"
Nan take gabanta ya fad'a, cikin tashin hankali ta mik'e tsaye,
"What? Me kake nufi? Bayan ka riga ' ka gama lalata mun rayuwa ta sannan
ka ce bazaka Aure ne niba, impossible wallahi ba ka isa ba Khaleel..."
komawa tayi ta zauna ' cikin b'acin rai take kallon shi,
"Baby ba laifina bane ' su Umma ne zasu Aura mun wacce bana So, amma kema
kin san inason ki "
"Kar kayimun wani dad'in baki Khaleel , kuma ka sani bazaka tab'a samun
kwanciyar hankali ba inhar baka Aure ni ba."
Hannu yasa ya tallabo fuskarta,
"Haba Baby! Ki kwantar da hankalin ki, kinga wannan Auren da zanyi '
zanyi shine kawai don faran'tawa Umma da Abba, Amma i can assure you that bayan na
Aureta da wata d'aya ke kuma zan Aure ki."
Murmushi tayi har saida dimples d'inta suka fito sannan ta ce,
"Da gaske kake?"
"Kwarai kuwa baby na!"
Kallon wristwatch d'in hannun shi yayi yaga *1:56pm* ,ya tuna da zaije d'auko su
Fadwa daga School sannan ya maida kallon shi akan Lubna.
"Lubna zakiyi mun rakiya ' zuwa wani waje?"
Kai ta d'aga mashi sannan suka tashi ' suka bar wajen, wajen mota suka nufa ' ta
zagaya ta bud'e ta shiga tukunna shima ya shiga.
Kai tsaye suka nufi School d'in , bayan isar shi cikin makarantar ne *2:00pm*
ya cika daidai, Nan Fadwa da Ilham suka fito ' Ilham ce ta fara hango Yaya Khaleel
tare da wata,
"Ha'a to wacece ita?"
Ta fad'a cike da mamaki, haka yasa Fadwa saurin tambayarta.
"Ita wa?
Ilham nuni tayi mata da yatsa ' sanin Fadwa ta fahimci abunda take nufi,
"Kin gani ko? Daman na fad'a miki sai kinyi da gaske!"
Girgiza kai kawai tayi sannan suka k'arasa wajen motar, Ilham sauri tayi ta
shige mota ' nan Yaya Khaleel ya tsaida Fadwa,
"Baby , wannan itace Fadwa ' wacce Abba da Umma suka zab'amin don na
aura, "
Nan Lubna ta tsaya ta na k'arewa Fadwa kallo, tamkar zata had'iye ta.
"Gashi kamar bata iya gaisuwa ba ma!"
Fadwa girgiza kai kawai tayi gami dayin Murmushi,
"Sannu!"
Abinda ta ce kenan ta shige mota ' cike da takaici a zuciyar ta, nan shima Yaya
Khaleel yai ma Lubna izni data shiga su tafi ' seat d'in gaba ta bud'e ta shiga.
Tunda suka fara tafiya babu wanda ya ce Uffan ' kowa sak'e sak'e kawai ya keyi a
ranshi.
A bakin gate d'in gida ya tsaya shi bai kaiga shiga ba,
"My love, restaurant d'in nan zaka mai dani, don mota ta tana cen."
Cewar Lubna,
"Ku kuma ku k'arasa ciki bara in maida ta,"
Ilham ce mai k'arfin halin cewa to, sannan suka fito suka shige gida ' shi kuma
ya juya domin maidata restaurant d'in.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*39-40pages*馃尮

Yana shiga, ya iske ta a kwance ' duk'unk'une cikin blanket, sautin kukan ta
kawai ke yi mashi zarya a kunnuwan shi.
Samun waje yayi ' ya zauna a bakin gado ' dai dai Fuskarta, sannan ya yaye
bargon ' nan ne Fadwa tasan da mutum a cikin d'akin, hakan yasa tayi saurin d'aga
kanta ' ta kalle shi,
"Meyasa kikeso ' kiyiwa kanki horo da yunwa? ko kinaso ' wani ciwon ya
kamaki ne?..."
Yayi maganar cikin sanyin murya ' Fadwa tashi tayi ta zauna, tare da had'e kanta
da gwiwa,
"Yaya Farook, zan cigaba da hora kaina da yunwa ' kuma zanyi k'ok'arin
ganin ciwo ya kamani, ciwon ma na zuciya ' saboda na tabbata haka kake buk'atar
gani, "
Ta fad'a tare da d'ago kanta, tana kallon cikin kwayar idon shi ,
"Fadwa, hak'uri shine abinda ya dace damu ' bayan wannan babu wani abunda
zamu iyayi, kuma inaso daga yau ' ki d'aukeni a matsayin Yaya Farook d'in da kika
sani ,"
Yana gama fad'in haka ya juya ' ya share hawayen da ke shirin zubo mashi a
fuska, bai ankara ba ' yaji ta rik'o mashi hannu, a hankali ya juyo ' ya kalleta,
"Please Yaya na, promise me that ' bazaka tafi ka barni ba, zaka tsaya tare
da ni ' a cikin *BABBAN GIDA*, "
Nan take ' yaji wani mugun tausayin ta ' ya kamashi, zuciyar shi rugugi kawai
take mashi ' hakan yasa yayi saurin tallabo fuskarta.
"I promise you that ' k'anwa ta, insha Allah bazan tab'a barin ki ba."
Nan yasa hannu ' ya share hawayen da ke fuskarta,
"yanzu ' inaso ki tashi muje parlor, ki ci abinci kuma kiyi walwala kamar
kowa."
To kawai ta ce mashi ' sannan ta hanzarta ' ta sauko daga saman gadon, suka
fito d'akin a tare.
Kai tsaye ' suka zarce wajen dinning table, Fadwa ta zauna kusa da Ilham '
tukunna shima Yaya Farook ya sami waje ' ya zauna, sannan Ilham ta mik'e ta zuba
mata abinci.
Tunda Fadwa, ta zauna ' Yaya Khaleel keta satar kallon ta, yana son tambayar
ta dililin da yasa take kuka ' ita kuwa ko a jikinta, abin cin ta kawai takeci '
kasan cewar Yaya Farook ya tausasa mata zuciya.
Bayan sun gama ' cin abincin ne , ta tashi ta wuce d'akin su, Ganin haka ' yasa
Yaya Khaleel shima ya tashi zaibi bayan ta,
"Ina zakaje?"
Cewar Umma,
Tsayawa yayi ' yana kallon plate d'inda ke gaban shi,
"Umma d'akina zanje fa!"
"Allah ya baka sa'a , kuma ka cigaba dayin abinda kaga dama Khaleel '
shigowar Abban ku kawai nake jira."
Had'iye miyau yayi dak'er, har ya juya ' zai tafi sai kuma ya tsaya,
"Umma, ko wani laifin akace nayi?"
"Khaleel, tambaya ta kakeyi?"
Nan ya sunkuyar da kai ' gami da sosa kanshi,
"A'a Umma kawai dai..."
"To ka bari ' sai Abban ku ya dawo, sannan kaji laifin da ka aikata ' kuma
ka wuce ka bani waje,"
Tana gama fad'in haka, Yaya Khaleel ya nufi d'akin su Fadwa kai tsaye, Yaya
Farook kuwa fita yayi ' ya shiga mota yayi tafiyar shi.
Jin gidan babu dad'i ne yasa ' Ilham kunna TV donyin kallo. Bayan shigan ' Yaya
Khaleel d'akin ne ya iske Fadwa tsaye, wajen window ta na kallon waje ' daka ganta
zaka fahimci cewa lallai tana cikin damuwa,
"Meyasa meki Fadwa?"
Maganar ce tazo mata ' zuwan bazata, haka yasa tad'an razana kad'an, sannan ta juyo
' ganin Yaya Khaleel ne yasa ta b'ata rai, ta juya ta cigaba da fuskantar window.
Murmushin gefe yayi ' sannan ya tako har inda take, tare da tallabo fuskarta '
da hannu biyu, suna fuskantar juna.
"Why are you ignoring me? Ko nayi wani laifin ne ' ban saniba Fadwa,"
Harara ta watso mashi tare da kauda ' fuskarta daga hannun shi, sannan ta ja
tsaki ' ta juya zata wuce, yayi saurin janyo ta cikin zafin nama ' tare da had'a ta
da bango, nan ta saki wani k'ara.
"Ahhhggh,"
Matse ta yayi sosai ' ga irin rik'on da yayi mata a hannu, nan da nan ' idanun ta
suka ciko da hawaye,
"Yaya Khaleel, you're hurting me.."
"Ni zakiyiwa tsaki?
Cikin kuka ' tace,
"A'a.."
Nan ya saketa ' suka koma suna maida numfashi, daga bisani ya juyo ' ya kalleta.
"idan kin gama kukan ' kizo d'akina ki sameni,"
Fita yayi ' ba tare da yajira abinda zata fad'a ba, Fadwa komawa tayi ' ta zauna
gefen gado, ta share hawayen ta ' sannan ta tashi ta d'aura towel, ta fad'a
bathroom donyin wanka.

*** *** *** *** ***

*Around 5:30pm*

Fadwa ta fito parlor ' cikin doguwar riga, english wears ' gown ce a jikin ta,
ta zauna a jikinta sosai ' don shape d'in jikin ta gaba d'aya ya fito.
Ganin babu kowane a parlon ' yasa ta nufi kitchen kai tsaye, tare da kwala wa
Ilham kira.
"Ilham!!!"
"Na'am Fadwa, ina kitchen." Haka yasata k'arasawa cikin kitchen d'in cikin
sauri,
"Me kike girka mana ' don nasan dai akwai abincin dare."
"Kin manta ' nace miki yau zanyi bak'o Fadwa?"
"Ayya! sam na manta ' to k'arfe nawa yace miki zaizo? "
"Zaizo around ' 8pm,"
OK kawai Fadwa tace ' sannan ta bar kitchen d'in, ta nufi d'akin Yaya Khaleel '
knocking k'ofar tayi taji shiru, kawai ta bud'e ta shiga .
Shigarta yayi daidai ' da fitowar shi, daga bathroom d'aure da towel a jikinsa
' da alama wanka yayi, ganin haka yasa tayi saurin juya mashi baya.
"Am sorry ' I didn't know that you were naked!"
Ta fad'a, haka yasa shi juyowa ' a 360 cike da mamaki, sakin baki yayi yana
kallon ta ' sannan ya maida kallon shi ga jikinshi,
"Naked???"
Nan ya b'ata rai, a zuciyar shi yace,
"lallai ' wannan yarinyar y'ar rainin wayo ce, wato tsirara ma nake ' a
haka kenan, Lallai zan koya miki hankali."
Ya fad'a a zuciyar shi tare da jan tsaki ' sannan ya kalleta,
"Sai yanzu kikaga damar zuwa?"
"wanka nayi shiyasa..."
Nan ya tsaye yana k'arewa halittar ta kallo, sun b'ata minti 5 a haka sannan
yayi gyarar murya.''
"Ke! Wane irin iskanci ne ' wannan? Bayanki nakeson gani kokuwa gabanki?"
Maganar ce tayi mata wani ' ga tsaitsai,
"Yaya Khaleel, nifa ba y'ar iska bace ' taya kakeso in kalle ka, bayan
babu riga a jikin ka?"
K'arasowa yayi kusa da ita, sannan ya juyo da ita ' da k'arfin tsiya, take ta
runtse idon ta gam gam.
"Zaki bud'e idonki kokuwa saina miki abinda zaki dad'e kina tuna shi,
acikin ranki!"
Banza tayi ta kyaleshi ' ba tare da ta bud'e idon ba,
"Kinaso kicemin ' kwalliyar dama ba donni kikayi ba, ko kuwa mene?"
"Yaya khaleel, nidai kayi hak'uri but i can't..."
Bata k'arasa maganar ba ' taji saukar lips d'inshi a kan bakin ta, hakan yasa ta
bud'e idanun ta cike da tsoro, k'ok'arin kwace wa takeyi ' amma ya riga yaci
k'arfin ta.
Jin jikin ta na rawa ne ' yasa shi kyaleta, amma sam bai yarda ya rabu da
jikinta ba ' ninshi kawai takeyi sama sama,
"what? Don't you love me? Didn't you feel me? Fadwa ' nasan kina sona ai
ko, but ni bana....."
Jin haka yasa ta dawowa hayyaci ta ' cikin d'an k'ank'anin lokaci,
"Yaya Khaleel, abinda kaimun ' Allah ne kawai zai sakamin, kuma inaso ka
sani cewa ' wannan maganar ' da kayi Insha Allah saikayi dana sani, "
Nan ya ture ta ' ta zube a k'asa.
"Wai don nayi kissing d'inki, shine kike fad'amin wannan magan ganun ' to
bari kiji in fad'a miki, nayi kissing d'in y'am mata da dama, wad'an da suka fiki,
kuma daga k'arshe sukemin godiya ' why not kema kiyi godiya , and stop pretending!"
Nan ta tashi ' cikin sauri ' ta bar d'akin, kai tsaye ta wuce d'akin ta fad'a
saman gado, wani wahalallan kukane yazo mata mai sauti ' cike da tausayawa kanta.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*_I_* *_dedicated_* *_this_* *_page_* *_to_* *_all_* *_members_* *_of_*


*SEEMALUV'S* *NOVELS* *GROUP*

*37-38* *pages*馃尮

Suna shiga ciki ' suka iske Umma a zaune saman kujera tana kallo, bayan sun
gaishe tane suka juya da niyyar wuce wa d'aki Umma ta tsaida su,
"Ina Khaleel d'in? "
Ilham ce ta kalli Fadwa ' wacce kanta yake a sunkuye,
"Ha'a wai baku nake tambaya ba?"
"Umma yaje maida budurwar sa gida, "
Cewar Fadwa,
"Wace irin budurwa kuma ' babu dad'in ji, "
Nan Ilham tayi saurin shiga maganar ,
"Eh Umma budurwa! Umma wallahi ba kiga yadda ya wulak'anta Fadwa ba,
harda cewa wai zab'in kune amma bashi ya ce yana sonta ba...."
Nan Umma ta dakatar da ita cikin fushi ,
"Naji, ya kuma isheni haka nan ' kuma shi Khaleel d'in zai dawo ya same
ni, ku tashi ku shiga ciki."
Mik'ewa sukayi a tare suka wuce d'aki, bayan shigar su ne Fadwa ta sami waje ta
zauna ' sannan ta maida kallon ta kan Ilham,
"Ilham dama akwai maganar da nakeso in fad'a miki, amma please kada
kid'auke ta da wani fuska daban."
Cikin zumud'i Ilham ta ce,
"No wait! bari in fara fad'a miki wani albishir tukunna,"
To kawai Fadwa ta ce ,
"Fadwa yau zanyi bak'o na musamman, "
"Wow! Kardai kicemin dashi za'ayi,"
"Kwarai kuwa , Insha Allah shine mijin Aure na."
Girgiza kai Fadwa tayi cike da dariya ,
"Ameen, to meye sunan sa?"
Wara idanu Ilham tayi gami da juya su ' tukunna ta ce,
"Sunan shi Al'ameen."
Nan Fadwa ta buga uban ihu ' cike da jin dad'in sunan ,
"Insha Allah ' sunan d'a na kenan na fari, "
Murmushi kawai Ilham tayi tace,
"To fad'amin abunda zaki fad'amin yanzu, "
Nan Fadwa ta d'anji jikin ta yayi sanyi, sannan ta rufe ido ta fad'a mata duk
abinda ke tsakanin ta da Yaya Farook. Ajiyar zuciya Ilham tayi ' cike da tausayawa
soyayyar su,
"Fadwa ba laifinki bane ' laifin Yaya Farook ne da baiyi saurin sanarwa
ba, kuma inaso kiyi hak'uri ki cire shi amatsayin masoyi ' don na tabbata bazai
aure kiba, kuma yanzu dole zaki jajirce don ganin kinsamo kan Yaya Khaleel ' don
kuwa shine mijin auren ki.!"
Ajiyan zuciya tayi nad'an lokaci,
"Ilham , Insha Allah zan k'ok'arta duk da nasan zansha wahala a wajen
shi,"
"A'a kar kice haka ' Fadwa ni zan taimaka miki wajen yak'ar wannan
budurwar tasa dayake ik'irari, "
Nan sukayi smilling ' sannan suka tashi suka nufi kitchen, shirye shiryen abunda
za'a ci na lunch sukeyi cikin hanzari, nan Diary d'in Yaya Khaleel ya fad'owa Fadwa
a rai.
"Amm Ilham , ki bani 5minutes zanje indawo yanzu ' and please karki tsaya
jirana, "
Ok kawai Ilham ta ce sannan Fadwa ta nufi d'akin Yaya Khaleel kai tsaye, bud'e
k'ofar tayi a hankali ta shige cike da sand'o.
Ta na shiga tahau yin bincike ' gami da bud'e drowers d'in d'akin, ganin bata
sami komai bane yasa ta koma gefe tare da cije yatsa ' tukunna ta haye saman gadon
shi, tana d'aga pillow taga Diary d'in, nan tayi ajiyar zuciya sannan ta d'auka
cikin sauri ta diro daga saman gadon ' ta baro d'akin.
D'akinsu ta nufa direct ta bud'e handbag d'inta ta saka ciki, sannan ta koma
kitchen ' tana shiga ta iske har Ilham ta gama d'aura sanwa,
"Har kin d'aura sanwan kenan?"
"Eh na gama ' yanzu kuma kece da zarya cikin kitchen, don na gama nawa.
"
Ya tsine baki tayi ' gami da cewa,
"To naji dai ' aini ba raguwa bace ' balle kice bazan jure ba !"
A tare suka bar kitchen d'in suka nufi parlor ' Umma suka iske a zaune ita
kad'ai tana kallo, sannan suka sami waje ' suka zauna,
"Fadwa kun d'aura sanwan ne?"
"Eh Umma mun d'aura,"
Tana gama fad'in haka Yaya Farook ya shigo cikin parlon cike dayin sallama ' suka
amsa, sannan ya sami waje ya zauna gami da sauke ajiyar zuciya.
"Ke Ilham kawomin ruwan sanyi, "
Cikin hanzari Ilham ta tashi ' ta nufi kitchen, ta d'auko mashi robar ruwan
sanyi da cup ' ta kawo mashi. Bayan ya shane yayi gyarar murya,
"Umma ' na sami transfer daga wajen aiki na, "
"Farook transfer kuma?"
"Eh Umma yanzu haka ma tare da transfer letter d'in nake, "
Hankalin Fadwa in yayi dubu ya b'aci, cikin damuwa taketa k'ok'arin had'a ido
dashi, shi kuwa yak'i yarda don kuwa yasan tabbas tana cikin damuwa,
"Yaya Farook ' ina ne suka maida ka yanzu?"
Cikin rawar muryar tayi maganar ' hakan yasa Ilham tayi sauri ta rik'e mata
hannu,
"Bangladesh suka tura ni, sun bani nan da 3days ' infara shirye shirye, "
Nan ta rafka salata ' salatin da batasan ya fito fili ba,
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,"
Da sauri Umma ta kalli Fadwa ' hawaye ne kawai ke fitowa daga idanun ta,
"Fadwa lafiya? Bafa tafiya zaiyi gaba d'aya ba! zai rik'a zuwa yana ganin
mu,"
Girgiza kai kawai takeyi cikin kuka ' ganin haka yasa Umma cewa,
"Ilham jata ku tafi d'aki ki lallashe ta, "
Kwallane cike a idon Yaya Farook ' kasa danne zuciyar shi yayi yasa yayi saurin
tashi ' ya wuce d'akin shi.
"Ohh ikon Allah ' shak'uwa kenan, Allah dai yak'ara sanya shak'uwa a zuciyoyin
ku. "
Cewar Umma,
Nan itama ta tashi ta wuce kitchen don duba ' girki.
Ilham lallashin Fadwa kawai takeyi ' amma sam tak'i daina kukan,
"Fadwa hak'uri fa zakiyi ' Yaya Farook ko ya tafi na tabbata zai rik'a
dawowa yana dubamu, "
"Ilham wallahi inason shi sosai ' zuciyata ta kasa hak'ura kibarni kawai
inyi kukan ko zansami sauk'i, "
Sake fashewa da kuka tayi ' cike da tausayawa,
"Fadwa, amma dai kinsan kukan nan bazai ammafana miki komai ba ko? Yes
nasan kina son shi sosai ' amma kinsan dai bazai aure ki ba yanzu!"
"Ilham, please ki daina tunatar min da haka ' its hurting me, i have a
stronge feelings that Yaya Farook shiya nemi wannan transfer d'in da kansa. "
Rik'e hannun Ilham tayi ' tare da cewa,
"Ilham, am pretty sure Yaya Farook ya na sona haryanzu a cikin zuciyarsa
' Ilham kawai bayason ganin biki nane dawani shiyasa ya nemi Transfer, "
Ilham d'aura kan Fadwa tayi a kafad'an ta gami da bubbuga mata bayanta,
"Kiyi shuru ki bar kukan nan ' and zuwa anjima idan zaki kwanta ki
tabbatar kinyi *istik'ara* domin neman zab'in Allah,"
Ajiyan zuciya tayi ' sannan tace to tukunna Ilham ta tashi ta tafi kitchen.

*Around* *3:00pm*

Yaya Khaleel ya dawo gida, Ilham ce d'auke da plates a hannun ta nufi dinning table
da shi, haka yayi daidai da shigowar Yaya Khaleel cikin parlon ' ganin har an gama
abinci ne yasa ya doshi wajen dinning table d'in kai tsaye. Samun waje yayi ya
zauna sannan ya tsayaya ruwan sanyi a cup yasha, itadai Ilham tana tsaye ta jera
abubuwa.
Umma ce ta shigo cikin parlon ' ta Umar ceta dataje ta kira Yaya Farook ya zo ya
ci abinci, Bayan Wucewar Ilham ne Yaya Khaleel ya gaida Umma da cewa,
"Sannu Umma!"
Umma ko kallon shi batayi ba ' balle ta amsa sallamar shi, ta sami waje ta zauna ,
hakan yasa hankalin shi ya tashi ' Yaya Farook ne ya shigo parlon Ilham na biye da
shi , sannan suka sami waje suka zauna Tayi sarving d'insu.
Bayan sun fara cin abincin ne ' Umma ta umarce Ilham taje ta kira Fadwa ,
"Umma tund'azu naimata magana, tace batajin yunwa ' inbanda kuka babu
abinda takeyi, "
Yaya Khaleel ne ' ya d'ago kai ya kalleta,
"kuka kuma? Me akayi mata take kuka, "
Yunk'urawa yayi zaije d'akin Umma tayi saurin dakatar da shi,
"ina zakaje? D'akin nasu zakaje domin kasake k'unsa mata wani bak'in
cikin kokuwa me?"
Komawa yayi ya zauna ' tare da girgiza kai Alaman A'a,
"Umma zanje induba ta ne!"
Tsaki taja ' ba tare da tace komai ba, sannan Yaya Farook ya tashi ya wuce
d'akin nasu domin duba halin da take ciki.

*Dedicated* *To* *My* *Fan's*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:50 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluvv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

@*_I want to use this opportunity ' to thanks everyone of you, for the birthday
wishes ' gaskiya naji dad'i sosai, kuma na gode ' Thank you so much guys, you
really make my day...thank U once more.馃槝馃槝馃槝_*

*41-42pages*馃尮

Jin tafiyar Ilham ne ' yasa tayi saurin share hawayen ta, tare da saukowa daga
saman gadon.
Bayan shigowar Ilham ' cikin d'akin ne, ta fahimci cewa akwai abinda yake damun
Fadwa.
"Fadwa? "
Juyowa tayi ta kalleta ' cike da sosa idanun ta.
"Na'am Ilham."
"Kamar kinyi kuka ' Fadwa, da abinda ke damun kine?"
Nan ta matso murmushin k'arfin hali.
"Laa! Wane irin kuka kuma? A'a babu abinda ke damuna, kawai kwaro ne ya
shigar mun ido."
Ok kawai Ilham tace ' sannan ta d'auki towel ta d'aura a jikin ta, ta shiga
wanka. Ilham komawa tayi a kwanta ' abunda Yaya Khaleel, yayi mata ne ' yaketa
fad'o mata a rai.

*Around 8:00pm*

Bayan Ilham tayi wanka ' harta gama shiryawa, cikin Riga da skirt ' atamfa, sannan
ta zauna a gaban mirrow ' ta fara cab'a ado. Fadwa wacce ke kwance ' a saman gado
ne tace,
"Waike, wannan wace irin make-up kikeyi haka?"
Ilham tsayawa tayi cak ' tana kallon ta cikin mirrow,
"Ha'a to ina ruwanki? Nifa banason sa ido ' in kinji haushi kema kiyiwa
Yaya Khaleel."
Tsaki taja ' tare da saukowa daga saman gadon, cikin b'acin rai.
"Ke dai kika sani!!"
Ta fad'a gami da ficewa daga d'akin, ta nufi parlor kai tsaye. zaman ta keda wuya '
Yaya Farook ya dawo, sallama yayi ta amsa ' tukunna ya sami waje ya zauna.
"ke kad'ai ce a parlon, ina Ilham tace?"
"Ilham, tana d'aki."
Ta fad'a ba tare da ta kalleshi ba. Yaya Farook ' zaiyi magana kenan yaji sallamar
Abba, a cikin parlon ' cikin hanzari ta tashi, ta tunkari Abba.
"Abba, sannu da dawowa." Fadwa ta fad'a gami da karb'ar jakkar shi ,
sannan ta kai mashi sashen d'in shi.
Bayan ya zauna ne ' Yaya Farook yayi ma Abba sannu da isowa, tukunna ya koma
k'asa ya zauna.
"Ina Umman taku take?"
Cewar Abba,
"Nima shigowa ta ' kenan Abba, amma ina tunanin tana d'akin ta."
"Alright! Naga sak'on ka ta Email d'ina, game da transfer d'inda akayi maka
' hope dai ka gama shiryawa?"
Hakan yayi dai dai ' da dawo war Fadwa cikin parlon.
"Eh Abba , na kammala shirina ' nan da next week Insha Allah flight d'ina
zai tashi."
Raras Fadwa taji ' gaban ta ya fad'i , a hakanli take saukowa ' daga saman
steps tare da cewa,
"Abba, nakai jakkar d'aki."
Muryar ta na rawa ta fad'i haka, jin haka yasa Yaya Farook juyowa ' ya kalleta a
tsorace.
Ganin ta nufi b'angaren su ne ' yasa shi mik'ewa tsaye tare da cewa,
"Abba , ina zuwa."
Uhm-hum, kawai Abba ya ce ' sannan Yaya Farook yabi bayan Fadwa cikin sauri,
hartasa hannu zata bud'e k'ofar d'akin su yayi saurin tsayar da ita.
"Fadwa, Please.."
A fusace ta juyo ' ta kalle shi, idon ta cike da hawaye.
"Bana son ji! Yaya Farook, babu abinda zaka fad'amin, kamin k'arya kuma ka
b'oyemin, and Insha Allah ' na hak'ura dakai for good, and if am where you ' zan
had'a kaya na ne gobe gobe intaf...."
Bata kaiga k'arasawa ba ' ya falla mata mari, jikake tasss ' nan take ta
zuk'unna gami sakin k'ara.
"Ahhhhgggh,"
"Fadwa, kinsan me kike fad'i kuwa? Kinsan wanene a gabanki kuwa?"
Cikin kuka ta mik'e tsaye ' tare da cewa,
"Kwarai kuwa, nasani ' kuma nagode!!!"
Tana fad'in haka ta bud'e k'ofar d'akinsu ta shige, nan sukayi kicib'us da Ilham
' tana k'ok'arin fitowa.
"Ke! Fadwa, harya iso."
Fadwa banza tayi ' ta kyaleta tashige d'aki, Ilham lura tayi da Yaya Farook a bakin
k'ofar ' ranshi a bace , a zuciyar ta tace.
"Topha! Ashe takuce ' ta had'o ku!!"
Saida ta tsaya ' ya wuce tukunna, itama ta wuce parlor ' gudun karya huce kanta.
Ilham wacce ta fita ' ta shigo da bak'on ta mai suna Al'ameen, cike da fara'a ta
zarce dashi ' parlon da bak'i ke zama.
Bayan sun gaisa ne ' ya yaba da irin Kwalliyar da taimashi,
"My baby, gaskiya kinyi kyau ' nawa za'a siyarmun da wannan kwalliyar?"
Murmushi tayi ' sannan ta tashi, tare da cewa.
"uhm ' bara in kawo maka ruwa!,"
Tana fad'in haka ta wuce ciki ' ta nufi kitchen kai tsaye, ta had'o mashi
drinks da abubuwan da ta shirya mashi.
Ilham, dawo wa tayi ' ta aje mashi a gaban shi, sannan ta bud'e drinks d'in ta
zuba mashi a cup ' ta mik'a mashi cike da ladabi, ta koma ta zauna.
Al'ameen, sau d'aya yasha ' sannan ya aje a k'asa,
"My baby na gode ' da tarba mai kyau, But nace nawa ' zanbiya kwalliyar
nan?"
"Sweetheart, ai bazaka iya biya ba ' so kawai kabarshi."
Nan suka cigaba da hirarsu ' ta soyayya, Fadwa kuwa na kwance a d'aki tana danna
wayarta, taga an bud'o k'ofa ' ga dubanta saitaga Umma ce ,
"Fadwa! "
"Na'am Umma?"
Umma k'arasawa ciki tayi ' ta zauna a bakin gado, itama Fadwa ta ' tashi ta zauna.
"Ki tashi ' kije Abban ku nason magana daku,"
To kawai Fadwa ' ta cewa Umma, sannan ta sauko daga kan gadon ' da niyyar
fita,
"Ina Ilham take?"
Cewar Umma,
"Amm, Umma ' tayi bak'one, suna k'aramin parlor."
To Umma tace ' sannan Fadwa ta fita zuwa parlor, ita kuma Umma ' zarcewa tayi
d'akin Yaya Khaleel ' da Yaya Farook.
Bayan Fadwa ' ta isa harabar parlon ne, ta iske Abba a zaune d'auke da laptop
a saman cinyar shi ' sai da ta gaishe shi tukunna, ta sami waje a k'asa ta zauna.
"Fadwa, ke kad'ai ce ' ina sauran suke?"
"Umma taje kiran su ne ' but ita Ilham, tana da b'ako ne shiyasa."
Ok kawai Abba ya fad'a, sannan ya maida kanshi ' ga laptop. Ana a hakan ne '
Umma ta shigo cikin parlon ' su Yaya Farook ' da Yaya Khaleel, suna biye da ita.
Umma zama tayi ' gefen Abba, tukunna suma suka zazzauna a k'asa cike da
ladabi, Abbane ya ajiye ' laptop d'in nashi, saman hannun kujera ' sannan yayi
gyarar murya.
"uhm Uhm! Ammm... dalilin ' taraku anan wajen shine, Magana ce akanka ' kai
Khaleeel."
Nan Yaya Khaleel ' yaji rasras a zuciyar shi. Sannan Abba ya cigaba da cewa,
"Tabbas ' duk naji abubuwan da kakeyi, a cikin gidan nan ' da kuma waje, da
irin wulak'ancin da kake nunawa ' ita wannan yarinyar Fadwa, to inaso ka bud'e
kunnuwanka sosai ' ka saurare ni, Fadwa ce ' zab'in mu a cikin gidan nan ba wataba
' kuma Aure tamkar an d'aurashi ne ' harkai ka isa kayi jayayya ' da zab'in mu?"
Cikin tashin ' hankali Yaya Khaleel ke girgiza kai.
"Kuma bari ' kaji in gaya maka, wani abinda baka sani ba ' aure kamar
anyishi angama ne, domin nida Umman ku ' mun yanke shawaran Next week za'ayi auren
ku, in Allah ya yarda."
Maganar ce, taiwa Fadwa tsawa a kai ' da k'arfi ta d'ago kai ta kalli Abba,
sannan ta maida kallon ta ' akan Yaya Khaleel, wanda shima ita yake kallo ' ranshi
a b'ace, tukunna ta maida kallon ta ' zuwa k'asa..
"To amma Abba, bikin nan fa kamar yayi kusa ' da yawa...."
Bai kaiga ' gama rufe baki ba, Umma ta daka mashi tsawa ' da cewa,
"Rufe mana baki, ja'iri kawai ' wato kai har wuyarka tayi kwarin da zaka
iya ' fad'a in fad'a da Abban naku? Lallai bakada kunya Khaleel."
"Umma, don Allah kuyi hak'uri."
Abinda ya iya fad'i kenan, sannan ya sunkuyar da kanshi k'asa.
Fadwa kuwa ' mamakin kanta ' ta rik'ayi ganin yadda idonta ' ya k'enk'eshe sam
babu hawaye a cikin sa.
Shi kuwa Yaya Farook ' komai baice ba game da maganar, sannan Abba ya ce.
"Ku tashi ' ku tafi."
Fadwa yunk'urawa tayi zata wuce, Abba ya tsaida ita.
"idan Ilham ta gama ' ki sanar da ita, ina neman ta."
To kawai ta ce ' sannan ta wuce d'akin su, ta haye gado ' a cigaba da danna
wayarta.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*43-44*
Yaya Farook kuwa ' yana shiga d'akin shi, ya hau shirya kayan shi ' cikin
trolley, daga bisani ya tsaya ' don kuwa yarasa meyasa yake sanya kayan shi aciki.
Komawa yayi ' ya zauna tare da goge zufar goshin shi, sannan ya tashi ' ya shiga
bathroom yayo alwala, yayi sallah raka'a biyu(Nafila) ' gami da rokon Allah yazab'a
mashi mafi alkairi.
B'angaren Yaya Khaleel kuwa, gaba d'aya ranshi ya riga ' ya gama b'aci.
Nan ya d'auki wayar shi ' da take kan mirrow d'in d'akin, cikin sauri yayi
dailing number d'in Lubna, harta shiga ' yayi saurin yanke call d'in gami da dafe
kanshi,
"Oh my God, what the hell ' is wrong with me!, meyasa su Abba zasuyi min
haka? Yes inason Fadwa ' but is just that ita ba ajita bace, and besides she's not
my choice."
Ita kuwa Lubna ' cike take da mamaki, yadda taga flashing d'in Yaya Khaleel a
cikin wayar ta ' girgiza kai kawai tayi, sannan tayi dailing number d'in shi itama.
Yaya Khaleel ' yana cikin wannan tunanin ne, yaga shigowar kiran Lubna ' cikin
hanzari yayi recieving.
"My love!"
"Yes baby ' ya kike?"
"Lafiya kalau my love!' I was surprised dana ga missed call d'inka."
Nan ya tuna cewa ' eh tabbas yayi dailing numbar ta,
"Oh yes baby, it was a mistake ' bansan na kiraki ba ma. "
Yana yin ' yadda yake magana ne, ta fahimci cewa ' akwai abinda yake damun shi.
"but my love ' is everything alright? "
"Of cause, baby zamuyi magana ' anjima Okay?"
Bai jira ' yaji abinda zata fad'a ba ' ya kashe wayar, sannan ya koma ya zauna
a Sofa.
Yaya Khaleel ' cike yake da tunani iri ' iri, a cikin zuciyar shi ' jinginar
da kanshi yayi a jikin kujera, zuciyarsa na maimaita mashi ' maganar da Abba yayi.
"Subhanallah!"
Abinda ya iya furtawa kenan ' ya tashi ya shiga bathroom, domin watsa ruwa.
Ita kuwa Fadwa ' pictures taketa kallo cikin wayarta, don kuwa duniya taimata
dadi ' tana cikin haka ne Ilham ta shigo cikin d'akin.
Zambur Fadwa tayi ta zauna ' fuskarta d'auke da murmushi.
"Har Al'ameen d'in ya tafi?"
"Eh ya tafi ' kuma yayi fushi, tunda bakizo kun gaisa na."
Uhm ' kawai Fadwa tace wa Ilham, Ilham lura tayi ' Fadwa ta sauya ba kamar
yadda ' ta barta ba.
"Fadwa akwai labari ne mai dad'i?"
"Uhm ' ai dama abinda naketa jira ki tambaya kenan."
Nan ta fad'a mata duk abinda ke faruwa, da kuma hukuncin da Abba ya yanke '
sannan kuma ta sanar da ita cewa Abba yana nemanta.
Miyau Ilham ta had'iye dak'er, gaban ta na dukan uku uku.
"Shikenan ' nima za'a badani, Allah dai yasa nawa ba kusa ' kusa bane
haka."
Ta fad'a tare da dafe k'irjinta, abinne ya bawa Fadwa dariya matuk'a.
"Haha! Lallaima Ilham ' to ba gwara kawai a had'a mu ' mu biyu ba?"
Girgiza kai kawai Ilham tayi ' daka kalli idon ta ' zaka gane cewa akwai fargaba
a cikin su, Ilham juyawa tayi ta nufi sashen ' Abba.
Bayan Yaya Khaleel ' ya fito wanka ne, d'aure da towel a jikin shi ' ya zauna a
bakin gado, ya hankad'a pillow ' don d'aukan diarry d'inshi, Hankalin shine yayi
matuk'ar tashi ' don ganin babu diarry babu alamar sa.
Nan yayi zambur ' ya tashi tsaye, gami da bud'e drowers d'in wajen ' duk da
yasan bai aje a wajen ba.
"Ha'a to a ina na aje shi?"
Yaya Khaleel ' saida yabi ko'ina ya bincike, amma kwatakwata ' bai gani ba. Fadwa
ce ta fad'o mashi a rai ' don kuwa yasan babu wacce zata iya d'aukar mashi diarry '
sai ita.
"Oh my God ' this gurl is so stubborn, ni bansan yadda zanyi ' da yarinyar
nan ba wallahy, mtswww."
Ita kuwa Fadwa tashi tayi ' tayi shirin bacci cikin rigar bacci transparent '
iyakarta gwiwa, sannan ta haye gado ' gami da janyo handbag d'inta, tana k'ok'arin
cire diarry d'in Yaya Khaleel ' domin karan tawa.
Yaya Khaleel ' abin duniya ne ya isheshi, ya ga bazai iya hak'uri ba ' hakan
yasa yafito daga d'akin shi ' daga shi sai towel a jikin shi, ya nufi d'akin su
Fadwa.
Yaya Khaleel ' bankad'o k'ofar yayi ' haka yayi daidai, da cirowar Diarry d'in
nashi ' daga hannun Fadwa.
A tsorace ta d'ago kai ' ta kalleshi, tsoro ne yasa tayi saurin yin wurgi da
diarry d'in k'asa ' cikin rawar baki tace.
"Yaya Khaleel ' are you looking for something?"
Ta fad'a tare da yin saurin rufe jikinta ' da blanket ma'ana bargo. Cikin fushi
ya k'arasa cikin d'akin cike dayin huci tamkar zaki, finciko ta yayi ' har sai da
hannun ta ya ansa, a tsiyace ya fizgota zuwa k'asa.
"Ke!! Where is my diary?"
Had'iye miyau tayi dak'er , sannan tace.
"Yaya Khaleel ' babu diary d'inka a wajena!"
Yaya Khaleel ' maida kallon shi yayi zuwa k'asa, sannan ya tuna lokacin da '
take wurgi dashi zuwa k'asa, Fadwa cikin tsoro ta kalli diary d'in ' sannan ta
maida kallon ta kan Yaya Khaleel suka had'a ido.
"Well ' am so sorry Yaya Khaleel, am just trying to..."
"trying to do what!!!"
Ya daka mata tsawa ' sannan ya duk'a ya d'auki diary d'in.
"For Goodness sake ' why are you so stubborn? Fadwa!"
Sunkuyar dakai tayi ' ita dai tsoron ta shine, kada ya tab'a lafiyan jikin ta.
Fadwa jitayi yayi shiru ' yasa tayi saurin d'aga kai ta kalleshi, ga duban ta
sai taga ' ashe k'irjin ta yake k'arewa kallo, kasan cewar rigar jikinta shara
shara ce.
Da sauri tasa hannu d'aya ' ta kare wajen ' don kuwa yana rik'e da d'ayan
hannun, ganin haka yasa Yaya Khaleel dawo wa cikin senses d'in shi.
Ganin yadda tsoro ya kamata ne ' yasa shi yin murmushi tare da tallabo
hab'arta.
"What? Meye kike karewa? Aren't you stubborn enough? And besides ' kin kusa
zama matata duk da bakida mu halli a zuciyata."
Nan ya fara k'ok'arin kissing d'inta ' tak'i yarda, jin tafiyar Ilham ne ' yasa
yayi saurin wulli da ita ' ta fad'a saman gado, sannan ya juya ya fice ' suka had'e
da Ilham a hanya, saida ta jira ya wuce sannan ' ta k'araso cikin d'akin.
"Fadwa ' meyafaru ne?"
"Me kika gani?"
Ilham K'arasawa ciki tayi ' ta nemi waje ta zauna.
"gani nayi ' daga ke har shi ' kunyi wani iri."
"hmm ke kuwa ' akwai ki da sonjin kwakwaf, babu komai fa kawai zuwa yayi '
yayi abinda ya saba."
Ya tsine baki Ilham tayi ' sannan ta shiga cire kayan jikinta, donyin shirin
bacci.
"Baki bani labarin yadda kukayi da Abba ba."
"Ke nifa wallahi ' yanzu bacci nakeji, ki bari sai munje school."
Ok kawai Fadwa tace mata sannan ' ta maida kallon ta kan wayarta

*Dedicated To My Fan's*
*_Seemaluv 馃憚 ' the brave!!馃挭_*
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚
&
*_Sumeeluv_*

www.Seemaluv.wapka.me

*_@Assalamu Alaikum, ina mai mik'a godiya ta agareki RUFAIDA YUSUF. Naji dad'i
sosai matuk'a da yadda kika nuna soyayyarki ga JAMEESHA ' bama JAMEESHA kad'ai ba
hardani, gaskiya munji dad'i sosai JAMEESHA tana godiya sosai..._*

*45-46*

A haka bacci yayi awon gaba dasu.


*Washe gari*
Da sassafe ' su Fadwa suka tashi, sai da sukayi sallah tukunna sukayi wanka ' Fadwa
ce ta fara shiryawa sannan ta shiga kitchen domin had'a breakfast, Ta na cikin
had'a tea ne Yaya Khaleel ya shigo .
Cikin muryar rashin lafiya ' yayi mata magana,
"Fadwa ' please ki had'a mun Coffee yanzu, ki kawomin d'akin...."
Bai kaga k'arasawa ba ' amai ya taso mashi, cikin sauri ya k'arasa wajen sink
d'in kitchen ' yaita kakarin amai.
Cikin hanzari ' Fadwa ta d'ibi ruwa a cup, ta tsiyaya ruwan a tafin hannun ta,
ta fara shafa mashi asaman kanshi.
"Sannu Yaya Khaleel."
Yawwa kawai yace ' sannan yabar kitchen d'in ya wuce d'akin shi. Nan tayi sauri ta
had'a mashi Coffee d'in ba tare data k'arasa had'a masu kayan breakfast d'inba.
Fadwa barin kitchen d'in tayi ' ta nufi d'akin Yaya Khaleel rik'e da cup a
hannun ta, ciki ta shiga ta iske shi kwance saman gado ' rik'e da cikin shi, sannan
ta sami waje ta zauna a bakin gadon.
"Yaya Khaleel ' gashi na kawo."
Tashi yayi ya zauna ' tukunna ya karb'a Coffee d'in ya rik'e a hannun shi.
"Ki bud'e wancen drower d'in, zakiga Cimetadine ki d'auko min."
Yayi mata nuni da yatsar shi ' haka yasa ta doshi wajen kai tsaye, ta d'auko
maganin sannan ta dawo ta mik'a mashi. Harta juya zata wuce ya tsaida ta cewa,
"Ina kuma zakije Fadwa?"
Yanayin yadda yayi maganar ne ' yasa tajin tausayin shi sosai, hakan yasa ta juyo
ta kalleshi tare da cewa.
"Na'am?"
"Baki bani ruwa ba ' zaki wuce kuma."
"Bari in kawo ma."
Juyawa tayi zata fita ' da niyyar wucewa kitchen, ya tsaida ita.
"Ina zakije kuma? Bayan ga robar ruwa anan,"
Babu musu ta dawo ' ta d'auki robar ruwan ta mik'a mashi, sannan shi kuma ya
b'alli maganin yasa a baku ta zuba mashi ruwan ya kora, Fadwa wani yarrrr takeji '
tsigar jikin sai tashi takeyi, don kuwa batason magani a rayuwar ta kokad'an.
Yaya Khaleel ' sai a wannan lokacin ya kalli kwalliyar da ke fuskar Fadwa, a
wannan lokacin ne yaji kishinta ya fara shiga cikin zuciyar shi 'Fadwa kam harta
juya zata wuce yasake tsaidata, sai da ta yatsine fuska sannan ta juyo.
"Dama a haka kike tafiya school d'in,"
Nan ta tsaya tana duba jikinta.
"A'a zan sanya gele ai."
"Nup! Ba dressing d'inki nake nufi ba, kwalliyar da kika cab'a nakeso ki
gogeta yanzun nan."
Sunkuyar da kai tayi ' tare da turo k'aramin bakin ta.
"Ga tissue cen ' ki d'auka ki share wannan janbakin dake kan lips d'inki."
Kallon wajen da tissue d'in yake tayi, sannan ta sake sunkuyar da kanta.
"Yaya Khaleel plea..."
Bata k'arasa ba ya daka mata tsawa.
"Bakiji abinda nace maki bane?"
Cikin tsoro ' ta d'auki tissue d'in ta zara ta goggoge bakin ta.
"Na share."
"Ke am not joking ' ko sokike in tashi maki?"
Ta girgiza mashi kai ' sannan ta matsa gaban mirrow d'in tana gogewa, ganin
yak'i goguwa ne ta gane cewa lallai 24hrs ta shafa a bakin ta ' cikin fargaba ta
juyo ta kalleshi suka had'a ido.
"Yaya Khaleel ' yak'i fita amma don Allah kayi hak'uri bazan sake sawa ba."
Nan take ya diro daga gadon ' gami da cewa.
"No ai saiya fita yau d'in nan."
A hankali yakeyo kanta ' tanaja da baya, Sai da yaji ya k'ureta a bango tukunna
ya kamo k'ugunta.
Ganin haka yasa Fadwa tsorata sosai ' k'ok'arin k'wacewa takeyi amma ta kasa '
Yaya Khaleel kuwa k'ok'arin kissing d'inta yakeyi amma tak'i bashi had'in kai.
"Ke!"
Ya daka mata tsawa ' cikin tsoro ta d'ago kai ta kalleshi.
"Bazaki daina wannan fizge fizgen ba?"
Hawaye kawai ke tsiyaya a fuskarta.
" Ya Khaleel ' kayi hak'uri don Allah, ka barni in wuce ' bazan sake sawa ba
i promise."
Jikinta rawa kawai yakeyi ' hakan yasashi sakin ta cikin sauri, gami da juya
mata baya.
"Get out!"
ya fad'a cikin tsawa, Fadwa sauri tayi ta fita cikin rawar jiki ' ta koma kitchen
tana maida numfashi.
Sunan ta taji ankira ' haka yasa tayi saurin juyowa, don ta duba waye.
"Are you Okay?"
ganin Yaya Farook ne yasa tayi saurin share hawayen ta ' tare da cigaba da had'a
tea d'in.
"Of cause."
Ta fad'a a tak'aice sannan ta cigaba da abinda takeyi.
Abin ne yabawa Yaya Farook haushi ' yasashi k'arasowa kitchen d'in cikin fushi.
"Bazaki fad'amin abinda ke damunki ba!"
Fadwa banza tayi ta kyaleshi ' ta zuba tea d'in cikin plast, sannan ta d'auka
zata wuce ya rik'eta.
"Ki fad'amun abinda ke damunki mana Fadwa.!"
Nan ta d'aga kai ta kalleshi ' tare da ajiyar zuciya.
"Ya Farook ' ni babu abinda ke damuna, kuka kuma da kaga inayi wannan tsakani
nane da wanda zan aura."
Tana gama fad'in haka ta fizge hannun ta ta wuce, ba tare da ta tsaya ko inaba
ta wuce parlor ' ta ajiye plast d'in, sannan ta koma d'akin su don sanarwa Ilham.
Tana shiga suka cikaro da Ilham tana k'ok'arin fitowa.
"Thought ko baki gama shiryawan bane,"
Cewar Fadwa.
Juyawa Fadwa tayi suka tafi parlon a tare, suka zauna a dinning table.
Zaman su keda wuya ' su Umma da Abba suka shigo parlon, sai da suka zauna
sannan Fadwa da Ilham suka gaishesu.
"Yawwa Fadwa idan kin tafi School ' ki nemi permission subaki hutu, don yau
nakeson a fara shirye-shiryen bikin nan."
To kawai Fadwa ta iya cewa ' don kuwa sai yanzu ne takejin damuwa a cikin
zuciyarta.
A gaban idonta Umma ta d'aga waya ta fara kiran dangi tana sanar dasu bikina '
wata kunya ce tazo mata had'e da bak'in ciki, yasa tayi zambur ta tashi tsaye.
"Ilham tashi haka nan ' wallahi lokaci ya k'ure mana yau."
Tashi Ilham tayi ta d'auki cups d'inda sukayi amfani dashi sannan ta zarce
kitchen ita kuma Fadwa ta wuce d'aki don d'aukar handbag d'inta da gele.
Su Fadwa basu wani b'ata lokaci ba suka fita driver ya d'aukesu suka bar gidan
zuwa school.
Bayan driver ya sauke su a school ne ' suka shige class cikin sauri, duk
d'aukan su akwai lecturer a cikin. Saida suka shiga suka iske aji kowa sharholiyar
shi yakeyi, tukunna suka sami waje suka zauna.
"Ilham kince zaki fad'amin yadda kukayi da Abba jiya."
"Hm aikedai bari kawai ' Abba cewa yayi in fad'awa Al'ameen cewa yanason
ganin shi, don idan akayi bikin ki da one-week za'ayi nawa."
"Toh Allah ya kaimu ' but ninaso ace tare za'a aurar damu wallahi."
Wata uwar harara Ilham ta watsama Fadwa ' haka yasa Fadwa darawa kad'an, sannan
tad'an bigi kafad'anta.
Suka cigaba da surutun su ' kafin wani malamin ya shigo.

*** *** *** ***

*Around 1:54pm*
Fadwa ta mik'e tsaye daga seat d'inta ganin lecturer na ciki ne yasa ta d'auki
permission d'in fita.
Kai tsaye ta wuce Office d'i shugaban school d'in ta sanar da ita komai,
sannan akayi signing wata takarda ' aka bawa Fadwa.
Koda ta fito daga Office d'in ta iske antashi duk an watse, sai Ilham ne kawai
dake tsaye a k'ofar class take jiranta.
Cikin sauri ta k'arasa wajen ' ta karb'i handbag d'inta sannan suka nufi inda
driver ke tsaye yana jiransu.
Shiga motar sukayi a gajiye ' tukunna yajasu ya maidasu gida, saida sukaji
yayi packing ' sannan suka fito daga motar suka nufi cikin gida.
Fadwa na bud'e k'ofar parlon taji wani shock a jikinta cak ta tsaya a wajen '
don ganin yadda mutane suka cika parlon , Ilham abinne ya bata mamaki ganin yadda
Fadwa ta tsaya awajen.
"Ke don Allah meye haka ' ji yadda kikasa mutane sunata kallon mu,"
Ilham gaishe su tayi da hanya ' sannan itama Fadwa ta gaishesu, Ilham ganin
Fadwa tak'i tafiyane yasa ta kama hannunta ta jata suka wuce d'akin su.
Bayan shigarsu d'akine Fadwa ta fad'a saman gado cike da gajiya.
"ai kwanciya bai gankiba tukunna."
"Kamarya?"
Fadwa tayi tambayar ta k'ok'arin gyara kwanciya.
"eh tashi zakiyi muje mu gyara d'akin saukan bak'i , don nasan ba wani datti
yayyi ba k'urace kawai, don wallahi bazan iya sharing toilet ba ' kina gani harda
mutane k'auye akazo, yoo koma mutanen birnin nefa?!"
Fadwa ajiyar zuciya ta sauke ' tare da cewa.
"To nidai yanzu ki daure kije ki farayi ' don wallahi agajiye nake."
"to naji."
Har Ilham ta tashi zata bar d'akin, sai kuma ta tsaya gamida juyowa.
"Yawwa Fadwa ya kamata fa ' muyi arranging yadda za'ayi KAMU."
"Eh jeki dawo dai ' koma menene saimuyi magana akai koh."
Ilham ficewa tayi daga d'akin don zuwa gyarawa bak'i inda zasuyita kara kainan
su, Fadwa kuwa nan bacci mai dad'i ya d'beta.

*Dedicated To My Fan's*
*_Seemaluv the brave 馃挭_*馃槣
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*


漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*47-48*

*Around 4:00pm*
Fadwa ta farka daga bacci ' tashi tayi cike da mik'a da hamma, a zaune taga
Ilham tana karanta english novel.
"Ilham bak'in nan sun tafi ne? Naji banji hayaniya ba."
"Eh basu dad'e da wucewa ba amma zasu dawo gobe."
Fadwa saukowa tayi daga saman gado ta nufi bathroom da niyyar yin alwala ' Ilham
ta tsaida ita da cewa.
"Fadwa guess what?"
Juyowa tayi ta kalleta cike da tambaya a idonta.
"Meye?"
"Anan zaku tare!"
"Kamarya?"
"Yes ' Abba yasa a gyara muku d'ayan part d'in nan."
Nan Fadwa tayi shuru nad'an lokaci sannan tace.
"Koshh!"
"Kosh kamarya ' ke wallahi don dai bakije kin duba bane, yafi wannan part
d'in kyau."
"Zan duba."
Abinda Fadwa ta iya cewa kenan ta shige bathroom, Ilham ta cigaba da karatun ta.
Umma ce ta shigo cikin d'akin nasu ta sami waje ta zauna sannan tace.
"Ina Fadwa?"
"Ta shiga bathroom."
"To dama Yayan kune Farook ' yace kuyi masa addua jirgin shi zai d'aga yau."
"Laaa Umma ' tun yau ya wuce d'in? Allah sarki Yaya Farook, aikam zamuyi ta
yimashi addu'a.
"Idan Fadwa ta fito ki sanar ita."
To kawai Ilham tace cike da murmushi ' sannan Umma ta bar d'akin.
Cikin d'an lokaci k'alilan Fadwa ta fito daga bathroom, Saida Ilham ta jira ta
idar da sallah tukunna.
"Fadwa kinsan kuwa Yaya Farook ya tafi?"
Wani abune ya cokari k'irjinta ta rasa ko menene, Cike da mamaki ta juyo ta
kalli Ilham.
"Ya tafifa kikace! Zuwa ina?"
"Bangladesh mana."
Nan gabanta ya sake fad'uwa, nan take hawaye suka fara yimata zarya a fuska.
"He left without even calling me! He left without telling me!! Ilham ki
fad'amin wasa kikeyi please."
Ilham tashi tayi tare da kamo hannunta suka zauna, Sannan Fadwa ta yaye hijab
d'in jikinta.
"Komai yai zafi ' to maganinsa Allah Fadwa, meyasa bazaki zama mai tawakkali
ba?"
"Ilham na yarda da k'addara kuma nina yarda cewa Yaya Farook ba mijina bane,
amma Ilham meyasa zai tafi bai fad'amin ba? Meyasa?"
Ilham sharewa Fadwa hawaye tayi ' cike da tausayawa."
"Is okay Fadwa ' ni banga abin kuka ba anan, may be yanada reason d'in yin
haka."
Kai kawai Fadwa ta daga mata ' alaman Eh.
"Hakane ' to yanzu kinsan me za'ayi Ilham? Mu tashi driver ya kaimu ' muje
musa a fara buga mana invitation card d'in, hope dai akwai abinci?"
"Eh akwai ' don naga bak'in nan sunyi kuma zaikai har dare."
Yawwa Fadwa tace ' sannan suka tashi tare da rufe jikinsu da gele, suka fita
wajen garage.
Anan suka iske Yaya Khaleel a zaune yana shan iska da waya a hannu ' baima lura
da suba, sannan suka nufi wajen driver kai tsaye.
"Yawwa don Allah taso zaka kaimu wani waje."
Cewar Ilham,
Cikin hanzari ya tashi ' rik'e da car-key a hannun shi, ga bud'e motar suka
shiga. Bayan shigar sune ' suka fad'a mashi inda zai kaisu.
Basu suka dawo gida ba ' sai wajen *7:30pm*, sakamakon tsayawan da sukayi aka
gama musu nan take.
Bayan driver yayi packing ne suka fito, Ilham ta farajin fargaban shiga gida.
"Wai don Allah miye haka kikeyi Ilham? Mun riga mun girma fa! Mu shiga kawai
ninasan abinda zan fad'a tunda dai ga invitation cards a hannun mu."
Haka nan dai Ilham ta yarda suka shiga cikin gida, shigar su parlor suka iske
Umma da Yaya Khaleel ' a zaune ya wani had'e rai.
Sallama sukayi a tare cike da ladabi.
"Sannu da gida Umma."
Cewar Fadwa,
Yawwa Umma tace ' sannan suka d'auki hanya zuwa d'akin cike da fiskewa 馃槑, Yaya
Khaleel ya tsaida su.
"Daga ina?"
Fadwa ce ta juyo cike da tsoro ' sannan ta koma wajen Umma ta zauna gamida nuna
mata invitation cards d'in.
"Umma ' kinga abinda ya tsaida mu nan, inba haka ba wallahi da tuntuni mun
dawo."
Murmushi kawai Umma tayi ' cike da fara'a tace.
"Amma ko kinyi dabara Fadwa ' za'aje a rabawa k'awaye kenan?"
"Eh Umma' da yake muna so muyi wani event ne (*KAMU*), shiyasa."
"To shikenan Allah ya kaimu."
"Ameen.!"
Abinne ya k'ufule Yaya Khaleel, cike da b'acin rai yace.
"Babu wanda zai had'a wani party a gidan nan, Walima kawai za'ayi."
Salati Fadwa ta shiga a cikin zuciyarta ' suka had'a ido da Ilham.
"A'a bazaka hanasu yiba Khaleel, kaidai idan bakkada ra'ayi shikenan ' amma
su zasuyi."
Cewar Umma,
Yaya Khaleel ' tashi yayi tare da cewa.
"Umma ke kike goya masu baya ' suna raina mutum."
Sannan yasa kai zai fita waje ' Umma ta tsaida shi.
"Ina zakaje? Ko ina zakaje aikabari kaci abinci ko ' kafin ka fita."
"A'a Umma ' akwai wacc..infact ma a restaurant zanci a binci."
"Toh ai shikenan."
Abinda Umma tace kenan ' sannan yasa kai ya fita, ita kuwa Fadwa a zuciyar ta cewa.
"Ahab! Wajen wannan ballagazar zaije ' wai ita Lubna."
Tana gama ayyana hakan ta mik'e tsaye da niyyar wucewa, Umma tace.
"Fadwa ki kawomin abinci inci ' na farajin yinwa."
To tace sannan sannan ' ta yaye gelenta ta mik'awa Ilham tare da Invitation
cards d'in.
"Don Allah wucemin dasu d'aki, ni bara inzarce kitchen kawai."
Ehem ' Ilham tace sannan ta karb'a ta wuce dasu d'aki ita kuma ta shige kitchen.

*** *** *** *** ***

A kwana a tashi ' gashi yau saura kwana d'aya kacal, bikin *Fadwa&Yaya Khaleel*.
Fadwa ce ke zaune a parlor ' tare da mai lallee, k'awaye zagaye da ita ' Ilhan
kuwa tana gefe tana video Covering d'inta.
K'awaye ko wacenta da shirinta tazo ' don kuwa *Around 4-5:00pm* za'a tafi KAMU.
Haka aka gyara Fadwa ' tayi kyau sosai, sannan Ilham ta kira makeup artist ta
zo taimasu kwalliya ta gani ta fad'a.

*4:00pm*

Lokacin tafiya wajen kamu yayi ' har wasu daga cikin k'awayen sun fara tafiya,
Fadwa ta tashi ta nufi d'akin Yaya Khaleel.
Bud'e k'ofar tayi without any tension, ta shiga tare da yin sallama ya amsa ba
tare da ya kalleta ba ' ganin shi tayi daga shi sai singlet sai boxer.
Fadwa tsayawa tayi daidai wajen k'ofa ' ita bata k'arasa cikin d'akin ba ta
sunkuyar da kanta k'asa tana wasa da y'an yatsunta.
Jin shurun yayi yawa ne yasa ya d'ago kai ya kalleta ' Wow ya furta a cikin
ranshi don ba k'aramin kyau tayi.
"Lafiya?"
"Yaya Khaleel ' dama lokacin tafiya wajen kamu d'in ne yayi, ti shine...."
Ya dakatar da ita cikin fad'a,.
"Karma ki k'arasa, angaya miki banda aikin yine?
Nan k'walla ta ciko mata cikin idanuwan ta.
"Yaya Khaleel please!!"
"Fitarmun daga d'aki please hutawa nakeson yi."
Juyawa tayi ' ta fita ba tare da tace komai ba, turo mashi k'ofa tayi sannan ta
share hawayen ta ' ta wuce d'aki.
Yaya Khaleel murmushi yayi har saida hak'aran shi biyu suka fito.
Sannan ya fad'a bathroom don yin wanka.

*Dedicated To My Fan's*
馃槣馃槣馃槣馃挭
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*49-50*

Bayan ta shiga d'akine ta iske Ilham da wata cikin k'awayen nata ita kawai suke
jira.
"Yawwa sai muzo mu tafi ko?"
Cewar Ilham,
Nan suka sanyawa Fadwa mayafinta mai kama da net, sannan suka fito wajen garage '
dangi da y'an uwa kowa idon shi na kanta.
Haka suka shige mota driver yaja ' suka tafi, Ilham kuwa sai aukin d'aukan
hotuna take kamar ba gobe.
"Wai ke baki gajiya ne Ilham?"
"Tab ya za'ayi nagaji da d'aukar amarya hoto? K'awata, y'ar uwata, bugu da
k'ari ma matar Yaya na!"
Smilling kawai Fadwa tayi gami da girgiza kai.
"Yawwa Fadwa ' kinsan gudun mawarda Abba ya bada kuwa?"
"A'a."
"Tow Abba ' ya zuba securities a wajen, sai wanda aka gayyata zai shiga
wajen."
"Wow, gaskiya naji dad'i kuma ina yiwa Abba godiya sosai."
Suna cikin hakan ne aka isa wajen ' babban fili ne ankewaye shi da decoration
gunun ban sha'awa, sannan suka fito daga mota suka k'arasa ciki.
Haka aka kunna wak'a kala kala k'awaye suka kewaye Fadwa, ita kuwa babu abinda
takeyi sai fara'a. Wuri yayi wuri ' Fadwa sai tashewa takeyi cikin k'awaye tare da
Ilham.
Suna cikin hakane ' Yaya Khaleel ya iso wajen dashi da ayarinshi maza, Yayi kyau
sosai cikin milk d'in shadda da hula k'ube.
Fadwa sauke idon ta tayi akan shi ' mamaki ya lullub'e ta, haka ya k'araso
tsakiyar filin ba tare da yaje ya zauna ba ya rik'o hannun ta, nan kid'i ya cenja
salo ' haka Yaya Khaleel ya rik'a juya Fadwa son ranshi, rawa sukayi sosai irin
rawar turawa.
Ita kanta Fadwa abin ya burgeta ' da yadda suka burge mutane, Ilham kunyace ta
lullub'e ta yasa taja gefe ta koma ta zauna aka bawa Amarya da Ango fili.
Zamanta keda wuya ' taga kiran Al'ameen d'in ta ya shigo cikin wayar, haka yasa
ta mik'e ta matsa daga wajen tayi recieving call d'in.
"Hello!"
"My beauty kizo ki shigo dani ' ina inda kuke event d'in yanzu."
"To"
Kawai ta ce mashi sannan ta kashe wayar.
"To waye ya fad'a mashi muna nan?"
Abinda tace kenan ta tashi ta fita domin shigowa dashi.
Tana kaiwa bakin gate d'in taja burki ta tsaya cak.
"Wow!!"
Ta furta a hankali cike da k'are mashi kallo, Al'ameen k'arasowa yayi kusa da ita
gami da hura mata iska a ido ' tayi firgigit ta dawo hayyacin.
"My beauty wannan kallo haka?"
Murmushi kawai tayi mashi ' sannan suka koma ciki suka zauna.
Ango da Amarya sunyi rawa kamar ba gobe ' saida suka gaji sannan suka koma suka
zauna, aka fara basu hannun.
Anfara shirye shiryen rufe wajen ne ' Ilham taja hannun Al'ameen suka keb'e.
"Inaso muyi magana."
"Okay."
"My dear kaje ka sami Abba kuwa?"
Murmushi kawai yayi mata sannan ya juya zai wuce ' ba tare da yace komai ba
tayi saurin rik'e mashi hannu.
"Kafad'amun."
Juyowa yayi ya kalleta gami da kashe mata ido d'aya.
"Karki damu, gwada ki kawai nayi ' naje kuma mun gama magana, Insha Allah nan
da 1month za'ayi bikin mu."
Ajiyar zuciyar tayi tare da yin murmushi kad'an.
"Alhamdulillah!"
Ta fad'a sannan suka koma wajen hole d'in, gani sukayi duk an watse babu kowa sai
masu gadi.
"Don't worry, muje in maidaki gida."
Abinda taji ya fad'a kenan tabi bayanshi suka shiga mota ' suka bar wajen.

*Around 5:56pm dot*

Suka isa gida ' saida sukayi sallama da Al'ameen sannan Ilham ta shige cikin
gida.
Yau ma kamar jiya ' don kuwa mutane ne mak'il a cikin parlon, cikin su kuwa
harda masu kwana.
Saida ta gaishe su tukunna ta nufi d'akin su, k'awaye uku ne a d'akin wad'anda
sukazo da niyyar kwana, Ilham waje ta samu ta zauna tare da masu ban gajiya ' saiga
Fadwa ta fito daga bathroom d'aure da towel a jikinta rik'e da k'aramin towel tana
goge gashin kanta da alama wanka tayi.
"Ilham ' ina kika shiga ne d'azun mukaita neman ki babu ke?"
Harara Ilham ta watsa mata ' tare da fincike d'ankwalin kanta ta aje agefe.
"Kaji ta! To ina zanje kuwa? Meyasa to baki jira ni ba?"
Ya tsine baki Fadwa tayi sannan ta wullar da towel d'in hannun ta saman gado.
"Dad'in abun madai Yaya Khaleel ne yace a tafi a barki."
"Ahh 馃槷! Masu miji kenan! Nima ai nakusa yin nawa!"
Nan gaba d'ayan su suka hau dariya, sannan Ilham ta mik'awa k'awayen nasu Camera
d'in don suyi kallo ' itama ta tashi ta fad'a bathroom donyin wanka.
B'angaren Yaya Khaleel kuwa ' sanye yake da towel shima, da alamun daga wanka
ya fito direct wajen wardrope d'inshi ya nufa da niyyar ciro k'ana nan kaya wayar
shi tafara ringing.
Zuwa yayi ya duba ' sai yaga Lubna ce cike da murmushi ya d'aga wayar.
"Hello babe how far?"
"Don't baby me please ' Khaleel meka d'aukeni? Me kakeso ka mayar dani? Duk da
baka gayyace ni zuwa event d'inka ba amma ai ankawomin video d'in har gida."
"Wait let me explain!"
Ya fad'a tare da samun waje ya zauna.
"Explain what? Don Allah bana sonji Khaleel ' har kana wani mak'ale mata kana
sunsunar wuyanta, for godsake what is all this? Ko kanaso ka cemin duk tsanar ce
wannan?"
"Lubna ki fahimce ni mana! Just inayi mata haka ne saboda yau ranar tane ' and
she deserves to be happy."
"To ni kuma fa?"
"Please ki bari zamuyi magana zuwa anjima ' kar kisa komai a zuciyan ki,
because ke da ita akwai banbanci yanzu."
Nan ya kashe wayar ba tare da ya tsaya yaji abinda zatace ba, Lubna shuru tayi
ta tsaya tana kallon wayar cike da mamaki.
"Me kake nufi da ' nida ita akwai banbanci? Kanaso ka cemin ita matar sunna
ce ni kuma ballagaza?, hmm lallai sunana kawai kakeji Lubna ' zan baka mamaki."
Yaya Khaleel k'ana nan kaya ya saka ajikin shi gami da d'aukan Car-key d'inshi
ya fice.
Kai tsaye ya nufi hotel ' ya kama d'aki sannan ya shiga ya zauna a bakin gado,
wayar shi ya zaro cikin aljihun wandon shi yayi dailing number d'in Lubna.
Ringing biyu tayi Lubna ta d'aga.
"I thought bazaka sake kirana ba!"
"Ba wannan na tambaye ki ba ' kizo yanzu hotel d'inda muka saba had'uwa, i
want us to spend a night together."
"馃槷 What!?"
Cike da mamaki take magana tana kallon wayar.
"Kinji abinda na fad'a ai ' so am waiting for you!"
Ajiyar zuciya tayi ' sannan tace.
"To."
Ta kashe wayar ' ta saka cikin handbag d'inta tare da ciro kayan baccin ta ta saka
a ciki, Lubna yafa gele tayi sannan ta fito parlor ' ganin babu kowa ne yasa ta
ajiyar zuciya sannan ta fice taja motar ta zuwa hotel.
B'angaren su Fadwa kuwa ' bayan fitowar Ilham daga wanka ne sukayi shirin bacci
cikin kayan bacci, sannan suka kwanta.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槏
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*51-52*

*Washe gari*
Asuban fari Yaya Khaleel ya tashi daga bacci ' rungume da Lubna a hannun shi, zame
jikin shi yayi a hankali ya fad'a bathroom donyin wanka.
Koda ya fito ya isketa a zaune ' harta tashi hannun ta akan waya.
"Kin tashi da wuri!."
Abunda ya fad'a kenan yana k'ok'arin sanya riga a jikin shi
"Eh wallahi my Love ' duk wahalar da ka bani ainayi k'ok'ari ko?"
"Yes kinyi k'ok'ari atleast ke ba ragguwa bace!."
Dariya ta d'an saki kad'an sannan ta sauko ta rungume shi.
"Please My Love ' karka tafi yanzu kad'an tsaya, akwai sauran lokaci."
"What! Yaufa za'aimun aure kinga kuwa yau ranata ce, dole zan nutsu."
Nan ta sakeshi daga rungumar da tayi mashi ' cikin b'acin rai ta koma ta zaune
tare da calming hannun ta.
Yaya Khaleel ' murmushi kawai yayi mata, saida ya gama shiryawa tukunna yayi
pecking d'inta a chick d'in ta sannan ya fice alamar gida ya wuce.
Tsaki Lubna taja mai sauti ' tare da buga k'afarta k'asa.
"Wannan yarinyar kina shiga mun hanci ' two days."
Nan ta tashi itama ta fara had'a kayanta da suka watse a k'asa, Ta sanyasu a
cikin handbag d'inta sannan ta fita tabar hotel d'in zuwa gida.
Yaya Khaleel yana isa yayiwa mai gadi hone ' domin ya bud'e mashi, Bayan ya
shigar da motar shi cikine ya fito zai shiga gida mai gadin ya tsaida shi da cewa.
"Yallab'ai tafiya kayi ko? Don da alamun ba'a gida ka kwana ba."
A fusace Yaya Khaleel ya dawo ya fuskance shi, cikin fushi yace.
"Non of your business malam ' ba abinda ya dameka bane wannan."
Yana fad'in haka ya juya ya shige cikin gida, Koda ya ratsa cikin parlor babu
kowa ' don da alamun babu wanda ya tashi bacci.
Haka Yaya Khaleel ' ya shige d'akin shi ya sanya key, d'auko diary d'inshi yayi
ya nufi kitchen ' yasa mashi wuta. Yaya Khaleel na tsaye saidaya tabbatar komai ya
k'one tukunna ya bar kitchen d'in ya koma d'akin shi ya kwanta, Wani wahalallan
bacci ne ya d'aushi.
Lubna bayan ta kai gida ne ' tayi packing sannan ta shiga ciki, a zaune ta iske
Mummy da alamun jirar dawo warta takeyi. Lubna tana ganin haka ta had'iye miyau
daker, wata zuciyar tace.
"Aiki shiga kawai kinsan babu abinda za'a miki so kici duniyarki da tsinke
kawai."
Nan ta k'arasa cikin harabar parlon, ta nufi d'akin ta Mummy ta dakatar da ita.
"Daughter daga ina kike?"
Lubna dawowa parlon tayi ta zauna.
"Hm... Mummy wata friend d'ita ce ' jirginta ya sauka d'azun a round 4:00am,
to shine ta kira awaya inzo in taimaka mata ' bak'uwa ce batasan ko inaba."
"Kinyi k'ok'ari Lubna ' to ina k'awar taki?"
"Hotel ta kama saboda tazo bikin wata k'awar mu ne."
Kai Mummy ta d'aga sannan Lubna ta tashi ta shiga d'akinta gami da dafe k'irjin
ta.

*** *** *** *** *** ***


*AROUND 8:30AM*
Su Fadwa suka tashi bacci cike da mik'a, d'aya daga cikin k'awayen ne tashiga
bathroom donyin wanka.
"Yau Amarya ita ce k'arshen wanka a d'akin nan."
Cewar Ilham,
"Nidai Ilham kamar a d'aga bikin nan nakeji ' jikina yana bani zansha
wahalar aure!!!."
Ilham jitayi kamar an buga mata dutse a k'irjinta.
"What!? What are you trying to say? Fadwa kin bani mamaki fad'amun hakan da
kikayi!, ban kuma tab'a zato ba!"
Cikin fushi Ilham tayi maganar.
D'aya daga cikin k'awayen ne ta d'an dafa kafad'an ta.
"Kiyi hak'uri Fadwa ai komai nufine na Allah, balle ma ke! Aikowa yasan cewa
kinyi dacen miji."
Hawaye ne yafara yiwa Fadwa zarya a idanun ta, Ta tashi taje kusa da Ilham
wacce ta juya banta ' tana fuskanta mirrow.
Hannu Fadwa tasa ta juyo da ita suka had'a ido, ganin hawayen da ke fuskar Fadwa
ne ya d'agawa Ilham hankali.
"Ilham ke y'ar uwata ce kuma dukda ' a cikin *BABBAN GIDA* zan tare still
inaji kamar zan rasa wani b'an gare na jikina, Ilham idan na wuce d'akina nan
d'akin zai miki fad'i zaki waiga kiga ke kad'ai ce babu ni!!... zaki..."
Bata k'arasa ba Ilham ta fashe da kuka, tare rungume junan su ' k'awayen su
suma kansu abun tausayi ya basu.
"Bazan tab'a bari wani abu ya cutar dake ba Fadwa, ni takice har kullum."
Ajiyan zuciya dukkan su suka sauke ' sannan wacce ta shiga wanka ta fito.
"Yawwa aiko yanzu zan shiga ' don so nake in rigaki wanka."
Cewar Ilham,

*** *** *** *** ***

*Wajen k'arfe 10:56am*


Su Fadwa ko wannen su yayi wanka ' amma babu wanda ya shirya cikin su, Don kuwa
sai wajen 1:00pm za'a d'aura aure a babban masallacin da ke layin.
"Kaii haba ninasan da walaki! Ashe bamu karyaba shiyasa naji cikina na
zafi."
Cewar Ilham,
"Ilham ki dafa mana indomie mana ' zaifi rik'e ciki."
Inji Fadwa.
Suna cikin hakane ' saiga Umma ta shigo dakin, Dukkan su gaisheta sukayi cike da
ladabi.
"Fadwa kun karya kuwa?"
"A'a Umma amma yanzu Ilham zataje ta dafa mana Indomie."
"Yawwa gara dai a hanzarta."
Fita Umma tayi daga d'akin ta basu wajen.
"Yawwa Ilham please ki dafa da Yaya Khaleel ' nasan babu abinda yaci kuma
kinsan yanada Ulcer."
"To naji."
Abinda Ilham ta fad'a kenan ta nufi kitchen.
Bayan wucewar Ilham ne Umma ta dawo cikin d'akin rik'e da robar youghout a
hannun ta amma sai dai ba youghout d'in bane a ciki , wani abunne dabam.
"Fadwa karb'a wannan inaso ki shanye shi tas, bayan kinci abinci ' kuma ki
kawomin robar d'aki."
Fadwa karb'a tayi sannan ta maida kallon ta kan Umma.
"Umma miye wannan?"
"Banason tambayoyi ' zan baki abunda zai kashe kine? To kisha tsumi ne zai
k'ara miki kuzari ne."
To kawai Fadwa tace ' sannan Umma ta juya ta fita, tana fita Fadwa ta ajiye
robar a k'asa.
"Ni aiba saina sha tsumi ba! Ahaka na inada kuzari ai."
D'aya daga cikin k'awayen ne tace.
"Kai Fadwa ashe haryanzu kina nan da rashin jin ki! To wallahi saikin shashi
' ai tunda kikaga ta baki to yanada amfani, kuma ai bata tab'a baki ba sai yau
saboda haka kisha kawai ' inba haka ba wallahi yanzun nan inje kiran ta."
"Ke! Rufamin asiri ' to naji zansha amma ai saina ci abinci ."
Suna cikin hakane Ilham ta shigo d'akin rik'e da plates dai cooler a hannun ta,
sai da ta aje sannan ta zubawa kowa nashi.
"Kin kaiwa Yaya Khaleel nashi ne?
Cewar Fadwa,
"Ke kinfa fara isata ' saikace akanki aka fara yin miji! Na kaimashi mana."
Murmushi Fadwa tayi sannan suka fara breakfast ' bayan ta gama ne ta d'auki abunda
Umma ta bata ta shanye tass ta wullar da robar.
"Meye wannan?
Ilham tayi tambayar,
"Umma ce ta bani ' tace in shanye tass zai k'aramin kuzari."
Okay kawai Ilham tace sannan ta d'aga kai ta dubi agoge.
"Shikenan wata ta kusa zama matar aure ' yanzu k'arfe 12:57pm."
Harara Fadwa ta watsa mata ' tukunna suka fara haramar gyara jikinsu.
Yaya Khaleel kuwa shiri yayi cikin fararen kaya shadda ' yayi kyau sosai,
Abokanan shine suka dame shi da kira ' hakan yasa ya fita zuwa Babban masallaci.
Zuwa yayi ya iske mutane mak'il a wajen abokan Abba da abokan shi ' suka cika
wajen gunun sha'awa, Wakilan Ango dana Amarya duk sun hallara a wajen.
*1:00pm dot*
Aka d'aura aure ' haka Abba ya kira Umma a waya ya sanar mata cewa aure ya d'auru.
Haka gidan ya cika da shewa da gud'a .
Nan cikin sauri su Ilham suka shirya Fadwa ' sannan wata tsohuwa daga cikin
dagin ta shigo d'akin.
"To kud'an bamu waje!"
Abinda ta fad'a kenan k'awayen suka bar d'akin, ita kuwa Ilham tana zaune ta kaso
kunnuwa.
Haka tsohuwan nan ta dunga yiwa Fadwa nasiha ' yi nayi bari na bari, Nasiha
sosai mai shiga jiki takewa Fadwa. Saida ta gama sannan ta tashi tare da cewa.
"Zaku iya kaita d'akin ta yanzu."
Abinda ta fad'a kenan ' Ilham tahau gud'a, da gudu k'awayen suka shigo d'akin
suma suka d'au gud'a.

*** *** *** *** ***

Haka y'an uwa da k'awaye suka yiwa Fadwa rakiya zuwa d'akin ta Ilham ce kan gaba,
Saida suka kaita bedroom d'inta sannan suka ajeta a saman gado ' suka juyo.
Aka barta daga ita sai Ilham sai k'awayen ta.
B'angaren Yaya Khaleel kuwa ' Yana tare da abokan shi sai murna ake tayashi.
*Dedicated To Sadnaf*
馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*53-54*

*AROUND 4:00PM*
Yaya Khaleel ya dawo gida ya iske duk mutane sun watse ' sai wata y'ar tsohuwa
wacce ta manyan ta zaune a parlor.
kai tsaye ya wuce sashen shi ya cire babban rigarshi, sannan ya fito parlor
suka had'e da Umma wacce dama shi take jira.
"Khaleel daga ina?"
"Amm Umma yanzu nake dawo wa ' daga wajen abokai na, zanje sashe na.."
Ya fad'a yana sosa k'eya.
"Ai indai da kunya to anjita.
Cewar tsohuwar da ke zaune a wajen, Yaya Khaleel juyawa yayi ya kalleta ' sannan ya
maida kallon shi kan Umma.
"Umma wannan wacece kuma?"
"Sunan ta Ige ' akwai wasa a tsakanin ku, zata cigaba da zama damu ne anan '
tana d'an taya Ilham aikin da ba'a rasa ba."
Ok kawai Yaya Khaleel ya ce ' sannan yasa kai zai fita Umma ta dakatar dashi.
"Ina kuma zakaje? Bata tare da mun gama magana ba? Duk zumud'in ne haka?"
Murmushi kawai yayi.
"To kaje sashen Abban ku yana nemanka yanzun nan."
Kai tsaye Yaya Khaleel ya nufi sashen Abba ' a zaune ya hange shi saman kujera,
Yaya Khaleel sallama yayi sannan ya shiga.
Abban ya amsa cike da fara'a.
"Sami waje ka zauna!"
Yaya Khaleel k'asa ya zaune cike da ladabi.
"Khaleel ' Alhamdulillah yau aka d'aura auren ku da Fadwa kuma ina fatan zaka
rik'ayin adalci a tsakanin ku."
"Insha Allah Abba."
"Kuma inayi maka albishir da cewa ' na bud'e maka company naka na kanka, domin
ka rik'a sarrafawa."
Yaya Khaleel bud'e baki yayi yana kallon Abba ' cike da mamaki.
"Kuma na sama maka ma aikata ' wad'an da zasu rik'a aiki a k'ark'ashin ka
yanzu kana zuwa sai dai ka hau aiki, Amma gobe insha Allah zan kaika domin ka ga
wajen."
Wani ihu Yaya Khaleel ya saki mai kama da kuka ' ya tashi ya rungume Abba cike da
jin dad'i.
"Abba na gode ' na gode sosai Abba ban tab'a jin dad'i irin na yau ba Abba."
"To sakeni mana Khaleel ' so kake ka k'arasa ni?"
Cikin sanyin jiki Yaya Khaleel ya koma ya zauna.
"Yanzu ka tashi kaje ' dama kiran kenan!"
"To shikenan Abba na gode ' Allah ya kaimu goben."
Ameen Abba ya ce ' sannan Yaya Khaleel ya tashi ya fita, Parlor ya shigo d'auke
da fara'a a fuskar shi zai wuce Umma ta tsaida shi.
"Ina zakaje?"
"Umma zanyi packing kaya na ne ' zuwa gidana!"
"Yayi kyau masu gida!!!"
Harya juya zai wuce Ige ta tsaida shi da cewa.
"D'an samari naga kana ta fara'a ne! D'an fesa mun inji me aka samo mana."
"Company Abba na ya bud'emun."
"Ohh shi dama kanunfarin bud'e shi akeyi?"
"Hahaha! Kinga illar zama a k'auye kenan, ki tambayi Umma ta fad'a miki ' ni
inada abunyi."
Wuce wa yayi ya kyaleta ita da Umma ' tana ta k'ok'arin fahimtar da ita.
Bayan ya d'auko trolley d'in shi da duk wani abu nashine ya nufi part d'inshi.
Karo yaci da k'awayen Amarya zasu koma gida.
"Haba kardai har zaku koma!"
Dariya sukayi dukkansu sannan d'aya daga ciki tace.
"Ango kenan kasha mai ' to ai mun dad'e anan kuma kai kawai Amarya take jira."
Murmushi kawai yayi sannan ya kira driver d'in gidan ya umarce shi ya kaisu gida.
Godiya sukayi mashi sannan ya shige cikin gidan shi, D'akin shi ya fara shiga '
ya ajiye kayan shi sannan ya nufi d'akin da Fadwa take.
Suna cikin hira ne da Ilham sukaji anyi gyaran murya ' hakan yasa Fadwa tayi
saurin maida gelenta ya rufe mata fuskar ta.
Yaya Khaleel k'araso wa yayi cikin d'akin fuska a d'aure sannan Ilham ta tashi
' ta fita cikin sauri ta wuce sashen su.
Ita kuwa Fadwa gabanta dukan uku uku kawai ya keyi ' saboda tsabar fargaba.
Yaya Khaleel gefen gadon ya zauna ' ya na kallon irin kyan da tayi cikin gele,
Hannu yasa ya yaye gelen ya cigaba da k'are mata kallon. K'ara matsowa yayi kusa da
ita yana k'ok'arin sunsunar wuyan ta, tayi saurin matsawa.
"Me hakan ke nufi?"
Banza tayi ta kyaleshi ' abun yayi matuk'ar b'ata mashi rai sosai, tashi yayi fita
daga d'akin ta bishi da kallo.
Parlor ya je ya zauna ' ya kunna TV ya na kallo, Haka Fadwa ta k'araci zaman ta
a d'aki ita kad'ai har aka kira sallar magrib ta tashi ta cire mayafin ta ' ta
shiga bathroom.
D'auro alwalar ta tayi ' ta shinfid'a dadduma ta fara sallah, Yaya Khaleel
shima tashi yayi ya shiga d'akin shi don yin sallah.
Bayan Fadwa ta idar da sallah ne ' ta koma ta zauna a kujerar d'akin Sofa, ji
tayi gaba d'aya batajin dad'in zama ita kad'ai hakan yasa ta tashi ta nufi parlor
da niyyar fita zuwa sashen su Umma.
Suka had'e da Yaya Khaleel zai shigo cikin d'akin, tsayawa cak yayi yana kallon
ta yadda surar jikinta suka bayya.
"Ina zakije?"
"Ammm Yaya Khaleel dama inaso ne inje wajen Ilham in karb'a phone d'ina."
"What!? Phone? Saboda ke dama kunya bata ishe ki ba ko? Yau yau da tarewar ki
' zaki kama hanyar yawo ko?"
Nan ta sunkuyar da kai ' ba tare da tace komai ba, Sannan ya matso kusa da ita.
"Bazaki fita ko nan da cen ba ' har sai nan da 2weeks, kuma babu mai shigowa
ya katse mun jin dad'i."
D'ago kai tayi ta kalle shi ' da y'ar kwallar ta a cikin ido.
"Yaya Khaleel please ' wallahi bazan iya zama ni kad'ai ba shiyasa."
"Nidai kinji abinda na fad'a miki."
Nan ya juya ya wuce parlor ' yayi zaman shi.
Koma wa cikin d'akin tayi zata cire kayan jikinta ta shiga wanka ' taji sallamar
Ilham, Abinci ta kawo musu cikin plask Yaya Khaleel ya ansa sannan ya umarce ta
data koma inda ta fito ' da gudu Fadwa ta nufo parlon.
Ta na isa taja burki ta tsaya ' ganin babu Ilham a wajen sai Yaya Khaleel wanda
ke rik'e da plask d'in abincin ya na kallon ta.
"Yaya kamar naji muryar Ilham ko?"
"Na ce ta koma inda ta fito! Wata matsala ce?"
Tsayawa kawai tayi tana mashi kallon mugu ' sannan ta ce.
"A'a."
Ta juya ta koma d'aki, ta hau cire kayan jikin ta sannan ta d'aura towel ta shiga
wanka.
Tana cikin wanka ne ' taji an bangad'o k'ofar bathroom d'in, cikin tashin
hankali da tsoro Fadwa ta rarumi towel ta rufe k'irjinta k'ok'ari take ta d'aura
amma jikinta rawa kawai yake yi.
Yaya Khaleel cak ya tsaya a bakin k'ofar yana k'arema jikinta kallo ' ita kuwa
babu abin jikin ta keyi sai rawa.
Sai da suka kwashe 5minutes a haka ' sannan ya juya ya rufo mata k'ofa ya koma
gefen gado ya zauna ' yana sauke ajiyar zuciya.
Ji yayi tana shek'a ruwa a jikinta alaman tana gab da fitowa ' haka yasa yayi
saurin bud'e wardrope d'inta ya ciro mata wasu fitinan nun sleeping gown shara
shara ya ajiye mata su saman gado sannan ya bar d'akin.

*Dedicated To Seemaluv's Novel Group*馃憣馃憣


*_Love you Gurls So Much_*
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*_@JAMEESHA! JAMEESHA!! JAMEESHA!!!, Hmm I Just Want All My Followers ' To Know
That This Name Means A lot To Me, And The Person Own The Name Means Everything To
Me. My Sweet JAMEESHA have a Wonderfull 馃憣馃憣 day!!!_*

*55-56*

Bayan ta gama wanka ne jikinta na d'ar d'ar d'in fitowa, Saboda sam ita bata son
su had'a ido da Yaya Khaleel ko kad'an.
Haka nan ta bud'o k'ofa ta lek'o gani tayi babu kowa a d'akin hakan yasa ta
sauke ajiyar zuciya ta fito daga bathroom d'in, Bata tsaya ko ina ba sai gaban
mirror ta zauna ' ta fara gogawa jikinta turaruka kala kala masu k'amshi.
Bayan ta gama ne ta nufi wardrope ' ta d'auki rigar bacci mai d'an kauri riga
da wando ta sanya, Sannan ta d'auki dogon hijab d'inta ta saka a jikin ta ' ta nufi
parlor da niyyar cin abinci.
A zaune ta hangi Yaya Khaleel a dinning table yana kallon shi ' da alama ita
yake jira, Cike da sallama ta k'arasa wajen ' Yaya Khaleel juyowa yayi ya kalleta
tare da amsawa, Ganin hijab d'in da ta kima ne yasa shi b'ata rai gami da maida
kallon shi a TV.
Bayan ta zauna ne zata zuba masu abinci ' ya watsa mata wani mugun kallo hakan
yasa tayi saurin sunkuyar da kanta k'asa tare da barin abincin.
"Cire min hijab d'in jikin ki!!"
D'ago kai tayi da sauri ta kalle shi.
"Au irin ban isa d'in nan ba ko?"
Ta girgiza kai.
"To ki cire mun hijab d'in jikin ki right now ' don ba wasa nakeyi da ke ba."
Mik'ewa tsaye tayi ta yaye hijab d'in ta barshi daidai wuyan ta. .
"Ba kiji abinda nace ba ko?"
Da sauri ta aje gefe tare da maida kallon ta zuwa k'asa.
"Damn it!, Kin raina ni ko?"
Ta girgiza mashi kai.
"Bakiga gown d'in da na ciro miki bane?"
"Yaya Khaleel wallahi ban gani ba."
"Kije tana nan saman gadon ki ' ki d'auka ki sa yanzun nan 5minutes na baki."
Cikin hanzari ta d'auki hijab d'inta ta wuce d'aki kai tsaye saman gadon ta
nufa, Nan ta hau cire kayan ta ' sannan ta d'auki sleeping gown d'in ta saka a
jikin ta.
Fadwa wajen madubi ta je ta tsaya ' tana kallon kanta.
"Tabdijam! Never in history! Wannan rigarce Yaya Khaleel zaice insa? Me ya
d'aukeni to ' nasan ba wani abu bane amma gaskiya bazan iya sa rigar nan ba ' komai
na jikina ya bayyana babu abinda ya b'oye , aiko abincin ma na hak'uri dama ba wani
yunwa nakeji ba!!"
Zuwa tayi ta sa key a k'ofar ta sannan ta haye gado tayi kwanciyar ta da rigar
a jikin ta.
Yaya Khaleel kuwa sai agogo yake kallo ' don ta haura lokacin da ya bata, Shuru
yaji har yanzu ba zo ba.
"Lallai yarinyar nan ' ni zaki mayar d'an iska! Zanyi maganin stubborness d'in
ki kuwa.!"
Zuba abinci yayi ' yaci sannan ya kashe kayan kallon ya wuce d'akin shi, Shirin
bacci yayi cikin singlet da boxer ya kwanta ' tare da d'aga pillow ya d'auko wayar
shi, Yayi dialing number d'in Lubna yaji switch-up ' nan yayi wulli da wayar gefen
shi.

*AROUND 12:30AM*

Dukkan su babu wanda yayi bacci ' Yaya Khaleel juyi kawai yake yi saman gado sam ya
kasa runtsawa, Tabbas yasan yana da buk'atar Fadwa a kusa dashi.
Fadwa itama kasa bacci tayi ' kasan cewar bata saba bacci ita kad'ai ba, tsoro
ne ya lullub'eta ga uban yinwa data dame ta ' babu arzik'i ta sauko daga gado ta
nufi parlor cike da tsoro, Plask d'in abincin ta gani a saman dinning table ' nan
ta k'arasa wajen cikin hanzari ta bud'e abincin ta fara ci a yunwace.
Bayan ta gama ne ta fara tunanin yadda za'a yi ta kwanta ita kad'ai a d'aki,
Mik'ewa tayi ta fara neman inda d'akin Yaya Khaleel ' wani d'aki ta murd'a taji a
bud'e haka yasa ta shiga ciki kai tsaye.
Duhu Fadwa ta gani kasan cewar wutar d'akin a kashe take, Cikin duhu ta dinga
lalube harta cinma gado ta haye ' Yaya Khaleel yana jin hawowar ta yayi shuru yaga
iya gudun ruwan ta.
Bayan ta hau saman gadon ne ' ta ja blanket d'in da yake lullub'e dashi ba tare
da ta sani ba, Yaya Khaleel yana jin haka ya sa hannu daidai saman kanshi ya kunna
wutar d'akin.
Fadwa sai ganin haske tayi fauu ' tashi tayi ta zauna cike da tsoro suka had'o
da Yaya Khaleel.
"Ke lafiya? Me kika zo yi a d'aki na?"
Yana maganar ya na kallon jikin ta ' ita kuwa ta ma manta kalar rigar da ke
jikin ta saboda tsabar tsoro, Jin tayi shuru ne yasa shi janye blanket d'in shi da
k'arfi.
"Oya! Fita mun a d'aki, Ko bakida naki ne?"
"Ina dashi..."
tayi maganar a sanyaye.
"To tafi d'akin ki, Ke zafin nan ma ko damun ki bayayi?"
"Yaya Khaleel don Allah ka barni in kwanta a nan! Please...."
"To bari in bar miki d'akin sai in koma parlor."
Nan idon ta ya cicciko da hawaye.
"Please Yaya Khaleel wallahi tsoro nakeji ' bazan iya kwanciya ni kad'ai ba."
Sauka yayi tare da d'aukan blanket d'in zai fita tayi saurin rik'e mashi riga.
"Yaya Khaleel please..."
Dawo wa yayi ya zauna ' tare da yin nazari sannan ya kalleta.
"Shikenan ba damuwa zaki iya kwanciya."
Dad'i taji sosai ' tare da yin ajiyar zuciya sannan ta kwanta shima ya kwanta,
Fadwa runtse idon ta tayi gami da takure wa waje d'aya.
"Matso nan!"
Abinda taji ya ce kenan ' tayi banza dashi tamkar tana bacci..
"Bakiji ba ko? Shikenan tashi ki barmin d'aki na!"
Aiba shiri ta bud'e idon ta ' ta matsa inda yake.
"Ke wai da aljani kike kwance ne? Ki matso nace..."
Maganar ya k'arashe a sanyaye tamkar bashi ba, Bud'e ido tayi suna kallon juna '
ganin bata da niyyar yin abinda yace ne ' yasa shi janyo ta da hannun shi ya had'a
ta da jikin shi yana jin d'umin jikin ta.
Sannan ya rufa masu blanket ' ya kashe wutar d'akin.
"Kince kinajin tsoro ko?"
Fadwa wata sassanyar murya taji yayi amfani da ita ' hakan yasa ta cewa.
"Uhm."
"Meye kuma Uhm? Ki amsamin da kyau!"
"Eh inaji."
"To sa hannun ki biyu ' ki rungume ni.."
"Na'am?"
Ta sake tambaya ' tamkar bata ji abinda ya fad'a ba.
"Kinji abinda na fad'a ai, so do what i say!!"
Fadwa hannu tasa ta rungume shi ' don tasan cewa bata da wata mafita bayan
hakan, Yaya Khaleel rungume yayi sosai ' a haka bacci mai dad'i ya d'auke su.

*WASHE GARI!!!*
*_AROUND 8:00AM_*

Yaya Khaleel ' ya tashi daga bacci ' sauke idon shi yayi akan fuskar Fadwa ' wacce
baccin ta kawai takeyi hankalin ta a kwance, Zame jikin shi yayi a hankali sannan
ya yaye mata blanket d'in da ke jikin ta.
Yaya Khaleel sai da ya b'ata 5minutes yana kallon jikinta da irin rigar da ke
jikinta, Sannan ya sauka daga gadon ya shiga bathroom yayo alwala.
Bayan ya fito ne ' ya ciro jallabiya ya sanya tukunna yayi sallah, Sallame
warshi ce tayi daidai da farkawar Fadwa daga bacci ' jin ta tayi fayaya tamkar babu
kaya a jikin ta ' hakan yasa ta bud'e idon ta a hankali ba tare da tayi kyakkyawar
motsi ba.
Kallon jikin ta tayi ' sannan ta tuna da irin rigar da ke jikin ta, Wuf tayi
ta tashi zaune a tsorace ' ji tayi an mata magana kamar daga sama.
"Ki tashi kije d'akin ki kiyi sallah."
Kunya ce ta rufe ta ' tayi sauri ta janyo bargo ta rufe jikin ta, Fadwa sauko
wa tayi daga gadon a hankali zata wuce d'akin ta ya dakatar da ita.
"Ina zakije mun da blanket? Come on dawo ki aje mun abuna!"
Kwata kwata Fadwa jitayi bakin ta ya kulle ' babu abinda zata iya cewa, Haka ta
yaye blanket d'in daga jikinta ta ' ta cilla mashi saman gado sannan ta juya ta
wuce.

*_Kuyi hak'uri da wannan page d'in babu yawa, Don ba'a nan naso tsayawa ba kamawa
tayi!!!..._*

*_Dedicated To My One And Only JAMEESHA!!! ' She mean alot to me!!!..._*
馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me
*57-58*

Yaya Khaleel binta yayi da kallo har ta b'ulle zuwa d'aki, Bayan Fadwa ta shiga
d'aki ne ta fad'a bathroom tayo wanka tare da yin alwala ' sannan ta fito tayi
sallah , Mik'ewa tayi nufi gaban mirror ta zauna ta fara gyara jikin ta.
Bayan ta gama ne ta tashi ' ta bud'e wardrope d'in ta ta ciro riga da skirt
d'inki mai kyau ta saka a jikin ta gamida kashe d'auri, Tana cikin hakan ne taji
ana k'wank'awasa k'ofa ' cikin hanzari ta bar d'akin ta nufi parlor ta bud'e
k'ofar.
Ilham ce rik'e da kayan breakfast a hannun ta, Shigowa tayi cikin parlon cike
da sababi.
"Kinyi aure amma mutum bazai huta ba?"
Murmushi kawai Fadwa ta bita da shi ' sannan suka zauna Ilham ta mik'a mata
ledar da ke hannun ta.
"Gashi ' Milk ne da bread da sauran su aciki, inji Umma."
Mik'ewa Ilham tayi zata wuce Fadwa ta tsaida ita da cewa.
"Tsaya! Mu tafi tare ' ingaida Umma da Abba."
To kawai Ilham ta ce sannan suka fita zuwa sashen su Umma ' Ilham a parlor tayi
zaman ita da Ige sannan Fadwa ta haura wajen su Umma ta gaishe su.
Bayan ta gaishe su ne ' ta dawo parlor ta zauna sannan suka gaisa da Ige.
"Y'an nan harkin gama cin amarcin naki ne?"
Cewar Ige,
"Hmm me kika gani?"
"Gani nayi harkin fara fitowa!"
Nan ta sunkuyar da kai ' Ilham tashi tayi ta matsa kusa da Ige.
"Ai Ige ' daga gani babu wani amarcin da sukaci, Ige Yaya Khaleel fa bak'in
rai ne dashi wallahi."
Nan Ige tayi zuk'u tana kallon Fadwa.
"Y'an nan abinda Ilham ta fad'i gaskiya ne?"
Fadwa d'aga kai tayi alaman Eh, Sannan Ige ta sauke ajiyar zuciya.
"Lallai wannan shine daidai lokacin da ya dace tsarabar da nai miki ' ki fara
aiki da ita."
Nan Fadwa da Ilham suka had'a ido, A tare su kace.
"Kamarya?"
Ige ta bud'e baki kenan zatayi magana Abba ya shigo parlon ' cikin hanzari.
"Fadwa tashi kije ki cema Khaleel ' ko ya manta akwai inda zamuje yau ne!"
To tace ' sannan ta tashi ta bar sashen cikin sauri, Ta na shiga sashen su ta
iske shi a zaune a parlor cikin shadda blue yayi kyau sosai ' waje ta samu ta zauna
ba tare da ya d'aga kai ya kalle ta.
"Ina kwana Yaya Khaleel?"
"Lafiya!"
"Amm... sorry na d'anje sashen su Umma ne na gaishe su ' so shine Ige ta
tsareni."
Banza yayi ya kyale ta ' ya cigaba da kallon shi.
"Yaya Khaleel ' Abba ya ce na fad'a maka wai ko ka manta akwai inda zakuje
ne?"
Jan tsaki yayi kad'an sannan ya mik'e tsaye ya fice, Fadwa bin shi tayi da kallo.
Tashi tayi ta d'auki kayan tea d'in ta nufi dinning table da su, Sannan ta wuce
kitchen ta d'ebo ruwan zafi a plask ta ajiye ' nan ta zauna ta had'a nata tea d'in
ta na sha kafin ya dawo ta had'a mashi nashi.
Fadwa ta na cikin haka ne ' Ilham ta shigo rik'e da y'ar k'aramar kwalba a
hannun ta, Zama tayi tukunna Fadwa ta aje cup d'in tea d'in ta zo harabar parlor
kusa da Ilham ta zauna.
"Yaya Khaleel ya fita ko?"
Cewar Ilham.
"Eh."
"To ga wannan ' inji Ige."
Ta mik'a mata kwalbar turare ' Fadwa ta karb'a.
"Ta ce duk idan lokacin kwanciya bacci yayi ne ' zaki shafa shi kad'an a saman
k'irjin ki."
"To meye amfanin shi?"
"Oh my God! Nikam aida kin bari na gama bayani na ko?"
"Uhm! Shikenan ina jinki!"
"Yawwa, Bayan kin shafa shi ' to muddin yaji k'amshi turaren zaiji babu wacce
yake sha'awa saike, Gaba d'aya zaiyi sanyi ' zaiji babu wacce yake so kamar ki!"
Ajiyar zuciya Fadwa tayi ' tare da juya kwalbar turaren cike da tsoro.
"Amma Ilham ' ni gaskiya inajin tsoro fa!, Kinga ance ba k'aramar wuya mutum
ke sha ba ' kema kanki kinsani."
Wata harara Ilham ta watso wa Fadwa.
"Ke wai meye haka? Anaso a taimake ki ' kina wani butsarewa haba Fadwa."
"A'a nidai bana so ' karb'a ki maida mata abunta, A hakan nina son Yaya
Khaleel yana sona."
"Oh Allah? A hakan ko? Amma karki manta fa ' yana da budurwa a waje, Saboda
haka anan zan aje shi ' idan kinga dama kiyi amfani dashi ' idan kuma kinso ki
yar."
Nan Ilham ta tashi ta kama haryat fita ' har ta kai bakin k'ofa ta juyo ta kalle
Fadwa wacce ke ta nazari.
"Kuma banma sake shigowa sashen shi."
Fadwa murmushi kawai tayi ' sannan Ilham tayi wuce warta.
"Inma baki shigo ba ' aini zaki ganni ne ai."
Fadwa tashi tayi ta bar turaren anan wajen ta koma dinning table ta cigaba da
shan tea d'in ta.

*AROUND 12:00PM*

Yaya Khaleel suka dawo gida ' shi da Abba, Abba ya wuce ciki ' shi kuma ya shige
sashen shi, A zaune ya iske Fadwa ta na kallo TV.
Ganin shigowar shi ne ' yasa tayi saurin mik'ewa tare da yi mashi sannu da dawo
wa, Yaya Khaleel bayan ya zauna ne ' Fadwa ta je ta had'o mashi tea don tasan yau
kam ya wuni da yunwa.
"Yaya Khaleel ga tea d'inka ' kayi hak'uri ban had'a da wuri ba sabo..."
Bata kaiga k'arasawa ba ya katse ta da cewa.
"Banason dogon surutu plaese."
Karb'a yayi ' Fadwa ta koma ta zauna ' sama sama ya sha tea d'in tukunna ya aje
a k'asa, Sannan ya jingina da jikin kujera.
"Amm... Fadwa Abba ya bud'e mun Company, Kuma Alhamdulillah yau ya kaini
wajen na gani ' Amma sai nan da 1week zan fara aiki."
"Wow! Alhamdulillah! Yaya Khaleel gaskiya naji dad'i sosai kuma Allah yasa
rai a kaiwa."
Amin ya furta ' sannan ya tashi zai wuce d'aki tayi saurin tsaida dashi.
"Yaya Khaleel to yaushe zaka kaini inga wajen?"
Tayi maganar a shagwab'e cikin sanyin murya.
"Bazaki je ba!"
Nan ta tashi ido cike da k'walla.
"Yaya Khaleel ' inaso inga wajen ne please!"
"To shikenan naji ' kar kuma ki dameni!"
Ya na fad'in haka ya wucewar shi d'aki.
Fadwa koma wa tayi zauna ta cigaba da kallon ta.
A ranar haka Fadwa ta k'arashi wunin ta ' bata sashin su Umma bata sashen ta.

*** *** *** *** *** *** ***

*WAJEN K'ARFE 6:30 NA YAMMA*

Bayan Yaya Khaleel ya dawo daga masallaci ne ' ya zauna parlor tare da ciro wayar
shi yayi dialing number d'in Lubna, Yayi sa'a ringing d'aya tayi ta d'ago tamkar ta
na da k'ishin shi.
"Baby!."
"Hm i was shock and surprise!"
"Well...don't be, Lubna you know that i missed you so much right?"
"Bawani nan! Bayan kanata cin angon cin ka ' ko zaka cemin baka kwanta da ita
ba?"
Fadwa da ke bedroom d'in taji kamar motsin mutum a parlor ' haka yasa ta fitowa
daga d'akin nata zuwa parlor don ta duba waye.
"Haba meyasa zaki rik'a fad'amun haka? Kema kinsan Lubna ba zab'ina bace and
she's not my class really..."
Haka yayi dai dai ' da isowar ta parlor, Cak ta tsaya jin abinda yake fad'a
haka yasa ta fahimci da Lubna yake waya.
Sai da ta jira ya gama wayar ' tukunna tayi gyaran murya, Da sauri ya juyo ya
kalle ta.
"Dama kina ciki ne?"
"Eh."
Juyawa tayi ta koma d'akin ta ' ta zauna a bakin gado.
"Ni nasan dama ba sona kakeyi ba Yaya Khaleel ' amma insha Allah komai ya
kusa zuwa k'arshe."
Turaren nan ne ya fad'o mata a rai ' haka tayi zambur ta tashi ta nufi parlor,
Sam ta manta da akwai Yaya Khaleel zaune a wajen ' kai tsaye ta nufi wajen inda ta
san cewa nan ta saki turaren.
Ta na ganin shi tayi ajiyar zuciya ' tukunna ta d'auka ta juya ta zata koma
d'aki ya tsaida ' haka yasa ga banta yayi mugun fad'uwa ta juyo ta kalle shi a
sanyaye.
"Meye ne wannan? ' kika zo zaki wuce kamar baki ga mutum ba?"
"Babu komai ' fitsari nakeji shiyasa na ke sauri."
Tana fad'in haka ta juya ' ta wuce cikin sauri harda k'arawa da gudu, Tana
shiga d'aki ta sa key ta kulle ' nan ta cire kayan jikin ta ta fad'a bathroom don
yin wanka.
B'angaren Yaya Khaleel ' text yayiwa Lubna da Address d'in Company d'in shi don
anan zasu koma suna had'uwa.
Bayan ya gama ne ' zai tashi ya wuce Ilham ta bud'o k'ofa rik'e da cooler d'in
abinci.
"Yaya Khaleel Fadwa fa?"
"Tana d'akin ta."
Ok kawai ta ce ' sannan taje ta ajiye abincin saman dinning table ta zarce d'akin
Fadwa.
Murd'a handle d'in tayi taji a kwulle.
"Kome takeyi oho!"
Ilham juyawa tayi ta koma sashen su.

*Dedicated To Seemaluv Novel Group 2*


馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me
*@I Proudly Dedicated This Page To My Sweet Bestie 鉂�(JAMEESHA 馃憚) "JAMEESHA! I
Just Want You To Remember That ' You Will Forever Be In My Heart!!!" Jealous One's
Can Die!!...*

*59-60*

Fadwa bayan ta fito daga wanka ne ' ta zarce gaban mirrow ta na taje gashin kanta,
Sai da ta gama ne ta fara gyara jikinta ' ta hanyar shafa turaruka iri iri, Sai da
ta kammala gyara jikin ta tsaf tukunna ta d'auko turaren da Ige ta bata.
Fadwa harta bud'e zata shafa sai kuma ta maida ta aje.
"Ba yanzu ba tukunna!"
Abinda ta fad'a kenan ta tashi ta nufi wardrope d'inta ta ciro rigar bacci Cotton
ta saka ' iya gwiwa rigar ta tsaya sai dai kuma rigar armless ce (wacce ba dogon
hannu ba).
"Duk rigunan babu na k'warai mtsww!"
Ta na cikin haka ne ' Yaya Khaleel ya k'wala mata kira, Cikin sauri ta amsa da
na'am! ' sannan ta fito daga d'akin zuwa parlor.
Ta na isa harabar parlon ta ganshi zaune a dinning ' da alaman abinci yake so
suci.
Fadwa k'arasawa wajen tayi ' cike da kunyar shigan da tayi, Sannan ta sami waje
ta zauna.
"Yaya Khaleel gani!"
"Yunwa nakeji ' ki zo ki samun abinci."
Fadwa mik'ewa tayi ta zuba mashi nashi ta mik'e mashi, Sannan ita ma ta zuba nata
ta fara ci.
Suna cikin cin abincin ne ' wayar shi ta fara ringing, Zai d'aga wayar kenan
Fadwa ta rigashi d'aukar wayar.
"Lubna ko?"
Ido kawai ya zuba mata ' ba tare da ya ce mata komai ba.
"Toh ta bari saika gama cin abinci tukunna."
Yaya Khaleel abun d'aure mashi kai yayi ' ya tsaya ya na kallon ta cike da
mamaki.
"Yaya Khaleel please eat your food! And stop bothering yourself about her."
Tana fad'in haka ta fiske ' tayi kamar ba ita tayi maganar ba.
"Fadwa kinsha wani abu ne?"
D'ago kanta tayi ta kalle shi ' sannan ta maida kanta k'asa ba tare da tace
mashi komai ba ' tashi tayi zata wuce d'aki ya dakatar da ita .
"Ina zaki je? Kin gama cin abincin ne?"
"Yaya Khaleel ' kawai na k'oshi ne, Don naga kafi d'aukan Lubna da muhimman
ci akaina ' ni da nake matar ka."
Jikin shine yayi sanyi ' jin abinda Fadwa ta fad'a sai duk yaji tausayin ta ya
kamashi ' kuma tabbas bai kyauta ba.
"Well Ok je ki kwanta d'in."
Juyawa tayi ta wuce d'akin ta cikin sanyin jiki, Ta na shiga ta fad'a saman gado
' tunani kawai takeyi yadda ta zata samo kan Yaya Khaleel.
Fadwa tashi tayi ta nufi gaban madubi ' don ta sha turaren nan ajikin ta,
Bayan ta d'auki turaren ne jikin ta na d'ar d'ar d'in shafawa ' ta fara kici niyar
bud'e kwalbar ba ta ankara ba duk turaren ya gama watse mata a jiki.
"Subhanallah ' gashi ance kad'an ake shafawa!"
Abinda ta fad'a kenan ta aje kwalbar a saman mirrow ' ta janyo towel cikin sauri ta
fara goggoge wa don rage turaren, Fadwa na cikin haka ne taji an rik'o hannun ta '
cikin tsoro ta d'aga kanta don taga waye.
Yaya Khaleel ne ' tsaye a kanta suna kallon kallo.
"Me kikeyi? inata kiran ki baki amsa ba?"
Fadwa had'iye miyau tayi da kyar ' cikin tsoro ta anshe hannun ta tare da ja da
baya.
"Amm... Yaya Khaleel kayi hak'uri banji bane...!"
"Is okay"
Ya fad'a tare da matsawa daf da ita, Sannan ya janyo ta ' ya d'aura kanta bisa
k'irjin shi ya na bubbuga bayan ta a hankali, Nan Fadwa tayi lamo ta na baza idanu
gaban ta na fad'uwa.
"Nasan abinda nayi was in proper ' ban kyauta ba, Amma yanzu nazo in gyara
b'arnar da nayi."
D'ago kai tayi ta kalle shi.
"Dagaske?
Ya d'aga kai alaman Eh.
"To Yaya Khaleel promise me ' zaka daina kulata."
"I promise baby!"
Fadwa har ta maida kanta jikin shi ' ya d'ago fuskar ta da hannu biyu.
"Baby ' kin zubar da turare ne a d'akin nan?"
Cike da tsoro take kallon shi ido cikin ido ' tare da karkad'a mashi kai alaman
a'a.
Nan ya hau shin shina jikin ta ta ko ina ' yana had'a mata da kiss a wuyan ta.
"Baby wannan wane irin turare ne?"
Gaba d'aya Yaya Khaleel ya fita hayyacin shi ' idon shi ya kad'a yayi jajir,
Fadwa kuwa k'afa funta rawa kawai suke ' ta na k'ok'arin zubewa k'asa.
"Yaya Khaleel ' ka daina please..."
"No Baby please let me!"
D'aga rigar ta yayi ' ya saka hannun shi a ciki, Fadwa wani zafi ta faraji a
k'irjin ta ' nan ta sa mashi kuka, Jin kukan ta na yana damun shi ne ya had'a bakin
da nata ya fara tsotsa tamkar ya sami sweet.
Fadwa k'ok'arin zubewa k'asa takeyi ' yayi saurin d'aukar ta cak ya aje saman
gado, Sannan ya cire kayan jikin shi tass ' ya rage daga shi sai boxer ya haye
saman gadon.
K'ok'arin cire mata riga ya keyi ' ta yi saurin rik'ewa.
"No Yaya Khaleel please don't, Kayi hak'uri don Allah."
Bai bi ta kanta ba ' ya fara cire bottles d'in rigar ta sannan ya yaye rigar
gaba d'aya.
Nan Yaya Khaleel ya k'ara rud'ewa tare da fita hayyacin shi, Ta inda yake fita
' ba ta nan yake shiga ba.
K'ok'arin shi kawai ya cinma burin shi, Fadwa ita kanta duk ta fita hayyacin
ta nin shi kawai takeyi sama sama a gajiye.
Ni Seemaluv 馃憚 wacce ke lab'e a bakin k'ofa ' sai ji nayi Fadwa ta saki k'ara.
"Ahhhggh."
Kuka takeyi amma sam babu sauti, Anan nasan cewa Lallai Yaya Khaleel yayi aika
aika.
"Sorry Baby ' ki barni insake koda round d'aya ne please...!"
"Nidai a'a bana so ' kabarni nidai please."
A shagwab'e tayi maganar da dashesh shiyar murya ' saboda tsabar kuka.
Yaya Khaleel sauka yayi daga saman ta gami da rufa masu blanket a jiki ' ya
rungume ta yana maida numfashi, A haka har bacci ya d'auke su.

*** *** *** *** *** ***

*WASHE GARI MISALIN K'ARFE 6:30AM NA SAFE! *

Yaya Khaleel ya tashi daga bacci ' Fadwa na duk'unk'une a jikin shi, Zame jikin
shi yayi ya shige bathroom d'in ta ya tara mata ruwan d'umi a baff ' sannan ya zuba
ruwan dettol a ciki.
Fitowa yayi yaje bakin gadon ' ya zuk'unna ya na k'are mata kallo.
"Baby nah! Ki tashi haka nan."
Ya fad'a tare da shafa fuskar ta, A hankali Fadwa ta bud'e idanuwan ta wad'an
da suka kumbura saboda kuka.
"Ina kwana?"
Ta fad'a ta na k'ok'aran tashi zaune.
"Lafiya k'alau Baby nah yaya jikin naki?"
Yayi tambayar cike da tsoka na ' hakan yasa ta kauda kai.
"Ki tashi kije kiyi wanka ' ruwan d'umi nacen na tara miki, Kuma ki tabbatar
kin gasamun ko ina na jikin ki ' don zan k'ara round d'aya da safen nan."
Waro ido tayi ta kalle shi ' cike da fargaba.
"Yes! Ko saina d'auke ki da kaina ne?"
"Yaya please d'an mik'omin towel to..."
Tayi maganar kamar zata yi kuka, Haka yasa shi d'auko mata towel d'in inda ta
sake shi ' ya mik'a mata sannan ta karb'a, Fadwa ta na cikin blanket ta d'aura
towel d'in tukunna ta sauko daga gadon ' zuwa bathroom tana takawa a hankali,
Saboda zafin da takeji.
Yaya Khaleel ' binta yayi da kallo gami da sauke ajiyar zuciya, Sannan ya tashi
ya cire bedshit d'in saman gadon ya sanya wani ' ya je ya ajiye d'ayan cikin kayan
wanki, Tukunna shima ya wuce d'akin shi don gyara jiki.

*Around 7:00am*
Bayan Fadwa ta fito daga wanka ne ' tayi sallah sannan ta gyara jikin ta cikin
atamfa purple doguwar riga, Fadwa wata yunwa ce ta yunk'uro mata ' yasa tayi saurin
barin d'akin ta zarce kitchen.
D'auko yourghurt Fadwa tayi mai sanyi ' sannan ta dawo parlor ta zauna ta sha,
Tana cikin sha ne Ilham ta shigo sashen nasu ' kamar yadda ta saba yau kuma indomie
ce aka dafa masu taji ingridient.
A sama sama suka gaisa da Ilham.
"Ke yau sauri nakeyi ' zan lek'a school."
"Oh toh in kinje ki gaishe mun su please."
Ok kawai Ilham tace sannan tayi tafiyar ta.

*DEDICATED To My Fan's 馃憣馃憣*


馃憚馃憚馃憚馃摑
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*61-62*

Bayan fitar Ilham ne ' Fadwa ta zuba indomie d'in ta fara ci a zaune a harabar
parlor, Saboda tsananin yunwan da takeji ba ta tsaya jiran fitowar Yaya Khaleel ba.
Tana cikin ci ne ya shigo parlon ' nan ta hau baza idanu tana kallon gefe
tamkar wacce tayo k'arya.
Yaya Khaleel zuwa yayi ya zauna a k'asa shima kusa da ita, Ya tsura mata ido na
d'an lokaci ' ita kuwa abincin ta kawai take ci ba tare da ta bari sun had'a ido
ba.
"Baby nah! Yau da yunwa kika tashi ne?"
Kai Fadwa ta d'aga mashi alaman Eh, Sannan ta cigaba da cin abinci ' tana cikin
haka ne ya rik'e mata hannu.
"Baby nah ' nima fa yunwa nakeji, Tare ya dace muci."
Fadwa aje spoon d'in hannun ta tayi cike da murmushi ' tayi shuru ta na kallon
plate d'in saboda tsabar kunyar da ta lullub'e ta.
"Dake nake fa! Kikaimin shuru."
D'ago kai tayi ta kalle shi ' da wararan idanun ta.
"To..."
Abinda ta ce kenan ' ta d'auki spoon ta fara feeding d'inshi itama ta na feeding
kanta, A haka har suka gama breakfast d'in su ' sannan Fadwa ta mik'e da niyyar
d'auko masu ruwan sanyi.
"Ina kuma zaki je?"
"Ruwan sha zan d'auko."
Yaya Khaleel tashi yayi da sauri ' ya matsa kusa da ita.
"No bari in d'auko mana! Don banaso ki wahala da yawa ' domin na lura Baby
nah ragguwa ce!"
Fadwa hannu tasa ta rufe fuskar ta da sauri ' saboda tsabar kunyar da ta rufe
ta.
"Of cause yes ' yanzu ki koma ki zauna."
Yana fad'in haka ya juya ya zarce kitchen, Bai wani b'ata lokaci ba ya dawo
parlor rik'e da robar ruwan sanyi a hannun shi.
Zama yayi sannan ya janyo ta jikin sa.
"Oya bud'emin baki."
Dun guna mata bakin robar yayi ' ba shiri ta bud'e bakin ta fara shan ruwa sai da
tasha ma ishi , Sannan shima ya sha.
"Uhm Uhm please Yaya Khaleel ' ka barni please!"
Ya fad'a cike da tsokana ' haka yasa Fadwa ta zaro ido ta kalle shi tare da
ballara mashi harara, Nan ta tashi ' ta rarumi pillow d'in kujera ta hau buga mashi
a baya.
Nan shima ya mik'e ya nufo kanta ' ya fizge pillow d'in da ke hannun ta cikin
jarumta, Hakan yasa ta jin tsoro.
"Oh! Toh tunda hakane abun ' bara in k'ara one round."
Nan Fadwa ta falla a guje ' suka fara zagaye parlon cike da wasanni.
"Wayyo am sorry ' bazan sake ba!"
Ta fad'a cikin dariya ' Yaya Khaleel sa'ar ta ya samu ya rik'e ta, Nan ya fara yi
mata cakulkuli ' Fadwa ji tayi kamar zata sik'e.
"Ahh! haha!! Yaya please barni haka!!!."
Nan ya sake ta ' suka baje a tsakar parlon suna maida numfashi.
"Baby nah! You know what?"
"Until you say it."
"Bana son kina kira na da Yaya!"
Murginawa tayi ta kalle shi.
"Me zan rik'a kiran ka dashi?"
"Ki kira ni da Sweetheart ' ko a gaban waye."
Dariya tayi kad'an ' sannan ta shafa fuskar shi.
"An gama my Sweetheart!"
"Yawwa Baby nah ' yanzu ki tashi ki shirya mu fita, Kinga daga nan sai inkai
Company d'ina ki gani ko?"
"Yessss!!!"
Ta fad'a da k'arfi ' cike da jin dad'i, Sannan suka tashi a tare ' har ta nufi
hanyar d'aki sai kuma ta dawo.
"Sweetheart?"
"Yes."
"Tunda Yaya Farook ya tafi kunyi waya kuwa?"
"Eh mana! Ya ce ma yana gaishe ki."
Ajiyar zuciya tayi ' sannan ta juya ta wuce ba tare da tace komai ba.
Gyale kawai taje ta yafo ' ta fito sannan suka fita, Sai da suka je sashen su
Umma suka gaisa tukunna suka fito.
Kai tsaye suka shige mota ' Yaya Khaleel ya ja, Basu tsaya ko ina ba sai wajen
huta wa ' wajen da manyan mutane ke zuwa tare da matan su.
Suna isa wajen Fadwa ta hangi wani waje ' wanda komai nashi green ne flowers ne
a wajen green colors, Wajen ya had'u sosai.
"Wow!"
Abinda tace kenan ' taja hannun shi suka k'arasa wajen.
Waje Fadwa ta samu tayi zaman dirshen a k'asa Yaya Khaleel ya kwanta ' tare da
d'ora kanshi bisa cinyarta.
"Baby nah! Please ki nunamin soyayya ' don yanzu nake sanin ta, Ban tab'a
sanin dad'in aure ba sai yanzu."
Fadwa wasan ta kawai takeyi da gashin kanshi ' tana sosa mashi.
"Baby nah ' kinata so ki karanta diary d'ina ko?"
Cikin sauri ta ce Eh.
"Toh kada ki damu ' ni da kaina zan fad'a miki abinda ya k'unsa."
"Toh Sweetheart ' ina jinka."
"No ki bari koba yau ba zan fad'a miki."
Ok kawai tace ' sannan ya yunk'ura zai tashi.
"Ina zaka je?"
"Zan kaiki Company d'in ne!"
"Haba Sweetheart tun yanzu?"
"Eh mana! Bana son mu dad'e a nan ne."
Tashi yayi ' tukunna ya mik'a mata hannu ya jata, Suka fita daga wajen suka shige
mota.
Company d'in nashi suka nufa ' suna tafiya suna surutu cikin jin dad'i.
A haka Fadwa taji ya tsaya ' a hankali ta juya ta kalli gefen motar.
"Oh har mun kawo ashe!"
Bud'e motar sukayi a tare suka fito ' ciki suka nufa cikin hanzari, Bayan shigar su
ne ' mutanen da ke aiki a wajen sukai ta zuwa suna taron shi ' tare da yi masu
maraba.
A tsaitsaye Yaya Khaleel yayi introducing Fadwa ' tukunna ya barsu nan wajen ya
ja hannun ta suka shige office d'in shi.
Shi kanshi office d'in yaci sunan shi ' don kuwa k'ayatuwa iya k'ayatuwa ya
k'ayatu, Haka Fadwa ta rik'a bin ko ina da kallo ' don cikin office d'in kuwa harda
guestroom.
"Sweetheart?"
Ya juyo ya kalle ta ' da hannun shi sanye a aljihu.
"Na'am Baby nah!"
"Wancen d'akin meye amfanin shi toh?"
"Haba Baby nah ' ai amfanin shi kenan idan muna tare sai mu shiga mu huta."
Murmushi tayi mashi sannan ta sami kujera ta zauna, Shima zuwa yayi ' ya zauna
kusa da ita yana shinshinar wuyar ta, K'ok'arin kai bakin shi yake yi cikin nata
wayar shi ta fara k'ara alamun kira.
Nan ya sanya hannun shi cikin aljihu ' ya ciro wayar cikin hanzari ya duba yaga
Lubna ce ke kiran shi, D'aga wayar yayi badon yana so ba.
"Hello!"
Ya furta idon shi na kan Fadwa.
"Haba my Love ' lafiya kwana biyu naji ka shuru? Ko irin kiran nan nawa ba
kayi ' ko laifi nayi?"
"You know what? Am busy now ' zan kiraki zuwa anjima."
Jin haka yasa gaban Fadwa ya fad'a, A zuciyar ta tace.
"Dama har yanzu baka rabu da ita ba? Daman dad'in baki kawai kakemin? Hmm
lallai..."
Yaya Khaleel katse ta yayi daga tunanin da takeyi ta hanyar tab'a fuskar ta '
haka yasa ta yin firgigit ta kalle shi.
"Baby nah? Tunanin me kikeyi?"
Girgiza mashi kai tayi ' alamun babu komai, Sannan ya rungume ta.
"Mu tashi mu koma gida ko?"
"Sweetheart ' tun yanzu?"
"Eh mana!"
"To shikenan muje."
Yaya Khaleel pecking d'inta yayi ' tukunna suka tashi suka fita daga wajen.
Bayan sun shiga mota ne ' har ya tada sai ganin wata mota yayi tazo ta tsaya a
gaban su.
"Ha'a waye wannan kuma?"
Yaya Khaleel kallo d'aya yayi ma motar ' ya gane wacece a cikin ta, Lubna ce ta
fito daga motar babu mayafi a jikin ta sanye da speck a idonta.
Yaya Khaleel fita yayi cikin hanzari ' Fadwa kuwa sam ta ma mance fuskar Lubna.
"Wacece wannan haka?"
Itama fitowa tayi daga cikin motar ' ganin ta yasa Lubna zare glass d'in da ke
sanye a idon ta, Tana k'arewa Fadwa kallo.
"So my suspicious was right! Ka cemin you were busy ' ashe soyayyar ka kawai
kake ci.
Fadwa maida kallon ta tayi a kan Yaya Khaleel ' sannan ta matsa kusa dashi.
"Sweetheart wannan wacece?"

*Dedicated To Seemaluv Novels Group*


馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:51 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*_@Well... Alhamdulillah ' i dedicated this page to, PURE MOMENT OF LIFE WRITERS
GROUP, And SEEMALUV NOVELS GROUP 1&2, And BABBAN GIDA FAN'S GROUP...Inason ku sosai
鈽篲*

*63-64*

Yaya Khaleel had'iye miyau yayi da kyar ' ya kama hannun ta tare da cewa.
"Shiga mota please!."
Lubna dariya kawai takeyi ' ta na kallon shi, Sannan ta tako har inda suke ' tayi
folding hannayen ta.
"Seems like ' kin manta fuska ta ko?"
Fadwa ido kawai ta zuba mata ' ta na mata kallon zargi, Lubna ta bud'e baki zatayi
magana kenan yayi saurin dakatar da ita cikin tsawa.
"Lubna!!! Karki tarwatsa mun nishad'ina da ni da iyalina, So please..."
A nan ne Fadwa ta tuna ko wacece Lubna ' hakan yasa ta k'ara mak'alewa a jikin
shi.
"Sweetheart ' mun zo yawon jin dad'i ne, So please mu koma gida tun kafin
farin cikin mu ya tarwatse."
Wani k'ululu ne ya tsaya ma Lubna a wuya ' tsabar bak'in ciki ya lullub'e ta, Da
sauri Yaya Khaleel ya rungume Fadwa ' sannan ya sami damar yiwa Lubna alama ta ido
' alaman ta wuce.
Nan ya ja hannun Fadwa suka shige mota ' itama Lubna ta shige motar ta, Sai da
suka wuce sannan ta tada mota itama ta wuce.
Tunda suka kama hanyar zuwa gida ' babu wanda ya ce uffan, Don kuwa Fadwa jira
kawai take su isa gida ' ta fara zuba nata bala'in.
Bayan sun kai gida ne ' driver ya bud'e gate Yaya Khaleel ya shigar da mota
ciki, Sannan ta suka shige part d'in su ' Fadwa fuska a d'aure.
Tana shiga ya rik'o hannun ta ' tare da murza wa.
"Baby nah?"
Amsawa tayi da na'am ba tare da ta juyo ta kalle shi.
"Baby nah! Nasan zuciyar ki tana cike da tunani kala kala ' but trust bazan
ci amanar ki ba."
A fusa ce ta juyo ta kalle shi ' tare da fizge hannun ta daga nashi.
"I should trust you? How? Bayan a baya kaimun alk'awari cewa ka daina kulata
' amma yanzu sai naga sab'anin hakan, Kenan ma harta riga ni sanin Company d'in
ka!."
"No Baby nah ' please ki yarda dani mana ai bazan cutar da ke ba! Besides
itace budurwa ta ta farko ' so ya kamata..."
Bai k'arasa ba ta katse shi da cewa.
"Kuma ita ce zab'in ka ko? Ni kuma zab'in su Umma ce, Saboda haka ban cen
cenci a nuna min so ba!."
"No ba haka bane ' ki saurare ni please, Lubna tana sona ' a dalili na ta
rabu da duk samarin ta, Fadwa ba kya tunanin idan na rabu da ita lokaci d'aya zai
iya zama mata matsala?"
Fadwa tsayawa tayi ta na kallon shi cike da mamaki ' yadda ya ke fad'a mata
magana son ranshi, Kasa cewa komai tayi don kuwa idanun ta gaff suke da su zubar da
hawaye ' Hakan yasa ta ja tsaki ta juya ta wuce d'akin ta.
Yaya Khaleel d'aki ya wuce ya d'auko laptop d'inshi ya dawo parlor ya zauna.

*** *** *** *** *** ***

*AROUND 2:00PM*

Fadwa ta fito daga d'akin ta ' zata fita zuwa sashen su Umma, Yaya Khaleel ya
tsaida ita.
"Baby nah ' ina zakije?"
"Zanje in duba Umma ne."
Ta fad'in haka tasa kai ta fice ' don karma ya tsaida ita, Fadwa ko da tashi wajen
su Umma a zaune ta iske su ' su na kallo ita da Ige.
Sai da tayi sallama tukunna ta sami waje ta zauna ' ta gaishe su, Suna cikin
haka ne Ilham ta dawo daga school ' ita gaida su Umma tayi sannan ta wuce d'aki don
ajiye handbag d'in ta Fadwa na biye da ita.
Bayan sun shiga d'aki ne Fadwa ta kwanta ta baje saman gado.
"Ya da kwanciya mun a gado? A'a gaskiya ki tashi ki wuce gidan ki."
"Ke ni ki barni please ' Ilham yau a nan zanyi rayuwa ta."
Zaro ido Ilham tayi cike da mamaki.
"Me kike nufi? Inma dai tsiya kukayi ' toh wannan ba hujja bace, Kuma sai na
fad'awa Umma."
"Ilham da gaske nakeyi fa! Ke dai ki zuba ido kiyi kallo ' kuma ko da Umma ta
gane, Ni nasan abinda zan fad'a mata."
Tab'e baki Ilham tayi tare da mik'ewa tsaye.
"Wannan tsakanin ku ne ' mata da miji, Ni nan yunwa ma nakeji ' Allah yasa
Ige ta kusa gama abincin."
"Ki d'an duba kitchen d'in mana to ' in ta gama ki zubo dani."
Ok kawai ta ce sannan ta fice daga d'akin zuwa kitchen, Ilham na fita Ige ta
shigo d'akin ' haka yasa Fadwa ta shi ta zauna.
"Y'an nan kinyi amfani da turaren nan kuwa?."
Kai Fadwa ta d'aga mata alaman Eh, Sannan Ige ta sami waje ta zauna.
"Tow yayi aiki kuwa?"
"Eh Ige ' yayi aiki sosai kuma har yanzu kan aiki yake, Amma ni akwai abunda
ke damuna."
"Me ke damun ki? Fad'amun shi y'an nan!"
"Ige ' wata budurwa ce yake da ita, To sun dad'e tare kuma bana tunanin son
ta zai fita daga ranshi."
"Wane shi! Wane shi!! Ai indai kina amfani da wannan turaren akai akai ' kuma
kina had'awa da addu'a, To gaba d'aya zai iya mantawa da ita."
Fadwa hawaye ne ya zubo daga idanun ta, Ta sa hannu ta share.
"Na gode sosai Ige ' ban san meyasa ba kwata kwata banason in rasa shi."
"Ai bazaki rasa shi ba y'an, Amma auren had'i ne tsakanin ku?"
Fadwa ta d'aga mata kai alaman Eh, Sannan Ige tayi ajiyar zuciya.
"Lallai a gaishe da Umman ku da aiki ' gaskiya ta raya zumunci, Kuma auren
had'i babu abinda ya kaishi dad'i."
Suna cikin haka ne Ilham ta shigo d'akin rik'e da plate a hannun ta, Ajewa tayi
a harabar d'akin ta koma ta kama k'ugu.
"Wannan dambun Allah yasa karya rik'a shak'e mutane, Ige nina tab'a ganin
dambu haka zak'o zak'o?"
"Kaji ja'ira, ke ce ta farko da zakiyi santi."
Dariya suka kwashe da shi ' dukkan su, Sannan Ige ta bar d'akin zuwa kitchen don
ta zuzzuba abincin.
Nan su Fadwa suka sauko k'asa suka fara cin abinci, Cen Fadwa ta d'an daka ta.
"Ilham please taimako!"
"Taimakon me?."
"Ki kaiwa Yaya Khaleel abincin shi ' wallahi idan naje bazai barni in dawo
ba."
"Cifd'i aiko babu inda zani! Ga matarsa a kusa ' sai nice zaki ce inkai mashi
abinci? Ayya kuwa Fadwa kina kula da shi yadda ya kamata?"
"Dalla cen banson iskanci ' in bazaki je bane kawai ki fad'amun!."
"Eh bazan je ba d'in."
Ajiyar zuciya Fadwa tayi ' gami da yin fuskar tausayi.
"Haba mana Ilham! Don Allah ki taimake ni ' ki kai mashi."
"Hahah! Idan anaso a moreka ansan ta inda za'a b'ullo su Fadwa."
Ilham tashi tayi ' ta nufi kitchen ta iske Ige ta zuba masa nashi a plate,
Sannan ta d'auka ta nufi part d'in nasu dashi.
Ilham bud'e k'ofar tayi d'auke da sallamar ta a baki, Yaya Khaleel dake zaune a
parlor ya amsa sallamar ba tare da ya d'aga kai ya kalle ta ba.
"Yaya Khaleel ga abincin."
"D'aura mun a kai."
Nan gaban Ilham ya fad'a, A zuciyar ta tace.
"Maida wuk'ar, karka huce kaina."
Wajen dinning table ta nufa ' ta ajiye mashi abincin, Sannan ta juyo zata fita
ya dakatar da ita.
"Tana ina?."
"Wace?"
Harara ya watso mata ' nan fa baki ya fara rawa.
"Oh Fadwa? Ta na cikin gida ' abinci take ci."
"Kice mata ina kiranta!"
To kawai tace sannan ta fice cikin sauri ' Ilham tana shiga cikin gida ta nufi
d'aki direct, Sannan ta zauna a k'asa.
"Yace kije yana kiran ki."
"To me zan masa?"
"Ha'a niko ya za'ayi in sani? Nidai kije kawai please, Don karma kice ban
fad'a miki ba."
D'an tsaki Fadwa taja ' sannan ta gyara zaman ta.
"Nikam babu inda zanje ' ina nan, Don nasan babu abinda zan mashi a cen d'in
a toh."
Yatsine baki Ilham tayi ' suka cigaba da cin abincin su.

馃憚馃憚馃憚馃憣
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*69-70*

Tana shiga suka had'e da Yaya Khaleel yana k'ok'arin fitowa.


"Baby nah?."
Ta d'ago kai ta kalle shi ' sam ta kasa b'oye damuwar da ke bayyane a fuskar ta.
"Yanzu na dawo daga masallaci ban ganki ba."
"Amm...Eh naje wajen su Umma ne."
Ta fad'i haka tare da k'arasawa ciki ta nemi waje ta zauna, Shima kusa da ita ya
zauna yana kallon ta.
"Baby nah! Are you alright? Ko dai jikin ne?."
"No! Babu komai Sweetheart ' gajiya ce kawai."
"Ok ' to yanzu muci abinci tukunna ko?"
Kai Fadwa ta d'aga mashi alaman to, Sannan ta tashi gami da rik'e hannun shi suka
nufi dinning table.
Sai da ya zauna tukunna ta juya ta wuce kitchen don d'auko abincin, Bayan ta
fito daga kitchen d'in ne rik'e da tuwo da miya a hannun ta ' ta ajiye zata koma
d'auko plates Yaya Khaleel yayi saurin rik'e mata hannu.
"Baby nah! Dawo ki huta haka nan ' ni sai inje in d'auko sauran kinga ba
kyajin dad'i.
"No Sweetheart bara kawai in k'arasa ladar tawa."
"A'a kema kinsan bazan bari ba ' so kawai ki hak'ura ki dawo ki zauna."
Murmushi ta sakar mashi ' hakan yasa shi jin dad'i sosai, Ya tashi yaja mata
kujera ta zauna ' tare da cewa.
"Yawwa Baby nah!."
Tukunna ya juya ya wuce kitchen d'in Fadwa ta bishi da kallo cike da murmushi.
Bai wani b'ata lokaci ba ya dawo parlor rik'e da plates a hannun shi da sarving
spoon & spoon, Bayan ya zauna ne ' ya zuba tuwo da miyan a plate d'aya, Sannan ya
fara kaiwa bakin shi.
"Ummm.... Yummy! Ashe dai na iya miya."
Da sauri Fadwa ta harare shi ' tare da turo baki.
"Na iya miya dai! Bayan kai burkawa kawai kayi? Kuma ma duk ka zubarmin da
miyan!."
"Oho dai! Ai dai akwai hannu na aciki ko? To oya bud'e bakin."
Babu musu Fadwa ta bud'e baki ya fara feeding d'inta ' yana yi yana sawa a bakin
shi shima, Sai da ya tabbatar ta k'oshi tukunna ya kyale ta.
"Baby nah! Nidai ban k'oshi ba tukunna sai na cinye tuwon tass."
"To ai gaka gashi ' daman don kai nayi shi ai Sweetheart, Kaga kuwa ai
baza'ayi maka rowan shi ba."
"Baby nah ' kinsan mene ne? Gobe insha Allah zan kaiki hospital a dubamin
lafiyar ki ' daga nan sai inkaiki saloon d'in ko?."
"To shikenan Sweetheart ' Allah ya kaimu."
Fadwa tashi tayi zata wuce d'aki ya tsaida ita.
"Ina kuma zakije?."
"Sweetheart ' rigar bacci zan sanya, zafi duk ya isheni."
"Haba Baby nah! duk da AC d'in nan?, Kuma ma aida kin bari sai anyi isha'i
tukunna."
"Ok to bari ind'an watsa ruwan sanyi."
Fadwa d'akin ta tashige don yin wanka tukunna Yaya Khaleel ya had'a komai na
wajen ya kai kitchen.
bayan ya dawo ne ya koma harabar parlor ya zauna, Nan wayar shi ta fara k'ara '
cikin hanzari ya cire ta daga aljihun shi ya duba, Ganin Lubna ce ke kiran shi yasa
yayi rejecting call d'in cikin fushi ' tare da jan tsaki.
Lubna sake kiran shi tayi ' ganin zata dame shine yasa ya d'aga wayar.
"Wace irin mace ce ke?."
Daram taji gaban ta ya fad'i.
"Ni mace ce wacce ' mukayi rayuwa tare kuma muke k'aunar junan mu."
"Lubna meyasa baki da tunani? for God sake ' bazaki kyaleni inyi rayuwa ta
ba.?"
"Khaleel ni kake fad'awa haka? Ni ce fa Lubna! Kana so kace min zaka watsar
dani kenan?"
"Eh inaso ne kema kije ' kiyi aure ki hutawa rayuwar ki, Lubna kid'au ka
rayuwar da mukayi a baya munyi ta ne a bisa kuskure ' kuma yanzu ne yakamata mu
fara istigfari."
"Am i dreaming?."
Ta fad'a cikin rawar murya ' tamkar zatayi kuka.
"No you are not! Lubna ina cikin kwanciyar hankali da mata ta ' and i love her
so much, Please try to understand ko dama cen kece kika cusa mun sonki ' tun banaso
har kika saba min."
"No!!! Stop it please! I have had enough ' Khaleel zan so mu had'u face to
face, Don wallahi ban yarda wad'an nan kalaman daga bakin ka suke fitowa ba..."
Ta fad'i haka cikin kuka mai tab'a zuciya, Haka yasa yayi saurin kashe wayar '
gami da cilla wayar saman kujera.
Yaya Khaleel mik'ewa yayi da niyyar shiga d'aki yaga Fadwa a tsaye tana kallon
shi.
"Baby nah ' har kin fito wankan ne?."
Da sauri Fadwa ta k'arasa ta rungume shi ' cike da jin dad'i, Shima matse ta yayi
da hannun shi.
"Sweetheart ' naji dad'i sosai! Hakane ya nuna min cewa lallai kana so na."
Bubbuga bayan ta yakeyi a hankali ' tukunna ya rabata da jikin shi suka zauna."
"Baby nah! Kiyi hak'uri da abunda ya faru a baya ' tabbas munyi zaman haramun
da bid'ala tsakani na da Lubna, Yanzu ne ya kamata mu gyara kuskuren mu ' and am
willing to do anything just to make you happy!."
Fadwa pecking d'in shi tayi a kumatu 馃槉, Sannan ta koma ta lafe a jikin shi.
"Thank you Sweetheart ' Yaya Khaleel d'ina na kaina!."
D'an ture ta yayi kad'an, Hakan yasa ta d'ago kai ta kalle shi.
"Bana ce ki daina cemin Yaya ba? Ai gara ki kira ni da Khaleel d'in ma."
"Ahhh! Haba ba ba ba...wane ni? Babu girma kenan Sweetheart."
Murmushi yayi ' tare da d'ago fuskarta zaiyi kissing d'in lips d'in ta tayi
saurin mak'ale bakin.
"Meye haka kuma?."
Girgiza mashi kai kawai tayi ' tare da bazo mashi idanu.
"Wannan d'in ma? A'a baki isa ba kuwa!."
Nan ya fara mata cakulkuli ' ta fara ihu cikin dariya, Ganin tana neman sik'ewa
ne yasa tayi saurin cewa.
"Ahh ahaha!.. Sweetheart ' wallahi ji nayi an kira sallah shiyasa, Kaje Mosque
kada alwallar ta karye."
"Kin sha! Amma ki bari in dawo ' sai bakin ki yayi tsini."
Tashi yayi ya fita zuwa masallaci ' idon ta na kanshi har ya fice bata daina
murmushi ba.
"Huh! Allah na gode maka ' daka misanya min da Yaya Khaleel, Wanda a yanzu shi
kad'ai kawai zan iya kallo inji sanyi a raina."
Tana gama fad'in haka ta tashi ta wuce d'akin ta ' har ta sanya hijab sai kuma ta
cire.
"Anya? Alwallar nan bata karye ba? Bari dai kawai in cenja wata."
Bathroom ta fad'a tayo alwala tukunna ta fito ' ta sanya hijab d'inta ta tada
sallah.
Bayan ta idar ne ' ta mik'e gami da cire hijab d'in, Sannan ta nufi madubi ta
jawo kwalbar turaren nan ' ta zuba a tafin hannun ta tukunna ta mutsits-tsika shi
ta shafa a jikin ta.
Fadwa sai da tabi ko ina na jikin ta ' ta shafeshi tass da turare, Tukunna ta
bud'e wardrope ta ciro rigar bacci 'yar k'arama dai dai gwiwa ta sanya.
Sai da ta gama shirya wa ' sannan ta fito parlor kai tsaye taje ta kunna TV ta
dawo ta zauna, Bata dad'e da zama ba Yaya Khaleel ya dawo daga masallaci ' sallama
yayi Fadwa ta d'ago kai ta kalle shi tare da amsawa.
"Sannu da dawo wa!."
Ta fad'a tare da mik'ewa tsaye zata nufi kitchen.
"Duk ki gama rara gefen ki ' yau bazaki iya k'watar kanki ba."
A tsora ce ta juyo ' ta kalle shi tare da yin innocent face.
"Sweetheart kana magana ne?"
Sai da ya sami waje ' ya zauna sannan ya ce.
"A'a da kaina nake magana!."
Yaya Khaleel ya fad'i haka tare da watso mata wani irin kallo, Fadwa juyawa tayi
ta wuce kitchen d'in gaban ta na d'ar d'ar, Fridge ta bud'e ta d'auko roban
youghout mai sanyi ' sannan ta juya ta dawo parlor tayi zamanta suka fara kallon
kallon.
"Baby nah ' inzo ki bani?."
A tsora ce ta kalle shi ' don tasan ba komai ke jan shi haka ba, Illa turaren da ta
sanya.
"Ko bazaki bani ba?."
Fadwa kasa magana tayi ' sai dai ta tsinci kanta da girgiza mashi kai.
Murmushin mugunta Yaya Khaleel yayi ' tare da mik'e wa tsaye yana takowa a
hankali inda take zaune, Hakan yasa Fadwa tayi wuff zata tashi gudu ' ya dank'ota
da hannu d'aya.
"Sweetheart bacci nakeji.?"
Waro idon shi yayi' cike mamaki.
"Bacci? Haba! Aiba yanzu ba tukunna."
Juyawa yayi ' yaje ya sanya key a k'ofa, Sannan ya dawo ya d'auke ta cak tamkar
wata baby ' yayi d'akin shi da ita a hannu.
Yaya Khaleel a saman gado ya a jeta ' tare da cewa.
"Ki fara addu'o'i kafin in kashe TV in dawo."
Had'iye miyau Fadwa tayi da kyar don kuwa duk tsoro ya gama cika ta ' sannan ya
fice, Bai wani b'ata lokaci ba ya dawo ' a zaune ya iske ta kanta a sunkuye.
Yaya Khaleel k'arasa wa yayi kusa da ita ya zauna ' ya fara sunsunar ko ina na
jikin ta, ganin hakan ba zaiyi satisfying d'inshi bane yasa shi kwantar da ita
saman gadon ' sannan shima ya haye.
Fadwa hannu biyu tasa ta tallabo fuskar shi ' cikin sanyin murya tace.
"I love you so much ' Sweetheart..."
"love you more Baby nah..."
Ni *Seemaluv* hannu naga Yaya Khaleel yasa ya kashe wutar d'akin, Hakan yasa na
tattara 'yan komatsai na ' na koma parlor na yada zango kafin gari ya waye.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me
*_@Dedicated To All Members Of PURE MOMENTS OF LIFE WRITERS, I like you gurls so
muah 馃拫, And To My Dearest JAMEESHA ' ban manta dake ba..._*

*71-72*

*Washe gari*
*AROUND 6:30AM*
Yaya Khaleel ya tashi ' zame jikin shi yayi daga jikin Fadwa wacce baccin ta kawai
takeyi.
Bathroom ya shiga yayi wanka tare da d'auro alwala tukunna ya fito ' yayi
sallah.
Bayan ya idar ne ' ya tashi ya fara shiri cikin manyan kaya shadda milk colour,
Fadwa bud'e ido tayi gami da tashi zaune cike da murza ido.
"Sweetheart ' ina kuma zaka je kake ta shiri da sassafe haka.?"
"Baby nah ' zan lek'a office ne yau, am sorry ban fad'a miki jiya ba!."
Nan ta sauko cikin sauri ' ta rungumo shi ta baya.
"Good morning!."
"Morning Baby nah!."
"Yanzu bari inyi sallah ' sai muyi breakfast ko?."
Ok kawai ya ce ' ya cigaba da sanya battle d'in wuyar rigar shi, Sannan Fadwa ta
juya ' ta wuce d'akin ta.
Tana shiga ta cire rigar baccin jikin ta ' ta sanya towel tukunna ta shige
bathroom don yin wanka ' tare da yin alwala.
Bayan ta fito ne ta sanya T-shirt ' tare da d'aura zani cikin sauri ta wuce
kitchen ' ta fara had'a musu abinda zasu karya dashi.
Sai da ta kammala ne ' ta fito daga kitchen d'in rik'e da cup guda biyu a
hannun ta, Tea ne a ciki mai kauri ta ajiye a dinning table ' sannan ta juya ta
nufi d'akin Yaya Khaleel.
Fadwa shiga tayi cike da sallama ' ya amsa rik'e da waya a hannun shi, Sannan
taje kusa dashi ta zauna.
"Sweetheart ' gafa breakfast d'in cen."
Ok ya ce ' tare da duba wristwatch d'in hannun shi ya ga 7:00am, Tukunna ya tashi
tare da rik'e hannun ta suka k'arasa parlor.
Yaya Khaleel kujerar dinning table d'in yaja ma Fadwa ta zauna sannan shima ya
koma ya zauna.
"Baby nah? "
Ta d'ago kai ta kalle shi ' cike da fara'a.
"Tea haka zalla? Ko bread babu?."
"Sorry Sweetheart! Kaga ai laifin ka ne ' inda ka sanar mun tafiyar ka office
yau aida tun jiya da daddare na aiki mai gadi ya siyo bread d'in."
"Haka ne fa!!."
"Tea d'in da kauri ai, zai iya rik'e maka ciki har ka dawo.!"
Murmushi kawai yai mata ' sannan ya d'auki cup d'in tea d'in ya fara kaiwa baki.
"Sweetheart k'arfe nawa zaka dawo?"
Fadwa tayi tambayar ' tare da kurb'a tea a bakin ta.
"K'arfe 6:00pm zan dawo.
Nan take ta sark'e, Cikin hanzari Yaya Khaleel ya taso daga kujerar shi ' ya yo
kanta gami da tallabo ta yana hura mata fuskar ta da bakin shi.
"So sorry ' Baby nah, me yayi zafi haka?."
Da kyar Fadwa ta sami damar cewa.
"Kaine ai!."
"Nine me?."
Cewar Yaya Khaleel.
"Kai kasa na sark'e!."
"Baby nah ' am sorry to, Ko sai na kawo ruwa ne?"
Girgiza mashi kai tayi ' sannan ya koma ya zauna.
"Nifa gaskiya ' 6:00pm, yayi yawa."
"Wasa nake miki ' 2:00am zan dawo, Saboda haka maida wuk'ar."
Murmushi tayi cike da jin dad'i, Suka cigaba da shan tea d'in.
A tare suka gama breakfast ' tukunna Yaya Khaleel yasake duba lokaci yaga wajen
8:30am, Nan ya mik'e tsayi tare da cewa.
"Baby nah ' zan makara da yawa."
"Alright Sweetheart..."
Fadwa tashi tayi gami da kama hannun shi ' suka nufi bakin k'ofa, Yayi pecking 馃槉
d'in ta.
"Am blushing, Sweetheart hope baka manta komai ba."
"A'a, Phone d'ina na jiki na ' documents kuma suna office."
"Tohm here you go...Allah ya kare min kai."
Ameen yace ' sannan ya juya ya wuce, Yaya Khaleel har ya kai bakin mota ' ya
laluba aljihun shi babu key, Hakan yasa shi juyawa ya koma.
Fadwa k'ok'arin d'aukan cups d'in da sukayi using dashi takeyi ' Yaya Khaleel ya
shigo.
"Baby nah!."
Juyowa tayi ta kalle shi ' cike da mamaki.
"Duba min key d'in mota a d'aki na."
Cikin hanzari ta juya ta nufi d'akin nashi, Fadwa bata wani b'ata lokaci ba ' ta
kawo mashi key d'in.
"Thanks ' and ki kulamin da kanki."
Ok Fadwa tace ' Sannan Yaya Khaleel ya fice yaja mota zuwa office.

*** *** *** *** *** ***

Bayan Fadwa ta gama kintsa parlon ne ' ta shige d'akin ta ta shirya cikin red
atamfa ' riga da skirt d'auke da makeup a fuskar ta.
Turare ta fesa mai suna *MISS HOT* ' Sannan ta fito zuwa sashen su Umma, Fadwa
shiga tayi d'auke da sallama a bakin ta ' Ige ta amsa kasan cewar ita kad'ai ce a
parlon.
"Ina kwana Ige?"
Cewar Fadwa.
"Lafiya k'alau 'yan nan."
"Ige ' Umma da Abba fa? sun tashi kuwa?."
"Eh Umman ku dai ' yan zun nan ta haura d'akin ta, Amma Abban ku nina kwana
biyu banji motsin shi ba!."
"Ok! Bara inje ' in gaishe ta."
Fadwa d'akin Umma ta nufa ' Ige na binta da kallo, Bayan shigar ta ne ' ta iske
Umma a zaune a bakin gado tana waya, Sai da ta tsaya Umma ta gama wayar ' sannan
ta duk'a k'asa ta gaishe ta, Umma amsawa tayi cike da kamala.
"Amm... Umma Abba na nan kuwa?."
"Aff! Bakisan yayi tafiya ba ko?."
"A'a."
"Jiya yayi tafiya zuwa garin bauchi ' next week zai dawo."
"To Allah ya dawo dashi lafiya!."
"Ameen."
Abinda Umma tace kenan ' Fadwa ta juya ta wuce zuwa d'akin Ilham.
Fadwa bayan ta sauko k'asa ne taga Ige still kallon ta takeyi ' hakan yasa ta
nufi d'akin Ilham kai tsaye, A zaune ta iske Ilham tana waya ' daga ji kasan da
Al'ameen take waya.
Fadwa samun bakin gado tayi ta zauna ' har sai da Ilham ta gama tukunna tace.
"Ilham ni banga ana preparation d'in komai ba!."
"Na d'aura tafashen shinkafa ne ' ke kuma sai kiyi miya.!
"Ok! Ai tashi zakiyi muje kitchen d'in."
"To naji muje ' ni karkuma ki takura mun."
Harara Fadwa ta sakar ma Ilham ' cikin zolaya suka tashi suka nufi kitchen.
Fadwa blending kayan miya tayi ta d'aura sanwan miyan, Sannan Ilham ta sauke
shinkafan ta wanke ' ta sake maida ta saman electric.
Bayan sun gama ne ' suka suka koma parlor suka zauna tare da Ige ' suna kallo.

*AROUND 12:00PM*
Su Ilham suka kammala komai ' sai da Fadwa ta d'aban ma mijin ta nashi tukunna,
Suka jera abincin a dinning table ' suna zaman jirar dawowar Yaya Farook.
Suna cikin haka ne Umma ta sauko parlon ' ta same su zaune suna a harabar
parlor.
"Har kun kammala ne?"
"Eh Umma ' mun kammala komai shi kawai muke jira, Hope dai da wuri zai
shigo!."
Cewar Fadwa.
"Insha Allah.!"
Abinda Umma ta fad'a kenan ta sami kujera ta zauna, suka cigaba da kallo.

*** *** *** ***

B'angaren Yaya Khaleel kuwa ' zaune yake a office d'in shi, yana duba wasu takaddu.
Yana cikin haka ne wayar shi ta fara k'ara, D'aukan wayan yayi ' ya duba amma
sam babu suna.
Yaya Khaleel receiving call d'in yayi.
"Hello who's on the line?"
Cewar Yaya Khaleel.
"Ka fito daga waje ' anbada sak'o ne a baka."
Yaya Khaleel muryar na miji yaji.
"OK! but waye?"
"Ka fito dai ' koma waye ai zaka gani, Muna sauri ne.!"
Ok kawai yace ' sannan ya kashe wayar tare da tashi ya fito daga office d'in,
Sakatariyan shi ya iske a zaune ya sanar mata cewa ' zai fita karb'o sak'o.
Haka Yaya Khaleel ya saka kai ' ya fita, Wasu mutane ya hango jingine a jikin
wata babbar mota ' wacce duk tasha tinted.
K'arasawa wajen yayi ' ya basu hannu suka gaisa.
"Kune ke son ganina?"
"K'warai kuwa!."
Wani dake sanye da bak'in speck ne ya bashi amsa ' tare da cuna mashi bindiga daga
cikin shi.
"Subhanallah!."
Abinda Yaya Khaleel ya furta kenan ' cike da tsoro.
"Wannan ne sak'on naka, saboda haka shiga mota mu tafi!."
"Subhanallah! Bayin Allah menai muku?.
D'ayan ne ya bud'e baki ya ce.
"Kada ka sake ' kayi wata k'wak-k'warar motsi, inba haka ba zamu harbe ka ' so
just get in."
Bud'e motar sukayi ' Yaya Khaleel cike da addu'a a bakin shi, Haka suka tunkud'a
shi ciki.
Yana shiga ya iske wasu a zaune ' Yaya Khaleel bai ankara ba yaji anfesa mashi
wani abu, Nan ya fara fita hayyacin shi ' take ya rasa inda yake suka ja mota suka
wuce.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃憣
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*73-74*

*AROUND 1:00PM*
Su Fadwa suna parlor zaman jiran Yaya Farook ' yunwa duk ta ishe su.
"Ni dai Umma ' muci abinci idan ya iso sai yaci nashi, Umma yunwa nakeji
Allah."
Cewar Fadwa.
Ilham ce tayi saurin taron numfashin ta ' da cewa.
"A'a Yaya Farook d'in guda? Gaskiya ki bari aci gaba d'aya."
Wani haushi ne ya lullub'e Fadwa, A zuciyar ta tace.
"Mtsw nikam ' yanzu ko sunan shi banson inji an fad'o, To meye ma dalilin shi
na dawo wa?."
Umma ce ta katse mata tunani ' da cewa.
"A'a ba takura! Je ki zuba abinci kici ' nima dai naga kamar bazai shigo da
wuri ba.
Fadwa tashi tayi tana ma Ilham dariya ' ta k'arasa wajen dinning table tayi zaman
ta, Sannan ta zuba abincin ta fara ci cikin kwanciyar hankali.
Sai da Fadwa ta gama ' tukunna ta tashi rik'e da plates d'in ta a hannu zata
shiga kitchen suka ji sallama, Cak Fadwa ta tsaya ' nan su Umma suka mimmik'e tsaye
tare da amsa sallamar.
Fadwa juyowa tayi a hankali ' ganin Yaya Farook ne yasa ta amsa sallamar tare da
bud'e hak'ora.
Sannu da dawo wa kawai suke mashi ' Ilham ta karb'i jakkar dake hannun shi cikin
jin dad'i.
"Sannu da isowa Farooku."
Cewar Ige.
"Haba tun d'azu muke ta jiran shigowar ka ' har Fadwa tayi gajin hak'uri ta ci
abinci."
Jin haka yasa Yaya Farook mai da kallon shi kan Fadwa ' wacce ke rik'e da plates
a hannu, Had'a ido sukayi ta sake mashi dariyar yak'e tare da cewa.
"Sannu da dawowa ' babban Yaya!."
"Yawwa."
Kawai yace ' sannan ya cewa Umma.
"Umma ' kuna da bak'uwa bari in shigo da ita."
Nan ya juya ya fita ' cike da mama ki su Umma suke kallon juna.
"Bak'uwa kuma?."
Cewar Fadwa.
Nan ta yatsine baki ta juya ' ta wuce kitchen don ajiye plate d'in da ke hannun
ta gami da wanke hannu.
Yaya Farook shigo da bak'uwar yayi cikin parlon biye a bayan shi, Wa ta kyak-
kyawar mace ce chocolate colour ' wacce bazata wuce 22yrs ba, Yaya Farook
introducing d'in ta yayi wajen su.
"Umma wannan sunan ta Safeena! Daga Bangladesh muka had'u da ita, A cen family
d'in ta da kowa nata suke ' kuma...."
Nan Umma ta dakatar da shi ' da cewa.
"Haba Farook! A tsai tsaye haka? aiko ruwa ne kwa bari kusha ko?."
Murmushi Yaya Farook yayi ' wanda sai da kyan fuskar shi ya bayyana.
Umma jagora tayi musu ' zuwa wajen dinning table, Ige da Ilham na biye da su.
Bayan sun zauna ne Fadwa ta fito daga kitchen zuwa parlor ' idon ta na kan
Safeena wacce ta bata baya.
Cikin hanzari Fadwa ta k'arasa wajen dinning table d'in don ta ga wace ce;
Fadwa jan kujera tayi ta zauna ' suna kallon kallo sa Safeena.
"Umma wace ce wannan?."
Fadwa tayi tambayar ' idon ta akan Safeena.
"Tare da Farook suka zo."
"Sannun ki da zuwa.!"
Cewar Fadwa.
"Yawwa sannu."
"Meye sunan ki?."
Safeena harta bud'e baki zatayi magana Umma ta dakatar da ita ' da cewa.
"Haba Fadwa ' amma kya bari dai ta gama ko? Sunan ta Safeena."
Murmushi Fadwa tayi wa Umma ' sannan ta maida kallon ta kan Ilham, Wacce abincin
ta kawai take ci.
"Ilham k'arfe nawa don Allah?."
"Babu waya a tare dani!"
Yaya Farook duba wristwatch d'in hannun shi yayi.
"2:22pm yanzu."
Fadwa na jin haka ' ta tashi tsaye zata bar wajen Yaya Farook ya tsaida ita da
cewa.
"Me zakiyi?."
"Wallahi Yaya Khaleel ne ' naji shi shuru, Shine zanje in duba ko ya riga ya
shigo."
"Ok."
Abinda ya ce kenan ta juya ' ta wuce sashen ta, Ta na shiga ta zarce d'akin ta '
wayar ta ta fara duba wa amma sam bata gani ba.
"Oh na tuna ' tunda nayi aure ban sake amfani da phone d'ina ba, Tabbas tana
d'akin Ilham."
Tana fad'in haka ta juya ta koma sashen su Umma ' kai tsaye ta zarce inda Ilham
take ta janyo hannun ta.
"Fadwa meye haka? Abinci fa nake ci!."
"Yes i know."
Fadwa janta tayi har zuwa d'aki sannan tace.
"Ilham don Allah! Waya ta zaki taya ni bincikawa."
"Tana nan ' na adana miki ai."
"Yawwa to d'auko min."
Ilham wajen drower d'in gado ta nufa ta bud'e, Sannan ta d'auko wayar ta mik'a
mata.
"Thanks sis ' to bani number d'in Yaya Khaleel."
Ok kawai Ilham ta ce ' tukunna taje bakin gado ta hankad'a pillos ta d'auko
wayar, Nan ta fara karanto ma Fadwa number d'in.
Sai da Ilham ta gama ' sannan Fadwa tayi dialling numbern, Ringing wayar tai
tayi ba'a d'aga ba harta tsinke.
"I hope shikenan?."
Cewar Ilham.
Kai kawai Fadwa ta d'aga mata ' sannan Ilham ta juya ta wuce.
Nan Fadwa ta sami waje ta zauna ' ta cigaba da kiran wayar, A k'alla sai da
taimashi 5 missed calls ' tana cikin na shidan ne taji anyi rejecting.
Nan take Fadwa ta mik'e tsaye gami da dafe k'irjin ta.
"To ko ansace wayar ne? Ko kuma yana meeting!."
Abunda ta dunga ayyana wa kenan ' ta baro d'akin ta dawo parlor, Gani tayi har
sun gama cin abincin sun dawo suna kallo ' haka yasa ta zarcewa inda suke ta zauna
cike da tunane tunane kala kala a ranta.
" 'Yan nan lafiya? Naga kinyi wani iri ne!."
Cewar Ige.
Hakan yasa kowa ya maida kallon shi akanta , Murmushin yak'e Fadwa tayi had'i da
cewa.
"Wallahi! Number d'in Yaya Khaleel ne nake ta kira ' amma ba'a d'agawa k'arshe
ma rejecting yayi, Kuma yace mun 2:00pm zai dawo."
Cike da damuwa ta k'arashe maganar.
"Ina ce yau ya fara zuwa office d'in?.".
Cewar Umma.
"Eh yaune ya fara."
"To k'ila aikin ne yayi mashi yawa, Kinsan dole yaje ya iske aiki sosai."
Kai kawai Fadwa ta d'aga ma Umma ' amma ita dai jikin ta yana bata kamar ba
lafiya ba.
"Amm... Umma wannan dai sunan ta Safeena ' kamar yadda na fad'a, Kuma Umma ita
ce wacce mukayi alk'awarin aure tsakanin mu.
Fadwa mai da hankalin ta tayi ' akan abunda Yaya Farook ke fad'a, Sannan ya ci
gaba da cewa.
"Umma ba komai yasa ta biyoni ba ' illa yardar da tayi dani! Da kuma son ganin
family d'ina da take so, Umma kuma bata taho nan ba sai da iznin iyayen ta ' kuma
suka ce idan na tashi dawo wa inzo da wani nawa don ayi maganar aure, Kasan cewar
sun gaji da zaman ta gida babu miji."
"To Alhamdulillah! Naji duk abinda ka fad'a Farook ' Allah ubangiji ya nuna
mana ranar lafiya, Insha Allah idan Abban ku ya dawo zan sanar dashi komai."
Cewar Umma.
Safeena ba k'aramin dad'in kalamin Umma taji ba ' ganin yadda aka karb'e ta hannu
bibbiyu babu tsangwama.
"Ilham tashi ki d'auki trolley d'in ta gata cen bakin k'ofa, Ki kai ta d'aki
tayi wanka ta huta."
To Ilham tace ' tukunna taje d'auki trolley d'in kamar yadda aka umarce ta.
Fadwa tashi tayi ' ta wuce sashen ta jiki a sanyaye, Bayan wuce war tane Yaya
Farook yake tambayar Umma cewa.
"Umma wannan kuma wacece?."
"Oh yaran zamani ' ai dama ba sanina zakayi ba."
Cewar Ige.
Abun ne ya bawa Umma dariya ta ce.
"To Ige ce dai ' daga k'auye take, Kuma abokiyar wasa ce a tsakanin ku."

*Dedicated To My Fan's.*
馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

#IG: @Bae_Seema 鉂�

*75-76*

Fadwa tana shiga sashen ta ' ta zauna a parlor saman kujera, Dialing number
d'in Yaya Khaleel ta sakeyi ' cikin sa'a aka d'aga wayar, Cikin muryar damuwa Fadwa
ta fara magana.
"Hello! Sweetheart ' fisabilillahi haka mukayi dakai? Tun d'azu nake cikin
damuwa wallahi, Kuma na kira ka baka d'aga ba why?".
Tana gama rufe baki ' taji an b'arke da dariya, Wata murya taji wacce bata Yaya
Khaleel ba ' hakan yasa ta tsora ta matuk'a.
"Ke!!!."
Ta ji an daka mata tsawa ' har sai da gaban ta ya fad'i.
"Baki ba mijin ki! Don bazai tab'a dawowa gareki ba!!, Zamu kashe shi ' bari ma
kiji."
Nan mutumin ' ya ware hannun shi ya zubama Yaya Khaleel duka a ciki ' wanda yake
a d'ad'd'aure, Haka Yaya Khaleel ya saki wani wahalallan k'ara.
Nan take Fadwa ta kama baki ' hawaye suka fara mata zarya a fuskar ta.
"Kinji ko?."
"Don Allah kayi hak'uri ka sakarmin mijina, Ko nawa kakeso ni zan ba..."
Bata kaiga k'arasa wa ba aka kashe ' Fadwa ihu ta saki mai sauti tare da sakin
wayar a k'asa ta zuk'unna tana kuka.
"Wayyo ni Fadwa na shiga uku...!"
Su Umma ne suka shigo sashen nata a guje ' cikin tashin hankali, Su ka isketa a
zuk'unne ta d'aura hannu biyu akai.
"Fadwa lafiya? Meyafaru?."
Cewar Umma.
Nan ta rik'a musu nuni da wayar ' cikin kuka.
Hankalin Yaya Farook kuwa ' inyayi dubu ya tashi, K'arasa wa kusa da ita yayi '
ya zuk'unna inda take.
"Meyasa bazaki bud'e baki kiyi bayani ba? ' don Allah ki fad'a mana meyafaru?.
"Yaya Farook zasu kashe mun miji! ' don Allah ka taimaka min karsu kashe shi,
Ina son shi."
Nan ta juya ta kalli Umma ' wacce idon ta duk ya cicciko da hawaye.
"Umma ' Umma don Allah ' ki fad'a musu karsu kashe shi..."
Ige karan kanta abun tsoro ya bata sosai ' hakan yasa ta koma gefe ta takure.
Yaya Farook daka ma Fadwa tsawa yayi ' har sai da gabanta ya fad'i.
"Fadwa!!! Ki natsu mana ' ki fad'a mana abinda ke faruwa.!"
Cikin rawar baki Fadwa ta fad'a mashi duk abinda ya faru.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!."
Abunda suka furta kenan a tare ' Umma jiri ya d'ibe ta zata fad'a Ige tayi saurin
rik'o mata hannu suka sami waje suka zauna.
Yaya Farook mik'ewa yayi ' yayi ta maza ya fita daga waje ' ya ciro wayar shi
daga aljihun shi, Yayi dialing number d'in Abba.
Bayan Abba ya d'aga wayar ne ' Yaya Farook ya sanar mashi duk abinda ke faruwa,
Nan take Abba ya rafka salati ' sannan ya ce.
"Zan kira commissioner of police in sanar dashi komai ' Insha Allah Khaleel
bazai mutu ba, Kuma nima gani nan dawo wa."
Ok kawai Yaya Farook ya ce ' sannan ya koma ciki aka cigaba da lallashin ta.

*** *** ***

Bayan Safeena ta fito daga wanka ne ' harta gama kintsawa, Sannan ta fito parlor
' ganin babu kowa a parlon ne yasa ta koma ciki wajen Ilham ' wacce ke amfani da
wayar ta.
"Ilham babu kowa a parlor ' ina suka je?."
"To k'ila suna waje ne ' yawwa bari ma mu shiga part d'in Fadwa."
Ilham ta fad'a tare da mik'ewa tsaye suka bar d'akin, Sashen Fadwa suka nufa '
nan Safeena da Ilham suka fara jin shesh-shek'an kuka.
Cikin hanzari suka k'arasa ciki da sallama d'auke a bakin su, Carko carko sukayi
a tsaye ' ganin yadda fuskar kowa ke d'auke da damuwa.
"Farook ' is everthing alright?."
Safeena tayi tambayar ' ba tare da ya bata amsa ba.
Ilham wajen Umma ta je ta zauna ' tana kallon yadda hawaye ke zuba a fuskar ta.
"Umma ' don Allah meke faruwa?."
Umma kasa cewa komai tayi ' sannan Ilham ta maida kallon ta ga Ige.
"Ige don Allah ki fad'a mun meya faru?."
"Ilham Khaleel ne aka sace ' kuma sunce kashe shi zasu yi."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."
Nan Fadwa ta sake fashewa da kuka ' da sauri Ilham ta juyo ta kalle ta, Yaya
Farook dafe kanshi yayi ya tashi da sauri ya bar wajen ' hakan yasa Safeena juyawa
zata bishi ' yayi saurin dakatar da ita tare da mata nuni da hannu alaman ta tsaya.
Ilham tashi tayi ' ta sauko k'asa inda Fadwa ke zaune dirshen tana kuka.
"Sis?."
A hankali Fadwa ta d'ago kai da rinan nun idanun ta ' ta kalli Ilham.
"Am here for you! Kiyi hak'uri ki bar kuka, Insha Allah Yaya Khaleel zai
bayyana ' kuma babu abinda zai same shi."
Ilham ta fad'a tare da kwanta da kan Fadwa bisa cinyar ta, Ta na bubbuga bayan ta
a hankali ' tukunna Safeena ta sami waje ta zauna.

*** *** *** *** *** *** ***

*AROUND 4:00PM...*
Lubna na zaune a parlor ' tare da Mummy da Daddy suna fira, Wayar ta ta fara k'ara
alaman kira ' da sauri ta kalli wayar number ce babu suna, Nan ta tashi cikin sauri
ta wuce d'aki tare da receiving call d'in.
"Hajiya! Mutumin nan fa na hannun mu ' yanzu haka ma a d'aure yake!."
Ya fad'a yana dariya!.
"What!? Khaleel d'in? Amma haka mukayi daku? Inace na fad'a muku cewa ku barshi
ni na hak'ura?.."
"Haha!.. Haba hajiya! Karfa ki manta kin riga kin fad'a mana address, Kinga
kuwa dole muje mu yagi namu kason ko?."
Rik'e baki Lubna tayi ' tana furta Innalillahi.
"Kar ki damu hajiya! Bazamu kashe shi ba ' wahalar dashi kawai muke, Har mu
samu mu sami abinda mukeso!."
"A'a kaga! Nidai ku sake shi please ' duk nawa kuke buk'ata nizan baku."
Dariya ya sakar mata ' sannan ya kashe wayar ba tare da yace mata komai ba.
Lubna wulli tayi da wayar saman gado ' ta kama bakin ta da hannu biyu, Ta fara
zagaye d'aki.
"Na bani ' ni Lubna! Zan sa kaina cikin matsala, Insha Allah gobe zanje gidan
su Khaleel na fad'a musu komai."
Lubna a bakin gado ta zauna ' tana nazarin irin halin da Khaleel ke ciki, Kila ma
babu abinda yaci ' nan tayi zambur ta mik'e tsaye cike da damuwa bayyane a fuskar
ta.
"Bazan iya bari har gobe ba! ' Yau zanje gidan su insanar."

*** *** *** *** ***

B'angaren Fadwa kuwa har yanzu kuka takeyi ba k'auk'auta wa.


"Ilham kama ta ' mu koma cen sashen zaifi."
Cewar Ige.
Nan suka tashi gaba d'ayan su ' Ilham ta rik'ewa Fadwa hannu ita kuma Ige rik'ewa
Umma hannu suka koma sashen su, Yaya Farook kuwa yana garege yana zaman jirar
isowar Abba.
Abba ba shi ya iso gidan ba ' sai wajen 6:30pm, Haka Abba yayi packing motar shi
ya fito ' Yaya Farook ya tareshi.
"Sannu da isowa Abba."
"Yawwa Farook."
Abba ya amsa tukunna suka k'arasa ciki, Sallama Abba yayi ma su Umma suka amsa '
tare da mik'ewa tsaye, Umma ce ta tako har inda yake cikin kuka.
"Alhaji! Kaji abinda ya faru da Khaleel ko?."
"Ki kwantar da hankalin ki ' police suna nan suna aiki akai.
Abinda ya fad'a kenan yaja hannun ta suka koma suka zauna ' Fadwa wacce ke zaune
kasa cewa komai tayi sai dai hawaye da keta kwaranya a idanun ta.
"Fadwa?."
Abba ya kira sunan ta ' ta sigar tausayawa, Ta d'ago kanta ta kalle shi.
"Na'am Abba."
"Kar kisa damuwa a ranki kinji ko? Insha Allah Khaleel zai dawo."
Girgiza kai Fadwa tayi cikin sark'ewar murya tace.
"Abba ' how sure are you cewar zai dawo? Abba inhar suka kashe shi ' to nima
bana tunanin zan iya rayuwa."
Abba girgiza kai kawai yayi ' alaman tausaya wa, Sannan Ilham ta cigaba da
lallashin ta.
Yaya Farook waje ya samu ya zauna ' yayi dailing number d'in Yaya Khaleel amma a
kashe.
Yana cikin haka ne ' suka ji sallama, A tare suka juya don suga waye.
Lubna ce ' a tsaye a bakin k'ofa rik'e da handbag d'inta a hannu.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槝

Follow #IG @Bae_seema 鉂�


[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

*79-80*

Sannan su Umma suka amsa sallamar ta ' Fadwa tsayawa tayi a gaban ta suna kallon
kallo nad'an lokaci, Tukunna ta ce.
"I hope kinzo min da labari mai dad'i."
Lubna k'arasawa tayi daga ciki ' ba tare da tace wa Fadwa uffan ba, Ta sami waje
ta zauna.
Bayan sun gaisa ne ' ta ciro wayar ta daga handbag d'inta tace.
"Umma! Jiya ban samu damar kiran su ba ' amma yau insha Allah zan kirasu agaban
kowa."
Fadwa ce ta dawo ta zauna ' cikin b'acin rai tace.
"Aiba mijin ki bane ' kuma bakisan halin da yake ciki ba, Shiyasa baki damu da
ki kira wad'an nan k'artan naki ba ' domin su sakar min mijina."
Wani mugun kallo Lubna ta sakar wa Fadwa ' gami da cewa.
"Fadwa ba don ke nazo wajen nan ba ' soyayyar Khaleel ce da har yanzu take
d'awainiya dani, And let me warn you! Karki sake fad'amin maganar banza ' because i
can change my mind at any time."
Fadwa har ta yunk'ura zata kai mata duka ' Umma ta daka mata tsawa.
"Fadwa! meyasa ke baki jin magana ne!! Ke bazaki tab'a kwantar da kai kibi
komai a hankali ba?".
"Umma ' ki bari in koya wa wannan 'yar barikin hankalin, Harni zata kalla tace
' soyayyar shi ne a ranta?!".
Ige ce ' ta taso tazo har inda Fadwa take ta kamo hannun ta, Suka koma suka
zauna waje d'aya tana lallashin ta.
"Ilham je ki kiramun Farook ' ni kuma bara inkira Abban ku."
To Ilham tace ' sannan suka sa kai ita da Umma suka tafi kiran su.
"Lubna! Please ki rik'a hak'uri da ita, Kinsan dama sai irin haka ta faru '
tunda taimako zakiyi kawai ki taimaka, karki saka wani haushi a ranki."
Cewar Safeena.
Fadwa yunk'urin tashi tayi Ige tayi saurin rik'e ta gami da girgiza mata kai.
"No Ige just let me talk!".
Kasan cewar Ige bata san abunda Fadwa ta fad'a bane, Hakan yasa ta sake ta '
Fadwa taje har gaban Safeena tare da tsira mata hannu.
"Baki san wacece ita ba! So please don't involved yourself in this matter!,
besides ke da kike bak'uwa ma! Ina ke ina shish-shigi?".
Hakan yayi dai dai ' da shigowar Yaya Farook da Ilham, Umma kuma da Abba cikin
parlon.
"Meke faruwa anan wajen?".
Cewar Abba.
"Rashin kunyar da take min ne ' a gaban idon ku, To yau shine take wa wannan
baiwar Allan ' ni Lubna Allah na rok'e ka haukan da Fadwa ke dashi akan ta, To
karya sami sauran mutane."
Lubna ta fad'i haka tare da d'aga hannun ta sama.
Ilham ce tazo taja hannun Fadwa suka zauna ' tare da cewa.
"Fadwa please ' ki daina kula ta, Ki bari idan Yaya Khaleel ya dawo to koma
mene ne ' sai ayi shi."
Hawaye ne ya zubo ma Fadwa a ido ' cikin sauri ta share hawayen.
"Lubna ki kira su please ' don asan inda suke, Nai waya da inspector d'in
police d'in suna nan zuwa yanzu."
"Ok".
Abunda Lubna ta ce kenan ' tayi dailing number d'in 'yan daban, Akayi sa'a kuwa
ringing d'ays tayi ogan nasu ya d'auka ' Lubna tayi sauri ta saka wayar a
loudspeaker.
"A'a yau kuma kiran ki ne ' da sassafe haka?".
"Eh aiba abun mamaki bane ko?".
"Eh haka ne ' gani ga wannan mutumin, Har yanzu a d'aure yake tun jiya ya kasa
cin komai ' amma hajiya ya kika sa wayar ki a loudspeaker?".
Nan Lubna ta zaro ido ' ta kalli su Umma wad'an da suke a tsaitsaye cike da
fargaba.
"Wace irin tambaya ce wannan? Kaya nake sanyawa shiyasa ' ai kasan haka nan
kawai bazan saba, A tak'aice dai kuna ina ne? Don inaso inzo yanzun nan ' inason in
ganshi ne kuma zan taho muku da d'an kud'i."
"Hahaha Hajiya kenan ' to muna tsohon ginin dake bayan gari, Amma fa ko kinzo
bazamu baki shi ba!."
"To shikenan ' sai dai nazo d'in."
Tana gama fad'in haka ta kashe wayar, Sannan ta juyo ta kalli Fadwa wacce hawaye
ne kawai ke kwaranya mata a fuska.
"Sai ki kwantar da hankalin ' mijin ki ya kusa dawo wa gare ki, Kuma ina fatan
laifina zai goge a idon ki ' don kuwa bazan so naje gidan miji na da zunubi a kai
ba."
Fadwa kauda kanta kawai tayi ' tare da sanya hannu a fuskar ta ta share hawaye.
"Thank you so much! Lubna kinyi mana k'ok'ari matuk'a!"
Cewar Abba.
Umma kuka kawai takeyi mara sauti.
"Haba Umma aiba kuka zakiyi ba ' gode wa Allah ya dace muyi."
Umma samun waje tayi ' ta zauna kusa da Ige, Tana share hawaye.
Sallama sukaji anyi ' hakan yasa suka juya gaba d'ayan su..
Inspector ne ' ya shigo ciki sanye da kakin shi a jiki, Ya k'arasa har inda suke
zaune ' Abba ya mik'e tsaye suka gaisa tukunna yayi musu jaje.
"Tare nake da yara na a waje ' hope a shirye kuke!".
"Insha Allah! Tare da wannan baiwar Allan zamuje ' don tayi magana dasu kuma
sun fad'a mata wajen, Infact dai yaran ta ne".
"OK muje ko?".
Haka Lubna ta tashi ' har zasu wuce, Fadwa ta tsaida su da cewa.
"Abba ' nima zan biku."
Yaya Farook ne ya waigo ya kalle ta ' cikin b'acin rai.
"A gida zaki tsaya! Tare da su Umma, Kima daina wannan maganar banzan."
Koma wa Fadwa tayi ta zauna ' sannan su Abba da Yaya Farook da Inspector d'in
suka juya suka wuce.
Lubna tana fita ta shige cikin motar ta ' suka bita a baya, Wajen waje ne mai
nisa ' don sai da suka dad'e suna tafiya sannan suka kai inda tsohon ginin yake.
Suna gaf dasu k'arasa wajen ne Lubna taja burki ta tsaya, Sannan ta fito suma
suka firfito.
"Bara in fara shiga tukunna".
Abinda tace kenan ' sannan ta k'arasa wajen da k'afa ta shige cikin ginin, Sai da
tad'an jima sannan suka bi bayan ta ' Abba da Yaya Farook suna daga waje.
Bayan ta shiga daga ciki ne ' ta sake kiran ogan 'yan daban, Yayi mata kwatance
da inda suke ' kasan cewar cikin ginin k'usurwa k'usurwa sunyi yawa.
Haka Lubna tabi kwatan cen da yayi mata ' tashige wani d'aki, Tana shiga ta fara
sauke idanun ta akan Yaya Khaleel ' wanda yake zaune saman kujera a d'aure idanuwan
shi duk sun kumbura saboda duka.
Cikin hanzari Lubna ta k'arasa inda yake ' ta zuk'unna idon ta cike da k'walla,
Shi kuwa uku uku kawai yake gani ' don baima san wanda ke kanshi ba.
Cikin kuka Lubna tace.
"Khaleel... haka suka maida mun kai?".
"Hajiya! Muna fatan dai ke kad'ai kika shigo wajen nan!".
Lubna mik'ewa tayi tsaye gami da share hawayen ta, Sannan tace.
"Ni kad'aice mana! Kuma don Allah na rok'e ku ' ku barni in tafi dashi gida."
Ogan umurtan d'aya daga cikin yaran nashi nayi, Da yaje ya lek'a ya duba yagani.
"Hajiya ' inhar aka gano cewa bake kad'ai kika zo wajen nan ba to zan kashe ki
daga ke har shi, Kuma maganar kud'in da kika ce zaki kawo mana kenan k'arya ce
kawai kikeyi!".
"Wallahi a'a, Kunsan ai bantab'a yi muku alk'awari na sab'a ba ko?".
"Eh haka ne hajiya! Amma don me zaki damu dashi haka? Bayan kin fad'a mana baya
son ki! ' kuma inda 'yan uwan shi sun damu dashi ai bazasu kyale shi haka ba".
Lubna juya wa tayi ' ta kalli Yaya Khaleel, Zuciyar ta cike take da tausayin shi.
Yaran da Ogan ya aika ne ' ya dawo a guje yana haki!.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
*_#IG: Bae_Seema 鉂*
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me
*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

*77-78*

Fadwa wuf tayi ta mik'e tsaye cike da mamakin shigowar ta cikin gidan.
"Me ya kawo ki gidan nan?."
Fadwa ta fad'a tana share hawayen da ke fuskarta, Kallon uku saura kwata Lubna ke
mata ' hakan yasa Fadwa k'arasa wa har gaban ta, Ta d'aga hannu ta sharara mata
mari a fuska.
A gigice Lubna ta dafe fuskar ' cikin wani irin k'ara.
"Ahhhhgh."
Nan Ilham ta taso tazo ta rik'e Fadwa, Su Ige da Yaya Farook tasowa sukayi sukai
kansu.
"Ke baki da hankali ne? Ya zaki mare ta haka? ' ku bari muji da d'aya mana!."
Cewar Yaya Farook.
"Kad'an ma ta gani wallahi ' inda ba'a raba ba kashe kine kawai bazanyi ba,
Banza kawai karuwa mai bin mazajen mutane."
Nan Fadwa ta sakeyo wani kukan kura ' zata sake marin ta Yaya Farook ya rik'e
hannun.
"Meyasa ba kyajin magana ne waike! ' ashe b'atan mijin ki ma bata dame kiba
kenan?."
Fadwa fincike hannun ta tayi daga nashi ' ta maida kallon ta kan Lubna, Wacce
har yanzu rik'e take da fuska ' Umma da Abba kuwa suna gefe a zauna abun duniya duk
ya ishe su.
"To kwartuwa! Ai saiki fad'i abunda ya kawo ki."
Safeena ce taja hannun Fadwa ' suka koma suka zauna.
"Haba! Fadwa ' ai fad'a ba naki bane yanzu."
Wata harara Fadwa ta watsama Safeena ' aiba arzik'i ta fita harkar ta.
Yaya Farook da Ilham ' suma komawa sukayi suka zauna.
"Baiwar Allah ' muna sauraron ki."
Lubna k'arasa ciki tayi ' ta sami waje ta zauna, Sannan ta d'ora k'afa d'aya kan
d'aya.
"Nidai suna na Lubna ' kuma ni budurwar Khaleel ce ada, Yana sona kuma nima
inason shi."
Had'a ido sukayi da Fadwa ta kalle ta ' ta watsar sannan ta cigaba da cewa.
"Wato a tak'aice dai nazo ne akan maganar kidnapping d'in Khaleel da akayi.
Nan Umma da Abba ' suka mik'e tsaye a tare suka ce.
"Kinsan inda yake ne?."
"Yes ' har mutanen ma nasani."
Gaba d'ayan su mik'ewa tsaye sukayi, Idanun Fadwa kyar akan Lubna.
"Baiwar Allah su waye? Ki fad'a mana don Allah."
Cewar Umma.
Nan Lubna ta kwashe duk abinda ya faru ' ta fad'a masu.
"Kun gani ko? So take ta raba ni da miji na ' duk abinda ya faru da miji na
itace sila, Don Allah ku barni inyi k'asa k'asa da ita anan wajen."
Fadwa ta fad'a haka cikin kuka.
"Umma don Allah ku zazzauna abi komai a hankali."
Cewar Yaya Farook.
Bayan sun zauna ne ' Yaya Farook yace.
"Yanzu ke basu fad'a maki inda suke a b'oye ba?."
"Basu fad'amun ba ' amma idan na nemi nasan hakan wannan abune mai sauk'i."
"Lubna ko?."
Ta d'aga mashi kai alaman Eh, Sannan ya ce.
"Zamu so ki taimake mu akan hakan ' don nasan dama taimako ne ya kawo ki."
"K'warai kuwa, Amma kasan cewar yanzu dare yayi *8:30pm* zamu bari sai gobe da
safe ' don zanje gida yanzu."
Yaya Farook zaiyi magana kenan ' Fadwa ta tari numfashin shi.
"Mtsw! Wai don kinga ana neman taimakon ki? ' ko kuwa don miji na ne?, Idan da
mijin kine fisabilillahi ya zakiyi?."
"Fadwa ' can't you be patient? Zamu iya jira har goben muddin wani abu bazai
same shiba."
Cewar Abba.
Fadwa shuru tayi ' idanuwan ta na zubar da hawaye.
"Lubna zaki iya tafiya ' Allah ya kaimu goben.!"
Lubna tashi tayi zata wuce ' har ta kai bakin k'ofa, Fadwa ta tsai da ita da
cewa.
"Inaso ki sani cewa ' ni Fadwa wallahi bazan tab'a kyale ki haka ba, Saboda duk
wannan abun da ya faru da miji na ' ke ce sila."
Lubna girgiza kanta kawai tayi ' tare da jan tsaki, Sannan tace.
"Da zakiyi ' hak'uri nima biki na saura kwana uku, So kinga kuwa babu abinda
zanyi da mijin ki ' kawai zan taimaka maku ne don har yanzu akwai sauran tausayin
sa a cikin zuciya ta".
Tana fad'in haka ta fice.
"Haba Fadwa! Bakya tunanin wad'an nan magan ganun zasu iya sawa ta cenja
ra'ayin ta?.
Cewar Yaya Farook.
Banza tayi ta kyale shi ' tukunna yaja tsaki gami da cewa.
"Abba ' muje masallaci muyi sallah, don bamu sami magrib ba ' ga isha'i ma."
Ok Abba yace, Sannan suka tashi suka fita zuwa masallaci.
Bayan fitar sune Umma da Ige suka haura sama ' don yin sallah, Fadwa da Ilham da
Safeena kuma ' d'aki suka nufa suma suyi nasu sallolin.
Bayan sun idar ne ' Fadwa ta haye saman gado, Ta sake dasa wani sabon kukan '
Ilham da Safeena suka shiga lallashin ta .
Ko da su Abba suka dawo cikin gidan ' kowa d'akin shi ya zarce cike da fargaban
abinda gobe zata haifar.
Haka suka kwanta babu wanda ya sanya komai a cikin sa, Fadwa kuwa bacci? ai sai
dai b'arawo.

*** *** *** *** *** *** ***

*WASHE GARI*
Da sassafe Fadwa ta tashi ' ta riga kowa tashi, kai tsaye ta wuce sashen ta ' wai
ko a tunanin ta zata ga mijin ta, Amma ko da ta shiga tsit taji ' babu motsin
komai.
"Sweetheart?."
Ta fad'a kamar zatayi kuka ' haka ta shige d'akin shi ta fad'a bathroom tayo
alwala, Sannan ta fito tayi sallah.
Bayan ta sallame ne ' ta tashi tsaye tana k'arewa d'akin kallo.
"Allah ka taimake ni ' Yaya Khaleel d'ina ya dawo lafiya."
Ta fad'i hakan gami da d'aga hannun ta sama.
Fadwa barin d'akin tayi ta dawo parlor ' tayi tsaye tana tuna irin wasan nin da
suka rik'ayi tare da shi, Nan da nan k'walla ta ciko mata ido.
Hakan yasa ta barin sashen nata cikin hanzari ' ta nufi sashen su Ilham, Fadwa
tana tafiya tana share hawaye ' ko da ta shiga iske Ilham tayi wajen dinning table
tana jera cups d'in da za'a sha tea wato breakfast.
Wajen dinning table d'in Fadwa ta nufa ' taje ta zauna tare da sunkuyar da kanta
k'asa.
"Fadwa in zuba miki tea d'in ne yanzu?."
Girgiza mata kai tayi ' tukunna Ilham ta sami waje ta zauna.
Umma da Ige ne ' suka shigo parlon suma suka zauna a wajen, Fadwa da Ilham suka
gaishe su ' sannan Ilham ta zuba musu tea d'in su a cup ta ajewa kowa a gaban shi.
Bayan su Umma sun fara karyawa ne ' Yaya Farook da Safeena suka shigo parlon
suma a tare suka ja kujera ' suka zauna, Kai zakace a d'aki d'aya suka kwana.
Safeena gaishe da su Umma tayi ' tukunna Ilham ta tsiyaya masu nasu tea d'in a
cup ita da Yaya Farook, Safeena ta b'alli bread ta mik'a mashi shima ya b'alla.
"Aww! Ilham na manta ' zubawa Abban ku tea d'in shi a cup ki kai mashi."
Cewar Umma.
To tace ' sannan tayi yadda aka umarce ta.
Ilham bayan ta kaine ta dawo ' ta cigaba da breakfast, Yaya Farook lura yayi da
Fadwa ' don tunda yazo baiga tana breakfast ba.
"Fadwa! Ke kin gama naki breakfast d'inne?".
Kai ta girgiza mashi ' tare da cewa.
"A'a bana jin yunwa."
"What do you mean by ' bakya jin yunwa? Come on ki zuba tea kisha."
D'ago kai tayi ta kalle shi ' idanuwan ta cike da hawaye.
"Yaya Farook kawai bana jin cin komai ne."
Zaiyi magana Umma ta dakatar dashi ' da cewa.
"Farook ' ka kyaleta , Ai tamayi k'ok'ari dole a d'aga mata k'afa don tana
cikin damuwa!".
"Amma Umma ai ya kamata tayi breakfast ' for her own health".
Yaya Farook kallon ta yayi ' yayi k'wafa, Sannan ya tashi ya wuce d'akin shi ba
tare da ya gama breakfast d'in ba.
Safeena kuwa kishi ya riga ya gama turnik'e ta yadda ya nuna damuwar shi akan ta
sosai, Don kuwa ya riga ya bata labarin rayuwar shi ' da wadda sukayi tare da
Fadwa a baya.
Hakan yasa Safeena jan tsaki ' tsakin da batasan zai fito fili ba, Da sauri Ilham
ta kalle ta.
"Lafiya Safeena?".
"Me kika gani?".
"Tsaki kika yi!".
"Well.. am just worried about Farook's health too, Don ya tashi ba tare da ya
gama breakfast ba."
"Oh! Ayya!."
Abunda Ilham tace kenan ' ta ajiye cup d'in hannun ta, Ta rik'o hannun Fadwa tana
tausar ta akan ta daure tasha tea d'in ko kad'an ne.
Suna cikin haka ne ' sukaji anyi sallama, hakan yasa Fadwa yin saurin juya wa
don taga waye.
Lubna ce ' a tsaye cikin pink d'in atamfa rik'e da wayar ta a hannu mai riga
pink ' komai nata pink ta saka, Cikin hanzari Fadwa ta tashi ' ta k'arasa har inda
take.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槡
*IG* *_@Bae_Seema 鉂*
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*81-82*
Ogan ne ya nufo shi cikin sauri.
鈥淵 a? Lafiya ka dawo a haka?鈥�.
Yaron nuni kawai yake yi da hannu ' dakyar ya iya bud'e baki ya ce.
鈥淲 allahi Oga police ne a ciki 鈥�.
Cikin tashin hankali ya juya ya kalli Lubna ' wacce ita ma duk a tsorace take,
Zaro bindiga yayi ya nuna mata.
鈥淜 in yaudare mu! ' kuma bazamu barki ba kema!鈥�.
Cikin tashin hankali Lubna tace.
鈥淓 h na yarda ku kashe ni ' amma ku barshi da rai, Wallahi yana da mata...鈥�
Nan ya dage ya buga mata kan bindiga a goshi ' Lubna zube wa k'asa tayi cike da
azaba ta dafe goshin jini kawai ke zuba.
Nan take yayi setin Yaya Khaleel ' zai harbe shi, Lubna ta d'ago da sauri tace.
鈥淣 ooo! Please don't ' don Allah karka kashe shi pls...鈥�
Ko kafin ta gama rufe baki ' taji tassss!, Alaman harbi.
Police ne suka k'arasa cikin wajen da sauri ' Lubna ganin sune sukayi harbin
hakan yasa tayi ajiyar zuciya, Tare da k'arasa wa wajen Yaya Khaleel tana k'ok'arin
kwance shi.
鈥淜 u ajiye bindigogin ku ' kada wanda ya motsa!.鈥�
Cewar inspector.
Yaran duk ajiye bindigan sukayi a k'asa ' shi kuwa ogan nasu rik'e yake da tasa
yana setin Yaya Khaleel.
鈥淜 afi k'arfin ka aje ne?鈥�.
Ganin yak'ine yasa ya harbeshi a k'afa , hakan yasa shi durk'ushe wa k'asa
bindigan ta sab'ule daga hannun shi tare da sakin wani k'ara.
鈥淎 hhhhhagghh 鈥�.
Nan sauran police d'in da ke tsaye a wajen suka kwashe bindigogin ' sannan suka
tarka ta 'yan daban waje ciki kuwa harda ogan nasu.
Lubna k'ok'arin taimaka wa Yaya Khaleel takeyi wajen ganin cewa ya mik'e sun fita
daga wajen ' amma ta kasa kasan cewar yafi k'arfin ta.
Inspector d'in ne ya taimaka mata suka d'aga kafad'un shi suka jashi zuwa waje,
Don kuwa Yaya Khaleel a wahale yake.
Abba da Yaya Farook ' da suke waje ne, Suka ga anata fito da 'yan daban hakan
yasa su jin dad'i sosai, Cen suka ga an fito da Yaya Khaleel cikin hanzari suka
nufo kansu.
Abba ganin halin da Yaya Khaleel ya shiga ne ' yasa k'walla ta zubo mashi a ido,
karb'ar shi sukayi suka nufu mota dashi ' suka saka shi a ciki.
Lubna kuwa dake ta tare tare da goshin ta ' da yake jini ne ta cire d'ankwalin
kanta ta d'aure wajen sannan ta nufi wajen motar ta.
鈥淏 aiwar Allah! Bazaki iya driving da wannan ciwon ba yanzu! Ki shigo motar mu
' mu nifu asibiti baki d'aya 鈥�.
Cewar Abba.
Haka ko akayi ' Lubna ta mik'awa d'aya daga cikin police d'in nan key d'in
motar ta don ya buyota dashi.
Haka ta shige ta zauna tare da Yaya Khaleel ' suka ja motar suka nufi hospital,
Su kuma police suka zarce station d'insu ' sai wanda Lubna ta bawa key d'in mota ne
ke binsu a baya.
Bayan sun isa harabar asibitin ne ' d'an sandan nan ya fito ya mik'a mata key
d'in sannan ya tari keke napep ya wuce, Yaya Farook ne keta kici niyar fito da Yaya
Khaleel daga motar Abba ya shiga cikin hospital d'in yayi magana aka had'o shi da
nurses guda biyu tare da keken da marasa lafiya ke zama akai.
Haka suka taimaka aka ciro Yaya Khaleel daga mota ' aka d'aura shi saman
keken , Sannan suka tura shi zuwa ciki Lubna tana biye dasu.
Suna shiga aka basu d'aki anan ciki aka kwantar da Yaya Khaleel ' ita kuma Lubna
suka tura ta d'akin wanke ciwo.
Bayan wuce warta ne likitan ya shigo ' suka gaisa da Abba cike da girma mawa ,
Sannan ya fara duba lafiyar Yaya Khaleel.
Sai da ya kammala tukunna ya juyo ya fuskan ci Abba da Yaya Farook.
鈥淎 mma! Meyasa meshi haka? Kamar yayi dambe?鈥�.
Nan Abba ya fad'a mashi duk abinda ya faru ' haka likitan tayi mashi jaje, Sannan
ya ce.
鈥淵 anzu bari inje ' inturo azo a d'ibi jinin shi domin akwai buk'atar yin test
鈥�.
Ok kawai Abba yace ' sannan likitan ya juya ya fice.
Motsi Yaya Khaleel yayi kad'an tare da cewa.
鈥淎 ina nake?鈥�.
Jin abunda ya fad'a ne yasa hawaye suka zubo wa Yaya Farook ' yayi sauri ya
share, Sannan yace.
鈥淜 haleel ' kana hospital ne yanzu haka, Allah ya tsiratar da kai 鈥�.
Ajiyar zuciya Yaya Khaleel yayi ' ya ce.
鈥淚 na Fadwa?鈥�.
鈥淜 arka damu Khaleel ' bari yanzu inje in d'auko su 鈥�.
Cewar Abba.
Haka Abba ya juya ' ya fice zuwa d'auko su Umma dake gida.
Bayan fitar shi ne ' Lubna ta shigo cikin ward d'in tare da Nurse d'in da zata
d'ibi jinin Yaya Khaleel.
Lubna a tsaye ta tsaya ' saitin wajen gadon shi, Saida nurse d'in ta d'ibi jinin
ta wuce ' tukunna Lubna tace.
鈥淚 na Abba? ' ya kamata a sanarwa su Fadwa da Umma 鈥�.
Ta fad'a tana kallon Yaya Farook.
鈥淓 h yaje kiranshi 鈥�.
鈥淥 k! Ni zan wuce gida yanzu ' insha Allah zan dawo nan da 1week, bayan nayi
aure kenan 鈥�.
鈥淭 o Lubna ' Allah ya kaimu, Gaskiya kinyi halacci ' kuma munji dad'i 鈥�.
Smilling kawai tayi sannan ta juya ta wuce.
Bayan wuce warta tane da d'an mintoci Nurse ta shigo wajen rik'e da drip a
hannun ta, Sai kuwa sakamakon gwajin jinin da akayi ta mik'awa Yaya Farook.
鈥淪 aka makon gwajin da mukayi ' an gano cewa yana da malaria, Gashi nan yanzu
zamu d'aura shi akan anti-biotics ' sannan kullun safiya za'a rik'a mashi gashi
ma'ana za'a rik'a gasa mashi jikin shi da ruwan d'umi 鈥�.
鈥淥 k ' shikenan babu damuwa 鈥�.
Nurse d'in juyawa tayi ' ta fara neman jijiya tukunna tayi setling d'in drip
d'in a jikin shi, Ta juya ta wuce.
Tana fita ne su Abba suka iso cikin harabar asibitin ' cikin hanzari Fadwa ta
bud'e motar ta fita ' ta falla a guje ta shige cikin hospital d'in.
Tana shiga ne aka tsare ta .
鈥淏 aiwar Allah wa kike nema?鈥�.
鈥淒 on Allah inane aka kwantar da wani ' yanzun nan mai suna Khaleel?鈥�.
Nan nurse d'in tayi mata kwatan ce, Haka Fadwa ta k'ara kwasa a guje ta shiga
d'akin, Yaya Farook ganin yadda ta shigo ne tana haki ' yasa shi ya tsaya yana
kallon ta.
Fadwa tsayawa kawai tayi tana kallon Yaya Khaleel ' wanda duk kaman nin shi sun
sauya, K'arasawa kusa da gadon nashi tayi ' da hawaye a idon ta.
鈥淪 weetheart! Haka suka maida mun kai?鈥�.
Ta fad'a tare da shafa fuskar shi ' hawayen ta suka d'igo mashi a fuska, A
hankali Yaya Khaleel ya bud'e idon shi ' duk da yana ganin jiri hakan baisa ya gaza
gane fuskar Babyn shi ba.
鈥淏 aby nah! Stop crying ok?鈥�.
Su Umma ne suka shigo ciki ' kowanen su k'ok'ari yake yaga Yaya Khaleel.
Kowa sannu kawai yake mashi ' cike da tausaya wa.
鈥淪 annu d'an nan gaskiya ka auna arzik'i.鈥�.
Cewar Ige.
Bayan Safeena taiwa Yaya Khaleel sannu ne ' ta juya ta fuskanci Yaya Farook dake
tsaye yayi folding hannayen sa.
鈥淒 ear! mud'an fita daga waje ' inason magana da kai 鈥�.
Ok ya ce mata ' sannan suka fita daga waje.
鈥淗 oney! Ina jinki 鈥�.
鈥淒'azu ne ' Mommy ta kira ni a waje, Ta ce lallai jibi take so ka tura maganar
auren mu 鈥�.
鈥淒 on't worry Honey! zan yiwa Umma magana ' zuwa anjima 鈥�.
Murmushi tayi mashi ' sannan suka koma daga ciki ' shigar su keda wuya! Nurse ta
shigo wajen tare da cewa.
鈥淎 na da buk'atar ku d'an fita daga waje, Saboda mara lafiya na buk'atar hutu 鈥
�.
Da sauri Yaya Khaleel ya rik'e hannun Fadwa, ya ce.
鈥淣 urse ' wannan mata ta ce, Please ki barta tare da dani 鈥�.
Ok tace sannan su Umma da Abba ' suka fita, Yaya Farook da Ilham da Safeena suka
bi bayan su ' tukunna nurse d'in tasa kai ta wuce.
Fadwa a bakin gadon ta zauna ' dai dai saitin kanshi, Tayi pecking d'in shi a
goshi sannan ta fara shafa gashin kanshi a hankali ' tace.
鈥淏 azan tab'a iya jure rashin ka ba Sweetheart, Inda ka barni to babu makawa
za'a biyu babu 鈥�.
鈥淪 hhhhh! Baby nah ' ki daina fad'in haka, Insha Allah tare zamu kasan ce 鈥�.
Sake manna mashi kiss tayi ' a haka har bacci ya kwashe shi.

*Dedicated To My Fan's*
馃憚馃憚馃憚馃槣
*#IG: Bea_Seema 鉂�*
[5/23, 2:57 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

*_@Today my dedication goes to Khadija Kabeer Yunusa(thank u for the covers)you're


such a great fan in any way, Sadnaf(鉂�) & Aisha Garkuwa(鉂�) luv u..._*
*Haba waya ce na manta da JAMEESHA?馃槙, kina raina*

*83-84*

Bayan ya fara bacci ne ' Yaya Farook ya shigo cikin ward d'in, ya same ta
rungume da kan Yaya Khaleel a cinyar ta.
鈥淎 mm... Fadwa ' bara inje in maida su Umma gida, Sun ce suna da b'ukatar suje
su shirya ' sannan su d'an yo abinci.鈥�
鈥淭 o sai kun dawo 鈥�.
Abinda ta ce kenan ' ta maida kanta ga kallon fuskar Yaya Khaleel, Shi kuma Yaya
Farook ya juya ya wuce.

*AROUND 2:00PM*

Su Umma suka dawo cikin hospital d'in ita da Ilham sai kuma Yaya Farook da yake
shine ya tuk'o su.
Ilham rik'e take da cooler d'in abinci a hannun ta, Cikin ward d'in suka shigo
cike da sallama ' suka iske Fadwa a tsaye tana lek'e ta window.
Sallamar su da taji yasa ta waigo ' ta kalle su gami da amsa sallamar.
鈥淪 annu Umma 鈥�.
Cewar Fadwa
Cike da fara 鈥檃 a fuskar ta.
鈥淵 awwa Fadwa 鈥� har yanzu bai tashi ba?鈥�.
鈥淓 h Umma ' ina ganin sunyi mashi allurar bacci ne 鈥�.
鈥淗 aka ne 鈥�.
鈥淜 e ni kizo 鈥� ki rabani da abincin nan, Na gaji 鈥�.
Cewar Ilham.
Murmushi Fadwa tayi ' sannan ta matsa kusa da ita, Ta ansa ta aje a k'asa.
Umma ce taja kujerar dake wajen ta zauna ' ta tsaya tana kallon fuskar Yaya
Khaleel.
Suna cikin hakane Yaya Khaleel ya farka daga bacci ' a hankali ya bud'e idon shi
ya fara saukewa akan Umma, Sannan ya tashi zaune.
鈥淪 annu da tashi 鈥�.
Cewar Fadwa.
鈥淵 awwa 鈥�.
鈥淪 annu Khaleel ' yaya jikin naka yanzu?鈥�.
Cewar Yaya Farook.
鈥淒 a sauk'i bro 鈥�.
Umma ce ta lura da drip d'in da aka sa mashi ya kusa k'are wa, Hakan yasa ta
umarci Yaya Farook da yaje ya kira nurse don tazo ta cire mashi.
Haka Yaya Farook ya fita ' ba tare da wani b'ata lokaci ba suka dawo tare da
nurse d'in.
Nan ta cire drip d'in sannan ta cire cannula d'inda ke jikin shi, Tare da cewa.
鈥淵 au insha Allah ' za'ayi discharging d'inku, Doctor d'in yaje ya dawo ne '
amma kafin nan zan kawo warm water ingasa mashi jikin shi 鈥�.
鈥淥 k ' ba damuwa ai 鈥�.
Cewar Yaya Farook.
Haka nurse d'in ta juya ta wuce ' sannan Fadwa ta zuba ma Yaya Khaleel ruwa a
cup, Ta mik'a mashi.
鈥淣 asan baza ka rasa jin k'ishi ba ko?鈥�.
Murmushi kawai yayi mata ' tukunna ya ansa ruwan yasha, Sannan ya mik'a mata cup
d'in ta ajiye.
鈥淯 mma ' akwai maganar da nakeso muyi nidake tun d'azu mantawa nayi bamuyi ba 鈥
�.
Cewar Yaya Farook.
鈥淚 na jinka Farook ' fad'i kawai 鈥�.
鈥淯 mma ' daman family d'in Safeena ne suka matsa, Akan lallai in tura magabata
na nan da kwana uku 鈥�.
鈥淭 o Farook ' insha Allah za'a tura abubuwan ne suka zo mana a hard'e, K'arshen
tama had'a ku za'ayi dakai da Ilham ayi shi rana d'aya 鈥�.
Jin hakan yasa murmushi ya sub'uto wa Ilham, Tayi sauri ta rufe bakin.
鈥淭 unda kaga auren Ilham ' yau saura kwana 5, To kaga kawai gwara a tura gobe a
sanar musu ' don su shirya 鈥�.
鈥淗 aka ne Umma 鈥�.
Suna cikin wannan maganar ne nurse ta shigo ciki ' rik'e da bucket d'in ruwan
d'umi, Fadwa tana ganin ta tayi wuf ta mik'e tare da cewa.
鈥淏 ara in gasa mashi jikin ' am his wife, so don't bother to 鈥�.
Nurse d'in mik'a ma Fadwa k'aramin towel d'in tayi, Sannan ta juya ta wuce.
Nan Fadwa ta fara gaggasa mashi jikin shi a hankali ' tana daddanna mashi wajen
da yaji rauni da towel, Bayan ta gama ne Ilham ta zuba mashi abinci a plates ta
mik'a mashi.
Yaya Khaleel ansa yayi ya fara cin abincin ' cikin sauri hakan yasa Fadwa tsaya
wa tana kallon shi, Cike da murmushi.
Yana cikin cin abincin ne Doctor ya shigo cikin ward d'in nasu, Gami da yi musu
sallama.
Dukkansu a tare suka ansa sallamar ' tukunna likitan ya mik'awa Yaya Farook hannu
suka gaisa, Sannan ya juya kan Yaya Khaleel.
"Gaskiya sauk'i ya samu Alhamdulillah".
Likitan ne ya fad'i haka tare da juyowa ya kalli Umma.
"Amm...Bayan ya gama cin abincin ma ' zaku iya tafiya gida, Insha Allah ba wani
problem".
"To Alhamdulillah".
Cewar Umma.
Doctor har ya juya zai fita ' Yaya Farook ya tsaida shi, Da cewa.
"Doctor nawa ne charges d'in mu?".
A hankali likitan ya juyo ya kalle shi ' d'auke da fara'a a fuskar shi.
"Haba! Aini baka sanni bane ' amma ni na sanka, Abban ku ya taimake ni a rayuwa
' saboda haka kuje babu komai zan iya yin fin hakan, Ai daga *BABBAN GIDA* kuke".
Murmushi gaba d'ayan su sukayi ' sannan likitan ya juya ya fita, Yaya Khaleel ya
ajiye abincin a gefen sa tare da cewa.
"Umma nina k'oshi haka nan, Mu tafi gida don na k'osa ingan ni a gida".
Dariya suka sake kwashe wa dashi ' sannan Ilham ta d'auki plate d'in abincin ta
maida cikin cooler, suka fara haramar barin cikin hospital d'in.
Su Yaya Khaleel ' bayan sun fito daga hospital d'in ne suka shiga mota suka koma
gida.

*A TAK'AICE...*

Haka Fadwa ta cigaba da kulawa dashi har na tsawon kwanaki uku ' har Yaya Khaleel
ya samu cikakken lafiya.
Abba da Yaya Farook kuwa ' maida Safeena sukayi cen Bangladesh, Abba ya tsaya ya
nema ma Yaya Farook auren ta.
Acen aka d'aura auren Yaya Farook da Safeena , Sannan su Abba suka dawo gida
nigeria ' Kafin gobe a kawo wa Yaya Farook matar shi.
B'angaren Ilham kuwa ' zaune take a d'akin ta tare da Fadwa sai kuma k'awaye
birjit a d'akin, Ado kawai ake cab'awa Ilham ' cikin jajayen riga da skirt .
"Allah sarki Ilham ' gwara ni ina tare da su Umma, ke kuwa Al'ameen zaizo ya
d'auke ki zuwa wani gida".
Nan hawaye suka fara cicciko ma Ilham a ido ' dakewa tayi ta cigaba da kallon
mirror ana mata makeup, Fadwa ta cigaba da cewa.
"Kuma sai da yardar shi ' zaki zo kiga su Umma da Abba dani kaina...".
Nan Ilham tayi sauri ta mik'e tsaye hawaye na sauko mata a fuska.
"Please Fadwa stop it ' bana so, kinyi alk'awarin bazaki sani kuka ba fa!".
Cikin rawar murya Ilham ta k'arasa maganar, Hakan yasa Fadwa ta rungume ta ' cike
da tausayi da bege.
"Am sorry sis ' na daina kinji so ki bar kukan".
Nan Fadwa ta zaunar da Ilham ' ta cigaba da facing d'in madubi, Sannan ta zari
tissue ta share mata hawaye.
Fadwa kallon wristwatch d'in hannun ta tayi, Taga 3:56pm.
"Ilham lokacin tafiya KAMU d'in nan ya kusa".
Fadwa juyawa tayi ta sanar wa k'awayen amarya, domin su kasan ce cikin shiri.
"Ilham bari inje ind'an sake gyara jiki na ko".
Kai kawai Ilham ta d'aga mata alaman to, Sannan Fadwa ta juya ta nufi sashen ta.
Fadwa ko da ta isa sashen ta ' a zaune ta iske Yaya Khaleel , cikin manyan kaya
Farar shadda, rik'e da laptop d'in shi a hannu.
K'arasa wa inda yake tayi d'auke da sallama a bakin ta, Ya amsa mata ' sannan ta
shige jikin shi.
"Sweetheart ' kayi kyau sosai Allah".
"Thank you Baby!".
Tare da manna mata kiss a goshi ' ya cigaba da kallon laptop.
"Wai meye ne ' a cikin laptop d'in, Ni ka bani hankalin ka nan".
Smilling yayi mata ' sannan ya rufe laptop d'in.
"To Baby nah ' gaba d'aya na tattara maki hankali na, Na baki".
Fadwa manna kanta tayi a k'irjin shi, Tana wasa da mab'allen rigar shi tace.
"Sweetheart ' zanje KAMU d'in Ilham, Dama kasan ya zama dole inje ko?".
"A'a bai zama dole ba! Baby nah bana so ko wane tom and jerry ya kallan mun ke,
So ki hak'ura kawai ' dama yau inason jin d'umin jikin mata ta".
Nan Fadwa tayi tsumu tsumu da fuska ' ta turo baki, zata zame jikin ta kenan ya
rik'eta, Ya cigaba da cewa.
"Baby nah ' inason yara please ki bani yara, kinji".
Ya fad'a tare da shafa ruwan cikin ta, Fadwa kuwa gaban ta dukan uku uku yake.
"Sweetheart ' bara inje in fad'a wa Ilham su tafi kawai kar su tsaya jira na".
"A'a yi zaman ki, bari in kira ta a waya".
"A'a karka kira ' ni dai kabarni inje in same ta, in ba haka ba akwai matsala".
Ok kawai ya ce ' sannan Fadwa ta tashi ta fita, Tana fita suka had'e da Ilham da
k'awayen a harabar garege da alamun ita suke jira.
Da hanzari Fadwa ta k'arasa inda Ilham take.
"Amm. Ilham kin san ' yaya za'ayi? Ku fara tafiya kawai, Yayan ki ya sani abu ne
' inhar na gama da wuri zai kawo ni".
"To amma please Fadwa kizo da dawuri ' karki dad'e".
To Fadwa tace ' sannan Ilham suka shige mota, Motaci uku sukayi amfani da ita a
ranar.
Fadwa sai da ta tsaya ta ga wuce warsu ' tukunna ta juya ta koma sashen ta.
Tana shiga ta iske shi ' har ya cire manyan kayan shi, Ya zauna daga shi sai
singlet sai boxer ' murmushi ta d'an mashi sannan ta fiske zata wuce wuce d'aki.
"Baby nah?".
A hankali ta juyo ta kalle shi ' sannan ya yi mata sign da ido cewar tazo nan,
Hakan yasa Fadwa d'aga kafad'ar ta d'aya tare da cewa.
"Um um".
Waro idanu Yaya Khaleel yayi ' tare da yunk'ura wa.
"To ni bara in taso".
Fadwa zabura tayi ta kwasa a guje zata shige d'aki yayi saurin taran gaban ta.
"Oh ashe kin iya gudu haka!".
Kafin ta bud'e baki tayi magana ya sunkuce ta ya sab'a ta a kafad'a, Ya nufi
d'akin shi da ita.
*DEDICATED TO MY FAN'S*
馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:58 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

*_ @Sadnaf I want to be the girl who makes your birthday better. The girl that
makes you say: "My life has changed since I met her." And yes that's me, I wish
you many more lifes ahead Sadnaf ' Happy Buffday!!!馃帀馃帀 _*

*85-86*

Yana shiga d'aki bai dire ta a ko ina ba ' sai saman gadon shi, Nan ya shiga raba
ta da kayan jikin ta ' Fadwa tun tana mutsu mutsu har ta kyaleshi.
Yaya Khaleel daga pant sai brazier ' ya barta dashi, Sannan ya haye saman gadon
' Fadwa kuwa d'ar d'ar kawai takeji a cikin ranta, Haka Yaya Khaleel ya shiga bata
hot kisses ta ko ina.
鈥淏 aby nah ' i missed you so much, so duk abinda zanyi ki barni kinji?鈥�.
Yana maganar yana ninshi sama sama ' Fadwa kuwa kasa cewa komai tayi, Sai kai da
take karkad'a mashi alaman a'a .
Yaya Khaleel hannu yasa ' ya kashe wutar d'akin, Ni *Seemaluv* ganin haka yasa
na juya na fita ' harna nufi parlor najiyo kukan ta, Hakan yasa na dawo da sauri '
na lab'e a jikin k'ofa.
鈥淎 hhhgh Yaya Khaleel ' don Allah kayi hak'uri ka kyaleni...鈥�.
Abinda Fadwa ke fad'a kenan cikin yanayi na kuka.
鈥淣 o ki barni please Baby nah ' ina mararin ki, in kika hana zan iya mutuwa 鈥�.
Kafin ya gama rufe baki ' Fadwa tayi wani wahalallen ihu, Hakan yasa na tabbatar
da cewa ya riga ya sami abinda yake so.
Yaya Khaleel sai da yaji he's well satisfied, Sannan ya sauka daga kan Fadwa '
wacce hawaye ne keta yi mata zarya a fuska, Yaya Khaleel gefe ya koma yayi ruf da
ciki yana maida numfashi.
Sai da yaji ya dawo normal ne ' ya murgino ya dawo kusa da Fadwa, yana shafa
mata gashin kanta tare da cewa.
鈥淎 m sorry Baby nah! I never meant to hurt you ' kema kin sani ko?鈥�.
Fadwa cikin rawar jiki ' ta janyo hannun shi ta share hawayen da ke fuskar ta
dashi, Sannan ta shige jikin shi gami da cewa.
鈥淪 weetheart ' ka rungume ni kaji, Please rungume ni zanfi samun sauk'i 鈥�.
Yaya Khaleel hannu yasa ' ya rungume ta tsam a jikin shi, Yadda kasan za'a k'wace
mashi ita.
Sai da suka d'auki lokaci a haka har bacci yad'an soma kwashe ta, Sannan ya zame
jikin shi zai sauka ' Fadwa tayi firgigit ta tashi zaune.
鈥淚 na kuma zaka je?鈥�.
鈥淶 anyi wanka ne ' kema ki tashi kije ki gyara jikin ki, Bedshit kuma ki barshi
zan cenja wani 鈥�.
Ok Fadwa tace ' tukunna ta koma ta kwanta tare da yin ajiyar zuciya mai k'arfi,
Sai da taga shigar shi bathroom ne itama ta sauka daga gadon ta d'auki zani ta
d'aura sannan ta nufi d'akin ta.
Fadwa bathroom ta fad'a tayi wankan tsarki ' tukunna ta fito ta shirya cikin
doguwar riga 'yar kanti had'i da dogon gele ta yafa akai, Sannan ta fito parlor.
Fadwa ganin Yaya Khaleel tayi a zaune ' cikin k'ananan kaya yana duba wasu
documents, K'arasa wa tayi cikin hanzari ta zauna kusa dashi.
Har ta d'auki remote zata kunna TV, Taji tsayawar motoci ' cikin hanzari Fadwa
ta tashi ta lek'a ta window, Ilham ce daga ni ta fito cikin motar sukuku a gajiye.
Fadwa juyawa tayi ta kalli Yaya Khaleel.
鈥淪 weetheart ' zan d'an fita, Su Ilham sun dawo 鈥�.
鈥淯 m Hum 鈥�.
Kawai ya ce ' sannan Fadwa ta fita cikin sauri, ta tari Ilham.
Ilham ballara mata harara tayi ' zatayi magana Fadwa dakatar da ita.
鈥淪 hhh karma kice komai ' nasan ni keda laifi, Amma yanzu mu shiga daga ciki
tukunna ' sai na sami damar bayani 鈥�.
Haka Fadwa da Ilham suka k'arasa cikin gida k'awaye na biye dasu a baya.
Sai da suka shiga d'aki tukunna Fadwa ta fara bada hak'uri, Dakyar ta samu Ilham
ta hak'uri sannan ta d'aga kai ta duba a gogon d'akin.
鈥淟 a la la!! Har 6:00pm ' ban d'aura abincin dare ba?鈥�.
鈥淲 hy not ki d'iban mashi na nan kawai!鈥�.
Cewar Ilham.
鈥淓 h abunda zanyi kenan ma ' bari inje inyiwa Ige magana, Allah yasa da saura 鈥
�.
Ameen Ilham tace ' sannan Fadwa ta tashi ta nufi parlor neman Ige, Kasancewar
parlon a cike yake da mutane.
Fadwa hangota tayi ' cikin mutane, Hakan yasa taje ta jawo hannun ta suka nufi
kitchen.
鈥淥 h oh 'Yan nan lafiya?鈥�.
鈥淚 ge don Allah akwai sauran abinci?鈥�
鈥淓 h akwai saura mana! Waye zai ci?鈥�.
鈥淵 aya Khaleel zan bawa 鈥�.
鈥淭 o ai sai kije ' ki d'auko inda zan sami maki 鈥�.
Fadwa juya tayi ' ta bar sashen ta nufi sashen ta, Shiga tayi cike sa sallama a
bakin ta Yaya Khaleel ya amsa sannan ta nufi kitchen kai tsaye, Fadwa cooler ta
d'auko ta fito zata fita ' Yaya Khaleel ya tsaida ita da cewa.
鈥淏 aby nah ' ina kuma zakije?"
Juyowa tayi ta kalle shi ' gami da bazo mashi idanu.
鈥淎'a abinci zan zubo maka, Wanda zaka ci 鈥�.
鈥淜 e meyafaru da naki abincin?鈥�.
鈥淎 mm... Sweetheart ' babu komai, Kaga ban d'aura girkin da wuri bane 鈥�.
鈥淲 annan ba reason bane ' to nidai bazan iya cin abincin biki ba!!鈥�.
Nan fa su Fadwa ido ya fara raina fata.
鈥淭 o me kakeso kaci Sweetheart?鈥�.
Yaya Khaleel gyara zama yayi ' tare da yin murmushi ' sannan yace.
鈥淕 ood!, kinga dai inaso inci jellof rice with beans ' kuma inaso inci dambun
shinkafa.鈥�.
Bud'e baki Fadwa tayi, Sannan tayi k'wal k'wal da ido.
鈥淒 uk a cikin wannan tala tainin daren? Haba Sweetheart..鈥�.
鈥淥 h to shikenan ' tunda bara kimun ba, Ni kuma babu abinda zanci!鈥�.
Tashi yayi shi a dole yayi fushi ' yayi fuuuu zai wuce d'aki Fadwa tayi saurin
binshi ta rungumo shi ta baya.
鈥淪 orry Sweetheart ' zanyi maka jellof rice with beans yanzu, Amma please ka
sauk'ak'a mun kabar dambun nan sai gobe 鈥�.
Juyowa yayi ya kalleta ido cikin ido, Amma sam baiga wani b'acin rai ya bayyana
a fuskar ta ba.
Tallabo fuskar ta yayi ' ya manna mata kiss a goshi, Sannan yaja hannun ta suka
koma suka zauna.
鈥淏 aby nah?鈥�.
鈥淣 a'am 鈥�.
鈥淜 arki damu wasa nake miki ' ki tashi kije ki shirya mu tafi restaurant, Kinga
sai muci abinda ranmu keso ko?鈥�.
Murmushi Fadwa tayi har saida hak'oran ta biyu suka bayyana.
鈥淭 hank you Sweetheart!鈥�.
Ta fad'a sannan ta tashi ta wuce d'aki, Fadwa wardrope ta bud'e ta ciro hijab
d'in ta pink ta sanya, Sannan ta fito.
鈥淣 a shirya...鈥�.
Abinda tace kenan ' Yaya Khaleel ya mik'e tsaye rik'e da car-key a hannun shi,
Sannan yasa kai ya fita Fadwa na biye dashi a baya.
Suna fita ta saka key a k'ofar, tukunna suka shige mota ' Yaya Khaleek yaja
motar suka wuce.
B'angaren Yaya Farook kuwa ' tunda suka dawo tare da Abba ya shige d'akin shi
yayi kwanciyar shi, Da waya a hannun shi yana danna wa.
Da kaga fuskar shi kasan da mutumiyar yake chart ' wato Safeena.

*WAJEN 9:00PM*

Yaya Khaleel da Fadwa ' suka dawo gida, Lokacin duk 'yan biki sun gama watse wa.
Packing Yaya Khaleel yayi a packing space ' tukunna suka fito a tare suka shige
sashen su.
Fadwa ta wuce d'akin ta direct ta cenja rigar jikin ta zuwa ta bacci, Sannan ta
fito ta wuce bedroom d'in Yaya Khaleel.
Ko da ta shiga ' iske shi tayi yayi shirin baccin shi kamar yadda ya saba,
Singlet ce da boxer a jikin shi ' yana kwance da waya a hannun shi.
Fadwa hayewa saman gadon tayi ' taja musu blanket, Tare da cewa.
鈥淧 lease ka rabu da wayar nan ' muyi bacci 鈥�.
鈥淏 aby nah ' bani two minutes 鈥�.
Tana jin ya fad'i haka ta fizge wayar cikin sauri tayi switching d'in ta, Sannan
tasa hannu ta kashe wutar ' tare a k'udun dune wa cikin jikin shi.
鈥淪 orry Sweetheart bacci!鈥�.
Murmushi kawai yayi mata ' sannan yasa hannu ya sake matse ta gam da jikin shi,
Nan bacci yayi awon gaba da su.

[5/21, 7:18 AM] Al~Husseen Abu~Sameer: .... *BABBAN...GIDA*

*_Pure Moment Of Life writers_*

© ```Written```
By
*_Seemaluv_*

www.Seemaluv.wapka.me
*#IG:* *_@Bae_Seema_*

*_ @Sadnaf I want to be the girl who makes your birthday better. The girl that
makes you say: "My life has changed since I met her." And yes that's me, I wish
you many more lifes ahead Sadnaf ' Happy Buffday!! _*

*85-86*

Yana shiga d'aki bai dire ta a ko ina ba ' sai saman gadon shi, Nan ya shiga raba
ta da kayan jikin ta ' Fadwa tun tana mutsu mutsu har ta kyaleshi.
Yaya Khaleel daga pant sai brazier ' ya barta dashi, Sannan ya haye saman gadon
' Fadwa kuwa d'ar d'ar kawai takeji a cikin ranta, Haka Yaya Khaleel ya shiga bata
hot kisses ta ko ina.
“Baby nah ' i missed you so much, so duk abinda zanyi ki barni kinji?”.
Yana maganar yana ninshi sama sama ' Fadwa kuwa kasa cewa komai tayi, Sai kai da
take karkad'a mashi alaman a'a .
Yaya Khaleel hannu yasa ' ya kashe wutar d'akin, Ni *Seemaluv* ganin haka yasa
na juya na fita ' harna nufi parlor najiyo kukan ta, Hakan yasa na dawo da sauri '
na lab'e a jikin k'ofa.
“Ahhhgh Yaya Khaleel ' don Allah kayi hak'uri ka kyaleni...”.
Abinda Fadwa ke fad'a kenan cikin yanayi na kuka.
“No ki barni please Baby nah ' ina mararin ki, in kika hana zan iya mutuwa”.
Kafin ya gama rufe baki ' Fadwa tayi wani wahalallen ihu, Hakan yasa na tabbatar
da cewa ya riga ya sami abinda yake so.
Yaya Khaleel sai da yaji he's well satisfied, Sannan ya sauka daga kan Fadwa '
wacce hawaye ne keta yi mata zarya a fuska, Yaya Khaleel gefe ya koma yayi ruf da
ciki yana maida numfashi.
Sai da yaji ya dawo normal ne ' ya murgino ya dawo kusa da Fadwa, yana shafa
mata gashin kanta tare da cewa.
“Am sorry Baby nah! I never meant to hurt you ' kema kin sani ko?”.
Fadwa cikin rawar jiki ' ta janyo hannun shi ta share hawayen da ke fuskar ta
dashi, Sannan ta shige jikin shi gami da cewa.
“Sweetheart ' ka rungume ni kaji, Please rungume ni zanfi samun sauk'i”.
Yaya Khaleel hannu yasa ' ya rungume ta tsam a jikin shi, Yadda kasan za'a k'wace
mashi ita.
Sai da suka d'auki lokaci a haka har bacci yad'an soma kwashe ta, Sannan ya zame
jikin shi zai sauka ' Fadwa tayi firgigit ta tashi zaune.
“Ina kuma zaka je?”.
“Zanyi wanka ne ' kema ki tashi kije ki gyara jikin ki, Bedshit kuma ki barshi
zan cenja wani”.
Ok Fadwa tace ' tukunna ta koma ta kwanta tare da yin ajiyar zuciya mai k'arfi,
Sai da taga shigar shi bathroom ne itama ta sauka daga gadon ta d'auki zani ta
d'aura sannan ta nufi d'akin ta.
Fadwa bathroom ta fad'a tayi wankan tsarki ' tukunna ta fito ta shirya cikin
doguwar riga 'yar kanti had'i da dogon gele ta yafa akai, Sannan ta fito parlor.
Fadwa ganin Yaya Khaleel tayi a zaune ' cikin k'ananan kaya yana duba wasu
documents, K'arasa wa tayi cikin hanzari ta zauna kusa dashi.
Har ta d'auki remote zata kunna TV, Taji tsayawar motoci ' cikin hanzari Fadwa
ta tashi ta lek'a ta window, Ilham ce daga ni ta fito cikin motar sukuku a gajiye.
Fadwa juyawa tayi ta kalli Yaya Khaleel.
“Sweetheart ' zan d'an fita, Su Ilham sun dawo”.
“Um Hum”.
Kawai ya ce ' sannan Fadwa ta fita cikin sauri, ta tari Ilham.
Ilham ballara mata harara tayi ' zatayi magana Fadwa dakatar da ita.
“Shhh karma kice komai ' nasan ni keda laifi, Amma yanzu mu shiga daga ciki
tukunna ' sai na sami damar bayani”.
Haka Fadwa da Ilham suka k'arasa cikin gida k'awaye na biye dasu a baya.
Sai da suka shiga d'aki tukunna Fadwa ta fara bada hak'uri, Dakyar ta samu Ilham
ta hak'uri sannan ta d'aga kai ta duba a gogon d'akin.
“La la la!! Har 6:00pm ' ban d'aura abincin dare ba?”.
“Why not ki d'iban mashi na nan kawai!”.
Cewar Ilham.
“Eh abunda zanyi kenan ma ' bari inje inyiwa Ige magana, Allah yasa da saura”.
Ameen Ilham tace ' sannan Fadwa ta tashi ta nufi parlor neman Ige, Kasancewar
parlon a cike yake da mutane.
Fadwa hangota tayi ' cikin mutane, Hakan yasa taje ta jawo hannun ta suka nufi
kitchen.
“Oh oh 'Yan nan lafiya?”.
“Ige don Allah akwai sauran abinci?”
“Eh akwai saura mana! Waye zai ci?”.
“Yaya Khaleel zan bawa”.
“To ai sai kije ' ki d'auko inda zan sami maki”.
Fadwa juya tayi ' ta bar sashen ta nufi sashen ta, Shiga tayi cike sa sallama a
bakin ta Yaya Khaleel ya amsa sannan ta nufi kitchen kai tsaye, Fadwa cooler ta
d'auko ta fito zata fita ' Yaya Khaleel ya tsaida ita da cewa.
“Baby nah ' ina kuma zakije?"
Juyowa tayi ta kalle shi ' gami da bazo mashi idanu.
“A'a abinci zan zubo maka, Wanda zaka ci”.
“Ke meyafaru da naki abincin?”.
“Amm... Sweetheart ' babu komai, Kaga ban d'aura girkin da wuri bane”.
“Wannan ba reason bane ' to nidai bazan iya cin abincin biki ba!!”.
Nan fa su Fadwa ido ya fara raina fata.
“To me kakeso kaci Sweetheart?”.
Yaya Khaleel gyara zama yayi ' tare da yin murmushi ' sannan yace.
“Good!, kinga dai inaso inci jellof rice with beans ' kuma inaso inci dambun
shinkafa.”.
Bud'e baki Fadwa tayi, Sannan tayi k'wal k'wal da ido.
“Duk a cikin wannan tala tainin daren? Haba Sweetheart..”.
“Oh to shikenan ' tunda bara kimun ba, Ni kuma babu abinda zanci!”.
Tashi yayi shi a dole yayi fushi ' yayi fuuuu zai wuce d'aki Fadwa tayi saurin
binshi ta rungumo shi ta baya.
“Sorry Sweetheart ' zanyi maka jellof rice with beans yanzu, Amma please ka
sauk'ak'a mun kabar dambun nan sai gobe”.
Juyowa yayi ya kalleta ido cikin ido, Amma sam baiga wani b'acin rai ya bayyana
a fuskar ta ba.
Tallabo fuskar ta yayi ' ya manna mata kiss a goshi, Sannan yaja hannun ta suka
koma suka zauna.
“Baby nah?”.
“Na'am”.
“Karki damu wasa nake miki ' ki tashi kije ki shirya mu tafi restaurant, Kinga
sai muci abinda ranmu keso ko?”.
Murmushi Fadwa tayi har saida hak'oran ta biyu suka bayyana.
“Thank you Sweetheart!”.
Ta fad'a sannan ta tashi ta wuce d'aki, Fadwa wardrope ta bud'e ta ciro hijab
d'in ta pink ta sanya, Sannan ta fito.
“Na shirya...”.
Abinda tace kenan ' Yaya Khaleel ya mik'e tsaye rik'e da car-key a hannun shi,
Sannan yasa kai ya fita Fadwa na biye dashi a baya.
Suna fita ta saka key a k'ofar, tukunna suka shige mota ' Yaya Khaleek yaja
motar suka wuce.
B'angaren Yaya Farook kuwa ' tunda suka dawo tare da Abba ya shige d'akin shi
yayi kwanciyar shi, Da waya a hannun shi yana danna wa.
Da kaga fuskar shi kasan da mutumiyar yake chart ' wato Safeena.

*WAJEN 9:00PM*
Yaya Khaleel da Fadwa ' suka dawo gida, Lokacin duk 'yan biki sun gama watse wa.
Packing Yaya Khaleel yayi a packing space ' tukunna suka fito a tare suka shige
sashen su.
Fadwa ta wuce d'akin ta direct ta cenja rigar jikin ta zuwa ta bacci, Sannan ta
fito ta wuce bedroom d'in Yaya Khaleel.
Ko da ta shiga ' iske shi tayi yayi shirin baccin shi kamar yadda ya saba,
Singlet ce da boxer a jikin shi ' yana kwance da waya a hannun shi.
Fadwa hayewa saman gadon tayi ' taja musu blanket, Tare da cewa.
“Please ka rabu da wayar nan ' muyi bacci”.
“Baby nah ' bani two minutes”.
Tana jin ya fad'i haka ta fizge wayar cikin sauri tayi switching d'in ta, Sannan
tasa hannu ta kashe wutar ' tare a k'udun dune wa cikin jikin shi.
“Sorry Sweetheart bacci!”.
Murmushi kawai yayi mata ' sannan yasa hannu ya sake matse ta gam da jikin shi,
Nan bacci yayi awon gaba da su.

*DEDICATED TO MY FAN'S*
[5/21, 7:21 AM] Al~Husseen Abu~Sameer: ... *BABBAN...GIDA*

*_Pure Moment Of Life writers_*

© ```Written```
By
*_Seemaluv_*

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema_*

*87-90*

Yaya Khaleel sai da ya d'auki lokaci mai tsawo yana kallon ta, Wayar shi ta fara
k'ara alaman kira ' hakan yasa shi tashi ya koma parlor, Don karya tasheta.
Yaya Khaleel ciro wayar yayi daga aljihun shi ' ganin kiran daga wajen aiki ne,
Yasa ya d'aga wayar cikin hanzari.
Haka sakatariyar shi ta sanar mashi da yazo cikin hanzari ' yayi manyan bak'i.
Ok kawai yace ' tukunna ya kashe wayar yana tunanin Fadwa wacce take baccin ta.
Yaya Khaleel juyawa yayi ya koma d'akin nata, Ya tab'a jikin ta ko akwai zafi '
jin babu zafi ne yasa shi juyawa ya fice daga d'akin zuwa parlor.
Ige ce a zaune tana kallon ta ' kasan cewar channel d'in hausa film ne.
"Ige ' zan fita zuwa wajen aiki, Please ki kula da ita ' don Allah Ige karki
tsaya biyewa wannan kallon".
"Kujimun ja'irin yaro! Wato kai mai mata ko? Lallai zamani".
"Ni na wuce".
"Allah ya bada sa'a ya kuma tsare"
Ige ta fad'a cikin dariyar tsufa, Sannan Yaya Khaleel ya fita gami da cewa Ameen.
Umma ce a tsaye cikin part d'in Yaya Farook, Tana duba 'yan gyare gyaren da
akayi ' yanzu komai ya zama daidai, Shiga ne kawai ya rage.
Part d'in Yaya Farook iri d'aya ne dana Yaya Khaleel, Sai dai abubuwan ciki ne
suka ban banta.
Bayan Umma ta gama duba komai ne ' ta sallame 'yan aiki suka wuce, Sannan taja
k'ofar ta rufe da key ta koma sashen su ta zauna a parlor.

*AROUND 12:30PM*

K'awayen Ilham suka iso cikin gidan ' kai tsaye suka zarce ciki, A zaune suka iske
Umma hakan yasa suka zuk'unna har k'asa suka gaishe ta ' sannan suka k'arasa ciki.
Suna shiga d'akin Ilham suka iske ta a zaune gaban madubi tayi jigum ' tana
kallon kanta.
"Ilham ya baki shirya ba? Kinsan k'arfe nawa kuwa yanzu? Ina Fadwa?".
D'aya daga cikin k'awayen ta fad'i haka, Tana k'ok'arin zuwa gaban madubin donta
shirya ta.
"Fadwa bata da lafiya".
"Oh ayyah aiko maje mu gaishe ta ' kafin lokaci yayi".
Nan suka fara yiwa Ilham gyara ' da kwalliya, Haka Ilham tayi kyau sosai ' sai da
suka kammala ne suka fara kashe hutuna ita da k'awayen ta.
"Wallahi hutunan nan bazasu yi kyau ba ' don babu Fadwa a ciki".
Tana fad'in haka ta kalli a gogon d'akin.
"Kunga yanzu *12:46pm* mubar hotunan nan haka ' muje mu duba jikin Fadwa, Don
Ango na yace da zarar an d'aura aure ' zasu turo motocin d'aukar Amarya".
To kawai sukace ' sannan suka bar d'akin suka nufi sashen Fadwa.
Suna shiga suka iske Ige a zaune ' hankalin ta na kan TV kallon ta kawai takeyi.
"Ige".
Cewar Ilham.
Firgigit Ige tayi ' ta juyo ta kalle ta.
"Ya akayi?".
"Fadwa bacci takeyi ko kuwa?".
"Bansani ba 'yan nan ' ki shiga ki duba mana".
Haka Ilham ta zarce ciki ' ita da k'awayen ta, Tana shiga taja burki ta tsaya
ganin bacci Fadwa ke yi.
"Bacci ma takeyi ' mu koma kawai".
Haka suka juya suka koma b'angaren su.
Yaya Farook dake garden a zaune ' yana kallon shukoki, Yunwa ce yaji ta yunk'uro
shi ' cikin sauri ya bar wajen ya nufi cikin gida, Kai tsaye ya wuce kitchen a
d'ibi abinci sannan ya koma parlor inda Umma take zauna ' ya zauna dirshen a k'asa.
"Farook ' kayi sauri kaci, Don lokacin d'aurin auren ya kusa".
Cewar Umma.
"To Umma ' aiya zama dole".
"Yawwa don shi Khaleel ya sanar dani cewa ' bazai sami halartar d'aurin auren
ba, Abban ku kuma yana cen".
Yaya Farook sama sama yaci ' ya tashi cikin sauri ya wuce d'akin shi, Cikin
hanzari ya cenja kayan jikin shi ' cikin shadda milk colour.
Saida ya kammala tsaf ' tukunna ya d'auki key d'in motar shi ya fice zuwa wajen
d'aurin aure.

*AROUND 1:00PM*

Mutane suka taru a babban masallacin izala ' Waliyyen Ango da Amarya duk sun
hallara, Tare da iyayen Ango da Amarya da kuma abokan arzik'i.
*1:...pm* aka d'aura auren Al'ameen da Fadwa, Haka ladan ya dunga shela ' gunun
ban sha'awa.

*** *** *** *** *** *** ***

Ilham na zaune a d'aki ita da k'awayen tane Angon ta ya kira ta awaya, Ganin
kiran shi yasa gaban ta ya fad'i tasan cewa lallai aure ya d'auru.
Haka jiki a sanyaye ta d'aga wayar.
"My king".
Ta furta a tsora ce.
"Alhamdulillah! My Queen ' and'aura aure, Kin zama mata ta ' ke kawai nake zaman
jira".
Murmushin jin dad'i Ilham tayi tare da cewa.
"Allah ne abin godiya ' my King".
Fadwa saurin kashe wayar tayi ' sakamakon ganin Umma da tayi ta shigo cikin
d'akin, Hakan yasa Ilham mik'ewa tsaye.
"Ku bani waje inason inyi magana da 'yata".
Nan Ilham ta had'iye miyau dakyar, Sannan k'awayen suka fita daga d'akin zuwa
parlor.
Umma ajiyar zuciya tayi ' ta k'arasa cikin d'akin ta zauna, Sannan itama Ilham
ta koma ta zauna kusa da ita.
"Ilham?".
Ilham d'ago kai tayi ta kalleta, zuciyar ta na k'una ' amma sam batasan dalili ba.
"Nasiha zanyi maki ' kin kasance 'yata kuma jini na! Wacce ta tashi cikin
*BABBAN GIDA!* mai cike da tarbiyya".
Umma hannun Ilham ta kamo ' da sauri Ilham ta d'ago kai ta kalle ta jin yadda
hannun take rawa.
"Ki kasance mai yiwa mijin ki biyayya ' Ilham.....".
Umma kasa k'arasa maganar tayi ' saboda rad'ad'in da ke cinta a zuciya, Na zafin
rashin 'yarta da zatayi a kusa da ita.
Hawaye ne suka zubowa Umma a ido ' tayi sauri ta goge don kada Ilham ta fahimci
wani abu.
Ilham kuwa duk ta fahimci haka ' itama wasu zafafan hawaye ke fitowa daga idon
ta, A hankali ta mik'e tsaye ta dawo saitin fuskar Umma ta zuk'unna.
"Umma na! Meyasa kike kuka?...".
Suna cikin haka ne ' d'aya daga cikin k'awayen ta shigo d'akin cikin sauri.
"Umma ' masu d'aukan Amaren ne suka iso".
Umma saurin share hawayen ta tayi ' sannan ta tashi tsaye tare da rufa mata
mayafin ta akai.
"Kije kawai ' zamuyi waya".
Umma na fad'in haka tabar d'akin cikin sauri, Hakan yasa Ilham had'iye miyau
dakyar ' sannan sauran k'awayen suka shigo d'akin cikin hanzari suka fara shirya
ta.
Bayan sun gama ne ' suka fito daga d'akin tare da amarya, Ilham tsayawa tayi
tana kallon harabar parlon.
"Haba Ilham lokaci na k'urewa fa! Sai kace ba'a gari d'aya ake ba?".
Haka suka fito waje harabar garege ' ta tsaya cak hawaye na zuba a fuskar ta.
Fadwa ji tayi kamar ance ta tashi ' haka tayi firgigit ta tashi, Cikin hanzari
ta diro daga saman gado ' duk da tanajin dizziness a jikin ta, Hakan bai hanata
zarcewa parlor inda Ige ke zaune.
"Ige?".
Ige juyowa tayi ' ta kalle ta.
"Na'am 'yan nan, Yaya jikin naki?".
"Amm...da sauk'i Ilham fa?".
"Ayya! Anya kuwa basu wuce ba?".
"Ina?".
"Ha'a gidan mijinta mana!".
Zaro ido Fadwa tayi ' gami da juyawa tabar parlon zuwa waje cikin hanzari.
Fadwa na fita ta iske ' k'awayen sai daga suke da ita akan suwuce, Amma sam
Ilhan tak'i.
Nan take k'walla suka ciko idon Fadwa, Hakan yasa ta k'arasa har inda take tare
da tallabo fuskar ta.
"Ilham...".
Ilham kallon Fadwa tayi ' da idanun ta da suka rine saboda kuka.
"Ni kike jira ko?".
Kai ta d'aga mata alaman Eh, Sannan Fadwa ta rungume ta cikin kuka.
"Please idan kinje ki kulamun da kanki! Kumayi biyayya a gareshi".
Tana fad'in haka taja hannun ta ' tai mata rakiya zuwa gaban mota.
Fadwa saka Ilham tayi a cikin mota ' tare da cewa.
"Sai nazo".
Sannan ta rufe ' suka koma kallon junan su ta glass d'in motar , Motoci bakwai ne
suka zo wajen ' amma mota uku ne suka cika da Amare, Sai da ko waccen su ta gama
shiga ' sannan gate man ta bud'e masu gate suka fito.
Fadwa kuwa idonta akan Ilham yake ' hakama Ilham, Har saida taga bata ganin
komai a wajen tukunna ta koma sashen ta.

*DEDICATED TO MY FAN'S*
馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:58 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

*89-90*

Yaya Khaleel sai da ya d'auki lokaci mai tsawo yana kallon ta, Wayar shi ta fara
k'ara alaman kira ' hakan yasa shi tashi ya koma parlor, Don karya tasheta.
Yaya Khaleel ciro wayar yayi daga aljihun shi ' ganin kiran daga wajen aiki ne,
Yasa ya d'aga wayar cikin hanzari.
Haka sakatariyar shi ta sanar mashi da yazo cikin hanzari ' yayi manyan bak'i.
Ok kawai yace ' tukunna ya kashe wayar yana tunanin Fadwa wacce take baccin ta.
Yaya Khaleel juyawa yayi ya koma d'akin nata, Ya tab'a jikin ta ko akwai zafi '
jin babu zafi ne yasa shi juyawa ya fice daga d'akin zuwa parlor.
Ige ce a zaune tana kallon ta ' kasan cewar channel d'in hausa film ne.
"Ige ' zan fita zuwa wajen aiki, Please ki kula da ita ' don Allah Ige karki
tsaya biyewa wannan kallon".
"Kujimun ja'irin yaro! Wato kai mai mata ko? Lallai zamani".
"Ni na wuce".
"Allah ya bada sa'a ya kuma tsare"
Ige ta fad'a cikin dariyar tsufa, Sannan Yaya Khaleel ya fita gami da cewa Ameen.
Umma ce a tsaye cikin part d'in Yaya Farook, Tana duba 'yan gyare gyaren da
akayi ' yanzu komai ya zama daidai, Shiga ne kawai ya rage.
Part d'in Yaya Farook iri d'aya ne dana Yaya Khaleel, Sai dai abubuwan ciki ne
suka ban banta.
Bayan Umma ta gama duba komai ne ' ta sallame 'yan aiki suka wuce, Sannan taja
k'ofar ta rufe da key ta koma sashen su ta zauna a parlor.

*AROUND 12:30PM*

K'awayen Ilham suka iso cikin gidan ' kai tsaye suka zarce ciki, A zaune suka iske
Umma hakan yasa suka zuk'unna har k'asa suka gaishe ta ' sannan suka k'arasa ciki.
Suna shiga d'akin Ilham suka iske ta a zaune gaban madubi tayi jigum ' tana
kallon kanta.
"Ilham ya baki shirya ba? Kinsan k'arfe nawa kuwa yanzu? Ina Fadwa?".
D'aya daga cikin k'awayen ta fad'i haka, Tana k'ok'arin zuwa gaban madubin donta
shirya ta.
"Fadwa bata da lafiya".
"Oh ayyah aiko maje mu gaishe ta ' kafin lokaci yayi".
Nan suka fara yiwa Ilham gyara ' da kwalliya, Haka Ilham tayi kyau sosai ' sai da
suka kammala ne suka fara kashe hutuna ita da k'awayen ta.
"Wallahi hutunan nan bazasu yi kyau ba ' don babu Fadwa a ciki".
Tana fad'in haka ta kalli a gogon d'akin.
"Kunga yanzu *12:46pm* mubar hotunan nan haka ' muje mu duba jikin Fadwa, Don
Ango na yace da zarar an d'aura aure ' zasu turo motocin d'aukar Amarya".
To kawai sukace ' sannan suka bar d'akin suka nufi sashen Fadwa.
Suna shiga suka iske Ige a zaune ' hankalin ta na kan TV kallon ta kawai takeyi.
"Ige".
Cewar Ilham.
Firgigit Ige tayi ' ta juyo ta kalle ta.
"Ya akayi?".
"Fadwa bacci takeyi ko kuwa?".
"Bansani ba 'yan nan ' ki shiga ki duba mana".
Haka Ilham ta zarce ciki ' ita da k'awayen ta, Tana shiga taja burki ta tsaya
ganin bacci Fadwa ke yi.
"Bacci ma takeyi ' mu koma kawai".
Haka suka juya suka koma b'angaren su.
Yaya Farook dake garden a zaune ' yana kallon shukoki, Yunwa ce yaji ta yunk'uro
shi ' cikin sauri ya bar wajen ya nufi cikin gida, Kai tsaye ya wuce kitchen a
d'ibi abinci sannan ya koma parlor inda Umma take zauna ' ya zauna dirshen a k'asa.
"Farook ' kayi sauri kaci, Don lokacin d'aurin auren ya kusa".
Cewar Umma.
"To Umma ' aiya zama dole".
"Yawwa don shi Khaleel ya sanar dani cewa ' bazai sami halartar d'aurin auren
ba, Abban ku kuma yana cen".
Yaya Farook sama sama yaci ' ya tashi cikin sauri ya wuce d'akin shi, Cikin
hanzari ya cenja kayan jikin shi ' cikin shadda milk colour.
Saida ya kammala tsaf ' tukunna ya d'auki key d'in motar shi ya fice zuwa wajen
d'aurin aure.

*AROUND 1:00PM*

Mutane suka taru a babban masallacin izala ' Waliyyen Ango da Amarya duk sun
hallara, Tare da iyayen Ango da Amarya da kuma abokan arzik'i.
*1:...pm* aka d'aura auren Al'ameen da Fadwa, Haka ladan ya dunga shela ' gunun
ban sha'awa.

*** *** *** *** *** *** ***

Ilham na zaune a d'aki ita da k'awayen tane Angon ta ya kira ta awaya, Ganin
kiran shi yasa gaban ta ya fad'i tasan cewa lallai aure ya d'auru.
Haka jiki a sanyaye ta d'aga wayar.
"My king".
Ta furta a tsora ce.
"Alhamdulillah! My Queen ' and'aura aure, Kin zama mata ta ' ke kawai nake zaman
jira".
Murmushin jin dad'i Ilham tayi tare da cewa.
"Allah ne abin godiya ' my King".
Fadwa saurin kashe wayar tayi ' sakamakon ganin Umma da tayi ta shigo cikin
d'akin, Hakan yasa Ilham mik'ewa tsaye.
"Ku bani waje inason inyi magana da 'yata".
Nan Ilham ta had'iye miyau dakyar, Sannan k'awayen suka fita daga d'akin zuwa
parlor.
Umma ajiyar zuciya tayi ' ta k'arasa cikin d'akin ta zauna, Sannan itama Ilham
ta koma ta zauna kusa da ita.
"Ilham?".
Ilham d'ago kai tayi ta kalleta, zuciyar ta na k'una ' amma sam batasan dalili ba.
"Nasiha zanyi maki ' kin kasance 'yata kuma jini na! Wacce ta tashi cikin
*BABBAN GIDA!* mai cike da tarbiyya".
Umma hannun Ilham ta kamo ' da sauri Ilham ta d'ago kai ta kalle ta jin yadda
hannun take rawa.
"Ki kasance mai yiwa mijin ki biyayya ' Ilham.....".
Umma kasa k'arasa maganar tayi ' saboda rad'ad'in da ke cinta a zuciya, Na zafin
rashin 'yarta da zatayi a kusa da ita.
Hawaye ne suka zubowa Umma a ido ' tayi sauri ta goge don kada Ilham ta fahimci
wani abu.
Ilham kuwa duk ta fahimci haka ' itama wasu zafafan hawaye ke fitowa daga idon
ta, A hankali ta mik'e tsaye ta dawo saitin fuskar Umma ta zuk'unna.
"Umma na! Meyasa kike kuka?...".
Suna cikin haka ne ' d'aya daga cikin k'awayen ta shigo d'akin cikin sauri.
"Umma ' masu d'aukan Amaren ne suka iso".
Umma saurin share hawayen ta tayi ' sannan ta tashi tsaye tare da rufa mata
mayafin ta akai.
"Kije kawai ' zamuyi waya".
Umma na fad'in haka tabar d'akin cikin sauri, Hakan yasa Ilham had'iye miyau
dakyar ' sannan sauran k'awayen suka shigo d'akin cikin hanzari suka fara shirya
ta.
Bayan sun gama ne ' suka fito daga d'akin tare da amarya, Ilham tsayawa tayi
tana kallon harabar parlon.
"Haba Ilham lokaci na k'urewa fa! Sai kace ba'a gari d'aya ake ba?".
Haka suka fito waje harabar garege ' ta tsaya cak hawaye na zuba a fuskar ta.
Fadwa ji tayi kamar ance ta tashi ' haka tayi firgigit ta tashi, Cikin hanzari
ta diro daga saman gado ' duk da tanajin dizziness a jikin ta, Hakan bai hanata
zarcewa parlor inda Ige ke zaune.
"Ige?".
Ige juyowa tayi ' ta kalle ta.
"Na'am 'yan nan, Yaya jikin naki?".
"Amm...da sauk'i Ilham fa?".
"Ayya! Anya kuwa basu wuce ba?".
"Ina?".
"Ha'a gidan mijinta mana!".
Zaro ido Fadwa tayi ' gami da juyawa tabar parlon zuwa waje cikin hanzari.
Fadwa na fita ta iske ' k'awayen sai daga suke da ita akan suwuce, Amma sam
Ilhan tak'i.
Nan take k'walla suka ciko idon Fadwa, Hakan yasa ta k'arasa har inda take tare
da tallabo fuskar ta.
"Ilham...".
Ilham kallon Fadwa tayi ' da idanun ta da suka rine saboda kuka.
"Ni kike jira ko?".
Kai ta d'aga mata alaman Eh, Sannan Fadwa ta rungume ta cikin kuka.
"Please idan kinje ki kulamun da kanki! Kumayi biyayya a gareshi".
Tana fad'in haka taja hannun ta ' tai mata rakiya zuwa gaban mota.
Fadwa saka Ilham tayi a cikin mota ' tare da cewa.
"Sai nazo".
Sannan ta rufe ' suka koma kallon junan su ta glass d'in motar , Motoci bakwai ne
suka zo wajen ' amma mota uku ne suka cika da Amare, Sai da ko waccen su ta gama
shiga ' sannan gate man ta bud'e masu gate suka fito.
Fadwa kuwa idonta akan Ilham yake ' hakama Ilham, Har saida taga bata ganin
komai a wajen tukunna ta koma sashen ta.

*DEDICATED TO MY FAN'S*
馃憚馃憚馃憚馃槝
[5/23, 2:58 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

*_I dedicated this page to my BESTY (ONE LOVE 鉂�)_*

*87-88*

*WASHE GARI*

Da sassafe Fadwa ta farka daga bacci ' cikin matsanancin ciwon kai, Ga jikin ta
yayi zafi rau.
A hankali ta tashi ' ta sauka daga saman gadon ta nufi d'akin ta.
Toilet ta shiga ' tayi alwala sannan ta fito tayi sallah, Bayan ta idar ne ta
mik'e tsaye tare da yaye hijab d'in ta, Ta nufi side-drower d'in da ke wajen gado
taja ta d'auko paracetamol (pain-reliever).
Fadwa fitowa tayi da maganin a hannu ' ta nufi kitchen tasha, tukunna ta dawo
d'akin ta ta kwanta gami da jan blanket ' don zazzab'i zazzab'i takeji.

*AROUND 7:00AM*

Yaya Khaleel ya tashi daga bacci ' cike da mik'a, Shafa gefen shi yayi baiji
Fadwa ba hakan yasa shi bud'e idon shi ' ganin bata d'akin ne yasa shi saukowa daga
saman gadon cike da salati a bakin shi.
Yaya Khaleel saida ya shiga toilet ' tukunna ya fito ya shiga bathroom don yin
wanka.
Bayan ya gama ne ya fito d'auke da alwala a jikinsa, Yayi sallah sannan ya fara
shiri.
"Yau kam da wuri zan tafi office ' don ina da aiki sosai, Allah yasa Baby nah ba
bacci ta koma ba".
Abinda ya fad'a kenan ya gama shirya wa, Sannan ya fito parlor cikin sauri.
"Baby nah!!".
Yaya Khaleel kiran Fadwa yakeyi amma bata amsa ba ' ganin haka yasa ya nufi
bedroom d'in nata.
A duk'un k'une ya hango ta saman gado ' sai rawar sanyi takeyi da sambatu, Cikin
sauri ya k'arasa kusa da ita ya zauna tare da tallabo ta.
"Baby nah! What's wrong?".
"Swe.. Sww... Sweetheart am feeling sick, Am not well".
Ta fad'a cikin rawar baki.
Yaya Khaleel rungume ta yayi ' yaji jikinta yayi rau da zafi, Cikin hanzari ya
ciro wayar shi ' ya kira wata Nurse, Kasan cewar abokiyar shi ce sosai.
Bayan sun gama wayar ne ' ya maida wayar shi aljihu.
"Baby nah! Yanzu za'a zo a dubamun ke, Don't warry ok?".
"Ok".
Kwantar da ita yayi ' tare da lullub'e ta sosai.
"Bari inje in gaishe dasu Umma ' sannan in fad'a masu bakya jin dad'i".
"Uhm Hum".
Tashi yayi ya fita ' ya nufi part d'insu Umma, A parlor ya same su ' ita da Ige
sai kuma Ilham wacce ke zauna a k'asa kanta a sunkuye.
Yaya Khaleel duk'awa yayi ya gaishe su ' sannan Ilham ta gaishe shi, Tukunna ya
sanar masu da rashin lafiyar Fadwa.
"Subhanallah! Meke damun ta".
Cewar Umma.
"Wallahi Umma yau ne ta tashi da zazzab'i, Amma nadai kira nurse zata zo ta duba
ta yanzu ' by the way Abba na nan kuwa?".
"Aiko bai dad'e da tafiya office ba".
"Ok".
Ilham ce tayi wuff ta tashi ' ta nufi sashen Fadwa cike da tausayawa, Tana shiga
ta wuce d'akin ta kai tsaye.
Kakarin amanta taji a toilet kasan cewar babu komai a cikin ta ' hakan yasa
Ilham ta nufi toilet d'in kai tsaye.
"Sannu Fadwa ya jikin?".
Fadwa d'ago kanta tayi ta kalli Ilham amma sam bata gani sosai.
"Ilham please ' jani ki maidani saman gado, Jiri nake gani".
Haka Ilham ta kama hannun ta ' ta maida Fadwa saman gado tare da ja mata
lullub'i.
"Fadwa me kikaci to?".
"Bana jin cin komai Ilham ' ki kyale kawai".
"Allah shi kyauta in kyaleki a haka! ' meye amfani na kenan?".
Suna cikin haka ne ' su Umma suka shigo cikin d'akin tare da Yaya Khaleel d'in.
"Amma ya kamata ace ' nurse d'in nan ta iso".
Yaya Khaleel ya fad'a yana k'ok'arin kiran nurse d'in a waya, Ringing d'aya tayi
ta d'auka.
"Idan baza ki sami damar zuwa bane ' ai saiki fad'amun in wuce da ita hospital
kawai".
"Ayya! Afuwan ' ina kan hanyan zuwa yanzu, Na kusa iso wa".
Tana gama rufe baki ' ya kashe wayar.
Umma da Ige ' gaishe da Fadwa sukeyi da jiki.
"Umma bari inje ko ruwan lipton ne in had'a mata".
"To shikenan ' ai yakamata".
Cewar Umma.
Ilham bata dad'e da fita ba ' nurse d'in ta kira Yaya Khaleel a waya cewar ta iso
yazo ya shigo da ita, Sai da ya fad'awa su Umma isowar Nurse d'in tukunna ya fita.
Nurse d'in shigowa tayi cikin garege ta tsaya, Yaya Khaleel ta hango yana isowa
gare ta cikin sauri.
"Barka da isowa! Muje ko?".
Ya fad'a tukunna ya juya ta bishi a baya, Part d'in Fadwa suka shiga kai tsaye ya
zarce da ita cikin d'akin.
Bayan sun gaisa da su Umma ne ' ta fara duba Fadwa wacce ke kwance jiki na rawa.
Saida ta gama ' tukunna ta rubuta musu magun gunan da zasu nema mata, Sannan ta
sanar musu da cewa Fadwa na d'auke da ciki.
Yaya Khaleel baki ya saki ' yana kallon Fadwa wacce idon ta ke rufe, Amma itama
zuciyar ta cike take da farin ciki.
Umma da Ige ' sun nuna farin cikin su matuk'a gami da yiwa Allah godiya.
"Alhamdulillah! Allah na gode maka, Friend kina da tukwaici mai tsoka ' karki
damu".
Cewar Yaya Khaleel.
"Uhm! To ina nan ina jira ' yanzu dai kar abata komai har sai tasha wad'an nan
magun gunan da rubuta inba haka ba zata cigaba da yin amai, Kuma zai galabaitar da
ita".
Nurse ta fad'i haka tana k'ok'arin d'aukar jakarta don ta koma wajen aikin ta,
Umma ta tsaida ita da cewa.
"To yanzu ko ruwan lipton bazata iya shaba? ' don batasa komai a cikin ta ba".
"Amm... Mama zaku iya bata ruwan lipton ba tare da milk ba a ciki".
Tana gama fad'in haka, Tasa kai ta wuce gami da yiwa Yaya Khaleel sallama.
Bayan wucewar ta ne ' Ilham ta shigo ciki rik'e da cup d'in lipton a hannun ta,
Zama tayi a gefen Fadwa tukunna ta tasheta ' ta rik'a bata a baki.
"Khaleel ' ka tashi kaje ka siyo mata maganin, don yau akwai aiki sosai a gidan
nan".
To yace ' sannan ya juya ya fice rik'e da car-key a hannun shi.
Umma ta maida kallon ta ga Ilham.
"Ke kuma! Idan kin gama ' kije ki shirya don nasan k'awayen ki suna kan hanya,
Kuma *1:00pm* za'a d'aura auren ' Ige sai ta tsaya da Fadwa a nan, Ni kuma zanje in
cigaba da duba masu aikin gyaran part d'in Farook, Don nasan amaren suma suna nan
tafe".
To Ige tace sannan ta tashi ta nufi parlor tare da cewa.
"Ni bari inje inyi kallo kafin Ilham ta gama".
Tukunna Umma ta tashi ta wuce sashen su, Zuciyar ta cike da farin ciki ' don
kuwa ta kusa ganin jikanta da iznin Allah.
Umma na shiga ' ta iske Yaya Farook zaune a parlor yana kallon news, Samun waje
tayi ta zauna ' sannan tace.
"Farook ' Fadwa batajin dad'i ya kamata kaje ka duba jikin ta".
"To Umma".
Abinda ya fad'a kenan ya mik'e ya nufi sashen ta, Nan suka ci karo da Yaya Khaleel
ya dawo zai shiga ciki.
"Khaleel ashe Fadwa batajin dad'i?".
"Eh wallahi Bro ' amma mu shiga daga ciki ku gaisa".
Haka suka k'arasa ciki ' har d'akin ta, Sannan Yaya Farook ya gaishe ta da jiki
' har ya juya zai wuce yaji tace.
"Sweetheart ' babu Injections a ciki ko?".
"Haba! Baby bah ' tsoron allura kikeyi?".
Yaya Farook ne yayi saurin taron numfashin shi ' da cewa.
"Eh Khaleel ' tana da tsoron allura sosai, Hope babu!".
Fadwa tsayawa tayi tana kallon shi cikin mamaki ' duk da batajin k'arfin jikin
ta hakan bai hana ta magana ba, b'ata rai tayi gami da cewa.
"Not really, Gaskiya sanin da akaimun ' amma banda yanzu".
Yaya Farook yana jin ta fad'i haka ya juya ya bar d'akin, Kai tsaye ya nufi
garden yayi zaman shi ' zaman jiran amarya.
Bayan Ilham ta gama bawa Fadwa ruwan lipton ne ' ta tashi ta nufi kitchen don
d'auko ruwan da zata sha maganin dashi.
"Sweetheart ' muga magun gunan to".
Yaya Khaleel mik'a mata ledar yayi ' ta duba taga babu injection ko d'aya aciki,
Hakan yasa tayi ajiyar zuciya.
"Baby nah ' karkiso kiga yadda nak'agara cikin nan ya fara girma".
Murmushi tayi tare da jinginar da kanta jikin gado.
"Karka damu ai kamar gobe ne".
Suna cikin haka ne ' Ilham ta shigo d'akin rik'e da robar ruwa a hannun ta, Ta
mik'awa Yaya Khaleel sannan ta juya ta fice tare da cewa.
"Fadwa bari inje inshirya ' a wuni da sauk'i".
"To Allah yasa".
Tana fita ' Yaya Khaleek ya b'alli magun gunan da zata sha yanzu ' ya bata ta
sanya a baki, Sannan ta kora da ruwa.
Fadwa bata wani jima ba ' bacci yayi awon gaba da ita, Kasan cewar cikin maganin
akwai maganin dake hana amai ' wanda kuwa shike sanya bacci.
Yaya Khaleel gyara mata kwanciya yayi ' sannan yaja mata lullub'i ya koma gefe
yana kallon ta.

*DEDICATED TO MY FAN'S*
馃憚馃憚馃憚
[5/23, 2:58 PM] Jameesha: .....馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮
馃尮馃尮 *BABBAN...GIDA*馃尮馃尮
馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

*_Pure Moment Of Life writers_*

漏 ```Written```聽聽 聽 聽
By
*_Seemaluv_*馃憚

www.Seemaluv.wapka.me

*#IG:* *_@Bae_Seema 鉂*

_@...Am sorry fan's for not posting on time!, Wannan page d'in naku ne ' My besty
(Jameesha) and (Rufaida Yusuf) thank you for caring, Loving and Support... 鈾モ櫏鈾
*

*91-92*

Fadwa zuwa tayi ta zauna kusa da Ige ' tare da cewa.


"Ige baki fito kinyi sallama da Ilham ba!".
"Zamuje gidanta ai ' nan da kwana biyu".
Fadwa ajiyar zuciya tayi ' ta jinginar da kanta jikin kujera, Cen kuma ta tashi
tare da yunk'ura wa da gudu ta nufi kitchen, Hakan yasa Ige tashi tabita cikin
sauri.
Ige iske Fadwa tayi tanata amai.
"Subhanallah! Zazzab'in ne kuma ya dawo?".
Ige k'arasawa tayi har inda Fadwa take ' ta d'iba ruwa a hannun ta ta shafa mata
akai, Sannan ta rik'o hannun ta suka dawo parlor.
"Sannu kinji?".
Cewar Ige.
"Ige ina Khaleel yaje?".
"Ya tafi wajen aiki ' ai bazai dad'e ba".
Kai kawai ta d'aga mata alaman to, Sannan Fadwa ta koma ta kwanta saman kujera.
Umma ce ta shigo sashen rik'e da waya a hannun ta, Ta zauna kusa da Fadwa.
"Fadwa yaya jikin naki?".
"Da sauk'i Umma".
Sannan Umma ta maida kallon ta akan Ige.
"Ige amare fa sun iso Nigeria ' don yanzu suka kirani suka sanar dani cewa suna
airport, Khaleel nake k'ok'arin kira yanzu ana cemin line busy".
"To amma kin fad'awa Farooku?".
"Eh na sanar dashi ' domin ya zauna cikin shiri, Kinga kuma dole sai Khaleel ya
dawo ' ko kuma kawai in tura musu driver.
"Eh Umma kawai ki tura driver d'in tunda kinga Yaya Khaleel yana office, A tura
driver kawai ' nasan dai bazasu rasa kayayyaki ba! So ya kawo su sai ya koma ya
d'auko masu kayan".
Cewar Fadwa.
A zuciyarta tace.
"Bazasu mayarmun da miji boyi boyi ba!".
Maganar da Umma tayi ne yasa tayi saurin dawo wa cikin hankalin ta.
"Eh tabbas abinda zanyi kenan! Bari in tashi ' intura masu driver kawai".
Umma na gama fad'in haka ta tashi ta nufi wajen driver ' ta sanar dashi, Sannan
ta fad'a mashi da motar daya dace ya tafi da ita.
Haka driver yaja mota ya fice zuwa airport.
B'angaren Ilham kuwa ' tunda aka kaita d'akin ta 'yan uwan mijinta wato Al'ameen
keta kai da dawo wa cikin gidan, K'annan shi kuwa sai zuwa sukeyi suna gabatar da
kansu ' Haka gidan ta ya cika tam da 'yan uwa!.
Ilham taji dad'in yadda suka karramata matuk'a.

*AROUND 3:00PM*

Mutane suka fara watse wa ' a gidan Ilham, Ya rage daga ita sai k'awayen ta sai
kuwa 'yar autar su Al'ameen mai suna Suhaila.
Suhaila mace ce wacce ta cika mace ' daka ganta kasan yarinya ce k'arama wacce
bata wuce tsarar Ilham ba a shekaru, Wannan shine dalilin da yasa jinin Ilham da
Suhaila ya had'u.
"Auntyn mu gaskiya ' naji dad'in kasance warki matar Yaya".
Ilham murmushi kawai tayi mata ' sannan Suhaila taci gaba da bata labarin yanayin
yadda gidan su yake.
Umma na sashen Fadwa ' suna zaman jiran amare ne sukaji tsayawar mota a cikin
garege, Hakan yasa Fadwa tashi ta lek'a window ganin wasu jajayen fata tayi suna
fitowa daga motar, Sai ita Safeena wacce take a gaban mota taci ado ' hakan yasa
Fadwa juyowa ta kalli su Umma.
"Umma sune suka iso".
Nan take Ige tayi zambur ta mik'e tsaye tare da cewa.
"To ai sai muje mu tare su ko?".
Hakan yasa Fadwa tayi sauri ta fita ' su Umma kuwa na biye a bayan ta.
"Sannun ku da zuwa!".
Cewar Fadwa cike da fara'a a fuskar ta.
Saida suka gama fitowa ne Safeena ta fito daga motar tayi hugging Fadwa '
tukunna suka rik'e hannu taja ta zuwa part d'in ta, Har k'awayen ta sun biyita Umma
ta dakatar dasu tare da mik'a musu key d'in part d'in Safeena.
"Ga key d'in gidan ta nan! Kamata yayi ku shiga kuga yanayin gidan da kuma
tsarin da zakuyi mashi".
Ansar key d'in sukayi, Sannan Umma tayi musu nuni da sashen suka nufi wajen.
Kasan cewar Safeena tare da mahaifiyar ta sukazo ' hakan yasa Umma da Ige suka
ja mahaifiyar Safeena zuwa sashen su, Domin ta zauna ta huta ta kuma ci abinci.
Bayan sun zauna ne Umma suka fara hira da Mahaifiyar Safeena ' suna cikin hakane
Ige ta tashi ta kawo mata abinci sannan ta kaiwa k'awayen amarya nasu abincin,
Bayan hakan ne Ige ta kaiwa Safeena nata abincin ta.
Sannan ta koma sashen Umma sukaci gaba da fira.
Yaya Farook ne ya fito daga d'akin shi ' yazo suka gaisa da Mahaifiyar Safeena.
Tayi musu 'yar tak'aicecciyar nasiha, Yaya Farook godiya yayi mata tare da nuna
farin cikin shi a fili ' sannan ya tashi ya fita zuwa part d'in shi a zaton shi
Safeena tana ciki.
Yana shiga ya iske k'awayen ta a ciki sai jera kayayyaki sukeyi ' kasan cewar
driver ya d'auko masu kayan dankin dake airport, Yaya Farook waje ya samu ya zauna
saman kujera ta gaishe su da hanya tukunna yace.
"Ina fatan dai kunci kun k'oshi!".
D'aya daga cikin sune ta bud'e baki tace.
"Yes mun k'oshi! Amma muna fatan dai Ango ba Amarya ya biyo ba!!".
Yaya Farook dariya yayi ' har sai da hak'oran shi biyu suka bayyana.
"To inba ita na biyo ba ' wazan biyo?".
"Taw Amaryar ka ' bata iso ba tukunna!".
Yaya Farook tashi yayi ' ya fice cikin fara'a, Ya zarce wajen driver ya mik'a
mashi 3,000.
"Kaza zaka siyo ' please yanzu...".
To kawai driver yace sannan ya shige mota yaja ya wuce ' inda aka aike shi.
Har Yaya Farook yasa kai zai koma wajen Umma ' yaji muryar Safeena a part Fadwa,
Da alama fira sukeyi.
Yaya Farook harya nufi wajen sai kuma ya juya ' ya wuce sashen su.
Driver bai wani b'ata lokaci ba ya dawo musu da sak'on da Yaya Farook ya bayar,
kai tsaye ya kaima su ' don yasan cewa nasu ne.

*AROUND 4:00PM*
Mahaifiyar Safeena da k'awayen ta suka fara shirye shiryen komawa gida, Umma da
Ige da kuma Mahaifiyar Safeena harabar garege suka fito ' nan ma k'awayen suka fito
gaba d'ayan su.
Fadwa da Safeena waje suma suka fito ' don suyiwa junan su sallama.
Haka aka shiga yiwa Safeena nasiha ' da jan kunne, Bayan ta gama ne ta shige
mota tukunna k'awayen suma suka shige, tare da d'agowa Safeena hannu.
Nan take idanun ta suka ciko da hawaye ' amma sai dai basu kaiga zubowa ba.
Tanaji tana gani ' Mahaifiyar ta da k'awayen driver yaja su suka tafi zuwa
airport.
"Fadwa ki kaita d'akin ta domin ta huta, Kuma ki lallashe ta".
Cewar Umma.
Kai kawai Fadwa ta d'aga sannan taja hannun Safeena donta kaita d'akinta.
Bayan sun wuce ne ' Ige tace.
"Kai nidai kam zanje in huta ' don wallahi agajiye nake".
"ai akwai gajiya kam ' ni sallah zanyi tukunna sai ind'an mik'e".
Cewar Umma.
Haka suka shiga daga ciki ' sukayi sallah sannan suka kwanta suna sauke gajiya.
Fadwa saida ta tabbatar Safeena ta manta da komai ' tukunna ta baro sashen nata,
Ta dawo sashen ta ' haka yayi daidai da fitowar Yaya Farook daga sashen Umma.
Kallon shi kawai Fadwa tayi ' sannan ta juya ta nufi nata sashen, Shi kuma ya
shige ciki.
Fadwa waje ta samu ta zauna saman kujera ' ta d'auki 'yar k'aramar wayar ta tayi
dialling number d'in Yaya Khaleel.
Saida ta kirashi wajen sau biyu ' tukunna ya d'auka.
"Babyna? Kiyi hak'uri ina driving ne, Gani nan dawo wa gidan yanzu".
Tanajin haka ta kashe wayar ' ba tare da tace uffan ba.

*4:30pm*

Yaya Khaleel ya dawo gida ' sai da yayi packing motar shi a packing space, Tukunna
ya fito.
B'angaran shi ya nufa kai tsaye cikin sauri, Shiga yayi cike da sallama d'auke a
bakin shi.
Ganin Fadwa yayi a zaune ' fuskar ta na kallon TV babu walwala sam, Hakan yasa
shi k'arasawa harabar parlon ya d'auki remote ya kashe TV, Sannan ya koma kusa da
ita ya zauna.
"Babyna sallama fa nakeyi!".
Fadwa maida kallon ta tayi akan shi ' idanu suka cicciko da k'walla.
"For God sake ' ni banda buk'atar kulawar ka ne? Kokuwa ban cancenta ka kula
dani bane? At this condition nafi buk'atar kulawar ka fiye da komai".
"Am so sorry Babyna ' wallahi naje na iske ayyuka ne da yawa! Kuma after that
saida na tsaya nati attending wani meeting, Kiyi hak'uri Babyna aikin san bantab'a
yi maka haka ba ko?".
Fadwa had'iye hawayen ta tayi ' tare da cewa.
"Anyway! Are you hungry?".
"No Babyna ' saida na tsaya restaurant naci abinci, Don naji yunwa sosai ' yaya
jikin naki?".
"Sweetheart jikina yayi sauk'i sai da aman ne haryanzu inayin shi".
"Sorry Babyna ' zai daina insha Allah, Let me hug you ' so that i can feel my
baby's move".
Dariya Fadwa tayi ' gami da cewa.
"How?".
Ko kafin ta gama rufe baki ' ya rungume ta sosai, ya zamo dakyar take sakin
numfashi.
"Is ok ' Sweetheart is ok! Zaka sani amai".
Da sauri ya sake ta ' sannan yayi pecking d'in ta.
"Bari inje in watsa ruwa".
"Wait! Amarya fa ta iso ' tun d'azu".
Zaro ido yayi cike da mamaki.
"Aunty Safeena! Wow Alhamdulillah, Nasan yanzu Yaya nacen baki har kunne".
"Eh mana".
"To bari inyi wanka ' sai inje mu gaisa".
Abinda ya fad'a kenan ya tashi ya shige d'aki, Fadwa na binshi da kallo d'auke da
smilling.
Yaya Farook tunda ya shiga ' yake zaune a parlor, waishi a dole kunya! Da kyar
ya tashi yayi ta maza ya shiga d'akin da Safeena take.
A zaune ya iske ta ' tasha lullub'i ga hannun ta yasha lalle, Safeena tayi kyau
sosai.
Sallama yayi mata ' ta amsa sannan ya k'arasa ciki ya zauna daf da ita.
"Habibty!...".
Safeena dad'i taji sosai har cikin ranta ta yadda ya kirata da wannan sunan.
Yaya Farook hannu yasa ya sauke mayafin data rufe fuskar ta dashi ' ya karkato
da fuskarta suna kallon juna.
Nan ya sauke wata gajiyayyar ajiyar zuciya, Gami da yiwa Allah godiya.
"Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah ' Allah na gode maka daka bani
Safeena a matsayin matar aure na".
Safeena kuwa kasa had'a ido tayi dashi, Sai dai ta maida kallon ta zuwa k'asa
don kunya.
"Ki d'ago kanki ki kalle ni".
Ya fad'a yana murmushi.
Haka Safeena ta kalleshi ido cikin ido, Nan da nan taji wani yarr a jikin ta '
hakan yasa tayi saurin kauda kanta.

.....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

*_Pure Moment Of Life writers_*

© ```Written```
By
*_Seemaluv_*👄

www.Seemaluv.wapka.me

*93-94*

Yaya Farook sake tallabo fuskarta yayi ' da niyyar kissing, Taji ana kiran sallah
' hakan yasa Safeena yin saurin mik'ewa tsaye tare da cewa.
"My dear! Lokacin sallah yayi ' please lets pray".
Cije leb'e yayi, Sannan ya tashi ya shige toilet yayi alwala ' tukunna ya fito.
"Na wuce masallaci ' ki shirya kafin indawo".
Abunda yace kenan yasa kai ya fice ' Yaya Farook yana fita suka had'e da Yaya
Khaleel shima zai wuce masallacin.
Haka suka sa kai ' suka tafi masallaci.
Had'a sallah akayi ' sakamakon hadarin da aka had'a.
Bayan an idar ne ' kowa ya tashi ya koma gida, Yaya Farook da Yaya Khaleel '
bayan sun shigo gida ne Yaya Khaleel yace.
"Yaya! Sai dai gobe da safe zamu gaisa da Aunty".
Ok kawai Yaya Farook yace ' sannan ko wannen su ya shige sashen shi.
B'angaren Ilham kuwa ' bayan tayi sallah ne ita da k'awayen ta, Sun zauna saman
gado suna hira ' sukaji shigowar Ango da abokan shi.
Hakan yasa Ilham tayi wuf taja mayafin ta ' ta rufe jikinta tare da fuskarta
gaba d'aya.
K'awayen tashi sukayi ' sukayi saurin fitowa daga d'akin tare da tare bakin
k'ofar.
"Sai anbiya kud'in siyan baki".
Cewar d'aya daga cikin k'awayen.
Nan Ango cike da fara'a a fuskar shi ' ya zaro 10,000 ya mik'a masu, Gaba d'ayan
su dariya sukayi sannan suka ce.
"To ga Amarya cen ' don Allah a rik'eta amana da aminci, A kula mana da ita".
Nan suka kama hanyar wuce wa ' abokan Ango sukabi bayansu, Domin su maida
kowacce gida.
Haka Al'ameen ya k'arasa ciki cike da sallama, Ilham ta amsa mashi cikin sanyin
murya.
Al'ameen k'arasawa yayi inda take ya zauna kusa da ita yana kallon ta cikin
lullub'i.
Nan ya d'aga hannun shi sama ya godewa Allah ' cike da nuna farin cikin shi,
Sannan ya maida kallon shi akanta.
Hannu yasa ya janye mayafin nata zuwa k'asa, Nan Ilham ta d'ago fararen idanun
ta ta kalleshi ' gami da sakar mashi murmushi.
"My beauty!"
"Na'am".
"Mu tashi muyi wanka ko?".
Shuru tayi ta kyaleshi ' ganin bata da niyyar tashine, Ya tashi ya wuce d'akin shi
donyin wanka.
Nan ne Ilham ta sami k'warin gwiwar tashi ta cire kayan jikin ta ta d'auko towel
ta sanya, Sannan ta shiga bathroom.
Ilham wanka tayi tare dayo alwala ' tana fitowa ta nufa gaban madubi ta fesa
turare tukunna ta bud'e wardrope ta d'auki rigar bacci mai d'an kauri armless
iyakarta gwiwa ta sanya, Sannan ta d'auki zani ta d'auri.
Ilham dadduma ta shimfid'a tayi sallah tukunna ta kwance zanin ta koma saman
gado tayi kwanciyar ta.

*AROUND 8:00PM*

Al'ameen ya shigo cikin d'akin ya k'arasa har inda take kwance ya zauna ba tare da
ta saniba, Domin kuwa Ilham har ta fara bacci.
Tab'ata yayi a hankali ' jin haka yasa tayi firgigit ta farka a tsorace.
"My Beauty tashi muje d'aki ko? Naga harkin fara bacci".
Babu musu Ilham ta sauko da saman gadon ' ta bishi suka nufi d'akin shi, Nuni
yayi mata da gado taje ta kwanta tare da jan lullub'i sannan Al'ameen ya kulle
d'akin da key shima yaje ya haye gadon.
Al'ameen cikin lullub'in ya shiga tare da runtse idon shi nad'an lokaci, Sannan
yajawo ta jikin shi.
Ilham jin haka yasa ta bud'e idon ta a hankali tare da had'iye miyau.
"My beauty ' i really need you! Am feeling you".
Ilham shuru kawai tayi gabanta na dukan uku uku, A hankali taji yana k'ok'arin
d'age mata rigarda ke jikin ta ' cikin wani irin shauk'i Ilham tace.
"My prince! Please ka barni ' bazan iya ba".
Al'ameen baibi takan taba ' ya shiga bata hot kisses a wuyar ta, Ganin hakan
bazai gamsar dashi bane yasa shi juyo da ita gami da k'ank'ame ta ajikin shi.
"Sorry Beauty ' bazan iya hak'uri ba".
Nan Ilham ta shiga yimashi magiya cikin kuka, Amma ina!!! Sam Al'ameen bai san
tanayi ba.
Sai da ya tabbatar ya samu abunda yakeso ne ' tukunna ya kyaleta tare da
mirginawa gefe.
"Kiyi hak'uri my Beauty".
Abinda Al'ameen ya dunga furtawa kenan har bacci yayi awon gaba dasu gaba d'aya.
B'angaren Yaya Farook kuwa tunda ya dawo daga masallaci ' ya toge a parlor yana
kallon shi, Safeena har sai da tayi wanka tayi sallah ta zauna ' tana jiran
shigowar shi.
Ganin baida alamar shigowa ne ' yasa ta tashi cikin sexy sleeping gown armless
mai sharashara, Ta fito zuwa parlor.
Safeena ganin Yaya Farook tayi a zaune abunshi ' yana kallon news.
"My dear...".
Ta kira shi cikin sexy voice ' tabbas Safeena wayayyace don kuwa tasan duk wani
salon da zatabi domin taja hankalin namiji, Yaya Farook juyowa yayi ya kalleta tun
daga sama har k'asa.
"Wow...".
Ya furta ba tare da yasani ba ' jin haka yasa Safeena takowa tazo har inda yake,
Ta zauna kusa dashi kai zakace kujerar ba wadatacciya bace ' saboda irin matse
shinda tayi.
"Haaabibtyy...?".
Ya kirata cikin sark'ewar murya.
"Na'am dear".
"Kiyi hak'uri ban shigo ba tund'azu , News d'in nan ne ya tsaida ni".
"My dear ' karka damu i can handle it".
Ta fad'a tare da d'aukar remote ta kashe TV d'in, Sannan ta juyo ta kalleshi.
"My dear lokacin bacci yayi".
Haka Safeena ta kama mashi hannu ' suka shige d'aki.
Nan Yaya Farook ya cire manyan kayan shi ' ya rage daga shi sai boxer, Safeena na
saman gado tana kallon shi.
Saida ya gama kintsawar shi ' tukunna ya haye saman gadon..
Nan Yaya Farook da Safeena suka raya sunna ' kamar yadda addinin musulunci yace.

*** **** *** *** *** *** *** ***

Haka rayuwa ta cigaba da wakana ' Yaya Farook da Safeena suna zaune cikin aminci
da k'aunar junan su, Yaya Khaleel kuwa yana tare da babyn shi Fadwa yana rainon
ciki, Ilham da Al'ameen sun kasance cikin zaman lumana da k'aunar junan su cike da
kulawa.

*Summarize!!!..😚.*
*2YEARS LATER...*

Fadwa ta haihu cikin k'oshin lafiya ta sami baby girl kyakkyawa ' wacce suka sa
mata suna *Iman* tare da taimakon Yaya Khaleel wajen bata kulawa daidai gwargwado,
Ilham da Safeena kuwa! Ko wanensu yana d'auke da jinjirin cikin da bai wuce wata
uku ba.

*_ALHAMDULILLAH!!!🙏_*

*A NAN NA KAWO K'ARSHEN LITTAFI NA ' MAI SUNA BABBAN GIDA, INA MAI MIK'A GIDIYA
TA GA FAN'S D'INA ABIN ALFAHIRA NA WANDA DA BADON KUBA ' DA BAZAN KAI WANNAN
MATSAYIN DA NAKE BA A YANZU!!! KUMA INA MAI BA FAN'S D'INA HAK'URI AKAN YANKE
LABARIN DA NAYI CIKIN WANNAN LOKACI, NA YANKE LABARIN NE BADON KOMAI BA ' SAI DON
WATAN RAMADAN D'IN DA ZAMU SHIGA, WANNAN SHINE DALILIN DA YASA NAYI KOMAI A
GURGUJE, NA GODE!!!*

*_BABBAN GODIYA TA ' NA MIK'AWA PURE MOMENT OF LIFE WRITERS MEMBERS, NA GODE SOSAI
DA TAIMAKON KU ' WAJEN GANIN LITTAFIN BABBAN GIDA YA HASKAKA A KO INA!!!_*

*INA TARE DAKU AKO DA YAUSHE ' SEEMALUV NOVELS GROUP123, Seemaluv taku ce ' nima
kuma naku ne😘...*
(*_KARKU MANTA BABBAN GIDA LITTAFI NE ' MAI K'UNCE DA SOYAYYA A CIKIN SHI, GAMI DA
GIRMAMA IYAYE ' DA KUMA GIRMAMA NA GABA DAKAI_*)

*ku saurari Seemaluv a littafin naga ba ' mai suna B'OYAYYEN AL'AMARI...*

*DEDICATED TO MY FAN'S*
👄👄👄

You might also like